DAMA TA BIYU BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK Page 1&2 Bismillahirramanirrahim Wasu k'wawawan motocine masu rai da lpy ke tafiya akan shimfidedden kwaltan dake unguwar London road dake garin minna, Duk Wanda yasan unguwan London road. Yasan unguwace ta manyan mutane .musamman manyan yan kasuwa, Kofar wani katafaren gida motocin nan sukayi parking gidane mai kyau. kuma ga dukkan alamu sabon gini ne ba a kai ga tarewa cikin saba, Ahankali marafen motocin suka fara budewa. Mataye ne suka fara fitowa daga cikin motocin nan. Yawancin matayen sanye suke da ankon wani hadadden atamfa yellow and brown colour. wasunsu kuma sanye da shiga ta alfarma, Saida suka gama fitowa kaf d'insu na lura da wata mota guda daya daga cikin motocin nan wadda ba a bude ba balle a kai ga fitowa daga cikinta, duka matayen nan tsayawa sukayi suna kallon motar nan. da alama jira sukeyi na cikin motar su fito , Marfin motar ne ya bude. A hankali wata dattijuwar mata da akalla zatakai shekara hamsin da haihuwa ta fito a motar cikin shiga ta alfarma. Sai kuma wata ta bude gaban motar ta fito ita muka sanye take da ankon dake jikinyawan cin matayen, Hannu yar dattijuwar data fara fitowa a motar ta miqa ta kamo hannu waccce ta rage a cikin motar.wacce nake tsammanin duka matayen nan ita suke zaman jiran fitowarta , A hankali ta sako fararen qafafunta waje Wanda yasha wani irin design na black and red henna. dai dai lokacin wasu daga cikin matayen nan suka saki bud'a ji kake "ayyiririririyyyyyy" wuri ya haustine da bud'a gwanin birgewa, Sai alokaci na fahimci meke faruwa a wurin wato dai amaryace aka kawo sabon gidan nan A hankali na qare ware idanuna akan amaryan sanye take da wani ubansun lace maroon colour mai duhu Wanda yayi masifar yima farar fatarta kyau an lilla'be mata kanta da wani babban mayafi peach colour kafarta da yasha design sanye da takalmi mai tsini shima peach dukda banga fuskar ta ba nasan wannan amaryar masha zatayi kyau ba qarya, Matan nan biyu da suka fito mota daya da itane suka sanya ta a tsakiya suna nufar gidan sannan sauran matan suka rufa musu baya. Dai dai get suka tsaya wannan dattijuwar matar tana karanta mata wani addua tana amsawa cikin sanyin muryarta daya shaqe tsabar kukan da tasha, Da bismilllah ta sanya qafarta cikin gidan . wasu matane suka taso cike da fara,a suka tarbesu har cikin babban plat din dake farkon gidan Masha Allah ginin bene ne babba Wanda ya gama tsaruwa kamar a Turai an qawatashi da kayan more Rayuwa na alfarma , saida suka sadata da bed room dinta dake upstair sannan suka firfito wasu suka zauna a falonta na sama wasu kuma suka sauqo kasa.. Nan aka gabatar musu da abincin tarbar amarya mai rai da lafiya kowa yaci abinda ranshi keso ya qoshi . nan dai wasu suka zazzaga gidan .. Gidan kam ya hadu sai sambarka Amarya kam tunda suka sadata da bed room dinta suka zaunar da ita a gefen bed dinta kanta me duqe lilli'be da mayafinta . kuka takeyi sosai kamar ranta zai fits sai shesheqa takeyi kamar zata shiqe. Ita kadai tasan abinda me damun zuciyarta game da wannan qadddararren auren ..dasun San halin da take ciki game da wannan auren da dukkansu sun tayata kukan baqin ciki, Dama ace zata iya bijirema Alhj baba akan wannan auren hadin daya hada data bijire mai, Saidai kuma kash ko giyar wake tasha bazata taba iya bijire masa ba , saidai mijin da aka aura matan ya kasheta kamar yadda yay ikirarin cewa. tayarda ya kashetan akan ta zama butulu gurin bijirna umarnin alhj baba.. Tunaninta ne ya katse jin motsin mutane suna nufowa dakin da take domin yi mata sallama . shigowa suka dingayi suna mata sallama da fatan alkhairi wasunsu na mata addua da tayata farin ciki yayinda wasu zuciyarsu kamar tayi bindiga ta fashe don tsananin baqin ciki . Wani kukane ya kufce mata ganin da gaske tafiya za suyi su barta a cikin wannan baqin gidan da ta tabbata shine ajalinta, Rarrashinta suka shiga yi da bata baki yayi da masu Jin haushinta musamman yan matan dake son auren mijin nata dakuma wadanda kema yayansu ko kannensu kwadayin auren wtakeyiba ya'kyawan santalelen matashin saurayin mai ji da kudi ga kyau ga 'kuruciya, ke mata kallon wawiya wacce batasan abinda takeyiba Shere and comment Fisabilillah🙏🏻 💖DAMA TA BIYU💖 BY {AYSHA NALADO} FREE BOOK Page 3 & 4 Wata mataCikin yan kawo amarya ta karasa kusa da amaryan ta tsuguna a gabanta ta mi'ka hannuta ta daura akan cinyoyinta a hankali cikin kwantar da murya tace "haba ASMA'U kukan ya isa haka mana tun jiya kike abu daya sai kace wacce aka kashewa iyaye ya kamata kibar kukan nan haka kodan lafiyarki" Wata kyakkyawan tsohuwa ta karbe zancen da cewa " ke da allah ya dubi maraicinki ya baki miji na bugawa a jarida. mijin da duk wacce ta sameshi ta gama more miji. kinsan yan mata nawa ne ke neman wannan damar amma allah bai basu ba ke ya baki, ba kuka ya kamata kiyi ba godema Allah ya kamata kiyi daya mallaka miki Muhammad aslam a matsayin mijin auren ki. Koda yake bazan ma ce kiyi shiru ba. yi tayi kinga idan ASLAM ya zo ya sameki da ido jajur dole ya lallabo ya dawo wurina tinda dama nice uwargida ran gida nice ta karfen " ta qarashe maganar cikin d'an zaulaya. Matar datayi magana dazu ne ta sake cewa tana kallon mutane dakin"jama a ya kamata muyi haramar tafiya magariba Na gabatowa motocin da suka kawomu suna waje suna jiran mu Allah ya basu zaman lapiya" da amin wasu suka amsa a fili wasu a zuciya yayinda wasu ke fadin ba amin ba a zuciyarsu. Wucewa duka yan kawo amaryan sukayi aka barta daga ita sai kawayenta kuma yan uwanta amira , zahra , da batool sai kuma kanwarta Khadijah. ********************* Misalin karfe shidda da Rabi Na yammacin ranar asabar zaune yake a bakin gadon dakin hotel da ya kama yau kimanin kwana uku kenan. sanye yake da singlet fari qal da wando 3quater, matashin sauryine Wanda a kalla zaikai shekara 30 da haihuwa. Kallo daya zaka masa kasan dolenema yan mata su haukace akan shi domin ya gama haduwa ta ko ina. fatar jikinshi kawai idan ka kalla kasan Hutu da jin dadin sun gama zama a jikin shi komai Na jikin shi me kyau ne tun daga sumar kanshi mai dauke da baqin saisayayyen gashi mai taushin gaske, fusskarshi mai dauke da kyakkyawan bakin saje a zagaye dashi. ga kuma wani Dan madaidaicin gemu daya tsayar irin na samari yan kwalisa masu ji da gayu, zuwa yanayin tsarin halilltar jikinsa irin Na cikakkun maza masu kyawun sura, Muhammad aslam kenan ,aslam mutum ne Mara, son hayaniya shiyasa da wuya ka ganshi yana magana indai ba mai mahimmanci bane, akoda yaushe fuskarshi a kame take, bai cika kyalkyata dariyaba saidai yayi murmushi .shima ba kowani lokaciba hakan yasa yan matan dake Neman kawo mishi wargi suke matugar shakkarsa. Yanada riqo da addini baya wasa da ibadah yana matuqar girmama iyayen shi hakan kuma ya samo asaline ganin yadda iyayen nashi ke girmama nasu iyayen suma, Abu daya ke bani mamaki ga rayuwarshi shine rashin son raini kwata kwata aslam baya son raini duk abinda zaiyi a rainashi ko cikin abokaine bayaso balle kuma a gurin qannen shi, hakan yasa qannwnshi ke kwasan gwale-gwale a hannunshi baya wasa dash ko kadan tsakanin shi dasu girmamawane Shere And Comment Fisabillillah🙏🏻💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 5 Wayarsace dake gefensa ta fara ringing ko bai kalla ba yasan bazai wuce amir ba, miqa hannu yayi ya dauki wayar ya duba, kamar yadda yayi tsammani kuwa amir d'inne, Kamar ko wani lokaci mayar da wayar yayi ya ajiye baiyi receiving ba, jota da biron da ke ajiye gefensa ya dauka, sai da ya tsaya yayi Dan Jim kafin daga bisani yayi rubutun da bai wuce layi uku ba ya falle page din ya linke ya ajiye , Kallon agogo dake manne a dakin hotel din yayi ganin 6:40pm yasa ya mike ya shiga toilet domin ya dauro alwala, Yana fitowa jallabiya ya dauka ya daura akan 'kananan kayan dake jikinsa. Paper da yayi rubutu da key ya dauka ya saka a aljihu ya fito d'akin d'auke da wayoyin shi a hannu , Kulle kofar dakin yayi ya fito a cikin hotel din ya nufi masallacin kusa da hotel din, Daf da zai shiga masallacin wayarshi ta fara qarar alamar saqo ya shigo, Dan dakatawa yayi ya duba message din ganin saqon da aka turo ya saka shi dialing number da aka turo message din, picking akayi cike da girmamawa Wanda ya kira din ke fading "yallabai gani nan Na karaso hotel din " A daqile yace "kasame ni a masallaci" Ya kashe wayar ya shige cikin masallacin, saida aka idar da sallan magriba suka samu ganin juna, bayan sun gaisa hannu yasa a aljihu ya Ciro paper dayayi Dan note dazu ya miqa mishi tare da fadin. "ka kai ma waccen yarinyar" Amsa yayi da hannu biyu amma ga dukkan alamu bai game wacce yarinya yake nufi ba , Dan sada kansa qasa kadan yayi alamar girmamawa sannan yace "yallabai wacce yarinya kake nufi" Kallon shi aslam yayi ya dauke kai yace" yarinyar da suka kai gida Na dazu" Murmushi ne ya kufce a fuskar bello yana Dan Sosa qeya yace "yallabai amarya kake nufi" Wani mugun kallo ya watsawa bello dayasa lokaci daya murmushin fuskarshi gimtsewa, Juyawa yayi zai wuce aiken da aka mai yana cewa "a huta lpy yallabai" Saida yayi taku kamar biyar aslam ya kira sunan sa "bello" juyowa bello yayi ya dawo yadan risina yace "yallabai gani". Saida ya bushi iska yace "kada kowa yasan ina nan ciki harda daddy da amir, babu wani mahalukin dayasan inda nake sai kai kad'ai don haka take care" yana gama fadin haka ya duya ya shige cikin hotel din abinshi.. ********************* Bayan yan kai amarya sun wuce amira da zahra ne suka sakata a tsakiya akan tayi shiru ta daina kuka haka Allah ya qaddaro mata amma ina ko sauraronsu batayi sai kukanta takeyi bil hakki . Khadijah CE itama ta matso gabanta ta tsuguna miqa hannu ta kama hannayenta ta riqe cikin muryan lallashi tace " yaya asmah ya kamata kibar kukan nan haka kada wani ciwo ya kamaki, idan fa wani Abu ya sameki Wanda kike kukan nan dalilin shi fa bashi da asara, muda muke sonki mukeda asara,mune zamu shiga wani hali idan wani Abu ya sameki pls yaya asmah ya isa haka"ta karashe maganar tana langwabar da kai idanunta cike da hawaye, Dago kai tayi ta kallesu baba daya sai taga sun bata tausayi, share hawayen fuskarta tayi tare da qaqalo wani bushasshen murmushin da iyakacinsa fatar baki tayi musu,"Na gode yan uwana yanzu Ku tashi muyi sallah magriba yayi" ta fada tana zare hannunta cikin Na Khadijah, suma murmushin sukayi mata Khadijah Na fadin "yaya kokefa, don Allah karki qarayin kuka kinji " gyada mata kai kawai tayi, Share And Comment Fisabilillah🙏 Date: Sep 27, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 6 A toilet din dake dakin gaba d'ayansu sukayi alwala banda batool dake kwance kan gado tana fashin sallah, hijjab da pray mat suka dauka a cikin sif kasance war an mata jerenta komai akwai a gidan hatta kayan sawanta suna cikin sit, zahra CE ta shiga wani app a wayarta ya nuna musu alqibla suka fara sallah, Batool dake kwance taji kamar ana kwala sallama a kofar parlour saurarawa tayi still taji an sake yin sallamar, tashi tayi ta sauko parlour tana amsa sallamar, Wani mutum ta gani me kimanin shekara arba'in , gaisawa sukayi cikin mutunta juna. Ya Dora da cewa"hajiya dama wani ne yazo yana waje wai mai gidan ne ya bashi saqo ya kawowa madam" Sai lokacin batool ta fahimci waye wannan mutumin wato mai gadin ne, "Kace yace yaya aslam ne ya aiko shi gurin asmah?"batool ta tambayeshi, "eh haka yace hajiya, yacema daga can babban gida yake" "OK muje na ganshi" batool ta fada tana nufar hanyar waje, bin bayanta mai gadi yayi suka fito compound din gidan, Karasowa bello yayi ganin mai gadi da batool sun fito, batool tace"mallam bello dama kaine" "Eh batool nine ya kike ya gujiba gujiban biki" Batool tace "lpy qlau ya naka gujiba gujiban don nasan kaima kasha gujiba gujiban"Dan dariya yayi tare da cewa"wlh kuwa balool kaman kin Sani, Allah dai ya basu zaman lpy da zuri'a dayyibah " "Amin thumma amin "batool ta amsa, saka hannu bello yayi a aljihu ya d'auko farin takardar da aslam ya bashi ya miqawa batool"gashi kiba madam inji yallabai yace a kawo mata"amsa batool tayi tana jujjuya paper sannan tace"to shikenan mallam bello insha Allah yanzu inna shiga zan bata" "Yawwa batool Na gode sai anjima"bello ya fad'a tare da juyawa ya wuce ,itama batool juyawa tayi ta shige parlon a ranta tana mamakin meye a cikin takar Dan nan da yaya aslam ya aiko dashi da bazai iya kira a waya ba Koda ta dawo dakin kusan dukansu sun idar da sallah saidai suna zazzaune a gurin suna azkar d'insu, komawa tayi bakin gadon ta zauna tana jiran su idar ta miqa ma asmah saqon, zamanta kamar da minti biyar zahra ta miqe tana linke hijab,kallon batool tayi tace"wlh batool kedai anyi mara hankali"tana balla mata harara , itama batool hararan ta balla mata tare da cewa mai Na miki kuma uwar kankanba , tsaki zahra taja tare da cewa "kinzo kinhau gadon amarya ko kunya babu bayan kinsan sarai mummy ta hanamu hawa gadon mutane, kumama don tsabar rashin kunya gadon yaya aslam din kika hau, to wlh saina gayawa mummy" , Harara batool ta balla mata tace" to gulmammiya ba mummy zaki gayawa ba inkinga dama kije ki gayawa yaya aslam din da kanshi ya kasheni ko kuma kije ki gayawa alhaji baba qarewa" Amira ce da itama idarwanta kenan tana like hijjab tayi gyaran murya uhummmmm duk juyowa sukayi suna kallon ta, itama su take kallo tace" kudai kunji kunya wlh ko ina akaje sai kun sai kun raba hali sai kace wasu qananan yara" Khadija ce ta kyalkyale da dariya tana cewa " wlh twins din mummy kuna ban dariya" kukan da sukaji asmah ta fashe da shine ya maida hankalinsu kanta, zaune take a inda ta yi sallah ta daga hannu sama tana kai kukanta gurin mahaliccinta, sosai take addu'a akan aurenta da Neman mafita mafi alkhairi, dukkan su da amin suke amsawa har ta gama ta shafa suma suka shafa tare da ita, batool ce ta matsa kusa da ita tare da miqa mata paper da bello ya kawo tana fadin "amaryan yayanmu wai gashi inji angon naki ya aiko mallam bello direba dazu kina sallah wai ya kawowa shibarsa" ta fada cikin sigar zaulaya, Dago kanta tayi ta Dan qurawa pepan dake hannnun batool ido kafin ta mika hannu ta karba, bud'e pepan tayi ta qurawa rubutun da baifi layi uku ba ido, Karantawa takeyi tana qara maimaita karanta abinda ke cikin pepan a zuciyarta. ganin dai tabbas abinda ta gani arubuce a cikin paper tabbas haka yake ba gizo idanunta ke mata ba,ya sata sakin wani qayataccen murmushin Wanda yasa yan biyu mummy da amira da khadija kallon kallo a tsakanin su, Zahra ce datafi kusa da ita ta miqa hannu ta karbi papern a hannunta warwarewa tayi ta fara karan tawa da qarfi yanda sauran zasu jita kamar haka Share And Comment Fisabilillah🙏🏻 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Na sadaukar da wannnan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah ka jiqan iyayen mu} Page 7&8 Ni muhammad aslam na saki matata asma'u saki daya saboda bana sonta bana kaunarta Na tsaneta,,(😱😱😱). Batool ne ta fizge pepan dake hannun zahra tana qara karantawa a zuciyarta don ita bata yarda abinda zahra ta karanta musu dai-dai bane, amira kuwa miqewa tsaye tayi hannunta dafe da girjinta tana zazzaro ido waje kamar wacce aka koda ma marin bazata sai maimaita innalillahi wa innailaihi raji'un takeyi a baiyane, Khadijah kuwa rarrafawa tayi ta qarasa gaban asmah tana jijjigata tama rasa mai zatace bakinta sai motsi yakeyi amma maganar taqi fitowa, Asmah ce ta bige hannun Khadijah daketa faman jijjigata ta miqe tsaye da qarfinta fuskarta dauke da kayatatcen murmushi kamar ba ita bace keta kuka mintuna kadan da suka wuce, Gyara zaman hijjab din jikinta tayi tana kallonsu tace "dama Na Sani Allah bazai taba barina haka ba, zai kawo min dauki arayuwata, domin dashi Na dogara kuma duk Wanda ya dogara da Allah to Allah ya Isar masa a komai" daga hannu tayi sama fuskarta dauke da murmushi tace "alhamdulillahi,, alhamdulillahi ,,alhamdulillahi ,, Allah Na gode maka" Amsar pepan tayi a hannun batool ,ta dauki wayarta dake ajiye kan mirror, sannan tace musu "kumuje gida ko" dukkansu sanqarewa sukayi suna kallon ta, anrasa mai bakin magana acikinsu, Ganin sun tsaya suna kallonta kaman wasu mutum mutumi yasaka ta nufar kofar ta barsu nan tsaye tayi facewarta , da Sauri batool ta bi bayanta tasha gabanta tace " yanzu da gaske tafiya zakiyi asmah " Wani kallo ta watsa mata tace "me zan zauna inyi miki" batool tace "dare fa yayi asmah " tace " saime to in dare yayi, Wlh ko qarfe biyu dare ne yanzu bazan kwana agidan nan ba batool " batool zata sake mata wani magana ta daka mata tsawa da cewa " dallah ki matsamin a gaba malama". Hakan yasa batool matsawa a gabanta ta bata hanya ta wuce . Komawa dakin batool tayi nan ta tarad da sauran, amira na trying number yaya kamal yaqi shiga, sake dialing number tayi cikin sa' a kuwa wayar ya fara ringing saida ya kusa katsewa kamal ya daga kiran tare da sallama , Ko amsa sallaman amira batayi ba ta fara magana cikin muryar kuka "yaya kamal kana inane don allah kazo yanzu Dan Allah yaya kazo ka taimakemu " jin abinada amira ke fad'i hankali tashe yasa kamal shima cikin Dan tashin hankali yace " meke faruwa ne amira kina inane yanzu"fisge wayar a hannu amira zahra tayi ta kara a kunne tace" yaya kamal kazo gidan yaya aslam dake London road inda akakai asmah dazu" "OK Ku jirani ganin nan zuwa yanzu" Asmah kam koda ta fito wucewarta tayi ko waiwayen su batayi ba,koda tazo get cikin sa'a mai gadi ya kewaya don haka sakata ta zare a qaramin kofa tai ficewarta, Bayanta suka biyo cikin sassarfa amma ko kafin su fito tayi nisa, suma ganin get a bude yasa su bin bayanta da sauri - sauri gudu - gudu , hongota sukayi tanata zuba Sauri tayi musu nissa sosai, hanyace miqaqqiya babu kwana har zuwa titi, don haka suka shiga binta a baya don karta bace musu. Kasancewa unguwace ta manyan mutane kuma gashi dare ne yasa babu abun hawa Na haya sai motar gida dake wucesu jefi jefi Share And Comment Fisabillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY AYSHA NALADO FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 9&10 Motar kamal ne ya shigo kwanar gidan a guje sai gudu yakeyi hakan yasa bai lura da asmah ba ya wuceta.......Amira ce ta fara hango motar don haka ta gaya wa sauran ga yaya kamal nan, hannu suka daga mai don ya ganesu , Gabansu yayi parking ya fito a rude yana tambayansu lpy meya samesu ina ita asmah? Duk hankalinshi a tashe yake. Khadijah ce tayi karfin halin amsa masa da "yaya asmah tàna gaba..... yaya kamal muje gida sai amaka bayani wlh akwai matsala" Shima bai qarayin magana ba ganinsu lafiyar su lay ba wani ciwo ko wani mugun abu a tare dasu, bude motar suka yi suka shiga baya dukkansu yayinda kamal ya zauna a mazaunin shi na direba,,, Rivas yayi suka kama hanyar gida,, hango asmah sukayi daidai ta isa bakin babban titi, parking kamal yayi a gabanta ya bude mata kusa dashi baice mata komai ba, itama ba musu ta shiga ganin kamal ne gashi kuma dare na qarayi......... Zaune yake a room na hotel daya kama hankalin shi kwance kamar bai aikata komai ba...babu alamar damuwa ko wata nadama at are dashi, baidamu da neman shi da akeyi a gida ba. sarai yasan irin neman shi da amir dasu Abba sukeyi acikin garin minna... Amma ya bace musu bat ba amo ba labarinsa duk inda akasan zai iya zuwa ya anje ba a sameshi ba duk hotel din da akasan zai iya zuwa amir yaje ya bincika baije nan ba... Kasancewan amir yasan halinshi nasan Babar harka yasa iya manyan hotel din dake garin ya duba bai duba qananan ba. Hotel din daya kama ba Wanda zaiyi tunanin zai iya zuwa nan...amir kan ba qaramin kunya yasha ba Na irin gayyatar da yayi na abokansu tun da secondary, Dana aboard inda sukayi karatunsu da abokanan kasuwancinsu, amma aslam ya watsa masa kasa a ido, ko zuwa su gaisa baiyi ba kuma bai halarci wajen daurin auren ba balle ayi maganar zuwa dinner da amir din ya shirya , duk tarin yawan aboka nansu da sukazo haka amir yara jigila dasu shi kadai tun daga abincinsu abin shansu wurin kwana su dadai sauran su sai kamal dake dan taimaka masa haka dai had yasamu aka gama daurin auren ya sallame su , kiran ways kuwa amir ya kira aslam a waya yafi sau Dari bai dagawa massages kuwazed'a magana, amma aslam yayi mursisi dashi ya share shi, System dinshi ya bude ya shiga gabatar da aikatotin shi Na yau da kullum da yake gudawarwa da suka shafi harkokin business dinsa saida ya gama tsab ya kulle system, wayarsa be ta fara ringing gyara zama yayi da kyau ya dauki wayar yana duba me kiran nashi... (zee my 💖) ya gani yana yawo akan screen din wayar saida kiran ya kusa katsewa yayi picking tare da sallama... cikin kashe murya da tsabar iyaya zee ta amsa sallamar tare da cewa" da fatan masoyina ya wuni lafiya " Wani kayataccen murmushi ne Wanda ba kasafai ake ganin irin shi a fuskarshi ba ya subucemai , amma kuma bai amsataba yadai amsa sallamarta a zuciyarshi.... Jin shirun yayi yawa yasa zee cire wayar a kunnenta tana dubawa ko yana kan layi , still dai call din nanan bai katseba, ganin haka yasa tasan yau yan miskilan na kusa, don haka tace "haba my husband to be yau kuma wani laifin na maka kake neman horani da shirunka" dan dakatawa tayi don tasan sarai bai cika son magana da yawaba, Shiru kamar bazaiyi magana ba can kuma sai yace" lafiya qalau na wuni kuma ina fatan kema hakan take a gareki " murmushi tayi tace"nima qalau na wuni saidai kewarka data hanani sukuni " "dagaske kina kewata"ya tambayeta " sosaima, inkaji kewa daya kenan " yace "ok to yayi kyau yasu mom" "Tana lafiya tacema na gaisheka ". "OK" kawai yace mata, Dan shiru sukayi gaba dayansu kowa naji da kanshi har garama zee saboda son da take mishi wani lokacin takan ajiye Jan ajinta ta mishi magana , yanzuma ita ta katse shirun da cewa,"wani labari Mara dadi nake taji abakin mutane wai kayi aure dis week " amsata yayi da cewa "waya gaya miki " tace"friends dina da suke 9ja mana, kusan mutun biyar suka kirani awaya suka gayamin sannan kuma na gani a Media......amma saboda baka gayamin ba ban wani yarda ba, saboda nasan duk duniya inba niba baka kala wata mace ni kadai ce zabinka "lumshe kyawawan idanunshi yayi ya bude a hankali sannan ya ce mata" da gaske ne nayi aure" ya fada mata haka ne kawai don ya gwada ta, domin kuwa dagasken ne kamar yadda ta fada itace zabinshin duk duniya, itace first luv dinshi kuma har yanzu ita yakeso, bashi da wani burin daya wuce ya mallaketa domin ta hada duk abinda yake buqata awurin diya mace musamman matar da zai aura Wanda yake ganin asmah ko RabinRabin shi bada shi Share and comment Fisabillillah. 💖DAMA TA BIYU💖 BY AYSHA NALADO FREE BOOK {Nasadaukara da wanna book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 11&12 Aiko ya gwadatan Dan wani iri kwance kwance gabanta yayi ya fadi, nan da nan hankalinta ya tashi ta birkice, mom dinta dake zaune kusa da ita tanajin duk abinda suke fad'a ta jawota jikinta ta rungumeta ganin tanason ta fashe da kuka, ita kuma mom bata son tayi kuka a gabanshi akan wanna maganan, Don acewarta idan yaga ta damu dashi haka sosai zai wulaqantata ne idan sunyi aure, bazai dinga kulawa da baccin ranta ba, don yana ganin tana bala'in sonshi komai zai mata bazata damu ba, wai ta dena nuna mai mahaicinso 'karya raina ta, hannu mom ta saka ta kashe wayar, Aslam jin shiru yayi yawa yasa ya cire wayar a kunnen shi ya duba gani yayi tayi ending call din , murmushi yayi don ya riga yasan hakan zata faru, yamaga qoqarinta da bata yi mai wani hauka ba, d'on yasan yanda takeson shi idan taji yayi aure ba qaramin tashin hankali zata shiga ba, Saidai abinda aslam bai saniba ranar da zee ta farajin labarin yayi aure saida tayi dan qaramin hauka, mom dinta ne ta dinga lallashinta sannan ita ta hanata nuna mishi ta damu da auren da yayi, ita ta hanata ta kirashi tun lokacin ta zuba mishi hauka, ta gaya mata ta nuna irin abin bai dameta ba, wai don idan ya gane ta na kishinsa ya samu lagonta kenan, ba a nunama namiji mugun so don ba yan goyo bane, Zaune take tayi irin zaman nan na tahiya kanta a kasa yayida gabanta kadan wani farin kyakkyawan tsohone hannunsa goye a bayansa sai safa da marwa yakeyi fuskan nan nashi a murtike babu alamar fara'a kai da gani kasan ransa a mugun bace yake, Sallama daddy da mummy sukayi amsa musu alhaji baba yayi neman guri sukayi daga gefen kafet din dake shimfid'e a tsakiyar parlon suka zauna, Asmah ce ta gaishe su cikin girmamawa sai lokacin dukkan su suka kula da itace a wurin amsa mata sukayi, zuciyoyinsu cike mamakin ganinta da kuma tarin fargaba, basu taba tsammanin ganin ta a nan a dai dai wannan lokaciba, don koda su zahra suka shigo basu gayawa mummy komai ba, koda ta tambayesu lafiya suka dawo ba sunce zasu kwana bane, ce mata sukayi lafiya qlau sudai sun dawo ne sun fasa kwanan , Ita kuma ganin yanayin su wani iri sai ta alaqanta hakan da qila yayansu ne ya korosu, Sallamar da aka kumayi ne ya katsewa mummy tunaninta, mamice tare da abbah sai kuma ummi dake bayansu, suma guri suka samu suka zauna suna mamakin ganin asmah , Dukansu hankalinsu suka mayar kan mahaifin nasu dake ta faman safa da marwa, Shima ganin duk yayan nashi sun hallara yasa ya juwo ya fuskancesu ransa a matuqar bace ya fara magana "Aisha" ya kira sunan mummy , Dago kai mummy tayi tana amsa masa da "na'am baba Yace" yace inason a matsayinki na mahaifiyar wannan yaro aslam ki kirashi ki bashi umarni nan da minti goma ko a ina yake yazo ina buqatar ganin shi a falon nan" Nan take gaban mummy ya yake ya fad'i kar aje wani mugun abu aslam yayi fa, don ita hankalinta bai kwanta da wannan kiran gaggawan da alhaji baba ya musuba duk da batasan kiran menene ba, hankalinta bai qara tashiba saida taga asmah a wajen yanzu kuma gashi ance ta kira aslam, haka dai ta daga wayarta don kiran aslam din , Yayinda alhaji baba yaci gaba da magana cikin dan danne yanayin da yake ciki na bacin rai ya kira sunan ya yan nashi guda uku da ya mallaka a duniya yace" abdullahi" "na'am baba daddy ya amsa," Yace "dakai da qannenka Yusuf da Amina da matayenku da yayanku .....Allah ya muku albarka" har suna hada baki gurin amsa masa da amin baba. Daidai nan kuma hjiya mama ta shigo dakin, tsohuwace mai kamala cikin shiganta na mutunci idanunta sanye da farin glass na qara karfin gani, tana dan dingisawa alamar kafa nadan matsa mata abinka da jikin tsufa, waidonma su tsufan nasu mai kyau ne angode Allah Neman guri tayi ta zauna a daya daga cikin kujerun falon .. Magana alhaji baba yaci gaba dayi" tun kuna qanana kuka kasance masu yimin biyayya a dukkan abinda na umurceku, sannan haka kuma horas da yayanku akan bin umarnina, Baku taba saba umarninaba daku da yayan Ku....nagode nagode Allah ya saka muku da alkhairi, kuma insha allahu zaku tsinci ribar biyayya a gaba koda bayan raina ne, sannan kuma Abu na biyu da yasa na kiraku nan shine" (Kuyi haquri dear fan's jiya banida chaji ne) Share and comment Fisabilillah🙏🏻 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK 🇳🇬🇳🇬HAPPY INDEPENDENCE򌰼🇳🇬🇳🇬 {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 13 & 14 "Maqasudin abin da yasa na tara ku anan shine "miqama Daddy takardan sakin da asmah ta kawomishi yayi, Hannu biyu daddy yasa ya karbi pepan amma bai bude ba yana jiran umarni. CI gaba Allah ji baba yayi da fad'in "wannan shine sakomakon abin da aslam ya sakamin da shi , Tunda nake cikin yayana da jikoki na ba'a taba aikatamin abinda aslam ya aikatamin yau ba, amma ba komai rayuwace" Alhaji baba ya qarashe maganar cike da bacin rai a muryarshi"abdullahi bude takardar Ku gani mana" daddy da duk jikin shi yayi sanyi qalau yayi karfin halin bude pepan da bismillah a bakin shi.....abinda ya gani rubuce cikin pepan ne ya sakashi sakin pepan ba tare da ya shiryaba, abbane ya miqa hannu ya dauki takardar ya duba..... Miqewa shima yayi a zabure ya maimata innalillahi wa innailaihi rajiun kafin ya bude baki yace "wani irin haukane aslam ya aikata haka" Ummi ne ta karbi takardar ta duba itama ta miqa ma mummy da mami , kowa hankalin shi ya tashi a falon nan idan ka cire asmah da alhaji baba.... A zabure daddy ya miqe yayi hanyar waje, Alhaji baba ya dakatar da shi da cewa "abdullahi dawo ka zauna" ba musu daddy ya dawo ya zauna , Alhaji baba kallan mummy yayi yace "Aisha kin kiramin shi ?" Amsawa mummy tayi da "na kirashi bai yi picking ba amma na mai text nasan inya gani zai kira yanzu" gyada mata kai alhaji baba yayi alamar gamsuwa...... Daidai wannan lokacin kuwa aslam ne ya fito wanka daure da towul a qugun shi, yana goge kanshi da karamin tawul d'in dake hannun shi, saida ya gama goge jikin shi ya dauki body lotion dinsa ya shafa da body spray dinsa mai shegen tsada da tsananin dadin kamshi, ya shirya cikin kayan barcinsa farare riga da wando marasa nauyi, pray mat ya shimfida ya gabatar da shafa'i da wutiri yayi addu'o'inshi , so yake ya kwanta barci da wuri , kallon agogo yayi ganin goma da Rabi na dare yasa ya Dane gado ya kwanta ya kashe fitila mai haske yabar dim light, wayar shi ce tayi qara alamar message ya shigo kamar ya share Dan d'azuma yana ji ana kiran shi ya share ko dubawa baiyiba balle yasan waye, shi duk zaton shi zee ce ko yanzuma yana zaton ita ce ta mai message , daukar wayar yayi da niyar kashe wa gaba daya don da gaske bacci yakeson yi da wuri, sai kuma ya tsaya don ganin message din daga mummy ne, ganin abinda ta rubuta ya sakashi saurin lalubo numberta ya kira jiki na rawa, daidai lokacin alhaji baba ke cema mummy ta sake kiran shi, Ringing wayar mummy ya fara ganin Aslam dinne yasa yasa mummy saurin d'agawa ko amsa sallamarsa batayiba tace a kausashe"kasameni a gida nan da minti goma kuma umarni nake baka ba shawara ba idan har ni na haifeka...... Idan kuma nima zaka bijiremin d'inne to bismillah shege ka fasa" git ta kashe wayarta ta barshi da way a manne a kunne, Nan shima hankalinshi ya tashi jin yadda mahaifiyarshi ta mai magana cikin bacin rai, ga dukkan alamu sakon abinda ya aikata ya iskesu kenan.....hankalinshi ya dan tashi jin muryar mummy cikin bacin rai da tsananin fishi don yasan fishinta ba sauqi har gara fishin daddy yafi sauqi akan nata, amma ko dar baijiba akan abinda ya aikata balle yayi nadama Tashi yaya ya shiga cikin qananan kaya ya dauki key din mota da wayarshi ya fice daga hotel din zuwa gida minti 15ya kaishi gida , direct sashen alhaji baba ya nufa son yasan sunacan suna jiranshi , Da sallama a bakinsa ya shiga parlon Abba da mami da hajiya mama ne kawai suka amsa mishi a fili , samun guri yayi ya zauna kusada abba, kanshi a qasa ya fara gaida mutanen parlon, kamar dazu daddy da mummy basu amsa mishi ba amma alhaji baba ya amsa mishi wannan karon, Kallon asmah yayi kanta duqe a kasa nan take ya qarajin tsanar yarinyar a ranshi, kamar ya shqeta ta mutu kowa ya huta haka yake ji a ranshi duk ita ta jawo mishi wannan matsalar da yace ciki iyayenshi na fushi dashi akanta, Kowa ya nutsu a parlon ana jiran hukuncin da alhaji baba zai yake gyaran murya yayi kafin ya fara da fadi "fadin Muhammad naga saqonko kuma na code amma ka Sani ka tabka babban kuskure Wanda zakayi Dana Sani nan gaba , lilokacin da Dana sanin bazai amfaneka da komai ba zakayi nadama loacinda nadaman ka baida amfani, kuma ka rubuta wannan maganar ka ajiye ko bayan raina zaka tina na taba gaya maka shi, "dago kai aslam yayi zai fara bada haquri,, Dakatar dashi alhaji baba yayi da cewa"banyi fushiba Muhammad kankan ka cuta baniba, wlh kayi babban asara , domin zabin da namaka zabine daya a ciki dubu amma kasa qafa kayi tafali dashi, har kana sakinta ranar da aka daura muku aure waidon ka kunyatani..kanka kama, ita kuma Asma'u zataci gaba da zama damu anan, Allah zai bata mijin da yafi komai tayi aurenta na aurad da ita kamar yadda nama kakanta aminina alkawari Yusuf inason idan zaka je yima yan biyu da amira registration ka hada da asmah, tunda auren bai yuwuba karatu zata ci gaba da shi kafin Allah ya kawo mata wani mijin " Sannan Abu na gaba"abdullahi ,Aisha,Yusuf, maryam da amina, inason Ku zama shaida na kamar yadda aslam ya Nina baya qaunar zabina asmah, to naji amince, amma babu aure zakanin shi da asmah a nan gaba na harantashi.......na haramta aure tsanin Muhammad da asmah ko bayan raina ban amince ba duk Wanda ya sake bashi auren asmah ko bayan raina ban amince ba," "Abu na karshe kai Muhammad ka sanar da iyayen ita yarinyar da kake so din cewa rana ita yau iyayenka zasu shigo gida ayi magana" Yana gama fadin haka ya miqe yabar parlon matarsa ma bin bayanshi tayi don ta rarrasheshi ganin ranshi ya baci sosai , Daddy ne ya fara miqewa yabar parlon Mummy ma bin bayansa tayi ko kallon inda aslam yake basuyiba , ummi ma da ranta ke matuqar bace da abinda aslam yayi ta kama hannun asmah suka fice daga falon, Sosai abbah kema aslam fada mami na taya shi saida suka tabbatar jikinshi yayi sanyi sannan suka qyaleshi ganin dare yayi 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 15 & 16 Sosai abbah kema aslam fada mami na tayashi.. Saida suka tabbatar jikin shi yayi sanyi sannan suka qyaleshi ganin dare yayi, bayan sun qara tabbatar mai lallai lallai ya nemi gafarar iyayen shi da kuma alhaji baba domin fushinsu a gareshi ba alkhairi bane.....dole aslam ranar a gida ya kwana don dare yayi sosai, Washe gari gida ya tashi a hautsine sakamakon farkawa da sukayi da wannan mummunan labari ... Baqi da sukazo daga nesa duk suna nan wasun su dama yau zasu wuce, sai ga wannan labari mara dadi, Duk wani masoyin wannan familyn saida yaji ba d'ad'i akan abin da aslam ya aikata...abune da bai taba faruwa ba a tarihin familyn ...yayinda a daya bangaren wasu da dama keta farin ciki da faruwan hakan kamar su zuna ruwa a qasa su sha saboda tsabar farin ciki, bama kamar zeee don tuni labari ya isketa kunsan abin duniya baya boyuwa mussan abin da bana alkhairi ba irin wannan an dinga yama d'id'i dashi kenan, Alhaji baba da kanshi ya sanarma kakan asmah Wanda yake babban aminin shi abinda ke faruwa, bai samu halartar bikin ba saboda baya qasa yaje aikin hajji kasancewar lokacin aiki haji ne... baiji d'ad'i ba amma kuma haka ya d'auki qaddara karshema shiya koma rarrashin alhaji baba Dan ganin alhaji baba yafishi d'aukan zafi akan lamarin ... Baqi dangin mahaifin asmah da dangin mahifiyarta da suka zo daga garuruwa mabanbanta don halarta bikinta a ranar suka jujjuya da labari Mara dadi ...suka bar asmah a gidan ba wanda yace zai tafi da ita tunda sunsan nan ne gidanta don tun tana qarama alhaji baba ya d'aukota bayan rasuwar mahaifanta yazo ya danqata a hannun mummy da daddy suka zame mata sabbabbin iyaye suka hadata da nasu yayan suka riqe ba tare da sun nuna mata wani banbanci ba ,,, yayinda a gefe guda alhaji baba da alhaji Mallam kankan asmah su kadai suka San dalinsu na zaman asmah a gidan.. Ba wani dalili bane kuma illah nason hada zuri'a a tsakanin su domin tun akan yayansu sukeda wannan burin, sai kuma ya kasance yayansu duka maza suka haifa alhaji baba Nada yaya uku, abdullahi mahaifin aslam Wanda ya kasance shine babba yana da matar shi d'aya Aisha mummy yayansu hudu Muhammad aslam ne babbah Wanda yaci sunan alhaji baba sai mai bi masa rabi'ahtu itama taci sunan hajiya mama ne tayi aure last year harda yarta daya hanifa, sai kuma yan biyu mummy wato zahra da batool Sai mai bi mishi Amina take auren wani Dan uwanta suna zaune a abuja itace mahaifiyar, amir Wanda ya kasance amini kuma Dan uwa ga aslam kasancewar tsararrakin juna Dan rana daya akayi bikin ta Dana daddy saboda kasancewarta mace, Sai kuma Yusuf shine mahaifin kamal da amira shima matan shi daya maryam mami, amira tsaran su batool ne shi kuma kamal ya kasance mate din rabi'ah , Daddy da abbah dukansu suna zaune ne a gida daya da mahaifinsu babban gidane kowa da part d'inshi Shi kuma alhaji Mallam kamar yadda jikokinshi ke kiran shi yaya biyu ya haifa kuma duka maza mahaifin asmah aminu shine babba sai kuma qanin shi Ahmad mahaifin Khadijah, Amintarsu ya samo asaline tun akan iyayensu da suka kasance suma aminai haka aka haifesu suka tashi tare ko ina zasu tare makaranta da gida yau suna gidan can gobe suna can har suka gama secondary school alhaji baba mahaifin shi shararren Dan boko ne kuma Dan kasuwa yayinda mahaifin alhaji Mallam ya kasance babban malamin addini.... Haka kowannensu ya gaji mahaifinsa yanzu haka alhaji Mallam babnan malamine da akeji dashi a fadin Nigeria,, inda iyayensu suka rasu suka barsu, amintarsu har taso tafi na iyayensu Dan daya baya aiwatar da komai saida shawaran daya....lokacin da sukayi aure sun qudurci niyyan idan Allah ya basu zuri'a zasu hadasu aure domin zumunci ya tabbata na har abada... saidai kicin ikon Allah yayansu suka kasance maza mace daya alhaji baba yake da ita Amina kuma sai ta kasance tsaran aminu( mahaifin asmah )saboda alhaji baba ya Riga alhaji Mallam yin aure Dan haka ya rigashi haihuwa,,lokacin da amina ta isa aure kasancewarta mace aminu ya mata yaro don haka tayi aurenta da wani Dan uwanta ta dangin mahaifinta.... Haka su alhaji baba suka haqura da wanna burin nasu na hada zuri'a ganin yadda Allah ya tsara lamarinsa, saidai lokacinda da suka fara samun jikoki burinsu nason had'a zuri'a ya dawo sabo dal ganin Allah ya fara azurtasu da jikoki maza da mata... Iyayen asmah sun rasa ransu ne ta dalilin hadarin mota da sukayi lokacin asmah na noziri sun ajiyeta a school kenan zasu wuce anguwa da kannenta biyu kasancewar ita ta fara zuwa school baza aje da itaba suka biya suka ajiyeta tana kuka zata bisu suka mata wayau suka wuce basuyi nisa da school dinba tayar motar ta fashe, motar ta dinga tambul akan titi, nan dai gaba dayansu suka mutu, sai mummunan labari alhaji Mallam yaji, sunji mutuwarnan sosai kowa sai tausayin asma u yakeji , bayan share makoki alhaji baba ya nemi abashi riqon asmah ya hadata da yan biyu tayi karatu don tafi sakewa cikin yara tunda nan ba wasu yaran tunda lokacin Ahmad baiyi aure ba ana dai shirinyi ne, anan alhaji baba yace idan ta girma kuma sai a hadats aure da dan'uwanta aslam,, nan take alhaji Mallam yayi na am da hakan saidai yace shi baida burin ya mace tayi karatu mai zurfi yafison tayi iya secondary in yaso in mijin ta ya aminci taci gaba a gidanta, take kuwa alhaji baba ya mishi alqawarin indai tagama secondary zai aurad da ita ga aslam din taci gaba a gidan shi anan suka binne wannan sirrin nasu suka barshi a ransu sai lokaci yayi kowa yaji inda sukayi fatan Allah ya hada kan aslam da asmah kafin lokacin don komai yazo musu da sauqi, sai dai kuma hakan bata kasance ba, Zuwan asmah gidan lokaci tanada shekara hudu a duniya yayinda aslam keda goma sha hudu, hannun mummy da daddy alhaji baba ya danqa amsah inda suka hadata dàsu batool suka riqe tsakani da Allah amira qaurowa tayi daga part din mami ta dawo part din mummy kullum tanacan in akace tazo ta wuce part dinsu har kuka takeyi ganin haka yasa mami barinta wa mummy ta hada duka su hudun ta riqe yayinda mazan kuma suka kasance yan dakin mami ...tun fil azal aslam baya qaunar asmah domin tun ranar daya fara ganinta ya dauki karan tsana ya daura mata bata mai komai ba shidai kawai abinda ya Sani idan ya hada ido da ita gaban shi faduwa yakeyi tun daga gani na farko hakan yasa ya tsaneta baya so ganinta har mayya take kiranta a cewarshi inba maitaba ya za'ace daka hada ido da mutum gabanka ya ringa faduwa, haka ya takura wa rayuwarta kwata kwata a gidan idan aslam nanan asmah bata da sukuni... Wani irin mugun tsoranshi ya dasu a zuciyarta saboda yadda yake azabtar da ita, duka zagi mari punishment haka yake sakata, yasha kulleta a toilet tun safe sai yamma, suma sauran qannenshi bawai sun sha bane a hannunshi suma yana dukansu amma ba kaman na asmah ba, a haka har suka shiga jss 1lokacin ne kuma aslam ya gama secondary school shida amir inda aka shiga fafutukar naman musu admission a qasar waje har lokacin ba abinda ya canja a tsakanin aslam da asmah yanda yakejin mugun tsanarta itama haka ta tsane shi....... 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayenmu} Page 17 & 18 Duk wannan abinda ke faruwa a tsakanin su iyayensu basu da labari, iya yara yaran gidan ne kawai suka san abinda ke faruwa su kuma ba daman fada tsoranshi sukeji kar su fada ya dake su, Kamal ne ma yake qoqarin hanashi in yana dukkanta yai ta bashi haquri amma ko kallon banza baya isansa, Rabi'ah kuwa tun ranar da tayi mai magana ya tsinka mata mari lokacin batayi aure ba taja bakinta tayi shiru ta zuba ma sarautar Allah ido....... Kamal yana matuqar tausayin asmah saboda irin abubuwan da aslam ke mata, haka zai sameta yaita rarrashinta yana bata baki akan tayi haquri wata rana sai labari, wani irin kulawa yake bata Wanda ko qannenshi baya basu irin wannan kulawan, kamal ya kasance mai yawan magana Dan haka zaizo yasata agaba yaita mata labaran ban dariya duk Dan ta manta da abinda aslam ke mata agidan... A hankali wani irin shakuwa ya shiga tsakanin, Su asmah sun shiga jss 1 lokacin aslam na shirye shiryen wucewa karatu kasan waje,,, FGC abbah yakaisu inda asmah da batool A class zahra da amira B class su hudu suke rayuwarsu gwanin sha'awa,, basuda wasu baren qawaye su hudun nan sune qawayen junan su. Ranar da aslam da amir zasu tafi makaranta a kasar Malaysia zo kuga murna gurin y'an mata mummy, bama kamar asmah har wani Dan qaramin party suka hada a dakinsu su hudu na murnan tafiyan aslam ... Tabbas y'an matan mummy sunji dadin tafiyan aslam, asmah tuni ta saki jikinta a gidan don dama aslam ne kadai matsalarta ... Agidan kowa nasonta babu mai nuna mata wani banbanci ta zama yar gida babu mai sanin rikonta akeyi a gidan ,,, alhaji baba ma qarara yake nuna mata soyayya fiye da sauran jikokinsa, domin ita din jinin amininsa ce mutum mafi soyuwa a gareshi, sosai yake kula da dukkan lamarinta,, hakan ya saka mata wani irin matsanancin kaunar tsohon da ganin girmanshi a zuciyarta, sosai take girmama shi, sosai take girmama dukkan lamarinsa, yanda ko layi yaja yace kar ta tsallake to bazata taba tsallakewa ba kuwa har illah masha Allah, Ta bangarenb kamal kuwa shaquwan dake tsaninshi da asmah ya rikide ya koma soyyaya a gare shi ,domin kuwa shi kadai yake kidanshi da rawanshi ita batasan yanayiba, ta dauka kawai sabon da sukayi ne yasa yake mata wasu abubuwan kamar na soyyayya, saidai kuma duk Wanda yaga yadda suke mu'amala saiya saka musu ayar tambaya❔, su zahra sunsha tambayarta wai kod'ai soyayya takeyi da yaya kamal, takanyi murmushi tace musu a'a ita yaya kamal yayanta ne ba wannan maganar a tsakanin ta dashi,, sukance mata ba wani nan intayi wari maji, Su aslam sunacan kasar Malaysia suna karatu hankali kwance tunda ya tafi bai taba dawowa gida Hutu ko ganin gida ba , yanadai kiran iyayenshi a waya suma suna kiranshi musamma mummy da mami, zuwansu da shekara shida suka hada karatunsu akan business, amir ya tattaro ya dawo qasarmu ta gado, shikuman gogan ya zauna ya fara aiki acan da wani babban kamfanin mahaifin abokinsa da sukayi karatu tare..... A Malaysia ya hadu da zee school dinsu daya amma ba Abu daya suke karantawa ba, zainab abdussalam yariyan wani. Hamshaqin attajirin Dan boko ne haifaffan Nigeria ma zaunin Malaysia,, zainab yar gata ce gurin iyayenta kasancewar ita kadai suka Haifa sangartatciya na qarshe,, bata iya komai ba sai rashin kunya, sai kuma ayi wanka a qure kwalliya a fita yawo da qawaye akashe kudi kamar basusan ciwonshi , kodayake basuwan ciwonshi ba tunda basu ke wahalar nemowaba, Zainab ta kasance kyakkyauwa ce yar kwalisa kuma macece mai class don ba kowani gara take kulawaba saita tabbatar kai wani ne ko Dan wani sannan zata yarda ta kulaka kuyi soyayya,, kana kawo mata maganar aure zaku watse don ita kwata kwata babu aure a gabanta, haka iyayenta, a cewarsu bata isa aureba shekara ashirin da shidda, wai saitakai thirty five zasu aurad da ita, Ranar da zainab ta fara ganin Aslam ta kamu da matsanancin soyyayyar shi, saidai shi baima son tanayiba kasancewar sa ba mai kule kule kulen mata bane , a hankali zee tafara shigema aslam, bayan tayi bincike sosai akanshi ta gano ko shidin wanene , sosai ta saka mishi ido a school din inyana waje zatazo ta zauna ta dauko book din ta tana karatu, tun bai lura da ita har ta fara daukan hankalinshi, tun bai riqe face dinta ba har yayi making face dinta a kwakwalwarshi ,, zainab ta hada duk abinda aslam yakeso a y'a mace , yana son kyakkyawar mace kamardai zee, yanason wayyayyar mace yar boko wacce tayi karatun boko mai zurfi,, yanason mace mai aji wacce ta iya daukar wanka wacce batada rawan kai irin na yan matan zamanin nan wacce in ya shiga da ita cikin taro baza'a raina shiba, zee ta gama hada duk wadan nan qualities din,bai tunkaretaba saida yayi bincike akanta ya gano ko ita wacce ce, sannan ya baiyana mata manufarshi, ba wani dogon Jan aji ta amince masa nan da nan suka qulla zazzafan soyayya Date: Oct 4, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayenmu} Page 19 & 20 A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah yaune su asmah suke candy sun kammala secondary school dinsu, sun zana waec & neco harma da jamb dinsu cikin aminci , sai zaman jiran result , sun samu kyaututtuka da dama musamma ma amsah data kasance head girl dinsu kuma daliba mafi qoqari a duk set dinsu, qanin mahaifin ta alhaji Ahmad da mai dakinshi mahaifan Khadijah , sunzo mata daga suleja inda suke da zama harma da Khadijah da kannenta maza guda biyu, A daidai wannan lokacin kuma ya aslam cika shekara 7cif cif a Malaysia kuma yake shiri dawowa qasarsa ta haihuwa wato 9ja , Ranar wata asabar gaba daya gidan ya hautsine da shirye shiryen tarban Muhammad aslam, kowa ka gani a gidan yana cikin farin ciki ba y'an qannenshi ba ba iyayensu ba, to ai dole shekara 7 fa ba kwana 7 bakwai ba ,... Asmah kam tunda taji labarin dawowar aslam Har zuwa yau da jirginsu ya taso gabanta faduwa yake ko kad'an bata farin ciki da dawowar shi, dariyar ya'ke kawai takeyi a yan kwana kin nan Dan kar jama'an gidan su gane halin da take ciki, su zahra sunyi matuqar mamakin yadda take nuna itama tana farin ciki da dawowarshi bayan sunfi kowa sanin tsananin su...Itakam a zuciyarta takance hmmmm kudai kawai fuskata kuke gani, bakusan abinda ke zuciyataba amma na ciki na ciki..... Kamal ne kawai ya fahimceta, ya kuma kwantar mata da hankali cewa ai yanzu ta girma bazai dinga mata abinda yamata shekarun baya ba ....da haka dai ya kwantar mata da hankali.... Mummy, daddy, abbah, da kamal sune sukaje daukoshi a airport jirgin su na sauka mutane suka fara saukowa daya bayan daya shine kusan na karshen sakkowa,, zaro ido waje mummy tayi tare da d'aga hannunta kamar zatayi addua ta kulle bakinta, ganin yadda aslam dinta ya koma kamar yani balarabe ya girma ya zama cikakken namiji kwata kwata ya sauya ya qara kyau kamar bashiba. ...shima saida yayi arba da iyayen nashi ya tabbatar yayi missing dinsu sosai da sosai, rungume shi mummy tayi tana hawaye tanabubbuga bayanshi tane hawaye sai fadi take "idonka kenan babana" shi kuma sai maimaita "mummyna mummyna I miss u yakeyi" haka suka rankaya suka dawo dawo gida...... Lokacin da yayi arba da yan qannenshi sai murna sukeyi sukazo suna mishi barka da dawowa , ya kallesu duk sun zama yanmata yace "lallai yaran nan kune kuka girma haka kuka zama yan mata Ashe mun kusa shan biki ya fada cikin zolayarsu " amira da zahra boye fuska sukayi waisu irin sunji kunya nan, batool da yake itace rasa kunya tace kai ya aslam mufa yarane bamu isa aure ba,.... Kallonta yayi yace ja'ira kina nan yadda kike da shegen surutun nan har yanzu ko tayi dariya ,,,,,,, hajiya mama dake zaune gefe tace, "eh lallai ba shakka aslam ka shahara harda wani cewa wadannan berorin sun girma ka kusha shan biki ko.....to ai sai ka bari ka fara auren tukkunna kafin kace zaka aurad da qannenka" ,,,, Sosa qeya yayi yace "nayi aure ke kuma nayi yaya dake matas, ai daga kanki na rude qofa "hajiya mama tace"ja'iri maji ma gani ai" Duk wannan bidirin da akeyi asmah bata wajen, hasalima ko haduwa da aslam din batayiba tunda ya dawo tana jin qaran diran motocinda sukaje tarboshi ta shige toilet su kuma su batool basu jirata ba suka wuce abinsu, yanzuma da suke zaune basu lura bata wajenba , don hankalinsu gaba daya nakan yayan nasu, haka ya wuni tareda yan uwanshi, sai dare ya samu ya huta sosai . Saida aslam ya kwana bakwai da dawowa amma bai hadu da asmah ba yana son ya tambaya ko anmaidata gidan kakantane bayan tafiyarshi, amma sai wani zuciyar yace mishi to kai ina ruwanka ma da wannan yarinyar mai kwala kwalan idanu kamar fitilan mota, kawai sai ya share zancen ya basar, sai a rana ta takwas da dawowarshi ya shiga part din mummy ya tarad da yan matan dukansu harda asmah da batason zai shigo yanzuba data gudu d'aki , gabanta ne yayi kwance kwance ya bada rassss, amma sai ta dake , gaishe shi suka shiga yi daya bayan daya ya, yana amsawa a dake kamar yadda ya saba amsa musu can baya, asmah ne qarshen gaishe shi, Suna hada ido gabanshi ya shiga faduwa kamar yadda yakemai a can baya, harma yaso yafi na da , dakewa yaya ya amsa mata kamar yadda ya amsawa sauran wato a dake, tashi suka yi dukansu zasubar falon don ya hanasu zaman falon indai yana nan, sai kace falon shi, daidai zasu hau step din da zai kaisu sama, da yake dakinsu na upstairs ne ya daka musu tsawa da cewa "ke zonan". Dukansu suka juyo amma sai yayi pointing din asmah yace "ke mai idon kamar na kwadi, dake nakeyi" dukkansu kallon asmah sukayi suna don sunsan ita yake kira mai idon kwadi, don sudai basu tabajin ya kira sunantaba saidai yace mai idon kwadi ko mai idon mazuru ko kuma yace mai idon mayu , Su kuma basuga iabin idanun asmah ba su haslima I don't a birge su yakeyi, ji sukeyi dama su keda irin idanunta,... Sanin da tayi ita yake kira da mai idon kwadi ya sakata nufoshi zuciyarata kuwa sai bugawa takeyi da qarfin gaske, anashi bangaren ma hakane saidai daurewa yakeyi karta rainashi ,.. Tsayawa su zahra sukayi suka fasa tafiya wani mugun kallo ulya watsa musu, sum sum suka bace a falon, Dan duqawa tayi a gabanshi tace "ya aslam gani " saida ya gama hararanta yace waike wacce irin mayya ce, Ashe dama har yanzu kina gidan nan baki koma gidan ubanki ba , hawayene suka fara tsere a fuskarta jin yadda ya ambaci marigarin babanta, dago dara daran idanunta da yake kira da idon mayu tayi ta sauke cikin nashi idon,, bugan da qirjinshi keyi ne ya ninku, fiskewa yayi yace "bazaki daina kallona da wadannan shegun idanuwan nakiba na mayu , saina tsokale miki su" saida ya gama zage tass ya qare da cewa "wlh na tsaneki ban yana tsanar wani Abu araina kamar yadda na ysaneki ba ". Tsaki yaja yaci gaba da cewa "shima wanna kinibabben tsohon mai shegen iyayin tsiya garin shegen kwashe kwashen shi na tsiya ya ya kwaso mana jaraba ". Dan qurawa fuskarta ido yayi kafin ya tattaro miyan bakinshi ya tofa mata a fuska sannan yace "tashi ki bani guri kafin inyi qasa qasa dake a wajan nan,... mayya kawai nafi qarfinki wlh kurwata kurr " Tashi tayi bata ko ganin gabanta ta wuce dakinsu, tana shiga ta fashe da wani irin kuka ta fada jikin batool data tarota su zahrama tasowa sukayi suka rirriqeta cikin kuka take fadin"na tsaneka bana bana sonka bana qaunarka, kuma bazan taba kaunarkaba har qarshen rayuwata,....na tsaneka!na tsneka!!na tsaneka aslammmm " Ta qarashe maganar da qara fashewa da , rarrashinta suka shigayi donsu a ganin su dukanta yayi kamar yadda ya saba shiyasa take kukana nan ********** Gaskiya fans in banga comment ba bazan sakeyin posting ba tunda naga kamar bakujin dadin labarin shikenan kawai gamma mu haqura, Don in baku comment sai naga kamar Baku karantawa ne jikina duk yayi sanyi. Tom gsky inbanga comment ba zan tsaya da typing ba gdy kadai nakeso ba wasuma ko godiyan basu iyayi, To sai Ku zaba ko kuyi comment ko indaina typing 😡😡😡😡😡😡 Date: Oct 6, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 23 & 24 Biki nata gabatowa yau saura kwana goma , kota ina sai shirye shirye akeyi , amma banda amarya Asmah , ta zama wata iri da ita kullum cikin kuka, amma batayi gaban mutanen gidan, shiga toilet takeyi ta kulle kanta taci kukanta ta koshi,...... Aslam ne ya fito daga part din Alhaji baba ranshi a hade da kaganshi kasan ranshi a mugun bace yake idanun shi yayi jajur.....direct part dinsu na samarin gidan ya nufa , da baya da baya ya fada kan daya da cikin manya manyan sofa set d'inda ke falon hannayenshi ya hada cikin juna ya dunqulesu da karfi...rintse ido yayi yana sakin wani zazzafan nunfashi ,......ba komai ne ya jefa shi cikin wannan yanayin ba sai d'an kace nace daya faru tsakanin shi da alhaji baba..... Aslam ya kafe kaida fata na cewa bazai auri Asmah ba nan dai alhaji baba ya shiga rarrashin shi, rufe ido Aslam yayi ya shiga zazzagawa alhaji baba rashin kunya yana gaggaya mishi maganganun dayasan zai fusata shi har yasa yayi fushi yace a fasa auren, saidai kuma hakan bata faruba don alhaji baba miqewa yayi ya wawwanke Aslam da zafafan maruka har guda har sau biyu sannan ya nuna shi da yatsa yace "kai Muhammad wlh karya kakeyi baka isa ba, ni zaka kawowa rashin mutunci," nuna shi da yatsa yayi yace "to ko ubanka abdullahi bai isa ba, ballantana kai qaramin alhaki, kuma ka sani aure ne sai an daura babu fashi, kaje kayi duk abinda zakayi, dai dai nake da kai , duk rashin kunyar dake damunka ni nan zan sauke maka shi"hmmm ran maza ya baci,.... Miqewa Aslam yayi yace "yace haka kace ko to shikenan" yayi kwafa ya fice daga falon..... Dalinlin shigar shi halin da yake ciki kenan, saqa ya shiga yi da warwara har ya samar wa kanshi famitan da yake ganin zata fille mishi, mataki biyu zai dauka idan ya kwada na farkon bai yuwuba, to zai aiwatar dana biyu Wanda zai girgiza kowa, Asmah bata qara tsanar Aslam ba sai ranar da yasa mummy ta turo mishi ita part dinsu , mummy da kanta ta shiga har d'akinsu , ta sakata ta wanke fuska ta shafa hoda da 'kolli, Wanda rabonta da su tun ranar da zataje gidan alhaji Mallam , hijab ta zumbula har qasa ta dauki hanky tana tafe tana share hawaye da majina , mummy kam ganin ta tafi ba musu yasakata a ranta ta dinga yin hamdala tana murna gani take duk yadda akayi sun fara sasanta Kansu ne tunda gashi har yana kiranta su tattauna, Dan shi cema mummy yayi zasu Dan tattauna ne yaji shirye shiryen ta akan bikin, Asmah na qara kusantar part dinsu Aslam gabanta na tsananta faduwa haka dai ta daure ta qarasa ta shiga falon da sallama a bakinta , ganin shi tayi zaune a falon sanye da qananan kaya yayi kyau sosai fuskarnan nashi a hade ba alamar mutunci, amma ita a idonta gani takeyi ba Wanda ya kaishi muni a lokacin , ko sallamarta bai amsaba ya watsa mata wani mugun kallo mai cike da tsana .....tsugunawa tayi daga can gefe ta rakube kamar tana jira ace tak ta ruga da gudu, watazabgegiyar wuqa Aslam ya zaro daga cikin gidanta mai shegen kaifi irin Wanda tsab za'a iya fille kan mutum dashi tashi daya, miqewa yayi daga inda yake zaune da wuqar a hannun tsirara , nufo inda take tsugune yayi gadan gadan , ganin haka yasa jikin Asmah ya fara rawa ta sadaqar yau kwananta ya qare,tasan tabbas Aslam zai iya mata abinda yafi kisa ma a yadda ya tsanetan nan, don haka ta fara maimaita Kalmar shahada a zuciyarta rintse idonta tayi da qarfi donma kar taga sanda zai caka mata , ji tayi yace cikin tsawa"keee mayya look up " dago da kanta tayi da sauri jikinta na rawa cike da tsoro , guntun murmushin mugunta ya saki saboda hango tsantsar tsoratan da tayi a cikin kwayar idonta, dama abinda yake son gani kenan kafin ya kora mata kyakkyawan warning din da yake son ya mata ......... Waning ya shiga kora mata da kashedin cewa , idan ta kuskura ta bari aka daura auren nan har aka kaita gidan shi a matsayin matarsa saiya yankata da wannan wuqar ya kasheta kowa ya huta, ya qarashe maganar yanayin alamar yankata da hannun shi, nan ya tsatsara mata abinda zatayi da zaisa afasa auren. Kuma karta kuskura ta bari sunan shi ya fito, ya qare da zageta Tass kafin yace ta bace mai da gani ,..... Aikam da sauri ta miqe ta fice daga part din cikin gudu gudu sauri sauri tana sharar hawaye, ta shige part din mummy, allah yasa mummy bata falo tana dakin daddy don haka direct dakinsu ya wuce ta fada kan gadonta tanata risgan kuka abin tausayi , su batool dake zaune zugum zugum suna zaman jiran dawowarta, dama tunda ta wuce jinin su a qumba yake, sai gani sukayi ta shigo da kuka dama sun tsammaci hakan, lalkashinta suka shiga yi cike da tausayawa, gani duk sun shiga damuwa yasa ta tsayar da kukanta, amma a ranta ta qudiri aniyar saidai Aslam ya kasheta amma baza taba aiwatar da. Abinda yace tayi ba, ta yarda in an kaita gidanshi ya yankata , Sannu bata hana zuwa yau gashi saura kwana uku daurin auren Aslam da Asmah , masha Allah gidan alhaji baba kam ya cika da jama'a baki na nesa dana kusa duk sun hallara , sai shirye shirye akeyi ,.. Duk wani gata daya kamata amarya yar gata ta samu Asmah ta sameshi , musamman ummi ta dauko wata mai gyaran amare tun daga suleja ,... Matar shahararriya ce sosai ta fanin gyaran amare ciki da bai , qyara Asmah ta shiga yi tsakanin da Allah don ba qaramin kudi ta amsa ba , saidai kuma amarya kwata kwata bata bata hadin kai yadda ya kamata don gaba days bata cikin walwala saidai tana qoqarin boyewa, Ko program da aka tambayeta cewa tayi ita baza tayi komai ba, mami ne tace ba'ayi hakaba ita ta shirya mother's night ran alhamis ran juma'a ayi walima 4pm to 6pm a alkausar hall inyaso in andawo walima asa lalli washe gari a daura aure, haka ko akayi....... Ta bangaren Aslam kam ganin shiru shiru ba a fasa biki ba saima qarin shirye shirye da akeyi, yasan lallai Asmah batayi abinda yasata ba, don inda tayi ya tabbatar alhaji baba zai dakatar da maganar auren nan , kwafa tayi cike da jin haushin duk wani mai hannun ciki wannan hadin including daddy da mummy , don haka ya qidiri aniyar aiwatar da mataki na biyu wanda yasan shine kankat, koda amir ya sameshi da maganar da maganar tsare tsare da gayyatar friend dinsu, hawa yayi kanshi da masifa yana neman ya sauke haushi a kanshi , qyale shi amir yayi yaci gaba da abinda ya kamata , ya gayyato friends dinsu tun daga na nan gida Nigeria dake mabanbantan garuruwa har na qasashen qetare da sukayi karatunsu tare, da kuma abokanan aikinsu, ba qaramin gayyata amir yayiba , har dinner yaso ya hada amma ganin aslam din yaqi bashi hadin kai yasa ya bar maganar dinner ,friend dinsu da amir ya gayyata suka fara isowa ,wasu kuma na kiran Aslam a waya suna mishi murna abin ba qaramin qona mai rai yakeyi ba , kowa ma haushi yake bashi mussamman ma amir dake ta wani zaqewa yana wani gayyata, ga cikin gida nan ma bai tsira ba daga ace ya bada kudin kaza sai ace ya kawo kaza, karshema ganin za'a dame shi ya tattara yanashi yanashi ya bar gidan ba tare da sanin kowaba , ya kama daki a hotel babu Wanda yasan inda yake, ya kuma qudiri aniyar yadda alhaji baba ya tilasta mishi auren wannan mayyar yarinyar mai idon mayu to wlh saiya kunyata shi tunda dai ya dakatar dashi, amma yaqi ji har yana marin shi , to yaje ya daura shi kuma yayi alkawarin ana daurawa zai saketa, yasan indai ya saketa aranar da aka daura musu aure ba shi kenan ba kunga dole a qyaleshi da wannan auren jarabar , qilama alhaji baba yayi fushi ya aurama amir ko kamal ita a ranar, hakan ce kuwa ta kasance don da wannan matakin aslam yayi amfani ya rattabawa asmah saki aranar da aka kaita gidanshi a matsayin matarsa zabin iyayensa CIGABAN LABARI Date: Oct 5, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 21 & 22 Haka rayuwa yaci gaba da tafiya, tsakanin Aslam da Asmah kuwa babu abinda ya canja saima abinda ya qaru, tunda ya dawo walwalarta a gidan gaba d'aya ya ragu ba qaramin uzzurama rayuwarta yakeyi, Saida ya cika wata uku cif da dawowa ya huta sosai har ya kama aiki a daya daga cikin kamfanonin Abba a matsayin general manager na kamfanin, Alhaji baba ya kira dukkan yayanshi ya gaya musu qudirinsu shida aminshi Alhaji Mallam akan son had'a Asmah da Aslam aure, Dukkan su sunyi farin ciki sosai saidai daddy ya kawo qorafin maganar karatun Asmah d'in, nan Alhaji baba ya sanar dasu yadda suka yi da Alhaji Mallam ranar da zai dauko Asmah na cewa baya son tayi karatun boko ya wuce secondary, dukkan su sun gamsu duba da yanayinsa na babban malamin addini, shike ma wasu fadan su aurad da yayan su in sun kai minzali kunga ai bazai bar nashi ba, Sosai mummy taji d'ad'in wannan maganar don dama tunba yau ba takeda wannan buri , Nan Abba ya sake kawo maganar ko Aslam da Asmah din suna son juna , nan Alhaji baba yace ko basu son juna sai anyi wannan lamari saje can su daidaita, abar komai a hannunshi shi zai sanar musu da kanshi, nan dai meeting ya tashi kowa zuciyarshi fal farin ciki domin Asmah yarinyace nutsatsaya mai hankali da duk wasu iyaye na gari zasuso ta kasance surika a garesu Alhaji baba da Aslam zaune suke a sitting room din Alhaji baba , fuskantarsa Alhaji baba yayi yace "Muhammad Aslam ba komai yasa na kiraka ba sai domin inason muyi wata magana dakai mai muhimmanci kuma na fahimtar juna, inason kabani aron dukkan hankalinka nan ,". gyada kai Aslam yayi yace "ina saurarenka alhaji" nan alhaji baba ya shiga sanar dashi abinda suka yanke nason hada shi aure da yar uwarshi Asmah cikin kwantar da murya alhaji baba yake mai magana da lalama,,... Tun kafin alhaji baba ya gama jawabinsa gaba daya aslam ya jiqe da zufa duk sanyi AC daya cika falon kuwa , qure alhaji baba yayi da ido kamar ranar ya fara ganin shi, daqar ya bude baki yace meyasa saini zaku aura ma ita meyasa bazaka aura mata wani cikin jikokinka ba , naga dai bani kadai bane jikan naka ai, to ni baba so akai kasuwa, idan hada zuri'ar Allah da annabi za ayi a aura mata kamal mana ko amir naga ai suma jikokin kane, kuma suma sun isa aure, to barin gaya maka gsky mallam tsoho bana son yarinyarnan bana kaunarta bata cikin tsarin matan da nake burin yin rayuwar aure dasu, don haka kayi gaggawar kwance wannan kullin da kayi , donni inada wacce nake son aura, wayyayya mai aji yar boko ba irin wannan kucakar yarinyar ba,"yana gama fadin haka ya miqe ya fice daga falon a fusace, Alhaji baba da mamaki ya gama kasheshi a zaune kasa ma magana yayi tunda yake wani daga cikin jikokinshi bai taba mai rashin kunya irin Wanda Aslam ya masa yau ba , shiru alhaji baba ya zauna yanata saqe saqe a zuciyarshi kafin daga bisani ya saki wani qayatatccen murmushi a fuskarshi bayan ya samarwa kanshi mafita, Aslam ranar daqar bacci ya daukesa bayan ya samarwa kanshi mafita yasan tunda alhaji baba ya fara wannan maganar to sai ya aiwatar,yasan tsohon da hegen nacin tsiya , don haka ya qudurci zai samu Asmah ya buga mata kyakkyawan warning akan karta kuskura ta amince da wannan hadin, yamasan ita karankanta baza tayi gogin amin cewa da auren shi ba, Haka aka ci gaba da shirye shirye Asmah bata da labari , su zahra kam sunji lbr saidai ba wacce tayi qarfin halin sanarda asmah a cikinsu , don su karan Kansu ranar da suka fara ji abin ya matuqar firgitasu ya basu tsoro don su kadai sukasan irin tsanar da Asmah da ya Aslam sukai wa juna.... An tsaida lokacin biki nan da wata daya masu zuwa, alhaji baba ya tura Asmah gidan alhaji Mallam tace ta musu kwana biyu kuma ta duba jikin Mallam din Dan kwana biyu baiji dadi ba, da murnarta ta shiya kayanta don ta kwana biyu rabonta da gidan , ta nemi rakiyar su zahra amma dukkan su sukace mata baza su samu zuwaba, tayi mamakin yadda yau tayi musu tayin zuwa gidan Mallam suka ce a'a , alhali da su suke cewa azo aje gidan alhaji Mallam ayi Hutu, haka ta shirya ita kadai bello driver ya kaita, ta tarad da kowa lfy sun tarbeta da murna da nuna jin kewanta kamar yadda suka saba , a dakin kakanta wacce take kira da kaka mahaifiyar mahaifinta ta sauka , domin matan Mallam biyu ne ya qara aure amma matar bata haihuba har gashi tsufa yazo , gidan cike yake da yayan yan uwa da kuma daliban Mallam wasu ma harda iyalansu, domin gidan Mallam babban gida ne sosai mai dauke da sashe sashe , .. Sai da daddare ta samu ganawa da alhaji Mallam bayan sun gaisa ya tambayeta yadda ta baro mutanan can gidan nasu tace lpy qlau nan suka Dan taba hira yana ta janta da Dan wasa na kaka da jika ita kuwa sai kunya takeji don bata saba irin wannan wasanda shi ba kuma gata bamai yawan magana bace, saida suka Dan taba hiran ya koma serious face dinshi shima, nan ya shiga sanar da ita abinda suka yanke akan aurad da ita ga dan uwanta Aslam, ya daura da yi mata nasiha mai ratsa jiki ya qare da cewa "wannan shine babban dalilin da yasa nace a turomin ke ni zan sanar miki da kaina, Don haka ki zama mai biyayya a garemu, wannan wata dama ce Allah ya baki domin samun miji natsattse mai hankali kamar aslam a wannan zamanin abune mai matuqar wuya dan haka sai ki gode ma Allah da irin zabin da ya miki" tuni Asmah ta daina fahimtar abida alhaji Mallam ke fad'a tundai ta fahimci aure ne akeson a hadata da babban maqiyinta mutumin da ta tsana a duniya fiye da kowa ,,,... Take wani zazzafan zazzabin farad daya ya lullubeta ci gaba Mallam yayi da yi mata nasiha wanda duk bata fahimtar komai ta Lula duniyar tunanin makomar rayuwarta, kaka ma data shigo ta same su daurawa tayi da nata nasihar, Kafin magriba zazzabin nan yaci qarfita saida Mallam ya kira family doctor dinsu yazo ya dubata ya bata magani da allurai, kafin Safiya zazzabin ya sauka saboda qarfin alluran da akamata , Kwanata biyu a gidan alhaji Mallam ta dawo gida, bayan dawowanta sai ta koma wata iri da ita bata walwala gata dama ba mai yawan magana ba sai ta qara komawa wata silent , kullum saidai ta zauna tana tunani duk ta rarrame kamar wata Mara lpya , koda yake itama Mara lpy ce don garama wani na kwance a asibiti a kanta ,..... Alhaji baba ma yasa an kirata shima dai nasihar ya mata sanna ya maimaita mata abinda Mallam ya riga ya fada mata, ya qara da cewa "amma baza muyi miki dole ba inkinga zaki cutu game da wanna lamari to kiyi magana wlh ni zan tsaya miki a fasa wanna auren, duk da cewa wanna cikar burinmu ne zamu haqura , haka Allah yaso ". Duqad dakai Asmah tayi qirjinta na bugawa wata zuciyar tana raya mata kawai ki gaya mishi bakison shi suyi haquri, yayinda wata zuciyar kuma ke tuna mata matsayin alhaji baba, daddy da mummy, a gareta bazata ta'ba iya cewa bata son jinin su ba intayi haka tayi butulci ,, wata zuciyar ta qara tuna mata da karatunta kenan yanzu onta yarda burinta na zama yar jarida yasha ruwa kenan sai dai taga su zahra suna zuwa school ita banda ita ,,,dago kai tayi da niyar furtama alhaji baba batason aslam kawai sai ta tsinci kanta da furta"alhaji bani da ja akan wannan zabin da kukamin, kune gatana , ban isa in take maganrku ba duk da kun bani zabi ,na amince da auren Dan uwana kuma yayana ya Aslam domin cikar burin ku na alkhairi , Allah ya tabbatar mana da alkhairi " qara duqad da kanta kasa tayi tana dauke hawayen dake zubo mata a idonta da wayau don kar alhaji baba yagani, ... Murmushi alhaji baba yayi yace alhamdulillahi, Allah ya yi miki albaraka dama nasan ke mai biyayyace a garemu, bazaki taba kunyatamu ba tashi kije insha Allah zaki samu y'ay'an da zasu miki biyayya fiye da yadda kika mana ,... Ta bangarn kamal da yaji labarin auren Aslam da Asmah ba qaramin tashin hankali ya shiga ba ranar da zazzabi ya. Wuni saida yayi kwana uku a kwnace kafin daga bisani ya lallashi zuciyarshi , ya tabbatar ya rasa asmah rashi na har abada, .... Shi babban tashin hankalinshi yadda aslam da Asmah zasuyi rayuwa a gida d'aya daki d'aya a matsayin mata da miji, yafi kowa sanin abinda ke tsakanin su ,tabbas yasan in akayi auren nan akwai matsala , yana dai roqon Allah yasa komai yazo da sauqi , ji yakeyi aranshi da zai iya da yaje ya samu iyasumu alhaji baba ya fada mai , amma ina! Ko giyan wake yasha yasa bazai taba iya tunkaran alhaji baba da wannan maganar ba Date: Oct 7, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 25 & 26 Yau kimanin wata daya kenan da faruwar wannan lamari , gida ya dawo normal kamar ba'ayi biki a ciki ba, ba'ki na nesa duk sun wuce , mutanen gidan kuwa yaransu da manyansu sun dauki dangana akan abinda ya faru , ko maganar babu Wanda ya sake tayarwa , sun maida abin kamar ba'ayi ba , Asmah ma da suke tunanin zata shiga damuwa sai suka akasin hakan , don ko'a jikinta, saima walwalarta data dawo sabanin da da take cikin qunci, Ta bangaren Aslam da'ker ya samu ya shawo kan iyayen shi suka daina fishi da shi suka yafe mai, saida alhaji baba ma yasa baki, duk da haka ba Ba wani sake mai fuska sukeyi ba daga mummy har daddy,... Shidai tunda ya samu sun yafe mai suna amsa gaisuwar shi , shike nan, sakemai fuskar ma yasan zasuyi a hankali,... Don shi har yanzu baiga ya aikata wani kuskure ba akan sakin da yama Asmah , ko so daya bai tabajin nadama akan hakan ba , shi yama manta da wata Asmah ya shafe babinta a rayuwarshi ,don tuni ma har ya gayawa zainab ta sanar ma iyayenta iyayenshi zasuzo next week,.... Itako zee anata bangaren ba qaramin farin ciki tayiba jin cewa iyayen Aslam zasuzo naman aurenta, duk da tasan akwai qura a gabanta , Hakance kuwa don tana sanarma mahaifinta have shi bai shirya aurad da ita yanzu ba ,.. Kwata kwata shekararta nawa da zata ce amata aure , to shi bai shirya ba idan Aslam zai iya jira nan da shekara bakwai to, idan kuma bazai iyaba to ya haqura kawai,...zee dama tasan hakan zai kasance don haka ta riga ta shiya ma hakan dama, rigima sosai akayi ta dage aure takeso kuma da Aslam , yayinda shi kuma mahaifinta yace ba yanzuba mom kuma ta goyama mijinta baya , zee gani wankin hula na Neman ya kaita dare, yasa ta dauki waya ta kira wan mahaifinta dake Nigeria, Wanda dama koda mahaifinta ya amince wurinshi za nemi aurenta , shima dai dan bokon ne kamar qanin nashi saidai shi duk abinda y'ay'anshi suke so shi yake mushi, banbancin shi da dad mahaifin zee kenan ,.....sanarai da abinda ke faruwa tayi nan ko yace tace iyayen Aslam din suzo gurinshi, zai daura mata aure da duk Wanda takeso, karta damu , kuma zai kira dad dinta ya mishi magan cikin jin dadi tace "to Daddy na gode" yace "karki damu y'ata abinda kikeso shi zan miki" Alhaji abdurrahim wan mahaifi zee ya kira dad ya kuma nusar dashi illan hanata auren tunda dai ita ta kawo mijin tace tana so, Shiko dad duk da haka bai gamsu da maganar wannashi ba karshe dai saida aka kai ruwa rana ya amince ganin zainab din ta dage kai da fata, itako zee tayi hakane saboda tasan hakan ne kadai mafita a gareta inba hakaba kuma tabbas zata rasa Aslam dinta, abinda kuma zuciyarta bazai gaba dauka ba kanan wato rashin Aslam. Ya kasance weekend yan matan mummy ne zaune a main falon mummy sai fira sukeyi anata shewa kamar yadda suka saba, ko wacce ta sheqa wankanta tayi shiga irinan zaman gida domin shan iska ,dukkansu qananan kaya suka sa amma ba mai bayyana jiki ba, zahra ce kawai ta saka dogon rigar material mara nauyi , safiyace don gama yin breakfast dinsu kenan suka dawo falo suna kallo suna hira, Ya kamal ne yayi sallama a qofar falon tare da shigowa fuskarsa dauke da murmushi kamar ko yaushe ,yasha kwalliya cikin qananan kaya shima sai zuba kamshi yakeyi , kusan hada baki sukayi gurin amsa mishi sallama tare da fara gaishe shi , amsa musu gaisuwar ya shigayi da sakin fuska kamar yadda ya saba musu , zaida kallonshi yayi akan zahra kasancewar yafi d'asawa da ita yace "sisto me zan samu a nan ne na breakfast" ya fada yana shafa cikin shi alamar yunwa, yaci gaba da cewa"wai tea suka sha, ni kuma wlh na gani da tea dinnan " Murmushi zahra tayi tace "aiko ya kamal kai kai taki sa'a yau dan yau Asmah ne ta mana masan nan nata mai shegen dadi da shi muka karya , kuma naga akwai saura bari zubo maka " murmushi kamal yayi jin abinda zahra ta fada sosai yake daukin cin masan badan masa ta dame shi ba saidan jin cewa Asmah ce tayi masan, . ...don wannan karon ya shirya tsab ba gudu ba ja da baya , bazai qara maimaita kuskuren daya , bazai yarda ya sake aikata iri sakacin daya aikata a baya ba, duk da cewa har cikin zuciyarshi baiji dadin abinda Aslam ya aikata mataba , amma shi a ganinshi wata dama ta biyu ne ya sake bashi akanta , kuma bazai yi wasa da damarshi ba , ... Zahra ce ta katsemai tunani ta hanyar ajiye mai filet din masan datayi serving dinshi a gaban shi, kamshin miyan taushen da yaji naman rago, hade da kamshin soyayyen Masan shinkafa ya daki hancinshi lumshe ido yayi tare da budesu akan Asmah sake zaune kushin din dake kallon nashi, filet din Masan ya daga sama yanaci yana Kallonta a fakaice , yana jin wani irin soyayyarta na qara narkar da zuciya, yayinda ita gaba daya hankalinta baya kanshi, yana kan amira da batool daketa musu akan wani Indian series da take haskawa a TV tashar Bollywood... 9:00am dai dai Aslam ya farka daga baccin safen daya koma bayan asubah, miqewa yayi ya shiga toilet yayi wanka , shiryawa yayi cikin jeans da t-shirt baqaqe masu kyau , main falo ya sakko yana shafa cikinsa yana yamutsa fuska alamar yunwa na sakad'arsa, frige ya bude ganin babu wani abun tabawa yasa dole ya fito direct kuma part din mummy ya nufa , daidai lokacin da kamal ke cin masa yayinda yan matan mummy ke zaune suna kallo.... Kuyi manDate: Oct 10, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} page 27 & 28 Gaidashi su zahra suka shiga yi, a daqile yake amsawa ganin haka yasa Asmah qin gaisheshi,...kamal ne ya miqa mishi hannu suyi musabaha da'ker ya mika hannunshi sai wani babbata rai yake, haka kurum yaji yana jin haushin kamal din, ...shiko baima San yana yi ba ci gaba da cin abincinshi yayi, yana yi yana kallon sahibarsa,..... Sake maida kallonshi yayi kan Asmah ganin kowa na gaishe shi ita ta dauke kanta kamar bata ganshi,..gyaran murya yayi "uhummm" dago kai tayi ta sauke idanunta cikin nashi , dukansu saida gabansu ya fadi , ...rabonshi da ganinta tun ranar da yasa mummy ta turo mishi ita part dinsu, gabanin Bikin nan ranar da ya mata warning da wuqa , da idanun shi ya mata alamar kallon fa, dauke kanta tayi daga kallon shi ta mayar kan tv still bata gaishe shiba, a zuciyarta tana cewa "wlh wannan ba Asmah da ka Sani da bace , eheeee wannan wata sabuwar Asmah ce da take daidai da rashin mutuncin ka, wacce kana ce mata kule zata ce maka cassss, don yanzu ba tsoranka nakeji, don duk wani girmanka a idona ka zubar ni kuma nasa qafata na taketa" duk wannan a zuciyarta take fada ,...shiko Aslam mamakinta ne ya kamashi ganin yadda ta dauke kai daga kallon shi kamar taga wani banza, ba wannan rawan jikin da tsoron shi dayake gani kullum a tattare da ita , shi sai yake ganima kamar kallon tsana take jifanshi dashi ma, ...kwafa yayi yana girgiza kai ya nufi dakin mummy ganin bai ganta a falon ba, ,a zuciyarshi kuwa yana aunawa Asmah zagi, mayya kawai mai idon mayu kurwata kur wlh, haka kawai da sassafen nan tasa gabana nata faduwa,.shiga dakin mummy yayi bai ganta ba. falon ya sake dawowa,batool ya kalla tare da cewa "kee mummy fa" da sauri batool ta amsa mai da tana part din daddy , hanyar fita falon yayi tare da ce mata "ki kawo min abinci part dina yanzu" ya fada fuskar nan a murtuke cike da isa, ya fice a falon, bai cewa kowa komai ba, batool ce ta mike cikin zumbura baki ta nufi kitchen, ta hado mai koma da komai a tire ,... Dukkansu basa son zuwa aikensa , saboda sunsan ba,a wanyewa dashi lpy karshenta mutum yasha rankwashi ko mari, yamafi Aiken amira duk cikin su, a cewarshi tafisu hankali da nustuwa ,... Ajiye Tiren batool tayi a kan table din dake tsakiyar falon, murtike fuska tayi exactly yadda Aslam ke murtuke musu fuska , gyara tsayuwarta tayi ta fara irin tafiyan shi, d'akin mummy ta nufa cikin kwaikoyan irin tafiyanshi, duk ido suka bita dashi yuuu suna kallonta, fitowa tayi daga d'akin mummy tana ciccin magani kallon zahra tayi tace "kee mummy fa" tana 'kwai'kwayan muryan shi, aiko gaba d,aya suka kyalkyale da dariya jin yadda ta kaurara murya irin na bosawa wai ita tana kwaikwayan muryan Aslam, itako batool bako alamar murmushi a fuskarta ta dake abinta, qara kallon zahra tayi dake kwasan dariya , ta sake cewa cikin 'kwai'kwayan Aslam "ki kawomin abincina part dina yanzu "ta fada exactly yadda ya fada tana mai fita a falon cikin irin takun shi , amira cikin dariya tace"Allah yasa kina leqawa Ku had'a ido" aiko dai tana leqawa ta hangoshi , Allah yasota ya juya baya bai ganta ba , da gudu ta kwaso ta dawo ciki tana haki tace"wlh amira bakin kai shegen kaifi gare shi "dukkansu qara kwashewa sukayi da dariya zahra tace"yar banza ga tsoro ga mugun aiki" ...."eh din "batool tace tare da kinkiman tiren tayi hanyar waje don kai mai abinci,....kamal daya gama shan dariyar diraman batool ya miqe tare da kallon Asmah yace "sister anjima da yamma zaki rakani shopping , inason inma budurwata shopping , kuma kinga ni bansan kan kayan mata ba ," ya fada yana langwabar da kai yayi fuskan tausayi don kar tace baza taje ba , murmushinta mai narkar mai da zuciya ta sake tare da cewa "to ya kamal Allah ya kaimu anjiman, zan sanar ma mummy inta amince"... Amira tace "Allah sarki ya kamal zanje nima" zahra tace "nima haka ya kamal don Allah" harara wasa wa watsa musu tare da cewa "Allah ya kiyaye wa zai fita da Ku, yara sai shegen rawar kai kaman ana kadaku da ruwan hanji, Ku bari gobe bello ya kai Ku," ya fada yana ficewa a falon don karma su qara hada shi Allah,... Yana fita Asmah ta tashi tana kwaso shoki tana musu gwalo, filon kujera amira ta dauka ta bita dashi, kwasa tayi da gudu hanyar qofa , saiga mummy ta sawo kai saura kadan suyi karo Allah ya kiyaye, ...mummy tace"ya haka amira mekefaruwa "langwabe kai amira tayi tana turo baki cikin shagwaba tace "mummy gwalo fa take mana " mummy tace"gwalo akan me" zahra ce ta labartawa mummy abinda ya faru,... gwalesu mummy tayi da cewa "aikam dai kamal yana da gaskiya, inya kwasheku ai sai kusa aje ata nunashi ana dariya, tsabar rawar kanku gara dai yaje da Asmah don itace ma dan dama dama a cikin ku'...... Da misalin qarfe hudu da rabi yan matan mummy ne dukkan su a cikin makeken dakinsu dake part din mummy , daki ne babba mai dauke da madaidaitan gadaje har guda biyu, iri daya da kuma maka makan wardrobe mai qofa shida shida shima har biyu , da kuma madubi babba guda daya shaqare da kayan kwalliya na mata da turaruka masu tsada kala kala, wannan duk aikin mummy ne,... Komai na dakin pink and milk colour ne idan ka cire fridge da kayan kallo da suka kasance baqaqe, hatta painting dakin pink and milk ne, dakin ya hadu sosai gwanin birgewa ,. .duk da wadan nan kayan dake dakin still akwai space sosai a dakin, domin ba qaramin babban daki bane,dukkan su a kwance suke akan rug carpet kowa na abinada take so batool na karanta novel, amira da zahra na charting a wani WhatsApp group dinsu na yan mata, Asmah kuma da fitowarta kenan a toilet tana tsaye a gaban dressing mirror tana kwalliya ,saboda shopping din da zata raka ya kamal, ...hoda ta shafa tare da zizara kwalli a idanunta , sai maskara data qara ma dogon eyelashes dinta,jambaki ta dauka pink ta shafa kadan akan pink lips dinta , sai gira da tayi amfani da brush na tage gira ta gyara , kallon kyakkyawan fuskarta tayi a madubi, ita karan kanta tasan cewa ita kyakkyawa ce koda kuwa ba Wanda ya taba fada mata hakan , balle kuma tasha jin hakan a bakin daruruwan mutane,...fari tayi da kyawawan idanunta da sukafi komai fusgan mutum idan yana kallonta ,murmushi ta sakarwa kanta tare da cewa "idon mayu",a hankali yadda ita kadai taji meta fad'a, batool ce ta dago ta kalleta jin kamshin turarenta ya cika mata hanci tace"waike malama Ina zakije ne da yamman nan kike wani kwalliya "kasancewar batool bata nan sanda kamal yace zata rakashi shopping yasa bata San da maganar ba , amsa tayi da "zan raka ya kamal shopping ne wai zaije yama budurwa shopping ". miqewa batool tayi zaune tare da cewa "kutumelesi shine bazakice nazo mujeba kiketa shiri ke kadai, bari kiga na watsa ruwa nima muje" ta fada tana shirin miqewa ,Asmah tace "kinga malama koma ki kwanta kici gaba da karata novel dinki, don su O,O ma dazu ba yadda basuyiba zasu yace bazai je da su ba sun fiye rawan kai"ta fad'a tana kallon side d',insu zahra ,Allah yasa basu jitaba , hankalinsu yayi nisa , komawa batool tayi ta kwanta tana cewa "nayi shiru"taci baba da karanta novel dinta ,.....wani dogon rigan atamfa chiganvy mai kyau ta zura, bayan ta saka inner wear dinta , rigan irin mai pocket dinnan da ake yayine ya kamata daga sama daga qasa kumaya bude sosai, wani fashion Dan kunne da abun wuya ta saka, parking din gashinta mai tsayi da laushi baqi sidik tayi, ta kashe daurinta zahra bihari bayan ta saka abin daurin dankwali a ciki ,mayafi golden color ta dauka qaramin kasancewar akwai golden color a jikin atamfar, ta yafa , pos ta dauka mai siririn hannun cen da takalminshi , suma gold color ne sunji Stone sai shining sukeyi ,qara fesa turare tayi a jikinta , sannan tace yan mata sai na dawo mai zan siyo muku, zahra ce ta dago kai ta watsa mata harara taci gaba da chatting dinta , don har yanzu haushi takeji ance baza,aje dasu ba sun fiye rawan kai ,batool ce tace ki siyomin rufaida yoghurt mai banana pls sis, karki damu tace mata tare da ficewa daga dakin ganin call din ya kamal na sake shigowa wayarta....... Zaune suke a compound din gidan a wani Dan rumfar bunu mai dauke da kujeru da table na katako mai kyau, Aslam ne tare da abokinshi Dr bashir , abokin shine tun na yarinta Wanda sukayi karatun boka Dana islamiyya tare a Jami,a suka raba jaha kasancewar shi Dr bashir pharmacy ya karanta shi kuma Aslam ya karanci businesses, Dr bashir baya qasar jiya ya dawo tunda ya tafi karatu qasar waje koda ya gama saiya kama aiki acan yakan zo ganin gida jefi jefi fira sukeyi inda Aslam ke sanar dashi ran Sunday gobe kenan, su Abba zasuje nema masa auren zee, a gurin wan babanta alhaji abdurrahim, kasancewar yasan komai game da soyyanshi da zee din, Zaro ido Dr bashir yayi yace"kace wallahi ". Harara aslam ya watsa masa tare da cewa "kasan na saba maka qarya, ai dole kace na rantse". Dariya dr bashir yayi, tare da cewa"ai abun ne da mamaki, ban taba zaton su Abba zasu sakko da wuri haka ba " tabe baki Aslam yayi tare da cewa" zasu sakko mana tunda wancen kinibabben tsohon yasa baki",Dr bash yace "amma baka da mutunci alhaji baba ne kibabbe" yace "kwarai ma kuwa, ko zaka je ka gayamai ne " bash yace "a,a ni bashi zan gayama ba daddy zan gayama", zaro ido Aslam yayi yace"ka rufamin asiri na samu daddy ya fara amsa gaisuwata da'ker" ...... Dai dai lokacin Asmah ta fito daga part din mummy ,cikin takunta mai Jan hankali , sai zuba kamshi takeyi, direct parking lot ta nufa inda ta hango motar ya kamal , ta bude gefen shi ta shiga tazauna , kamal ne yace "sister barka da yamma " a kunyace ganin ita ya kamata ta fara gaishe tace"yawwa ya kamal , sorry na shanyaka a mota ko, wlh naje yima mummy sallama ne ta aike ni kitchen, shiyasa na dade"murmushi kamal yayi tare da cewa "ba komai sister bari muje yamma naqara yi" ya fada tare da tada motar yayi ribass ya fice daga gidan, Sai lokacin lokacin Dr bash da yayi mutuwar zaune tun fitowar Asmah ya sauke wani wawan ajiyar zuciya tare da juyowa ya kalli Aslam,.... Aslam Wanda kanshi ke duqe yana lallatsa phone dinsh, sai lokacin ya dago kanshi, tun fitowarta daga part din mummy kallon daya ya mata ya dauke kai, ganin ta shiga motar kamal, ta'be baki yayi ya daga kafadunshi alamar I don't care dinnan,, Dr bashi yace"yace Aslam kardai kace min su yan biyu ne suka girma haka " girgiza mai kai yayi yace"no nasu bane". "To amira ce "Dr bash ya sake tambaya "ba ita bace" ya bashi amsa Dr bash ya sake "cewa to wacece wannan mai kyau din". Hade rai Aslam yayi jin Dr bash ya kirata da mai kyau haka kawai ya tsinci zuciyarshi dajin haushin Kalmar, cikin dan hasala yace"kai dalla wani bin kai banza ne wlh,kan wannan qaramar mara kunyan rayinyar duk ka wani rude kanata jeromin tambaya kamar wani sabon dan jarida, maimakon Dr bash yaji haushin ihun da Aslam ya masa , amma sai ya kasa,qara qasa yayi da murya tare da cewa "Aslam Dan Allah wannan din itama yar gidan nan ce" share shi Aslam yayi bai bashi amsaba , murmushi Dr bash yayi yana shafa girjinshi dai dai gefen heart dinshi yace"ta sace zuciyata a gani na farko , kyawunta, nutsuwarta , kamalanta , masu Jan hankali ne ,kuma insha Allah naga matar aure" . qara hada rai Aslam yayi yana watsawa bashir wani banzan kallon,zuciyarshi ta dauke zafi sai tafasa takeyi haka kawai, shi karan kanshi bazaice ga abinda ya tunzira shi ba, cikin bacin rai yace "amma wlh ka bani mamaki kuma kaji kunya bashir " miqewa yayi yana tartare wayoyin shi manya guda biyu dake ajiye kan table din wajen ,juyawa yayi ya nufi hanyar part dinsu, ko qala bai qara cema Dr bash ba, Shima bashir bai damu ba don yasan halin abokin nashi , yanzu haka zaice zai jawo mai raini ne gurin qannen shi , shiyasa ya hasala haka , miqewa yayi ya nufi motar sa ya shige ya bar gidan da qudirin gobe zai dawo ya samu mummy Dan jin wacece wannan mai kyau din,age da wannan yau banda chaji sosai Date: Oct 11, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 29 & 30 Wani babban shopping mall sukaje , shopping sukayi sosai na kayan kwalliya da turaruka masu kyau da tsada , sai kayan kwalama dangin su chocolate, sweet, biscuit,dadai suransu, Juyowa tayi ta kalli ya kamal dake tura mata Dan kwandon da take zuba siyayyarta a ciki, tace "Ya kamal mu barshi haka , wad'an nan ma nasan zasu birgeta. " Kamal yace"kin tabbatar sun isa kuwa" tace "eh" yace "kodai mu hada mata da suttura haka". Tace"eh to saidai ko abaya" ok yace "muje shagon da ake saida abayas din saiki zabar mata".... Kai kayan da suka saya suka yi akayi musu packaging dinshi kamal ya biya suka bar mall din, R.U all store sukaje dake nan kan titin bosso road. Babu kalan abayan da babu a wajen, Har tasa hannu ta fara dubawa dai kuma ta juyo ta kalle shi tace "ya kamal zo ka zabar mata kaga ni bansan size dinta ba , tunda ban taba ganinta ba " Murmushi yayi yace "ki daukar mata size dinki, don inaga a tsayi da jiki zata kaiki" Dan Jim tayi tuna dazuma data tambayeshi colourn skin d'inta dan ta zavar mata mai da powder, cewa yayi ta daukar mata irin wanda take amfani dashi Dan haskensu zaizo daya, yanzu kuma yace size din jikin su daya. Kawar da wannan tunanin tayi tare da zaban wasu ubansun abaya's masu shegen kyau da tsada , kala biyar dai dai jikinta nuna mai tayi yace "sunyi kyau kuma daga gani ba qaramin kyau zasu mata ba" murmushi kawai tayi cewa yayi itama ta dauki abinda take so, girgiza kai tayi tare da cewa"ni babu abinda nakeso saidai naga irin turaren alhaji baba zan daukar mishi " "OK" yace, Turaren ta dauka guda biyu ta daukar ma hajiya mama ma nata,yoghurt da ice cream din rufaida ta daukar musu ita da kawayenta, kamal ya biya suka fito, Daidai parking lot wani mutum da dukkansu suka lura da bibiyarsu da yakeyi tun dazu , ya musu sallama , Amsa mishi sukayi kamal ya miqa mishi hannu sukayi musabaha, tare da tambayarshi lafiya dai ko, Murmushi mutumin yayi yace"lafiyarce ta kawo ni, ni suna na Ali m Ali, inason nayi magana da sisterka ne inba damuwa "hade rai kamal yayi jin abinda Ali m Ali ya fad'a, yace "haba bawan Allah ya daga ganin mutane zaka tsare su haka akan titi baka San ko su waye ba , to wannan da kake gani matar aure ce kuma tare take da mijn ta" . Murmushi Ali yayi yace "Mallam wannan ba matar aure bace kuma kai ba saurayinta bane, don naji da ya kamal take kiranka, don haka nake roqonka ka bani dama numbar wayarta kawai zan amsa , ya fada yana hade hannu alamar roqo🙏 pls ya kamal" Qara hade rai kamal yayi yace "nan ba shine wajen daya dace kayi magana da ita ba, in kana son yin magana da ita gida zakabita," Kallonta tayi yace "muje" ba musu ta bude mota ta shiga ko kallon ali dake binta da mayen kallo batayi ba, kamal ya figi mota da karfi, furkar nan a hade kamar bai taba dariya ba, a zuciyarshi yace "haka kawai yazo ya batamin mood d'ina na farin ciki , a fili kuma yayi tsaki ,Wanda yasa Asmah saurin kallon shi, ganin kamar ransa ya back sosai akan abinda ya faru, yasa tace "kayi hakuri ya kaml wlh nima koda baka wajen bazan kulashi ba, don ni yanzu babu batun soyayya a gabana karatu nake sonyi" Ajiyar zuciya kamal ya sauke tare da cewa cikin sanyin murya "da gaske kikeyi Asmah" gyad'a mai kai kawai tayi alamar eh , maida kanshi yayi yaci gaba da tuqi kamar bazai qara cewa komai ba, sai can ya kira sunanta "Asmah " "naam ya kamal" ta amsa shi , yace "akwai wata magana da nakeso nayi dake in bazaki damu ba" , bai bata daman amsawaba yaci gaba da cewa "amma bansan ya zaki kar'bi batun ba Wanda tuna hakan na matuqar tsinkar min da zuciya, nakan shiga tashin hankali idan na tuna daga ni. sai mahaliccina mukasan halin da zuciyata take ciki a kanki, Asmah zuciyata ta makance ta kurmance bata gani da ji si naki, naso in danne bugatarta har sai kin kammala karatunki na bayyana miki, amma bazan iyaba Asmah ina tsoran abinda ya faru dani a wancen karon ya sake faruwa dani, Wanda na tabbata idan wancen karon na dauki dangana wannan karan zuciyata bazata iya dauka ba, nauyin bakin da nayi a baya yasa na kusa yin babban rashi a rayuwa ta, sai kuma ubangijin taliqai ya sake aramin dama ta biyu akanki " Dai dai lokacin ya parka motar tare da fuskantarta sosai yace "Asma'uu..I love u. ina sonki Asmah ina qaunarki qauna Mara iyaka, don Allah Asmah nima kisoni karkice A'a ya fad'a yana hade hannayenshi alamar roqo🙏🏻" Kamar wawuya haka ta tsaya tana kallonshi, bata taba tsammanin hakan daga gare shi ba , duk da kuwa irin tarin kulawarshi gareta, Ta dauka tausayi da sanin darajar Dan Adam da yake dashine yasa yake bata kulawa fiyye da yadda yake ba qannen shi kulawa , Ashe abin ba anan ya tsaya ba, Tabbas kamal ya cancanci ta soshi domin ya hada duk wani Abu da mace ta gari zataso mijinta ya kasance dasu ta ko ina, saidai bata jin shi a ranta ko kadan, amma duk da haka baza ta taba watsa mai qasa a ido ba, kodan ta quntatawa Aslam kuma ta cika burin kakaninta, zatayi soyayya da kamal kuma ta aure shi, indai har zai iya jiranta ta kammala karatunta Wanda a yanzu shine babban burinta.... Ganin shirunta yayi yawa ne yasa kamal cewa ya bata kwana biyu taje tayi tunani, abinda ta yanke zai saurareta, haka ya tada motar suka qarasa gida,dai dai ana kiran magriba, don haka yana sauketa yayi masallaci bayan ya bada dukkan shopping da sukayi an shigo mata dashi ciki, Koda ta shiga ba kowa a falon qasa don haka dakinsu ta wuce,da lelodin shopping dinta niqi niqi a hannu, Sallah ta taras su zahra nayi don haka itama alwalata dauro ta tada nata sallan. bayan sun idar karatun alkur,ani mai girma sukayi har zuwa isha'i sukayi sallah , nan ta fito musu kayan kwalaman suka ci suka ture, bayan sun gama suka shiga tambayarta dame dame ta zabarma budurwar ya kamal din, shiru ta musu ganin zasu dameta tace musu kanta na ciwo su kyaleta , ganin haka yasa suka kyaleta suka shiga wani hirar daban. Kwanciya tayi bayan ta cire kayanta ta sakana bacci ta fad'a duniyar tunanin gobenta ,a haka bacci ya kwasheta ko abinci bataci ba, tunda sun riga sunyi ciye ciye d'azu. Washe gari Abba da wasu abokan daddy guda biyu sukaje nema ma Aslam auren zainab, saida aka shanya su na kusan awoyi biyu lafiyayyu ba ko ruwa , alhaji badamasi daya daga cikin abokan Abba da bashi da haquri ya fara fad'a yace su tashi su tafi wannan ai wulaqanci ne su ba yan iska bane da za'a a shanyasu kamar wasu marasa aikin yi, Abba ne ya shiga tausar sa da qar ya haqura ya zauna, yana fuffuka , sai fad'i yake a ina Aslam ya had'u da wannan yar gidan marasa mutuncin ne.. Sai chan mom da dad da alhaji abdurrahim suka fito suka zauna, mom ta daura qafa d'aya kan d'aya tana hura hanci bako gaisuwa, shima dad hade rai yayi shi a dole bada son ranshi zai bada yar shiba,alhaji abdurrahim nema, mai Dan dama dama , Su Abba kam sunga ikon Allah yau, tunda suke basu taba gani N wannan lamari ba , amsan gaisuwa harda uwar amarya, Alhaji badamasi da bai bari ta kwana ya dubi mom dake cika tana batsewa yace"madam kidan bamu guri maganar maza da maza zamuyi " dad yayi caraf yace "ku fad'i abin da. zaku fad'a a gabanta ba damuwa, Alhaji badamasi zai qara magana Abba ya dakatar dashi Gabatar da abinda ya kawosu sukayi, na buqatar hada zuri'a da su , Dad sharesu yayi yana daddana waya Alhaji abdurrahim ne ke amsa su , nan dai yace ya basu ya fadi dukiyar aure suka bayar a take , maqudan kudi kuwa bana wasa ba , a nan aka tsayar da lokacin biki nan da wata daya Haka suka taso kowa ranshi a dagule , ba mai bakin magana cikin su kowa da abinda yake saqawa a ranshi .......... Oum ummeetarh 07041130088 Share & comment🙏 Date: Oct 12, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 31 & 32 Gaba daya gidan ba wani mai farin ciki da wannan auren na Aslam, mummy kam ma fakewa tayi da matsayin sa na d'an fari, tace ita ba ruwanta da batun aurensa, su mami ne uwayen shi ita ba d'anta bane, da haka ta zame hannayenta cikin lamarin ta bar su mami da ummi a ciki. Su suka had'a lefe bayan Aslam ya basu card d'inshi, yace su cire ko nawa zai isa, Sunko cire Dan lefe na gani na fad'a suka hada ba algus ko baqin ciki a ciki, Ta bangaren zainab kam shirye shirye sukeyi ba kama hannun yaro, daga ita har iyayen ta abunka da wayayyu yan boko partyn da suka shirya ya kai kala bakwai, don tun ana saura sati d'aya daurin aure zasu fara program, ta nan bangaren ma Aslam ba qaramin kud'i ya sake musu ba , kamar bai San zafinsu ba Shiko anashi bangaren shi kadai yaketa shirye shiryen shi, ya qara qyara gidan shi na London road dan can zasu zauna _ part dinshi ba part din da aka kai Asmah ba. ; Dole ya nemo amir ya bashi hakuri akan abinda ya mishi a wancen lokacin, don yasan duk wani zirga zirga bazai iya shi kadai ba,saida mataimaki, kuma amir d'inne, kadai zai iya tsaya mai yamai komai tsakani da Allah, abinka da 'yan uwa kuma aminai, take amir ya manta da komai na baya suka shiga zirga zirga tare... Yau yan matan mummy suna cike da farin ciki kasancewar admission d'insu ya fito kuma alhmdllh dukansu sun samu abinda suke so, Asmah da batool masscom, zahra da amira pharmacy , duk university daya suka samu babban university na minna, ranar Monday kuma zasuje su fara registration, Zaune suke a d'akin su, suna fira batool tace "biki fa na qaratowa inaga yau saura 2 week fa ;". Zahra ta ta'be tace "nifa ko akaina bana kawo wannan bikin, da ayi da kar ayi duk uwarsu daya". Amira tace"ni Allah yasa ma kafin lokacin mun fara attending class , da ko bani da lecture ranar sai naje school " Asmah tayi murmushi ta fahimci duk wannan abin da sukeyi , sunayi ne don tayata jin haushin wulaqancin da d'an uwansu ya mata ne, tace " duk kallon ku nakeyi ai wlh baku isa ba, bikin ya Aslam sukutum kuce wani ba ruwanku da shi , harda me cewa zata je school ranan ko, akan me to na fahimci ni kuke tayawa jin haushi ko , to wlh na yafe , aini wannan abinda da ya faru gaba ta kaini , ba gashi yanzu xanyi karatuna hankali kwance ba, da bai sakeni ba da yanzu inacan Allah kadai yasan halin da nake ciki" ai ni in kuna sona da gaske har haka kamata yayi ku taya ni murna, don haka ku manta da wannan caftar ku dauka kamar ba'abayi ba, har ankon yini dana dinner na zabar mana a wurin anty ummi,wani atamfa da wani material na gani a status dinta masu kyau sababbin shigowa , anjima bello zai karbo mana gobe sai mu mukai dinki daga nan mu biya gidan ya rabi'ah. Haka ko akayi washe gari tunda safe bello yaje gidan anty ummi a unguwan darussalm ya amso musu atamfar da material din da Asmah ta zabar musu a matsayin ankon bikin, mummy ce ta biya musu kudin kayan da kyar don da tace ba wani ankon da zasuyi saida suka ta roqonta ta amince, Wuraren sha daya da rabi suka cikin shirinsu na zuwa kai d'inki daga nan kuma zasuje gidan ya rabi'ah, kamar yadda suka tsara. part din mummy suka biya don gaisheta kamar yadda suka saba kullum, mami bata falo tana ciki don haka suka nemi guri a falon suka zauna jiranta, zamansu ba jimawa mami ta fito cikin shirin fita anguwa, ganinsu yasa ta fadada fara'arta, nan suka shiga gaisheta tana amsawa cikin kulawa Mami tace"sai ina kuma haka naga anci wannan kwalliya ". Zahra ne ta amsa"mami zamuje mukai dinki ankon mu ne daga nan zamu biya gidan ya rabi'ah kullum complain take mana bama son zuwa gidan ta " mami tace"lallai yaran mummy kunaji da wannan yayar taku harda wani anko kukayi" Batool tace "eh mami Asmah ce ma ta nace sai munyi ankon, itace ma ta zabar mana atamfar ta yini data dinner ' mami ta kalli Asmah tana mata hararan wasa tace"wato shine mu baza'a nuna mana ankon bako" a ranta kuma tana mamakin sauqin hali irin na Asmah , ace duk wannan wulaqancin da Aslam ya mata har tana wani fitar da anko dan zaiyi aure" Asmah ce ta katse mata tunaninta da cewa "mami AI ankon fa na yan mata ne ba naku bane " mami tace "ba namu ba mu suwa". Asmah tace "tsofaffi mana". Mami ta zaro ido tare da cewa "ja'ira nice tsohuwa ". Dukkansu dariya suka sa mata , inda suka tashi suna cewa mami sai mun dawo , tace"to Allah ya tsare, ku gaida min da Rabin da wannan mummunan yarinyar nata mai kwace miji " Asmah da zahra suka amsa mata da to mami, batool tace" kai mami kodai kina kishi ne ta fiki kyau, ta kwace miki miji " mami tace wanna beran tama isa ta kwace min miji ne da wani hancinta kamar Biro, dariya suka saka suna fita falon tare da ce mata mami sai mun dawo. Asmah ce gaba suna fitowan part din mummy suna kwasan dariyan da mami ta basu hankalinta , kwata kwata baya kan kofar sai ji kawai tayi ta gwabza karo da mutum, da sauri tayi baya tana riqe goshinta tare da cewa wasshh subhanallah... Shima Aslam dan baya yaja don ganin da wa yayi karo haka, idanunsu ya sarqe cikin na juna , da sauri ta dauke kanta daga kallon shi tare da furta "sorry " a hankali yadda bama lallai yaji ba, amma yajin, Suma su batool dake binta a baya ganin abinda ya faru , yasa suka shiga firgici da tsoro duk a tunaninsu mari zai kai mata kamar yadda ya saba marin ta a baya. Amma sai sukaga akasin hakan, Bi tayi ta gefenshi ta wuce suma ganin haka yasa da sauri suka bi bayanta. Mota suka shiga bello yajasu suka bar compound din gidan, A tsaye yake a inda ta barshi ko qafanshi ya qasa dagawa daga wajen, tunda idanun su ya sarqe da juna ya tsinci kanshi cikin wani yanayi mai wuyan fassaruwa ga kuma faduwan gaban da muddin zai hadu da ita sai ya tsinci kanshi acikin shi, ya tasar mai wannan dalinlin yasa yake kiranta mayya, yoo imba maita ba ace kullum idan ka hada ido da mutum sai faduwan gaba, abinda ya bashi mamaki har yasa ya kasa motsawa kuwa ba komai bane sai ganin yadda yarinyar ta canza gaba daya ,a lokaci daya, ya tabbata inda Dane yadda sukayi karonnan da tuni ta zube a kasa tana kuka tana bashi haquri cike da tsoran shi, amma yanzu ji yadda ta kalle shi a wulaqnce tace mishi wani sorry ta gifta shi ta wuce ba wani damuwa a tare da ita , qwafa yayi ganin mami ta fito.ganin shi nan tsaye yasa tace "yawwa Aslam muje ko" shima sausauta fuskar shi yayi tare da cewa "to mami " , parking lot suka nufa suka shiga mota ko ina zasu ohoo..... Wani babban shagon dinki inda suka kai dinki sukaje, bada dinku nan sukayi telan ya nuna musu style a wayanshi suka zazzaba sanna suka bashi rabin kudin dinkin suka fito, direct gidan ya rabi'ah bello ya kaisu inda ya barsu said a yamma zai koma ya daukosu...... Sun tarad da ya rabi'ah tana tsaka da aiki kace kace , abokin mijinta barrister Adam zaizo kuma ba qaramin ji dashi mijin ta keyiba don abokin shi ne tun na yarinta, a secondary school suka hadu Wanda yake boarding ne , Allah ya hada jininsu shikenan abota mai karfi ya qullu a tsakanin su , Wanda ya kaiga har iyayen su suma suka zama abokai sanadiyar su. Barrister Adam ba yaro bane don a kalla zaikai shekara arba'in da biyar ko hamsin, amma abinka da dan gayu dan boko , ba kowa ke gane ya kai wadannan shekarun ba zaka dauka baifi 35 zuwa 38 ba yanada mata daya maryam da yaya hudu, banufen bidda ne iyayen shi gaba da baya nufawa ne amma kuma wayyayyun yan book ne,. Kama mata aikin sukayi nan da nan kuwa suka kammala, daidai lokacin kuma uncle nura mijinta ya kira waya yace mata barrister Adam din ya iso, ta kawo mishi abin mosta baki daganan su gaisa, yana falon baqi, OK tace mishi tana ajiye wayar, ta kalle su tace" kunji ba wai ya iso yana falon abban hanifa gashi ni kuma ko wanka banyi ba sai warin kitchen nakeyi". Zahra tace "to yaya ki kai mishi abin motsa baki daga nan ki gaishe shi , sai kizo kiyi wanka ki koma ' shiru tayi alamar tunani sai kuma tace" no zahra ba haka za'ayi , barin had,a miki abin tabawan a tire kije ki kai mishi, ni kuma nayi wankan sai inje mu gaisa " OK kawai zahra tace mata,... Kitchen ta shiga ta hado komai data shirya domin taran barrister Adam a tire ta miqawa zahra tace takai palon Abba hanifa ita kuma ta shigab room dinta donyin wanka, .. Tiren zahra ta dauka ta nufi falon uncle nura da sallama a bakin ta kutsa kai cikin falon, dagawo dukkan su sukayi suna kallonta tare da amsa mata sallamarta , A hankali cikin nitsuwa ta qarasa stakiyar falon ta jawo wani dan table dake gefen kushin ta daura tiren akai ta dan matso dashi gaban gaban Barr Adam , dagowa tayi fuskanta sake tace "ya nura ina wuni" Abba hanifa ya amsa da "lpy qlau , yau yan biyun mummy ne agidan namu"murmushi yayi tace "eh yau mun kawu muku ziyara' yace "to madalla munko gode, ina sauran yan'uwanki"tace "suna ciki"yace "ok" juyowa tayi ta kalli barrister Adam da tun shigowarta ya kamata da ido baiko qeftawa tace "ina wuni " shiru yayi don baima jitaba , hankalinshi yayi nisa , gashi dai yana kallonta amma baijita ba said a abban hanifa yace "barrister ana gaishe ka " dan firgigit yayi yace "oh sister ya kike "tace "lpya qlau ya hanya "yace "alhamdulillahi mun sameku lfy tace "lpy qlau " yace"masha Allah"... Miqewa tayi ta fice daga falon , da kallo barrister Adam ya rakata harta qurema ganin shi , saida abban hanifa yayi gyaran murya , sannan ya juyo da sauri ya kalle shi, d'age mai gira daya Abba hanifa yayi tare da cewa "yane" ajiyar zuciya barrister Adam yayi tare da cewa"finally yau Allah ya hada ni da ita , a cikin garin minna " Abban hanifa yace "ita wa kenan" "Amaryata da naketa mafarkin na aura"abban hanifa yace"bangane amaryanka ta mafarki ba me kake nufi"barrister Adam yace"kona maka bayani yanzu bazaka taba ganewa ba, yanzu dai bari na tambayeka don Allah ". Abban hanifa yace "ina saurarenka ". Kasa yayi da murya kamar wani zai jisu yace "wannan beautiful young lady dinnan da ta fita yanzu wacece ita" murmushi abban hanifa yayi don ya gano abokin nashi kamar ya zurma yace "kanwar madam ce yan biyu ne ma suke bi mata a haihuwa" barristers Adam yace" wonderful Ashe shiyasa yau tunda na tashibacci naji kamar magnet na Jana zuwa minna a she abinda zan samu babba ne"abban hanifa yace"kamar yaya banfa gane abinda kake nufi ba Mallam" barrister Adam yace "ina nufin ina sonta, ina son aurenta, inason ta zama matata kuma amaryata " bata rai Abban hanifa yayi na wasa yace "kaga Mallam ayi haka dani ba kaima kasan nida maryam 5&6ne bazan bada goyan bayan a mata kishiya ba", Barr Adam kai dai ka Sani tunda ka fara wannan maganar nasan bazakamin abin arziki ba don haka ta hannun rabi'ah zan bi, "oho nidai ba ruwana kaida maryam,". Yace" eh din dama Vance da ruwanka ba ai" Ranar su Asmah a gidan ya rabi'ah suka wuni sai magrin bello yazo ya daukesu. Washe gari Monday suka fara shiga school don fara yin registration dinsu......... Finally zahra ma ta samu nata rabon💃💃💃💃💃💃💃 Date: Oct 13, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanna book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 33 & 34 A kwana a tashi ba wuya yau gashi saura kwana uku daurin auren Aslam da zee , tun ranar Monday aka fara program ba kama hannun yaro , Ta bangaren zee biki akeyi gagarumi yayinda ta bangaren Aslam abin dai gashi nan kadaran kada han, don mummy ma cewa tayi bazata gaiyace kowa ba,yoo ta gayyaci mutane ta ce musu me , bayan ko wata uku ba'a rufa ba data gayyato su bikin Aslam, yanzu kuma ta sake ce musu suzo bikin Aslam again, gsky baza ta iyaba. Biki dai ba wani bare daya zo duka dai yan gida ne wadan da zuwa bikin ya zame ma dole, Yau ne akayi kumbo kuma yaune ango ya fara halartan program daya daga cikin ukun daya zaba zaije, A babban hole din dake mai jama'a hotel akayi 4:pm aka fara aka tash70:pm, daga dangin ango kam ba wanda yaje. Sai shi kadai da abokansa sai ko kamal, su zahra dama sukayi niyyan zuwa kuma mummy tace bazasuje ba, haka suka haqura, Misalin qarfe takwas da rabi na dare, Aslam ne da wasu daga cikin abokan shi zaune a palon shi suna fira, su niyara ne Aslam, amir, Dr bash, sai wasu baqin fuska su biyu, Fira sukeyi suna dan rahan su irinta abokai suna dariya, kamal ne yayi sallama ya shigo , ganin su a palon yasa shima ya zauna akaci gaba da hiran da shi , Amir ya dubi Dr bash yace"bash kasan ni ban iya boye, boye ba arayuwa ko mutum zaiji haushi na saina fadi abinda ke raina" Dr bash yace"kwata kuwa nasan da haka " amir yace "a gaskiya ina taya abokina kuma dan uwana jaje" duka sauran abokan nasu da shi kan shi Aslam din maida hankali sukayi kan shi don jin me zai fada,Dr bash yace "jajen mefa" amir yace "na rashin kyakkyawa kuma natsatsiyar yarinya kamar Asmah mana" hade rai Aslam yayi ganin amir na naman yaci mai mutunci, bash dake kunshe dariyar shi ganin yadda lokaci daya fuskar Aslam din ta koma, yace, "amir me kake nufi kana nufin kace ita zainab bats da kyau da nastuwa ne " amir yace"a a nifa bance ba ta da nutsuwa ba tanada nutsuwarta dai dai gwargwado, amma batun kyau kam abarshi, mace a tsaye sambal sai kace bigun katako " dariya sauran abokan suka saka, anas yace "gaskiya amir baka da mutunci wlh". Aslam kam qara hade fuska yayi tamau iya kunnuwa kuwa ya kunnu sosai , ji yake kamar ya tashi ya rude amir da duka, amma ya fuska ya qyaleshi, Amir ya amsa ma Anas da cewa "nida shi wayafi wani rashinmutunci , ai tunda ya wulagantamin qanwa akan wannan figaggiyar yarinyar mai zubin tabarya , wlh daga shi har ita sun shiga uku dani, kuma wlh asaran shi don nayi imanin bazai taba samun kamar taba balle wacce ta fita, tun yanzu AI gashi nan Allah ya fara kamashi, kaga bashir na daya Asmah akwai natsuwa, hankali, ladabi, biyayya kunya , ilimin addini Dana book tarbiya, uwa uba gata da wani irin kyau mai fisgar duk wani lafiyayyen namiji, asalin figure 8 nake gaya maka mallam, komai yaji " miqa mai hannu bash yayi suka fata suna dariya , yaci gaba da cewa "wlh badadon nayima kaina wani tanadaiba da ba abinda zai hanani yin wuff da ita kuma ko yanzu ma bata baci ba " a fusace Aslam ya miqe kamar wani mayunwacin zaki ya kaima amir wawura, amir da tun dazu yake ankare da Aslam din sanin da yayi hakan zai iya faruwa, yayi wuff ya miqe yayi hanyar qofa, tsayawa Aslam yayi yana huci ganin bai samu nasaran damqarsaba yace"banza dan iska kawai" juyawa yayi ya wuce sama fuuuu daki ya shiga ya buga kofa da qarfi ji kake bamm, don ranshi ba qaramin baci yayi ba inyace zai tsaya yin magana lokacin bazai fadi alheri ba, Amir daya gama tikar dariya ,ya dubi su bashir yace ku tashi na rakaku ku tafi, yayi qwafa tare da cewa "ai wlh dani kake zance Aslam duk wula qancin da kamin a lokacin wancen bikin saina rama" tashi sukayi suka fice suka bar kamal shi kadai, Kamal da yayi mutuwar ...... Manage pls Date: Oct 14, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanna book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page35 & 36 Kamal da yayi mutuwar zaune tun lokacin da amir ya fara magana akan Asma'unshi, jiki ba kwari ya miqe ya shige room d'inshi, ba abinda yafi tsaya mai arai irin cewa da amir yayi , (wlh bada don nayiwa kaina wani tanadi ba. da ba abinda zai hana nayi wuff da ita kuma ko yanzu ma bata baci ba") ya maimaita wannan kalman a fili da zuciyarshi yafi sau hamsin Me hakan ke nufi karfa ya tsaya sanya ya sake rasa Asmah a karo na biyu , karfa yayi saken da zai kuma rasa second Chance d'inshi, Tunawa yayi har yanzu fa Asmah bata bashi gamsasshiyar amsa game da maganar su ta rannan ba , a fili ya furta "ya zama dole ki bani amsata a gobe goben nan, ya zama dole nasan matsayi na a gareki, ya zama dole manyan mu Susan da maganar nan, Susan da zamana kar na zauna kallon ruwa kwado yamun qafa, a haka ya kwanta barci yanata tuna ni da'ker bacci barawo ya dauke shi... Asmah anata bangaren ta riga ta gama shawara tsakanin ta da zuciyarta , ta karbi soyayyar ya kamal da hannu bibbiyu ko dan kyauta tawanshi gareta, ina laifin masoyinka. Ita kam dai ta amince da kamal indai har zai mata alfarmar barinta tayi karatun ta lpy ba tare da manya sunsan da maganar ba , Washe gari ummi ta iso daga abuja ita da yan biyun ta maza kannan amir, wadan da qanana ne baza su wuce shekara takwas ba, don bayan haihuwar amir ta dade kafin ta sake haihuwa har an cire rai ma, ta sauka a d'akinta dake part din hajiya mama Wanda in tazo anan take sauka , yau yan matan mummy ummin su tazo, suna can part din hajiya mama acan suka wuni sai surutu suke zuba mata , ita kuma tana biye musu taji mastalolinsu, tana basu shawarwari inna bada shawaran ne , don tun basu kai haka ba ta basu wannna daman na duk abinda ke damun susanar mata , kar su yarda su sanar ma wani a waje damuwarasu,ta jasu a jiki sosai ta maida su tamkar qawayenta, Ranar yan matan mummy part din hajiya mama suka wuni kwana ne kawai basuyi can ba , don sai wuraren goma suka dawo part dinsu lokacin na mummy na sashen daddy,don haka dakinsu suka wuce suka kwanta sai bacci. Washe gari juma'a ma haka suka tashi cikin hada hada don gida yadan cika, duk da ba'ayi gayyata ba saida mutane suka zo, Zahra da Asmah sallama suka wa mummy zasuje amso dinkin su don tailorn ya kirasu ya gama , su biyu zasuje don amira da batool na sashen mami suna taya ta wasu aiyukan, cikon kud'in d'inkin mummy ta basu suka nufo parking lot da niyyar bello ya kaisu, nan suka tarar bello naya nan wai Aslam ya aike shi , juyawa sukayi da niyyar komawa ciki su jira shi, mai gadi ya wangale get motar yaya kamal ya kunno kai cikin gidan , zahra na ganin shi ta fara murna tace "yawwa ga ya kamal nan ma bar in roqeshi ya kaimu" Asmah dai shiru ta mata, da sauri zahra ta nufi motar kamal daya paker ko fitowa bai kaigayi ba , ta window tadan duqa tace "sannu da dawowa ya kamal " d'agowa yayi jin magana ta window ganin zahra ce yasa shi sakin murmushi sannan yace"yawwa zahra'u ya gida ". tace "lpy qlau, don Allah ya kamal ka kaimu tunga road mu amso dinkin mu na biki da zamusa gobe , munzo bello ya kaimu wai baya nan ya Aslam ya aikeshi" kamal yace "kai zahra na gaji fah bakiga dawowa na kenan daga gurin aiki ba gashi lokacin masallaci ya kusa "marairaice fuska tayi tace "don Allah ya kamal, tana hade hannayenta alamar roqo🙏, dagowa yayi ya kalleta ganin yadda ta marairaice yace"dondai kece fa sis zahra, da batool ce da ba inda zanje, shiga muje na kaiki"tsallen murna tayi tana jin dadi tace "nida Asmah ne " daga murya tayi tace "Asmah zo muje ya kamal ya kaimu" bude gaban mota tayi ta shiga ,Asmah tazo ta bude baya itama ta zauna sannan tace "sannu da dawowa ya kamal ya aiki" ta cikin madubi ya kalleta kafin ya amsa mata da "lpy qlau my Asmah" Rivas yayi da motar mai gadi ya bude musu get suka fice daga gidan, Kamal ta cikin madubi yake Satan kallon Asmah dake zaune a bayan mota duk d'agowan da zatayi kuwa sai sun hada ido Dai dai zasuhau kan babban titin da zai kaisu tunga road suka gifta motar Dr bash, shida Aslam da amir ne acikin motar, zasuje gida ne donyin shirin sallan juma'a, kasancewar motar Dr bash mai duhun gilashi ne , kuma basu San motar shi ba balle Susan ko sune aciki, suko su Amir rass suka gane su,sboda dukkan su sunsan motar kamal kuma glass d'inshi fari ne ana iya ganin na cikin motar, Bash dake tuqi ya kalli Amir dake gefen shi yace "wai dan Allah Amir na tambayeka mana" Amir yace"inajinka Allah yasa na sani" bash yace "yammatan da na gani a motar kamal yanzu su waye" Amir yace" meyasa kake tambaya " bash yace "kaga wannan na bayan motar" Amir yace "eh Asmah kenan" Dr bash yace "tun ranar dana fara ganinta washe garin ranar dana dawo 9ja wlh zuciyata ta kamu da sonta ko baccin kirki bana iyayi saboda tinaninta, amma kullum nama Aslam maganar ta saiya shareni kokuma yace min shi bai ganeta ba, alhali ranar muna tare na fara ganinta ta fito daga part din mummy" Amir ya juyo ya kalli Dr bash yace"da gaske kakeyi bashir " bash yace "na taba maka irin wasan nan ne"Amir yace"aiko zan shige maka gaba indai da gaske kake don wlh yarinyace na tsattsatsiya mai hankali, duk Wanda ya samu daman aurenta kuma ya saki yayi babban asara," ya qarashe maganar yana kallon Aslam ta madubi, bash yace"to wacece ita a gare ku". Amir yace "kanwarmu ce, jikan alhaji Mallam cefa ba kasan shi ba babban malamin nan aminin alhaji baba, kasan shi ai" bash yace "sani kai, da muna yara har kwana na tabayi a gidan shi da mukaje da Aslam ruwan sama ya tare mu sai muka kwana, tsohon kirkine wlh" Amir yace " to jikan shice ta wurin danshi na fari alhaji aminu mai rasuwa. marainiyace iyayenta sun rasu tun tana qarama a gidanmu ta tashi, sunanta Asma'u". Bash yace "Allah sarki Allah ya jiqansu, to ita wacce ta zauna a front sit dinnan fa" Amir yace yan biyu ne fa baka ganeta bane zahra ce fa". bash yace "haba don Allah" amir yace "Allah kuwa" bash yace "eh lallai girman mace ba wuya yan biyu ne suka girma haka , Allah mai iko, to amira fa?' bash ya sake tambaya murmushi Amir ya sake ganin an ambaci sanyin idayanshi yace"tana nan lpy itama ta zama ammata, ko Aslam,?" Ya fada yana dan juyowa ya kalli Aslam , Aslam da tun dazu ranshi ke tafasa jin abinda suke fad'a ya watsawa Amir mugun kallo ya dauke kai, ranshi in yayi dubu ya baci, kwata kwata a rayuwarsa baya son raini da qasakanci, amma ya lura bash da Amir suna Neman ja mishi raini a gurin qananan yaran daya goya a bayan shi, yaran da yake kallo har yanzu a mastayin jarirai, daidai lokacin mai gadi ya bude musu get suka shiga gidan don yin shirin masallaci..... Har qofar shagon dinkin kamal ya kaisu, ya kuma biya cikon kudin dinkin, basu wani tsattsaya ba ,suka dawo gida domin lokacin sallah ya kusa, kamal dimma inbaiyi sauri ba da'ker ya samu sallah, Don haka yana sauke su zahra ta dauki ledan kayan ta fara yin gaban ,tana cewa"ya kamal mun gode Allah ya saka maka da alheri,' ta shige ciki, Asmah ma godiya ta masa ita ma, ta fito zata wuce tanama zahra qorafin bata jirata ba, Kamal ya kira sunanta , juyowa tayi ta sauke mishi wadannan dara darn idanun nata daya sashi jin wani yarrr ajikin shi ,murmushi ya sakar mata tare da cewa " I hope kin gama tunanin ko", shiru tayi , yace "well ki shirya anjima zanzo naji amsata " gyada mai kai kawai tayi , yace "OK barin je masallaci saina dawo ' to kawai tace mishi tayi gaba, shima motar ya koma yayi Rivas ya fice daga gidan don zuwa masallaci....... Oum ummeetarh 07041130088 Share and comment fi sabilillah🙏 Date: Oct 15, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rada mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 37 & 38 Itama Asmah direct sashen mummy ta wuce, a falo ta samu su zahra da ummi da yan biyu sai bude dinkunan sukeyi suna kallo, kowacce ta dauki nata, tana gaisar da ummi batabi takan su batool ba ta upstairs ta hau direct ta wuce dakinsu, ruwa ta watsa ta dauro alwala daya daga cikin abayan da ya kamal ya sai mata ta dauki wani maroon color mai shegen kyau yaji tsone ta ko ina,ta saka abinka da farar fata ba qaramin kyau ya mata ba, sallan azahar tayi tana idarwa, ko abinci bata nema ba ta hau gado ta kwanta, tana tunani a haka bacci ya kwasheta.... Ummi jin shiru Asmah bata sauko ba yasa tace Alhasan yaje ya kirata,tazo ta duba nata dinkin, Dawowa Alhasan yayi yace"tana bacci". Ummi tace "ikon Allah bacci kuma, jiya fa bakuyi bacci da wuri ba" Haka sukaita sabgoginsu a falon mummy saida aka kira la'asar zahra ta haura sama donyin sallah, Su kuma su amira suka bi Ummi part din hajiya mama, . Har lokacin bacci Asmah keyi, alwala zahra ta dauro ta gabatar da sallan la'asar, saida ta idar ta tashi Asmah, ganin batada niyyar motsawa, Tana falkawa taga zahra tace "subhanallahi bacci nayi ashe" zahra tace"eh gashi har an idar da la'asar ". Da sauri ta miqe ta shiga toilet ta d'auro alwala, pray mat din da zahra ke nilkewa ta amsa ta shimfida ta gabatar da sallah, koda ta idar zahra bata d'akin, don haka itama ita saukowa qasa tayi, falo ta samesu yanzu harda mummy da wasu daga cikin dangi, Gaishe su tayi ta wuce dining don tafara jin cikinta na kiran ciroma, abinci ta zuba kadan taci, ta tashi daga dining din ta dawo falo akaci gaba da hira da ita, Hanifa ce ta shigo falon mummy. Da dan tsalle tsallenta na yara, don hanifa kwata kwata batafi shekaru hudu ba , direct gun Asmah ta nufa ta fada jikinta tare da cewa"Anty Acmah wai kijo inji Uncle kamay" gabanta ya fadi tunawa da tayi dazu yace zaizo yaji amsarsa, amma ta dake tace "yana inane Uncle kamay din" ta fada cikin kwiykwayon muryar hanifa mai tsami, "yaya garden " hanifa tace , dan lakace hancinta Asmah tayi tace"oya kije kice masa ina zuwa" tom" hanifa tace kafin ta zura da gudu ta fice , mummy na kiranta ko amsawa batayi ba balle ta juyo, Ten minute ta qara zaune a falon, kafin ta tashi ta haura sama , d'akinsu ta shiga gaban mirror ta tsaya , ta dauki turarenta mai sanyin kamshi ta fesa kad'an, kwalli ta zizara a fararen idanunta masu sheqi sai man lebe data shafa mai d'anqo, mayafin abayan jikinta ta dauka tayi rolling dinshi, ba qaramin kyau tayi ba farin kyakkyawan fuskarta sai shining yake, wayarta ta dauka tare da zura wani plat shoe mai kyau ta sauko falon, kusa da mummy take tadan rusuna dai dai kunnenta tace ," mumyy wai ya kamal na kira na " "ok" Mummy tace mata , don haka ta nufi hanyar fita palon, batool ne tace "sister sai ina" alamar tana zuwa ta mata da hannu ta fice daga palon, Hanyar garden ta nufa cikin takunta na natsuwa, garden din yana cen ta bayan gidan ne, don haka sai an wuce part din su Aslam dake farkon gidan kafin a isa garden din, Dai dai ta gifta kofar part din shi kuma Aslam ya fito don ya amsa call, kasancewar falon cike yake da abokanan shi, hayaniya yayi yawa, Ita bata ganshi ba amma shi ya ganta kuma ya gane itace kasancewar yaga gefen fuskarta datazo giftawa, Samun kanshi yayi da tambayar kanshi ina kuma wannan yarinyar zata je?, ba mai bashi wannan amsar Haka kawai ya samu kanshi da bin bayanta a hankali yanda bazata ganshi ba, gani yayi ta nufi garden ta bud'e dan guntun get din wurin ta shiga, ci gaba da binta yayi ba tare da ya bari ta sani ba, Tana shiga ta hango ya kamal zaune akan wani shimfidadden kafet mai laushi, zaune yake yana facing cage na tsuntsayen kanari kala kala sai shawagin suke yi gwanin sha'awa, hankalinshi gaba d'aya ya raja'a akansu. Qarasawa tayi tare da yimai sallama, juyowa yayi kyakkyawann fuskarshi dauke da murmushi yana amsa mata Sai a lokacin Aslam dake la'be yaga ahse kamal ne don da baiga fuskarshi ba kasancewar ya juya baya, gani yayi kamal din ya nuna mata gefen shi yace ta zauna, zaman kuwa yaga tayi dan nesa kadan da kamal d'in,itama tana facing cage din, Samun kanshi yayi da jin haushin ganin su haka da yayi, a zuciyarshi yace yadda suka zauna dan Allah sai kace wani miji da mata kokuma budurwa da saurayi,tsaki tsaki yaja a fili , wata zuciyar ce ta kwa'be da cewa to kai ina ruwanka, tsaki ya kuma ja ya juya zai wuce, Saidai kuma me! Samun kanshi yayi da son jin abinda zasu fad'a, Kamar Wanda ake controlling dinshi da remote haka yake bin umarnin zuciyarshi, Samun kanshi yayi da qarasawa cikin garden din sad'af sad'af. Yadda baxasuji takun step d'inshi ba. Gurin ya samu dan nesa dasu yadda zai iyajin abinda suke fada ya zauna , kasancewar sun juya mai baya yasa basu ganshi ba, shiko hakan yamai dai dai,waya ya dauko ya qara a kunnenshi kamar yana amsa call nan ko dukkan hankalinshi na Kansu , yayi hakane koda zasu juyo su ganshi sai yayi pretending.. Kamal ya juyo ya kalli Asmah yace" my Asmah" barka da juma'a, dan boye fuskarta tayi tana murmushi alamar taji kunyar sunan da ya kirata dashi, shima murmushi yayi mai sauti yace "yau kuma kunyata kikeji ne,". Still batace komai ba, ya qara cewa "to shikenan ina jinki, bani amsata" shiru tayi kanta na qasa bata ce komai ba, kamal ganin shurun nason yayi yawa ne yace"ke nake saurare my Asmah" Dagowa tayi ta kalleshi shima din ita yake kallo, idanu suka had'a tare da sakar ma juna murmushi , saurin kauda kanta gefe tayi, sannan a hankali kamar mai ciwon baki tace"na amince da soyayyarka ya kamal Allah ya shige mana gaba,'. Tana gama fadin haka ta saka kanta cikin qafafunta ta 'boye fuskarta, alamar kunya, Aslam dake zaune a bayan su, da sauri ya dago kanshi yana kallonsu jin abinda Asmah ta fada What!!! Soyayya, gaban shine ya shigafaduwa, hankalinshi ya tashi, tsoro da firgicine suka ziyarceshi a lokaci daya, Shi karan kanshi baisan dalilin shi na shiga wannan yanyinba daga jin wannan maganar, Kamal ko jin amsar data bashi wani irin farin ciki ne ya lullu'beshi, juyowa yayi ya kalleta fuskarshi cike da farin ciki yace "da gaske kike my Asmah". Kanta dake cikin cinyoyinta ta girgiza mai alamar eh, Hannu ya daga sama yace "Allah na gode maka da kasa wannan baiwa taka ta amince da soyayyata cikin sauqi, ya Allah ka mallakamin ita cikin sauqi,". Sauke hannayenshi yayi ya juyo ya kalleta yace"nagode my Asmah kuma na mika alqawrin insha Allah zaki sameni miji daya tamkar dubu" Dago kai tayi ta marairaice fuska tace"sai dai ina buqatar wani alfarma a gare ka ya kamal" yace "yace wani irin alfarma kike nema " tace "so nake maganar soyayyan mu ta zama sirri tsakanin nida kai, banason kowa ya sani har sai na kammala karatuna," yace "saboda me" tace "saboda bana son na rasa daman yin karatu a karo na biyu, domin muddin alhaji Mallam yaji wannan maganar nasan bazai barni nayi karatu ba , aure zaimin kuma banaso" ajiyar zuciya kamal ya sauke yace "karki damu indai don wannan ne bazan sanar ma kowa ba, nima bana son ayi auren yanzu sai mun qara fahimtar juna, kafin nan kin kammala karatun ki". , d'ad'ine ya lunlu'beta, jin y amince da maganar ta. Aslam sad'af sad'af ya tashi ya fice daga garden d'in yana hard'e hanya, Idan ya fahimci inda maganganunsu ya dosa , kenan soyayyace suka kulla a tsakanin su Kai! Ina! Hakan bazai taba faruwa ba , wannan ai cin amana ne, kamal yake son yamai, bai taba tunanin kamal xai mai haka ba , yarasa dawa zaiyi soyayya saida ex wife dinshi, Lallai baiga ta zama ba , bazai taba barin hakan ta faru ba , to ta haramta ga duk wani d'a namiji indai jininsa ne, taje can ta nemi mijinta a wani familyn badai nasu ba Da wannan tunanin ya qarasa part d'insu, inda ya taradda abokanan nata firansu kamar yadda ya fita ya barsu..... Guri ya samu ya zauna yana saurarensu baicewa kowa komai ba,jikinshi duk a sanyaye, su karan Kansu abokan sun lura da sauyin da ya samu yanzu yanzu daga fita amsa call, Asmah kam kimanin awa d'aya suka dauka suna firan su kafin suyi sallama ta koma cikin gida........ Jama'a gobe daurin auren Aslam dinku da zee his luv 🤏😎 general invite to all readers of dama ta biyu💖. Kudai ku biyoni muje yanzu wasan zai fara, Much luv 🥰🥰🥰to all masoyan dama ta biyu, ina jin dadin comment dinku👍🥳 Oum ummeetarh 0704 1130088 Date: Oct 16, 2022 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 39 & 40 A haka wunin ranar ya qare jikin Aslam a sanyaye minti kadan tunanin kamal da Asmah ya fadomai a rai, minti kadan hoton su lokacin da suka sakar ma juna murmushi ya fado mai a rai, da'ker ya samu ya yaqi zuciyarshi yayi fatali da wannan tunanin, yaci gaba da harkokin gaban shi, har zuwa dare, Dare nayi anan ne ya raina kanshi don kasa bacci yayi. Sai tunane tunane yake, yana saqa yadda zai ruguza wannan soyyaya na cin a mana, yasan ko yakai maganar wurin manya babu mai goyan bayan shi, zasuce meye hujjan shi na hana kamal Auren ta tunda shi ya qita, zasu zata ko sonta yake, shi kuma yanzu a zuciyarshi babu burbushin sonta ko kad'an a ciki zee dinshi ita kadai ce a ranshi ita yake so itace za'binshi, itace irin macen da yakeso wayayya yar boko, shi mai zaiyi da wata Asmah baya sonta baya kaunarta, hasalima shi ya tsaneta, kuma tsanan da ya mata ne yasa baya son ta auri wani makusancin shi, (kai dai kasani Mallam Aslam muna nan muna jiranka ka gama kewaye kewayenka zaka dawo kan hanya ne😬) Da ire iren wadannan tunaninkan yaketa juyi akan makeken bed dinsa, baiyi aune ba sai ji yayi ladan na kwada kiran assalatu, zabura yayi ya miqe tsaye ya kunna wutan d'akin ,kallon shi ya kai kan agogon bangon dake d'akin biyar saura kwata ya gani, mamaki ne ya kamashi na tsowan lokacin daya dauka yana tunani, da haka ya shige toilet ya dauro alwala raka'atanil fajir ya gabatar kafin ya wuce masallaci. A can ya taradda mazan gidan duka,manya da yara , baqi da yan gida, ana idar da sallah miqewa yayi yaje ya gaisar da iyayen shi , da kuma alhaji baba , su amir da kamal ma hannu ya basu sukayi musabaha,sannan ya fice daga masallacin bai jira kowa ba , don bacci yake son yayi kafin lokacin tafiya daurin aure yayi, Amir ne ya biyo bayanshi da sassarfa yana cemai "haba ango kasha kanshi , na zainabu Abu mai tagyayen suna bako jira" share shi yayi bai tanka ba , a haka suka iso part dinsu na samari, Amir nata tsokanan shi yaqi tankawa , Kowannen su daki ya shige , Aslam bacci yake ji sosai don haka yana shiga dakinshi ya haye kan bed dinshi ya duqunqune cikin bargo sai bacci, ko azkar da karatun alkur'anin daya sabayi kullum bayan asuba bai samu yayi ba, bacci ne ya kwashe shi mai nauyi, kasancewar bai samu bacci da daddare ba, Daurin auren qarfe Tara na safe za'ayi don haka , su Abba da daddy da abokansa , da duka wani mai niyyar zuwa wajen daurin auren qarfe takwas kowa ya shirya, Amir ne ya sakko downstairs cikin manyan kaya harda babban riga light blue, ya murza hula dark blue da ratsin light , sai zuba kamshi yake, a nan falon ya tarad da kamal shima cikin nashi shigar ta manta kaya iri daya dana Amir din, wasu daga cikin friend dinsu ne suka fara shigowa cikin , suma dai shadda light blue dinnne a jikinsu, da alama shadda light blue shine ankon da abokan ango suka fitar don zuwa wajen daurin a auren, zama sukayi , wadannda zasuyi breakfast suka fara yi, don tun saven thirty mami da sukaba kwangilar had'a breakfast din abokan ango ta aiko musu da shi, Anas ne yace"ya kamata mu hanzarta kundan dai san anguwar da d'an nisa ". Dr bash yace"wai nikam ina angon ne " ya fad'a yana kallon Amir, Amir yace"may be yana shiryawa kasan shirin angwaye daban yake, amma dai barin shiga na fito mana dashi ". Miqewa amir yayi ya nufi upstairs don dubo Aslam, Yana isa kofar d'akin knocking yayi shiru ba amsa, sake kwankwasawa yayi shiru again ,don haka ya kutsa kai tare da sallama , ba kowa a falon don haka ya nufi bed room tare da sallama , Wani irin zaro ido Amir yayi tare da furta"kutumelesi! Dalilin hango Aslam da yayi qudundune cikin bargo yana kwasan baccinsa hankali kwance, kunnna wuta mai haske amir yayi don dama ta cikin dim light yake hangoshi, tsayawa Amir yayi a kanshi ya riqe qugu yama rasa ta ina zai fara tashin shi, takaici duk ya gama cika shi ji yake kamar yata sharara mai mari a fuska, Da zaimai mugunta da wlh Alhaji bab zaije ya dakko mai, saidai kawai yaji ruwan carbi a kanshi, amma yasan inya tsaya wannan duk bata lokaci ne, Wata yar qaramar waya Amir ya zaro daga aljihunshi, itel ne wayan irin mai shegen qarannan, danno wani ringing turn mai uban tsiwa da kaudi hadi da vibration yayi, saida ya manna wayar a kunnen Aslam sannan ya danna play, Aslam da yayi Nisan bacci sai jin wani irin kuwwa hade da vibration yayi a cikin kwkwalwan kanshi, a zabure yayi wurgi da duvet din da ya lilliba ya miqe tsaye, kanshi na wani irin sarawa,bude idon shi da sukayi nauyi yayi akan Amir dake ta kwasan uban dariya, Aslam bai ce mishi komai ba don gaba daya kanshi ciwo yake mai bazai iya magana mai tsawo ba, Saida Amir yayi dariyarshi mai isansa sannan ya bata rai ya koma serious face ya kalli Aslam dake lumlumshe ido alamar baccin bai ishe shi ba yace"dalla Mallam ware kaje kayi wanka ka shirya, kowa ya shirya ana jiran ka don tsabar iskanci Ashe kai kana nan qudundune cikin bargo kana barci". Sai lokacin Aslam ya tuna da daurin auren dake gaban shi"subhanallahi " ya furta yana mai d'an ware idanun shi dake lumshewa, daddafa bango yayi ya shiga toilet, wanka yayi shap shap ya fito, daure da tawul, nan ya tarad Amir ya ciro mai kayan da ya tanada don zuwa daurin auren, Gaban mirror ya tsaya ya shafa mayukanshi da turarukan shi masu kamshi na jiki, wasu fararen sababbi fil din singlet da boxer ya ciro daga cikin wardrobe, turare ya fesa musu sannan ya koma toilet ya sanyo, saboda amir daya qureshi da ido, Yana fitowa ya fara shiryawa cikin shaddan shi milk color mai mugun kyau da tsada, sai maiqo takeyi, Riga ne da wando da babban riga dinkin zamani, an mishi aiki da zare coffee color, hulla milk da ratsin coffee ya saka, sai takalma cover shoes suma coffee, ba qaramin kyau Aslam yayi ba abinka da kyakkyawa cikin kyawawan kaya, abin ba'a cewa komai sai masha Allah. Amir ne yace"wow wow angon zainab kaganka kuwa, gaskiya kayu kyau,kayi maza ka gama muje kaga su bash nata kirana, nasan kuma sunga na dad'e ne, shiyasa"ya fad'a yana ficewa daga d'akin zuwa main falo inda su bash suke, Aslam saida ya daura agogon shi rolex mai kyau sannan ya biyo bayan Amir d'in, yana shigowa falon abokanshi suka dauki sowa da tafi ana tsokanan shi ango kasha kamshi, kasa amsa musu yayi don kanshi ba qaramin ciwo yake mashi ba, saboda baccin da baiyi jiya ba,gashi kuma Amir yazo ya tashe shi da dan iskan itel dinshi mai shegen qara , ya qara mai ciwon kan, Kasancewar time yaja yasa basu tsaya wani bata lokaci ba suka dunguma suka fito coumpond din gidan,koda suka fito su Daddy da sauran jama'a tuni sun wuce, suma motocin su suka hau suka kama hanya kusan dukkansu suna da mota sai d'ad'd'ya wadan da ba aka rasa ba. Wucewarsu ba dadewa, yan matan mummy na hango sun fito daga part d'in mami, da alama dai aiki suka taya mamin don dukkansu ba wacce tayi wanka a cikin su, sashen mummy suka nufa donyin wanka su shiya cikin ankon su na yinin biki, gidan yadan fara cika da mutane don haka falon mummy na qasa dana mami ma da suka baro cike yake da mata, Gaisar da mutanen falon kawai sukayi suka wuce dakin su don shiryawa,. Batool ce tayi wuff ta kama qofar toilet zata shige, zahra tayi caraf ta kamota tace "wlh baki isa ba keda kike shegen dadewa a wanka, shine zakice ke zaki fara shiga,wlh bazaki shiga sai na fito, Nan batool itama ta cakumo ta suka fara kokawa, dama sun saba kusan kullum sai sun ta'ba, Amira na ganin haka ta lalla'ba ta shige toilet d'in tana musu dariyar mugunta, karar rufe qofar ne ya dawo dasu haiyacinsu, nan ko suka koma kan amira cacacaca batool harda cewa allah ya isa ci mata layi da amira tayi, Amira na jinsu tayi muqus gata itama ba baya ba wajen dadewa a wanka, Asmah dai na zaune gefe kasancewar ta mara son haya niya yasa bata saka musu baki ba,shiru dai tayi tana bin kowa da ido in sunyi abin dariaya ta dara, Amira don mugunta saida ta kwashe sama da rabin awa sannan ta fito batool ta shiga ,itama sai gungumi take alamar sai ta dad'e itama, Wani tunani ne ya fado ma Asmah arai, take kuwa ta miqe tace musu tana zuwa, zahra tace"ina zuwa kuma" tace"kedai ina zuwa nace" ta fice d'akin mummy ta nufa don tayi wanka a can ta huta da bin layi , tasan ba kowa a d'akin mummy yanzu, cikin sa'a kuwa tana murda handle d'in, kofar ta bude, mummy bata kulle kofa ba kenan, shiaga tayi kamar yadda tayi tsammani ba kowa a dakin,toilet ta shige donyin wanka. Karfe tara da minti goma aka daura auren Muhammad Aslam abdallah, da Zainab Abdussalam, akan sadaki masu yawan gaske, Masha Allah daurin aure yayi jama'a saidai muyi fatan Allah ya zaunar dasu lpy, Aslam da abokanshi sun shiga sunyi gaisuwar surukai kamar yadda yake a al'adar mutanen minna, Direct kuma gida suka wuto in da zasu gabatar da reception kamar yadda Amir ya shirya, A part d'insu Aslam din suka yada zango, nan ma'aikatan da aka turo daga galaxy hotel, inda akayi order abincin reception d'in suka shiga serving dinsu, Abinci masu rai da motsi duk abinda mutum keso shi za'a zuba mai, ga drinks kala kala duk Amir ne ya dauki nauyin komai. Cin abinbin su sukeyi suna firansu group group , kasancewar falon babbane yasa ya dauke su baki d'ayansu. Aslam na zaune cikin kujera one sitter ya cire babban riga ya ajiye sai binsu yake da kallo, abin duniya gaba daya yabi ya dameshi, shi d'an farin cikin da mutum keyi bayan daurin auren shi, shi neman nashi farin cikin yayi ya rasa, kanshi ne ke matsanan cin ciwo ga kuma hayaniyar da friend dinsa keyi na qara mai ciwon kai, sai tsokanan shi sukeyi irin yadda abokai keyi, yayi shiru yaqi cewa komai saidai d'an murmushin yaqe, Suma kasancewar sunsan halinshi na rashin son magana yasa basu wani damu ba. Bacci yakeji sosai kuma yana gani idan har ya samu yayi baccin kanshi zai rage ciwo koma ya bari gaba d'aya, miqewa yayi da nufin yaje upstairs d'akin shi ya kwanta, wani tunani ne ya fado mai a rai, yasan indai ya kwanta a d'akin shi abokanshi baza su bari ya samu bacci yanda yake so ba, don haka rivas yayi daga niyar hawa saman ya nufi hanyar waje, ganin Anas nason tsaidashi yasa ya kara waya a kunnen shi kamar yana amsa call, Sashen mummy ya nufa, yasan d'akin tane kawai zai samu yayi bacci hankali kwance , kuma su amir baza suyi tunanin yana can ba don ko d'akin mami yaje bai tsira ba tunda sunsan ya saba zuwa, zasu iya cewa bari su duba can in suna Neman shi, Ganin alamar akwai mata cike da falon yasa yabi ta qofar kitchen ya haye sama ba wacce ta ganshi, Dakin mummy ya shige ya qure A,c , sannan ya haye kan makeke bed d'inta' ya qudundune cikin bargo, inba mutum ya kula sosai ba bazai san a kwai mutum kwance a wajen ba. Asmah wankanta ta sheqa sosai a toilet din mummy, bayan ta gama ta d'auki tawul d'aya daga cikin tawul d'in da ta gani a rataye a toilet d'in, ta daura, fitowa tayi kanta tsaye don tasan ba kowa a d'akin, Aslam jin motsin an bude qofar toilet yasa ga bud'e idanun shi don ganin ko waye, Asmah ya gani ta fito daga toilet d'in daure da d'an,qaramin tawul da bai gama rufe mata cinyoyinta ba Numfashin shi ne ya shiga seizing gabanshi ya shiga fad'uwa zuciyarshi ya shiga bugawa da sauri da sauri, Asmah kam direct gaban mirror mummy ta nufa kasancewar tasan duk abinda take buqata na shafa akwai a kan mirror mummy, yasa taga gara ta tayi shafe shafenta anan gaba d'aya, inyaso tana komawa sai dai tasaka kayanta kawai, Madubin na fuskantar gado ne don haka juyama Aslam baya tayi, kwata kwata bata lura da wani Aslam a d'akin ba, Qurama bayanta ido yayi qur baya ko qaftawa, tun daga sama hara qasa yake qare mata kallo, dogon baqin gashinta dake kwance a bayanta, yabi da kallo kasancewar ta wanke kai yasa gashin kwanciya luf luf a kafad'unta ,sauko da idanun shi, yayi kan mazaunanta da suke nan masha Allah dasu,ga wani irin lafiyayyen hips da Allah ya hore mata kamar wata babban mace, Tunda yake bai taba sanin haka qirar yarinyar nan yake ba, bai taba sanin haka take da kyawun diri ba sai yau , irinta ne maza kema laqabi da mai coca cola shape wasu kuma suce figure 8, Yana wannan tunanin ne yaga ta sauke tawul d'in ta daurashi a qugunta taci gaba da shafa manta hankali kwance, baya ganinta ta cikin madubin kasancewar fitilar dakin bamai haske bane sosai, Tana gama shafa mai a jiki yaga ta miqa hannu zata sauke tawul d'in qasa gaba daya donta shafa mai a qasanta , Wani munafikin tarine ya sarqe aslam wanda baisan daga ina ya fito ba , jinshi kawai yayi yana tarin , A firgice Asmah ta juyo jin tarin mutum a bayanta, idanunta ya sauka akan Aslam dake duqunqune cikin bargo, yayinda shi kuma idanun shi ya sauka akan tsayayyun madaidaitan breast dinta da suke cike tam tam a qirjinta, Wanda tsabar tsoratan da tayi jin motsin mutum a bayanta yasa ta juyo ba tare da rufesu ba, don ita duk zatonta gamo tayi, Wani gigitaccen qara ta saki tare da tsugunawa ta qamqame jikin ta a wurin tana maqerqerta, gaba daya kwakwalwarta tsayawa yayi da aiki a lokacin, tama rasa me zatayi donta kare kanta, banda tsugunawar nan da tayi ta dunqule wuri daya kasa aiwatar da komai tayi, Aslam kuwa lokacin daya juyo tsayayyun breast d'inta ne suka fara mai sallama,wani Yarr Yarr yaji a jikinshi kafin kuma wutan kanshi ya dauke dif ,na wucin gadi, daga bisani kuma ya miqe kamar an tsikareshi ya buga wani uban tsaki, cike da borin kunya yabar d'akin, ta qofar kitchen din daya shigo tanan ya bi ya fice daga part din jiki a sanyaye🚶‍♂️🚶‍♂️🚶‍♂️🚶‍♂️ Karku manta comment d'inku shike qaramin qaimi wajen sambad'a muku typing🥰 Oum ummetarh 07041130088 Share And Comment🙏🏻 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 41 & 42 Asmah jin qarar qofa alamar ya bar dakin, ta tashi da sauri ta rarumi hijabin mummy data gani, ta zura akan tawul din jikinta ta fice daga dakin itama duk ilahirin jikinta rawa yakeyi, Saida ta tsaya a qofar dakinsu ta saisaita kanta sannan ta shiga, samunsu tayi suma duk sunyi wanka suna shiryawa, wucesu tayi ta fada kan gado rigingine, Kallon kallo su zahra suka shigayi a tsakanin su, Amira ce tayi qarfin halin qarasawa bakin bed d'in, ta dago kan Asman ta daura kan cinyarata, sannan tace, "lafiya sister meya sameki" alama Asmah ta mata da hannu kanta ke sara mata, Batool ce ta qaraso da sauri ta zauna kusa da ita tace " ayya sannu Asmah, sannu kinji, kwanta ki huta qila aikin hada breakfast d'in da mami ta saka mu dazu ne, yasa mata ciwon kai kunga ita ta zage taketa aiki sosai , kunsanta da rashin ganda," Zahra tace barinje na dauko miki maganin ciwon kai a d'akin mummy, girgiza mata kai tayi alamar ta barshi bazata sha ba, Kwantar da ita Amira tayi suka ci gaba da shirin su, sunyi suna mata sannu,rintse idanuwa tayi kamar mai bacci, take abubuwan da suka faru few minutes da suka wuce,suka shiga dawo mata fresh a kwakwalwarta, innalillahi wainnailahi rajiun ta shiga maimai tawa acikin zuciyarta, gaba d'aya ranta a jagule yake, gsky Aslam ya cuceta , kuma Allah ya isa ganin jikinta da yayi, bata yafe ba, A hankali ta fara samun relief a cikin zuciyarta , saida ta kwashe kusan fourty minutes a haka kafin ta yunqura ta miqe, ganin tunanin ba abinda zai haifar mata sai qarin takaici da damuwa, tunda abinda zai faru ya riga ya faru , sai a kiyaye gaba, Zuwa lokacin su Amira sun gama shiryawansu tsab da su sunsha makeup kowacce ta kashe daurin zamani kamar sune amaren, Ganin ta miqe yasa suka shiga jera mata sannu, tare da tambayar ta ya kan, da sauqi tace musu ta shiga toilet ta wanko fuskarta, tazo ta zauna itama batool ta tsantsara mata makeup, tayi kyau kuwa sosai kamar wata balarabiya, Amira ta miqo mata nata kayan tasanya, Wow masha Allah Asmah kam tana da kyau sosai tun daga kyawun fuska, kyawun diri, uwa uba kyauwun hali da kyawun zuciya, Kashe dauri tayi itama suka fantama cikin gida akaci gaba da yinin biki dasu, Asmah kam jikinta a sanyaye yake, tun abinda ya faru dazu amma haka ta daure taci gaba da harkokin gabanta, har zuwa dare inda nan suka kuma caba wani adon cikin ankon su na dinner. Aslam kam yana barin part din mummy, parky lot ya wuce ya bude motarshi ya shiga back sit ya zauna , tunanin abinda ya gani few minutes ago ne ya shima mai yawo filla filla a cikin brain dinshi, yana kisima kyau da tsaruwar halittan yarinyar, tunanin daya dinga yi kenan har baisan tsawon lokacin daya dauka yana zaune cikin mota yana tunanin ba , baccin dai da bai samu yayi ba kenan, Can kuma kamar daga sama yaji wani bangare na zuciyarshi na kwa'banshi da cewa, meye haka kakeyi Aslam, ka zauna kana bata lokacin ka a banza kana tunanin wannan mayyar yarinyar, me take dashi da har zaka tsaya kana tunanin ta, kaida kake da amarya kamar zee babban yarinya meye na jikin wata mace zai rudeka, har ka zauna kana 'bata time d'inka a banza a hofi, tsaki yaja a fili tare da fitowa daga motar ya nufi sashen su, yana isowa kuwa ya taradda wasu friend d'insa nata neman shi sumai sallama, zasu wuce, yayinda wasu da dama sun riga sun wuce saida a had'u wurin dinner anjima. A mooris event za a gudanar da dinner Wanda za,a fara 9 a gama 1am, Misalin 9:30 na dare yammatan mummy na hango zaune a falon mummy sun sha makeup, sai zuba kamshi sukeyi,kamar wadanda zasuje gasar zabar sarauniyar kyau, su biyar ne yau harda Khadijah da suka zo d'azu da mamanta, mamanta bazata kwana anan ba gidan alhaji Mallam zata kwana, ita kuma Khadijah tace anan zata kwana don tana son zuwa dinner, da'ker mama ta barta saida mummy ta saka baki, Itama Khadijah taci kwalliyarta cikin lece dinta milk colour kasancewar ita batada ankon su Asmah Kamal ne yayi sallama yace su taso suje, dama shi suke zaman jira, don yace in sun shirya su jirashi ya zo ya daukesu. Miqewa sukayi suka bishi, suna shiga harabar gurin taron Kamal yayi parking suka fito suka shiga cikin hall d'in, wuri saka nema suka zauna , had'ad'd'un samarin dake wajen kuwa sai binsu da kallo sukeyi sunga kyakkyawan yammata, wuri ya tsaru sosai amarya da ango sun zuba kyau, kamar wasu wata da zahra a cikin sararin samaniya, anfara gudanar da komai cikin tsari da wayewa,an kira amarya da qawayenta sun taka, haka ma ango saidai shi angon baiyi rawa ba sabanin amarya da ta tiki rawar ta, kamar ba itace amarya ba, liqi kam anyishi kamar ba gobe su zahra ma sunje summa yayansu liqi amma basuma zee don duk haushinta sukeji, (tab zee bata samu shiga ba wajen qannen miji😅) Kamal kam kasawa yayi ya tsare Asmah ganin irin kallon da mazan gurin ke binta da shi, guri ya samu kusa da ita ya zauna yana gadin kayarsa, suna dan fira jefi jefi, Amir dake zaune a high table kusa da ango a matsayin babban abokin ango,tun shigowar su Asmah hara zuwa sanda sukaje sukayi liqi hankalinshi na Kansu, ganin yawanci mazan wurin hankalin su na Kansu yasa yaji gaba daya hankalinshi bai kwanta. Shawarar da zuciyarshi ta bashi yabi, sakkowa yayi daga kan high table din, ya nufo inda suke, suna ganin shi suka shiga gaishe shi amsa musu ya shiga yi cikin sakin fuska yana dan tsokanansu irinta abokan wasa, kallon Amira yayi yace"am Amira pls zoki tayani shigo da wasu kaya daga mota ," to Amira tace tare da miqewa tabi bayan shi suka fita daga hall din, suna Zuwa gurin motar shi mai makon taga ya bude mota ya dauko mata kayan daya ce,sai gani tayi ya jingina da jikin motar ya tsaya yana kallonta,itama kallon nashi tayi taga meya tsaya yi bai dokko mata kayan ba, suna had'a ido ya sakar mata wani kyakkyawan murmushi mai dauke da manufofi kala kala, gabanta ne yayi wani irin faduwa,ya salam ta furta a zuciyarta, batun yau ba ya Amir ke burgeta musamman in yana wannan murmushin nashi mai masifar kyau, Ya Amir kyakkyawan gaske ne gashi da masifar sauqin kai ba kamar ya Aslam mai shegen girman kai da rashin fara'a ba, Amir ne ya katse mata tunani da cewa "Amiran mami an girma yanzuma shekaran ki nawa " d'ago kai tayi tana kallonshi jin tambayar da ya mata, aiko gani tayi ya qara mata ido sai murmushin shi mai kyau yake saki, kunyarshi taji ya kamata ganin irin kallon da yake mata, fuskarta ta rufe da tafukan hannayenta tana murmushi tace" sha takwas fah'. Amir yace"masha Allah ashe dai yarinyar ta zama ammata, to yaushe zaki turo mana sirikin mu yazo ya gaishemu mu big big brother's". Aiko da sauri ta bude fuskarta tace "laaa ya Amir nifa bani da saurayi" wani boyayyan ajiyar zuciya Amir ya sauke tare da ce mata "da gaske" tace ". Eh " yace "aiko ya kamata kiyi saurayi kin zama ammata yanzu eighteen years fa" Haka Amir yaci gaba da jan Amira da fira yana bugan cikin ta yana mata wasu tambayoyi da wayau, hakan yafi mai kwanciyar hankali akan ya barta cen wasu qattin banza su dinga kalle mai tanadin shi na shekara da shekaru har a samu wani mai tsaurin ido yazo yamai shigar sauri, wanda yake ganin bazai taba lamuntar hakan ba, A can cikin hall kam anata ci gaba da gudanar da programs hankali kwance, wayar Amira dake hannun batool yayi qara, kallon su zahra batool tayi tace "kunga Amira daga zuwa dauko kaya shiru shiru tana neman kwashe awa guda, ko lafiya" zahra tace "wlh nima tambayan da zanyi kenan kika rigani, a baki". Wayar ne ya sake ringing batool tace"gashi ma anata kiranta barin kai mata wayar daga nan na duba ko lfy " Cikin sauri sauri ta miqe riqe da wayar Amira a hannunta, ta nufi qofar fita daga hall hall din, tana d'an gudu gudu sauri sauri dinta samu ta kai mata wayar kar call din ya katse, dai dai qofar fita suka zabga wani uban karan da saida kofin glass d'in daka hannushi cike da ruwan taceccen lemo ya fadi qasa ya tarwatse bayan ruwan lemon ya xubar mishi a jiki, baya tayi taga taga zata fad'i , Allah ya taimaka jinta tayi a jikin mutumin da suka zabga karo ya tarota jikin shi, handset din amira dake hannunta tuni ya fadi qasa, kallon fuskarta Dr bash yayi don yaga da wa yaci karo haka, idanun shi ya sauka ana batool da itama ta dago kai a fusace , fusge jikinta tayi daga nashi, cike da tsiwa da rashin kunya tace"dalla Mallam baka ganine, ko kai makaho ne ko, baka da ido ne ko idonka a tsakiyar ka yake da zakazo ka bangaje ni ka watsamin lemo mai sanyi a jikina, mutane kuna tafiya bakwa kallon gabanku sai kace wasu tumaki, " takwai karshe tare da banka mai wata uwar harara kamar idanunta zasu fad'o qasa, Zuciya ne ya d'ebi Dr bash ya d'aga hannu zai wanka mata mari sai kuma ya dunqule hannunshi ya naushi iska ya fasa marinta, kallonta yayi cikin bacin rai tare da nunata da yatsa yace ke wacece da zaki bangaje sannan kizo kina gayamin maganar banza maimakon ki bani hakuri, kinsan ko ni wanene, muza hannunshi daya nunta dashi yayi yatsarshi ya bada wani sauti tas tas, yace kinci albarkacin Aslam da mummy da yau saina nuna miki ke qaramar Mara kunya ce tsaki yaja sanan ya ra'bata ya wuce abin shi, Binshi tayi da harara kafin tana tsaki tare da cewa "aikin banza aikin wofi AI da ka mareni da wlh yau sai kasan ka taba. husaina fatima batool abdallah, " (Tofah ku kuma kalan naku salon kenan hmmmm ku dai ku biyoni muje zuwa in garin ba nisa) Daukar wayar amira dake qasa tayi ta duba ba abinda ya samu wayar, fitowa waje tayi dan kaima amira wayar, Hango amiran tayi ta nufo ta tsayawa tayi har amiran ta isota ,miqa mata wayarta tayi, batace mata qala ba don ranta ya Riga ya gama baci da abinda mutumin da sukayi karo ya mata, Amsar wayar amira tayi ganin miss call din mummy yasa tabi kiran da sauri, mummy ta daga tace"Amira ina kuka shiga ne inata kiran wayoyinku a kwashe , da'ker ma na samu naki oyaa maza ku kamo hanya ku dawo gida daddynku yace ku dawo haka dare yayi sha daya ta gota,". Qarasawa sukayi ciki nan ta sanar zasu saqon mummy, aiko babbata lokaci suka miqe da niyyar komawa gida duk da ba'a tashi ba, Ya kamal d'in da ya kawosu shiya maidasu , a hanyarsu ta komawa gidane batool ke basu labarin karon da tayi da Dr bash tanayi tana kwashe mai albarka tunda ita bawai sanin shi tayi ba, a haka suka iso gida, A mooris event kuwa sai 1am aka tashi a daga dinner bagan nayi ciye ciye anyi shaye shayen drinks, anyi rabe raben sobeniyas kala kala mutane suka watse , ango ma ya dauki amaryarsa suka wuce gidansu dake London road, bakin dan rakiyan nan da akema amare wai su yan boko😕 sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya Oum ummeetarh 07041130088 Share and Comment Fi sabillah🙏🏻 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen nu} Page 43 & 44 Direct gidan su dake London road suka nufa, Aslam nayin parking ya fito ya bude na amaryarsa kofa, fitowa tayi tana lumshe ido alamar bacci takeji sosai, ganin haka ya sa Aslam daukarta cak a haka suka qarasa har cikin katafaren falon su mai kama da aljarnar duniya, don iyayen zee ba qarya sun kashe mata kud'i sosai a gidanta, A main falo ya ajiyeta kan daya daga cikin manya manyan kujerun dake zagaye da falon, komawa mota yayi ya dauko kunshin ledar daya tanada na kayan ciye ciye , da ake buqatar ko wani ango ya riqe idan zai fara shiga dakin amaryassa, rufe motar yayi ya koma falon , a kwance ya samu zee a inda ya barta ko hannunta bata iya dagawa,saboda tsabar gajiyan da tayi, don ba qaramin rawa ta tiqa ba a gurin dinner nan, A jiye ledar hannunsa yayi akan center table, zama yayi a kujeran da zee ke kwance, daukan kanta yayi ya daura akan cinyarshi, zame mata goggoron dake kanta yayi, take dogayen kitsonta na attached ya bayyana. dan kurama kitsonnata idanu yayi, a zuciyarshi kuma tunani yake , kardai ace duk gashin zee dayake gani dogo attached ne dama, tirkashi indai haka ne kam akwai matsala, don gashi na d'aya daga cikin abinda yake matuqar so a gurin mace, wani dan tunani ne ya fad'o mai arai , take ya lumshe idanun shi, ba komai yake hangowa sai hotan Asmah dazu a d'akin mummy, natural black hair dinta dogo mai sulbi dake kwance a gadon bayanta yana digar ruwa yake hangowa, Kamar kuma an tsikare shi yayi fatali da wannan tunanin, ya bude idanun shi akan fuskar zee dake kan cinyarshi, zara zaran eye lashes din data qara yake bida kallo kafin ya sauke idanun shi akan dan qaramin bakinta daya sha jambaki rad'am, makeup d'in da tayi na dinner nanan bajau a fuskarta kamar yanzu aka gama mata shi, Gsky zee ma kyakkyawa ce tana da kyawun fuska don ba Wanda zai kalleta ya kirata mummuna, saidai dirin jikin ne sai a hankali don irin matan nan ne da ake ma laqabi da muciya da zani, don a miqe take sambal kamar sandan agwai, sai uban tsayi masha Allah, kyawun fuska da hasken fata da tsayi kam akwaisu kamar ita taima kanta, Iskan bakin shi ya shiga dan hura mata a fuska yanayi yana dan shafa kumatunta a hankali cikin wani irin salon soyyaya, So yake ta tashi suje suyi sallan nafila , yasan tana saka ruwa a fuskarta zata watsake, bayajin zai iya d'aga mata qafa a Daren nan,don a matuqar bugace yake, don tunda safe da sukayi clashes da Asmah yake jin wani matsanancin felling na addabarsa, amma ga mamakinsa gani yayi ta miqe tsaye ta kalle shi tana sakin hamma baki bud'e, tace"honey zan shiga ciki na kwanta wlh bacci nakeji gud night" dan matsawa tayi kusa da shi, ta sakar mai kiss a forehead d'in shi, sannan ta haura upstairs, ta barshi nan sake da baki, Binta yayi da kallo har ta kule ma ganin shi ya kasa furta koda A , me hakan ke nufi? yake tambayar kanshi, Kodai bata san yaune first night dinsu bane, wani tunani ne yazo mai kai, na cewa qila tsoro takeji yasa tace tana jin bacci. Don ance mai wasu matan tsoro sukeji da'ker suke yadda da miji a Daren farko, Can kuma yaja dan guntun tsaki to tsoran me kuma, shifa shiyasa ya auri babban mace wayayya don baya son harkan kauyanci, haka dai ya zauna ya saka wancen ya kwance wancen , kuma ko kadan baiga baqin zee akan hakan ba (kunsan ance amarya bata laifi, kota kashedan masu gida,) to yauma hakan ce ta kasance da Aslam, Miqewa yayi ya haura saman shima daya daga cikin dakunan ya shiga , toilet ya wuce yayi wanka da alwala , shiryawa yayi cikin kayan bacci ya fesa turare ya gabatar da shafa'i da wutirin da bai samu yayi ba tun dazu , yana idarwa ya fito ya nufi d'akin da yake da tabbacin zee na ciki, A hankali ya tura qofar bed room d'in ya shiga ya maida qofar ya rufe, hango zee yayi akan bed tayi d'ad'd'aya tana bacci hankali kwance, tsakar d'akin yabi da kallo, ta cire duk wani kaya na jikinta tayi watsi dashi a tsakar d'akin, ta sauya na bacci, Shi mutum ne da baison tarkace any how, don haka bi yayi ya kwarkwashe kayan data warwatsar harda su bra da pant, ya Adana , sannan ya raba gefen ta ya kwanta bayan ya kashe wuta yayi addu'a ya tofe su dashi, Daqar bacci ya dauke shi don ya riga ya shiryama daren yau, gashi amarya zee ta bata mishi shiri duk da ya mata uziri akan gajiyan biki ne yasa tamai haka, Kiran assalatun farko a kunnen shi, miqewa yayi ya shiga toilet ya watsa ruwan zafi,yayi alwala ya fito, tashin zee ya shiga yi ta tashi sallah, amma taqi tashi kamar wacce ta suma, ganin zai rasa sallah yasa ya fice daga d'akin da sauri yana mamakin nauyin baccin zee, Yana fita daga d'akin zee ta gyara kwanciya, duk tashin da Aslam ke mata tanajin shi, bata ga daman tashi bane kawai don bata saba ba, a gida sai wajen sha biyu take sallan asuba,wata rana ma saidai ta had'a Dana azahar , wata ran ma mantawa takeyi batayi kwata kwata, Koda Aslam ya dawo a kwance ya sameta yanda ya barta,karasawa yayi ya hau kan bed din yaye bargon data lullu'ba yayi , fuskarta ya shiga shafawa a hankali yana kiran sunan ta, da'ker zee ta bude idanu cike da bacci,murmushi suka sakar ma juna , Aslam yace "mrs Aslam duk gajiyar bikin ne haka , har yanzu bata sakar keba, oya it's time for subhi prayer now tashi kije kiyi alwala kinga ni har na dawo masallaci, " shagwa'be fuska tayi kamar zatayi kuka tace" kai honey don Allah ka barni mana da safe sai nayi wlh har yan " "shiiiiiii "ya katseta ta hanyar daura mata yatsarshi a le'benta, dan bata rai yayi yace no tashi kije kiyi sallah, in kika idar zan miki tausa duk sauran gajiyar zata sakeki , badon taso ba ta miqe ta shiga toilet d'in, wanka tayi da brush da sauran uzirorinta, sannan ta dauro alwalan ta birki tacce don ba wani iyawa tayi ba, tawul ta dauka ta dauro kayan baccin data cire kuwa nan ta barshi cikin bayin a watse, Akan pray mat ta samu aslam yana azkar, kaya ta sanya marasa nauyi ta dauki hijab ta kabbara sallah, cikin minti biyu ta duddungura sallan ta sallame bako tasbihi balle addu'a, ta kwabe hijjab din ta yasar nan, Duk abinda takeyi Aslam na kallonta , gaba daya mamaki ya gama kama shi badai har ta idar ba take nufi, lallai akwai matsala , tunanin shine ya kaste jin ta shige jikin shi ta kanannaye shi, baisan sanda carbin hannunshi ya fadi ba, Wani irin tafiyan tsutsa ta shiga yimai a baya, take kuwa jikinshi ya amsa, (dama mai neman kukane aka jefeshi da kashin awaki). Dago face dinta yayi ya hade bakinsu ya shiga kissing dinta, aiko caraf ta kama ta shiga mayar mai da martani ko kunya babu kamar ba amarya ba, Duk da halin da yake cika saida abin ya bashi mamaki, saida suka kwashe mintuna masu yawwa sannan suka saki bakin juna duna maida nunfashi, Kallon cikin idawanshi tayi da murmushi a fuskarta tace" gud morning honey'. Hannu yakai ya shafi fuskarta yace "morning amryata kin tashi lpy, ya gajiya, I hope duk gajiyar ta wuce yanzu ko' kashe mai ido tayi cikin wani salo tace"yess'. Murmushi yayi Wanda shi kadai yasan ma'anar shi, jima yayi bazai iya ci gaba da azkar d'in ba, don haka miqewa yayi ya miqar da ita makunnin wutan d'akin ya laluba ya kashe, jawota yayi jikin shi suka fada bed, Zazzafan romance ya shiga sakar mata cike da shauqin so, aiko kamar jira take itama ta shiga maida martani , tafiya tai tafiya daga karshema Aslam dan kallo ya koma a filin,, Mamaki da tsoro ne suka kama Aslam, me hakan ke nufi? Amma da ya tuna ko wacece zee da inda tayi rayuwa yasa mamakin shi raguwa, fatanshi Allah yasa tunanin shi ya zama ba gsky ba, A jiyar zuciya ya sauke lokacin daya tabbatar tunanin shi ya zama karya, domin kuwa a virgin d'inta ya sameta, kamar yadda tsammata, Zee ba mazinaciya bace asalima ita yin sex baya burgeta barta dai da romance, a nan tafi auki iyakarta nan, shima bawai tana yi bane , takan dai kalla fina finan da akeyi ne, don haka ta iya abubuwa da yawa ta wanan fanni, bugu da qari kuma gabanin bikin nan mahaifiyar ta da kanta ta zaunar da ita ta din ga koya mata abubuwa, yadda zata sarrafa namiji, da yadda in tayi zai haukace a kanta, duk mom da kanta ta koya mata wasuma practical ta mata ba kunya ba tsoran Allah, Saidai fa iya wannan zee kawai ta iya , iya su kawai aka koya mata, a bangaren aiki kam zee bata iya komai ba don hatta dauke filet bayan anci abinci zee bata sanshi, komai yan aiki ke mata abinda ta iya kawai tayi wanka tayi kwalliya a tafi yawo da kawaye, sai ko charting a raba dare a nayi, shima wankan da da hali yimata shi za'a dinga yi, don idan kuna neman lazy women wacce bata iya komai na mata ba akazo kan zee kankat kenan, Iya murzuwa zee ta murzu a hannu Aslam tun tana daurewa kar tayi kuka Aslam ya rainata da girmanta da wayewarta har dai abin yafi qarfinta,ihu ta shiga kurmawa iya qarfinta tanayi tana kwashema Aslam albarka, ina Aslam ko jinta bayayi yayi nisa , Abu biyu suka taran mata na daya qasanta dake mata wani irin radadi kamar ana yankata da reza, a matsayinta na virgin na biyu kuma mugun gajiyar da tayi sosai, don tun tana sa ran a Aslam zai sarara mata, shiru saida ya kwashe mintuna masu yawan gaske, iya jigata zee ta jigata a hannun Aslam don ba sani ba sabo ya mata, Duk da dai ba wani gyaran da aka mata shi hakan ma ya mai tunda ya samu ya sauke damuwar shi na dogon zango, duk da dai da alamar amaryar tashi raguwa ce sosai Bayan komai ya lafa cike da tausayawa Aslam ya dubi zee , saidai wani uban hararan data banka mai yasa , sawunshi a likkafa ya shige toilet, Yana gama tsarkake jikinshi ya hada mata ruwan zafi, zuwa yayi yace ta taso ya taimaka mata ta gasa jikinta, da kukan shagwaba ta fashe mai wai baza ta iya tashi ba, daukanta yayi zuwa toilet din , shiya taimaka mata ta gasa jikinta, tana yi tana ihun raki, saida ya tabbatar ta gasu ya bata umarnin yin wankan tsarki ya fice a toilet d'in, Wanka tayi abinta soso da sabulu ta fito abinta tana dingisawa , da wani irin kallon mamaki yake binta ganin kanta a bushe ba alamar ruwa, (Tofah jama'a kodai wankan tsarkin ma zee bata iya bane😢) 💖More comment more typing💖 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabillillah🙏 💖DAMA T A BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 45 & 46 Da kallon mamaki yake binta ganin kanta a bushe ba alamar ruwa, ganin kallon yayi ya wa yasa tace "honey lpy wannan kallon fa haka". bata rai yayi yace"zainab wankan tsarki nace kiyi kuma naga kin fito haka bakiyi ba" tace"honey nayi wanka mana me ka gani" yace" kanki ba alamar ruwa kice min kinyi wankan tsarki". Tace,"oh wlh nayi wanka kaina ne kawai ban wanke ba, kaga kitson attached ne baya son ruwa " cikin dan tsawa tsawa don ranshi ya fara baci yace"wankan janaba nace miki ba wanka ba " kallon shi tayi jin ya fara mata ihu "meye kuma wankan janaba, ni bansan wani wanka ba bayan wanka da nakeyi kullum da soso da sabulu" whatttt! Ya fada cikin tsawan da babai shirya ba, kafin daga bisani yakai hannu ya dafe kanshi ya shiga maimaita innalillahi wa inna ilaihi rajiun, can kuma ya tsinkayi muryarta tana cewa" ohhh na tuna wai wani wanka da akace anayin in mutum ya gama period ko , na tuna shi amma wlh na manta yanda akeyi, don so daya mom ta taba koyamin lokacin dana fara jini, tun ranar da ta koyamin ban sakeyi ba, cos koda na sake yin wani jinin da naje yin wankan sai na manta yadda ta koyamin ni kuma ban tambayeta ba," wani zafi yaji zuciyarshi ta dauka amma haka ya daure yace su je toilet d'in ya gwada mata yadda akeyi, ba wani damuwa a tartare da ita tace to, shima dan taga ya bata rai ne inba hakaba cewa zatayi yayi haquri next time tayi, Shiga sukayi ta kunna tap na ruwan dimi, koya mata yadda akeyi ya shiga yi, yana fada tanayi inda ba tayi da kyau ba ya gyara mata, da suka zo gurin wanke kai saida ya tabbatar ko ina ya samu ruwa da kyau , suka gama suka fito, ranshi duk a jagule duk farin cikin daya kamata ace ango na ciki a washe garin aurensa shi baya ji saima akasin hakan dayake ji, Haka ya shirya ya bar gidan ko breakfast bai tsaya yi ba , direct family house ya nufa sai saqe saqe yake a ranshi, shi wa zai tunkara da wannan babban matsalan, don wannan ba abinda mutum zaiyi shiru bane, Wannan wani arin musiba ne Allah ya jarabceshi da shi, yanzu wannan itace uwar ya'ya shi, wacce zata musu tarbiya,nononta zasu tsotsa, tab lallai akwai babban kura a gabashi, furzar da wani iska mai dumi yayi daga bakin shi, a hankali ya furta "ta ina zan fara ne," hmmmm ya sauke numfashi, kafin yace"ya Allah kaji kaina, astagfurullah na tuba" (😅 tukunna ma mallam aslam baka tuba ba tukunna ,ai wannan shafin farko kenan, tunda kace iyayen ka basu iyaba, Kaine dan iya ,kai ka iya , sai kaje ka qarata da iyawarka, gaka ga zee, bakaga komai ba ma tukunna😕) Yanzu wa zai fara tunkara, Amir? ya tambaya kanshi , tunda bashi da kamar Amir din , girgiza kai kuma yayi a fili ya furta "no ba amir ba,don indai ya bari Amir yasan da wannna matsalan to dariya zaimai,yakuma cemai Allah ya qara, alhakin Asmah da iyayen shi ne" mami ce next data fado mai a rai, take yayi na'am da wannan shawaran , don ita yafi sabawa da ita zai iya gaya mata komai, ba kamar mummy ba da bata wani sakewa da shi, mastsyin shi na d'an fari, Da haka dai ya daure ya qarasa gidan,horn yayi, mai gadi ya bud'e mai get , parking motar shi yayi a parking lot, ya fito,da rabon zaiga abinda zai qara tayar , mai da hankali kamar ance ya kalli gefen daman shi ya hango, kamal da Asmah, kamal na jingine jikin motar shi ,sai murmushi yake saki ita kuma ta juya baya tana facing kamal d'in, duk da baisan mai suke fad'a ba zuciyarshi ya bashi kalamai soyayya kawai suke gayawa juna, don wannan murmushin da kamal keta saki ba banza ba, Take ya manta da matsalar data kawo shi ji yayi zuciyarshi ta qara daukan zafi, fiyeda da, wato har yanzu Kamal na nan akan bakan shi na cin amanar shi kenan ko, lallai kuwa zaiyi maganinshi yanzu yanzu nufosu yayi a zafafe gadan gadan kamar wani kububuwa, fuskar nan a murtike , (Duk dauka na zai je ya shaqe kamal ne kokuma ya wanwanke shi da mari, dan har na kwashi yan qafafauna nayi bakin get , da shirin kota kwana, na gyara riqon takarda da birona, amma ga mamakina sai naga, ) Ya zo ya wuce su, kamal na shirin gaishe ko kallon banza bai mai ba balle na arziki, sai lokacin Asmah ta ganshi , kamal cikin dan damuwa yace "meya same shi haka kuma" cikin nuna i dont care, Asmah tace"ohoo masa, shiya sani " direct part d'in mami ya nufa, cikin sa'a ba kowa a main falo haurwa yayi upstairs , a falon sama ya sameta a zaune ita kadai, tana amsa call, Mamin ganin Aslam a wani irin yanayi yasa tayi sallama da wacce suke wayar ba shiri , ita har ta tsorata wlh , ita tunanin ta qila amaryarce bai samu virgin ba, don ita yadda aka bata labarin zee har ce mata akayi tanabin maza, (kunsan dai halin mutane da qara gishiri a miya, in sata kake ace harda maita😤) Cikin dan shiga rudu mami tace "subhanallahi Aslam lpy meya faru" Zama yayi da baya akan kujeran dake facing mami, yana furzar da hucin bacin rai,ruwan sanyi mami ta miqe ta dauko mai a fridge ta miqa mishi ya amsa amma still be ce mata komai ba sai huci yakeyi, sake kwantar da murya mummy tayi tace"tace pls my son gayamin abinda ke damunka zaka samu relief a zuciyaraka," Goran ruwan ya bude ya kafa kai saida ya shanye shi Tass,ya cillar da goran ruwan , bude baki yayi da niyyar sanar da ita kalar cin amanar da ake shirin yimai, a cikin gidannan, saidai kuma tuna wanene kamal a wajen mami yasa ya qasa gaya mata, sai tsintar kanshi yayi da fada mata maganar zee na rashin sanin komai akan addinin islama, Kallon shi mami keyi quri, ta riga tasan wanene Aslam tun ba yauba, wannan abinda ya fada bai isa ya saka shi cikin irin wannan bacin ran ba , saidai in ba iyakar maganar kenan ba, ganin dai iya abinda ya fada kenan yasa bata takurashi ba, tace"sai hakuri Aslam kariga kasan wacece zainab da inda ka aurota don haka dole kayi hakuri da duk abubuwan da zaka fuskanta a tattare da ita , sai a hankali zata gyara wasu abubuwan, yanzu dai kaga ace mutum baligi baisan addininsa ba ai akwai matsala, kuma gashi yanzu Kaine mijinta duk wannan haqqin na kanka yanzu, don haka abinda zamuyi mafi sauki shine kai zaka dinga koya mata wasu abubuwan a gida idan ka samu lokaci, sannan kuma zan ma malamin da ke zuwa gida yana ma su zahra karatu, magana idan yana da wani sauran extra time sai ya dinga zuwa itama yana biya mata a gida. Tunda kaga yaro ne qaramin amma Allah ya bashi baiwar ilimin addini , idan kuma hakan bai yuwu ba da kaina zanje har islamiyar su ta nan bayan mu inda suke zura a weekend dinnan nayi magana da mai makarantan ya bamu malama mace da zata dinga zuwa gida tana koya mata mu gani, in Allah ya taimaka sai kaga an dace, ai ba a barta haka ba kodan tarbiyan y'ay'a nan gaba," Duk abin da mami ke fada Aslam jinta kawai yakeyi amma hankalin kacokam baya kanta, yana nan yana tunanin qila ma har yanzu suna cen tare suna cin amanar shi, Itama mami ta lura hankalin shi baya kanta, ta sake cewa"to Aslam kaji yadda ya kamata muyi kenan ". Aslam yace"to mami sai ayi qoqari a samu malamin, da wuri nima zan fara koya mata kafin nan," mami tace"yawwa to shikenan , kuma karka gaya ma kowa wannan maganar mu barta tsakanin mu. Kasan mutane yanzu gulma bata musu kad'an, ko cikin gidan ba Wanda zaiji indai daga bakina ne kar azo gaba a goranta mata, kasan mu mata sai a hankali, gaka da kanne mata karsu rainata" Miqewa yayi yace" mami bari naje " to kawai mami tace mai tana qara jaddada mai yayi haquri da matarsa, Ya fito part din mami gaba daya hankalin shi na parking lot, gani yayi basa gurin , bama motar kamal din kwata kwata a gurin sake birkicewa yayi , nan ya shiga tunanin ko tare suka fita, take yaji kamar jiri jiri na dibansa, Sashen su na samarin gidan ya nufa yana shiga main falo ya nemi kujera ya zauna ya dafe kanshi da hannayenshi biyu ya runtse idanun shi, cikin yanayin dacin zuciya ya shiga furta" ni muhammad Aslam, ni za'a wulaqanta da raina da lafiyata, to wlh bazai yuwu ba sai dai ran kowa ya baci , a cikin gidan nan, don bazan taba bari hakan ta faru ba indai ina nunfashi a doron qasa, koda tsiya koda arziki sai na raba wannan cin amanar," shiru yayi yana girgiza kai can kuma yayi kwafa yaci gaba da cewa" kamal! kamal!! Kamal!!! Hmmmm wato har wuyanka ya isa yanka da zakayi takara dani ko, to wlh saina nuna maka kwaruru ba tsaran wake bane , ko banza na baka shekara uku a haihuwa , shekara uku kuwa ba kwana uku bane, inba ma rashin kunya da tsaurin idoba matata zaka aura, kana qanina "a bayyane yake duk wadannan sambatum, cikin fitar hayyaci, Amir da tashin shi bacci kenan yayi wanka ya sakko dan zuwa part din mummy ya samawa kanshi abin tabawa, tun daga kan tsep yake ta jiyo maganganu kamar na Aslam, aiko dai Aslam dinne zaune a falo yana ta zaro zance kamar wani tababbe, zuwa yayi daf da shi , ganin Aslam d'in baima San da wanzuwar shi a gurin ba , yasa yadan duqa yana leqa fuskarshi tare da sauraren sambatun sa, Amir bai fahimci komai ba yadaiji yace kamal zai auri matarshi, to wata matar zainab d'in kamal zai aura ko wa? kasa haquri Amir yayi yace "zainab d'in kamal zai aura ? " ya fad'a da dan qarfi yanda Aslam zai ji shi, bude ido Aslam yayi akan fuskar Amir, yace ba zainab ba Asmah, Amir yace "Asmah! Asmah!! Wace Asmah dama kana da wata mata Asmah bayan zee da aka daura aurenku jiya " shi Amir kwata kwata bai kawo cewa Asman mummy yake nufi ba, Cikin d'an hasala Aslam yace "Asmah nawa muke da ita a gidan nan, ' Amir yace "to naji kace matar ka ita kuma Asman gidan nan naga ba matar ka bace,' Aslam yace "ka rantse baka halarci daurin auren mu ba" Amir yace "da aka daura ba ka kwance ba" cikin daga murya yace "Dana kwance shine shi zaizo yace ya sonta, akan wani dalili zai so ta, ya bari wani can bare ya aure ta mana , amma saboda ya raina ni shine zaice yana son ex wife d'ina, Amir da sai yanzu ya fahimci takamaiman meke faruwa, yace "hmmmm wato kamal da Asmah suna soyyaya, shine kai kuma kake kishi da kamal akan Asmah ko? am I right?, to na tambayeka mana Aslam dama kana sonta ka saketa," Aslam ya daqo ya kalli Amir yace"so, soyyaya, ni ke son wa? wai Asmah " ya fada yana nuna qirjin shi, Amir yace "kwarai kuwa Mallam kar ka yaudari kanka ko kaso ko kaqi kana son Asmah soyayya mai tsanani kuwa daya haifar maka da matsanancin kishinta, har kake gani kamal ya ci amanar ka, gara taje ta auri bare, to bari na gaya maka , koda wa ka ganta ba kamal kadai ba sai kaji kishinta, kawai ka yarda Mallam sonta kake, kuma wlh tun wuri gara ka cire ta a ranka ,don ka riga kayi wasa da damanka tun farko" Miqewa Aslam yayi ya kalli kamal yace"baka da hankali nike son, wannan Mara kunya yarinyar, to hasashenka bai zama gsky a kaina ba , " Miqewa Amir yayi ya dafa kafadar Aslam da hannu daya ya saki murmushi yana kallon shi yace"dadina da kai abokina taurin kai amma ka rubuta ka ajiye nina gaya maka kana son Asmah makahon so ma kuwa, ko ka yarda ko kar ka yarda, " Bige hannunshi Aslam yayi bai qara ce mai qala ba ya fice daga part d'in, motar shi ya shiga ya bar gidan yanata nanata kalaman Amir a zuciyarshi, can kuma ya kaima sitiyari duka yace" kai impossible hakan bazai taba yuwuwa ba,' da haka ya iso gidan, rabon zai qara tarad da wani kayan takaici yana saka kanshi a falon idanunshi ya sauka akan, (Oh ni indo me kuma Aslam ya tarar a gida?) Oum ummetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 47 & 48 Aslam na shigowa falon ya hangi mutane cike da falon , butum biyu kawai ya waya a cikin su mom da dad d'in zee,sai sauran da bai taba ganin su bama, hango zee yayi kanannade jikin wani qaton mutum fari Sol da gani kasan bature ne, sai wani kukan shagwaba take mishi, tana cewa zatayi missing dinshi sosai, shi kuma sai shafa bayanta yakeyi yana bata hakuri, sauran mutanen falon kuwa sai dariya suke including mom and dad, Jiki a sanyaye Aslam ya qara so cikin falon zee na ganin ta miqe daga jikin best friend d'in nata, tazo da sauri ta rungume shi, ci gaba tayi da mai kukan shagwaban tana cemai wai mom da dad da friends d'inta da suka zo mata biki daga Malaysia zasu wuce su barta, Badan yaso ba yayi hugging nata back, qarasawa yayi ya gaida mom da dad, a yatsine mom ya amsa da lfy, dan ita har yanzu haushin shi takeji gani take shi ya hure ma zee kunne har ta nace sai ta aure shi, Dad d'in ma dai a dake ya amsa kamar an masa dole, iya su kadai ya gaisar a falon ,don duk sauran , yan matane qawayen zee sai wannan namamajon best friend d'in zee d'in, zame ta yayi daga jikin shi ya tashi zai haura sama , har zai fara taka step ya tsinci muryar dad na cewa " uhmm Ashmal kake kowa," zee tace "Aslam fa". Yace"koma wanene zo nan inada magana da kai" a gadarence Dad kemai magana, datajar sukurtaka Aslam ya duba ya dawo , zama yayi a kujeran dake facing Dad , a wulaqance Dad ya kalle shi yace"kayi nasara a kaina ka rusamin tsarina kasa na aikata abinda baya cikin tsarin rayuwata a yanzu, wato rabuwa da my one and only daughter ta , well done kayi qoqari , bazan ce ka riqeta da kyau ko amana ko whatever ba , amma ka sani duk abinda ya samu y'ata na cutuwa saina daureka , koda kuwa ciwon Kaine , ka kiyaye, duk abin da ake mata a gidansu shi zaka mata duk abinda tace tana so shi zaka mata dole kaji na gaya maka," Kallon matar shi yayi yace "ku tashi muje kunsan jirgin qarfe goma zamuje bi gashi har nine thirty yayi" cikin kuka zee taje ta rungume dad da mom tana kuka , mom saida ta share hawaye itama saboda kewar yarta, fita sukayi suka shiga motocin su suka bar gidan , zee daqar ta rabu da jikin iyayeta, Aslam kam kasa musu rakiya yayi, yana zaune a falon jikin shi a sanyaye, zee ta shigo ta same shi, Zama tayi kusa da shi tace "honey yunwa nake ji" kallonta yayi yace"ki dauki kazar dana shigo dashi jiya ki mana warming dinsa sai ki had'a tea ki karya dashi" yatsina fuska tayi tace"honey gsky ni bazan iya wani warming d'in kaza yanzu ba a san dai yacce za'ayi, kokuma mu fita kawai muyi breakfast a waje," kamar zai musa mata kawai yace taje ta shirya suje to, miqewa tayi ta haura sama danta shirya, Yana zauneta sakko cikin riga da wando d'amammu, ta yana wani dan siririn gyale a kanta ta saka wani uban hill, Binta yayi da kallo kafin yace"ina zakije a haka " kallon jikinta tayi , ita bata ga wani abun da saya yake mata wannan tambayar ba, tace "na shirya muje ko" yace "kije ki sanya hijabi kinsan yanzu fa ke matar aurece bazaki dinga shiga any how ba" ranta bai so ba haka ta juya , a zuciyarta tana mita Aslam ya fara kaita bango fa, komai tayi sai yace baiyi daidai ba ita fa batason takura , tana daga mai qafa nefa, Zuwa tayi ta dauki after dress ta daura akan kayan don ita Allah ya gani baza ta iya fita da hijabi ba , sai kace wata tsohuwa, Shima bai ce mata komai ba ganin ta rufe qananan kayan , suka fice, Wani babban restaurant sukaje , suka yi order abinda sukeso, Aslam tsakara ya dinga yi, danshi baya son girkin waje , ko girkin qannen shi ba kullum yake ci ba, balle wannan da baisan wasu qazamai suka girka ba, musulmai ne ko arna, ita ko zee hankali kwance take cin abincinta, Suna gamawa suka dawo gida, wanka suka qarayi tare, suka shirya cikin kayan shan iska, dawowa falo sukayi suka zauna, Aslam na zaune kan dogon kujera ita kuma tana kwance, kanta akan cinyarshi, charting takeyi da friend dinta , shi kuma lulawa yayi duniyar tunanin kalaman amir na dazu, ga yunwa dake sakadar cikin sa , dole miqewa yayi ya nufi kitchen da kanshi yayi warming gasasshiyar kazar jiya ya hada tea ya sha , yana ci zee ba kunya tazo ta saka hannu sukaci tare , suka gama ta wanke hannunta ta tashi ko plate d'in shiya dauke , Da rana haka suka qara fita cin abinci, haka da daddare, Aslam haka ya wuni da yunwa, don ba abincin kowa yake iya Ciba, a kwaishi da kenkyami, saidai ya sha drinks da cake, Da daddare ba yanda baiyi ba da zee ta bashi had'in kai taqi, saida ta biye mai suka sha romance kala kala, ta zame jikinta , dole ya hakura ya kwanta, nan kuma tunanin Asmah da kamal ya mai sallama da'ker ya samu bacci ya daukeshi, Washe gari da asuba bayan ya tada ta da'ker ya tafi masallaci kafin ya dawo har ta idar ta koma ta kwanta , tashinta yayi yace tazo zai fara koya mata karatun addini, qin tashi tayi , saida ya mata Jan ido ta taso tana gungumi, Karatun suratul fatiha yace tamai, tiryan tiryan tayi , sai dan kuskure kad'an kad'an daya gyara mata, surori ma ta iya falaqi da nas da iklas, ganin ta iya na sallah , yasa yaci gaba da koya mata alwala da farillansa da sunnonin sa, da yake taga ranshi a had'e yasa ta maida hankalinta sosai har tadan fahimta, iya nan suka tsaya , yace gobe zasu tashi a sallah da farillanata, jibi kuma suyi wanka, A haka suka kwashe sati daya da aure kullum sai sun fita safe rana dare yawan cin abinci, ga tunanin Asmah da kullum yake addabar zuciyarshi, ba abin da yake sonyi kullum sai ganinta, zuwan shi gidan uku baya ganinta taje school, Yau dai Aslam ya gaji da yawan zuwa cin abinci a restaurant , ya qudiri aniyar yau zee zata fara girki, Bayan sun idar da karatun su na asuba daya zamema zee matuqar takura, nan ya sanar mata batun girki yi tayi kamar bata jishi ba , dama duk haqurinta ya gama karewa akan shi kiris take jira, Komawa tayi ta kwanta bayan sun gama karatun ba ita ta farka ba sai sha biyu, lokacin tuni Aslam ya fita ya siyo bread ya had'a tea ya qarya, don ba irin tashin da bai mata ba tana ji ta share, Warwatsi tayi da kayan data cire a nan tsakar d'akin ta, ta shiga toilet tayi wanka , ta shirya cikin kayanta na gado , qananan kaya, Falo ta sakko nan ta samu Aslam zaune yana danna system dinsa, baiyi fushi da ita ba, bud'e mata hannayenshi yayi fuskarshi dauke da murmushi zuwa tayi ta shige jikin shi, yace"gimbiyata kin tashi " murmushi tamai , ki tashi kije kiyi breakfast, OK tace Miqewa tayi taje dining nan ta tarad da kayan tea da sinkin biredi sai kofina duddubawa tayi taga iya su kenan akan dining d'in, dawowa tayi gun Aslam wai bataga abincin akan dining ba , ko suna kitchen ne, Dagowa yayi yace"baki ga biredi da kayan tea akan dining ba " tace "nagani dama sune abincin" yace "eh, tunda baki girka mana ba ai dole tea zamusha" tace"gsky honey ni bazan ci biredi ba , kasan dai yadda zakayi dani don yunwa nakeji, kokuma kaje ka siyo min abinci, " yace "wlh ba inda zani yau inkin matsu ki shiga kitchen a kwai komai ki girka abinda kike buqata " Tana zumbura baki ta nufi kitchen d'in , kwai ta fasa zata soya , ta kusa kwashe awa daya ta fito tana hada uban zufa,da kwan ba'ki kirin da shi duk ya qone gashi ya ji uban gishiri, hada tea tayi ta zauna , loma daya tayi ta furzar dashi, dole dai boredin taci tabar kwan a gurin ta wuce ta kwanta abinta ba shara ba wanke wanke, Aslam saida ya gama aikin da zaiyi a system dinshi ya tashi zai gifta ta kusa da kitchen yaji qauri na tasowa da sauri ya nufi kitchen d'in, frypan d'in data soya kwai ya gani akan hot plate d'in data kunna ta soya kwan, frypan yayi jajur kamar garwashi, da sauri ya qarasa ya kashe hot plate d'in, ya sauke frypan din, Juyowan da zaiyi ya zame ya fad'i qasa tim, kallon qasan yayi fasassun kwaine kusan uku, ruwan su duk ya zube a qasa shi kuma bai kula ba ya taka ya zame, dama ga tsantsin tiles, kitchen d'in yabi da kallo yayi caca yau d'aya da madam ta fara shiga soya kwai, cikin dan fusata ya nufi dakin ta. Ganinta yayi kwance tayi dai dai tana charting da friend d'inta tana kwasan dariya bata ma San ya shigo ba, ga d'akin baza baza da kaya , Qarasawa yayi yasa hannu ya fisge wayarata, dagowa tayi tana kallonshi, cikin dan fushi yace"haba zainab ki tashi ki danyi share share mana kinga kitchen yanda kika barshi ba kyan gani ga falo tunda kikazo gidan nan baki ta'ba share shi ba duk ko ina yayi qura ,kalli dakin nan pls for god sake, bama a batun toilet, haba da Allah komai sai ance kiyi , wa kike son ya gyara miki ke ko kunya bakiji, kiyi baqi," Miqewa tayi daga kwancen data ke, tace"dakata Aslam ban gane me kake nufi wai nice zan dinga wanke wanken kowa? Lallai ma da sake, kalleni sama da qasa banyi kama da yar wanke wanke da shara ba tun wuri inzaka nemo mai aiki ka nemo, danni a gidan mu ko tsinke bana kawar wa, aure na kayi ba baiwar ka bace kaji da kyau, OK sai yanzu na gane dama ka auroni ne dan nazo na dinga maka bauta, to wlh baka isa ba karyarka tasha karya " ran Aslam yayi qololuwar baci a tsawace yace"zainab ni kike gayawa irin wadannan banzayen maganganun," tace "na gaya maka kai waye , duk shiru shirun da kaga ina maka qyale ka kawai nayi amma tunda na fahimci baka da mutunci wlh nima bani da shi, " shammtarsa tayi ta fizge wayarta a hannunshi , ta kwanta taci gaba da dannawa. Ba qaramin kai zuciya nesa Aslam yayi ba da bai rufeta da duka qafa da qulli ba, fita yayi a dakin yaje falo , kasa zama yayi sai safa da marwa yakeyi, daga karshe tausasa zuciyarshi yayi ya dauki tsintsiya da mopa ya share ko ina na part d'in except dakin zee, yayi mopping , ya feffesa air freshener, shi kwata kwata baya son qazanta, kuma babu abida yafi tsana kamar yan aiki a rayuwarshi , saboda kenqaminshi ko dakinshi shi da kanshi yake sharewa a gida ya wanke toilet dinshi da kanshi , kuma haka ya tashi gidansu banda driver da mai gadi bai taba ganin wani ko wata da sunan mai aiki ba ,komai kannen shi da iyayen shi keyi a gidan su, dan haka shima baiga dalilin daukar yar aiki a gidan shiba , yana gamawa dakin shi ya shiga ya yayi wanka yabar gidan , har Allah Allah yakeyi hutun daya dauka a wajen aiki ya cika ya fara fita yana bar mata gidan, Direct family hause ya nufa part mami ya fara shiga suka gaisa ta sanar mishi Mallam dinsu Asmah ya amince zai fara zuwa gida sati da lahadi yana koyama zee karatu amma da safe zai dinga zuwa sabanin su zahra da yake zuwa da yamma, Yana fitowa ya shiga part din ga jiya mama nan suka gaisa tana tambayarshi ina kishiyarta , "wai bazai kawota mu gaisa bane, kodan tasan nafita kyau ne take tsoran zuwa mu gaisa" , dariya yayi yace "wane ke kifi amaryata kyau" tace "ba wani nan inda gaske ne ka kawota mu gwada kyau a gani'dariya ta bashi wai su gwada kyau , aiko ya dara , a nan yadan rage damuwan dake damun shi, yana son hajiya mama, itama tana sonshi sosai cikin jikokinta, daga nan falon alhaji baba yaje suka gaisa kadaran kadahan , don har yanzu ba wani shiri sukeyi ba tun abinda ya faru , na kwanaki, Daga karshe ya yada zango a part din mummy don yau duk yadda za'ayi ko dare zai kai a gidan sai ya tsaya yaga Asmah , don akwai abinda yake son gaya mata, A main falo ya samu mummy , nan ya zauna suka gaisa , ta tambayeshi zee yace tana lpy,ta sake tambayar suna dai zaune lpy ba wani matsala ko , nan ma yace lpy qalau, mummy tace masha Allah, taja bakinta tayi shiru, tunda dama bawai sun saba fira bane ,iyakarsu gaisuwa, Katse shirun yayi da cewa"mummy yaran nan fa su zahra" mummy tace"sunje school,amma inaga suna hanya don sunce yau da wuri zasu dawo, lpy dai ko kake neman su". "Lafiya qalau"ya amsa ma mummy, can kuma ya tambayi abinci, mummy tace bai qarasa yace to ,ganin zaman shirun yayi yawa, wayar shi ya Ciro ya bud'e data ya hau WhatsApp dan ya debe ma kanshi kewa , message ne suka fara rige rgen shigowa, dan yafi sati rabonshi da hawa WhatsApp, saida suka gama shigowa , kaf ya fara bi daya bayan daya yana dubawa Wanda zaiyi reply yayi, daya gama duba message ya shiga status, Da status din kamal ya fara cin karo, wani short video ne na hotunan Asmah kala kala, wani tana murmushi wani ta bata rai wani tana dariya , ga sunan dai barkatai , wani kuma ita dasu batool, wani wakar soyayya na hamisu bireka yasa akan video ,a kasa kuma gurin caption yasa emojin luv da arrow a jiki guda uku💘💘💘, Aslam ji yayi kanshi na juyawa ganin wannan status din na kamal, zuciyarshi yaji ya dauki zafi , Girgiza kai ya fara yana kwafah can kuma yayi tsaki, mummy dai na zaune tana kallonshi, bata ce kala ba amma tana mamakin , meya canza mai mood yanzu yanzu haka Bata gama tunani ba taji yana cewa "lallai kamal watan cin ubanka ya kusa kamawa wlh " mummy dake gefe tace "subhanallahi Aslam kana da hankali" firgigit ya juyo ya kalli mummy , Ashe zancen zucin da yakeyi ya fito fili, ta sake cewa"me kamal d'in ya maka kake cewa, watan cin ubansa ya kama, " miqo ma mummy wayar yayi ya kunna mata video yace " mummy kalla , kalla fa abin ya saka a status dinshi , duk qattan duniya fa sai sun gama ganinta ," mummy na gama kallo ta d'ago tana kallon Aslam duk mamakinshi ya gama cikata tace" ikon Allah to kai ina ruwanka don yasa hotan Asmah a status dinshi, meye naka a ciki meye damuwarka a ciki, ka sanima ko soyayya sukeyi, tunda kai ka qita, sai Allah ya musanya mata da kamal yaron kirki , kai kuma ya musanya maka da zainabu ba shike nan , ai wannan ba abinda ya shafeka bane" Duk da Aslam ya Riga yasan kamal da Asmah , soyayya sukeyi saida kalaman mummy ya dake shi , a fili ya dinga furta "soyayya! soyayya!! Kai ina bazai yuwu ba , yanzu mummy inma soyayyan sukeyi sai ku barsu , bakwa ganin kaman cin amanata akayi kenan yana matsayin qani a gareni ya auri ex wife d'ina" Mummy da mamakin Aslam ya gama kasheta cikin tsawa tace "kaiii Aslam wani irin maganar banza kake yi haka, to a hir dinka inma Asmah da kamal soyayya sukeyi nice wacce zanfi kowa farin ciki da hakan , kai Allah yasa hakan kaje anci amanar taka kayi abinda zakayi, " kamar zaiyi kuka ya dinga maimaita " haba mummy haba mummy haba mummy" mummy tace"don't call me" ya bud'e zai CE wani Abu Asmah tayi sallama a falon, dukan su juyowa sukayi suna kallonta, ita karan kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin wannan kallon........... Pls fan's kuyi haquri kwana biyu muna biki ne ,amma mungama jiya, posting will be continue, insha Allah, no stop Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar sa wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 49 & 50 qarasowa tayi cikin falon tace "mummy sannu da gida " murmushi mummy ta sakar mata tace"yawwa daughter har kun dawo" tace"eh mummy" Kallon Aslam tayi daya qure ta da ido kamar yau ya fara ganinta, ita ta manta da wani Aslam don rabanta da shi tun washe garin auren shi da yazo da safe, "sannu ya Aslam " tace, bata jira amsarsa ba ta haura sama abinta, binta yake da wani irin kallo har ta bace ma ganin sa , Mummy na lura da duk wani motsin shi, ta gama harbo jirginshi kaf, akan Asmah, murmushi tayi a zuciyarta tace"yaro man kaza" Su batool ne suka shigo suna hayaniyar su ,turus sukayi ganin shi a falon su , don rabonsu da shi tun a gurin dinner, gaida shi suka fara yi ya amsa musu kamar yadda ya saba a dake, kamal ne ya shigo shima dauke da jakar Asmah , ganin su a falo ya gaida mummy , miqama Aslam hannu yayi , da'ker ya miqa nashi hannun ganin irin mugun hararan da mummy ke watso mai, ohoo shi kamal bai sanma yana yi ba, Mummy tace" my son kaima har ka dawo ne haka da wuri yau" yace" a'a mummy nad'an samu free time ne , shine nace bari na dauko qannai na da kaina," mummy tace"kako kyauta wlh" murmushi yayi yace "mummy bari na koma" tace "to kamal Allah ya tsare". rarraba idanu ya shiga yi a falon alamar yana neman Abu , duk mummy na hankalce da shi, ganin dai bata falon yasa ya miqama batool jakar ta , yace"batool ga jakan Asmah ki bata " juyawa yayi ya fice a falon yana qara ma mummy sallama, Suma su batool d'aki suka wuce bayan sun gaida mummy, mummy ma miqewa tayi ta nufi kitchen, don ta duba abinci ganin yaranta sun dawo, koda ta gama kuma bata dawo falon ba ta wuce d'akin ta. Aslam ci gaba yayi da zama a falon shi kadai sai saqe-saqe yake, kusan twenty minutes mummy ta dawo ta duba abincin ta yayi ,don haka ta jere a dining, Falon ta dawo tace ma Aslam abincin yayi ready , cewa yayi yace ,"ya qoshi" daga kafad'a mummy tayi , alamar, ko a jikina d'innana, ta wuce dinning abinta, Su batool saida sukayi wanka sukayi sallah , sannan suka fito falon donyin lunch, still Aslam na falon, Yana jin mostin step ana saukowa daga upstairs ya dago kai ya qurawa hanyan ido, kuri idanunshi a kanta baya ko keftawa, Su basu ma san yanayi ba , dinning suka nufa , anan suka tarad da mummy , serving d'insu mummy tayi suka fara yin lunch d'insu hankali kwance, Ganin sun manta da wanzuwarshi a falon ne yasa ya miqe ya nufi dining d'in, mummy ta kalle shi tace "ya akayi ne , ko zaka koma kenan " yace " no zanje part dinmu ne wajen amir, kibra Asmah abincin ta kawo min inta gama' to kawai mummy tace, fita yayi daga sashen mummy ya nufi nasu sashen, Zama yayi a falo yana jiran zuwan Asmah, so yake ya gargad'e ta , ta rabu da kamal taje ta samu mijinta a wani zuri'ar , ba tasu ba, shi daso samune ma ta samu miji acan wani gari inda zai daina ganin ta ko zai samu salama da irin azabtarwar da zuciyarshi ke mai akanta, can kuma wata zuciyar ta gargade shi da cewa kana tunanin zaka iya jure rashin ganinta idan tabar gidan nan, zuwa gidan wani , bama garin minna ba, a fili ya furta" inaaa! zuciyata baza ta lamunta ba," cigaba yayi da cewa "wlh Aslam ka zama ragon maza tunda baza ka iya tursasa zuciyarka akanta ba, don jarumi shine wanda yake iya tursasa zuciyarshi ya hanata abinda take so" tsaki yaja , ya dunqule hannunshi ya naushi iska tare da furta "Ooh shirt" Amir da shigowan shi falon kenan ya qaraso da sauri hango Aslam da yayi zaune yana naushin iska, yace " lafiya Mallam kazo kana mana naushe naushen iska a d'aki, kaida waye, ko amaryar take ce ta kunno ka " kallon amir yayi yace "nida wad'an nan yan rainin wayon ne kamal da Asmah" Amir a zuciyarshi dariyar qeta yakeyi amma a fili yayi kamar yana taya Aslam jin haushi, cikin yanayin nuna jin haushin su yace "me kuma suka qara yi maka yau" Aslam kunno status din kamal yayi ya miqawa Amir yace "kalla fa" Amsar wayar amir yayi yana kallon hotunan saida ya gama kallo tsab ya kashe da wata irin dariyar mugunta harda riqe ciki, a jiye wayar yayi ya tashi tsaye, ya fara rawa yana wakar ♪♪♪abin ya mosta♪ ♪♪♪yana dukan rai♪ ♪♪♪ya bakin ganga♪ ♪♪♪soyayya ce ♥ Qara kunnuwa Aslam yayi ji yake kamar ya shaqe Amir d'in, kozaiji sanyi , A part d'in mummy kam suna gama cin abincin mummy ta had'a ma Aslam abinci a tire ta miqawa amira tace taje ta kaimai , a ranta tana cewa yaro in kasan wata baka San wata ba ai, Batool tace "mummy Asmah fa yace aba " mummy ta mata daquwa tare da cewa "gidan ku batool, ni kurma me ce kenan, banjiba ko" batool tace "sorry mummy" mummy tace "cikin Amira da Asmah wa ya saba aika " batool tace "Amira" tace "to kin gani may be yazo cewa Amira ne ya manta yace Asmah'" Amira na sallama a falon Amir ya tsaya da rawar da yakeyi ya nufota da sauri yana cewa" babyna keda kanki, " murmushi tayi , ya amshi tiren hannunta , gaishe shi tayi ya amsa mata cikin kulawa , tace"abincin ya Aslam' ne mummy tace na kawo mishi". "OK to barin miqa mishi, yanzu kije ki huta anjima zanzo muyi hira kinji" cikin dan jin kunya ta amsa mishi da to sannan ta juya ta wuce, Ajiye abincin a gaban shi Amir yayi yace "bismillah" ji yayi gaba d'aya abincin ya fita ranshi , mummy ta rusa mai shirin shi miqewa yayi ya fice fuuu ya nufi tsohon d'akin , yabar amir nan yana tsokanan shi ko kulashi baiyi ba, Amir yace zama ka dawo hanya ne uban yan taurin kai , zanga karshen wanna girman kan naka, kana son yariya amma girman kai ya hana ka yarda , kuma insha allahu Asmah sai kamal donni bana goyan bayan qarya ehee, Kwanciya yayi a kan tsohon bed d'inshi yayi ruf da ciki, tambayar kanshi ya shiga yi shin wai da gaske sonta nake, to indai wadannan abubuwan da nake ji game da ita sune so, meyasa banjin hakan akan zee da take matata da mukayi auren soyayya, kai ina hakan bazai taba zama so ba, saidai in wani mugun abin tamin, tunda dama jikar Mallam ce, wayar shi ya dauka ya shiga Google don yin bincike akan alamomin soyayya, ,( hmmmm su Mallam Aslam an shiga ajin sanin alamomin soyayya, Allah ya bada sa'a😅) Zee kam yau taga rayuwa, tun karfe biyu take saka ran ganin Aslam, shiru shiru har la'asar , yunwa ta gama sakad'arta, duk tayi laushi, kitchen ta nufa ko zata iya sarrafa wani abun ta samu ta zuba ma tumbinta, indomie ta dauka guda biyu , duba bayan ledan tayi anan taga yadda ake dafawa, nan tayi ta bin method din da taga ni a bayan ledar indomin har ta samu ta kammala da'ker, duk da haka ba wani dadi haka dai ta cuccusa, maganin yunwa , baza baza tayi da kitchen d'in kamar ba dazu Aslam ya gama share wa ba , nan ta bar shi haka ko cokali bata wanke ba , amma dai yanzu ta kashe hot plate d'in, Aslam sai kusan magriba ya gama binciken da zaiyi a Google, duk wani amsa da yake nema ya same shi, yanzu kam ya tabbata son Asmah yakeyi soyayya mai tsanani ma kuwa ,soyayyar da tun baisan kanshi ba tun bai gama zama cikakken mutum ba take fama da ita, soyayyar da ta qullu a gani na farko, soyayyar da ta dauki tsawon shekara goma sha biyar a cikin zuciyarshi tana wahalar da ruhin shi, yanzu wa zai tunkara, ta ina zai fara, yasan duk ta inda yace zai fara akwai babban matsala, shawara d'aya, ya yanke shine zai fara ta kanta , zai fad'a yaqin neman soyayyar ta yasan idan yayi nasara a kanta komai zai iya zuwa mishi da sauqi, (hmmmm Aslam kana ruwa) Sai qarfe takwas Aslam yabar yabar gidan bayan ya cika tumbinsa da abincin da momi ta aiko mai d'azu, saida ya sake biya wa sashen mummy ko zai samu, qara ganin Asmah, amma kowa ma bai samu gani ba , haka ya shiga motar shi ya tayar ya nufo gida cike da fargaban mai zai tarar kuma,, Yana shiga harabar gidan ya tarar ba daya motarshi dake fake a compound din gidan , sharewa yayi ya shiga falon bai kawo komai a ranshi ba, yana shiga baiga zee a falo ba , duba dakinta yayi baibganta ba nan ya shiga kwala mata kira shiru, neman duniya yama zee a gidan bata nan, neman gurin yayi ya zauna a falon ya rafka tagumi, Zee kam tana ganin 7:30 yayi Aslam bai dawoba , taci kwalliyar ta ta dauki key motar shi ta bar gidan a cewarta baza ta iya zama ita d'aya a gida kamar mayya ba, yawanta ta dinga yi kamar yadda ta sabayi a gida, dama duk qafarta qaiqayi take mata kwana biyu nan da tayi bata fita ba, bata nan bata can haka ta dinga yawo , saida taga tara tayi ta biya safara food tayi take away ta kamo hanyar gida Tun a wurin parking ta ga motar da Aslam ya fita da ita alamar yana ciki kenan tabe baki tayi, ta dauki ledarta ta nufi cikin falon , bako sallama ta shiga , Aslam dagowa yayi ya kalleta cikin bacin rai yace"daga ina kike" tace "nad'an fita shan iska ne' yace"wa kika tambaya " tace "bangane wa na tambaya ba, kana nufin idan zan fita a gidan nan saina tambayeka,' yace "of course saboda zamana kikeyi a gidan nan' wani murmushin rainin wayau tayi tace " haba dai sai kace wata qaramar yarinya da duk inda zani saina tambaya"yace " haka kikace ko to wlh kika sake fita a gidan bada izinina ba sai na nuna miki true colour na" tabe baki tayi ta wuce ciki abinta bata ba maganar shi wani muhimmanci ba, A d'akin ta taci abincin ta ta yadda take away din a gurin taci gaba da sana'ar tata na charting, Aslam kam zama yayi abun duniya duk ya ishe shi, lamarin zee ya fara gundirar sa, ganin baida wani abinyi yasa ya ciro wayar shi ya bud'o hotunan Asmah da yayi saving , ya kunna yana kallo' inya qare ya sake danna play kamar wani mara abinyi, Zee ganin shiru shiru Aslam bai shigo ba yasa ta tashi ta biyo bayan shi don ta bashi hakuri a tunanin ta fushi yayi don ta fita ba izini , tana sakkowa falon ta hangoshi ya duqufa yana kallo a waya, baima san ta sakko ba, bi tayi ta bayanshi ta duqa don ganin me yake kallo haka, Bata San sanda ta qunduma wani irin ashar ba ganin , hotunan wata kyakkyawan young lady na yawo akan screen din wayar shi, juyowa yayi da sauri yana kallonta , itama kallonshi tayi tana zazzare ido cike da masifa tace"wace yar iska ce wannan kake kallo".......... 💖More comment more typing💖 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} page 51 & 52 Ranshi ne yayi mugun baci jin kalmar da ta jefi Asmah da shi, na yar iska, cikin tafasan rai yace "waike zainab me yasa baki da hankali ne, saboda ina kallon hotanta shine zaki kirata da yar iska. Kinsan ko wacece ita a gare ni,". Tace "kwarai kuwa yar iska , inba yar iska ba me hotanta yakeyi a wayar mijin wata,inba karuwanci da iskanci ba, naga dai ba kanwarka bace balle ". Miqewa Aslam yayi tsaki ranshi na qara baci , yace "bari kiji wannan da kike kira yar iska karuwa tafi min ke sau dubu" Juyawa yayi da niyar wucewa d'akin shi ya barta nan tsaye, don inyace zai biye mata zai aikata mata abinda zaizo ya dame su daga baya , don bazai iya jurar jin irin zagin cin mutunci da takema Asmah ba, Aiko tayi kukan kura tasha gabanshi taci kwalar shi, don Kalmar daya fad'a na Asmah ta fita so dubu ya dake ta sosai , cikin masifa da zafin kishi tace " karuwar taka ce ta fini sau dubu" ranshi ya fara tafasa cikin tsawa yace"keee jahila karki qara kiranta da karuwa" itama cikin tsawan tace" na fad'a karuwa karuwa karuuu" ji kake tauuu! Ya dauke ta da wani irin gigitaccen marin da bata taba zata ba , Zee bata San sanda ta sake Aslam ta zube a gurin tana kurma ihu ba , don ba qaramin shigarta marin yayi ba, ita zata iya ranstuwa tunda tayi wayau ba wani mahalukin da ya taba marinta a fuska, tsallaketa yayi ya haura sama , yana huci don ranshi in yayi dubu ya baci, Saida ta gama ihun kukanta na kusan awa d'aya ta tashi ta haura sama ,ta dauki wayar ta , ta danna ma Dad call, ko la'akari da can yanzu dare ya tsala batayiba, Dad na daga wayar ta qara fashewa da wani gigitaccen ihu kamar lokacin aka mare ta , Cikin rudewa da tashin hankali Dad ya miqe tsaye yana tambayar ta "daughter lfy?, kina inane? meya same ki? meke faruwa?" Cikin sheshsheqan kuka tace "Dad mari na yayi" Cikin yanayin masifa da bala'i Dad yace"whattttt! Mari,? wani dan kazakaza uban ne ya mare ki" tace "Aslam ne" yace "mijinki kike nufi " tace "eh" yace "yanzu kina inane" tace "d'aki na" yace "passport dinki na kusa " tace "eh Dad" yace "gobe da asuba kibar mishi gidan shi , ki biyo jirgin karfe bakwai na safe ki taho Malaysia, shi kuma ki barni da d'an Abu kazakazan uba , sai na ladaftar da shi ladaf tarwan da bazai qara marmarin Marin wani mahaluki a duniyar nan ba, sai yasan ya taba one and only daughter alhaji abdussalam naira," zee tace "Dad ni bazan iya qarqare kwana a gidan shi ba yanzu zan fita na tafi airport d'in na qarqare kwana zuwa Safiya,". Dad yace "da kyau daughter , haka nake son mutum yasan ciwon kanshi, kar kije airport ki kwana ki kama d'aki a hotel mafi kusa dai zuwa safen" tana share hawaye tace "to Dad " Lallashinta Dad ya dingayi har tayi shiru kafin sukayi sallama, nan Dad ya labartama mom abinda ke faruwa , aiko ranta har yafi na Dad baci, Had'a kayanta tayi cikin qaton trolley ta dauki passport d'inta ta fito nata jan trolley da'ker, Aslam yana shiga d'akin shi zama yayi bakin bed ya rafka tagumi, haka kurum ya dinga jin. Ba dadi akan marin dayama zee bai kamata ya mareta ba, kwanan su nawa da aure da za'ace har an fara kai mari, wata zuciyar kuma tace , ita taja koma mai ka mata akan me zata dinga danganta maka Asman ka da karuwa, wata zuciyar kuma ta bashi shawara akan yaje ya lallasheta, ko ba komai kishin ka ne yasa ta furta wannan kalma akan Asmah, inda bata Sonka baza ta damu ba, Da wannan shawaran ya miqe da nufin zuwa d'akin ta, ganin gilmawanta yayi da qaton akwati tana ja , bin bayan ta yayi yana kira"zee baby, zainab, zee, my luv" Ko kallon shi ba tayi ba balle ta amsa, sauri ya qara ya cimmata a falo, hugging d'inta yayi ta baya, tsayawa tayi cak da tafiyar da takeyi ta saki hannun trolley , ganin haka yasa Aslam cikin rad'a da muryar lallashi da kwantar da hankali cewa, "ina mai baki haquri akan kuskuren dana aikata na marin wannan kyakkyawan fuskar taki, nasani rashin fahimtane ya kaini da aikata miki hakan , kishi nane yasa kika fad'i mummunan kalma akan Asmah, kuma ba'a kishin mutum sai ana sonsa, na sani zainab kina sona nima kuma ina matuqar qaunar ki , auren soyayya mukayi da juna, kar mu bari shaid'an yayi tasiri akan mu, kiyi hakuri zainab ki yafe min," Juyowa tayi ta bashi wani irin kyakkyawan runguma, ta fashe da kuka, ita karan kanta tasan idan tace zata iya rabuwa da Aslam , ta yaudari kanta , bata taba son wani mahaluki kamar yadda take son Aslam ba apart from iyayenta, ta haqura amma ta qullacin wannan yarinyar data yi dalilin da mijinta ya mare ta , ta tsaneta bata kaunarta bata fata ma Allah ya hada ta da ita a zahiri, idan kuwa suka hadu saita tafka mata rashin mutunci, A hankali ya ringa shafa bayanta cikin sigar rarrashi, yana gaya mata kalaman soyayya masu ratsa zuciyar masoyi a kunneta , Luquss tayi a faffadan girjinshi,tana sauke ajiyar nunfashi, anan gurin aka bar trolley ya kwana , ranar ta bashi had'in kan da tunda sukayi aure bata taba, bashi irin shi ba, Aslam ranar yasha bidirin shi kamar ba gobe, sai dai duk inda ya shafo a jikinta sai Asmah ta fado mai a rai, tunani ya dingayi da ace itace da yasan sai yafi haka jin sweet, Iyayen zee ranar basu koma bacci ba saboda, tsabar bacin, rai , ita kuma gata can jikin mijinta suna shàn luv tama manta da abinda ya faru, (Hmmmmm tsakanin miji da mata sai Allah) Washe gari da asubahi , saiga kiran Dad , nan ya tambayeta, tana hotel dinne tace "a'a bata je ba, Aslam din ya bata haquri sun daidaita dama laifinta ne, aiko nan Dad ya rufeta da fad'a abinda bai ta'ba mata ba tun tasowanta,haquri ta shiga bashi, da'ker ya haqura kuma yace duk abinda Aslam ya mata karta kuskura ta qara sanar mai , taje ya yafe ma Aslam ita, ita dai ta yarda tunda baice dole dole ta dawo ba aida sauqi, Kwana uku suka kwashe suna barzar luv , sai nan nan akeyi da juna, Aslam tun ranar bai qara zuwa family hause ba amma duk matsin da zaiyi Asmah nanan maqale cikin zuciyarshi, hotunan ta dake wayarshi bai daina kallo akai akai ba amma saiya faki idon zee gudun sake afkuwar wani matsalan, tsawon kwana ukun nan duk wani aiki na gidan Aslam keyi tun daga shara wanke wanke wankin toilet girki, shi keyi zee kam ko taye don ta riga ta gaya mai ya nemi yan aiki, ita ba baiwa bace, kuma inya gama girki ba kunya har ta fishi ci wani bin, Yau Monday Aslam zaiyi resuming aiki hutunshi ya qare, suna ta shi da safe yace ta shirya ya ajiyeta a gida ta gaida su mummy da yamma inya dawo ya biya ya dakko ta badan tasoba ta amince , don mom ta Riga ta mata hudubar dangin miji basa da mutunci tayi taka tsantsan dasu, Suna isowa mai gadi na bude get motar bello driver ne ya sawo kai ya ya dauko su zahra zai kaisu school, Asmah ce a gaba kusa da bello gaisawa sukeyi yana dan tsokanan ta , tana murmushi kasancewarshi mai yawan barkwanci, Aslam tuni ya hade rai don gani yayi kamar, bellon ma soyayya suke, bello na gaishe shi yayi kamar baiji ba , a ranshi kuwa fadi yake ya zama dole ya bugama bello warning akanta karya qara daukarta a gabon mota haka suna fira kamar wasu masoya, Zee bata kula da su ba amma su sun ganta sarai a gaban mota, sun dauki harya batool tace," nifa gasky matar ya Aslam dinnan haushinta nakeji, kwata kwata bata kwanta min a rai ba, da ganinta zatayi wulaqanci, kuga yadda take wani huhhura hanci a gaban mota" Zahra ta kar'be da cewa" saidai ta wulaqanta su wlh badai ni ba , ba sai ka nuna kasan da mutum zai samu daman wulaqantaka ba, " Amira tace "ay shiyasa ranar da mummy tace yaushe zamuje muga d'akin amarya , nace mata sai mun shirya, haka kawai , muje mijinta ya dizgamu a gabanta ta rainamu,don kunsan halin ya Aslam shima wani bin ba mutunci ne dashi ba" Asmah tace "kudai kar kuyi shedar zur ku bari ta muku kafin ku qaras, " A haka suma qaraso school din su zahra na sussukan zee, Asmah na kare mata (Allah sarki Asmah baiwar Allah ,zee nacen ta kullaceki ke kuma kina nan kina kare mata fad'a😕) Aslam na parking part zee ta fito, tana wani kallon gidan a yatsine, part din mami ya fara kaita , mami ta tarbeta da fara'a tana lale lale da y'ata, daga tsayen da take a wani d'age ta gaida mami da ina kwana, taja bakinta ta tsuke sai bin falon takeyi da kallo, mami ta amsa da "lfy qlau zainab,ya gida ya baqunta , da fatan kuna lafiya ba wani matsala dai ko" ke mai karatu inkin tanka zee ta tanka, shiru tayi tana dai tsaye abinta kamar mashi, Mami a ranta taji ba dadi , amma a fuskarta bata nuna ba , saima cema zee tayi ta zauna mana, zama tayi akan kujera ta daura qafa daya kan daya, Aslam gaba daya kunyan abinda zee tama mami ya gama kamashi, harara ya dinga balla mata , yana mata alamar , ta amsa ma mami mana, tabe baki tayi ta dauke kai daga kallon shi, Aslam gaisar da mami yayi a ladafce kamar yadda ya saba, mami ta amsa mai cike da kulawa, yace" mami gata nan in tayi ta shishiga sauran part's d'in ta gaishesu, ni zan wuce office sai na dawo' mami "tamai addu'a da fatan alkhairi " yasa kai ya wuce, Ruwa da leman kwalba mami ta gabatar ma zee, ba sannu bare nagode ta dauka ta sha, Dan zama mami tayi tana d'an mata hiri , nan ma shiru, sai charting dinta take, mami a ranta tace, lallai Allah ya had'a Aslam da yar iskan mata, Ganin abin zee d'in harda rainin arziki yasa mami fita sabgarta ,karshema, ta tashi ta bar mata falon, Aslam na office amma tunanin Asmah da bello da takema murmushi yaqi barin barin brain dinshi, can dai ya kasa haquri ,ya dauki waya ya kira bello , ya wanke Shi tas ba laifin fari bana baqi , ya kuma tamabyi lokacin da zai koma ya daukosu, gaya mai bello yayi, nan yace kar yaje shi zaije ya dauko su da kanshi , shidai bello mamaki ya gama kashe shi gaba daya. a ranshi yace wata sabuwa inji yan caca, meke shirin faruwa ne haka, yanzu kamal ya kirashi yace kar yaje dauko su Asmah shi zaije, dama sun saba haka da kamal d'in, yanzu kuma ga Aslam shima, jan dan bakin shi yayi ya tsuke koma meye gaba zai nuna inda rai da lpy. Uku daidai Aslam ya isa school d'in su Asmah , Asmah da zahra department d'insu daya dan haka, tare suka fito daga lecture da suka shiga 2 to 3 pm, nufo inda ya kamal ko Mallam bello suke tsayawa in sunzo daukarsu sukayi, Tun daga nesa zahra ta fara hango kamar ya Aslam ne jingine jikin motar shi, a gurin da aka saba jiransu in anzo daukarsu. Suna qara matsowa kuwa ta tabbatar shi d'in ne, riqe hannun Asmah tayi gam cikin rada rada tace"Asmah ya Aslam' itama sai lokacin ta kula dashi, zahra tace "meya kawo shi nan kuma Allah yasa dai lfy" Qarasawa sukayi , dagowa yayi idanshi akanta itama dai kallon shi takeyi , wani kyakkyawan murmushi ne ya subuce mai Wanda shi karan kanshi baisan sanda hakan ta faruba, ba Asmah da akama murmushin ba hatta zahra da ke gefenta saida shock ya kamata ta zaro ido, Asmah kam suman tsaye tayi tunda take a rayuwarta zata iya cewa yaune rana ta farko da Aslam ya mata murmushi mai sunan murmushi ba murmushin mugunta ba, Husnah ya furta a kan la'b'bansa , husnah ta maimaita sunan kamar yadda ya fad'a, dage mata gira d'aya yace yes my husnah............ Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO ~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah ya jigan iyayen mu} Page 53 & 54 Waige waige ta farayi alamar tana neman wacce ya kira da my husnah, daidai nan su batool suka qaraso , suma ganin Aslam ya basu mamaki , gaidashi sukayi, sannan suka ce, zahra , da Asmah suzo suje ya kamal na jiran su a get, yau bazai qaraso ciki ba sauri yakeyi, kafinma su gama rufe baki tuni Asmah ta kama hanyar get, ranta fal mamakin Aslam, to kodai kunnenta ne ya jiyo mata karya, kai ina kunnenta ne ,bataji mai ya fad'a da kyau bane, anan ta watsar da maganan bata wani dauke shi da muhimmanci balle ya dameta, haka suka qarasa har wurin motar ya kamal , suka shiga ya ja su zuwa gida, Aslam kam suna barin shi a wurin , ya naushi iska , ranshi na matuqar tafasa , ganin yadda ta wuce ta barshi a tsaye kamar wani sakarai , a fili ya furta wato daga an ambaci sunan shi ko tsayawa ta saurareni batayiba ta tafi gareshi ni kuma ta barni a tsaye kamar mara aikin yi ko, zakuyi bayani wlh Daga ke har shi yau zan kawo karshen wannan cin amanar naku zabura yayi ya fad'a mota ya bi bayan su kamal a guje, kamar ana binshi a baya, ranshi na tafasa, yau zaije ya samu kamal ayi wacce za'ayi , yau za'ayita ta qare komai zai faru ya dad'e bai faruba Zee taga idi yau, dan mami tunda ta haura sama bata qara waiwayarta ba , yunwa ne ya fara sakadarta, tun tana daurewa, hardai ta miqe zaune ta rafka tagumi , da hannu bibbiyu, ta ajiye waya , juice da ruwan da mami ta ajiye mata d'azu tuni ta shanye, sai goru nan, Ya kamal na fakin ,suka fito zasu wuce, Jakarta ya dauka kamar yadda ya saba har ta kama hanya zata bi bayan su zahra ,ya kira sunanta da "my Asmah", juyowa tayi tana kallon shi da murmushi a fuskarta itama cikin sassanyar daddadar muryarta tace "na,am my kamal" murmushin fuskarshi ne ya fad'ad'a, bata taba kiranshi da wannan sunan ba sai yau wani dad'i yaji ya lullubeshi, Yace "me Aslam yajeyi a makarantarku" dan shiru tayi kafin tace"nima ban sani ba kawai ganin shi mukayi kuma kafin wata magana ta had'a mu, ka iso shi kenan muka wuce muka barshi a can" wani d'an murmushi takaici kamal ya saki kafin yace"ni nasan meya kawo shi, na riga na gama gane take takensa tun ba yau ba , amma kuma na lashi takobin wannan karan bazai taba bari yayi nasara a kaina, inason na roqeki wata alfarama dan Allah asma,u" kallan shi tayi da daradaran idanunta , da suka fi komai fusgar mutum idan yana kallonta, cikin sanyi jiki tace"wacce irin alfarma ce wannan ya kamal, ka fad'e ta, indai batafi qarfina ba zan maka bi'izinillah" yace "inaso ki bani dama na sanar ma magabatan mu batun soyyayar mu, domin na fara ganin alamun wasu suna mana bita da kulli" bata fahimci inda maganarsa ya dosa ba amma bata wani tsaurara binkice ba tace"nà amince maka indai hakan zai faranta ranka masoyina" don ba qarya itama yanzu ba kadan ba take jin ya kamal din har cikin zuciyarata , saboda kulawar da yake nuna mata da irin soyayyar da yake nuna mata , da irin kyautatawan shi a gareta, har , yakai matakin da zata iya hakura da karatun ta, ta auri Kamal , ta amince daga baya ta qarqare karatun a d'akin sa , tunda tasan ba zai hana ta ba, Kallonta yayi cikin tsananain farin ciki fuskarshi na qara fad'ad'a da murmushi yace"da gaske kike my luv " gyada mai kai tayi itama tana murmushi, Daidai lokacin Aslam ya danno kan motar shi cikin gidan a guje , hangosu suna sakarma juna murmushi ya qara fusatashi aikuwa ya nufo Kansu gadan gadan , zuciyarshi na gaya mai yabi takan kamal kawai kowa ya huta , Da wani irin zafin nama kamal ya kauce ganin mota ya nufosa gadan gadan, Asmah kam duqewa tayi ta daura hannu akai ta Riga ta gama sadaqarwa ta mutu kawai, daidai da ita ya taka wani irin mahaukacin birki , A wani irin fusace ya fu bud'e murfin motar ya fito , zagayowa yayi ya kama , hunnun Asmah cikin bacin rai da rufewar ido ya figeta zuwa part din mummy , da sauri kamal ya rufa musu baya, Dan Allah kuyi hakuri wlh kwana biyu bana samun time sosai ne , kuyi manage da wannan ba yawa, karkuyi fushi fa mutanena😄 Oum ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa Mahaifiya, Allah kajiqan iyayen,} Page 55 & 65 Kokawar fisge hannunta takeyi amma ta kasa, karfi ba d'aya ba , bai tsaya ko ina ba sai tsakiyar falon mummy, Mummy dake zaune a falo tana amsa kiran daddy ta wayar tafi da gidan ka(telephone) dake falon sai ganin Aslam tayi ya shigo a fujajan. riqe da hannun Asmah yana janta ita kuma tana ciccijewa, Bata san sanda tayi wurgi da wayar hannunta ba , ta miqe tsaye tana sallallami, Sakin hannunta yayi yana huci ya nunata da yatsa , yace " ke wlh baki isa ba karyarki tasha karya ki wulaqantani, nayi tattaki nabar tarin aiyukan dana keda shi a office na tafi makarantarku saboda ke , amma kika wulaqanta ni kika wuce kika barni , kika bi wani banza maci amana ko, ta daga ke har shi zanyi maganin ku , baza ku mayar dani mahaukaci ba wlh" Mummy ce cikin tsawa ta katse shi da cewa " kai Aslam wai meke damunka ne haka, kana cikin haiyacin ka kuwa, " yace "kwarai mummy cikin haiyacina nake, yarinyar nan tana neman ta zautar dani , mummy soyayya fa takeyi da kamal , " mummy tace " toh so what! Idan tana soyayya da kamal,ina ruwanka meya shafeka, yace " mummy bazan iya jurewa bane zuciyata zata fashe idan na ganta tare da ko wani d'a namiji bama kamal kadai ba " mummy tace " akan wani dalilin zuciyarka zata fashe, kai asuwa" yace " zuciyata zata fashe ne a dalilin ina sonta ina kaunarta, bazan iya jurar ko wani namiji ya rabeta ba , mummy bazan iya ba " Mummy kamar saukar aradu taji zancen shi ya daki zuciyar ta, duk da ta ruga ta hasashe wani Abu dama, cikin wani irin mamaki mummy tace "what! me kace, Aslam kanada hankali kuwa , ta barin gaya maka idan mafarki kakeyi ka farka kada ma ka bari wani yaji wannan maganar a cikin gidan nan," Asmah kam suman tsaye tayi jin yau Aslam da bakin sa yake furta yana sonta yana qaunarta , bata san sanda ta bude baki tace ",wlh mummy karya yakeyi , ya Aslam baya sona baya kaunata, ba kuma zai taba sona ba , ya tsaneni , tun ban mallaki hankalin kaina ba nasan da hakan, kamar yadda nima na tsaneshi , bana sonsa bana kaunarsa kuma bazan taba sonsa ba, har qarshen rayuwa ta, mummy ya kamal nake so shine masoyina na hakika , shi nake kauna , mummy kuma da shi zan rayu" Kamar saukar wuta a maqoshi haka Aslam ya dingajin saukar kalaman ta cikin zuciyarshi, cikin wani irin zafin kishi da rufewar ido , ya isa gabanta ya shaqo wuyarta , cikin managa ihu ihu yake cewa " ni kike cewa baki so husnah, ni kike cewa kin tsana bazaki taba soba har warshen rayuwarki , a gabana kike cewa kina son wani d'a namiji bani ba , to wlh sai kin sona ko kina so ko bakya so sai kin aure ni kin zauna dani har qarshen rayuwarki , domin kuwa domin ni kadai aka halicce ki" Kokawar kwatar kanta takeyi a hannunshi ta kasa , sai zazzare I do takeyi, mummy cikin kururuwa ta daura hannu a kai tana kiran sunan Allah , Cikin tsananin fusata da zafin zuciya kamal yayi wani sufa ya shaqi wuyan Aslam ta baya muguwar shaka kuwa, baisan sanda ya saki Asmah ba yana sake ta ta tafi sululu zata fadi , batool da Amira , da hayaniyar da suka ji daga falo ya fito dasu daga d'aki ba shiru, suka tarota ta fad'o jikin su, Kokawa kwatar kanshi ya shiga yi har Allah ya bashi sa'a , nan kuma aka shiga kaima juna kulli, baji ba gani, dambe sosai kamar wasu yan wrestling ,ko wanne zuciya na diban shi , basu ko sauraron kukan da mummy ta keyi tana kiran sunan su, zahra da saukowarta kenan daga upstairs, don sanda su batool suka fito tana toilet , ganin abinda ke faruwa ta fita compound din gida da gudu tana kiran sunan duk Wanda ya zo mata baki cikin mutanen gidan, Daddy ne ya fito daga part dinsa sanye da jallabiya ta baibai, kallo d'aya zakasan a matuqar fusace yake, tun lokacin da yake waya da mummy , yaji ta yarda wayar ta kama sallallami, ya kasa kunne yana sauraran meke faruwa , gaba , daya ji yake kamar in ya riqe Aslam ya kama duka kar ya barshi har saiya kwantar dashi a asibiti, Zahra karo tayi da Abba da shima dawowar shi kenan daga aiki , riqeta yayi ganin a rude take yana tambayar ta meke faruwa kasa managa tayi sai nuna mai part d'in mummy kawai takeyi, Daidai nan zee da mami ma suka qaraso garesu , ganin tana nuna part din mummy yasa da gudu suka dunguma zuwa can, Daddy na shiga falon , daidai lokacin Aslam ya samu sa'ar kaima kamal naushi a gefen kumatu , take baking shi ya fashe yana tsartuwar jini, wani gigitaccen tsawa, daddy ya daka musu ba shiri suka rabu , kowa na sauke munfashin fusata, qarasawa gaban Aslam yayi ya daukeshi da wani irin gigitaccen mari kafin ya dawo haiyacinsa ya qara daukesa da wasu marukan har gida biyu, Dafe kumatu yayi , yana bin daddy da wani irin kallo, nuna shi daddy yayi da hannu cikin tsakanin fusata, yace" fita kabar gidan nan kafin na rufe idona na bud'e mutumin banza mutumin hofi" bude baki yayi zaiyi magana , daddy ya katseshi da cewa " I said get out from dis hause" Abba ne ya qaraso yana tambayar meke faruwa ne , kowa shiru yayi an rasa Wanda zai maida ba'asi , Daidai nan alhaji baba ya qaraso falon hajiya mama na rufa mai baya, ganin da ya musu a tsaye cirko cirko yasan ba lafiya ba , yana zaune a falon shi, shida hajiya mama , bello ya shigo cikin rudewa yake shaida mai wani Abu na faruwa a part din daddy , don a idonshi zahra ta fito tana neman agajin mutanen gidan, Bai tambayi ba'asi ba saida ya nemi guri ya zauna , umartan su yayi da cewa kowa ya zauna, ba musu kuwa kowa ya nemi guri ya zauna a qasa daddy da Abba suka zauna a qasa wurin qafar alhaji baba, suka sakashi a tsakiya, Asmah na kwance jikin mummy , su batool ma duk suna rakube kusa da mummy su, zee ma na zaune kusa da mami, kamal da Aslam ma duk suna zaune , Gyaran murya alhaji baba yayi zai fara magana saiga Amir ya shigo shima guri ya samu ya zauna kusa da Aslam, Kallon mummy alhaji baba yayi yace "Aisha meke faruwa "mummy kwallar da ta taru a idontane ya sauko kan kumatunta, share wa tayi kafin cikin sanyi murya ta labartawa alhaji baba abinda ya faru A to Z shuru falon ya dauka , kowa da saqe saqen da yakeyi a ransa , alhaji baba baiba kowa daman magana ba sai mummy don haka ba wanda ya isa yayi magana a d'akin, Mummy na gama wa, alhaji baba ya watsa ma Aslam wani mugun kallo, wanda yasa gaban Aslam yankewa ya fadi , cikin murya mai dauke da amon bacin rai yace" ina fatan har yanzu baka manta da maganar dana taba fada maka watannini baya da suka shud'e ba, to idan ma ka manta bari na tuna maka, ni Muhammad nace ko bayan raina ban yarda , wani cikin yayana ya qara daura maka aure da Asma'u ba , ballantana kuma ina Raye da raina da lafiya ta," wani murmushin takaici alhaji baba yayi , ya maida dunansa kan kamal yace" kamaluldeen da gaskene kaida Asma'u kuna son junan ku, " kamal yace"eh alhaji, har mun dai daita ta bani dama naje na samu ,su daddy da maganar," Alhaji baba yace "masha Allah , komai yayi daidai, ni Muhammad, a matsayina na wanda aka wakilta na aurad da Asma'u na baka aurenta kuma na tsayar da lokaci nan da wata uku masu zuwa insha Allah," Kusan gaba d'aya muatanen falon saida fuskarsu ta nuna farin cikin a bayyane, except Aslam da yayi kamar ya kurma ihu Ci gaba alhaji baba yayi da cewa Abu na gaba" suma y'an uwan Asma'u wato y'an biyu da kuma Amira na basu nan da wata daya daya ko wacce ta gabatar da nata manemin domin kuwa gaba daya za'a had'a ayi bikin tare da na Asma'u da kamalu idan yaso kowacce taje ta qarqare karatun ta a dakin mijinta, duk kuma wacce bata da tsayayye ni zan Neman mata miji na gari na hada ta da shi, na riga na gama yanke wannan hukuncin koda na mutu yau kada a fasa ai wayar da wannan lamari" Gaba daya kowa na falon yayi farin cikin , saidai zuciyar yan matan mummy cike take da fargaba, ko wacce na tunanin wa zata gabatar a matsayin mijin aure , a cikin wata d'aya masu zuwa, har gwara amira don jiya jiyan nan ya Amir ya gabatar mata da kanshi a matsayin masoyinta , yanzu haka ma bata bashi amsa ba, duk da ta riga ta gama aminta dashi, a cikin zuciyata , dama tun can ya amir na matuqar burgeta, Amir ne ya dan sunkuyar dakai yana Sosa keya kamar wani Mara gaskiya , yace "Allah ya qarama alhaji lpy da Nisan kwana inada watsa magana mai muhimmanci da nake son nima na gabatar maku, na tabbata zata sanyaku farin ciki matuqa," Kallo ne ya koma kan amir d'in, alhaji baba yace" fad'i maganarka kai tsaye Amiru nuna saurarenka" Qara qasa yayi da kai yace" nima nida kanwata yar uwata Amira mun daidaita kanmu" Masha Allah masha Allah haka kowa na falon yake fadi tun daga kan alhaji baba, hajiya mama, daddy, mummy, Abba, mami,kowannen su yayi matuqar farin ciki da jin wannan batu na Amir, Murmushin jin dad'i alhaji baba yayi yace"masha Allah Abu yayi kyau Amiru Allah ya tabbatar mana da alkairi" Da amin aka shiga amsa wa. Kowa zuciyarshi wasai amma manta da batun wani Aslam a fallon, Miqewa yayi a fusace ya kalli alhaji baba yace " dama na Dade da sanin baka kaunata a cikin ahlinka , to shiken nan Abu yayi kyau, ga gidanka nan yau zanbar makakaida yayanka , daga rana mai kama ta yau bazan qara tako qafa ta cikin gidan nan ba, " kafin ya kai karshen rashin kunyarshi tuni , daddy ya miqe ya qara sauke mishi wasu zafafan zarukan da sukafi na dazu shigarshi matuqar , hankada shi daddy yayi ya fitar dashi daga fallon ya wugo shi waje, Cikin matuqar fusata ya nufi motar shi ko waiwayen baya bai qarayi ba, ganin haka yasa mami miqar da zee tsaye tace "zainabu kibi mijin ki" Da sauri ta rufa mai baya don ita wannan hukinci na alhaji baba ba qaramin dadi ya mata ba , ji takeyi kamar ta goya alhaji baba ta zaga garin minna....... Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanny book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 57 & 58 Da mahaukacin gudu ya bar gidan bayan zee ta shiga motar , saura kadan yabi takan me gadi, Allah ne kadai ya kaisu gida lpy don Aslam gaba d'aya baya cikin haiyacin sa, Yana yin parking ya fice a fusace ko qala baice ma zee ba, Direct d'akin sa ya nufa ya kulle kofar ta ciki ya bar key a jiki, Kan bed dinshi ya fad'a rigingine , ya shiga sauke wasu irin ajiyar zuciya, kai da kaji kasan bana lfy bane Zee kam ganin ya fice baice mata kala ba , ko ajikin ta, hakan ko kadan bai dameta, ita yau jinta takeyi wasai , saima wani nishadi na musamma daya risketa , a yau Wanda ta dad'e batayi irin shi ba, Cikin yan waqe waqenta tana rausaya ta shiga falon, ganin baya nan , ta ta'be, ta haura sama abinta, dakin ta ta shiga tayi wanka tayi sallan azahar da la'asar, sai lokacin ma ta tuna da yunwan da takeji dazu, Kitchen taje ta dafa indomie ta zauna taci , har lokacin bataji motsin Aslam ba, nan tabàr plate d'in ta wuce dakinta ta kwanta ta kama sana'ar tata (charting), Har dare ba motsin Aslam ba labari, fitowa zee tayi dan ta samawa cikinta abin tabawa, har ta wuce qofar d'akin Aslam , ko me ta tuna kuma ta dawo , tura qofar tayi ta jishi a kulle da key, knocking ta shiga yi shiru ba amsa, daqe kafada tayi alamar , kai ka sani dinnan , Kitchen taje still indomie ta qara dafawa, don shi kadai ta iya , zama tayi ta cuccusa abinta tasha lemo da ruwa , ta qara gaba abinta , kamar d'azu, Da safe sai gurin qarfe goma zee ta farka tayi matuqar mamakin ganin gari ya waye,kenan yau Aslam bai tasheta sallan asuba bane kome, A bangaren Aslam kam tun jiya da ya shiga d'aki ya kulle , ba abinda yakeyi sai aikin tunani, takura zuciyarshi yayida kwakwalwarshi , da tunani da damuwa, ga baci ba sha , don da safe bai karya ya tafi office, kuma a office d'in coffee kawai ya sha, hakan yayi sanadin da zazzafan zazzabi ya rife shi ruf, Kan gari ya waye tuni ya fice a hayyacinsa , sai wuraren goman safe ya samu dan sauqi ya watsa ruwan sanyi, yayi sallah ,first aid box din dake d'akin ya duba ya dauki , maganin zazzabi dana ulcer yasha bayan yad'an sha ruwan tea da cake, Komawa yayi ya kwanta yaci gaba daga inda ya tsaya jiya, a tunani, Zee bayan tayi wanka , ta fito falo ganin ba Aslam, yasa tayi tunanin ko ya wuce office ne abinshi, komai bata ji aranta ba , saima cewa da tayi a fili, "kai ka Sani,nidai tunda , baba tsoho ya hanaka, auren wannan yar iskar yarinyar, mai kama da 'kwara, ya gama min komai duniya,". Ji tayi baza ta iya cin indomie da safe ba don haka , ta koma d'aki ta dauko makullin mota , saida ta isa parking lot d'in taga motar Aslam alamar, yana cikin gidan bai fita ba, Ficewa tayi abinta daga gidan ko ajikinta, Aslam yana d'akin shi kwance yaji tashin motar zee alamar tabar gidan, Tsaki ya ja a fili ya gyara kwanciya, yaci gaba da tunanin mafita da yadda zaiyi ya cire soyayyar Asmah a zuciyarshi , kozai samu salama daga irin azalzalan da take mishi ba dare ba rana, Yau wasai kamal ya farka daga barci duk wani fargaban shi , ya kau ji yake kamar ma andaura auren shi da Asmah an gama, shiya kaisu school , kuma shiya daukosu, Su zahra sai tsiya sukema Asmah wai dama soyayya takeyi da ya kamal shine ta 'boye musu, Da misalin qarfe hudu na la'asar uncle nura mijin ya rabi'ah ya faka dalleliyar motar shi a parking lot d'in gidan surukan nasa, fitowa sukayi shida abokin tafiyar nashi, ba kowa bane kuwa face barrister Adam , Suna fitowa abban hanifa ya wurgawa brr Adam harara yace" hankalinka ya kwanta yanzu, kasaka ni kawo ziyara gidan surukai ba shi" murmushi brr Adam yayi " sorry bestie na tallafi ruhin abokin ka wlh in bankai kaina ga iyayenta ba yau bazan iya rintsawa ba, ka wala ni da yawa , kaji tausayin mijin maryama, angon fatima zahra to be, insha Allah" Bello ne ya musu iso zuwa part din daddy , da fara'a daddy ya tarbesu, gaida shi sukayi cikin mutuntawa kamar yadda suka saba, Bayan sundan taba hira kad'an , abban hanifa ya gabatar da buqatar su , na neman izinin shi game da neman auren zahra, Daddy yaji dadin wannan lamari, saboda ya dad'e da sanin brr Adam a gurin abban hanifa , yasan mutumin kirkine kamar yadda abban hanifa ya kasance mutumin kirki, don hausawa kance , in kana son sanin halin mutum ka dubi abokin sa, Take ya tabbatar musu ba'ayi mata miji ba , kuma ya basu izini su naimi soyayyar ta da yardarta. Nan suka shiga zuba godiya kamar bakinsu zai tsinke, sai da daddy yace ya isa , sallama sukayi da daddy suka fito, da niyar zasu dawo gobe, Suna fitowa brr ya dubi abban hanifa , yace "yanzu sai mu shiga ko " abban hanifa yace "ina?" Yace "Ciki mana, muje na ganta , na gaya mata kasan ance da zafi zafi akan daki karfe" harara abban hanifa ya watsa mai yace" to ai sai ka shiga ka sameni a gida " ya fada yana bud'e motar shi ya shiga, shima bar Adam din shiga yayi , suka fice , a hanya yake cewa" to wlh kuwa yau a minna zan kwana, ni da komawa bidda har sai na samu yardar ta da soyyayar ta," abban hanifa tace" in kuma baka samu bafa " baisan sanda yakai hannu ya bame mai baki ba yace" annabin rahama yace fadi alkhairi ko kayi shiru, insha Allah zan samu amincewarta , bakin ka ya sari dutsen faida" abban hanifa yace" to nidai ba ruwana, ka tattara ka koma bidda gobe ka dawo , don kar ka had'a ni da maryama taga kamar da ni aka had'a baki aka mata kishiya , duk da dai nasan komai zan fad'a ba yarda zatayi dani ba , tunda kanwar matata ce, qilama tace ni na had'a ku" dariya brr Adam yayi yace " ohoo dai kai ka sani, ai kunfi kusa, inagama kai zan dauka ma kakai mata kayan fad'an kishiya" abban hanifa yace "rufamin asiri ni bana zuwa irin wad'anan abubuwan , bazan manta ba wani abokina , da ya raka abokin shi kai kayan fad'an kishi ,waishi irin zai mata wa'azi , da makaranta suka tashi ta shaqo shi, saida yayi kwana uku a asibiti ana qara mai ruwa" brr Adam kam mai zaiyi ba dariya ba, cikin dariya yace"kaidai wlh matsora cine abokina",abban hanifa yace"eh naji komai zakace kace, ai mata akan kiyashi zasu iyayin komai , saidai kuma wasu nasu kishin da sauqi akan na wasu," da haka suka qaraso , gida, nan suka qarqare wuni sai dare abban hanifa ya kaishi masauki dan firr qin kwana gidan yayi, Aslam yauma haka ya kwana cikin mugun ciwo Wanda har yaso yafi na jiya,gaba daya ya fad'a cikin kanqanin lokaci, ya qara haske yayi fiyat dashi, yau abincin ma qin zama yayi a cikin sa , da yasha shayi amai yata kwara wa harda jini jini a cikin aman, gaba d'aya ya gama galabaita, gashi ya saka wayar shi a airplane mood, ba Wanda zai iya kiransa balle asan halin da yake ciki, Kalaman alhaji baba duk bayan minute amsa kuwwa sukeyi a kunnen shi(ni Muhammad , a mastayina na Wanda aka wakilta ya aurad da Asma'u , na baka aurenta kuma na sanya lokaci nan da wata uku masu zuwa) yanzu shike nan ya rasa husnah kenan , yanzu haka zai zuba ido yana ji yana gani husnah ta auri wani d'a namiji ba shi ba, kai ina hakan bazai taba yuwuwa ba ya zama dole yayi wani Abu akan lamarin nan, Tunawa yayi da waye alhaji baba , tsayyaye ne kaifi daya, baya magana biyu, take sabon zazzabi ya lullubeshi, wayar shi ya zaro ya kunna hotunan Asmah na rannan yana kallo , da haka ya d'an samu relief, Zee bata dawo gidan ba sai bayan isha'i don yau garin yawonta ta hadu da wata qawa, wai ita bebalo,bazawara ce, auren ta biyar taqi zama, sai shegen yawo kwararo kwararo lungu lungu, bata nan bata cen, haka suka kulla kàwance, sukayi musayar numbar waya ( dama ance sai hali yazo d'aya ake abota) Me gadi ne bayan sun gaisa yake tambayar ta Aslam , ganin tun shekaran jiya da ya shigo bai qara ganin fitar shi ba, sai lokacin ta tuna rabonta dashi tun shekaran jiya, tace"kana nufin tunda na fita yana cikin gidan nan bai fita ba?" megadi yace "eh hajiya ,nima naga shirun yayi yawa shiyasa na tambaya ko lfy" "Ba komai" ta amsa mai , sannan ta nufi cikin gidan zuciyata babu dad'i, duk da tasan akan wannan shegiyar yarinyar ya saka kanshi cikin wannan halin, D'akin shi ta fara biyawa tayi knocking yafi sau goma , yana jinta amma ya shareta , dan itama yanzu haushinta yakeji gaba d'aya, kowa na duniya haushin su yake ji Asmah kadai yake ji da gani, Ganin yaqi tankata yasa ta wuce abinta , duk da zuwa yanzu lamarin ya fara bata tsoro, Washe gari ma haka aka maimaita yaqi bude qofa , ita kuma ganin haka ta shirya ta fita yawanta da sabuwar qawarta beebalo, Misalin qarfe goma na safe Dr bash yayi parking motar shi a harabar gidan su Aslam , kwana uku kenan yana neman Aslam ba amo ba lbr har office dinsa yaje amma ance rabonshi da office yau kwana uku daga can ne ya nufa gida dan ya tambaya ko lafiya, Part d'in samarin gidan ya nufa ba, ba kowa kamal da Amir duka basa nan, kamal na gurin aiki Amir kuma ya fita, ganin haka yasa ya nufi sashen mummy, A falo yasamu mummy gaisawa sukayi cikin mutunta juna, mummy ta tambayeshi hajiyan shi, da aikin shi duka ya amsa mata da lpy qlau, Hira suka ta'ba mummy tace"abokin ka dai yayi aure kaima saika fito da taka matar ka aura , tunda dai anyi karatun angama har an kama aiki , Ai kuma sai a godeme Allah a fito da mata ayi aure" cikin dan jin kunya yace "mummy insha Allah muna dubawa , a taya mu da addu'a Allah ya bamu ta gari" mummy tace" amin amin bashir Allah ya baka ta gari" amsawa yayi da amin sannan yace "mummy mutumin nazo nima tun shekaran jiya nake kiran wayar a kashe , naje office kuma aka ce yau kwana uku rabonsa da office shine nazo in duba Allah dai yasa lpy " tabe baki mummy tayi tace"lpy qalau bashir ai lafiya ke buyà inji hausawa" bashir yace "mummy dadai an bincika tunda bawai ya saba yin hakan bane" tace "bashir wannan abokin naka sai a hankali "nan ta labarta wa bashir abinda ke faruwa, Sai lokacin bashir yasan wacece Asmah daya mace akanta, maganarta yana d'aya daga cikin dalilin da yasa yake neman Aslam ruwa a jallo, jin kuma an bada ta ga kamal harma an saka lokacin biki , a take ya kabbeta daga cikin zuciyarshi, ya dauki dangana da haquri, duk da yasan ba lallai ne ya manta da ita farat d'aya ba, Bashir yace" mummy a mana afuwa munyi kuskure kar kiyi fishi damu fushinki babban matsalace a garemu, wlh ni karan kaina mummy wata ran nakan rasa gane kàn Aslam , adai cigaba da mana addu'a" mummy tace"ai kudinne bashir kuna kai mutane iyaka, ace kune manya a gida amma qanana ma sun fiku hankali" Nan dai bashir ya shiga ba mummy hakuri, kafin ya miqe da niyar wucewa ya kuma CE zaije can gidan Aslam d'in ya gani, Dai dai lokacin motar kamal daya d'akkosu daga school ya paker a harabar gidan , a guje batool ta balle murfin motar ta kwasa da gudu zuwa part din mummy, saboda tsokanan zahra da ta dingayi a hanya , akan wani lecturer daya ce yana sonta ,ita kuma zahra ta tsani mutumin kwata kwata ko zance bataso,shine fa batool ta samu taketa guma mata,ita kuma ta cika tam kamar ta fashe jira kawai takeyi ya kamal yayi parking su yada hali, ita kuma sanin bata da gsky yasa ta kwasa da gudu cikin gida, Daidai bashir ya sawo kai zai fito itama ta sawo zata shigo, yauma wani karon suka sake maimaitawa kamar dai rannan, Kowannen su ja da baya yayi , yana Sosa goshi, idanun su ne ya sarqe dana juna , cikin matuqar mamaki har suna hada baki gurin furta , "you again"............. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO ~ FREE BOOK { na sadaukar da wannan lillafin ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen Page 59 & 60 Da kallon mamaki suke bin junan su, lokacin da wancen karon ya faru ya ɗaɗe bai manta fuskar yarinyar ba , tsiwar ta da rashin kunyar ta ya dade yana bashi mamaki, Itama tayi matuƙar mamakin ganin shi a gidan su , kuma a part din mummy, amma hakan bai hanata ɓalla mai harara ba, cikin tsiwa , tace" wai kai Mallam me kake nema danine, ko wani lokaci muka haɗu sai ka bangaje ni, to wallahi kayi na farko kayi na karshe, duk sanda ka sake bangazata saina sa Allah ya isa" ta qareshe cikin murguɗa baki, Shi abin ma dariya ya bashi, amma ya dake baiyi ba don kar ta rainashi, don ya lura yarinyar kwata kwata bata da kunya, kara hade rai yayi, cikin dakewa yace"waike me yasa baki da nutsuwa ne, kullun in zanganki kina cikin gudu sai kace wata qaramar yarinya , koda yake yarinyar ce, don da ganin ki ba kifi twelve years ba" Cikin zaro tace "kan uba, nice Mara nutsuwa" Kafin ya bata amsa su Asmah da kamal sun karaso wajen Hannu kamal ya bashi suka gaisa, su Zahra ma suka gaisar da shi , a fakaice yake satan kallon Asmah, a zuciyarshi kuma yana raya "lallai kamal yayi dace, yanzu dama Aslam wannan zuqeqiyar yarinyar aka aura mai ya saki, lallai ya tafka babban kuskura, yayi wasa da damar shi ta farko, gashi kuma bai samu dama ta biyu ba, Ganin sunzo gurin yasa batool ta hadiye sauran rashin kunyar da tayi niyyar sauke mai , amma fa sai banka mai uban harara takeyi, duk yana lura da ita, Shigewa ciki yan matan sukayi yayinda Dr bash da kamal suka tsaya suna magana, Suna shiga batool ko gaida mummy batayi ba tace" mummy dan Allah mutumin daya futa yanzu daga part ɗinnan meye alakar mu dashi ne, ni wlh haushin shi nake ji, ya fiye shegen iyayi wlh" Mummy zuba mata ido kawai tayi tana kallonta ta inda take shiga bata nan take fita ba sai masifa takeyi , kamar zata ari baki Suma su zahra duk tsayawa sukayi suna kallonta, saida tayi mai isarta , sannan ta lura da kallon da suke binta dashi, Kwashewa tayi da dariya mummy tace"sannu mandiya ci gaba mana, ko har kin gama kenen," Cikin dariya tace "wlh mummy mutumin bashi da mutunci rannan fa wai marina zaiyi, ranar dinner ya Aslam, har ya daga hannu kome ya tuna naga ya sauke hannun yana kwafa kamar ya Aslam na tafe yana binshi a baya," Mummy tace " ai wlh bashir bai biya ni da kakkafta miki mari ba tunda ke kince baki da kunya" Cikin tura baki ta tashi tana haurawa sama tana dan gungunin, a hankali "tab wlh yana wanka min mari zan rama" Mummy tace" me kike cewa , ki tsaya kiyi a gabana mana, rasa kunya," Su Asmah gaisar da mummy sukayi , sannan suka haura sama dan su kimtsa kafin su fito suyi lunch. Dr bash yana tuki yana tunanin batool , shi kadai sai murmushi yake yi, can kuma a fili ya furta " kan uba nice mara nutsuwa " cikin kwaikwayan muryanta,murmushi ya kuma saki, kafin a hankali ya furta "ta cika tsiwa" haka kawai ya tsinci kanshi cikin wani irin nishadi na musamman, Da haka ya iso gidan Aslam , gaisawa sukayi da mai gadi, nan yake shaida mishi matar gidan bata nan amma me gidan yau kwana uku bai saka shi a ido ba, kuma ya tabbata yana cikin gidan bai fita ba , don inda ya fita zai sani ,tunda shi zai bude mishi get, Cikin mamaki yace ka "tabbatar yana ciki " megadi "yace kwarai yallabai , don ko jiya da hajiya ta dawo ta tabbatar min yana ciki kuma yana lfy" Dr bash yace " anya kuwa yana lfy, yanzu dai zanje na dauko dan uwan shi Amir zamu shiga mu duba , idan kuma madam ta rigani dawowa ka gaya mata Dr bashir ya zo," Megadi ya amsa da to "to yallaɓai a dawo lfy" Motar shi ya shiga yabar gidan , don zuwa ya dauko Amir, Karfe biyar daidai na yamma motar brr Adam ta parker a harabar gidan alhaji baba, fitowa yayi daga cikin motar sai zuba kamshi yakeyi, yaci kwalliya cikin dañyar shadda ash colour, sai maiqo takeyi, gsky brr Adam ma ya hadu over,Baki ne dogo kyakkyawan gaske mai siffar dakakkun maza, kallon daya zaka san ma'abocin ibadah ne , saboda yadda fuskar shi ke cike da kamala da haiba, na hasken musulunci, Megadi ne yamai iso gurin daddy, daddy dama ya riga yasan da zuwanshi don , kuma yasan ba wurin shi yazo ba gurin Zahra ne, don haka ya bada umarnin a kaishi sitting room , a kuma je a gaya wa mummy baƙon zahra yazo Haka ko akayi mummy dama ta riga tasan za zancen, don jiya daddy ya fada mata komai, itama tayi na'am dashi ganin yadda mijin nata yayi na'am dari bisa dari, tasan bazai yi na'am da abinda zai cutar da ɗiyar wani bama balle ɗiyar shi, Wayarta ta laluba ta kira zahra, tace ta sameta a falon ta yanzu yanzu, Zaune suke dama suna karatun alkur'ani da sukeyi duk bayan sallan la'asar, ranar da Mallam ɗinsu bazai zoba dama haka sukeyi su biyama junan su, dogon hijabine har ƙasa a jikinta irin mai dan kwalin nan, Miƙewa tayi tace ma su Amira tana zuwa ,mummy na kiranta, a falo ta samu mummy, zama tayi a gabanta tace"mummy ganin," Kallonta mummy tayi kafin tace"kinyi baƙo, yana sitting room din daddy, dauki ruwa da lemo ki kai mishi , daga nan kuma ki saurari meya kawo shi gareki " Cikin dan mamaki tace"tace mummy baƙo muka, nifa banba kowa izinin zuwa gidan mu ba, ita a tunanin ta wannan lecturer ne daya dameta a school," Mummy tace "to tunda ya riga yazo sai kije ki gani ko" amsawa tayi da to mummy sannan ta fice , kitchen ta fara biyawa ta ɗauki abinda mummy ta umarceta sannan ta nufi hanyar sitting room d'in, Da sallama ta shiga falon, yana zaune ya ƙurawa ƙofar shigowa ido jira kawai yakeyi yaga ta inda zata bullo, yarinyar da tun gani na farko har yau ya kasa cireta a zuciyarshi daidai da minti daya, Amsa mata sallaman yayi shigowa tayi cikin natsuwar ta, gabanshi ta nufa ta ajiye tiren hannunta , sannan ta koma baya ta nemi kujera ta zauna, Sai sannan ta dago kai ta kalleshi, ji tayi gabanta ya yanke ya fadi, da sauri ta dake kai daga kallonshi, don yayi mata kwarjini sosai, gani takeyi kamar tasan fuskar shi amma kuma ta manta inda tasan shi, Cikin siririyar muryarta tace "ina yini" taja bakin ta tayi shiru, Tunda ta shigo yake binta da kallo sai yanzu ya tabbatar Ashe rannan ma kallon tsoro ya mata, yanzu ne yake qare mata kallo mai sunan kallo, Cikin kulawa da maida dukkan hankalin shi gareta ya ̃amsa mata da" ina gajiya faɗeema, ya gida ya makaranta " ta amsa da lfy qlau, Shiru sukayi dukkansu sai can ya katse shirun da cewa " nasan kin manta ni ko" dagowa tayi ta kara kallonsa a karo na biyu, still bata tunashi ba, Murmushi yayi yace "dama nasan ni kadai nake kiɗa na da rawa na," A karo na biyu tace" kayi hakuri dan Allah ban gane kaba, amma kuma kamar na taba ganin fuskar ka a wani wajen" Cikin jin ɗaɗi yace"well hakan ma na gode tunda kin tuna kamar kin sanni,naji ɗaɗi kuma nagode, amma kinga ni tun gani na dake na farko ko daidai da second daya ban qara manta ki a cikin zuciyata ba, nine abokin Abban hanifa, nan da muka hadu a gidan kwanaki kika kawo min ruwa " Cikin mamaki ta dago tace "Ooh sai yanzu na gane ka, dan kayi hakuri ban gàne ka bane da farko, ya hanya ,ya iyalai". Yace "lafiya qalau sunce ma na gaida ki" Tace "aiko nagode ina amsawa," Dan shiru sukayi kowa da saƙesaƙen da yakeyi cikin ransa, Can dai brr Adam ya katse shirun ta hanyar cewa"a gaskiya faɗeema wani magana ne mai muhimmanci ya kowa ni gareki, fatan zaki bani aron hankalinki, kuma ki saurareni da kunnen basira, a gaskiya tun ranar dana fara ganinki , kikayi awan gaba da tunani na , na koma gida na kasa samun natsuwa a zuciyata, kaunar ki tayimin kamun farat d'aya, bansamu kwanciyar hankali ba har saida na dangana da mahaifinki, yayi na'am dani kuma shine ya bani daman nazo gareki na nemi yardar ki da soyayyar ki, ina fatan zaki tausaya min ki karɓe ni da hannu bibbiyu a matsayin mijin aurenki " Sunkuyar da kanta kasa tayi tunda ya fara magana , ta kasa ƙara dagowa ta kalle shi, wani bala'in kunyar shi ne ya lullbeta, Kallanta yayi ganin bata da niyar cewa wani Abu yasa yaci gaba da cewa" nidai sunana Adamu Aliyu badegi , ni mutumin bidda ne kuma ƙabilar nufawa, nasan kinji hakan a muryata, ko?" ya qarqare maganar yana murmushi, ƙarayin kasa tayi da kanta , ci gaba yayi da cewa,"inada matata ɗaya maryama, da yara hudu, ni lawyane me zaman kanshi, bayan wadannan ki faɗi duk wani abin da kike son sani game dani sai na faɗa miki," Shiru dai ba amsa, kara zama yayi kusan na 20 minute yana zayyano mata kalaman soyyaya, Wanda shi karan kanshi baisan ta yaya akayi suke fitowa daga bakin shi ba, Ganin dai bazata ce komai ba yasa yace mata zai koma amma taje tayi shawara da zuciyar ta, zai kirata a waya anjima inya isa gida, amma dan Allah ta yanke shawara mai kyau, Da haka sukayi sallama bayan ya ajiye mata yan dubu dubu guda a shirin, yace ta saka kati. Saida taji tashin motarshi , sannan ta iya fitowa daga falon, cikin sauri ta qarasa sashen su, Dr Bash har wajen aikin Amir yaje ya ɗauke shi , suka nufi gidan Aslam har lokacin zee bata dawoba, shiga cikin gidan sukayi, ba kowa falon upstairs suka haura duka sauran ɗakunan a buɗe suke harda na zee, ɗaki dayan da suka gani a rufe suka shiga knocking, shiru ba amsa, Daidai wannan lokacin Aslam ya gama sheqa aman shi a nan kan gadon don zuwa yanzu ko tashi matuq'ƙar wuya yake bashi, baga ɗaya, ya fice a hayyacinsa damuwa taima zuciyarshi mugun kamu, Jin ana knocking yasa ya kasa kunne sosai , muryar Amir dana Dr bash yaji suna sallama , mƙewa yayi daƙer yana layi yana ganin jiri ya nufi ƙofar ya bude musu , yana bude ƙofar ya fada jikin Amir daya fi kusa dashi, Cikin gigicewa da tashin hankali suka shiga jijjigashi amma ina, daƙer yake bude ido yana lumshewa , kallon Dr bash amir yayi cikin tashin hankali yace " Dr pls do something" bash yace "muje asibiti dashi kawai shi zaifi kaga nan ba wani kayan aiki" Cikin abinda baifi minti ashirin ba suka isa asibitin da Dr bash ke aiki, ganin su tare da Dr yasa cikin gaggawa aka kawo keken tura marasa lafiya aka shiga da shi ciki, direct emergency akayi dashi Dr bash ne ya shiga duba shi tare da wasu abokan aikin shi har guda biyu, Amir kuma yaje bude mai file na asibitin, Kusan awa ɗaya suka kwashe akan shi kafin su gano taka maiman meke damun sa , ruwa aka daura mai, da alluran bacci masu karfi, Lokacin da su Dr bash suka fito Amir tuni har ya kira gida ya faɗa mami, da Abba da hajiya mama tuni har sun iso, Mami ne ta nufi Dr bash tace "Dr bashir ya ake ciki ina my son a wani hali yake ciki" Dr bash yace "da sauƙi mami mun samu mun shawo kan matsalar, yanzu yana bacci, mum mishi alluran bacci , zaidan jima yana bacci kafin ya farka, ta haka ne zuciyarshi da kwakwalwarshi zasu huta" Daidai lokacin daddy da mummy da Kamal suka qaraso, daddy yace " bashir meke damun shi ". Dr bash yace "daddy muje office sai na maka bayani" Office suka rankaya kusan gaba dayan su, zama wasu sukayi wasu na tsaye, daukar file dinshi yayi yayi rubuce rubuce, Kallon su yayi cike da tausayawa ganin dukkansu yanda suka shiga damuwa, Yace, " a gaskiya akwai matsala Aslam ya ɗauki damuwa ya saka a zuciyarshi, kuma baya barin kwakwalwar shi ya huta, saboda tunani, ga rashin bacci, ga rashin cin abinci, ulcer shi yayi mummunan tashi, sannan tunanin da damuwar da yasa a rai, yana barazana ga zuciyarshi, idan , badan Allah ya taimaka ba, da yaci gaba da zama a haka tsawon kwana uku komai ma zai iya faruwa dashi, ciki harda bugawar zuciyarshi, kokuma mu rasa shi ma gaba daya" Tsit dakin yayi kowa da irin abin da yake saqawa a ransa dukkansu basa buqatar sanin abinda ya jefe shi a cikin wannan halin , saboda Abu ne da yake bayyane kowa ya riga ya sani, Mami ce ta fashe da kuka tana maimaita innalillahi wainnailaihi rajun,mummy ma duk iya dauriyarta da kawaicinta saida ta share hawaye a fakaice, Dr bash ne ya shiga kwantar musu da hankali matsayin shi na likita , duk da shima cikin tsananin damuwa yake, Saida komai ya natsa mami ke tambayar ina zainab, nan Amir ya sanar musu abinda megadi ya fada musu na cewa ta fita tun safe gashi har dare bata dawoba, Daidai lokacin zee na tare da beebalo, fitowa su kenan daga labour kutigi, ana wani biki , ba dangin iya bana , baba beebalo ta jata suka tafi, zama sukayi suma cikin yan biki, suka saje,dangin ango zasu zata dangin amarya ne suma dangin amarya kuma su zata dangin ango ne su, Haka suka shiga fili suka sha rawa har sunfi wasu dangin ma'auratan zaqewa, Bayan sun fito ne zee na jansu a mota zata sauke beebalo a gida kafin itama ta koma gida dan dare yayi, karfe takwas ake nema, Beebalo ta kalli zee tace" kawata kince min kina da aure amma baki taba nunamin mijnki ba koda a hoto ne"dariya zee tayi tace "Abu mai sauki ". Dalleliyar wayarta ta dauka ta nemo hotunan Aslam ta miqama beebalo, Beebalo na gani ta zazzaro Ido waje a zucyarta ta furata bantan uban can, tabdijan akwai bura'uba kenan dama wannan tsalelen saurayin ne mijin zee, tabdijan wannan shine irin mijin da ta dade tana mafarkin samu, Wanda rashin samun irin shi ya hanata zaman aure, lallai da sake, dole zatasan duk ƙulleƙullen da zatayi ta kara zee ta samu ta maye gurbinta, a gidan Aslam. Ganin tayi shiru yasa zee tace "yadai naga kinyi shiru ko kinsan shi" cikin murmushin yaƙe tace "wlh ban taba ganin shi ba sai yau gaskiya kawata kinyi dace da miji kyakkyawan gaske ga kudi, masha Allah irin mijin novel muma Allah yasa mu a danshin ku" Cikin jin dadi zee tace"amin amin kawata" nan ta shiga gaya mata wasu sirrikan Aslam' ita kuma beebalo sai bugun cikin ta takeyi taba nadar abin da zata Nada, kafin su rabo saida ta gama sanin abin da take Neman sani fak akan Aslam, don beebalo akwai shegen wayau, ita kina zee ba wayau sa iya hege😁 Karfe Tara daidai ta iso gida , tun kan tayi parking me gadi ya tare da mummunan labari, nan take hankalinta ya tashi, don duk iya shegenta tana matuqar kaunar Aslam, Take ta ɗauki hanyar zuwa hospital....... 💖more comment more typing💖 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book ɗin ca duk wscce ta rasa mahaifiya, allah kajiƙan iyayen mu } page 61 & 62 Koda zee ta isa asibitin duk su mummy sun riga sun wuce sai mami, kawai aka bari da zata kwana da shi, Da tambaya ta gane ɗakin da aka kwantar dashi , tana shiga ta tarad da mummy zaune a kujera dake gefen gadon , carbi ne hannunta tana ja , sanye take da hijab dinta da alama ma salla tayi don ga pray mat nan a shimfide a ɗakin, Guri ta samu bakin gadon ta zauna ta miqa hannunta tana shafa fuskar Aslam, gani tayi duk ya koma mata wani iri dan kwana biyu nan da data ganshi, saida ta gama tabe tabenta, Sannan ta dago ta kalli mami tace"sannu ma " Mami da mamakin ganin wanga irin rashin kunya na zee ya kasheta , tace " sannu dai aike zanwa sannu" Cikin ko inkula zee ta ɗauke kanta daga kallon mummy ta mayar kan Aslam, Nan dakin ya dauki shiru ganin dare yayi yasa mami miƙewa taje ta kwanta , a daya gadon dake ɗakin ta juya musu baya, sai dai tana yi taba farkawa ta duba ko Aslam ya farka don har lokacin bacci yakeyi, bai farka ba, Zee kam akan kujera ta kwana rike da hannun Aslam, a haka har gari ya waye, har lokacin Aslam bai farka ba, A can family hause kuwa mummy ne ta shirya breakfast , taba batool tace maza taje bello ya kaita asibiti ta kai musu , daga nan taga jikin Aslam ɗin, Har ɗakin wata nurse ta kaita bayan tayi tambaya , shiga tayi ta tarad da mami zaune kan bakin gado, zee kuma akan kujera, ta tasa fuskar aslam a gaba tana kallo, Gaida mami tayi tana tanbayar ta ya mai jikin mami tace"da sauƙi batool ya gida , saidai har yanzu bai farka ba," batool tace "subhanallahi, to Allah yasa dai lafiya " mami tace " insha Allah lafiya alluran da suka mai ne yana da ƙarfi sosai" Juyowa batool tayi ta kalli zee tace"ina kwana " saida ta kare mata kallon banza ganin kamannin ta da Aslam haka ya tabbatar mata kanwar shi ce, sannan ta amsa da " lafiya "a yatsine, Batool a kan labbanta ta furta kan uba! Hada ido sukayi da mami , mami ta girgiza mata kai alamar karta tanka , ƙwafa , tayi amma a zuciyarta ta qudiri aniyar , daga yau bata ƙara gaida zee,in anyi duniya dan ma'aiki, Kwandon abincin ta jawo tace mami ga abinci bari nayi serving ɗinki , hada ma mami tea tayi ta zuba mata , arish da kwai ga kuma bread da butter, Gdy mami tayi ta amsa ta fara ci, zee na zaune duk kamshi ya gama cika mata ciki, tana jira batool ta gama zuba ma mami ta zubo mata,don yunwa takeji, amma ga mamakin ta sai taga batool ta rufe kuloli ta koma ta zauna , Mami na lura da ita sarai ta gane abinda take jira, amma taqi saka musu baki , gara abarta da batool ɗin don dama ance , Karen bama shike maganin zoman bana, Batool da mami dan fira suka shiga yi jefi jefi, can kuma kaman ance mami ta waiga ta hango Aslam na motsi da idanu alamar zai farka, Da sauri mami ta miqe tsaye tace " alhamdulillahi batool ya farka" itama zee sai lokacin ta lura dan kallon fuskan shi kawai take amma hankalin ta gaba daya yana kan abincin dake kula a rufe, Mami tace "batool yi sauri ki kira Dr bashir " da sauri batool ta fice tambayar wata cleaner tayi office din Dr bashir , nuna mata layin da office's din doctoci yake,tace tabi zata ga office din da aka rubuta Dr bashir ta shiga nan ne, Da sauri ta qarasa ta duba cikin sa'a kuwa ba ko wani patient don haka ta shiga, Har ta bude baki zata fara gaishe , shi idanun su ya sarqe dana juna cikin gwalalo idanu cike da mamakin ganin mutumin ta, a mastayin Dr bashir, Shi kuma wani irin farin ciki ne ya lullubeshi , nan take yaji wani nishadi na shigar shi na ganin ta ,jiya daidai da second daya tunanin ta bai barshi ya huta ba, duk kuwa da halin da Aslam ke ciki bai hana shi kwana tunanin ta ba, Daure fuska yayi kamar bai taba ganin ta ba tunawa da yayi wacece batool , yanzu zata zube mai fitsara Cikin dakewa yace" madam ya zaki shigo min office haka ba excuse , saikace zaki shiga toilet, ai ko toilet ne naga sai mutum yayi addu'a kafin ya shiga" Saida ta fakaici idanshi ta watsa mai harara ,sannan tace " patient dinka Aslam ya farka" Duk harare hararen da takeyi yana kallonta ta gefen Ido amma jin abin da ta faɗa , na cewa Aslam ya farka yasa ya miqe da sauri , yana tattara kayan aikin shi ,yayi waje ,rufamai baya tayi, Koda suka isa dakin ya buɗe Ido tangararas , yana kallon kowa, fita waje Dr bash yace suyi, sannan ya shiga duba shi, Alhamdulillahi abinda ake buqata komai ya daidaita bugun zuciyar shi ya dawo normal kwakwalwarta shi ya samu Hutun da ake son ya samu, saidai rashin qarfin jiki da kuma ulcer Wanda waɗannan dama sai a hankali zasu daidai ta, Nurse Dr bash ya aikata yace tace ma mami a haɗa ma Aslam tea , yasha , don cikin shi ya warware kafin yaci abinci yasha magani, Mami cewa tayi batool taje ta haɗa, don shakkar cewa zee taje tayi takeyi, ganin tun sannun da ya haɗa su jiya har yanzu wani mahimmin magana bai sake haɗasu ba, Ɗakin ta shiga ta haɗa mai tea mai kauri yana turiri , ta miƙa ma Dr bash Wanda shi zai bashi , cikin rashin sani wuri karban shayin hannun sun ya tabina juna , Da sauri ta saki kofin shayin ta shiga yarfe hannu kamar wacce wuta ya lasar ma hannu kokuma wutar lantarki yaja, Allah ya kiyaye Dr bash ya riqe kofin da sauri da ba abin da zai hana shayin zubewa, Murmushi Dr bash yayi a zuciyarshi yace lallai ma yarinyar nan , dan hannu na ya taba nata take wannan yarfe yarfen,? Hmmmm zakiyi bayani ne yarinya, A fili kuma ya watsa mata harara yace" waike me yasa bakiyin Abu a hankali ne for god sake" Murguda baki tayi sannan ta fice ɗaga dakin, Haka Aslam ya wuni a asibiti cikin kulawa , kan dare jiki yayi sauqi alhamdulillahi , don sosai mami take takura mai yana cin abinci, yana shan magani, kan kwabo sai gashi har yana zama da kanshi, Dangi ana ta zuwa dubashi , alhaji baba dai baizo ba, daddy ma jin ya farka kuma jiki da sauƙi yasa bai koma ba ,don har yanzu bai huce da rashin kunyar da yama mahifinsa rannan ba, mummy ma kawaici ya hanata komawa, Zee kam ganin har sha biyu ba Wanda ya mata tayin abinci yasa ta fita wajen asibitin ta siya abinci taci, da rana ma koda aka mata tayi ƙinci tayi , wai ita tayi fushi, yanda bata damuwa da lamarin su ,haka ba Wanda ya damu da taci ko bata ciba, Ƴan matan mummy basu samu zuwa asibitin ba sai dare ya kamal ya kwashe su , suka tafi, suna shiga suka tarad da ya Amir da Dr bash a ɗakin sai kuma zee, dake gefe tana charting, Jin motsin shigoya yasa Aslam dago kai yakai duban shi ga ,ƙofa akan fuskarta idanun shi suka sauka, itama kuma hakan ne ta kasance a gareta, Da sauri suka dauke idanuwansu daga kan juna, tsohon miki ne ya tashi, don ji yayi zuciyar shi na bugawa da ƙarfi fat fat fat, Qrasowa sukayi cikin dakin , gaidashi suka shiga yi tare da tambayar sa ya jiki,cikin jimla ya amsa musu da,"da sauƙi" hannu kamal ya miƙama su Amir da bash suka gaisa, Zahra CE ta dubi gefen zee tace "ina wuni anty zee " amira da Asmah ma suka gaishe ta , batool kam dauke kai tayi kamar bata ganta ba ta juya fuskan ta gefe tana tabe baki, Tun shigowar su sai lokacin ta dago kai daga charting dinta don ganin su wanene ma , idanunta ne ya sauka akan Asmah , aiko ji tayi zuciyarta tayi baƙiƙirin kishi ya motsa , wani mugun kallon sama da qasa ta watsa musu kafin taja wani mugun tsakin da saida ya jowa hankalin kowa na dakin kanta, Mursisi yayi ta dauke kallonta daga garesu taci gaba da charting dinta, Jiki ba kwari suka nemi guri suka zazzauna , Amir ne ya tashi ya fita yace musu yana zuwa, can harabar asibiti yaje ya nemi guri ya zauna, wayar shi ya laluba ya danno lambar Amira da yayi saving da baby, Suna zaune a dakin kiran ya shigo wayar ta , ganin ya Amir ne ke kira yasa ta daga , cikin magana kasa kasa yadda ko Asmah dake kusa da ita bataji me take cewa ba tayi sallama, magana sukayi na yan sakonni ta ajiye wayar tana murmushi, Minti uku ta qara kafin ta miƙe tace "sisters ina zuwa, " zahra tace "sai ina " tace "nan waje", ta fice da sauri dan kar su ƙara tambayar ta wani abin, Samun shi tayi a inda ya mata kwatance nan suka zauna suka shiga firan su na masoya da tsare tsaren bikin su hankali kwance, Kallo daya zakasan wadannan masoyane da suke cike da tsantsar kaunan juna da shauɗin juna, A can dakin kam Aslam tun bayan kallo dayan da ya mata ya zame a hankali ya kwanta,zuciyar shi na buguwa , kishi mai tsanani yana taso mai ji yake kamar , ya tashi ya shaƙe kamal har sai ya dena nunfashi, zuciyar shi ce ta dinta tunzura shi, amma cikin ikon Allah ya shiga maimaita innalillahi wainnaialahi rajiun, lamo yayi ya lumshe ido kamar me bacci , da haka har baccin gaske ya kwashe shi kasan cewar yasha magunguna masu ɗarfi, Fira aka shiga yi a dakin tsakanin kamal da Dr bash sai jefi jefi su Zahra na saka musu baki, Zee jin sun dameta yasa ta miƙe tare da jan tsaki ta fice daga ɗakin , Harara batool ta rakata dashi kafin ita ma ta ja nata tsakin , Dr bash da dama duk abinda yakeyi hankalin shi na kanta , a zuciyar shi yace " yawwa dama nasan ko kowa bai tanka ba , ai hajiya masifatu ta tanka," CI gaba sukayi da hira, can Dr bash yace "subhanallahi wlh na manta akwai wani allura guda daya da za'amai cikin dare gashi bamu dashi anan sai anje pharmacy a waje an siyo" kamal yace"ayya to kawo na siyo mana" Rubuta mishi sunan alluran yayi ya miqa mishi, amsa yayi ya miƙe har yakai bakin ƙofa ya juyo ya kalli Asmah, yace asmy ba rakiya, cikin dan jin kunya ta watsa mishi hararan wasa , tana murmushi, hannu ya haɗe mata alamar roƙo yayi fuskar tausayi, saida ta ja mai aji sannan ta miqe tabi bayanshi, Dakin ya rage daga batool da zahra sai Dr bash, sai aslam dake bacci, Dr bash ya dubi zahra yace "kanwata zahra ya makaranta ya karatu," cikin murmushi ta amsa da "makaranta alhamdulillahi , karatu kuma akwai wuya ya bashir" bash yayi murmushi yace "karatun ma balle irin namu sai mai ƙoƙari, kuma ke da gani zakiyi ƙoƙari, ganin yadda kike da nutsuwa da hankali , ba kamar wasu yan matan ba da zaki gansu kullun cikin guje guje kamar yan nursery," Dagowa batool tayi da sauri ta kalle shi jin abin da take cewa ,ko ba'a fad'a ba tasan da ita yakeyi, Zahra ko cikin jin dadin yabon da aka mata, tace " nifa ya bashir bani da wani qoqari saidai taimakon Allah kawai, dama batool kace itace mai kokari don duk cikin mu ta fimu ƙoƙari," cikin son ya tsokani batool yace"kai zahra wannan shirmammiyar yarinyar da ganin ta baza tayi wani qoqari ba, irinsu ne fa masu yin espo a class, da ganin idonta na rashin kunya ta kware a iya espo" Kan uba aiko dai ya taro masifa don dama tun dazu daurewa kawai takeyi amma a cike take fam dashi kamar zata fashi, Aiko nan ta shiga zazzaga mai ruwan rashin kunya tanayi tana murguda baki, ta inda take shiga ba tanan take fitaba, Aiko dai Dr bash mutuwar zaune yayi yana kallonta , ɗan bakinta da take masifa tana mugudawa yake bi da kallo , gaba daya masifarta burge shi yakeyi, abin na mishi ɗaɗin kallo yana sakashi nishadi, Saida tayi mai isar ta tayi shiru, zahra kam tagumi tayi da hannu bibbiyu tana kallon ikon Allah , don tun ɗazu take ce mata ya isa amma taqi kulata , ganin haka yasa ta yi tagumi tana kallonta, Su kamal ne suka shigo dakin , ganin haka yasa kamal tambayar ba'asi ,nan ta shiga labarta mishi abinda bash yace tana yi, kamal kunshe dariyar shi yayi yace, "Kai ammafa Dr ka samu kanwata da yawa ita kake kira da me espo a class, to kiyi hakuri wasa yake miki ai,da'ker ya lallabata ta hakura ," Daga nan sukayi sallama da Dr bash, a waje suka dauki Amira suka koma gida, Kwanan Aslam uku jiki yayi sauqi sosai , nan yace shi ya gaji da zaman asibiti a sallame shi , ƙin sallaman shi bashir yayi yace sai yayi sati, tada balli yayi ba shiri Dr bash ya rubuta mai sallama,............ Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fi sabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan littafin ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan mahaifan mu} Page 63 & 64 Bayan kwana biyu Aslam tuni ya gyagije , kamar bashi bane aka kai asibiti rai a hannun Allah, saidai fa karfin hali kawai yakeyi , bai bari ya saka damuwa a ranshi ba , ƙokari yake ya yakice ta daga zuciyar shi,amma Abu ya gagara, kullum burin shi ya ganta , duk randa bai sakata a idanun shi ba baya iya barcin kirki, zee kam gaba daya ya tattara al'amarinta ya watsar don yanzu bata gaban shi, kullum cikin yawanta take , ita da beebalo, abu daya ya sani, ya saka ana bibiyar mishi ita duk inda kafar ta ta taka a garin minna , akwai masu bibiyarta,idan kuma ta dawo da daddare, idan ta kowo kanta gare shi zai biye mata, saboda fita hakkin ta, idan kuma bata kawo ba , a sauka lafiya kowa na dakin shi , da safe kuma ba lallai suga juna ba , saboda Aslam da sassafe yake fita, zaije can farkon layin shiga family hause yayi parking ya zauna ya jira har bello ko kamal ya dauki su Asmah zuwa school, a nan yake samu ya ganta kullum , duk kuma ranan da bai ganta a nan ba . har school yake binta a boye a boye, dan kawai ya ganta, idan ba haka ba kam ranar ba zaman lfy , da daddare ma saiya manna hotanta akan kirjin shi yake iya samun bacci, Yau dai daya kama kwana ashirin cif da sallamar sa daga , asibiti ya gaji, muryarta kawai yake son ji, gashi ba daman yaje family hause, a halin yanzu, dana sani ya shiga yi na cewa da yayi bazai kara zuwa gidan ba yanzu gashi yana son zuwa kodan yaji muryarta amma ba hali, zuciyar shi Ce ta shiga bashi shawarwari iri iri na yanda zaiyi ya samu jin muryarta, Ya yanke shawaran kawai gidan zai tunkara ya fuske ya shiga falon mummy ya zauna , wata zuciyar kuma tace yayi ɓadda kama ya shiga gidan , a mastayin abokin Amir q Ƙila ya samu ya ganta, wata kuma tace yayi shigar mata yaje, shawarwari dai marasa kan gado iri iri, Karshe dai yaga ba ta yadda zaiyi ya shiga gidan ba tare da angane shi ba a haka ya ajiye batun zuwa gida ya barshi a zai tare a school kawai ayi wacce za'ayi , imma zagin shi zatayi tayi, shidai kawai yaji muryarta, A family hause kam shirye shiryen biki ya kankama , ƙannen mahaifin amir sunzo , neman auren amira kuma an basu, abinka da tuwona maina , ba wani bata lokaci aka gama komai, haka ma batun Asmah da kamal, shima dai duk na gida ne ba wani tsatstsayawa , Soyayya tsakanin Barr Adam da zahra kam abin ba"a cewa komai kullum suna maqale a waya, cikin kankanin lokaci yayi nasaran sace zuciyata, tun tana jin kunyar shi tana ɗari ɗari dashi har ta zage ta shiga mayar mai da martanin zafafan kalaman soyayyar da yake gaya mata, don Barr Adam ya iya bi da ita sosai, dama kuma can zahra akwai sauƙin kai ba kamar batool bace, suma dai magana tayi karfi don har an shiga gida an gana gemu da gemu, Matsalar su ɗaya maryama uwar gidan Barr Adam , tana can ta tada balli, ita bata son kishiya ,saidai ya zaba ko ita ko zahra, shi kuma yace duka yana sonsu, har wayar shi ta dauka ta kira zahra ta zageta tass wai ta rabu mata da miji, zahra kam shiru tayi, aiko batool dake gefenta ta fisge wayar ta shiga mayar mata da martani, kaca kaca sukayi a wayan, Wanda na tabbata da a kusa da juna suke ba abinda zai hana a doku, Kuka zahra ta fashe dashi wai ita ta hakura da auren Barr Adam aiko batool ta mata ca aka tace " tab tunda nake nikam ban taba ganin wawuyar mace irinki ba, dan kawai kishiya ta kiraki ta miki wannan dan barazanar shine zakice kin fasa auren masoyin ki, to wlh sai anyi auren nan kodan mu gyara ma wancen karkatacciyar matar tashi zama, " ƙwafa tayi tace "kai Allah yaga aniyar jaki yasa baiyi shi da kaho ba, da nine a matsayin ki,da saina ci uban wannan wawuyar matar tashi la'ada waje, kema dole ki ƙarfafa zuciyarki inba haka ba zaki sha wahala a hannun kishiya". Zahra cikin kuka tace "wlh batool bana son tashin hankali ko kaɗan " Kiran Barr Adam ne ya katse musu maganar da suke, kin dagawa zahra tayi, batool Ce ta daga ta saka shi a hands free , cikin rawar jiki tana dauka ko gaisawa basuyi ba Barr Adam ya shiga bama zahra hakuri cikin lallshi , da kwnatar da kai, tsoran shi ɗaya kar tayi fushi tace ta fasa auren shi , saboda abin da maryama ta mata, don yasanta sarai bata son tashin hankali, don idan ta fasa auren shi shikam ya shiga uku, Tausayin shi ne ya kama batool ganin yadda ya ruɗe lokaci ɗaya , lallai yana son yar uwarta sosai, tatabbata idan ta shiga gidan baza ta wahala ba, kwandon masifar da tayi niyyara sauke mai ta mayar ta Adana abinta, miƙama zahra wayar tayi ta mata alamar ta amsa mishi, Amsa tayi ta nuna ba komai ta hakuri nan ya shiga zuba godiya , abin tausayi, Aiko suna gama wayar ya haura dakin maryama a fusace, kamar wani mayun wacin zaki, (to nidai nace Allah ya huci zuciyar Mallam adamu,) Bangaren bash kam ya riga ya gama gane soyyayar batool ta gama mai mugun kamu , har fiye ma da yadda yaji son Asmah, a kwana kin baya, Saidai kuma shi kaɗai yake kiɗan shi kuma ya taka rawar shi don ita a maƙiyi ma ta ɗauke shi, yanzu gidan ya zame mishi wurin zuwa kullum, haka zaije yata tsokanar ta ita kuma tana zuba mai masifa, Shima ko a fuska bai taba nuna mata yana sonta ba kullum cikin hade mata rai yakeyi karta raina shi, dan yasan halinta, tsokananta dashi kullum tayi kwantai bata da farin jini an kawo kudin auren kowa banda nata, kilama ko saurayi bata dashi, Aiko wadannan kalmomi na fusata batool , nan zata shiga zuba ruwan bala'i , randa mummy kuma ke kusa ta tsawatar mata , to ranar kuwa har kuka sai tayi, tayi tayi ya daina zuwa gidan , ya daina shiga harkarta yaƘi, Kowa na gidan ya dasa musu ayar❓ gadai su ba wanda zaice soyyaya sukeyi an rasa takamaimai meye a tsakanin su, ko mutum yayi tunanin soyayya suke , idan kuma kaga yanda suke yar tsama sai ka cire wannan mutanin a ranka, Asmah da Amira kam tsokanan ta sukayi da ta Dr bash , kodai da bash za'ayi, tako ce Allah ya kiyaye wannan dan banzan mutumin, ni wlh ku daina haɗani dashi , don wlh nafi karfin sa ko maza sun kare, Amira tace umumfa batula karfa muzo rashe ya juye da mujiya , Ɗan wannan kwana kin da Dr bash ya kwashe yana zarya gidan , ba ƙaramin sabawa batool tayi da, yanayin tsokanar shi ba, a kullum har Allah Allah take yi lokacin zuwan shi yayi , haka zata zarya tana duba agogo, Yau dai bai samu zuwa ba, luƙuss tayi a kan bed bini Bini ta duba agogo har wurin ƙarfe yadan dare babu shi babu labarin sa , Zahra ta dubi Asmah dake gefenta ta nuna mata batool , da zunɗe, kallon batool din tayi suna dariya ƙasa ƙasa, cikin rada zahra tace "yau mutumin ta baizo ba duk ta wahala , in anyi magana tace bata sonsa Allah ya kiyaye," Asmah tace "aiko dai yau zan gwada ta naga karshen karya," Tashi tayi ta fita daga ɗakin tadan labe can kuma ta shigo da sauri hankalinta adan tashe, tana cewa" innalillahi wainnailaihi rajiun, Allah sarki Dr bashir " zahra itama cikin pretending, tace "subhanallahi me ya samu Dr din'. tace "yanzu aka bugo ma mummy wai yayi accident," Batool da dama tunda Asmah ta shigo ta miqe daga kwance da take , jin kuma abinda akace yasa ta miƙe a zabure , tana dafe kirjinta dake bugawa da karfi kamar zai fado kasa tace " da gaske kike Asmah? Innalillahi wainnailaihi rajiun na shiga uku na lalace " gani sukayi ta zube akan gado dabass, tana wani irin numfashi kamar zata sume, Cikin dan tsorata Asmah ta kalli zahra suka hada ido aiba shiri Asmah tace"kefa da wasa nake miki, kawai munyi ne muji bakin ki," Dagowa tayi ta kalli Asmah tace"da gaske wasa kike" tace "wlh wasa ne kinji na rantse " ajiyar zuciya ta sauke kafin ta koma ta kwanta rigingine, .aiko dariya suka shiga kwasa suna mata tsiya , wai wannan wane irin gulmammen soyayya ne, gara inza a fito fili tun lokaci bai ƙure musu ba ehee, Duk rawan kan batool kasa tanka musu tayi , don da gaske maganar ya dake ta sosai, itadai baza tace ga dalilinta na damuwa har haka ba dan kawai ance bash yayi hatsari, dan ita dai tasan bata sonsa shima kuma yasha gaya mata shi me zaiyi da ita, Amira kam bata ɗakin tana cen wajen Amir dinta suna hira a main falo, saidai ta dawo aka gaya mata ,me zatayi kuwa itama ba dariya ba , haka suka saka ma batool zafi ranan ,ita ko kasancewar jikin ta ya mutu yasa ta kasa tankasu, Saidai sukayi mai isarsu suka kyaleta, har ummi dake abuja saidai zahra ta kirata ta bata labari, kasancewar sun dauketa kamar kawarsu basa boye mata komai, itama ummi dariya tayi , tace gulmammiyar banza ku kyaleta kawai nan gaba zata gane kuranta, Shima bash a nashi bangaren kasa sukuni yayi yau gaba daya bai sakata a Ido ba bai ji muryarta ba ,baiga dan cikulin bakinta dake bala'in burgeshi na murgudawa ba , duk sai yake jinshi kamar Mara lfy, Kasa daurewa yayi dole ya lalubo wayar shi ya danna ma lambarta da ya dauka a wayar Amir kira, Tana kwance jiki a mace call ɗin ya shigo wayar ta, ganin number mara suna yasa taqi dagawa har ya katse, sake kira yayi dan haka ta daga, danjin wake damunta a tsohon Daren nan, Shiru tayi batace komai ba kuma bata katse kiran ba ta dai daga ta kara a kunne, Daga can bangaren Dr bash yayi sallama, tunkan ya karkare sallaman ta gane muryan shi, take wani dadi ya lullubeta, bata San sanda ta saki murmushi akan laɓɓanta ba Amsawa tayi, tare da tambayar "dan Allah wake magana" shima acan bangaren yace "pls dawa nake magana". Miqewa tayi daga kwnacen da take ala dole bata gane shi ba tace "Mallam ya zaka kirani kuma kana tambaya wake magana, bakasan wacece ba ka kira," danne dariyar sa yayi ya dake yace "nima gani nayi anmin flashing da wannan number yanzu , shiyasa na kira naji kowa ke damuna cikin wannan Daren," Zaro ido tayi waje jin sharrin da zai mata wai tamai flashing, tace " wlh ya bashir kaji tsoran Allah niban kiraka ba banima da lambarka" Dariya ya kwashe dashi yace"Ashe dai kin gani ne, ni zaki kawowa rashin M kice wani wake magana, to Dr bashir ne yaro mai farin jini san kowa kin Wanda ya rasa, kyakkyawa ajin farko, ba irin wata ba" Aiko nan ta shiga kushe shi, shi kuma yana wasa kansa yana tsokanan ta , yana kunna ta bai barta ba kuwa saidai ya sakata kuku, su karan Kansu basu San dare ya tsala haka ba saida suka kashe kiran , Washe gari da misalin sha biyu na rana Aslam ya isa school ɗin su Asmah, daidai lokacin ta fito daga, canteen ruwa ta siya ta sha dan kishi takeji, zahra kuma taki rakata wai akwai rana, Tun daga nisa ya hangota , cikin tafiyarta mai jan hankali, shagala yayi da kallonta kafin kuma a hankali ya furta"ya Allah ka mallakamin wanna baiwar taka badan halina ba Allah badan na isa ba," gani zata wuceshi yasa ya tada motar nufanta yayi gadan gadan kamar zai tureta da mota , har ta gama sadaqar wa ta mutu, ya taka burki a gabanta daf da ita, fitowa yayi ya sha kwalliya sosai cikin kananan kaya,sai zuba kamshi yakeyi, don kuwa saida ya tsaya ya mata kwalliya mai sunan kwalliya sannan ya baza turare ya kamo hanya, .ganin ya Aslam yasa gaban ta yankewa yayi mugun faduwa, nan ta shiga a'uziyya a zuciya , Takowa yayi gabanta ya jingina bayanshi da jikin motar, zura hannaye a aljihu ya zuba mata idanu, itama dai ƙuri tamai idanunta cikin nashi babu alamar kunya ko shakkar shi a cikin kwayar idanunta sabanin da ,da idan ta ganshi ko daga kai bata iyayi a gabanshi balle har ta kalli cikin idanunsa, Ganin kallon kudan yaƙi ƙarewa yasa tace "lafiya Mallam zaka tsaidani a tsakiyar hanya, inada abinyi fa" ta fad'a cikin hade giran sama data kasa, Dadi ne ya lullubeshi shi jin muryarta daya dade yana begen ji, Murmushi mai ciwo yayi yace"husnah ina sonki" Idonta kur cikin nashi tace"karya kakeyi Aslam baka sona kuma baka taba sona ba,yaudaran kanka kakeyi da cewa kana sona, bakin da ya furta ki koya zo ya furta so daga baya karya ce kawai, to barin gaya maka ko ka soni ko ka qini Aslam ni bana sonka bana sonka bana sonka , ka fita a hanyata Kamal nakeso domin shine ya soni ya tallafi rayuwata tun bansan kaina, " hade hannayenta tayi alamar roko , tace"dan Allah na roqeka Aslam karka kara shiga sabgata, domin na zama mallakin wani , nan da yan kwana ki , zan zama mallakin farin cikin zuciyata kamaluddeen" Tana kaiwa nan ta juya a fusace kamar kububuwa ta barshi nan tsaye kamar mutum mutumi, Ya kusa kwashe twenty minutes a tsaye a wurin bayan wucewarta, kafin ya shiga motar shi ya figeta da wani irin mahaukacin gudu yabar cikin school, Zaune suke a chicken republic, sunyi order abinci , kowaccensu cikin kwalliya ,da kagansu kaga manyan bebs, ma'aikacin wurin ne ya gabatar musu da abincin da sukayi order, ana ajiye abincin kamshin shi ya bigi hancin zee take taji zuciyata na tashi, amma haka daure ta kai loma daya bakinta,wani irin amai ne ya taso mata, mai karfin kan kace koba ta shiga kelayashi a cikin mayafinta, yawancin mutane dake wurin masu kyama , tashi suka dingayi suna fita da gudu, Ma'aikatan gurin ne sukayo kanta suna mata sannu, beebalo ma ba'a barta a baya ba , saidai ta amaye abincin da taci ranar kaf, beebalo ta tallabeta , ta kaita toilet ta wanke fuskarta da bakinta, Mayafinta kam cleaner din gurin ta dauke ta saka a bola ta gyara wurin, A mota bayan sun fito daga wurin hade kanta da sitiyari , tayi, tana sauke numfashi, beebalo da tun d'azu ta diga mata ayar❓ta kalleta tace "kawata badai ciki kikayi ba," da sauri zee ta dago ta kalleta tace "ci me" beebalo tace "ciki "zee ta girgiza kai tace "ina ba zai yuwu ba ciki adan shekaruna , ke bani da wani ciki " beebalo tace "taya kika tabbatar baki da ciki , yaushe rabonki da al'ada" take gaban zee ya fadi don ita ta manta da wani Abu waishi al'ada,don kan aurenta da Aslam rabonta da shi, Ganin yanayin rudun da ta shiga hakan ya tabbatar ma da beebalo hasashenta ya tabbata kenan, murmushin mugunta tayi a zuciyata tace"na samu hanya mai sauqi da zan rabaki da aslam har abada , wawuya kawai, kin mutu tunda kia dauki amana kika damƙama beebalo taƙizama".................... Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillaha🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 65 & 66 Beebalo ta kalli zee tace "ke nake saurare ƙawata nace yaushe rabonki da ,period" zee tace"tun kafin bukina yau wata biyu kenan" beebalo tace"tabdijama aikam dai bamuga ta zama ba, dole ne muje a gwada mu gani ko cikin ne, " zee tace" a'ina zamu gwada bayan yanzu dare ne ko wani asibiti mukaje kinsan dai zasuce muje mu dawo gobe ne, kawai mu bari goben sai muje, " murmushi beebalo tayi tace, " ba asibiti zamuje ba kedai kawai kibar komai a hannuna, tabbatar cikin kawai muke da buƙatar ji yanzu, muje pharmacy mu siya P-test mu gwada mu gani," Tada mota zee tayi suka gangara na'uzo family pharmacy suka siyo P-test din har guda biyar , Gidan su beebalo dake unguwar limawa suka nufa , gida ne da ba kwabo komai yaro yaga dama yayi , toilet suka nufa zee tayi fitsari a wani dan karamin kwalba irin na turaren duri, saka abin gwajin sukayi, minti daya kuwa ya nuna musu layi jajaye guda biyu, Ciki ya tabbata a jikin zee, ɗaura hannu tayi aka tace "na shiga uku ni zainabu na lalace, wlh bana son cikin nan ban shirya haihuwa yanzu ba , wlh bana son jikina ya lalace, yanzu dana haihu shike nan , nono na zai zube abubuwa da yawa zasu canja a jikina , Aslam zai daina sona, zanyi saurin tsufa, ", beebalo tace baki shiga uku ba ƙawata ni zan tsaya miki mu zubar da cikin nan cikin sirri yanda ba Wanda zai Sani, muyi abin mu mu binne , ajiyar zuciya ta sauke, ta rungume beebalo, tace"nagode ƙawata Allah ya bar kauna," hararan bayanta beebalo tayi sannan ta amsa da "amin amin ƙawata" a zuciyarta kuwa tana aiyana zakici uban ki ne yarinya, ƙwance yake akan makekan bed dinshi, sai juyi yakeyi, tsakar dare ne don kimanin ƙarfe daya ne na dare,bacci gaba ɗaya yau ya kauracewa idonsa, kalamanta na yau ba karamin matsuguni suka samu a zuciyar shi ba , tunda yake wani magana bai taba tada mai hankali ba kamar yadda kalaman ta na yau suka tada mai hankali, ko wani motsi zaiyi sai kalaman ta sun fado mai a zuciya kamar a lokacin take sanar dashi kamar haka (karya kakeyi Aslam baka taba sona ba,yaudaran kanka kakeyi da cewa kana sona, bakin da ya furta ki koya zo ya furta so daga baya karya ce kawai, to bari na gaya maka ko ka soni ko ka qini Aslam ni bana sonka bana sonka bana sonka , ka fita a hanyata Kamal nakeso domin shine ya soni ya tallafi rayuwata tun bansan kaina, dan Allah na roqeka Aslam karka kara shiga sabgata, domin na zama mallakin wani , nan da yan kwana ki zan zama mallakin farin cikin zuciyata kamaluddeen") A fili ya furta "mallakin wani nan da yan kwaniki , ina! wlh baki isa ki zama mallakin wani ba matuƙar ina numfashi, kamal wlh ka rabu da matata kokuma na maka mugun lahani wlh, baka isa ka shiga gonata ba, zanyi maganin kane kamal, ni za,a yaudaya ni za,a munafunta" Haka yayi ta sambatu kamar wani taɓaɓɓe, Karshe dai wata zuciyar ta bashi shawara daya tashi yayi alwala yakai kukan shi gurin mahalicin shi, Haka ko yayi ya miƙe ya dauro alwala yazo yayi nafilfili, yana idarwa ya shiga miqa kukan shi gurin mai duka, baiyi aune ba sai ji yayi ana kiran sallan assalatu, Tashi yayi , ya shiga toilet yayi alwala ya tafi masallaci, yana dawowa ya biya dakin zee tana nan kwance kamar gawar sababi, har aka gama kiraye kirayen sallah, aka tada sallah aka idar ko motsi batayi ba, tashinta yayi, ta hanyar zuba mata duka a cinya, a firgice ta farka bako addu'a, Tsaki yaja ya fice daga dakin, cikin sauri ta duro daga kan gadon tunawa da tayi, yau beebalo zata rakata asibiti , a zubar da cikin nan tun kafin ya bayyana, ta yadda kwallon mangoro ta huta da ƙuda, dan itama akan batun cikin nan jiya daƙer tayi bacci , saida ta kira iyayen ta ta gaya musu, dukkansu cewa sukayi taje ta zubar , wai bata isa haihuwa ba, .yana shiga dakin shi ya zauna yayi azkar , da karatun alkur'ani mai tsarki a karshe ya dukufa yana ta kai kukan shi gurin mahakiccin shi, cikin kaskantar da kai da mika wuya, Kafin gari yayi haske kuwa , ya samu sauki sosai a cikin ranshi, damuwa da baqin cikin da yake ciki ya ragu fiye da kaso hamsin cikin dari, har yana jin yau zai shiga office Wanda rabonshi da office din har ya manta, sai assistant shi ke tafiyar da komai na kamfanin, Wanka yayi ya shirya cikin shirin fita office, yana gamawa kuwa ya leka ɗakin zee ya sallameta, dama dai ba batun karyawa a gida, Shiga motar shi yayi ya nufi gurin da yake zuwa yayi parking kullum dan ganin Asmah ,yau kam taci sa'a ya samu ganin ta, sabanin wataran da ko yazo bazai ganta ba, saboda wani bin lecture rana take dashi , Suna wucewa shima ya dauki hanyar zuwa office, message ne ya shigo wayar shi , sharewa yayi dan yasan kila , kamfanin layi ne, Saida ya isa kamfani ,ya samu shiga office ya zauna tukun , sannan ya dauki wayar shi da niyar kiran P A dinshi ya tuna da message d'in, budewa yayi ya fara karantawa tun kan yakai karshe yaja wani mugun tsaki , indai irin wadanan sakonnin ne ya saba cin karo da su jifa jifa, Sakone na kalaman soyayya zafafan daga beebalo, delete din sakon yayi ya ci gaba da duba aiyukan dake gabanshi, Can kuma wani massage din ya sake shigowa, kamar bazai duba ba sai kuma zuciyar shi ya dinga azalzalan shi akan ya bude sakon ya gani, budewa yayi ya fara karntawa, tun kan ya ƙarasa karanta, sakon yaji kanshi na juya mishi, a fili ya furta"whattttt! Impossible, cikin nawa zata zubar tana hauka ne hala," zama yayi daɓass akan kujeran shi mai jujjuyawa, Can kuma ya zabura ya mike , yasan zee zata aika, yanzu mai zaiyi dan ya dakatar da ita, Number da aka turo mai sakon ya shiga kira, acan bangaren beebalo ta daga kiran cikin kisisina, tace "amincin Allah ya tabbata a gareka ya kai Aslam tauraron zuciyata," ckin tsawa ya katse ta da cewa"wacece ke me kuma kika sani game da matata," murmushin barikanci tayi"matar ka ko maƙiyarka, lallai aslam har zainab kake kira da mata, to bari na gaya maka zaune kake da kasungumar makiyarka baka sani ba," katseta yayi da cewa "ba abinda na tambayeki kenan ba, kin tabbatar abida kika fad'a min gaskiya ne , don idan nayi bincike na gane wani abu daban rashin ki ya bushe, wlh matuqar kina cikin duniyar nan baki mutu ba ko ina kika shiga sai na lalubo ki," ya karashe maganar cikin wani irin razanannan tsawa tare da dukan table din gabanshi, saida takardun dake kai suka warwatse, Cikin beebalo ne ya bada wani sauti ,kulululululululululu, alamar zawo na haduwa , dan ba karamin firgitata kalaman aslam da tsawan daya da ka mata yayi ba, Amma kasancewar ta gogaggan yar duniya yasa ta dake ta fashe da kukan munafurci ,cikin kuka tace "wlh Aslam ni masoyiyarka ce, hakan ne ma yasa na kiraka don bazan so wani abin cutuwa ya sameka ba, ni ƙawar zainab ce mun hadu kimanin wata daya kenan da suka wuce, kuma kullum takan gayamin ita bata kaunar ka ta tsaneka. Dana sanin aurenka takeyi, ita wlh da zata samu dama kasheka zatayi har lahira, ni kuma haka kawai sai Allah ya daura min so da ksunarka na gaskiya , ni nake tausanta na hanata aiwatar da mugun nufinta akan ka, tasha kawo maka farmaki ina kare maka, kwatsam jiya ta same ni da batun cikin ka daya bayyana a jikinta, amma tace ita zubarwa zatayi, baza ta iya hada zuri'a da kaiba,na bata hakuri na bata hakuri taqi hakura, a haka muka rabu, shine d'azu da safe tazo gidan mu wai nazo na rakata ta zubar da ciki , nace baza ni, ba itama na shiga mata nasihar kar tayi haka , amma ta fice ko waiwayena batayiba wai innaga ta fasa zubar da cikin nan yau ranta ne ya fita daga gangar jikinta, tana fita nata kiran ta taqi dagawa, shine na tuna da wani number data taba bani wai number Kane , shine na kiraka ko kai zaka iya dakatar da ita, amma na rantse maka bayan wannan bayanin da na maka bansan komai ba a game da wannan magana," ta karashe maganar cikin fashewa da matsanancin kuka, kamar da gaske Aslam da gaba daya jiri ke diban shi ya koma da baya ya zauna akan kujeran shi daya tashi, daɓasss, cikin matuqar sanyin jiki yace, "wani asbiti tace miki zata je " cikin sheshsheka tace"bansan wani asibiti zataje ba bata gaya min " Godiya yama beebalo kafin ya katse kiran , maganar beebalo yayi tasiri sosai a zuciyar shi, kusan minti ashirin ya kwashe zaune a gurin yama rasa ta ina zai fara, Can kuma kamar an tsikare shi ya dauki wayar shi da sauri ya shiga kiran lambar zee. Beebalo na gama waya da Aslam ta kwashe da wani irin maketacin dariya, saida tayi mai isarta, sanan ta saisaita kanta , komawa tayi cikin wani karamin asibitin kudi , da sukeje don zubar da cikin,zee nanan zaune a inda beebalo ta barta , tace ta jirata, Dawowa beebalo tayi gurin zee tace "ƙawa dan Allah kiyi hakuri nadan tsaya gaisawa da wani yayana ne" zee tayi murmushin yaƙe tace "ba komai ƙawa" Duk jikinta a mace yake ji takeyi kamar ta fasa zubar da cikin nan dan haka kurum takejin gabanta na faduwa, kallon beebalo tayi tace,"kawa ji nakeyi kamar na fasa zubar da cikin nan wlh, haka kawai nakeji a jikina akwai matsala game da wnnan lamari, gara kawai na barshi ,idan ckin ya isa haihuwa sai amin aiki kawai a ciro shi ba sai na haihu da kaina ba, kinga sai a dinga ba babin madaran yara a samo mishi nanny ba shikenan ba" Beebalo tace "tab wlh karki kuskura kiyi wannan gangancin na barin cikin nan idan har kina so kici gaba da zama da Aslam, dan wlh yana gane akwai cikin nan ya dinga wulakanta ki kenan, karshe ma ya sake ki a banza akan wani dan qaramin ciki, bakisan maza yanzu basa son mace da anyi aure tayi ciki ba, kuma kinaga zaki iya rainon ciki akwai wahala fa mata da yawa suna mutuwa ta wannan hanyar, kawai tunda mun riga munzo ki zubar da wannan kawai in yaso idan kin samu wani cikin sai ki barshi ," Zee dai duk da hankalinta bai kwanta ba haka ta yarda da shawaran beebalo, Dr din da suke jira ne ya ƙaraso, sun riga sun gama magana da beebalo a waya, ta gayamai harda irin alluran da takeson ama zee, Binshi office sukayi, beebalo ta kara mai bayani sannan ta fice daga office din ta barshi da zee , dake kawance akan gadon dakin donya gwada ta yasan irin alluran da zai mata, Tana fita wayar zee dake hannun ya fara qara dubawa tayi taga , lambar Aslam ne murmushi mugunta tayi tare da qin daga kiran Kira yake yana sake kira a haukace, bata daga ba daga baya ya tura mata da message na karta kuskura tayi gangancin zubar mai da ciki, beebalo na karanta message din tayi delete dinshi a wayar ta kashe wayar gaba daya, Sake kiranta yayi, yaji wayar a karshe take hankalin shi ya kara tashi, miqewa yayi da wani irin sauri ya fita daga office ya shiga motar shi ya figeta da wani irin mahaukacin gudu, Dr na gama gwada zee ya kalleta da wani irin tausayawa, alluran da beebalo ta biya shi makudan kudi danya ma zee sun mata karfi da yawa zasu iya hallakata har lahira, Har ya dakko zai mata yaji tausayin ta ya canza alluran ya mata Wanda bai kaishi karfi ba, Kiran beebalo yayi yace tazo angama, su wuce gida maza maza, zee kam tuni ta fara ganin jiri jiri, kafin su qarasa mota har ta hada wani uban zuba ,beebalo sai zuba mata sannu takeyi cikin matuqar tausayawa, Beebalo ne taja motar kasancewar zee bata cikin haiyacin ta, har gidan ta kaita mai gadi wa wangale mata get , tana parking ta tallabo zee har cikin falon kwantar da ita tayi akan dogon kujera, kafin ta juya ta fice daga falon da sauri, Kaman kar beebalo tabar falon wani irin matsanancin ciwon Mara ya tasowa zee, birgima takeyi tana malelekuwa a cikin falon, tafi minti takatin a haka kafin jini ya balle mata da mugun karfi harda guda guda, kan kace kobo falon yayi faca faca da jini kamar an yanka ƙaramin dabba , Aslam saida ya je asibiti ashirin yana Neman zee dana kudi Dana gwamnati amma ko mai kama da ita bai gani ba, gashi wayar ta a kashe , duk da haka bai daina karanta ba, Sai yamma ya dowa gida a galabaice,tunda ya danno kan motarshi ya hango motar zee fake a parking lot, Ko gama parking din kirki baiyi, ya balle murfin motar ya fito da gudun tsiya , burin shi yaga bai wuce ace yana shiga ya tarar duk karya ne abinda beebalo ta fad'a mai ba, saidai kash yana shiga falon ya hangi zee kwance a kasa cikin jini face face, a fili ya furta"ya furta innalillahi wainnailaihi Rajiun, shikenan ta faru ta kara, " Zee kam hannu ta shiga mika ma aslam numfashinta na wanj irin fusga idonta na lumshewa, lokaci daya ta fede , ta rame ta ƙara fari fat, Zuciya Ce ta debe shi ya karasa gabanta a fusace ya dagota ya hada ta da bango ya shaqe cikin fitar haiyaci yake cewa" meyasa kika zubar min da gudan jinina , mai na miki zaki sakamin da wannan mummunan sakamako, me jinina ya miki zaki salwantar min da rayuwar shi kika sani ko shi kenan kwaina a duniya, kin cuceni zee tsakani na dake Allah ya isa, ki gayamin wani likitane ya miki wannan aikin ,wa kuma ya baki wannan gurguwar shawaran ,ki fad'a min domin daga ke har duk wani mai hannu a cikin salwantar min da gudan jinina bazan barshi ba na rantse da Wanda raina ke hannun sa " Zee kam tun taba zazzare ido , har jikinta ya saki numfashinta ya dauke ta sume, yana ganin haka yayi wurgi da ita ya shiga toilet ya ciki ruwan sanyi a katon bokiti ya sheka mata, take ta shiga sauke ajiayar zuciya, Ganin ta farka yasa ya kara cin kwalarta yace"tambayarki nakeyi keda su waye kuka salwantar min gudan jinina" cikin kuka ta bude baki tana magana amma tsabar azaba maganar ma bata fita sosai, Ganin taƙi bashi amsa yasa ya ya shiga gwada kanta da bango yana marinta , saida ya mata dukan tsiya ta ƙara sumewa , ya yasar da ita a wajen ya tsallaketa ya wuce, Dakin shi ya shiga ya hada kayanshi kaf a cikin trolley ya fita ya shiga motar shi ya bar gidan da mahaukacin gudu, Me gadi kam tun ganin yanda ya shiga gidan d'azu da gudu yasan ba lafiya ,wani Abu Mara kyau na faruwa,ganin fitar Aslam a haukace jikin shi duk jini, yasa da gudu ya nufi falon yana shiga yaga zee a sume ga fuskarta duk a kumbure ga jikinta duk jini, sallallami ya shiga jerowa kafin kuma ya fita da gudu ya debo ruwa ya watsa mata, Aslam kam direct family hause ya nufa saida yayi horn mai gadi ya bude mai get kuma ya masa qarsawa cikin gidan, tsayawa yayi yana tunanin ta yadda zai saka kafar shi a cikin gidan yau.............. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 67 & 68 A galabaice ta shiga sauke numfashi, idanunta arufe , me gadi kam daura hannu yayi aka ya shiga fareti, shikam yau ya shiga uku ya zaiyi da rayuwar sa , Fita yayi da gudu makota, ya shiga buga musu get, me gadin Gidan ne ya taso ya bude mishi, kasancewar sunsan juna, nan ya shiga rattabamai abin da ke faruwa, shima cikin jimami ya nufi cikin gidan, hajiyan gidan ya samu ya gaya mata abin da, me gadin .gidan Aslam ya gaya mai, Hajja fati Macece mai tausayi, dattijuwa ce bata da miji, saidai tanada yaya manya maza da mata, wasunsu ma sunyi aure, anan take zaune,yar gata ce, dan ba abinda yayantsa basa mata, kuma itama metro ce a general hospital, Cikin tashin hankali ta zari hijabinta ta bi bayan shi, har cikin falon mai gadin gidan Aslam ya mata jagora, Ganin halin da zee ke ciki yasa hankalinta ya qara tashi, kallo daya ta mata ta gane inda matsalar take kasancewar ta babban ma'aikaciyar jinya mai matsayin metro, dagata tayi ta shigar da ita toilet din dake falon ta hada mata ruwan dumi ta saka ta ciki, Sosai ruwan ya ratsa zee, take numfashinta ya fara daidaita ta fara bude idonta da suka lumshe, don batasan inda kanta yake ba , Saida ta gasata da kyau, ta barta a toilet ɗin tace ta lallaba tayi wanka, suje asibiti taga Dr, Fitowa hajja fati tayi ta shiga gyara falon ,duk inda ya baci, saida ta gogeshi tas ,koda ta gama zama tayi a falon tana jiran zee, shiru shiru zee bata fito ba don haka ta tashi ta leƙa toilet ganinta tayi a zaune a toilet din ta gama wankan ta daura tawul amma fitowa ya gagareta domin baza iya tafiya ita kaɗai ba jiri take ji sosai, Kamata hajja fati tayi suka fito daga toilet ɗin zaunar da ita a falo tayi ta haura sama ta duba ɗakinta ta dauko mata kaya marasa nauyi , dubawa tayi bata samu pad ba don haka ta aika mai gadi ya siyo musu , bata tayi ta saka, ta saka kayan sannan ta ce ta jirata ta dauko mota suje asibiti, Duk abinda ke faruwa zee hawaye takeyi, tana sauke ajiyar zuciya, ta kasa tsaida hawayen dake bin idanunta, ta ƙudiri aniyar ko Aslam ne autar maza ta rabu da aurensa , tunda ya saka hannu ya mata irin wannan bugun dan kawai ta zubar da ciki, Tayaya akayi yasan ta zubar da ciki waya faɗa mishi bayan daga ita sai beebalo sai allah suka san da wannan zancen, Lallaɓawa tayi ta miƙe daƙer ta dauki wayar ta ta kunna , lambar dad ta kira, yana ɗagawa ta fashe da kuka tace "dad zai kasheni , dad kazo ka rabani dashi bana sonsa na fasa auren dad zan koma na zauna tare daku,kazo ka daukeni kar ya kashe maka ni" Dad cikin tashin hankali yace"daughter meke faruwa, waye zai kasheki , " cikin kuka tace "Aslam ne" nan ta labarta mishi abin ya faru , aiko ran Dad in yakai dubu ya baci,take fuskar shi tayi jajur zabar bacin rai har wani tiriri yaje jin yana fita daga kunnuwanshi, nan ya shiga aunawa Aslam zagi da ɗiban Albarka kafin daga karshe yace ta bi hajja fati zuwa asibiti, kuma tasa idon ganin shi a nigeria nan da wasu ƴan awanni, zaizo saiya koyama aslam hankali, saiya gwammace da bai taba haɗuwa da ke a duniya ba , Karfafa zuciyar shi yayi ya rufe ido ya danna kan motar shi cikin gidan, yana parking ya fito, ina zai dosa yanzu , part din mami, haka zuciyar shi ta umarce shi, can ɗin ko ya tunkara,mami tana ganin shi tasan ba lafiya ba daga yanayin da taga fuskar shi a mugun hade idanun shi jajir, can kuma ta lura da jinin daya bata mai jiki, Innalillahi wainnailaihi rajiun ta shiga maimatawa kafin da sauri mami ta iso gareshi ta mika hannu ta rike mai hannayenshi, cikin tashin hankali ta shiga furta "my son meya faru, meya sameke , daga ina kake haka, meke faruwa" Zaunar da ita yayi akan cushion shima ya zauna suna fuskan tar juna, a hankali ya bude baki yace"mami me na mata da zata saka min da irin wannan mummunan sakayya, mami na cancanci haka daga gareta, mami zee ta zubar min da cikina dake jikinta," cikin kaduwa mami ta shiga sallallami, tana tafa hannaye, Tace "garin yaya ta zubar da cikin kun samu wani sabani ne" yace " wlh mami ba abinda ya haɗani da ita, to mami imma wani Abu ya hadani da ita saita zubar min da ciki" mami tace"kai waya gaya maka, yanzuma ina zainab din take", kwashe komai yayi ya gayama mami tun daga message din da beebalo ta turomai har zuwa wutowar shi nan gidan, amma bai gaya mata a sume ya wuto ya bar zee, Shiru mami tayi cike da tausayin shi hawaye ya cika mata idanuwanta, "Yanzu kaje kayi wanka ka canza wadannan kayan da suka lalace, sai kazo musan abinyi, miƙewa yayi zuwa part dinsu, direct dakin shi ya shiga domin yayi abinda mami ta umarceshi," Yana wucewa mami tabi bayanshi da kallon tausayawa, gsky Aslam baiyi sa'ar mace ba, a dan shekarun shi wadanda da kaɗan suka haura talatin , yana fama da irin wanan kalubalen Rayuwa kala kala, ga rashin dacen mata, ga kuma soyyaya na dawainiya da zuciyar shi , da tana da iko da babu abinda zai hana ta aurawa Aslam Asmah a karo na biyu, kozai samu saukin Rayuwa, idan ya auri Asmah ya rage wani matsalar daga cikin mastalolin rayuwar shi , sai yaji da batun zainabu , amma tasan bata da wannan ikon, Abu daya ta San zata iyayi, shine tausa kamal ya janye daga neman auren Asmah ya barma Aslam, a matsayin ta na mahaifiyar shi, to tasan ko tayi haka tayi a banza, tunda dai ta Riga tasan wanene mahaifin mijinta wato alhaji baba , kaifi ɗaya ne baya magana biyu idan yace yes ta zauna haka zalika idan yace no, shima ta zauna, mutum ɗaya ne take da tabbacin duk fadin duniyar nan zai iya canja maganar alhaji baba, amma duk da hakan baza ta zuba Ido kawai ba, zatayi wani Abu akan lamarin, Koda yayi wanka kwanciya yayi a dakin yana nazarin abinda ya faru yau tundaga farko har karshe, koda yazo kan beebalo diga ma lamarinta question mark yayi,❓zai binciketa don bai yarda da ita sosai ba, idan ya gano da hannunta acikin wannan lamarin zai hukuntata hukunci mai tsanani ba ita kadai ba, da koma wanene , mai hannu akan salwantar mashi da gudan jinin shi , Haka ya zauna yayi ta saƙe saƙe , ko sallan magriba da isha, a ɗakin yayi bai fita ko ina ba, babu Wanda yasan ya kwana a gidan hatta mami tayi tsammanin ya fice daga gidan ne, duk Wanda yaga motarshi baya kawo kamai a ranshi, daddy ne ma daya dawo da daddare yaga motar yadan zargi wani Abu, koda yama mummy maganar tace baizo ba saidai ko amir ne ya kawo motar gidan, bai wani gamsu ba , yadai barshi da niyar da safe zai tambayi mai gadi, Washe gari da misalin karfe biyar na asuba jirgin da Dad ya biyo daga Malaysia zuwa Nigeria yayi landing a airport na garin minna, direct kuma general hospital direban da yazo daukar shi ya wuto dashi, A Amenity word aka bama zee gàdo tun jiyan da sukazo likitoci sun dubata nan suka yi iya kokarin su suka tsayar mata da jinin da take zubarwa, sannan suka daura mata ruwa, sannan sukace aje a siyo jini za'a kara mata, don ta zubar da jini ya wuce misali, hajja fati tambayar zee tayi ko ina mai gidanta taga har sun kwana bai zo ba , bayan jiya zee ta tabbatar mata da cewa yasan abinda ya sameta, cewa kawai tayi baya nan, Tun daga haka hajja fati bata kara mata wani tambayar ba, ita dai tana taimakon ta ne saboda Allah da kuma kasancewar ta mace mai tsananin tausayi, Daidai lokacin kuma dad ya iso. cikin asibitin, Amenity ya nufa kamar yadda zee ta fad'a mai a waya, ganin yadda zee ta koma ba ƙaramin tashi hanakalin dad yayi ba , take ranshi ya kara baci fushin shi ya lunku sosai fiyeda da, take ya ciro waya ya kira wani tsohon abokin tun na yarinta, ɗan sanda ne mai babban muƙami, ya sanar dashi yana son a kama Aslam a mai duka , a kulle shi a cell, kullum ana dukan shi, kuma kar a bada beli shi ga ko waye har sai shi ya bada umarnin a sake shi, Nan ya buƙaci da mutumin ya turo account number, take kuwa ya tura da account number din ganin yawan makudan kuɗin da dad ya mai transfer yasa ba shiri, ya aika yara mota uku zuwa gidan su Aslam domin a kamo shi, Dad daga nan kuma ya nufi office din Dr don jin taka maimai meke damun zee, Dr yamai bayanin komai harda batun jini Leda daya da akeson za'a kara mata, take Dad yace a dibi jininshi tunda iri daya ne da nata haka ko akayi, Da asuba ma Aslam bai fito masallaci ba, a daki yayi sallah asubah don kwata kwata baya jin dadin jikinshi ma, Daddy bayan sun idar da sallah ,ya tambayi me gadi Aslam ya shigo gidan ne, nan kuwa mai gadi ya tabbatar ma da daddy cewa ya shigo tun jiya da yamma kuma dai baiga fitar shi ba yana da tabbacin yana cikin gidana, har yanzu, Tun kafin su fito daga masallacin jini yar motar police ya karade layin gidan gaba daya, koda suka fito sunyi matuqar mamakin ganin motocin police ɗin a kofar gidan su, da sauri suka karasa wurin su bayan sun gaisa Abba yake tambayar ko lafiya wa suke nema, nan wani baki me murtukakken fuska gabjeje da shi yace, "Aslam muke nema", abba yace "lafiya dai ko" mutumin Wanda da alama shine shugaban tawagar ya kara cewa"zamu tafi dashi office idan kana son jin Karin bayani zaka iya bin bayan mu" Abba yace" Aslam baya gidan nan banan bane gidan shi,"daddy ne ya katse Abba da cewa yana "cikin gidan ku shiga ku taho dashi," Abban da sauri ya maida kallon shi ga daddy da yayi wannan maganar, Daddy ne ya musu jagora har zuwa part ɗin su Aslam ɗin, sauran mutanen gidan basu San meke faruwa ba , kasancewar da sassafe ne kowa na daki wasu ma sun koma baccin bayan asubahi, Yana zaune akan sallaya yana mika kukan shi ga mahaliccin shi yaji bugun kofa, ba kakkautawa, gaban shi ne yayi wani irin faduwa haka kawai yaji hankalin shi bai kwanta da wannan bugun kofa ba, amma haka ya daure ya bude kofar, Mamakine ya kusa kashe shi ganin mutane har biyu sanye da kakin police abakin kofar dakin shi, Kallon su yayi yace "malamai lfy , " daya daga cikin su yace"u ar under arrest, munzo mu tafi dakai office ne" yace "saboda me zaku tafi dani office me nayi, zakuzo har cikin gidan ubana kuce zaku tafi dani," Dayan ne yanzu ya amsa da"Mallam da Allah kar ka wahalar damu , kazo muje office duk abinda kake son sani kaji daga baya acan" Shiru ya danyi na some seconds kafin yace"muje to zan biyo ku a baya da mota ta, " kin amincewa sukayi, kasancewar suma ogan yadan san musu wani Abu cikin abin da ya samu akan case din, kuma ya gaya musu no mutunci, Hannunshi suka kama zasu saka mishi handcuffs yaqi amincewa , dole yana ji yana gani ya shiga motar police suka tafi dashi, suna fita Abba ya kalli Daddy yace " me yasa ka yi haka yaya," Daddy yayi murmushi yace" idan nace musu baya nan baza su yadda ba , sai sun shiga sun dudduba, haka kawai su tasar ma iyalan mu da hankali suna cikin hutawa ba laifin fari bana baki, gara dai su tafi dashi cikin salama, ai tsunstun daya ja ruwa shi ruwa kan duka" Abba yace "to yanzu zamubi bayan su ne" Daddy yace"A'a nifa baza ni ba idan kai zaka bisu bismillah" Abba yace "aikam banga ta zama ba bari na shirya nabi bayansu" dage kafadu daddy yayi alarmar, I don't care ya nufi part dinshi ,shima Abba part dinshi ya nufa don ya shirya yabi bayan su zuwa station, Suna isa station ba'a bashi daman yin wani magana ba aka shiga da shi cell , ogon su ya bada umarnin a mishi dukan tsiya, Aslam na tambayar me yayi ba Wanda ya saurare shi, mutum biyu ne jibga jibga suka shiga dukan shi da kulake baji ba gani, Ko kafin Abba ya karaso sun hada mishi jini da majina, Abba daya nemi jin ba'asi folder case din Aslam ɗin da ka bude aka dauko mishi, mahaifin matar shi ya shigar da kara akan dukan tsiyan da yama ƴar shi da karamin ciki Wanda hakan yayi sanadiyyar zubewan cikin, yanzu haka tana asibiti a kwance rai a hannun Allah, Dukar da kai Abba yayi ya shiga maimata innalillahi wainnailaihi rajiun, dagowa yayi idanun shi sun rine, yace "yanzu oga meye abinyi," oga yace" abinyi shine zamu rike shi anan gurin mu har sai yarinyar ta samu lafiya, sannan mu mikashi kotu a yanke hukunci daidai da laifinsa," Abba yace "ko za'a iya bamu bellin shi kafin, komai ya daidaita" ba, Oga yace "ba zaiyuwu ba" Abba zai ci gaba da magana oga ya dakatar dashi ta hanya daga mai hannu yace "na gama magana, bana sonjin wani magana data shafi beli" Abba ganin yadda ya daure fuska alamar yana so yaci mai mutunci, yasa dole yayi shiru da bakin shi , ya mike ya fice daga station din, jiki a sanyaye. A gida kam ba Wanda yasan abinda ke faruwa, don daddy dama abin ko ajikin shi, bai damu ba, balle har yaje gayawa mummy, Abba kuma kin gayawa mami yayi don karta shiga damuwa, Koda ya sanar ma daddy abinda oga ya fad'a mai , na cewa Aslam ya daki matar ya zubar mata da ciki. Mahaifinta, ya shigar da kara gurin yan sanda , da yadda sukayi na batun beli, daddy cewa yayi Allah ya kyauta, Wasa wasa kwanan Aslam uku a station kullum kuma sai am mishi dukan tsiya safe da rana da yamma, Abba kam kullum cikin zarya yake amma oga yaki sauraren shi, Alhaji baba Abba ya sama da maganar , shima dai Allah ya kyauta kawai yace, Mami kam ta shiga zullumin don tun ranar da Aslam yazo mata da batun zee ta zubar da ciki take ta saka ran kara ganin shi amma shiru kakeji,ta zuba ido shiru ta kirashi a waya shiru, Bayan kwana uku zee ta warke ta samu karfin jiki sosai , nan Dr ya sallameta, Dad ɗaukanta yayi sukaje station din da aka rufe Aslam sawa yayi aka fito mai dashi, Innalillahi karkuso kuga Aslam yanda ya koma abin tausayi, duk jikin shi yayi shedan duka wani gurin ma ya fashe, fuskar shi kam ya kumbura sintim kamar ba Aslam ba kwata kwata ya fice daga haiyacinsa , taso shi gaba yan sandan sukayi, har gaban dad, kallon banza ya watsa mai kafin yace," Aslam kake kowa,kayi babban kuskure da daga hannu ka dukarmin yarinya, koni Dana haifeta ban taba dukanta ba sai kai, don kawai ka mata asiri ka aure ta kuma sai ka hada da duka, so yau asirinka ya karye, daga yau babu kai babu zainab, ko a hanya karka kuskura ka kara nuna ka santa, " kallon oga yayi dake ta washe baki kamar gonar auduga yace a "sake shi haka", Kallon zee yayi data miqe tsaye ta dafe girjinta , tun fitowar Aslam ganin yadda ya koma yasa tuni hawaye ya fara bin kuma tunta, tana son Aslam sonda ko iyayenta bata yi musu irinshi, koda take cewa ko shine autar maza ta barshi , fad'a kawai takeyi, don ita kanta tasan karya takeyi, kawai bacin Raine ya saka fadar haka , Ganin yanda take kuka, yasa dad mikewa a fusace ya figi hannunta suka bar cikin station, daga nan kuma airport suka nufa, basu zame ko inba sai Malaysia, Aslam kam rigar shi wani kurtun dan sanda ya miko mai ya karba ya saka wasu takaddu ya sassaka hannu kafin suka sallameshi daga station din.............. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillahi🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan page din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 69 & 70 Keke napep ya hau zuwa London road, babu ko sisi a aljihun shi, don ƙananan polisawan nan tass suka yashe shi, jiran shi me keken yayi ya ƙwanƙwas get din gidan me gadi ne ya taso ya buɗe yana tambayar waye,sauran maganan ne ya maƙale ganin Aslam tsaye cikin wani mawuyacin yanayi, da'ker Aslam ya buɗe baki yace, " ka sallami mai keken nan, " "To yallabai to yallabai" haka me gadi ya dinga maimaitawa jiki na rawa. Bayan me gadi ya biya kuɗin napep dawowa yayi yana ta jerawa Aslam sannu tare da tambayar shi meya same shi haka, Aslam ya bashi Amsa da cewa"tsautsayi na samu amma da sauki sosai alhamdulillahi" bayan haka bai ƙara cewa komai ba ya wuce cikin gida. wanka kawai yake bukata a halin yanzu, don haka yana shiga ya wuce toilet ya hada ruwa mai zafi ya shiga cikin bathtub ya gasa jikin shi da yayi mugun tsami ta ko'ina, saida ya kwashe fiye da awa ɗaya sannan yayi wankan sabulu,ya fito daure da tawul a kugunshi. Gaban mirror ya tsaya yana karewa jikin shi kallo, yanzu lafiyayyar farar fatarshi mai shegen sulbi da daukar Ido ne ya koma haka cikin kwana uku kacal, duk dabbare dabbare , jaja jaja fari fari, ga wasu wurare sun tattashi saboda cizon sauro, fuskar shi ya kalla, nan take wani kululun baƙin ciki ya tokare mai wuya, ganin yadda halittar fuskar shi ta sauya, gaba daya kamar ba shiba, ƙasan idon shi na dama ya wani kumbura , haka ma labbanshi na kasa shima yayi simtim , goshin sa kuma wani makeken ciwo ne. ƙwafa yayi a zuciyar shi yana aiyana ta ina zai fara ramakon wannan cin mutuncin da Dad din zee yasa aka mishi, ya lashi takobi ko ba jima ko ba dade ,saiya rama ,ko ba ta hanyar duka ba kuwa,sai ya mishi abin da zaiji zafi kwatan kwacin irin zafin da saka shi ji ,koma fiye da haka, tunda yake a rayuwar shi bai taba zuwa police station da sunan belin din wani ba balan tana kuma ace shi aka rufe, sai gashi yau wai ta dalilin zee shine ya kwana uku a cikin cell, ana dukan shi ana azabtar da shi, zee din daya bijirewa zabin iyayen shi saboda ita,Wanda daga ƙarshe yazo yana nadama da danasani, babu abinda auren zee ya tsinana mai sai asara da wahala, a ƙarshe harda cin mugun duka. Wata zuciyar ne ta shiga raya mai Aslam baka ga komai a rayuwar ka ba, tukunna matuƙar baza kaje ka nemi gafaran iyayen ka ba, ka tsuguna har kasa ka nemi gafaran alhaji baba ba, Asmah kuma ka sakama zuciyar ka haƙuri da juriya akan lamarin ta , ka zama jarumi , ka dauki rasata da zakayi a matsayin kaddaranka. Mai me zafi ya dauka ya shafa a inda duk ke mishi ciwo , kaya ya dauka marasa nauyi ya saka, sannan ya sauko ƙasa ya hada tea mai kauri yasha , yasha maganin pain relief, Dana ciwon gabobi, ya nemi waje ya kwanta,. Saida Aslam ya kwashe sati daya a gida yana jinyar jikin shi , zuwa yanzu ya warke rass duk ciwukan da ke jikin shi sun warke sai abin da baza a rasa ba,fuskar shi ma ta dawo normal kamar bai taba samun wani matsala a wurin ba, baya fita ko ina daga gida sai masallaci, abincima mai gadi yake aika ya siyo mushi. A gefe guda kuma ya daura damaran yaki da zuciyar shi domin ya cire tunanin Asmah a zuciyar shi , ya tabbata ya rasa ta har a bada, tunda idan lissafin shi daidai ne yau saura wata daya cif ta zama mallakin wanin shi, Sai dai kuma ko ɗigo bai ragu daga soyayyar da yakema Asmah ba, saima abinda yayi gaba , ba karamin kokawa yakeyi da zuciyar shi ba dan ganin ya yakice ta daga zuciyar shi amma ina,yanzu ta kaiga har gizo take mishi idan yana zaune a daki, shi karan kanshi abin har mamaki da tsoro yake bashi , hotunan ta kuwa yanzu sune komai na wayar shi ko ina ka bude a wayar shi hoton ta ne, hatta password din wayar shi yanzu husnah ne, Ganin yana azabtar da kanshi a banza yasa ya yanke shawaran da yake ganin shine daidai a gareshi, aikawa yayi mai gadi ya siyo mai sim card na mtn har guda biyu, saka sim din guda ɗaya yayi ya buɗe WhatsApp dashi, da suna M,M ma'an mahaukacin masoyinki, lambarta da take WhatsApp dashi ya dauka , ya yi saving a cikin sabon sim din, ya kunna data, nan take kuwa account dinta yayi applying a wayar shi, shiga yayi ya mata sallama, bata online ,dan haka ya sauka , bini bini ya duba yaga kota hau online amma shiru , har washe gari, sai kusan yamma ta hau online , tana cikin duba message taga message d'in Aslam, bata son number ba, shiga tayi ta duba taga sunan M,M , daurewa tayi ta amsa sallaman, lokacin kuwa yana online don duk bayan minti minti yake kunna data ko zata mai reply, kamar jiya yakeyi, ya shiga jero mata gaisuwa da bangajiya, sannan ya gabatar da kanshi a matsayin yar class dins ce ,a wani group na yan department dinsu ta dauki numberta, jin haka kuma macece ba namiji ba yasa ta saki jiki da shi suka dinga fira , daga karshe har exchanging hotuna sukayi, ya lalubo hotan wata ma,aikaciya a kamfanin su data nace tana sonshi take turo mai hotuna ya tura ma Asmah a mastayin nashi. Ba karamin dadi wannan lamari yama Aslam ba, har voice takeyi jefi jefi in suna hira, shi kuma bai taba yin voice ba , itakuma bata taba kowa ana iya yin haka ba, don haka tunanin ta bai taba kawowa wai Aslam bane. A kwana a tashi ba wuya yau saura sati hudu cif bikin su Asmah, ta kowani bangare shirye shirye akeyi ba kama hannun yaro, kowa ka gani a gidan yana cikin shirye shirye ne baga iyayen su ba baga amaren ba, baga angwayen ba, shirye shirye akeyi kamar ba'a tabayin biki a gidan ba , yoo kukuwa amare uku rerass angwaye biyu, don har zuwa lokacin maganar batool da bash bai daidaita ba , a bangaren diraman su ko sai abinda ya karu, har takai da iyaye maza ma sunsan da wannan yar tsaman dake tsakanin su, Abu dai sai gaba gaba yake yi. Yau da ta kama ranar laraba alhaji baba ya kira daddy da Abba don yaji shirye shiryen me suke yi don shima yasan ta inda zai fara nashi shirin, dan jin wannan bikin yake a ranshi kamar bai taba aurad da ɗa ko jika ba. Daddy yace "mun gama magana da mummy su zan bada kuɗi aje Dubai ayi musu siyayyar kayan furnitures da kuma kayan kitchen ,da dai sauran duk wani tarkace da ya kamata a sai musu, na bata na gaba daya su hudun ne dukda ita batula har yanzu naga bata fitar da tsayayye ba, amma dai na bada harda nata kasancewar bamusan yanda Allah zaiyi ba," Alhaji baba yace"masha Allah komai yayi Allah yayi albarka ya kara budi" gaba dayan su da amin suka amsa. Alhaji baba ya kalli Abba yake"kai kuma fa yusufa me kake shiryawa". Abban yace" dama nima munyi magana da maryam akan batun kayan ɗakin dana kitchen d'in amma tunda yaya ya rigani furtawa shike nan, ni zan dauki nauyin duk kayan da amaren zasuyi amfani dashi, na fitan biki dama na kwalliyan amarci, sai kuma batun abincin da za'a ci tun daga satin da aka shiga bukin har zuwa sanda baki zasu gama komawa na dauki nauyi, drinks ruwa nama, kifi , komai ma da za, a ci na dauki nauyi," Alhaji baba yace"alhamdulillahi kamai yayi Allah ya muku albarka, to aikun gama kwashe duk manyan hidimomin , to ba damuwa nima baza a barni a baya ba , zan saiwa kowaccen su sabuwar mota , na kuma bata kudi million ɗaya, ta rike a hannunta wacce zatayi sana'a sai taja jari koya kuka gani, lefe dama ko wani ango mun basu dama suje hu hado abinsu da gumin su haka ma sadaki kowannen su ya Ciro daga aljihunshi, gurin zama dama kowannensu ya gama gininsa,me kukace, " Daddy ne yace"komai yayi alhaji Allah yasaka da alkhairi ya kara girma" shima Abba godiya ya shiga kwararowa wa tare da addu'an Allah ya kara nisan kwana. Alhaji baba yace"magana ta biyu da yasa na kiraku akan batula ne, har yanzu bata gabatar mana da kowa ba, kuma gashi yau biki saura sati hudu, idan muna da yawan rai, to karku manta dama nace duk wacce bata da tsayayye ni zan zabar mata miji nagari, a kwai wani jikana na wurin abokina alhaji hudu, mai rasuwa Mahmud nasan kunsan yaron , ya gama karatun shi na sojoji, yanzu haka soja ne me mukamin captain, to dashi zan hada ta saurayine baida mata, to amma kuma hajiya ta sameni da wani magana wai tana ganin kamar yaron nan bashiru kamar soyyaya sukeyi da batulan, to nidai nace mata anya kuwa don inda soyyaya sukeyi yanaji anata shirye shiryen aurad da yan,uwanta dole zan yi wani yunkuri shima, to tunda kukaga haka kila zato ne kawai mukeyi, amma duk da haka zankirasu anjima shida batulàn naji ta bakinsu,". Daddy yace"gaskiya ne nima ina zagin kamar akwai wani Abu a tsakanin su duba da yanayin yadda suke mu'ala a ƴan kwanakin nan, to dana samu mummyn su da maganar tace min ba soyyaya sukayi yi hasalima gani takeyi kamar babu jituwa a tsakanin su." Alhaji baba yace"koma dai menene yau zan kirasu naji ta bakin su, don kar mu shiga hakkin su , koya kuka gani" Nan take daddy da Abba sukayi na'am da shawaran alhaji baba, haka suka ci gaba da tattaune muhimman maganganu kafin sukayi sallama da shi suka wuce, A bangaren Dr bashir kam yana cikin tsaka mai wuya , shi yanzu damuwar shi daya ta yaya zaiyi ya furta wa batool soyyaya, yasan a halin yanzu idan ya furta mata so baza ta saurareshi, shi kuma yana tsoran tace bata sonsa dan bazai iya jurewa ba, kuma bayaso ayi bikin nan ace banda su a ciki, imba haka ba da ya bata lokaci , har zuwa lokacin da itama zata kware mai, to amma bashi da ishashshen lokaci, dan haka ya yanke shawaran , kawai zai turo iyayen shi ne yace ita tace ya turo su , inyaso sai ya toshe kunnen shi daga masifar ta wuyar ta dai a daura idan ta shiga hannun shi zai ladaftar da itane. Yana tsaka da wannan sake saken ne kira ya shigo wayar shi daga Amir wai alhaji baba na neman shi yau da daddare, sauke ajiyar zuciya yayi a ranshi yana fatan abinda yayi hasashe ya tabbata, Da daddare bayan ya idar da sallan isha'i yayi wanka ya fesa adon shi kamar yadda ya saba idan zaije tsonaka nan fada, daukar key din motar shi yayi ya fice daga gidan su zuwa gidan alhaji baba, Daidai wannan lokacin batool na hango zaune a gaban alhaji baba, kallonta yayi yace"batula abinda yasa na kira ki dama naga har yanzu baki gabatar da naki manemin ba kuma gashi naga yau har saura sati hudu biki, ina fatan baki manta da magana na ba na cewa duk wacce bata fitar da miji ba zuwa lokacin dana baku ni zan zabar mata miji da kaina". Gaban batool ne yayi wani irin faduwa nan take ta shiga haɗa zufa, ita dai a halin yanzu bata da Wanda zata gabatar a matsayin mijin da zata aura , don ko saurayi bata dashi, ita yanzu babban damuwar ta batasan Wanda alhaji baba zai zabar mata a mastayin miji ba , kilama daya daga cikin almajiran wannan abokin nashine alhaji Mallam. Wani zuciyar ne ta ce mata ya bashir fa, take kuma wata zuciyar tace Allah ya kiyaye ki da auren wannan dan banzan mutumin, wata zuciyar kuma tace, to aiko gara ya bashir d'in akan almajiran alhaji Mallam dan ko ba komai shi dan gayu ne kuma kyakkyawan gaske, wata zuciyar kuma tace kina hauka ne batool idan ke kina iya auren shi to shiya gaya miki yana sonki ne,haka tata saƙe saƙe ta saka wancen ta kwance wancen. Alhaji baba ganin shirunta yayi yawa yasa yayi gyran murya tare da cewa "ke nake saurare fa batula,". Dagowa tayi ta kalle shi bayan ta hadiye wani busashen miyau tace"ni bani da wani zabin kaina a halin yanzu, dama dai za'a kara mini lokaci ne zuwa gaba kadan" alhaji baba "yace babu wani lokacin da za'a kara miki nasan kinsan halina sarai bana magana BIYU, yanzu tambayan da zan miki ki bani amsa tsakanin ki da Allah idan kika boye wani Abu kin cuci kanki, menene tsakanin ki ba Dr bashir?" . Sautin bugun zuciyarta ne ya kara karfi jin an ambaci sunan shi, itako menene tsakanin ta da Dr bashir banda rashin mutunci, ita ko'a fuska bai taba nuna mata alamar yana sonta ba,amma tanaji a zuciyarta da ya furta ba shakka zata iya auren shi, don tana jinshi sosai a ranta, Cikin kasalalliyar murya tace"babu komai a tsakanin mu , daya danganci soyyaya" murmushi alhaji baba yayi yace "to masha Allah , tashi kije daga nan zuwa ko wani lokaci zaki iya tsinkayar kirana" Dr bash kam yana isowa part d'in mummy ya fara nufa da nufin ya ganta kafin yaje amsa kiran Alhaji baba, shiga yayi main parlour ba kowa sai katon TV dake kunne yanata aiki , neman guri yayi ya zauna, ko wani daga cikin su zai sakko. Cikin harde hanya ta fito daga part d'in alhaji baba, innalillahi wainnailaihi rajiun me tayi kenan me hakan ke nufi hakan na nufin za'ayi sarakar ta kenan, ga almajiran alhaji Mallam , tabdijam Ashe akwai kallon rashin M a gidan nan don wlh baza ta yarda ayi sarakarta ba saikace wata kosai, A haka ta shiga parlourn hankalin ta duk a tashe, jin motsin kofa yasa. Dr bash dake zaune a falon sauri dagowa ya kalli bakin kofar, aikuwa caraf idanun shi ya sauka akanta, wani dadi ne ya lullubeshi shi , take ya saki wani kayataccen murmushi , saidai kwata kwata ita bata ganshi ba, ganin haka yasa , tana zuwa daidai shi zata giftashi ya saka mata kafa. Tuntube tayi da kafar shi hakan yasa tayi baya zata faɗi, harta rintse idonta don ta sadaƙar ta fadi ta gama, saidai jinta a jikin mutum yasaka ta saurin bude idanun ta, irin rikon nan ya mata kamar suna rawan indiya , karaf idanuwansu ya sarke Dana juna , kallon kuda suka shiga yiwa juna na some seconds. Hannayenta ta mika ta tunkude shi , ba shiri ya saketa, balla mai harara tayi ta buga tsaki, ita yau bata jin yin surutu don tana da tunanin yi a gabanta, raba shi tayi ta wuce shi, cikin salon takunta na yanga juyawa yayi yana kallonta har ta kama kafar bene zata haye, ta tsinci muryar shi yana cewa" mutum mummuna sai shegen yanga haka, ke ba kyauba amma iyayinki yafi karfin ki, tsabar muni ko saurayi baki dashi duk yan uwanki ankai kudin aurensu banda ke, kibani dama kawai na taimake ki na rufa miki asiri na lallaɓa nace ma su daddy kince kina sona, nayi maneji dake don barinki haka a gida a aurad da yan uwanki, zaki zama abin tausayi ne,". Wani irin juyowa tayi tana kankance idanu cike da masifa, lip dinta har rawa yakeyi , tsabagen an tabo ta ,tace"Allah ubangiji ka tsare ni,"tuf ta tofar da yawu gefe, kafi ta tako gabanshi cikin wani irin cat walk, dan nisa dashi kadan ta tsaya ta kalle shi a yatsine ta daga yastanta tana nuna kanta daga sama har kasa tace " kalleni frm up to down , wlh nafi karfin ayi maneji dani, kuma da kake batun kyau nasan ko gasar kyau aka saka tsakanin mu kafin mutum dari su jefe maka kuri'a mutum billion sun jefamin, aure ne dai bazan aure ka ba, baka daga cikin tsarin irin mazajen da suke burgeni ka gane ai" ta karashe tare da daga mai gira da murza hannunta ya bada sauti Tass. Tunda ta fara magana yake binta da wani irin kallon kauna, dan bakinta yake bi da kallon sha'awa ji yake yi kamar ya kamo ta ya shiga kissing dinta madly, har mafarki yakanyi jefi jefi gashinan yana tsotsan bakin ta. Saida ta juya zata bar wajen ya dawo daga duniyar begen lips dinta, wani irin taku ta shigayi da gayya Wanda yafi na d'azu daukar hankalin shi, daga murya yayi yace"karfa kiyi tunanin sonki nakeyi taimakon ki zanyi kar azo ana kwatance dake a anguwa , wannan wadda tai kwantai dinnan to tunda kuma bakya so kin hutashsheni" ko juyowa batayi ba balle ta tanka shi ,saida ta kule wa ganin shi , sannan ya sauke ajiyar zuciya, wani kyakkyawan murmushi ne ya kufce mai tunawa da gadar zaran da yake shirin daura mata tabi takai, na turo iyayen shi yace injita,kwafa yayi yace yarinya zakiyi bayanine Allah dai yakai damo ga harawa. Juyawa yayi ya fice daga part d'in zuwa na alhaji baba, yana nan a inda ya gama magana da batool bai kai ga tashi ba, bayan sun gaisa harda dan taba wasa na kaka da jika, alhaji baba ya kalle shi yace "abinda yasa na kiraka bashir tambayar ka nake so nayi tsakanin ka da Allah ka gayamin gaskiya, menene tsakanin ka da batula". Wani irin farin ciki ne ya lullubeshi , hamdala ya shiga jerowa a zuciyar shi kafin yace" alhaji soyyaya muke yi, inason ta tana sona, amma taƙi bani dama na turo magabatana , nayi nayi taki amince min , wai ita bata da ra'ayin a hada bikinta dana kowa tafi son ayi bikinta ita kadai, wai na bari sai angama bikin yan uwanta saina fito, to dama nima gobe nake son na samu su Abba da zance". Alhaji baba yace"kai madallah Abu yayi kyau tashi kaje Allah yama albarka gobe kacema alhaji usman ina son ganin shi". Godiya bashir ya shiga zubawa kamar bakin shi zai tsinke, saida alhaji baba yace ya isa haka............... 💖more comment more typing💖 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 71 & 27 Washe gari kuwa iyayen Dr suka zo ba bata lokaci akayi abinda za'ayi, a take suka bada kudin komai da ya kamata su bayar na àl'ada, iya mazan gidan ne kawai suka san da maganar don hatta mummy da mami basu Sani, balle kuma su Asmah. Ummi mahaifiyar Amir da ke zaune a abuja yau ta sauka kasancewar da ita za'aje dubai domin siyayyan kayan amare, ita da mummy zasuje, don mummy cewa tayi ita da kanta zata je ta zabar a yan matàn ta kayan daki domin tafi kowa sanin abinda kowaccen su take so,da kuma kalan da take so. Yan matan Mummy ba karamin murna sukayi da zuwan Umminsu ba, kamkameta sukayi suna murna da tsalle kamar wasu yan three - three years, Amira kan baya taja tana murmushi da sunsusne kai, ita ala dole tana jin kunyan ummi, matsayin ta na mahaifiyar Amir. Dagowa ummi tayi ta kalli Amira cikin zaro ido da mamaki tace , "me zan gani haka yau ni Aminatu, Amira yau ni kuma kike jin kunya, oya oya zokima umminku oyoyoo" ta fada tana jawo amira ta rungume ta , "wani Amir d'in wofi zai shiga tsakanina da daughter na, karna sake ganin haka ki sa a ranki ke na haifa ba Amir kinji" gyada kai Amira tayi tana murmushi. Haka suka wuni tare tana ta jansu da hira , tsaraban kayan kyaran data fara zuwa musu dashi ta babbasu wadan da zasu fara amfani dashi tun yanzu,irin su sabulu wanka da turaren wanka dana jiki , Dana wanke kai da dai sauran su, don tace maganar gyaran amare na hannunta ita zata musu komai na gyara , aiko karkuso kuga murna, wurin amaren. Kwanan ta biyu da zuwa jirgin su ya daga zuwa Dubai ita da mummy, Alaka zakanin M,M da Asmah sai kara karfi takeyi, kullum cikin charting suke, koda wasa Aslam bai taba tauko mata zancen abinda ya shafi aure ko saurayi ba , don yana tsoran jin abinda zai iya saka zuciyar shi bugawa. Yau dai suna ciki charting Asmah tace, "friend wai ko na tambayeki ki mana " yace " ina jinki Allah yasa na sani" tace"kina aure ne?" yace "A'a kawa me kika gani" tace "ba komai nadai tambaya ne, niko kinga biki na saura sati uku yau insha Allah". Wannan magana ba karamin sharking ya saka zuciyar Aslam ba, shi yama manta da batun cewa zatayi aure tunda ya samu yana charting da ita 24 hour yasa yake jinshi cikin nishadin da yasa ya manta abin da ke gaban, sauka yayi daga online ɗin don ji yayi gaba daya zazzaɓi ya rufe, hankalin shi ya tashi nan take duniyar ta shiga juya mai, ba shiri ya nemi guri ya kwanta. Asmah na jira kawar tata ta bata amsa taji shiru karshe ma taga bata online, bata kawo komai a ranta ba saima hoton zannuwan ankon yinin bikin data tura mata, tare da short voice na cewa idan aka buga invitation card zata turo mata , sai taga programs d'in bikin gaba daya. Wasa wasa Aslam ciwo sai karfi yake yi ,ya lallaba ya tashi yasha magani amma kamar bai shaba, tun yana iya daurewa har abin yaso yafi karfin shi. Waya ya dauka da'ker ya lalubo number Dr bash ya danna mishi kira, lokacin da kiran ya shigo wayar bashi dawowan shi kenan faga aaibiti , so yakeyi yayi wanka ya huta zuwa yamma kuma ya lwka batool don ya kwana biyu rabon shi da ita tun ranar da alhaji ya kirashinnan, ji yakeyi kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi a gabanta. Bashir yana daga wayar, Aslam yace"bash don Allah kazo gida ka same yanzu yanzu " yana yin maganar tari ya sarke shi ya shiga yi ba kaukautawa. Daga yanda bashir yaji muryan Aslam yasan ba lafiya, tambaya ya shiga yi "Aslam, Aslam meke faruwa " ina Aslam bai amsa shi ba don tari yaci karfin shi, cikin gaggawa bashir ya mike ya kwashi wasu daga cikin kayan aiki da yake dasu a gida da allurai da magunguna ya shiga motar shi ya nufi gidan Aslam d'in, yana shiga direct cikin main falon ya dosa , a kwance a kasa ya hango Aslam , da alama ya fado ne daga kan kujeran da yake kwance. Da sauri ya karasa ya dago sa , ganin halin da yake ciki take ya gano inda matsalar take, kasancewar shine likitan daya duba shi last cikin tashin hankali ya shiga furta"Aslam why why, meyasa make neman ka kashe kanka saboda mace for god sake". Kwantar da shi yayi ya koma mota ya tsintsinto duk abinda yasan zai yi amfani dashi don taimakawa Aslam din, allura ya fara yi mishi, ya daura mishi ruwa , nan take ya shiga sauke ajiyar zuciya barci mai nauyi yayi awon gaba da shi, guri bashir ya nema ya zaune a kujeran dake facing d'in na Aslam d'in ya zuba tagumi da hannu bibbiyu yana kallon shi. Saida yayi baccin awa hudu lafiyayyau sannan ya farka, to jikin dai da dan sauki, har lokacin bashir na tare dashi bai motsa ko nan da can ba, tasowa yayi ya taimaka mai ya zauna. Cikin lallama bashir ya shiga yi mai fada akan abinda yake yi nason hallaka kanshi, yace "kayi hakuri Aslam, komai idan kaga mutum bai samu ba a rayuwa ba rabon shi bane, akan me zaka saka damuwa har haka a ranka, nidai shawaran da zan baka shine ka karfafa zuciyarka, karka bari kaima kanka lahani a banza, addu'a ya kamata ka dage dashi, yanzu ciwon ka dabe dade da lafawa ba ke neman tashi har fiye da yadda yayi maka kwanaki, zuciyar ka na daf da bugawa, idan kai baka son rayuwanka mu muna sonka,". Dagowa Aslam yayi da'ker ya kalli bashir a hankali ya bude baki yace "bashir bazaka gane halin da nake ciki bane, ba Wanda zai gane irin radadin da nake ji a zuciyata sai wanda ya taba shiga makamancin halin dana ke ciki a yanzu, kayi hakuri bashir amma bazan iya cireta a zuciyata na, domin bani na saka ta ciki ba Allah ne , ya sakata, shi zaka taya ni roka ya cire sonta tunda ba alkhairi bane a gareni, ka bani iya taimakon da zaka iya bani kawai kaje abinka " Girgiza kai Dr bash yayi, magunguna ya bashi da kuma alluran da zai dinga zuwa duk bayan kwana biyu yana mishi , harna sati biyu, allura ne mai kyau kuma zai taimaka ka mishi sosai akan ciwon shi, nuna mishi yadda zaisha magani yayi, sannan yayi mai sallama ya fice jiki a sanyaye. Kwanan su mummy takwas a Dubai suka dawo duk wani siyaya da zasuyi sunyi shi cikin aminci har kayan ma sun rigasu sauka a 9ja. Washe garin dawowar su, ana saura sati biyu biki , dangin Barr Adam suka kawo lefe, dan kari! kar kuso kuga kayan set d'in akwatina mai guda shida shida da kit ne aka kawo har set uku, kowannen su makare da kaya na ganin na fada, abin ba,a cewa komai, Wani washe garin kuma aka kawo na Asmah dana Amira, woohoho wani kaya sai amale, set hudu hudu ne na akwatina masu guda hudu hudu da kit, mami ne ta hado kayan tana daga zaune a gida tayi siyayyarta, ta online wurin wata kawarta da take saro manyan kaya daga kasashen duniya, kusan yawancin komai na akwatinan iri daya ne saidai banbancin size da kuma colour. Har zuwa wannan lokacin batool bata San da batun ta da Dr bash ba, saidai su mummy da mami duk sun Sani, kuma sunyi farin ciki, sosai. Washe gari kuma aka kawo kayan batool daga gidan su Dr bash, shima dai masha Allah abin ba'a cewa komai ita kuma set biyu aka kawo mata mai guda goma goma da kit, Lokacin da aka kawo kayan su batool basa nan sunje kai dinki, koda suka dawo tararwa sukayi an bude akwatina a falon mummy ana kallo, cikin da mamaki natool ke tambayar ummi, "kayan waye wannan kuma , inace an gama kawo lefen , ko karowa sukayi ne". Mami ta kalleta da murmushi a fuskarta tace"nakine batool yanzu aka kawo daga gidan su Dr,kaiii kaya sunyi kyau Masha Allah, gaskiya basuyi kauron komai ba komai yaji masha Allah". Jin abinda mami take cewa yasa batool sakin murmushi , don ta dauka mami zolayar ta take yi don mami kan zolaye su wani bin, bata dauki maganar serious ba , haurawa ma sama tayi abinta don fitsari takeji, suma su Asmah biyo ta sukayi , don in ana kallon kaya basa zuwa kallo don kar ace sunyi , rashin kunya , har zuwa yanzu cikinsu ba wacce taga kayanta, Asmah zama tayi ta kunna data , kwana biyu tana ta tsumayin sabuwar friend dinta amma har yanzu rabonta da hawa online tun shekaran jiyan can, dan bata fuska tayi, bata ji dadin hakan ba ,koba komai sun saba cikin kankanin lokaci, ita kanta tana mamakin yanda tayi sabo da kawarta m,m haka cikin sauki, duk da kasancewar miskila,. Tana cikin wannan sake saken ne wayar ta tayi ringing, wani kyakkyawan murmushi ne ya kufce mata ganin sunan Wacce ke kiranta , my sisi, picking tayi , tare da sallama, acan bangaren /Khadijah ta amsa fuskar ta cike da farin cikin isowarta minna lfy, bayan sun gaisa cike da kewar juna khady tace "ya Asmah albishirinki" cikin zakuwa tace "goro fari Sol my sister" Khady tace "yanzu haka ina mobile a tsaye ,yanzu motar mu ta sauka, ko minti biyar bamuyi da sauka ba" zabura Asmah tayi ta mike zaune"dan girman Allah da gaske kikeyi khady" dariya Khadijah ta kwashe da shi jin yadda duk yayar tata ta rude, tace"wlh yaya, da gaske nakeyi, AI bazan iya jira muzo tare dasu mimi ba , wai su fa sai cikin week din biki zasu zo, nidai kam bazan iya jira ba , na roki didi shine fa da kyar ya barni saida nayi kuka, tukun na" cikin tsananin jin dadi Asmah tace, "kai sister gaskiya naji dadi sosai wlh ,ki jirani yanzu gani nan zuwa na dau keki". Suna ajiye wayar ta kalli su zahra da suke jira ta gama waya su tambayeta wacece ta rigasu da cewa"Khadijah ce fa tazo daga kontagora yanzu haka wai tana mobile zanje na daukota ne" tana gama fadar haka ta fice cike da daukin ganin yar kanwar tata,. A falo ma sanar masu mami zuwan Khadijah tayi da kuma daukota da zatayi daga mobile, dukkansu sunyi murna da zuwan Khadijah , sannan suka mata a dawo lafiya,. Bakin get ta nufa domin ta samu bello don ya kaita ta taro Khadijah, tana isa motar ya kamal na shigowa cikin gida, ganinta yasa yayi saurin yin parking ya fito daga motar daga wurin aiki yake don sanye yake cikin bakaken suite dinshi na lauyoyi,. Itama ganin haka yasa ya kalleshi fuskarta dauke da murmushin kauna tace" sannu da dawowa farhatal kalb " cikin jin dadi yace "yawwa nurul ayn, ina zakije haka cikin rana, nifa bana son kina shiga rana , wannan kyakkyawan fuskar taki bata dace da jin rafin rana ba" murmushi ta saki tace"wai Khadijah Ce ta iso tana mobile shine nake son naje na daukota " yace "A'a A'a kice sisin mu ne tazo oya muje mu dauko ta" ya karashe maganar yana nufar motar shi ya shiga , itama bin bayan shi tayi suka fice daga gidan don dauko Khadijah. Ummi ne ta shigo dakin su batool bayan tafiyan Asmah kallon batool tayi , kasancewar haka take mu'amala dasu kamar kawayenta , tace "waii batool kinga kayan ki kuwa zankadi gsky Dr shima yayi kokari ya narka dukiya sosai a lefen nan". Kallon mami takeyi cikin rashin fahimta, tace............. Kuyi hakuri yau ba editing saboda lokaci zai kure ban fara typing din da wuri ba , kuyi hakuri da kurakurai😁 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 73 & 74 Dagowa batool tayi cikin rashin fahimta ta kalli ummi tace "umminmu dan Allah ki dena min irin wannan wasan wlh dakin faɗa gabana faduwa yake yi,"dariya ummi tayi ganin dai kamar batool bill hakki bata yarda da abinda ta faɗa , tace "wlh dagaske kayanki ne ,kinsandai baki bina bashin rantsuwa ko". batool cikin dan fargaba ganin harda ranstuwa ummi tayi tace"kaya na to waya kawo kaya,wa zan aura?" ita farabanta ɗaya kar ya zama ɗaya daga cikin almajiran alhaji Mallam. Tunanin ta ne ya katse jin ummi na cewa"wanda kika tura mana ,shiya kawo kaya, ko su nawa Kikà ba dama da har kika kasa tantance wàñne daga cikin su ya kawo kaya,". Cikin son tà fashe da kuka tace,"ummi dan Allah ki gayamin wlh da gaske nakeyi bansan wa zan aura ba," ummi tace "ikon Allah sai kallo ,to bshir ne , ina nufin Dr bash". Wani zabura tayi ta mike tana dafe kirji, nan ta shiga maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun, daura hannu tayi akai a baiyane ta shiga furta "na shiga uku na ni fatima batula kun kasheni, shike nan tawa ta kare" can kuma sai hawaye shar kamar an bude famfo. Ummi dasu Amira kuwa mai zasuyi imba dariya ba , aiko ganin haka yasa batool kara sautin kukanta , kuka kuwa sosai bana wasa ba, harda sheshshka, tun su ummi na daukar abin wasa har lamarin ya fara basu tsoro. Tafe suke suna hirar su mai ɗaɗi irin ta tsàntsàr màsoya, fayyace mata irin dokon soyyayar ta da yayi ne tun baisan menene so ba, sai gashi kafin ya bayyana kanshi gareta , mai afkuwa ta afku, wato aka aura mata Aslam nan ya shiga baiyana mata halin daya shiga lokacin da zancen haɗa ta aure da Aslam ya riskeshi, har rashin làfiyan ɗaya kwanta na ciwon rashinta saida ya bata làbari, kafin kuma daga bisani allah ya kara bashi dama ta biyu akan ta,. Dariya ta shiga kwasa, cikin dariya tace "ashe ragwazozo ragon maza zan aura,wato harda kwanciya ciwo kayi , Ashe haka kake sona, da yawa" kallonta yayi shima yana murmushi yace"aini nafi ragwazozo ragon maza ragwanci indai akanki ne," cikin jin ɗaɗi tace" gaskiya naji dadi da Allah ya bani masoyi irin ka, kuma ina màka albishir da cewa zakayi alfahari dani ya kamal , domin zan zame maka farin cikin gidan duniyar , kai harma da kiyama insha Allah". Da haka suka karaso mobile, tun daga nesa Asmah ta hango Khadijah, matashiyar budurwace mai kimanin shekara goma sha bakwai a duniyà, doguwa ce sosai don tamafi Asmah tsawo, siririyace sosai don Asmah ta dan fita gwabi kadan , saidai akwai boobs da hips kamar dai Asmah, sanye take da riga da skirt na atamfa , am mata dinki daidai jikin ta , mayafinta da takalmi ta to mach ne da atamfar ta kafadarta rataye da wani kyakkyawan karamin jaka mai hannun chain , fuskarta kuwa bajau da make up , idanunta sanye da wani faskeken sun glasses pink colour daya kusa rufe rabin fuskarta, saidai ba karamin kyau ya mata ba dogon hancinta ya fito zirr, dashi, tsaye take ta maida hankalinta kan motacin dake wuce wa akan titi, hannun ta rike da hannun katon trolley dinta pink colour mai hotan Barbie a jiki, Khadijah kam yar wanka ce ta bugawa a jarida. Da sauri Asmah ta bude marfin motar ta fito da dan gudu gudu ta nufeta, itama sai lokacin ta lura da tahowar Asmah, aiko sake hannun trolley din tayi suka ba juna kyakkyawan runguma, kamal ma fitowa yayi daga motar shi bayan ya gyara parking , ganin sunki sake juna kuma hankalin mutanen wajen ya fara yowa Kansu , yasa kamal dake tsaye bayan su yin gyaran murya, sake juna sukayi kowacce fuskarta yalwace da farin ciki, zare tafkeken glass din dake fuskarta tayi, wow nace saboda ganin tsananin kama da nayi Wanda idan ba yan biyu ko yaya da kanwa uwa daya uba daya ba , ba'acika samun shi ba, fuskarta sak na Asmah harda manyan idanuwan su iri daya ne, banbancin su kawai yanayin jiki ne, da kuma tsayin da Khadijah tafi Asmah, Fuskar ta dauke da kyakkyawan murmushi ta sauke idanun ta cikin na kamal,wow ta furta a zuciyarta, cikin zare idanunta masu masifar kyau irin na Asmah tayi, hakan kuwa ba karamin kyau ya kara mata ba, cikin yanayin muryanta na masu surutu da saurin baki tace "laaaa ya kamal dama kaine, wlh banganeka ba sai yanzu, ina wuni mun sameku lafiya ya shirye shirye," cikin dan murmushi yace "ban amsawa , ai dama bazaki gane ni ba tunda bata ni kikeyi ba ta sis dinki kikeyi" hade hannayenta tayi tace"afwan ya kamal , wlh ya Asmah ne na tara kewarta da yawa shiyasa," dukansu dariya sukayi kafin kamal ya dauki trolley dinta ya saka a boot, suka shiga motar suka nufo gida, Asmah a gefen kamal , khady kuma a baya. A can gida kuwa batool abin nata ya soma wuce hankali , rarrashinta ummi ta shigayi ganin haka kuwa yasa ta fara wani mimmikewa tana wasu sambatu , ita aladole ta hau iska , sai cewa take , wlh bana sanso wlh karku aura min shi in ba haka ba zan kashe kaina, wayyo na shiga uku, abidai yayi kamari,zahra cike da tsoro ta fice da gudu don ta je ta sanar da su mummy abinda ke faruwa , don ita gaba ɗaya ta tsure, tunda suke cikin su ba wacce ta taba hawa iska sai yau da batool ta hau na karya. Su mummy suna zaune suna tattaaunawa ga akwatina nan a barbaje a gabansu ba'akai ga kwashewa ba, hango zahra sukayi a guje dankwali a hannua, da sauri mami ta tare ta , tana tambayar ta lafiya, nan ta rattaba musu abinda ke faruwa, da sauri suka dunguwa zuwa ɗakin , daidai batool na tsaka da tsula tsiyarta, mami ganin haka hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba mummy kam kallo daya ta mata tasan cewa na karya ne , kasancewar ta San yan matan nata farin Sani, tasan halin kowacce, tasan abinda kowaccen su zata iya aikatawa,. Ummi karasawa tayi ta tallabota ta shiga tofa mata ayatul kursiyu,mummy kam kwafa taja ta fice daga dakin dakinta ta nufa ta dauko wayar chargi mai kauri ta linka shi biyu, ta dawo ɗakin kallon ummi da mami tayi ta musu signal da Ido akan su kauce, kasancewar idanun batool a rufe yake yasa bata san wainar da ake toyawa ba,ummi ta bude baki zatayi magana mummy ta mata alamar shiiiii da hannun, kaucewa kuwa sukayi,. Batool jin su mami da suka rirriketa sun saketa yasa taci gaba da birgima tana bige bige, tana cewa "wlh bana sonsa wlh karku aura min shi inba haka ba zan kashe kaina ,wayyo Allah na" takai wannan ayar zata dauki wani taji saukar bulala , a jikin ta , ba shiri ta buɗe idanu, mummy kam ganin haka yasa taci gaba da lafta mata wayar charjin duk inda ta samu a jikin , tana cewa "zaku fita ko baza ku fita ba, kaga shedanu,nace zaku fita" batool da zafin duka ya fara ratsata, ta shiga cewa "munfita mummy munfita wlh munfita kiyi hakuri , Mummy batool ce batool ce," ganin mummy ba ta da niyyar kyaleta yasa ta mike ta saiti hanya ta fice da gudu daga dakin, mummy tace "ja'ira mu zaki kawowa shedanci" biyo bayanta tayi, aiko ta kara kwasa da gudu,. Daidai su Asmah da Khadijah sun shigo falon , faɗawa jikin Asmah tayi ta kamkameta , mummy kam ta na zuwa ta shiga neman inda zata ci gaba da zuga ma batool charji, aiko ba hanya dan duk inga mummy ta daga bulala ita kuma zata tura Asmah , ganin haka yasa mummy kyaleta don karta je ta zuga ma Asmah bataji ba ba ta ganiba,. Daidai nan ummi tazo ta janye batool d'in ta rungume ta , suka nufi dakin su, sai sauke ajiyar zuciya takeyi akai akai,. Kwantar da ita ummi tayi tana share mata hawaye, da haka baccin wahala ya kwasheta sai sauke ajiyar zuciya takeyi , har a cikin baccin,. Washe gari hajiya addawiyya mai gyaran amare ta dira a gidan kawar ummi ce, ta kware gurin gyaran jikin amare da kayan mata ingantattu, ciki da bai take gyara amare, katon shago gareta, bata bin mutane gida inba mutum ya gayurta ba, wannan ma saboda Ummi ne yasa ta amince ta zo, albarkacin kawance, daki aka bata guda a part din mummy, dakin dake kallon nasu batool,. Ba bata lokaci hajiya addawiyya shiga gudanar da abinda ya kawota gidan, Asmah zahra da Amira gyara suke amsa na musamman ciki da bai, batool kam cewa tayi ita bata son ko wani gyara ita baza tayi ba, rarrashin duniya ummi ta mata amma taki amincewa saida ta gaji ta hada ta mummy ta mata Jan I do sannan ta yarda anayi tana matsar kwalla ita fa bill haqqi bata so. Kwana biyu da zuwan addawiyya su Asmah suka fara daukan haske, kowa ya kalle su saiya kara tun ba'aje ko'in da gyaran ba kenan, ganin haka yasa Khadijah yin tsallen albarka ta dire tace itama sai an mata , dole ummi ta saka baki hajiya addawiyya ta aminc ta haɗa da ita......... Manage pls yau ban wuni a gida bane🙏 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiy ! ea Allah kajiqan iyayen mu} Page 75 & 76 ~ASLAM~ Yau kimanin kwana bakwai kenan yana fama da matsanancin ciwon kirji da zazzafan zazzabi, idan abin ya turnike shi ya kama wani irin tari, a wahalce yana kaki daya tofar jini ne haɗe da majina , abin tun yanayi kadan kadan, har ya rinjaye shi gashi baci ba sha , Dr bashir ne ke zuwa har gida yana kula da shi, yana matukar tausaya ma halin da Aslam yake ciki , yayi yayi suje asibiti a duba shi da kyau don dole wani abin sai Anje asibiti amma Aslam yaki, taurin kan Aslam da kafiyar shi ba karamin Mamaki yake bashi ba, idan ya cika damun shi da magiya akan ya yarda suje hospital, sai yace ya bar shi kawai ya mutu indai bazai samu Asmah ba baiga amfanin ci gaba da Rayuwa ba. Amir Dr bash ya samu da maganar ganin idan har yayi shiru Aslam ya mutu a wannan halin yana da Alhaki akai , Amir ma abin ya bige shi, hankalin shi bai tashi bama, saida yayi ido biyu da Aslam, wayyo Allah shikam kasa juriya yayi saida ya zubar da hawaye, yana tsugune a gaban shi rike da hannunshi yana hawaye , wani amai ne ya tasowa Aslam d'in kan kace kwabo ya shiga kwara shi,amai ne na jini harda guda guda yana gamawa ya shiga sauke wani irin numfashi kamar zai shiqe a take, kamkame hannun shi Amir yayi yana hawaye da majina, cikin muryar kuka yace"dan Allah dan uwana kar ka mutu ka barni , dan Allah ka tashi , akan Asmah ka saka kanka a ciki wannan halin, " wani murmushi ya saki Wanda da ka kalla kasan na tsananin azabar ciwo ne, ya kara kamkame hannun Amir dake cikin nashi , da'ker ya bude baki yace,"dan uwana Amir rayuwata ba ta da anfani idan har babu Asmah a tare dani, itace rayuwata idan har ban mallaketa ba na tabbata mutuwa zanyi ɗan uwa ka dena wahalar da kanka a kaina, ni nasan tawa ta kare, a duniya" Amir yace "kadena fadin haka ɗan uwa, ka amince akaika asibiti, nikuma na maka alkawarin samo maka Asmah, zata zama mallakin ka , da izinin ubangiji" juyowa yayi ya kalli Amir a wahalce yace"ta yaya zata zama mallaki na,? ta yaya bayan alhaji baba ya riga yayi mummunan furici akan mu, cewa fa yayi ko bayan ransa bai yarda na kara mallakar ta ba, bayan haka kuma ga ɗan uwa na Kamal na tabbata shima yana sonta kwatan kwacin yadda nake sonta,sannan kuma ita karan kanta Asmah bata sona ba ta so na ba ta so na" haka ya ta maimaitawa tun yana fadi dakyau har ya koma faɗi a rarrabe kafin, kuma hannun shi dake cikin na amir ya saki, idanun shi ya kakkafe numfashin shi ya dauke diff. Innalillahi wainnailaihi rajiun , Amir ya shiga furtawa hankali tashe , dan ya riga ya gama sadakarwa sun rasa Aslam, cikin fitar hayyaci ya mike ya fice daga gidan bai zame ko ina ba kuwa sai tsakiyar falon alhaji baba, . Alhaji baba na zaune a falon shi yana kallon labarai a tashar BBC , sai gani yayi Amir ya shigo mishi falo afujajan, idanun shi jajur, nil down yayi a gaban Alhaji baba dake zaune akan kujera 3 ya daura kanshi a cinyar alhaji baba, ya mika hannu ya rungume alhaji baba a hakan da suke , kafin ya fashe da wani irin kuka maiban tausayi,. Tun shigowar shi falon kallo daya alhaji baba yamai gabanshi yaji wani irin mugun faduwa gaba , take ya shigar maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun a zuciyrshi, har zuwa sanda ya rungume shi yana kuka abinda yake fadi kenan,bai yi kokarin dakatar dashi ba saida yayi kukan sa ma,ishi, ya shiga sauke ajiyar zuciya ,ganin haka yasa alhaji baba cewa "Amir menene meke faruwa" cikin dasasshiyar murya yace,"alhaji mun rasa shi , mun rasa shi saboda furucin ka , mun rasa shi saboda tsautsauran ayinka, dan uwana Aslam ya bar gidan duniya saboda , kaunar abinda yake halal a gare shi kaikuma ka haramta mai". Mummunan faduwa gaban Alhaji baba yayi, dajin furucin Amir, koda Aslam yake mara biyayya a gare shi, yana matukar kaunar shi, kaunar ce ma ta sa ya zabe shi a cikin zaratan matasan jikokin nashi har su uku ya bashi auren Asmah,. Kafin yakai ga furta wani kalma wayar Amir ta dauki ringing dubawa yayi ganin Dr bash ne yasa Amir daga kiran ya kara a kunne cikin sanyin jiki, daga can bangaren Dr bash yace"Amir bai mutu ba suma yayi ,yanzu haka muna asibiti, saika sanar a gida, ka kwantar da hankalin ka amir insha Allahu everything will be alright, yanzu dai ga doctors nan sun rufa a kanshi insha Allah za'a shawo kan matsalar, idan hakan bai yuwu ba dole akwai wani aikin da za,amai wanda muje da tabbacin za,a dace" ajiyar zuciya amir ya sauke a baiyane ,yayinda shi kuma Alhaji baba ya sauke nashi a boye. Gaskiya wannan lamarin ba karamin tayar mai da hankali yayi ba ,amma da yake namijin gaske ne dakewa yayi , dan kuwa Amir dake tsugune gaban ya kura mishi ido yana so yaga yanayin yadda zai karbi maganar, bai fahimci komai ba, bude bakin shi yayi cike da dattako yace"kul nasake jin wadannan kalmomin na fitowa daga bakin ka Amir kada bacin rai yasa ka tuhumeni da dalilin ciwon dan uwanka , Aslam shiya hallaka kanshi da kanshi , cikin girma da arziki na dauki Asma'u na bashi ita ba tare da ko sisin shi ba , amma daga karshe kaga abinda ya saka min dashi, sakin ta yayi fa ranar da aka kaita gidan shi a mastayin matar sa, wani kiyayyace tafi wanna , ina mai fada baisan ya bani hakuri ba , baisan yaba iyayenshi hakuri ba , don shi gani yakeyi bai aikata wani laifi ba, na barshi da zabin nasa ya aura , to da yake shi Allah kasan kamun sa , ba irin namu bane , cikin ruwan sanyi Allah ya bi mana hakkin walakantamu da yayi , nasan kanada lamarin komai daya faru tsananin shi da zabin nashi, ko wannan bai ishe shi ishara yasa ya dawo da baya ya nemi garafan iyayen shi ba, ina cikin haka kwasam na samu labarin wai yana son Asmah, wlh da farko ban yarda ba saboda nasan inda kunya bai isa ya budi bake yace yana son Asmah ba, koda ace kamal bai Ce yana son Asmah ta bazan yarda Aslam ya kara aurenta ba , sai kuma abin yazo cikin sauki kamalu ya nuna yana da muradi, Allah sarki rashin Sani yafi dare duhu, inda nasan haka zai kasance da kamal din zan aura mata tun. farko da duk abin bai zo da haka na, amma sorry to say ya makaro kaima shaida ne bana magana biyu , Aslam inhar son Asmah zai hallakashi saidai ya mutu indai nine Wanda zansa baki ya aure same ta " da sauri amir ya mika hannu ya daura akan bakin Alhaji baba, alamar yayi shiru karya karasa fadan abin da yake son fada, shi tsoran shi daya ma kar Alhaji baba ya rantse dan idan ya rantse abin zaifi rashin kyau. Kamal dake labe bakin kofa ja ya dingayi da baya da baya idanun shi sunyi jajur, tun shigowar Amir gidan akan idanun shi ne ganin yanayin da ya shigo kamar ba cikin hayyacinsa yake ba yasa yabi bayan sa , saidai jin kalmomin dake fitowa daga bakin Amir yasa ya ci wani wawan birki daga bakin kofa, yana gama sauraran komai ya juya da wani irin sauri ya bar gurin mortar shi ya fada ya figete da wani irin gudu mai ban tsoro, A can asibiti kam kusan awa shidda kwarara manyan likitoci suka kwashe akan Aslam kafin su shawo kan matsalar, a kwance yake kamar gawa fuskar shi sanye da na'uran jawo numfashi wato oxygen A kofar dakin da aka kwantar da Aslam kuwa , kamal, Amir, Abba, Daddy, mummy, ummi, mami, hajiya mama, bello, yam matan mummy, Khadijah, duk zaune suke wasu a tsatstsaye wasu na safa da marwa, kowa ka kalla cikin su fuskarta, ko fuskar shi dauke yake da matsanancin damuwa masu kuka nayi masu hawaye nayi masu addu'a nayi,. Baifi minti ashirin ba da wani babban likita ya tabbar musu da cewa wannan baccin da Aslam keyi , zai iya daukar kwana uku a haka yana bacci , bayan kwana uku zai iya farkawa a kowannen lokacin, idan ya farka ma ana saka ran Abu daya cikin uku ,either ya farka qlau, asamu nasara ,kokuma ya farka ciwon ya qaru har fiye da nada Wanda hakan zaija sai an fitar dashi kasar waje anmai aiki, shima din aikin cikin kila wa kala don zai iya yuwuwa kafin a fara aikin sai sun nemi a saka hannu akan yarjejeniyar , idan anyi aiki ,dayan biyu zai iya kasancewa, either Rayuwa ko mutuwa, na uku kuwa shine mai gaba daya wato zai iya yuwuwa daga wannan barcin ya zarce kushewa, zuciyar shi Ce ta tabu sakamokan saka mata tunanin wani Abu da kuma yake da tabbacin bazai samu ba , wannan dalilin ya haifar mai da wannan irin tabuwar zuciya mai hadarin gaske. Wanna jawabin na Dr James shiya kara hargitsa tunanin wadannan family na Alhaji baba, gashi gaba daya an hana su ganin Aslam din don dakin da yake kwance ba mai ikon shiga sai likita da nurse,. Idan kuna bukatar ganin majinyacin ku saidai a nuna muku shi ta CCTV dake dakin,. Haka suka karkare wuni a wurin sallah ne kadai ke tada su, abinci kam ranar sun manta da ana cinsa a duniya don ba Wanda yaji yunwa a cikin su , sai wurin karfe goman dare daddy ya tarkata su kowa ya wuce, ummi da mami da kamal da Amir ne suka tsaya suka kwana a asibin tare dashi. Washe gari ma haka suka wuni gwanin tausayi , kamal kam tuhumar kanshi yakeyi da cewa idan Aslam ya mutu dasa hannunshi a ciki domin tun farko daya hakura da Asmah lokacin daya gane Aslam na Santa da duk hakan bata faruba gaba daya ya dauki laifin komai ya daura ma kansa. Ranar daya cika kwana uku yana barci da misali goma na Safiyar asabar Wanda yayi daidai da sati daya ya rage daurin yan matan mummy, Aslam ya fara motsi alamar zai farka daga daga baccin daya tafi na kwana uku, ma'aikaciyar dake kula da bangaren CCTV na asibitin ne ta farga da farkawar shi ba shiri ta dannawa babban likita dake kula da case din Aslam waya Dr James ,. Cikin gaggawa ya nufi dakin da Aslam ke kwance oxygen ya cire mai da wasu na'urorin dake jikin shi. Ja yayi da baya ya hade hannaye ya kulle ido ya shiga jero addu'o'in su nayan choci , far far ya fara yi da idanun shi a hankali kafin daga bisani ya bude su tar, akan fuskar Dr James dake tsaye shi daya kwllin kwal a dakin, daidai shima ya gama jero addu'a ya bude ido,. Daga yanayin yadda yaga kwayar idanun shi kadai ya tabbatar da insha Allahu aiki yayi kyau, motsa baki Aslam ya shigayi alamar yana magana ne amma rashin karfin jiki yasa maganar bata fitar da karfi, ganin haka yasa Dr James ya matsa kusa da Aslam din ya tasa kunnen shi a wurin bakin shi yana sauraran me yake fada,. Alhaji baba daddy mummy nake son gani yanzu, sanin irin laruran shi daya shafi matsalar zuciya, gara a bashi dama ya fadi abinda yake son fadi kar ya kara saka shi a zuciya ya dawo musu da aiki baya,. Dr James fita yayi wurin tarin yan uwan majinyacin da suke matukar bashi tausayi, ganin yadda suka zuba mai idanu yuuuuu yasa tun daga nesa ya fara sakar musu murmushi alamar aiki yayi kyau, Abba ne ya fara tambayar sa yaya ya farka, don tun da aka sanar musu da ya motsa gaba daya suka shiga zulimin , a wani hali zai farka, wanne daga cikin ukun da Dr ya gaya musu ne,.............. Kuyi hakuri yauma dai abin ba yawa ga ba editing🙏 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu.} Page 77 & 78 Dr James ya kalli Abba yace,"ya farka, kuma we thanks God, ga dukkan alamu aiki yayi kyau, saidai kuma akwai wasu abubuwa da ya kamata a kiyaye, wanda kiyaye su shine zaiba patient din daman gama warware da wuri rashin kiyaye su kuwa zai kasance makamashi ne na fama ciwon har fiye da da,". Daidai lokacin Alhaji baba da Alhaji Mallam suka shigo cikin asibitin, dukkansu fuskokin a haɗe alamar kaman sun samu wata matasala a tsàkaninsu, Alhaji Mallam zuwànshi asibitin na uku kenen yayinda alhaji baba zuwan shi na farko kenan,. Kusan kowa yayi mamakin ganin Alhaji baba a asibitin, amma kuma ba Wanda keda ikon tambaya akan dalili , Abba ne ma a zuciyar shi yayi hasashen duk yadda akayi Alhaji Mallam ne ya sako shi a gaba zuwa asibitin, domin duk duniya babu Wanda ke iya saka Alhaji baba kuma ya hanashi ya hanu kamar Alhaji Mallam, haka shima Mallam din, Alhaji baba kadai ne kedai iya tursasa shi yin Abu, tun suna yara suka ba junan su wannan daman. Bayan gaggaisawa Dr James yaci gaba da cewa"kafin na faɗa muku abubuwan daya kamata ku kiyaye a game da patient dina a matsayinku na ƴan ruwan shi, a kwai wani roƙo guda ɗaya da nakeson na maku, nasan nan cikin ku akwai mahaifiya da mahaifin shi akwai ƴan ruwan mahaifansa akwai yayyi da kannen sa kai harma da kakanin sa ko",amsawa wasun su sukayi yayinda wasu suka gyda kai,. Dr James yaci gaba da cewa"dan Allah idan kunsan abinda patient dina yake so da har ya saka shi a rai ya haifar mai da wannan mummunan ciwo ku bashi ko kumu shi abinda yake so, idan kuka mai haka ina mai tabbatar muku zaku nemi ciwon nan ku rasa gaba ɗaya a jikin sa, domin shi ya haifar da cutan, kunga kenan shine original maganin da zai warkar da shi gaba ɗaya don wannan aikin ba yana nufin ya rabu da ciwon kwata kwata bane,yadai kwantar da ciwon ne kuma zai iya tashi akoda yaushe, so ina rokon ku pls and pls ku mai abinda ya keso" Abu na biyu patient ɗina yana da bukatar ganin, mummy da Daddy da kuma Alhaji baba, to idan suna nan zamu Baku dama ku shiga gare shi , amma banda hayaniya da yawa kuma banda fada mai maganganun da suka shafi ciwon shi, ma'ana abin da zai iya tayar mai da ciwon shi,. Abba yace ta "Dr mun gode amma inda hali ka Bari mu shiga gaba ɗayan mu domin dukkan mu nan muna bukatar ganin sa , ko dan hankalin mu ya kwanta" Dan shiru Dr yayi kafin yace"zaku iya shiga amma, dan Allah banda hayaniya , banda kuma maganar da zata tayar mai da hankali, amma ku bamu minti biyar mu canja mai daki tukunna, " juyawa Dr James yayi ya koma dakin kamar da minti uku sai gashi an fito da Aslam daga wannan dakin da mutane basa shiga zuwa na kusa dashi, Wanda anan ake ajiye duk Wanda ya fito daga wancen dakin, Har cikin dakin ya Dr James ya musu jagora, yana kwance akan gadon marasa lafiya na ɗakin, karin ruwa ɗaure a hannun shi, dukkansu da kallon tausayi suke binsa , ya rame ya jeme ya ƙara fari fat, idanun shi sun zurma sunyi zuru zuru, abin gwanin tausayi. Ware idanu yayi yana bin mutanen dakin gaba daya da kallo, akan Alhaji baba ya tsaida kallon shi, buɗe baki yayi a hankali , idanunshi sun cicciko da ruwan hawaye idanun shi cikin na Alhaji baba yace"na Sani ni mai laifi ne a gareka, laifi kuma mai girma, na tuna ranar da kake cemin, wata rana zanyi nadamar abinda na aikata ,ranar da nadamar baza ta amfaneni ba, yau ga ranar tazo, kuma as u say a lokacin da danamar bazata amfaneni ba,", haɗe Hanna yenshi yayi muryar shi ta fara rawa, idanun shi still akan alhaji baba ya cigaba da cewa "dan girman Allah Alhaji baba, dan darajer annabin rahama( S a w) ka yafemin abinda na aika ta a gareka ina rokon ka gafara, bazan iya tashi daga kan gadon ba balle na duƙa maka, nayi babban kuskure a rayuwa ta, kuma na gane kuskurena, na Sani wannan ciwon da nakeyi shine ajali na, inaji a jiki na bazan tashi daga kan gadon nan ba, don Allah kace ka yafe min ko na kwanta kabari na cikin salama," daidai lokacin wani kuka ya kufce mai , mai ban tausayi,. Tuni daki ya kacame da koke koke masu ruwan hawaye kuwa tuni ya wanke musu fuskoki , babu abinda ke tashi a ɗakin sai sheshshe ƙan kuka, mazan ne ma masu taurin zuciya , suma ko wanne ka kalla cikin su idanu yayi jajur kamar garwashi,. Idanun shi ya mayar kan Daddy da Mummy, cikin muryar shi dake fita a wahalce yaci gaba da cewa "iyaye na daddy mummy ,kuma kuyi hakuri akan duk laifin da na aikata muku, duk bacin ran dana sanyaku tun daga haihuwata har zuwa yau, ku dubi girman Allah ku yafe min, idan da fushin ku ko kannani a tare da ni bazan ji ɗaɗin kwanciyar kabari na ba", sauran mutane dakin yake bi da kallo yana kiran sunan kowannen su yana cewa su yafe shi shidai yana ji a jikin shi karshen shi yazo ,. Lokacin da idanun shi suka sauka akanta, idanunta sunyi jajur fuskarta kuwa ta cabe da majina da hawaye, sai sheshsheka takeyi tana ajiyar zuciya, saida ya kureta da kallo na kusan mintuna biyar, kafin ya buɗe baki idanunshi a kanta yace"ki dena kukan nan haka husnah ta , kukan ki yana taba min zuciya ,digar hawayen ki daidai yake da digar, ruwan dalma a zuciyata, bana so na koma ga mahaliccina na barki kina kuka, share min hawayenki kinji my husnah" abin kamar almara samun kanta tayi da bin umarnin sa wato ta shiga share hawayenta da hijabin ta, kallon shi ya mayar kan kamal, dake tsaye kusa da Daddy, yace"dan uwa kamal wasiyyar da zan bar maka itace, dan Allah ga amanar husnah ta nan a hannunka, zan mutu zan koma ga mahalicci na saboda rashinta, ka rike min amanarta karka bari hayawe su kwaranya daga idanunta , itace rayuwata farin cikina sanyin idaniyata,bayan raina ka kula min da ita ka wanzar da farin ciki a cikin duniyar ta, kowani bawa da kalan kaddaransa ni nawa kaddaran rayuwar, itace husnah, ina son husnah so mai tsanani Wanda na tabbata, soyyayar ta itace ajalina , nayi wasa da damata ta farko Dana samu akanta, gashi kuma har yanzu Allah bai bani dama ta biyu akanta ba, kai Allah yaba dama ta biyu akanta soda haka ka riƙe daman ka da kyau ɗan uwana". Girgiza kai kamal ya shiga yi idanun shi jajur cikin tsananin tashin hankali, kasa tsaya wa yayi, da sauri ya karasa gaban gadon ya rungume Aslam a jikinsa dukansu suka fashe da wani wani irin kuka mai ban tausayi, cikin muryar kuka kamal yake cewa,"A'a ya Aslam dan Allah ka dena fadin irin wadanan kalaman marasa ɗaɗin ji a kunnuwan mu, insha Allah baza ka mutu ba zaka rayu, zaka rayu tare da husnan ka , kuyi aure ku hayayyafan ma su Abba jikoki, indai har saboda Asmah ne ka shiga wannan halin wallahi na hakura da Asmah na bar maka ita duniya da lahira, dama matarka Ce nima karanbani nayi nake Neman shiga gonar da ba tawa ba nayi kiwo," kamkame shi Aslam yayi, a hankali ya shiga furta"A'a ɗan uwana ban cancanci haka ba kada ka sadaukar da farin cikin ka akaina,domin nima ban sadaukar da farin cikina akan na iyayen mu ba". kamal yace "A'a yaya Aslam kafini bukarta ta a halin yanzu na sadaukar maka da soyyaya ta domin rayuwar ka ya Aslam" Daga bayan su suka tsinci muryar Alhaji baba , yana cewa"ban amince ba, na riga na faɗa ko bayan raina ban amince Aslam ya auri Asma'u ba dan haka ina nan akan bakata , idan kai ka hakura ka janye ka bar masa ni ban janye ba,maganar yafiya kuma daya nema zan yafe masa amma da sharaɗi zan kuma yi masa zabi a karo na biyu, idan har ka amince da zabi na na yafe maka Aslam, Allah ya yafe mana baki daya, kuma kowa ma a nan ina son ya dubi girman Allan daya hada mu dashi ya yafe masa, amma maganar auren Asma'u kam babu shi, na fada na kara, zabina na biyu kuma za'a hada bikin tare da nasu kamalu ne, iya alfarman da zan iya maka kenan" Sakai yayi ya fice daga dakin abin shi ko jiran Alhaji Mallam da suka zo tare baiyi ba,. Shiru falon ya dauka kowa da irin tunanin da yake sakawa a zuciyar shi, Alhaji Mallam ne yayi gyaran murya, dukkansu suka maida hankalin su a kanshi , Cikin muryar shi ta dattijan da tsantsar ilimin addini ya ratsasu ya soma cewa"a gaskiya Aslam ka aikata babban kuskure a baya amma alhamdulillahi tunda har ka gane gaskiya kuma ka nemi yafiyar wadanda ka bata wa, saidai abinda zan fada maka shine kayi hakuri da Asma'u, tunda kaga haka watakila ita ba alkhairi bace a gare ka , maganar zabin da Alhaji baba yace zai maka ina mai baka shawara da ka karba da hannu bibbiyu , na tabbata zata zame maka farin ciki, kuma ta sakaka ka manta da cewa ka taba son Asmah a rayuwar ka," Aslam ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya yace"Alhaji a halin yanzu na Riga na cire rai da rayuwata, tunda har na rasa Asmah, domin kuwa itace rayuwata, amma duk da haka nayi farin ciki da zabin ku kuma na karba da hannu bibbiyu , kuma insha Allah zakuyi alfahari da ni a karo na biyu, nasan baza ku taba zabar min abinda zai cutar dani ba wancen karan ma , kuruciya da wauta ne ya sakani aikata aikin danasani," Alhaji baba dake laɓe a bakin kofa yana sauraran komai sauke ajiyar zuciya yayi sanna yasa kai ya wuce abinshi bai jira Mallam ba don fushi yake yi da shi ko mai ya hada su ohoo nan gaba zamuji. ~MALAYSIA~ Yau kimanin sati uku kenan da barowarta 9ja , tunda ta saka kafarta a cikin gidan bata kara lafiya ba, hoton yanayi da ta baro Aslam a ciki a police station ya ki fita daga kwakwalwarta, kullum Daren duniya kuka take kwana , ji takeyi da da hali da ta koma 9ja gurin mjinta ta rungume abinta da hannu bibbiyu, amma ina lokaci ya kure mata domin iyayenta babu abinda suka tsana sama da Aslam a duniya wayar ta ma tuni Dad ya amsa ya canja mata wani da wasu layukan, yanzu bata da buri daya wuce ta samu lambar beebalo ta kirata tasan beebalo mai kaunarta Ce zata iya mata duk abinda ta saka ta, mom ne ta turo kafar dakinta ta shigo hannun ta dauke da plat shake da kayan marmari yankakku, masu sanyi, zama tayi a bakin gadon da take ta mika hannun ta taba wuyanta, jikin na nan da zafin kau kamar ko yaushe , tunda ta dawo Malaysia bata kara lafiya ba ga kukan da ta aura tanayi kullum dare ,ga kuma rashin cin abinci,ko ruwa bata iya sha saita amayar fruit kadai take iya CI ta zauna lafiya shima idan taci da yawa sai sun dawo, ga kuma wani tsinkakken miyau dake addabarta, wannan lamari ya matukar daga hankalin iyayen zee, sunje asibiti ance fever ne,. Yau dai sukayi da wani babban likitan mata Dr habu sarki, kan cewa zaizo har gida ya dubata, kwararren likita ne da samun ganin shi ko Malaysia sai wane da wane, yasan aikinsa sosai ba karamin wuya Dad yasha ba kafin ya samu Dr habu sarki ya amsa gayyatar shi, saida ya zube makudan kudade bana wasa ba,. Tasar da ita mom tayi tana bata fruit din abaki tana sha kadan kadan , suna cikin haka dad ya shigo dakin , ya sanar dasu isowar Dr, mom tace saidai ya shigo nan ya dubata kaga jikin ba karfi baza ta iya sauka kasa ba , Haka ko akayi Dr ya shiga har dakin zee, babu kayan kirki a jikinta kayan bacci ne mai shara shara kanta babu dankwali amma iyayen ta ko a jikin su, dauke kai Dr yayi daga kallonta domin shidai musulmine dan 9ja kuma ba fasiki bane hasalima tare yake da iyalinsa suke zaune anan Malaysia, Tambayoyi ya shiga mata akan abinda ke damunta tana bashi amsa, yana rubutawa,akan yanayin da take ji ajikinta, bayan ya gama ya bukaci miyanta da fitsari ba bata lokaci aka bashi na'urorin daya zo dashi ya dauka ya shiga gwaje gwaje akan miyau da fistarinta , yana gamawa bayan ya samu amsar abinda yake nema ya kalli Dad yace"Alhaji abdussalam, daughter ka tana dauke da juna biyu ne karami, Wanda ke bata wahala ,duk wadannan abubuwan da takeji a jikinta saboda ciki ne laulayi takeyi" Cikin tsnananin tashin hankali da kiɗami dad da mom har suna hada baki wurin cewa ciki kuma Dr, Dr yace" yes tana da ciki tabbas" mom tace"Dr wani irin ciki kuma kadai sake gwadawa dakyau"nanta labarta mishi batun zubar da cikin da zee tayi, Dr yace "ana samun haka Ai alluran da wancen likitan ya mata bamai karfi bane kuma ba'ayi wankin ciki ba , to cikin na nan baiyi komai ba saidai yadan koma baya ,ma'ana ya zuba, watannin shi sun ragu,". Dad da mamaki ya gama kashe shi yace to Dr yanzu abinda nake so dakai"allura zaka mata Wanda zai wanke shegen cikin nan , domin ni bana bukatar hada zuri'a da wannan dan iskan yaron,da daughter ta haife wannan cikin gara taje ta yo cikin shege a waje ta haifa, yafi min alheri akan ta haifi cikin wannan tsinanan yaron Aslam". Zee tunda Dr ya ambaci cikin jikin ta nanan wani irin farin ciki ya lullubeta , ta shiga yiwa Allah godiya, amma jin kalaman dake fitowa daga bakin Dad yasa ta saurin dagowa ta kalle shi,. Dr mamakin dad ne ya cika shi kicin mamaki yace"ba cikin aure bane, ma'ana cikin sunnah" dad yace "eh" Dr yace "meyasa make son a zubar ku barshi mana , idan aka kara mata wani alluran zubar da ciki akan Wanda akayi da mahaifarta baida kwari zai iya samun matsala" dad yace" ba komai ayi ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba, na gwammace ta rasa mahaifar ma gaba daya da ta haifi wannan la'a nannen cikin" Dr yace "A'a fa Alhaji rabo yana kisa fa , tunda kaga cikin nan duk gwagwar mayar da yasha bai fita ba Allah ya kaddara rayayye ne idan ka matsa akan a fitar dashi akwai matsala" Dad cikin rufewar ido yace" kayi abinda na umarce ka Dr ko nawane zan biya ka," daga kafada Dr yayi alamar l don't care tunda na gaya maka gaskiya kaki ji ɗinan,. Wani ruwan allura ya zuka a sirinji, ya saita daidai adadin yawan da ake so na alluran ya nufo zee dashi........... .. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 79 & 80 Wani uban tsalle zee ta daka, nan take sai gata a bakin kofar toilet, kamar ba ita bace kwance shame shame ba lafiya, da kallon mamaki duk suka bita, Dad yace"meye haka daughter ki tsaya ya miki allura mana, ki rabu da wanna cikin da ke wahalar min dake" girgiza kai tayi tace"no Dad bana so kar a zubar inason abuna, zan haifeshi inason cikina" sanƙare wa Dad yayi yama kasa furta ko kalma ɗaya tsabagen mamakin, yace "daughter pls kar muyi haka dake, ki taimakeni a cire cikin nan kinfi kowa sanin yadda na tsani mahaifin cikin nan , bazan iya jurar haɗa zuri'a dashi ba," maƙe kafaɗa tayi kamar wata karamar yarinya yar two years, mom Ce ta kara da cewa"haba daughter kizo mana kinga munbar Dr a tsaye fa " still kin zuwa tayi haka suka shiga rarrashinta da tsoratar da ita akan maganar haihuwa da irin azabar da zata sha, amma ta.musu ƙememe, ta gwammace ta sha ko wacce irin azaba Ce indai baza ta mutu ba akan ta sha azabar rabuwa da Aslam, tasan idan Allah ya taimaketa ko ta dalilin wannan cikin na jikinta dole wata rana zata sake haɗuwa da Aslam ɗinta. Dr kam ganin sunata lallshinta ta ki yarda , ya ajiye sirinjin ya zare safar dake hannun shi, ya shiga haɗa kayan shi don yana da gurin zuwa da yawa. ~9ja~ Yau Aslam ya cika kwana uku da farkawa, jiki alhamdulillahi yana samun sauki sosai, dan zuwa yanzu yakan mike tsaye da kanshi ya shiga toilet, yana samun kulawa sosai gurin likitoci da kuma yan uwanshi,. A gida kuwa shirye shiryen biki ake tayi ba kama hannun yaro , tuni baƙi sun fara sauka daga garuruwa mabanbanta, ranar asabar da karfe goma ne za'ayi daurin aure a babban masallacin juma'a dake minna. Gayyata kam ko ta ina yinsa ake gaba ɗaya gari ya dauka da maganar wannan daurin aure na amare biyar ya gama baibaye garin minna da kewaye , hatta gidajen radio maganar da suke yi kenan a yan kwanakin na, haka gidan TV. NTA minna, duk wata kafar sada zumunta , saida maganar bikin nan ya leka,. Ba wani program za'ayi sosai ba, saboda matsalar rashin lafiyan Aslam badan haka kam , program din da suka shirya yi yakai bakwai, yanzu kam ummi ta shirya mother's day , sai walima, sai kumbo, sai kuma kidan kwarya da za'ayi ranar yinin biki. Amir kam baiji dadi ba da alhaji bana yace baza ayi dinner ba , sai cizon yasta yakeyi, dan dinner nan ba karamin shiri ya mishi ba, rashin kunyar daya tanada buhu buhu zaiyi a wurin dinner nan yawa ne dasu, dan duk cikin angwayen Amir ya fisu rawan kafa, hatta pre wedding pictures ba Wanda sukayi, sai shi baban rawan kai, har asibiti yaje kamar abin arziki, ya samu Aslam ya wanke tass, wai ciwon son shi bai tashi tashi ba saida ya bari bikin shi ya zo ya gama tsara bikin shi da irin rawar da zai sha a wurin dinner, gashi yanzu ya rusa mai shiri. Dariya Aslam ya shiga yi mai dan yafi kowa sanin yanda Amir yaci burin yin abubuwa sosai a bikin shi, suna haka Dr bash ya shigo ɗakin, haduwa sukayi suna tama Aslam tsiya, harda tuna mai lokacin da yake cewa su daina neman ƙana nan yara zasu jamai raini a wajen ƙannen shi, sai gashi shi saboda soyyayar ƙaramar yarinya ya kwanta ciwo harda cewa shiya sadaukar da rayuwa husnah Ce ajalin shi, nan Amir ya tashi yana kwada ma Dr bash abinda ya faruwa ranar da su Alhaji baba sukazo yana kwaikwayan muryan Aslam, dayake bash din baya wurin, aiko dai bashir yasha dariya harda rike ciki,. Amare sai shan gyara sukeyi ta ko'ina, idan kaga daya daga cikin su idan ba kamata farin Sani ba bazaka ganeta ba , sun daina fita ko compound din gida saida kwakkwaran dalili, batool kam har yanzu bata saduda ba kullum akazo yi musu wani abin da kuka take amincewa, wani ma saidai a kyale ta idan ta tubure. A bangaren Alhaji baba kuwa ya Riga ya gama magana da iyayen yarinyar da ya zabar ma Aslam a mastayin zabin shi ta biyu a gare shi, kuma alhamdulillahi sun bayar, da hannun bibbiyu, lokaci kawai ake jira,. Yau ta kama laraba kuma yaune mother's 's day da za'a gudanar a nan fillin gidan karfe hudu ne zuwa magrib, tunda sassafe yayata ta kaina anti bebi mai design da ummi tayi booking dinta tun ana saura sati uku biki ta sauka a gidan, ita da mukarraban ta , wato yaran aikinta, nan ta shiga zanawa amaren design ma gani na fada, lokacin da tazo yiwa batool, batool nata botsare botsare, ita bata so ganin haka anti bebi ta shiga hada kayanta , to dayake kunsan halin mutuniyar tawa badai saurin fushi ba , saida ummi ta jata gefe ta gaya mata matsalar batool d'in, sannan ta yadda ta lallabata suka gama, suna gamawa saiga Khadijah, wai itama anti bebi zata mata batason na yaran aikinta, aiko dai sisina tace batayi, ita amare kadai akace zata ma design, dayake itama yayan nawa kaifi daya ce inda kukasan Alhaji baba ya yayeta, saida aka dinga saka baki sannan ta dan zizara mata kadan baikai na amaren yawa ba, amma shima ya tsaru ba laifi, wata hajiya ce cikin kawayen mummy tace itama na anti bebi take so, tattara kayan ta tayi ko amsa bata ba hajiyar ba, ummi ne tace "anti bebi ki mata mana ko kadan ne" ta dago rannan a hade kamar zatayi kuka tace "gsky ummi baza ta samu ba, baban mami karfe uku yace na dawo idan na wuce lokacin yace bazai kara barina zuwa design gidan mutane ba, ga Rukayya nan ta iya sosai itama, ta mata,. Yaran aikinta Rukayya da yaya sukuma suka shiga yiwa sauran mutanen gidan , da bakin da kenan da duk Wanda ke bukata, kasancewar suna da sauri karfe uku sun gama ma kowa, nan aka shiga wanka domin shirin zuwa wajen mother's day, haka dai anti bebi ta bar gidan nan ba tare da tama hajiyan nan design ba saidai sunyi canjin lambar waya saboda wata rana.😅 Tun azahar masu decoration suka fara aikinsu kafin la'asar guri yayi shar ba mai cewa compound din gidan Alhaji baba ne,. Karfe uku da rabi masu makeup har mutum biyu suka diro gidan suka shiga shirya amare, Karfe biyar gida ya cika ya timbatsa da manyan hajiyoyi kawayen su ummi Dana mummy da mami, da yake ranar ta uwayen amare ne, aiko sun amsa gayyata ba karya. Ummi da mummy da mami anko suka sha cikin wani uban sun lace fari kar, mai tsadar gaske Wanda a kalla kudin shi yakai rabin million, banda awarware da yankunnaye da abun wuyan gold da kowaccen su ta zuba wuya da hannu, masha Allah su ummi sun sha kyau iya kyau , kana zuwa gurin ba sai ka tambaya ba zaka gane asalin uwayen amare,. Lokacin da amare suka fito tsit wurin yayi , wasu kuwa miƙewa tsaye sukayi , zabar kiɗima , sunga haduwa iya haduwa, Can rumfar dake kusa da na amare na hango yan dama ta biyu fan's , kowaccen su ta kure wanka , ta sako na kasan akwati, an hakince akan kujera ana daddana waya,wasun su kuma na fira kasakasa, suwaibaaliyu Ce ta kalli anty naimcy dake gefenta hakimce tace "yaudai karya zai kare zamuyi ido hudu da Asman data rikirkita mana tunanin Aslam din mu" bata kai aya ba, amare suka fito, kakus Hadiza jafar dake zaune gaba gaba, Sai kallon su mummy takeyi tana jero masha a zuciya, ta fara ganin su zabura yayi ta mike dafe da girji, tana zare ido, ta gidan dan darmay kuwa suman zaune tayi, nikam ina zaune kusa da kawata Fulani gal, muna sirri kasa kasa, dan bamuson kowa yaji mu, Kiy kura dake zaune kusa dani ganin ban ma San wainar da ake toyawa ba yasa ta kai min tsunguli a gefen fuska, zafin tsungulin ya ratsani na dago da niyyar kai mata dundu, dan nidai gaskiya ban bari ta kwana, ganin inda take nuna min yasa tuni zafin tsungulin ya gudu, kawata ma ganin na sake baki da hanci ina kallo yasa itama ta daga kai ta kai idonta inda nake kallo, Oum habeeba wayar dake hannunta tana dannawa ne ya subuce ya fadi ba tare da ta Sani ba, Allah ya somu bai fashe ba, daba na karantawa dama ta biyu yau, Fateema kam wutan kanta ne ya dauke dif, zainab kam da yake ta maka bakin glass irin no respect din nan yasa ban gane halin da take ciki ba, daughter Mr salis kam baki da hanci da kunne duka ta bude tana kallon su dashi, fatima bala gazara , salima abdullahi maman lubna, duk suna zaune, suna ba ido abinci,kai wlh dama ta biyu fan's muna da yawa in nace zanta lissafo sunan ku da daydaya sai mu cinye page dinnan bamu gama ba , masu comment wacce bata ji sunan ta ba ma hade a next page, Sanye suke cikin wani dankareren lace babban nasu mummy, saidai su nasu black color ne kasancewar su farare sol ga kuma gyaran da fatar su ta dauka, karkuso kuga yanda ya musu kyau , an nada musu goggoro ash colour, takalman kafar su masu tsini suma ash hannayen suna rike da wani dan gudul din pos shima ash ,wuya da hannayensu kuwa gold ne kirar dubai, fuskar su kuwa tasha heavy makeup ko wacce na zuba kamshi, kyau kam kowacce ka kalla, sai kayi tunanin tafi su kyau duka idan kuma ka kalli wata itama haka,. Wurin da aka tanada dan zaman amare , suka zauna cake dankarere mai hawa biyar na daga gefe, haka aka shiga gudanar da program, cikin wayewar kai , mummy ummi da mami kowacce ta fito ta yi godiya ga Allah ta kum nuna irin farin cikin da take ciki ayau haka wasu daga cikin dangi, dakuma wasu kawayen su mummy,. Anci mai kyau ansha mai kyau, yan dama ta biyu fan's ranar kakansu ta yanke saka, sai cin kaji ake ana kari, kakus kam tunda ta danki dangwalelen kaza, ta tasa a gaba bata karama kowa magana ba, har aka tashi, garin da tace zata bari ma tuni ta manta da batun,. Gab da magriba aka tashi a wajen taron,. Washe garin ma haka akasha kumbo shima a gida akayi, gida ya cika ya tumbaza har fiye da jiya , dan yan dama ta biyu fan's, harda wadanda basu zo jiya ba yau sunzo dan sunce ba'za a barsu a baya ba, kwanda suje su kashe kwarkwatan idanu,. Ranar juma'a kuma akayi walima, a labour kutigi, karfe hudu zuwa shidda, manyan malamai ne mata, masu ji da ilimin addini Dana zamanj suka bada lecture a wurin waliman nan, gaba daya jikin amaren nan yayi sanyi kalau karma batool taji labari, Asmah da zahra kam harda kukan su shabe shabe da majina,. Karfe shidda daidai aka tashi, can na hango yan dama ta biyu fan's ana shararowa da kafa zuwa bakin titi, dan dai labour kutigi opposite government hause yake ba kowani lokaci ake samun keke napep ba gashi daga gurin zuwa titi da dan nisa ko rabi basuyi ba aka kira magariba , tuni kafa ya dauke a hanyan, su kakus ido ya raina fata, gashi kowacce tayi lodin sabeniyasa kaya guda dan wasu ma irinsu ta gidan dan darmay so bibbiyu suka karba, ana cikin haka Allah ya turo wani mai hilux,nan muka shiga dagamai hannu , yana tsayawa mukaga Ashe bello ne, haka dai ya taimake mu ya lodo mu a bayan hilux din nan zuwa babban titi, daga nan wasun su masauki suka nufa dan kafa yai tsami,nidai da yake inason na dauko mana rahotan , sa kalle da za'ayi bayan magrib , dole na tari napep zuwa gidan alhaji baba nida Kiy kura da Fateema da Oum habeeba,. Ana idar da sallah aka shiga sa lalle, hajiya mama da kanta ta saka amare a lallai, zo kuga kuka gun yan matan mummy, inda kukasan an riga an daura aure ne, abin tausayi suna tunanin rabuwa da juna , to ai dole tun yarinta tare ake kwana ake tashi, mummy kam kasa tsayawa tayi a wurin a hankali ta silale ɗakin ta , taje ta sha kukanta na kewan rabuwa da yan matan ta, ummi kan dariya ta dinga musu tana tsokanar su kamar yadda ta saba karshe ma wayarta ta dauka ta shiga ri musu video,. WASHE GARI Akace rana bata karya, saidai uwar diya taji kunya, tunda sassafe, gida ya dauki harama baki ta gabas ta yamma ta kudu da arewa, kafin karfe tara gida ya cika makil, da jama'a na masaka tsinke,. Karfe goma daidai babban masallacin juma'an minna ya cika makil da jama'a, idan kaga mutane zaka dauka sallar idi akeyi motoci kuwa tun daga complex har mobile parking ne , yan sanda ke faman kula da gyara fakin motoci, bosso road ranar kasheta akayi saboda cinkoson jama'a indai zakabi hanyar saidai ka zagaya ta bay pass,. Saida duk wani mai muhimmanci ya hallara sarakuna daga garuruwa mabanbanta, haka manyan malamai daga fadin duniya , ga governor da sauran kusoshin gwamnati,. Haka aka shiga gabatar da daurin aure bi da bi, har saida aka daura na amare biyar rerasss,akan sadaki mafi karanci da albarka, masha Allah angwaye idan ka gansu bakin nan har kunne, karma amir yaji labari sai daukan selfi yakeyi da friend dinsa, Alhamdulillahi aure ya dauru saidai muyi fatan Allah ya bada zaman lafiya,. Har zuwa wannan lokacin Aslam na kwance a gadon asibiti, amma har nan labari ya iske shi na daurin auren, shidai har zuciyar baya jin zai so wannan zabin na alhaji baba kamar yadda yake son Asman shi amma zai yi iya kokari shi ya danne son da yake ma Asmah tunda yanzu ta zama mallakin wanin shi zaiyi hakuri da koma wacece aka daura mai aure da ita, kawai don dai yama iyayen shi biyayya, zai ta rokon Allah ya saka mishi son ta a zuciyar shi ya kuma cire mishi son Asmah, tunda ba rabon shi bace, yayi imani ya dauki kaddara zaici gaba da jinyar zuciyar shi , har ta warke daga wannan mummunan ciwo da take dauke dashi na son maso wani , amma a zuciyar shi ya kudiri aniyar ana sallamar shi a asibiti zaibar Nigeria dan bazai iya tsayawa yana ji yana gani wani ya angwance da Asmah bashi ba, bazai iya jura ba, ƙasa mai tsarki zai tafi, yaje yata rokon Allah a gaban dakinshi mai tsarki har sai yaji sanyi a zuciyar shi zai dawo 9ja,. Acan gida kam yinin biki ake yi cikin girma da arziki ko ina manyan mata ne ta ko'ina sai watayawa akeyi, karfe uku daidai jumai mai kidan kwarya ta dasa a tsakar gida, nan kuma aka shiga caskalewa , dama ta biyu fan's kam an samu abinda ake so tunda suka shiga fili kallo ya kama Kansu, nan suka shiga kwangwajewa, jama'a sai yan gulmace gulmace ake yi kasa kasa , su waye wadannan kuma da suka zake haka sunata rawa, basu suka bar tsakiyar fili ba saida jumai ta nade kayanta,. Duk wannan shagalin da akeyi Asmah nacen kwance kudundune cikin bargo wani zazzafan zazzabi ne ya lullubeta, tun bayan da aka gama daurin aure alhaji Mallam ya kirata ya damka mata sadakin ta a hannu ya mata nasiha mai ratsa jiki, da kuka shabe shabe ta baro falon Alhaji baba tunda ta fada kan gadonta ta kwanta, zazzafan zazzabi ya lullubeta, gashi Neman duniya tama Khadijah a cikin gidan bata ba labarinta , ko mai kama da ita bata gani ba duk Wanda ta tambaya saidai ace mata bari a kira mata ita, saidai tashi shiru a haka har bayan magrib inda motocin daukar amare suka layu a kofar gidan alhaji baba,.............. DAGA YAU INSHA ALLAH DA RANA KO DA YAMMA ZAN DINGA POSTING🙏 dan allah ruwan comment dan mu samu mu karkare da wuri mu shiga sabon buk (MIJIN NOVEL, zan aura) daga jin sunan kunsan zai nishaɗan tar daku fiye da dama ta biyu kudai kawai ku bani haɗin kai comment dinku kawai nake bukata, ba sai yan dama ta biyu fans kaɗai ba. NAGODE SOSAI MASU MIN COMMENT HAR KULLUM DAKU KADAI NAKE TAFIYATA😍 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanna book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 81 & 82 Tun daga farkon layin gidan alhaji baba har karshen sa motoci ne laye iya ganin mai hange, wanka amare sukayi mami da kanta ta shirya su shirin barin gida, sai sharar kwalla sukeyi, Asmah kam da yake bata da lafiya wata kanwar mahaifiyar ta da suke uwa daya uba daya , da suka zo biki, ita ta mata wanka ta shirya ta har zuwa lokacin jikin da zafi kau. Bayan sun idar da sallan magriba, ummi har falon alhaji baba ta musu rakiya, acan suka samu daddy da Abba da sauran yan uwa da abokan arziki, zubewa su kayi a tsakiyar falon kowacce kanta a kasa tana hawaye, alhaji baba ya fara buɗe taro da addu'a, kafin ya daura da nasiha mai ratsa jiki take jikin su ya kara sanyi, bakajin sautin komai a falon bayan amon muryar alhaji baba sai shehsshekan kukan amare, yana gamawa, Alhaji Mallam ya ɗauka daga nan sauran abokanan su kowa saida yasa musu albarka, Daddy da Abba ma sun musu nasiha sosai. Daga nan wurin hajiya mama aka kaisu, itama ba'a barta a baya ba, haka aka ta bi dasu, suna sallaman dangi, mummy kam ɗakinta ta shige ta ɓame, koda ummi ta tura ƙofar dakinta taji shi a rufe a waya ta kirata wai tana inane amare zasuyi sallama da ita, jin haka dama abinda take dugarma ke nan, sai cewa tayi bata cikin gidan su tafi kawai Allah ya bada sa'a. Mutane ƴan zakiyar amare tuni kowacce ta samu mota ta kame, ƴan dama ta biyu fans haka suka lodu cikin motoci wasu kan cinyan wasu, wasu ma har a boot, nima allah ne ya soni har zan shiga boot dan ban samu guri ba ,kiy kurs ta yafito ni na zauna a cinyarta, su kakus dai ana boot ido ya raina fata, tare za'ayi tafiyar' ma'ana zasu raka junan su, za'a fara kai batool daga nan akai Asmah, sai Amira, sai kuma a zarce bidda inda za'a kai zahra,. Kowacce motar da aka kawo na musamman domin ta aka nufa don sakata saidai hakan bai yuwu ba , dan zahra da batool kam kankame juna sukeyi , suna wani irin kuka mai ban tausayi ganin haka yasa dole aka saka su a guri ɗaya,. Gidan batool aka fara zuwa dake nan M,I sauka akayi aka shiga da ita gidan sama ne dankarere Wanda misalta muku shi bata lokaci ne, sabo dal haka ma kayan cikin gidan sababbi ne, ga kuma sabuwar amarya, da sabon ango,Abin zad dadi,. Bayan dangin Dr bash waɗanda da suke nan dan kar bar amarya sun karbe ta, abincin tarbar amarya mai rai da lafiya aka gabatar musu kasancewar suna sauri yasa suka saka a mota idan an koma gida aci,. Tashi aka shigayi ana fitowa domin tafiya, nan fa kallo ya koma sama dan amare dai kamkame juna sukayi su hudu suna sharban kuka, da'ker aka samu aka banbare su daga jikin juna,. Kasancewar basu da wasu kawaye sosai yasa wasu kawayenta sabbi ne ma dan a school ta haɗu da su su biyu suka tsaya da ita zuwa sanda ango zai shigo suma su san nayi a bar ango da amaryarsa,. Ganin abinda sukayi a gidan zahra yasa lokacin da suka isa gidan Asmah, ba'a bari Amira da zahra sun fito daga mota ba, a nan aka barsu aka shiga aka mata rakiya,. Itama dankarern gida ne mai girman gaske don yayi Na batool biyu, saidai shi part uku ne a gidan dan haka aka lalubi nata aka sakata, itama sabbin kawayenta ne suka tsaya da ita,. Haka aka garzaya gidan Amir dake albishir, daga nan kuma waɗanda zasu koma gida suka koma waɗanda zasuyi rakiya zuwa bidda kuma suka dauki hanya, saidai muyi fatan Allah ya kaisu lafiya,. nikam dai bani cikin yan zuwa bidda dan allah allah nakeyi naje gidan batool naga ya zasu kwashe da dr bash, harna kama hanya na ni kaɗai zan tafi, na dawo cikin sanɗa na yafito ummu muhammad naser, na mata kuskus a kunne, itama saɗaɗowa tayi ta biyo ni, ganin haka yasa ameera dake ankare da duk wani motsin mu yasa ta biyo mu a baya da gudu ba yacce muka iya dole muka tafi da ita. Bari mu fara da mutuniyar taku😜 ~BATOOL~ Bayan wucewar su ummi kukanta taci gaba da rerawa, kawayenta sai tsiya suke mata, ko kulasu batayi ba, wata matashiyar mata ne ta shigo cikin dangin ango waɗanda suka amshi amarya da basu kai ga wucewa ba zama tayi a bakin gadon da batool ke zaune can kurya sai sheshshekan kuka takeyi, kasa kasa, hannayenta ta miƙa ta kamo na batool ta rike cikin nata tana dan murzawa a hankali, jin haka yasa batool ta ɗago kai a hankali ta sauke idanunta akan matar matashiya ce don duka duka baza ta haura talatin ba, tsananin kamar ta da Dr bashir yasa batool ta raya a ranta duk yadda akayi kanwar shi ce, murmushi mai kayatarwa ta sakar mata, a hankali cikin sassayan muryarta tace"haba amaryar mu wannan kuka haka sai kace sato ki mukayi, oya ki daina kuka haka bana son yaya yazo ya same ki haka bazai ji ɗaɗi ba, kinsan yadda yake sonki bazai so ganin hawaye a idanunki ba, nasan kina kukan rabuwa da family ɗinki ne ko," gyada mata kai batool tayi, ido jajur ansha kuka, taci gaba da cewa "to kidai na kuka jinki, insha Allah mu zamu zame miki sabon family masu kaunar ki zakiji dadin zama da mu ƙilama fiyye da naki familin" dagowa ta sakeyi ta kalleta jin tace wai fiye da familin ta, murmushi ta mata tace "eh mana nan gaba zaki tabbatar da abinda nake gaya miki, kedai kawai ki kula mana da babban yaya,kuma sai kinyi hakuri kin zama jaruma,kinsan yaya na tuzurune sai a hankali" daga bakin kofa suka ji wata murya shigen na wannan tana cewa "yayi kyau zubaida, kuma kamar a kunnen yaya kika faɗa , ba tuzuru ba, shuka kikai a idan makwarwa, zuwa zañyi nace kinje kin samu amaryar shi kina ta tsoratata harda cewa idan bata bika a hankali ba sai ka dinke ta kamar kwarya" kwalalo ido tayi tare da cewa " dan Allah yaya amrat ki rufa min asiri yadda yake dokin amaryàn nan, wlh kina faɗa yarda zaiyi kijamin bakin jini ɗan alert din da nake ji karshen wata kisa wannan watan nan naji wayam," Dariya yaya amrat tàkwashe dashi, tace"to cigaba da tsoratar mai da mata, Allah zan saka ya saka ki a black list wannan month din, oya ki taso mu wuce anzo daukar mu". Kallan batool tayi tace "amaryan mu zan wuce anzo daukar mu,amma zan dawo very soon, ni sunana ashmat, sister na kuma amrat dukan mu kannen Dr ne amrat ke binshi a haihuwa sannan ni, dukkan mu matan aure ne amma akwai sauran kannen mu mata su uku, zaki sansu very soon, autar mu ma kila kuzo mate da juna, dan Allah a kula mana da yayan mu muna sonshi sosai shi kadai ne namiji a cikin mu,"sake hannun batool tayi saida ta kai bakin kofa kusa da yaya amrat tace "amaryan mu a buɗe ma yayana ƙafa da kyau anjima fah" dariya kawayen batool suka kwashe dashi, yaya amrat kam kunnen ashmat ta kama ta jata, suka fice tana cewa"kedai bakin nan naki har yanzu bazai tsarkaka ba ko?". Batool manya wata uwar harara tà raka su dashi,tare da jan wani dogon tsaki tace"A'a ba ƙafa zan buɗe mishi ba baki zan bude mishi, iskancin banza kaii" cikin dariya daya daga cikin kawayen ta tace"bakin ma inta kama ki bude, budewan zakiyi" aiko dai nan batool ta hayayyako mata da masifa kamar zata cinye ta ɗanye, haushin su ashmat data kunsa duk ta sauke shi akan ta, suko kasancewar sunsan halin mutuniyar yasa basu kulata ta ba saima dariya da suke mata saida tayi mai Isar ta tayi shiru. Ita yanzu duk Wanda ya shafi Dr bash haushin sa takeji, balle kuma Wanda zaice tamai biyayya, ji take kamar ta shake mutum, shi karan kanshi jiran shi take yi dan ta kudiri aniyar antaya mai bahon rashin mutunci a ka , har sai ya gaji da halin ta ya maida ta gidan su, tunda dai ita bata Ce tana sonshiba,. (Hmmmmm nikam dai nace batool abi a hankali yanzu dai gidanku daya da Dr Allah yasa ya iya jure rashin M dinki, kada shima ya miki kalan nashi rashin M d'in). Su ashmat na wucewa, motocin abokanan ango suka fara dira a compound d'in gidan, falo kawayen batool suka fito, su biyar ne harda angon, samari yan kwalisa, sunsha wankan shadda sai tashin kamshi sukeyi , bayan yan gaishe gaishe da addu'o'i zaman lafiya, akayi siyan baki , aka dan taba wasa tsakanin abokan ango da kawayen amarya, nan sukace tunda sun siya baki a fito musu da amarya su gaisa, Dr bash yace "wata amaryan za'a kira muku ku gaisa, abeg ku tashi na rakaku jooo, koni banji muryar ta ba tukun saiku gandan gandan daku"dariya suka saka suna cemai yayi duk abinda yaga dama zasu rama ne,daya daga cikin su yace dan allah dr abi mana ƙanwa a hankali fa. Rakiya ya musu suka tafi tare da kawayen batool d'in zasu sauke sua gidajen su Batool kam tun jin shigowar su kawayenta suka fita mikewa ta yi ta shiga toilet tayi wankan ta ta fito ta ɗauki kayan bacci Riga da wando ta saka ta faɗa gado abinta ta kwanta, acewar ta ita ba amarya bace tunda auren dole aka mata da mijin ba sonshi takeyi ba,. Dr bash na dawowa ya buɗe bayan boot ya fito da tsarabar amarya da abokan shi suka siyo, ya nufi dakin amaryar a falo ya ajiye ledar shi ya nufi dakinta da addu'o'i fal bakin shi. Tsaya wa yayi a bakin bedroom din da yake da tabbacin tana cikin sallama ya shiga yi a hankali, shiru ba amsa , har yayi so uku ganin haka yasa a hankali ya murda handle din kofar ya shiga gaban shi na faduwa dan baisan mai zai tarar ba, dakin duhu ba haske wayar shi ya laluba ya haska ya kunna wuta mai haske, a kan gadon ya hangota kwance ta gudun dune da bargo baka ganin komai nata sai fuska, "ikon Allah" Dr bash ya furta a zuciyar shi, ya saba kallo ko a film amare lullubi suke sha ango yazo ya bude musu fuska, amma shi tashi amaryar ta fita daban da sauran amare,. Duk sallaman da yake ta kwadawa tana jinshi ta share,saidai ta amsa a zuciyar ta,jin ya kunna wuta yasa ta bude idanunta da sauri, sai cikin na bash kallon kallo aka shiga yi, ba komai ya fado mata a rai ba sai zanan da mummy ta mata ranar da ta hau iskan karya, take wani haushin shi ya kara turnike ta, Daga kwancen da take tace"lafiya Mallam?" bai tanka ba sai karaso wa da yayi bakin gadon zai zauna ta wani zabura ta karasa can karshen gado tana antoyo mai harara, shi dariya ma ta bashi amma ya dake baiyi ba, zaman yayi abinshi, yana kallonta, shiru ya ratsa na wasu mintuna shi yana kallonta ita kuma tana hararan shi, can dai yace "ke baki iya gaida mutane bane, ko haka aka ce miki ana ma miji," cikin tsiwarta tace "mijin wa Allah ya kiyaye nidai kai ba miji na bane ehee , tun wuri ka nemi matarka dan ni ba sanka nake ba auren dole akayi min" bash yace"to nima sonki nake aka gaya miki , mace sai muni haka , bari na gaya miki abinda baki sani ba, ina zaman zamana Alhaji baba ya kirani, da nazo yace, wai ga batula nan dan Allah na taimaka na aure ta tayi kwantai duk , yan uwanta an kawo kudin aurensu amma ita bata da mashin shini na taimaka, ganin bazan iyamai musu ba yasa na karba, badan inaso ba don ni inada budurwata Fateema, da muke soyyaya ita zan aura, amma tunda an riga an manna min ke dole haka zamu hakura mu zauna da juna mu hayayyafa, kila albarkacin ƴaƴan naji na dan fara sonki kaɗan" batool da tunda ya fara magana bakin ta ke bude tana binshi da kallon mamaki jin abinda yace wai su hayayyafa bata San sanda tace "kutumelesi, kaida wa zaka hayayyafa, to wlh ahir dinka karma ka taɓa tunanin ko yatsar hannunna zaka samu tabawa balle jikina, balle har ta kaimu da haihuwa, jikina rabon masoyina ne , ba wani ƙato ba, " tunda ta fara magana dan bakin ta yake kallo yadda take masifa tana wani tsuke shi ba karamin burge shi yake yiba,aiyana irin taushin da lips ɗinta zasuyi in ana kissing ɗinsu yakeyi, zuciyar shi ce ta bashi shawara da cewa yaudai gaka ga wannan ɗan bakin da ke hanaka sukuni, kadan tsotsa mana ka rage zafi, kallon ta yayi yace" tunda dai baki da masoyin yanzu jikin naki ya zama raboda ai tunda na biya sadaki bari ma ki gani" mika hannu yayi zai riko ta, aiko ta daka tsalle ta dira daga gadon zatayi waje da gudu, fisgota yayi ta faɗa jikin shi baiyi wata wata ba ya hade bakin shi da nata ya shiga kissing dinta cikin wani irin salo mai birkita tunanin ɗiya mace,. Wohohoo Dr bash an samu abinda aka dade ana mafarkin samu, gaba daya wutar kanshi daukewa yayi, yadda yake tunanin zakin saliva din ta abin ya wuce haka, yadda yake tunanin laushin lips dinta abin ya wuce haka, uwa uba yadda yaji taushi da tsantsin fatar ta ga wani mahaukacin kamshi dake fitowa daga jikinta yana shiga hancin shi, ai sai ya birkice mata gaba daya,. Ita kam batool da farko tsoro ne ya kamata , tunda take ba'a taba kissing dinta ba sai yau, tanajin kiss a baki amma bata taba sanin haka yake ba sai yau, da farko kokawar kwatar kanta ta shigayi amma da yake ba rikon wasa ya mata ba yasa ta kasa kwacewa , da tafiya tayi tafiya lukusss tayi a jikin shi tana amsan sakon da yake aika mata, (maganin hajiya addawiyya na aiki),. Bashir kam gaba daya ya fita daga control, shida yayi niyar kiss sai gashi yana neman wuce gona da iri, tuni ya fara kai hannunshi sassan jikin ta, rigar jikin ya shiga kokarin zarewa , jin haka yasa hankalinta dawowa jikinta kuka ta fashe dashi tana ci gaba da kokawar kwatan kanta, zuwa time din jikin shi gaba daya ba karfi, hakan yasa tayi nasaran kwatar kanta a dis time, toilet ta nufa ta rufo kofar da karfi ta jingina bayanta a jikin kofar tana maida nunfashi,. Dr bash kam kifa wa yayi ya kwanta akan bed din ya runtse ido yana sauke ajiyar zuciya, hannunshi ya mika ya kama ya kama AK47 dinshi jin yadda take harbin iska,. Saida ya kwashe kusan thirty minutes a haka, kafi ya yunkura ya mike ya fice daga dakin gaba daya,. Madam batool kam saida ta gama maida numfashi, hankalinta ya gama dawowa jikinta , taji yadda lips dinta ke mata wani irin raɗaɗi, gaban mirror dake tsaye a toilet din ta karasa gani tayi lips dinta yayi jajur, gashi ya dan kumbura, kuka ta fashe dashi tana shafa lips dinta, ruwan dumi ta hada tayi wanka tanayi tana ma bash Allah ya isa, data gama ta fito ta canja wasu kayan bacci ta hau gadon ta ta kwanta tana mastar kwallah,. Bash kam wani bedroom din ya shiga , tube shaddar jikin shi daya gama cukurkudewa yayi ya fada toilet, wankan janaba yayi sannan ya daura dana sabulu, yana fitowa shiryawa yayi cikin kayan bacci dogaye, ya lallaba ya koma ɗakin batool, dan shidai bazai yarda da kana wani ɗaki matar ka na wani ba,gara su saba kwana tare tun yanzu,. Yana shiga ya sameta can karshen gadon kudun dune cikin bargo, duk da cikin duhu ne hakan bai hanata antaya mai harara ba, ganin ya kwanta a daya side din yasa tayi wuf ta dauki pillows ta jera a tsakanin su, asuba ta gari , amarya da ango............. nikam nida yan rakiyana ummu muhammad naser da ameera, ganin sun kwanta yasa muka lallaba muka hito bakin titi dare ya tsala aiko daƙer muka samu napep, gulma yayi ɗaɗi😜 Toh mutanena gobe da wani gidan zamu fara ne, gidan Aslam ko gidan kamal ko Amir, kokuma bidda zamuje? Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 83 & 84 ~AMIRA~ Sai gurin sha daya su Amir ya suka gidan zuwa lokacin tuni kawayenta sun kama gabansu kasancewar unguwan da aka kaita unguwace mai shegen nisa, suna ganin goma babu Wanda yazo yasa kowacce ta zargawa karenta igiya, dan dai yanzu ba'a yayin kwana gidan amare balle ma an mata jeranta gidanta komai tsab,. Itama dai ganin goma da rabi , tun tana zaune tana hamma bata San sanda bacci ya kwashe ta ba, koda motocin abokan ango sukayi parking a harabar gidan bataji ba, baccinta yayi nisa,. Zama sukayi a main parlour, Amir kuma ya haura sama dan dubota, tazo su gaisa da friend's ɗinsa, dan shidai ɗan bagu ne, yana so suga kalar zabin sa, tunda ba'ayi dinner balle su ganta a can iya kacin su da ita a hoto,to yafiso suga zahiri, su san shima ya kace raini. Yana bada baya ɗaya daga cikin friend dinsa ya kalli na kusa dashi yace sagir "fatan dai ka bashi" , sagir yayi murmushin mugunta yace "bar dan iska ai biyu ma na bashi, kuma saida na tabbatar yasha" ɗayan ne yace yana zaro ido "kai sagir har biyu, be mai yawa ba kuwa, karfa kasa ya farke yar mutane " sagir yace "ai alkawari na daukar ma kaina idan Amir ya tashi aure sai namai ramuwar gayya ka manta iskancin da yamin kenan ni babyna ba yar mutane bace, shima yaji inda ɗad'i, " dayan da sai yanzu ya tsoma baki yace"ai sagir kamin daidai dan ma bani bane da uku zan antaya ma hege, nima ka manta haka yamin, yasa ni aikata aika aika, " sagir yace "OK harda kaima yama ko , to ku rabu da dan bura uba, shima yau zaiji a jikin shi". (Allah sarki Amira na tausaya miki wollah😪) Daidai nan Amir ya karaso wurin su yana zame hulla zama yayi yace"guys baby tayi bacci" Anas yace " hada dai bacci tun yanzu, aikuwa gara ta tashi yau ba ranar barci bane" Ahmad ne yace " ba wani baccin da tayi kawai wayau ne irin nasu na amare, ta kulle ido kamar tana bacci" sagir yace "aiko dai komin wayan amarya sai ango yasha manta ko ba haka ba friends"dariyar shakiyanci suka kwashe da shi dukkan su. Haka suka zauna suka taba cafta irin tasu ta abokai kafin, daga karshe ya musu rakiya ya kulle gidan ya dawo ciki, gaba daya jin jikinshi yakeyi wani iri don pill's d'in da sagir ya bashi d'azu a cikin fura tuni ya fara aiki daurewa kawai yakeyi,. Dakin da Amira ke kwance ya koma, babban rigar jikin shi ya cire ya linke ya ajiye,zama yayi daf da ita yana kallo ta, tunani yake ta ina zai fara tashin ta, dan yanayin da yakeji a jikin shi ya fara bashi tsoro, ga hajiya babba sai haniniya take mai, tana azalzalar shi, cikin haka wayar shi ta dauki ringing,. Karar ringing din wayar ya ratsara har cikin dodon kunnenta, da sauri ta ware idanunta , sai cikin nashi , murmushi ya sakar mata, itako saurin lalubar mayafin ta tayi ta rufe fuskarta irin da amare keyi ɗinnan. Dariya ya kwashe dashi yace"kin makaro yarinya Ai na riga na gama gani ba wani yangar da zaki min" shiru tayi bata tanka shi ba, karasawa gabanta yayi ya yaye mayafin, yace, tashi na tayaki yin alwala muyi nafila mu mika godiya mu ga Allah , daya mallaka mana junan mu a yau, cikin ɗan jinkunya ta kalle shi, tana sakar mishi murmushin ta mai kayatarwa, shagala yayi da kallonta, gani yayi ta kara wani bala'in kyau dan kwana biyu nan da bai ganta, dan tunda aka shiga satin biki, shida ita sai gani daga nesa,. Ji yayi kamar ya saka ta a jikin shi ya rungume ta amma ya daure, har toilet ya rakata ya barta tayi alwala, shima wani bedroom yaje yayi alwala ya dawo yana dawowa tana fitowa pray mat ya shimfiɗa musu, suka gabatar da sallah nafila raka'a biyu, bayan sun idar ya kama goshinta ya shiga jero addu'o'i, bayan sun gama mikar da ita yayi ya ya zare mata hijab din jikinta, sai sissinne kai takeyi, taki yarda su hada ido shiko sai kallon fuskarta yake yi yana sakin murmushi,. Cak taji ya raba kafafunta da kasa, ya mata irin daukar da ake ma jinjirai, zaro ido tayi tana tana kallon fuskar shi gabanta na faduwa bai dire ko ina ba sai a kan kujera 3 sitter dake karamin parlour, kitchen ya nufa ya dauko plate ya juye gasasshiyar kazar da ya da shigo dashi sai kamshi yake bazawa jan gashi, cup ya dauka ya juye fresh milk mai sanyi a ciki, komawa yayi kusa da Amira dake zaune kamar tsatus tana binshi da kallo ya zauna dago plate ɗin kazar yayi yace baby "haaaaa😮" girgiza kai tayi alamar A'a shima ya girgiza mata alamar Eh, murmushi ta saki kafin a hankali ta buɗe ɗan bakin ta ya saka mata. nikam da nake laɓe wani busassan miyau na haɗiye mukut, wollah raina ya biya tana tauna ina mata haɗiya😋 naji kamar na miƙa hannu na dauki yanka ɗaya amma ba dama, dan idan na kuskure Amir ya ganni ina musu laɓe hmmmm😬 Haka ya dinga ciyar da ita yana bata fresh milk a baki , saida ya tabbatar ta ƙoshi ya ƙyale ta, ganin yana tattara plate da sauran kazar zai mayar kitchen yasa ta bude baki a hankali tace"yaya" juyowa yayi ya kalleta tare da ɗage mata gira tace tana nuna plate ɗin hannun shi"bakaci ba" yace "na ci nawa tun ɗazu kina bacci" yadai faɗa ne, kawai dan hankalinta ya kwanta, amma badan yacin ba dan baya jin zai iya cin komai a halin yanzu inba😛. Dawowa yayi ya kara daukarta zuwa bedroom, tana ta mutsu mutsu ya sauketa ta taka yaki, tuni dankwalinta ya zame a falon dogon sumar kanta daya sha gyara ya bayyana,bai tsaya bi ta kan dankwalin ba yaci gaba da tafiya. Bakin bed ya ajiyeta ya ya buɗe wardrobe ya Ciro wani kayan bacci red colour masu kyau da sulbi, hannu ya mika zai zuge mata zip, kaya yake son ya cire mata ya sanya mata na bacci, hannunshi ta rike tana girgiza kai, kallon ta yayi ganin ta rike mai hannu yace "baby ya haka, gara ki saba danni indai ina gida komai ni zan dinga miki da kaina" kin sakewa tayi ganin zata bata mai lokaci yasa ya saka dayan hannu ya shiga yi mata cakulkuli, ba shiri ta sake mai hannu tana kwasan dariya,. Duk abinda amir keyi gaba daya dauriya kawai yakeyi yana yi yana matse kafa, so yake ya bita a hankali dan karta tsorata da shi,. Ganin ta sake shi tana dariya yasa ya shammaceta ya zuge zip din rigar ya zare shi ta gaba, take fararen boos dinta suka bayyana suna sanye cikin beziya fari kar, ji yayi gaba daya kanshi ya kwance, binta yakeyi da wani irin kallon sha'awa, ita kam rintse idanunta tayi ganin yayi nasarar zare mata riga,. Kasa jurewa yayi wani irin wawan ruguma ya kai mata ya hadeta da jikin shi ya matse da karfi kamar zai hade su wuri daya, su zama mutum guda, yar ƙara ta saki cikin shagwaba tace "wash yayana zafi"dan taji zafin matsar daya mata, rikicewa amir yayi lokacin da kamshin shu'umar humuran da hajiya addawiyya ta masu aiki dashi ya ziyarci hancinshi,take ya shiga kissing dinta ta ko ina yana sauke wani irin numfashi,. Gaba daya jikinta ya saki jin irin yadda yake bin lungu da sakon jikinta da tsotso, (hajiya addawiyya👍) kwantar da ita yayi ya mike ya rage kayan jikin shi,ya rage da boxer, gaban boxern kuwa kamar ya tokar rake yankan yankan hamsin. Kashe wutar dakin yayi ya nufi kan bed d'in ya janyo amarya sa,. Tabdijan wannan irin cafta haka ba dani ba alkur'an, bazan tsaya ayi kisa a gabana,Amira Allah yajiƙan ki, nidai na tafi da safe nazo dubiya. ~ZAHRA~ Yan kai amarya sun isa lafiya, kuma alhamdulillahi sun samu tarba na musamman daga yan uwan Barr, zahra na rungume jikin ummi sai kuka takeyi gwanin tausayi har zazzabin dole ya kamata, dayake da dare suka iso yasa ba daman komawa ranan dole su kwana, gidan ta daya da uwar gidan Barr saidai part din kowa dabam haka shima mai gidan part dinshi daban wacce keda girki taje part d'in miji,. Uwargida maryama itama yau tayi taronta, kawayenta ta tara manyan mata suka zauna sai yada habaici sukeyi suna zagin dangin amarya dana ango,. Bayan an natsa ummi tace ma wata kanwar mummy data zo biki , ya kamata su kai zahra gurin uwar gidan shi, tunda gobe da sassafe zasu dauki hanyar minna. Haka ko akayi ummi da anty Jamila suka saka zahra a tsakiya suka nufi part din maryama, falon damkam yake da kawayenta ana zaune sai ciye ciye da shaye shaye suke suna yada habaici, sun kunna speaker sun kure volume wakar anty uwar gida na tashi. Su ummi na sawo kai wakar, Kusa kidan antynmu uwargida ♪ Anty muna gaishe ki uwargida♪ An buga an barki uwargida♪ Allah gatanki. uwargida♪ Kin darasu da maki. uwargida♪ Mijin na kaunarki. uwargida♪ Kuma yay miki maki uwargida♪ Anty dole su barki uwargida♪ Labule asirin daki. uwargida♪ Yama su sallama anty Jamila ta rike baki tare da cewa tohfa, haka dai suka daure suka karasa bakin kofar suka yi sallama, wata kanwar maryama ne Mara kunya tazo ta bude , tana ganin su taja wani dogon tsaki kamar dogon bakinta zai tsinke, sannan ta buga musu harara daga sama har kasa, ta juya ta koma ciki, sun kusa kwashe 10 minutes a tsaye anty Jamila sai buga tsaki takeyi tana ƙari, ummi kam sai hakuri take bata, candai ta gaza jurewa ta kama hannu zahra dana ummi tace, "wlh bazai yuwu ba kuzo mu wuce sai kace wasu yan iska zasu barmu a tsaye, shiru shiru fa ba tsoro bane" cikin haka yarinyar ta kara bude kofar ta jefe su da wani wulakantaccen kallo kafin tace "ku shigo" ta juya abinta,. Anty Jamila tace "umminsu baza mu shiga ba mu wuce kawai " ummi tace "ba'a yi haka ba anty jamy bari mu shigan dai tunda muke nema". Badan ran anty Jamila taso ba ta bi ummi suka shiga, hamshakiya maryama tana hakimce tana zuba mulki taci kwalliya da wata uwar lessi kamar itace amaryar, fuskar nan ta dau makeup bajau, duk kawayenta sun ciccika kujerun falon ba wani sauran guri da su ummi zasu zauna, kuma ba wacce tayi niyar basu guri dan su zauna d'in,kuma ba wacce tace musu ƙala, wannan lamari ya matukar kona ran anty jamy , ji take kamar ta tanka, amma tasan in ta tanka rigima ne zai barke , karshe azo ace dangin amarya sunbi uwar gida har daki sun zageta,. Daga tsayen da suke ummi tace "bayin Allah sannun ku", shiru ba wacce ta tanka saima bisu da kallon banza da suke yi, ummi ta sake cewa "uwar gidan Barr muke nema mun kawo mata amarya ne" daga bayan su sukaji wata hamshakiyar murya tace "gani nan turmin tsakar gida nake sha luguden mahassada, uwar gida saurautar gida nice ta fari nicen uwar yayan gida, duk wata karamar yar iskar data auran min miji, wlh nayi mata alkawarin cin burauba ta, da kafarta zata fita tabar min gidana da takalma a hannu dan uban ubanta, gidana daga ni sai mijin sai yayana babu wata karamar yar iskan data isa ramin kura sai yayanta," yan koranta ne suka dauki sowa tare da rangada bude suka shiga jero mata kirari Ummi tuni ranta ya gama baci da wannan irin cin mutumcin da maryama ta musu, amma matsayin ta na babba kuma mai hankali da ilimi yasa ta danne zuciyar ta, anty Jamila kam kasa hakura tayi ta zabga shewa tare da cewa"ai wallahi maryam kike kowa,baki cika babban ƙwaruwa ba tunda har kikayi saken da mijiki, ya kalli wata mace a waje har ya sota ya kuma bada sadaki dan ya mallaketa ba, inda kin cika Babbar yar iska kamata yayi ki hana ayi auren bawai bayan anyi kizo kina cikawa mutane kunne da kurarin banza ba, kuma fatima zahra kainuwace dashen Allah ta shigo gidan nan kenan ita da barrister mutu ka raba,saidai ke ki fita ki bata fili tunda ke jakace wawiya mara hankali jahila kawai". Wai wai wai jar ubancen, nan yan koran maryama sukayo caaa akan anty jamy harda masu shan gabanta kamar zasu daketa, ita kuma mandiyan na zaune kafa daya kan daya, duk da zagin da anty Jamila ta mata ba karamin dukan zuciyar ta yayi ba. Ganin haka yasa ummi sauri damkar hannayensu ita da zahra suka bar part d'in cikin sauri,. Suna shiga daki zahra ta fada kan gadonta ta fashe da wani irin marayan kuka, aiko anty jamy da ranta ke bace ta hau kanta da masifa tana cewa "ki zauna dai da wannan raguwar zuciyar taki ,wlh inbaki tashi tsaye , bakar wuya zakisha a hannun wannan yar iskan kishiyar taki, shiyasa batula ke burgeni kuma nake ɗasawa da ita , wlh ita ta biyo gida sak, kin zauna kina zubar ma kishiya hawaye sai kace ba jinin mu ba, tir da wannan raguwar zuciya taki," ganin abin na Neman yin yawa yasa ummi ta shiga kakkare Zahra tana ba anty jamy hakuri. Ummi saida ta raba dare tana ma zahra nasiha , da koya mata dabarun zama da kishiya, take taji zuciyar ta yadan karfafa, ga kuma hargagin anty jamy shima ya taimaka. A haka suka kwana ran kowa a dagule washe gari kuwa ko haske gari bai gama yi ba aka kawo musu motocin da zai maida su minna, dan su suka bukaci hakan. Haka zahra ta wuni ita kadai taci kuka ta gode Allah, an kawota an barta, ita kadai , hmmmm aure kenan babu inda baya kai mace. Sai dangin Barr dake dan zuwa baki da suka zo biki daga nisa suna son su koma, shine suke ta zuwa ganin dakin amarya. Hankalin zahra ya kwanta ganin yadda dangi miji ke sonta suna haba haba da ita, sai yada maganganu sukeyi akan maryama , da alama kam ita da dangin miji basa ga maciji, ita ba ruwanta murmushi kawai take binsu dashi. Abincinta daga can family hause dinsu Barr aketa kawo mata safe rana dare, abinci mai rai da motsi, ta dan caccakura ta barshi kasancewar bata cikin yanayi mai dadi. Sai wurin karfe tara Barr ya shigo gidan zuwa lokacin ba kowa dan yan ganin daki tun magriba kafarsu ta dauke. Cike da jin kunyar shi ta tsuguna har kasa tana gaishe shi, yaji daɗin hakan kuwa tunda Dama su nufawa tambarin su kenan ladabi, shiyasa take son ta fara koya tun da zafi zafi donta saba tun wuri, kar nan gaba tazo ta samu matsalar zama da dangin shi. Hannunta ya kama ya mikar da ita tsaye ya zaunar da ita kan cinyar shi, kunya kamar tace kasa ya tsage ta shige haka take ji, murmushi yayi yace "Babyn Adam bana son irin wannan gaisuwar tsakanina dake indai ba cikin mutane muke ba", girgiza kai tayi alamar to, yasake cewa "kinci abinci" nan ma dakai ta amsa mai, murmushi yayi ganin alamar duk a tsorace take dashi,. Hannunta ya rike suka nufi bedroom, dinta alwala yace taje tayi a toilet ba musu kuwa tayi bayan ta fito shima ya shiga yayi, sallah yajasu raka'a biyu bayan sun idar ya kama goshinta yayi addu'o'i, mikewa yayi ya dauko mata kayan bacci a wardrobe ya bata yace ta sanya yana zuwa fita yayi daga dakin zuwa nashi dakin dan yayi shirin kwanciya shima,. Saida ta gama saƙe saƙen tasa ne ko kar tasa itafa gaba daya a tsorace tace, ƙudunbale tayi ta saka rigar dan kar yace daga zuwanta har ta fara mai rashin biyayya tana sakawa ta haye gado ta kudundune cikin bargo,. Saida ya gama abinda zaiyi ya kulle ko ina dama ya riga ya sallami maryama tsiya tsiya ma suka rabu , badan yakai zuciya nesa ba daya shashara mata mari da daddaren nan ma,. Ganinta gudundune a bargo yasa shi sakin miskilin murmushi, ya fahimci gaba daya a tsorace take dashi, shikam ba sauri yakeyi ba zai bita a hankali har sai ta saki jiki dashi tukunna zai kusanceta, yuwar ta dai ta zama mallakin shi , hankalin shi ya kwanta, shi ba yaro bane yasan yadda zai lallaba abarshi har ita da kanta ta mika wuya,. Hawa gadon yayi bayan ya kashe wutar dakin, jawota yayi jikin shi ya rungumeta, gabanta ne ya shiga faduwa da karfi har yana jin sautin shi kasancewar manner suke da juna, peck ya kai mata a goshi tare da cewa "ki kwantar min da hankalinki babyn Adam babu abinda zan miki bayan hakan, bacci kawai zamuyi mu huce gajiyan biki", gyada mai kai tayi kafin ta shiga sauke ajiyar zuciya, hankalinta ya kwanta, take bacci mai daɗin gaske ya kwashe ta, Ba dole ba hajiya zahra anji ɗumin jikin miji.......... ~ASLAM ~ Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏..💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanna book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 85 & 86 ~ASLAM~ Zuwa yanzu jikin Aslam yayi sauki sosai har idan ba mutum ya Sani ba bazai taba yarda yayi wani ciwo makamancin wannan ba, ramace dai kawai yayi sai kuma hasken daya kara, hakan ko ba karamin kyau ya karamai ba,. Washe garin ranar da aka miƙa amare dakin su ranar lahadi kenan, a ranar aka bashi sallama daga asibiti, babu kowa a tare dashi a lokacin sai Abba, bayan Abba ya gama biyan duk abinda ya kamata a biya, wani cleaner ya hahhaɗa musu kayan su zuwa motar Abba. Sallama Aslam yayi da Dr James nan ya kara bashir shawarwari game da yadda zai kara kula da kanshi dan gujewa sake faɗawa irin halin da ya faɗa, sosai yama Dr James godiya , Abba na tayashi, sannan suka kamo hanya. Lokacin da suka hau kan babban titi Abba ya juyo ya kalli Aslam, yace "nasan kanada labarin daurin aure ko" shiru Aslam yayi kafin daga bisani ya amsa da "eh Abba" Abba yace "to masha Allah , amarya tana gidan ka, tun jiya" da sauri ya juyo ya kalli Abba jin abinda yake cewa, a zuciyar shi yana cewa, wannan wani irin azarbabi ne ba sai a bari a sallame ni daga asibitin ba tukun a kawota Tunanin shi ne ya katse lokacin da yaji muryar Abba yana jehomai tambayar "gidan ka zan kaika ko family hause" a zuciyar shi yace gida na gurin uwar wa, a fili kuwa yace "A'a Abba a dai kaini can gida na ƙara hutawa , na gaida alhaji da gajiyar biki, inyaso zuwa dare sai na je can din" Abba yace "to ba matsala hakan ma yayi kyau", kafin ya dauki hanyar family hause. Gidan har yanzu akwai sauran baki na nisa dukda wasu sun dauki hanya yau da sassafe , yayinda wasu sai gobe zasu wuce. Abba na parking ya bude motar ya fito, Abba ma fitowa yayi ya kalli Aslam d'in yace kaje tsohon part d'in ku kayi wanka ka kimtsa zan sanar ma maminku ka dawo ta hado ma abinci ,idan kaci saika shiga ka gaggaisa da mutane, ka huta zuwa dare sai ka tafi gidan ka kamar yadda kace, Aslam ya amsa da to Abba. Tsohon part dinsu ya nufa kamar yadda Abba ya umarce shi, fallon ba kowa, saidai akwai datti ba'a kai ga gyara wa ba, haurawa upstairs yayi ya nufi tsohon dakin shi, dakin nanan tsab kamar yadda ya bar shi saidai dan kura da yayi, take ranar da yan sanda suka zo har kofar dakin suka tafi dashi ya fado mai arai, inbai manta ba rabonshi da dakin tun ranar , kai gidan ma baki daya, yana wannan sake saken gaban shi ya yanke yayi wani mummunan faduwa sakamokon tunowa da yayi da zee, amma tunawa da abinda ta aikata mai yasa take yaji wani haushin ta ya turnikeshi, fatali yayi da lamarinta ya fada toilet ya hada ruwan zafi yayi wanka, a ɗarare yake wankan kasancewar bayin ya kwana biyu ba'ayi amfani dashi ba duk yayi kura abinka da komai fari, ji yake da zai iya daya fara wanke toilet d'in tukun to amma jikinshi ba karfi bayajin zai iya yin hakan. Fitowa yayi daure da towel a kugunshi , wani karami kuma a hannunshi yana goge suman kanshi dashi, gaban mirror ya tsaya yayi shafe shafe shi, wardrobe ya bude ya dauki ƙananan kaya ya saka, take ya fito fess dashi, ana ciwo ayi muni shi Aslam wani kyau da haske ya karayi, masha Allah. Daga bakin kofa yaji ana sallama , basai ya tambaya ba ya gane muryar mami, amsa sallaman yayi, ya nufi kofar ya bude, amsan tray hannunta yayi tare da cewa "sannu da kokari mamina" marmushi mami ta sakar mishi tace "masha Allah my son jiki yayi kyau Allah mungode maka" baice komai ba sai murmushi da yake ta binta dashi. Karasawa tayi har cikin dakin ta dauki kofi ta hada mishi tea ta kuma zuba mai abinci, a plate ta tura mai gaban shi, daukan kofin tea din yayi tare da cewa "nagode mami na". Zama dashi mami tayi har ya kammala cin abincin, yadan ci sosai kuwa ba laifi, bayan ya gama ta ballo mai magungunan shi ta bashi yasha,. Kallon mami yayi yace "mamina bamu gaisa ba, ina wuni ya gida ya akaji da jama'a kuma ya gajiyan biki" mami yace "my son alhamdulillahi anyi taro lafiya an gama lafiya amare kowacce na dakin ta , saidai mu biku da addu'a Allah ya Baku zaman lafiya," da "amin thumma amin" Aslam ya amsa, mami ta sake cewa "yanzu tunda kaci abinci kayi wanka kasha magani, ba kwanciya zakayi ba , ka tashi ya je part din mummy ka gaishe ta ka mata bangajiya daga nan kuma kaje ka gaida alhaji baba da hajiya, dama sauran dangi da kenan" Aslam ya amsa ta "to mami". Tare suka fito daga part din mami ta nufi nata shi kuma ya nufi na mummy. A Palo ya tarad da mutane musamman yan uwan mummy na nesa da suka zazzo, binsu yayi daya bayan daya ya gaida su, amsawa suka shiga yi cikin so da kauna da kulawa, suna kuma yimai murnan auren da yayi,. Mummy bata falon don haka bayan sun gama gaisawa ya mike ya nufi dakinta, sallama yayi a bakin kofar, daga cikin mummy ta amsa mai shiga yayi , zaune ya sameta bakin gado handset dinta rike a hannunta, gama wayarta kenan da ummi tace mata suna hanya sun kusa isowa, zama yayi a gabanta sanan ya shiga gaisheta da mata gaisuwar gajiyan biki, amsa mai tayi tana binshi da kallo, sannan itama ta tambayeshi shi jikin shi, ya amsa mata da cewa da sauki. Shiru ne ya ratsa dakin na wasu sakanni, kafin mummy ta katse shirun da cewa"Aslam" dagowa yayi ya kalleta don mawuyacin abune mummy ta kira sunan shi, CI gaba tayi da cewa "a baya ka aikata babban kuskure, Wanda yasa mukayi fushi mai tsanani da kai, to amma yanzu alhamdulillahi komai ya wuce, ka nemi afuwar wadanda ka batawa, kuma kowa ya yafe, a yanda lamarin ya sauya lokaci daya ma, ba karamin abin mamaki bane, amma ba'a mamaki da ikon Allah, abinda nake so na gaya maka shine, Aslam ga zabi nan alhaji ya kuma maka a karo na biyu," duk da yasan da maganar amma jinta daga bakin mahaifiyar shi saida gaban shi ya yanke ya fadi kamar yanzu ne ake gaya mai batun, ji yayi kamar yace ma mummy wacece ita, amma ba hali don babu yar haka a tsakanin su. Ci gaba mummy tayi da cewa " Allah ne ya mallaka maka ita ba wayon ka ko dabaran ka bane, muma iyayenka ba iyawar mu bane,haka ma Alhaji, dan Allah Aslam ka riketa amana marainiyace gaba da baya, mune gatan ta Kaine gatan ta Allah ne gatanta,kar naji kar na gani,ka kula da hakkokinta da Allah ya daura maka, ka wanzar da farin ciki a duniyar ta, kada ka kuskura ka bayi ruwan hawaye su kwaranya daga idaniyarta, ka wanzar da murmushi akan fuskarta, ka maye mata gurbin iyayenta data rasa, kamar yadda muka maye mata a lokacin da take a gaban mu" Aslam kam duk abin da mummy ke fada shiga kawai sukeyi ta right su fita ta left, jinta kawai yakeyi, shi a duniya akwai macen da ta isa ya mata duk wadanan abubuwan da mummy ta lissafo inba husnah ba, ya daiji zai sauke mata hakkokinta da Allah ya daura mai,amma batun farin ciki , murmushi waye waye saidai tayi hakuri dashi. Tunanin shi ya katse jin mummy na cewa "shi kenan, nidai iya abinda zan iya gaya maka kenan jeka Allah ya maka albarka kaida yan uwanka ,Allah kuma ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyaba" addu'o'i mummy ba karamin faranta mai rai sukayi ba , take ya shiga amsawa da amin thumma amin , kafin daga bisani ya shiga kwasan godiya. Daga part d'in mummy part din Alhaji baba yaje, suna tare da hajiya mama, Aslam yayi matukar mamakin ganin yau Alhaji baba ya sakar mai fuska ya amsa gaisuwar shi cikin kulawa, idan ba karya idanunshi suka mai ba kamar harda murmushi ma yaga yadan mai. Gaishe su ya shigayi cike da ladabi da girmamawa, bayan sun amsa ya musu ban gajiyar biki, kafin ya mike ya koma kusa da hajiya mama ya zauna ya kalleta yace "madam ya akayi ne," tace "gawa taki rami idonka kenan, wai lallai Asma'u ta cire tuta, wanwar takai maza kasa tana daga zaune mike da kafafu, to Allah dai ya baku zaman lafiya" ga mamakin sa ji yayi Alhaji baba yace "wannan ne maza, ragwazozo dai ragwan maza," hajiya mama tayi dariya tare da cewa "aikai ya gado" hararan wasa ya watsa mata, cikin dariya tace" bar wani harare harare, ko kuma yanzu na tara yan jikokina na basu tsohon tarihi, suji yadda Aslam ya gado wannan ragwanci". Aslam kam na gefe yana kwasar dariyar wannan lamari, yadda tsofaffin nan ke gudanar da rayuwarsu kamar wasu sababbin ma aurata abin na matukar birgeshi cikin dariya yace"a bankado mana wannan tsohon tarihin gaskiya ,bari na taro yan kannai na muzo mu zauna mu sha story," dakuwa Alhaji baba yamai tare da cewa "ungo naka Aslam tashi ka wuce ka barmin sashe na" haka dai suka dan taba wasa yau harda Alhaji baba abinda Aslam ya manta rabon shi da ganin hakan, bayan sun gama ne kuma ya daura da nasiha akan zabin da yamai, yana yi yana mai wasu irin zaurancen da Aslam din kwata kwata bai gane inda ya dosa ba, a part din ya wuni sai la'ar suka fito shida Alhaji baba zuwa masallaci daga nan kuma bai koma can ba sai ya nufi part din daddy nan ya tsaye har magriba, inda yaje yayi sallah harda isha'i, daga nan suka shigo tare da Abba, tare suka yi dinner a part din mami, bayan sun gama suka dan zauna hira , Abba ganin Aslam baida niyyar cewa zai tashi ya wuce , yasa yace"Ahh Aslam ya kamata kazo ka tafi gida haka anbar amarya ita kadai tun jiya, maza tunda jiki da sauki aje a ganta ko" murmushi yake ya shiga yi yana dan sose keya, mami tayi murmushi tare da cewa "ya kamata kuwa son aja a duba min lafiyar yata" mikewa yayi ya musu sallama,rakoshi Abba yayi har parking lot. ya shiga motar shi ya tayar ya dauki hanya a zuciyar shi sai sake sake yakeyi. Baiso Abba ya tuna da batun wucewar shi ba , dan shi so yayi ya lallaba yayi shigewar tsohon part dinsu ya kwanta abinshi,dan bayajin zai iya zuwa gareta a halin da yake ciki yanzu na rashin husnan shi, shawagin shi ya dingayi a gari sai gurin sha biyu dare ya dawo layin yayi parking d'in motar can nesa kadan da gidan , ya lallabo a hankali ya kwankwasa get, mai gadi cikin dan baccin shi da baiyi nisa ba, yaji ana knocking din get kasa kasa, tashi yayi ya dauki torchlight da gora ya nufo bakin get din tare da tambayar wanene,Aslam cikin kasa kasa da murya yace "nine Mallam madu Aslam ne", mai gadi yace "yallabai ne" Aslam yace "eh nine" bude get din mai gadi yayi bayan ya tabbatar da cewa Aslam d'in ne, sadaf sadaf ya shigo ,mai fadi yace cikin dan rudewa tunda abune da bai taba faruwa ba"lafiya yallabai " Aslam ya amsa da lapiya lallabawa yayi ya shige tsohon part d'in su ya lalibi dakin shi ya shige ya kwanta. ~AMIRA~ Amir kwata kwata bai bi ta a hankali ba, hasalima kanshi kwancewa yayi tunda ya dafeta, bai kara sanin inda kanshi yake ba, kuka takeyi tana rokanshi yayi hakuri amma ina baima San tanayi ba, yakushi cizo kuwa yasha shi yafi cikin buhu, tun tana magiyar da kai yakushi har tayi tsit numfashi ya dauke. Duk wannan bidirin dake faruwa Amir baida labari yana cen duniyar sama, saida yayi good five round, sannan yadan fara jin daidai, duk da haka bawai abin ya sake shi bane. Karfe hudu saura na dare ya kyaleta, bawai dan ya gamsu ba saidan shima ya gaji, kwankwason ciyo yake mai da kafafun shi da bayanshi , jikin ma gaba daya, to abinka da sabon shiga Kwanciya yayi a gefenta take baccin gajiya ya kwashe shi bashi ya farko ba sai karfe takwas na safe. Bai lura da halin da take ciki ba saida ya lallaba ya shiga toilet ya tsarkake jikin shi, da'ker ya samu ya gama ya lallaba ya fito,gaba daya zazzabi ke neman rufeshi, Kasancewar ko ina a rufe yake rufe ruf, ga kuma manyan labulayya masu kauri yasa dakin ya kasance da duhu. Wutar dakin ya kunna mai haske, nan take idon shi ya sauka akan gadon, wani irin yankewa gaban shi yayi ya fadi, baisan sanda ya kara mika hannu ya kashe wutar ba, take dakin ya koma da duhun shi, innalillahi wainnailaihi rajiun ya shiga jerowa take zazzabin da ke neman rufe shi d'azu ya rufeshi rufe yanzu. Jinin da yaga ya bata bed sheet din ba karamin daga mai hankali yayi ba, Ganin tsayuwar baida amfani yasa ya kunna wutan ya lallaba ya karasa kan gadon, ya tallabota, hankalin shi bai idasa tashi ba saida a ya kula bata numfashi. Jijjgata ya shiga yi yana kiran "baby baby dan Allah ki tashi baby karki mutu, na shiga uku, innalillahi wainnailaihi rajiun" gaba d'aya ya rude ya rasa ma da mai zai taimaketa , duk wani tunani na kanshi ya a lokacin ya shafe, Abu daya kawai ya iya zuwa mai a rai shine ya kira mami. Harya dauki waya zai kira mami wani zuciyar ta kwabe shi da cewa kasan wa make shirin kira kuwa mahaifiyar Amira ce fa, canja akalar kiran yayi da niyar kiran mummy saidai by mistake ya kira ummi bai kula ba duk a rude yake jikin shi na rawa. Ummi dake ke kan hanyar dawowa daga bidda fshigonwan su cikin minna kenan suna daidai kure market kiran Amir ya shigo wayarta. ummi na dagawa bai jira komai ba ya shiga cewa "mummy ta mutu mummy Amira ta mutu gata nan mun tashi da safe, bata numbashi innalillahi wainnailaihi rajiun " ciki tsananin rudewa da tashin hankali yake magana daga ji ma kasan ba a cikin haiyacin sa yake ba , ummi bata tsaya jin karshen zancen shi ba ta katse kiran tare da daura hannayenta duka biyu a aka , anty Jamila dake gefenta ta shiga tambayar ta lafiaya meke faruwa, ba amsa sai cewa driven tayi ya kaita albishir, shi direba baisan albishir ba , sai anty jamy ne keta mai kwatance har suka isa gidan. Tana nan yanda take bargo kawai ya iya rufa mata, ummi na shigowar ita da anty Jamila ta shiga kwada sallama a main falo, da sauri ya mike zumbur ya fito sanye da jallabiya, yayi matukar .mamakin ganin ummi a maimakon mummy ,cikin tashin hankali ummi tace " ina Amiran" nuna mata sama yayi , tace "wuce ka kaini inda take nace" ba shiri ya juya da sauri, rufa mai baya su kayi . Suna shiga ummi ta yaye bargon daya rufa mata, wani irin zaro ido waje tayi, ganin abinda ya dauke wutan kanta na hucin gadi, tafa hannu anty Jamila ta shiga yi taba sallallami. Ummi kam mikewa tayi , batayi wata wata ba ta shararawa Amir mari kafi ya gama dawowa haiyacinsa ta kara sauke mishi wani, cin kwalar shi tayi cikin bacin rai ta shiga furta, "kai wani irin baqin mugu ne haka, dama baka da tausayi da imani har haka ban Sani ba, kasheta kayi niyyar yi da kome?" Gani bai bata amsa ba ta sake jijjgashi tace "nace kasheta da kayi niyya?". Anty Jamila ne ta kama hannun ummi ta banbare a jikin shi tana cewa"ba wannan bane a gaban mu yanzu umminsu" toilet ta shiga ta hada ruwa a bathtub mai dumi sosai tazo ta ciccbi Amira ta wuce da ita toilet, kallon Amir da yayi tsuru tsuru ummi tayi, tace"tsayuwan me kake mana aka kana binmu da kallo" sadaf sadaf ya fece daga dakin sai lokacin ma ya tuna baiyi sallar asuba ba. Anty Jamila na sakata aruwan dumin ta sauke wani marayan ajiyar zuciya, kafin ta , ta shiga cewa "wayyo Allah mummy Asmah batool zahra kuzo ku taimake ni,na shiga uku, yaya amir dan Allah kayi hakuri kamin rai, wayyo zan mutu zafi zafi yaya amir" haka ta ringa wasu irin sambatu abin tausayi, girgiza kai anty jamy tayi, ta fahimci gaba daya Amira bata cikin hayya cinta, gasata tayi da kyau, ta nado ta a tawul suka fito, kwantar da ita tayi jikin nan ya daura zafi zau,. Falo ta fita ta samu ummi ta gaya mata sun fito, ummi tace "to na kira wata kanwar mijna Dr ce anan garin take aure tana hanya" anty jamy tace"yawwa to shike nan dama maganar da zanyi kenan," zama tayi itama kusa da ummi suna jiran zuwan Dr. Zaman su ba dade wa Dr ta karaso, har dakin Amira anty Jamila ta rakata bayan sun gaggaisa, bayanin komai ta mata, ta fice ta barta da Amiran. Duba ta ta farayi ta gani ko akwai tear, subhanallahi Dr ta furta bayan taga irin aika aikar da Amir yayi, ita kanta ta dade bataga irin wannan case din ba,ta matukar tausayawa Amira. Dinki ta mata bayan ta kashe zafin wurin, ta daura mata Karin ruwa, ta rubuta wasu magunguna ta bayar tace a siya tayi amfani dashi kuma ta d'in ga shiga ruwan zafi akai akai, insha Allah nan da 3 days zata warware, shi kuma Amir kar ya kuskura ya kara kusantarta sai ta warware sosai. Bayan tafiyan Dr ummi kiran amir tayi bayan ta gama mai fada sosai, tare da tabbatar mai da cewa da zata wuce abuja shida ganin ta sai tayi wata biyar kwarara, tunda yace shi baida hanakali, bashi takardar maganin tayi yaje ya siyo. Ranar a gidan ummi ta wuni tana kula da Amira bayan ta kira waya ta labarta ma mummy komai dake faruwa, mummy kan tausayin Amira harda kwallah tayi, take ta shiga jimamin halin da sauran ukun yammatan nata suke ciki suma. ~ASLAM~ Saida ya jera kwana uku kwarara yana satan kwana a family hause ba Wanda keda labari,sai tsakar dare zaizo ya kwanta da asubar fari ya bar gidan kafin kowa ya fito daga shi sai mai gadi sukasan da hakan, koda wasa kuwa baije gidan amaryar shi ba, a kwana na hudu ne Allah ya toni asirin shi, ya dawo sadaf sadaf zaiyi shige wurin sha biyu dare, karaf a idan Abba dake tsaye jikin window, mamaki kuwa kamar ya kashe Abba, da asuba ya tirke mai gadi nan ya labarta mishi kaf abinda ke faruwa a yan kwanakin nan, godiya Abba yamai ya wuce yana sake saken ta ina zai fara. Da misalin karfe takwas na Daren ranar Abba ya daga waya ya kira Aslam, ya riga ya gama samo mafitan yadda zai bullo wa lamarin, bayan ya daga Abba yace "son ya kwana biyu ya karfin jiki ya kuma amarya" Aslam ya "jiki alhmdllh ,amarya kuma tana lafiya," Abba yace "masha Allah kakoma gida ne ko? inason ka rakani wani guri ne" Aslam yace "eh Abba ina gida ne amma bari na fito yanzu" Abba yace "ok to in kuma kana ganin amarya zata damu ku taho tare kawai"Ai da sauri ya amsa da "A'a Abba ba damuwa tace zata zauna naje na dawo ba matsala" Abba yace to shi kenan sai ka iso, ya ajiye wayar tare da saki murmushi yàce ja'iri dani kake zance. Sai kusan tara Aslam ya iso gidan dan karya yakeyi baya gida hasalima yana nisa da unguwan sosai hakan yasa ya bata lokaci kan ya iso. Yana isowa baikai ga parking ba Abba dake zaune cikin motar shi yama jiran shi ya fito, shima yana parking ya fito , bayan sun gaisa Abba ya nunamai motar yace muje ko. Ba musu ya shiga motar Abba suka bar gidan, Abba na tuƙi yana dan janshi da hira, yahuza suya sport , Aslam yaga sun je Abba yace mai" jira ni a mota pls 10 minutes" ya fice zuwa cikin wurin, har zuwa lokacin Aslam bai kawo komai a ranshi ba. Bayan minti kadan Abba ya dawo ya bude bayan mota ya ajiye siyayyar da yayi ya shiga motar suka ci gaba da tafiya, saida suka gama shawagi a titi sannan Abba ya daki hanyar London road,. Kallon Aslam yayi yace "bari na sauke a gida tunda dare yayi gobe bello ya kawo maka motar da safe", da sauri yace "A'a Abba ba damuwa muje kawai na dauke," Abba yace"kaidai bari tunda gashi har mun kawo gidan goben bello ya kawo maka motar, kaje gida kabar min daughter ita kadai" ba yacce Aslam ya iya dole haka yayi shiru, ya kudiri aniyar Abba na ajiye shi a bakin get inya bada baya shi kuma zai fice abinshi, ga mamakin shi gani yayi Abba yana danna horn a bakin get, mai gadi kuwa cikin azama ya wangale get, Abba ya kutsa motar shi ciki. Yana parking ya fito ya bude bayan motar ya dauko manyan ledodi guda biyu, har lokacin Aslam na zaune jiki a mace baida niyyar fitowa daga motar, Abba yace "fito mana son kai nake jira fah" jiki a sanyaye ya balle marfin motar ya fito, mika mishi ledar yayi tare da cewa "oya ga tsarabar daughter akai mata saida safe" karba yayi yana sakin murmushin yake yace"to Abba ta gode saida safe" jira ya danyi irin Abba ya shigayi motar nan shi kuma ya samu ya gudu amma ga mamakinsa gani yayi Abba ya jingina da jikin motar ya nuna mai hanyar plat din da ke gabanshi,. Sai lokacin Aslam ya fara hasashan wani abu to kodai Abba ya gano shine, wani busasshen miyau ya hadiye mukut, tare da kama hanyar nufar kofar plat din, har ya kai bakin kofa ya tsaya ya waigo still idanunta Abba nanan akan shi, dole yayi shahada ya murda handle din kofar ga mamakin sa gani yayi kofar ya bude, a zuciyar shi yace lallai ma yarinyar nan haka take barin kofa a bude abinta, shigayi yayi da sallama a bakinsa kasa kasa................... Ba editing🙏 Oum ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacceta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 87 & 88 Tun daga ranar da aka kawota cikin gidan a matsayin amaryar mai gida, har yau da take cikin kwana na biyar bata saka angon a idanunta ba, hakan kuma ko kaɗan bai dameta ba, harkar gabanta takeyi hankalinta kwance, ita rashin zuwan nashi ma ya mata daidai dan bata buƙatar ganin fuskar shi a halin yanzu. Yau data kama kwana na hudu tun safe data tashi baƙi takeyi, yan ganin zuwa ɗaki, basu suka sarara mata ba sai wurin magarib, gyara gidanta tayi dukda ba wani datti yayi ba ta kunna burner turaren wuta take ko ina ya ɗauki kamshi,bayan ta idar da sallah isha'i ta shiga kitchen ta dafa jellop din couscous, daidai cikin ta, kwashe wa tayi a kula ta ajiye,ɗakinta ta koma tayi wanka tana fitowa gaban mirror ta tsaya tayi shafe shafenta, tare da feshe jikinta da daddaɗan turarukanta, masu shengen ɗaɗin kamshi da tsadar gaske, wasu sleeping dress ta ciro sababbi fil, ruwan light pink ta sanya, dogon gashinta dake daure da ribbon ta warware, dan bata iya kulle shi in zata kwanta damunta yakeyi, cumb ta dauka ta kwantar dashi, take kuwa ya sakko har kusan tsaki yar kafaɗunta, dan man leɓe ta shafa kaɗan, sanna ta fito ta nufo kitchen ta dauki couscous dinta ta hada da kwalin exoctic, da ruwan gora ta dawa palo, tana ci tana kallon, kwana casa'in, a tashar areaw 24. Koda ta gama cin abincin saida ta jira aka gama shirin sannan ta kwashi plate da cup ɗin da ta bata ta kai kitchen ta wanke su. Dawowa falon tayi ta kwanta a 3 sitter ta kunna data, ta shiga WhatsApp tana dan chart a groups, wani program ake gabatarwa a wani group , mata saida ado, da take ciki, program ne akan yadda mata zasu kula da tsabtar jikinsu, shirin ya dauki hankalinta sosai, gaba daya ta tattara hankalinta da nutsuwarta ta mayar kan wayarta, domin kuwa abin karuwa ake gabatar wa. Murda handle din kofar yayi a hankali ya buɗe ya shiga bakin shi ɗauke da sallama kasa kasa , yana shiga, wani daddaɗan kamshi hade da sanyin ac yamai salama , baisan sanda ya lumshe idanun shiba, jingina bayan shi yayi da jikin kofar bayan ya mayar ya kullu, har zuwa lokacin idanun shi a lumshe suke yana shakar daddaɗan kamshin dake tashi a falon. Ganin ya shige yasa Abba dake tsaye jikin motar shi sakin murmushi tare da, komawa cikin motar yayi ya tayar ya shiga ya bar gidan, yana me rakasu da addu'a zaman lafiya da zuri'a ɗayyaba. Ya kusa kwashe 10 minutes a haka kafin a hankali ya ware idanun shi a cikin falon yana bin ko' ina da kallo, idanunshi ne ya sauka akanta, gaba daya hankalinta yana kan handset dinta dake hannunta, ji yayi gaban shi ya bada rasss, da sauri ya lumshe idanun shi ya sake budewa still dai ita ya sake gani again, bai yarda ba ya dauka gizon data saba yi mai ne wasu lokutan yauma ta ke mai, kara saka hannu yayi ya murza idanun shi ya kara budewa, sai lokacin ya tabbatar ita ne ba gizo bane. Karfin bugun zuciyar shi ne ya linku, jikinshi take ya fara wani irin tsuma,me hakan ke nufi, yanzu hakan na nufin itace amaryar da aka aura mai, itace dama zabin da alhaji baba ya mai na biyu, kokuwa dai Abba gidan kamal ya kawo shi, kokuwa dai mai kama da itace. Wata zuciyar Ce tace Aslam ka nitsu karka ruɗa kanka, wannan gidan ka ne, kuma Abba da kanshi ya kawoka, kasan dai bazai kaika gidan kamal a matsayin naka ba ko? Tambayar zuciyar nashi ya kara yi, to ita kuma husnah mai takeyi a gidana, bayan tana matsayin matar kamal. Amsa zuciyar shi ta bashi da cewa, tunda ka ganta a gidan ka , to tabass itace zabin da alhaji baba ya maka, tabass dama ta biyu Ce ka sake samu akanta. Wayyo Allah dadi Aslam rasa ina zai tsoma ransa yayi dan farin ciki, har zuwa lokacin hankalinta nakan wayarta bata san da wanzuwar mutum a kanta ba. Daidai lokacin aka gama program din da ake gabatarwa a group din, mikewa zaune tayi tana sakin murmushin ta mai kayatarwa, wayar ta ajiye tayi ɗaga hannayenta sama tana miƙa, still fuskar ta a washe dan program din ya fadakar, da ita kuma ya ilimtar da ita ta karu sosai da wasu abubuwan masu muhimmanci. Sai lokacin ya kara tabbatar da ita ɗince ba mai kama da ita ba, da wani irin doki, azarbabi, shauƙi, ya dira a gabanta, shi kanshi da za'a tambayeshi baisan yadda akayi ya iso gabanta ba, shidai kawai yaji wani irin Abu na janshi gareta kamar magnet. Ganin mutum a gabatan ta kamar daga sama yasa ta saki wani irin ƙara,kafin ta shiga furta a'uzubi kalmatillahi, ba karamin tsorata tayi ba, hakan yasa ta kasa tantance wanene, mutum ɗinne ma ko aljan. Ganin haka yasa Aslam da shauƙi ke dibanshi ya tashi ya rungumota jikin shi, ya kamkame ta. Luf kuwa tayi a faffaɗan kirjin shi, tana shakar kamshin daddaɗan turarenshi mai kwantar da hankali, idanunta a rintse sai sauke ajiyar zuciya takeyi, shi kuwa a hankali ya miƙa hannu ya shiga shafa bayanta, yana dan bubbugawa, alamar yana rarrashinta,ita dai batasan a ina take ba, dan gaba daya hankalinta baya jikin ta Zuciyar shi kamar ta fito daga kirjin shi, tsabar azalzalan shi da takeyi, wai yau shine rungume da husnah a jikin shi, wayyo dadi kashe shi, ji yayi tunda yake a duniya bai taba riskar wani yanayi mai dadin da yakai Wanda ya riski kanshi a ciki yauba. Saida suka kwashe minti biyar a haka kafin ta samu nutsuwa hankalinta ya dawo jikinta, jinta tayi dare dare a rungume jikin mutum, yana shafa bayanta, a hankali ta dago fuskarta daga kan kirjin shi, ta kai kallonta a fuskarshi, zaro manyan idanunta waje tayi, kafin ta zabura ta mai wani irin kyakkyawan hankaɗa, daya zo mishi bagatatan, ba shiri ya saketa tare da hantsilawa da baya kamar zai fadi,Allah ya taimakeshi bai fadin ba, dan gaba daya jikin shi ba kwari. Mikewa tayi a zafafe tana binshi da wani irin kallo, gashi nan shi ba harara ba amma mutum zai gwammace dama hararan shi akeyi akan wannan irin kallo. Duk da tariga tasan Aslam shine kaddaran ta ,wannan karon ma shine mijin da aka aura mata a karo na biyu sabanin zaɓin zuciyar ta kamal, ta kuma yi kukan hakan kamar hawayenta zasu kare, tayi baki ckin hakan kamar ta hadiyi zuciya ta mutu ta huta, tayi zazzafan zazzabi akan hakan kamar bazata kara lahiya ba, amma daga karshe ta fawwalawa Allah komai ta amshi kaddaranta da hannu bibbiyu. Amma yau ganin shi a gabanta har yana wani sakata acikin jikin shi yasa taji gaba daya mikin da tayi kokarin dannewa kwanaki biyu da suka wuce ya dawo sabo dal, ji tayi kamar a lokacin, ake sanar da ita , Aslam ne mijinta ba kamal ba, ta tsani Aslam tun bata San kanta ba, bata sonshi bata kaunar shi daidai da kwayar zarra a zuciyar ta. Ganin tana jifan shi da wani irin kallo yaji gaba daya jikin shi yayi sanyin, bazai iya juran irin wannan kallon daga gareta ba, zuciyar shi tarwatsewa zatayi,a hankali ya shiga takawa zuwa gabanta. Ganin yana nufota yasa ta juya da wani irin sauri sauri gudu gudu, ta haura upstairs ta shige dakinta ta banko kofa da karfi. Ganin haka yasa ya zube guwowin shi a kasa, cike da tsantsar farin ciki, rasa ma me zaiyi,yayi ji yake kamar ya daddage ya kurma ihu tsabar farin ciki, yesssssss ya furta da karfi yana dunkule hannayenshi kamar zai kai naushi, na sameta na mallaketa Allah na gode maka, goshin shi yakai kasa yayi sujud, ya shiga rerowa ubangiji kirari da godiya, yana dagowa kuwa, ya fashe da wani irin dariya kamar sabon kamu, take duk wani kulle mai nauyi da yakeji a zuciyar shi ya kau, komawa yayi da baya ya kwanta rigingine akan titles yayi filo da hannunshi yana kallon pop din falon yana sakin murmushi. (Tabdijan jama'a Asmah a gidan Aslam, tayaya akayi hakan ta kasance ,tayaya akayi matankadi ya shiga gora ne wai,? Shin ina kamal din mu ne wai, aikam dai banga ta zama ba, gidan kamal nayi yanzu, na dauko mana rahoto) ~GIDAN KAMAL~ Zaune yake a main parlour, akan daya daga cikin kujerun da sukayi wa kyakkyawan katon falon kewanya, system ne akan kafar shi ya tattara dukkan hankalin shi akai da alama wani aiki yakeyi mai muhimmanci, sanye yake da singlet, da kuma wando 3 quarter, yana aiki amma fuskar shi dauke da kyakkyawan murmushi kamar wani sabon ango. (au na manta Ashe shine ma😅) Wani daddaɗan kamshi turare ne yamai sallama a hancinsa, lumshe idanu yayi yana kara faɗaɗa murmushin fuskar sa, kafin yakai ga bude idanu yaji tausasan tafukan hannunta akan idanun shi,ta rufe mishi ido dasu, tana tsaye daga bayan shi, daukar laptop din shi yayi ya lalubi table din dake gaban shi ya daura tukun, sannan ya mika hannu ya zagayo da ita gabanshi, bai mata masauki a ko'ina ba sai kan cinyàr shi, sai lokacin ta bude mishi idanu. Wowww ya furta yana zaro idanu waje ganin irin wankan data dauka, cikin ƙananan kaya masu shegen kyau da suka bi lafiyar jikinta suka bayyana wasu sassa na jikinta, kai gaskiya deeja yar gayu ce, irin sosai dinnan. Kiss ya shiga kai mata a ko'ina ya samu bakin shi ya sauka, dariya ta shiga kwasa, bayan ta cusa hannayenta cikin lafiyayyar suman kanshi daya sha gyara sai kamshi yake yi, Saida yayi mai isar sa, ya dago ya kalli kyakkyawan fuskarta kalan na Asmah sak, saidai ita ma'abociya kwalliyace ba kamar Asmah ba, da bata cika caba ado a fuska ba. Yace "my deejah wannan irin wanka haka, Ai saiki karkare susutani, ammin na safe ammin na rana, yanzu kuma gana dare, gsky ni dan gata ne," fari tamai da idanu, tana sakin murmushi, ci gaba yayi da cewa, "gsky wannan wankan ya wanku kuma kwalliya ta biya kudin sabulu, ki tashi muje daga ciki na biya wannan wankan , dan bazai tafi a banza ba" gaban ta ne ya fadi jin abinda yake cewa , tsab ta gane inda ya dosa ganin ya fara yawo da hannayenshi a sassan jikinta, marairace fuska tayi take takoma kallan tausayi, harda dàn taro kwalla a idanunta, cikin shagwaba tace"ya kamal dan Allah kayi hakuri har yanzu ban gama warkewa bafa, wurin zaf" bai bari ta karasa ba yayi saurin dakatar da ita ta hanyar, kai mata dan karamin cizo akan lip dinta na kasa, zafi taji, tace"wash ya kam" ai saurin kai tafikan hannunta ta tayi kan bakinta ta kare labbanta, ganin ya sake duƙo dakai, alamar zai kuma cizonta. Dan bata rai yayi, yace "so nawa zan gaya miki banason jin kamal daga bakin nan naki"sai lokacin ta tuna mai tayi aka cijeta, murmushi tayi tare da kama kunnayenta duka biyu tace "sowy bazan kara ba mantawa nayi" kire mata hannun yayi daga kunne ya lakace mata hanci, dariya ta kwashe dashi, tana cusa kanta a girjin shi, shima murmushi ya saki, tare da Ciro wayar shi ya shiga kashe musu selfie, dan ba karya kwalliyar ta yamai kyau sosai, Khadijah akwai son photo dama , ganin haka yasa tayi ta canja style yana daukansu hotuna kala kala in romantic way, wani hoton ma bazai yuwu wani ya gani ba saidai iya su biyu suga abinsu, suna gamawa yace "oya tashi muje ciki na baki tukwuci," make kafada tayi tace inyin, yar dariya yayi tare da cewa "yarinya Ai baki isa ba, yau fa kwanana biyar ban sake zuwa ba, tunda naje so daya" tace " to da da baka da aure kwana nawa kakeyi baka je ba," yace "da bansan yadda garin yake bane,amma yanzu tunda na sani kullum sai naje ba ɗaga kafa tunda kin warke, oya tashi muje" kin tashi tayi,ganin haka, yasa ya ciccibeta suka karasa bedroom. Tun ranar da ya bude fuskar amaryan da akace an musanya mishi da Asman shi yaga photo copy dinta Ce,shikenan hankalin shi ya kwanta tunda dai ya tabbatar ya rasa daman shi ta biyu a kanta,gashi kuma ya samu makamanciyar ta, banbancin su kadan ne, a ranar ya kaddamar mata,itama da yake tana so, don tunda aka gaya mata ta hau murna , take ta bada kai bori ya hau, zaman su ɗagwas ɗagwas , zaki dauka wasu tsofaffin masoya ne,cikin kwanaki biyar din da sukayi tare deejah ta mantar dashi komai ciki kuwa harda Asmah, don idan ba'ita ta ambace ta ba sai a kwana a wuni bai tuno ta ba, shi yanzu ji yake da za'a bashi dama ya zaba daya tsakanin Asmah da Khadijah to ba shakka Khadijah zai zaba, don farat daya Allah ya daura mishi kaunarata matsanancin,irin kaunar da baima Asmah ba. ~WAIWAYE~ A ranar da Kamal ya biyo bayan Amir zuwa sashen alhaji baba, har ya saurari tattaunawar da sukayi, wato ranar da akakai Aslam asibiti, hankalin shi ba karamin tashi yayi ba jin halin da Aslam yake ciki, Aslam zai rasa ransa saboda soyayyar Asmah, idan ya bari haka ta faru bai cika dan uwa na gari ba , kuma ya tabbatar tunda yaji alhaji baba ya furta, ba Aslam ba Asmah ko bayan ranshi, ya furta kenan ruwa da iska bazasu iya sauya mai ra'ayi ba, take zuciyar ta cemai saidai mutum daya, tambayar zuciyar tashi yayi waye wannan mutumin, a take ta ba shi amsa da amininsa alhaji mallam take ya fada motar shi ya figeta da mahaukacin gudu bai tsaya ko ina ba kuwa sai gidan Alhaji Mallam. Tundaga yanayin shi Mallam yasan ba lahiya ba, sallaman kowa yayi suka kebe da Kamal d'in, nan ya shiga zaiyana ma Mallam abinda ke faruwa tun daga A har Z, kwarai ya tausaya ma Aslam kuma yasan tunda Alhaji baba yayi wannan furucin yayi kenan, bazai canja ba kuwa koda Aslam zai mutu ne saboda son Asmah yafi kowa Sani irin kafiya da taurin kan alhaji baba a duniyar nan, amma duk da haka zaiyi wani Abu akai, nan kamal ya sanar dashi shi ya hakira da asmah har zuciyar shi ya barma ɗan uwan shi aslam, domin ya fanshi rayuwar shi, take alhaji mallam ya shiga saka mishi albarka kuma ya mishi alkawarin zai musanya mishi da ƙanwar Asmah indai yana so. Mallam bai kara tausaya ma Aslam ba saida yaje asibiti ya gan shi kwance rai a hannun Allah ko numfashi saida oxygen yake iya yi,koda ya koma gida, da lamarin ya kwana a ranshi dan cikin dare kasa bacci kirki yayi saboda tausayin Aslam d'in, washe gari kuwa tunda sassafe ya koma asibitin ya kara duba jikin Aslam d'in, haka nan ya ganshi jiya i yau, tambayar Abba yayi ko alhaji baba yazo asibitin nan Abba ya sanar mai baizo ba, haka ya koma gida ranar ma cike da jimami, jikin shi ya kara yin sanyin da lamarin, take ya kudiri aniyar gobe zai samu Alhaji baba su tattauna akan matsalar nan ya zama dole ya tirsasashi ya baiwa Aslam Asmah, kodan suyi ceton rai, duk da yasan hakan abune mai matukar wahala sauya ra,ayin alhaji baba. Washe gari kuwa da safe ya dira gidan alhaji baba bagatatan ba notice, saidai ganin shi yayi daga sama, bayan sun zauna sun gaisa sun dan taba hira, nan yake tambayar shi yamai biki, daga yanayin yadda yaga Alhaji baba ya asma mishi yasan lallai akwai matsala. Serious face mallam ya koma, kafin ya dauko mai tattaunawar da sukayi da kamal a shekaran jiya, da kuma sadaukarwan da kamal yace yayi yabar ma dan uwan shi Aslam Asmah, da kuma musanya ma kamal da Khadijah da yake da niyyar yi. Alhaji baba bai katse mallam ba saida yakai karshen jawaban shi, ya dubi idanunshi yace "ban amince ba ni, idan kamal ya amince ya hakura ya yafe mishi ita ni ban amince ba, sanin kanka ne bana magana biyu" mallam yace tabbas nasan baka magana biyu dan ni zan karass, saidai a wannan karon ya zama dole kayi magana biyu, domin idan har Aslam ya mutu sanadin wannan lamari, kaima kanada alhaki a ciki, saboda ka haramta mai abinda Allah ya halas ta mishi, nan ya shiga mai wa'azi cikin lalama, amma kafiya irinta Alhaji baba , yana nan akan bakanshi, tuni ran mallam ya baci, nan ya shiga mai faɗa, shima gani haka ya shiga mayar mai da martani kowa na kokarin kawo hujja akan bukatar shi, ran mallam yayi kololuwar baci, mikewa yayi a fusace ya kalli alhaji baba yace"Nagode Muhammad yau ka nuna min yadda ka dauke ni , ka nuna min inda ka ajiye matsayin amintarmu, sannan ka nuna min ban isa da ahalinka ba , naji nagode, na Barka kaje kayi duk abinda zakayi amma ka Sani idan Aslam ya rasa ransa akan wannan lamarin to kasani babuni babukai". Tirkashi , koda suke yara idan Alhaji baba yama mallam ba daidai ba da wannan kalman yake horashi(Ka Sani babu ni babu kai) wannan kalmar fitar ta daga bakin mallam tana matuqar firgita shi, har ciwo yakan kwanta a zamanin suna yara idan mallam ya furta mai wannan kalma, tunda suka mallaki hankalin Kansu hakan bai kara shiga tsakanin su ba sai yau. Jikin Alhaji baba yayi mugun sanyi hankalin shi yayi mugun tashi, ganin mallam ya juya zai bar fallon, da sauri ya riko hannun shi ta baya yace" ka dawo aminina na amince, kayi hakuri ka isa da ni kaina ma ba iyali na kadai ba" juyowa Alhaji mallam yayi suka rungume juna da Alhaji baba. Riko hannun shi Alhaji baba yayi suka koma suka zauna,ya dubi mallam yace " na amince ce saboda kai da kuma amintar mu, amma wlh baɗan Aslam ba, kuma zan bashi auren Asmah kamar yadda ka bukata amma harga Allah bada son raina ba, yaci darajar ka da darajar aminta, tunda wancen lamarin ya faru Aslam baisan ya bada hakuri ba, har yanzu zancen da nake maka daga ni har iyayenshi bai ba hakuri, sannan Abu na gaba Asma'u nidai wannan karan bazan iya kallonta nace mata zan baiwa Aslam aurenta ba, bayan nasan sarai tana soyyaya da kamal, gaskiya ina ganin mun shiga hakkinta da yawa tunda dai munsan bata son Aslam kamal take so, kuma a yanzu bamu da ikon zabar mata miji tunda matsayin bazawara take," murmushi Alhaji mallam yayi yace" indai ta Asma'u ne babu wani matsala yarinya Ce mai biyayya , nasan zata min biyayya ta karbi Aslam a karo na biyu, kuma ita kanta baza ta so Aslam ya mutu ta dalilin taba, ni zan sanar mata komai, amma sai bayan daurin auren" Alhaji baba yace "to shikenan Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, saidai kafin nan akwai wasu jarabawar da zanwa Aslam, idan ya ketare yayi nasara, amma idan ya fadi kasani ya rasa Asma'u har abada"murmushi mallam yayi a zuciyar shi yace wannan mutum bazai taba canzawa ba , a fili kuwa yace "yace ba damuwa kana iya mai ko wani irin test insha Allah kuma nasan zai ketare" nan ya labarta mai maganar boye ma Aslam asalin gaskiyar magana yace mai wa tace ya zabar mai ba Asmah ba idan yayi biyayya a karo na biyu ya karba to idan kuma ya butulce yama kanshi. Bayan sun gama tattaunawa sun tsaida magana nan Alhaji mallam ya bukaci da suje asibiti tare ya duba Aslam fir yaqi saida suka sake kai ruwa rana ya amince badan yaso ba suka tafi, inda suna zuwa kuma komai yazo musu da sauki, Aslam ya nemi yafiya shi kuma alhaji baba ya nuna yamai wani zabi, bayan su Abba sun dawo gida ya Tara su tare da matayensu ya gaya musu halin da ake ciki, kusan dukkansu sunyi farin ciki da hakan dan a lokacin ba karamin tausayi Aslam yaba kowa ba. Hakance ta kasance haka aka daura auren Asmah da Aslam, Khadijah da Kamal, bayan daurin auren mallam kamar yadda yayi alkawari shida kanshi ya sanar ma Asmah bayan ya damka mata sadakin ta a hannu.............. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 89 & 90 A nan kan tiles din Aslam ya kwana dukda ma ba wani baccin kirki yayi, tunani ya lula ta yadda akayi aka bashi Asmah, kai shikam koma waye ya mai wannan babban alherin , saiya tsuguna har kasa ya gode mai, inda halima har goyo saiya mai ya zagaye gari dashi, ya kudiri aniyar gobe zaije ya samu Abba ya fayyace mai komai, daga karshe kuma ya koma tunani da tsare tsaren yadda zasu gudanar da rayuwar auren su shida husnar shi , har adadin yayan da zasu haifa tare saida ya tsara su a cikin daren nan, sai gabanin asubah bacci ya kwashe shi cike da mafarkai barkatai, gashi nan shida husna da yaran su. Kasancewar bai samu bacci da wuri ba yasa bai farka ba sai da gari ya waye garass karfe bakwai na safe. A zabure ya mike yana salati, ganin haske ya cika falon, anan toilet din falon yayi alwala ,ya dawo ya kabbara sallah, addu'o'i yayi sosai akan Allah ya taimake shi yasa Asmah taso shi itama ko kwatan sonda yake mata ne, bayan ya gama ya mike ya nufi hanyar dakin ta, a hankali yake tafiya har wani dan sanɗa yake yi kamar Wanda yazo sata, cike yake sosai da daukin ganin kyakkyawan fuskarta da ya kwana yana mafarkin shi, saida ya kwashe kusan minti goma tsaye yana tunanin ta yadda zai shiga ɗakin, karshe dai yayi shahada ya murda handle d'in kofar ya tura, saidai kuma gam yaji kofar amalar ta murza key, a hankali har yana wani kashe murya ya fara kwaɗa sallama a bakin kofar yanayi yana dan yin knocking kasa kasa Jiya da'ker bacci ya kwasheta, saida ta gama shan kukanta, da tunanin kamal dinta, sai ayyanawa take, yanzu kamal nacen tare da Khadijah, ko a wani hali suke oho ko sun daidai oho, kai tasan ma zasu daidaita ne, dan Khadijah ma ba kanwar lasa bace, take taji wani tausayin kanta ya kamata, itafa son kamal daidai da kwayar zarra bai ragu a zuciyar ta ba, (aikam dai kina ruwa yarinya inzaki kama dahir ki kama, don kamal dai tuni deejah yar gayu tamai formatting heart d'in shi😅) Duk da rashin bacci da wuri da batayi ba jiya hakan bai hanata tashi da wuri ba don tun, karfe hudu ta tashi, tayi ta idabah har aka kira assalatu ta kabbara sallah, bayan ta idar ma bata kwanta ba, azkar dinta tayi, tare da addu'o'i sosai, ta roki Allah da ya yaye mata son kamal a zuciyar tunda yanzu ta zama mallakin wanin shi, bayan ta gama kuma ta shiga karatun alkur'ani mai girma. Daidai lokacin kuma Aslam ya shiga yi mata knocking yana sallama, sarai taji shi amma haushin shi da takeji bai bari ta iya koda kallon kofar bane balle takai ga budewa, ganin haka yasa ya shiga magiyan ta bule amma fir taki, dan ko muryarta baici arzikin ji ba balle yaga fuskarta da yake maitan son gani. Gajiya yayi da magiya ya bar kofar ɗakin jiki a sanyaye, falo ya koma ya zauna yana jiran fitowarta shiru shiru awa daya awa biyu, bata ba labarin ta, tashi yayi ya koma ya sake bugawa, zuwa lokacin kam bacci ta koma bata San ma yanayi ba,jin shirun yayi yawa, yasa ya hakura da knocking, tunani ya shigayi me zataci gashi har ana neman karfe goma na safe, yanke shawaran girka mata breakfast yayi yasan idan ta fito ta samu yayi breakfast zataji dadi, shi kuma fatan shi a yanzu bai wuce yayi abinda zai burgeta ba. Kitchen ya shiga nan kuma yaja ya tsaya yana tunanin mai zai girka mata, wani irin abinci tafi so, tunawa yayi rannan yaji suna fira da batool kowacce na fadin abincin da tafi so idan bai manta ba da kunnen shi yaji tace masar shinkafa da miyar taushe , gashi shi kuma bai iya masa ba, wayar shi ya dauka ya shiga Google ya dubo yanda ake masa , take yaga abin Ashe ba sauki, don sai anjika shinkar,kuma sai barshi ya tashi wannan duk bata lokaci ne, kar ta fito ta bukaci abincin ya zama bai gama ba, dan haka fasa yin masar yayi , ya duba yanda ake doya da kwai, nan yaga yafi sauki, dan haka ya dauki doya ya fere da kyar duk ya zafzaftare doyan ya gama ya yayyanka, ya kunna gas ya daura, yana dahuwa ya tsiyaye ya fasa kwai ma'ishi ya zuba kayan dandani ya hau suya, ya gama ya dafa mata ruwan shayi mai peppermint ya juye a flask ya kwasa ya jera a dinning, kar kuso kuga Aslam at dat time, ya hada wani uban gumi, bayan ya gama ya koma kitchen din ya wawwanke kayan daya bata, ya share ko'ina ya goge dama ya iya share share dan ko lokacin zee shikeyi idan ya gaji da ganin gidan da datti. Sai kusan sha daya saura ta farka, toilet ta shiga ta sheka wankanta tayi su brush da sauran uzirorinta ,ta fito gaban mirror ta tsaya tana daure da tawel, kallan kanta tayi taga duk ta dan rarrame,ta kara haske," murmushi ta sakarma kanta tunowa da yan uwanta da tayi, a fili ta furta"Ooh su hajiya batool ko a wani hali ake ciki, nasan dai Dr bash zai sha jaraba, Allah yasa dai kar ya raga mata, dan batool inta samu miji laku laku ba karamin wuya zaisha a hannunta ta ba". shafe shafenta tayi nasu mayukanta da turarukanta, harda su humra da hajiya addawiyya ta hada musu na magani ,fuskarta kam hoda ta dan shafa sama sama da zizara kwalli, sai dan man lips data dan shafa mai danƙo. Bude tafkeken wardrobe dinta tayi ta dauki kayan ciki ta saka pant da bra, maida kallon ta tayi wurin manyan kayanta dake nan Jere rerass a cikin wardrobe d'in, wani lace ta zaro kalan dark green da ratsin milk, dinkin Riga da zani ne saidai rigar karamine mai play, ta sanya abinka ga faran fata, kalon ba karamin kyau ya mata ba, abin wuya ta dauka fation ne mai kyau da dan kunnayensa da warwaraye ta sanya, dauri ta kashe mai kyau na yan matan zamani,bayan ta yi fakin din dogon gashinta, sai ta fito da jeler shi ta tsakiyan ɗaurin, nan ta fito dass da ita, amarya sak, dirinta mai kyau ne ko wani irin dinki ta saka kyau yake mata, bata taran dinki ko wanne yi tajeyi skirt, zani ko dogon riga, duk Wanda ta saka karɓar ta yake yi, plate shoes ta saka mai kyau, ta bude kofar ta kamo hanya kitchen danta samawa cikinta abinci. Bata taba tsammanin samun shi a kitchen ba, amma ga mamakinta tana shiga ta ganshi lokacin ya gama mopping yana wanke hannu a cikin sink motsinta yasa shi saurin juyowa, idanunsu ya sarke da na juna, take fuskar shi wa washe da fara'a yayinda ita kuma tayi kicin kicin da nata, ganin shi a kitchen d'in gaba daya yasa yunwar da takeji ma tuni ya koma, cikin tsananin jin dadin ganin ta yace "gud morning my luv fatan kin tashi lafiya ya bakunta," jin abin tayi wani banbara kwai a zuciyar ta tace, wai my luv, waye my luv d'in, wlh badai ni ba, can dasu gada, a kai kasuwa. ganin taki amsawa tana mishi wannan kallon nata dake sage mai gwuywa, yasa cikin faɗaɗa fara'arsa yace"kina bukatar, abincin breakfast ne, ai nama riga na girka miki, nasan zakiji dadin girkina sosai muje dining nayi serving dinki kinji baby na" ya karashe maganar yana kokarin riko hannunta, bige hannun shi tayi tare da banka mai harara, kafin taja tsaki ta juya ta bar shi nan tsaye. Falo ta dawo ta zauna, ganin shi da tayi da safen nan gaba daya taji ranta ya baci, zuciyarta tayi kunci, kwata kwata bata bukatar ganin fuskar shi a halin yanzu, ada tana jin haushin shine saboda irin musguna mata da yayi a baya,ya nuna mata tsantsar tsana da tsantsar kiyayya, Hakan yasa itama tamai mugun tsana mai tarin yawa, amma a yanzu tanajin haushin shi akan rabata da masoyin ta na gaskiya da yayi, tasani shine ya mata shamaki da auren zabin zuciyarta, wai yana sonta ta ya ya zata yarda da wannan tatsuniyar gizon, Ai ko duk jikin ta kunne ne baza ta taba yarda da hakan ba, karya ce kawai yaudarace, kuma Allah ya fishi ta Allah ba tashi ba. Shikam tana wucewa ya bita da kallo yana sakin murmushi, ko kadan hakan bai bata mai rai ba saima wani mugun kyau da yaga hararan ya mata, shida zai samu ma ta dinga mai irin wannan hararan ai zama zaiyi ya dinga kallonta kamar TV, da sauri ya biyo bayan ta zama yayi a gefenta, yadan karkato ta yana fuskan tarta, cikin lallashi yace"baby na debo miki abincin na kawo miki nan ne," share shi tayi kamar batasan Allah yayi ruwan mutum a wajen ba, bai daddara ba ya kara cewa "to ko na hada miki tea ne, na dafa miki ruwan shayi mai peppermint, nasan kina sonshi sosai ko" nanma shiru tamai bai damu ba yaci baba da cewa " to in baki son su duka ki faɗa wani abinda kike so saina girka miki," shiru again, mararaice murya yayi yace "don Allah my husnah ki bude bakin ki kimin magana naji muryar ki hankalina ya kwanta,dan Allah, ko zagina ne kiyi, shirun ki a gareni tamkar poising ne". Gaba daya ya gama takura rayuwarta itafa duk wani Abu daya shafi Aslam bata son shi, a yanzu, maganar nan da yake mata ji take kamar yana diga mata ruwan dalma a zuciya, fahimtar da tayi sonjin muryarta yake kamar hauka, yasa ta kudiri aniyar saidai ya mutu amma ko shekara zaiyi yana mata magana baza ta tanka ba, kai ko zaginta yayi zata iya daure wa dadai ta bari yaji muryan ta da yake maitar son ji. Zuciyar shi ce ta bashi shawara kan yajeya debo abincin ya biyo ta dashi nan wata kila inta ganshi taci, tsam ya mike ya nufi dinning ya shaqo plate da doya da kwai ya kawo ya ajiye a gabanta ko kallon inda plate d'in doyan yake batayi ba, sake komawa yayi ya hado mata tea ya kowa, ganin tana nan yanda ya barta ko fallon abincin batayi ba yasa ya dauki plate d'in ya zauna daf da ita ya dago doya daya a hannun shi ya kai kusan bakinta yace"haaa my husnah na ciyar dake da hannayena har sai kin koshi," shiru ba amsa, kara matsawa da doyan yayi daf da bakinta har yana dan mannuwa da lips dinta, ranta ne taji ya kara baci,a zafafe ta mika hannunta ta bangaje hannun shi, da karfi , take plate d'in doyan ya kufce ya watse a falon, tashi tayi ta banka mai harara, taja dogon tsaki, ta tsallake shi ta wuce ciki abinta. Binta yayi da kallo har ta bace ma ganin shi, murmushi ya saki yana girgiza kai, ko kadan baiji haushiba saima wani burge shi da ta kara yi. A haka suka kwashe kwana uku,ba wani sauyi har zuwa lokacin kuwa Asmah bata taba cema Aslam ci kanka ba, yayi nacin jin muryar ta harya gaji, girki kuwa haka zai mata na safe ya mata na rana da daddre ma ya mata, amma bata taba ɗanɗanawa ba koda wasa, shi kuma bai fasa yi ba, kuma bai taba gani ta shiga kitchen da suna girka wani Abu dan taci, baisan me take ci ba, a ɗan kwana ukun nan idan kuka ga Aslam duk ya sukurkuce ya zama wani iri sai rama yake karawa, dama bai gama maida jikin shi ba, na ciwon da yayi. Yau kam da suka cika kwana hudu tun safe yake zarya kofar dakin ta yana knocking, tun safe bata fito ba balle ya samu ya ganta, har gashi karfe ukun rana ake nema, gaba daya hankalin shi ya tashi gashi yayi yayi tayi magana taki, ko waya zata yi dasu zahra ko mummy kasa kasa takeyi da murya don kar yaji. Da gangan taki fitowa yau kwata kwata, abincin kam cincin da cake dasu dublan da soyayyen naman da take dasu a dakin su takeci tasha ruwa abinta, tanajin shi yana ta magiya amma ta share ko kadan bai fara bata tausayi ba, gajiya yayi ya silale anan kofar dakin nata ya zauna ya hade kai da gwuiwa. Zuciyarta Ce ta bata shawaran cewa , me zai hana kiyi amfani da wannan daman da Allah ya baki akan Aslam ki rama duk cin zali da musgunawan da ya miki a baya, ki bautar dashi ki maida shi abin tausayi, yanda baiji tausayinki ba kema karkiji nashi, take kuwa tayi na'am da wannan shawara na zuciyarta, murmushin keta ta saki a fili ta furta"Aslam ka shiga uku dani, dame zan fara ne" ta tabayi kanta, murmushi ta saki tunawa da tayi da wankin ta data dan tara don tunda tazo gidan bata yi wanki ba, kwasa tayi ta cire kakkauran zanin gadon dake kan gado da bargon shi ta hada da kayanta kusan kala bakwai ta tattaro harda kyar take dauka ta bude kofar, abin tausayi yana zaune ya hada kai da gwuiwa yana gyangyadi, ji yayi kawai an watso mai tulin kaya a kai ba zato ba tsammani, firgigit ya bude ido tare da dago kanshi, saidai ganin ta yasa shi sauke wani ajiyar zuciya, kafin ya shiga sakar mata murmushi, kallon shi tayi a yatsine, kafin ta bude baki cikin yauki da yanga tace"ga kayana nan ka wanke min su kuma yau nake bukatar su ka gane ko" wani dadi ne ya lullubeshi maimakon yaji haushi jin muryar yau yafi komai yimai dadi, take jikin na rawa ya kwashi wankin ya ya shiga toilet din dake falon ya fara wanke wa a washing mashin yanayi yana jin wani nishadi na musamman, yau husnah ta bukaci ya mata wani abin wayyo dadi, shi wlh ko abinda yafi wanki zata saka shi zaiyi, haka ya gama wankin nan yaje ya shanhsanya su a waje ya dawo. A falo ya sameta cike da dauki yana washe baki ya shiga sanar mata cewa ya gama wankin ya shanya, kallonshi tayi ba yabo ba fallasa tace" ka kyauta ma kanka" iya abinda tace kenan ba godi bare nagode, shiko ko a jikin shi a ganin shi Ai hakan wani ci gaba ya samu tunda gashi tana mai magama kuma ta sakashi aiki, shidai hakan yafi mai alheri akan shirunta a gare shi, zama yayi a gefen ta, ta juyo ta kalle shi tace, "pls ka koma ta cen" ta fada tana nuna mai kujeran nesa da ita sosai, ba musu kuwa ya tashi ya koma, shiru ne yadan ratsa tsakanin su, can ya dubeta yace "abincin ki na kan dining tun dazu na girka ko na kawo miki nan ne," dagowa tayi ta kalle shi cike da yanga da jan aji tace" zubo mi gani ko zan iya ci" tashi yayi jiki na rawa yau tace zataci girkin shi, yaje ya shakaro plate da jellop din shinkawa , yako hadu ko a ido, sai tashin kamshi yakeyi, mika mata yayi , ta nuna mai gabanta tace ajiye a nan , ba musu ya ajiye ya koma wurin zaman shi na dazu, daukar abincin tayi ta kai cokali daya bakin ta, ta fara taunawa abincin yayi dadi ba laifi a matsayin shi na namiji ya girka shi, yayi kokari sosai, amma dan wukakanci furzar dashi tayi tana ɓata fuska, shiko tsuru yayi yana kallonta , cikin bata rai tace"wannan wani irin girki ne haka ba dadi sai uban yaji , kamar girkin mayu, gaskiya ni bazan iya cin wannan abincin ba, ka tashi yanzu ka girka min sakwara da miyan taushe sannan ka min farfesun cow tail dan Allah kayi sauri dan in ka bata lokaci zai iya fita raina na fasa ci" tasowa yayi ya dauke plate din gaban ta yace"dan Allah kiyi hakuri my husnah wlh yajin ne yau ya kufce min amma yanzu zanyi miki abin da kike so ki bani 30 minutes kacal" tace "to yadai fi maka " ta maida kanta kan handset dinta taci gaba da charting dinta. A daukance ya nufi kitchen din ya shiga fereye doyo................. Ina team Aslam ku kawo mishi dauki hilis karku barshi ya daka doyan nan😁 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 91 & 92 Da kallo ta rakashi har ya shige kitchen d'in, sauke ajiyar zuciya tayi, gaskiya yanda taga yana rawan jikin nan sai ya bata tausayi, a ranta ta shiga tunanin anya abun da tayi ya dace kenan, ko ba komai Aslam mijinta ne kuma miji yafi gaban wasa, don yana sonta bai kamata ta ringa mai haka ba, gaskiya ya bata tausayi, ya Aslam d'in da ta sani giant baya wasa baya son raini dan gayu dan kwalisa, wanda da ko kallon ta yayi ada sai taji kamar ta saki fitsari a wando tsabar kamewan shi da rashin daukar wargi shine ya dawo haka a hannunta, hmmmm lallai duniya juyi juyi, take shedaniyar zuciya ta shiga ce mata, wai kina nufin har kin karaya kin fara jin tausayin shi, kin manta abubuwan da ya miki a baya kenan, to wlh karki kuskura kiji tausayin shi yanzu saiya kara gasuwa, Allah ne ya kama miki shi ya kuma baki dama akan shi kema ki rama musgunawan da ya miki a baya, shima yaji a jikin shi. Da haka shedan yayi tasiri akanta ɗan tausayin shi data faraji nan ya wuce. Minti arba'in ya kwashe yana faman aikin girka sakwara da miyan taushe, harda farfesu, gas biyu yayi don ya yi sauri ya gama kar ranta ya baci ta fasa ci,lokacin da ya fara daka taji kamar taje ta ce ya barshi kawai , amma ta dake, tana nan zaune ya gama ya jera a dinning, zuwa yayi ya shaida mata ya gama,yana dining, kallon shi tayi, ganin duk ya hada zufa, gashi duk ya wani rarrame, yasa taji ya ba'il baya tausayi, tsintar bakin ta tayi da cewa "sannu da aiki ngd" wani dadi ne ya lullubeshi jin abinda tace,kenan ta yaba tunda gashi har da gdy, ya fahimci tana da raguwar zuciya, ta farajin tausayin shi,murmushi ya sakar mata, a zuciyar shi yace na samu logonki yarinya, saura kiris nayi nasara a kanki , zan jure koma meye, har zuwa sanda zaki shiga hannun, zakiyibayanine, saina birkita miki kwakwalwa ta yanda zakiji inba Aslam ba sai rijiya rijiyar ma mai kwalabe. Ganin ya tsaya kanta yana kallonta yana sakar mata kyakkyawan murmushin shi, yasa tace "pls ka zubomin zuwa nan bazan iya zuwa dinning dinnan ba" yace "angama babyna" juyawa yayi da niyyar zuwa ya zubo mata, tace "wait Aslam" juyowa yayi yace "na'am sweetie" tace " pls daga yanzu baba sonjin baby, ko sweetie ko husnah or whatever, kawai ka kirani ni Asma'u na yafimin" yace "to shikenan an gama mrs Asmah". Zuwa yayi ya zubo mata sakwaran katon malmala, ya zuba miya a gefe ya zubo farfesun a wani plate din dabam, ya dauko ruwa da juice ya hado a tray ya kawo mata. Ajiye mata yayi ya koma garin zaman shi data nuna mai ɗazu, daukan sakwaran tayi ta kai loma daya baki, so yummy ta fada a zuciyar ta, gaskiya yayi dadi, ware wa tayi taci gaba cin sakwwaranta hankali kwance tana Santi, ji tayi idanun shi sun mata yawa akai har tana neman kware wa, ɗagowa tayi ta kalle shi, shima ganin zata dago kai take ya koma fuskar tausayi, aiko dai ya bata tausayin. Tace "kai baza kaci sakwaran bane" yace "babu saura ai duka na zubo miki" dage kafaɗa tayi taci gaba da cin abincin ta, can dai ta kasa jurewa, tace "ka wanko hannu kazo muci tare to" cikin zumudi yace "da gaske" tace "eh kobaza kaci bane?" yace "A'a zanci" wanko hannun yayi yazo ya zauna kusa da ita yasa hannu sunaci tare, sai kallonta yake yana murmushi, can kuma dan samun guri ya guziro sakwaran wai zai bata a baki, hararan shi tayi, ba shiri ya maida hannunshi bakin shi, haka suka gama, zai kwashe kwanukan tace ya barshi, ita ta kwashe ta kai kitchen ta shiga wankewa, tana ciki yi ya shigo yace ta barshi, itama tace ya barshi haka suka haɗa hannu suka wanke tanayi yana dauraya, har suka gama, ta share kitchen d'in yayi mopping, haka dai suke aikin kadaran kadahan ba wani fira a tsakanin su, ta daure fuska shi kuma sai murmushi yake mata. Bayan sun gama tsab ta kama hanyar dakinta zata je ta dan huta binta ya shigayi a baya batare da ta sani ba, saida ta buɗe ƙofa zata shige juyowan da zatayi taga mutum a bayanta, gabanta ne ya faɗi don ya bata tsoro, kallon shi tayi tace "lafiya" cikin alaman rashin gaskiya ya shiga Sosa ƙeya kafin karya da zai mata ya faɗo mai, yace" ji nayi kamar kince nazo muje na miki tausa" harara ta wurga mai kafin ta shige dakinta, ta banko kofa tana Jan karamin tsaki. Murmushi ya sake wani irin nishadi na musamman yake ji yau, jinshi yake makar an bashi kyuatar ticket ɗin shiga Aljanna, a fili ya furta"tausayin na takeji, tausayi kuma alama ce ta soyyaya, zan biki yadda kikeso,zan miki duk abinda kikeso zan maida kaina ba kowan komai ba a gabanki har sai na wanke kaina da dukkan tarin laifuka na a gareki, zan dasa miki soyyaya ta a zuciyarki, ba tare da kin shirya ma hakan ba, zan sakaki ki soni irin soyayyar da baki taba yima wani mahaluki a duniya ba,nayi miki alkawari" ya karashe maganar yana dunkule hannayenshi alamar maganar daga zuciyar shi take fitowa kai tsaye. ~BATOOL~ Yau kimanin wata daya kenan da auren su, kuma har zuwa wannan lokacin babu jituwa a tsakanin su kullum cikin rigima suke da juna,soyyaya ce zazzafa ke dawainiya da zuciyar ko wannan su, amma sun kasa ganewa balle su tsaya suyi rayuwar aure mai ma'ana, Dr bashi da matsala don shi tun ba yauba ya riga ya gane sonta yakeyi bana wasa ba, matsalar daga gare tane, taki ta gaskata zuciyarta dake azalzalan ta kullum akan lamarin Dr d'in. Kowa zaman kanshi yakeyi a gidan, kowa shi zai neman ma kanshi abinda zaici, batool girkinta takeyi lafiyayye ta zauna taci a gaban shi, yana haɗiyan yàwu, amma ko siɗi saidai yaje yayi takeaway a waje yazo gida yaci kokuma yaje gidan hajiyan shi yaci, kullum cikin fada suke kamar wasu tom and jerry, duk wannan yanayi da suke ciki basu taba raba makwanci ba, ɗaki ɗaya suke amfani toilet daya komai daya duk da akwai wasu dakuna a gidan amma Dr bai yarda da hakan ba, duk fadan da zasuyi kuwa, ba yadda batool batayi ya bar mata dakin ba ya koma wani amma fir yaqi tayi naci tayi mita harta gaji, saidai insunzo kwanciya ta jera pillows a tsakanin su,ta juya mai baya, gata da birgima ta gama jere jeren pillows d'in karshe wataran a kirgin shi take kwana, shiko da ta birgimo jikinshi ya kara rungume ta susha baccin su,inta farka ta ganta a nan kuwa ta hau bala'i tace shine ya matsota dama dan haka yaki canja ɗaki. Yau ta kama lahadi babu aiki kuma yaune ya saka rana zai dauke ta suje ta gaida hajiyan shi, don tunda akayi bikin bata fita ba, hajiyan da kanta ne tace karta fara fita yanzu ta bari ta dan kwana biyu sai ya kawota, kannen shi kuwa yammata zuwan su uku, kuma ba laifi tadan saki jiki dasu, dan kwata kwata basu da matsala ƙauna suke nuna mata sosai, anty sama anty ƙasa, duk da sun girmeta a shekaru ƙaramar su ce kawai zasu iya zuwa sa'anni, ashmat da amrah ma sun dawo so d'aya. Misalin karfi takwas na safiyar ranar lahadi, kwance take a gadon ɗakinsu tayi daddaya abinta , don tunda ta idar da sallah, tayi azkar da addu'o'in ta ta koma ta kwanta bacci mai nauyi ya kwasheta, cikin baccin taji ana yayyafa mata ruwa a fuska , ba shiri ta ware idanunta cike da masifa,dan tasan aikin wanene wannan, wannan Ai wulakanci ne. Maganar da zatayi ne ta makale hango shi da tayi tsaye gaban mirror daure da tawul a kugu ya juya baya, da alama daga wanka ya fito, lallausar farar fatan jikinshi mai sulbi dauke yake da dotdot naruwan wankan dayayi, mataji ne a hannun shi yana sharce jikaken gashin kanshi da gangan kuma yake yarfa mata ruwan a fuska, don tsokana, yanayi yana kallonta ta mirror ganin ta bude ido yasa yayi sauri dauke kallonshi a kanta. Duk tsiwar batool idan ta ganshi a cikin irin wannan yanayi ,lukus tajeyi duk kunya ya cikata bata iya kallon shi a haka, gashi shi kuma ɗan duniyan kanshi ne, duk in yayi wanka haka yake fitowa abinshi kullum yazo yayi share shafen shi a gabanta ya shirya a gabanta, itako taita sunne sunnen kai, bata iya dagowa har sai ya fita, yaukam ganin ya juya baya ne baya kallonta yasa ta kurama bayanshi ido bako keftawa tana kisima tsaruwa da haduwar surassa. Duk kallon kurillan da take mai yana kallonta ta mirror, yana murmushi, saida ya gama duk abinda zaiyi ya juyo da sauri auko tayi saurin maida idonta ta rufe kamar bata farka ba, dariya ya kwashe dashi a fili ya shiga rera wakar "muna furci dodo maiyi baza yaci riba ba, haka" tana jin shi bata kanta ba, yana gama wake waken shi na habaici yace " ni bana son munafurci kince bakya sona bana burge ki wacece wacece yanzu kuma kinzu kina satar kallon min jiki kinga haɗaɗɗiyar sura me kyau, irin wanda baki taba gani ba ko'a tv, to wannan haɗaɗɗiyar surar na nana faɗima ne, amma tunda an ƙaƙaba min ke zan iya sammiki kafin mai guri yazo mai tabarma ya naɗe" jin kalaman son ranshi da yake faɗa yasa ba ta San sanda ta buɗe ido warass ba ta manta ma baccin karya takeyi, tashi tayi zaune ta rafka wata uwar shewa tana tafa hannaye, kafin ta kwashe da dariyar rainin hankali,cikin dariya tana nuna shi tace"ina haɗaɗɗiyar surar take a nan, dallah mallam ware cen, in ana maganar haɗaɗɗu ka daina saka kanka a cika, jibe ka fa" ta karashe tana kwasar dariyar ta, haushi yaji yace "ni kike cewa ma bani da haɗaɗɗiyar sura to kalli nan kiga" wani irin bubbuɗewa ya fara yi yana baza kwanji yana daga kirji sama da kasa, sannan yayi wata irin tsayuwa na aftoci, take taga ya rikiɗe mata ya koma mata kamar wani barden soja ba Dr ba,dunkule hannun hagun shi yayi ya tara Pawern shi guri daya yana bubbgawa gurin da daya hannun, nan take damatsen hannun shi suka koma kamar na wani dan wrestling, da sauri ta dauke kanta daga kallon shi dan gaba daya wani yamyam take ji a jiki ta, duk yana lura da yanayinta tsaf, taɓe baki tayi tana kawar da kai gefe tace"to na gani kana da naman kirji da hannaye ba shike nan ba" dariya ta bashi wai naman kirji, aiko ya shiga darawa, yace"kwanji ake cewa ba naman kirji ba" tace "oho dai koma menene ni bai wani burge ni, bari kaga na tashi na samawa ciki na abinci" mikewa tayi ta nufi hanyar fita daga dakin yace "ke kazama ina zakije a haka ki dawo kiyi wanka tukun " bata kula shi ba ta wuce kitchen abinta, shima ganin ta wuce yasa ya shiga shirya wa don hatta kayan sawan shi rabi na dakin. Kitchen ta shiga ta hada lafiyayyar breakfast mai rai da motsi, tuni kamshi ya bade lungu da sako na part d'in, Dr yana gama shiryawa cikin kananan kaya bakin wando da riga red colour, masu mugun kyau da tsadar gaske, ya fito yana baza kamshi yayi kyau kuwa ba kadan ba, tunda ya sako kafarshi waje daddadan kamshin girkinta ya nurnike mai hanci, shaka yayi yana lumshe ido take miyan shi ya tsinke,gsky koma meye wannan take girkawa yayi alkawarin yau sai yaci shi saidai ayi duk bura'uban da za'ayi, falo ya nufa ya zauna yana lallatsa faskeken wayar shi. Saida ta gama tsab ta kwashe a kula ta jere a dining,sannan ta fito a kitchen din tana miƙa, ganin shi tayi zaune, yana ganin ta yace "sannu da aiki, " harara ta watsa mai tare da cewa "ban sannu ba ina ruwanka da aiki na" ta karashe tana murguda baki, yace "to naji je ki zubo muci yunwa nake ji wlh," tace "yau naji wani sabon salo hammata a diraya, na saba dafa abinci da Kaine dama" yace "to yau dai dani kika dafa dan wlh sai naci" tace "aikodai baza kaci shiba in ciki gara yau saidai ya zube, bari kaga naje nayi wanka nazo naci abincin na oh" ta karashe maganar tana miƙewa zuwa dakin su, don ragon azanci anan tabar kulolin abincin ta wuce. Tana bada baya ya saki wani murmushin keta a fili yace"yarinya man kaza, in bakiyi sharar masallaci ba kyayi ta kasuwa ai" mikewa yayi tsam ya shiga kitchen ya dauko plate ya nufi dining bude kulan abinci yayi dan kadan kuwa tayi daidai cin mutum daya, murmushi yayi yace "kin ma kanki da kinyi da yawa da saina diba na bar miki, amma wannan ba wani isana ma zaiyi ba balle na rage miki" juye abincin yayi tas a plate din har yana karkade kulan, ya dauki kofi daya ya hada kakkauran tea , ya dauki plate dinshi da kofin shayin shi ya nufi daya extra bedroom din ya bamo kofa............... Tabɗijam Dr ka taro mach😳 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU 💖 KƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKINANE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYA MIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZI NINA BA❌❌❌❌ (In👂👂👂yaji gangar jiki ya tsira👌a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 93 & 94 Mintuna talatin batool ta dauka kafin ta fito a shirye tsab cikin Riga da skirt na atamfa, ta kashe daurinta ture kaga tsiya, sai baza kamshi yakeyi, cike da takama zatazo tama Dr shegantaka, bata ganshi a falo ba hakan yasa ta nufi dinning taja kujera ta zauna zatayi ɗa'amun, saidai tana jawo kula taji ya biyota ba nauyi, da sauri kuwa ta ƙarƙare buɗe kullan wayam. Cikin zaro idanu ta furta "kutumelesi" mikewa tsaye tayi ta rike kwankwaso tana girgiza kai, kafin ta taƙarkare tace"basharrrrr" da ƙarfi saida ko'ina na gidan ya amsa , zuwa lokacin kam Dr ya gama tanɗe abincin tas ya suɗe plate, jin ihun muryarta tana kwaɗa mai kira yasa shi tasowa da plate din a hannu ya buɗo ƙofa yana lasar hannu da jan yaji, ga plate da cup empty a hannun shi, tsayawa yayi a gabanta yace "lafiya naji kina ta kwala min kira kamar naci miki bashi"yanayi yana suɗar yatsu tsut tsut. Takaici kan takaici ina wuta batool ta jefe Dr bash, ba ta san sanda ta karasa gabansa taci kwalar shi ba cikin tsiwa tace"bashar ina abincina" Ajiye plate d'in hannunshi yayi ya shiga tafa hannaye yace "la'iha'illallahu! yarinya wuyarki ya isa yanka ni kike çima kwala kike kira na da bashar gatse gatse, lallai na fahimçi kina so mu cire raini a tsakanin mu, kinaso aba hammata iska, karki damu nasan meke damuki, zaki samu dont worry" jijjigashi tayi da yake ya sake mata jiki, tace "ni ba wannan na tambayeka ba, nace ina abinci na" buɗe mata baki yayi yana nuna mata cikin bakin shi ma'ana ya lamushe. Tsabar takaici da bakin ciki sake shi tayi ta zube a gurin ta b ɓare baki tana risgan kuka, shiko dariya ya hauyi mata yace "kuma yarinya daga yau kika karayin girki ke keɗai a gidan nan muddin inanan to ba rabonki bane, Allah kinji na rantse" sautin kukanta ta kara tanayi tana shushura kafa kamar wata sabuwar ƴar yaye, kai da kaga kukan kasan na zallan shakiyanci ne. Saida tayi ma'ishi duk yana zaune yana kallonta da taga ba sarki sai Allah, ta tashi tana gungumi tana hararan shi, baiji mai take cewa ba yace"inba tsoro ba ayi da karfi naji mana" bata tanka shi ba ta wuce daki abinta ta kwanta. Bayan kamar 10 minutes ya shigo idan ta biyu ya wuce ta ya shiga toilet ya rage cikin shi, yana fitowa ta kalle shi kasakasa tace"anci abincin Allah ya isa ba dole ata kashi ba" tayi maganar ne kasa sosai yadda bazai jiba amma cikin ikon Allah karaf a kunnensa, haura wa yayi kan gadon hawa kanta yayi ya zauna ya danne mata kafa, haɗe hannayenta yayi duka biyu ya rikesu gam da hannu daya yadda baza ta iya kwacewa ba, dayan hannunshi kuwa ya mika ya hade leɓenta na sama dana ƙasa ya matse da karfi, azaban zafi taji sai mutsu mustu takeyi ta kasa kwacewa, yace "wannan wannan ɗan bakin naki ya iya rashin kunya manya manya duk randa na samu dama ta biyu a kanshi sai na kusa cinyeshi" batool dai ba baki azaba ya isheta sai hawaye tajeyi, ganin haka yasa ya saketa ya tashi a kanta, aiko ta rushe da kukan gaske ba irin na ɗazu na shakiyanci ba, don ba karya taji zafi sosai,sai Allah ya isa take jero mai amma a zuciya dan kar yaji ya ƙara mata. Fita yayi ya bar mata dakin ya koma falo yana kallo, ita kuma daga wannan kukan bacci yayi awon gaba da ita, wani American film akeyi mai kyau a mbc 2, saida aka gama ya mike yana kallon agogo, ganin sha biyu harya dan gota yasa ya nufi dakin, bacci yaga tanayi ga layin hawaye nan daya bubbushe mata a fuska, kawai sai yaji ta bashi tausayi, hawa gadan yayi a hankali ya shiga shafa mata fuska yana hura mata iskar bakin shi a fuska, bude idanu tayi akan shi, murmushi ya sakar mata kamin yakai hannu ya rike kunnayenshi yace"sorry batulan bashir, nine na saka ki kuka ko?"jin haka yasa ta kara narkewa idanunta suka ciko da kwalla, cikin shagwaba ta gyada mai kai alamar eh shine, yace "to hi hakuri bazan ƙara ba kinji, ki tashi ki samu wani abu kici ki shirya muje gidan hajiyata ki gaisheta" aiko a ɗokance tace to , dan ta gaji da zaman gida tana bukatar ta fita taga gari, tashi tayi ta shiga toilet tayi wanka koda ta fito bai dakin dan haka ta saki jiki ta shirya tsab abinta ciki dogon rigar lace, ta kashe dauri nan ta fito shar da ita saidai dan kumburin da idanunta yayi saboda kukan da tasha, a falo ta same shi zaune yana jiranta, tana fitowa yace"inyeee kinyi kyau gaskiya zo muyi selfie" murmushi tayi jin yau shida kanshi yace tayi kyau, ba ta gama murmushin ba ta tsinci muryarshi yana cewa ,"saidai ko kaɗan baki kama kafar faɗima na a kyau ba" take murmushin fuskarta ya bace bat, itafa ko wacece faɗiman nan tashi ta mata mugun tsana wlh, ji take da zasu hadu zata iya shaketa har sai ta daina numfashinta. Haka suka fito suka shiga mota yajasu sai gidan hajiyan shi,(batool a gidan surukai a dawo lafiya,nidai fatana Allah yasa karsu yada hali a can😕) ~AMIR~ Zaune yake a falon gidan shi ya rafka uban tagumi da hannu bibbiyu, abin duniya gaba ɗaya yasha mai kai, gama wayar shi kenan da ummi, amma kwata kwata bata saurareshi ba, tace kar ya kuskura ya tako kafar shi Abuja idan kuma ba haka ba zai fuakanci bacin ranta mai tsanani. Tun ranar da ummi tazo ta tarad da aika aikar daya aikata, ta shiga fushi dashi, a gidan ta kwata tana kula da Amira da shan maganinta da shiga ruwan zafinta, Amir kam tun ranar bai kara saka amira a idanun shi ba don ummi ta kasa ta tsare, kwananta biyu a gidan Amira ta wartsake saboda kulan da take samu sosai gurin ummi , a ranar kuwa Ummi ta tattara ko family hause bata koma ba don ma karsu daddy su hanata tafiya da Amira, direbanta da zai maida ta gida ta kira,yazo har cikin gidan ya ɗaukesu sai abuja, a lokacin Amir baya gidan yana dawowa ya tarad da wannan mummunan lamari, ummi ta wuce da Amira abuja, tashin hankali.(hmmmm kujimin Hadiza da kokari,kekuma ummi haka akeyi hisabillilahi😁) Tun ranar yake kiran wayar ta taki dagawa saida aka kwana aka wuni sannan ta daga, magiya ya fara zuba mata da ban hakuri tuni ta dakatar dashi,tare da mai kyakkyawan warning akan kar ya sake kiranta indai akan wannan maganar ne Amira zata riƙeta hartayi gud five months tukun na zata dawo da ita punishment dinshi kenan akan abida yayi. Amir ya shiga tashin hankali ba kadan ba , har wani rama ya fara yi a tsaye, gashi yana jin kunyan yakai karanta, yasan asirin shine zai tonu sai kowa yaji abinda ya aikata, haka yaci gaba da boye magana a can family hause kuwa ba Wanda yasan abinda ke faruwa. Yau da Amira ta cika wata daya acan kuma yau hakurin shi ya kare ya kudiri aniyar zuwa Abuja ko ganin tane ya yasa mu yayi, tun safe yake kiran ummi saida tagama jamai rai ta dauka, yace zaizo tace karya kuskura, amma bayajin zai iya hakura dan haka ya tashi ya shirya ya dauki hanya. A bangaren Amira kam tasananin kewa da kaunar mijinta ke damunta, amma tsananin kunyar ummi yasa ta kasa, nunawa, gashi ba waya sukeyi ba sai a kwana a wuni basu gaisa ba da yake wayarta ya lalace gabanin biki dana ummi suke gaisawa, daki guda ummi ta ware mata suna zaman su qalau dan koda wasa bata taba nunama Ummi alamar ta gaji da zaman ba gidan angonta takeso. Da wuraren karfe biyar na yamma suna zaune a falo ita da ummi twins sunje islamiyya, abban Amir ne ya shigo dan haka Ummi ta tashi ta bishi dakin shi domin ya kimtsa, zama tayi ita kadai tana kallon faskeken plasma dake manne a bangon falon a zahiri zàka zata shirin da ake haskawa take kallo amma a baɗini ta lula duniyar tunanin mijinta ne, yau kwanan su biyar rabon da suji muryar juna, ganin tunanin bazai fishsheta ba yasa ta mike ta nufi hanyar dakinta domin tayi wankan yamma. Daidai nan kuma Amir ya shigo cikin falon a darare bakin shi dauke da sallama kasa kasa fatan shi ace Abban shi na gida , idan yananan duk hukuncin da ummi zata mai nakin jin maganar ta dayayi zaizo da sauki, ganin gilmawanta yayi ta shiga dakin bakin dake nan kusa dana su twins, waige waige ya shiga yi a falon ganin alamar ba kowa yasa cikin sanɗa ya lallaba yabita dakin data shiga, koda ya shiga ta riga ta shiga toilet dan haka zama yayi a baki gado yana jiran fitowarta, minti 10 kacal tayi ta fito abinta daure da tawel. Turuss ta tsaya ganin ya Amir ɗinta zaune a bakin bed yana sakar mata murmushi, tsayawa tayi tana kallonshi itama cike da kewar shi,ware mata hannayenshi yayi alamar tazo gareshi, kasawa tayi, da sauri ta juyamai baya , kunyar shi takeji, basuyi irin wannan sabonba ,dan tunda wannan lamarin ya shiga tsakaninsu basu kara ganin juna ba sai yau. Wani irin kewanta yake ji bana wasa ba, da sauri ya tashi yayi hugging dinta ta baya, yana sauke ajiyar zuciya da sauri da sauri, cikin tsananin farin cikin ganin ta ya shiga cewa " I miss u so much babyna, nayi kewarki sosai wlh, kema kinyi kewata ko" gyada mai kai tayi, yace"in babynmu na farko macece baza musa sunan ummi ba kinji" ta sake gyada mai kai, sake ta yayi ya ruko hannunta suka dawo bakin gado zama yayi sannan ya zaunar da ita akan cinyarshi,lafewa tayi a jikinshi ta manna kanta a kirjinshi,tayi shiru, tana sauraren bugun zuciyarshi,shikuma ya mika hannu ya kewaye ta ya lumshe idanu, haka suka zauna shiru abin tausayi kamar wasu sababbin marayu. Ummi kam tana gamawa da Abban Amir, tace bari taje falo tabar Amira ita kadai, koda ta fito falon bata ba labarin ta, a fili tace "ta wuce ɗaki kenan, yanzu zata je ta kama bacci,bari na kirata ta farayin dinner tukunna, inba haka ba inta kwanta, baza ta samu taci abinci ba kenan" tana maganar tana karasawa kofar dakin Amira, tura kofar tayi ta shiga, ganin su tayi makale da juna ayadda bama susan ta shigo ba saɗaf saɗaf ummi ta sake kofar ta koma da baya, mamaki fal ranta yaushe Amir ya shigo gidan nan har ya tsallake faluka ya shiga bedroom din Amira bata da labari, komawa tayi dakin Abban Amir jiki a sanyaye, ganinta haka yasa yace"lafiya naganki haka ina Amiran take" rike baki tayi tace "hmmmm Abban amir kaidai bari yau naga abinda yafi karfina" zama yayi kusa da ita yace"mekefaruwa ne gayamin pls kin sakani cikin zulumi" labarta mishi abinda ta gani yanzu tayi, aiko Abba amir maizaiyi ba dariya ba, nan ya shiga yi mata dariya, yace"kece bakijin magana na gaya miki ki mayar mai da matarsa kinki, waike kina kwatar mata enci, waya gaya miki yaran yanzu ana musu haka,to wlh in baki tattarssu kin bashi matarsa ba, gobe abinda zaki gani saiya hanaki bacci ma," sauke ajiyar zuciya tayi tace ""hmmm aiko naga kwatar enci, ja'ira bakaga yadda ta lafe a jikin shi ba fah, yanzu Allah kadai yasan da wani ido take kallona Oh ni Aminatu naga ta kaina" Abban Amir yace"to ai sai gobe ki tattara masa matarsa ya tafi da ita inba so kike ayi cikin ɗan luv a a gadon ki" tace "aiko bakace be Abban amir, Allah dai ya kaimu goben". Amir kam saida yaji ana shirin kiran magriba ya salalo ya fito cikin amincin Allah ba kowa a falon, ya fice da sauri ya nufi masallaci, ummi dake hangenshi tana daga kitchen, ta sauke ajiyar zuciya kamin taci gaba da aikinta, ita yanzuma kunyar Amira takeji bata san wani irin kallo take mata ba, daga yadda ta ganta kwance jikin amir tasan tayi kewar mijinta sosai, sai yanzu take ganin wautar abinda tayi. A can masallaci amir ya hadu da Abban shi nuna mai yayi kamar saukar shi kenan ko gidan ma bai shiga ba yace bari yayi sallah, Abba yace "Allah sarki haka nefa" shidai bai gane nufin Abban ba haka suka runtumo zuwa gida, yayin mamakin yadda ummi ta tarbeshi a sake ba wani nuna alamar tana jin haushin shi, take wayar da sukayi ɗazu ya shiga fado mai arai, a zuciyar shi yace kamar ba ita bace keta min masifa dazu a waya, to kodai Allah ya karbi addu'a nane dana ke tayi akan ya daurani akanta. Tunanin shi ya katse jin ummi na cewa "aiko dai kazo akan gaɓa dama gobe nakeson nakiraka kazo ka dauki matar ka, sai gashi Allah ya kawo kama," wayyo Allah dad'i amir ya furta a ranshi bai zaci abin zai zomai da sauki haka ba, Allah maji rokon bawa. Nan ya shiga rerowa ummi godiya kamar ya ari baki, har tausayi ya bata yadda taga ya susuce, bai nemi ganin Amira ba don kar ummi taga ya cika azarbabi tace ta fasa, dakinshi da yake sauka idan yazo gidan ya sauka,washe gari a wurin breakfast ne yaga Amira, iya dauriya yayi ya samu suka gama ckin abincin nan lafiya baiyi wani abinda zaiji kunya agaban iyayen shi ba, don ba karamin kyau yaga ta kara mai ba , balle ma kwalliyan da yaga tayi, sai yakeji kamar ya zauna yata kallonta, kamar tv, duk a kage yake dasu keɓe, ya samu yadan rage zafi. Ana gama breakfast , cikin azarbabi yace ma ummi da Abba shi zai koma, ummi duk ta gane azarbabi yake yi ya dauki matar shi, shi yasa yace zai tafi tun yanzu,cikin son ta gwada shi tace "aiko gashi Amira bata gama ba ko zaka tafi inyaso next week ka dawo ka dauketa" har bakin shi na rawa wurin cewa "A'a ummi zan jirata mu tafi taren ko nan da zuwa yamma ne" Ummi tace "wai da nace kar ka bata lokaci tunda naga Sauri kakeyi" yace "A'a ummi ba damuwa ta gama mu tafi kawai zan jirata" Abban amir na zaune sai kumshe dariyar shi yake yanajin diramin uwa da ɗanta. Kiran Amira ɗaki tayi ta bata wani babban leda cike da kayan mata ingantattu tace kowanne akwai bayanin yadda zatayi amfani dashi ajiki ta rubuta mata, hada kayanta ta tayata dama kayan ba wasu masu yawa bane, ja mata kunne tayi akan karta kara zama ya mata irin damkar da ya mata wancen karon, intaga abin zaiyi yawa, har ya mata illah ta gudu, itakam Amira kunya kamar tace kasa ta tsage ta shige. Har mota ta rakata ta shiga suka dauki hanyar minna twins kuwa harda kwallah na kewan anty Amiran su To amarya da ango safe journey, asha amarci lafiya💋 Gidan Aslam haka rayuwar su yaci gaba da tafiya, kullum cikin bauta ma Asmah yakeyi da abinda ta saka shi da Wanda bata sakashi ba duk yi yakeyi, girki kafin ta tashi da safe ya gama breakfast, ya gyara gida ko ina yadau kanshi,ita dai baza tace mai sannu ba bare na gode, abinci kam zama takeyi taci hani'an idan ya girka, aikin gida kam duk ta sakar mai saidai tayi wanka taci kwalliya na fitar hankali ta kame a falo tana charting haka zaita kallonta yayta lasar laɓɓa, kamar tsohon maye, wanki da gugan kayanta duk ya dauke mata, batun zuwa office kuwa tuni ya jingine shi gefe sai assistant dinshi ne ke tafiyar da komai. Asmah kam zuwa yanzu ta rage mugun tsanar da tamai ada yanzu dai kadaran kadahan takejin shi, itadai bayajin tsanar shi kamar da kuma bata jin sonshi a ranta ko kaɗan, tasan dai yana mugun bata tausayi, Yau data kama ranar Sunday da misalin karfe takwas da rabi na safe taji ana mata knocking, ko bata tambaya ba tasan Aslam ne tashi tayi ta bude kofar ganin shi tayi dauke da tsintsiya da moppa a hannu, fuskar shi dauke da murmushi yace"gud morning mrs Asmah" amsawa tayi da "morning" yace "dama nace yau bari na share miki dakinki ne" har zatace ya barshi, don duk share sharen shi bai taba share mata dakinta ba, wata zuciyar tace ,barshi yayi Allah ne ya kama miki shi ya zama bawanki, cemai tayi"bismillah" tana kuacemai a hanya ya shiga, wow ya furta aranshi dakinta ya hadu sosai gashi a gyare tsab ba wani tarkace komai kimtse a muhallin sa, uwa uba kuma daddaɗan kamshi dake tashi mai saka nutsuwa dayake tashi hade da zabar Ac, kai gaskiya ita tanada tsabta ba kamar zee ba komai nata tsab stab, irin wannan wayewar yake nema yaje yayi lalube cikin duhu a baya. Toilet dinta ya shiga ya fara wanke wa shima fess yake kara dai daurayewa yayi sama Sama, sannan ya dawo bedroom din nanma ya gyare shi tsab, ya ko iya gyara gado kamar wani klinan hotel, yana gamawa ya kunna heater ya hada mata ruwan wanka don yaga alamar batayi wanka ba ko. A falo ya sameta yace "mrs Asmah nace na gama gyara dakin, saura wanka ko zaki tashi muje na taya ki na riga ma na sirka ruwan" harara ta watsamai, nan yayi fuskar tausayi tare da cewa "pls mrs Asmah wlh zan cuɗa ki da kyau" dariya ma ya bata, aiko ta shiga darawa, nan ya shagala yana kwallonta kamar yasa harshe ya lashe ta haka yakeji don so........... Naceba wai baza ku tambayeni ina babyn Adam bane😤 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKINANE BAN YARDA WATA KO WANI SU JUYAMIN LABARI TA KO WACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌❌❌ (In👂👂👂yaji, gangar jiki ya tsira👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 95 ~BABYN ADAM~ Har Barr ya gama kwanaki bakwai daya kamata miji mai mata yayi a dakin amaryarsa budurwa,babu abinda ya shiga tsakanin su, na auratayya, saidai a yan kwanakin nan ba karamin sabo sukayi da juna ba, ta riga ta gama sakin jiki da shi duk dari darin da takeyi dashi da yanzu ta dena,yakan dan taba wasa da ita amma iyakanshi kenan bai taba nuna yana son wuce hakan ba, wannan yasa hankalinta ya kwanta, ta saki jiki da shi tunda abinda take ma tsoron, taga baida alamar yi, da amala dai ita nata miji ba dan air bane.😛 Har yayi kwana bakwai a dakinta bata fara girki da kanta ba daga gidan su ake aikowa, dan maryama cewa tayi baza tayi ba, Duk motsinsu akan idon maryama, ta sanya musu ido sosai sometimes har labe take musu, ta fahimmci babu abinda ya shiga tsakanin su har yanzu, hakan kuwa ba karamin daɗi ya mata ba. Tsakanin ta da Barr kuwa babu zaman lafiya kwata kwata, kullum cikin tayar mai da hankali take, gaba daya lamarin ta ya isheshi, kawai daurewa yakeyi yana kai zuciya nesa. Yau ta kama zai koma ɗakin uwar gida ya gama kwanakin shi bakwai a dakin amarya, zahra harda kukanta shaɓe shaɓe haka yasa ta a jikin shi yana lallashi kamar wata jinjira, da'ker ya samu tayi shiru, tashi yayi ya shiga toilet ya haɗa mata ruwan wanke, yace tayi wanka ta same shi a dakin shi zai hada ta da maryama ya musu nasiha daga nan kuma yaji ra'ayin su,yanayin kwanakin da zasu raba. Bayan fitar sa ta tashi ta shiga toilet d'in ta sheka wankanta da sabulanta masu kamshi na gyaran jiki, ta wanke dogon gashinta ta fito, zama tayi kan kujeran gaban mirror tayi shafe shafen ta, na mayukanta da turarukanta haɗaɗɗun gaske, tsantsararren makeup ta ɓata lokaci tayi a fuskarta, lokaci ɗaya ta dauki wani irin mugun kyau kamar wata balarabiya, dama ko batayi kwalliya ba mai kyauce balle kuma, lace ta ciro tsantsararre maroon color sai ratsin peach, ɗinki riga da skirt, dinki ya dan kamata haka yasa ya fito mata da shape sosai, dass ta fito kamar wata yar tsana, dauri ta kashe mai kyau na yayi, mayafinta karamin ta dauka peach ta ratayeshi a kafaɗa, turare ta dauka ta kara fesawa a kayanta, ta zura takalmanta mai tsini mahadin mayafinta ta dauki handset dinta ta nufi sashen Barr. Bayan shigan shi daki wayar shi ya dauka ya danna ma Maryama kira, ringing wayar keyi tana kallo taki dagawa, har ya katse kara kira yayi saida ya kusa yankewa ta daga, ta kara a kunne batace ƙala ba, jin haka yasan baza tayi magana bane,don wani bin ji take da izza kamar wata jinin sarauta, da kausasheshen murya yace"na baki nan da 10 ki kimtsa ki sameni a part ɗina" kit ya kashe wayar sa, yanayin yadda taji muryarsa tasan ba wasa a maganar shi yasa ta tashi ba wani kimtswan da tayi kayan bacci ne a jikinta riga da wando da hulla haka ta taho abinta, Maryama ba kazama bace, amma tunda akayi mata kishiya ta dauki wahalallan kishi ta daura ma kanta shikenan komai nata yaja baya, har a gurin miji kimarta ya ragu, saboda wannan haukan da tajeyi da sunan kishi, saiyaji duk ta fice mai a rai, duk ta sukurkuta kanta a banza a wofi, tunda gashi dai duk tsiyar ta bai hana shi aure ba kuma bai hanashi kawo amaryar cikin gidanta ba, ( pls mata a kiyaye asan irin kishin da za'a dingayi ba kishin da zaki zubar ma kanki mutunci a gurin miji ba, duk sonki da miji idan ya tashi aure, kiyi hakuri ki danne kishinki, ba'ace karkiyi kishin mijinki ba amma kisan irin Wanda zakiyi, idan kika kama girmanki sai kiga duk wani abinda zai gudanar a lamarin aurenshi saida yardan ki, kece zaki zama bai bashi shawara komai zaiyi saiya gaya miki saiya nimi shawaran ki, tunda yaga kin bashi goyan baya, anan saiki yagi abinda kika yaga,amma in kika yi hauka zaki tashi a tutar babu ne, wasu ne can zasuci moriyar lamarin, idan kikayi kishin hauka kika tayar mai da hankali, kimar ki zaki zubar a idanun shi da idanun dangin shi,idan akwai wacce Baku shiri cikin yan uwanshi, ta samu hanyar da zata kuntata miki,saidai kiga ana abubuwa baki da labari, amma kin kama kanki, sai ki kange komai, komai sai anbi ta hannun ki, ya sakar miki ragamar komai, dan Allah a kiyaye kuma duk tsiyar da zakiyi bazai hanashi auren da yayi niyya ba, kijama kanki raini a gurin kishiya may be ma kin girmeta kin fita komai, Allah yasa mu dace). Samun shi tayi zaune a falo yana amsa call a waya, guri ta samu a kujeran dake facing nashi ta zauna tana cika tana batsewa, ci gaba yayi da wayar shi ko kallonta shima baiyi ba, zaman ta kamar da minti biyar zahra tayi sallama cikin zazzakar muryarta mai dadin amo, daidai lokacin kuma Barr ya gama wayar da yakeyi, kamshinta ne fara musu sallama kafin a natse ta ɗago labulen falon ta shigo, da idanu suka bita yuuuu, kowa da irin kallon da yake mata, maryama ganin zahar da irin wankan data dauka ga wani zazzafan kamshi dake tashi a jikinta, saida gabanta ya yanke ya fadi rasss, take ta raina kanta a wurin ji tayi duk ta muzanta, kishi da ƙyashi da baƙin ciki suka mata kawanya a lokaci daya, take ta shiga aunawa zahra wani irin mugun kallo mai cike da tsantsar tsana. Shiko Barr wani irin kallon so da tsananin ƙauna yake binta dashi, ji yake kamar ya tashi ya taro ta ya saka a kirjinshi, ko zaiji saukin zillon da zuciyar shi take mai akanta, yana tsananin son uwar gidan shi sosai amma sonda yakema zahra special ne. Murmushi ya shiga jifanta dashi, hakan yasa itama ta shiga mayar mai da martani, matsawa yayi daga tsakiyar kujeran da yake zaune 2 sitter ya koma gefe, ganin haka zahra direct kusa dashi ta zauna a daya gefe. Har ta zauna Maryama nabinta da wannan mugun kallon, cikin sakin fuska ta kalleta tace"yaya Maryama ina kwana" wani mugun tsaki taja kamar bakin ta zai tsinke, a madadin ta amsa gaisuwar ta sai cewa tayi"wlh kaji kunya Adam yanzu ɗan wannan abun ka iya cire kudinka ka bada sadaki da sunan kana so, kazo ka ajiye kana kwanciya da ita, yarinyace fa ƙarama Wanda na tabbata da kayi auren wuri da ka haifeta, wannan abin kunyar dame yayi kama, na tabbata wannan yarinyar idan ta girmi hanan(yar su ta fari)da nisa ta bata shekara biyar, yanzu kai baka jin kunyar ka tube zindir a gaban yar cikin ka, kalli kanka ka fa har furfura kake dashi" tsaki taja kafin taci gaba da cewa "suma iyayenta ne basu da hankali wannan ai child abuse ne". Wani gigitaccen tsawa Barr ya daka mata wanda saida hantar cikinta ya kada, amma ta dake tana huhhura hanci, zahra kam zaro ido tayi waje maganar Maryama na karshe yayi mugun dakar mata zuciya, iyayenta ne basu da hankalin, tabdijam aikam baza ta kyaleta taci bulus ba, itama fa ta iya masifar nan da rashin kunya kawai dai batayi ne saboda Allah yayi ta da sanyin hali, yoooo ita da takema yar uwar batool danja har a gwada mata masifa da fitsara da rashin kunya, buɗe baki tayi da niyar yaba mata maganar da har ta mutu baza ta manta dashi ba, fahimtar hakan yasa Barr ya damki hannunta dake kusa dashi da karfi dagowa tayi ta kalle shi ya girgiza mata kai alamar kar tace komai, zahra a kwai biyayya kamar dai Asmah😅. Sauke kanta kasa tayi sai hawaye sharrr, kamar an bude famfo, a zuciyar ta tace maryama kinyi da meyi zan nuna miki aiki karamar yarinya a aikace, amma kafin nan saina mallakama mijina kai na mun dawo g-g dake, sai kinyi nadamar zagin iyayena da kikayi. Barr kam fada yahau Maryama dashi karshe ya koma nasiha yana dasa aya tace "oho dai andaiji kunya wlh girma ya fadi" bai tanka ta ba yace "yanzu ki fadi kwanakin da kikeson ku dingayi ma'ana ku raba girki," budar bakinta sai cewa tayi "Allah ya kiyaye na raba girki da yar cikina" cikin fushi yace "haka kika Ce ko to shi kenan ni na raba kwana 1-1 zaku dingayi daga yau, kuma kin amshi girki yau, da rana zaki fara zuwa breakfast din gobe, abinci kuma breakfast da dinner tare zamu dinga ci" yana kaiwa nan ya tashi ya bar masu falon , itama Maryama tsaki taja ta mike ta watsa ma zahra harara, tace "wlh ki sake mai jiki ya kwakuleki a banza dan ba zama kika zoyi gidan nan ba, na miki alkawarin saina fitar dake dan bazan yi kishi da yar cikina ba, in zaki rike budurcinki ki rike kyasamu ki kaima asalin mijinki" tana kaiwa nan ta bar falon, a fusace kamar kububuwa. Lokaci daya taji hawayen dake fita a idonta ya kafe,murmushin takaici ta sake,a zuciyarta tace wato ma saka mani idanu takeyi tana kallon ko wani motsi dake gudana a tsakanina da mijina ko,inba haka ba ya akayi tasan babu abinda ya shiga tsakanin mu, hmmmm to zan shayar dake giyar mamaki Maryama. Tashi itama tayi ta bar part din ta koma nata, abin daya faru ya tsaya mata a rai sosai, wayar ta ta ciro tana tunanin shawaran wa zata nema, Ummi , zuciyarta ya bata amsa lallai ummi ce tafi cancanta, saboda yadda suke da ita kamar kawaye, zata bata shawara mai kyau a bayyane baza ta rufe mata komai ba, take ta lalubo numbar ummi ta danna mata kira,ummi ta daga bayan sun gaisa, nan ta sanar mata abinda ya faru, da irin maganganun da maryama ta yaɓa mata, da zagin iyayenta da tayi. Nutsuwa ummi tayi ta bata shawarwari masu kyau wadanda zasu billar da ita, aikam shiru tayi tana recoding d'in abinda ummi ke gaya mata, sun dade kafin sukayi sallama, haka ta wuni a daki ita kadai, ba Wanda yazo gurinta itama bata fita wajen kowa ba, maryama bata kira cin avinciba itama bata nema ba, anam part dinta ta samar ma kanta abinda zataci. tun da safen nan kuwa bata sake saka Barr a idanunta ba sai bayan isha'i ya shigo ya same ta kwance a kan gadonta, tana ganin shi ta tashi zaune ta shiga mai sannu da zuwa, zama yayi a baking bed d'in, yana kallon ta cikin muryar kwantar da hankali ya shiga lallashinta yana bata hakuri akan abinda ya faru dazu,nuna mai tayi ba komai, komai ya wuce, dadi yaji ya kara gode ma Allah daya mallakamai zahra a matsayin matar sa, yarinyar tanada hankali da hangen nesa sosai, sallama ya mata zai wuce wurin Maryama, har bakin kofa ta rako shi tana sharar kwallah kishi fall zuciyarta, shima ji yakeyi kamar kar ya tafi ya barta, ganin hawaye yaki dauke mata yasa ya jawota jikinshi ya dago fuskarta ya shiga lashe mata hawayen dake fitowa a idanunta, yana gamawa kuma ya hade bakinsu guri daya ya shiga kissing dinta, 5 minutes suka dauka a haka kafin ya saketa yana maida numfashi yace"kiyi hakuri babyn Adam kidena min asarar hawayenki, insha Allah gobe war haka muna tare shiyasa na zaɓi 1-1 days saboda ni kaina bazan iya wuce kwana daya bakya kusa dani ba" murmushi tayi jin abinda yace, tace"gud 9t my hrt bit, ka kulamin da yayata da kyau" ta juya da sauri sauri gudu gudu ta haura dakin fadawa gado tayi tana risgan kuka kishi da kewar mijinta na addabar zuciyarta, ta kudiri aniyar mallaka mishi kanta a gobe idan ya dawo dakin ta wanna kuwa daya daga cikin shawaran ummi ne. Saida ya kulema ganin ta sannan ya fice daga part d'in da sauri, acan kuma yana zuwa ya tarad da bala'in Maryama, ganin zata hana shi bacci yasa tsakar dare ya korota waje ya bame kofar shi, haka suka cinye daren ba wani armashi ko baccin karki ba Wanda yayi cikin su ukun kowa da abinda ke damunsa. kuyi manage yau bani da isasshen caji,🙏 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKI NANE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KO WACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 96 Washe gari zahra koda ta tashi bayan tayi sallar ta na asubahi, komawa baccin ta tayi, wuraren 8 ta tashi, share part ɗinta tayi ta gyare ko ina tsab ta shiga toilet ta fesa wankanta ta zo taci kwalliyar ta kamar yadda ta saba, bata jira breakfast daga Maryama ba, ta shiga kitchen ta Samar ma kanta abinda zataci, tana cikin ci ne Barr yayi sallama ya shigo cikin shirin shi na fita. Tashi tayi da sauri ta tare shi, ware mata hannayenshi yayi ta faɗa jikinshi ya mayar ya kulle, gaskiya jiya ta wahala da kewan shi da'ker bacci ya dauke, iya sati ɗaya da sukayi tare, ba karamin sabo sukayi da juna ba, haka tayi ta juye juye, sai daga karshe ta gargadi zuciyarta da cewa, wai me akayi ma da har zaki fara damuwa irin haka, kin manta mijin wata kika aura, karki bari ki sabar wa kanki da wannan yanayin, tun wuri dan wahala zakisha, tunda dai kinsan dole hakan zaidinga faruwa daga yau. Da wannan ta samu ta yakice shi a zuciya tayi bacci, ammafa pillow nanan rungume a jikinta, madadin shi kenan. Cikin farin cikin ganin shi ta shiga cewa"nayi kewarka sosai mijina jiya da'ker bacci ya daukeni"baice komai ba sai wani wahalallan ajiyar zuciya daya sauke,karasawa sukayi wurin da takecin breakfast dinta, zama taga yayi yaja plate din gabanshi, cikin mamaki tace"A'a ya haka abinci nane wannan fa, inace har breakfast din yau yaya Maryama zatayi" yace "to bataga daman yi ba dani da yara yau horon yunwa take mana , ko jiya wurin anty innagi naci abincin dare, haka ta barmu a gantale" zahra cikin tausayawa tace "yara fa me zasuci su" yace "na bari hanan na dafa musu indomie". Barin shi tayi yaci gaba da cin abincin shi kaɗai dan kaɗan tayi bazai ishesu su biyu ba, daukar tea din da ta haɗa yayi ya kurba sannan ya kalleta, yace "ya kika tsaya kizo muci mana" girgiza kai tayi tace "kaci kawai ni dama na riga na koshi" bata saba mai karya ba don haka ya yarda. (Pls mata a dena yima miji karya, komai zaije ya dawo ki fadi gaskiya,karki kuskura mijinki ya miki shaidan karya, heee sister kin bonu, ya dena yarda dake, wlh wanibin ko gaskiyar kika fada bazai taba yarda ba saidai yaji ki kawai, ki gama rantse rantsenki a banza, dan Allah me yafi wannan ciwo da gaskiyar ka amma a ki yarda da kai, amma idan ya shaide ki da gaskiya wlh watara ko ɓacin rana ne yazo kika dan shillo karyarki yarda zaiyi ba ganewa zaiyi ba, tunda yasan ke mai gaskiya, Allah yasa mu dace) Gama wa yayi ya tashi ya wanke hannun shi a washing basin dake wurin dinner, daukar briefcase dinshi tayi ta rakoshi har bakin kofa, suna zuwa nan ta mika mishi jakar shi, kallonta yayi "yace iya rakiyar kenan" murmushi tayi tace "eh,mana wayo kake son kamin, na raka ka ka wuce ka barni gara dai na tsaya iya nan" amsan jakar shi yaya yace"kinsan dai yau kece da ni ko " fari ta mishi da ido wanda saida yasa gaba ɗaya tsigar jikin shi tashi, tare da cewa "ina sane dan har nama fika zumuɗi don kaji" dadi yaji na furucin ta yace "inyee a she dai ana sona har haka, to me za'a tanadar min " tace "me kake so" don ita duk daukar ta abinci yake nufi, sai gani tayi ya kama kunnenta ya mata raɗa, ai ba shiri ta zaro ido, tare dakai tafukan hannunta rufe fuskar ta, kamin kuma ta kwasa da gudu zuwa ciki tana kwasan dariya, shima dariyar ya shiga yi yana girgiza kai, a ranshi kuwa sake sake ne kala kala. Yana tsaye ya shagala da kallon haryar da tabi, yaji wani irin mahaukacin knocking na tashin hankalin, kamar za,a balla kofar , ba shiri ya dawo hayyacinsa, bude kofar yayi da sauri dan ganin wane mahaukacine wannan, arba yayi da uwar gida tana wani irin huci, ranta a bace, tana ganin shi tace"to alagumgumi maci amana, har yanzu dai lokaci na bai wuce ba da ka shiga dakin yar yarinya karama ka taushe ta, wlh adamu ranar lahira da shanyayyen barin jiki zaka tashi insha Allahu, tunda gashi tun ba'aje koina ba ka fara nuna rashin adalci a tsakanin mu, insha Allahu sai wutar Allah ta cika,azzalumi kawai, mak" sauran zance ne ya katse jin saukar biyar dinshi a fuskarta, mari ya mata bana wasa ba don saida ya daidaici idanunta sun rufe ruf da masifa ya ware yatsu yasauke mata su da hannun hagu ma kuwa. Wani ihu ta kwarara mai matuqar kara ta duke a gurin dafe da kuncinta, shikan, da ranshi ya gama baci, ko kallonta bai karayi ba yabi ta gefenta ya wuce abinshi, hanan da komai ya faru akan idanunta ne ta karaso da sauri ta kama hannun mamanta da idanta ke rufe bata ma ganin gabanta tayi part dinta da ita. A falo ta zube tana risgan kuka tare da tsine ma zahra albarka, tanayi tana daukar alwashin rama marinta a jikin zahra saidai in sakin ta zaiyi ya sake ta, amma tayi alkawarin, cin uban zahra la'ada waje, take ta dauka wayarta ta kira wata kawarta Mara mutunci, da wannan Mara kunyar kanwar tata wacce tama su ummi tsaki ranan nan. Take dukkansu suke Ce ta basu nan da ƴan awanni gasunan zuwa, share hawayen ta tayi, tayi kwafa, tace wlh yau saikin gwammace da baki taba sanin mijina ba a duniya. Allah sarki zahra sha ɗaya nayi ta shiga kitchen cike da ɗoki , yau zata fara girki a gidan aurenta. Tunanin me zata girka ta shiga yi, da'ker ta samu ta tsaida abinda zata girka, a nutse cike da kwarewa ta fara aikinta, kafin 2 ta kammala abinka da gas, mai kai takwas😝 White rice tayi da stew, da yaji naman kaza, ta hada pineapple juice , da farfesun cat fish, sai coslow, dayaji dafaffiyar kwai da hanta.😋 Sababbin kula mai kyau ta dauka ta zuba abincin a ciki, tunani ta shigayi, ta ina zata samu ta Sanar ma Maryama ta gama lunch, ita dai baza taje part dinta ba,ita ba saboda maryama tayi girkin ba tasan ba lallai taci ba don yara tayi, tausayin su ya kamata tun daga lokacin da Barr ya gaya mata, maryama bata basu abinci ba tun jiya sai hanan ne ke jagwalgwal musu, tana wannan sake saken taji ana knocking zuwa tayi ta bude, hanan ta gani tsaye rike da hannun karamin kanin su Ahmad, murmushi hanan ta sakar mata tare da cewa"anty ina wuni" itama zahra mayar mata da martanin murmushin tayi tace "A'a yaya hanan ina gajiya ya gida" da yake ta Riga tasan su tun kafin suyi aure tasan hotunan su da sunan kowanne su, zahra tace "ku shigo mana hanan" kin shigowa sukayi sai ma dan wayge wayge da taga hanan d'in nayi kafin a hankali cikin raɗa tace"anty dan Allah kina da abinci kiba ahmad tun ɗazu sai kuka yakeyi yunwa yakeji mummy bata bamu abinci ba tun jiya" tausayin yaran ne ya kara cika zuciyar zahra har taji kamar ta zubar da kwallah, amma ta dake, tace "karki damu hanan ni nayi muku girki mai dadi shigo ki karbar muku kije kuci," tsayawa hanan tayi tana kallonta taki shiga gane kamar yarinyar tsoron shiga dakin take da alamar an mata kyakkyawan gargadi akan shiga lamarin zahra, cewa zahra tayi ta jira ta bari ta , dauko masu, komawa tayi ta dauko kulolin ta samu tire ta jera musu komai akai ta fito ta mika mata, cikin tsananin jin dadi hanan ta mika hannu zata karba, sai ji sukayi an bangaiji tire kamar daga sama, daga zahra har hanan ba Wanda ya lura da tahowar maryama, abincin gaba daya ya zube ko kadan be rage a kullan ba, wani wawan mari maryama takai ma hanan kafin ta mude mata kunne ta figi hannun Ahmad taja su kiyy zuwa part dinsu tana shiga ta rufe hanan da duka da zagi. Zahra na tsaye a inda suka barta tanajin duk abinda ke faruwa, kwallah ne suka sauka akan kuncinta na tausayin hanan ,dukawa tayi ta tattara kulolinta, ta shige dakinta. Daidai lokacin kuma kanwar Maryama farida da kawar ta atika suka diro cikin gidan. Tarar wa sukayi maryama na dukan hanan nan suka hana tare da tambayar ba'asi, kwashe abinda hanan d'in tayi na zuwa tambayar abinci gun zahra tayi ta gaya musu, nan farida ta kara mata da rankwashi da zagi. Kallon su maryama tayi tace "abinda yasa na kiraku so nake muje ku tayani naci uban wancen karamar yar iskan, so nake in nuna mata ƙwaruru ba tsaran wake bane, wai harni ni Barr zai Mara akan wannan yarinyar, tunda mukayi aure shekar goma sha hudu kenan ko dungurina bai taba yi ba, sai yau dan ya auro wannan figaggiyar, " a zabure farida tace "ma me? mari fa kikace yaya maryam, kuma akanta, lallai yau zamuci uban yarinya, la'ada waje, ta yadda ko ganin ki tayi sai gabanta ya fadi" itama atika kumfar baki ta shiga yi kafin suka rankaya zuwa part d'in zahra. Hanan na jinsu duk hankalinta ya tashi, ita dai bata son su je su duki anty amaryarsu mai kirki kamar yadda ta lakaba mata, tunanin me zatayi dan dakatar dasu ta shigayi,dan hanan yarinyace mai matukar wayo. Zahra bayan ta koma dakinta da kwanukanta da maryama ta barar kitchen ta wuce dasu ta wanke abinta, kafin ta zuba nata abincin ta wuto parlour ta zauna tana ci tana tunanin su hanan, Ahmad ma ne yafi bata tausayi shida yake karamin yaro màra wayo ace an barshi da yunwa haka, tana wannan sake saken ne taji ana buga mata kofa kamar za'a balla. Allah sarki baiwar Allah kamar baza ta bude ba sai kuma tayi tunanin kosu hanan ne suka dawo ajiye abincin ta tayi ta tashi ta isa wurin kofar ta bude, gabanta ne ya yanke ya fadi ganin Maryama, da wasu watsatstsun mata biyu tare da ita, suna binta da mugun kallo suna huci, kafin takai ga tambayar su lafiya , farida ta sauke mata mari a fuskarta kau , tare da hankada ta cikin falon, baya tayi ta fadi saboda bata shiryama hakan ba, kuma ba karamin hankada ta mata ba, kafin ta kai ga mikewa, sun rufeta da duka ta ko'ina baji ba gani kamar Allah ne ya aikosu. Wayyo zahra sunfi karfinta sarkin yawa yafi sarki karfi itadai kokari take ta kare fuskarta kar suji mata a fuska, Maryama hawa kanta tayi ta zauna a ruwan cikin ta, tana tumurmusa. Daidai lokacin motor barr ya shigo harabar gidan da mahaukacin gudu, waya ya samu daga hanan tana kuka take gaya mai ga mummyn su ta kira anty farida da anty atika sunje dakin anty amarya wai zasu mata duka, iya abinda ya iya tsayawa ya saurara kenan,ya katse kiran ya shigo motar shi da mahaukacin gudu ya nufo gida........... Yauma dai kumin hakuri mutane na bani da isasshen caji again🙏 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKINANE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌❌ (In👂👂👂yaji! gangar jiki ya tsira👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 97 Ko parking d'in kirki bai tsaya yi ba ya balle murfin motar ya fito da wani irin sauri sauri gudu gudu ya tunkari part d'in zahra tunkan ya ƙarasa yakejin hayaniya da hargowa na tashi , hakan yasa ya karasa a guje, idanun shine ya hango mai maryama zaune ɗare ɗare a ruwan cikin babynsa tana dukà ga kuma ga farida da atika nan suma ba'a barsu a baya ba. Jin zuciyar shi yayi kamar an watsa mata fetir an cinna ashàna, wani irin zafi da kuna ta ɗauka, take ya shiga fidda wani irin huce, Barr irin mutanen na ne da idan ransu ya baci , idanunsu ke rufewa komai ma sukan iya aikatawa a lokacin, yana da matukar zuciya idan aka taboshi. Dukkansu sunyi nisa babu wacce ta lura da shigowar shi falon, dunkule hannu yayi ya kaima atika naushi a gefen fuska dayake ita ke kusa dashi, take baki ya fashe jini yayi tsartuwa saiga hakora uku a kasa. Kafa yasa ya tokari Maryama sai gata a gefe a share share a kasa, baibi ta kan wannan ba yasa kafa ya dinga ball da ita a falon ganin haka yasa farida rugawa da gudu ta shige kitchen d'in zahra ta bamo ɗofa, itama atika lallabawa tayi zata fece ya ankare da ita figo ta yayi ya hada da Maryama ya cigaba da kwallo dasu a falon idanun shi gaba daya ya rufe, baibarsu ba saida yaga kamar sun mutu, ya koma kan zahra ya dagota ya rungume gam, ta daku ko hannunta bata iya dagawa, da'ker take sauke numfashi a wahalce,ciccibanta yayi ya kaita bedroom dinta ya kwanta, dawowa yayi ya tarad da su Maryama a yadda ya barsu, wani baƙin ciki ne ya kara tirnike shi, wucesu yayi fuuu, har yakai bakin kofar fita ya sake juyowa a fusace take atika dake da sauran kwari ta fara ja baya, ita Maryama ba halin gudu dan kamar ma tayi targade a kafa takeji. Gabanta ya tsaya ya nuna ta da yatsa ciki kausassar murya mai cike da amon bacin rai, yace "maryama! na baki nan da 10 minutes ki tattara kibar min gidana ki je gida ki koyo hankali saina nameki, karki kuskura na dawo gidan nan na tarad dake , idan kuma hakan ta faru na rantse miki da Allah na lahira saiya fiki jin dadi," dawo da kallonshi yayi kan atika yace "ke kuma shari'a daga nan har kotun koli nidake ,saikin gayamin dalilin da yasa kika bi matata har cikin dakin ta kika daketa, saina sa an daureki dan ubanki, inga uban daya daure miki gindi a Niger state" fuuu ya juya ya fita yana huci kamar wani mayun wacin zaki. Jin tashin motar shi yasa farida fitowa daga maboyarta tana zazzare ido kamar na ƙwaɗi, cikin yarfe hannaye take cewa "mun shiga uku yaya Maryama yanzu ya zamuyi yace minti goma ya bamu" atika cikin muryar kuka tace "dan Allah Maryama ki tashi mu tafi karki bari mahaukacin mijin nan baki ya dawo ya taradda mu a gidan nan, na tabbata kashemu zaiyi har lahira" Maryama cikin wahalallalliyar murya take cewa"bazan iya tashi ba atika ya karya mun kafa ya gama dani" jin haka yasa farida cewa"bari na taro mana napep ko kama kama muyi dake yaya kibar gidan nan, shawaran da zan baki kenan, kar kice zakiyi taurin kai ki tsaya kin dai ji abinda yace" fice wa tayi a guje ta nufi get ta fece kiran napep, cikin sa'a tana fita babu bata lokaci ta samu, har cikin harabar gidan ta shigo da napep d'in tara in tara sukayi da maryama suka kawota napep d'in kafa yai tsami bai takuwa atika kam tuni baki yayi sintumtum, amma ita a yanzu wannan bai dameta ba burinta taga tabar gidan kan Barr ya dawo, har farida zata shiga napep d'in ta tsinci muryar Maryama a wahalce tana cewa"farida yarana wlh bazan bar ma maƙiyata ƴaƴana ba ki kwaso su dasu zan tafi," farida tace"kedai anty ki barsu daga baya kyau dawo ki kwashe su,kar yaya Adam ya dawo wlh a tsorace nake kar nima na samu rabona, ke ƙafa atika baki kila ni kuma ido zai ƙwaƙwulemin" ciki zafin ciwo maryama tace"dan uban ki farida ki kwaso min yarana nace" jin haka yasa farida kwasa da gudu part din maryama , a falo ta same su a rakuɓe abun tausayi hanan ta hada Kansu sun dunƙule waje daya sai kuka sukeyi, cikin tsawa farida tace"hanan tashi dan ubanki ki hado kan kannenki mu tafi" hanan cikin muryar kuka tace "anty farida ina zamu tafi" "tsaya kina tambayata karki taso dai" "anty gsky mu baza muje ko ina ba daddyn mu yace mu jira shi yana zuwa yanzu" bata tsaya jin karshen zancen ba ta finciko Ahmad da anisa, ta kama Jan hannunsu zatayi waje dasu, take hanan da suhail suka bita suna jan yan uwansu, kin sakesu tayi a haka suka fito har coumpound d'in gidan daidai nan kuma motar Barr ya shigo gidan. Gaba dayan su saida hantar cikin su ta kada, atika hannu ta daura aka tace"mun shiga uku yau shikenan mun mutu sai gawa, mai napep dan Muhammadu rasulullahi kaja mu tafi" mai napep kam dayake irina na ne akwai son ganin kwan zomo gyara zama yayi abinshi zai ba ido hakkinsa😅. farida kam saida fitsari ya fara kufce mata a wando tsabar razana. Parking yayi ya fito a fusace hango yadda farida ke jamai ƴaƴa kamar wasu ukuyoyi, gadan gadan ita ya nufa. (dama dazu bai samu ya sassaɓeta ba ita😁) Ganin haka yasa ta saki hannun yaran ta fara ja da bawa, tana matsawa yana matsota saida suka ƙule a bango,kafa mata idanunshi da suka rine sukayi jajur yayi kafin cikin razananniyar murya mai firgitarwa, "ina zaki kaimin ƴaƴana" shiru tayi tana kara mannewa da bango kamar zatabi ta cikin bangon ta wuce, gani taki bashi amsa yasa ranshi ya kara ɓaci ware hannu yayi ya wanka mata mari, sannan cikin daka tsawa ya kara cewa"nace ina zaki kaimun ƴaƴana" still shiru kara kai mata wani Marin yayi Wanda yafi na farkon gigi tata, take ta saki sauran fitsarin da ya fara kufce mata ɗazu, ganin ta kara mai shiru yasa ya kara kai mata wani, tare da cewa cikin tsawa "baza kiyi magana ina zaki kaisu nace" tuni nunfashin farida ya fara sizing, bai damu ba kara kai mata wani marin yayi saidai yanzu kafin ya sauka a fuskarta yaji an cebe mai hannu ta baya, ganin haka yasa farida kwasa da mugun gudu ta nufi napep d'in su, tana shiga atika tace "dan kutumar uban ka mai napep kaja mu tafi, kar ya juyi kanmu wlh baida hankali idan yazo nan har kai zai hada" jin baida hankali yasa mai napep , shiga taitayin shi, ya tada napep din suka bar gidan, dan shima yaga alamar mutumin kamar baya cikin hayyacinsa. Kallon kanin shi Dr Ali daya rike mai hannu yayi, girgiza mai kai Dr yayi yace"ya isa haka yaya kayi hakuri" bai iya amsawa Ali ba sai idanshi daya mayar kansu hanan dake ta faman risgan kuka , kamo su yayi ya rungume,yana sauke ajiyar zuciya ya dade a haka kafin suka dunguma zuwa part din zahra, har dakinta suka shiga dukkan su har Dr dan kuwa shakikin shi ne, koma ba wannan ba lafiya ya wuce wasa. Tana kwance yadda ya kwantar da ita, hawaye na zuba a idanunta wani kan wani, abin tausayi, duk hayaniyar da akeyi a kunnenta , saidai bata jin zata iya motsa koda dan yatsa a halin da take ciki. Cike da tausaya wa Ali yace"sannu anty zahra" jin haka yasa hanan itama tace"sorry anty zahra" su Ahmad ma suka dauka, karfin gudun hawayenta ne ya karu, Barr kam gaba daya tausayin ta ya gama cika shi saida ya fakaici idanun su ma ya share hawaye, yanzu duk akan shine zahra ta shiga wannan halin, ya rabota da garinta ya kawota inda bata da kowa sai Allah sai shi, gashi kuma ya kasa kareta daga shiga irin wannan yanayin gaba daya sai ya dauki laifin ya daura ma kanshi. Cikin sanyin murya yace "kiyi hakuri faɗima, duk abinda ya faru lefi nane, amma na miki alkawarin zanyiwar tufkar hanci, Abu makamancin hakan bazai kara faruwa ba, ga Ali nan zai duba ki"wani kallo tabi shi da shi Wanda mai wuyar fassaruwa Wanda ita kadai tasan ma'anar kayanta. Dubata Dr Ali yayi kuma alhmdllh ba wani babban Marsala saidai tsamin jiki, nan ya rubuta mata maganin da zai warwrar mata dashi, yace tayi wanka da ruwan dumi sosai zuwa gobe zataji garau. Ranar kwana sukayi Barr yana jigilar kula da ita motsi kwakwkwara tayi saiya taso a zabure yana mata sannu, har saida ya far ba zahra tausayi, ta tabbatar ba karamin so Barr yake mata ba, abinci abaki ya dinga bata wanka ma shiyaso yi mata amma taki yarda badon yaso ba ya kyaleta ganin ta dage, dakin dake kusa da nata ya nuna masu hanan a kwai makeken bed a cikin dakin,kai suka hau suka kwanta ita da yan kannenta, bayan ya musu takeaway sunci sunyi nak, dan ya hana zahra shiga kitchen duk da taso tayi musu ko jellop din spaghetti ne ya hana. Kwanan ta biyu ta ware ta dawo daidai kamar ba abinda ya faru, su hanan kuwa a iya kwanaki biyu dinnan sunyi wani irin mugun sabawa da ita saboda sakewar da tayi da su da yadda take mu'amalantar su ko mummyn su bata masu haka, ba wanda ya tuna da wata maryama a cikin su sai Ahmad da yake shi karamine, yakan ambaceta jefi jefi, dan yanzu yadda ya saki jiki da zahra ko maman shi bai saki jiki da ita haka ba, bacci kawai ke rabasu, shima a jikinta yake yi, idan yayi nisa take daukar sa ta kaishi dakin su da aka ware musu shida yan uwan shi, tamaso ya dinga kwana a wurin ta Barr ya hana. Tsakanin ta da barrister kuwa yanzu duniya sabuwa, soyyaya suke sha na bugawa a jarida, ya sangartata sosai da salon shi, gaba daya ta gama mika wuya, shi karan kanshi ya lura da haka, amma ya bari ta kara warware da kyau, duk da ta gaya mai ta warware sosai, shi karan kanshi a matukar takure yake, dan wasannin basa mishi, amma haka yake daurewa, don gani yake yi har yanzu bata gama warware ba. Maryama kam mai napep bai dire su ko inaba sai kofar wani karamin gida , a wani unguwa na yaku bayi, yana tsayawa suka sauka ita da farida, atika kam cewa tayi mai napep ya kaita general hospital, ko kallon su Maryama batayi ba mai napep yaja suka wuce. Maryama kafa yaki takuwa fah jama'a, ga farida itama ta kanta take balle ta taimaka mata su shiga gida, Allah ne ya turo wani kaninta namiji, irin yan oyya dinan da ganin shi ma yana bushe bushe, zai shiga gida ya ganta yace"A'a hajiya Mairo kece, sannu da zuwa, zan samu na sigari nan " cikin muryar azaba tace "gali dan Allah taimakeni ka kama ni na shiga gida" sai lokacin ya lura da kafarta yadda ya kumbura, dariya ya kwashe dashi, tare da cewa "ke kuma wa miki eyane a kafa haka," tace "bansan surutu gali dan Allah ka kamani" yace"zan taimaka miki amma a nawa dan kinsan yanzu gwamnati ta hana aikin banza, zaki bani dari biyu in samu na korawa anjima" ba yadda ta iya dole haka ta ciro dubu daya ta bashi ya dawo mata da canji, sannan ya taimaka mata ta shiga, farida dama tuni ta shige, a tsaye suka tarad da mahaifiyar su sai sallallami takeyi ita kuma farida na zaune kan wani tsohon tabarma tana kuka, tana hango maryama ta kara karfin salatinta tana direwa tace "shike nan kin kaso auren kinji dadi sai kizo ki zauna ai ga duwawuna ga naki" tana gama fadin haka ta shige dakinta dake nan ciki daya bata kara fitowa ba kuwa saida mahaifin su Maryama Wanda suke kira da Dada ya dawo, yayi mallakin ganin Maryama a gida har war haka dan bata taba kaiwa ba in tazo inta dade awa biyu, kuma ko ruwan gidan bata iya sha, balle abinci, mamakinshi bai girmamaba saida yaga kafarta a kumbure ita kuma farida ido daya a kumbure yana Neman likewa. Mahaifiyar su wanda suke kira da mama ta fito ta tare shi bayan ya huta yake tambayar lafiya mai ya samu Maryama da farida mai Maryama keyi a gida har yanzu bata koma ba, labarta mai abinda farida ta gaya mata " ashsha " yace tare da girgiza kai daga haka kuma bai kara cewa komai ba. Bayan Dada ya fita sallan isha'i ne ya shigo tare da wani dan unguwar su surajo mai gyaran targade, surajo na ganin Maryama za'a ma gyara ya cije baki yana girgiza kai, surajo irin mutanan nan ne masu shegen ruko,dan tun Maryama na budurwa wani sabani ya taba hadasu, har kanin ta gali ya kira yan kaura suka mai duka, duk da a lokacin ya rama dukan da su gali suka mai dan kwana su kusan goma a cell, amma duk da haka yana nan kullace da maryama, yau kuwa gani zai mata gyara yasa ya kudiri aniyar ramawa. Dada yace "Maryama ki gyara ga surajo na kira ya duba miki kafar nan taki, da alama targade ne" ba yacce ta iya da'ker ta mike kaɗan, surajo na tabawa ta tsallara ihu, dagowa yayi yacema Dada "wannan fa baza ta tsaya ba a samo katti su riketa " karaf a kunnen gali da abokin shi baure da suka zo daukar tuwon dare, gali yace "gamu nan mune nan kattin mu zamu daddaneta inta kamama mu ɗaɗɗaureta Allah wlh, kai shege baure matso tanan operation ya samu" magana yakeyi cikin muryar su ta shiryayyu, banace ba shiryayyu. Baure yace "A'a'ah mairo sannu mairamu" ba tausayi haka suka rirriketa, tana ta zabga ihu ga kannenta ta nan rututu kusan rai goma maza da mata don itace ta farida gidan daga ita sai gali sai farida, Allah ne ya taimaketa ya tsamota ya hada ta da Barr ya aure ta,surajo ko tunda ya duke ya damki kafar saida ya gama luguguce shi tana ihu na kusan minti goma sannan ya fara mata gyaran tsakani da Allah. Wayyo maryama dan azaba harda su fitsari a wando, su baure kuwa sai dariyar keta suke mata, saida aka gama gyaran, suka sake ta tare da lalemata yar wayar ta da dan kudinta da tazo dasu har ATM card dinta don pos din gaba daya suka dauke. Bayan mama ta gama tuwo ta zubo mata miyyar kukan nan Kore shar yako ji daddawa sai kamshin shi ke tashi, da tuwan jan dawanta da aka tukashi tun wurin azahar duk ya sassandare. Ko kallon abincin maryama batayi ba, haka ta hakura zata kwana da yunwa, bata raina kanta ba saida suka zo kwanciya, innalillahi daki daya dan karami ita da kannenta mata su kusan bakwai, gashi mutum hudu a cikin su na fitsarin kwance, wani yagalgalallan katifa ne a dakin Wanda farida dame bi mata suke kwana akai sauran kuma suyi shimfida a kasa su kwanta, da'ker farida da hansai suka sauka suka bata katifar, hansai kuwa datafi farida tsiwa sai yaɓa mata magana takeyi a kaikaice kamar zata zageta dama basu ɗasawa saboda rashin kunyarta sunfi shiri da farida. Washe gari Dada ya nemi ganin Barr donji ta bakin shi, don baice ma Maryama komai ba tukun sai yaji ta bakin Barr da yake Dada tsohon karki ne kuma yasan mutunci sosai. Brr bai bata lokaci ba ya same shi har shagonshi a sabon kasuwa, don nan hace yaje ya sameshi, bayan sun gaisa Dada yace"Adam abinda yasa na kiraka nan, in son miyi magana a sirrance, ka gayamin gsky tsakanin ka da Allah mai ya hada ka da matarka Maryama har kace taje gida saika neme ta"sauke kai Adam yayi komai na dawo mai fresh a ido kamar lokacin abin ke faruwa, bai boyema Dada komai ba kuwa ya zayyane mai abinda ke faruwa tun daga lokacin daya fara Neman aure har zuwa abinda ya faru jiya. Jinjina kai Dada yayi yace"sannu Adam da hakuri Ashe haka kata fama da rashin hankalin wannan yarinya maryama, Allah ya maka albarka kayi abinda ya dace kuma ko nine iya abinda zanyi kenan, nasan ta kaika iyaka ne yasa kace taje gida, ka kuwa kawo kuka gidan mutuwa, insha Allah Maryama baza ta dawo gidan ka ba sai tayi hankali, ka barta a gida na tsawon wata uku kwarara karka wawwayeta koda wasa, ni kuma zan idasa maka aikin, idan tayi hankali da kaina zan nemeka kazo ka tafi da ita" godiya Adam ya shiga zubawa da zai wuce ya kawo dubu goma ya bashi da'ker ya amsa sukayi sallama. (Nawawooo Maryama kinshiga uku😤 sai Adam da babynshi sun gama cin amarci zamu lekoki muga wani hali kike ciki, Dada good job Allah ya kara girma) Jinshi yakeyi wasai wlh kwana biyu daba Maryama har ƙiban shi yadan fara dawowa, haba wlh masifa bata da dadi ko kanɗa😔 Yau kimanin sati guda kenan cif da faruwar wannan lamari, misalin karfe bakwai da rabi na dare fitowa shi kenan daga masjid din kusa da gidan shi, dawowa shi kenan yau tunda ya fita tun safe bai samu dawowa gida ba sai yanzu wani baban uzirine ya rikeshi. Motar shi ya shiga ya karaso gidan shi mai gadi ya wangale mai get ya shigo ciki, parking yayi a inda a parking lot, fitowa yayi ya bude bayan motar ya dauki ledodin shi na tsaraba daya siyo ma zahra da yaranta, ya nufo part dinta fuskarsa dauke da kayataccen murmushi. Zaune suke a falo bayan sunyi sallar ishan su,sunyi dinner, sanan sukazo suka zaune zahra na koya musu musu karatun alkur'ani, Hadda sukeyi danda kai take musu, jin dirar motar Barr, daga ita har yaran ba'asan wa yafi ɗokin ganin shi, duk da karatu sukeyi kowannen su saida farin cikin hakan ya bayyana a fuskar shi, sallama yayi cikin daddaɗan muryassa sannan a hankali ya dago labule ya shigo falon, amsawa kawai sukayi fuskar su dauke da madaukakin farin ciki,ba daman su tashi sumai oyoyoooo tunda suna karatu, Ahmad da anisa kam da yake kananane kasa jurewa sukayi saida suka tashi suka nufe da gudu, da sauri cikin zakuwa ya tare su ya cira Ahmad sama, bubbuga kafa anisa ta fara yi zatayi kuka saura ita, ajiye Ahmad yayi itama ya dagata sama take ta shiga babbaka dariya, suma su zahra dake kallon su saida suka dara. Rike hannun yaran yayi suka karasa inda su zahra suke zama yayi a kusa da ita kan 3 sitter yayinda su hannan ke zaune a kasa sun lankwashe kafa suna daukar hadda. Ganin ya dawo yasa suka dakata haka addu'a tayi musu suka ansa da amin harda Barr, suna ashafawa hanan da suhail suma suka tashi suka rungume daddyn nasu suna mai sannu da zuwa, amsa musu yayi yana tambayar su ya gida, suhail yasa rigima wai shima a ɗaga shi kamar yadda akama su Ahmad, ɗaga shi Barr yayi, ganin haka hanan dake gefe taba murmushi tace "daddy nima" dariya suka sa mata zahra tace "harda ke ƙatotuwa dake 13 years fa aikin wuci ɗauka" Barr cewa yayi"zo oh daughter na ɗagaki ni a gurina baki wuci ɗauka ba, har itama data girmeki zan iya daukarta, balle ke"zuwa kuwa tayin ya dagata itama, barin su yayi nan falo ya mike zahra zata bishi yace ta zaune da yara zai dan watsa ruwa ne yana zuwa, bata son musu dashi don haka ta zauna din suka ci gaba da hira suna wasanni, gwanin sha'awa. 15 minutes ya kwashe sannan ya fito sanye da jallabiya, yayi wanka ya rage kaya masu nauyi,zuwa lokacin tuni Ahmad da anisa sunyi barci su hanan suma sai hamma sukeyi, ganin haka yasa yace su tashi ya rakasu su kwanta gobe akwai school. Har dakinsu suka rakashi shida babynshi, addu'an bacci zahra ta musu ta tottofa musu, sannan suka musu sallama suka kashe musu wuta suka ja musu kofa. Falo suka dawo tana gaba yana bayanta, sun iso daidai tsakiyar falon taji ya mata wani irin wawan runguma ta baya ya manna kanshi a dokin wuyanta, a hankali ya rada mata a kunne "na dawo kowa ya rungume amma banda ke ko," murmushi tayi tace "kayi hakuri hubby naga idanun yaran mu ne shiyasa, amma next time zan kiyaye" ajiyar zuciya ya sauke, kafin ya sake ta ya kama hannun ta suka nufi dinning , yau gaba daya jinshi yakeyi wani iri, feeling ne mai tsanani yake damunshi, tunda safe daurewa kawai yakeyi. Bayan sun gama cin abinci dan fira suka taba ya tashi ya wuce dakinshi dan yayi shirin bacci, itama haka tayi,ta wuce dakinta ta sheka wanka , tsayawa tayi gaban wardrobe ta zabi wani kayan bacci mai shegen kyau irin na turawa dan karami ta saka, wani kwalbar turare ta dauka,ɗan karami , daya daga cikin wanda Ummou Aslam na dama ta biyu fans ta aiko mata dashi, shu'ummin turarene duk yadda mace ta digashi ko kadan ne hmmmmm ba magana............ Masu comments inayinku iri sosai dinnan, kar ku damu inada dogon list na sunayenku. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE, BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yiji, gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) (Nasadaukar da wannan book din ha duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu) Tallah!💖 Tallah!! 💖Tallah!!!💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzo.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 98 Tana nan tsaye gaban mirror ya shigo dakin cikin shirin baccin shi, bakin shi dauke da sallama, amsawa tayi, ba tare ta kalle shi. Direct inda take ya nufo a hankali ya mika hannunshi ya ya zàgayeta dashi ya daura kanshi a dokin wuyanta,lumshe ido yayi jin wani irin sihirtaccen kamshin daya doki hancinsa, a kasalance ya buɗe idanu, kallon juna suka shiga yi ta cikin mirror na wasu sakanni kafin, kuma a tare suka sakar ma juna murmushi. A hakan da suke ya janyetà daga gaban mirror , suka koma bakin bed,zama yayi yana rumgume da ita ta gaban shi, hakan ya bata daman zama akan cinyar shi. Hancinshi ya manna sosai a wuyanta yana sunsunan wannan daddaɗan turaren na jikinta yana lumshe idanu ji yakeyi kamar tuñda yake bai taba jin turaren daya kaishi daɗin kamshi a duniya ba. A hankali ya miƙa hannunshi dake zagaye da ita, ya ɗage dan ficilin rigar bacci dake jikinta, ware tafikan hannunshi yayi akan shafeffen cikinta, yana shafawa a hankali. Jin yau yakeyi na musamman a gareshi, ji yakeyi wani irin ƙaunarta da matsanancin sha'awarta na azalzalan shi, fiye da na kullum. Lumshe ido zahra tayi lokacin da taji ya mika hannayenshi sama ya sauke su akan boobs dinta, ita kanta yau ta fahimci lamuran nasa na musamman ne. Kasa daurewa yayi , daura bakinshi yayi a kunenta çikin shakakkiyar murya yace"babyn Adam" cikin kasallaliyar murya tace"na'am" yace "ya sunan wannan turaren naki ne" ita karan kanta bata San sunan shiba, kawai yadda ta ganshi kenan cikin farin karamin kwalba yar ɗuri, tsintar bakinta tayi da cewa "fatima zahra" dan ware idanun shi da suka rine zuwa launi ja yayi tare da cewa "Wow no wander, dole ya kasance da irin wannan sihirtaccen kamshi, tunda ya amsa suna Fatima zahra, kinsan wani Abu?" Kasa buɗe baki tayi ta bashi amsa jin irin yadda yake sarrafa albarkatun kirjin ta cikin wani irin salo mai birkita tunanin duk wata lafiyayyar mace, sai girgiza mai kawai tayi alamar A'ah bata sani ba,yace "tunda nake a duniya ban taba jin turaren daya kaishi daɗin kamshi ba, kema ko?" ya tamabayeta, wannan karon kam kasa bashi amsa zahra tayi, gaba ɗaya ta gama yin laushi, ta gama mika wuya, wani irin sako jikinta ke amsa na musamman, shima bai kara cewa komai ba da lamura sukayi nisa, dama duk sambatune, to yanzu lamarin ma ya wuce na sambatu. Zuwa yanzu kam Abun yayi kamari daga bakin bed an koma tsakiyar bed, saida ya tabbatar gaba ɗaya ya gama fitar da ita daga duniyar mu zuwa duniyar sama'u, sannan ya dauki hanya, tsayawa kuma yayi kome ya tuna ohoo. A wahalce ya bude rinannun idanunshi, ya kalli kyakkyawan fuskarta ta cikin hasken dim light da suka bari, idanunta a runtse suke, gashinta ta gaba daya ya hargitse ya rufe mata kusan rabin fuska, dakyar ya buɗe bakin shi yace"Fatima zahra" a hankali ta ware idanunta itama , saidai idanunsu na haduwa ta mayar da nata ta runtse da sauri, dan murmushi yayi ya kara cewa"kin amince min yau na mayar dake cikakkiyar mace, kin amince min yau dani dake mu zama Abu guda, kin amince min yau nazama ke, kizama ni?". Saida gabanta ya fadi jin tambayar da yake mata, tana matukar tsoron wannan ranar, dan tasha karantawa a novels da yawa yadda, lamarin yake wasu har suma sukeyi wasu kuma su samu tear sai an musu ɗinki, wasu har gado ake basu a asibiti, gadai abubuwa da yawa dake biyo bayan lamarin, kamar tace A'a dukda ita karan kanta tana da muradi, sai kuma maganar ummi da sukayi rannan ya fado mata a rai. Daurewa tayi, tayi ƙundinbala ta girgiza mai kai alamar e ta amince,wani kayataccen murmushi ya saki, kafin kuma a bayyane taji ya furta"Allahumma jannabnin shaidani, wa janabash shaidani ma razaktana,". Barr yayi namijin kokari gurin bin Zahra a hankali, ba tare da garaje ba, har komai ya kammala wato ya maidata shi , shi kuma ya zama ita. Zahra tayi matukar mamakin yanda nata lamarin yazo mata da matukar sauki haka, dukda taji zafi sosai matsyinta na virgin, amma yadda tasama kanta bargabar lamarin bata zaton zaizo mata da sauki haka ba. Aiko bata tsaya ragonta ba, ita ta ma kanta komai da safe, ba tare da ta nemi taimakon kowa ba, har shi Barr, ba yadda baiyi ta bari ya mata wanka ba taki yarda. (To Fatima zahra asha amarci lafiya Allah ya kawo kazantar daki😍) ~BATOOL~ Saida ya tsaya a R & U global enterprise, suka yi ma maah tsaraba sosai na manyan zannuwa, da lesuka, da turaruka masu kyau da tsada, suma kannen shi su Afifa batool bata barsu ba saida ta siya musu dankunnaye da abun wuya fashion masu kyau kala bibbiyu, suma ta hada musu da turaruka, sannan suka kama hanya. A tafkeken coumpound d'in gidan yayi parking, fitowa sukayi a tare ya bude back sit ya kwaso manyan manyan ledodin siyayar da sukayi mai dauke da tambarin R & U global enterprise, gaba ya shiga tana biye da shi a baya, har suka isa kofar da zai sada ka da babban falon dake baban part d'in da yafi kowanne part girma a gidan. Doorbell ya danna, jim kadan Afifa autar su ta buɗe kofar, ganin su yasa ta daka wata uwar sufa ta rungume batool, tare da cewa da karfi"Oyoyoooo anty batool Oyoyoooo my anty" hakan ya jawo hankalin Afnan da Afrah harma da maah da suke zaune a falo, suma a guje suka taso suka rungume ta, Dr bash kam girgiza kai yayi yana murmushi ya shige ciki ya barsu, muryar hajiyan da suke kira da maah suka tsinta daga ciki tana cewa "wai meye haka kukeyi saikun kayar da itane, harda ke Afrah gotai gotai dake ko" sai lokacin suka saketa tare da kamo hannun ta suka shigo da ita ciki. Tun da ta saka kanta a fallon maah ta fara tafa hannu tana cewa "lale lale da ɗiyata batula maraba lale lale" a kunyace ta karasa gaban maah zata duka ta gaisheta, da sauri maah ta tarota ta jawota jikinta ta rungume ta daga zaune da take, kusa da ita ta mata mazauni, sannan ta kalli Afifa dake tsaye tana ta faman fara'a tace "auta akawo mata ruwa da abun tabawa" da sauri Afifa ta nufi haryar kitchen, dan kawo mata. Dr bash yana zaune yana binsu da kallo ba Wanda yabi ta kanshi, duk sun rude takan batool kawai sukeyi, kamar ma sun manta tare suke da batool d'in, inda dane da bai auri batool ba, da duk rawan jikin nan shi zasu dinga wa. Gyaran murya yayi duk suka juyo suna kallonshi yace"OK tunda ni ba mace bace shine ake nuna min wariyar launin fata a gidan nan ko, ba damuwa nasan zamana da kowa daga yau " duk dariya suka sa masa Afrah tace "sorry big bro wlh anty batool ne ta dauke mana hankali, kuma dama yanzu nakeson gaishe da kai, shine ka rigani magana" hararan wasa ya wurga mata, nan ta kwashe da dariya, sannan ta shiga gaishe shi, afnan ma gaishe shi tayi, ya amsa musu yana tambayarsu ya karatu, suka amsa da lafiya lau yayanmu. Tashi yayi yaje gaban maah ya duƙa har kasa ya gaisheta, fuskarta a sake dauke da fara'a tana binshi da kallon so da kauna ta amsa mishi tare da tambayar lafiyar shi Dana batool, ya amsa da lafiya qalau, murmushin jin daɗin hakan ta saki, sannan takai hannu ta shafa mishi kanshi mai dauke da tarin kyakkyawan suma tace"Allah yai maka albarka bashir, Allah ya baka zuri'a ɗayyaba,". Daidai nan Afifa ta fito daga kitchen hannunta dauke da tray shake da kayan ciye ciye da shaye shaye, ta dire a gaban batool, batool data kasa sakewa saboda kunyar maah dake wurin ta kalli Afifa tace "nagode sister, jazakillahu khair". Zama su Afnan sukayi suka saka ta a tsakiya sai fira suke mata, maah dake gefe tana Kallon su tana murmushi, ganin zahra bata ci komai tace "daughter kici, wani Abu mana, Afnan ki zuba mata juice ki bata," da sauri batool tace "A'a Afnan barshi, maah nagode," maah tace "ki saki jikin ki fa daughter nan gidanku ne, kici abinda kike, oya Afifa zuba mata" batool ganin maah ta dage yasa ta hakura ta amsa saidai ta rike a hannu taki sha, ganin haka yasa maah ta saki wani kayataccen murmushi. Ba komai bane ya fado mata a zuciya sai cewa batool ciki gareta shi yasa taki shan juice din wata kila bata sha'awar shine, dama tun dazu take ta mata kallon tuhuma ganin yadda fuskarta da idanunta suka dan kukkumbura,(kukan data sha kafin su wuto) a zuciyar ta tace bari na kara gwada ta na gani dan na tabbatar, tace "daughter ya baki sha ba ko bakison kalan wannan dinne a chanzo miki wani kalan, akwai ma sobo mai dadi ko shi za'a kawo miki," dama batool akwai son sobo da sauri tace "to maah nagode". Gani sukayi maah ta daga hannu sama tana cewa "Alhmdllh zargi na ya tabbata, bashir amma baka kyauta min ba dama ciki ne da batula shine baka gaya min ba, haba nidai ince naga fuskarta ya kumbura yayi danye danye kamar na mai yaron ciki Ashe kuwa shi d'inne, alhmdllh bana munyi abun kai bari na kira alhaji na gaya mai, wai masha Allah sannu kin ji batool" abinda ke fitowa daga bakin maah kenan cike da tsantsar farin ciki,. Innalillahi batool gaba daya kunya ya gama lullubeta, ji tajeyi kamar ta nitse a kasa, tuni ta haɗe kanta da gwuiwa. Dr bash kam tsayawa yayi kamar saƙago yana Kallon maah baki buɗe, ta dauki waya tana ta kiran mutane yan uwa da abokan arzikinta tana sanar dasu batool nada ciki, kasa hakuri yayi ganin ta gama waya da kanwarta dake bimata tana cewa yanzu kuma bari na kira yaya mustafa na gaya mai shima,shi tausayi ma ta bashi ganin yadda duk ta ruɗe, da alama dama jiraye take da samuwar cikin, dama yasan hakan zai iya faruwa yasan burin maah a kullum shine yayi aure ta samu jika daga ɓangaren shi, kusan kullum maganar ta kenan ɗaya, dalili kuwa shine maah irin matan nan ne da Allah ya zuba musu Son ƙananan yara, kamar kamar me, Amrat me bima Dr yayan ta uku, amma saiya kasance, baban yaran irin mazan nan ne masu shegen nuna iko akan yayansu, tana bala'il son yaran insunzo haka zata rasa ina ka saka ina ka ajiye dasu, sau dayawa takan bukaci abar mata yaran su kwana a wurinta ko kwana daya ne idan suna hutun school, kiri kiri zai hana yace tayi hakuri, takan ce "ku tafi da yayanku, Allah ya kyauta kuje ku dafa ku cinye , dama jikoki daga tsatson Mace ba abin dogara bane, ku zuba ido muna nan daku bashir dina zaiyi aure ya haifar min yan dagwai dagwai wadanda na isa dasu da mahaifinsu gaba daya, sai yadda nayi dasu" wannan lamari na daya daga cikin abinda yakara ma maah kwadayin samun tsatso daga bashir d'in. Tana gama waya da yaya mustafah ta sake cewa yanzu bari na kira kawata hajiya luba na fada mata itama ta tayani murna. Kasa hakuri Dr bash yayi ya katseta da cewa "maah wai waya gaya miki batool nada ciki" datatawa tayi daga niyyar kiran hajiya luba da tayi, dagowa tayi ta zuba mishi ido na wasu yan sakanni, kafin ta mai dakuwa tare da cewa "gidan ku bashir," zaro ido yayi yace "maah" ta katseshi da cewa "nace gidanku bashir, kana nufin kace karya nakeyi kenan ko me? Ka kalli yarinya yadda ta koma ɗanya sharaf kace wai bata da ciki, irin sakacin ku kenan yayan zamani, banda shashanci kana likita amma ka kasa gane matar ka nada juna biyu," nan fa maah ta shiga fada ta inda take shiga bata nan take fita ba, fada fah sosai. Ganin haka yasa Dr bash yace"kiyi hakuri maah nima sai yanzu da kikayi magana na kula da sawu alamomin cikin a tare da ita". Washe baki maah tayi dama, tsoranta kar bashir yace mata ba cikin shiyasa ta fitittike tana ta fada ba gaira ba sabar, tace"ah to to madallah yanzu naji batu," juyo da kallonta tayi kan batool tare da cewa "sannu kinji batula Allah ya raba lafiya" kara kasa da kai batool tayi, ganin ta takura sosai yasa Afrah ta mikar da ita tace"antyna mu shiga daga ciki ki fada min abinda babynmu ya ke so na girka mishi" don suma su Afrah ba'a barsu a baya ba murna sukeyi jin cewa matar big bro nada ciki, dan suma kamar maah dinne wajen son kananan yara, Suna wucewa maah ta kalli Dr bash tace "dan Allah bashir ka kulamin da yarinyar nan da abida ke cikinta, duk abida take son ji ko sha kanemo mata, kar ka barta ta dinga aiki masu wahala, saboda cikin karamine, aiki mai nauyi zai iya girgiza shi, sai kuma Abu na karshe bashir dan Allah kar kaje kata haike mata da yawa azo cikin nan ya zuɓe a rana in kayi so ɗaya ya isa shima a hankali, kana jina ko?" Bashir kunya ne gaba daya ya gama lullubeshi, ya riga yasan halin mahaifiyar nashi haka take magana ita, bata da boye boye komai fadi takeyi abinta gaba gaɗi, saidai kai data fadawa kaji kunya. Ranar a gidan batool ta wuni taga gata iya gata tuni ta saki jiki sosai a gidan dan samun guri harda wani shagwaba shagwaba take musu magana, sai dare suka baro gidan bayan maah ta kara tsare su na kusan 30minute tana sake jaddada ma bashir abubuwan da zai kiyaye. Bayan wucewar su ne maah ta bude ledan tsarabar da batool ta kawo mata, "wai wai wai cancadi, wainnan tsala tsalan zannuwa da lesuka haka masu mugun kyau haka"turaren ta dauko tana dubawa, zaro ido tayi ganin irin launikan turarukan, masu mugun kamshi da tsada wa'inda ba'a koina ake samun irinsu ba a Nigeria, ledar kayan ta dauka ta duba a ina akayi wannan kayataccen siyayar haka, tana gani murmushi ta saki tare da cewa a bayyane"dama nasan saidai can inba a R & U global enterprise ba a ina za'a samu irin wadannan kaya masu kyau haka duk fadin garin nan " A hanyar su ta komawa gida kuwa shiru yayi a motar, tunda suka taso ba Wanda yace da dan uwan shi kala, kowa da sake saken da yakeyi a zuciyar shi, Dr bashir gaba daya tausayin maah ne ya kamashi ganin yadda ta dauki son duniya ta daura ma cikin data kakaba musu, yanzu mai zai faru idan ta gane babu cikin nan, wai ranar yasan a kwai gwarama, fatan shi dai kafin lokacin su daidaita da batool, don yanzu baya tunanin za'a iya samun ciki nan kusa. Batool kam gaba daya jikinta yayi sanyi da wannan lamari, amma fa duk da haka ba wai ta saduda bane ita dai kawai tasan ta tausayawa maah, a fili ta tace Allah sarki maah na tausaya miki, kin dauki kwanda wahala kin daura wa kanki Wanda bansan ranar da zaki sauke shiba, dan nidai da ɗanki, ba haihuwa a tsakanin mu tunda bawai son juna mukeyi ba,................ Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen} Tallah!💖 Tallah!!💖 Tallah!!!💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 99 Kallon ta Dr bash yayi jin abinda take cewa, wai basa son juna, juyawa yayi yaci gaba da tukin shi, a haka har suka karaso gida, yana yin parking suka fito suka nufi cikin gidan, batool ɗakin barcin su ta wuce ta rage kayan jikinta kasancewar tayi wankan ta fess a gidan maah kafin su taso, kananan kaya ta sanya Riga karami mai kyau nashan iska, pink colour, da wando legis mai kamar jeans blue colour, tayi parking gashin kanta mai tarin yawa, tayi kyau sosai dass da ita kamar yar tsana babie, takalminta na yawo a ɗaki tàsako ta ɗauko wayarta ta dawo falo ta zauna tana kallon tv. Dr bash kam wanka ya shiga koda ya fito bata dakin, tsane jikinshi yayi , yayi shafe shafen shi wardrobe ya bude da nufin ya samu kayan shan iska ya saka shima, sai kuma idanshi ya sauka akan wani rantsasttsen suits da wani abokin karatun shi ya bashi kyuatar shi da zaiyi aure, mai mugun tsada ne dan kudin suits din zai ishi wani mara karfin zama babban attajiri a dare daya, kalan shi ash ne mai duhu, na cikin shi kuma fari, samun zuciyar shi yayi da sha'awar saka kayan dan yama batool kwalliya ya burgeta,ciro kayan yayi ya Sanya bayan ya saka inear Wear's a cikin, masha Allah kar kuso kuga Dr bash hmmm abun ba'a magana, koni kaina badan badan a kwai Abban ummeetarh ba ko hmmm bari dai nayi shiru kar batool ta jini, su rabi iyayen gulma saura kuma ki je ji gaya mata, dan nasan zaki aika. Tsayawa yayi a gaban mirror yana kare ma kanshi kallo, shi karan kanshi yasan ya haɗu iya haɗuwa, wani irin kayataccen murmushi ya sakar ma kanshi, cumb ya dauka ya kara gyara gashin kanshi ya canza mai style take ya fito kamar wani jarumi salman khan. Tana kwance a 3sitter tana kallon wani carton mai kyau da ake haskawa a mbc 3 batool ma badai son carton ba kamar Oum ummeetarh,bata gajiya da kallon aljanan roba, kamshin tsadaddan turaren shi ne ya mata sallama, a hankali ta lumshe idanunta tare da shakar kamshin har cikin zuciyar takejin kamshin na taɓawa. Cike da wani irin takun cikakkun maza, ya taho bai zame ko ina ba sai gabanta yayi wani irin tsayuwa mai kayatarwa tare da saka hannayenshi a aljihu, fuskar shi dauke da kayataccen murmushi. Jin kamshin na daɗa karuwa a hancinta, yasa ta bude idanunta daga lumshe sun da tayi, idanunta bai sauka a ko ina ba kuwa sai cikin nashi, yana tsaye a gabanta yana sakar mata wani irin tsadadden murmushi, zuciyarta ne ya shiga bugawa da wani irin sauri, ba karamin kyau ya mata ba , ji take zuciyarta na bata umarnin ta tashi ta rungume shi kawai, ko zata samu saukin yanayin da takeji game dashi a zuciyarta, amma dake jinin alhaji baba ce badai tauri kai ba. Tabe baki tayi tare da dauke kanta daga gareshi kamar bata ga komai ba, alhali kuwa taurin kanta ne kawai ya hanata rungumarsa. Zaro ido Dr bash yayi ganin irin kallon da tamai ta dauke kai, mamakin karfin hali da taurin zuciya irin na batool yakeyi, sarai ya daɗe da sanin itama ta kamu, a zuciyar shi yace, lallai yarinya man kaza nikuma yau nayi alkawarin sai naga karshen taurin kanki. Batool jin har yanzu yana tsaye a kanta bai matsa ba yasa ta dago kai ta harare shi tare da cewa "lafiya mallam nifa bana son tsayuwa a kai, mutane na basa son ana tsayamin a kai toh na gaya maka, inba so kake yanzu kaji shaka ba kuma to" kin tashi yayi a kannata ya tsaya yaga karshen rashin kunyar ta, tashi tayi zaune tace"dan allah wai bakaji mai nace bane, nace maka bana son ana tsayamin akai " Dr bash yace "naji abinda kikace sarai shakar da kikace zaki min nake jira tukunna" karamin tsaki taja tare da komawa ta kwanta tana dan cuno dan karamin bakinta tana gungumi kasa kasa, cikin son ya tsoratata ya miko hannu kamar zai kamo ta ai ba shiri ta dunkule wuri daya, dan bata manta da muguntar da ya mata da safe ba ya matse mata lips har yanzu zafi wurin ke mata. Komawa yayi kujeran dake facing Wanda take kai, zaro wayar shi yayi ya dan lallatsa kamar yayi dialing wani number, can kuma ya kara akunne, cikin kashe murya yace da dan karfi yadda ya tabbatar batool zataji "Amincin Allah ya tabbata a gareki yake saurauniyar birnin zuciyar Muhammad bashir" Kamar saukar guduma haka kalman ya daki zuciyarta, bata San sanda ta tashi ta zauna ba, idanun shi baya kanta amma sarai yana kallonta ta kasar ido, ci gaba yayi da cewa "lafiya kalau sweetheart ya karatu yasu mom, ya kuma fama da soyyaya ta," shiru yayi alamar ana mai magana ta daya bangaren, kwashewa yayi da wani irin dariya cike da farin ciki yace"wow naji daɗi sosai my teema, a she har haka kikayi kewata, gsky na yarda ba karamin sona kikeyi ba, nima kuma ina mutuwar kaunarki bana iya hada soyayarki data kowacce mace a zuciyata," dan dakatawa yayi kamar yana sauraren daya bangaren can kuma ya tabe baki tare da cewa"tana nan gama tanan tana jina, karki damu kanki da ita, ba wai sona takeyi ba, nima kuma ba wani sonta nakeyi ba kawai dai ba yadda na iya da itane" shiru ya danyi kafin yace "wlh baby yadda kikayi kewata haka nima nayi kewarki sosai, yanzu dai albirinki, ki bani nan da 20 minute gani nan zuwa gida yanzu nan" shiru yayi can kuma ya kwashe da dariya yana cewa"baby duk murnan zuwanane haka, gsky naji dadi nasan kuma kina ji dani, yanzu ki tashi kije ki shirya min kwalliya ta musamman, nima gani nan zuwa na caba miki ado irin Wanda nasan yana matukar burgeki" daka tawa ya danyi, sannan yace "OK baby bye sai na iso I luv 2 " ya fada tare da ba wayar wata irin kiss mai sauti muuuaaahh💋, kashe kiran yayi tare da rungume wayar a kirjinshi ya lumshe idanu yana sauke ajiyar zuciya. Wani irin huci yaji a kanshi ba kakautawa, dagowan da zaiyi yaga batool a gaban shi rike da kwankwaso, fuskarta murtuk kamar an aiko mata da saƙon mutuwa, idanunta sunyi ja tsabar wutar masifar kishin daya kunnu a zuciyarta lokaci guda, hankalinta ba karamin tashi yayi ba dama duk wannan uban kwalliyar da yaci ma wannan yar iskan fatiman yayi, aiko dai akwai bala'i yau a gidan nan, ko sama da kasa zasu hade yau bazai fita agidan nan ba saidai duk bura'uban da za'ayi ayi ta yau. Murmushi ya sakar mata yana mike wa tsaye, baya ya danja yana dudduba jikinshi yana kakkaɓe kakkaɓe, can kuma ya dago ya kalleta cike da zumudi yace"batool pls tayani duddubawa ina da inane basuyi ba" yana magana yana dan jujjuyawa a gabanta, wani kululun bakin ciki ne ya tokare ma batool makoshi, ji tayi kamar ta lailayo ashar ta kunduma mai, amma ba hali, jin shiru bata ce komai ba yasa ya dago ya kalleta, yi yayi kamar baisan halin da take ciki ba, yace mena miki kuma kike harara na, daga naiman taimako,ki duba min inda baiyi ba na gyara dan na birge baby teemah shine zaki kama harara na ,in bazakiyi ba kawai kice bashir bazan duba ba, ba sai kin harareni ba"cikin tsiwa tace "wai kai mallam me kake nufi naga kamar shirin fita kakeyi" amsa mata yayi da "eh wlh sauri ma nake yi zanje zance ne wajen baby teemah" tace "kana nufin a cikin tsohon Daren nan zaka fita ka barni a gida ni daya kamar wata tsohuwar mayya, to wlh baka isa ba babu inda zakaje ka barni ni daya" dariya ke cinshi,ganin gaba daya yadda hankalin ta ya tashi daga ji yace zaije zance, dakewa yayi yace "zan fita zanje gurin masoyiyata, mai son farin ciki na wacce zata iya haihuwa dani ta samar ma mahaifiya ta farin ciki, idan kin isa kin cika sunan ki batool ki hanani fita" yana gaman fadan haka ya juya ya kama tafiya, a guje batool ta biyo bayan shi, ganin haka yasa ya fice da gudu daga falon yayi waje binshi tayi saidai yana zuwa parking lot ya lalubi makullin motar yaji wayam, sai lokacin ya tuna yana aljihun kayan daya cire, dafe goshin shi yayi tare da cewa "kash, amma banji dad'i ba wlh" dai dai lokacin batool ta iso da gudu saida ya bari ta miko hannu zata rike mai riga, ya wala ta yabi ta gefenta ya kara kwasa da gudu, zuwa ciki zai dauko car key, bata yi kasa a gwuiwa ba ta rufa mai baya, koda ta iso falon ya haura sama,da sauri ta maida kofar ta rufe da key,tare da zare makullin, rasa inda zata boye tayi jin takun shi yana sakko yasa ta Saka key din a rigarta ta sama, ta boye shi a tsakanin boobs dinta, saurin tashi tayi a wajen ta koma kan kujera ta zauna. Saukowa yayi hannunshi dauke da makullin mota, a ranshi yana mamakin mai ya hanata biyoshi har sama, mamkinshi ne ya dadu ganin ta zaune abinta tana kallon tv ko kallonshi batayi ba, har karkada key yayi irin wai ko bata San ya sakko bane, tanaji tayi kunnen uwar shegu, dage kafala yayi alamar ko ajikina d'in nan, ya nufi kofa abinshi zai fice, saidai yana tura kofar yaji shi a garkame, kuma ba key a jiki. Juyowa yayi ya kalleta, still idanunta nakan tv bata kalli inda yake ba, cikin dan muryar fada fada yace "kee ina key din kofar nan yake" inda kukasan da dutse yayi magana, ya sake cewa "wai baki jina ne nace ina key, ki bani makulki zan fita" share shi tayi yanzuma bata tanka ba, yace "OK wato ga ɗan iska na magana kin kyale ni ko" Dawowa yayi fa fara dube dube a falon , lungu da sako har su kasan kujera , har cikin flower vase, harda su kasan center carpet, ba key ba dalilin shi , batool na zaune duk abinda yakeyi tana kallon shi ta kasan idanu, duk inda yasan zata iya saka key dinnan ya duba a falon nan bai gani ba, take zuciyar shi ya bashi key dinnan na jikinta ta, dagowa yayi ya kalleta daidai tana gyara zaman rigarta da kyau, itama cikin sa'a lokacin ta kalleshi, yace "batool ina key" cikin tsiwa yace"ni ban dauka key ba, ka dameni da tambaya,ko ka bani ajiya ne wai" kara maimaita mata tambayar yayi "nace ina key yake" ya fada yana nufo ta , ganin haka yasa tayi wuff ta mike, hakan yaba key din dake jikinta daman yin kara kasancewar makullin ba daya bane a hade suke wajen guda hudu, tsab yaji karan kuma yaji daga ina karan ya fito, nufota yayi gadan gadan, aiko ganin haka yasa ta juya a sittin ta yanka da gudu, binta yayi taku biyu ya cimmata ya damko ta. Mutsu mutsu ta shigayi tana neman kwatan kanta, cikin tsiwa da rashin kunya take cewa "wlh nidai ka sakeni babu wani makullin Dana dauka ka sakeni ka sakeni " bai saurari hargaginta ba ya hade hannayenta wuri daya ya rike, ya manna bayanta da kirjinshi ya matseta da karfi yanda ko motsi bata iyawa. Daya hannunshi yasa ya shiga cajeta tun daga kasa, yana labubeta shine hannunshi har cikin pant dinta yana neman key, bai samu anan ba hakan yasa ya dawo da hannunshi sama, saka hannu shi yayi a cikin rigarta ta sama, wani shork ne ya ziyarcesu a tare daga shi har ita, lumshe idanu yayi jin yanda boobs dinta keda wani irin laushi da dadin tabawa, lalube ya shiga yi yana matse mata boobs da sunan yana neman keys sarai yaji key din a wajen amma haka kawai yaji ya kasa Ciro hannun shi daga wurin, luf batool tayi tana jin wani irin yanayin da bata tsintar kanta a ciki ba, na ziyartar ta. Dr bash kam mantawa yayi ma wai key yaje dauka, idanunshi alumshe, yake ya daddage sai lagudeta yake yi, cika hannunshi yayi da guda daya kafin cikin yanayin fitar senses ya matsa da dan karfi, jin zafi kamar daga sama yasa batool fashewa da kuka, kafin ta daddagewa ta kwalla ihun kiran mummy "wayyo Allah na mummy na, zai fasa min" wannan sound din ne ya dawo da Dr bash hayyacinsa, da sauri ya sake mata ya zare key ɗin tare da sakinta, idanunshi har sunyi jajur tsabar fitina, baya ta matsa idanta dagaje dagaje da hawaye ta watsa mishi wani mugun harara, tare da cewa "Allah ya isan min mugu kawai ɗan iska" zaro ido bash yayi, jin abinda tace harda su mugu dan iska, ziciyar shi ce ta ba shi shawara da cewa ya kamata dai yau ka fidda wannan rainin dake tsakanin ka da yarinyar nan ka nuna mata kwaruru ba tsarar wake bane, cikin yanayin da yake ciki na tsantsar bukatuwa yace yana nuna kirjinshi "ni kike kira mugu dan iska dan na tabaki, da sadakina akanki kike kira na da dan iska ko?, aiko yau zakiga iskanci zahiran muararan, zan nuna mini ni cikakken dan iska ne akanki" yana maganar yana balle maballan riga yana nufo ta, ja da baya ta shiga yi dan sosai ta tsorata da wannan yanayin nashi, duk jijiyoyin kanshi da jikin shi sun mimmke, ƙule ta yayi a bango yasa hannu ya dago fuskarta baiyi wata wata ba ya hade bakinsu waje daya, kissing dinta yake yi a yunwace, yadda yake tsotsan lips dinta kamar wani tsohon maye, batool kam sai zare idanu takeyi dan ta tsorata iya tsorata, saida yayi mai isarsa sannan ya sureta sai tsakiyar bed dinsu. Ashe wargi ma wuri ya samu, batool ko uffan ta kasa Ce masa, shegen bakin nan tuni ya mutu muruss tunkan lamura suyi nisa, sai kerma da jikinta keyi, kamar maijin sanyi, ohoo shi baima kulaba, burin shi kawai ya ida nufin shi yau akanta, ya wanke mata wannan rashin kunyar dake dankare a brain dinta. Fiffige kayan jikinta ya shiga yi yana wurgawa duk inda ya samu, saida ya maida ta haihuwar uwarta, sannan ya shiga bin ko ina na jikinta da sumba, ranar babu inda Dr bash bai tsotsa ba a jikin batool, ɗama yanada haushin ta sosai ba karamin tara ta yayi ba. Kamin wani ɗan lokacin batool ita da gunki basu da babbanci ko yatsarta bata iya dagawa, banda kerma babu abinda takeyi, tuni ta dade da barin duniyar mu, wani irin dad'i take ji yana ratsa duk wani hudon gashi dake jikinta idanunta alumshe sai karbar zazzafan romance d'in da yake mata takeyi, bata dawo hayyacinta ba saida taji wani irin mugun zafi ya ziyarci ƙasanta, kwallah wani wahalallan kara tayi, kafin tasa hannu ta shiga ture shi, ganin bazai turu mata ba yasa ta shiga kai kulki da yakushi, ta ko,ina, amma a banza dan ko gezau baiyiba. Dr bai sarara mata ba saida ya tabbatar ya maidata cikakkiyar mace, a wannan dare.............. Kai wlh batool baki jin magana ki bada kai da lalama, a biki a sannu kamar ko wacce amarya kinki gashi kinja an miki fyade, nidai Allah yasa ma ba tear😔 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen} Tallah!💖 Tallah!!💖 Tallah!!!💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 100 Kwanci ta tashi har yau Aslam da Asmah suna neman kwashe wata uku da aure, amma babu abinda ya canza a yanayin zaman su, Aslam duk abinda zaiyi dan ya burge Asmah yi yake da Wanda ta saka shi da wanda bata saka shiba, bangaren girki kuwa zuwa yanzu ko ita baza ta nuna mai komai ba, duk wani nau'in abincin da yasan tana so ya gama kware wa a iya girkashi. Zuwa yanzu Asmah ta dan fara sake mai fuska saidai har zuwa lokacin kamal nanan a ranta, amma ta rage jin shi a ranta ba kamar da ba farko farkon aurensu, takan zauna suyi hira da Aslam, duk da rabin hirar shi keyi, takanyi mamakin yanda ya Aslam ya koma mai surutu haka lokaci guda, kodai dama yana da surutun girman kai ne ke hana shi yi, yata wani ɗaɗɗaure musu fuska, yana musu muzurai. Allah sarki abinda Asmah bata sani ba, Aslam bashi da surutu soyyaya ce ta mai kamun kazar kuku, ita kaɗai yake iya sake baki yama magana sosai da sosai, ita kaɗai ne yake iya sake ma fuska yayta mata murmushi kamar wani gaula, ita kaɗai ne yake iya ɓare baki yayta dariya a gabanta kamar sabon kamu, a gabanta yakan kasa controlling kanshi, yakan rasa nutsuwar shi idan yana tare da ita, wata irin soyyaya yake mata kamar wacce ta asirce shi, kuma ba ɗaya kanwar biyu, kamun Allah ne kawai daya fi na mutum. Yau data kama ranar Friday, misalin karfe 9am Asmah ne zaune a bakin bed dinta ta caba kwalliyar ta cikin kananan kaya Riga da skirt yan kanti, skirt d'in street ne me tsagu ta baya black colour, daya matseta tsam ya fito mata da shape sosai, rigarta kuma yellow ne mai shegen kyau, dan Cass dashi, kanta kuwa ta nada wani irin turban mai kyau na yayi, cikin irin wanda take da videos dinsu a wayarta, haka takeyi kullum aikinta kenan ta caba ado mai kyau da tsari abinta, bata aikin komai daga kwanciya sai kwanciya, ko plate sai taga daman daukewa idan taci abinci, Allah sarki Aslam bawan Allah haka zaita binta da kallo yana lasar lips, gashi ko hannunta bashi da zarran taɓawa Wannan ne karo na biyar data dago kai ta dubi agogon dake manne a Wall din dakin, fuskar ta cike take matukar da damuwa, a fili ta furta "wai mai ke faruwa ne yau, har karfe tara banji motsin shiba, anya kuwa lafiya hankalina ya kasa kwanciya ga shi gabana sai faduwa yake," daga hannunta tayi sama tace "ya rabbi kasa lafiya kalau" komawa tayi ta kwanta ta rintse ido, a zuciyarta tace bari na dan kara bashi lokaci na gani ko yau bacci ne ya kwashe har zuwa wannan lokacin bai nemeni ba,can kuma tace to kodai bai samu yimin Masan da mukayi zai min da safe bane yasa yaki nemana har yanzu, haka dai tayita sake sakenta ita kadai duk zuciyarta ba dadi. Allah sarki Aslam jiki da jini, jiya har gurin karfe goman dare suna tare da Asmah a falo suna kallo, lafiyar shi qalau, ita tace ta fara gajiya da kallon ta mike, ganin haka yasa ya kalleta yace"mrs Asmah kardai har kin tashi" tana mika da hamma tace "eh wlh bacci nakeji," tashi yayi yana cewa "OK ba damuwa Allah ya tashe mu lafiya, muje na rakaki dakin ki " bata musa ba ta shiga gaba yana bayanta har kofar dakin ta, har ta kama handle kofar zata shige ta tsinci muryar shi yana cewa "Am mrs Asmah nace da safe mai zan girka miki na breakfast" murmushi ta saki ba tare data juyo ba tace "umm masa da miyar taushe" dan zuwa yanzu Aslam ya kware a wurin iya soya masa, badan kartayi karyaba da sai tace tunda take bata taba cin masa mai dadin nashi ba. Dariya ya kwashe dashi yace "ai dama saida na ayyana a zuciyata yanzu zaki ce masa da miyar taushe,to karki damu gobe insha Allah idan muna da rai da lafiya, zaki farka barci ne ki tarad da masan ki yayi ready" juyowa tayi ta kalleshi, tsintar kanta tayi da sakar mai murmushi tare da cewa "thanks, gud 9t" shima murmushin ya mayar mata da martani tare da cewa "bye kiyi mafalkina kinji" tafin hannun ya kai saitin bakin shi ya sumbata muuaah💋 sannan ya hura mata. Da sauri yasa kai ya wuce, murmushi tayi, sannan ta juya ta shige dakinta cike da kewar shi, haka kawai takeji kamar kar su rabu. Aslam falo ya koma ya kashe tv da sauran abubuwan daya kamata a kashe idan za'a kwanta bacci, daganan kuma dakin shi ya nufa alwalan kwanciya bacci yayi ya shirya cikin kayan baccin shi, kashe wuta yayi ya haye godo yaja duvet ya gudundune bayan yayi adduan baccin ya shafe jikin shi. Kewar tane yaji ya lullubeshi kusan kullum dama haka yake fama indai suka rabu yazo kwanciya bacci, pillow ya dauka ya rungume kamar pillow ne Asmah, daya hannun kuma ya lalubi wayar shi ya dauko hotunan ta da yake yawan daukarta ba tare da ta Sani ba, ya shiga kallo yanata sakin murmushi abin tausayi, shifa indai zai zauna da ita a haka yana ganin ta kullum yana mata hidima ya isheshi rayuwar duniya, tunda ya sameta har yau ciwon shi bai sake tashi ba , kai daker ma idan bai rabu da ciwon kwata kwata ba don dama Dr James yace idan dai ya samu abinda yake so zai iya rabuwa da ciwon baki daya. Haka yana kallon hotunan ta har barci ya rinjaye shi, kifa wayar yayi akan kirjinshi ba tare da ya fita daga wurin hotunan ba. Allah mai girma da buwaya cikin wannan daran ya saukar ma Aslam da wani irin zazzafan fever, ya kwanta lau abinshi, amma ya farka da ciwo, haka yata fama cikin daren nan, sai makyarkyatan sanyi yakeyi, ga jikinshi ya dau zafi, bai iya daga koda dan yatsan shi, haka yata fama har asuba ko sallah bai iya tashi yayi ba, sai bayan asuba wani wahalallan barci ya kwashe, hatta numfashin da yake fitar wa na hucin zafi ne, bai farka ba har wurin karfe goma safe. Asmah tana cen cikin damuwar rashin ganin Aslam, tun bakwai da wani abu take ta saka ran ganin shi kamar yadda ya saba, saidai shiru har gurin takwas duk bata damu ba, ganin tara yayi yasa ta fara shan jinin jikinta ta shiga damuwa da tunanin anya lafiya kuwa, ta tashi tayi wanka ta shirya ta share dakin ta, ta koma ta kwanta har zuwa lokacin shiru, bacci ne yadan kwashe ta adan kishingiɗar da tayi, ta kishingiɗa ne da damuwan rashin ganin Aslam, batasan yadda akayi bacci ya kwashe ta ba, cikin wannan dan baccin da baifi na 30minutes ba tayi mafarkin Aslam yana cikin mawuyacin hali gashi nan kudundune ko yatsar shi bai iya dagawa, a firgice ta farka ta shiga jero addu'o'i da duk yazo bakinta, durowa tayi daga kan gadonta da sauri da niyyar taje ta duba shi, hankalin ta zaifi kwanciya, zuciyar ta ce ta shiga ce mata meye haka kikeyi ne wai kan Aslam duk kinbi kin ruda kanki, kin saka damuwar shi a gaba har kina wani mafarkin shi, kilama babu abinda ya same shi kin saka damuwar shi a rai har yana sakaki mafarkai barkatai, komawa tayi ta zauna jiki a sanyaye. Can dai ta kasa hakura ta mike ta fice daga dakin da sauri bata tsaya ta biyem.a wasu wasin zuciyarta ba, falo ta fara dubawa bashi nan daga nan ta nufi kitchen babu ma alamar wani ya shiga kitchen din dan yana tsab yadda ta barshi jiya, dafe goshin ta tayi a fili ta furta "ina Mr Aslam ya shiga ne wai, to kodai ya fita ne, bai dawo ba" nan tayi na'am da cewa fita yayi kila, kitchen ta shiga ta Samar ma kanta abin tabawa, gani tayi bazata iya zaman falon ba hakan yasa ta hada abincin ta a tray ta dauka ta nufi hanyar dakin ta, tazo gifta daidai wani bedroom Wanda sai an wuce shi za'a isa nata taji kamar kakarin amai, bata San takamaimai wani daki Aslam yake kwana ba a gidan tunda ba shiga lamarin shi takeyi ba shike shiga nata. Kara kasa kunne tayi dan ta tabbatar kakarin ne kokuwa kunnen ta ne ya jiyo mata karya, still ta karajin Wanda yafi na dazu karfi ma, da sauri ta tura kofar bedroom din da tray dake hannunta, dakin da duhu sosai laluabar wuri tayi ta ajiye tray dake hannunta, sannan ta kuma lalubar makunnin wuta ta kunna,take haske ya gauraye dakin. Idanunta ne ya sauka a kanshi, daga kwancen da yake yadan yi kokari ya karkato da kanshi gefen bed din yanata kelaya amai a kasa, zaro idanu tayi tana furta Kalmar innalillahi wainnailaihi rajiun, kafin kuma ta kwasa da gudu ta karasa gareshi batayi wata wata ba ta haura kan bed d'in ta talloboshi jikinta, nan yaci gaba da kelaya a man ajikinsu ita dashi gaba daya,a mai yakeyi sosai tun yanayin na abincin dake cikin shi har ya kamo kakarin kawai yakeyi ba komai a cikin. Da'ker suka samu kakarin ya tsagaita, sai lokacin ma ta kula da yadda jikinshi ya dau zafi zau, hankalin ta yakai matukar kololuwar tashi, yanzu ya zatayi wani irin taimakon gaggawa ya kamata ta bashi. Aslam kam jinshi a jikin mutum saiya kara narkewa gaba daya ya sake mata dukkan nauyin shi dukda ba cikin haiyacinsa yake ba, lallabawa tayi da'ker ta samu ta zare jikinta daga nashi ta ture shi gefe, saukowa tayi ta fita daga dakin jim kadan ta dawo ta canja kayan jikin ta daya baci,hannunta dauke da kayan share share dangin su mopa da tsintsiya, aman dake kasa ta fara kwashewa ta gyara wurin tsab tayi mopping, kan gadon ta koma ta tattare bargon ta nannadeshi tayi toilet dashi ta sakashi a cikin washing machine, ta kunna dawowa tayi tana tuananin ta ina zata fara raba shi da kayan jikinshi shi, daya baci da a mai, tsayawa tayi na kusan minti biyu tana sake sake kafin kuma daga bisani tayi huɓɓasa ta haura kan gadon, yana nan kwance rigingine idanunshi a lumshe yana dauke wani irin nunfashin wahala, ba bacci yake yi ba idanun shi biyu amma baya cikin haiyacinsa. A hankali ta mika hannunta ta shiga balle maballan rigar baccin shi ta gaba, take faffadan kirjin shi mai dauke da kyakkyawan kwantaccen suma ya bayyana, da sauri ta dauke idanunta daga kallon kirginshi, saidai kuma cikin rashin sa'a idanunta ya kuma sauka a kan cikin shi, wandonshi yadan ja kasa hakan yasa har saman marar shi ta gani, rintse idanunta ta tayi tana maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun, take jikinta ya fara dan kerma, a haka idanu a rintse ta samu ta gama cire mai rigar gaba daya, wandon dama bai baci ba saboda duvet din daya lullubeshi shi. Har zuwa lokacin ba abinda ya ragu daga zazzafan fever dake damun shi, tsayawa tayi akanshi idanunta sun cika da kwallah, yanzu meya kamata tamai dan ya samu sauki take zuciyarta ta bata ansa da ki nemo Dr yazo ya duba shi mana, sai lokacin ta tunada abinda ya kamata tayi kenan tun kafin ta tsaya share a mai, tunani ta shigayi yanzu wani likita zata kira ita bata San wani likita ba, tana cikin wannan sake saken ne idanunta ya sauka akan handset dinshi da rabin shi ke karkashin Aslam ma'ana ya kwanta akan wayar sobada dama wayar nakan kirjinshi barci ya kwashe shi. Janyo wayar tayi cikin sa'a babu security ko daya, yana nan a yadda yake wato a wajen gallery, da hoton ta ta fara cin karo cike da mamakin take bin hoton da kallo, tabas idan ba idanunta sun mata karya bane hotone da aka daukeshi anan gidan, ajiye mamakin ta tayi a gefe tuna abida ke gabanta, ta fita daga gallery din ta shiga contact, letter D ta danna take sunan Dr James ya bayyana a farko, dan haka bata tsaya duba sauran lambobin ba ta antaya mai kira. Dr James a na ɗaga wayar yace "hi Mr Aslam" da sauri Asmah ta katseshi da cewa "ba shi bane Dr matar shi ne" Dr James yace "oh madam, lafiya kuwa meke faruwa ne" dan tun a muryarta ya fahimci akwai matsala Asmah ta bashi amsa da cewa"Dr Mr Aslam ne baida lafiya mun tashi da safe na same shi cikin matasanancin fever" Dr yace"Jesus! yanzu kuna ina ne" Asmah tace "gidan shi dake London road," Dr yace"OK ganin nan zuwa yanzu ki kwantar da hankalin ki madam, komai zai daidaita". Bayan sun gama waya komawa tayi ta tsuguna a bakin bed din tana karema kyakkyawan fuskar shi kallo cike da tsantsar tausaya, idanunta tuni sun fara zubar kwallah ba tare da ta sani ba. Tana a haka taji diran motar Dr a farfajiyar gidan, da sauri ta nufi falo tana isowa yana danna doorbell, har tana hadawa da gudu gudu ta karasa ta bude mai kofa, kwata kwata ta manta da sigar dake jikinta saida taga Dr na binta da kallo sama da kasa, yasa ta sha jinin jikinta, daurewa tayi ta nuna mai dakin da Aslam yake bayan sun gaisa,ita bata shiga ba sai ta zarce dakinta ta zumbulo dogon hijabi ta dawo, koda ta shigo tuni Dr James ya dukufa akan Aslam yana checking dinshi, neman guri tayi nesa dasu kadan ta tsaya. Minti ashirin Dr James ya dauka kafin ya dago ya kalleta yace "madam karki damu fever ce kawai irin wanda stress ke haifarwa, yanzu zan daura mai drip na bashi injection da magunguna zazzabin zai sauka" gyada mai kai kawai tayi. Cikin ten minutes ya gama aiwatar da duk abinda yace, magungunan ya dauko ya mikawa Asmah , tare da gaya mata yanda zai dinga sha, nuna mata yadda akeyi cire drip yayi, yace idan ruwan ya kare ta cire mai , ya samu ruwan dumi yayi wanka yasha ko tea ne sannan yasa magani, insha Allah zaiji sauki. Godiya ta shiga yiwa Dr dake ta faman tartare kayan aikinshi a jaka zai wuce. Bayan tafiyar Dr James zama tayi ta rafka tagumi hannu bibbiyu ta saka fuskar Aslam daya koma bacci a gaba tana kallo, tuni tama manta da breakfast dinta ko yunwar ma bata ji, a haka har ruwan ya kare, daidai nan kuma Aslam ya farka wannan karan yadan fara dawowa haiyacinsa saboda alluran da Dr yamai masu kyau ne sosai suna matukar yin aiki cikin kankanin lokaci. Da sauri ta matsa kusa dashi tana mishi sannu, juyowa yayi ya kalleta duk da halin ciwon da yake ciki hakan bai hanashi sakar mata murmushi ba, cikin jin daɗin ya fara samun sauki tunda gashi har yana murmushi tace"alhmdllh sannu Mr Aslam bari na hada maka ruwan dumi kayi wanka kamar yadda Dr yace" bata jira amsarshi ba ta fada toilet ta hada mai ruwan wankan, fitowa tayi , yana kwance yadda ta barshi idanunshi akan kofar toilet din , don tunda ya rakata da kallo ta shige, bai dauke idanunshi a wurin ba fitowa tayi still ya binta da kallo, karasowa tayi gabanshi tana cewa "na hada maka ruwan ka daure ka tashi kaje kayi wankan" shiru taji ba'a amsata ba hakan yasa ta kalle shi, girgiza mata kai yayi yana murmushi ta gane yana nufin bazai iya tashi bane, gani tayi ya miko mata hannu alamarta taimake shi ya tashi, mika hannu tayi ta kamo nashi tanaja yunkurawa daya sai gata a jikinshi kane kane ta fado, baida lafiya jikinshi ya sake ya mata nauyi baza ta iya dagashi ba, shi kuma yasa karfin shi ya tashi jinta rike shi baisan ba karfi kirki gareta ba, sai gashi ta biyo shi. Dago da kai tayi tana zare ido, idnunsu ya sarke dana juna,kallon juna sukayi na kusan 30sec, kafin da sauri ta yunkura ta dire kasa. Daurewa yayi ya daddafa katakon gadon ya mike da'ker yana layi jiki ba kwari, yana mikewa kuwa jiri kwashe shi zai fadi tayi azaman taroshi tasa dukkanin ɗan karfinta ta rirrike shi a haka ta taimaka mai har suka shiga toilet, zaunar dashi tayi akan abin da ake zama a toilet d'in juyawa tayi zata fita karaf taji an riko hannunta, da sauri ta juyo ta kalle shi, marairaice fuska yayi kafin a hankali ya bude bakin shi yace"pls mrs Asmah ki taimake ni kimin wankan" wani irin zaro😳idanu Asmah tayi cike da tashin hankali..... Tabdijam lallai Asmah kya zaro ido koni dake cikin Celine ina dauko rahoto saida na zaro ido😳balle ke Oum ummeetarh 07041130088 .. Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen} 💖Tallah!💖 Tallah!!💖 💖Tallah!!!💖 💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 101 Ganin ta tsaya kallonshi tana zare ido yasa ya marairaice fuska tare da cewa"pls mrs Asmah ki taimaka min" ganin zai karyar mata da zuciya yasa ta fizge hannunta da sauri ta fice daga toilet d'in, ko hauka takeyi ita ta ina zata iya mai wanka katoto dashi, yanzu shi ko kunya sai ya iya tubewa zirr a gabanta, lallai maza sai abarsu, yoo shi baisan riga ma da babu ajikin shi daure kawai tayi ba, tunda ta cire mai Riga har yanzu bata yarda ta sake kallon shi ba, kunya takeji balle kuma ace ya cire harda wondo. Saida ya kwashe kusan 15 minutes a zaune yadda ta barshi kafin ya lallaba, ya mike da'ker ya fara wankan, bayan ya gama lallabawa yayi, yayi brush da alwala da daddafa bango ya samu ya fito daure da tawul, bata dakin dan haka ya samu ya lallaba ya zauna bakin bed, Asmah kam tana dakin tunda ta barshi a toilet, jin motsin zai fito ne yasa tayi sauri ta fice a dakin dan tasan ba kunya ya ishe shi ba kar yazo ya fito mata haka zirr, dining ta nufa inda kayan tea suke, nan ta samu Kofi ta hada mishi tea mai kauri da zafi zafin shi, saida ta kwashe kusan 15 minutes tasan dai duk tsiya zuwa wannan lokacin ya gama shiri ya saka kaya,daukan dan karamin tiran data daura kofin tea d'in tayi ta nufi dakin da sallama a bakin ta ta tura kofan dakin, yana nan zaune a bakin bed d'in tunda ya fito toilet ya zauna bai motsa a wurin ba jira yake tazo ta taimakeshi ta dauko mai kaya ya saka yayi sallah, Kallo daya tamai tayi saurin dauke kai daga kallonshi gabanta na faduwa, lallabawa tayi ta duka kusa da kafar shi ta ajiye mai kofin tea d'in, tace "ga tea nan na hada maka kasha, sai kasha magunguna" mikewa tayi tana niyar barin dakin, dan gaba daya jikinta rawa yake yi, ganin shi zaune daga shi sai tawul,har takai bakin kofa ta tsinci muryar shi yana cewa"pls mrs Asmah karki barni, kizo ki taimakeni ki saka min kaya nayi sallah" daskarewa tayi a gurin bayan ta zaro duka idanuwanta waje,kamar wacce aka dannawa pause, a zuciyarta tace innalillahi mutumin nan na neman ya kasheni da sauran kwanaki a duniya, ta kasa juyowa tayi abinda ya sakata ta kuma kasa yin gaba, har kusan 3minutes a haka ganin da yayi bata da alamar yin gaba ko baya yasa ya kara cewa "pls to ko ciromin kayan kizo kiyi daga sif" jin haka yasa ta daure ta juyo bata kalli inda yake ba ta wuce gaban wardrobe din tace "wani irin kaya zan ciro maka" yace "kowanne" jin haka yasa ta duba side din da jallabiyas suke ta ciro mai wani sabo mara nauyi, ta duba gurin kana nan kayan shi ta dauko mai singlet da boxer ta hado mai dasu. Mikamai tayi ba tare da kalle shi ba, amsa yayi da gangan ya hada harda hannunta ya riko, a zuwan bai sani ba,da sauri ta fisge hannunta,kallon yayi yace "oh sorry" cewa tayi "kasa kayan kasha tea din bari na baka waje" yace "ki tsaya pls karki wuce" kamar zata ce wani sai kuma idanunshi dake kanta suka mata kaifi da yawa, bata ce komai ba ta samu guri a gefe ta zauna ta juya mai baya, daga zaunen da yake ya saka boxer, singlet d'in ya dauka zaisa amma yadda zai daga hannu ma wahala yake bashi, yayi yayi ha saka rigar ya kasa, ita kuwa Asmah tunda ta juya mai baya bata juyo ba balle tasan wainar da yake toyawa, ganin bata da niyar juyowa balle taga halin da yake ciki ta taimaka mai yasa ya saki wani kara mai sauti"ahhhccchh" a firgice ta juyo ta kalleshi gani tayi ya dafe kirjinshi yana yamutsa fuska kamar kirjin na mishi ciwo, bata san sanda ta isa gabanshi ta rirriko shi ba, sai faman sannu take jera mai ba kakautawa,ganin haka tuni ya kara narkewa ya sake mata nauyin shi duka a jiki, tuni tama manta da kunyar da takeji na ganin shi ba riga, cikin yanayin zafin ciwo yake cewa"rigana, rigana ki sakamun Rigana" jiki na rawa ta dauki singlet din ta saka mishi, duk rabin jikinshi na najikinta, da'ker take iya ture shi taja mai singlet din da kyau, a haka ta saka mishi har jallabiyan ma, tanayi tana "sannu na saka maka , sannu sannu" gyada kai yayi yana yamutsa fuska, ya daddafa gado ya mike yana layi, tashi tayi zata rikoshi yace "shimfida min pray mat, nayi sallah" da sauri ta dauka ta shimfida mai, nan ya kabbara sallan a tsaye ya fara amma karshe a zaune ya karkare, dan da gaske yana jin jiki, dan ma yana da dauriya sosai ne. Tana gani ya idar ta dauki kofin shayin ta mika mai, kin amsa yayi ya girgiza mata kai alamar bazai sha ba, marairaicewa tayi tace"pls ka karba kasha ko kadan ne sai ka samu ka sha magani" da gangan yaki karba so yake ya sakata ta bashi a baki, Asmah ta kada ta raya amma yaki karba, saida yaga tana niyyar fashe mai da kuka ya bude baki da'ker yace"to kiyi hakaru karkiyi kuka zan karba, amma bazan iya sha da kaina ba, saidai in zaki taimakeni ki bani a baki" dake a matse take da yasha yasa ta amince zata bashi d'in. Gyara zama tayi a gaban shi tana dibo tea d'in da cokali tana kaiwa bakin shi, yana sha yana yamutsa fuska kamar baiso, dan samun guri ma, idan ta debo wani bin ma bai karba saiya gauce fuska gefe, kamar wani dan karamin baby, haka zata ta bin shi da cokalin duk inda ya juya fuska, sai ya gama wala ta ya amsa, a haka ya shanye tea tass ba tare da ya Sani ba, sai gani yayi ta ajiye kofin, kallon cikin kofin yayi yaga wayam, saida yadan zaro ido yana mamakin yadda akayi ya shanye tulin shayin nan shida baida lafiya, ko lafiyar shi kalau ma baya wani shan tea da yawa. Tana lura da yadda ya kalli kofin yadan zaro ido hakan yasa tace "ko a karo maka ne" da sauri ya girgiza kai alamar A'a, tashi tayi ta fita da cup din can kuma sai gata ta dawo da goran ruwa mara sanyi da wani cup, komawa tayi mazaunin ta nada ta bude ledar maganin ta ballo mai duka Wanda zaisha a lokacin ta mika mai ba musu ya karba ruwa ta tsiyaya mai a cup ta mika mai, karba yayi yasha maganin, yana yamutsa fuska. Cup d'in ta dauka ta mayar kitchen ta dawo, kallonta yayi ya nuna mata breakfast dinta da ta ajiye tun dazu har ya sandare ya huce, sai lokacin ta tuna bata karya ba, dauka tayi takai kitchen ta ajiye dan bata jin zata iya cin wani abinci a halin da take ciki a yanzu. Tana fita ya tashi da'ker ya lallaba ya koma kan bed ya kwanta, baifi 10minutes da kwanciya ba bacci ya kwashe shi, koda Asmah ta dawo dakin ta samu yayi bacci, fitowa tayi a wuce dakin ta ta dan kwanta itama bata dade da kwanciya ba bacci ya kwashe ta, ba ita ta farka ba sai karfe 2 da gudu ta duro daga gadon tana salati tunawa da Aslam da tayi watakila ya tashi tun tuni yana jin yunwa, ga kuma maganin shi, dakin shi ta nufa har zuwa wannan lokacin bai farka ba , ajiyar zuciya ta sauke ta fice daga dakin, kasancewar ba sallah zatayi ba yasa direct kitchen ta nufa, tunani ta shigayi na me zata girka masa mai sauki a matsayinsa na mara lafiya, haka ta tsaya ta saka wancen ta kwance wancen, karshe dai ta yanke shawaran dafa mai spaghetti jelop ta maishi mai ruwa ruwa ko zai iya ci, take ta daura sanwan cikin abinta baifi minti talatin ba ta gama dafa haddenden jellop din taliya mai ruwa ruwa da yaji kayan lambu, ga kuma kifi busasshe irin manyan nan da tayi amfani dashi, kwashe wa tayi a kula ta ajiye, ta gyara kitchen din tsab, komawa tayi dakin, ta dubo ko ya farka, samun shi tayi zaune bakin bed ya dafe kanshi, amsa mata sallama yayi a hankali,karasawa tayi gaban shi tace"sannu Mr Aslam ka tashi ya jikin" dagowa yayi ya kalleta tare da sakar mata murmushi, dadi taji ganin jikinshi da sauki, tunda gashi har ya tashi da alama ma yayi sallah, itama murmushin ta sakar masa tare da cewa , "tunda naga kamar har kayi sallah bari na zubo maka abinci kaci, kasha maganin ka na rana" bata jira amsar shi ba ta fice daga dakin, kitchen ta nufa ta dauko kular abincin da plate da spons da su ruwa duk ta hado komai akan tray ta dauko. A kan dan table d'in dake dakin ta ajiye, sannan tayi serving dinshi taliyan da uban yawa ta mika mai, kin amsa yayi ganin haka yasa tace "Mr aslam pls ka amsa kaci, idan baka cin abinci baza ka warke da wuri ba, in kuma bakason wannan abincin ne sai ka fadi wani kalan da kake so na girka maka" da sauri ya girgiza mata kai, alamar A'a yanaso, don tunda ta bude kulan abincin daddan kamshin girkin ya buge shi miyon shi ya tsinke ranshi ya biya, kawai dai wayau yake so ya mata ta sake bashi a baki kamar dazu, dan dazu ba karamin dadin hakan yaji, tsabar farin ciki ya Asmah na bashi abinci da hannunta, koda bacci ya kwashe shi mafarkin abin yatayi. Ganin yayi shiru yasa tace "bakace komai ba" kallon ta yayi yana yamutsa fuska alamar yana jin jiki da ciwon yace"pls ki sake min irin taimakon dazu ki bani a baki na, bazan iya ci da kaina ba," tausayi ya bata yadda taga yana yi da fuska ta San ba karamin jin jiki yakeyi ba, ba musu ta matsa gaban shi zata zauna shi kuma yana zaune bakin bed, da sauri ya taro ta ya zaunar da ita a kusa da shi, a gefen shi, bata damu ba ta dago plate din tana diba da fork tana bashi, kadan kadan, sai amsa yake yana kallon fuskarta yana murmushi, ji yake kamar tunda yake bai taba jin daddaɗan jellop din spaghetti irin wannan ba, zuciyar shi wasai, bai ankara ba sai emty plate, da matukar mamaki yake kallon plate d'in, a zuciyar shi yana aiyana yanzu duk tulin abincin nan ya cinye, lallai yayi babban aiki, magani ta ballo tabashi ta, ta tsiyaya mai ruwa ta mika mai, yanzu kam dan samun guri har ruwan shan maganin cewa yayi,ta bashi har zata ƙi zuciyarta ta kwabeta da cewa ki mishi Asmah ciwo yafi gaban wasa, kinsan inda kene kike cikin wannan halin abinda zai miki sai yafi wannan da kike mai, daga yanzu dai ki lallaba kimai duk abinda ya bukata har zuwa yaji sauki. Bashi tayi yasha ya kalleta yace "nagode mrs Asmah," murmushi kawai tayi ba tare da ta amsa ba ta kwashe kwanukan abincin ta fita dasu, sai lokacin hankalin ta ya kwanta ganin Aslam yaci abinci yasha magani, zuba abincin itama tayi kadan a plate ta zauna taci a kitchen d'in, jin ulsa na so ya tashi mata. A haka Aslam da Asmah suka wuni Asmah jinya takeyi tuburan tsakanin ta Allah, motsi kadan idan yayi zata isa gareshi a firgice tana tambayar shi menene me ke mishi ciwo a ko a kira Dr da dai suransu. Yayinda Aslam zuwa lokacin ya ji garass sosai kawai sai dan kafin jiki ne, Wanda shi kuma dama sai a hankali, ammafa ko a fuska bai Nuna mata yaci sauki ba, abubuwa iri iri yake mata tsabar samun guri yanzu ko magana zai mata har wani shagwaba shagwaba yake hada wa da shi common toilet zai shiga sai ta tallabo shi, abincin dinner kuwa data kawo bata tsaya wahalar mika mishi ba direct ta zuba ta dinga bashi, ko musa babu ya amsa. Jinshi yakeyi kamar wani sabon dan yaye , gani yake duk tsawon rayuwar shi bai taba riskar wuni mai dadin wanna ba. Asmah na tare dashi har wurin goma da rabin dare, duk ta gaji libis burinta ya kwanta ta samu itama ta wuce dakin ta ta kwanta ta huta,ta kaishi toilet yayi wanka daker, ya fito ta dauko mai kayan bacci, ya sa wandon ta saka mai riga, ya hau gado ya kwanta, duk zuciyar shi ba dadi yasan tabbas sun kusa rabuwa kenan dan yana kwanciya ya tabbata dakin ta zata koma itama ta kwanta, tunani ya shigayi na abinda zaiyi ya hanata tafiya dakinta, take ya saki wani murmushi bayan ya samu salutation. Tsaki ya fara saki ƙanana, yana dafe kai, dagowa tayi da sauri ta kalleshi, tace"lafiya Mr Aslam meke faruwa kuma ko jikin ne" cikin yanayin yamutsa fuska kamar da gaske ya nuna mata kanshi alamar kai ne ya tasar mai, ganin haka tace "ayya sorry" tana dawowa dakin ta zauna, tana mai sannu yana gyada kai. Zamanta da kusan 20minutes ya fara lumshe idanu, dan bacci yakeji, itama daga zaunen da take sai gyangyadi takeyi, can ya bude ido daya ya kalleta, tausayi ta bashi ganin yadda take bacci a zaune, gadai shi yayi dabara ya hanata tafiya sai dai kuma kamar ya shiga hakkinta, yake gani, wani dabaran ne ya sake zuwar mai, nan take ya fara rawan sanyi yana karkarwa har hakorin shi na haduwa yana bada sauti, da sauri ta ware idanunta jin sautin karan haduwan hakoranshi ga kuma nishi da yakeyi a wahalce. Baiwar Allah bata San sanda ta dira gabanshi ba, cikin tashi hankali ta shi furta "innalillahi wainnailaihi rajiun, na shiga uku, Mr aslam dan Allah karka mutu, na shiga uku ni Asma'u" take ta haura kan bed din ta tallabo shi jikinta tuni har hawaye sun fara sintiri a fuskarta, tsabar rudewa ko kula da jikin shi ba zafi batayi ba, Aslam kam da'ker ya bude baki a wahalce murya na rawa rawa yace "pls mrs Asmah ki rungume ni sanyi nakeji, ki rungume ne na samu dumin jikin ki sanyi zai kashe" yana fada karkarwar da yakeyi na karya na daduwa. Bata San sanda ta fada jikinshi ta kamkameshi ba, tana hawayen tausayin sa, jinta a jikinshi gaba dayanta haka, saida wutar kanshi ya dauke na wucin gadi, ga tudun boobs dinta yana ji a kirjinshi, lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya, hannu yakai ta bayanta ya rungumota shima, a hankali kuma jikin nashi ya daina karkarwan da yakeyi hakoran shi suka tsaya da haduwan da sukeyi. Jin haka yasa Asmah tayi tuananin rungume shin da tayi ne yasa ya daina jin sanyin da gaske, shiru tayi lafe a jikin shi tana sauran bugun zuciyar shi, a haka taji yana suke numfashi alamar bacci ya daukeshi. Ajiyar zuciya ta sauke itama ta maida idanunta ta lumshe ta Lula duniyar tunani da tausayin halin da aslam yake ciki a haka bacci barawo yayi awan gaba da ita. Aslam jin tayi bacci yasa ya bude idanunshi dake lumshe,ya sauke ajiyar zuciya tare da sakin wani miskilin murmushi, a baiyane yace"Allah nagode maka da kakawo min karshen wannan game ɗin cikin sauki, husnah daga yau kin shiga uku dani, na samu saukakekken hanyar da zan miki kamun kazar kuku, ni danasan zakiji tausayi haka idan banida lafiya Ai da tun farko na kirkiri rashin lafiyar karya".............. kuyi hakuri da kura kurai banyi editing ba🙏 Oum ummeetarh 07041130088. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen mu} 💖Tallah!💖 Tallah!!💖 💖Tallah!!!💖 💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 102 ~BATOOL~ Yau kimanin sati biyu kenan da mai afkuwa ta afku tsakaninta da Dr bash, tsaye take a kitchen gaban gas, sanye take da zumbulelen hijabi dogo har ƙasa breakfast take haɗawa domin kuwa safiyace, daga inda take tsaye ta juyawa kofar shigowa kitchen din baya. Takun shi ta fara ji daga bayanta alamar yana kusan to kitchen d'in, take gabanta ya fara faɗuwa, jikinta ya dauki karkarwa, har saida Cokalin miyar dake hannunta ya subuce ya faɗi. Daga bakin kofar kitchen ɗin ya tsaya ya harɗe hannu a kirji yana kallonta, koda wasa batayi gigin juyowa ba, tsayuwar kusan minti biyar yayi kafin ya juya ya bar kofar kitchen. Ajiyar zuciya ta sauke jin ya bar kofar kitchen d'in, dukawa tayi ta dauki cokalinta ta daureye, taci gaba da girkinta, cikin sauri sauri ta karkare , ta zuba mai nashi a kula ta ajiye mai a gurin data saba ajiye mai a kitchen d'in nata kuma ta zuba a plate, ta dauka ta kamo hanyar fitowa daga kitchen d'in saida ta fara lekowa taga ko yana falon, yana nan kuwa saidai ya juyawa hanyar kitchen d'in baya, cikin sanɗa ta lallaba ta haye sama, tana samu ta haye ta ƙarkare da gudu ta shige dakinta ta banko kofa. Dr bash yana zaune a falo ya juyawa hanyar fitowa kitchen baya amma duk abinda takeyi yana kallonta ta jikin glass din tv kasancewar tv a kashe yake, girgiza kai yayi cike da damuwa ya mike ya shiga kitchen din ya dauki nashi abincin ya shige sabon bedroom d'in shi dake nan a kasa. Abinda ke faruwa shine tun ranar da Dr bash yayi nasaran raba ta da budurcinta, gaba daya batool tayi wani irin laushi, tsoran shi takeji kamar wani malaikan daukar rai, saboda ba karamin azaba tasha a hannunshi ba, tayi dana sanin rashin mutuncin da ta dinga mai tuntuni, da tasan haka aure yake da wallahi, saidai in gawarta za'a aurar,ta kai kusan 3 days ko taka kasa bata iyawa da kyau, wani irin tsoran shi hade da kunyar shi ne ya darsu a zuciyar ta tun daga ranar, tun ranar har yau taki bari idanunta da nashi su haɗu, idan kuwa yazo kusa da ita tsorata takeyi jikinta ya kama karkarwa, wasan buya take yi dashi sosai, Dr bash tun yana daukar abin wasa yana mata dariya yana tsokanarta har dai lamarin ya fara bashi tsoro, dan ranar da ya gaji ya kara nuna alamar son ya sake kusantar ta duk da rawan da jikinta keyi tana kuka bai saurare ta, tubeta yayi ganin da gaske yakeyi, yasa take numfashinta ya fara sizing kan ya farga ta sume mai. Hankalin shi yayi matukar tashi, rasa yaya zaiyi da ita yayi,kamar ba likita ba, can dai ya debo ruwa ya yayyafa mata, tana farkowa kuwa kuwa da kuka ta fara tana rokon shi dan Allah yayi hakuri, karya ya sakeyi mutuwa zatayi, a take bash ya yarda lallai ba, iskanci bane da gaske ta tsorata da shi, dole dan kar ya dinga firgitata yasa ya tattara ya bar mata dakin hakan kuwa ya mata dadi,tun daga lokacin kuma ganinta ya nemi yimai wuya a cikin gidan, sai ya kwanta ya wuni bai ganta ba, dan bata fitowa sai ta tabbatar yabar gidan, zata fito ta shiga kitchen sauri sauri tayi girki, duk abinda ta girka kuwa saita ajiye mai, yau ma gajiya yayi da rashin ganin ta dan kusan kwana biyu kenan a Jere ko motsinta baiji ba, hakan yasa yayi dabara ya shiga mota ya fita da sassafe yabar gidan, jin haka yasa ta fito da sauri ta fada kitchen donta haɗa breakfast, parking d'in motar shi yayi a kofar gidan ya lallaba ya dawo shinefa ya sameta a kitchen, wannan rayuwar shi suke fuskanta a gidan tun daga wannan ranar da mai afkuwa ya afku, abudai kamar shafan aljanai, bashir kam ya shiga damuwa abin har ya fara shafar aiki da lafiyar shi. (Allah sarki bash kai kuma taka ta sameka, Allah ya taro maka ita da gaggawa) ~MR & MRs-AS~ Tsawan sati daya kenan da fara rashin lafiyar Aslam, har zuwa wannan lokacin kuwa jikin dai gashi nan ba sauki, abun na matukar damun Asmah, duk tabi ta damu kanta, inka ganta duk tayi zuru zuru kamar itace a kwance, yayinda Aslam tuni ya gyagije yanzu haka da za'a dubu su sai an samu ya fita lafiya ya samu kwanciyar hankali yayi wani fresh dashi ya kara haske harda dan kiba. Yana daga kwance komai ita kemai, abinci saiya zaba wanda yakeso zata girka ta shakare mai plate ta bashi a baki yana mata yanga yana walata a haka zai tanɗe tass, da zarar anyi sallah ishs'e kuma ya kama rawar sanyi karya yace ta rungume shi sanyi zai kasheshi, haka nan tana hawaye saboda tausayin shi yata rungume shi, a haka har barci ya kwashe ta. Tsananin tausayin ta yasa ta kasa gane karya yakeyi lafiyar shi lau, bata taba lura da cewa jikinshi ba zafi ba, haka idan yana rawar sanyin shi na karya tace bari ta kashe Ac bai taba yarda, cewa yakeyi ta barshi, duk da haka bata taba harbo jirgin karyan shi ba,zuwa yanzu ita kanta tayi wani irin sabo da shi, jin shi tajeyi har cikin zuciyarta, takan shagala da kallonshi musamman idan yana mata shagwaba, sai ta tsinci kanta da biye mishi ta dinga lallashin shi kamar wani dan yaye. Yanzu haka tsaye take a kitchen tana ta faman dama mai kunun gyada da kosai dan yau shi yace yana so na breakfast, tana aikin amma zuciyarta cike da tunane tunane, idan lissafinta dai dai ne yau ya kama Aslam zai gama shan maganin sa duka , don idan yasha na dare yau shike nan mugungunan sun kare, kuma ita ta duba ta dubo bata ga wani saukin da ya samu ba gashi har magani ya kare yanke shawara tayi, zata tuntube shi su je asibiti, kokuma ta kara kiran Dr James, da wannan tunanin ta kammala hada lafiyayyar kunun gyadanta da yaji madara da kuma kosai mai hanata da kwai a ciki, jerawa tayi a tray ta dauka ta nufi dakin. Aslam na zaune bakin bed waya yake yi da Amir, sai kwasan dariya yakeyi , Amir na bashi labarin tsiyar da ummi ta mashi da irin wuyan da yasha da kuma yadda ummi ta mayar mai da matar shi cikin sauki ba tare da wani tashin hankali ba, Aslam kam sai dariya yake ma Amir d'in harda su kwanciya, yana rike ciki, hankalinshi yayi nisa baiji sallamar Asmah ba. Sallama tayi har kusan so uku ba'a amsa mata ba hakan yasa ta kutsa kai don duk tuananin ta ya koma barci kokuma yana toilet shiyasa bai jita ba, saidai ga mamakin ta sautin dariyar shi taji, kafin ta kai kallonta kanshi ya Ankara da shigowarta, dif yayi da dariyar da yakeyi, tare da yamutsa fuska,take ya maida muryar shi na marasa lafiya, hannunshi kuma dake tallabe da cikin shi tsabar dariya, ya kara dannan shi akan cikin kamar dai gurin namai ciwo, a wahalce ya shiga cewa "ba damuwa bross na gane na fahimceka ba komai bari zan kira ka letter, bana ɗan jin dadi ne" mamaki ne ya nemi kashe Amir a daya bangaren, saida ya cire wayar a kunnen shi ya duba sunan da kyau ya sake mayar wa kafin yace wani Abu kit yaji Aslam ya katse kira, da sauri ya sake kira amma Aslam ya danna mishi busy, har so biyu dole ya hakura , a ranshi yana aiyana lallai akwai lauje cikin nadi, dan shidai ya san ruwa baya tsami banza amma koma meke ciki yayi alkawarin bincikowa. Daskarewa Asmah tayi take ta shiga tunanin to kodai kunnayenta ne suka jiyo mata sautin dariyar shi, dan dai ita ko kur'ani aka bata zata rantse taji dariyar shi, sai dai kuma a yadda ta ganshe sai ta rantse bai taba dariya a duniya ba, kawar da wannan tunanin tayi ta karasa ciki ta ajiye tiren ta akan table din datake ajiye wa, ta fara serving dinshi tanayi tana bashi hakuri bisa dan bata lokacin da tayi, kallonta yayi yace "ba komai yar Aljannah, nagode da dawainiyar da kikeyi dani Allah ya saka miki da gidan Aljannah madaukakiya, Allah kuma ya baki ƴaƴan da zasu miki fiye da yadda kika min" dadi da kunya ne suka lullubeta a lokaci guda dadin addu'o'in da ya mata da kuma kunya maganar shi ta karshe da yace Allah ya bata ƴaƴa, ganin ta kawar da idonta gefe cike da kunya yasa ya fakaici idanta ya mata gwalo, sannan yaci gaba da cewa "insha Allah zamu haifar ma su daddy jikoki kyawawa masu kama dake, kina so" kunya ya ya kara lullubetata ta lura shidai Aslam kwata kwata babu wani Abu wai shi kunya a lamuran shi, yana ta wani magana akan haihuwa haihuwa, ta yaya zasu haihu, ita dai tasan ko anyi aure akwai wasu abubuwa dake faruwa kafin akai ga samun ciki har a haihu, take ta ƙara yin kasa da kai tuno ta yaya akeyi a samu cikin ma har a kai ga haihuwa, tanada wannan muradin itama kuma tana sha'awar ta haihu amma fa da Kamal kawai take da wannan sha'war bada kowa ba. Aslam ganin tayi kasa da kai tayi shiru kamar ta Lula wani tunani yasa ya katseta da cewa "kinyi shiru Mrs Asmah ko baki son mu haihu ne" firgigit tayi jin maganar shi kamar daga sama, bata bashi amsar wannan tambayar ba sai cewa da tayi" oh sorry ga abincin na zuba maka" tana magana tana karasawa gaban sa da plate da cup d'in kunun data zuba mai, bata tsaya bata ma kanta lokaci ba ta shiga diba tana kaiwa bakin shi, karba ya dingayi yana ci yana kallon fuskarta yana sakin murmushi, wani irin dad'i yake ji a zuciyar shi, inama ace bawai saboda bashi da lafiya bane take mai wadanan duk abubuwan da take mai inama ace dai soyyaya ce tayi sanadin da take bashi abinci haka a baki ba tausayi ba. A haka ta gama ciyar dashi, ta mike zata bar gurin komar da ita yayi ya zaunar, sannan ta mike a hankali ya dauki plate da cup din ya isa inda sauran abincin suke a kula, ita dai binshi takeyi da kallon mamaki, mai zaiyi da abinci kuma bayan yace mata ya koshi, mamakin ta bai ƙaru ba saida taga ya ciko plate da cup da kunu da kosai ya zauna gabanta ya dibo yakai bakin ta, kin bude baki tayi ta tsaya kallon shi, katseta yayi da cewa "umhumm ke nake jiya oya haaa" girgiza kai tayi ta bude baki zatayi magana, katseta yayi ta hanyar daura dan yatsar shi akan labban shi yace "shiiii bana son musu kawai kiyi haaa" yadda ya bata rai sai taga ya koma mata asalin ya Aslam data Sani a baya ba wannan Aslam d'in ba dake binta sau da kafa kamar wata uwar shi, bata San sanda ta bude ɗan bakin ba kuwa ya shiga bata a hankali tana karba, gaba dayansu wani irin nishadi suka tsinci kansu a ciki a daidai wannan lokacin, ji suke kamar su tabbata a haka, har saida ya tabbatar ta koshi sannan ya barta, kwashe kwanukan tayi ta kai kitchen ta wanke, sannan ta dawo ta bashi magani yasha,ta wuce kuma toilet ta hada mishi ruwan wanka. Kamar kullum yauma mika mata hannu yayi ta dagashi, tsayawa tayi tana kallon shi tunawa da dazu daya mike yaje ya dibo mata abinci ai bata dagashi ba kuma taga ya iya tashi da kanshi, muryar shi ta tsinta yana cewa cikin shagwaba "pls mana Mrs Asmah tunanin me kikeyi" jiki a mace ta mika hannu dan ɗaga shi, saidai ji tayi ya fisgota ta fado jikinshi, komawa da baya sukayi kan bed d'in,tana a sama shi kuma yana a kasa ya mutsa fuska yayi yana cewa"wash Allah kirgina kin fado min a kirji zaki karyamin kashin hakarkari, gaki da nauyi, kamar buhun siminti, wash kirjina zai balle" jin abinda yake cewa yasa tayi maza ta sauka akanshi, ta shiga bashi hakuri a rude kan bata San yanda akayi ta fado kanshi ba, dago kai yayi ya kalleta ganin duk yadda ta rude tana ta faman bashi hakuri, yasa ya saki murmushi a zuciyar shi a fili kuma fakan idanta yayi ya mata gwola, saidai cikin ikon Allah karaf a kan idanunta, turuss tayi ta tsaya daga ban hakurin da take mai tana kallonshi ganin haka yasa, ya shiga pretending yana zaro harsher waje yana mayarwa, yana jan yaji, cikin rasa madafa ya shiga cewa "wash harshena yaji, kai gsky yau kosan nan naki yayi yaji sosai wlh hala tarugu guda goma kika zuba"Asmah kam tsabar mamaki daskarewa tayi a tsaye a gurin, kosan da yaci kusan 30minute da suka wuce duk baiji yaji ba sai yanzu, ita dai ganin idanunta ta kamashi yana mata gwalo, sharewa tayi amma a ranta ta sakama lamarin ? mark, na biyu kenan dazu ta kamashi yana tikar dariya yanzu kuma gashi yana mata gwalo, amma ya fake da wani abinda hankali ba bazai dauka ba wai yaji. Bata dai nuna damuwar komai ba ta tallabo shi zuwa toilet d'in kamar yadda ta saba kullum, rabin jikinshi na cikin nata ta kaishi toilet d'in ta fito, ta Ciro mai kayan da zai saka ta bar dakin zuwa falo,zama tayi ta shiga tunanin abubuwa biyu da suka faru yau a kusan lokaci daya da suka matukar bata mamaki, shin da gaske ne abinda idanu da kunnayenta suka gano da juyo mata, kodai karyace kawai sukeyi yi mata, kai gaskiya da gaskene dan tasandai bata da matsalar ji da gani balle tace ciwon su ne ya motsa mata yau, to kodai mr Aslam ya warke kawai pretending yake mata dan ta dunga kulawa dashi, kai anya ya za'ayi mutum da girman sa da hankalinsa yayi kar yar ciwo haka, ajiyar zuciya ta sauke mai karfi kafin a fili tace koma me ke ciki zan Saka ido sosai domin na gano gaskiyar lamarin, inko karya yake min ko hmmmm ta kareshe tare da girgiza kai. Aslam koda ya gama wankan shi ya daura tawul gyaran murya ya mata alamar ta shigo ta taimaka mai ya fito, dan dama haka sukeyi yanzu har fitowa toilet d'in sai ta taimaka mai yakeyi, jin shiru alamar bata dakin abin ya matukar bashi mamaki, haka ya mike a hankali ya leko ganin da gaske bata dakin yasa ya fito da kanshi, zaman jiranta yayi tazo ta shafa mashi mai da sauransu amma har ya bushe shiru ba amon ta ba labarin ta, take yasha jinin jikinshi, lallabawa yay, yayi shafe shafen da kanshi ya saka kayan, kamar yabi bayanta ya dubo ko lafiya amma sai wata zuciyar ta kwabe shi da cewa muddin kayi haka sai ta zargi wani Abu, dole ya hakura ya koma ya kwanta amma zuciyar shi gaba daya babu dadi, a haka bacci ya kwashe shi Mara dadi mai cike da mafarkai barkatai, harda Wanda Asmah tagane Ashe kalau yake, ta kuwayi mummunan fushi wai harda su gaggauramai mari tayi a makarkin. Koda ta gama zaman ta a falo lekashi tayi taga yayi bacci dan haka itama ta wuce dakinta ta kwanta, tana son tayi bacci saidai kash baccin yaki zuwa sai juyi tajeyi akan makeken bed dinta,jin ta tajeyi kamar a bude take dukda taja kakkauaran bargonta ta rufa, ji takeyi gadon ya mata wani irin mugun fad'i, karshe dai saida ta lalubi pillow ta rungume sannan ta iya baccin. Sai bayan azahar ta tashi bata ɓata lokaci ba ta gabatar da sallanta, sannan ta nufi dakin Aslam, ta tarad shima ya tashi da alama ma ya dade da tashi don har yaje masallaci yayi sallan azahar ya dawo, sannu tamai da jiki, nan ya shiga yamutsa fuska yana amsa mata a wahalce kamar gaske, tambayar shi tayi abinda zaici ya fada, ta wuce kitchen taje ta girki ta kawo ta bashi a baki kamar kullum. Haka dai suka wuni ranar har zuwa dare inda bayan ta gama bashi abinci ta dauko sauran maganin shi Wanda idan yasha wannan shikenan ya kare ta bare mishi tayi ta bashi, bayan ya gama sha ta kalleshi tace" Mr Aslam idan kasha wannan maganin na yanzu ka gama shanye duka magungunan da Dr ya baka gashi kuma ni banga alamar kaji sauki ba , ya zama dole ka yarda muje asibiti kokuma na sake kiran Dr yazo gida ya kara dubaka, ni abinda yafi bani tsoro ma, wannan rawan sanyin dake tashi maka da daddare kaga rannan baka ma Dr complain dashi ba kar azo kuma ba fever d'in bane wani ciwo ne na dabam"tsayawa yayi ya rasa wani amsa zai bata can dai ya daure yace "to Allah ya kaimu goben sai ki kira Dr James din ya canza min wasu magungunan, tunda dai wadanan basuyi ba", kamar kullum yauma haka rawan sanyin nan ya sake kama Aslam, bata jira yace ta rungume shi ba, tana ganin haka ta shige jikinshi suka Lula barcin su mai dadi cike da kwanaciyar hankali. ~ZEE~ Yau kimanin 3month kenan rabonta da Nigeria, zaune take a garding d'in gidansu ta mike kafafunta tana zaune a kasa ta shimfida dadduma, gaban ta littattafan addinine kanana irin su kawa'idi arba'una hadis durusul arabiya da sauransu, hannunta kuma kur'anine izifi biyar ta bude suratul jinn tana nazari a bayyane. Daga bayanta taji an mata sallama, da fara'a a fuskarta ta juya ta kalli wacce ke mata sallaman ba wata bace illa malamarta dake zuwa har gida tana koyar da ita karatun addini, a wani babban Islamic school dake garin da suke a Malaysia ta dauki malama macce wacce zata dinga zuwa har gida tana koyar da ita, makaranta taso ta dinga zuwa tana daukan karatau saidai babban malamin ya nuna basa daukar matan aure balle ita gata harda ciki, hakan yasa ta nemi alfarman a bata malama mace wacce zata dinga biyota gida tana koyar da ita in yaso duk wata zata dinga biyanta albashi mai tsoka, babban malamin ya amincene kawai saboda ganin yadda ta nace da gaske tana son karatun, hakan yasa ya duba cikin yan unguwan da suke ya hadata da sumaita, balarabiya da zama ya kawo iyayenta Malaysia. Zama sumaita tayi suka gaisa cike da mutunta juna , nan zee ta shiga biyo mata karatuttukan da sukayi jiya ba laifi kuwa kanta yana dan ja, kara mata sumaita tayi sukayi sallama ta tafi ita muka zee ta zauna tadanyi nazari na dam wasu mimtoci kafin ta lallaba ta tashi da'ker tukeken cikinta najanta gata ba auki ba,ta hada kayan karatunta a jaka ta linke dadduman ta ta nufo cikin gidan. Sanda ta shigo falon mom da dad na zaune bata ce musu kala ba bayan sallamar data musu ta wuce dakinta da yanzu ya dawo falon kasa saboda hawa stairs na bata matukar wahala. Da idanu suka rakata har ta kule ma ganin su, Dad ne ya sauke ajiyar zuciya yana kallon mom yace"lamarin daughter ya fara shamun kai, anya ba asiri wannan dan iskan yaron ya mata ba kike gani, ki duba kiga yadda ta canza gaba daya cikin dan wasu watanni ta zama wata silent da ita, ko magana bata mana idan ba da kwakwaran dalili ba, naji na hakura na janye na bar mata cikinta ta Haifa tunda dai ita taji ta gani zata iya , amma duk da haka ban tsira ba" mom tace "bana tunani asiri ya mata nafi tunanin soyyaya ce take mishi mai matukar girma, lokacin da ta fara zuwa makarantar koyan girki Dana tamabayeta dalili, direct ta gayamin saboda Aslam ne , saboda duk randa ta koma dakinta t,ya kasance ta iya girki Aslam zaiji dad'i zaiyi alfahari da ita" dad ya daura da cewa "haka nima dana tambayeta game da wannan karatun da takeyi, ce min tayi saboda Aslam ne, saboda yana son tasan addinta ni wannan lamari ya fara isana fa , yanzu cikinta yakai wata nawa" mom tace shekaran jiya da mukace asibiti dai akayi scanning Dr yace wata bawai kenan cif" sauke ajiyar Dad zuciya fuskar shi dauke da matsanan cin damuwa yace "Allah ya sauke ta lafiya" mom ta amsa da amen ya rab , itama zuciyarta babu dad'i............... Comment nake so ta ko'ina kokuma mu koma tsallake tsallake baban gora😁 ehee kundai ji na fada ko naga comment kokuma update ya koma yau ayi gobe a huta. Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen mu} 💖Tallah!💖 Tallah!!💖 💖Tallah!!!💖 💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 103 Washe gari bayan sun tashi da asuba, taimaka mai tayi yayi alwala ya tafi masallaci, ita kuma a nan dakin nashi tayi sallah bayan ta idar zama tayi tayi azkar da sauran addu'o'i da takeyi, a karshe ta roƙi Allah yaba Aslam lafiya, alkur'ani ta dauka ta shiga karatun a bayyane. Bayan an idar da sallah a masallaci, shima dai zama yayi a can yayi dukkan addu'o'i shi a karshe ya roki Allah yasa Asmah ta soshi koda Rabin sonda yake mata ne, Allah ya kawo mishi karshen komai cikin sauki, daga nan kuma gida ya dawo direct. Tun daga bakin kofa yake jin zazzakar muryarta tana karanta alkur'ani mai tsarki cikin suratur nisa'i, dakatawa yayi daga sallamar da yayi niyya, ya tsaya yana saurarenta yana lumshe idanu, godiya da kirari ya shiga jerowa ubangiji daya mallaka mishi Asmah a matsayin matar sa, take kuma zee ta fado mishi a rai, ya tuna fama da gwagwarmayar daya ke sha kullum idan yana koya mata karatu, sai ranshi yayi matukar baci, ya mata jan ido take maida hankali, kuma washe gari idan yace ta biya da'ker take iyawa. Minti kusan 15 ya kwashe a tsaye a wurin yana saurarenta kafin kuma, a hankali ya tura kofar bakin shi dauke da sallama, bata amsa ba saida takai wayar da take karantawa sannan ta yi sadakallahul azim, ta amsa sallaman shi, kara sowa ciki yayi ya zauna a bakin bed, addu'o'i tayi ta shafa sannan ta juyo ta kalleshi tace mashi "in kwana Mr Aslam " murmushi yayi cikin jin dadi ya amsa mata da "lafiya lau, kin tashi lafiya ya hidima dani" martanin murmushin ta mayar masa sannan tace"lafiya qlau alhmdllh ya jikin ka" ya amsa mata da cewa "da sauki"tace "Allah uban giji ya kara afuwa, ni zanje nayi wanka a dakina, daga nan zan shiga kitchen me kake so na girka maka" shiru yayi kafin yace "yau dai na baki zaɓi ki dafa duk abinda kike son ci nima zanci" OK kawai tace sannan ta tashi ta nade pray mat ɗin ta ajiye a ma'ajiyar sa ta fice daga dakin, Dakinta ta je ta fara gyara wa ta share duk da ba wani datti yayi ba, tana gamawa ta shiga toilet dan tayi wanka. Bayan fitar ta zama yayi ya dauki alkur'ani data ajiye yana karantawa shima, daga gefen sa wayar sa dake ajiye ya fara ringing, daukan yayi ya duba mai kiran, Amir ya gani dan haka ya saki murmushi kafin yayi picking call ɗin yana dagawa daga cen bangaren Amir yace"sannu hakimi, wai har yanzu baka gama cin amarcin bane, yau wata nawa rabonka da da kaje office" dariya Aslam ya kwashe dashi sannan yace"yau kuma wutar masifa ke cinka, naga ko gaisawa bamuyi ba ka hauni da tambaya" Amir yace"abin naka ne ai ya fara wuce gona da iri idan ka ajiye aikin ne sai ka faɗa kawai ayi replacing din wani da kai, haka kawai kabar dan taliki da aiki,kai kana na can kana sharban amarci kama manta da mutane idan ba mutum ya kira ka ba kai baza ka kira ba" Aslam yace"sannu daddy ai sai kayi replacing dina da wanin mu gani, da kake ta wani maganar amarci amarci, ni na gaya maka amarci nake sha " dariya Amir ya kwashe dashi kafin yace"ai nasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya" Aslam yace " kai dai bari kawai ka tayani da addu'a ina nan inata kokarin kafa gwamnatina" Amir yace "rannan muna waya naji ka sako min wasu soki burutsu" kwashewa da dariya Aslam yayi, take kuma ya shiga bama Amir labarin abinda ke faruwa. Kyalliyarta tayi kamar kullum sai tashin kamshi takeyi, fitowa tayi ta nufo hanyar kitchen don hada musu breakfast,kunun tsamiya takeson yi yau da alale, la'akari da tayi da bai da lafiya bakin shi ba dadi ƙila zaizo Abu mai dan tsami tsami, har ta dauki sacet din garin kunun ta fara gwabawa sai kuma ta tsaya tana tunanin anya zai sha dan dai ko a gida bata taba ganin yasha wani kunu ba inba na gyada ba, zuciyarta ta bata shawara da cewa kije ki tambaye shi mana, ki cire kokwanto aranki, shawaran zuciyarta tabi ta ajiye kwabin da tajeyi ta nufi dakin shi. Daidai lokacin Aslam ya fara ba Amir labari, har takai hannu zata tura kofar ta tsinkayi muryarsa da abinda yake fadi cike da nishadi yake bada labarin, yanayi yana kwasan dariya, kusan suman tsaye tayi a bakin kofar nan, kanta ya daure, yanzu dama duk wannan rashin lafiyar na Mr Aslam na karya ne dama pretending yake yi, yaji sauki tuntuni, take taji ranta ya baci, tunani ta shiga yi ta shiga ne kota koma, wani zuciya ya bata shawara ki shiga kawai ayita ta kare, dakewa tayi ta tura kofar ta shiga ranta a bace, ya juya baya baima San da shigowarta ɗakin ba daidai lokacin Amir yana cewa"lallai Aslam ka cika ɗan air, wato sanyi kakaji zai kashe ka ta rungume ka ko" kwashewa yayi da dariya yace "baiwar Allah har hawaye takeyi saboda tsabar tausayina, haka zataji tana sannu Mr Aslam jikin ne innalillahi na shiga uku,dan Allah Mr Aslam karka mutu" yana mganar ne cikin kwaikwayon muryarta, suna dariya shida Abokin cin mushen nashi,dai dai time d'in kuma Allah ya bashi ikon juyowa, idanunshi ya sauka a kanta ta rike ƙugu tana wani huci, take hantar cikinsa ta kaɗa gadaishi rike da waya a hannu, shi tsoran shi daya baisan tsawan lokacin data ɗauka tsaye tana sauraran shi ba, duk da haka bai karaya ba , maida murya yayi ya komar dashi na marasa lafiya yace"wlh dan uwa husnah yar Aljannah ce tana kokarin kula dani sosai, tana da zuciya mai kyau" yanayin yana dafe kirji yana sakin yan ƙananun tari, daga daya bangaren Amir najin haka ya gane abinda ke faruwa, shiru yayi yana suraren diramar nan, yana jin nishadi. Harara ta wulla mai tare da cewa "yau dubun ka ya cika kabar wani pretending na gano ka, sannu da kokari ka kyauta" iya abinda ta iya fada kenan ta juya ta fice daga dakin, kasa koda kwakwaran mosti yayi, gadai waya a kunnenshi har zuwa wannan lokacin ya kasa saukewa,a baiyane ya furta"innalillahi wa inna alaihi rajiun shike nan ta kare min "daga can bangaren Amir ya kwashe da wani irin dariyar keta don duk abinda ke faruwa yana sauraren su, sai lokacin ya tuna wayar ma a kunne take Ashe budar bakin shi sai cewa yayi "Allah ya isa tsakanina da kai Amir, ina zaman zama na da safen nan ka jawomin tonuwar asiri" cikin dariya Amir yace"Allah ya kara sauƙi Mr Aslam sai munzo dubiya, ka gaida min kanwa da kokari " tsabar haushi yanke wayar yayi, tare da yin jifa da shi Allah ya taimaka ya fadi akan gado. ~BATOOL~ Haka suka ci gaba da Rayuwa har tsawon sati hudu babu wani sauyi a game da zaman su, Dr bash yayi iya kokarin da zaiyi ya shawo kanta yayi Abu yaci tura, dole ya koma gefe ya zura wa sauarautar Allah ido ,gefe daya kuma ya dukufa da addu'a, kuma alhmdllh yaga alfanun hakan dan yanzu rawan jikin nan da takeyi idan ta ganshi ta daina, takan fito falo ta zauna tayi kallo wani bin ma suyi tare ammafa tana a takure dan ko kallonshi bata iya yi, idan ya mata magana zata amsa shi amma ba tare da hada ido dashi ba, yakan shiga dakin ta idan bukatar hakan ta taso yanzu ta daina garkamewa, shima kuma bai kara nuna yana son koda rike hannunta bane,duk da a matukar takure yake, kullum daren duniya daker yake iya bacci amma ya daure yaci gaba da gayawa mai duka, hakan kuma yasa ta dan fara sakin jiki kadan kadan dashi. Zaune take a dakinta a gaban dressing mirror fitowarta daga wanka kenan, zata yi shafe shafe,cike take da tsantsar damuwa tun last 2 Weeks take ta zuba idon ganin period dinta amma shiru, abin tun tana dauka wasa har gashi ta kwashe sati biyu cur ba amo ba labari, abinda bai taba faruwa da Ita ba, tunda ta fara al'ada bai taba kin zuwa mata ba, kuma bai taba canza mata lokaci ba, imma ya canza baifi ya kara kwana uku ko biyu ba amma wannan karon gashi har 2 weeks, da wannan tunanin ta shiga shafa man shafa warta, tun kan tayi nisa ta fara jin kamshin man da take mutuwar so yana shiga mata hanci yana tayar mata da zuciya daure wa tayi ta CI gaba da shafawa a jiki, ta gama da jiki tana kai hannunta fuska wani irin yun kurin amai ya taso mata ba shiri ta mike da gudu zuwa toilet ta shiga kelayawa. Daidai wannan time d'in Dr bash cikin shirin shi na tafiya hospital, ya nufo dakinta dan ya mata sallama, wayar shi kare a kunnenshi, waya yake yi da maah, tana kara jaddamai mai ya kula da batula da abida ke cikinta kuma in ya tashi aiki ya biyo akwai jike jiken da masu ciki kesha maganin zaki da sanyi , tasa an hado ma batool d'in ya biyo ya karba, shidai kawai da to yake amsa mata yana mata godiya, a karshe ta nemi ya hada ta da batool d'in taji lafiyar ta. Yana isa kofar dakin yayi sallama har sau uku bata amsa ba hakan yasa ya kutsa kai kawai cikin dakin yana shiga yaji kakarinta a toilet ga kofar toilet d'in a bude, baisan sanda ya katse kiran maah ba ya ajiye jakar sa ya nufi toilet d'in da sauri, aamunta yayi duke a toilet din ta dafa kwamin wanka da duka hannayenta, sai kwarara amai tajeyi baji ba gani, da gudu ya karasa ya tallabota jikinshi, a haka ya samu ta gama aman, amai tayi bama wasa ba don babu abinda yayi saura a cikinta na daga ruwa da abincin da taci. Jikin ta gaba daya ya saki lokaci gudu, taimaka mata yayi ta kuskure bakin ta ta wanke fuskarta, rungumota yayi ya fito da ita a toilet d'in, yadda tayi lamo a jikinshi abin ya matukar bashi mamaki, idan ya kula da kyau harda kara cusa kai yaga tanayi a kirjinshi tana shaqan kamshin jikin shi tana sauke ajiyar zuciya a wahalce, kan gado ya direta yana binta da kallo, matsayin shi na Dr baya bukatar Karin bayani daga bakin wani tsab ya fahimci meke damunta, farin ciki ne fall a ransa kamar ya daddage ya tsala ihu haka yakeji amma sanin wacece batool yasa ya Adana farin cikin shi ko a fuska bai nuna wani abuba, ba karamin aikinta bane ta saka mai rigima bata son cikin, bazai yi gangancin sanar da ita ba har saiya tabbatar tana son cikin tukunna, take kuma idan shi ya sauka akan wayar shi dake ajiyar bakin bed, maah ce ta fado mai arai baisan sanda wani kayataccen murmushi mai sauti ya subuce mai ba, Wanda har saida batool dake kwance kan bed idonta a runtse, ta ware idanu akan fuskar shi. Wani yarr taji a jikinta, tsigar jikinta ya fara tashi, wani irin azabebben feeling taji ya ziyarce a lokaci daya, bata San ta ƙura mai idanu ba, Dr bash mamakin irin kallon da take binshi dashi yake yi, tunda abin nan ya faru a tsakanin su bata taba bari sun hada idanu sun kalli cikin idan juna ba , amma yau a lokaci daya ji yadda take binshi da wani irin mayen kallo kamar zata cinye shi. Dage mata gira daya yayi tare da cewa "yadai" sai lokacin taji wani kunya ya kamata tayi kasa dakai, murmushi ya saki tare da cewa "zan tafi office inada theater da karfe goma sha daya, amma zan kira maah ta turo miki Afrah tazo ta zauna dake kafin na dawo bazan wani dade ba yau saboda ke ina gama abubuwa masu mahimmanci zan dawo" ba tare da ta kalleshi ba ta gyada mai kai, sa kai yayi ya fice daga dakin bayan ya dauki wayar shi da jakar shi. Da kallo ta raka bayan shi har ya kule ma ganinta, ji take kamar ta jawo shi ta shige jikinshi ta shaki daddaɗan kamshin turarensa ko zata samu sauki akan abinda takeji yana taso mata game da shi,rutse ido tayi tana matse kafa, a bayyane ta furta"innalillahi wainnailaihi rajiun, meke shirin faruwa da nine ni batool na shiga uku na ya rabbi ka kawo min dauki"............... Masu comment dina,ina mika muku dinbim godiya wlh naga zafafan comment ɗinku jiya kuma na karanta na yaba, wlh saboda ku kawai yau nauyi typing, kuyi min hakuri kar kuga ban yi reply ba, bani da isahen time da kuma caji ne, amma wlh duk na gani naji dadi sosai wlh inayinku irin totally dinnan💋 a ci gaba da gashi dama ta biyu insha Allahu yazo gangara saura kiriss💖 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen mu} 💖Tallah!💖 Tallah!!💖 💖Tallah!!!💖 💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 104 Ko awa ɗaya Dr bash bai rufa da fita ba Afrah da afnan suka iso, har zuwa wannan lokacin tana kwance inda ya barta, dan kwata kwata batajin karfin jikinta,cike da tausayawa suke jero mata sannu kai kawai take iya gyada musu, Afnan ne ta gyara toilet d'in ta wanke shi gaba daya saboda amai da ya bata, ita kuma Afrah tambayar batool tayi me zataci, dan Dr bash yace idan sunje su Samar mata abinda zataci, saida ta tsaya tayi dogon tunani kafin tace "banbara," Afrah tace "bambara kuma anty, kina da tawaska ne?" batool ta girgiza mata kai alamar babu, Afnan ne da ta gama wankin toilet ta fito take tambayar menene babu, Afrah tace "wai bambara take so kuma babu tawaska a gidan" Afnan tace "Ai dole a nemo tawaska duk inda yake, a kwai a gida,bari na kira maah taba direba ya kawo sai a mata" ba bata lokaci kuwa sai gashi nan kuwa maah ta bayar an kawo. Cikin abinda baifi 40minute ba suka gama soya mata shi yako ji albasa da mai, da suka kawo mata har rawa jikinta keyi tsabar yunwa da takeji gashi idan ba banbaran ba batajin zata iya cin komai, hannu baka hannu kwarya take ci ko kula da zafin shi batayi, kan kace kobo sai plate d'in. Tana gama ci kuma take wani sabon al'amari ya ziyarceta,babu abinda take bukata a halin yanzu irin mijinta, feeling takeji sosai, ga kuma kamshin turarensa da take maitar so, daurewa tayi ta share, sunata fira dasu Afrah, can dai ta kasa daurewa dan ji tayi kamshin nata dakin ya fara tayar mata da zuciya, Afrah ta kalla tace "dan Allah anty Afrah kije ɗakin yayanku dake kasa ki dauko min duka turarukan sa da kika gani akan mirror" Afnan cikin wasa tace "tofah! da alama dai wannan babyn namu dan rigima ne, yanzu kuma turaren big bro yake so" dariya suka saka ita da Afrah, itadai batool bata wani fahimci zancen da sukeyi ba. Afrah fita tayi taje dakin ta kwaso mata duk wani turare dake kan mirror manya masu tsadar gaske kusan kala bakwai, da sauri ta amsa ta shiga budewa ɗaya bayan ɗaya tana shaƙa, daga Wanda zai kusa sata amai, sai mai mata warin asibiti, harda mai kamshin hypo duk taji, ba shiri tasa aka tattara su aka mayar, duk sun tayar mata da hankali, karshe dai saida ta a maye banbaran da taci hankalin ta ya kwanta. Nan kuma taji cikinta kamar wacce ta kwana uku bata ci komai ba tsabar yunwa har jikinta na rawa, dauko mata sauran banbaran ta sukayi, amma tana kallon shi wani yunkurin amai ya taso mata ba shiri suka ɗauke, ga dai yunwa tana ji kamar ta mutu, saidai ba komai zata iya ci ba, Afnan tace"anty batool to me zakici, ki fadi abinda kike so na girka miki yanzu yanzu" a wahalce tace "ki duba kitchen akwai cabbage ki dauko min dan Allah" a haɗa miki coslow ne kokuma a miki kwaɗan shi da kuli kuli, batool tace"ki kawo min shi haka kar ki haɗa da komai" cikin mamaki tace "haka gaya zakici" tace "eh, dan Allah kiyi sauri, ba sai kin tsaya yankawa ba a kawo min shi haka"cikin minti biyu ta kawo mata cabbage din ta saka wuka ta raba shi hudu ta wanke ta ɗauro mata guda ɗaya akan tray, wawura tayi ta kai bakinta ta fara gabza kamar wata mayunwaciyar akuya, kan kace kobo ta cinye tace a karo, ɗaya aka karo mata shima cikin kankanin lokaci ta gama dashi tasha ruwa tayi gyatsa, zuwa lokacin kam ta koma ba su Afrah tausayi, dan duk tagumi sukayi da hannu bibbiyu suna kallonta, nan kuma cikin yan mintuna bacci yayi awon gaba da ita, haka su Afnan suka tsaya suna kallon ta kamar tv, can kuma wayar Afrah yayi kara dubawa tayi taga, yayansu ke kira da sauri ta daga, kafin ma yakai ga tambayar ta , ta shiga labarta mai abin da ke faruwa, shi kanshi saida yaji wani irin tausayin ta, sallama sukayi yace indai ta tashi su kira shi su haɗasu ta waya,wani uzuri ya rike shi sai yamma zai dawo, baccin ta tayi sosai bata ko juyi, kamar wata matacciya, har akayi azahar bata farka ba ,su kuma basu tasheta ba , sai daf da la'asar ta farka, basa ɗakin duka suna falo, lallabawa tayi ta tashi ta ɗauro alwala tayi sallan azahar da na la'asar gaba ɗaya. Bayan ta idar kuma ta fito falo,sai sannan suka San ta tashi, sannu suka shiga jero mata,murmushi kawai ta iya sakar musu, Afnan tace "anty batool yaya ya kira ɗazu kina barci yace idan kika tashi, a haɗa ku a waya" tace "OK ina zuwa tukun" ta faɗa tana nufar kitchen, sai gani sukayi ta fito hannunta dauke da plate shake da gayan kabeji, da idanu duk suka binta, bata kula dasu ba ta nemi guri ta zauna ta hau cin kayanta har wani lumshe idanu take tana mai mai da baki,saida ta take abinta Tass tasha ruwan ta ma'ishi, sannan ta kalle su tace "yadai naga an zubo min na mujiya ne" Afrah tace"Ai dole anty batool Allah dai ya raba lafiya" tabe baki tayi sannan tace "amin" ita fa har zuwa wannan lokacin bata San tana da ciki ba, maganar su Afrah bai sa ta gane komai ba duk a tunanin ta don sunji maah ta faɗa rannan ne yasa suma suke faɗi. Nan suka shantake a falon sunata fira, har zuwa wajajan karfe shidda , saida sukaji karan horn din motar Dr sannan suka tuna yace a haɗa shi a waya da batool. Bakinsa dauke da sallama ya shigo falon, da sauri Afnan ta amshi jakar hannunshi, har suna haɗa baki wurin yimai sannu da dawowa, cikin sakin fuska ya amsa musu. Tunda ya sanyi kanshi cikin falon daddaɗan kamshin turaren da take maitar son ji ya ziyarceta, lumshe ido tayi tana shaƙa, wani irin natsuwa da kwanciyar hankali taji yana ziyarceta a lokaci guda, karasowa cikin falon yayi idanunshi akanta, har ya isa daf da ita bata da labari, saida taji kamshin ya ƙaru sosai a hancinta sannan ta buɗe idanu, abinda taji ɗazu da safe game da shine still yanzu ma ta ƙara ji, na yanzu ma har yaso yafi na safen, tsikar jikinta gaba ɗaya ya tashi, kamar ya fahimci halin da take ciki hakan yasa ya kalli su Afrah yana kallon agogo yace "oya kumuje na saukeku a gida kafin magrib," duk da ba haka suka so ba amma cikin su babu Wanda keda zarran yi mai musu, dole suka amsa masa da to, kallon batool yayi yace"bari na sauke su daga nan zan tsaya nayi sallan magriba,me zan siyo miki "budar bakin ta tace cabbage, "cabbage" ya maimaita abinda ta fada gyada mai kai tayi, har zai kara yin wani magana ko mai ya tuna kuma, ya fasa, su Afrah sallama suka mata tace su gaida maah, haka nan cike da kewar juna suka wuce. Suna wucewa aka ana fara kiraye kirayen sallah, tashi tayi, ta daura alwala anan toilet din falon, a nan kuma falon tayi sallah. Lallaba tayi ta koma dakinta ta kwanta, tana ta tunane tunanin make faruwa da itane haka, me yasa take jin haka game da Dr bash, Wanda da ko kaɗan bata jin haka daga gareshi, hasalima ita tsoran lamarin take, amma daga safiyar yau zuwa yamma duk inta daura idanunta a kanshi, sai taji wani mugun feeling dinshi ya taso mata, ɗazu ma matukar dauriya tayi bata rungume shi ba saboda ganin idanun su Afrah, ita dai fatan ta Allah yasa ba wani ciwo bane ya kamata. Bayan ya sauke su Afnan a gida suna tafe suna bashi labarin yadda batool ta dinga cin gayan cabbage da kuma yadda tasa aka kwaso duka turaren sa, yana sauraren su wani nishadi na musamman na ziyartar shi, daga nan masallaci ya nufa yayi sallah, sannan ya nufi Neman cabbage duk inda yasan zai samu, cabbage yaje duk sun tattashi, saboda dare daker ya samu wani mutum yayi mashi kwatancen wani waje a kasuwan gwari, ai ko dai ya tula da yawa dan kusan manyan kwallo goma ya jidar mata, koda ya kamo hanyar gida isha,e ake kira dole ya samu guri yayi sallah sannan ya karaso gida. Tana kwance kan pray mat din da tayi sallan isha,e, taji diran motar shi, wani daɗi ne ya lullubeta ko ba komai zata samu ta shaki kamshin da take so, bata gama wannan tunanin ba taji shi yana sallama a bakin kofar ɗakinta, da sauri ta yunkura ta tashi zaune, tana bubbuɗe kofofin hancinta jira take kawai taji saukar kamshin sa a hancinta. Aikam dai ko minti bai kara ba ya ziyarceta, wani wahalallan ajiyar zuciya ta sauke, tana kara daddaga hanci, tun shigowar shi idanunshi ke kanta duk abinda takeyi yana karantar ta tsab. Hankalin ta yayi nisa wajen shakar kamshin sa, bata ko kula ba har ya ƙaraso cikin ɗakin ya zauna bakin bed, ganin dai ta shagala da yawa yasa yayi gyaran murya, da sauri ta juyo ta kalleshi, yarr yarr haka ta dinga ji a jikinta, idanunta kawai ya kalla ya harbo girkinta kaf, ya gama fahimtar komai, wato dai kakar shi ce ta yanke saka. Ya fahimci irin cikin nan Allah ya bata mai saka jaraba, hakan kuwa ba karamin dadi yamai ba shikam ai gaba ta kaishi, shi yana gani ma addu'an da ya tayi ne na Allah ya taro mai ita, Allah ya karba ya taro mai ita cikin sauki ta wannan hanyar. Fuskewa yayi ya dauke idanshi a kanta yace "ya jikin naki," tace da "sauki" tana binshi da wani irin mayen kallo, yace "to alhmdllh tunda da sauki ni zan wuce ɗakina, cabbage dinki yana kitchen" ya faɗa yana mikewa ya nufi hanyar waje, kasa daurewa tayi, take taji a jikinta idan bata rabi jikinshi ko yaya bane nunfashin ta zai iya daukewa, bata San sanda ta mike ba saidai ji yayi an mai wata irin kyakkyawan runguma ta baya, ta daura kanta a bayanshi tana sauke ajiyar zuciya, hannayenta gaba ɗaya ta zagaye cikin shi dashi. Daskarewa yayi a wajen dama mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki, baiyi wata wata ba kuwa ya zagayo da ita gabanshi ya haɗe bakinsu guri ɗaya, ya shiga kissing dinta a zafafe, batool bata taba sanin ta iya kiss ba saida ta tsinci kanta da mayar mai da martani baiwar Allah jikinta har rawa yake yi, tafiya tayi tafiya lamarin ya wuce na tsayuwa, daga shi har ita basu San yadda akayi suka isa kan bed ba, cikin kankanin lokaci ya rabata da duk wani sitira na jikinta, bai tsaya bata lokaci ba ya dauki hanya, don a yadda ya lura idan yace zai kara wasu mintuna kafin ya shigeta zata iya zaucewa, shi har tausayi ta bashi yadda take abubuwan yasan ba yin kanta bane, abin fa har tsoro yaso ya bashi, amma tunawa da yayi akwai mata da yawa da ciki ke maida su jarababbu, sai ya ajiye tsoron shi a gefe yaci gaba da gashi. Ya samu gamsuwa da jin dadin da bai taba tuananin ana samu a duniya ba, duk wani sha'awan daya tara na kwana da kwanaki saida ya sauke su tsab a wannan daren, bayan gaba dayan su sun samu gamsuwa rungumeta yayi, yana hawayen farin ciki a hankali ya shiga furta"ina son ki my teema, ina mahaukacin kaunar ki, ina son ki my batool, nagode Allah ya saka miki da alkhairi, ina kaunar ki fiye da yadda nake kaunar rayuwata, kece farin cikina kece zabin raina, ina sonki da dukkan ruhi da zuciya," kamar a mafarkin haka taringa jin saukar kalaman sa cikin kunnenta, ya rufe ido sai sambatu yake yi, duk da halin da take ciki na matsanancin kunyar shi hakan bai hanata ɗago da kai ta kalleshi ba, cikin sa'a shima ya bude idanunshi, cikin rawar lebe tace "da gaske kakeyi dama kana sona ba liƙa mata ni akayi kamar yadda ka faɗa ba" tausayi yaji ta bashi sai yake ga kamar bai kyauta ba da yace mata haka, cike da kwarin gwuiwa ya shiga girgiza mata kai yana cewa" kwarai kuwa batool babu Wanda ya liƴa mini ke ni da kaina naje na nemi auren ki, saboda so da kaunar da nake miki,kece my teema kece Fatima ta kece kaɗai macen da zan iya so acikin zuciya ta" wani irin ƙanƙameshi tayi, cikin tsananin farin ciki da jin dad'i ta shiga furta"I luv u 2 mijina nima wlh ina tsananin sonka ina mahaukacin kaunar ka, tare da matsanancin kishinka" kalamanta wani irin daɗi da suka mishi sun samu matsuguni a can cikin zuciyar shi, wani shaukin so da kaunarta ne suka ɗebe shi, take ya sake lalubarta bakinta ya haɗe da mashi, suka koma ruwa, dama itama tana da bukatar hakan. Saida suka sake jiyar da juna daɗi, duk sun gaji hakan yasa ya rungumeta suka shiga bacci sai gabanin asuba suka farka, suna farkawa ya yunkura da niyyar tashi yaje ya haɗa musu ruwan wanka, sai ji yayi ta ruko hannun shi ta baya, kwayar idanunta kawai ya kalla ya fahimci komai, baiyi kasa a gwuiwa ba kuwa ya biye mata, ko da suka yi wanka ya makara sallah a masallaci har an idar dole a gida sukayi jam'i tare, bayan sun idar ya janyota suka koma bed suka shiga ramakon baccin jiya da basu samu yi sosai ba............ hmmmmmm batool da Dr bash rayuwa sabuwa, amma fa da alama fa Dr bash ya manta da warning ɗin maah😊 tun da wuri ku tuna mai, ɗan tayin cikin baiyi kwari ba, kar aje garin cin amarci a jawo ma maah arasa😜 Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌ (In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls) {Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen mu} 💖Tallah!💖 Tallah!!💖 💖Tallah!!!💖 💖 Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da _Rantsattsun lesussuka💃, _Atamfofi manya da k'anana💃 _Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃 _Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃 _Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃 Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu.......... Ga numbern mu kamar haka👇 08062160424 08066891424..... Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌 Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌 Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃..... Page 105 ~ASLAM~ Bayan fitar ta daga dakin dafe goshi yayi ya kama fareti a dakin, yakai gwauro yakai mari ya kasa zama, can dai ya naushi iska tare da cewa"oh my god, yanzu miye mafita" dan tsayawa yayi daga faret din da yakeyi da alama wani tunani yayi, can kuma ya furta "yesss" kafin ya fice daga dakin da sauri kitchen ya fara nufa bata nan, dan haka ya duba falo nan ma wayam, nan take ya tabbatar tana dakinta tunda bata wuraren nan biyu daya duba, dakin nata ya nufa cikin sauri sauri har ya mika hannu ya kama handle din kofar zai tura, take wani shakkar ta ya lullubeshi , zuciyar shi ta shiga ce mishi yanzu in ka shiga mai zaka ce mata, take yaba zuciyar shi amsa da babu, da baya da baya ya dinga yi har ya bar kofar dakin. Tunda ta shige daki ta lalubi bakin bed ta zauna dabass, take duk abinda ya faru tun daga fara ciwon Aslam har zuwa yau ya shiga dawo mata tsab a brain dinta, ta tuna yadda yake tsananin jin jiki da yadda kullum Daren duniya yake fama da matsanancin zazzabi, Ashe duk karya yake mata dan dai kawai ya samu ya rabi jikin tane, bata son karya, balle ma irin wannan karyar da zaka ma Wanda ya aminta dakai, take Kamal dinta ya fado mata a rai, Kamal bai taba yi mata karya ba, hawaye taji yanaziraro mata tunawa da irin yadda Kamal ya nuna mata soyyaya da kulawa, a fili ta furta"Allah sarki ya Kamal, Ashe dai nida kai baza mu zamto abokan rayuwar juna ba" daga haka kuma ta zame ta kwanta girkin da bata karasa ba kenan, haka tayi ta tunane taunane daga nan kuma barci barawo ya sace ta mai cike da mafarkan kamal. Aslam ganin bata fito ba har azahar gaba daya hankalin shi yayi matukar tashi, kusan so biyar yana zuwa kofar dakinta da zumar shiga, sai kuma ya kasa, haka yata zarya bashi falo bashi daki, ko abinci bai samu daman ci ba, kai yunwar ma gaba daya bai jita ba, sai gurin yamma da yaji ulcer na shirin tirnike shi, ya shiga kitchen ya Samar ma kanshi abin tabawa. Sai gurin karfe biyu ta farka, a firgice, take ta shiga furta astagfurullah, mafarkin da tayi a yanzu ya tayar mata da hankali, ta sani ya kamal ya haramta a gareta, tunda ya kasance a yanzu mijin yar uwa kuma kanwarta,amma yadda ta kwanta tana tunanin shi barci ya kwashe ta yasa har take mafarkin shi, kallon agogon dake manne jikin wall din dakin tayi biyu harda minti 10, lokacin tuni har an idar da sallan azahar a masallatai, alwala ta dauro ta fara gabatar da sallah, bayan ta idar kuma ta koma ta kwanta, Aslam ne ya fado mata a rai, ji tayi gabanta ya yanke ya fadi, samun zuciyarta tayi da son sanin wani hali yake ciki yanzu, take taji zuciyarta na azalzalan ta akan ta tashi ta fita ko ganin shi ne kawai tayi, da'ker ta samu tayi yaki da zuciyarta ta tayi fatali da wannan umarnin da take bata, wayar ta ta dauka ta kunna data ta shiga WhatsApp d'inta Wanda rabonta da shi yafi sati, message na gama shigowa ta fara bi daya bayan daya tana dubawa Wanda zata amsa tayi Wanda zata share ta share, haka har takai kan message d'in Khadijah, budewa tayi, idanunta ne ya sauka akan wasu zafafan hotunan da Khadijah ta turo mata yau kimanin kwana uku kenan, hotunan ta ne ita da kamal masu shegen kyau, kala kala cikin wanin irin yanayin da ita kanta baza ta iya fassarashi ba take bin hotunan da kallo, gasu fess da su sunyi wani fresh shar dasu, kallo daya zakama hotunan kasan ma'abota hotan cike suke da tsantsar so da kaunar junan su, yanayin murmushin dake dauke a fuskokinsu kadai ya ishi mai kallo shaidar hakan balle kuma idan ka kalli yanayin styles d'in hotunan, a kasan hotunan ta rubuta, "komai ya daidaita a tsakanin mu yar uwata fatan kema haka daga naki bangaren" Bata sanda ruwan hawaye ya fara wanke fuskar ta ba sai gani tayi yana diga akan screen d'in wayar, ta bata lokaci akan kallon hotunan fiye da awa daya, can kuma Kamar wata tabbabiya ta saki wani kayataccen murmushi, a fili ta shiga furta "na taya ki murna yake yar uwata Khadijah, hakika Allah ya baki miji daya tamkar da dubu, Allah ya zaunar daku lafiya,ya Allah wannan soyayyar junan su da na gani kwance akan fuskokin su Allah ka dauwamar musu dashi har abada" reply ta mata da "wow masha Allah, perfect mach, gsky hotuna sunyi matukar kyau yar kanwata, tunda nake ban taba ganin couples d'in da suka yi marching sosai da juna irin wadan nan ba, kyawawan masoyan asali, Allah yabar kauna romeo & Juliet " a karshe ta kawata rubutunta da emoji kala kala, na murna dana murmushi tayi sending, sauka tayi a WhatsApp din ta koma gallery folder daya ta ware na hotunan kamal zallah, take ta shiga folder ta fara deleting d'in duk wani photo da ta Sani na shi dake wayarta, yadda take deleting hotunan shi haka takeji yana fita a zuciyarta, saida tayi deleting duk wani abu daya shafi kamal a wayarta, daidai da app da tasan shi ya saka mata a wayar saida ta goge dan kar ta dinga tunawa da shi, bata bar komai ba hatta da phone number dinshi saida tayi deleting a wayarta, take taji zuciyarta ya samu wani irin space mai girma wanda a da babu shi a zuciyarta ta, lallai kamal ba karamin wawakeken gurbi ya samu a zuciyar ta ba,wasai take jin kanta a yanzu babu kowa a zuciyarta. Wayar ta da yayi ringing ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, sunan da ta gani na yawo a saman screen d'in wayar yasa bata san sanda ta saki kayataccen murmushi ba, cike da dauki ta daga wayar tare da cewa "Assalamu alaiki yake ummin mu" daga daya bangaren ummi tayi murmushi mai sauti sannan ta amsa mata da "wa'alaikissalam Asma'ul-husnah fatan kuma lafiya ya my son yake da fatan ana kula da shi sosai ko" murmushi tayi cike da jin kunyar maganar ummi tace "yana lafiya umminmu" ummi tace " masha allah yana gida ne ko ya fita don nata kiran wayar shi yanzu kafin na kira naki bai daga ba" Asmah tace "gsky bansan ko yana nan ba ko ya fita" ummi cikin zare ido tace "na shiga uku ni Aminatu, ban gane bakisan ko yana nan ko ya fita ba" Asmah cikin ko in kula tace "wlh umminmu ni rabona da shi tunda safe" ji tayi ummi ta rabka wani uban salati, kafin tace "Asma'u! kardai kice min zaman da kukeyi kanan ke da Aslam d'in wata da watan ni, Ashe baki da wayau ke shashasha ce ban Sani ba" tuni Asmah ta shiga zazzaro ido jin kalmomin dake fitowa daga bakin ummi, take ummi ta rufeta da fada ta inda take shiga bata nan take fita ba, hankalin Asmah bai kara tashi ba saida ta tsinci muryar ummi na cewa "nasani, nasan abinda yasa kika ki bama Aslam dama duk da irin tarin soyayyar daya yake miki, kamal ne ko? To wlh ki kama kanki dan kamalu tuni ya shafe babinki, yanzu haka zancen da nake miki Nana Khadijah ciki ne da ita har na wata biyu, ke kina nan kin tsaya wasa da daman ki " tuni hawaye ya gama wanke fuskar Asmah, cikin muryan kuka ta bude baki tace "ummi wlh b" cikin tsawa ummi ta katseta da cewa "wlh me? ni babu abida zaki gaya min a yanzu, ki Sani shi so da kike gani tamkar tsuntsune dake sauka akan bishiya domin yayi kiwo, idan ya sauka a bishiya ya rasa abin da zai kiwata dole zai fira daga wannan bishiyar ya koma wata, idan kuma ba'ayi a hankali ba bazai sake wai wayar wannan bishiyar ba kenan har abada, idan zaki kama kanki ki kama, Aslam yayi miki laifi mai girma a baya kuma ya gane kurensa, tunda kika ga Allah ya sake hada ku a karo na biyu shi kadai yasan abinda ya boye a tsakanin ku, kiyi hakuri ki rungumi kaddararki da hannu bibbiyu, bari na tuna miki wani abinda kika manta kinsan dai bake kadai bace mace a gurin Aslam ba ko? ina fatan kina tune da zainab" take gabanta yayi wani irin faduwa,jin abinda ummi ta fada tabdijam har ga Allah ta manta da wata zainab matar Aslam, wahayenta ne suka kara karfin gudu, take ta kara yunkurin yin magana dan ta kare kanta, ummi lura da ta yi jikinta ya gama yin sanyi yasa wannan karon ta bata daman cewa wani Abu, baki na rawa tace"wlh umminmu ba abinda kike tunani bane, wlh ummi a halin yanzu babu burbushin soyyayar ya kamal ko digo a zuciyata," take kuma ta shiga bama ummi labarin abinda ya faru yanzu yan mintocin da suka gabata, kasancewar basa iya boye ma ummi komai dake damunsu a rayuwar su. Sauke ajiyar zuciya ummi tayi yanzu hankalin ta yadan kwanta jin hakan daga bakin Asmah, tasan komai zaizo sa sauki tunda babu kowa yanzu a zuciyarta, kwantar da murya ummi tayi cikin sigar lallashi ta fara cewa" alhmdllh naji dadin jin wannan maganar daga bakin ki Asmah, yanzu kuma lokacin yayi da zakiba Aslam dama domin ya mallaki wani fili daga zuciyar ki, Aslam yayi miki laifi kuma ya gane kurensa a halin yanzu ya kamata ki saurare shi, tunda kikaga haka Allah kadai yasan menene ya boye a tsakanin ku, kuma nasan keme bazakice a yanzu bakijin Aslam ko kadan bane a ranki, ko nayi karya?" Ummi ta tambaya, shiru Asmah tayi ta kasa bata amsa, dan kam idan har tace batajin shi a ranta yanzu tayi ma Allah karya, jin shiru yayi yawa yasa ummi tace "uhummm ke nake saurare fa" cikin sanyin murya tace "umminmu a halin yanzu wlh bana jin kin yaya Aslam a raina kuma kai tsaye bazan iya cewa ina sonsa ba,nasan dai ina jin matsanancin tausayin shi a raina, kuma nakan ji kewan shi idan baya kusa dani bayan wadanan, bazance ga wani Abu da nake ji game da shi ba Ummi" murmushi ummi tayi a daya bangaren a zuciyarta tace ahaf magana ya kare, a fili kuma tace "naji hakan ma wani ci gaba ne da sannu zaki soshi, amma fa sai kin saka ma ranki hakan, nidai yanzu abinda nake so dake, idan har bakyaso nayi mummunan fushi dake, na baki nan da sati guda naji kyakkyawan sauyi, a zaman takewarku, idan kuma ba haka ba wlh zanje na samu Alhaji baba, da mallam na gaya musu, sannan kuma na samu mummyn ku da daddy na gaya musu suma, kinsan dai wanene Aslam a gare su baza suji dadi ba idan sukaji abida kike masa" girgiza kai takeyi kamar a gaban ummi take, ummi nayin shiru ta shiga cewa a firgice "dan Allah ummi kiyi hakuri kar ki gaya musu Wlh zan sauya, insha Allah zan karbi kaddarata da hannu bibbiyu" wani wahalallan ajiyar zuciya Ummi ta sauke sannan tace "alhamdulillahi naji dadin hakan, kuma ina nan ina tsumayen jin daddadan labari, nifa so nake kafin shekara ta zagayo kowaccen ku ta ajiye min jika, inso samu ne ma yan bibbiyu ko uku uku nake so" dariya Asmah ta kwashe dashi, daga nan kuma ummi ta shiga janta da wasa kamar wasu kawaye , karshe kuma ta shiga koyar da ita dabaru kala kala wadan da zasu amfaneta sosai nan gaba , Asmah taji dadin hakan sosai, nan ta bude memory tana ta saving dinsu, suààaàà࣠Aàqnfi awa biyu suna waya kafin sukayi sallama. Komawa tayi da baya ta kwantap akan bed dinta tayi lamo maganganun da sukayi da ummi ya matukar shigar ta , jikinta gaba daya yayi sanyi kalau, musamman kan cewa da ummi tayi zata fadama su mummy abinda ke faruwa,koba komai mummy da daddy sune mutanen da take matukar so bayan iyayenta, kuma baza suji dadi ace taki abinda suka haifa ba, koba komai Aslam jininsu kuma jinin mutum mafi daraja a idanunta Alhaji baba........... Oum ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabillilah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 106 Haka suka ƙare wannan yinin cike da damuwa a zuciyar kowannen su, a bangaren Asmah Abu biyu ke damunta, maganganun da sukayi da ummi ɗazu, sai kuma, tunani da kewar Aslam daya addabi zuciya da ruhinta, gaba ɗaya jinta take kamar wata Mara lafiya, a haka har lokacin kwanciya barci yayi, koda ta kwanta kasa bacci tayi sai juyi kawai takeyi a makeken bed dinta, karshe ta janyo pillow ta rungume a kirjinta kamar yadda ta saba amma a banza, ji takeyi kamar ta tashi ta fita ta ganshi koda a boye ne,ba tare daya ganta ba,ba karamin dauriya tayi ba da ta hana kanta aikata hakan, daga karshe ta kwabi kanta da cewa, ya kamata ta kama ajinta koba komai ai shiya mata laifi shi ya kamata ya fara nemanta ba ita ya kamata ta fara neman shi ba. A bangaren Aslam kam ya ma fita shiga damuwa, har karfe goman dare ya kai a falo yana zaman jiran tsamanin fitowarta, amma shiru gashi shi kuma ya kasa zuwa ya tunkareta, ganin goma da kwata yasa ya mike jiki ba kwari ya nufi dakin shi, wanka yayi tare da shirin bacci, kashe wuta yayi ya haye bed dinshi ya kwanta, saidai koda gigin wasa babu alamar bacci a idanun shi, gani yayi ma gadon ya mishi wani irin mugun fadi da girma, kai gaba daya ɗakin ma, ga wani irin sanyi da yakeji yana shigar shi duk da kuwa ƙudundunewa da yayi da katon bargo. Idanun shi a bude kerr agogo ya buga 12am dai dai, kasa daurewa yayi ya mike ya kunna wutan dakin tare da zura slipas dinshi ya fice daga ɗakinshi ya doshi nata gaban shi Na faduwa, gara yaje ya tunkareta ayi wacce za'ayi komai ta fanjama fanjam, don ya tabbatar idan bai sanyata a idanunshi yau ba lallai bazai iya rintsawa ba. Saida yayi tsayuwar kusan minti goma a bakin kofar yana tunanin anya kofar ma a bude take ko a kulle, a hankali yakai hannunshi kan handle din kofar ya murda tare da tura kofar a hankali, wani wawan ajiyar zuciya ya sauke jin kofar a bude. Ware idanunta tayi daga lumshesun da tayi jin motsin ƙarar taba ƙofar dakinta, kafin tayi tunanin wani Abu ta ga ya tura kofar ya shigo dauke da munafukar sallama a bakin shi, ita ba a boye ba kuma baza'a kirata a fili ba ,wani irin mugun dadi ne ya ziyarceta, take ta sauke wani boyayyan ajiyar zuciya, a halin da zuciyarta ke ciki kiriss ya rage ta tashi ta bishi a cikin tsakiyar daren nan, saidai gashi Allah ya kawo mata shi, lamo tayi tana kare mai kallo ta cikin hasken kofar daya bari a buɗe. Shikam Aslam bai ganta ba kasancewar dakin dimdim yake da duhu, kuma daga haske ya fito,idanunshi baya iya ganin komai sai duhu, jin bata amsa sallaman shi ba, hakan ya Tabbatar masa tayi bacci, wayar shi ya kunnu ya haska dakin ganin haka yasa tayi saurin rintse idanunta ba tare da ya ganta ba, lallabawa yayi a hankali ya kwanta a bayanta, duk abinda yakeyi tana jinsa, shiru sukayi daga ita har shi Na kusan 20 minutes, shi yana tunanin tayi bacci, ita kuma mamakin karfin halin shi na neman kashe ta, tayi shiru tana jiran taga mai yake shirin aikatawa. A hankali ya dinga matsawa kaɗan kaɗan jikinta, har ya manna kirjin shi da bayanta, jin shiru bata motsaba yasa ya mike hannu a hankali ya rungumota jikin shi sosai, yana sauke ajiyar zuciya. Kamar daga sama yaji tayi gyaran murya tare da cewa "welldone" ba shiri ya saketa tare da mikewa zaune, itama mikewan tayi tare da lalabur makunnin wutar dakin mai haske ta kunna. Kallon cikin idanun juna suka shiga yi, kowannensu idanunshi cike da kewa da begen Dan uwanshi, zuciyoyinsu kamar yayi tsalle ta fado kasa tsabar a zalzalan da take musu, yadda ya ganta haka sanye cikin kayan barcinta masu dan kauri riga da dogon wando ga kuma gashin kanta daya barbazu kasancewar bata dauresu ba, sai tashin kamshi take ba karamin hargitsa shi tayi ba ji yake kamar ta wuff ya rungumota amma babu hali. Marairaice fuska yayi, cikin wata irin marainiyar murya yace,"my husnah dama kema bakiyi bacci ba? " shiru tayi bata amsa ba saima dauke kanta da tayi daga kallon shi, ganin haka yasa ya matsa gabanta ya mika hannunshi ka kamo nata ya rike cikin nashi, a hankali cikin marainiyar muryarshi ya fara cewa"kiyi hakuri Mrs Asmah na San na miki laifi mai girman gaske, amma ina mai baki hakuri kisani wlh ni ba makaryaci bane, hasalima na tsani duk makaryaci, soyayyarki ce ta maidani haka kaunar kice ta rikiɗar dani na koma haka, ina sonki Asmah nasani kema zaki shaida haka, Dan Allah ina rokon ki da kiji ƙaina ki tausaya min ki bani dama na mallaki wani sashe a zuciyarki komin kankantarsa,zuciya ta na daf da kaiwa matakin da baza ta iya juriya akanki ba, hakurina ya kusa karewa a kanki, na miki alkawari husnah zan maki duk wani abin da kike tsammanin samu daga wurin mijinki fiye da yadda kike hasashe, zan nuna miki zallar madarar soyayya mara sirki, fiyye da yadda kike tunani, zan kula dake fiyye da yadda zan kula da kaina da tarin dukiyoyina, zan biya dukkan bukatarki,wanda na sani da Wanda ban sani ba fiyye da tunaninki, zan kare duk wani hakkin ki daya rataya a kaina iya karfina na, zan biya miki bukatar rai da gangar jikin ki yadda baki taba tsammani ba, Dan Allah Mrs Asmah ki bani dama komin kankarta ta, ki yarda dani da abinda nake fada miki wlh baza ki tabayin nadama ba,ina sonki my husnah ina mahaukacin kaunarki, ki tausayamin ki dubeni Dan fiyayyen halitta annabin rahama,sallahu alaihi wasallam" A zuciyarta tama annabi salati itama, tare da dagowa ta sauke mishi dara daran idanunta a kanshi, shima dama idanun shi nakan fuskarta, kallon idanun juna sukeyi, kowanne da abinda yake karanta a cikin idanunn ɗan uwanshi, ta hangi tsantsar matsanancin soyayyarta a cikin kwayar idanunshi tare da tsantsar gaskiya akan abinda ya fada mata yanzu, yayinda shi kuma ya hangi tausayi, da burbushin soyayya da kaunar shi a idanunta. Itace ta fara katse kallon ta hanyar zare hannunta cikin nashi, tare da juyawa mai baya ta kwanta, gaban shi ne ya yanke ya fadi me hakan me nufi, yes take nufine kokuma A'a. Sun kwashe kusan 20 minutes a haka babu Wanda ya sake cewa komai, kundunbale yayi ya, mika hannu a hankali ya daura akan damtsen hannunta, wani irin shock taji a jikinta, lumshe idanunta tayi tare da budesu a hankali. Ganin tayi shiru bata hanashi hakan ba, yasa a hankali ya shiga shafa hannun yana matsawa a hankali, daga karshe kuma ya koma ya kwanta, tare da janyota jikinshi ya rungume, a tare suka sauke ajiyar zuciya. A hankali ya shiga cusa kanshi cikin sumar kanta dake nan a kwance Dan Sam bata iya parking din gashinta idan zata kwanta, yana shakar daddar kamshin dake tashi a cikin gashin, yayinda ya mika hannushi, ya dage Dan rigarta na barci ya daura tafukan hannayenshi akan shafaffen cikinta yana shafawa. Sun kusan kwashe 30 minutes a haka, ko wannensu cike da begen Dan uwansa, a hankali ya farayin sama da hannayenshi yana kokarin kaisu inda zuciyar shi ke muradi,inda tun daga ranar daya gansu har yau hoton su bai taba bace mai a idanun shi ba, jin haka yasa tayi tsam tana zazzare idanu. Kamar Wanda aka dannawa tsop, haka ya tsaya ƙem da hannayenshi, zuciyarshi ce ta kwabe shi da cewa, kul Aslam me kake shirin aikatawa ne haka, ka cika zalama wlh, kabi komai a hankali ka samu kaɗan raba ta ƙyaleka kuma kana neman ka wuce gona da iri, ka kiyaye ka maida zalamarka ka Adana, ka lallabata ka koya mata yadda zata saki jiki da kai ta yadda wata rana ita da kanta sanda zata mika maka kanta bata da labari, amma yanzu idan kayi haka saita dauka ba soyayyar gaskiya kake mata ba wani Abu kake bukata a jikinta, da wannan shawaran ya dingayin kasa da hannun shi harya maida shi inda yake da. Ajiyar zuciya ta sauke jin bai karasa can ɗinba, shiru sukayi suna sauraren bugun zuciyar juna kowannen su zuciyar shi cike da anashuwa, kusan awa daya a haka kafin a hankali wani irin daddadan barci da ta daɗe ba tayi irin shi ba ya kwasheta. Saukar nunfashinta da yaji ya tabbatar mai da barci ya kwashe ta, murmushi ya saki tare da kissing tsakiyar kanta, shima a hankali ya lumshe idanu ba bata lokaci barci ya kwashe fuskar shi dauke da kayataccen murmushi. Wani irin barci mai dadi sukayi ranar wanda suka daɗe basuyi irin shi,bacci suke hankali kwance kowannesu furkarshi dauke da murmushi mai kayatarwa, gaba daya ya kanannadeta a jikinshi ta yadda ko kwakkwaran motsi tayi saiya a farka. Basu suka farka ba kuwa saida hasken rana ya ratso cikin dakin,ita ta fara farkawa,gani tayi haske gaba daya ya cika dakin alamar har rana ya bullo, bin jikinta tayi da kallo ganin yadda ya kanannadeta gaba daya, ya saka ta ajikin shi bata da damar motsawa kallon fuskarshi tayi, fayau da shi yana dauke da murmushi sai sharar barcin shi take hankali kwance, kura mishi idanu tayi ta kalle shi son ranta,gaskiya yaya Aslam kyakkyawa ne ajin karshe, ta ayyana hakan a ranta, murmushi ta saki, bata San sanda takai ɗan bakinta tamai kiss a wuya ba, ahankali kuma ta shiga zare jikinta daga nashi, harta gama ta yunkura a hankali zata mike karaf taji ya cafkota ya maidata ya kanannade har fiyye da da, cikin murya mai ciki da barci ya shiga ce mata a kunne "ina zakije? Dan Allah karki gusa kibar mahaukacin masoyinki shi kadai" cikin in,ina tace"gari ya waye fah" ba shiri ya waye idanunshi tare da sakinta ya mike zaune yana furta"subhanallah astagfirullah" mikewa yayi ya shiga toilet din dakin da sauri yayi brush tare da dauro alwala ya fito, a bakin bed ya sameta zaune ta ziro kafafunta kasa, jin motsinsa yasata dagowa ta kalle shi murmushi ya sakar mata tare da mika mata hannu alamar ta miƙo nata, ba musu ta mika mishi, Dan ta daukarwa ummi alkawain cewa duk abinda ya umarceta zatayi matukar bai sabawa Allah ba. Ita kuma ummi tayi amfani da wani hikima ne ta manya ta daurawa Asmah wannan nauyin tasan hakan zai bada gagaruman gudunmawa wajen daidaita tsakanin su. Har cikin toilet din ya kaita, tare da kokarin yi mata alwala, tana da uzirin kama ruwa, ganin baida niyyar fita, yasa ta naimi alfarman ya bata waje zata kama ruwa, ba musu kuwa ya fice daga dakin ma baki daya, kama ruwan tayi tare da yin brush a karshe ta dauro alwala, koda ta fito baya dakin, direct gaban wawakeken wardrobe dinta ta nufa, wani dogon Riga Mara nauyi ta fitar tare da hijjab din da take sallah dashi ta ajiye a bakin bed, cire kayan jikinta na barci tayi, har pant din kuwa bata bari ba dan bata yarda da tsarkinsa ba, dama babu maganar saka bra, wani sabon wankakken pant ta dauka ta saka sannan ta dauki dogon rigarta, ta daga zata zira kenan ya shigo dakin dauke da sallama, kallo daya ya mata yayi saurin dauke kai kamar baiganta , yayinda ita kuma tayi saurin karkare zira rigarta, sannan ta saka hajab dinta. Sanye yake da jallabiya na maza ruwan hanta mai guntu hannu, direct inda take ajiye pray mat ya karasa dauka yayi ya shimfida duka biyun, nashi a gaba nata a bayan nashi daga gefen dama, ganin haka bata tsaya bata lokaci ba, ta daidaita sahu, jam'i ya jasu kara'i saboda makaran da sukayi, bayan sun idar kuwa, sunyi tasbihi, ya shiga kwararo musu addu'o'i manya manya, batayi wani mamaki ba kasancewar ta riga tasan shiɗin yana da ilimin addini sosai tunba yau ba. Bayan idar da dukkan addu'o'in juyowa yayi da murmushi a fauskar shi yana kallonta, cikin sa'a kuwa itama ta dago kai tana kallon shi, wani irin kyau kwarjin da haiba taga ya kara mata ba shiri tayi kasa da kanta tare da cewa "ina kwana ya Aslam" shiru yayi bai amsata ba, bai kuma daina kallonta ba, jin shiru yasa tayi tsammanin ko baiji bane, hakan, yasa ta sake maimaita gaisuwarta, da Dan karfi wannan karon, still ba amsa, hakan yasa ta dago kanta ta kalle shi, tare da sake cewa"ina kwana Mr Aslam" maimaikon ya amsa mata sai gani tayi yakai Dan yatsan shi manuniya kan labbanshi, yace mata "shiiiiiiii" da mamaki take kallon wannan irin ikon Allah, murmushi ya saki tare da cewa, "daga yau na haramta irin wannan gaisuwar a tsakanin mu indai a ba agaban mutane muke ba" kamar sokuwa haka take binshi da kallo ganin haka yasa yace kinsan wani irin nake so, girgiza mai kai tayi alamar A'a, yace kina son ki sani, sake girgiza mai kai tayi alamar Eh. Aiko kafin tayi wani tanani taji ya janyota jikinshi ya hade bakinsu ya lalubi harshenta ya cafke ya shiga bata wani irin slow kiss mai saurin kashe gaɓɓai. Wani irin zaro idanu Asmah tayi, take firgici mamaki da tsoro suka diran mata a lokaci guda, tunda take a rayuwarta wannan ne karo na farko da wani mahaluki ya sumbaceta............... Comment dinku shine zai tabbatar min da cewa kunyi farin cikin dawowana online😍 Daga yau posting zai ci gaba insha allahu har sai mun ɗire💖 Ɗinbin godiya a gareku masoyana masuson farin ciki da da cigaba na, wadanda sukayi contributing din kudi domin su bani kasancewar sun samu labarin wayata ta samu Matsala, na gode muku Allah ya saka muku da alkhairi Allah yabiyaku da Gidan aljannah madaukakiya, inayinku over💋 Wadanda sukayi niyar bayarwa Allah bai basu iko ba kuma na gode Allah yaga niyyarku, wadandama basu niyya ba duk na gode Allah yabar kauna😬 Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce tarasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 107 Tun daga wannan rana rayuwar Aslam da Asmah ya canja, wani irin kulawa da soyayya yake nuna mata kamar ya hadiyeta, gaba daya ya sangartar da ita ya koyar da ita soyayyar shi mai tsanani bataji bata ganin kowa a halin yanzu sai Mr Aslam ɗinta, tun daga wannan rana basu kara raba gurin kwanciya, kullum Daren duniya tare suka bacci rungume da juna, yanayi yana lallatseta da wayau musamman gurin yi mata addu'an barci yace zai shafa mata, wani bin sarai takan gano shi saidai tayi murmushi a ranta wani bin kam har yayi abinda zaiyi ya gama bata fahimtar komai kasancewar shi gwanin iya pretending, tun tana ɗari ɗari da shi har ta saki jikinta dashi sosai, zuwa yanzu ko kasheta akace za'a idan bata rabu da Aslam ba, saidai a kashe ta kam, badai ta taba furtawa mashi so ba, amma ko ita karan kanta a yanzu ta shaida ba karamin so take mashi ba, komai tare sukeyi a Gidan suyi girki tare suci abinci tare suyi aikin gida tare suyi wasanni tare, harda kallon kafa yi suke ga TV game daya koya mata shima sunayi, tun bata iyaba in sun zauna saidai yaita cinyeta harta kware itama, wasa harda su goyo goyo da doki duk yi sukeyi, wanka ne kawai basayi tare shima ita ta taka mai burki, Dan indai tashine tasan wannan duk mai sauki ne a gareshi, duk wannan sabon da sukayi bai taba nuna yana son ya kusanceta duk da kuwa a kullum burin shi bai wuce hakan ba, har addu'a yakeyi idan yayi sallah akan hakan, alkawari ya daukarwa kanshi na cewa saita saki jiki dashi, saiya haukatar da ita da soyyar shi ta yadda duk randa ya bukaci hakan baza ta iya hanawa ba , duk da ko yanzu yasan tana tsananin kaunarshi fiyye da yadda ya zata, yasan kuma ko a yanzu bazata iya hana shi kanta ba. A bangaren Asmah kam a halin yanzu ba kanta ba ko duniya idan tana dashi Aslam ya nema a gurinta da gudu zata mallaka mai, balle kuman kanta, ita kanta a halin yanzu bata da burin da wuce su zamo Abu guda, saidai koda wasa baza ta taba nuna mai hakan ba koda kuwa a fuska ne domin kuwa ita macece, mace kuma da kunya da kamun kai da kuma aji aka Santa, bancin haka wannan ba irin tarniyar da mummy ta basu kenan ba, amma kuma a shirye take tana maraba dashi a duk sanda ya gama kwana kwanan shi ya dawo kan hanya. ~BATOOL~ Yau kimanin wata ɗaya kenan da bayyanar cikin batool, babu abinda sukeyi sai barzar amaraci, batool fa da gaske ta zama jarababbiya ta karshe kullum indai Dr bash na gida suna makale da juna ana harka idan kuwa ya fita ta ta dinga damunshi da kira kenan tana tura mai text a kai a kai, wata ran har daga asibiti sai ya dauki excuse ya dawo idan ta saka mai kuka. Shima a nashi bangaren yana matukar kokarin biya mata bukatarta amma duk da haka saida ta nemi ta kure shi duk da kuwa cewa shima ba baya ba, ganin haka yasa dole ya nemi wani ingantaccen maganin bature na kara karfin maza yana hadawa dashi, zuwa yanzu tasan da ciki a jikinta kuma tayi matukar farin ciki, yadda ta nuna farin cikinta abin har yaso yaba Dr bash mamaki, haka suka shiga tattalin cikinsu a tare cike da tsantsar soyayya da kulawa, Dr bash wannan karon da kanshi ya samu maah ya gaya mata batool ta samu ciki, maah najin haka tace "ahaf dama ai na fada kake min musu" da'ker Dr bash ya samu maah ta fahimci yanzu ne aka samu cikin da babu, yayi haka ne kuwa Dan yaga yadda taketa lissafin watannin cikin kar azo lokacin data lissafa za'a haihu taga ba'a haihu ba su shiga uku, Dan sarai yafi kowa sanin rigimar maah farin sani. Da kanshi ya kira Aslam ya fada mai batool nata hana shi amma yaki ji, da wai harda su daddy zai kira ya fada musu, saida ta saka mai kukan shagwaba tana daka tsalle sannan ya bari, yana dan Allah ta rufa mai asiri ta daina wannan tsalle, tum daga nan batool ta samu logon shi,da tace Abu yaki yi sai ta saka kukan shagwaba karshe ta tashi ta kama dira tana tsalle ko baima Allah dole ya mata. Lokacin da Dr bash ke sanar da Aslam batun cikin batool wani irin tsam Aslam yaji a ransa take zee ta fado mai a rai, har a bada bazai taba manatawa da abinda zee ta mai ba na salwantar mai da gudan jininsa da tayi, sharewa yayi ya shiga taya Dr bash murna karshe ya shiga tsokanar shi kamar yadda suka saba yima juna matsayin su na abokai, dariya Dr bash yayi jin abin da Aslam dinke cewa, bai tankashi ba kamar yadda ya saba saima cemai yayi"duk abinda zakace kace bazan tanka ka ba kasan yanzu kai babban yayan mune,ni wlh ma yanzu kunyarka nake ji" Aslam bàisan Wanda ya lailayo ashar ya durawa bashir ba, ba shiri ya katse kiran yana tikar dariya, bayan gama wayarsu Aslam zama ya gyara ya kwantar da kanshi a jikin kujeran da yake zaune a falon shi, wani irin kwadayin son haihuwa ne ya taso masa, gaskiya yana son yara sosai yana matukar son yaga jinin shi a doran kasa shiyasa har yau ya kasa yafewa zee abinda ta mai, damuwa sosai ya wuni dashi a wannan ranar,har saida takai Asmah ta fahimci halin da yake ciki duk da kuwa kokarin boye matan da yaketa yi. Bayan sunyi shirin kwanciya yana daga zaune tsakiyar bed yana karanto addu'o'in Neman tsari yayinda mutum zai kwanta barci, zuwa tayi ta zauna a gabanshi ta kwantar da kanta a kirjinshi, saida ya gama addu'o'in ya shafa, sannan ya tsinkayi muryarta tana cewa"meyake damunka ne yau Mr Aslam gaba ɗaya yau baka cikin walwala kamar wani Abu na damunka, Dan Allah ka sanar damuwarka muyi shearing matsalolin mu shine amfanin zaman tare" yaso ya boye mata amma haka kurun yaji ya kasa, take ya labarta mata abinda ke damunshi ba tare da ya iya boye mata komai. Duk da taji dadi sosai tayi farin ciki da jin cewar batool nada ciki, amma bata nuna hakan a fuska ba saboda halin da mijin ta ke ciki, kwarai ta tausaya masa, sake kamkameshi tayi da kyau, cikin murya mai nuna tsantsar tausayawa ta shiga cewa, "kayi hakuri ya Aslam hakika zainab bata kyauta maka ba, ta zalunceka, kaci gaba da addu'a Allah zai baka wasu masu albarka "ba karamin dadi yan kalmominta da basufi a kirga ba suka mai, take yaji wani irin nutsuwa ya saukar mai a zuciya, dago da kanta yayi yana kallon fuskarta, itama nashi fuskàr ta kalla idanunshi ya sarƙe da juna, a hankali cikin sanyin murya ba tare da ya dauke idanunshi cikin nata ba yace"husnah ta kin tabbatar da abinda kike fada" cike da garfafa gwuiwa ta girgiza mai kai kafin tace"duk wani mumini na kwarai baya taba yanke kauna da rahamar ubangiji, insha Allahu ya Aslam Allah zai musanya maka da wadansu yayan masu albarka" ciki da tsananin jindadin kalamanta ya kankameta da karfi yana sauke ajiyar zuciya, itama luf tayi a faffadan kirjinshi tana sauraren bugun zuciyar sa. ~ZAHRA~ Misalin karfe takwas da rabi na dare, zaune suke gaba daya su a falo ita da yan yaranta, Ahmad na rungume a jikinta yayi lamo alamar yana shirin barci , Anisa kuma tayi pillow da cinyarta, yayinda hanan ke kwance akan 2 sitter, suhail kuma na daga gefenta, wani cartoon suke kallo mai dadi a mbc 2, gaba dayansu cikin ado da kwalliya suke musamman ma ita uwar gayyan, kullum haka zaka gansu fesfes kamar wasu kwankwasan injin, gaba daya hankalin su ya raja'a akan kallon da sukeyi. Sallaman Barr ne ya dawo dasu hayyacinsu, da gudu duka yaran suka nufeshi, suna fadin daddy oyoyo, daddy oyoyo, ba shiri kuwa ware musu hannayenshi ya rungume su gaba daya, dago kai yayi ya kalleta ganin ita bata taso tamai oyoyon ba tare da yara kamar yadda suka saba kullum, suna hada ido saima yaga ta dauke kanta ta mayar kan TV, murmushi yayi a zuciyar shi yace "babyna Yar daru" daukar Ahmad yayi ya rike hannun Anisa yayinda hanan da suhail suka amso kayan hannun shi karaso cikin falon sukayi, ya nemi waje ya zauna yaran kuma suka baibaye shi, kallon shi tayi ba yabo ba fallasa, a dole tana fushi dashi tace"sannu da dawowa daddyn hanan" "Daddyn hanan! ya maimaita sunan da ta kira shi dashi yau, maimakon habibi da take kira kullum ko a gaban waye kuwa share wa yayi ya amsa ta da "yawwa my baby ya gida ya yara" a takaice take "lafiya" tare da mikewa tace bari na haɗa maka ruwan wanka, ta riga ta sani wanka yake fara yi idan ya dawo kafin yayi komai, dakatar da ita yayi ta hanyar cewa, "ki barshi bari na hada da kaina ki zauna da yara ina zuwa" ba musu kuwa ta dawo ta zauna, mamakin tane ya kara baibayeshi, ya Tabbatar lallai yau baby na fushi dashi, inda haka kurum ne yace tabar hada ruwan wankan nan baza ta taba yarda ba, cewa zatayi zai hanata samun lada, amma yau yana mata magana ba musu ta bari. Mikewa yayi ya wuce ciki, domin yin wanka, dakinshi daya ke nan cikin part dinta ya nufa,dan tun bayan tafiyar maryama ya kulle nashi part din ya tattaro ya dawo nan baki daya, Dan bazai yuwa su dinga tafiya can suna barin yara su kadai ba. Bayan shigewar shi ta dauki ledar tsarabar daya kawo musu ta bude ta damkawa kowa nashi, kayan kwalama ne dangin su chocolate biscuits, sweet da sauransu, nan suka zauna kowa ya shiga cin nashi, bayan sun gama har zuwa lokacin bai fitoba, ga dare nayi kuma yara gobe akwai school, kawai tace su tashi ta rakasu dakinsu, ba musu kuwa suka tashi, kinkiman Ahmad tayi da ya riga yayi barci suka wace, saida ta gama musu komai na shirin kwanciyar su, ta musu addu'a tana shirin kashe musu wuta ta fice ya shigo dakin, karasawa yayi shima ya musu addu'o'i ya shafa musu shima, ganin ya gama ya mike zai fice yasa ta saurin ficewa ba tare data jira shi ba. A dining ya sameta tana serving dinshi dinner, kujera dake facing dinta yaja ya zauna, yana kallonta sai wani ciccin magani take tana kumbura fuska, dariya yake mata a zuciyar shi sarai ya gane abinda takeyiwa fushi, shi mamaki ma take bashi, lallai Zahra tanada kyakkyawan zuciyar. Plate ɗin data tura mai gabanshi ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya Lula, kallonta yayi yana murmushi tare da cewa "nagode amaryata inasonki sosai babyna" wani harara ta zuba mishi mai kayatarwa, dariya ya kwashe dashi tare da cewa "wow wannan kallon luv din gaskiya ya kayatar dani, ki dinga min irin shi kullum kiñji my baby" jin haka yasa ta gimtse hararan tare da dauke kanta gefe, tana turo baki, a haka ya gama cin abincin yana yi yana tsokanarta, yana mata dariya, ita ko sai kara kunbure fuska take a dole tana fushi. Mikewa yayi bayan ya ajiye cokalin ya daukin tissue yà goge baki, gyatsa yayi yana shafa cikin shi, tare da cewa ”alhmdllh girki yayi dadi yama fi na kullum dadi, inaci kamar kunne na zai tsinke" yanzu ma still bata tanka shiba saima kara cuno baki da tayi tare da mikewa tana kimtsa dinning ɗin, tattare kwanika masu datti tayi ta kwasa zuwa kitchen, ba tare da ta tanka shiba, binta yayi a baya zuwa kitchen din yana ta mata magana ta share, sai ma wanke wanke data tsiri hadawa zatayi, ganin alamar zata wàhalar dashi yasa ya shammaceta ta baya tana cikin hada ruwan kumfa taji anyi sama da ita ta baya, wutsil wustil ta fara yi tana son kwacewa amma ba hali donba rikon wasa ya mata ba, ganin dai da gaske bazata iya ba yasa ta hakura tare da yin lamo a hannun shi kamar wata yar jinjira. Ganin ta nutsu yasa ya fara takawa da ita a hañunshi a hankali, bai diretà ko ina ba kuwa sai tsakiyar bed dinsu,kafin tayi yunkurin tashi ya bita da sauri ya danne , kokarin ture shi ta shiga yi ta kasa, hannunta ya hada duka ya rike tare da cewa cikin muryar lallashi, "haba my baby meke faruwa ne haka, wanene ya taba min ke ne haka yanzu mu fara shari'a dashi daga nan har kotun koli, uhummm, gayamin kinji babyna" kukan shagwaba ta fashe dashi tana matsar kwallah tare da cewa "ba kaibane" zaro ido yayi tare da cewa "subhanallahi ni da kaina?" ta girgiza mai kai alamar eh, yace "um umh amma kuwa ban kyauta ba dana ɓatawa babyna rai, yanzu ki gayamin laifina na hada hakuri" cikin shagwaba tace"ba Kaine nace ka dawo mana da yaya maryama ba kaƙi, kullum inna maka magana baka amsani" shiru yayi ya tsira mata idanu yana kallonta dama ya riga yasani, idan akwai abinda ke haɗa su rigima to wannan maganar ne, ta dage kai da fata itafa sai dawo da uwargidan shi, yayinda shi kuma yake ta doje wa, ya tuna yadda suka rabu yau da safe kafin ya fita aiki, duk dai akan maganar, ya rasa wani irin zuciya kega Zahra, shidai bai taba ganin mace mai kaunar kishiya ba tunda yake sai ita, kishiyar ma irin maryama wacce idan aka bata wuka tsab zata iya daba mata a kahon zuciya. Sheshshekan kukanta ne ya dawo da shi hayyacinsa baya son bacin ranta ko kadan, rarrashinta ya shiga yi, amma sai kara sautin shashshekanta takeyi, bata bari ba kuwa saida taji yana cewa"naji naji ya isa haka baby zan dawo da ita naji na amince" tsayawa tayi da kukan da take ta kalle shi ido gaje gaje da hawaye tare da cewa "da gaske kake?" ya girgiza mata kai alamar eh, ta sake cewa "kayi alkawari" yace "nayi" tace "to yaushe " yace "yaushe kikeso " cikin zakuwa da jin dadi tace "gobe" yace "an gama amaryar Adam"kamkameshi tayi cike da farin ciki ta shiga zuba mai godiya. Dakatar da ita yayi tare da cewa "ni wannan godiya gaskiya bata gamshe ni ba, ba irinta nake bukata ba," fuska a washe kamar ba ita bace ta gama fushi yanzu ba tace"ka fadi duk irin Wanda kake so zan maka habibi" murmushi yayi tare da raɗa mata irin Wanda yake so ɗin a kunne, da Sauti ta kai hannu ta rufe fuskarta tana dariya kasa kasa, yace "uhummm ke nake saurare ko baza ki iya bane" a kan labbanta ta "furta zan iya" kafin takai hannu a hankali ta shiga balle mai maballan gaban rigarshi............. Rashin samun comment da yawa shekaran jiya shiya hanani karfin gwiwar yi muku posting jiya, in kuna son mu gama da wuri mu daura wani to oya naga ruwan comment masoya😍 Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} 109 ~MALAYSIA~ Bayan wata uku Dad ɗin zee na hango zaune a cikin wani ƙaton falo mai dauke da kujeru sama da guda hamsin, a cikin falon akwai wani ɗaki mai wawakeken kofar glass, zaune yake ya zuba tagumi da hannu bibbiyu yayinda gabanshi kaɗan mum ne sai safa da marwa takeyi ta kasa zaune ta kasa tsaye, basu kaɗai bane a falon a kwai wasu mutanen amma kowa da abinda ya dameshi babu mai shiga harkar kowa, Daga kaina nayi na kallin sunan da ke rubuce a saman dakin ~labour room~ abunda idanuna suka hango min kenan. Suna a wannan yanayin bini bini dad kan amsa call a waya yayinda mum kam gaba daya bata cikin hayyacinta, sai yi take tana aza hannu a kai tana saukewa, can bayan kamar 30 minutes sukaga an budo kofar glass din an fito, wani mutumi ne fari sol kamar zabiya sanye da kayan likitoci ya fito daga dakin, da sauri Dad ya zabura ya mike,shida mum har suna rige rigen isa gareshi, a ruɗe. Dad ya fara cewa "Dr ina daughter ta haihun,ko har yanzu?" Mum ma cewa take "pls Dr ina daughter na, wani hali take ciki, Dr idan abin bazai yuwu ba kawai ayi mata theater" Dr kam rasa ma wani amsa zai basu yayi, ganin yadda suka tare shi, gashi shi kuma sauri yakeyi yasa yace musu"excuse me pls" tare da dojewa ya wuce su da sauri, hannu mum ta daura akai tana hawaye tare da ambaton "innalillahi wainnailaihi rajiun" Dad kam bin bayan Dr yayi da sauri saidai kafin ya cin masa ya shige wani office, Wanda babu mai ikon shiga sai likitocin asibitin, dawowa yayi jiki a sanyaye ya nemi gurin shi Nada ya kuma zama. Tsakanin shida mum an rasa mai jarumtar rarrashin wani, kimanin awa goma kenan da suka kawota asibitin, tun cikin dare naƙuda ya tasar mata gadan gadan, ba shiri kuwa aka shige da ita labour room, saidai har zuwa yanzu karfe goman safe bata haihu ba kuma ba Wanda yace musu wani Abu game da ita, saidai kawai gani sukeyi likitoci da nurses nata zirga zirga a ɗakin. Hankulansu gaba ɗaya yakai matukar ƙololuwar tashi, tsoron su gaba ɗaya kar su rasa ta, itace farin ciki su, ita kaɗai suka mallaka suna matukar tsoran rasata. A wannan yanayin maimakon su tayata da addu'a, amma ina abinka da jahilai, Dad sai zufa yake hadawa idanunshi sun rine jajur,in yayi ya lailayo ashar ya ɗura wa Aslam, yayinda mum ta kasa tsaye ta kasa zaune sai fareti takeyi tana risgan kuka. Bayan mintunan da basu gaza goma ba wata nurses ta fito daga ɗakin, nan itama suka mata caa aka, kallon mutanen falon tayi fuskarta dauke da murmushi tace,"su wanene iyayen zainab Abdussalam" bakin na rawa Dad yace "yes mune mune" mum ma tace "eh nice mahaifiyar ta, wani hali take ciki" nurse tace "alhmdllh ta sauka lafiya yanzu an samu baby boy," tsabar farin ciki mum batasan sanda ta rungume nurse ba, Dad kuma kallonta yayi yace "nurse wani hali take ciki" cikin murmushi tace," tana lafiya yanzu haka ana gyarasu ita da babyn nan da yan mintoci za'a fito da ita zuwa ɗakin Hutu, sai ku samu ku ganta" dad" ajiyar zuciya Dad ya sauke tare da shiga jero ma nurse ɗin godiya, nan kuma ya ɗauki waya ya shiga kiraye kiraye. Nurse kam da'ker ta samu ta kwace kanta a hannun mum ta koma ɗakin da ta fito. Ba'afi 20 ba kuwa aka gunguro zee daga labour room zuwa ɗakin Hutu, sai lokacin su mum suka samu ganinta, tayi fiyaut da ita, ta kara haske, basu Daɗe a ɗakin ba akace su fita su barta ta samu barci sosai an mata alluran barcine, kasancewar ba karamin wuya tasha ba, tayi nakuda mai tsayi kamin ta samu ta haihu da taimakon kwararrun likitocin asibitin. Babyn dake nannade cikin farin shawel an mishi wanka an shiryashi cikin tsadaddun kayan sanyi aka mikoma mum, hannu na rawa ta karɓa, tsurawa yaron idanu tayi tana kallo, Dad dake tsaye ganin haka yasa shima ya matso don yaga mai take kallo haka, abinda ya faru da mum ne shima ya faru dashi, kallon yaron sukeyi babu ko keftawa. Bacci yake yi idanunshi a kulle fari sol ƙato da shi mai kama da Aslam sak, babu abinda ya banbantasu,kwata kwata bai dakko komai na zee ba, duk da mum da Dad basa kaunar Aslam hakan bai hana ɗanshi samun kyakkyawan matsuguni a zuciyoyin su ba, farat daya yaron ya shiga ransu, a kallo na farko. Gaba ɗaya sun shagala da kallon yaron saida sukaji, muryar nurse tana musu magana sannan suka dawo hayyacinsu,saƙon Dr ta sanar musu na cewa da yayi su same shi a office, Dad ne yabi bayan nurse din zuwa office ɗuin Dr yayinda mum ta rungume yaron tsam a kirginta tanajin wani irin son shi da kaunar shi na huda kofofin zuciyarta. Saida zee ta kwashe awa shidda kwarara tana barci kafin ta farka, wuraren la'asar, zuwa lokacin kam asibiti ya cika makil da yan'uwa da abokan arziki yan gayu masu abin hannu,yawancin su ma turawa ne wadan da su mum ke hulɗa dasu, kowa ya dauki yaron nan kallon daya zakaji ya shiga ranka, da alama dai baiwarsa ce hakan. Zee ta farka da sauƙi sosai don bayan Dr ya duba ta, ya tabbatar musu nan da gobe ma za'a iya sallamarta taje gida abinta, bayan mum ta bata shayi mai zafi tasha ta kuma sha magunguna, sannan aka bada daman mutane su shiga su dubata, kowa barka yake mata, bata iya amsawa sai smiling kawai take musu, lokacin da aka bata babyn kuwa tsura mishi idanu tayi tana binshi da wani irin kallo, babu abinda take gani a fuska da jikin yaron sai Aslam dinta, take wani irin kewa da kaunar mijinta ya turniketa, rungume yaron tayi sosai a jikinta tana jin wani irin kaunar shi na huda zuciyar ta, bata San sanda ruwan hawaye ya wanke mata fuska ba, ta shiga risgan kuka harda sheshsheka, ganin haka yasa mum ta miƙa mata hannu alamar ta bata yaron girgiza mata kai tayi alamar A'a dole mum tayi hakuri ta bar mata abinta. Zuwa dare babyn ya fara kuka, Dr yace ya kamata a bashi abinci yunwa yakeji, Dad yace Dr ya rubuta musu madaran da za'a dinga bashi yaje ya siyo, da mamakin su ji sukayi zee tace , A'a kar a siyo madaran ita zata shayar da ɗanta, Dr yace well dama haka ake bukata, nan wata nurse ta gyara mata shi sosai ta koya mata yadda zata rikeshi a yayinda da zata shayar da shi, nonon aka sa mai a baki ba shiri kuwa yaro ya kama yana tsotsa, duk da matsanancin zafin da takeji hakan baisa ta fasa shayar dashi ba, nurse din data fahimci tanajin zafi ta shiga kwantar mata da hankali da cewa karta damu zai daina, idan ya kwana biyu yana sha, shikenan baza ta kara jin zafi ba kuma. A asibitin suka kwana zuwa washe gari ta ƙara samun sauki sosai don haka Dr ya rubuta musu sallama suka dawo gida, kulawa sosai zee ke samu daga gurin iyayenta ita da little Aslam dinta, wata babban nurse mai zaman kanta, wayayya mai wadataccen ilmi Dad ya daukar musu ita ke kula da komai nasu ita da babyn bangaren wanka tsaftar su da abincinsu, kai komai ma daya shafe su. Zee taji dadin yadda iyayenta suka karbi yaron da yadda suke nuna mai kauna da kulawa, bata taɓa zaton haka ba, ganin yadda suka dauki karan tsana suka dorawa uban ɗan. Kafin sati ya zagayo tayi bulbul ita da babynta gwanin sha'awa, jego takeyi na yayan gata, baza ayi taron suna ba, raɗin suna kawai za'ayi dad ne ya siya duk wani abinda ake bukata na radin suna kamar rago da sauransu,tambayarta sukayi sunan da take so a saka ma ɗanta babu kunya ko kara tace Muhammad Aslam, haka ko akayi, duk da Dad yaso ace sunanshi ta zabar wa yaron. (kuji min Dad da ƙoƙari wai da sunanshi ta zaba😒 babu kunya ba tsoron allah cikin da yayi niayyar hallakawa) Hankali kwance take jegonta bata da matsalar komai babu abida ke damunta sai kewar mijinta, bayan haihuwartan nan , abin ma saiya daɗa nunkuwà, kullum dashi take kwana take tashi a zuciyarta ji take kamar tayi tsunstuwa ta ganta a agabanshi, ta mika mishi ɗanshi, cikin farin ciki,ta kusa kai matakin da baza ta iya jurewa ba, jira takeyi yaronta yayi kwari, ta lashi takobin zata koma gidan mijinta koda son ransu ko babu, koda tsiya koda tsiya tsiya. ~9ja~ Yau kimanin wata biyar kanen da auren yan matan mummy,kuma har zuwa wannan lokacin cikinsu babu wacce ta taba zuwa gida da sunan ganin gida, kowacce tana gidanta hankali kwance, duk da kuwa cikinsu ba wacce batayi nacin son zuwa gida ba amma mazajen suka hana wannan kuwa umarnin alhaji baba ne. Soyayya kamal da khadija ba'a magana, tattalin da kulawa suke ba juna na musamman, idan kaga yadda suke gudanàr da rayuwarsu zaka dauka sunyi shekara goma suna soyayya kafin suyi aure, a halin yanzu Khadijah Nada cikin ta dan wata huɗu. Haka ma Amir da Amira sukam bama a magana, kalar nasu salon soyayya ta dabance, basa jin kunyar uban kowa a gaban kowa nuna ma juna soyayya sukeyi, ƙiri ƙiri mutane suka guji zuwa gidansu, saboda idan kaje indai kana da kunya, ta baza ka iya awa ɗaya a gidan ba,suma dai a kwai cikin ɗan luv, saidai fatan Allah ya raba lafiya. Su batool ma yanzu komai nomal,babu abinda suke sai shan soyayya da cokali mai yatsu, bangaren yadda sukeji da cikin su kuwa ba'a cewa komai,tunkan a haife shi, shikaran kanshi cikin yasan shi dan gata ne, abinka da masu abin duk sati ake scanning, ta bangaren maah ma ba'a barta a baya ba, duk abinda ta gani indai na jariri ne siya takeyi ta ajiye, abin kwalama kuwa na masu cikin kullum cikin yi takeyi tana aikama batool dashi, bama ci takeyi ba wani bin saidai Dr yaci idan Wanda zai iya cine, ita dai barta da cabbage dinta, yanzu kam an samu ci gaba ta daina cinshi gaya, saidai ta kwada da kulikuli taci, rigima kam yayi sauƙi a gurin batool saidai kunsan ance mai hali baya fasa halinsa, duk da haka duk randa ya tabota haka zata kwana tana masifa, musamman yanzu da wata Dr a gurin aikinsu ta nace tana sonsa, tunda batool ta samu labari ya shiga uku ko minti talatin ya kara akan lokacin da yake dawowa haka zai sameta ta cika tayi fam, komai zai ce mata baza ta yarda ba kawai gurin Dr basira ya tsaya, kishin sa take sosai da sosai ji take da tana da hali da nikab zata saka shi ya dinga sakawa, saukin shi ma yanzu yana da loggonta data fara zai lalubeta ya fara sakar mata zafafan romance daga nan zancen zai mutun sai kuma na gobe. A bangaren zahra kam, yanzu babu abida zamu ce sai alhmdllh, tsakaninta da miji babu komai sai tsantsar soyayya da kaunar juna, da gasken fa baby take a gurin Barr Adam ji yake da ita kamar Yar jinjira, musamman yanzu data samu ciki, kula yake bata na musamman kamar ya hadiyeta, tsakanin da maryama yanzu kuwa babu komai sai girmama juna da mutunta juna, dama zahra kwata kwata bata da matsala, matsalar daga maryama ne, kuma a halin yanzu gaba daya tayi laushi, bayan dawowarta Barr a gaba ya sakata ya mata nasiha tare da sanar da ita wlh ta gode ma Allah daya haɗa ta da kishiya irin Zahra bata samu mai irin halinta, nan ya sanar da ita cewa zahra ce ta tirsasa shi ya dawo da ita badan haka ba da har yanzu tana cen, take taji wani nadama ya shige ta lallai ta gode ma Allah dabai haɗa ta da mai irin mugun halinta ba don ta Tabbatar inda itace a matsayin zahra,da wlh zahra tabar gidan kenan har a bada asaidai a bita da takardan ta, tayi nadama, ta tuba taubatan nasuha, washe gari kuwa har part ɗin zahra taje ta same ta nemi gafarar abinda ta mata, Allah sarki zahra dama bata riketa a raiba, nan dai tace ta yafe mata, tashi tayi ta rungume ta tana mata godiya, a haka Barr ya samesu, ba karamin dadi yaji a ranshi ba, take ya haɗa su ya nusu nasiha, tare da nuna musu irin tsantsar farin cikin da yake ciki a ranar saboda hada Kansu da sukayi, tun daga ranar kuwa suke zaune lafiya abin su, yara yanzu sun zama yan gata masu uwaye biyu, maryama suna kiranta da mummy zahra kuma suna kiranta da mum, dakinsu nanan a part din zahra data ware musu, lafiyayye Dan yama fi dakinsu na part din maryama haɗuwa, in sunga dama su kwana a gurin mummy insun ga dama su kwana gurin mum, maryama ce ta fara gane zahra nada ciki, aiko dai tayi farin ciki har zuciyar ta, take ta shiga tsokanarta tana kiranta da maman yan biyu, tun zahra na daukar abin da wasa har dai lamarin ya tabbata, saidai muyi fatan Allah ya raba lafiya. A bangaren su Asmah kam yanzu sun wuje romeo da Juliet, soyayya suke zubawa kamar zasu cinye juna, da'ker da sidin goshi Asmah ta samu Aslam ya koma wajen aiki, shima da yarjejeniyar, yana aiki suna video call, haka dai tace mishi ta yarda, ta samu ta lallabashi ya tafi ranar farko daya fara zuwa, yana isa ko office bai shiga ba ya kirata ƙin ɗagawa tayi dan burinta a halin yanzu bai wuce ya maida hankali kan aikinshi ba, cikin abinda baifi awa daya ba ya mata missed call yafi hamshi ta share, aiko dai ko Rabin a waya bai kara ba saijin horn din motar shi tayi ya dawo, washe gari kuwa kin tafiya aikin yayi, ganin dai da gaske yakeyi, yasa itama ta ɓata rai ta daina kula shi ta fita sabgarshi, ta daina kwana tare dashi, kwana biyu suka kwashe a haka gaba dayan su sunji jiki, ba shiri yace mata yaji ya yarda zai koma aiki, amma sai inzasu dinga yin waya duk bayan awa ɗaya, ba yacce ta iya haka ta amice, amma da sharidin duk kira ɗaya bazai wuce 5 minutes ba, shima haka ya amince, da haka ta samu ya koma office. Har zuwa wannan lokacin babu abinda ya shiga tsananin su, ta bangaren auratayya saidai zuwa yanzu an samu ci gaba sosai dan sukan sha romance dinsu na fitar hankali, saidai fa iyakar ta nan, ita kanta tana mamakin yadda akayi ya kasa nemanta har yanzu tun abin bai damunta har ya fara dan damunta, har take tunanin anya ma sonda yace yana mata da gaskene kuwa, dan indai akwai soyayyan dole zaiso su zama Abu guda ai, Allah sarki Asmah bata San Aslam yama fita bukatar hakan ba, saidai yana nan akan bakanshi, na cewa saita nemi hakan da kanta tukunna. Gaba daya Aslam ya manta da wata zee a babin rayuwarsa, Asmah ce kawai a gabanshi a halin yanzu. Yau gaba daya familin sun tashi da tsantsar farin cike, ba komai bane kuwa face haihuwan da akayi musu gagarumi, yayansu Rabi'a ce ta haihu maman hanifa, ta samu ɗa namiji wannan karon, da safiyar yau mami ta kira su dukkansu daya bayan daya tana gaya musu, duk wacce ta kira ,sai taji ta daka tsalle tana murna tare da tambayarta dama tana da ciki ne, tasan duk abinda sukema wannan tsallen murnan koba komai zasu zo gida zasu haɗu da juna, to ai dole, wata biyar fa ba kwana biyar ba, duk da suna waya da juna, da kuma iyayen nasu...... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan littafin ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 110 Ƴan matan mummy dukkansu sunje sunga babyn ya Rabi'ah sunyi barka, kowaccen mijinta ya kaita saidai cikin rashin sa'a a mabanbantan lokuta suke zuwa, ranar da batool taje ma tana isa Asmah na wucewa, dan Aslam bai barta ta zauna ba, tare suka shiga kuma ko minti talatin basuyi ba yace tazo su wuce, Rabi'ah kam bakin ta sake take kallon ikon god yadda suke wani nannan da juna dan ko da zai zauna saida ya bari ta zauna sannan ya zauna a kusa da ita ya riƙo hannayenta, bakinta cike fal da gulma amma ba daman yi, saboda Aslam daya kasa ya tsare, saidai insuyi su kalli juna ita da abban hanifa dayake shima yana gida lokacin hakan ne ma yasa aslam ɗin shiga gidan,aiko suna tafiya rabi'a ta shiga gulman aslam tana ba abban hanifa labaran diraman da a kasha waɗanda baisan dasu ba, dariya ya dinga yi tare da cewa "ina ruwan baban yaya"zahra ne kawai bata samu zuwa barka ba itama dan tana da nisa ne, kuma ga karamin ciki, Barr tsoro yakeji, hanyar bidda to minna bashi da kyau, yadai mata alkawarin zai kaita da kanshi idan ana gobe suna kuma zai barta har washe garin suna sañan yazo ya dauketa, takoyi murna take ta kira su batool ta gaya musu, nan suke yanke shawaran suma sai ranar da zata zo zasu ƙara komawa tunda zai kama ran aikin suna gashi kuma ranar ummin su zata iso itama. ~ASMAH~ Ranar da ta kama ranar aikin suna, wato ranar asabar, tunda ta tashi da asuba bata ƙara komawa ta kwanta ba saboda ganɗoki, bayan tayi sallah kitchen ta shiga ta fara haɗa breakfast, Aslam na masallaci, koda ya dawo maimaikon ya sameta tana karatun alkur'ani kamar yadda yasaba tarar wa kullum sai yaga ɗakin wayam, fitowa yayi ya shiga nemanta ɗaki ɗaki amma shiru, can ya zo gilmawa ta wurin kitchen yaji ɓuruntun kwanuka, mamaki ne ya kamashi bai taɓa tunanin ganin ta a kitchen a dai dai wannan lokacin ba, balle ma yau da take asabar ba aiki zaije ba, kara sawa yayi da sauri yana mata alamar lafiya me take yi a kitchen yanzu da hannu, don lazimi yakeyi bai da daman yin magana, da fara'ar ta tace" breakfast nake hadawa da wuri, kasan yaune aikin suna inason kafin takwas da rabi na isa cen" bata rai yayi shifa maganar zuwa aikin sunan nan ya fara bashi haushi, ko jiya bata da magana sai zancen zuwa aikin suna har dare, shi har zancen ya gundureshi ma, yaga sai wani rawar kai takeyi zata fita, wai wani takwas da rabi ya mata acen. Baice mata komai ba saida ya gama lazimin shi ya shafa, sannan yace "karfe nawa kikace zakije aikin sunan ma?" tace "wai da nace ko takwas da rabi ya min a cen, koya ka gani,ko kana ganin yayi latti da yawa" hararan ya wurga mata sannan yace "wato yayi latti ko, to ni nama soke batun zuwa aiki suna, na fasa, matata ba baiwar kowa bace ba wacce zakije kima aiki" jin haka bata San sanda ta iso gaban shi ba, shima sai kawai ganinta yayi, kafin ya ƙara faɗan wata kalma ta haɗe bakinta da nashi, jin haka sai ya kara tallaɓe fuskarta kawai shima, tayi hakane dan karma maganar tayi nisa ya kaishi ga rantsuwa dan yanzu maganar nan daya faɗa gabanta saida ya yanke yayi mummunan faɗuwa,tasan sarai zai aika dan baya kaunar abinda zai rabashi da ita kona minti ɗaya ne, itako baza ta iya jure ya hanata fita aikin sunan nan yau ba, dan tsabar sa abin da tayi a rai har mafarki tayi gata ga yan uwanta ƙawayenta, shiyasa ma yau ta tashi da ganɗokin abin fiyye da yadda takeji jiya. Saida suka kwashe mintuna masu ɗan yawa suna kissing din juna kafin, ta kwace kanta dan taga alamar baida niyyar saketa, dan Aslam mayen kiss ne baiki suyi awa haka ba, bata kai kanta ba ma ya ta kare balle, dukkansu sauke ajiyar zuciya suka shigayi kamar waɗanda sukayi wasan tsere, yana kallonta da idanunshi da suka canja launi, ya buɗe baki zaiyi magana tayi wuff ta rigashi da dace "dan Allah da manzon sa ya Aslam kayi hakuri kar kace zaka hanani zuwa aikin nan, wlh in ka hanani zazzabi zai iya kamani" yana kallon cikin idanunta ya mika hannu ya dungure mata goshi cikin sigar wasa, tare da cewa "nace baza kije ba koh" aiko inda kuka san ya wanka mata mari, ta fashe da kuka amma daga jin kukan kasan na zallàr shagwane, tsayawa yayi yana kallonta, cikin muryar kukanta da takeyi na shagwaba tanayi tana bubbuga kafa a kasa kamar ƴar yaye, tace "nidai dan Allah dan Allah dan Allah fa nace yayana plsssssssssss" ta kare da jan pls din sosai cikin wani irin siga najan hankali Wanda ita kanta bata San tayi ba. Wani irin yarr yarr yake ji a jikinshi, gaɓobin jikinshi gaba daya sun amsa gayyatar da take musu, ba shiri ya juya da nufin barin mata kitchen ɗin, don bai gama lazumum shi duka ba yanzu ma karatun alkur'ani yake son yaje yayi, aiko da sauri ta bishi ta cukuikuiyeshi ta baya tare da kwantar da kanta a bayanshi, hannayenta kuma ta zagayeshi dashi, ta daurasu daidai marar shi, kasancewar ya fita tsawo sosai, ba shiri har bakin shi na rawa wurin cewa "naji naji na amince zan kaiki amma tare zamu kafata kafarki kin yarda" jin haka yasa ta shiga tsallen murna tana cewa"yess! Nagode nagode ya Aslam ɗina" aiko tsallen da takeyi sai ta ƙarkare birkita shi, zagayo da ita yayi gabanshi ya daga ta sama cak ya karasa main parlour da ita, girkin da ba'a karasa ba kenan. Dan suna zuwa falon kan 3 sitter ya direta ya bita ya danne, a zafafe ya shiga aika mata da zafafan romance, duk da ba mayar mai da martani takeyi ba dama, don bata iyawa sai takega kamar zaiga rashin kunyarta, hakan bai dameshi ba, sai da ya rage zafi sosai ya rabu da ita, duk da bawai ya samu yadda yake so bane, gaba daya jikinta ya matu, ita fa ba iya haka taso wasan ya tsaya ba, ji tayi kamar ta kamo shi ta dawo dashi ya sosa mata inda yake mata ƙaiƙayi amma baza ta iya ba, sai binshi tayi da idanu har ya ƙule ma ganin ta, ji tayi kamar ta tsala ihu,i tafa wannan lamarin ya fara isar ta. Ɗakin shi ya shiga ya faɗa toilet ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, idanunshi a runtse, hannun ya kai yana yamutsa suman kanshi, shi karan kanshi ya gaji a halin yanzu matar shi kawai yake bukata, yana bukatar ƴaƴa shima, yana matukar kauna ya ga kwanshi, kamar daga sama yaji zuciyar na, cewa "duk kai ka jawo wa, kanta wannan bata lokacin, ta yaya zakace kana jiran abinda kasan bazai taba yuwuwa ba, to inzaka yunkara ka yunkura, idan ba haka ba kuwa zaku shekara a haka" da haka ya karkare wankan da zaiyi ya shirya ya fito, koda ya fito falon bata nan, hakan yasa ya nufi ɗakinta a kudundune ya ganta cikin bargo, shima bargon ya ja ya shiga tare da jawota jikin shi, babu Wanda yace ma dan uwansa ƙala kowa da abinda yake saƙawa a ransgi, a haka barci ya dauketa yayinda shi kuma ko alamar gyangyadi baya ji haka ya cinye lokacin barcin safen da tunane tunane, Wanda a karshe ya Samar ma kanshi mafitar da yake ganin zata bulle mai. Sai gurin sha ɗaya ta farka, lokacin Aslam tuni ya Dade da tashi,lalubashi tayi taji baya kusa da ita, kallonta takai kan agogon bangon dake dakin, sha biyu saura ta gani, salati ta rafka, tare da dirowa daga kan bed din, ta nufo falo, bata gashi ba kawai sai ta nufi kitchen da nufin ta haɗa musu breakfast mai sauki tunda lokaci ya kure har haka, yanzu fa kamata yayi ace tana shirye shirye daura abincin rana, tana shan kwanan hanyar da zai kaita kitchen ɗin tunkan ta karasa taji wani azababen kamshin na mata sallama da sauri ta karasa, ya juya baya hakan yasa baisan da isowarta ba, saiji yayi an rungume shi ta baya, murmushi yayi tare da cewa "kin tashi kenan" amsa ta bashi da "shine baka tasheni ba ko" ta faɗa kamar zatayi kuka yace "sorry bana son na katse miki barcin ki ne" tace "nidai ba wani wayo kawai kamin ɗan ka shirya breakfast ɗin kai kaɗai, kuma dai Allah ya tashe ni, sai ka barmin na karkare,mai gurin yazo mai tabarma ya nade" dariya ya kwashe dashi tare da cewa "kin makaro yarinyar saidai na gobe dan na riga na gama komai sai ci kawai ya rage" taya shi tayi suka kai abicin dining, nan suka zauna zaman ci yace shi zai bata a baki haka sukai ta cin abincin suna wasa kafin su Ankara karfe ɗaya, Aslam da gangan ya dinga mata wayau yana mata mata lokaci dan da gaske baya son fitar nan nata, amma ba yadda ya iya ne kawai. Haka suka tayin komai a shiririce, basu suka shirya ba sai karfe uku, shima da'ker ta samu yayi wanka, dan da cewa barci zaiyi, gashi kuma su batool da Amira sai kiranta sukeyi anjita shiru, saida ta saka mai kuka, sannan ya mike kenan. Koda yayi parking a kofar gidan ya Rabi'ah, da'ker ya bari ta shiga ciki, da cewa yayi ma zai jirata harta gama ta fito su tafi, saida tayi ta roƙonsa ya yarda zaije ya dawo, amma saita mai kiss, zaro ido tayi tana bin inda suke da kallo, ga mutane na gilmawa jefi jefi wasu a ƙafa wasu a mota, ga glass ɗin motar su farine ana iya ganin mutum kuma a sauke yake ma, ganin tayi shiru yace "uhummm ke nake saurare" wani dabara ne ya fado mata tace "na yarda amma nima da sharadi, zaka rufe idanunka tukum" bai kawo komai a ranshi ba ya rufe ido tare da cewa "oya bismillah" hannun ta takai saitin idanun shi tayi weaving taga bai motsa ba alamar dai ya rufe idon da gaske, miƙa hannu tayi ta buɗe kofar da sauri ta fice daga motar tana mai dariya, jin haka yasa ya bude ido, shima dai dariyar ya shigayi kafin cikin ɗan daga murya yadda zataji shi yace, "zakiyi bayani ne yarinya gobe ma ranace," gwalo tamai tare da shigewa get din gidan, saida yaga ta maida kofar ta rufe, sannan ya tada motar shi, yabar kofar gidan direct kuwa asibiti ya nufa gurin Dr bash dan sun kwana biyu basu hadu ba saidai a waya. Gaba dayansu suna zaune a falon zagaye da umminsu da batayi awa daya da isowa ba, Asmah ce kawai babu a cikin su, fira akeyi cike da zakuwa da farin ciki da marmarin ganin juna. Tun kafin ta karasa bakin kofar shiga main parlourn ya Rabi'ah takejin hayaniya da surutunsu na tashi, cike da zakuwa ta karasa baking kofar da sauri har tana dan haɗawa da gudu, gani tayi kofar a bude yake hakan yasa bata tsaya wahalar yin knocking ba ta faɗa falon bakinta dauke da sallama, daidai lokacin da ummi ke cewa Rabi'ah mikomin wayata na kira Aslam ɗin naji ko lafiya har yanzu bata iso ba, saijin sallamanta sukayi kamar daga sama....... Oum Ummeetarh 07041130088 Share Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 111 Cike da tsananin zaƙuwa dukkansu suka mike tare da rige rigen yi mata oyoyo, ƙamƙame juna sukayi gaba ɗayansu, suna tsalle kamar wasu ƙananan yara, ko nauyin jikin su basaji. Sauran yan tsurarrin mutane dake falon tuni suka bar abinda sukeyi suka shiga kallonsu, sake juna sukayi kafin kuma ta shiga binsu ɗaya Bayan ɗaya tana rungumewa, lokacin data rungume Amira kam tsayawa tayi jin tudun Abu ya tokareta, dagowa tayi ta matsar da ita baya kaɗan tana ƙare mata kallo, tun daga sama har ƙasa, gane abinda take kallo yasa Amira saurin kai duka tafukan hannayenta ta rufe fuskarta,Asmah ta bata kunya, kuma ga ummi a wajen, dariya ta kwashe dashi, tare da cewa "kaiii masha Allah Abu yayi kyau aure yayi albarka" Ummi dake kallonsu tana murmushin ganin abin nasu bana ƙarewa bane yasa tace "to ya isa haka ku kyalemin ƴa tazo ta gaisa da umminta," sai lokacin Asmah ta lura da ummi aikam dai kwasa da gudu tayi ta faɗa jikin ummi dake zaune kan kujera, ta ƙamƙame, tana tsallen murna, ummi kam cewa take "yi a hankali Asma' u karki kada umminki" ina ko sauraren ummi batayi ba, saida taji muryar ya Rabi'ah a bayanta tana mata magana sannan ta sake ummin ta dago fuskarta fal farin ciki, duk sunyi cirko cirko a tsaye suna kallonta kowacce cikin matuƙar farin ciki. Ya Rabi'ah tace, "yayi kyau wato ta ƙawayenki da umminki kawai kikeyi ko" ƙarasawa tayi ta rungumeta itama tana cewa "sorry yayana kema ai zan dawo gareki" ummi kam sai binta takeyi da kallo kuri, i tafa ta hanga ta hango bataga wani alamar cikin a jikin Asmah ba, idan idanunta ba karya suke mata bama sai tace taga kamar har yarzu a virgin dinta take, dan daga yanayin tafiyarta kawai ta gane hakan, dan ummi Allah ya mata wani baiwa irinsu ne matan da da summa mace kallon ɗaya suke gane yanayin da take ciki, shiyasa kallon ɗaɗɗaya tama su zahra ta gane kowacce nada kunshi, gabanta ne ya faɗi, jin tunanin daya faɗo mata arai na cewa to kodai har yanzu basu sasanta bane, tabdijam aiko da sake, bari dai ta natsu koma meke ciki zantaji. Zama sukayi nan gaban ummi aka shiga firan yaushe gamo kowa na fadin irin yadda yayi missing din sauran ana dariya, batool ce ta kalli zahra ganin, yadda taketa zare idanu, yunwa takeji dan tunda ta samu cikin nan da taci abinci ko awa bata iya kaiwa zataji cikinta kamar anyi yasa, gashi daga zuwanta aka bata abinci taci, bai wani daɗe ba, gashi bata son tace zataci abinci kar suyi zargin wani Abu,dan kuwa a irin tulin abincin data narka ɗazu, idan tace tana, jin yunwa yanzu dole su saka mata alamar tambaya, itako baza taso haka ba, son kunya takeji , tunda tazo taketa muku muku da abinta, tunda cikin bawai ya fito bane, na Amira ne kawai ya fito sosai saiko na Khadijah wanda shima idan mutum ya kura ido zai iya gani, saidai fa ta makaro don tuni ummi ta gane kaf ciki ne dasu saidai bata nuna ma ta gani ba, batool tace "kekuma lafiya, kiketa muzurai kamar me jin kashi" hararanta tayi tare da cewa"A'a maijin zawo dai" dariya su Amira suka kwashe dashi, ummi tace "oh Allah na gode maka ni Amina, anyi aure, yau watan ku biyar rabonku da ganin juna amma hakan baisa kun fasa wannan hali naku ba ko, kullum kamar masu ganin hanjin juna minti biyu shiri minti biyu faɗa"batool cikin dariya tace "ummi kalla fa yadda take yamutsa fuska tana muzurai kuma kawai dan na tambaya sai ya zama laifi" ummi tace "to aikena bakiyi tambayar a mutunceba, ya zakice mata kamar maijin kashi" batool tace "wlh ummi nayi missing ɗinta ne sosai so nake mudan tuna baya" dariya suka sa dukkansu ummi tace "to kin kyauta" Zahra kuma tace "kedai wlh baza ki canza ba"Khadijah ce ta faki idanunsu ta saka hannu cikin dan pos ɗinta da tunda tazo yake kamkame a hannunta ta ballo farin kasarta(kalba) ta afa a baki tana tsotsa a hankali,Asmah data lura tace "sisto abin kuma yar haka ne, wani daɗi kika samune, kike ci ke kadai, to kowa yaci shi ɗaya ya mutu shi ɗaya" zaro ido Khadijah tayi jin Asmah daga zuwa zata tona mata asiri tun dazu take Ballan abinta babu Wanda ya lura sai ita, Amira tace"haba shiyasa tun dazu nakejin kamshi na buso ni to a sammana, tunda sai mun roƙa " ta faɗa tana mika hannu zata dauki pos dinta dake ita ke kusa da ita, aiko saurin tayi wuf zata kamkame abinta, saidai cikin sa'a Amira ta rigata fisgewa, cakumota tayi zata amsa da sauri ta wurgawa ya Rabi'ah, aiko tana caɓewa ta balle botir ɗin pos ɗin ta saka hannu a ciki, saiga farin kasa cike da Santana. Daga ledar tayi tana nuna musa tare da cewa"Lalalalaaa kice abin yazo inji mai tsoron wanka, masha Allah naga biyu, kice gaba nan gaba inada suyan rago kashi kashi, saura su O'o da O'o, Allah ya raba lafiyar mrs kamaludden " tuni Khadijah ta saka kanta a cikin cinyoyinta ta dunkule wuri daya, duka dariya suka saka mata, suna tsokananta ta kasa dagowa saboda ummi, ummi kam dake musu dariya ganin abin zaiyi yawa sun sakata gaba karma batool da tafi zakewa yasa tace"kyale su oh Khadijah, ai bake kadai nabe naga kema batool ai cikin ne dake ko?" da sauri batool ta dago tana kallon umminsu, zaro mata ido ummi tayi tace"eh haka nace kema cikin ne dake ko nayi karya," kasa bata amsa batool tayi, ta maida kallonta kan zahra tace "dakema zahra" aiko dai zahra tayi tsuru tsuru Ashe duk boyon banza takeyi tun ɗazu, ummi taci gaba da cewa "a toh naga gara ayi tone tonen tunda haka kuma zaɓa, ga Abu a jikinku kuma, amma kun take kun saka min ƴa a gaba" shiru kakeji batool baki ya mutu, ya Rabi'ah kam guɗa ta daddage ta rangaɗa iya karfinta, kafin tace "masha Allah alhmdllh, waiko mummy Nada wannan labarin kokuma ni zan fara mata albishir," ummi tace "ta ina zata sani nima duk yanzu na gansu da abubuwan su" ya Rabi'ah tace"to ummi banji kinyi lissafi da madam misisi ba matar oga" kallon Asmah ummi tayi tace "kai ita naga kamar babu ko?" ta fada tana kallon Asmah alamar ita take tambaya, ya Rabi'ah kuwa kallon Asmah tayi ta rike haba tare da cewa "ke ko ma'ulle me kika tsaya jira haka, ake neman a barki a baya," ummi tace "barni da ita, zata gaya min bayani ne anjima" ta faɗa tana dan haharan Asmah, Wanda ita kaɗai ta fahimci hararan me ummi ke mata, duk tasha jinin jikinta dama tun da taji kowa nada ciki banda ita jikinta yayi sanyi. Zahra kam silalewa tayi ta shiga kitchen, ta samu abinci a nan ta zauna ta shake flate ta hau ci, koda ta fito duk sun shiga ciki don yin sallan la'asar da, aketa kira, itama cikin ta nufa, a dakin da ummi ta sauka ta samesu suna sallah. Bayan sun idar zahra tambayar ya Rabi'ah tayi ko akwai aikin da Za'ayi ne, ya Rabi'ah tace "ba wani aiki duk ayyukan ba'anan za'àyi ba a can family hause dinsu za'ayi raɗin suna, duk abinda ya shafi raɗin sunan a cen za'ayi, ni kuma nawa abinci yourbawa zasuyi,saidai ko ku jera drinks da ruwan da aka kawo dazu a fridge kubi duka fridge din da kuka sani a gidan nan ku cikashi da ruwa da drinks harda na dakunan bakin cen dake rufe Na waje, bari Na Baku keys " ta faɗa tana mikewa ta dauko keys din a cikin side drower ta mikawa Amira, amsa tayi tace "to kumuje mu gama ko kafin fira ya barke mu kasa tashi" zahra tace "aikuwa dai muje" miƙewa sukayi zasu wuce Ummi Na zaune kan pray mat tana addu'a, gyaran murya ta musu duk suka juyo suna kallonta,nuna Asmah tayi sannan ta mata alamar ta tsaya ita, cikin sanyi jiki ta dawo ta zauna a bakin bed, gaba ɗaya walwalarta ya ragu, haka kurum takeji kamar ta aikata wani zunibi ne, ganin duk yan uwanta da aka musu aure tare suna da juna biyu amma ita har yanzu tana nan matsayin virgin bama akai ga maganar ciki ba tukunna, su batool kuwa tafiya sukayi suka kama aikin da zasuyi. Bayan ummi ta idar ta shafa addu'an bata rai tayi sannan ta juyo ta kalli Asmah, ganin yanayin fuskar ummi saida gabanta ya faɗi, da gani tasan babu wasa a fuskarta, umminsu kenan Zuma ga zaki ga harbi, ita kuma ummi tayi haka ne dan ta samu Asmah ta faɗa mata gaskiyar abinda take son sani don idan ta sake mata fuska zata iya mata karya duk da ba halinta bane karya, zataji kunyar gaya mata wasu abubuwan idan taga dariya a fuskarta. Cikin dakakkiyar murya tace "wato bakiji maganar dana gaya miki rannan ba ko, wai yaushe kika zama mai kunnen kashi ne Asmah, bansanki da wanna halin bafa" take idanun Asmah suka Tara kwalla, ummi bata saurareta ba taci gaba da cewa "wato ke baza'a miki magana kiji ba ko, kin tsaya shashanci da sunan baki son miji kin manta da abinda ke gabanki ko, waya gaya miki ana wannan yayin yanzu, ko mutanen da, da suke da duhun kai basuyi wannan kauyancin ba balle ku yaran yanzu da kuke a waye, Na gaya miki rannan namiji duk sonda yake ma mace idan bai samu kulawarta ba wlh soyayyar nan bacewa takeyi bat a zuciyar shi, take zakiga ya fara hangen wata, to balle naki ma da yake da wata matar a gefe, wlh idan ya gaji ajiyeki zaiyi a gefe ya dawo da matar shi, shikenan kin shiga uku, keda mijinki saidai hange daga nisa" nan fa ummi ta rufeta da fada ta inda take shiga bata nan take fita ba, don ita duk a tunaninta har yanzu Asmah bata ba Aslam dama bane, tunda gashi har yanzu auren nasu bai cika ba. Tuni Asmah ta duƙar da kai kasa ta fara kuka harda sheshsheka, jikinta ya ƙara yin sanyi musamman da ummi ta tuna mata da zee, saida taji ummi tayi shiru sannan ta dago kai idanu gaja gaja da hawaye, cikin muryarta mai dauke da amon kuka tace "umminmu wallahi tallahi abinda kike tunani ba haka bane, wallahi ummi tun daga ranar da kikamin magana, komai ya fara daidaita a tsakanin mu" katseta ummi tayi da cewa "rufe min baki karya kikeyi, idan komai ya daidaita mai yasa har yanzu babu abida ya shiga tsakaninku ta fannin auratayya" cikin kuka tace "wallahi ummi ba laifina bane , ba daga gurina bane matsalar wallahi ba daga ni bane" ummi jin ta fara kamo bakin zaren yasa ta kara bata rai tace "to daga waye" ganin ba wasa a fuskar ummi yasa batayi tunanin wani batun kunya ba tace "shine bai taba nuna yanaso ya kusanceni ba" ummi cikin zaro ido jin abinda Asmah tace dan ta ji tsoro kar ace baida isashen lafiya ne tace "ban gane ba kina nufin kodan romance haka dasu dan kiss bai taba yi miki ba" Asmah tace "yana duk wannan amma bai taba wuce haka ba, koni abin Na damuna umminmu" Gyara zama ummi tayi a bakin bed, tufka takeyi tana warwarewa,a zuciyarta, ta yarda da batun Asmah Na cewa sun daidaita, tun daga yanayin yadda Asmah keta zuba mata rantsuwa, kuma ta gamsu Aslam kalau yake tunda yana da sha'awa, tunda gashi har yana iya wasanni da ita, to daga ina matsalar take ne? Jin amsar da zuciyar ta ya bata yasa ta juyo da sauri ta kalli Asmah tare da tsatsare ta da idanunta masu kaifi a kansu tace,"ya taɓa nuna yana bukatar kusantarki koda so ɗaya ne kin hana" da sauri Asmah ta girgiza mata kai, a fili ummi tace "A'a to meke damun son ne wai" shiru tayi ta dafe kai, cen kuma tace "to ko yana nufin cewa ke zaki fara neman shi" shiru Asmah tayi don bata San amsar da zata bata ba, ganin bata bata amsa ba hakan ya tabbatar mata da cewa bata San amsar da zata bata bane, tace "aiko dai idan ma hakan yake nufi to kuwa yayi wauta dan kuwa hakan bazai taba saɓuwa ba wai bindiga a ruwa inji hausawa, dole shizai fara nemanki don wannan ba tarbiyar mu ta Mallam bahaushe bane, sai kace wasu ƙabilu,zamuyi maganin shi, inyasan wata ai baisan wata ba" "Ki bani hankalinki da kyau, ki amsamin tambayata, idan kuna wasannin kina mayar mai damartani ne?, girgiza kai Asmah tayi kafin tace "A'a ummi bana iyawa kunya nakeji" ummi tace "OK hakan ma yayi, to kina jin alamar abinshi ya miƙe idan kuna wasan" dagowa tayi bata gane me ummi ke nufi ba hakan yasa tayi shiru"ki bani amsa nace kinajin alamar abinshi yana miƙewa so nake Na tabbatar kalau yake dan insane irin matakin da zan dauka" Asmah cikin rashin fahimta tace"ummi wani Abu" daƙuwa ummi ta mata tare da cewa "gidanku Asmah, kibani amsa ba wasa nakeyi dake ba, nace kina ji ko ganin abin shi Na maza abin fitsarin shi nake nufi, kinaji yana yin karfi idan kuna wasa" sai lokacin Asmah ta fahimci ummi, take wani irin kunya ya lulluɓeta ba shiri takai tafukan hannayenta ta rufe fuskarta ganin haka yasa ummi cewa aɗan kausashe "zanci gidanku fa ki bani amsa, ko kinga wasa a idona" girgiza kai tayi still idanunta na rufe, ta tuna sometimes takanji abin ya miƙe ya zama ƙato yayi karfi kamar katako, har taji yana zungurinta wani bin, duk da dai bawai ta taɓa taɓawa bane, ,takanyi mamaki, har ta tambayi kanta to dama haka nasu yake da karfi ko kuwa nashine haka, da'ker ta daure tace "umminmu ban sani ba amma shidai nashi abin yana da karfi sosai kamar katako " tafa hannu ummi tayi tare da cewa "to wlh garau yake wulakanci ne so yake ya ƙure ki, to kuwa saidai ke ki ƙure shi, ina fatan set din kayan da addawiyya ta haɗa miki suna nan baki kyautar ba" Asmah tace "eh ummi suna nan banma taba buɗe kwalin ba" ummi tace "yawwa to yau inkin koma gida ki kulle kofarki, dakyau ki farke kwalin duka kayan ki daukomin hotonsu a wayarki gobe kizo dasu zan nuna miki waɗanda zakiyi amfani dasu, sanna zan buga ma anty maryar muktar yar zamfara ta aiko min da turaren (kokaƙi Allah) dashi zamu yi amfani ta ruwan sanyi duk taurin kanshi, saiya sauke shi, ke ko aljanu ne ke hanashi sai sun sake shi a lokacin, yanzu bari na baki tsarabar dana zo muku dashi, tunda naga sauran duk suna da kunshi, kene me bukatar su a yanzu, wani ƙaton jaka ta dauko ta buɗe take ta shiga fito da magunguna, magungunane masu kyau da inganci Wanda tayi orden su a gurin anty maryam muktar ana saura kwana biyu zata zo, amma ba bata lokaci har kayanta ya iso cikin sauƙi, nan ta ba Asmah waɗanda tasan ya kamata tayi amfani dasu tace taje ta fara sha kafin goben tazo da hotunan waɗancen na gurin ta,amsa tayi tana yamutsa fuska ganin haka yasa ummi cewa "bani nan da ganin yadda kike yamutsa fuska ba abin arziki Zakiyi ba", da kaina zan dinga baki, waɗanda zata iya sha a nan take ummi ta ritsata tasha sauran da sai anjima kuma ta saka mata a jaka tare da ja mata kunnen akan ta tabbatar tasha a gida . Daidai nan su zahra suka dawo, batool tace tana bin kayan magungunan dake barbaje a ɗakin da kallo "wai ummi ƙusƙus din me kukeyi ne tun dazu fiyye da awa ɗaya" ya Rabi'ah kam cewa tayi"ayya ummi wato tunda kinfi ɗasawa da ya Aslam shine kika ware tashi matar kike gyara mashi ita mu kuma ko oho ko" dariya Rabi'ah ta bata, ummi tace "eh mana ai zamanin kowa kanshi ya sani nima ɗana kawai na sani," kallon Amira da Khadijah tayi tace "ku kuje gurin mummy ta gyaraku, itace sirikarku" batool tace "to mu gurin wa zamuje umminmu" ya Rabi'ah cikin dariya tace kowa taje gurin uwar mijinta, daƙuwa ummi tama ya Rabi'ah, sannan ta kalli su batool tace " daughters ni zan gyaraku, to kuma naga kowacce taci wake ta koshi, ya za'ayi kenan, amma dai bari na gani ko akwai irin naku" wani ummi ta dauko a roba anyi sillin din bakinshi ta mikawa batool, zahra tace "ummi nifa" ummi tace ke bazan baki shi ba saboda bake kaɗai bane gurin Barr in nabaki zamu shiga hakkin maryama, kukan shagwaba zahra tasa tana diddira ƙafa tace "ummi don Allah ki bani sai Musha tare da ita ai" tafa hannu ummi tayi tare da cewa "iyyee yaran mummy fa angirma" batool dake dudduba robar maganin da ummi ta bata cak ta tsaya tare da dagowa ta kalli zahra dake kukan abata itama tace"wait zahra naji kamar kince a baki magani kuje kusha da kishiyar ki?" Zahra ta harareta tare da cewa "haka nace what is ur problem" dariya batool ta kwashe dashi tana nuna zahra cikin dariya take cewa "kuji wani ɗiɗiɗi, yau naga zallar iyayi da neman suna,lallai zahra baki da hankali kishiya zaki ba kayan mata ta sha" su Amira da Khadijah kam batool ce ta basu dariya, nan suka shiga yi, ummi ma saida ta gama cin dariyarta sannan tace "to ina ruwanki batool, zaman lafiya ne ya kawo haka, koba haka ba zahra " ummi ta karkare maganar tana kallon zahra data cika fal tana aunawa batool harara, nan kuma aka koma caftar kishiya da kishi, batool na basu labarin budurwar Dr bash, data nace tana sonshi wai ita Dr basira, nan ta shiga basu labarin diraman da suke kwasa da Dr bash akan basira suna ta shan dariya gwanin sha'awa, ummi na jinsu kawacce na kawo nata firan da abinda ya shafi nata gidan, ummi na jinsu duk in taji abinda zata gyara masu ta gyara musu , tana yi tana kara koyar dasu dabarun zama da miji da yadda zasu samu rabo duniya da lahira, a haka aka kira mangariba suka tashi domin zuwa su gabatar da sallah. Bayan ya ajiye Asmah bai zame ko ina ba sai asibiti gurin Dr bash, saida ya shiga harabar asibitin yayi parking sannan ya daga waya ya kira shi, yana dagawa yace "gani na kawo maka ziyara asibiti" Dr bash dake zaune a office ɗinshi ɗaga kai yayi ya kalli harabar asibitin, inda ake parking motoci, aiko idanunshi ya sauka kan motar Aslam, sai lokacin ya yarda, don da jinshi kawai yayi, aiko cikin son ya jashi yace, "aiko dai ka makaro, dan yanzu nabar asibiti, kaima, kayi ganganci kasan yau weekend ne ba kowani time zaka sameni a asibiti ba" Aslam da idon shi kekan motar Dr dake fake a kusa da shi yace"to shi kuma motar nan na uban waye, Mallam karka raina min hankali mana" dariya bashir ya kwashe dashi yana cewa "ta kaima irin wannan ziyara haka ba notice" Aslam yace "to ko na koma ne" da sauri bashir yace "ni na isa nace ka koma yi hakuri ka karaso babban yayan mu" kashe wayar yayi batare da ya amsa mashi ba, ya fito ya kulle motar shi tare da nufar cikin asibitin......... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOk {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} 112 Yana shiga office ɗin Dr bash ya taso da sauri hannun shi rike da hanky ya shiga kakkaɓe mai kujeran dake gaban table ɗinshi, yanayi yana faɗin "sannu da zuwa babban yayan mu, sannu da zuwa sannu da zuwa maraba maraba lale lale" da jin ma yadda yake maganar kasan harda shaƙiyanci a cikin lamarin, yana gama kakkaɓewa yace "bismillah yaya ga gurin zama" Aslam bai tanka shi ba ya nemi guri ya zauna, fridge Dr bash ya nufa ya ɗauko mai ruwa da lemon kwalba da cup ya ajiye mai, sannan ya nemi guri ya tsuguna ta gefen Aslam, harda wani duƙar da kai, irin dai yadda ake gaisar da sirikai, cike da ladabi kamar da gaske yace "barka da yamma yaya, an wuni lafiya ya aiki ya iyalai, ya ɗoƙari" Aslam kam shiru yayi ya kasa amsawa a ranshi yana jinjina shaƙiyancin bashir, jin shiru Aslam bai amsa shi ba yasa ya dogo ya kalle shi tare da cewa "yaya a dai ta hakuri damu bansan laifin da nayi ba baka amsa gaisuwata ba," share shi Aslam yayi bai tanka ba saima wayar shi da ya zaro a aljihu ya shiga lalubar lambar Asmah, bashir ƙin tashi yayi a tsugunen,kallo fuskar Aslam yakeyi yana karantar shi, sai yake ga kamar akwai damuwa a tattare da shi, Aslam kuwa share shi yayi, ganin haka yasa bashir miƙewa tare da cewa "wlh Aslam kai mugun dan air ne, " kallon shi yayi ya watsamai harara tare da cewa "har nakai ka, ai baka cika babban dan iska ba tunda ka tashi ai na ɗauka a wurin zaka kwana" dariya Dr bash ya kwashe dashi, yana zagayawa ya zauna a nashi kujeran irin mai jujjuyawa da mutum ɗin nan, yace "to yane meye labari kwana biyu saduwa tayi wuya" Aslam yace "wlh Abubuwan ne yanzu sai a slow" Dr bash yace "wlh fa sai a hankali, to ya amarya ya Amarci, fatan dai anci Amarci lafiya" kallon shi Aslam yayi "tare da cewa ina ruwanka, tunda kai kaci naka ai shikenan" dariya Dr bash yayi tare da cewa "faɗi ka kara naci sosai kuwa inama tsakiyar cine yanzu haka, kaii aure da daɗi wlh nake gaya maka ma Mallam, abin sai wanda yayi, my teema duniya ce" hararan da Aslam ya watsamai yasa yayi sauri daura hannu a baki, yana zaro ido, can kuma yace "au na manta a shefa kai sirikina ne yanzu bai kamata na dinga faɗa maka irin wadannan maganganun ba" Aslam yace "kaidai ka sani da iskancinka, kuma wlh Abi min kanwa a hankali ba motar hawan mutum bace da zaike hawa any how" Dr bash yace "sannu fa yaya mai kanwa, inace kaima kanwar wani ka ajiye a gidanka, kake hawa " Aslam yace "karya kakeyi ba kanwar kowa na ajiye ba kanwata ce" bash yace "nafa ga alama, daɗin abin nima dai inada kanwowi bama kanwa ba" Aslam yace "to naji parrot sarkin surutu, ni yanzu duk ba wannan ya kawoni ba" gyara zama bashir yayi, ya maida hankalin gaba daya ga Aslam dama tun farko ya fahimci kamar yana da damuwa, "ina jinka friend meke damunka" huci mai zafi ya furzar daga bakin shi, sannan ya kalli Dr bash fuskar shi ta koma serious alamar abinda zai fada mai mahimmanci ne yace, "wlh neman mafita nakeyi shawara nakeson ka bani" bash yace "ina saurarenka abokina menene damuwarka"tiryan tiryan Aslam ya shiga ba bashir labarin abinda ya faru tun farkon aurensu har zuwa halin da suke ciki a yanzu. Tun kafin labarin yayi nisa wani mugun dariya ya turnike Dr bash, matsewa kawai yakeyi saboda yana son yaji karshen labarin kuma a yadda Aslam yaci serious akan maganar yana yin dariyar nan zai bata komai karshenta ma yayi zuciya ya tashi ya wuce, saidai idan ya faɗi abinda bazai iya jurewa ba yayi sauri ya tsuguna kasan table ɗin dake tsakiyarsu kamar yana duba wani Abu anan zai samu yayi dariyar shi mara sauti sannan matse ya dago yaci gaba da sauraren Aslam yana gyada kai kamar yana jimamin maganar. Saida Dr bash ya tabbatar Aslam yakai karshen labari, ya kalle ya kece da wata irin dariyar keta har yana dukewa yana rike ciki,a hargitse Aslam ya zaro ido yana bin bashir da kallo, a fili yace "kan bantan uba " ina bashir baisan yana yi ba, a fusace ya miƙe tare da dukan table din dake tsakiyar su da karfi, sannan ya juya yayi hanyar fita, bugun table dinne ya dawo da bash hankalinshi, da sauri yabi bayan Aslam ya riko mai hannu, still kuma bai daina dariyar ba, Aslam kallo shi yakeyi a zuciyar ji yake kamar ya buga mai kulli a baki sai hakoranshi sun zubo kasa, Fisge hannun shi yayi, ya kara yunkurin fita a office din, a karo na biyu Dr bash ya sake riko hannun shi, Aslam yace"bashir sakeni ko na maka gula wlh, wato ga kasurgumin mahaukaci ko, na baka labari ka sakani gaba kana min dariya wato ga sabon kamu daya kwanto daga sakatiri" da'ker bashir ya sausauta dariyar shi, yana haki yace"dan Allah da manzonsa friend kayi hakuri, wlh in ban samu nayi dariyar nan ba bazan iya magana bane, dan Allah kayi hakuri ka koma ka zauna pls for d sake of Allah badan niba" zare hanninshi yayi cikin na bashir ya koma ya zauna ammafa fuskar shi babu alamun rahma. Shima bashir mazaunin shi nada ya koma ya zauna, da'ker ya saisaita kanshi sannan ya kalli Aslam yace,"A gaskiya Abu baiyi dadi ba abokina sannu fa da hakuri, har ina tambayar ka ya amarci,mutanen gari duk inda kabi ana ango kasha mai ashe ko ruwa baka sha, Ashe kai har yanzu muna ango ne, ayya wlh abin tausayi, amma fa indai zan faɗa maka gaskiya kaji, zance kayi wauta, ta yaya zakace mace budurwa ba wai bazawara ba diyar Mallam bahaushe ta fara nuna bukatar ta akan ka sannan ka kusanceta, na farko fa bawai kun tabayi bane fa, haba haba Aslam kaima kasan wannan lamarin bamai yuwuwa bane, kumama kai ba wai ka taba nuna kana so bane fa ta hana balle kace ka kyaleta sai Randa ta so, yoo ni dana nuna inaso aka hana ai ban tsaya daukar wannan iskancin na amaren zamani ba kof daya na mata kawai aka wuce wurin, to balle kai dana tabbata a yanda ka bani labari irin soyayyan da kukema juna wlh baza ta hanaka ba, ka cire tsoro ka jaraba abokina wlh zakazo ka bani labari nina gaya maka, idan kuma baka da isashen lafiya ne kana tsoron karta rainaka, ka faɗa min na hada maka yan kwayoyin da zasu taimake ka baza ta gane ba " harara Aslam ya watsamai tare da cewa "an gaya maka kowa ma irin Kane,ni duk ba wannan ne ke damuna ba" Dr bash yace "to meke damunka, na gane Mallam kawai tsoronta kake, me tsoron mata kawai" ya kare maganar cikin sigar zolaya, Aslam yace "kaima shaida ne niba matsoraci bane, koda cen balle yanzu" Dr bash yace "na sani ai ba tsoron kowa nake nufi ba tsoron Asmah nake nufi" Aslam yace"ko ita bana tsoron ta" bash yace "karya kake yi meyasa ranar da asirinka ya tonu ta gane ciwon karya kakeyi ka kasa tun karanta kai tsaye saida kaga ka kasa bacci sannan kaje " Aslam yace "ai laifi na mata shiyasa bawai dan tsoro bane" Dr bash ya kwashe da dariya tare da cewa "ka yarda kawai Mallam kana tsoronta" ran Aslam fa ya fara baci ganin yadda Dr bash ya dage akan tsoron Asmah yake" haka sukaita musu, Aslam na magana a zafafe, yayinda yake ta kokarin kare kanshi, bashir kuma nata kwasan dariya da gangan kuma yaketa kokarin kunna Aslam din" saida ya tabbatar ya kunnu iya kunnuwa sannan yace" yanzu naji, kadai dage ba tsoron ta kake ba, to naji amma fa bawai na yarda bane, idan kana so na yarda yau ka tabbar min da hakan ni kuma Wlh idan har yau kayi dis virgin dinta zan yarda ba tsoron ta kake ba, musa bet ma wlh ka faɗi duk abinda kake so " Aslam cikin huci yace "haka kace ko to shikenan ni kuma zan tabbatar maka da hakan yau basai gobe ba" a haka suka ajiye wannan caftar suka kama wata, basu suka bar asibiti ba sai da ana kiran mangaruba, a masallacin bakin asibitin sukayi sallah bayan sun fito bash yace "sai ina yanzu" Aslam yace "gidan Rabi'ah zanje na dauketa muje gida daga nan kuma mu gaisa da ummi" bash yace "nima nan zani na dauki batool to amma da nace sai nayi sallan isha'e amma muje kawai kasan ance tafiya bibbiyu yafi dadi" kowanne motar shi ya shiga suka dauki hanyar anguwan fadukwai inda gidan ya Rabi'ah yake. Suna isa kofar gidan motar Abban hanifa na shawo kwana ta dayan hanyar, dukkansu kusan a tare sukayi parking nan suka shiga gaisawa, Dr bash sai lokacin yamai barka baki da baki, nan kuma ya kira Rabi'ah ya gaya mata gashi dasu Aslam, sannan suka shiga, bama kowa a falon duk suna ciki, zama sukayi Abban hanifa kam dakin shi ya nufa, basu fi 5 minutes da zama ba Ummi tayi sallama a falon, fuskar washe take cewa "oyoyo yarana sannunku da zuwa ina azkar naji Rabi'ah na fadin isowarku" daidai nan ta karaso ta zauna a daya daga cikin kujerun falon, Dr bash ne ya fara saurin sauka daga kan kujera ya shiga gaisheta tare da mata barka da isowa lafiya, Aslam kam matsawa yayi gabanta ya tsuguna tare sa kamo hannunta daya ya rike fuskar shi cike da farin cikin ganinta yace"sannu da zuwa ummi fatan kin iso lafiya," murmushi tayi tana daura daya hannunta akan tarin suman kanshi, tace "lafiya qalau my son fatan na sameku lafiya" yace "lafiya qlau , nayi kewarki sosai ummi " tace "nima haka my son, ya aiki ya iyali" yace "alhmdllh ummi" tace "masha Allah, Allah ubangiji ya muku albarka, baki daya,ya karamuku zaman lafiya da kwanciyar hankali ya Baku zuri'a dayya ba" kusan haɗa baki sukayi dukkansu bashir, Aslam, ya Rabi'ah da batool da fitowarsu kenan daga ciki da kuma Amir da shigowar shi kenan falon, gurin cewa "amen ummin" sai sannan ta sauke hannunta akan Aslam shima sakin hannunta yayi ya nemi guri kusa da kafarta ya zauna, Amir kuwa hannu yaba Aslam da Dr bash sukayi musabaha, sannan ya tsuguna ya gaida ummi, kafin ya koma kusa da dr bash ya zauna, ya Rabi'ah data zagayo ta zauna kusa da ummi ne tace "ya Aslam ya Amir da Dr ina wunin ku" Amir ya amsa da lafiya qalau sisto, Aslam ya amsa da ina gajiya yayinda Dr bash yace lafiya qalau anty Rabi'ah barka fa Allah ya raya, da amin suna amsa, batool ma karasowa tayi ta gaida Aslam da Amir ta nemi guri ta zauna, a fakaice Dr bash ke hararanta,ganin ta gaida kowa ban dashi, hararanta ummi tayi tace "shi bashir din uwa ya kashe miki hala" kallon ummi tayi tana dan zumɓuro baki sannan ta kalleshi tace "to ina wuni" duk dariya suka saka mata, banda Aslam daya kalleta ya dauke kai, shifa har yanzu baijin zai iya sake musu fuska , don rashin son raini a jninsa yake, Asman shi ne kawai zai laminci ta raina shi ita ma albarkacin soyayya. Daidai nan Amira ta shigo falon samun tayi suna dariya, bata San ko na meye ba, ta dai ƙaraso, zama tayi a hannun kujera kusa da ya Rabi'ah ta kalli su Aslam da Dr bash ta gaishesu a tare, amsa mata sukayi, gaba daya, sannan ta maida kallonta kan Amir da tunda ta sawo kai falom yake ta binta da kallon luv yana murmushi tace "yayana barka da dare, ka dawo lafiya ya aiki" fuskar shi a washe cikin farin ciki da annashuwa ya amsa mata cike da kulawa, ya Rabi'ah tace "oh ni Rabi'ah duniya mutane kala kala wancen taki gaida nata mijin,wannan kuma saida ta ware shi dabam sannan ta gaishe shi bata hadashi cikin jam'in mutane ba,lallai yaran mummy kuma sha'anin ku, kai kuma ya Amir babu ko kunya kake mata irin wannan kallon a gaban mu " hararanta Amir yayi, sukan dan taba wasa da Rabi'ah kasancewar su abokan wasa, ummi ce ta kalle ta tare da cewa "ya isheki haka Rabi'ah saka idon ki ya fara yawa ina ruwanka wai" dariya ya Rabi'ah tayi. Su Asmah da zahra da khadijah ma fitowa sukayi bayan gaisuwa suka zazzauna aka shiga dan fira jefi jefi, ya Rabi'ah ta mike ta kawowa su Aslam Abinda tabawa, Abban hanifa ne ya fito yayi wanka ya canja kaya, kallonsu yayi yana ba amir hannu Wanda shine basu gaisa ba yace " Ah'ah guys kuce duk kana nan kenan" matar shi ta amsa da "ba dole ba kowa ya biyo sahu" dariya yayi sannan ya shiga gaisar da ummi, daidai nan kuma aka fara kiran isha'e, kallon yayi yace "nidai nayi masallaci" Amir ne ya mike tare da cewa "muje nima" sauran ma suka mike, Aslam ya kalli ummi yace" umminmu bari muyi sallah" tace "to sai kun dawo" sannan suka fice. Suma matan ciki suka koma sukayi sallah, dama sun riga sunci abinci, nan ummi ta bude jakar Asmah ta kwaso sauran magungunan data bata tace "karbi ki shanye ki bani hannu tunda kinci abincin anan shikenan yanzu inkinje gida ba lallai kisha ba" saida ummi ta mata kat a lokacin nan, sannan ta barta haka. Koda su Aslam suka dawo basu shigo ba' Abban hanifa ne daya shigo ya shaida musu, mazajensu na jiransu waje, kowacce kuwa ta tattaro kayanta sukayi sallama da ummi suka fito har main falo suka rakosu, har Asmah zata fita daga falon ummi ta kira ta a kunne ta raɗa mata "daga yau ki dinga mayar mai da martanin kinji" cike da kunya ta gyada kai, Rabi'ah data gama kasa kunne bata jiyo komai ba tace"wai umminmu nifa ban gane ba" ummi tace "ai baza ki gane ba rabi, kuje oh abinku karku ɓata musu lokaci sai da safe, kuzo gobe da wuri kunji ko" da to ummi suka amsa sannan suka fice. Kowacce motar mijinta ta shiga suka dauki hanyar gidansu,suna fita layin kamal na shigowa, shima bai wani dale ba ya dauki deejanshi suka wuce. A hankali yake tukin cike da kwarewa, zuciyar shi kuwa cike take da annashuwa, yanayi yana kallon ta yana murmushi, itakam Asmah gaba daya hankalinta naga maganganun da sukayi dazu da ummi, babu abinda yafi tsaya mata arai irin cewa da ummi tayi, ta dinga mayar mai da martani, Aslam ganin tayi nisa yasa ya kunna wakar *saida ke* na hamisu bireka yana bi a hankali, sautin wakar ne ya dawo da hankalinta kanshi a kan dan bakinshi ta sauke idanunta inda yake motsashi a hankali yana bin wakar. Karki barni, sahibaaata♪ Karki ƙini ki fahimmmta♪ Saidake zani huuuta♪ Zuciya ta dake ne ta lallabo♪ Ta amince ki madani dan dako♪ Shiru tayi tana sauraren wakar da yakeyi, har cikin zuciyarta ko wani baiti daya na wakar ke tabawa, ji take kamar ita aka rairawa wakar,har suka karaso gida babu Wanda yayi ma wani magana cikinsu, bayan ya kashe motar yayi parking, zagayowa yayi ya buɗe mata kofa, dagowa tayi ta kalle shi fuskarta dauke da murmushi tace "nagode Mr Aslam" kashe mata ido yayi tare da cewa "u ar wlcm" fitowa tayi ya kulle motar tare da daukar Jakarta suka shiga ciki, suna shiga falo ya zauna a kujera yana cewa "wash yau nagaji gaba daya jikina ciwo yake min" ita kam Jakarta ta dauka tare da karasawa ciki, wanka tayi ta shirya cikin kanana kaya marasa nauyi tayi wanka da daddaɗan turarenta sannan ta fito fallon, tana baza kamshi, a tsaye ta same shi, yana niyyar shiga ciki, kallonta yayi tayi mai kyau sosai, murmushi ya sakar mata tare da cewa "har kinyi wanka," murmushi tamai itama ba tare da ta tanka ba, yace "to nima bari nayo nazo ki bani labarin abinda ya faru yau a gidan aikin suna" tace "aiko je ka dawo kasha labarai bari na Samar maka abinda zakaci kafin ka fito" yace "OK tnx" ya wuce ya shiga ciki ita kuma ta wuce kitchen. Jelop din spaghetti da yaji kifin gwangwani da kayan lambu ta mai, sharp sharp kuwa ta gama ta kwashe, ta kawo dinning , tana cikin jerawa ya fito shima cikin ƙananan kaya, kujera yaja ya zauna, tare da cewa "masha Allah yar aljannah sannu da kokari" murmushi tayi tare da daukar plate ta shiga serving dinshi, shake plate tayi taf sannan ta tura mai gaban shi, fork ya dauka ya d ɗibi taliyar ya kai loma daya bakin shi, ajiye fork din yayi yana lumshe ido tare da muymuy da baki, hannu yakai ya rike kunnenshi daya yana murzawa yana gyada kai, tana ganin ya fara haka tasan karshen maganar, dariya ta kwashe dashi,tana cewa "zaka fara kenan ko" bude idanu yayi yana murmushi yace "to aike ne wlh kin iya girki mai dadi da saka mutum santi, test din girkin ki daya dana mummy, kai naki ma yafi nata dadi, dan yanzu ita tadan manyanta komai nata ya rage quality" zaro ido tayi tace "innalillahi Mummyn kake cema haka, to kuwa sai na gaya mata" dariya ya kwashe dashi yana cewa "ai nasan baza ki iya bane yarinya", haka yake ta cin abincin suna fira cikin nishadi harya kammala. Falo suka dawo ya zauna akan 3 sitter tare da daukan remote yana chanza Chanel, zuwa tayi ta kwanta a kujeran daya zauna tare da yin pillow da laps dinshi tana kallon fuskar shi, shima kallonta yayi bayan ya gama canza Chanel din ya saka Wanda yake son ya kalla, kashe mata ido yayi tare da cewa yanzu kuma sai ki bani labarin abin da ya faru yau a gidan Rabi'ah, murmushi tayi tare da cewa "oya karkabe kunnenka kasha labari" karkabewan kuwa yayi, tiryan tiryan ta fara bashi labarin tun daga zuwanta gidan irin rungumar da suka ma juna ita dasu batool da irin farin cikin da sukayi na ganin juna, har aka gangaro batun ciki. Kallon fuskarta yakeyi, babu ko keftawa zuciya cike da wani irin rauni, tunda ta fara bashi labarin batun cikin da yan uwanta keda shi zuciyar shi ta karye tausayin Kansu ya kamashi, daga yanayin yadda take bashi labarin cike da zakuwa da shauki ya tabbatar mai da abin ya shigeta sosai, take yaji a zuciyar shi ya zama wajibi yau shima ya ajiye duk wani Abu gefe ya kusanceta, ko suma zasu samu nasu cikin, gefe guda kuma ga bet dinshi da Dr bash dake dawo mai dalla dalla a zuciya kamar a yanzu suke kullawa. tuni idanunshi sun rine ya ma daina fahimtar labarin da take bashi, da wani irin sauti ya kira sunanta, take hankalinta ya dawo kanshi ta dago da idanunta ta sauke a cikin nashi, ji tayi gabanta ya fadi meya same shi ne haka yanzu yanzu, shima yana kallon cikin idanunta yace "kina son ciki kema" jim tayi kaɗan kafin a hankali ta gyada mai kai don da gasken tanaso itama, ya sake cewa, "kin amincemin a yau na baki ciki da yardan ubangiji"duk da ta daɗe tana jiran wannan rannan saida gabanta ya yanke ya fadi...... Me kuke tunani zai zama amsar Asmah, yes or no, 😅 Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO ~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 113 Duk da ta daɗe tana jiran wannan rana saida gabanta ya yanke ya faɗi, zuba mata rinannun idanunshi yayi yana kallon fuskarta,zuciyar shi na bugawa da wani irin sauri, cike yake da fargaban amsar da zai fito daga bakin ta. Asmah kam gabanta ne yaci gaba da faɗuwa, ta sani a yadda take jin soyayyar shi a zuciyarta a halin yanzu babu abida zai nema a gareta ta hanashi muddin tana dashi, kuma bugu da kari ai ciki yace zai bata, wanda a halin yanzu babu abunda take bukata sama dashi. Ganin tayi shiru tana tunanin amsar da zata bashi, yasa ya sake cewa "dan Allah my husnah karkice no, ki bani dama muma mu samo namu cikin yau" kallon cikin idanunshi take ta kasa cewa komai, marairaice fuska yayi yana binta da irin kallon pls ki tausaya min ɗinnan, lumshe dara daran idanunta tayi ta buɗe akan fuskar shi, sake tambayarta yayi cikin marainiyar murya, "kin amince min ko my husnah?" A hankali ta sake lumshe idanunta ta buɗe a cikin nashi, a cikin kwayar idanunta ya fahimci mai take nufi, hakan na nufin ta amince mai su zamto Abu guda kenan, wani irin Sanyi yaji yana ratsa zuciyar shi, wayyo dadi yau shi Aslam zai mallaki husnar shi, yau shi husnah ta amince ta mallakawa kanta, wani irin shauki ne yaji ya ɗibeshi a zafafe ya haɗe bakinshi da nata ya shiga bata wani irin hot kiss mai birkita brain. Bai kara birkicewa ba saida yaji ta mika hannu ta tallabo keyar shi, ta shiga mayar mai da martani da irin nata salon da bata san ma tanayi ba, birkice mata yayi take ya shiga mika hannun shi ko wani sako da lungu na jikinta, tun daga sama har kasa yake laleta, yayinda bakinsu ke nan manne cikin na juna, yadda take jin sakon shi nayau na shigarta ya linka na kullum so goma, hakan nada nasaba da haɗin ingantattun magungunan da ummi ta mata ɗuransu ɗazu, ita karan kanta a halin yanzu da zaice zai barta haka to ba shakka baza tasan sanda zata nemeshin ba kamar yadda yaso tun farko. saida suka kwashe kusan 20 minutes a haka kafin ya raba bakunan su dana juna,ajiyar zuciya suka shiga saukewa, idanuwansu sun rine kamar gauta, tayar da ita zaune yayi kafin ya shiga kokarin rabata da rigar jikinta yau kam bata hanashi ba, saima taimaka mishi data shiga kokarin yi ta hanyar daga Hannayenta harya samu nasaran zare riga, take fararen madaidaitan cikakkun yan biyu ta suka bayyana ɓaro ɓaro babu ko bra a jikinsu. Yaune ganinshi dasu na biyu a haka zahiran muraran tun ranar daya fara ganisu a ɗakin mummy ranar daurin aurenshi da zee har yau daya sake ganinsu a karo na biyu daidai da minti daya hotonsu bai taba gogewa a brain dinshi ba. Yau kam kallon ƙurillah yake binsu dashi kallon halal ba irin kallon tsoron da ya musu ɗakin mummy ba, tabbas kallon tsoro dan yaune yake ganin Asalin kyau da tsari da cikar da Allah ya masu, a hankali ya mika hannayenshi tare yi musu wani irin cafka cikin wani irin style na musamman. Asmah ji tayi kamar numfashinta zai dauke tsabar wani irin shock da taji a lokacin da hannayenshi suka sauka a kansu, shikam Aslam wutar kanshi ne ta dauke dif na wucin gadi, duk yadda yake hasaso taushi da laushinsu abin ya wuce haka, ya Daɗe yana mafarkin wannan ranar da zai cika hannayenshi da wadannan kyawawan halittu na kirjin husnar shi. Wani irin murza ya shiga musu na musamman yana wasa dasu cike da kwarewa, take jikinta ya kama wani irin karkarwa tana neman ta kasa zaunuwa charging point dinta kuwa ji tayi yana mata wani irin zillo mai gigitarwa, ganin haka yasa ya kwantar da ita kan kujeran tare da kifa kanshi a kirjinta ya cafki boobs dinta guda ɗaya ya shiga tsotsa cike da kwarewa dayan kuma ya kifa hannunshi akai yana murzawa. Shikenan kuma Aslam ya idasa birkitata, take ta matse kafafunta da karfi dan ji take kamar ƙasanta zai zillo ƙasa,hannu ta saka ta ƙara danna kanshi sosai a kirjinta, tana yamutsa suman kanshi, saida ya tabbatar gaba daya bata cikin hayyacinta bata ma San me takeyi ba, sannan ya mika hannunshi ƙasa ya zare dogon wandon dake jikinta, ya cillar ya rage daga ita sai pant,gaba ɗaya hankalinta ya gushe bata san wainar dayake toya wa idanunta a runtse suke ta kasa buɗewa ta kalle shi, shima gaba daya jikinshi rawa yakeyi, nashi kayan ya shiga zarewa da ɗaɗɗaya yana cilli dasu, saida ya rage daga shi sai boxer, gaba daya burinshi bai wuce ya jishi yana iyo a tekun zumar ta ba, baya jin yana da karfin da zai iya daukarta zuwa ciki a halin yanzu kuma ya tabbata baza ta iya takawa da kafarta ba, gara kawai su tsaya anan ɗin haka allah yaso su kuma a falo zasu fara cin nasu amarcin,cikin rawar jiki ya miƙe ya kashe wutar falon ko ina yayi duhu sai dan hasken dake ratsowa ta window. Dawowa yayi ya saka hannun shi dake karkarwa ya zare pant din daya rage mata a jiki yayi cilli dashi, yatsar shi manuniya ya mika a hankali ya shiga zageye charging point dinta dashi, yana mata wasa da gurin,ji yayi gurin yayi wet sosai ga wani irin taushi da yake dashi. Jin Abu na yawo a indai ke mata ƙaiƙayi yasa ta shiga wani irin mimmiƙewa tana sakin wani irin nishi mai tayar da hankalin mai sauraro idanunta dai a runtse batama San tanayi ba, ganin haka take yaji marar shi ta wani irin kulle ga Ak dinshi sai wani haniniya take yi ba shiri ya janye hannun shi da sauri tare da gyara mata kwanciya dakyau akan sofan yadda zaiji dadin harka, ya maye gurbin hannun shi da Ak 47 dinshi data kumbura ta kara girma da tsayi. A hankali yayi niyyar shigarta, saidai yadda yaji gurin a tsuke sosai kamar ma babu alamar akwai hanya, yasa yaga kamar idan ya tsaya bi a hankali zai bata lokaci ne , burin shi a yanzu bai wuce ya mallaki husnar shi ba, gani yake kamar idan ya jinkirta wani Abu zai iya mai shamaki da hakan, take kawai ya danna kai da karfi bayan ya karanta addu'ar saduwa da iyali, dan ma Allah ya taimake ta wurin a jike yake shakaf. Wani irin gigitaccen ƙara ta saki tare da ƙamƙame hannayenshi daya riketa da kyau dashi, dan ji tayi lokaci ɗaya kamar amsa reza an mata ket a wajen,kafin kuma raɗaɗo ya baibaye wajen gaba daya,take hawaye ya shiga ambali a fuskarta idanunta dai a runtse. Aslam kam suman wucin gadi yayi jinshi a wata wata sabuwar duniya ta daban, Wanda bai taba tunanin mutum na iya zuwa ba, take ya rasa a ina yake ne mawai, sama yake ko ƙasa, duniya yake ko a aljannah , ji yayi kamar ya kurma ihu tsabar daɗin da yaji, daƙer ya samu ya hana kanshi aikata hakan, da zafi zafi karfi karfi ya shiga aiki ba ji ba gani, to an Daɗe ba'a hadu ba. Asmah kam tunda ta saki ƙaran nan na farko bata kara buɗe baki ba, ji tayi kamar andanna ma bakin ta padlock, yama ki buduwa kwata kwata, sai hawaye dake sharara, tana juya kanta left and right, wani irin azaba takeji Wanda zata iya rantsuwa tunda tazo duniya bata taba jin irinshi ba, wai damma ita din mai juriya ce sosai. Aslam bai sarara mata ba saida ya samu cikkaken gamsuwa wannan tunda yake bai taba samun irinshi ba, kamkameta yayi baisan sanda hawaye ya fara bin fuskar shiba shima, a fili ya shiga furta, "alhmdllh rabbil alamin,alhmdllh alhmdllh" dagowa yayi ya kalli face dinta daya kenan gaja gaja da hawaye ya sakar mata kiss a forehead, tare da kara rungume ta ya manna bakin shi saitin kunnen ta a hankali ya shiga raɗa mata"nagode my husnah da kika mallakamin kanki, nagode da wannan babban kyauta da kika bani, nagode da kika adana min kanki kika kawo min budurcin ki,Allah ya saka miki da alkhairi, kin shayar dani zumar da ban taɓa shan mai zaki irin shi ba, nagode Asma'ul husnah ina sonki da dukkan zuciyata " duk da halin da take ciki na radadin azabar da charging point dinta ke mata ga kuma sanyi sanyi da ta faraji kamar zazzaɓi na shirin rufete, saida ta saki murmushi mai kayatarwa, ji take kamar ta furta mishi itama tana matukar sonshi a halin yanzu saidai kuma kunya baza ta barta ba. Sake ta yayi tare da lalubar boxer dinshi ya mayar, sannan ya kunna wutar falon, duk da idanunta a runtse suke har yanzu hakan bai hana ta gane ya kunnan wuta ba, tuna a halin da take ciki na tsiraici yasa tayi sauri ta juya baya ta fuskanci jikin bayan kujeran, juyowa yayi ya kalleta jin motsinta, gani yayi ta juya baya, murmushi yayi a fili yace a hankali yadda baza ta jiyo shi ba, "sarkin kunya kenan wanna ai shi ake kira bonono rufe daki da barawo" ya karashe maganar idanunshi na sauka akan lafiyayyen hips dinta, da kuma ash dinta dake nan mai kyau da daukar hankali, take Ak dinshi ya fara haniniya, kallon wurin yayi tare da bubbuga hannun shi akai yana cewa"easy mana kai" zuwa yayi ya sunkuceta ta baya bai dire ta ko ina ba kuwa sai bed room dinta, ajiye ta yayi kan bed ya lulluɓeta da duvet, sannan ya wuce toilet ɗin tsarkake jikin shi ya fara yi sharp sharp sannan ya haɗa mata ruwan dumi cikin jacuzzi, dauro tawel a kugu yayi ya fito, samun yayi ta a yadda ya barta saidai da alamu kamar barci yadan kwasheta, duk da dai dama idanunta a lumshe yake, amma daga yanayin yadda take sauke nunfashi ya fahinci hakan duk da haka sunkutar ta yayi zuwa toilet din. Jinta a hannun shi yasa ta farka daga dan baccin daya sureta, jinta kuma a cikin ruwa yasa a firgice ta ware idanunta da tunda aka fara wasan suke lumshe, take suka faɗa cikin nashi da sauri tayi maza ta mayar ta rufe su. Wani irin dadi taji lokacin da ruwan ya fara ratsa ta, take ta nemi raɗaɗin da takeji ta rasa, bata San sanda ta fara ware ƙafa ba, saida ruwan ya salance ya kara canja mata wani kusan so biyu, duk wannan abinda akeyi taƙi yarda ta bude idanunta, haɗa wani ruwan yayi ya shiga yi mata wankan tsarki, tana jinshi tana so tace ya bari tayi da kanta amma baza ta iya bude baki tayi magana ba, dan wani irin yanayin ciwo ta fara ji ajikinta haka ya gama mata wankan tare da daura mata alwala, sannan ya nannaɗota a tawul ya fito da ita. Kamar kar su fito daga toilet ɗin, take wani zazzafan zazzaɓi ya rufeta cikin abinda baifi five minutes ba, kwantar da ita yayi akan gado ya kashe Ac dake kunne ya rage gudun fanka, sannan ya bude wardrobe ya dauko mata riga da wando masu kauri, rigar mai dogon hannu, mai kamar rigar sanyin don harda hulla gare shi da wandon shi shima dogo mai kauri ya sanya mata, kara taba jikinta yayi yana nan da zafin shi saima karuwa da zazzabi yakeyi, hankalin shi kuma take ya tashi, me zai bata tasha ya saukar mata da zazzabin,wani taimako zai bata na gaggawa, take zuciyar shi ta bashi shawara ya kira Dr James ya gaya mishi, tsabar rudewa yama manta sunada first aid box a gidan, dako paracetamol ya bata, garin kiran Dr James kasancewar a rude yake ya dannawa Dr bash kira, saboda sunan su kusa da juna yake kasancewar Dr dake gaban sunan kowannen su. Suna cikin baccin su mai daɗi kanannaɗe da juna, wayar shi dake yashe gefen fuskar shi ya fara vibration, kasancewar sa mara nauyin bacci yasa take ya buɗe idanunshi da suke cike da barci, dan suma basu daɗe da yin barci ba an gama shan harka ko wanka ma basuyi ba, duk tunanin shi daga asibiti ne kiran, dan sau dayawa yakan samu kiran tsakar dare musamman idan aka kawo Mara lafiya babba Wanda ba kowa ni likita ne zai iya duba su ba, sai a kirashi saboda yadda Allah ya bashi kwarewa sosai akan aikinsa, hannun ya mika ya dauko wayar, sunan da yaga yana yawo a gaban screen ɗin wayar ne yasa take idanunshi suka watsake, har hannun shi na rawa wajen saurin amsa call ɗin karya tsinke. Aslam bai Ankara da Wanda ya kira ba saida ya tsinci muryar Dr bash na rafka sallama ta cikin sifikan wayar shi, sauke wayar yayi a kunnen shi ya duba sunan aiko dai Dr bash ya gani a rubuce madadin Dr James da yake tunanin ya kira, Dr bash jin shiru yayi yawa yasa ya shiga cewa "hello Aslam ya akayi ne" Aslam dai baida wani mafita tunda ya riga ya kirashi, tunda dai dashi da James din duk Abu daya zasu iya mishi, dama shi tsoron shakiyancin bashir yasa ya ga gara ya kira bare, inba don haka ba ai Dr bash dama ya kamata yakira tun farko. Aslam yace "Dr bash pls taimakon gaggawa nake nema wlh husnah ce yanzu yanzu jikinta yayi mugun zafi, daga yin wanka" Dr bash da dama tunda yaga kiran abinda ya kiyasta a ranshi kenan, ya kece da dariya kafin yace "attakbir Allahu Akbar, masha Allah, masha Allah, ango kasha kamshi, Allah yasa dai ba farke ta kayi ba, yasa har zazzabi ya rufeta haka" Aslam ganin zai cikashi da surutu yace"bashir zan ci ubanka fa, ka faɗi min abinda zanyi wa matata, tana jin jiki, kaƙi kuma kana Neman ka cika min kunne da surutun ka na wofi" Dr bash cikin dariya yace"kaga Mallam bani ne fa nakar zoman ba, ratayar ma ni ba'a bani ba, ka hauni da zagi sai kace ni na daura mata ciwon ,kokuma uban wani yace ka haike mata karka bita a sannu, ka nemi paracetamol da panadol ka bata mu gani zuwa safe idan abin yaƙi ku taho asibiti na dubata daga nan idan da dinki na dinke ta " Aslam yace "Allah ubangiji ya tsari gatari da saran shuka, dana bari ka dinketa bashir ai gara na dinketa da kaina" yana gama faɗin haka bai jira amsar dr bash ba ya katse kiran. Dr bash a can bangaren dariya ya kwashe dashi, dama tsokanan shi yayi dayace ya ɗinketa yaba son yaji abinda zaice, a fili yace kuji dan banza, wai wani ya dinketa da kanshi. Dakin da first aid box dinsu yake ya nufa ya bude,cikin sa'a kuwa ya samu paracetamol din da panadol, dauko wa yayi tare da ruwa mara sanyi yazo ya tallabota ya bata, har sannan jikin da zafi, saidai tana shan magungunan kafin kace kobo barci ya kwasheta, hayewa gadon yayi shima ya jawota jikinshi ya rungume , zafin jikinta na shiga nashi ya ja musu bargo, kasa barci yayi sai tunanin abinda ya faru yan awannan baya da suka wuce yakeyi shi kadai yaketa sakin murmushi kamar wani sabon kamu fatan shi bai wuce Allah yasa ya jefe kollo a raga a cikin wannan daren ba.......... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 .💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 114 Baisan sanda bacci barawo ya kwashe shi ba, sai kiran Assalatu daya ji a kunnen shi ya farkar dashi, kallon fuskarta yayi har lokacin bacci takeyi sosai, mika hannu yayi ya taɓa jikinta, alhmdllh zazzabin ya sauka babu zafin nan kau kamar na jiya sai lan dumi Wanda dama shi nomal ne. Zare jikinshi yayi a hankali don karta farka ya lallaba ya shiga toilet alwala ya dauro sharp sharp yazo ya shirya cikin dogon jallabiya ya kabbara sallan nafilan raka'atanil fajr, yana idar wa ana shirin tada sallah a masallaci, don haka ya fito ya nufi masallaci donya samu jam'i, daya iso main falo saida ya tsaya yana kare mai kallo jin alwalan shi na shirin earewa yasa ya fice da sauri. Tun farkawan shi itama ta farka saidai batajin zata iya motsin da har zai fahimci ta farka ɗin, matsanancin kunyar shi takeji, bata jin zata iya kuma haɗa ido dashi. Yaye bargon daya rufe ta dashi tayi, sannan a hankali ta lallaɓa ta tashi zaune tare da ziro kafarta kasan bed din,jikinta gaba daya ba karfi, saidai taji sauki sosai akan yadda take ji jiya, radadin da kasanta ke mata ma, yanzu taji ya ragu kusan kaso talatin cikin Dari, a hankali ta taka kafarta kasa ta mike tsaye, ji tayi gurin yana mata zafi, kasancewar ta mace mai juriya yasa haka ta daure taci gaba da takawa, duk in ta taka sau daya saita dan dakata, ga tafiyar agwaggwale da kadan yafi na dan kaciya. Da'ker ta karasa toilet din bayan tayi fitsari ruwa tasa mai dumi sosai tayi tsarki dashi, take taji gurin yadan sake mata bakamar yadda ta tashi barci dashi ba,neman guri tayi ta zauna sannan ta fara gabatar da alwalanta cikin tsanaki, koda tazo fitowa tafiyarta tadan gyaru ba kamar yadda ta shiga ba saboda ruwan zafin da tayi tsarki dashi yanzu. A tsaye ta gabatar da sallanta don tana ganin a tsayen zaifi sauki ma akan tace ta zauna ta lankwashe kafa, Allah Allah takeyi ta gama ta koma ta kwanta abinta kamar bata tashi ba, bayan tayi salati ga ma'aiki, tayi tasbihi, azkar dinta tashiga gabatarwa bayan ta gama kuma ta fara gabatar da addu'o'inta nayau da kullum kamar yadda ta saba, da sauri takeyin komai yau don ta samu ta tashi kafin ya shigo, saidai cikin rashin sa'a tana shafa addu,an yana shigowa dakin, shi kuma yau kasa tsayawa yayi a masallacin yayi addu'o'in shi gaba daya hankalin shi na kanta karta farka baya nan shiyasa ya dawo da wuri, ganin ta kan pray mat kuwa abin ya matukar bashi mamaki, da sauri ya karaso cikin dakin. Jin sallaman shi ba karamin faduwa gaban ta ya yanke yayi ba, runtse idanunta tayi a ranta tace,"shikenan sauri ya kare, ya tadda ni, wayyo na shiga uku da kunya niya zanyi" tunanin ta ya katse lokacin da taji alamar ya tsuguna a gabanta. Kallon fuskarta yakeyi cike da wani irin soyayya da tausayawa, hannun shi ya mika ya kamo nata, cikin tattausar murya yace "alhmdllh Allah mungode maka, lallai jiki yayi sauki,tunda gashi har kin iya tashi da kanki kiyi sallah, to fatan kin tashi lafiya ya karfin jiki ya kuma gajiyar daren jiya, gaskiya husnah keta musamman samun kamarki cikin mata dubu sai an tona, " Asmah ji tayi kamar ta nitse a kasa tsabar kunya, take ta kara rintse idanunta da karfi, a ranta tana cewa "wai shi wanna baisan kunyar shi nake ji bane" murmushi yayi ganin yadda duk ta kara rikicewa, hannunta dake cikin nashi ya shiga murzawa a hankali, kafin yace "wannan kunyar yana neman ya fara shigar min hanci da ƴudundune, ina ganin saina zage munba hammata iska dashi tukunna zai kiyaye ni, nasan kinajin yunwa ko?" ya wurga mata tambaya, kwarai tanajin yunwa amma kuma bazata iya fada mai ba don haka tayi shiru kawai da bakinta, murmushi yayi ganin tayi shuri yace "wato kunyar nan banda ido harda baki ya kulle miki ko, to zanyi maganin shi kuwa, ki jirani bari na samo miki abinda zaki ci" ya karkare maganar yana sakin hannunta tare da mikewa yabar dakin, saida ta tabbatar yafice daga dakin ta bude idanunta, tabi hanyar daya bi da kallo kamar shi take kallo. Kitchen ya nufa ba bata lokaci ya soya mata kwai, tare da hado mata tea mai kauri ya dauki silin bredi mai yanka guda uku a fridge ya haɗo dashi, koda ya shiga dakin tana kudundune a bargo, ajiye tiren yayi a kasa yyace "taso kici abinci husnah sai ki kara shan magani,ba sai munje asibiti ba tunda naga zazzabi ya sauka" sarai tajishi amma bata ko motsaba, tashi tsaye yayi ya rike kugu da hannu daya yana kallonta, a ranshi yace"wannan kunyar fa ta husnah ta fara wuce gona da iri dole nayi wani Abu a kai," hauarawa yayi kan gadon tare da yaye bargon data rufa, tadata yayi zaune tare da tàllebe fuskarta da tafukan hannun shi, kallon fuskarta yakeyi yadda ta wani rintse idanunta da matukar karfi, hura mata iskar bakinshi yayi a fuska, kafin a hankali ya bude baki yace "bude idanunki ki kalleni husnah," shiru ba alamar zata buɗe ɗin, ya sake cewa "ki bude fa kafin na dau mataki' don na gaji da wannan punishment din da kike bani" still taki budewa yace "OK nagane so kike mu sake maimaita na daren jiya ko, to ba matsala" ya kareshi maganar yana hade bakinshi da nata, ba shiri ta ware idanunta jin alamar da gàske fa yakeyi,aiko sai cikin nashi idon dake bude yana kallon nata, kallon kallo suka danyi na mintoci bakin su tsill na hade, kafin kuma ta zabura ta shiga kokawar kwace bakin ta dake cikin nashi, ganin haka yasa ya sake ta, zata maida idanun ta rufe yace " kul! kina rufewa, second round babu fashi"dole ta dakata da rufewan tuna bakar azaban da tasha jiya. Murmushi yayi ganin ta dakata, yace "sauko kici abinci" ba musu ta lallaba a hankali ta sauko dan tana tsoron tace "A'a yace zai je second"murmushin ƙeta yayi ganin ya samu lagonta cikin sauki, lallabawa tayi ta zauna a gaban tiren ganin yadda take wani lallaba wa, yasa yaji gabanshi ya fadi karfa maganar Dr bash ya tabbata na cewa kodai farke ta yayi, aiko ya zama dole ya duba ya gani. Zama yayi a gaban tiren shima ya dauki kofin tea din yakai bakin ta, a hankali ta bude bakin ta amsa, kadan kadan ya dinga bata tana kurba, saida ta kusa shanyewa sannan ya ajiye sauran, fork ya dauka ya dinga gutsiran soyayyan egg ɗinnan yana kaiwa bakinta wani bin ya hada da biredi, idan taci taci kamar so uku ya bata tea ta kurba, tadan ci sosai kuwa duk da bakinta babu dadi, amsa kawai takeyi dan karyace zaije second round, ganin alamar ta koshi yasa ya barta haka, sannan ya cinye sauran ya dauki kwanukan ya mayar kitchen tare da dauko sauran maganin ta na jiya da ruwa ya dawo dakin. Balla yayi ya mika mata ta amsa ya mika mata ruwan daya tsiyaya a cup ta sha, yace "to oya muje gado na dubaki wannan tafiyar taki ban yarda da shi ba," da sauri ta dago ta kalle shi wai ya dubata me zai duba? gira ya dage mata tare da cewa, "kinga idan da ciwo sai na dinke miki ko?"ƙin tashi tayi hakan yasa ya dauketa ya dire kan bed ɗin tare da kokarin zare wandonta. Hankalin Asmah kololuwar tashi yayi, dan har zuwa lokacin bata gane mai zai duba ba, take ta fashe da kukan shagwaba tare da rirrike hannun shi da karfi, tana cewa "dan Allah ya Aslam dan Allah karkace zaka kara yi wlh gurin namin ciwo" yace "ki sake min hannu ki gani babu abinda zan miki dubawa kawai zanyi naga ko nayi aika aika " cikin shagwaba tace "inyin nidai ban yarda ba wayau kake so kamin" dariya yayi sannan yace"kefa yanzu kin zama big girl bazan iya miki wayau ba, duba wa kawai zanyi" tace "to naji saika yi min alkawarin baza ka wuce haka ba" ba tare da tunanin komai ba yace "nayi" sauke ajiyar zuciya tayi kafin ta sake mai hannun, karkare zare dogon wandon yayi hade da pant dinta sannan ya ware kafar ta duk da a hankali yayi saida ta saki dan siririn kara cikin kissa, kasancewar dakin a wadace yake da haske, yasa direct idanunshi ya sauka akan gurin, take yaji gaba daya duk wani jijiya na jikinshi ya amsa, dan dukar da kai kasa yayi yana kara lekawa dakyau, babu alamar ciwo a wajen saidai gurin yayi jazur ya ɗaɗe alamar yasha gurza. Saidai kuma an samu akasi dan ji yayi gaba ɗaya hankalin shi ya tashi, gashi yayi alkawarin iya dubawa kawai zaiyi, haka ya tsirawa wajen ido yana hadiye baƙin yawu, jin shiru shiru bai dago yace komai ba yasa ta dago taga ya ake ciki, ganin ya tsirawa wajen ido yana binshi da wani mayen kallo, yana hadiyar miyau kamar wani tsohon maye yasa tayi saurin hade kafarta daya ware, firgigit ya dawo hayyacin shi, kallonta yayi adan birkice yace "alhmdllh babu ciwo"ya fada yana maida mata da wandonta, Jan bargo yayi ya rufe mata har kirji, sannan ya shafa kanta tare da cewa "ki kwanta bari na gyara falo kar muyi baki da sassafe su gane mana sirri" da sauri yasa kai ya fice daga dakin yana matse kafa, yana fita ya fada daya dakin dake kusa da nata , toilet ya fada tare da sakarwa kanshi ruwan sanyi yana sauke ajiyar zuciya,saida ruwan ya ratsa jikinshi sosai ya fito daure da tawul yana share ruwan fuskar shi, a fili ya furta ya zama dole na dage na gasata dakyau, dan bazan iya jira ba,dole na koma round two zuwa dare inba haka akwai matsala. Shiryawa ya shiga yi yanayi yana surutai, akan ina bazai iya daga kafa ba gaskiya, in kuma hoton abinda ya gani yanzu ya fado mai a rai sai yaji Àk shi ya shiga Harbin iska, da haka ya gama shirin cikin kananan kaya, falo ya nufa, tsayawa yayi yana bin ko ina da kallo, kayansu daya warwatsar jiya suna nan a yadda suke, komai nanan yadda sukabarshi, wani irin nishadi na musamman yakeji da annashuwa, wayar shi ya ciro ya shiga yiwa falon short video wai zai ajiye tarihi. Gyara falon yayi tsab ya share ya goge yayi mopping ya kunna burner ya bude show glass ya dibi turaren wuta ya zuba take ko'ina ya dauki kyalli tare da daddadan kamshi, zuwa lokacin karfe takwas na safe yayi, zuwa yayi gaban kujeran da sukayi harka jiya, ya tsaya ya kalle shi up and down sannan ya sumbaci hannun shi ya manna ma kujeran, sannan ya bar falon. Ɗakin ta ya koma ya samu tayi barci, lallabawa yayi yahau gadon ya jawota jikinshi ya rungume tare da gyara musu rufa da kyau, take shima bacci ya kwashe mai cike da mafalkai kala kala. Karfe takwas akayi raɗin sunan babyn ya Rabi'ah inda yaro yaci suna umar, sunan uban mijinta aka saka, duk Wanda yasan Aslam saida yayi mamakin rashin ganin shi a gurin taron sunan nan, har Barr dake nesa yazo, shida maryama da yara, Dr bash da buhu buhun shakiyancin shi yazo da zai saukewa Aslam sai dai cikin rashin sa'a babu shi babu mai kama dashi, Amir kam kasa hakuri yayi saida ya kirashi a waya har sau uku amma ba amsa haka suka watse kowa da nutanin da yake. A gidan suna kuwa wuraren karfe 10 duk kowa ya hallara cikin su banda Asmah, duk wacce ta zo kuwa ita take fara tambaya, saidai ummi tace musu kila tana hanya, a haka har sha daya rana babu Asmah babu labarinta, zuwa lokacin kuwa hankalin ummi ya fara tashi fatan ta Allah yasa dai lafiya, batool da Amira da Khadijah kam ko wacce ta mata misesd call yakai biyar, kowacce tayi ne bada sanin sauran ba, zahra kam tana cen tare da maryama da su hanan da suka zo bata San wainar da ake toyawa ba, zuwa sha daya da rabi hakurin ummi ya kare, take itama ta fita cikin taron jama'a ta lalubi lambar Aslam ta kira har sai uku ba Amsa, dole ta juya akalar kiran kan Asmah. Daidai lokacin kuwa Allah ya farkar da Asmah, a firgice ta tashi don makarki tayi su batool nata kwala mata kira, tashinta a firgice ne ya farkar da Aslam, zaune ta tashi hakan yasa shima ya tashi zaune tare da rikota yana cewa "subhanallahi lafiya husnah menene" tace "ya Aslam karfe nawa don Allah, kallon agogo yayi yace sha biyu saura" ji yayi kawai tace"innalillahi wainnailaihi rajiun, " tana kokarin sauka a gadon, rikota yayi da sauri ya manna ta da jikinshi yana cewa "lafiya husnah menene? meya faru" dan shi harga Allah ya tsorata, gashi shaf ya manta da batun wani suna. Tace "ya Aslam suna, gidan suna, yau sunan ya Rabi'ah, innalillahi gashi barci ya kwashe ni har sha biyu rana tayi" sai lokacin hankalin Aslam ya kwanta take ya saki wani ajiyar zuciya, jin Ashe ma akan zuwa gidan suna take wani firgita, sake yunkurwa tayi zata mike, ya sake rikota tare da cewa "wai kina nufin gidan sunan zakije, baki da lafiya fa" tace "ya Aslam idan banjeba zasu iya yin tunanin wani Abu" yace "idan kikajema sai sun fi gane wani Abu" dagowa atayi ta kalle shi tare da cewa "kamar yaya" yace"idan bakije ba kika ce musu bakiji dadi ba,baza su gane komai ba saidai suyi tunanin ciwon kai ne ya hanaki zuwa , amma kika kuskura kikaje kowa sai ya gane abinda kika aikata jiya" zaro ido tayi tare da cewa "to yanzu ya zamuyi" yace "kawai mu kira waya ki gayawa ummi" tace "anya kana ganin ummi baza ta gane ba kuwa,"yace "baza ta gane ba kawai bari mu kirata" ya karashe maganar yana mika hannu ya dauki wayoyinsu da ya sakasu a silent tun Daren jiya. Daidai time din kuma missed call din ummi na bakwai na shigowa wayar shi, duk da shiyace a kira ummi saida gabanshi ya fadi ganin kiranta rututu, dagawa yayi tare da saka wa a speaker ya mikawa Asmah. Muryan ummi suka tsinkaya tana cewa "Asma'u ina kuka shige ne kuka bar waya anata kira tun dazu,lafiya kuwa meke faruwa wlh hankali na ya tashi sosai, nakira Aslam shiru kema na kiraki shiru,yanzu nake cewa bari na biyo sahu" take bakin Asmah ya fara karkarwa bata iya karya ba a rayuwarta take abinda sukayi shirya da Aslam zata fada ya bace mata bat, ummi jin shiru ta kare" Asmah lafiya kimin magana mana, meke faruwa innalillahi wainnailaihi rajiun" jin yadda hankalin ummi yayi mugun tashi yasa tace tana zaro idanu "ummi ciwo ne" ummi hankalin tashe tace "what! ciwo subhanallahi waya ji ciwo" Asmah mai makon taba ta amsa sai kawai ta mika wa Aslam waya, da yayi tsuru tsuru shima, yana amsa ummi nacewa "kimin bayani Asmah wayaji ciwo cikin ku" shima ji yayi gaba daya ya ruɗe maimakon ya nustu ya bada amsa sai cewa yayi"hello ummi ina kwana" jin muryar Aslam yasa ummi dake firgice don ita kwata kwata hankalinta bai kawo kan kashe boss akayi ba, hankalinta tafiya yayi kan cewa ko sun fito zasu zo ne sukayi accident sukaji ciwo shiyasa duk ta rude, tace a rude"son, son dan Allah ka gaya min mekefaruwa hankalinta ya tashi" cikin rudewa ya samu kanshi da bata amsar da Asmah ta bata yace"ummi ciwo ne" daura hannu ummi tayi aka tare da cewa "innalillahi wainnailaihi rajiun gani nan zuwa gidan yanzu" kit ta kashe wayarta............ Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Naceba🙋‍♀️ Kina bukatan jikinki yazama so fresh ba kwarzane ko daya ballantana kuraje ko tabo, sunburn,acne, ko knuckles? Kije kigwada products na mg's insha Allah zakiga ynd fatarki zedawo fiye da tsammaninki zakigyara jikinki naturally batare da kinbata fatarki ba jikinki yayi fresh kiyi smooth kizama kalar Madara kirar models kiringa walwali kina haskawa duk inda kikayi😍 Kidena kokonto cewa kingwada baki Dace ba insha Allah kijaraba products dinsu bi'iznillah zakiji dadinshi🙏 kayansu akwai kamshi especially sabulun kamshin yakama jikinki ko kindade da wanka jikinki zaidinga fidda ni'imtaccen kamshi bayinki ma zakiji kamshin dazai Kama😍sunada kit special domin amare Wanda indai kinyi using kit dinnan Baki bukatar kikara Kai kudinki gurin dilke domin ainihin yanda fatarki zehaska yagoge kidinga shining abun sewanda yagani😍 Mai bukatar kayan mg's chat:08062991549,07046881166,07067210195 Call:08064532391 Hausawa nacewa adade anayi sai gaskiya Kuma siyan nagari maida kudi gida🤝 💯 tested nd trusted Natural/organic🥰 Page 115 Tsayawa Aslam yayi yana bin wayar dake hannun shi da kallo kamar ranar ya fara ganin waya a duniya, yayinda Asmah ta daura hannu aka, a ruɗe tace"mun shiga uku ya Aslam ga ummi nan zuwa, yanzu ya zamuyi"sai sannan ya dauke kanshi daga kallon wayar ya mayar kanta jiki a sanyaye, ya amsa da "nima bansan yadda zamuyi ba husnah" haka suka zauna tsuru tsuru kowannensu jikinshi a sanyaye, can Aslam yace " na samo mana mafita" a kage tace"yawwa ya Aslam, dan Allah ka taimaka karka bari ummi ta gane komai" yace "kawai abinda zamuyi idan tazo ni zan fita falo kekuma saiki kwanta a ɗaki kiyi barcin karya, kawai sai nace mata kinyi barci" shiru tayi bayan ta gama sauraren shi, tunani takeyi anya wannan shawara ta ya Aslam zata bullar dasu kuwa, ganin tayi shiru yasa Aslam cewa"kinyi shiru husnah koke kinada wani mafitar data fi wannan ne ki kawo" tace "ya Asmah ummi ne fa sai kace baka san umminmu" dafe goshi yayi tare da cewa "kash! to yanzu ya zamuyi" karyar da kai gefe tayi, tare da taɓe baki kamar zatayi kuka, idanunta sun cika da hawaye, jayota yayi ya rungume ya shiga rarrashinta yana bubbuga bayanta kamar wata yar goye, ita kuma sai wani narkewa take karayi tana kukan shagwaba. Ummi na katse kiran bata koma cikin gida ba, direct wajen get ta fito da nufin taje ta samu keke napep, hankali tashe take tafiya tanayi tana gyara zaman mayafin, ko kudin napep din bata dashi daga ita sai wayar hannunta, kallo daya zaka mata kasan hankalinta a tashe yake, kwata kwata bata cikin hayyacinta, tana isowa bakin titi motar Abba hanifa na isowa shima. Tun daga nesa ya hango wata mata mai kama da ummi, saidai kwata kwata bai taba zaton ummi bane, don duk Wanda yasan ummi farin sani idan ya hango yadda take tafiya daga nisa bazai yarda ita bace, domin ummi yar gayu ce sosai tafiyar ta kuwa a tsanake takeyi, cike da nutsuwa irin na manyan mata da suka amsa sunan su, wasu ma cewa sukeyi tana hadawa da yanga idan tana tafiya. Saida ya iso daf da ita sannan ya tabbatar itace, itako bata ma kula da shi ba burinta bai wuce ta samu napep din da zaikaita London road ba, da sauri Abban hanifa yayi parking tare da fitowa a motar shi, har ta gota shi, haka ya bita da sauri yana yana kiranta, ummi jin ana kiranta kuma taji muryar Wanda ta sani ne yasa ta waigo, daidai nan kuma ya cimmata. Ganin Abban hanifa yasa ummi dauke ajiyar zuciya, ko gaisuwar da yake mata bata amsa ba take"yawwa nura nagode Allah ma gaka, muje ka ka kaini London road gidan Aslam" yadda take maganar a rude yasa shima cikin dan rudewa yace "subhanallahi,ummi wani abin ne ya faru" kama hanyar moto tayi tana tafiya ta amsa shi da "inafa lafiya nura, nidai Allah yasa ciwon ma ba mai tsananin bane" ta karashe maganar tana bude motar Abba hanifa ta shiga gidan gaba ta zauna, shima zama yayi a mazaunin driver ya tada motar suka dauki hanya. Jin horn din mota a bakin get din gidan ne ya dawo da hankalin Asmah da Aslam jikin su, ita dake kwance jikinshi ne ta fara jiyowa zabura tayi ta fizge jikin tana zare ido tare da yarfe hannaye, tana cewa "shikenan ya Aslam ummi ta iso" tsayawa yayi yana kallonta bai gane nufin ta ba, saida yaji mai gadi na bude get sannan ya ankare da abin da take nufi tashi yayi tsaye a rude ya nufi window ya ɗan bude labule kaɗan ya leka, daidai nan motar Abba hanifa na kunno kai cikin compound din gidan, da sauri ya sake labulen ya juyo ya kalleta, yana zare ido, Asmah da kenan tsuru tsuru dama ganin haka yasa ta kara aza hunnu akai. Kallonta yayi yace kinsan abinda za'ayi yanzu" da sauri ta girgiza kai, yace "kwanta" kamar zatayi kuka tace "yaya Aslam k" bai bari ta karkare ba adan tsawace yace "ki kwanta nace" ba shiri ta kwanta, ya lullubeta da duvet har kirji, yace ta rufe ido tayi barcin karya, tuni jikin Asmah ya fara karkarwa don kwata kwata bata iya Abu na rashin gaskiya ba, balle ma yanzu da take rude. A kwancen ya barta ya fice daga dakin zuwa falo, ummi ita kadai ta shigo Abban hanifa kuma ya tsaya daga waje, sallama ta rafka a bakin kofar main falon dake kulle ta ciki, Aslam da dama ke tsaye a falo yana jiran karasowarta, ya amsa da sauri tare da nufar kofar ya bude mata, sàwo kai tayi cikin falon tana kare mishi kallo, hakan bai mata ba ta mika hannu ta tattaba fuskar shi, shikam yana nan tsaye gabanta, sai yaƙen dole yake yi. Ummi dai ganin tabbas Aslam garau yake babu ko gwarzane a jikinsa yasa, ta ayya na a zuciyar ta, to lallai Asmah ne taji ciwo bashi ba, kallon shi tayi suna haa ido ya washe mata baki tare da cewa "sannu da zuwa umminmu." Ya karashe maganar yana kama hannunta zuwa ciki, jiki a sanyaye ummi ta bishi, gurin kujera ya kaita zai zaunar da ita tace, "son ina Asmah, meya same ta a ina taji ciwo." Murmushi yayi yana sosa keya alamar rashin gaskiya ya bayyàna a fuskar shi muraran, cikin inda inda yace "tadan kwanta ne ummi, to ta ɗan samu bacci ne yanzu, dama ba fa wani ciwo bane, kawai kanta ne ke dan ciwo kaɗan kaɗan mà yama yi sauƙi" yadda yake maganar duk kame kame sai wani kasa kasa yake yi da kai yana Sosa ƙeya ummi ta fahimci karya yake yi. Hankalinta ne ya kara tashi, take zuciyar ta ta raya mata,to ko Abin ya tsananta be yasa yake boye mata kar hankalinta ya tashi, kallon shi tace a tsawace tace "kaiii Aslam bafa wasa nake dakai ba, nace maka ina Asmah take meya sameta" ganin yadda ummi ta hassalomai yasa baisan sanda ya nuna mata hanyar dakin Asmah ba. Da sauri kuwa ta nufi hanyar daya nuna mata shima ya take mata baya, tana isa ta faɗa kofar dakin da ta gani a gurin, Asmah jin muryar ummi na sallama a dakinta yasa rawan da jikinta akeyi ya karu. Hango ta ummi tayi kan gado da sauri ta karasa tare da dagota tace "subhanallahi Asmah meya sameki, a ina kikaji ciwo garin yaya kuma" rasa amsar da zata ba ummi yasa ta fada jikinta ta fashe da kuka, aikuwa take ummi ta idasa rikicewa, take ta shiga cewa"innalillahi wainnailaihi rajiun, kai Aslam dan ubanka nace ka gayamin gaskiya mekefaruwa ne" ganin yadda ummi ta zubo mai idanunta masu kaifi akan su, yasa baki na rawa yace yana nuna Asmah dake rungume jikin ummi"ummi ki tambayeta ta gaya miki." Juyawa ummi tayi da sauri ta kalli Asmah tace"Asma'u meke faruwa." Itama shi ta nuna tace cikin muryar kuka "ummi ya gaya miki shi." Ummi ranta ya fara baci jin yadda suke ta gara ta kamar ball, ta dago a fusace da nufin ta balbale Aslam da fada, sai gani tayi wayam baya dakin, juyawa tayi kan Asmah tace "to tunda shi ya gudu ke gaya min, kokuma na hada keda shi na muku dukan tsiya, ladan ɗaga min hankali da kukayi da rana tsaka." Shiru tayi tana shesheka ita dai bata iya karya ba, gashi maganar ya mata nauyi, aiko ummi ganin haka tace a tsawa ce"ke nake saurare fa Asmah." Cikin sheshsheka ka tace "ummi shine fa jiya" sai kuma tayi shiru tana ci gaba da sheshshekan ta, ummi tace "uhumm ina saurarenki shine jiya me" tace "shine jiya bayan mun dawo gida ya umm, ya ." Sai kuma ta fashe da kuka ta kasa karasawa, zuwa yanzu ummi ta fara harbo jirgin su, wani ajiyar zuciya mai karfi ta saki jin abinda hankalinta kwata kwata bai je gurin ba. "Kai amma wlh yaran nan kun shammaceni da yawa kun dauki alhakina." Ta karashe tana daga Asmah da tayi luf a jikinta tace "kalleni nan Asmah." Da'ker ta da go da fuskarta amma bata kalli cikin idon ummi ba, ummi tace"a gurin ne a kwai ciwo ko ina" a kunyace ta gyada kai, sannan ta daura da cewa "amma ya duba dazu yace babu ciwo." Ummi tace "kin tabbata ya duba." Ta sake gyada kai ummi tace "to tunda yace babu babun ne." Kin shiga ruwan zafi, nan ma ta gyada kai ummi tace "tun yaushe." Asmah tace "tun jiya."Ummi ta sake tambayar ta kuma gurin har yanzu yana zafi ta sake gyada kai, ummi tace "to baki gasu bane,ina zuwa ki gani" ta karashe maganar tana mikewa ta nufi toilet din dake dakin. Ruwan dumi ta haɗa mata ta debo dan gishiri ta zuba sannan, tace oya ta taso, ganin yadda take tafiya yasa ummi tace "ah lallai baki gasu ba kam, da sauranki" suna shiga toilet ummi tace ta shiga ruwan, tsayawa tayi tana matsar kwallah, ummi tace "shiga mana, nemar miki lafiya na ke yi, yanzu idan baki gasu ba zuwa anjima yace zai koma ai baza kiji da daɗi ba, kuma nasan sarai ba lallai ya daga miki kafa ba, dan ku yaran yanzu ba kuda hankali ba hakuri ne da ku ba akan komai ba balle wannan harka." Cikin shagwaba tace "to ni ummi dan Allah ki fita wlh zan shiga." Tafa hannu ummi ta shiga yi, tace"ikon Allah, yanzu Asmah ni kike kora kar naga jikin ki, inda Aslam ne ai baza ki kore shi ba shi, yara muci kashin ku da fitsarin ku, amma ku raina mu haka, to shikenan ai kin huta, zan fita amma wlh in baki shiga ba kika fito zan gane, sai kin koma na gasa ki da kaina kuma da tafasheshen ruwa, kinji na gaya miki kenan," ta karkare maganar tana barin toilet din. Sauke ajiyar zuciya tayi sannan ta tube ta lallaba ta shiga ruwan duk da kuwa zafin shi don yafi na Aslam daya hada mata zafi, dan taga gara ta shiga wannan kar taƙi ummi tazo ta sakata da kanta a tafasasshen ruwa. Ummi kam falo ta fito Neman Aslam baya nan dakin shi ta duba nan ma wayam, nan ta shiga Neman shi cikin gidan saidai babu ko mai kama dashi, fita waje tayi ta samu Abban hanifa, yana ganin ta yace "ummi meya faru ne , Allah yasa ciwon da sauki" ummi tace "hmmm nura bar tuna min abin haushi, yaran nan ai sunci tuwo a kaina babu wani ciwon dake damun su fa, sheɗantaka ce kawai irin ta Asmah da Aslam." Dariya Abban hanifa yayi, ummi tace "wlh kuwa nura, kaje abinda kawai Aslam zai maidani idan na gama" yace "to ummi sai kin dawo shima ogan yanzu naga ya fita mun gaisa wai zaije masallaci duk da naga kamar lokaci da saura" ummi tace "ai yasan tsiyar daya shuka, to ko Makkah zaije yaje ya dawo zai same ni ai" Abban hanifa yana dariya yace "umminmu adai mishi hakuri." Bata tanka shi ba saima cewa da tayi "to sai anjima nura saina dawo nima". Koda ta dawo zama tayi a bakin bed tana jiran Asmah, saida ta kwashe kusan 30 minute sannan ta fito, dan itama kanta taji dadin ruwan sosai, tun daga yana yin tafiyarta ummi ta tabbatar ta shiga ruwan sosai bata ma kanta algus ba. Kaya ummi ta Ciro mata masu kyau riga da skirt na atamfa ta saka, zama tayi a darare ta kasa hada idanu da ummi, dariya ummi tayi tace "um um amarya kinsha kamshi" cusa kai tayi cinyoyinta tana dariya, nan ummi ta shiga tsokanar ta kamar yadda takan musu wani lokaci lokaci idan ta kama, saida ta gama tsokanar ta, Asmah duk kunya ya cikata kamar ta nutse a kasa, sannan ummi ta daura da nasiha, ta shiga koya mata yadda zata ɗauke bukatar mijinta da kyau yadda bazai ma kalli wata mace a waje ba balle yayi sha'awa, ta gaya mata mahimmanci da tasirin tsarewa miji bukatun shi na shimfida keda shi, har akayi sallah suka gabatar tare da Samar wa kansu abin tabawa sukaci, suka dawo falo suka daura, daga inda suka tsaya, Asmah ta tattara dukkan hankalinta tana sauraren ummi, tana naɗar duk abinda ta gaya mata m card din kanta. Aslam bai dawo gidan ba saida yayi sallan la'asar, duk tsananin shi ummi ta tafi musamman da baiga motar Abba hanifa ba, hankali kwance ya shigo falon saidai ganin su zaune yasa yayi turuss, ummi tace "yayi kyau son dazu muna magana sai dai kawai na juyo ban ganka ba." A daburce yace "ummi kiran gaggawa na samu daga office shiyasa na tafi ban gaya muku ba." Ummi tace "ai nasani" Sosa keya ya shiga yi yan murmushi, tace nidai kafin ka zauna muje ka maida ni gidan suna. Haka ko akayi Aslam ya maida ummi gidan suna a mota itama nasiha ta shiga yi mai akan ya kula da matar shi ya rike amana ya kula da hakkokinta, karshe ta shiga jero musu addu'an samun zaman lafiya mai dorewa da kuma zuria dayyiba. Kwana biyu kunjini shiru ko? Kuyi hakuri wlh ban samu zama bane muna sha'ani, amma yanzu insha Allah zan maida hankali mu gama littafin nan, nasan kuma kun gaji ai, ku kara hakuri in-sha Allah saura kirisss. Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne, knuckles,wrinkles,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulun mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗 Mai bukata should Chat👇 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Team glow🧖‍♀️ Page 116 Koda ummi ta koma gidan suna da gudu su batool suka taso suna tambayar ta lafiya mai ya samu Asmah din, dan Abban hanifa ya kira ya Rabi'ah ya gaya mata, halin da ake ciki ita kuma ta gaya musu nan fa suma hankalin su ya ɗaga suka shiga tsumayen jiran dawowar ummi. Ummi tace masu "babu komai ba wani ciwo bane mai tsananin, wai jiya da zazzabi ta kwana da ciwon kai, to yau ma ko kafin na isa ta wartsake abinta, tace ma zata zo sunan mijinta ne ya hana, tunda jikin ba kwari." Cike da tausayin ƴar uwar su suka shiga yi mata addu'a akan Allah ya ƙara sauki, ya Rabi'ah kuwa dariya tayi, tace "to kodai itama ta harbu ne, dan jiya dama bata cikin lissafi" ummi tace "lalai kam, to sai ki buga ma yayan naku waya ki tambaye shi dan ki tabbatar"zaro idanu ya Rabi'ah tayi tare da cewa "ni shegiya, inji dan daudu, dan Allah umminmu ki rufa min asiri na zauna a ɗakin mijina lafiya." Duk dariya suka saka mata kafin kuma kowa ya kama barkan gabansa, kowacce zuciyar ta cike da tausayin Asmah, duk sun dauki niyyar zuwa har gida su dubota, zahra ma cewa tayi gobe zataje saboda jibi zata koma bidda. Da'ker Aslam ya samu ya iya danne zuciyar shi ya daga ma Asmah kafa a ranar, washe gari kuwa tunda sassafe ya nemi hakkinsa, dan Daren ranar da'ker ya samu ya rintsa, itama bata hana ba, amma gabanta sai faɗuwa yake yi, dan ta dauka zataji zafi ne kamar yadda taji ana farko, duk da ya ce mata babu zafi sosai, ba wani yarda tayi ba, sai dai ga mamakin ta wannan karon babu zafi sosai ɗin, sai ma daɗi da ta dinga ji yana rinjayar zafin, ranar kuwa ba round ɗaya yayi ba sai da yayi biyu lafiyayyu. Bayan sunyi breakfast yace bazai je office ba zai tsaya yayi jinyar ta, gashi ranar monday kuma yana da abu mai matukar muhimmanci a office ɗin ranar, don tun da sassafe bayan sun gama harke yake ta amsa call akai akai kuma tana ji duk akan maganar ne, dan haka da yace bazai je ba tace ya tafi abishi ita taji sauki, ƙin tafiya yayi saida ta saka mishi kuka tukunna daƙer ya tafi, yanayi yana kaiwa gurin mota ya dawo yace yayi mantuwa karshe duk da yadda take jin jikin ta ba kwari saida ta rakashi gurin shiga motar da kanta taga tafiyar shi sannan ta sauke ajiyar zuciya tare da dawowa ciki ta kwanta abinta. Da wuraren sha biyu zahra ta kira ta a waya gata nan zuwa, dan daɗi har da tsalle ta ringayi, zahra naji tace"lallai kin wartsake, to nidai da Allah ki daina wannan tsallen kar amana asarar babyn mu." Ko minti talatin kuwa bata ƙara ba ta iso, kamkameta Asmah tayi tana mata oyoyoo, tunda aka aurad dasu yaune rana ta farko da daya daga cikinsu ta ziyarci gidan daya, rasa inda zata saka ta tayi, karshe dai suka ƙule a bedroom, kafin kace kwabo ta cika mata gabanta da kayan ciye ciye, bayan sun gaisa ta mata ya jiki, suka dan taba tsokanar juna, nan hira ta barke a tsananin su, da'ker suka shiga kitchen sukayi girkin abinda zasu ci. A gidan Asmah zahra ta kusa wuni dan sai da ta jira Aslam ya dawo daga office suka gaisa, gashi ranar bai dawo da wuri ba, sai bayan la'asar tabar gidan inda zata wuce family hausa ta kwana a nan gobe Barr zai zo ya ɗauke ta da yamma, Asmah kam harda kukan ta da zahra zata tafi, balle ma da taji family hau zata, ai ji tayi kamar dama itace zahra, tana matukar son taje gidan nan musamman dan taga mummy da Alhaji baba, amma ƙememe Aslam ya hana. Ganin yadda hankalinta ya tashi da zahra zata tafi yasa yace ta shigo matar su kaita gidan tare amma da sharaɗin baza su shiga ciki ba, ba haka taso ba, amma hakan ma ai ta rage zafi ko ba komai yau zata bi hanyar gidan. Daren ranar ma haka suka kasance da juna, suka faranta ran juna suka shayar da juna madarar farin ciki, ranar kam Asmah bata ji zafi ba ko kaɗan, hakan yasa ta zage sosai ta biye mishi duk yadda ya juyata bata ki sai ma kokarin ta gyara mai da kyau da take yi yadda zaiji dadi sosai, aiko dai ya yaba, domin saida yayi round uku ranar, kwarai ya sara mata yadda take da juriya sosai da kuma kwazo sarai ya fahimci ta gaji amma take ta kokarin ta samar mai farin ciki don ko a fuska bata nuna ta gaji ba, saida ya samu gamsarshiyar gamsuwa, sannan ya ɗauke ta zuwa toilet, ya mata wanka shi ma yayi suka fito suka kwanta Ko minti goma basu yi da kwanciya ba barci ya sureta, dan da gaske ba karamin gajiya tayi ba, to abinda bawai mutum ya saba bane, wai danma ita din matar novel ce😂 Kallon kyakkyawar fuskar ta yayi, idanunta a runtse tana sauke numfashi a hankali, hucin numfashinta na sauka a kirjin shi, tasbihi ya shiga jerowa abangijin sammai da kassai da kuma kirari da yabo, daya dube shi ya mallaka mishi Asmah, ya sani tabbas Allah ya soshi da rahma daya sake ara mishi dama ta biyu a kan ta, take yaji idanun shi ya bushe kamas babu alamar barci, samun kanshi yayi da son yin sallar nafila domin kara mikawa Allah godiya, kiss ya kai mata a goshi kafin a hankali ya zare jikinshi a nata ya maye mata gurbin shi da pillow, sannan ya miƙe. Ranar kusan kwana Aslam yayi yana Abu daya, gaba ɗaya duk Wanda keda hannu a cikin haɗa auren shi da Asmah saida ya musu addu'a, musamman kamal da Alhaji baba da muka Mallam. A cikin satin nan Asmah da Aslam babu Abu da suke yi sai barzar amarci, sunyi wani fresh sunyi shar dasu kamar ƙwenƙwasan inji, duk wanda ya san Aslam sosai idan ya ganshi a yan kwana kin nan sai ya sake kallon shi ya kara. Ita ma Asmah ba'a barta a baya ba, har wani dan ƙiba tayi na jin dadi da samun kwanciyar hankalin, lafiyayyun hips dinnan suka kara bajewa, boobs kuma suka kara cika suka tumbastsa, kullum burinta tayi abinda zai faranta ma Mr Aslam rai. Ranar da suka cika sati biyu da fara shan amarci Aslam dai kasa jurewa yayi yana zaune a falo bayan isha'e ta fito cikin kwalliyarta da take zuba wa na kece raini a cikin yan kwanakin nan, sanye take cikin kananan kaya riga yar figil dako cibiyarta bata gama rufewa ba,ga saman a buɗe kusan rabin boobs dinta na waje, ga kuma wando jins Wanda bai gama kai mata kasa ba 3 quarter damamme, ta gyara dogon gashin kanta tayi fakin dinshi ta gefe, sai baza kamshi take yi tana warwali kamar wata diamond, tunda ta sawo kafarta a falon ya bar abinda yake yi, ya zuba mata idanu, tare da baza hanci yana shakar daddaɗan kamshin ta mai tayar mai da hankali a ko yaushe. Cikin wani irin taku mai matukar Jan hankali take tahowa gare shi, tana sakar mai kayataccen murmushi, tun kan ta karaso ya ware mata hannayenshi, bata yi kasa a gwuiwa ba tana zuwa ta iso gareshi ta ɗane kan cinyar shi ta zauna ta gaba tana facing ɗin shi, tare da mika hannu ta sagale wuyar shi. Wani irin kallon luv suke bin juna dashi kamar zasu hadiye juna, sai wani kashe mai ido take yi tana sakar mai wani irin kayataccen murmushi, hura mata iskan bakin shi yayi a idanunta, runtsewa tayi tayi fari dasu ta sake zuba mai su a fuska, a hankali yace "idon mayu." Kallon juna suka yi suka kwashe da dariya, tuna lokacin da yake kiran ta da haka, cikin dariya tace "gaskiya yaya Aslam ka zazzageni sosai fa,nice mai idon mayu nice mai idon muzuru nice mai idon kwadi du..." Bai bari ta kai karshen maganar ta ba yayi sauri ya daura yatsar shi akan lips dinta tare da cewa "shiiiii, abar tuna baya, duk sone ya janyo hakan, tsananin kauna ne ya janyo hakan, a lokacin da zuciya ta ke tsananin so da kaunarki ni kuma Nike kokarin tursasata da cusa mata tsanarki, pls daga yau bani son kina tada maganar baya kinji my husy" gyada mai kai tayi. Hannu ya mika yana shafa hips dinta da yaga sun baje sosai saboda zaman da tayi a kan cinyar shi yace "husy ban gane ba kwana biyu naga sai kara cika suke yi, su da nan" ya karashe maganar yana daura dayan hannun shi a boobs dinta da dun dazu suke ta tsole mai idanu, kashe mai ido tayi tace "to ai kaima naga ka canja cikin kwana kin nan." Yace "ai ko Rabin canzawar ki banyi ba, anya kuwa banyi ajiya a nan ba kuwa." Ya faɗa yana maida hannun shi dake kan Boob's dinta kan lafaffen cikinta, tace "haba dai tun yanzu." Yace "to me zamu jira, oya tashi muje muyi test mu gani dan ban yarda da wannan kibar da kike mulkawa ba" cike da mamaki tace test "yace kwarai ko test zomuje kiga yadda akeyi" ya faɗa yana mikar da ita tsaye, shima ya mike, ya kama hannunta suka nufi dakin shi, mamaki bai idasa kashe Asmah ba saida taga Aslam ya bude wardrobe dinshi ya zaro p-test guda ɗaya, tsabar mamaki yasa kasa rufe baki tayi, lallai Aslam ba karamin so yake ma haihuwa ba, ba ƙaramin ƴaƴa yake yi ba, har ya siyo p-test daga fara Abu yau sati biyu, to yaushe ma ya siya ya shigo dashi cikin gidan bata da labari. Muryar shine ya katse mata tunani, "oya muje toilet, ki bani fitsarin." Cike da zaƙuwa ta mika mishi hannu ya jata hannunta zuwa toilet ɗin, itama tana son cikin sosai fatan ta ace bai wuce hasashen Aslam ya zama gaskiya ba, murfin shampo dinta dake jere a toilet din ya cire ya miko mata, amsa tayi ta shiga cikin jacuzzi tayi fitsari ta tari kaɗan a cikin ta miko mai, amsa yayi ya ajiye, tare da bare ledar p-test ɗin ya tsoma cikin fitsarin, dagowa yayi yana kallo, Asmah ma matsowa tayi ta tsaya kusa da shi suka zuba ma abin idanu, zuciyoyin su na luguden bugawa. Bayan kamar 2 minute ya nuna musu result ɗin, jiki a sanyaye suka kalli juna, kwabe fuska tayi zatayi kuka ya jayowa jikinshi ya rungumeta yana bubbuga bayanta kaɗan kaɗan, a kunne ya raɗa mata "karki damu my husnah, in-sha Allah zan kara himma muma zamu samu ciki kinji." ta gyada mai kai,daga nan kuma ɗaki suka dawo suka buɗe sabon shafin soyayya. (Hmmmm na lura Aslam da Asmah Kansu kawai suka sani, sun manta da umman little baiwar Allah, nidai kam daga nan Malaysia zanyi na dauko mana rahoto) ~MALAYSIYA~ Tafe take cikin harabar wani babban private hospital da ake matukar ji dashi a kasar ta Malaysia, cike da nutsuwa take tafiyar ta rungume da katon kyakkyawan babynta dan 6 months ɗaya hannun ta kuma rateye da wani babban jakan masu goyo mai kyau na yan gayu, little Aslam ne yau ya tashi da zazzabin hakori shine ta kawo shi asibitin domin suna da kwararun likitan yara, dan bangaren da ake duba yara a cikin asibitin ma dabam yake, ta samu ganin kwarararen baban likitan yara ya duba shi ya bata magunguna, biyawa tayi pharmacy dake cikin asibitin ta siya dukkan magungunan da aka rubuta mashi, sannan ta kamo hanya zuwa inda tayi parking motar ta, bude back sit tayi ta ajiye jakarta dake cike taf saboda magunguna data siya duk ciki ta zuba su, sannan ta dawo gefen mai zaman banza ta daura little boy dinta akan kujeranshi na musamman dake gurin na yara Wanda idan zata yi driving anan take zaunar dashi ta daddaura mishi belt ɗin kujeran, domin Allah yayi ta da rashin jumirin goya yaro, bata ma iya goyo ba ƙarewa, kuma dake abin ba dadata yayi da kasa ba bata maida hankali ta koya ba. Zaga yawa tayi ta buɗe gefen driver zata shiga kenan daga bayanta taji ance "zaynab abdussalam mai naira." Juyowa tayi jin wannan kiran haka, tasan ko wanene wannan ya mata farin sani, suna hada ido ta zaro ido, baki na rawa tace....... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} *Mg's skincare* Manyan mata afito a gyara jiki inkin gyara ke kanki zakiji dadi baki fargaban shiga ko Ina always fatarki tazam tana shining kina walwali ba kwarzane ko daya😍amma kiga wata fuska duk kuraje da tabo😖 ko fuska tass amma kafa baki ko gabobin hannu wuluk🫣 wasu Kuma sunburn yabatamasu fuska sister's sannan ynx lokacin sanyine ko kinagyara fata dole saikin Kara dagewa Sabida dakinyi sake jikinki zai lalace😩Kiga Fata na bushewa tana yakwanewa haba dan Allah mufa Mata dagyara akasanmu☺️macen data amsa sunanta tundaga kallo daya ake ganota🤗duk wacce take bukatan kayan gyaranjiki @mg's skincare sun shahara sun zarce tsara indai awannan bangarenne sbd wnn yanayin ma sunkawomuku ingantattun products Wanda zai Dace daku dakuma yanayin da akeciki baruwanki fatarki zatazam 1 in town😍 domun keda kanki zakidinga sha'awar skin dinki ma balle wani yagani🥰kuma kayansu 100% natural/organic Mai bukata should chat 08062991549,07046881166,07067210195 Call 08064532391 Team glow/clear skin 👩‍👩‍👧‍👦 Page 117 "Dr bala!" Ta faɗa cikin tsananin mamakin ganin shi a gabanta, murmushi yayi sannan ya ƙaraso gabanta, tare da cewa "na'am zaynab" tace " da gaske Kaine a gabana, me kazoyi nan ya mutanen 9ja ina ƙawata beebaloo, nasan tunda na ganka tabbas zan samu koda number ta da na Daɗe ina nema ne" fuskar shi dauke da murmushi yace"duk wadannan tambayoyi haka a Jere zaynab wanne zan fara amsawa." Ita ma murmushin ta mayar mai tare da cewa "kowanne Dr, wlh nayi matukar farin cikin ganin ka, na daɗe ina fatan haɗuwa da mutumin da na sani ɗan Nigeria." Yace nima nayin farin cikin ganin ki "zaynab kodan na nemi tafiyar ki akan abin da na aikata miki nida ƙawarki beebaloo." Kallon shi take yi cikin rashin fahimtar inda maganganun shi suka dosa, ganin yadda take binshi da kallon ban fahimce ka ba yasa yace "nasan baza ki fahimce ni ba zaynab saidai idan ni da kaina na warware mini komai, zanso ace kinada isasshen lokacin da zaki iya aramin koda minti talatin ne muyi magana." Tace "OK babu komai domin nima inason na nemi wani taimako a wajen ka." Waiwaigawa yayi yana Neman musu inda ya dace su zauna, can ya hango kujeru guda biyu a bakin wani umbrella tree, cikin inuwa daga gefen su, nuna mata wajen yayi tare da cewa "idan babu damuwa zamu iya zama a cen." Kallon gurin tayi inuwa ne kuma bugu da kari ba hanya bane babban da mutane zasu dinga wucewa barkatai, "is ok." Kawai tace tare da rufe motar ta, ta zagaya ta buɗe gefen da little boy dinta yake ta dauke shi. Bayan sun zauna, zee ta ce "Dr na tambayeka ina ƙawata baka ce komai ba nayi missing dinta sosai kullum fata neke Ina addu'a Allah ya haɗa ni da wani dan Nigeria wanda na sani,na aikeshi gareta,ban samu ba sai yau da Allah ya haɗani da kai." Mai makon Dr bala yaba zee amsa sai ya shiga binta da wani irin kallon tausayi, a zuciyar shi ya ayyana lallai mutum abin tsoro yanzu dama haka zaynab ke kaunar beebaloo amma taci amanar ta, ganin yayi shiru yana binta da wani irin kallo yasa da dan karfi tace "Dr bala " firgigit yayi kafin ya sakar mata murmushi, yace "sorry zaynab kinga na tafi wani tunani daban ko,ina mamakin yadda mutanen duniya suka dauki cin amanar masoyin gaskiya Abu mai sauki" kallonta yayi ya fesar da zazzafan huci daga bakinshi sannan ya fuskance ta sosai yace"zaynab na haɗa ki da girman Allah, da darajar da Allah yayi wa ma'aiki ki yafe min." Cike da mamaki tace "Dr bala yafiyar me kake nema a gareni ni baka min laifin komai ba." Yace "na miki zaynab, nine fa nayi sanadin zubewar cikin jikinki, Wanda sanadiyar hakan na fuskanci tarin ɗalu bale yanzu haka maganar da nake miki, an sallameni daga aiki, sannan an kulle min asibiti na mai zaman kanshi, bugu da kari mahaifina jin labarin abin da nake aika tawa na zubar ma da mata ciki a asibiti na , ya kamu da ciwon zuciya take ya yanke jikin ya faɗi, tun daga ranar har yanzu baisan inda kanshi yake ba, da yaɗan bude ido sunana kawai yake kira yana cewa na cuce shi, shi ba irin wannan tarbiyar ya bani ba, yanzu haka likitoci sun hanani zuwa kusa dashi saboda samun lafiya shi, duk wannan abin ya faru ne ta dalilin alluran dana miki. Nufasawa yayi kafin ya daura da, cewa, "na zubar ma da mata sama da ɗari ciki a duniya amma akan naki naga aya, ban sani ba amma ina kyautata zaton mijin kine yayi binkice ya gane nine na miki allura, shine ya kai sunana ministry of health, aka shiga binkice a kaina har allura ta tono galma, yanzu haka case lin bawai ya mutu bane kotu zamu shiga nan da wata ɗaya, nan kuma da kika ganni mahaifina ne jikin yaki daɗi shine aka turo mu nan, shiyasa dana ganki naji daɗi domin na nemi yafiyar ki,ko Allah zai tausaya min ya rangwanta min." Tun kan ya gama bata labarin idanunta ya cika da hawayen tausayin shi, girgiza kai tayi cikin tusayawa tace "ash'sha! Gaskiya Abu baiyi daɗi ba, na tausaya maka màtuƙà, kuma ni dai baka min komai ba Dr saboda nina kawo kaina gare ka, Allah kayi wa laifi Dr shi ya kamata ka roƙa ya yafe maka, nima a lokacin jahilci ne yakai ni ga aikata hakan,amma yanzu alhmdllh Allah ya raba ni da wannan mugu ciwo na jahilci duk adalilin abinda ya faru, wannan lamarin daya faru ya zama silar shiryuwa ta,ta farkin Allah madaukakin sarki ya zama sillar tonuwar asirinka a duniya domin ka tuba ga ubangiji kafin ka riskeshi a matabbata, sannan Allah kadai yasan mutane nawa wannan lamarin yayi sanadin fitarsu daga halaka, kamar yadda ya zama silar fitar mu nida kai." Tunda ta fara magana yake bin ta da kallo, lallai wannan zaynab din tasha bambam da wacce ya sani a watanni baya da suka shude, zaynab ɗin da ke gaban shi wayayya ce mai hankali da nutsuwa mai hangen nesa, ba kamar zaynab din daya sani a baya ba shashasha mara wayau, wacce wata ballagazar mace kamar beebaloo ke Jan ragamar rayuwarta. Cigaba tayi da cewa " duk wannan faɗi tashi da aka sha bai sa mun iya kashe abinda bamu muke da ikon kashewa ba." Ta karashe maganar tana mika mishi little Aslam dake hannunta, da wani irin mamaki ya ɗago yana kallon yaron da take mika mishi, tace "ka daina tantama ko shakka wannan ɗan da kake gani shine dai Wanda ni da kai da ƙawata muka so hallakawa Allah bai nufa ba." Da wani irin sauri Dr bala ya amshi Aslam a hannunta ya rungume shi a kirgin shi, ya shiga jerowa ubangiji kirari da yabo. Yana gama wa ya daga yaron sama ya caɓe tare da cewa "hakika kai dan baiwa ne Wanda zuwanshi duniya ke tattare da wani bayyanan nan haske." Ɓangale baki yaro ya fara yi yana dariya kamar yasan abinda Dr bala ke cewa juyowa yayi ya kalli zee yace"ki bani labarin yadda akayi cikin nan ya rayu." Sauke numfashi zee tayi take idanunta suka fara tsiyayar hawaye tuna wa da tayi da abinda ya faru tsakanin ta da Aslam dinta bayan barowar ta Asibiti, saida ta share hawaye sannan a hankalinta shiga labarta wa Dr abinda ya faru tun daga barowarta asibiti, matsanancin ciwon maran da taji jinin da ta zubar dawowar Aslam dukan da ya mata kwanciyar ta a asibiti zuwa kiran mahaifinta da tayi kulle Aslam da yayi da irin dukan daya sha a station, har zuwa fisgarta da mahaifinta yayi daga police station zuwa airport da dawowar ta Malaysia, karbe wayoyinta da yayi zuwa bayyanar cikin ta yunkurin zubar da cikin da iyayenta suka yi, kin amincewar ta har zuwa haihuwar ta, yadda ta koma islamiyya da nasarar da ta samu a komawar da tayi, har zuwa yau da ta haɗu da shi. Sauke numfashi Dr bala yayi yace "hakika kinga rayuwa kema,amma kinsan duk waɗanda suka jefa ki cikin wannan walagigin rayuwar." Girgiza kai tayi alamar A'a yace "mutum biyu ne, na daya sune iyayenki wadanda suka haifeki, na biyu kuma wacce itace ummul kaba'isin din faruwar komai, wacce kika dauki yarda da soyayyar gaskiya kika daura mata ita kuma taci amanar ki, ba kowa bafe face ƙawar ki beebaloo." Zaro ido waje zee tayi tare da cewa "meye haɗin beebaloo da faruwar wadannan abubuwa." Murmushin takaici Dr bala yayi, kafin kuma ya shiga zaiyane ma zee komai da manufar beebaloo akan zigata da tayi ta zubar da ciki, da kuma kiran Aslam da tayi ta gaya mishi. Tun kan ya karkare labarin hankalin zee yayi matuƙar tashi, take hawaye suka fara ambaliya a fuskarta, jikin ta ya kara yin sanyi, ta kara yadda Allah abin tsoro ne, duniya abin tsoro ne mutanen cikin tama abin tsoro ne, ta karajin lamarin mutane ya kara fice mata a kai, lallai beebaloo taci amanar yarda taci amanar aminta taci amanar soyayya, da zuciya daya ta riƙe ta, ta dauki ragamar komai na rayuwar ta ta bata duka wani sirri nata ta fallasa mata, bayan Aslam daya kasance miji a gareta a Nigeria beebaloo ce mutum ta biyu da zee ke tsananin kewa da begen gani, lallai ta yarda mutum mugun ice. Idanunta da suka rine sukayi jajur ta sauke a kan Dr zuciyar ta a dake ta jeho mai tambayar, "dan Allah Dr bala ka fada min gaskiyar abinda ka sani, shin beebaloo tayi nasarar auran min miji bayan barowata 9ja kokuma Allah bai bata nasara ba." Girgiza kai yayi yace "banajin ta samu narasa akan mijin ki domin kuwa naji daga majiya mai karfi cewa...... ~BEEBALOO~ Bayan ta sauke zee a gida ranar da ta kaita asibitin Dr bala aka mata alluran zubar da ciki, da wani irin farin ciki da anushuwa tabar gidan dan ta tabbatar boom ɗin da ta dana zaiyi gagarumar tashi, duk abinda ya faru tsananin zee da Aslam tana da labari komai dan renting ɗin waɗanda zasu dinga bibiyar mata komai tayi na musamman, tun daga kan dukan da Aslam yama zee har zuwa kan barin zee naija tana da labarin komai. Ranar da zee tabar naije ranar ta fara bibiyar Aslam, ta takura rayuwar shi da kiraye kiraye a waya da message, tun yana dauka har ya gane number ta ya daina dauka, daya gaji ya daga kiran ya mata wankin babban bargo, sannan yayi blocked dinta, hankalinta ba karamin tashi yayi ba hakika tana kaunar Aslam burinta bai wuce a ce yau ta mallake shi a matsayin miji ba, domin ta cika burin ta na auren kyakkyawan namiji mai kuɗi dan babban gida, Wanda kowa yasan wannan dalilin ya hanata zama gidajen aurarrakin ta na baya. Batayi kasa a gwuiwa ba ta sake siyan wani layin taci gaba da bibiyar Aslam, tana ci gaba da yada manufar ta bata fasa ba, kwatsam ta zo ta daina samun shi kwata kwata a waya duk wani hanyar sadar wa da take bibiyar shi ta yanke, a lokaci guda, (idan Baku manta ba lokacin da ake tsaka da tirka tirkan nan kenan, lokacin da ya kwanta rashin lafiya kafin bikin shi da Asmah). Hankalin beebaloo yayi matukar tashi fa kasa samun Aslam da tayi kwana biyu, ita fa ta lashi takobin ko ta halin ƙaƙa saita mallaki Aslam, domin wahala da faɗi tashin ta bazai tashi a banza ba, ta shiga damuwa a cikin kwanakin nan taje gidan shi yafi sau a kirga tana samun gidan garƙame da kwado, har ciwo tayi a cikin yan kwanakin nan. Tana cikin wannan halin Allah ya haɗata da wata tsohuwar kawar ta tun na yarinta, wata rana taje asibiti ganin likita, nan kawar ta mai suna hajo ta tambayeta meke damunta, bata boyema hajo komai ba ta gaya, murmushi hajo tayi tace"kawata kwantar da hankalinki in-sha Allah kakar ki ta yanke saƙa nizan taimaka miki ki mallaki koda uban Aslam ne bama Aslam ba, ki tanadi kudi masu dan kauri ki shirya jibi zan raka ki gurin mallan kamsusi, aikin shi kamar yankan wuƴa yake."cikin tsananin farin ciki beebaloo ta shiga jerowa hajo godiya gida ta koma ta shiga buga buga ta saida wance ta saida wannan ta samu ta haɗa kudin ta masu kauri, bayan kwana biyu suka dauki hanyar gurin malam kamsusi ko sallama da gida beebaloo batayi ba. Tafiya sukayi sosai a mota kafin su sauka a bakin hanya, suka tari me kabu kabu Wanda zai shigar dasu cikin kauyen, tun a gurin cinikin kudin me kabu kabu beebaloo ta sha jinin jikinta, dan cewa sukayi su bada dubu uku uku, ga mamakin ta gani tayi hajo tace muje "ba tare da wani damuwa ba" ita dai bata tanka ba amma a zuciyar ta tace "dubu uku sai kace mutum zaije kano daga minna" haka ta dai ta hau mashin suka dauki hanya, tun ana tafiya ta marmari har aka gaji, har tafiyar ta koma ta fitar hankali, tuni hantar cikin beebaloo ya fara kaɗawa dan ta sadakar hajo ta siyar da ita, take ta fara jero kalmar shahada tun tanayi a zuciya har ta fara yi a baiya ne, babban tashi hankalinta yadda hanyar kwata kwata bashi da kyau, sai shiga ramuka suke yi suna fita, wani tudun kuwa idan mashin ya hau daga ita har driven mashin din sai sunyi sama duwawunsu ya rabu dakan sit din mashin din sannan su dawo su zauna daɓar, tuni beebaloo ta fara kuka hawaye uku uku, basu suna sauka akan kabu kabu ba saida sukayi tafiyar awa biyar kwarara. A wani dan tsukukun kauye suka sauka, a tunanin beebaloo sun ido ne, amma sai taji hajo na cewa "a nan zamu kwana beebaloo gobe da asuba ba sai mu daura da kafa mu karasa aslin kauyen da mallam kamsusi yake, da kafa zamu karasa domin daga nan ne mashin ke iya tsaya wa a gaba babu hanyar mashin." A wargaje beebaloo ta zaro idanunta da suka kankance sukayi jajur tsabar azaba tace "hajo kina nufin dama ba nan bane asalin inda muka zo." Hajo tace "eh ba nan bane karki damu kawata munyi rabi, ni na saba zuwa ,kema dan yaune zuwanki na farko yasa kike ganin wahalar shi. (Hmmm akace sa kai yafi bauta kuji hajo wai ta saba zuwa) A nan dan tsukukun kauyen suka kwana, inda suka dunga bin gida gida daker suka samu wacce ta amshe su ta basu dakin awaki su kwana a ciki, ba tare da damuwa ba hajo ta shiga ta nemi guru ta zauna, babu alamar damuwa a tare da ita da alama dai ta shiryama faruwan hakan. A darare bebalo ta samu guri itama ta rakube, a haka gari ya waye musu, hajo tadan gyangyada yayin da beebaloo idanunta Kamas, yadda taga dare haka taga rana, duk wannan azabar wahalan da suke sha,idan ta tuna at the end zata mallaki aslan ɗinta sai ta saki murmushin farin ciki. Da asuban fari suka dauki hanya suka fara shatatawa da ƙafa babu batun sauke farali bare salati, tun suna tafiya suna dan taɓa fira har kowa yayi gum sai Jan kafa sukeyi shakataf shakataf, jefi jefi sunan hadu da mutane a hanya wasu na shiga kauyen wasu na fitowa, a haka suka hadu da wata a gwai suka sayi fura da nono babu ko suga suka shiga kwankwaɗa, basu suka shiga asalin kauyen da mallam kamsusi yake ba saida rana ta take, sun tarar da layi sosai, amma basu damu ba, hankalin beebaloo ya kwanta ganin ta gata ga bukkar mallam kamsusi, inda take da tabbacin zai share mata kukan ta gani takeyi kamar ta auri Aslam ta gama....... Shin mai ya faru ne burin beebaloo na auren Aslam bai cika ba har yau, duk da kuwa zuwa wajen mallam kamsusi da tayi, ku biyo diyar nalado danjin yadda z aka kaya. Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wanna book din ga suka wacce ta rasab mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 118 Saidai sukayi zaman fiyye da awa uku sannan layi yazo Kansu, zuciyar beebaloo wasai yau tazo inda take da tabbacin za'a share mata kukan ta, tare suka shiga cikin bukkar mallam ɗin ita da hajo, guri ya nuna musu suka zauna kan shimfiɗar buzu, so ɗaya beebaloo ta iya kallon fuskar mallam kamsusi da sauri ta dauke kai gabanta na faɗuwa, duk inda muni yake Allah ya tattarawa mutumin nan, baƙi ƙirin dashi, gashi dan cukuli kamar a kife da kwando sai katon kai, yasha wani uban rawani ƙato a kanshi, gaban shi kuma kasa ne mai kyau fari tas , hannun shi rike da wani dogon carbi irin mai guda dubu ɗinan yana ja sai wani musmus yake yi da baki. Tun shigowar su ya kafe mici micin idanunshi akan beebaloo, yana kare mata kallo daga Sama har kasa, yana sauraren radar da aljani dan misra ke mai a kunne game da ita, lallai ta tafi da nutsuwa shi, gani ɗaya yaji ranshi ya biya kuma bawai na lokaci daya ba inso samu ne yana bukatar ya aureta, ido ya zura mata kamar mai bukatar hango wani abu a jikinta yayin da ita kuma ta kasa kara dagowa ta kalle shi. Hajo ne ta fara cewa cikin dukar da kai da tsantsar ladabi "barka da war haka ya babban malami, malamin malamai na duniya baki daya, gani na sake dawowa gareku da bukatata,fatan na same ku lafiya" sai lokacin ya dauke idanunshi akan beebalo ya dawo da shi kan hajo, fuska a murtike babu alamar fara'a yace "mun amsa gaisuwa hajo, fatan kin isa gida lafiya" tace "lafiya lau mallam aiki yayi kyau tun kafin na ƙarasa gida ma komai daidaita yanzu haka ko kara na ajiye baya iya tsallakewa." Sai lokacin mallam kamsusi ya saki wani shegen murmushi, cikin sa'a saidai lokacin beebaloo ta ɗago kai da niyar ta saci kallon shi a karo biyu, idanunsu ya sarke dana juna, ba shiri ta mayar da kai kasa tana karanto duk addu'an daya zo bakinta, ita wallahi tsoro yake bata, gaba daya fuskar shi kamar ta buri hancin nan a nane. Lokaci daya ya maida fuskar shi ya murtike sannan ya fuskanci hajo yace"kwarai kuwa muna da labarin komai domin tun kina nan gabanmu zaune muka aika dan auta yaje ya cika miki aiki,yanzu me ke tafe dake." Hajo tace "Allah yaja zamanin babban malami wannan kawata ce itace na rako gareka da bukatar ta." Maida kallon shi yayi kan beebaloo, yana ci gaba da binta da wani irin mayen kallon har wani lashe lips yakeyi kamar wani tsohon maye. Saida ya kalleta son ranshi sannan yace"menene bukatar ki." Firgita tayi ta kara kasa da kai jikinta na rawa jin yana mata magana, shiru tayi ta kasa magana, ganin haka yasa hajo ta mika hannu ta tsunguleta a gefen ciki, dagowa tayi ta kalli hajo suna hada ido ta mata alamar yi magana mana, baki na rawa tace"ma malam, umm dama dama, wani ne Wanda nake son ya aure ni, nake son shi, shi kuma baya sona kwata kwata baima San kalar fuskata ba, shine nake son dan Allah a taimaka min ya soni ya aure, dan Allah mallam." Tunda ta fara magana mallam kamsusi ke gyada kai,shi kadai yasan me yake sakawa a ranshi, yace "to zamu taimaka miki mu miki abinda ya dace, kuma bama bukatar ko sisin ki, zamu muki aiki da zaici kamar yankan wuka, amshi nan" ya karashe maganar yana mika mata wani Abu nanade cikin ganye, hannu na rawa ta karba tana godiya ammafa idanunta na kallo gefe don ta kasa haɗa ido dashi, yace" kije ki daka wannan ciyawar ki shanya ya bushe ki raba shi gida biyar ki jiƙa kashi ɗaya kisha, kashi ɗaya ki zuba a ruwan wanka, kashi ɗaya kiyi hayaƙi dashi kashi ɗaya ki zuba a baki ki tattauna kashi daya kuma ki kwaba da fitsarin ki ki shafe a jikin ki da daddare idan zaki kwantar, to insha Allah in dai kikayi yadda nace zaki mallake shi duk inda kike zai biyo ki ya aureki, zai soki sonda bai taba yiwa wani mahaluci a duniya ba, zaki juya shi sai yadda kikayi da shi da dukiyar shi." godiya suka shiga jero mai ita da hajo kamar bakin su zai tsinke. Dakatar dasu yayi mici micin idanunshi nakan beebaloo sai murmushi yake yi, yana lasar lips, lambar wayar shi ya rubuta ya mika beebaloo dan yasan tabbas ta aikata abinda ya umarceta daidai dole zata bukaci lambar shi. Yadda suka shatata da kafa sukaje haka suka kara shatatowa suka fito saidai wannan karan ko kadan beebaloo bata ga wahalar hakan ba tunda ta samu biyan bukata, dan gani take kamar ta auri Aslam ta gama, banda yadda zata sha soyayya da Aslam da yadda zata zuba mulki a gidan shi babu abinda take tunani,sai alkawarurruka take ma hajo kala kala, harda cewa ita ce zata zama mai bata shawara na hannun daman ta, a wannan tsukukun kauyen suka kara kwana washe gari suka kara hawa kabu kabu ya fitar titi suka samu mota suka dawo gida. Koda ta dawo bata bi takan faɗan da iyayenta ke mata ba suna tambayar ta ina ta je ta kwana har kwana biyu, tace musu tafiya tayi kuma bata ga daman ta gaya musu bane,taja tsaki tare da shigewa dakinta ta banko kofa yana gungumi da kananun zage zage ƙasa ƙasa. Kuka mahaifiyar ta ta fashe da shi, tana cewa "ni kike zagi beebaloo insha Allah saikin haifi wacce zata miki dukan tsiya kije kici gaba duniya ce ai faɗi gareta." Mahaifinta ne ya shiga rarrashin mahaifiyar ta, yana kwantar mata da hankali da cewa"yi hakuri marka baryi mata baki, aiko baki buɗi bakin ki kince komai ba, wannan hawaye da tasaka kika fitar hakkin su ya ishe ta." Cikin kuka mahaifiyar ta tace"mallam barni nayi mata baki, wannan wannan baza taga annabi ba, taƙi zaman aure tasa ana zagin mu a gari, sannan mu kuma a gida bata kyale mu ba, cin mutuncin yau dabam na gobe dabam, aiko bamuyi tsirar komai ba baci albarkacin haihuwar ta da mukayi, wasu ma banza da bamu Haifa ba sun girmama mu balle ita." Girgiza kai mallam yayi cikin tsananin takaici, yace "wallahi babu abinda yafi ban takaici game da beebaloo irin kin zaman aure da tayi abin yana taɓa min zuciya bani fatan na mutu na barta a haka tana gantali." Tana jinsu daga ɗaki sai tsaki takeja, tace " yen yen yen yen, mugaye kawai yan bakin ciki, zanyi aure ai zan auri zabin raina cikar burina, kyakkyawa mai kuɗi dan babban gida, wallahi inna yi kudi bazan taimaka muku ba yadda na same ku a tsiya ce haka zan barku ku mutu a tsiya ce." Ita kadai take ta sababin ta basu ma San tanayi ba. A ranar ko hutawa batayi ba ta aikata duk abinda mallam kamsusi ya umarce ta dayi, cike da annashuwa take aiwatar da komai, duk yadda yace mata haka tayi ba tare da ta yi mistake ba, da tazo kwanciya tayi fitsayi ta kwaba kashi na, karshen ta shafe jikin ta da shi, takwanta da yaki nin ta auri Aslam ta gama. Washe gari beebaloo ta farka da wani saban lamari, tun da ta farka taji a rai da zuciyar ta babu Wanda take son gani sai mallam kamsusi, zuciyar ta babu Wanda take so da kyauna sai mallam kamsusi, da ta rufe ido mummunan fuskar shi ya mata gizo, zuciyar ta har wani tafasa takeyi saboda tsananin kaunar shi, ji takeyi idan bata sanya shi a ido ba zuwa dare zaucewa zatayi tuni ta manta da wani Aslam, mallam kamsusi kawai take ji da gani, hannu na rawa ta jawo Jakarta ta zaro number shi daya bata, ba shiri ta antaya mai kira, yana daga wa, ta sauke wani wawan ajiyar zuciya kamin baki na rawa ta shiga gaishe shi, tare da cewa "mallam beebaloo ce kawar hajo." Daga cen bangaren yace "nagane ya akayi beebaloo." Take ta fashe da kuka kafin kuma ta tsinci bakin ta da cewa "mallam dan girman Allah ka taimaka ka aureni wlh sanka nakeyi, bazan iya rayuwa babu kai ba, na fasa auren Aslam ɗin yanzu kai nakeso na maji na tsane shi kwata kwata a rayuwar dan Allah ka taimakeni ka taimakeni ka aure mallam." Wani shedanin murmushi mallam kamsusi ya sake tare da cewa "karki damu beebaloo zan taimakeke na aurenki kamar yadda kina bukata, zaki zauna dani inada mata biyu, kuma a wannan kauye da kikaje anan nake rayuwa ta kin amince zaki zauna acen." Baki na rawa tace "wlh mallam na amince ko ta biyar ce ni na yarda, kauye kuwa ko gaba da nan ne zan je." Yace "to shi kenan ki sanar da mahaifan ki zanzo jibi." Kafin jibin kullum sai ta kirashi fiyye da so goma a rana, ta zama wata zautacciya soyayyar mallam kamsusi kawai ke nukurkusar zuciyar ta,gaba daya bata cikin haiyacin ta, ta sanar da iyayen ta za'a zo Neman aurenta jibi, mahaifinta dan murna kamar ya zuba ruwa kasa yasha, ko ba komai zai rabu da mugun iri. Jibin kuwa mallam kamsusi ya dira a cikin garin minna shi da mukarraban sa su uku, ba ɓata lokaci ya kira beebaloo, da kanta tazo ta tare su, jikina rawa ta masu jagora har cikin zauren gidan su saida ta gabatar musu da lafiayyen girkin da ta musu suka cinye Tass suka kora lemon kwalba sannan ta musu iso gurin mahaifinta, wanda shida kanin shi da abokin shi ne suka tare su. Mahaifinta yayi mamakin ganin mal kamsusi amatsayin Wanda beebaloo ta tsayar zata aura, kasancewar ya San burin beebaloo nasan auren mai kuɗi kuma kyakkyawan na miji, amma wannan ai ko cikin munanan sarkin su ne, yadda take ta rawan jikin ya dauka wani shahararraen dan masu dashin da take burin aura ne ta samu. Cikin abinda baifi awa daya ba suka gama tsayar da duk abinda zasu tsayar ciki harda daura auren beebaloo da mallam kamsusi, a ranar kuwa ya bukaci tafiya da ita,ba Wanda ya hana shi matar shi, suma iyayen nata neman kai suke da ita, itama kuwa burin ta kenan ta ganta gidan shi matsayin matar sa shine kwanciyar hankalin ta. Mutum biyu ne kawai suka mata rakiya daga kanwar mamarta uwa daya uba daya sai, kanwar ta mai bi mata da take aure nan kusa da su da ƴaƴan ta biyar. Tun a hanya yan rakiya suka fara shan jinin jikin su, itako beebaloo ko a jikinta, basu shiga tashin hankali ba saida suka ga yadda ake ta zurarawa da su cikin gungurmin daji a mashin, tafiya yaki karewa, hankalin su bai idasa tashi ba saida akazo gurin tafiya da kafa, sunayi suna hutawa ,kanwar mamarsu kuwa sai zagin beebaloo takeyi take, tana cewa da tasani da bata zoba, a galabaice suka isa. Gida ne fankacece mai dauke da dakuna hudu ƙananan, daya uwar gidan daya na mai bi mata daya na miji sai daya na yara wanda nan aka gyara wa beebaloo,abinda yaba yan rakiyar beebaloo matukar mamaki, yadda suka ga da murna da farin ciki sauran matan mallam kamsusi suka amshe su, tuni suka gabatar musu da tuwan dawa da miyar gari harda ruwan randa mai sanyi, gaba dayan su ba wacce ta iya hadiye lomar farko na tuwon, saboda rashin dadin sa mayar salam sai uban yaji, karshe da yunwa ta ciwo su dole dama tuwan sukayi suka sha shi kamar koko, Allah Allah suke gari ya waye su baro kauyen. Da safe uwar gidan mallam kamsusi ta kawo musu kunun garin dawa da dumame, cikin fara'a ta gaishe su babu alamar kishi ko kaɗan a fuskarta, kasa hakuri kanwar beebaloo tayi tace"baiwar Allah naji ance mana kece uwar gidan shi, kuma banga alama ba nace koba ke bace." Cikin washe baki tace "wlh nice uwar gidan shi." Da mamaki ta kara ce mata"shine babu ko alamar kishi a fuskar ki." Kallonta matar tayi da mamaki tace"kishi fa kikace baiwar Allah,kishin wa?kishin mallam wai, aini idan yau mallam zai karo wata matar ya cike ta hudu sai nafi kowa farin ciki, ko ba komai raba kwana zamuyi, aini nafi kowa farin cikin da auren nan na mallam badan kar nayi karya ba da sai nace har shi nafishi farin ciki da auren, kardai na cika ku da surutu bari na barku ku kimtsa." Ta faɗa tana mikewa ta fice, kallon juna yan rakiyar beebaloo sukeyi, cike da mamakin wanga lamari, to duk yadda akayi a kwai lauje cikin nadi......... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} 109 ~MALAYSIA~ Bayan wata uku Dad ɗin zee na hango zaune a cikin wani ƙaton falo mai dauke da kujeru sama da guda hamsin, a cikin falon akwai wani ɗaki mai wawakeken kofar glass, zaune yake ya zuba tagumi da hannu bibbiyu yayinda gabanshi kaɗan mum ne sai safa da marwa takeyi ta kasa zaune ta kasa tsaye, basu kaɗai bane a falon a kwai wasu mutanen amma kowa da abinda ya dameshi babu mai shiga harkar kowa, Daga kaina nayi na kallin sunan da ke rubuce a saman dakin ~labour room~ abunda idanuna suka hango min kenan. Suna a wannan yanayin bini bini dad kan amsa call a waya yayinda mum kam gaba daya bata cikin hayyacinta, sai yi take tana aza hannu a kai tana saukewa, can bayan kamar 30 minutes sukaga an budo kofar glass din an fito, wani mutumi ne fari sol kamar zabiya sanye da kayan likitoci ya fito daga dakin, da sauri Dad ya zabura ya mike,shida mum har suna rige rigen isa gareshi, a ruɗe. Dad ya fara cewa "Dr ina daughter ta haihun,ko har yanzu?" Mum ma cewa take "pls Dr ina daughter na, wani hali take ciki, Dr idan abin bazai yuwu ba kawai ayi mata theater" Dr kam rasa ma wani amsa zai basu yayi, ganin yadda suka tare shi, gashi shi kuma sauri yakeyi yasa yace musu"excuse me pls" tare da dojewa ya wuce su da sauri, hannu mum ta daura akai tana hawaye tare da ambaton "innalillahi wainnailaihi rajiun" Dad kam bin bayan Dr yayi da sauri saidai kafin ya cin masa ya shige wani office, Wanda babu mai ikon shiga sai likitocin asibitin, dawowa yayi jiki a sanyaye ya nemi gurin shi Nada ya kuma zama. Tsakanin shida mum an rasa mai jarumtar rarrashin wani, kimanin awa goma kenan da suka kawota asibitin, tun cikin dare naƙuda ya tasar mata gadan gadan, ba shiri kuwa aka shige da ita labour room, saidai har zuwa yanzu karfe goman safe bata haihu ba kuma ba Wanda yace musu wani Abu game da ita, saidai kawai gani sukeyi likitoci da nurses nata zirga zirga a ɗakin. Hankulansu gaba ɗaya yakai matukar ƙololuwar tashi, tsoron su gaba ɗaya kar su rasa ta, itace farin ciki su, ita kaɗai suka mallaka suna matukar tsoran rasata. A wannan yanayin maimakon su tayata da addu'a, amma ina abinka da jahilai, Dad sai zufa yake hadawa idanunshi sun rine jajur,in yayi ya lailayo ashar ya ɗura wa Aslam, yayinda mum ta kasa tsaye ta kasa zaune sai fareti takeyi tana risgan kuka. Bayan mintunan da basu gaza goma ba wata nurses ta fito daga ɗakin, nan itama suka mata caa aka, kallon mutanen falon tayi fuskarta dauke da murmushi tace,"su wanene iyayen zainab Abdussalam" bakin na rawa Dad yace "yes mune mune" mum ma tace "eh nice mahaifiyar ta, wani hali take ciki" nurse tace "alhmdllh ta sauka lafiya yanzu an samu baby boy," tsabar farin ciki mum batasan sanda ta rungume nurse ba, Dad kuma kallonta yayi yace "nurse wani hali take ciki" cikin murmushi tace," tana lafiya yanzu haka ana gyarasu ita da babyn nan da yan mintoci za'a fito da ita zuwa ɗakin Hutu, sai ku samu ku ganta" dad" ajiyar zuciya Dad ya sauke tare da shiga jero ma nurse ɗin godiya, nan kuma ya ɗauki waya ya shiga kiraye kiraye. Nurse kam da'ker ta samu ta kwace kanta a hannun mum ta koma ɗakin da ta fito. Ba'afi 20 ba kuwa aka gunguro zee daga labour room zuwa ɗakin Hutu, sai lokacin su mum suka samu ganinta, tayi fiyaut da ita, ta kara haske, basu Daɗe a ɗakin ba akace su fita su barta ta samu barci sosai an mata alluran barcine, kasancewar ba karamin wuya tasha ba, tayi nakuda mai tsayi kamin ta samu ta haihu da taimakon kwararrun likitocin asibitin. Babyn dake nannade cikin farin shawel an mishi wanka an shiryashi cikin tsadaddun kayan sanyi aka mikoma mum, hannu na rawa ta karɓa, tsurawa yaron idanu tayi tana kallo, Dad dake tsaye ganin haka yasa shima ya matso don yaga mai take kallo haka, abinda ya faru da mum ne shima ya faru dashi, kallon yaron sukeyi babu ko keftawa. Bacci yake yi idanunshi a kulle fari sol ƙato da shi mai kama da Aslam sak, babu abinda ya banbantasu,kwata kwata bai dakko komai na zee ba, duk da mum da Dad basa kaunar Aslam hakan bai hana ɗanshi samun kyakkyawan matsuguni a zuciyoyin su ba, farat daya yaron ya shiga ransu, a kallo na farko. Gaba ɗaya sun shagala da kallon yaron saida sukaji, muryar nurse tana musu magana sannan suka dawo hayyacinsu,saƙon Dr ta sanar musu na cewa da yayi su same shi a office, Dad ne yabi bayan nurse din zuwa office ɗuin Dr yayinda mum ta rungume yaron tsam a kirginta tanajin wani irin son shi da kaunar shi na huda kofofin zuciyarta. Saida zee ta kwashe awa shidda kwarara tana barci kafin ta farka, wuraren la'asar, zuwa lokacin kam asibiti ya cika makil da yan'uwa da abokan arziki yan gayu masu abin hannu,yawancin su ma turawa ne wadan da su mum ke hulɗa dasu, kowa ya dauki yaron nan kallon daya zakaji ya shiga ranka, da alama dai baiwarsa ce hakan. Zee ta farka da sauƙi sosai don bayan Dr ya duba ta, ya tabbatar musu nan da gobe ma za'a iya sallamarta taje gida abinta, bayan mum ta bata shayi mai zafi tasha ta kuma sha magunguna, sannan aka bada daman mutane su shiga su dubata, kowa barka yake mata, bata iya amsawa sai smiling kawai take musu, lokacin da aka bata babyn kuwa tsura mishi idanu tayi tana binshi da wani irin kallo, babu abinda take gani a fuska da jikin yaron sai Aslam dinta, take wani irin kewa da kaunar mijinta ya turniketa, rungume yaron tayi sosai a jikinta tana jin wani irin kaunar shi na huda zuciyar ta, bata San sanda ruwan hawaye ya wanke mata fuska ba, ta shiga risgan kuka harda sheshsheka, ganin haka yasa mum ta miƙa mata hannu alamar ta bata yaron girgiza mata kai tayi alamar A'a dole mum tayi hakuri ta bar mata abinta. Zuwa dare babyn ya fara kuka, Dr yace ya kamata a bashi abinci yunwa yakeji, Dad yace Dr ya rubuta musu madaran da za'a dinga bashi yaje ya siyo, da mamakin su ji sukayi zee tace , A'a kar a siyo madaran ita zata shayar da ɗanta, Dr yace well dama haka ake bukata, nan wata nurse ta gyara mata shi sosai ta koya mata yadda zata rikeshi a yayinda da zata shayar da shi, nonon aka sa mai a baki ba shiri kuwa yaro ya kama yana tsotsa, duk da matsanancin zafin da takeji hakan baisa ta fasa shayar dashi ba, nurse din data fahimci tanajin zafi ta shiga kwantar mata da hankali da cewa karta damu zai daina, idan ya kwana biyu yana sha, shikenan baza ta kara jin zafi ba kuma. A asibitin suka kwana zuwa washe gari ta ƙara samun sauki sosai don haka Dr ya rubuta musu sallama suka dawo gida, kulawa sosai zee ke samu daga gurin iyayenta ita da little Aslam dinta, wata babban nurse mai zaman kanta, wayayya mai wadataccen ilmi Dad ya daukar musu ita ke kula da komai nasu ita da babyn bangaren wanka tsaftar su da abincinsu, kai komai ma daya shafe su. Zee taji dadin yadda iyayenta suka karbi yaron da yadda suke nuna mai kauna da kulawa, bata taɓa zaton haka ba, ganin yadda suka dauki karan tsana suka dorawa uban ɗan. Kafin sati ya zagayo tayi bulbul ita da babynta gwanin sha'awa, jego takeyi na yayan gata, baza ayi taron suna ba, raɗin suna kawai za'ayi dad ne ya siya duk wani abinda ake bukata na radin suna kamar rago da sauransu,tambayarta sukayi sunan da take so a saka ma ɗanta babu kunya ko kara tace Muhammad Aslam, haka ko akayi, duk da Dad yaso ace sunanshi ta zabar wa yaron. (kuji min Dad da ƙoƙari wai da sunanshi ta zaba😒 babu kunya ba tsoron allah cikin da yayi niayyar hallakawa) Hankali kwance take jegonta bata da matsalar komai babu abida ke damunta sai kewar mijinta, bayan haihuwartan nan , abin ma saiya daɗa nunkuwà, kullum dashi take kwana take tashi a zuciyarta ji take kamar tayi tsunstuwa ta ganta a agabanshi, ta mika mishi ɗanshi, cikin farin ciki,ta kusa kai matakin da baza ta iya jurewa ba, jira takeyi yaronta yayi kwari, ta lashi takobin zata koma gidan mijinta koda son ransu ko babu, koda tsiya koda tsiya tsiya. ~9ja~ Yau kimanin wata biyar kanen da auren yan matan mummy,kuma har zuwa wannan lokacin cikinsu babu wacce ta taba zuwa gida da sunan ganin gida, kowacce tana gidanta hankali kwance, duk da kuwa cikinsu ba wacce batayi nacin son zuwa gida ba amma mazajen suka hana wannan kuwa umarnin alhaji baba ne. Soyayya kamal da khadija ba'a magana, tattalin da kulawa suke ba juna na musamman, idan kaga yadda suke gudanàr da rayuwarsu zaka dauka sunyi shekara goma suna soyayya kafin suyi aure, a halin yanzu Khadijah Nada cikin ta dan wata huɗu. Haka ma Amir da Amira sukam bama a magana, kalar nasu salon soyayya ta dabance, basa jin kunyar uban kowa a gaban kowa nuna ma juna soyayya sukeyi, ƙiri ƙiri mutane suka guji zuwa gidansu, saboda idan kaje indai kana da kunya, ta baza ka iya awa ɗaya a gidan ba,suma dai a kwai cikin ɗan luv, saidai fatan Allah ya raba lafiya. Su batool ma yanzu komai nomal,babu abinda suke sai shan soyayya da cokali mai yatsu, bangaren yadda sukeji da cikin su kuwa ba'a cewa komai,tunkan a haife shi, shikaran kanshi cikin yasan shi dan gata ne, abinka da masu abin duk sati ake scanning, ta bangaren maah ma ba'a barta a baya ba, duk abinda ta gani indai na jariri ne siya takeyi ta ajiye, abin kwalama kuwa na masu cikin kullum cikin yi takeyi tana aikama batool dashi, bama ci takeyi ba wani bin saidai Dr yaci idan Wanda zai iya cine, ita dai barta da cabbage dinta, yanzu kam an samu ci gaba ta daina cinshi gaya, saidai ta kwada da kulikuli taci, rigima kam yayi sauƙi a gurin batool saidai kunsan ance mai hali baya fasa halinsa, duk da haka duk randa ya tabota haka zata kwana tana masifa, musamman yanzu da wata Dr a gurin aikinsu ta nace tana sonsa, tunda batool ta samu labari ya shiga uku ko minti talatin ya kara akan lokacin da yake dawowa haka zai sameta ta cika tayi fam, komai zai ce mata baza ta yarda ba kawai gurin Dr basira ya tsaya, kishin sa take sosai da sosai ji take da tana da hali da nikab zata saka shi ya dinga sakawa, saukin shi ma yanzu yana da loggonta data fara zai lalubeta ya fara sakar mata zafafan romance daga nan zancen zai mutun sai kuma na gobe. A bangaren zahra kam, yanzu babu abida zamu ce sai alhmdllh, tsakaninta da miji babu komai sai tsantsar soyayya da kaunar juna, da gasken fa baby take a gurin Barr Adam ji yake da ita kamar Yar jinjira, musamman yanzu data samu ciki, kula yake bata na musamman kamar ya hadiyeta, tsakanin da maryama yanzu kuwa babu komai sai girmama juna da mutunta juna, dama zahra kwata kwata bata da matsala, matsalar daga maryama ne, kuma a halin yanzu gaba daya tayi laushi, bayan dawowarta Barr a gaba ya sakata ya mata nasiha tare da sanar da ita wlh ta gode ma Allah daya haɗa ta da kishiya irin Zahra bata samu mai irin halinta, nan ya sanar da ita cewa zahra ce ta tirsasa shi ya dawo da ita badan haka ba da har yanzu tana cen, take taji wani nadama ya shige ta lallai ta gode ma Allah dabai haɗa ta da mai irin mugun halinta ba don ta Tabbatar inda itace a matsayin zahra,da wlh zahra tabar gidan kenan har a bada asaidai a bita da takardan ta, tayi nadama, ta tuba taubatan nasuha, washe gari kuwa har part ɗin zahra taje ta same ta nemi gafarar abinda ta mata, Allah sarki zahra dama bata riketa a raiba, nan dai tace ta yafe mata, tashi tayi ta rungume ta tana mata godiya, a haka Barr ya samesu, ba karamin dadi yaji a ranshi ba, take ya haɗa su ya nusu nasiha, tare da nuna musu irin tsantsar farin cikin da yake ciki a ranar saboda hada Kansu da sukayi, tun daga ranar kuwa suke zaune lafiya abin su, yara yanzu sun zama yan gata masu uwaye biyu, maryama suna kiranta da mummy zahra kuma suna kiranta da mum, dakinsu nanan a part din zahra data ware musu, lafiyayye Dan yama fi dakinsu na part din maryama haɗuwa, in sunga dama su kwana a gurin mummy insun ga dama su kwana gurin mum, maryama ce ta fara gane zahra nada ciki, aiko dai tayi farin ciki har zuciyar ta, take ta shiga tsokanarta tana kiranta da maman yan biyu, tun zahra na daukar abin da wasa har dai lamarin ya tabbata, saidai muyi fatan Allah ya raba lafiya. A bangaren su Asmah kam yanzu sun wuje romeo da Juliet, soyayya suke zubawa kamar zasu cinye juna, da'ker da sidin goshi Asmah ta samu Aslam ya koma wajen aiki, shima da yarjejeniyar, yana aiki suna video call, haka dai tace mishi ta yarda, ta samu ta lallabashi ya tafi ranar farko daya fara zuwa, yana isa ko office bai shiga ba ya kirata ƙin ɗagawa tayi dan burinta a halin yanzu bai wuce ya maida hankali kan aikinshi ba, cikin abinda baifi awa daya ba ya mata missed call yafi hamshi ta share, aiko dai ko Rabin a waya bai kara ba saijin horn din motar shi tayi ya dawo, washe gari kuwa kin tafiya aikin yayi, ganin dai da gaske yakeyi, yasa itama ta ɓata rai ta daina kula shi ta fita sabgarshi, ta daina kwana tare dashi, kwana biyu suka kwashe a haka gaba dayan su sunji jiki, ba shiri yace mata yaji ya yarda zai koma aiki, amma sai inzasu dinga yin waya duk bayan awa ɗaya, ba yacce ta iya haka ta amice, amma da sharidin duk kira ɗaya bazai wuce 5 minutes ba, shima haka ya amince, da haka ta samu ya koma office. Har zuwa wannan lokacin babu abinda ya shiga tsananin su, ta bangaren auratayya saidai zuwa yanzu an samu ci gaba sosai dan sukan sha romance dinsu na fitar hankali, saidai fa iyakar ta nan, ita kanta tana mamakin yadda akayi ya kasa nemanta har yanzu tun abin bai damunta har ya fara dan damunta, har take tunanin anya ma sonda yace yana mata da gaskene kuwa, dan indai akwai soyayyan dole zaiso su zama Abu guda ai, Allah sarki Asmah bata San Aslam yama fita bukatar hakan ba, saidai yana nan akan bakanshi, na cewa saita nemi hakan da kanta tukunna. Gaba daya Aslam ya manta da wata zee a babin rayuwarsa, Asmah ce kawai a gabanshi a halin yanzu. Yau gaba daya familin sun tashi da tsantsar farin cike, ba komai bane kuwa face haihuwan da akayi musu gagarumi, yayansu Rabi'a ce ta haihu maman hanifa, ta samu ɗa namiji wannan karon, da safiyar yau mami ta kira su dukkansu daya bayan daya tana gaya musu, duk wacce ta kira ,sai taji ta daka tsalle tana murna tare da tambayarta dama tana da ciki ne, tasan duk abinda sukema wannan tsallen murnan koba komai zasu zo gida zasu haɗu da juna, to ai dole, wata biyar fa ba kwana biyar ba, duk da suna waya da juna, da kuma iyayen nasu...... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 119 Sudai shiru sukayi bakin su kanin kafar su, burin su bai wuce su gansu sun fita daga wannan kasurgumin kauyen ba. Ko bi takan kunun da uwargidan mallam kamsusi ta ajiye musu basuyi ba, kimtsawa suka shiga yi duk in suka tuna uban tafiyar dake kansu sai gaban su ya yanke ya fadi, kanwar mamar su inna ta kalli beebaloo tace "wlh beebaloo baki ma kanki adalci ba, duk mazan duniya nan da tarin maneman ki,ki rasa Wanda zaki aura sai wannan mutumi, ki rasa inda zaki karkare rayuwar ki sai wannan kasurgumin kauyen, to nidai munyi sallama kenan dan keda kara ganina sai dai in kin kawo mana ziyara, amma nidai bazan sake zuwa wannan kauye ba, ni abin dayafi bani mamaki ma shin a ina kika hadu da wannan mutumin har kuma daidaita har ya kaiku da aure" taɓe baki kanwar ta tayi tace "hmmm inna ai Allah ne ya kama yaya beebaloo, ki duba kiga mazajen data aura a baya masu rufin asiri amma taki zama, ki duba irin zawarawan yaya beebaloo amma, duk ciki wai ba Wanda ya mata, ita sai kyakkyawa mai kudi dan babban gida, to ai ga kyakkyawa ta samu wanke hannu ka taɓa, karewar dan babban gida ma wannan shi karan kanshi ne babban." Ta karashe maganar tana kunshe dariyar da ke son kubce mata, inna ko duk da halin da take ciki na fargaban tafiyar dake gaban su saida ta dara tare da cewa "Allah ya kyauta Allah yasa wannan ya zama izna ga masu irin halin ki, kedai ga naki karshen kin gani." karfe tara sun gama kimtsawa, beebaloo kam sai binsu da kallo take a ranta tanajin kamar ta bisu amma babu hali, dan tunda ta saka kafar ta cikin gidan ko marmarin fita kofar gida bata kara yi ba. Sunyi sallama da sauran matan mallam kamsusi, sai godiya suke zuba musu kamar wadanda suka kawo wa wata gagarumar kauta ba kishiya ba. Sha tara ta arziki mallam kamsusi ya musu na kayan amfanin gona, da sauri inna tace "A'a mallam mun gode Allah ya saka da alkhairi, wlh baza mu amsa ba Allah dai ya kara arziki." Ta fadi haka ne tuna azabar tafiyar dake gaban su, yoo da wanne zasuji da Kansu ko da tilin kaya, haka suka baro ta ko kofar gida ta kasa rakasu daga bakin kofar dakinta sukayi sallama, suna fita sai ga hawaye shar a idonta ji take kamar ta bisu da gudu su tafi tare amma kuma ko daga kafarta ta kasa dan ji take kamar an saka mari an daureta, bugu da kari soyayyar da take wa mallam kamsusi bazai barta ta iya barin garin ba, dan ji take kamar idan ta rabu da shi ta rabu da rayuwar ta ne baki daya. Ranar a daki ta wuni a kwance kamar Mara lafiya, da rana sukayi abinci aka zubo mata ko kallon shi bata yi ba balle tasan wani iri ne, haka da dare, aka zubo mata shima nan ta hada su ta Jere, rabonta da mallam kamsusi kuwa tun jiya da suka iso, kewar shi takeji kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a gabanshi. Bashi ya shigo gidan ba sai gurin sha dayan dare, da kullin gasashen kazar shi a Leda, amarya kota buzuzu ce daraja gare ta, samun guri yayi ya zaune tare da sauke kayan uban rawanin dake kanshi ya ajiye gefe, kallonta yayi yana sakar mata murmushi, tare da cewa "amaryata beebaloo kenan, sannun ki da zuwa gidan kamsusi." Kallon fuskar shi tayi, da sauri ta dauke kai, harga Allah tsoro fuskar shi ke bata, amma kuma a zuciyar ta kaunar shi take. Tura mata ladar kazar yayi tare da cewa, "ga tsarabar amare nan ki tashi kici ki more nima na more." Ya fada yana washe wakeken bakin shi mai dauke da jajayen hakora duk goro ya gama gwagwuye su, sa mun kanta tayi da kasa musa mishi, jiki na rawa ta dauki ledar kazar ta kwance ta shiga ci, tura wa kawai take yi badan dadi ba, sai dan mici micin idanunshi daya kafe ta dashi. Tana gama ci baiyi kasa a gwuiwa ya mika fata fatan hannun shi ya janyo ta tare da fara kokarin tubeta, a ranta bàta so amma kuma baza ta iya hanawa ba, sai zazzare ido da takeyi kamar an tsoma ɓera a buta shiko ko a jikin shi ci gaba da abinda yayi niyya kawai yake yi, jikinta ne ya dauki rawa jin kausasan hannun shi akan nonuwanta yana matsawa, hankalinta bai kara tashi ba saida ya hade bakin shi da nata, innalillahi ji tayi kamar ta hankede shi amma kuma ba hali. Tana ji tana gani mallam kamsusi ya shige ta, da gagjejiyar Abin shi kamar na doki, dan azaba bata San sanda ta saki ihu ba, uwar gidan shi da dakin ta ke manne dana beebaloo, tana jin ihun ta ta kwashe da dariya tare da cewa"har na tausaya miki yarinya, yau zakisan Allah daya ne, gara dai wasu su dan taba muma mu huta kwana biyu." Iya azaba beebaloo ta shata, har addu'a ta shiga yi a zuciyar ta Allah ya dauki ranta ta huta, daker da sidin goshi ya kawo, jin haka ta shiga sauke ajiyar zuciya a tunanin ta ya gama kenan, saidai bata gama dawowa hayyacinta ba taji yana canza mata style zai koma, ai tunka ya saka ta fara yanka ihu, shiko ko a jikin shi, sai ma wani kara kaimi da yakeyi. Aiko dai ranar kwana mallam kamsusi yayi akanta tun tana saka ran zai gama shiru shiru sai da garin Allah ya waye, alfijir ya keto. Kasa tashi tayi daga kwance da take sai kuka take yi Abin tausayi, yana tafiya masallaci matar shi mai bima uwar gida mai suna kande ta fado dakin, cikin tausaya wa ta taimaka mata ta tashi zaune tanayi tana jero mata sannu. Ita ta taimaka mata ta ririketa ta kaita Bayan gida, uwar gida kuma ta kawo katan baho da ruwan zafi, itama sannun take jero mata tanayi tana kumshe dariyar ta. Koda ta gasa jiki ta fito tuni zazzabi ya rufeta, sai kuka takeyi, uwan gidan ta kalleta tace "amarya shawaran da zan baki in zaki, kama jikin ki kama domin kuwa aiki na gaban ki , dan yauma dakin ki zai kwana kuma ina mai tabbatar miki mutuwa kawai Zakiyi mallam ya daga miki kafa." Jin haka tuni ta kara rushewa da kuka tare da daura hannunta akai tace "na shiga uku ni beebaloo Allah ka yafe min." Kande tace "aiko dai ko kukan jini zakiyi sai dai kiyi." Kwana ukun da mallam kamsusi yayi a dakin beebaloo mutuwa ne kawai batayi ba, suma dai tayi shi yafi sau biyar a mabanban tan lokuta, gashi idan yazo bata iya hanawa, ko ture shi bata iya yi, ita kanta bata San dalili ba, ko musu bata iya yi mai komai yace mata jiki na rawa zatayi. Gashi a zuciyar ta dai bata so amma kuma baza ta iya hanawa ba. Ranar da ta fita a girki ya Tara su da sauran matan yace ya raba girki, su kwana dadaddaya ita kwana biyu. Ma'ana idan yayi kwana daya dakin uwar gida, yayi kwana daya dakin kande, sai yayi kwana biyu dakin beebaloo sannan a zagayo dakin uwar gida. Su kande dadi kamar ya kashe su yayin da ita kuma sai hawaye kebin idanunta bibbiyu, kallonta yayi ya washe baki tare da cewa"ko ba haka ba amarya ta, kinga sai mu samu muci amarcin mu sosai ko" da sauri ta gyada kai alamar eh haka ne, ya kyalkyale da dariyar mugunta kafin ya sa kai yabar gidan yana fita ta daura hannu akai ta fashe da kuka, kande ne ta shiga rarrashinta yayinda uwar gida ta shiga sheka dariya. A ranar da girki ya dawo hannunta kuwa taga tashin hankali tun da sassafe aka kawo mata tsabar dawa da garin kuka, da daddawa da gishi wai shi zata girka, ta ina zata fara, kande dake ta dan fi uwar gida tausayi itace ta gwada mata yadda zata surfa dawan ta daka shi yayi laushi sannan ta to tuwo da miya, Wanda a ranar ake bukatar shi a matsayin abincin dare. Aiko haka tayi shi babu Wanda ya saka mata hannu tana yi tana sharban hawaye da majina,kande na rarrashinta tana dan gyara mata idan tayi ba daidai ba. Kafin sati biyu da auren su ta lalace gaba daya ta fice a kamanninta ta kode ta jeme ta rame, ga wahalar aiki indai ke keda girki aikin gidan ke fa Zakiyi ba mai taya ,ki sannan da daddre da zaki huta, miji yazo da nashi jidalin a kwana anayi kullum kuwa ba daga kafa, ga nata daya fi na kowa kwana biyu. Wannan shine halin da beebaloo ta tsinci kanta, sakamakon son zuciya, taki zaman aure tace sai kyakkyawa mai kudi karshe Allah ya nuna mata aya, ta bige da auren mallam kamsusi ga muni, ga talauci ga shi a kauyen kayau, ga jidalin miji, ga aikin gida, Allah kasa mufi karfin zuciyar mu. Da'ker zee ta iya driving zuwa gida Bayan ta gama sauraren labarin beebaloo daga bakin Dr bala, tayi kuka kamar ranta zai fita, kukan Abu biyu takeyi, na farko saboda tausayin kanta beebaloo taci amanarta,itace ta farraqa tsakanin ta da farin cikin ta wato Aslam, take taji wani irin shauki da kaunar mijinta ya taso mata, na biyu kuma kukan tausayin beebaloo ne, kwarai ta tausayawa beebaloo duk da adadalin cin amanar ta ne Allah ya nuna mata ikon shi reshe ya juye da mujiya. Mom na falo zee ta shigo ta wuce ta idanu jajur ko kula da ita batayi ba, ta shige dakin ta ɗan ta dauke a kafadar ta, hankalin mom ya tashi sosai rabon data ga zee a cikin irin wannan yanayin tun kafin ta haihu, lallai akwai matsala, take ta dauki waya ta danna ma Dad kira ta labatamai abinda ke faruwa, ko minti talatin bai kara ba ya shigo gidan hankali tashe, zee ta kasancewar itace weekness din iyayenta suna mata so bana wasa ba, basa wasa da farin cikin ta, akan Aslam suja fara samun sabanin ra'ayi da iyayenta Wanda tsananin kaunar da suke mata ne ya janyo suke ganin barin ta tare da Aslam cutuwa ne gareta. Tare suka shiga dakin samun ta sukeyi ta kifa kai a bakin bed dinta ta ajiye little boy dinta a gefe tana ta risgan kuka, da sauri har suna rige rige suka karasa cikin dakin mom tayi nasaran dago ta ta rungume ta, ta shiga dan bunbbuga Bayan ta alamar rarrshi. Shima dad zama yayi tare da daukar little Aslam ya rike, cikin sanyin jiki yace "daughter is OK, kukan ya isa haka nan, kiyi shiru ki gaya mana abinda ke damun ki,mune fa iyayenki mu muka haifeki, muna sonki daughter muna kaunar ki idan muka ganki cikin damuwa hankalin mu tashi yake yi,mukan shiga kunci zuciyoyin mu kanyi zafi, idan muka ganki cikin irin wannan hali, kiyi wa Allah ki gaya mana damuwar ki, ni kuma nayi miki alkawarin zan share miki hawaye ki indai hakan zai zama farin cikin ki,zaisa ki daina zubar da hawayen ki." A hankali sauti kukan nata ya dauke dif, sai ajiyar zuciya ta shiga saukewa akai akai irin na Wanda ya yaci kuka ya koshi, ganin haka yasa dukkansu sukayi shiru suna sauraren ta, saida ta kwashe kusan 10 a haka kafin a hankali ta dago da jajayen idanunta ta sauke akan Dad, sannan tace"kayi min alkawarin idan na gaya kama damuwa zama share min hawaye na ko?" Da sauri ya gyada kai tare da cewa "kwarai daughter na miki wannan alkawarin" tace "Dad gidan mijina nake son komawa.".......... Oum Ummeetarh 07041130088 Share And Comment Fisabilillah🙏 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 120 Ta ke duk wani annuri dake kan fuskar Dad ya bace ɓat cikin abinda baifi second ba, yayin da wani mummunan bacin rai ya bayya na ƙarara a fuskar sa.kallon kallo suka shiga yi shida mom, wannan kalma data fito daga bakin zee ya matukar razana Dad, kwata kwata bai yi tsammanin jin wannan Kalmar daga bakin ta ba, ya riga ya gama sakankan cewa ta cire Aslam daga zuciyar ta, duba da yadda kwata kwata ta daina zancen shi ta tattara lamarin ta watsar, ta cire duk wani damuwa a ranta. Ita ko idanunta ƙer akan Dad amsar da zai fito bakin shi kawai take jira. Miƙewa yayi bayan ya ajiye little Aslam dake hannun shi akan bed, ba tare da ya bata amsa ba, ya nufi hanyar fita daga dakin fuskar shi a haɗe kamar bai taba dariya ba, da kallo suka rakashi ita da mom, har ya kama handle din ƙofar zai buɗe,sai kuma ya dakata ba tare da ya juya ya kalle su ba yace"Wannan ya zama karo na karshe da zaki sake ambatar sunan wannan tsinannen yaron a gaba na, zan iya yi miki kome kike so a duniya nan amma banda barin ki a hannun wannan yaron Wanda baisan darajar ki ba." Yana gama faɗin haka yasa kai ya sa kai ya bar dakin a fusace. Wani sabon Kuka ne ya kufce mata mai ƙarfi wanda yafi nada, fadawa jikin mom tayi ta kamkame ta, tana risgan kuka kamar ranta zai fita.bubbuga Bayan ta mom ta shiga yi tana rarrashinta tare da kwantar mata da hankali,cikin kuka tace "mom ina son mijina shima ya na sona, menene yasa kuke ƙoƙarin raba mu, me yasa kuke ƙoƙarin son ku raba sunnar ma'aiki, Wlh mom ina son miji na shine farin cikina, duk abin da ya faru ba laifin mu bane nida shi munaƙisa aka shirya mana, masu son ganin bayan mu don su farraƙa tsakanin mu, dan Allah kiyi wani Abu akai, ke mahaifiya tace. ke mace ce, zaki fi Dad fahimtar damuwa ta."Ta karashe maganar cikin matsanancin kuka. Cikin lallashi mom tace "ya isa daughter ki share hawayen ki, na fahimce ki kuma insha Allah zan tsaya miki zaki koma dakin mijin ki, Dad ɗinki yana da tsatsauran ra'ayi, idan ya tsani Abu da wuya ya dawo daga baya ya so shi, amma nasan kodan saboda little boy dole zai hakura ki koma ɗakin ki, nasan shima bazai so yaron ya taso yana tambayar ki wanene ubansa ba, alhalin kuma shi ba shege bane, karki damu zan taya ki yaƙin domin farin cikin ki shine nawa." Hankalin ta ya dan kwanta jin mom ta fara supporting dinta, tasan mom takan iya sauya ra'ayin Dad, idan ta tirje, duk da abune mai baƙar wuya, amma tana da tasiri agurin shi, da idan ta nace yaja taja yakan saki. Ci gaba mom tayi da kwantar mata da hankali da kuma tabbar mata da cewa ta kwantar da hankalinta zata koma gidan mijin ta ko yanzu ko anjima, da'ker da siɗin goshi mom ta samu zee tayi shiru. Sauke ajiyar zuciya take yi a kai a kai tana sauraren maganganun mom dake ƙara kwantar mata da hankali, a haka barci ya fara fusgarta, ganin haka yasa mom kwantar da ita a gadon ta, tare da daukar little Aslam ta fice daga dakin, hankalin ta kuma gaba daya sai ya koma kan Dad wani yanayi yake ciki a halin yanzu? tasan duk inda yake a halin yanzu yana cikin tsananin bacin rai ta sani itace shaida akan irin tsanar da yama Aslam, fatan ta dai Allah yasa bai bar cikin gidan ba, ya zame mata dole tayi wani Abu akan wannan lamarin matsayin ta na mace kuma uwa, ta sani sauya ra'ayin Dad musamman akan Aslam abune mai matuƙar wahala amma ta dauki damarar ko ana ha maza ha mata, zata kafe kai da fata, sai inda karfin ta ya kare tunda har yayi hakuri ya bar zee da cikin Aslam ta haifa a gaban shi, to kuwa zai yi hakuri ya barta ta rayu da mijin ta, saidai tasan abin ne da kamar wuya. Inda take kyautata zaton samun shi ta nufa wato ɗakin shi, kamar yadda ta zatan kuwa a nan ta same shi,ran shi a bace kamar wanda aka aikowa sakon zagi, sai safa da marwa yakeyi from wall to wall na ɗakin, ya kasa tsayuwa waje daya ya kai gwauro yakai mari. Jin motsin shigowar ta yasa ya juyo ya kalle ta, tare da cewa a kausashe "Kin sani na sani wannan bukata ta daughter bazai taba yuwuwa ba idan da Wanda na tsana a duniya to Bayan wannan yaron yake, na tsane shi ina jin haushin shi na kullace shi sosai a zuciya ta , shine mutum na farko daya fara warware mini tsari na, ban taba tsara zan aurad da daughter a daidai wannan lokacin ba, amma yaron nan ya karya mini tsari ta hanyar cusa mata soyayya har ta nemi tayi fito na fito Dani akan shi, ban taba samun banbancin ra'ayi da ita ba, duk abin da na zabar mata shi take bi, duk abinda nace tayi shi take yi, duk abin da na hanata bari take yi. amma akan wannan yaron ta tirje ta dage ta kafe ta rufe idanunta ta manta da matsayina a gare ta har sai da ta saka na aika ta abinda banyi niya ba, Bayan haka wanan yaron shine mutum na farko daya fara daga hannu ya marar mini fuskar ɗiya Wanda ni mahaifinta tunda na haifeta har takai shekara ashirin da shida a gabanta ban taba koda dun gurin kanta bane, har ila yau shine mutum na farko daya fara dukan mini ɗiya, Bayan Marin da ya mata." Mom da tunda ta shigo bai bata damar cewa komai ba tayi sauri ta tari nunfashin shi da cewa "Kuma shine mutum na farko da zaka fara baiwa hakuri domin ya taimake ka ya karbi ƴarka a karo na biyu." Take idanunta Dad suka wani ƙankance jin maganar bazan da mom keyi, to maganar banza mana a ganin shi, shi take nufin zai bawa wannan yaron hakuri,nuna kanshi yayi yace "ni, kina nufin ni zan bashi hakuri, to saboda me akan me zan bashi hakuri sh.. " bata bari yakai karshe ba ta sake taran numfashin shi da cewa "saboda farin cikin tillon ƴarka, idan har da gaske kana mata irin son da kake faɗa kana mata to ka sasanta da mijinta ka kuma barta ta koma ɗakin ta taje su raini ɗansu a gaban su kamar yadda muka Raine ta a gaban mu." Ranshi yaji yana kara ɓaci, ji yake yi kamar zagin shi mom akeyi idan tace ya bari zee ta koma gidan wannan yaron, cikin masifa da hargagi yace "kinga karima fitar min daga ɗaki kafin na buɗe idanuna na rufe." Ya karkare maganar yana nuna mata hanyar fita, ganin haka yasa mom ficewa daga ɗakin salin alin, ya rakata da harara tare da cewa"maganar banza maganar wofi,Idan naki bari ta koma fa, me zaki iyi yi." Koda mom ta fito bata koma ɗakin zee ba ɗakin ta ta koma ta lalubi bakin bed ta zauna, tasan dama hakan zai kasance amma duk da haka baza ta sare ba, zata ci gaba da lallaba har, ta samu haƙan ta ya cimma ruwa. Koda zee ta tashi mom bata gaya mata yadda sukeyi da Dad ba itama bata tambaya ba, ta dai gama yanke shawara ta tsaida matsaya ɗaya, zata basu haƙƙin su na iyayen ta da haihuwar ta da sukayi ta bisu sauda ƙafa, idan har suka tirje to lallai zasu neme ta su rasa, ko mai tsira da amince yace kada kuyi biyayya ga abin halitta wurin sabon Allah, ita zata bi mijin ta domin shine aljannar ta. (Allah sarki zee duk wannan abin bata San Aslam yayi nasaran auren Asmah ba fa😟) ~9JA~ Bayan wata biyar Jiki a sanyaye Aslam ya miƙa hannu ya karbi farin fefan da Dr ke mika mishi, kallon su Dr Aysha tayi cikin tsananin tausayawa tace " Amm Mr and mrs Aslam wannan shine result din scanning ɗin da aka mata, bamu ga komai ba, kuma still babu ciki, amma dan Allah kar ku damu karku cire rai, in-sha Allah zaku samu ciki, yanzu dai zan daura ku akan magunguna kuje kuyi ta sha na wata daya ne muga yadda hali zaiyi." Tuni hawaye suka fara zarya akan dakalin fuskarta, yayinda shi kuma gaba daya fuskar shi ta dagule ta koma kalar tausayi, kwantar da kanta tayi akan ƙirjin shi ta side ɗin da take zaune, shi kuma ya rungume ta yana ɗan tapping Bayan ta a hankali, Dr Aysha ta kalle su, tayi murmushin ta mai kayatarwa, zancen gaskiya Mr and mrs Aslam suna matukar burgeta, ta Daɗe bata ga ma'aurata masu nuna ma juna tsantsar so da kauna kamar su ba, basa shakka kowa basa shayin kowa a gaban kowa suna nuna ma junan su kulawa, wani bin ma basu sanin sunyi wani abin, tana kuma matukar tausaya musu sosai akan rashin samun cikin da basu yi ba wannan ne karo na biyar da suka zo gare ta, ta lura daga matar har mijin sun kwallafa ransu akan samun haihuwa. Ya duƙu fa gurin lallshin ta da alama ma ya manta a office din Dr suke, dan dago face dinta yayi da nufin ya lashe hawayen dake kwarara a idanunta, ganin haka yasa Dr Aysha saurin yin gyaran murya, da sauri duka suka kalle ta, Asmah ta dan dukar dakai alamar kunya yayin da shi kuma da ba ruwan shi da kunya idanunshi ker akan Dr murmushi tayi tace"kuyi hakuri masoya na katse muku hanzari ko, to nece wannan shine magungunan da zaku siya kusha na 1mnth idan Allah ya yarda sai kuga an dace" ta kare maganar tana miƙa wa Aslam farin fefan da tayi rubutun, amsa yayi yana mata godiya sannan suka fito daga office din tana tallabe a jikin shi suka fito suka nufi parking lot, mutane sai kallon su akeyi suko ko a jikin su. Saida ya buɗe mata ta shiga ta zauna sannan shima ya dawo ya bude gefen driver ya shiga suka dauki hanya, suna tafe yana ƙara kwantar mata da hankali, duk da shima karfin hali yakeyi, idan da zai samu dama shima kukan zaiyi sai dai kasancewar shi namiji yasa ya dake yana lallashin ta, ita ko sai ruwan hawaye take zubar wa tana shehseka, sun zo dai dai kofar gida har mai gadi ya wangale get, wayar shi dake hannunta yayi ringing, ko dubawa batayi ta mika mishi, ganin Amir ne me kiran yasa ya daga, daga can bangaren Amir cikin yanayin tsantsar farin ciki yace"broh matata ta haihu, yanzun nan yanzu haka muna standard hospital ko sallaman mu ba'ayi ba." Aslam a ruɗe yace "iyeee kace ta haihu." Ai jin maganar haihuwa yasa ta tsaya da kukan shagwaban da take yi, tare da zazzaro manyan idanunta ta waje gabanta na faduwa tace"honey waye ya haihu" cikin washe baki yace"Amira ce" wani irin zabura tayi ta rungume shi tana faɗin "alhmdllh alhmdllh Allah mun gode maka." Tana cikin murnar kuma yaga tayi tsit, can kuma sai kuka......... Kwana biyu kun juna shiru wlh nadan samu uziri ne kuyi tamin hakuri dai. Oum Ummeetarh 07041130088💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 121 Ko ba'a faɗa ba yasan kukan me take yi, ta ke yaji gaba ɗaya jikin shi ya ƙara yin sanyi, haka dai ya daure ya shiga rarrashin ta, yana kwantar mata da hankali, ɗago fuskar ta da yayi gaje gaje da hawaye tayi daga jikin shi ta zuba mi shi idanun ta da sukayi jajur tana kallon shi, shima nashi idanun ya zuba a cikin nata, tare da kamo hannayen ta ya riƙe cikin nashi yana murzawa a hankali, a hankali ta buɗe bakin ta tace "ya Aslam sai yaushe ne nima zan haihu, sai yaushe nima zan samu ciki, tsoro nake yi kar ace na kasa cika maka burin ka na samun haihuwa, na San kana son haihuwa sosai kana son kaga gudan jinin ka a duniya, nima kuma ina so domin duk abin da Aslam yake so shi Asmah take so. Inajin tsoran na kasa cika maka wannan burin naka, har hakan ya janyo ka juya min baya wata rana, Wanda duk ranar da hakan ta kasan ce sai dai a kwashi gawar Asmah, domin Asmah baza ta iya rayuwa ba tare da Aslam ba, dan Allah ya Aslam kamin alkawari komai rintsi baza ka juya min baya ba." "Shiii!" Ya faɗa tare da daura dan yatsar shi akan lips ɗinta, girgiza mata kai yayi tare da cewa "kada na sake jin kwatan kwacin irin wadannan maganganun suna fitowa daga bakin ki, Aslam na Asmah ne, ruwa da iska babu abin da zai sa ya juya mata baya, iya wuya muna tare, kuma in-sha Allah zaki samu ciki ki haifa min kyawawan ƴaƴa masu kama dake, zaki shayar dasu kamar kowacce uwa, zaki basu tarbiyya irin Wanda mummy ta baki, kinji my hussy." Gyada kai tayi hawaye naci gaba da kwaran ya daga idanunta ta, sakin hannayen ta yayi, ya jayo fuskarta daf da tashi a hankali ya shiga dauke hawayen dake zubowa a idanun ta da harshen shi, yana gamawa kuma ya haɗe bakin su ya shiga kissing dinta a hankali, sai da yayi ma'ishi ya dago yana kallonta itama shi take kallo yace"oya yi murmushi." Wani murmushi tayi Wanda da gani yasan iya fuska kawai ya tsaya.girgiza kai yayi yace "wannan bai yi ba." Sake wani tayi Wanda babu banbancin dana farko, sake girgiza kai yayi yace "wannan ma bai min ba, bari kiga irin Wanda nake so." Kafin ta Ankara taji ya fara mata cakulkuli, ba shiri ta shiga kwalkwala dariya tare da kokarin zillewa tana buge hannun shi. Ganin haka yasa ya kyale ta, shima yana mata dariya, hararan wasa ta watsa mai cikin muryar shagwaɓa tace" Kai ko ya Aslam yanzu dana mutu fa, baka San ance cakulkuli kanin mutuwa bane." Cikin kwaikwayon muryar ta yace"to ba kene kika ki yi min murmushi ba tun dazu sai kuka kikeyi kina ta min asarar hawayen ki masu daraja."dungure mai kai tayi cikin sigar wasa tare da murguɗa baki. Dariya yayi tare da cewa "bari dai mu karasa ciki, na baki wani labari mai daɗi." Ya karashe maganar yana kokarin tada motar, riƙe hannu shi tayi tace"dan Allah ya Aslam ka kaini naga babyn mu hankali na ya kwanta." Yace"eh to da nima naso hakan, amma yanzu na canja shawara, kimu shiga daga ciki ki ɗan dumama ni sannan mu tafi." Ya kara she maganar yana ɗage mata gira tare da sakar mata wani shu'umin murmushin da ita kaɗai tasan fassarar sa, ba yadda ta iya, tunda ya bukaci hakan tasan idan ba yi yayi ba kuwa baza ta samu sa'ida ba, don haka bata ƙara cewa komai ba ya tada motor suka ƙarasa ciki. Kasancewar tana son zuwa ganin baby duk rabin hankalin ta nacan yasa ta ringa yin komai sauri sauri, hakan kuwa yamai daidai sakar mata ragamar komai yayi ita ta buga wasan, Bayan sunyi wanka abinci ta girka musu mai sauki sukaci, basu suka bar gidan ba kuwa sai Bayan la'asar. Koda suka isa asibitin an sallame su, Aslam yace "gida zamu je kenan." Ya faɗa yana karya kan motar ya dauki hanyar zuwa albishir inda gidan Amir yake. Suna tafe suna hirar su ta masoya Wanda duk rabin hirar akan batun babyn su ne suma, inda musu ya barke Asmah tace namiji take so shi kuma yace mace yake so. Wayar ta ne ya dauki ringing shuru sukayi duka ta Ciro wayar daga cikin hand bag dinta, ganin me kiran ne ya saka ta sakin murmushi, kallon ta yayi yace"wake kira." Tace "matar Dr." Ya mutsa fuska yayi alamar bai gane ba, kafin ya tambayeta wacece haka har tayi picking call din ta saka a amsa kuwwa sai ji yayi muryar batool ya karaɗe mai kunne tana cewa"yar uwa ina kika shige ne tun a asibiti nake ta zuba idon ganin ta ina zaki bullo, gashi har anyi sallama mun wuce gida shiru shine nace bari dai na kira naji ko lafiya." Murmushi tayi tace"ke dai bari yar uwa tun ɗazu naso zuwa, wani dan uziri ya rike ni, amma gani a kan hanya yanzun nan insha Allah." Dariya batool ta kwashe dashi cikin son ta tsokane ta tace "uzirin oga babba ba ai nasan shi ya rike mana ke, yana nan yana danne mana yar uwa amma in yazo nan mu yai ta wani mazurai, yana ciccin magani, fuskar nan a haɗe kamar wani na Allah, zaki rantse bazai iya kallo mace ba balle yayi eh yane da ita, to munsan komai." Wani iri wawan burki ya taka jin abinda batool ke fadi Asmah kam wani dariya me haɗe da tari ya sarke ta lokaci guda, batool tace "wlh kuwa sister ba batun dariya bane ai da ganin idanun wannan mutumin zaiyi jaraba ba kaɗan ba, dama kinsan ance irin shiru shirun nan sunfi kowa naci a wannan fanni, a fuska kamar in an saka musu yatsa a baki baza su iya cizawa ba." Dariyar da yaci karfin ta yasa ta katse kiran cikin sauri tana kallon Aslam daya kasa rufe baki tsabar mamaki da al'ajabi sai kuwa zazzaro ido yake yi yana muzurai take maganar batool ya fado mata a rai, ta kara kwashe wa da dariya har da riƙe ciki. Shima dariyar ne ya kama shi ya shiga taya ta, Girgiza kai yayi yace"lallai ma yaran nan haka na zama a wajen su, haka suka raina ni dama, lallai ma yaran nan sunga gadon barcina ." Ya faɗa cikin tsantsar mamaki dan shi abin ya ba'in daure mashi kai inda wani ya gaya mai wlh baza yarda ba, duk da yasan batool zata aika, indai ita ce daya sani. Cikin dariya tace "honey kasan batool shakiya ce, babu Wanda ta ragawa, idan abin ta ya motsa har su daddy yi musu take." Yace "aiko dai zata ci kaniyar ta yau a hannu na, sai ta maimaita abinda ta faɗa a gaba na badai zama da wancen ƙara min ɗan iskan ya kara koya mata fitsara ba." Cikin zaro ido tace "kai honey kar kasa naƙudan dole ya taso mata, kasan dai ko giya ta sha baza ta iya maimaita wannan maganar a gaban ka." Yace "ta ko sha mari, ai har yanzu ina nan a Muhammad Aslam ɗina nada da ta sani." Dariya tayi tace "haba dai honey matar wani ce fa." Yace "matar wani ko? To ko mijin nata ne yamin dukan tsiya zan mai balle ita dana ma wanka na goya a baya na." Dariya ta kwashe dashi tare da cewa "Dr din zaka daka." yace "kina mamaki ne ." tace "eh mana." Yace "ki tambaya kiji koda muna yara dukan tsiya nake mai yayi ta kuka hawaye da majina shaɓe shaɓe gashi fa ya fini girma a lokacin"Asmah don dariya harda hawaye ciki dariya tace "dan Allah ya Aslam ka tada motar mu wuce kar kasa cikina ya fashe dan dariya." Dariya yayi tare da ta da motar, har sun far tafiya kiran Amir ya shigo nashi wayar ɗagawa yayi yace "angon ƙarbi angon ƙarni." Amir murya cike da damuwa yace "dan uwa sun kassara ni." Aslam cikin ɗan ta shin hankali yace "su waye kuma." Amir yace "su mummy." Aslam yace "me suka yi." Amir kamar zai fashe da kuka yace"wai bana nan na je gida kwaso wasu kaya, likita ta basu sallama, wai kafin na ƙaraso sun wuce da ita can family hause wai wani acen zata yi wanka sai nan da kwana ar'ba'in zata dawo." Dariyar ƙeta Aslam ya fashe dashi tare da cewa "subhanallahi sannu." Sannan ya ci gaba da kwasar dariya irin mai kara cusa haushin nan, Amir daya gama ƙulewa cikin fushi yace "shege dan iska kawai." Tare da katse kiran ma gaba ɗaya. Asmah tace "menene?" Yace "su mummy ke Neman su saka mishi hypertension wai matar shi suka dauke zuwa gida wani wai zata yi wankan jego a gida." Ya karashe maganar yana shan U turn da motar suka dauki hanyar family hause, tace "to shine kake mishi dariya, yau dai ga mutum gobe gare ka." Yace "ina! Ba wannan maganar , aini babu Wanda ya isa ya min irin wannan talalan mai kamar tsaki, wlh bazan yarda ba kinji na rantse idan kuma suka matsa to sai dai su bamu daki ɗaya a gidan muyi zaman wankan tare." Tace "haka kace ko to a dai yi mu gani idan tusa zata hura wuta." Yace "za kuwa ki gani Allah dai ya kaimu lokacin." Tace "Amin kuwa" ganin yadda yake tukin a slow yasa tace "dan honey kayi sauri na matsu naje naga babyn mu." Minti 20 ya dauke su, suka iso family hause, direct kuwa part din mummy suka yi,inda suke kyautata zaton samun su. Falon mummy cike da yan uwa Mami, ya Rabi'ah, batool, Khadijah, hajiya mama, kamal, da kuma Amir. A na zazzaune fuskar kowa cike da farin ciki banda Amir dake ta ciccin magani. Asmah ce a gaba tana sallama batool ta taso da sauri tana mata oyoyo kamar yadda suka saba yi ma juna da tirtsetsen cikin ta da ko nauyin shi bata ji, cike da kulawa ta tare ta tare da cewa"ayya yar uwa da kin bari ni na karaso na miki ai." Aslam dake Bayan su ganin sun tare mai hanya yasa yayi gyaran murya, sauri batool ta sake ta, tare da kallon gefen da ta jiyo muryar ya Aslam, suna haɗa ido ya galla mata hararan da saida babyn cikin ta yayi zillo. da sauri har tana dan risina wa tace "sannu da zuwa ya Aslam, ina wuni." Bai amsa ta ba sai ma qare hade rai da yayi kamar bai taba dariya ba, kallon shi Asmah tayi ta juya ta kalli batool da tayi tsuru ta dukar da kai kasa cikin ladabi. Kawai sai ta kwashe da dariya, ita ma hararan ya watsa mata, tare da bi ta gefen su ya shige falon, Jan hannun batool tayi suka bi Bayan shi, ita dai batool a tsora ce take, bata son taga ya Aslam cikin irin wannan fuskar, domin duk ranar daya tashi musu da irin wannan fuskar uban su yake ci, kowacce sai ta samu rabon ta a cikin su ranar ko mari ko rankwa shi. Aslam dake gaba shiya fara karasawa gaban hajiya mama dake rugume da babyn ya asma, cike da farin ciki da wani irin so da shauki yake kallon babyn bakin shi yaki rufuwa take fuskar shi ta washe ya shiga sakin wani irin kayataccen murmushi, itama tana shigowa falon abinda idanunta suka hango mata kenan babyn dake hannun Aslam, da sauri ta saki hannun batool ta ƙarasa bagan shi tana kallon fuskar kyakkyawan yaron itama fuskar ta dauke madaukakin farin ciki. Gaba daya mutanen falon kallon su sukeyi cike da sha'awa da tausayawa, kowa yasan yadda suke matuakar kaunar haihuwa gashi har yau allah bai basu ba, mika hannun tayi zata karbi babyn a hannushi ƙin bata yayi tare da ƙara rike babyn da kyau, sake kai hannu tayi zata karba ya kara hanata, sai kawai ta fashe da kukan shagwaba tana bubbuga kafa. Muryar hajiya mama suka tsinta tana cewa "yayi kyau tantabaru sarakan soyayya, to muna nan dai." Cak ta tsaya da kukan da take yi kamar wacce aka danna mata stop, dariya su batool dasu ya Rabi'ah suka saka musu, harga Allah hankalinta bai kai kan mutanen dake falon ba gaba daya idanunta ya makan ce babyn su kawai ta ke gani, a kunyace ta juya ta karasa gurin hajiya mama dake zaune ta rungume ta, ture ta hajiya mama ta shiga yi da wasa tana cewa "ni daga ni dallah can karki karkare ni." Batool tace "lallai ji matar nan ma dan ma kin gode ta rungume ki, kema sister ga Mami da zaki rungume kinje kin rungume wannan taohuwar." Hada idanun da sukayi da Aslam ya dalla mata harara yasa tayi shiru. Gaishe da sauran mutanen falon tayi su Mami ta musu barka sannan ta nemi guri ta zauna kusa da Khadijah dake ta sakar mata murmushi, Khadijah tace"naji muryar ki yar uwa amma wlh kafata tayi tsami na kasa tasowa na tare ki." Cike da tausawa take binta da kallo tayi wani ƙiba, kafafun ta duk sun kumbura. Tace "ayya sister sannu kuma Allah ya sauke ku lafiya." Gaba daya aka amsa da amin. Hajiya mama ta kalli Aslam tace "to ai sai ka bata ɗan ita ma ta dauka ko." Kallo ta yayi tayi narai narai da ido, tayi fuskar tausayi suna hada ido ta sakar mai kallon pls mana, badan ya gaji ba ya mika mata, innalillahi Aslam ji tayi kamar ta maida babyn cikin ta gaba daya ta tattara dukkan hankalin ta akanshi tana kallo tana sakin murmushi. Fira aka shiga yi amma ita kwata kwata hankalinta baya Kansu bata San me ake cewa ba, batool kuwa duk ta takure don duk haɗa idanun da zasuyi da ya Aslam sai ya banka mata harara gajiya tayi ta mike salin alin ta nufi dakin su Nada dake upstairs kusa dana mummy inda nan ne dakin da Amira zata zauna, tana shiga suna fitowa daga toilet da alama wanka akama Amira, batool ta kalle ta tayi wani jajur abinka da farar fata, mummy tace yawwa batool dauko babyn ki kawo shima a masa wanka, komawa tayi da nufin amsar babyn a hannun Asmah takai ma mummy ƙememe Asmah taki bata, ta kara kamkamewa sai dariya su Mami ke mata, kar she dai cewa tayi ita da kanta zata kaima mummy yaron, haka suka rankaya ita da yar Aiken suka koma sama, samun Amira sukayi ta saka kaya riga da zani harda sock da dan karamin hijjab mummy ta zuba mata ruwan zafi sai sha takeyi tana yarfe zufa, ga ɗakin dunɗum ko fanka ba'a kunna ba balle Ac, kallon juna sukayi suka sake kallon Amira dake kurban ruwan zafi, takr batool taji cikin ya bada ƙulululu..... , Oum Ummeetarh 07041130088. 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqanñjjn iyayen mu} Page 122 Tana jin labarin jego jego kuma tana farƙgaban wankan nan da aka ce mata ana yi da tafasashen ruwa, yanzu kuma ganin Amira na kurban ruwan zafi sai abin ya ƙara girgiza ta wato bancin wanka da tafasashen ruwa har tafashen ruwan mutum ke sha, bata gama wannan tunanin ba taga mummy ta miƙo ma Amira kunun kanwa cike da Kofi sai tiriri yake, "oya maza maza ki kurɓe shi da zafi zafin shi ki gaggasa cikin ki jego ba abin wasa bane." Kwabe fuska Amira tayi zata yi kuka, mummy tace "oh lallai a haka da mijin ki ke neman mu bashi ke ya tafi dake gida, gashi a agaban muma kenan, to bari na gaya miki cikin ci nan naki a halin yanzu danye ne sharaf, kamar gwambo. shan abubuwa masu zafi su zasu saka ya warke, idan kuma kika ƙi sha ki ruɓe, kita wari sai dai kiga Amir ya auro galliyar amarya ya aje ki a kwandon shara." Ba Amira ba hatta batool da Asmah sai da suka zaro ido mummy tace "kwarai kuwa ba kun wani ƙolalo min idanu ba, wannan wankan da shan ruwan zafin nan da shiga ruwan zafi da tsarki,da cin abinci sosai mai jego taci abinci sosai taci tuwo tasha kunun kanwa tasha shayi ta koshi ta gasa ciki shine jego, in kika ƙi yin waɗannan abubuwan wlh kanki zaki cuta, bari na baku labari, lokacin muna yan mata a unguwar mu, wani gida akwai wata mata data haihu, taki yarda a mata wanka taki yarda tayi tsarki da kyau, taki shan ruwan zafi,wacce aka kawo mata dan ta ringa mata wanka tayi tayi da ita taki, kawai sai ta kyale ta, hmmm kunsan me ya same ta kuwa." Har suna haɗa baki wurin cewa "A'a mummy." Tace "to haukacewa tayi" batool cikin ta shin hankali tace "haukacewa fa kika ce mummy." Amira kam tuni ta kafa kofin kunun kanwa abaki ta fara kwankwaɗa, mummy tace "kwarai kuwa hauka tuburan, tana zaune kawai sai a ga tana zabure zabure kamar ta ɓaɓɓiya aka rasa mai ke damun ta, karshe miji ya koreta Gidan su ya dallo amarya." Asmah da duk tafi su ruɗewa tace "ta yaya aka gane rashin yin jego da kyau ne ya saka ta hauka." Mummy tace " labarin Nada tsowo kudai bari na barku a nan, dare nayi kuma zanwa yaro wanka." Ta amshi babyn a hannun Asmah ta fice dashi. Zama Asmah tayi a bakin bed jiki a sanyaye tace "Allah mun gode maka, abubuwa iri iri daga wannan a shiga wancen,Allah dai ya raba ku dashi lafiya kuma." Ta faɗa tana kallon batool, "ke kuma Amira wlh ki tsaya kiyi wanka nan da kyau kin dai ji abin da mummy tace idan ba'ayi da kyau ba haukacewa akeyi ni wlh duk jiki na yayi sanyi, gashi haihuwar ma ba karamin azaba bane dashi aka ce." Zaro ido Amira tayi tare da cewa "kaiii azaban ma, in kinji azaba kara mashi S." Batool da duk ta ƙara tsurewa tace "dan Allah sisters mu bar wannan zance kar kusa na kasa barci yau."dariya suka saka mata Amira tace "yar banza ga tsoro ga mugun aiki." Itama dariyar ta kama yi tace "wlh Allah jikiña yayi sanyi, ga kuma wancen mutumin sai harara na yake yi, tunda ya shigo falon nan yake ta auna min harara, duk hankali ya tashi wlh."Amira tace "wa kenan" tace "wa kika sani banda yaya babba" Asmah ta kwashe da dariya tare da cewa "Zakiyi bayani ne, duk rashin M din da kika gama zazzaga mishi a waya ɗazu a kunnen shi." Dafe kirjinta da yayi wani irin buga wa tayi tare da cewa "dan girman Allah." Asmah tace "wlh kuwa" daura hannu tayi aka tare da cewa "na shiga uku na ni batula." Duk dariya suka shiga yi mata Asmah naba Amira labarin yadda abin ya wakana. Guri ta samu ta zauna a bakin gado tare da cewa"kinga tunda na zauna a nan nida fita a ɗakin nan sai yabar Gidan nan kokuma in Dr yazo nabi ta kofar kitchen ɗin mummy na same shi a parking lot, dan Allah Asmah idan ya tambaye ki ina nake kice na tafi gida." Haka suka zauna a dakin Amira suna ta fira suna shan dariyar batool, mummy ta dawo da baby tayi mai wanka ta shirya shi tsaf, sai tsoston hannu yake yi, ganin haka yasa mummy tace Amira ta bashi nono, da'ker ta bashi wai kunya, yana kamawa kuwa taji zafi ta tsallara ihu, tana kiran Amir, mummy tace "kice Allah yaso mu dai da muka yo gida dake." Kan ta rufe baki saiga Amir ɗin ya shigo dakin a ruɗe ko ta kan su batool bai yi ba ya nufi matar shi zai tallabo sai cewa yake "baby me ya sameki meke faruwa meke miki ciwo." Mummy ce ta daka mai tsawa "kai Amir." Dakatawa yayi yana Sosa keya tace "fice ka bani guri" ta faɗa tana nuna mishi hanyar kofa saɗaf saɗaf ya fice daga dakin. Tunda aka samu yadan tsotsa duk da ba ruwa Asmah ta karɓe shi ta hana kowa, duk mai son ganin shi ya gan shi a hannun ta, zahra ta kira waya sun gaisa an dauki hotunan babyn an tura mata sai murna take yi, tana cewa zata zo suna. Nan Gidan suka karkare wuni ranar sai gurin Karfe taran dare suka bar Gidan lokacin tuni su ya Rabi'ah da Khadijah sun wurwuce, batool ma sun tafi amma fa kamar yadda ta faɗa ta kofar kitchen tabi dan kar ta haɗu da ya Aslam. Tunda Amira ta haihu kullum Asmah da Aslam sai sunje gida ganin babyn haka zasu ta rigen rigen ɗaukar shi, idan Asmah ta samu ta dauke shi kuwa duk Wanda yazo sai dai ya kalle shi a hannunta, idan zasu tafi kuwa da'ker take tafiya, ranar ma cewa tayi a bata babyn ta tafi dashi da safe zata dawo dashi da safe, dariya su Mami suka fara mata, ita ko bilhakki da gaske take, sai daker mummy ta lallaɓa ta, ta tafi harda hawayen ta kuwa. Ana gobe suna ummi ta iso, zahra kam Barr ya hana dan itama tayi nauyi, tako sha kuka, haka ta kira ummi a waya tana gaya mata tana kuka da'ker ummi ta lallaɓa ta ta kwantar mata da hankali. Ranar suna ansha shagali yaro yaci sunan daddy Abdallah za'a kira shi da Ayman, ƴan dama ta biyu fans basu samu zuwa ba wannan karan saboda matsalar rashin jirgin kasa da suka samu, dan har sun shishshirya sun hadu a tashar jirki aka ce musu ba jirgin da zaije minna a ranar, su zainaba har da kuka. Bayan sunan Amira da kwana 7 Khadijah ma ta haihu, ita ma namiji, wohoho, kar kuso kuga murna gurin wannan ahli, ba'a magana, abin sai Wanda ya gani, ita ma dai gida su mummy suka daukota amma ita a part din Mami ta sauka, wannan karan ma dai Zahra bata zo ba oga ya hana, Asmah kam liyafa taci gaba yaran ta sun zama biyu, kullum sai taje gida, idan bata je da rana ba koda daddare ne sai Aslam ya kaita taga babies. Ranar suna yaro yaci sunan Abba, yusuf za'a kira shi da na'eem, haka taron suna ya watse lafiya lafiya, aka bar masu jego a family hause inda suke samun kulawa sosai a gurin iyayen su, ummi ma tuni ta koma Abuja. Yau data kama sati biyu da haihuwar Khadijah, daidai kuma da sun gama shan maganin da Dr Aysha ta rubuta musu na 1mnth yau kuma suke saka ran komawa asbiti, cike kuma da fatan samun dacewa, dan tun last week suka ta saka ran zuwan period dinta shiru gashi har yau da suke shirin komawa hospital babu shi babu labarin shi, da wuri ta tashi ta gama duk wasu aikin dake gabanta har da hada breakfast Aslam na gefen ta yana taya ta ɗan miƙo wancen dauraye wancen, bayan sun shirya dining, wanka suka shiga a tare dan dama tunda komai ya daidata a tsakanin su tare suke wanka muddin zaiyi wanka to dole ne tayi koda kuwà fitowar ta kenan daga toilet sai ta koma sunyi tare, tun tana yi har itama ta saba indai ba taren suka yi ba bata jin daɗi. Sun bata lokaci sosai wajen wankan suna wasanni dan karshen ta saida aka kashe boss a toilet ɗin sannan suka fito maƙale da juna daure da tawul, zaunar da ita yayi gaban mirror ya shiga busar mata da gashi ta dake jike, sunayi suna hira, yace "my hussy ina ji a jikina kamar wannan karon mun dace da maganin nan, saboda kinga gashi har yau date 15 bamuga period dinki ba." Tace "Allah kuwa honey nima haka nake ji a jikina har mafarki na yi jiya wai gani dauke da babyn ka babba har ya kai 1ysr amma kuma banga sanda nake da ciki ba banga sanda na haife shi." Cike da zakuwa Yace "da gaske hussy." tace "wlh kuwa, ai dana farka saida nayi sujudul shukur." Yace "shine baki gaya min ba nima nayi, aini da har saraka sai nayi duk da ko yanzu ba bata baci, bari ma nayi sauri na gama miki, mu shirya wlh har naji na matsu muje asibitin nan, badan p- test ɗinmu ya kare ba da sai mu gyada tun yanzu ma." A haka ya gama mata ya shafa mata mayukan ta da take amfani dasu ya taje mata shi yayi mata parking ɗin shi, tsaf ta fito kamar wacce taje saloon, Aslam ya gware sosai gurin gyaran gashi, don yana matukar son gashi, wata ran ma har kitso yake mata ya kwance. Mai ya shiga shafa mata yau har makeup shiya mata, ya Ciro mata kayan da yake son ta saka, tana zaune tana gyara fuskar ta duk inda bai mata ba, tashin da zata yi gaban mirror da nufin ta saka kaya, saiga jini a bayan tawel din dake daure a jikin fari, ita bata ma kula ba, shine ya fara gani sai da gaban shi ya yanke ya faɗi. cikin zaro ido yace "meye wannan husnah." Cikin rashin fahimta tace "A' ina." Yace "a bayan ki."waigawa bayan ta tayi da sauri, ganin bata fahimci inda yake nuna mata ba yasa ya kamo tawel din ya janyo wurin ya nuna mata, a tsora ce ta ƙara ware idanunta a kan abinda yake nuna mata baki na rawa tace "honey kamar jini fa." Shima cikin tashin hankali yace "husnah ba kama bane jinin ne.Inna lil lahi wa inna ilaihi raji un." Ya shiga maimai tawa, yayinda ita kuma tuni ta fara hawaye , kwarai da gaske sun saka rai wannan karan sosai ganin Dr aysha ta basu magani sunsha har na 1mnth bugu da ƙari kuma rashin ganin jinin da basu yi akan lokaci ba, abin ka da mai nema duk sai suka saka rai da cewa lallai cikin ne. Ranar gaba ɗayan su haka suka wuni kamar wa inda kama mutuwa, asibitin ma fasa zuwa sukayi, karshe Aslam yace baza ma su sake zuwa wani Asibiti ba daga yau, zasu zauna su zuba wa sarautar Allah ido, sannan suyi ta addu'a Allah ya basu masu albarka dan shine mai bayar wa. Haka ko akayi tun ranar basu kara zuwa asibiti ba,sai dai fa kusan kullum suna hanyar family hause, don babu abinda ya ragu a zukatan su game da kawazucin son babies saima abin da ya ƙaru, mummy Mami da su daddy,kai duk sauran mutanen Gidan suna matukar tausaya musu, kowa fata da addu'a yake musu akan Allah ya basu nasu suma, hajiya mama har yan jike jiken su tayi na mutanen da taba Asmah amma shiru kake ji wai mallam yaci shirya yasha ruwa. A haka su Amira suka yi arba'in ko kwana daya kuwa basu kara ba mummy ta tattara ta tace ta su tafi Allah ya raya don ta gaji da rashin mutuncin Amir, kullum sai ta mai Jan ido yake tafiya, badan ma tayi kaffa kaffa ba, da kila tun jini bai tsaya ba zai haike mata, Tasha kama shi yana lalube ta, rannan ma badan Allah ya kawo ta ba da bata San me zafi faru ba, aiko tana ganin su ta koma da baya da sauri Allah yasa su basu ganta ba sun yi nissa,komawa bakin kofa tayi ta rafka sallama tuni suka shiga dawurwura daga shi har Amiran to ba gaskiya. Korar shi a dakin mummy tayi, ta rufe Amira da faɗa, tun lokacin ta kara saka ido sosai akan su, jini kuma na yanke mata, ta shiga yi mata gyara na gani na faɗa gyaran da ko da za'a aurad dasu basu samu irin shi ba, shiya sa suna cika 40 days ta tattara su tace suje Allah ya raya. Sati daya da wucewar Amira itama Khadijah ta wuce, Aslam da Aslam sunji matukar kewa sosai wucewar su Amira, sai dai ba'a rufe sati ba suje gida jensu suna yaran ba. A cikin wannan yanayin Zahra ma ta sauka,itama dai namiji, murna gurin Asmah kamar ita ta haihu, Barr kememe ya hana ta zuwa wanka gida wai sai dai azo a zauna da ita a mata, ba yadda suka iya, shike da iko da ita don haka aka tsayar ummi zata je ta zauna da ita, tun washe garin haihuwa Asmah tace ita bidda zata tafi, sai anyi suna, Aslam ko yace baza ta ba, nan fa ta shiga zuba mishi rigima kullum kuka karshe har ƴararta ya kai gurin ummi, da'ker ummi ta samu ta sasantasu bayan ta mata nasiha mai rasta jiki, ana gobe suna duk suka dauki hanyar bidda ya Rabi'ah,Asmah,Amira, Khadijah, ummi,hajiya mama, banda batool da ake saka ran haihuwa ko yau ko gobe, Dr shima hanawa yayi aiko dai hauka ne kawai ba yi ba dan bai gaya mata baza taje ba saida ta gama shirya kaya, taci kuka harda su hawa iskan karya, aiko tun daga lokacin ta tasar ma da kanta nakuda. Wannan karon dai dama ta biyu fans an samu halarta, aiko dai da yawan su sukaje, dan wannan karan harda wadan da basu samu zuwa biki ba.sai ga su inna habee a bidda, su zainaba wannan karon dai babu kuka bakin nan har kunne, su sweetie an sako na kasan akwati, ranar gani ga daughter na sai shagwaba take zubamin, maryama uwar gida ce ta amshe mu da fara'ar ta, ta kaimu falon ta, su O'O sai zunlen ta akeyi ana dariya, nace ba rabi baza kiji tsoron Allah ba ko ina sai kin nuna hali, nan take ta shiga jigilar gabatar mana da abinci, kala kala harda su tuwon shinkafa miyar wake abincin nufawa, aiko dai duk shi suka rufar wa,ana shan miyan wake ana santi, nidai nace musu asha miyar wake a sannu,kakus ko dake cikin ta bai da kwari tun a gidan ta fara zawo, zainaba tsabar santi memo ta dauko wai dan Allah a gwada mata yadda ake miyar nan in ta koma garin su ta ringa yi, oum Aneesarh dake duk itama irin zahra ne banufe take aure ta gware a iya miyar wake, ita ta dinga koya mata yadda akeyi, sai ga inna habee ma ta dauko nata memon tana rubutawa teema kam data fara lashe plate saida ya koma kamar an wanke, anty mahmaa kuwa anga yan uwa sai yare take ta zuba wa ba kama hannun yaro. Haka aka shiga gabatar da suna cikin farin ciki da annashuwa, yaro yaci sunan mahaifinta Barr, za'a kira shi da sultan.ana tsaka da shan suna mummy ta kira su batool ta haihu mace, nan fa aka shiga wani sabon farin ciki. Mami tace "ita kuma batula ana yayin samari sai ta tashi ta haifo kishiya ,to tunda dama bana gari ta haihu na bar ma mummy." Dariya suka saka mata ya Rabi'ah tace "Mami ya da saurin karaya haka tun baki ga kishiyar ba." Haka suka shiga wasa da dariya cike da farin ciki. Lokacin da su O'o akayi arba da zahra duk rudewa sukayi, ta kara wani kyau tayi fresh duk yadda suke hasashen ta ta wuce nan, nan fa su zee da su rabi aka shiga kashe selfie nima dan kar a barni a Baya shiga nayi muka dinga dauka na samu na daurawa a status. Washe garin suna su Asmah dasu mami suka dauko hanyar minna yayin da aka bar ummi akan sai ran suna zata zo ta koma ranar saboda ita ke kula da zahra a nan. Batool anji maza wurin naƙuda abinka da mai baki, sai surutai kala kala take yi, ita karan kanta Dr dake amsar haihuwar duk tausayin ta saida batool ta saka ta dariya, Dr bash dama cewa yayi bazai iya karbar taba, dan koda ta fara a gida kasa tabuka mata komai yayi kamar ba likita ba, sai da ya kira maah kenan ta dauko wata likita makwabciyar su suka zo kenan, aiko yasha faɗa gurin maah kamar zata mare shi. Bayan an mata wanka da babynta an kimtsa su, zuwa dare maah tace oya maza ya haɗa mata kayan batool zasu tafi, zaro ido yayi yace "maah me kika ce." Tace "gidan ku bashir abinda kunnayen ka suka jiyo maka shi kace." Gyada kai yayi a zuciyar shi yace akwai ƙura kuwa, ba yadda ya iya haka ya haɗa musu kayan ya kai mota ya zuba musu, sannan ya gaya musu ya gama suka fito suka tafi, ɗakin bash nada maah ta sauki batool kusan da nata ɗakin. Bayan ya kaisu komawa yayi shima ya jido kayan shi sai gashi da katon a kwati mai taya yana ja, lokacin da ya shigo duk suna falo banda batool dake can kwance tana baccin huce gajiya. Su afifah sun zagaye maah suna kallon ta na gasawa yarinya cibi, an kashe fanka an kashe Ac falon ya dauki dumi sosai, duk idanu suka kwalalo mai, maah tace"ka manta ne da sauran kayan su batulan?" Yace "maah ba kayan su bane nawa ne?" Tace "naka kamar yaya, ko ka amso guga ne" yace cikin babbata rai dan ma kar tace A'a "maah nima na dawo nan Gidan da zama ne har san da zasu komo mu koma tare." Sallallami maah ta shiga, tare da cewa ",yau ni zuwaira naga karshen rashin kunyar yayan zamani, wato biyo matar ka kayi bashiru." Da sauri yace "A'a fa maah." Tace "to idan A'a ne ɓace min da gani kafin na sassaɓa maka." ta faɗa tana nuna mishi hanyar fita magiya ya shigo mata, har da cewa wai tsoron Gidan yake ji bazai iya zama shi kadai ba, harara maah ta watsa mai tare da cewa "to wlh sai dai in a baskwata zaka zauna don nan dai babu ɗakin zaman ka." Ba irin nacin da baiyi ba maah ta kafe kai da fata, dole haka ya amince zai zauna a BQ din ko ba komai kullum zai samu ya dinga ganin batool kafin ya fita da idan ya dawo. A washe garin ranar da su Asmah suka dawo kowacce ta hallara agidan maah, don yima batool barka, nan fa suka ga baby kyakkyawa da ita kamar afnan sak, Asmah kamar ta hadiye babyn ko yan barka da'ker take basu sai anyi magana ma take mikawa, da kayi minti biyar kuwa zata amsa. A haka sati ya zagayo akasha suna mai ƙaya tarwa yarinya taci sunan maah juwairiyya, z'ake kiran ta da Ummeetarh, saboda sunan uwar miji taci. Duk wani gata da kulawa da mai jego ta zata biɗa batool ta samu fiyye da haka a gurin maah, ta tsaya kai da fata tana kula da ita fiyye da yadda zata ma su amrat. Tsakanin ta da Allah take mata komai, gafe guda Kuma.ga wani irin so da take nunawa baby Ummeetarh, daga ita harsu afnan,a hannun su babyn take wuni sai tayi kuka ake kawo mata ita ta bata nono su kara daukar ta. A bangaren Dr bash kuwa dirama suke kwasa da maah sosai, kwata kwata ta hana shi sakewa ya kasa samun yadda yake so, daya lallaba ya shige ɗakin batool sun dan keɓe,minti biyu zata kwala mai kira, haka dole zafi fito yana gungumi, idan har ya samu ya zauna tare da ita ya Daɗe to a falo ne cikin mutane . ~MALAYSIYA~ Yau kimanin watanni biyar kenan bayan haɗuwar zee da Dr bala, tun ranar da ta ambata wa Dad zata koma Gidan mijin ta ya nuna bacin ranshi bata sake furta kalma makamanciyar wanana ba, ta kyale shi ta zuba wa sarautar Allah ido har zuwa iya wa'adin data dibar mishi, a bangaren mom kam tayi iya bakin kokarin ta sosai wajen ganin ta shawo kan Dad amma abin yaci tura, karshe ma yace idan ta sake tada mai maganar a bakin auren ta, tun daga lokacin ta saka ma bakinta ta sakata ta kulle bata sake koda bashi labari mai kama dana Aslam ba. Yau ne ta kama little Aslam ya cika shekara ɗaya, kuma yau ne Dad shirya mai gagarumin taron birthday irin na ƴaƴan gata Wanda zee bata San da zancen ba don ita ma tana can tana nata shirin da ba Wanda yasan na meye daga Allah sai ita. Karfe Tara na safe Dad ya fito daga dakin shi cikin shirin fita mom na biye a bayar shi, har ya sa kai zafi fita zuciyar shi ta kasa jurewa yau tun safe baiji motsin su ba, baiji ko da kukan little ba, alhali ba haka ta saba yi ba duk safiyar Allah takan fito ta iske shi a dakin shi ta gaishe shi ta bashi little su gaisa, yau gashi har zai fita bata zo ba kuma baiji koda motsin ta ba. Kallon mom yayi yace "dubo min daughter kiga ko lafiya yau kwata kwata banji motsin ta ba." tace "wlh nima haka, ka riga ni furtawa a baki ne kawai dama yanzu nake shirin in ka tafi na shiga na dubota"ta karashe maganar tana nufar hanyar dakin zee.sallama tayi shiru ba amsa haka yasa tayi knocking nanma shiru , kawai sai ta murda kofar ta shiga, tana shiga ba zee a dakin ba little hakan yasa tadan kasara bakin toilet tana magana don duk tunanin ta tana toilet saidai jin ba alamar motsin kowa a toilet yasa cikin tashin hankali ta tura kofar toilet din nanma wayam ba kowa, ai da sauri ta dawo tana gaya wa daddy bata ɗakin cikin mamaki yace "bata dakin! to ina taje" mom tace "wlh nima ban sani ba." Bai yarda ba hakan yasa ya nufi dakin zee din da kanshi mom ta rufa mai baya, yana zuwa ko sallama bai samu daman yi ba ya tura kofar ya faɗa ɗakin, karaf idanunshi ya sauka akan farar linkakkiyar paper akan makeken bed din ta ta daura Biro ta danne shi, baki na rawa ya nuna wa mom papern tare da cewa "meye wancen"......... Dan Allah ku dinga comment mu samu mu gama littafin nan wlh na gaji nasan Kuma kun gaji ko? Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} *ASSALAMUALAIKUM SISTERS* Abun da mamaki ta yanda watan axumi yaketa qaratowa cikin Dan taqin lokaci. Me kika tanadarwa kanki dama yaran mu yar uwa? Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosay d bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166 Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166 Akway takalma Suma kyawawa daga kan 1k zuwa sama,07046881166 Sannan munada tsala tsalan frames d madubai n gyaran gida masukyau d arha sosay,07046881166 Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166 Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade, Semunjiku 07046881166 Page 123 Wani irin zaro ido mom tayi, lokacin da idanun ta sukayi arba da abin da yake nuna mata, gaban ta ne ya shiga faɗuwa hankalin ta ya tashi, cikin rawar jiki ta ƙarasa gaban bed ɗin ta miƙa hannun ta dake karkarwa ta ɗauki pepan ta miƙa mishi. Kasa amsa yayi sai zuba mata idanu da yayi yana binta da kallo kamar wani dolo, ganin haka yasa tayi karfin halin warware linkakken fefan ta fara karanta abin da ke rubuce a bayyane kamar haka: Amincin Allah ya tabbata a gareku yaku iyayena, barkan ku da wannan lokaci, kafin nace komai zan fara da Baku haƙuri akan abin da zaku tsinkaya a cikin wannan bakar wasiƙar, ina me neman yafiya da sanya albarkan ku a duk inda nake, a daidai wannan lokacin da kuke karanta wannan wasiƙar tawa, jirgin mu ya daɗe da keta hazo, zuciya ta gaza hakuri, na kasa juriya na tafi Neman aljannah ta ku sanya mini albarka, sannan kuma ku yafe min ina kaunar ku iyayena. Tun kafin mom takai karshen karatun tuni hawaye ya gama wanke mata fuska yayin da Dad shi kuma tuni ranshi ya gama baci,zuciyar shi ta dauki wani irin zafi kamar zata fesar da aman wuta.Wani irin numfashin fusata ya shiga fesarwa, mom bata ankara da yanayin da yake ciki ba sai da taji ya fisgi fefan dake hannun ta ya shiga cukurkuɗe shi a hannun shi ya dunƙule shi da karfi, da karfi ya furta "why daughter, why Zainab me yasa zaki min haka, kece raunina ta farko a duniya, meyasa meyasa meyasaaaaaaaa?" Tuni hankalin ta ya ƙara tashi ganin halin da ya shiga cikin kankanin lokaci gaba daya ya fita daga kamanni shi idanun shi sunyi jajur jijiyoyin kanshi sun tashi.Tsoron ta Allah tsoran ta kar ciwon shi ya tashi, cikin kuka tace "Dadyn zee ka tashi duk ba wannan ya kamata muyi ba, duk yadda akayi daughter gidan mijin ta Asl..." Katse wa maganar ta yayi sakamakon lafiyayyen Marin da ya ɗauke fuskar ta dashi , tsananin firgita saida ta taune harshe, dafe kuncin tayi ta zuba mishi idanun ta da ke zubar hawaye , tun da sukayi aure da shi yau kimanin shekaru talatin kenan cif a duniya bai taba koda zagin ta bane balle har takai ga mari. A matuƙar fusace ya nuna ta da yatsa tare da cewa cikin kakkausar murya "wannan shine hukuncin ki a duk lokacin da kikayi gigin sake ambatar sunan wannan la'anannen yaron a gaba na, nasan da haɗin bakin ki zainab ta bar gidan nan domin tun farko kin nuna kina goyan bayanta, to ki sani kiyi duk yadda zakiyi ki dawo min da ɗiya ta gaba na, idan kuma ba haka ba wallahi wallahi zan dauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ki daga ke har wancen ƙaramin dan iskan." Yana gama faɗin haka ya fice a ɗakin a fusace da wani irin sauri kamar zai tashi sama, tunda ta ɗaura hannunta a fuskar ta kafe shi da idanu ta kasa koda kefta ido ne, ita Abdus-salam zai Mara yau akan ƴar shi, ƴar da ita ta dauki cikin ta a jikin ta na tsawon wata tara da daɗi ba daɗi, yar da ta tsaga jikin ta ta fito, par da ta shayar da ita da nononta, par da taci kashi da fitsarin ta, lallai zata nuna mishi ita ɗin uwa ce,zata nuna mishi matsayin uwa a gurin ƴarta, lokaci yayi da zata dawo daga rakiyar Abdus-salam. Tunanin ta ne ya katse jin wani irin gurnani da hayani ya na tashi daga compound din gidan, muryar Dad ta jiyo yana cewa "wlh sai na kashe ka, da haɗin bakin ka ɗiyata ta bar gidan nan, munafiki ka gaya min da saka hannun ka ko A'a." Da wani irin gudu Mom ta fito daga cikin gidan tun daga nesa ta hango shi ya shaƙi wuyar get man da ke musu gadi shekara da shekaru, sai kwalfa mishi mari yake yi bai ko kula da cewa a girme kila mutumin ya girme shi ba kokuma suzo tsara. Kara girgiza shi yayi tare da cewa a tsawa ce "Da kai nake magana fa, baza ka bani amsa ba saina illata rayuwar ka." Daidai lokacin mom ta ƙaraso gurin ta rike Dad ta baya tana ƙoƙarin ta raba shi da me gadi, ina ko gezau baiyi ba da alama ba a cikin hayyacin shi yake ba. Ganin ta kasa ga me gadi na wani irin numfashi kamar ran shi zai fita yasa ta sake shi ta durƙushe kasa tare da fashe wa da wani irin kuku, mai ban tausayi. Daidai time din kuma aka buɗo karamin get din gidan aka shigo, hango yanayin da suke cika yasa alhaji Abdur-rahaman da wani mutumi ƙaraso wa cikin gidan da gudu, ganin ƙanin nashi na shirin yin kisa yasa baiyi wata wata ba ya dauke fuskar shi da maruka har biyu lafiyayyu. Take jini ya fara bulbula ta hancin Dad kafin kace kobo kuma jikin shi ya saki idanun shi ya shiga kakkafewa a hankali ya saki me gadi, yayi baya zai fadi da gudu daya mutumin da suka shigo da Alhaji Abdur-rahman ya tallabe shi yayin da shi kuma Alhaji Abdur-rahman ya tallabe mai gadi da shima yayi taga taga zai faɗi, ganin haka yasa Mom fasa wani irin gigitaccen ƙara tare da cewa"innalillahi wainnailaihi rajiun, na shiga uku shikenan Abdus-salam ya tafi ya barni, wayyo Allah naaa!!" ~9JA~ Niger tsate airport mekunkele. Janye take da katon trolley dinta a hannun ta na hagu yayin da hannun ta na dama ke rike da hannun ɗan kyakkyawan yaron ta dake sanye cikin wasu irin shegun kayan Sanyi masu masifar kyau kafar shi sanye da kwambas mai mugun tsada,kanshi sanye da hular sanyin dake jikin rigar ,yayinda ita kuma take sanye da kayan ta na gado ƙananan kaya riga da wando saidai ta daura after dress mai kauri a saman su yayin da ta yane kanta da mayafin rigar. Kallo daya zaka musu ka tabbatar tafiyayyu ne daga wata kasar dabam wacce ba Nigeria ba ba kuma maƙotan ta irin su niger da sauran su ba. Wani irin daddaɗan iska take ji yana ratsa huhun ta da duk wani kafar iska na jikin ta, rabonta da shakar irin wannan iskar tun ranar da ta saka kafar ta tabar Nigeria yau kimanin shekara daya da rabi kenan cif. Wani irin kwanciyar hankali da ta Dade bata ji irin shi bane taji ya saukar mata lokaci guda take ta shiga sauke wani irin ajiyar zuciya tana lumshe fararen idanun ta. Daga bayan ta taji yana cewa "Hajiya salamu alaikum." Da sauri ta juyo ta sauke idanunta akan dan matashin saurayin dake mata magana, sai lokacin taji hankalin ta ya tashi sai lokacin ta tuna in da ya kamata ta dosa, take zuciyar ta ya bata amsa da gidan mijin ki mana, yayin da ɗaya sashen ke cewa gidan iyayen shi, domin sune babban matsala shin da wani ido zasu karbi little a matsayin jinin su kuma jikan su ɗan Aslam wanda basu San da zaman shi a duniya ba. Muryar dan saurayin ne ya kara katseta da cewa "Hajiya baki amsani ba Nine driver da mai gida ya turo domin na kaiki masauki." Gyaɗa mai kai kawai tayi alamar ok, amsar trolley ɗinta yayi ya nufi inda ake parking motoci ya sanya a cikin motar shi, buɗe mata baya yayi ta shiga yayin da shi kuma ya buɗe gefen driver ya shiga ya tada motor suka ɗauki hanya. Sai da suka daidai ta akan babban titi ta buɗe baki a karon farko tayi magana"kure area zaka kaini." Dan juyowa yayi ya kalle ta tare da cewa "Ok hajiya, amma mai gida cewa yayi na kaini shaanu wani sabon ƙaramin gidanshi da ya saya kwanan nan gama keys ɗin gidan nan a hannu na." Tace "no ka kaini kure area kawai." Yace "toh hajiya." Bai sake cewa komai ba sai daukar hangar unguwar data ambata mashi yayi, motar su na kara kusantar unguwar gabanta na kara faduwa yayin da hankali ta ke kara kwanciya, ta rasa wanne ne ya rinjiyar wani tsakanin kwanciyar hankali da nutsuwar zuciyar da take ji da kuma faduwar gaban da ya tasa ta a gaba. Dai dai kofar tamfatsetsen gidan Alhaji baba ta umarci driver da yayi parking, bai musa ba kuwa yayi parking din tare da fitowa ya buɗe mata ƙofa, ta fito sannan ya buɗe boot ya fito mata da akwatin ta, jakar ta na hannu ta rataye a kafaɗar tare da riƙe hannun little suka doshi get din gidan yayin da drivern ke binta a baya dauke da trolley ɗinta. Cikin sa'a karamin kofar gidan a buɗe yake, da bismillah ta sanya ƙafar ta cikin gidan, hannunta rike dana little, juyowa tayi ta kalli drivern ta sakar mashi murmushi tare da miƙa mishi hannu alamar ya bata trolley ɗinta. Ba musu ya mika mata kuwa, tace " n Nagode sosai fa." Murmushi yayi tare da cewa "Ba komai hajiya akan aikina nake." Sallama sukayi ya juya ya tafi yayin da ita kuma ta fuskanci cikin gidan tana ƙare wa ko ina kallo. Babu kowa a compound ɗin gidan kasancewar gida ne da babu ƙananan yara a ciki, tambayar kanta take yi wani part zata dosa, sauke idanun ta tayi akan part din Mami, wanda nan ne part din da taɓa shiga har tayi zaman fiye da awa ɗaya a cikin shi. A hankali ta daga ƙafarta ta fara takawa zuwa part ɗin mami, sai da tayi bismaillah sannan ta danna doorbell, so ɗaya ta dauke hannunta tare da jiran tsammani. Mami da sakkowar ta kenan falon ta fito da nufin ɗaukar wayar ta data manta a falon ɗazu da safe, taji ƙarar ƙofa, hakan yasa ta nufi ƙofar ta buɗe domin duba ko wanene. Kusan suman tsaye tayi lokacin da idanun ta suka sauka cikin na zee, cike da tsantsar mamaki tace "zainab! Kece da gaske ko idona ne." Ga mamakin ta sai gani tayi zee ta sakar mata wani irin kyakkyawan murmushi, tare da kallon little dake dan jan rigar ta, sai lokacin idanun mami suka sauka akan little dake tsaye kusa da mahaifiyar shi hannunsu sarƙe dana juna. Gaban ta ne ya yanke yayi wani irin faɗuwa rass, take ta ƙure yaron da kallo bata ko keftawa, ba kowa take gani ba fa ce Aslam a wasu shekaru masu ɗan nisa da suka shuɗe, lokacin da aka auro ta gidan tana amarya. Dago da kai tayi ta kara kallon zee ta sake kallon little, ko shakka babu wannan jinin Aslam ne, ko shakka babu wannan jinin daddy da Abba ne ko shakka babu wannan yaron jinin Alhaji baba ne, babu bukatar ta tambayi ɗan waye domin ko makaho ne kuwa ya laluba zai tabbatar da hakan balle kuma ace mai ido biyu. Durkushewa tayi ta maida tsawonta daidai na little kafin kuma ta kaima yaron wani irin runguma sannan ta fashe da kuka, ba komai ne ya saka mami kuka a daidai wannan lokacin ba face tunawa da irin yadda Aslam yake kaunar yaga gudan jinin shi a duniya, kamar yadda yake ta faɗi tashi yaga ya samu ɗan kanshi a doron ƙasa, ta fi kowa sanin sirrin Aslam tafi kowa sanin yadda yake kaunar yaga ya haihu, yana iya boye ma kowa sirrin shi a duniya amma banda ita zata iya rantsuwa banda Asmah data kasance abokiyar rayuwar shi itace mutum ta biyu da zata bugi kirji ta faɗi wanene Aslam. Ɗagowa tayi tana share hawaye ta kalli zee tace "Zainab muje cikin gida wannan lamarin ba abinda zaki tunkare ni da shi ni kaɗai bane." Daukar little tayi ta ta rungume ta doshi part din Alhaji baba,yayin da zee ta rufa mata baya. Kabbara Alhaji baba ya shiga yi a bayyane yayin da hajiya mama ta shiga sharar kwallah, a lokacin da suka yi arba da little. Tuni jikin zee yiyi sanyi mekefaruwa ne,to kodai Aslam ya mutune, take gabanta yayi wani irin mummunar faɗuwa, take itama hawaye suka shiga wanke mata fuska hannun mami dake zaune kusa da ita ta damke da karfi Wanda saida mami ta juyo a firgice ta kalle ta, ganin hawaye a fuskarta yasa mami bule baki da sauri da nufin tambayar ta mekefaruwa saidai muryar ta ya katse ma mami hanzari, cikin sheshekar kuka tace"Mami ya mutu ko, Aslam ya mutu ya barni ko."Da sauri mami ta shiga girgiza mata kai kafin ta bule baki tace "A'a zainab karki sake faɗin wannan Kalmar Aslam bai mutu ba yana nan da ranshi da lafiyar shi." Zubawa mami idanu tayi tana kallon ta bawai dan ta yarda da abin da take gaya mata ba, ita yanzu idan ba ganin Aslam tayi ido da ido ba babu wanda zai ce mata yana raye ta amince. Mummy ce ta fara shigowa falon domin amsa kiran gaggawar da Alhaji Baba ya mata, a ruɗe take matuƙa don tasan irin wannan kiran gaggawa daga Alhaji baba, ba karamin muhimmin Abu bane, tana shigowa idanun ta akan little dake rungume a jikin hajiya mama ya sauke, wani irin wawan burki ta taka, yayin da doguwar sallamar da ta rafko ya katse, bakin ta ne ya shiga rawa alamar tana son ta furta wani Abu amma kuma ta kasa buɗe baki, hajiya mama ne tace tana share hawayen farin ciki"kyayi abinda yafi haka ma Aisha karaso ciki." Mami ne ta Ƙarasa gare ta ta riƙo hannunta zuwa cikin falon ta zaunar da ita kusa da hajiya mama, mummy kam dama bata iya ruɗewa ba, lokacin da tayi arba da zee sai ta kura mata ido kamar tana son ta tuno inda tasan ta harga Allah ji tayi kamar an mata formatting lin komai daga kwakwalwar ta. Daidai nan daddy ya shigo Amir na biye dashi ko zama basuyi ba Abba ma ya rafko sallama, duk da suma sun kaɗu da ganin zee tare da yaro mai kama da Aslam hakan baisa sun ruɗe ba kasancewar su mazaje masu dakkakkiyar zuciya.zama sukayi domin amsa kiran Alhaji baba, babu Wanda ya furta koda A ne daga cikin su, domin duk sanda Alhaji baba yayi irin wannan kiran kowa natsuwa yake yi ya saurare shi babu mai ikon yin magana har sai yaba da umarnin yin hakan, kamal ma ya karaso daga gurin aiki yake ma ya dauki excuse ya taso, Allah yasa ba sa wani Abu mai mahimmanci. Aslam kawai ake zaman jira kasancewar an bashi umarnin ya taho harda Asmah, kuma yana office dole saiya biya gida ya dauko ta hakan yasa yayi jinkirin isowa, falo yayi tsit sai kallo kallo akeyi a tsananin juna, fuskar kowa cike da zaƙuwan sonjin ta yaya akayi matankaɗi ya shiga gora, domin dai dukkanin su kallo daya suka ma little suka tabbatar cewa lallai shiɗin jinin su ne, kamar yadda yaron ya kasance mai farin jini da saurin shiga rai tun haihuwar sa, farin jinin shi nanan har yau babu abinda ya dakushe a ciki saima ƙaruwa da yayi, domin dukkansu a kallo ɗaya yaron ya shiga ransu kaunar shi ya kama zuciyoyin su kowanne su burin shi ya ɗauki yaron saidai babu daman yin hakan saboda girmama wa ga Alhaji baba har sai ya gama fadar abin da yasa ya tarasu sannan zasu samu daman yin hakan. Bayan kamar minti goma da haduwar kowa da kowa a falon Alhaji baba, motar Aslam ta faka a farfajiyar gidan, jiki a sanyaye ya buɗe motar ya fito, tunda ya tashi barci yau gaban shi keta faɗuwa lokaci zuwa lokaci har sai da takai ya gayawa Asmah, abin da ke damun shi, har yake cewa shi bai da tafiya bazai iya fita office ba, ita ta karfafa mai gwuiwa tare da cewa yayta ambaton innalillahi wainnailaihi rajiun, a haka ta samu ta lallaɓa shi ya tafi. Lokacin da kiran gaggawa daga Alhaji baba ya riskeshi ji yayi bugun da kirjinshi keyi ya nunku fiye dana da. A bangaren Asmah kam ita ma kwarai da gaske jikin ta a sanyaye yake tunda maganar kiran nan ya risketa haka kawai take ji a jikin ta wani Abu Mara daɗi zai bakunci rayuwar ta. Kasa fitowa daga motar tayi saida ya buɗe Mata tare da cewa "bismillah husnah muje Allah yana tare da mu koma meke ciki in-sha Allahu zaizo mana da sauƙi." Mika mata hannu yayi yana sakar mata murmushin karfafa gwuiwa, itama martanin murmushin ta mayar mai kafin ta mika hannun ta ta saka cikin nashi ya mayar ya damƙe gam kamar wani zai kwace mishi ita a haka suka doshi falon Alhaji baba hannun su cikin na juna............ Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen mu} *ASSALAMUALAIKUM SISTERS* abun d mamaki Tayanda watan axumi yaketa qaratowa cikin Dan taqin lokaci, Me kika tanadarwa kanki dama yaranmu yar uwa? Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosay d bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166 Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166 Akway takalma Suma kyawawa dgakan 1k zuwa sama,07046881166 Sannan munada tsala tsalan frames d madubai n gyaran gida masukyau d arha sosay,07046881166 Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166 Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade, Semunjiku 07046881166 Page 124 A tare suka haɗa baki wurin yin sallama kafin su sa kai cikin falon hannun su sarƙe da juna. Tunda ta jiyo muryar shi yayi sallama , zuciyar ta ya shiga wani irin luguɗen bugu da karfin gaske. Ƙofar shigowa falon ta kafe da idanun ta tana kallon jiran tsammani. Shine ya fara bayyana a falon kafin ita, kamar had'in baki daga shi har ita idanun su, akan fuskar zee ya sauka,wani irin wawan burki ya taka daga bakin ƙofar, yana bin ta da wani irin kallo mai cike da tsantsar mamaki. A firgice ta mik'e tsaye tare da zaro dukkan girman idanun ta waje, furgici da tashin hankali ne suka bayyana ƙarara akan fuskar ta, kallon Asmah take yi kamar wacce keson ta tantance shin ita d'in ce kokuwa idanunta ne ke mata gizo, mayar da idanunta tayi kan hannayensu dake sarƙe dana juna, sannan ta ƙara sauke idanunta akan Aslam dake tsaye yana kallon ta kamar wata sabuwar halitta. Gaba d'aya mutanen falon shiru sukayi suka zuba musu idanu, cikin su ukun an rasa Wanda zai fara janye idanun shi daga kan wani, kowanne da ma'anar kallon da yake bin ɗan uwan shi da shi. Zee tana bin Asmah da Aslam ne da kallon furgici da tsananin tashin hankali tare tambayar kanta shin meye alaƙar mijin ta da Asmah da har suka shigo cikin falon Alhaji baba a tare hannunsu sarƙe da juna, duk da tasan ita d'in burin shi ce zabin shi ce abar kaunar shi ce, tun kafin ta bar gidan shi, amma bata taɓa kawo tunanin cewa bayan bata zai mallake ta ba, saboda a gaban ta ranar Alhaji baba ya tsayar da lokacin bikin ta da kamal a wancen ranar, shin menene alakar su? Take zuciyar ta ta bata amsa da cewa Aure, ji tayi numfashin ta na neman gagarar ta ja, indai ko alaƙar aure ne a tsakanin mijin ta da Asmah ta shiga ukun ta, domin ita shaida ce akan irin tsananin so da kaunar da yake ma Asmah wanda tana da tabbacin ko rabin rabinshi baya mata. Asmah kam kallo tsoro da zallar madarar kishi take bin zee da shi, shin meya dawo da ita rayuwar su a daidai wannan lokacin? me tazo nema me ya kawo ta? A daidai lokacin data shaku da Aslam ta zama shi ya zama ita ta miƙa mishi dukkan ragamar rayuwarta, lallai akwai gwarama, don a yadda take kaunar Aslam a halin yanzu bata jin zata iya raba shi da wata p ƴa mace a duniya. Shi kam Aslam da wani irin kallon mai cike da tsantar mamaki yake bin ta, har ga Allah ya manta da ita gaba ɗaya a shafin rayuwar shi, bai taba kawowa a ranshi a kwai wata rana da zata juyo ya sake haɗa idanu da ita ba,tun daga ranar da ya mallaki Asmah,bai ƙara kallo duk wata diya mace da sunan mace ba, yakan tunata a wasu lokatan musamman idan yana cikin alhini rashin samun haihuwa, a duk sanda ya tunata ranshi ne ke mugun baci, bai taba tuna alkharin ta ba ko kaɗan, a duk sanda zai tuna ta baƙin ta kawai yake tunawa,nadama da dana sanin auren ta kawai yake yi a duk sanda ya tuno ta, sau da yawa yakan furta ta cuce shi kuma yana ji har duniya ta nade bazai taba iya yafe mata abin da ta mashi ba, shin me ya kawo ta gare shi a halin yanzu? "Mommahhhhhh." Zazzakar muryar yaron ne ya katse musu tunani gaba ɗayan su, har cikin zuciyar shi sautin muryar yaron ya daka , kusan a tare dukkan su ukun suka juyo dan kallon mamallakin wannan muryar, ruɗu, al'ajabi, mamaki, ne suka ziyarci shi a lokaci guda, wani irin waro ido yayi waje yana kallon yaron da ke zaune a jikin hajiya mama yana yana miƙa ma zee hannu alamar ta dauke shi, Asmah kam suman tsaye tayi, take kuma a lokaci guda taji kibiyar so da kaunar yaron ya caki zuciyar ta, har sai da ta dafe daidai saitin kahon zuciyar ta, duka idanunta ta baza tana kallon tana yaro mai kama da Aslam ɗin ta sak kamar yayi kaki, shin ɗan waye wannan a cikin ahlinsu bata taba ganin shi ba, kuma dai kallo ɗaya tamai tasan lallai shi ɗin jinin ahlin gidan ne. Gyaran muryar da Alhaji baba yayi ne ya dawo da hankalin kowa kanshi, kallon su yayi yace "Muhammad, Asma'u, zainab ku nemi waje ku zauna." Jiki a sanyaye suka nemi guri suka zauna, Asmah kusa da mummy ta zauna a tare da kwantar da kanta akan cinyar mummy Aslam kuma kusa da Abba, yayin da zee ta koma mazaunin ta nada kusa da mami ta zauna. Bayan kowa ya nutsu ya bada dukkan hankalulin sa, kallon Abba Alhaji baba yayi yace "bismillah Yusuf a buɗe mana taro da addu'a." Amsawa Abba yayi da "to Alhaji." Kafin ya shiga kwararo addu'a suna amsawa da amin, bayan sun shafa addu'a, shiru falon ya dauka na yan wasu mintuna, sauke numfashi Alhaji baba yayi kafin ya bude bakin shi cikin dattako da kamala da Allah ya hore mishi yayi sallama cikakkiya, kusan gaba ɗaya hada baki sukayi gurin amsa sallamar shi, yace "alhmdllh alhmdllh alhmdllh har kullum ina godewa Allah daya bani ku a matsayin yaya da kuma jikoki na, Allah ubangiji ya muku albarka baki ɗaya." Da amin suka amsa gaba dayan su kamar ɗazu, yaci gaba"dalilin da ya saka na muku wannan kiran na gaggawa shine, maryam (mami) tazo ta same da wani lamari mai girman gaske, ba komai bane kuwa face, zainab matar muhammad wacce kowannen ku a nan yasan irin rabuwar da sukayi da Muhammad badan ya sake ta ba, da kuma dalilin rabuwar tasu, to sai gashi zainab ta zo gare mu tare da ɗa bayan tsowon shekara ɗaya da rabi wanda ta gabatar min da shi a matsayin ɗan Muhammad ne." Kusan kowa a falon saida ya dago ya kalli Alhaji baba cike da kaɗuwa jin Abinda ya faɗa,bama kamar Aslam da Asmah da suka fi kowa shiga shock, duk da cewa dukkansu tun kallon farko da suka ma yaron suka tabbatar da cewa lallai jinin su ne amma basu taba kawo cewa zai zama dan Aslam ba, duk da kuwa ganin zee da sukayi zaune a gurin saboda suna da labari duk abinda ya faru tsakanin ta da Aslam wanda har hakan yayi sanadiyar faruwa a bubuwa da dama a baya ciki harda rabasun da mahaifinta yayi na tsayin shekara ɗaya harda ɗoriya. Ci gaba Alhaji baba yayi da cewa "duk da ba'a gaban mu zainab ta haifi wannan yaron ba jikina da zuciyata sun gama aminta da cewa lallai wannan yaron jinina ne, amma dai kafin mu yanke kowannen hukunci akan wannan lamarin zamuso ji daga bakin zainab shin ta yaya a kayi cikin da kowa ya tabbatar da zubewar shi ya rayu." Ya karashe maganar tare da kallon zee dake zaune kusa da mami kanta a kasa tana sauraren shi, dukkan su kuwa ita suka zubawa idanu alamar suna son jin Karin bayani daga bakin ta kamar yadda Alhaji baba ya umurta. Ɗago da kanta tayi ta kalli little da ke ta wasan shi a hannun hajiya mama, take kuma wasu siraran hawaye suka ziraro mata, a hankali cikin sanyin murya da sanyin jiki ta shiga basu labarin abinda ya faru tun daga auren ta da Aslam da haɗuwar ta da beebaloo barin ta Nigeria halin da ta shiga bayan komawar ta Malaysian, bayyanar cikin little har zuwa haihuwar shi haduwar ta da Dr bala labarin beebaloo,da kuma dawowar ta Nigeria a karo na biyu domin ta zauna tare da mijin ta su raini ɗansu a gaban su. Ta karashe labarin tare da fashe wa da matsanancin kuka zamowa tayi daga kan kujerar da take zaune ta sanya gwuwowin ta biyu a ƙasa ta haɗe hannayenta alamar roko da neman gafara, cikin kuka tace "ku dubi girman Allah da darajar da Allah yayi wa ma'aiki yaku wadannan ahli masu mutunci da karamci ku yafe min.a baya nasani na aikata muku abubuwa da yawa na rashin ɗa'a da rashin ganin girman ku da mutuncin ku a matsayin ku na iyayen mijina wanda nake tsananin so da son kasncewa da shi har karshen rayuwa ta, nasan ban kyauta ba kuma nasan ba Abu me kyau nake yi ba a lokacin to amma rashin ilmin addini da jahilci ke ruɗa na a waccen lokacin, amma yanzu wlh na sauya zainab din da kuka sani a da ba ita bace kuke gani yanzu a gaban ku, na muku alkawarin zaku same ni fiye da yadda kuka yi zato na, dan Allah ku karɓeni a cikin ku a karo na biyu." Ta kara she maganar cikin kuka sosai. Gaba ɗayan su jikin su yayi matukar sanyi, irin su Asmah da mami kam tuni sun fara tsiyayar da hawaye, tsit falon yayi kowa da Abin da yake saƙawa a ranshi, mummy ce tayi karfin halin miƙewa ta ta isa wurin zee ta ɗago ta daga duƙen da take ta rungume ta a jikin tana bubbuga bayan ta alamar rarrashi, kafin kuma ta maida ta mazaunin ta nada ta zaunar da ita. Gyada kai Alhaji baba yayi cike da tausayin zainab da kuma gamsuwa da tuban ta, domin kallo daya zaka mata ka tabbatar abin da take faɗa daga zuciyar ta yake fitowa, cike da isa da yarda da kai akan zantar da ko wane irin hukunci a tsakani ahlin sa yace "ya isa haka zainab mun fahimce ki, mun kuma yafe miki akan abin da kika mana kuma mun karɓeki a karo na biyu a matsayin suruka kuma jika a gare mu kije ku zauna tare da mijin ki da ɗanki da kuma abokiyar zaman ki." Da wani irin sauri Asmah ta sauke idanun ta akan Alhaji baba dake magana, kafin kuma ta juya da dasu kan zee da ake cewa suje su zauna tare, itama zee ɗin kan Asmah ta sauke idanun ta da suke nan gaje gaje da hawaye, kallo kallo suka shiga bin junan su da shi, kowacce da abinda take rayawa a zuciyar ta. Muryar Aslam ne ya dawo dasu hayyacin su, cikin wani irin dakkakkiyar murya mai nuni da cewa abin da yake faɗi daga cikin zuciyar shi yake fitowa yace "Alhaji a gaskiya bazan iya zama da mace fiye da ɗaya ba ahalin yanzu ba, bazan iya haɗa husnah da kowacce mace ba a halin yanzu, bazan iya yin adalci a tsakanin su ba, idan kuma ka takura to lallai zaka jefe rayuwa ta cikin halaka."yana gama fadin haka ya miƙe tare da daukar little dake kan cinyar hajiya mama ya nufi har yar barin falon, har ya kai bakin kofar fita ya tsinci muryar daddy yana cewa "Muhammad kada ka kuskura ka fita daga falon nan, kuma umarni nake baka ba shawara ba."........ Oum Ummeetarh 07941130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen mu} Hg *ASSALAMUALAIKUM SISTERS* abun d mamaki u watan axumi yaketa qaratowa cikin Dan taqin lokaci, Me kika tanadarwa kanki dama yaranmu yar uwa? Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosay d bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166 Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166 Akway takalma Suma kyawawa dgakan 1k zuwa sama,07046881166 Sannan munada tsala tsalan frames d madubai n gyaran gida masukyau d arha sosay,07046881166 Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166 Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade, Semunjiku 07046881166 Page 125 Cak ya tsaya a bakin ƙofar shi bai tafin ba kamar yadda yayi niya kuma bai dawo ciki ba kamar yadda daddy ya umarta, mummy ce cikin fushi tace "Wai ba dakai ake magana bane, kana jin mutanen." Daga yadda yaji amon muryar mummy yasan ranta a bace yake, take jikin shi gaba ɗaya yayi sanyi duk wani karsashi da yake da shi tuni ya neme su ya rasa, baya kaunar abin da zai sa mummy tayi fushi da shi komai ƙanƙantar abin yana gudun bacin ranta a duniya fiye da yadda yake gudun na kowa, ba ta da sauki idan tayi fushi, har gara Fushin daddy so goma akan nata. Jiki a sanyaye ya juyo ya dawo mazaunin shi daya tashi ya zauna. Shiru falon ya sake ɗauka kamar babu wani ɗan Adam a cikin shi, miƙewa Alhaji baba yayi fuskar shi a kame yadda ba kasafai mutum zai gane yanayin da yake ciki ba, kallon daddy da Abba yayi yace "Na riga na gama yanke hukunci akan wannan lamarin." Iya abin da ya faɗa kenan ya bar folon, duk da kallo suka rakashi har ya ƙule ma ganin su, bo kowa bane a falon ya fahimci inda Alhaji baba ya dosa sai su ɗin da ya ma maganar, rai bace daddy ya juyo ya kalli Aslam cikin tsananin fusata yace "kai ƙaramin mara kunya wlh baka isa ba, mu nan mu muka haife ke ba kai ka haife mu ba har kai dan ƙaramin alhaki dakai zaka zauna a gaban mu mahaifin mu yana faɗa kana faɗa, kai waye me ka taka, kai ɗin banza, to wlh ka sani babu inda zainab zata je kamar yadda Alhaji ya umarta, dakin ta zata koma ta zauna ta raini ɗan ta, idan ka isa kuma ka cika cikekken mara kunya, ka hana ta shiga gidan, maganar banza maganar hofi, inace nan akan zainab din ne ka wulakan ta mana namu ɗiyar, wani irin rashin mutunci ne baka mana ba akanta, sai yanzu saboda ka maida mu yan iska ka kalle mu kace kai baka sonta, to wlh baka isa ba, dama ina jiraye dakai akan abin da ya faru kwanaki, kaga nayi shiru bance komai ba shine yanzu ma zaka sake bijiro mana da makanman cin shi, to karyar ka tasha karya, daga yau ni Abdallahi ɗan Muhammad nayi rantsuwa da girman Allah baka isa ka sake bijera mana ba, baka isa ka sake bijere wa umarni mu ba, domin mu muka haife ka ba kai ka haife mu ba, wanda kayi a baya ya isa haka, kuma zainab zata koma dakin ta, ta share ta zauna a yau kamar yadda Alhaji ya fada, ni kuma umarni nake baka, kada kuma ka bari naji wani Abu mara kyau ya taso daga ɓangaren ka, zan saka idanu sosai a cikin gidan ka." Kallon zee yayi dake ta risgar kuka mara sauti yace "anjima ki shirya zan mayar dake ɗakin ki da kaina, a karo biyu, idan ya isa shi ɗan halak ne ya hanaki shiga." Yana kaiwa nan yasa kai yabar falon yana huci, duk shiru sukayi ana sauraren daddy an rasa mai karfin halin bashi hakuri, dama duk wurin Abba ne zai iya, kuma shima a wannan karon yana supporting din daddy akan hakan domin shima ranshi ya baci sosai akan abin da Aslam din yayi, mikewa mummy tayi itama ta kalle shi tace"daddyn ku ya fanshe ni ya gama fadin abin da duk zan fada, ga zainab nan ta dawo zata zauna a dakin ta, a bisa umarnin mu, idan kuma itama ma zaka sake ta ne to bismillah dama ba yau ka fara ba, Amma ka sani muddin kayi mata wani abu mara daɗi, zaka haɗu da matsanancin fushi na irin wadda baka taba gani ba." Ita ma bin bayan daddy tayi ranta a bace ba tare da ta kalli kowa ba a falon. Shiru falon ya dauka babu mai koda kwakwkwaran motsi ne.kowa ka kalla a lokacin fuskar sa a jagule, musamman Aslam da idanun shi sukayi wani irin jazur jijiyoyin kanshi suka fito, hankalin shi ya tashi, ba wai maganar komawar zee gidan shi bane ya daga mishi hankali, illah tsananin fushin da ya gani akan fuskar iyayen shi, abu na biyu kuma Asmah, yana tausayin ta, ita din marainiya ce ita din abin tausayi ce, ga halin da take ciki na rashin samun haihuwa, sannan kuma a dauko zee a ce su zauna a tare, shi kadai yasan wacece zee, domin shi ya zauna da ita a baya, yasan abin da zata iya aikatawa da wanda baza ta iya ba, duk wannan kukan da ta keyi tana cewa ta shiryu menene da menene shifa ba yarda yayi ba, abu daya zaisa ya yarda shine idan ya gani a aika ce amma wai dan wannan kururuwar nata duk bai dame shi ba, sannan kuma ga matsalar mahaifinta, shin yanzu da sanin shi ta taho gare shi da yardan shi da amincewar shi kokuwa A'a gaban kanta tayi, domin a wannan karan bazai juri cin zarafi daga gareshi ba sai dai ayi wacce za'ayi shi yasa tun forko baiso ya karbe ta ba, dan shi kadai ya hango abin da ya hango amma yanzu kam alkalami ya riga ya bushe. Muryar hajiya mama ne ya katse mishi tunani, "Muhammad, nima dai yau zan magantu akan sha'anin rayuwar ka a karo na farko, kada ka kuskura kace zakayi musu ko wani Abu akan wannan hukuncin da mahaifan ka suka tsayar, kuma ma in banda abin ka Muhammad ai nasan kai karan kanka har zuciyar ka baza kace baka kaunar Zainab ba, domin kuwa soyayyar farko yana da tasirin da ba kasafai ake ayi cireshi a zuciya ba, ɓacin raine kawai yasa kake ganin kamar ka tsane ta baka sonta har kake gani baza ka iya zama da ita a karo na biyu ba, nidai rokon da zan maka shine ka bata *dama ta biyu*, kamar yadda ta nema, na tabbatar zaka sha mamaki, to waima banda abinka Muhammad ai kana son zainab har yanzu tunda har ka kaunaci abin da ya fito daga tsatson ta, a duk sanda mace ta fita daga zuciyar namiji yakan tsane komai daya shafe ta ciki harda yayan da suka Haifa a tare, ka daure ka bata *dama ta biyu* na tabbatar zakayi alfahari da ita a gaba, nasan duk wannan kauke kaucen kanayi ne saboda Asma'u, to karka damu Asma'u yarinya ce natsattsiya mai hankali da hangen nesa, ina mai tabbaatar maka baza ka samu matsala da ita ba, ka haɗa kan matan ka kuje ku zauna in sha Allah wata rana sai kayi alfahi da hakan." Nan kuma ta dawo da hankalin ta kan Asmah da zee, ta shiga yi musu nasiha mai ratsa zuciya mai kashe dukkan gaɓɓai mai tausasa zuciyar mutum duk karfin ta, falon yayi tsit bakajin komai sai shehsshekan kukan Asmah da zee, hajiya mama ta ɗaure su da jijiyoyin jikin su. Ba iya su kadai nasihar ta taba ba hatta mami da Abba dasu Amir sai da jikin su ya mutu, sai da ta tabbatar sunyi laushi, sannan ta kare da yi musu addu'an zaman lafiya da samun zuri'a dayyiba, bayan ta gama ta mike a hankali cike da nutsuwa tabi bayan mijin ta. Bayan tafiyar hajiya mama, Abba ne ya daura da nashi, kafin a karshe ya rufe taron gaba daya da addu'a. Mikewa Asmah tayi tana share hawaye ta fice daga falon, ba tare da ta ko kalli inda Aslam yake ba, da kallo suka bita har mami ta buɗe baki zata tsayar da ita Abba ya daga mata hannu, shima Aslam yunkurin bin bayan ta yayi, still shima Abba ya dakatar da shi badan yaso ba ya dawo ya zauna, idanun shi a kanta har ta fice daga falon. Tafe take tana harɗe hanya kamar wacce tasha ta maku. Can cikin zuciyar tane take ji yana mata ciwo, da ace ita butulu ce da ta buɗe baki a yau tace su mummy da da daddy dama gaba daya ahalin nan basa kaunar ta, sai dai ita karan kanta ta sani idan ta fadi haka sai Allah ya tuhume ta a ranar gobe kiyama, ina zata saka zuciyar ta ne taji sanyi, kishin mijin ta take, tausayin kanta take, babban tashin hankalin ta ɗaya, shin menene makomar ta, a nan gaba a gurin Aslam, tunda gashi ya dawo da uwar gidan shi, uwar danshi, first luv dinshi, wacce take da mahaifan Haifa mishi ƴaƴa, wacce zata iya cika mishi burin shi na duniya, ta sani dole nan gaba Aslam ya ƙi ta ya komawa matar sa saboda ita ɗin ce take da abin da zata iya saka shi farin ciki da shi. Da wannan tunanin ta ƙaraso falon mummy ba tare da ta sani ba, dan gaba daya idanun ta sun rufe bata ganin gaban ta. Mummy dake nan tsaye a falo ta kasa zaune ta kasa tsaye sai safa da marwa takeyi, jin motsin mutum a kofa ya saka ta saurin juyowa ganin Asmah ce ya saka ta saurin nufar ta ta rungume ta a jikin tsam kamar wacce za'a kwace mata ita, jinta a jikin mutum wanda ta tabbatar mummy ce yasa ta fashe wa da wani irin kuka mai ban tausayi, ita kanta mummy hawaye ne ke ziraro mata, ba kowa zai fahimci ciwon Asmah ba sai wanda ya taba riskar kanshi a irin halin da ta riski kanta a yanzu, ita din abin tausayi ce a halin yanzu, tafi kowa jin zafin wannan lamarin domin kuwa ita uwace ga Asmah, dole duk wata uwa ta gari a lokacin da ɗiyar ta shiga damuwa tafi ɗiyar shiga damuwa, haihuwar Asmah ne kawai bata yi ba amma a halin yanzu zata iya rantsuwa babu wanda ya kaita jin ciwon Asmah a zuciyar ta, ta goyi bayan zee ta dawo ne badan wani manufa ba sai dai sani da tayi cewa ɗa na kowa ne kuma ko ba komai suma sun aurar a wani gidan baza su so haka ya kasance da nasu ƴaƴan a ki karbar su ba, sannan bugu da ƙari tayi amfani da Karin maganar nan ta hausawa da su ke cewa kaso naka duniya ta ki shi, ka ki naka duniya ta so shi. Muryar Asmah ne ya katse mata tunani, cikin kuka tace "mummy shike nan zan rasa ya Aslam, shike nan lokacin rabuwar mu ya gabato,mummy ya Aslam zai juya min baya ko?"goge hawayen ta tayi kafin kafin ta tausasa muryar ta tace"wa ya gaya miki haka Asmah? Kar na sake ji kin fadi haka Aslam bazai taba juya miki baya ba domin kuwa yana tsananin kaunar ki."tace "Mummy tsoro nake ji gabana faduwa yake yi." Mummy tace "Kiyi ta maimaita inna lillahi wa inna ilaihi rajiun, zaki samu sauki a zuciyar ki." Gyada kai kawai ta ringayi tare da sauke wasu irin ajiyar zuciya, dago ta mummy tayi daga jikin ta, ta tallaɓe ta nufi ɗakin ta da ita. Zaunar da ita tayi a bakin bed ta taba jikin ta zafi zau kuwa daman tasan za'a rina, magani ta kalli ta bata dakyar ta haɗiya tana gama sha sai amai shaa, cike da tausayawa mummy ta tallabe ta, har ta gama a mayar da duk abin da taci, toilet ta kaita ta kuskure baki ta wanke mata fuska, ta zame mata dan kwali ta zuba mata ruwan sanyi a kanta, sannan ta tallabo ta ta dawo da ita dakin ta kwantar da ita akan bed ta gyara wurin, ko kafin ta gama tsabtace gurin bacci ya kwashe ta, sauke ajiyar zuciya mummy tayi tare da rage mata karfi Ac ta fice daga dakin ta ja mata kofa a hankali. A tare Aslam dasu Amir suka fito daga falon Alhaji baba, Kamal yana sauri zai koma gurin aiki don dama excuse ya dauka, hakan yasa bai shiga cikin gidan ba ya fada motar shi jiki a sanyaye yabar gidan, wannan abin da ya faru ya taba mai zuciya sosai, kwarai ya tausaya wa Asmah. Amir kuwa bayan Aslam yabi domin ganin duk yadda ya duburbuce ya susuce a halin yanzu yana bukatar mai kwabatar mishi da hankali, binshi yayi da sauri ya kama hannun shi hakan yasa Aslam sauke mishi jajayen idanun shi, gyada mishi kai Amir yayi kafin a hankali ya shiga jan shi suka fara tafiya, parking lot suka iso ya buɗe motar shi gidan baya ya ce ma Aslam "Bismillah bro magana nake so muyi." Shiga motar yayi Amir ya maida kofar ya rufe tare da zagayowa ta daya side din shima ya shiga ya zauna tare da rufe kofar, a tsanake ya kira sunan Aslam cikin kamewa hakan ya tabbatar wa da Aslam cewa maganar da zai fada mishi mai muhimman ci ne, shima tattara dukkan hankali da nutsuwa shi yayi ya baiwa Amir din, domin a halin yanzu yana bukatar wanda zai rarrashe ya kwantar mashi da hankali shi ya bashi shawara ta gari, kuma yana da tabbacin zai samu duka wandannan abubuwan daga dan uwan shi abokin shi yayan shi Amir. A can falon Alhaji baba kuwa zee mami da Abba ne kawai suka rage. Abba kam dan nasiha ya ƴara ma zee din ita kadai, akan cewa ta kwantar da hankalin ta kar abin da Aslam ya faɗa ya firgita ta, shima ɓacin raine ya saka ya faɗi haka taje ta kwantar da kai tayi ladabi tayi biyayya, ta nuna mishi da gaske ita ɗin ta canja daga yadda ya santa a baya, in sha Allah komai zai daidaita, ta toshe kunnen ta ta rintse idanun ta danne zuciyar ta akan dukkan abin da zata fuskan ta daga wurin Aslam, idan tayi hakuri naɗan wani lokaci komai mai wucewa ne. Nutsuwa tayi ta bada dukkan hankalin ta tana sauraren nasihar Abba, bayan ya gama tashi yayi ya fice daga falon nan mami ma ta daura da nata. Daga karshe kuma suka baro part din alhaji baba suka dawo na mami. Kusan awa daya suka kwashe yana bashi baki tare da kwantar mai da hankali yana kuma kara koya mai dabarun yadda zai zauna dasu su biyu ba tare da ya shiga hakkin daya ba, sai da Amir ya tabbatar ya kwantar mai da hankali, daga karshe ya dinga zolayar shi har sai da yaga yayi murmushi, kafin ya barshi, nan sukayi sallama, Amir ya tafi gidan shi yayin da Aslam ya nufi part ɗin mummy, domin duk abin da yake yi karfin hali ne kawai saboda bai San halin da take ciki ba. Koda ya shiga bai ganta ba mummy kawai ya samu a falo, zama yayi suka gaisa ba wani sakin fuska, daga gaisuwar kuwa duk zama sukayi shiru, yana ta zuba idon ganin ta ina zata fito shiru gashi har yana neman kwashe awa ɗaya a zaune, can dai ya da ya gaji, yace "Mummy husnah tana ciki ne ina son tazo mu wuce." A dake tace "eh tana ciki amma yanzu tana barci ka je kawai bayan isha'i sai ka dawo ka dauke ta." Tana gama faɗin haka ta mike tayi ciki domin ta gama abin da ya zaunar da ita a falon. Badan yaso ba dole ya sa kai yabar gidan domin dai mummy bata daukar wargi, balle yadda ranta ke bace yau gaba daya...... Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 126 Kamar yadda daddy ya faɗa karfe biyar na yamma daidai ya sauke zee a farfajiyar gidan Aslam, makulli part ɗinta daya amsa a hannu Aslam ɗazu ya damka mata, har kasa ta tsuguna cike da ladabi tana godiya, yace "Ba komai zainab ɗa na kowa ne, Allah ubangiji ya Baku zaman lafiya da zuri'a ɗayyaba." Ta na tsaye har motar shi ya bar harabar gidan, mai gadi ya maida get ya rufe. mai da kallon ta tayi kan ɗaya plat ɗin da yake nan sak irin nata, ji tayi wasu siraran hawaye sun ziraro mata ko shakka babu nan ne part ɗin Asmah, compound ɗin gidan tabi da kallo tsab tsab dashi yana nan yadda ta sanshi a baya, sai dai a yanzu yafi da kyau sosai nisa ba kusa ba, domin ga dukkan alamau yana samun gyara da kulawa fiye da lokacin da ta ke gidan a baya. Jiki a sanyaye ta ƙarasa gaban na ta part ɗin ta saka makullin da daddy ya ba ta buɗe, sai da ta yi addu'o'i sosai sannan ta kama hannun little suka shiga da sallaman ta a bayyya ne. Falon dumɗum da dubu ba haske kuma ko ina a kukkule, makunnin wuta ta laluba ta kunna take kuwa haske ya gauraye mai falon, bin ko ina ta shiga yi da kallo, take ranar ta, ta karshe a falon ya shiga dawo mata fresh a kwakwalwar ta, ranar da take ta malelekuwa a tsakiyar falon nan jini na kwaran ya daga jikin ta, ranar da Aslam ɗin ta ya saka hannu ya buge ta kamar yana bugun kato tsaran shi, kallon little tayi da yake ta wasan shi, a falon babu damuwar komai a tare da shi, samun kanta tayi da durkushewa a hankali a gurin da take tsaye tare da fashe wa da kuka tunawa d tayi duk abubuwan da suka faru akan zuwan shi doron duniya ne, gashi karshe duk gwagwarmayar da aka sha sai da ya shaki iskan duniya, tayi imani da maganar magaba ta da suke cewa, a duniyar nan babu wanda ya isa ya kashe wani ruhi face sai idan lokacin wannan ruhi yayi, sai dai kawai mutum ya zama sanadi amma badai shi ya kashe shi ba, Allah ne mai kashe wa kuma mai rayawa a duk sanda yaso, shi yake fitar da rayayye cikin matatce haka nan shi yake fitar da matatte cikin rayyaye kamar yadda ya faɗa a cikin alkur,ani mai tsarki. Ta kusa kwashe 30 minutes a haka sai kuka take tana ƙara tunani da miƴa wuya akan lamarin ubangiji, sai da little ya gaji da wasan shi ya dawo ya faɗa jikin ta yana ce mata zai sha ruwa sannan ta dawo hayyacin ta. Ko ina yayi kura a part ɗin tun daga kan falo kitchen dakunan barci toilets da sauran su, gashi kuma yamma yayi, hakan yasa cikin sauri ta kau da duk wani tunani da damuwan ta gefe, cike da himma ta fara gyara falukan ta cikin kankanin lokaci ta ƙalƙale shi fess nan kuma ta koma kitchen shima haka tamai ta goge na goge wa ta wanke na wanke wa, dakin barcin ta ta shiga yana nan yadda ta barshi ga kayayyakin ta nan ba'a kawar da komai ba, toilet ta shiga ta fara wanke wa sannan ta dawo dakin shima, ko kafin ta gama duk wadannan abubuwan magrib ta gaba to alwala ta daura, tayi sallah, sannan ta duba store kayan abincin ta data bari na nan yadda ta barsu komai akwai amma bata jin zata iya cin komai a cikin suu, ga kuma little dake ta dan mata kukan rigima alamar yana jin yunwa, hijjab ta zura tare da dauko kudi ta nufi bakin get, mai gadi na ganin ta cike da mamakin ya shiga gaishe ta, rabon shi da ita tun ranar da ya kira hajiya makofciyar su, suka dauke ta rai a hannun Allah zuwa Asibiti,tun daga ranar kuma bai gani ko jin labarin ta ba, yau kuma koda yaga Alhaji babba ya sauke mace da yaronta ta shiga ciki bai taba tunanin ita bace, yadda ta amsa mishi a mutum ce ba kamar a baya ba da wani bin ma sai taga dama zata daga mishi hannu shi karan kanshi abin ya bashi mamaki, cikin girmamawa da dan jin nauyi ta gabatar mai da bukatar ta nasan ya siyo mata ruwan gora saboda sha, taliya idomie da kayan shayi sai mai dasu magi, da dai sauran abin da zata bukata nan kusa irin su sabulu da amo sannan ya biyar ya mata takeaway a safara foods, ba tare da damuwa ba kuwa ya amsa da to ta kawo ba damuwa, kudi mai yawa ta bashi wanda yafi karfin abin da ta bukata tace harda na napep amma dan Allah yayi sauri saboda yaro. Sai lokacin ya kalli yaron, zaro idanu yayi cike da al'ajabi magana fal bakin shi amma ba daman yi, haka ya tafi aiken yana tafe yana sambatu, to abin ne da daure kai, shidai yasan ance ciki ne a jikin ta a ranar da suka kaita asibiti kuma ya ɓare, yanxu kuma ya ganta da yaro mai kama sak da mai gidan. ~Asmah~ Bacci tayi sosai dan sai bayan la'asar ta farka, mummy kam koda akayi azahar bata tashe ta ba, ta barta ne tayi barcin sosai ko zata samu natsuwar zuciya, sai dai tana yi tana leka ta lokaci lokaci, ganin anyi la'asar bata farka ba yasa ta nufi dakin da nufin ta tashe ta, tayi sallolin dake kanta kuma taci abinci. Tana shiga dakin ta tarad da ita a zaune bakin bed ta dafe kanta alamar tashin ta kenan, itama jin motsin an turo kofar yasa ta dago kai mummy ce, kamar yadda dama ta zata, murmushi mummy ta sakar mata, tare da nufar ta ta taba jikin ta don taji koya zazzabin ya sauka, salam kuwa babu alamar zazzabin, alhmdllh ta furta tare da cewa "sannu Asma'u kin tashi ya karfin jikin kuma." Gyada kai kawai tayi alamar da sauki don ji tayi bakin ta ya mata nauyi, mummy tace "to sannu kinji ki daure ki tashi ki lallaɓa kiyi wanka da ruwan dumi zaki ji daɗi sai kizo kiyi sallolin dake kanki kinji." Nan ma sake gyada kai tayi, tana yunkurin tashi, taimaka mata mummy tayi ta mike a hankali ta nufi toilet din wanka tayi da ruwa dumi kamar yadda mummy ta umarce ta, ta kuwa ji daɗin shi sosai, alwala ta dauro ta fito daure da towel, samu tayi mummy ta ajiye mata abaya mai kyau sabo fil da hijab gashi kuma ta shimfida mata pray mat, ko mai bata shafa ba ta saka rigar bayan ta maida kayan ta na ciki data cire tunda bata da wani a gidan, tana cikin sallah mummy ta shigo dauke da tray da kuloli a kai, ajiyewa tayi a gefe, ta zauna tana jiran ta ta idar. A nutse ta gabatar da sallan ta, bayan ta gama kuwa daga hannun tayi ta shiga kwararo addu'o'i sosai akan lamarin dake tunkaro ta, da kuma rokan allah ya sassauta mata kishi ya bata hakuri da juriyar jure abin da zata fuskan ta a gaba.Tun tana yi a ciki har bata San sanda ta fara yi a bayyane ba, karshe ta fashe da kuka, duk mummy najin ta tana kuma amsawa da amin, a tare suka shafa addu'ar da mummy, tasowa tayi daga kan pray mat din ta iso gaban mummy dake zaune a bakin bed, daura kanta tayi akan cinyar mummy ba tare da tace komai ba, hannu mummy ta daura akan ta, ta shiga shafa mata kai a hankali, sauke ajiyar zuciya ta shiga yi, sun dauki tsawon minti 10 a haka, kafin mummy cikin rarrashi tace "Asma'u ki kwantar da hankalin ki, na fahimci abin da kike tsoro, kar ki saka ma kanki damuwa Aslam yana sonki bazai taba wulakan ta ki ba, idan ma yace zaiyi ninan zan tsaya miki sai inda karfina ya kare, ki kwantar da hankalin ki kinji, in sha Allah kema zaki samu naki ɗan da yardan ubangiji ki cire tsoran komai a ranki kinji." Gyada kai tayi alamar to! Mummy ci gaba tayi da kwantar mata da hankali tana gaya mata maganganun masu sanyi ma zuciya natsuwa. Daga yadda ta nutsu tayi shiru ta daina sauke ajiyar zuciyar da take yi mummy ta fahimci zancen ta na shiga ta sosai, hakan yasa cikin dabara ta shiga kowar da ita dabaru zama da mutanen cikin hikima yadda baza ta cuci kowa ba kuna baza a cuce ta. Kwarai ta samu nutsuwar zuciya sosai daga kalaman mummy, ta samu karfin gwuiwar da ta rasa a ɗazu, zafin da zuciyar ta ke mata da ragu sosai daga kashi talatin cikin dari. A baki mummy ta bata abinci don tasan idan tace ta ci ba ci zata yi ba, duk da haka bata wani ci ba. Bayan sun gama still mummy bata gaji ba ci gaba tayi da koya mata wasu abubuwan da zasu taimake ta a zamantakewar ta na yau da kullum. A massallacin kofar gidan yayi sallan isha'i, ana kuwa idar wa bai ba bata lokaci ba ya shigo cikin gidan a kagare yake daya sanya ta a idanun shi, ya damu matuka da son sanin halin da take ciki, haka kawai zuciyar shi ke bashi tana cen tana kuka, duk da yasan mummy baza ta bar ta tata kuka ba. Koda ya shigo falon mummy ba kowa sai TV dake ta zuba shi kadai, kasa hakuri yayi ya nufi dakin mummy dan yana da tabbacin tana can, da sallama ya tura kofar dakin ya shiga, tana zaune a bakin bed tayi tagumi bata san ma ya shigo ba, ita kadai ce a dakin mummy ta fito ta dauko mata sako, wanda bata San sakon menene ba. Ganin ta a halin tunani yasa da sauri ya karasa gaban ta duƙawa yayi a hankali ya saka hannun shi ya sauke mata tagumin data yi, zuba mishi idanunta tayi da suke nan a ƙorɗe babu kalli ko ɗis gashi sun kumbura sunyi luhu luhu, kallo daya mutum zai san taci kuka yau taba uku lada. Shima idanun nashi ya zuba mata yana kallon ta, take yaji zuciyar shi tayi kunci take yaji wani haushin zee ya kara turnike shi, duk ita ce musabbabin wannan fitinar yana zaman zaman shi ta zo ta jagula mai lissafi, shi wlh da ace shi ta tunkara kai tsaye da amshe ɗanshi zaiyi ya miƙawa husnah kuma bazai taba barin ta ta isa wajen iyayen shi ba balle har su tursasa mishi zama da ita. Cike da tausayawa yace "husnah kuka ko?" Rintse idanun ta tayi saiga wasu sabbabin hawaye sun ziraro, kafin yakai ga kara cewa wani abu mummy tayi sallama, hakan yasa da sauri ya sake mata hannu tare da amsa sallaman mummy,batayi wani mamakin ganin shi a dakin ba domin dama tana tafe tana tunanin kila ya ƙaraso domin kuwa ita tace mai bayan isha'e. Guri ta samu ta zaune take ya shiga gaishe ta amsawa tayi adan sake ba kamar ɗazu ba, duk da dai ba wai ta sake gaba daya bane. Gyara zama tayi tare da cewa "Aslam! Aslam! Aslam!." Ya amsa da "na'am mummy." Tace "sau nawa na kira ka." Yace "sau uku." Tace "dakyau, ga Asma'u na nan zan damka mika ita a hannun ka a yau, koda gigin wasa kada ka kuskaura kace zaka canja mata ko zaka wulakan tamin ita saboda dawowar matar ka uwar ɗanka, nasani ne ku maza kuna da wuyar sha'ani kuma Baku da tabbas shi yasa tun farko nake buga maka warning karka kuskura kar naji kar na gani, domin wallahi! wallahi! wallahi! A wannan karon bazan laminci ka tozar ta min ɗiya akan wata matar ka ba." Cikin tashin hankalin yace "Mummy dan Allah ki dena fadar irin waɗannan kalaman, tsoro suke bani." Daga hannu yayi sama yace "ya Allah kada ka nuna min ranar da zan juyawa husnah ta baya, idan kuma ka kaddara hakan zai faru a rayuwa ta ya Allah na roke ka, ka dauki raina kafin lokacin." Tuna Asmah ta shiga girgiza kai tana hawaye jin abida yake cewa wai Allah ya dauki ranshi, to ita kuwa meye makomar nata ran idan babu nashi ran, domin Aslam shine ran nata ran. Ita kanta mummy sun bala'in bata tausayi har saida ta dauke kwallah a kafaice, ta kima kara tabbatar wa ba karamin so Aslam yake ma Asmah itama Kuma ba karamin so take mishi ba, shiyasa ta ke tsananin kishin shi. Lallai zee ta shiga hakkin su, amma kuma baza suyi jayayya da ikon Allah ba domin Allah kadai yasan abin da yasa ya turo ta cikin su a daidai wannan lokacin ita dai adduar ta shine Allah yasa zuwanta cikin su yazame musu alkhairin duniya da lahira. tana da tabbacin yadda suke son junan su soai haka mawuyacin abu ne aslm ya juya mata baya sai fai idan sun haɗu da shu umancin mace domin dai tasan wasu matan shu,umai ne Kasa ci gaba da faɗin abin da tayi niyyar faɗawa Aslam ɗin tayi, domin idan tace zata yi magana zata iya fashe wa da kuka, mikewa tayi ta mikar da Asmah tsaye ganin haka yasa shima ya mike, mika mata wani babban leda tayi tace "in kinje ki duba na miki bayanin komai a ciki, kuje, ki bishi kuje gida Allah ubangiji ya muku albarka, Allah Kuma ya cika muku burin ku ya baku ƴaƴa masu albarka." Rungume mummy tayi ta fashe da kuka, shi kam Aslam gaba yayi ya bar ɗakin ya dawo falo, domin sauraren kukan ta zai iya saka shi shima ya fashe da kukan a yadda yake jin kukan ta na taba zuciyar shi. Dakyar mummy ta samu ta raba ta da jikin ta, ta kamo hannunta ta zuwa falo tana zuwa ta kama hannun Aslam ta saka mishi hannun ta a ciki tace "kuje Allah ya baku sa'a." Da sauri ta juya ta haye upstairs. Jawo ta yayi ya tallabe ta a jikin shi ta gefe, a haka suka iso parking lot ya buɗe motar shi ya sanya ta a gefen mai zaman banza shima ya zagaya ya shiga gefen direba, ya bar gidan yaso ya kaita tayi sallama dasu Mami da Kuma Alhaji baba da hajiya mama, to yadda yaga yanayin ta yasan hakan bazai yuwu ba, har suka iso gida babu wanda yace ma wani kala a cikin su, zuwa lokacin ta daina kukan sai shehsheka da ajiyar zuciya take sauke wa akai akai. Lokacin da motar su tayi parking a compound ɗin gidan su daga shi har ita idanun su akan part din zee ya sauka, ganin wuta a kunne ko ina ya dauki haske hakan ne ya tabbatar musu da cewa daddy ya cika aikin shi wato ya kawo zee gidan ta a matsayin matar Aslam a karo na biyu kamar yadda ya faɗa...... Allah sarki Mr and Mrs Aslam sabuwar rayuwa muna muku fatan alkhairi nida mutane yana dana ta biyu fans Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu} Page 127 Shi ne ya fara yin karfin halin buɗe murfin motar ya fito, ya zagayo ta gefen da take ya buɗe mata ita ma, cikin matuƙar sanyi jiki ta fito, mayar da ƙofar motar yayi ya rufe, tare da kama hannun ta suka nufi nata part ɗin. A hankali ta saki labulen windon data dan ɗage kaɗan tana kallon su, da baya da baya ta ringa ja har ta isa bakin bed ta zauna dabass, tagumi ta rafka da hannu bibbiyu tayi shiru tana jin zuciyar ta na mata wani irin zafi ga wani ƙululun abu daya tokare mata kirji shi bai sauka ba shi bai hau ba,ba sai ta ba kwakwalwar ta wahala gurin gano ko menene wannan ba, ko bata tambaya ba tasan menene, kishi ne, kishin shi take yi matuƙa gaya, kishi kuwa bana wasa ba, amma ta ɗaukar ma kanta alkawari zata jure zata danne, kodan ta dawo da martabar kanta a idanun shi, domin a yanzu tasan da ita da kashi duk daya suke a wajen shi, take hawaye suka balle mata kamar an buɗe fomfo, little na ganin tana kuka yazo ya rungume ta kamar yadda yaga tana yi mishi idan yana kuka ya shiga rarrashin ta yana cewa "Mummah kiyi shiru ki dena kuka zan siya miki sweet mai tsinke da ice cream." Samun kanta tayi da sakin murmushi jin abin da yake cewa, yaron yana da matukar wayo ga uwa uba surutu duk da ba ko wsni lokaci yake magana ba, idan yayi wani maganar takan yi matuƙar mamaki, sau da yawa takan ce, my boy a ina ka kwaso surutu haka, me sunan ka dai shiru shiru ne. Share wahayen ta tayi tace "OK my boy nayi shiru kaji, oya zo ka kwanta haka dare yayi." Kai ya gyada kawai ɗaukar shi tayi suka haye kan bed ɗin suka kwanta, addu'ar bacci ta shiga karanta mishi yana amsawa kamar yadda take mishi kullum, bayan sun gama ya shiga rero mata surutu, shiru tayi ta rufe idanun ta kamar ta yi barci ganin haka yasa shima yayi shiru take kuwa barci ya kwashe shi. Jin alamar yayi barci yasa ta mike a hankali ta zare jikin ta cikin nashi, bata jin bacci kwata kwata, dan ji tayi idanun ta sun bushe ƙamass Ta dawo gidan Aslam burin ta ya cika kamar yadda take so, sai dai Kuma hankalin ta ya kasa kwanciya kamar yadda ta zata, ta dauka idan yau ta ganta a cikin gidan Aslam a matsayin matar sa a karo na biyu shike nan duk wani damuwar ta ya yaye a she abin ba daga nan take ba, a lokacin da ta ta babbatar Aslam ya auri Asmah bayan bata, bata damu ba domin a wannan lokacin bata wannan take yi ba burin ta kawai Aslam ya amshe ta a karo na biyu, amma yanzu bayan ta samu wannan daman sai wani irin masifaffen kishin Asmah ya turnike ta, sai dai ta daukar wa kanta alkawarin zata yi yaki da zuciyar ta baza ta bari ta saka ta ta aikata aikin dana sani kamar yadda ta sakata ta aika ta a baya, toilet ta nufa dauro alwala tayi tazo ta gabatar da sallan nafila raka'a hudu, bayan ta gama ta dauki kur'ani ta shiga karatu, sosai tayi karatun ta, bayan ta idar kuma ɗaga hannu tayi sama ta shiga kwararo addu'a, duk dai akan Allah yasa Aslam ya yafe mata, Allah kuma ya bata karfin halin jure duk wani abu da zai mata, ya kuma rage mata kishin Asmah a ranta. Ba ita ta tashi ba sai kusan karfe ɗayan dare, koda ta hau gado ta kwanta gaban ta ne ya yanke ya faɗi tuno shin a wani hali iyayen ta ke ciki a yanzu, ta sani dole zasu shiga matsanancin tashin hankali musamman Dad, daga kwancen da take ta shiga yi musu addu'a akan Allah ya basu hakuri da juriyar daukar wannan lamari. Ba ita ta samu barci ba sai kusan karfe ukun dare. A bangaren Aslam da Asmah kam yau suma haka suka kwana, kadaran kadahan, duk da Aslam yayi iya yin shi dan ganin ta saki ranta amma abin ya gagara, ya mata uziri yana ta binta yadda taso, har zuwa safiya bata cikin walwala, ganin yadda duk yabi ya damu sai wani lallaɓa ta yake yi, yasa taji ya bata tausayi dole ta aro walwalan karya ta yafa wa kanta, idan yayi wani abin dan ya saka ta dariya tayi murmushin yaƙe, hakan kuwa ya mai daɗi ganini haka ya samu karfin halin fita office duk da bai daɗe ba sha biyu ya dawo. A haka suka kwashe kwana uku, zuwa lokacin Asmah ta sake sosai ganin ko kaɗan Aslam bai canza mata ba sai ma wani ƙarin kulawa da tattali na musamman da yake nuna mata, tuni ta ajiye batun wani kishi da wata zee suka bude sabon shafin soyayya, kuma har tsawon wannan kwanakin daga ita har Aslam din babu wanda ya saka zee da little a idanun shi, Asmah tana sane da hakan don lokaci lokaci sukan faɗo mata a rai, sai dai tana tsoron ta saka musu baki dan tana gani wannan tsakanin su ne matsalar su ce su ta shafa, kullum Aslam na part ɗinta bai taba cewa zaije wajen su ba, yadda ma yake yi kamar ya manta da wasu halitta a gidan, itama bata ce yaje ba, sai dai fa a can ƙasan zuciyoyin su tunani da kewar little ya hana su sakat, so ɗaya ta taɓa saka yaron a idanun ta amma ya kama zuciyar ta fiyye da yadda bata yi zato ba, shima Aslam ɗin haka kullum da tunanin yaron yake kwana yake wuni sai dai yaki zuwa gareshi saboda wani dalili da shi kadai ya bar wa kan shi sani, amma fa daure wa kawai yake yi. A bangaren zee kam duk fitar shi da shigar shi akan idanun ta, takan kwana kuka kamar hawayen ta zasu kare, little yayi ta rarrashin ta idan taki yin shiru shima sai ya fashe da kuka, daga karshe ta yanke shawaran da take ganin shine zai ɓullar da ita kan hanya, zatayi amfani da nata kalar hikimar ta karkato da hankalin mijin ta gare ta, bada tsiya koda tashin hankali ba, domin idan wannan tace zata yi a halin yanzu ita ce baza taci riba ba, dan ta riga ta sadakar Asmah ta sha gaban ta, ta ko wanne fanni. Yau da ta kama kwana biyar da dawowar ta gidan komai na ɗan kayan abincin da ta aiki megadi ya siyo mata sun kare hakan ya saka bayan tayi wanka sun karya ita da little ta laɓe a abakin window kamar yadda ta saba, tana kallo har Aslam ya bar gidan, yana fita kuwa ta zaro galenta ta riko hannun ɗanta suka fito so take ta sake aikar megadi ya kara siyo mata kayan abinci. Daidai sunzo kofar part din Asmah, ita kuma ta buɗe kafar ta fito hannun ta dauke da kwandon shara da alama shiya fito da ita dan ta juye a babban drum dake waje, turuss suka ja birki dukan su suna bin juna da kallo, zee ce tace ta kawar da kallon ta hanyar sakar mata wani irin kyakkyawan murmushi, tana ƙarasowa wajen ta tace "manya idanun ku kenan, kun shige ciki shiru ba ajin ko motsin ku, to yau dai gashi mun haɗu ina kwana ya gajiya ya zaman shiru." Sororo ta tsaya can kuma ita ma ta sakar mata murmushin yaƙe tace "ina kwana." Kama basken ɗin sharan zee tayi tace bari na taya ki zubar wa, saboda tsabar mamaki bata San ta sakar mata kwandon ba. Zee na tafiya ta mai da idon ta kan little da ke tsaye yana kallon ta, wani irin sanyi taji a zuciyar ta ta wahalu da kewar yaron, tsugunawa tayi ta maida tsawan ta dai dai nashi tace " zo my boy." Ta faɗa tana mika mishi hannu, sai da ya kare mata kallo sannan a hankali ya isa gare ta samun kanta tayi da saka shi a jikin ta ta rungume tsam, tana sauke ajiyar zuciya, zee data gama juye sharan kamar ance ta juyo, idanunta ya sauka akan abin da ke faruwa, da sauri ta dauke kanta tana sakin murmushi, abin ya burge ta lallai yarinyar bata da damuwa da alama. Gurin megadi ta ƙarasa ta bashi saƙon daya fito da ita koda ta juyo samun su tayi a gurin suna fira little sai dariya yake yi ko me take ce mishi oho. Tana isowa tace "iyyee mummy and son anata fira to me ake cewa nima a gaya min." Dagowa tayi wannan karon da murmushi gaske bana yaƙe ba ta kalle ta, taji daɗin yadda zee ta kira ta da sunan mummyn yaron, tace "sannu anty zee nagode." Zee tace."Ba komai anty Asmah." Sai kawai suka kwashe da dariya kamar sun saba da juna, zee tace "bari mu karasa ciki." Ta faɗa tana kamo hannun little maƙe kàfada yayi tare da lafewa a jikin Asmah duk dariya suka suka mai zee tace"iyee lallai yaro yaga mummyn shi na asali, to bari na barka a gurin ta zuwa anjima." Ta fada tana kallon Asmah, cikin jin dadi Asmah tace "ai kuwa nagode na samu dan taya hira." Cikin dariya zee tace "kin samu dan saka surutu dai." Kallon shi tayi tace "wai haka my son." Make kafaɗa yayi, zee tace "ai dama bazai ce eh ba sai kunje zaki gane nufi na, nidai nayi nan." Ta fada tana wucewa part din ta, Asmah ma daukar shi tayi suka shige nata part din. Ranar tayi wunin farin ciki sai wasa take mai ta dafa mai indomie ta bashi a baki ta bashi wannan ta bashi wancen karshe har ya gaji yayi barci ta kaishi dakin ta ta kwantar, har yamma yana gurin ta, gashi ranar Aslam bai dawo da wuri ba, dan tun 2 take ta zuba ido shiru, wanka ta mishi itama tayi da yamma taci kwalliyar ta bata da kayan yara don haka tace bari taje ta amso gurin zee, koda ta fito falo ta samu ana knocking da sauri ta karasa ta bude duk a tunanin ta Aslam ne duk da bata ji diran motar shi ba, sai dai ga mamakin ta zee ta gani a bakin kofar murmushi suka sakar wa juna, Asmah tace "laa anty zee dama gurin ki nake shirin zuwa yanzu na amsar wa my son kaya sai kuma gaki shigo daga ciki mana kin tsaya a waje." Ta fada tana kauce wa ta bata hanya, zee tace "A'a anty Asmah ba sai na shigo ba naga yamma yayi nace bari na zo na dauke shi, Allah yasa dai bai miki rigima ba." "Ba wani rigiman da yayi min wasan shi ya dinga yi, yaron yana da saurin sabo ai." "Hmmm make dai kawai yayi ma haka, nima nayi mamaki sosai yadda ya aminta da ke lokaci daya yaron dake da shegen kyuyan tsiya." Murmushi tayi tace"Ki shigo mana anty zee." Zee tace "kin dai dage kar mai gidan yazo ya same ni." Dariya ta kwashe dashi tace "kaji anty zee dai to sai me idan ya ganki a nan ɗin ai abin da yayi kara shi yayi ciyawa." Zama tayi tana ƙarewa falon Asmah kallo, masha Allah komai yaji dan babu abin da nata zai nuna ma wannan ɗin ita sai take ga kamar wannan ɗin ma yafi nata tsaruwa, ruwa da darinks ta gabatar mata, sannan ta zo ta zauna, kan kace kobo fira ya barke a tsakanin su, kamar wasu wadan da suka daɗe da sanin juna, duk rabin firan dai a kan little ne, hankalin su ya tafi har basu ji Duran motar Aslam ba sai karan doorbell suka ji, gaban zee ne ya yanke ya fadi, take ta zazzaro ido waje kamar wata mara gaskiya, yayin da Asmah ta saki wani kayataccen murmushi, mikewa tayi da sauri ta nufi kofar fuskar ta dauke da madaukakin farin ciki. Tana bude kofar ya shigo baiko lura da su zee ba ya jawota ya rungume, lumshe idanu yayi yana sauke ajiyar zuciya kicin kicin kwacewar data shiga yi ne yasa shi saurin bude ido jin wani sabon abu yau, kasancewar shike facing cikin falon hakan yasa idanun shi suka sauka akan little kafin ya gama tunanin wani abu kuma ya hango zee zaune tayi kasa da kanta, sake ta yayi tare da hade rai yayi kicin kicin kamar bai taba dariya ba, duk walwala da anashuwar daya shigo dashi kan fuskarta shi take ta bace fat, ita kanta Asmah sai da ta firgita gani yadda ya juye lokaci guda, raɓa ta yayi ya haye sama abin shi ya bar ta anan sake da baki. Tunda ta ji dirar mota hankalin ta ya bata shine ya dawo, cike da dauki na san ganin kyakkyawar fuskar shi ta dago kai tana kallon kofar sai dai abin da ta gani ya matukar dukar zuciyar ta, har sai da taji kamar zuciyar ta zai zillo kasa ya faɗo, da sauri ta dukar da kanta ta shiga kokarin komawa da zuciyar ta, tana maimai ta innalillahi wainnailaihi rajiun, kallon ta Asmah tayi, gaskiya taji babu dadi don ko ita ne baza taji dadi ba duk da dai baisan suna falon ba, kuma ji yadda ya wuce kamar bai ganta ba, kawai sai taji zee ta bata tausayi, nufar ta tayi tana kirkiran murmushi tana magana ta shiga ta mata amma bata san tana yi ba da alama tayi nisa sosai cikin tunani sai da ta ce "Anty zee!" Da karfi sannan tayi firgigit ta dago ganin ta yasa ta saki murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo amma fa na ciki na ciki. Tace " kin gani ba kin tsai dani gashi oga ya zo ya tarad dani gaskiya naji kunya kuma duk laifin kine." Ta fada tana mike wa da nufin daukar little su tafi sai dai ga mamakin su wayam ba yaro ba dalilin shi, zaro idon da tayi ne yasa Asmah saurin juyawa, itama abin ya daure mata kai to ina little din yake, abu kamar almara babu shi a falon babu alamar shi, Asmah tace ina zuwa ko yabi "honey sama ne." Da sauri ta haura tabar zee nan gaban ta na faduwa. Samun shi tayi zaune a bakin bed ya rage kayan jikin shi ya bar dogon wandon suit da singlet little na kamkame a kirgin shi ya rungume yaron kamar zai mai da shi jikin shi, sauke ajiyar zuciya tayi ganin yaron a nan, fitowa tayi da sauri dan ta gaya wa zee ga ya cen gurin Aslam sai dai ga mamakin ta wayam taga falon, ko shakka babu ta wuce, wannan abu bai mata dadi ba gaskiya, zama tayi na kusan mintin goma tana tunane tanane lamarin Aslam ya mugun daure mata kai, yana son danta amma yace ita baya son ta to ko shakka babu wagga batu karya ce , jiki a sanyaye ta mike ta nufi upstairs tun kafin ta tura kofar dakin ta ringa jiyo dariyar shi shida yaron kamar zasu tada dakin, da sauri ta karasa ciki a kan gado ta hango su Aslam na kwance ya daura little akan kafarshi ya daga shi sama yana mishi lilo shi kuma yana ta kwasan dariya, ikon Allah tace a ranta, wannan lamarin da daure kai yake. Karasa wa ciki tayi ya dago yana kallon ta, rasa abin cewa yasa tace "sannu da dawowa." Sauke little yayi ya mike zaune yace mata "me ya kawo ta part din nan." Tace "kamar yaya." Hararan wasa ya watsa mata tare da cewa "kamar yayo." Dariya ta kwashe da shi tace "hira tazo muyi ko haramun ne kishiyoyi suyi hira a tare." Yace "bazan hana ki ba amma wlh kibi a hankali dan da kike ganin ta haka shalau shalau ba kanwar lasa bace." Dariya ya bata wai shalau shalau ta kuwa dara sosai tare da cewa " kai dai ka sani, koma ya take ai dai zabin ka ce, kuma sai na gaya mata." "Kin daɗe." Ya fada yana mikewa "muje ni da Allah ki bani abinci naci na kwaso yunwa da gajiyar aiki." Ranar dai a part dinsu little ya wuni, a tsakanin su sai ji dashi suke yi suna wasa dashi, cikin kankanin lokaci yaron ya saba dasu, ko tunanin su maida mata ɗanta basu yi ba har gurin karfe taran dare, Asmah ce tayi hankalin cewa "Baza mu mayar mata da shi ba, kaga dare yayi kuma ita kaidai ce a part din ta nasan tana cen tana jira." Share ta yayi, sai da ta sake maimai tawa sannan ya kalle ta yace "A nan zai kwana." Bata rai yayi ya mike tare da daukar little suka wuce sama dan ma kar ta samu daman yi mai wani magana, baya jin zai iya rabuwa da yaron koda na minti daya ne ba tare da wani kwakwarar dalili ba, zama tayi tayi shiru tana tunani, gaskiya basu kyauta wa zee ba idan suka yi haka, to amma ya ta iya, yanzu yanda ya haɗe ran nan tana magana cibi zai zama kari, a tsakiyar su yaron ya kwana ranan dan tsabar gata. A bangaren zee kuwa hakan bai dame ta ba, sai ma dadi da ya mata, domin duk wanda ke kaunar danka ai masoyin ka ne, ko iya haka suka tsaya wlh sun nuna mata soyayya, a bangare daya kuma abin da ya faru dazu yana tsungulin ta a rai, sai dai tana danne wa , duk yadda sheɗan yaso yasa ta taga bakin Asmah taƙi yarda duk yadda zuciya ta hasaso mata sai ta kauce, ta daukar ma kanta alkawari tun da Asmah bata nuna mata wani mugun hali ba to kuwa ita baza ta nuna mata komai ba zata jata a jikin ta su zama kamar yan uwa hakan ma wani mata ki ne da zata samu kusanci da burin ranta. Washe gari daker ya tafi aiki karshe ma cewa yayi zai tafi da yaron, daka tsallen albarka tayi ta hana, dan tasan idan har ta kuskura ta bashi wannan daman so daya ya dinga yi kenan kuma bazai maida hankali kan aikin shi ba. Yana tafiya ta dauke shi suka tafi part din zee dama sun riga sunyi wankan su sun karya. Da fara'a ta tare su babu alamun damuwa a fuskar ta, bayan sun gaisa Asmah tace "sai kika jimu shiru jiya ko." Murmushi tayi tace "ba komai ai yaro ya koma wajen Asalin mummy shi." Hakan data fada yama Asmah dadi take ita ma ta fara bata labarin yadda Aslam ya karbi yaron da yadda ya dinga mai harda cewa da yayi zai tafi dashi office, dariya zee ta ringa yi zuciyar ta wasai, Asmah ta bata wannan labarin ne dan ta faran ta mata rai kuma ta kwantar mata da hankali , aiko dai kwalliya ta biyu kudin sabulu, ranar a part din zee ta wuni tuni wani irin sabo da shaƙuwa ya shiga tsakanin su kamar ba kishiyoyi ba tare sukayi girki anan Asmah taga basu da kayan abinci sai wanda ta siya ta kuma kudiri aniyar yiwa Aslam magana, sai gurin karfe ukun rana ta koma shiyar ta ta daura ma Aslam girki, tuwon shinkafa tayi lafiyayye kuma gaba daya ta girka harda zee, tako ji dadi ta amsa tana ta mata godiya. Cikin abinda baifi sati daya ba sun gama fahimtar juna, duk da kowacce zuciyar ta cunkushe yake da kishi musammam ma zee dan ita Asmah har yanzu bata San dawan garin ba tunda kullum tana tare da miji, zee na matuaƙar kokarin danne wa amma fa kullum Daren duniya sai tasha kuka ta gode Allah, Aslam gaba daya bata gaban shi kasancewar yanzu tana yawan zuwa part din Asmah dan tare ma suke hada dinner kullum duk idan ranar tayi rashin sa'a suka hadu takan gaishe shi, a dake yake amsa mata kuma kallo daya yake mata babu kari wannan abin shi yafi komai kona mata rai, bata da matsala ko kaɗan da Asmah sai wanda ba'aka rasa ba, little kam zuwa yanzu ya zama mai uwaye biyu yau ya kwana a nan gobe ya kwana a nan duk dai inda yaga dama. Yau ma kamar kullum tare suka gama haɗa dinner, sunayi suna hira, Asmah ce ta fara kawo zancen Aslam cikin firan nasu, da sauri zee ta kauda maganar ta canza wata hiran Asmah ta lura sau da yawa haka take mata da ta dauko zancen Aslam zata doje, tausayi take bata sosai na yadda Aslam ya wofintar da ita, sau da yawa takan auna kanta a matsayin zee taga idan ita ake wa haka zata iya jura kuwa, duk sanda tayi wannan tunanin takan jinjina wa zee da hannu bibbiyu. Bayan sun kammala hada mata nata a basket Asmah tayi kamar yadda take yi kullum, dauka tayi ta tashi dan lokacin dawowar Aslam yayi daf, cikin tsokana tace ma little "muje." noƙe kafada yayi alamar bazai bita ba dariya suka zaka mai tace "dama tsokanar nake yi zaman ka wurin mummyn ka." Har takai kofa yace "Mummah." Ta juyo yace "kar kiyi kuka yau kinji." Kallon juna sukayi da Asmah, Asmah tace "kuka kuma?" Murmushin yaƙe tayi tace "shirmen little ne kawai rabu dashi." Tana gama fadin haka ta sa kai tabar part. Kuka kuka haka tayi ta maimaita kalman, tabbas yaro baya karya, to meke saka ta kuka ne, da sauri ta kalli little dake ta wasan shi tace "my boy Mummah ka na kuka kace." Yace "eh mana mummy kullum sai tayi kuka da daddare, ta ringa cewa Allah ya dawo mata da hankalin mijin ta,Allah yasa ya yafe mata, zuciyar ta zata fashe." Zama tayi dabass tana maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun, lallai suna shiaga hakkin zee, baiwar Allah a she tana cikin damuwa har haka amma ko a fuska bata taba nunawa ba, kila ma tana jin haushin ta , kila ma ta ringa ganin kamar ita ta hana Aslam dawowa gare ta, tasan ba abinda baza ta ayya na ba tun da dai ita zuciya ai bata da ƙashi lallai Aslam yau ya dawo zata same shi suyi magana ta fahimtar juna. Bayan sunyi shirin kwanciya yana zaune bakin bed yana wasa da little, zuwa tayi ta zauna a gefen shi, ta kalli little tace "my boy." Yace "na'am." Tace mema "Mummah ka ke cewa kullum idan tana kuka." Cike da rashin wayau yaron ya shiga jero wa harda wadan da bai fada dazu ba, kallon kallo suka shiga yi a tsakanin su, tace "to kaji daga bakin da bai san karya ba." Shiru yayi baice mata komai ba shi karan kanshi yasan abin da yake yi bai kyautu ba, amma bawai dan wani manufa yayi haka ba gwada ta yake yi yaga shin da gaske tayi hankalin kamar yadda ta sanar ko a'a kuma alhmdllh ya samu gamsuwa sosai da tuban nata, ya tabbatar tayi taubatan nasuhan kamar yadda ta fala kuma shima yana shirin ya koma gare ta amma shakkar Asmah yake yi, yana so ya koma gare ta,kodan fita haƙƙin ta,duk da dai har yanzu bawai yana jinta a ranshi bane kamar yadda yake jin Asmah, sai dai ya bata wani matsayi mai girma a ranshi ko ba komai ta ciri tuta domin ta kawo mishi farin cikin ruhin shi wato little...... Oum Ummeetarh 07041130088t 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALDO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu.} Page 128 Ganin yayi shiru ya tsaya yana kallon ta alamar ya faɗa tunani, yasa tace "dan Allah ya Aslam duk abin da zaka yanke ya zama adalci, kada ka dube ni ko wani, ubangiji zaka duba ka dubu haƙƙin ta dake wuyan ka, tana zaune ne a gidan saboda kai saboda soyayyar da take maka, nasan tayi maka laifi mai girma kuma alhmdllh daga baya ta gane kurenta ta nemi yafiya, dan Allah da manzon sa ka yafe mata haka, taci koda albarkacin little ne da ta haifa maka, ka duba halaccin da ta maka, ta rainar maka cikin da ka cire rai dashi a jikin ta na tsawon watanni tara ta haife shi ba tare da sanin ka ba, ta shayar da shi ta raine shi, duk baka da masaniya ta kawo shi gareka a lokacin da kake tsananin bukatar shi, anty zee tana kaunar ka ya Aslam dan Allah ka tashi kaje gare ta ka share mata hawayen ta." Tsura mata idanun yana kallon ta har kai karshen zancen ta, ganin bai amsa ta ba,yasa ta mike ta isa gaban shi ta kama hannun shi ta shiga janshi da niyyar ta miƙar dashi tsaye, kasa wa tayi dan bai bata wannan daman ba, sai ma shi daya jawo ta ta faɗo jikin shi, dago da kanta yayi suna kallon cikin idanun juna, a hankali ya furta "ba kya kishi na ko husnah, kin dena sona ko?" Da sauri ta shiga girgiza mai kai cikin rawar murya tace "wlh ina son ka ya Aslam kuma ina tsananin kishin ka, son da nake maka ne yasa nake kwadaitar da kai kayi adalci a tsakanin matan ka domin bana so ka tashi da shanyayyen rabin jiki ranar gobe." Tana magana hawaye na taran mata a ido kamar kar ya ambaci kishi, ai sai taji hankalin ta ya fara tashi, ƙokarin mayar da hawayen ta ta shiga yi dan bata so ta basu daman da zasu zuba dan idan tayi haka zata karya mai zuciya ne har ya kasa tafiya wajen zee ɗin. Yace " zaki iya kwana ba tare dani a gefen ki ba." Karfin gyada mai kai tayi alamar eh, girgiza kai yayi yace " To ni banajin zan iya kwana ɗaya ba tare dake a gafe na ba." Da sauri tace "zaka iya dole zaka yi tunda haka Allah ya riga ya rubuto maka a cikin shafin kaddarar rayuwar ka, kullum kakan ce min na roke ka ko meye a duniya idan kana da halin shi zaka min, to yau gashi ina rokon ka dan Allah kaje wajen anty zee jiki na yana bani tana cen tana kukan rashin ka." Sauke ajiyar zuciya yayi kafin yace "Zanje gareta saboda ke da kuma little, amma bawai dan wani abu ba, zata ci darajar ku da kuma darajar su daddy sai kuma darajar igiyar aure." Murmushin yaƙe ta saki wanda yafi kuka ciwo jin hawaye na shirin ziraro mata yasa tayi saurin shigewa jikin shi ta boye fuskar ta a kirjin shi yadda bazai gane yanayin da take ciki ba, sun jima a haka, ganin baida niyar tashi yasa ita ta fara zare jikin ta sannan ta kama hannun shi dan tayar dashi a karo na biyu wannan karon bai hana ba miƙewa yayi jallabiyar shi ta mika mishi ya daura akan ƙananan kayan jikin shi, riƙo hannun shi tayi ya fara janshi jiki a sanyaye ya biyo ta ji yake kamar ya fasa tafiya, har bakin ƙofar falo ta rako shi sake mishi hannu tayi ta coge daga nan kallon ta yayi, ta sakar mishi murmushi, yace "muje mana." Ta girgiza kai, tare da komawa bakin falon daga ciki ta tsaya, kallon ta yake yi,itama daga bakin kofar da take tsaye ta zuba mishi idannu tana kallon shi fuskar ta dauke da murmushin karfin hali tana hannu ta shiga ɗaga mashi alamar bye bye, ganin bai tafi ba yasa tace "ka tafi mana honey." Girgiza kai yayi yace "kedai ki fara tafiya." Maƙe kafaɗa tayi tace "naƙi." Yace "zan dawo fa." Bubbuga kafa ta shiga yi tare da saka mishi kukan shagwaɓa, ganin haka yasa yace "to ya isa naji bari na tafi." Ya fada yana juyawa domin tafiya har yayi taku biyu tace "baka ji ba." Ya juyo tace "ina son a samo mini baby yau dan Allah." Gadan gadan ya nufo ta ganin haka yasa ta shige da gudu tare da banko kofar ta murza key, murmushi yayi sannan ya juya ya nufi part ɗin zee zuciyar shi babu daɗi. Jingina bayan ta da jikin kofar tayi tana sauke wasu irin ajiyar zuciya a jejjere, duk abin da take yi karfin hali ne, kawai amma zuciyar jin shi take kamar tayi bindiga. Jiki ba kwariya ƙarasa kofar part ɗin zee har zai danna doorbell sai kuma ya gwada murɗa handle din kofar, cikin sa'a kofar ta buɗe shiga yayi da sallama ciki ciki, sai dai ga yadda ya zata bata falon, ga dai komai a kunne harda su TV,bin falon ya shiga yi da kallo, rabon shi da shigowa falon nan har ya manta, zama yayi yana jiran fitowar ta , shiru har yana Neman kwashe minti 30, hakan yasa ya tashi ya nufi bed room ɗin ta, tun kan ya karasa yake ta jiyo sautun kukun ta tare da shesheka mai karfi, da sauri ya karasa dan ji yayi babu daɗi a zuciyar shi, yana shiga ya hangota durƙushe a bakin bed ta kifa kanta a bed sai kuka takeyi bata san ma ya shigo ba,cikin wani irin murya mai cike da tsananin tausayawa yace "zainab!" Cak ta tsayar da kukan ta kamar an kashe engine, tabbas taji muryar kuma taji kiran, amma bata gaskata ba, ganin haka yasa ya sake maimaita ta kiran "zainab." A hankali ta fara juyo da kanta kaɗan kaɗan zuwa inda ta juyo sautin muryar, jajayen idanun ta da suka rine tsabar kuka ta sauke a cikin nashi, cike da tsantsar mamaki take kallon shi yayin da shi kuma yake bin ta da kallon tsananin tausayi, fuskar ta gaja gaja da hawaye , sai ajiyar zuciya take saukewa, ta kasa dauke idanunta akan shi shima a nashi bangaren haka ne, ji yayi wani abu na tsungulin shi a zuciya, a hankali ya fara taka sawayen shi yana nufar ta, tsoro taji ya lulluɓe ta dan bata san da wanne yazo ba, sai dai ga mamakin ta tsugunawa yayi ya ɗago ta ya miƙar da ita tsaye tare da bata wani irin kyakkyawan runguma, jinta yau a jikin Aslam ɗin ta yasa taji kamar ba'a duniaya take ba, wani irin kuka ne mai masifar karfi ya kufce ce mata cikin kuka ta shiga cewa "Aslam ka yafe min wlh ina kaunar ka, na tuba nabi Allah nabi ka kayi hakuri." Bubbuga bayan ta ya shiga yi alamar rarrashi, ganin taki yin shiru yasa ya buɗe baki yace "ya isa haka my love ki daina kuka na yafe miki, karki sake kwatan ta abubuwan da kikayi a baya kinji."gyada kai tayi, tare da kara yin lamo a jikin shi, sai sauke ajiyar zuciya take yi akai akai, ganin tayi shiru yasa ya dago fuskar ta kallon cikin idanun juna suka yi, take ya sakar mata wani irin kyakkyawan murmushi, wanda yasa ta shagala da kallon shi, ganin haka yasa ya hura mata iskar bakin shi a fuska cikin raɗa yace "na canja ne." Samun kanta tayi da sakin murmushi tace "sosai ma, anty Asmah ta iya kiwo." Jim ta ambaci sunan ta sai da yadan tsaya yayi jim, gudun kar ta zargi wani abu yasa yace "Really." Tace "uhumm." Sai kuma ya saki wani murmushi mai sauti, Jan ta yayi suka nufi bed zaunar da ita yayi shima ya zauna a gefen ta ya kamo hannayenta ya rike cikin nashi, zura mata idanu yayi yana karewa fuskar ta kallo sai yau yake mata cikakken kallo mai sunan kallo tun bayan dawowar ta gare shi. Tana nan a zee babyn ta, babu abinda ya canja sai dai yaga tadan rame mishi kadan a ido. Ganin kallon da yake mata yayi yawa yasa tace "kana kallon duk yadda na tsofe ko, soyayyar ka da ɗanka ne suka mai dani haka." Murmushi yayi yace "waye yace kin tsofe gaki kamar bake kika haifi boy ba sai naga kin ƙara min yarinta sosai, kamar wata yar 15." Dariya ta kwashe dashi wanda tà dade bata yi irin shi ba, tsura mata ido yayi yana kallon ta, yana jin wani abu na sukar zuciyar shi game da ita. Ranar sun raya wannan daren sosai cike da ɗokin juna,sun sha soyayya kamar su kadai je a duniya, lokacin da yaji shi rungume da zee samun kanshi yayi da jin kunyar asmah sai yake ga kamar bai kyauta mata ba duk da ita ta bashi dama, Aslam ya tausaya ma zee sosai ya kuma tabbatar ba ƙaramin kaunar shi take yi ba, take yaji a ranshi bai kyauta mata abin da ya mata, sai dai kuma a wani bangare na zuciyar shi sai mamaki yake yi, lallai ya tabbatar da zancen hausawa da suke cewa mata suna suka tara, sun sha romanace zafafa, wanda shi karan kanshi yasam yayi missing dinsu, domin ba karya zee gwana ce sosai a wajen romance sai dai kuma lamarin ya canza lokacin da ya shige ta, salam yaji kamar gari ba sugar, haka dai ya daure ya bar abin a ranshi ko a fuska bai nuna mata komai ba. A bangaren Asmah kam ranar bata iya barci ba sai juyi kawai takeyi a makeken gadonta, tana yi tana zirarar da hawaye, zuciyarta na hasaso mata ga ya Aslam ɗinta cen da zee suna soyayya, tayi kuka kamar me har sai da tayi dana sanin tura shi gurin zee ji tayi dama ta kyale shi kawai duk ranar daya ga dama yaje gare ta, haka zuciya tai ta hasaso mata mugayen abubuwa, har da kudirin cewa baza ta sake bari Aslam ya je gurin zee ba idanunta sun rufe kishi kawai ke kwakwular zuciyar ta, cikin ikon Allah kamar daga sama taji wani bangare na zuciyar ta na cewa, me kike yi haka kuma Asma'u? So kike ki kwashe ladar ki a wajen Allah maza kiyi istigfari, samun kanta tayi da cewa astagfirullah a baiyane, kamar kuma an tsungule ta, ta diro daga kan bed din ta fada toilet ta dauro alwala, nafila ta gabatar sannan ta shiga addu'o'i daga karshe ta dauki kur'anin ta ta shiga karan tawa a nan gurin barci ya kwashe ta mai cike da daddadan mafarki wai tana dauke da juna biyu. Da a suban fari ta farka take mafarkin da tayi ya shiga dawo mata dalla dalla, daga hannu tayi sama tace "ya Allah ka tabbatar da wannan mafarkin nawa kasa wata rana ya zama zahiri ba mafarki ba." Sakayau ta farka zafin da zuciyar ta ke mata na kishin zee ya ragu sosai sai ɗan burbushi wanda baza a rasa ba. Bayan ta gabatar da salla wanka tayi ta shiga gyara gidan ta bayan ta gama kuma ta shiga kitchen ta haɗa breakfast bata haɗa da Aslam ba, sanin cewa yana gurin zee iya ita da boy kawai ta haɗa suka ci abinsu suka koshi ta dawo falo ta zauna zaman jiran shigowar Aslam dan wlh kewar shi take kamar ta bishi take ji, tana yi tana kallon agogo har karfe takwas babu shi babu alamar shi, take taji ranta yana so ya ɓaci, cikin taimakon Allah harshen ta ya shiga karanto innalillahi wainnailaihi rajiun, tana nan dai zaune a falo karfe Tara da minti goma dai dai taji an danna doorbell, da rawan jikin ta, tashi ya shiga buɗe ƙofa sai dai abin da ta gani ya kusa tarwatsa zuciyar ta... Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book ɗin ga duk waccce ta rasa mahaifiya allaha kajiƙan iyayen mu} Page 129 Aslam da zee ta gani tsaye a bakin ƙofar hannunwan su sarƙe dana juna, fuskar su dauke da wani irin annuri kai da ka musu kallo ɗaya kasan suna cikin madaukakin farin ciki, a tare suka sakar mata murmushi, hakan yasa tayi karfin danne ƙululun daya taso mata ya tokare mata zuciya, ta mayar musu da martanin murmushin da suke mata, idanu ya tsura wa fuskar ta yana karantar yanayin ta, ji yayi babu daɗi a zuciyar shi, take duk wani farin ciki da annashuwar da yake ciki ya fara gushe wa, hanya ta basu suka shigo zama zee tayi a falo shi kuma ya haura upstair, ita ma zama tayi a kujeran dake fuskantar na zee, zee ce ta fara gaishe ta, fuskar ta a sake ta amsa mata suka gaisa cike da mutunta juna, Asmah har da karfin halin tsokanar zee, ita kam zee sai murmushi take mata ba tare da ta tanka mata ba. Kasa zama yayi koda ya isa ɗakin shi, daga yadda yaga yanayin idanun ta yasan tayi kuka, dama shi yayi mamakin karfin halin ta, yayi mamaki yadda ta nuna ya tafi wurin zee ba tare da wani alamun kishi ko wani damuwa a fuskar ta ba, har sai da yaji abin a ranshi dan a tunanin shi ta daina son shi ne, ko kuma soyayyar shi ya ragu a zuciyar ta, baiwar Allah ashe jira take ya tafi ta yi kuka Allah ka ɗai yasan halin data kasance a daren jiya, gaskiya ya jinjina ma kokarinta, a wannan marran ba ko wace mace bace zata iya aikata abin da ta aika ta sai yar baiwa kamar dai ita, ji yayi so da kaunar ta sun ninku a zuciyar shi sannan ga wani irin matsayin da girma data ƙara a idanun shi, uwa uba kuma wani irin tausayin ta daya lulluɓe shi, Allah Allah yake su kebe ya rarrashe ta ya kwantar mata da hankali. Hira suka shiga yi kamar yadda suka saba, fuskar kowacce su a sake, sai dai fa a karkashin zuciyoyin su kowacce da abin da take ji game da yar uwar ta, tana sane tayi banza da shi ta share shi bata je gare shi ba, shikuma yana can yana ta faman jiran ta, ganin bata da niyar zuwa yasa ya lalubi number ta ya kira, wayar ta dake kan hannun kujeran da zee ke zaune ne ya fara kiɗa, da jin ringing din tasan shine domin kuwa ringing ɗin shi na musamman ne a awayar ta,dukan su kallon wayar suka yi zee da yake tafi kusa da wayar yasa idanun sa suka sauka akan sunan da ta saka mishi, honey boo💕 sai da gaban ta ya ɗan faɗi amma a fuskar ta bata nuna komai ba sai ma murmushi da ta sake tare da cewa "kaiii! anty Asmah kin share honey boo ɗin ki gashi ya gaji da jira yana kira fa." Ta faɗa tana miki mata wayar, kamar kar ta karɓa amma ta daure ta karɓan tare da ɗagawa ta kara a kunne "ki same ni a ɗaki na." Shine kawai abin da ya faɗa a dake dan karma ta kawo mai wargi, kallon juna suka yi da zee suka sakar wa juna murmushi "Bari na tafi tun kan oga yazo yayi ƙasa ƙasa dani, yace ni ce na tsare mishi ke." Hararan wasa Asmah ta mata tare da cewa "kaji anty zee dai da wani zance." Cikin dariya tace "wani zance ko gaskiya." Miƙa wa little hannu tayi alamar yazo suje cikin sa'a kuwa ya je gare ta alamar zai bita, daukar shi tayi sukayi hanyar ƙofa tana cewa "to anty Asmah bari naje na ɗan kwanta wlh barci nake ji sai anjima." Bada wani manufa ta fadi wannan maganar ba har ga Allah, don da tasan yadda Asmah zata fassara shi da bata fada ba,Kamar saukar aradu haka maganar zee ya doki zuciyar ta, take jikin ta yayi wani irin sanyi kalau kasa tashi tayi ta mata rakiya kamar yadda ta saba, me take nufi da zata dan kwanta barci ma take ji? Zuciyar ta ta bata amsa da cewa jiya da dare bata samu barci ba kenan suna tare da ya Aslam ɗin ki yana mata abin da yake miki, hawayen tausayin kanta ne suka ziraro mata, shike nan yau ya tabbata ta raba Aslam din ta da wata macen duniya abinda in da wani ne ya bata labarin cewa nan gaba zai faru har tayi karfin halin iya jurewa baza ta taba yarda ba, ringing ɗin da wayar ta ya sake yi ne ya dawo da ita hayyacin ta, da sauri ta shiga share hawayen ta tare da daidai ta fuskar ta don kar ya gane halin da take ciki. Sallama ta yi a bakin kofar dakin , amsa mata ya yi daga ciki, hakan ya sa ta shiga abin ta kai tsaye tare da mai da ƙofar ta rufe, ɗakin babu wadataccen haske, ware idanun ta ta shiga yi tana neman ta inda zata hango shi, duk hange hangen ta bata hango shi ba, kiran sunan shi ta shiga yi , amma shiru ba amsa, take mamaki da tsoro suka bayyana a fuskar ta, kofar toilet tayi da nufin ta duba ko yana nan, nan ma dai bai nan,mamakin ta ne ya ninku da sauri ta nufi haryar ƙofar fita dan ta fara tsorata tun da dai ita tabbas taji muryar shi a ɗakin ya amsa mata sallama, tsam taji ya rungume ta ta baya ya kwantar da kanshi akan dokin wuyan ta, ajiyar zuciya suka shiga sauke wa a tare cikin wani irin kasallalliyar murya yace "nayi missing ɗin ki sosai husnah ta." Bata tanka shi ba dan haka kawai zuciyar ta kece mata karya ya ke yi ba wani missing ɗin ki da yayi, jin tayi shiru yasa ya juyo da ita da sauri, ta gaban shi tare da cewa "ke bakiyi kewa ta ba ko husnah ta." A maimakon ta tanka sai hawaye sharrr "subhanallahi, dan girman Allah ki bari, wanda kika yi jiya da dare ma ya isa haka." Ya faɗa tare da mika yatsa yama share hawayen dake zubowa, amma ina yana share wa wasu na zubowa kamar an kunna famfo, ganin haka yasa ya nufi bed da ita ya kwantar, tare da saka harshen shi yana tsotse hawayen dake zubowa, sai da ta gaji dan kanta ta bar kukan jin haka yasa ya mai da akalar tsotsar shi kan bakin ta, lukuss tayi tana karban sakonnin shi, tun daga kan kumatun ta zuwa wuyar ta yake tsotse wa yana hura mata iska a kunne cikin ƙwarewa ganin yadda tayi lukuss yasa a hankali ya raɗa mata "shine jiya Bayan na wuce kike ta kuka ko? Kuma da safe da kika gan ni kika share ni kamar baki gan ni ba ko, kika barni ina ta jiran ki, cikin shehsheka me haɗe da shagwaba tace "ba Kaine ba jiya ka kwana gurin anty zee shine kuma da safe ba kazo da wuri na gan ka ba kuma kasan da kewar ka na kwana da'ker barci ya dauke ni." Yace "innalillahi dan Allah kiyi hakuri my hussy daga yau bazan sake zuwa wani waje kwana ba, tare zamu ringa kwana abin mu kamar yadda muka saba." Tace "nifa ban ce ba kawai cewa nayi baka zo da wuri ba da safe ka barni ina ta kewar ka." Yadda take maganar cike da shagwaba da salon jan hankali yasa yaji gaba daya hankalin shi na tashi wani irin sha'awar ta na bijiro mishi, hannu ya miƙa a hankali ya shiga laluɓe ta, jin yana shirin wuce gona da iri yasa tayi sauri damke hannun shi kallon ta yayi da idanun shi da suka fara juyewa cike da sha'awa, girgiza mai kai tayi , a hankili tace "yau fa ba kwana na bane kwanan anty zee ne." kamar ta caka mishi wuka haka yaji maganar ta ta daki zuciyar shi, cikin zaro ido yace "waye ya gaya miki kwanan ta ne yau." Tace "ba sai an gaya min ba, kwana 2-2 zamu din ga yi kayi daya saura da..." Bai bari ta kara sa ba ya katse ta da ɗan ƙarfi "ban amince ba ni kwana 1-1 zaku ringa yi nama riga na sanar mata, dan bazan iya jure yin har kwana biyu ba tare da ke ba." Tace "saboda me naga duk abin da zaka samu gare ni zaka same shi gurin anty zee har ma fiye da yadda zaka samu gare ni." Numfashi ya sauke "hmmm baza ki gane bane husnah ta." Mika ɗayan hannun yayi da nufin ya ci gaba da abin da yake so , sake rike dayan hannun tayi tare da cewa "to ai ba yanzu zan karɓe ka ba sai dare, har yanzu kana dakin ta ne, idan kana da bukatuwa ne kaje gare ta dan Allah." Kwace hannun shi yayi ya tashi yazauna bakin bed tare da dafe kai, ganin haka yasa ta dauka ko fushi yayi, hankalin ta yaɗan tashi, amma a ranta ta ayyana, wlh bazan baka daman da zaka faɗa halaka ba, in sha Allah bazan zama silar da zaka tashi da barin jiki a shanye ba ranar alkiyama kamar yadda mata da yawa a zamanin nan suke yi suna sane miji ba daidai yake aikatawa ba amma baza su taba hana shi ba su a ganin su hakan so ne, to wlh cuta ne tunde kema da aka haɗa kai dake aka zalinci wata Allah bazai barki haka ba. Daga bayan shi ta tsaya ta fara shehshekan kuka irin wanda tasan zai tada mishi hankali, ai kuwa a sukwane ya juyo ya jawo ta ya shiga rarrashi, cikin shehsheka tace "dan Allah kar kayi fushi dani ya Aslam, wlh ba wai na hana ka kaina da gangan bane, idan na bari ka aikata hakan mun shiga hakkin anty zee kuma Allah bazai barmu ba,bana son ka zama mara adalci a tsananin mu tun kafin tafiyar tayi nisa." Tana maganar tana kara matsar kwallah, take yaji babu dadi a zuciyar shi cikin muryar rarrashin yace "ya isa haka my hussy, na fahimce ki, kuma in sha Allah zan dage sosai nayi abin da kike nusar dani, ke ta dabam ce a cikin mata husnah ta, Allah ubangiji ya miki albarka." Rungume shi tayi sosai ta kwantar da kanta a jikin shi. A part ɗin ta yayi shirin zuwa aiki tunda a nan kayan shi suke, har falo ta rako shi tana rike da jakar laptop din shi, a falo ta mika mishi ba yadda baiyi ba ta raka shi wurin mota ta ki, a cewar ta zee zata hango su kuma baza taji dadi ba tun da ba kwanan ta bane, sai da ya biya part din zee ya sallame ta ita ma sannan ya dauki hanya. Yadda suka saba gudanar da harkokin su haka suka gudanar babu wani canji a tare da su, sai dai yau Asmah ta dage a part ɗin zee za'a shirya dinner tunda a nan Aslam din yake,in yaso idan ya gama zai kwanta sai ya dawo nata dakin har zuwa wani daren tun da ya ce kwana 1-1 zasu yi, koda ya dawa ɗakin Asmah ya fara biya wa ko zama bata bari yayi ba ta kora shi wajen zee, da da daddare kuma da zai yi dinner ya saka zee ta kira ta suka yi tare, ya kuma ce kullum tare zasu dinga yi duk wacce keda miji a je part din ta ayi. Da daddare Bayan ya sallami zee guraren karfe 9 ya dawo part din ta yadda ya din ga rawan jiki a kanta sai da abin ya daure mata kai, zaka rantse irin kamar wanda yayi wata da watanni bai kusance ta bane, sai sambatu yake yi, yana saka mata albarka tare da yabo yana cewa ita ta dabam ce a cikin matan duniya dan Allah duk rintsi kar ta rabu dashi, kaza kaza haka yaita yi kamar zautattce wani abin ma bai San yana fada ba, ita dai mamaki ya ne ya cika fal, bayan sun nutsu yadda ya ringa tattalin ta kamar wani daren farko abin har dariya ya din ga bata, hakan ya faran ta mata ko ba komai ta ji dadi duk da ya dandani wata macen bai wofintar da ita ba, shikam ai sai lokacin ya ƙara tabbatar da darajar ta da kimar ta lallai ya tabbatar yayi sake a baya, daya bari ta subuce mishi, badan Allah yaso shi ba da duk wannan romon lagwalan daɗin bazai San akwai su a duniya ba. Bayan wasu satittika gidan Aslam ya gama daidai ta, idan kaga yadda Asmah da zee suke gudanar da rayuwar su sai kayi rantsuwa ba kishiyoyi bane, sun maida juna kamar wasu yan uwa, suna girmama juna anty sama anty ƙasa basu taba bari wani sabani ya shiga tsananin su ba, sun haɗe Kansu ban da tattalin abin da zasuyi su faran ta ran Aslam babu abin da suke yi. Sai dai fa Asmah tana shan fama sosai da Aslam,kullum cikin taro shi take a kan hanya madaidai ciya idan ya bauɗe, tana namijin kokari wajen ganin cewa yayi adalci a tsananin su, sau da yawa har faɗa suke yi idan yayi wani abin daba daidai ba ta nuna mishi bai kyauta, amma faɗan baya nisa dan a take suke shirya wa, tana tausayin zee sosai dan takan ce, lallai Allah ya sota da rahama daya sa ita ce ta kasance abokiyar zaman ta idan da ta samu muguwa da wlh zaman gidan Aslam sai ya gagare ta, a dai yadda yake nuna yafi son ta karara a bayyane, kuma ko a gaban waye, sai dai itama zainab yana iya bakin kokarin shi wajen sauke duk wani hakki nata dake kanshi kuma yana bata kulawa kamar yadda yake ba Asmah, yana kuka matukar respecting dinta ganin yadda ta tsare girman ta ko a fuska bata taba nuna tana da muwa da wasu abubuwan da yake yi ba wata ran ma har yakan ji babu dadi shi karan kanshi, a gefe guda kuma ga kambun daya bata na uwar gida kuma wacce ta fara bashi farin cikin daya kasa samu a tare da Asmah wato haihuwa. Duk abin da Aslam yake yi zee bata taɓa nuna damuwa ba koda kuwa akan fuskar ta ne, takan kauda idanun ta idan yayi wani abin, ta riga ta sani takuma sadaƙar cewa Asmah ta yi mata fintinkau a zuciyar Aslam, tana tsananin kishi da Asmah sosai, amma kishi irin na matan annabin rahma, don duk abin da taga tayi na kwarai har Aslam ya yaba koda kuwa kwalliya ce ko girki kokari take ita ma ta takwatan irin shi kokuma wanda ya fishi koma wanda bai kai shi ba, a bangaren iyayen ta kuwa tana da labarin duk halin da suke ciki a wajen wan mahaifin ta Alhaji Abdur-rahman wanda dama shine ya shirya mata komai na tahowar ta Nigeria yana a Malaysia jirgin ta ya daga zuwa Nigeria hasalima shine yayi mata komai na barin kasar ita da ɗanta ba tare da sanin ƙanin nashi ba, jirgin ta ya daga da daddare da safe ya nufi gidan ƙanin nashi da nufin ya sanar dashi abin da ke faruwa kuna ya nusar da shi gaskiya shine fa ya tarrar ana tsaka dawan nan tataburzar. Iyayen shi sunyi matuƙar farin ciki da wanan lamarin kuma hankalin su ya matukar kwanta wa ganin yadda suka haɗe Kansu abinda basu taɓa zaton zai zo da sauki ba, dama bata Asmah suke to ji ba don ita sun riga sunsan wacece ita su suka raine ta sunsan abin da zata iya da wanda baza ta iya ba, zee suke ji duk da kuwa ta ce masu ta shiryu, basu gaskata hakan ba sai da suka gani zahiran muraran, dan duk ran da zata je family hause tare suke zuwa, kowa a gidan ya shaida lallai Kansu a haɗe yake kuma suna gudanar da tsabtataccen kishi wanda da wuya a samu irin shi a zamanin nan na matan yanzu. Duk wanda yaga Aslam yasan ya samu nutsuwa da kwanciyar hankali dan har wani dan kiɓa yayi mai ban sha'awa, haka suma matan Asmah kam ta murje ta ƙara haske itama da dan kiɓa ta kara cika cif cif kamar yadda yake so, sai dai abin da ke bata haushi tumbi da taga yana son fito mata, haka kurum taga cikin ta na tasa wa alamar tumbi zata yi, tuni ta dena cin duk wani abu da tasan yana saka kiɓa da tumbi amma a banza abu sai ƙara gaba yake yi tun ba wanda ya kula har ta kai Aslam ma ya kula, aikuwa ya din ga mata dariya yana tsokanar ta ganin da gaske ba so take yi din ba. Cikin haka zee ta fara zazzabi koda akaje asibiti wai ciki ne dan sati biyu, zo kuga murna gurin Aslam da Asmah tuni suka fara buge bugen waya duk wanda suka kira yaji abin da ke faruwa sai yama Asmah kwallah dan tausayi tare da fatan itama Allah ya bata nata, yadda take farin ciki har taso tafi Aslam din zee kanta abin na matukar bata mamaki lallai Asmah daya ce tamkar dubu a cikin alumma samun kanta tayi da saka ta a addu'a itama Allah ya bata nata na kanta. A can Malaysia kuwa a daidai wananan lokaci, ankai ruwa rana sosai da Dad lokacin daya farko ya ganshi a asibiti ciwon shi ne ya motsa sosai wanda rabon daya tashi yafi shekara ashirin tun zee na yar ƙarama, tun da ya farka bashi da wani abin fada sai daughter shifa a nemo mishi ɗiyar shi, ya ki kwantar da hankalin shi bare a samu ciwon ya kwanta,sai alluran barci ake ta ɗirka mashi, likitoci ma da suka ga abin yaki ci yaki cinyewa suka tambayi su mom wacece daughter ɗinnan ne dan Allah idan tana nan su kowa mishi ita, sai lokacin Alhaji Abdur-rahman yake sanar wa mom cewa shine ya fitar da zee da ɗanta zuwa Nigeria kuma yanzu haka tana ɗakin mijin ta, mom bata yi wani mamaki ba sanin halin Alhaji Abdur-rahman na ƴanci da son ƴaƴa, shifa duk abin ɗa yake so ko daidai ne ko akasin hakan baya taba hana wa, shi kuma kalar nashi jarabtar kenan, ta tuna lokacin auren zee da Aslam shine dai yayi uwa yayi makarɓiya, hankalin ta yadan kwanta tun da yanzu tasan inda zee take, duk da dama tayi zargin hakan. Dabara ne ya fado mom nan ta samu Alhaji Abdur-rahman sanar dashi take suka haɗa baki yama Dad daɗin baki cewa anga zee ta dawo gida amma tace baza ta iya zuwa asibitin ta duba shi ba sabo da baza ta iya jure ganin shi a kwance babu lafiya ba yanzu dai ya daure a karfaffa jikin shi ya samu yaji sauki a samu a sallame shi yaje gida yaga zee, kamar wani ƙaramin yaro haka ya yarda da zancen su, dan da gaske zee ta kasance ita ce raunin nashi na farko a duniya kamar yadda yake faɗa. Cikin kankanin lokaci ya wartsake aka sallame, dama Alhaji Abdur-rahman ya riga ya gama tsara yadda zai sanar dashi komai ya gayyato manyan malamai har su biyu da zasu mai wa'azi, tun kan akai karshen maganar da dai ya fahimci in da suka dosa ya birkice musu abin ka da jahilci zagi ta uwa ta uba, ya kuma lashi takobin zaije ya dauko yar shi koda da jan ciki ne kuma sai ya wulaƙan ta Aslam wulaƙanci mai tsanani,lamarin da yasa sukayi kaca kaca da ɗan uwan nashi ya gaggaya mai magana ya kuma ce yayi hankali dai da shiga lamarin aure da ma'aurata domin wani rabon tabbas yana kisa, ranar ya tattara ya dawo Nigeria rai a bace, yana dawo wa kuwa ya samu daddaɗan labari wai zee nada ciki, yayi murna sosai dan shima akwai son yara. Anyi haka kamar da kwana biyar Dad ya dira a Nigeria shi kaidai dan ko mom bai gayawa zai zo ba, direct a Niger state ya sauka, ko huta baiyi ba ya dauki shatar taxi yayi ma gidan Aslam diran mikiya, part ɗin ta daya sani tun farko ya nufa mai gadi na tare shi ya wanka mishi mari, suna zaune a falon ta kamar yadda suka saba suna hira, cikin nishaɗi zee nata tsokanar Asmah dake ta mata complain akan maganar tumbi,zee na cewa to kodai ciki ne, Asmah tace cikin lafiya ban fa Dade da gama period ba sai dai idan wani ciwon ne nidai wlh asibitin zani, kafin zee ta samu daman bata amsa , suka ji an shiga bubbuga ƙofa ba kaukau tawa duk sun tsorata musamman Asmah da take da saurin tsora ta har sai da taji wani abu yayi zillo a cikin ta, zee da yake ta ɗan fita karfin hali, ita ce ta tun kari kofar ta buɗe, gaban ta ne yayi wani irin mummunar faɗuwa har sai da ta yi saurin dafe shi, take kuma marar ta yayi wani irin murdawa, wanda ta gani a bakin kofar yana huci kamar mayuncin zaki tabbas ba kowa bane face Dad ɗin ta take ta duke a wajen tare da kama marar ta duk da haka kuma tana karfin hali ja da baya dan ta tsere mishi, duk da Asmah bata San shi ba ta tsora ta ainun da ganin shi hakan yasa itama ta fara da ja baya tana yarfe hannu, shigowa falon yayi ya tunkari zee da ke daga kafa daker daker tana rintse idanu numfashin ta na seizing baiyi wata wata ba ya dauke ta da wani irin mahaukacin lafiyayyen mari, abin da bai taba shiga tsanin su ba a tarihin rayuwar ta wai Dad ya mare ta, ko lura da yanayin da take ciki bai yi ba idanun shi sun rufe fisgar hannun ta yayi ga shiga janta, tana daga duƙe dafe da marar ta, ta shiga dan kokarin coge wa amma ina bata da wannan karfin ganin haka yasa Asmah kwasowa da mugun gudu ta biyo su ta rike ta da karfi tana kuka tana canja, tun da dai ita ba sanin Dad tayi ba, baza taba bari ya tafi da zee a gaban ta sai dai ko ya haɗa su, su biyu ya tafi da su, ganin Asmah ta na jan zee yasa ranshi ya ƙara ɓaci da wani irin karfi ya fusge su gaba daya dukan su sai da suka watse a kasa, Asmah ta bugu da kujera bai bi takan hakan ba ya fisgi hannun zee da karfi gaske yayi waje da ida, daidai sun iso tsakiyar compound din gidan cikin hukunci ubangiji motar Aslam ta shigo gidan duk da lokacin dawowar shi bai yi ba, akan abin dake faruwa direct idanun shi suka dira, wani irin burki ya taka tun daga bakin get da wani mahaukacin gudu ya fito daga motar ya nufosu, baiyi wata wata ba yasa hannu ya fisge zee daga hannun Dad take ta zube a wurin yaraf ba numfashi tsugunawa yayi akan ta yana jijjigata da karfi yana ambaton sunan ta hankali tashe, muryar Dad ne ya katse shi,a fusace cikin kaukausar murya yace kai tsinanne dan matsiya ta ka kyale min ƴa ta dan uban ka." Jajayen idanun shi ya dago ya zuba a fuskar dad, zuciyar shi yaji yana tafasa tsabar fusata har wani rawa labenshi yake yi baki ya bude zai yi magana amma ya kasa, kuma hakan ya taimaka dan duk abin da zai faɗa a lokacin bazai zama alkhairi ba , wani irin tafasa zuciyar shi ta shiga yi, tun daya kafe Dad da ido bai ko kefta ba , kawai hasaso ta ina zai kai mai makura yake yi....... Idan naga ruwan comment akwai update anjima Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Page 130 Ganin yadda Aslam ya kafe shi da jajayen idanun shi yana huci kamar wani mayunwacin zaki, sai da ya firgita , amma dake riƙƙeƙen ɗan duniya ne daure wa yayi ko a fuska bai nuna ya razana ba sai ma ci gaba yayi da cewa"Ba da kai nake magana ba fitsararre ka zuba min wasu kwala kwalan idanun ka makar na kwadi, nace dan uban uban ka ka kyale min ɗiya ta." Bai dauke idanu akan shi ba kuma bai kyale tan ba, "OK baza ka kyale ta ba ko? To ina zuwa a kwai wadanda zasu shiga tsakani na da kai, zaka gane ƙaramin ɗan iska ne kai." Yana gama faɗin haka ya juya da sauri fuuu kamar zai tashi sama ya fice daga gidan, abu biyu ne ya saka shi fice wa ba tare da zee ba, na farko dan ya gujewa wannan kallon da Aslam ke mishi dan har ga Allah ya tsora ta da yanayin shi, yasan bai da ƙarfi yin dambe da Aslam koda hakan ta kama sai dai a nakasa shi a banza, na biyu kuwa dan ya kwaso police suzo su tafi da Aslam, dan wannan karon yayi alkawarin sai ya wulakan ta shi, don idan ya kulle shi a wannan karon, in ba wani ikon Allah ba sai dai ya kare rayuwar shi a gidan maza. Har ya fice daga get ɗin Aslam bai ɗauke kanshi daga kallon shiba , ba komai ne ya hana shi haɗa ma Dad jini da majina ba, sai dan darajar mutum biyu masu daraja a gareshi na farko little na biyu kuwa ita ce zee, duk lalacewar Dad mahaifin ta ne, Kuma su iyaye komai munin halin su ba'a kin su tana son uban ta sosai kamar yadda shima yake son ta, idan ya mishi wani abu makamancin duka ko zagi tabbas idan ta farka baza ta ji daɗi ba, ga kuma little da sauran ƴaƴan da zasu haifa nan gaba tare da ita, idan har ya duki Dad zai zama abin gori ne a gare su kuma ma ai shi yana da ilmi idan ya biye mishi sun zama ɗaya kenan. Da'ker ta samu ta lallaba ta lalubi jikin kujera ta dafa ta mike, tana jin ta tsaye kan ƙafafun ta take duk abin da ke faruwa ya shiga dawo mata da gudu ta nufi waje tana kwala kiran anty zee hango sun da tayi yasa ta nufo su, ganin zee kwance a hannun Aslam bata numfashi yasa ta sauri duƙewa cikin tashin hankalin da tsinkewar zuciya ta shiga jijjjgata tana kiran sunan ta, shiru babu ko alamar zata motsa, dago hannun ta da zata yi da nufin ta tashi taje ta kawo ruwa a yayyafa mata sai ganin hannun tayi caɓal da jini, hankalin ta ne ya kara tashi cikin kuka tace "innalillahi wainnailaihi rajiun,shike nan ya Aslam ya kashe mana ita." Sai lokacin ya lura da hannun Asmah shima hankalin shi ba karamin tashi yayi ba yunkurawa yayi ya miƙe da ita sai ga jina faca faca ya na bin jikin ta, a guje ya nufi mota da ita ya buɗe bayan ya kwantar da ita, itama Asmah rufa mai baya tayi ta buɗe gefen me zaman banza ta shi a haukace ya figi motar ya fice daga gidan, sunzo dai dai fita kwanar gidan wanda zai hau da su babban titi suka ga cincirundon mutanen a tsatstsaye tun daga nisa ya din ga danna horn, ganin yadda yake mugun gudu yana danna horn yasa tun kofin su karaso wajen mutanen suka dare suka basu hanya, bai tsaya bi ko tambayar meke faruwa ba ya harba kan babban titi ya dauki hanyar wani babban private hospital, yana shiga aka karbe ta akayi emergency room da ita, likitoci kusan uku suka rufa akan ta domin ceto rayuwar ta abin ka da asibitin masu kumbar susa A fusace Dad ya bar gidan Aslam da nufin ya nufi police headquarter ya debo ƴan sanda ya biya manyan su kudi dan suzo suci mutumin Aslam sumai dukan tsiya sannu su tafi dashi su kulle shi kuma ya dauki yar shi ya tafi da ita, yana tafe yana sambatu yana zage zage kamar wani taɓɓaɓe gaba daya hankalin shi baya jikin shi burin shi kawai ya ganshi a police station, yazo tsalleke titin domin ya koma hannu da zai samu taxi cikin rashin sani wani tsohon Sharon ya shararo da gudu birke ya tsinke mai tun daga nesa yake ta danna ma Dad horn amma ina baiji ba hankalin shi baya jikin shi idanunshi sun rufe kunnuwan shi sun ɗoɗe tsabar bala'in dake cin zuciyar, aikuwa cikin hukuncin ubangiji mai Sharon ɗinnan yayi sama da Dad kuma ganin ba kowa abin ka da unguwan yan gayu yasa mai Sharon dinnan fece wa ya bar Dad nan kwance rai a hannun Allah, me gadin dake farkon Layin ne ya fito da nufin yin wani uzirin sai ganin mutum yayi kwance cikin jini shine fa yayi kururuwa mutane suka dan fiffito yawancin su ma masu gadin gidajen unguwan ne, koda suka fiffito tsayawa suka yinyi cirko cirko ana shawara an rasa wa zai taimaka mai zuwa asibiti, suna cikin wannan tsayuwar ne motar Aslam tazo ta wuce su da mugun gudu, kasancewar cikin tashin hankali yake yasa bai kula da abin da ke faruwa ba, wani he ya bada shawara a shiga gidajen dake kusa a gaya musu suzo su duba ko dan uwan su ne moto ya buge dan ga dukkan alamu daga cikin wannan unguwar ya fito, da wannan shawaran suka fara bi gidanjen da ke kusa cikin haka ne suka zo gidan Aslam, me gadi dake nan duk cikin shi ya duri ruwa ya kasa zaune ya kasa tsaye don duk abin da ke faruwa akan idanun shi ne abin da yafi daga mai hankalin shine yadda yaga Aslam ya figi mota a tsiya ce , ya tarbi mutum biyu da suka yi sallama a kofar gidan , jin abin da ke tafe dasu kuwa baiyi kasa a gwuiwa ba yace suje ya gani duk da ko kusa bai kawo tunanin Dad bane yama fi ba cewa to ko Aslam ne ya buge mutumin tunda yaga ba cikin hayyacin shi ya figi motar ba. Ko da suka je kawai sai yaga mutum da ya fita a gidan su mintuna ƙalilin da suka wuce mutumin da ya mare shi yanzu yanzu ba tare da ya mishi komai ba, "Allahu Akbar." ya furta lallai dan Adam ba'a bakin komai yake ba yanzu wannan bawan Allah idan da yasan zai shiga cikin wannan mawuayacin halin nan da yan mintuna me zai kai shi aikata abin daya gama aika ta wa yanzu yanzu. Zuciyar musulumci take yaji tausayin Dad ya kama shi, dan kuwa duk wani mai imana idan yaga Dad dole ya tausaya mishi bai yi kasa a gwuiwa ba wurin cewa bai san shi b, amma ya bada shawaran a taro napep akai shi asibiti in yaso su likitocin saji dashi, take fa yawa suka amince da zance, ya samo me napep akayi general hospital da Dad kafafuwa na lilo alama Likitoci sun sha matukar fama sosai kafin su samu su tsaida jinin daya barke mata da'ker suka ceto rayuwar ta, Aslam da Asmah kam sunan nan a kofar emergency room din Asmah sai kuka take yi Aslam yayi rarrashi har ya gaji ya kyale ta, shi karan kanshi karfin hali kawai yake yi, dan ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai safa da marwa yake yi, lokacin da daya daga cikin likitocin dake duƙufe akan zee ya fito har rice rige sukeyi da Asmah wajen tambayar shi halin da take ciki, be basu amsa anan ba sai cewa da yayi su biyo shi office, bayan sun zauna file din ta ya bude ya shiga dan rubuce rubuce, Asmah kam ta kosa taji wani hali zee ke ciki hakan yasa tace "Dr pls wani hali take cike meya samu yar uwata." kallon su yayi tare da gyara zaman siririn farin glass din dake idanun shi yace "patient din da kuka kawo mana wato zainab Abdus-salam, ta samu miscarriage sakamokon wani tashin hankali da firgici data shiga na lokaci daya." Kamar saukar aradu haka Aslam yaji saukar maganar Dr a zuciyar shi Asmah kam tuni ta rushe da wani irin kuka kwace ce mata akayi zee din ta rasu, Aslam kam innalillahi wainnailaihi rajiun ya shiga furtawa a zuciyar shi, Dr ne y shiga rarrashin ta yana kwantar mata da hankali, dan Aslam bashi da karfin halin iya rarrashin ta a halin da yake ciki, ji yayi zuciyar ta kara daukar zafi,rintse idanu yayi yana jin tsanar Dad na kara baibaiye lungu da sako na zuciya shi, alkawari ya dauka tare da lasar takobin wannan karon bazai bari mahaifin zee ya shashi silla ba shari'a zai yi dashi bakin rai bakin fama daga nan har kotun koli na duniya sai anbi mishi hakkin shi akan Dad koda duk abin da ya mallaka zasu kare, jajayen idanu shi bude akan Dr cikin murya mai dauke da tsananin bacin rai yace "Dr wani hali matata take." Shi karan kanshi Dr abin ya bashi mamaki amma ya dauka duk bakin cikin rasa cikin ne yasa yake mai magana a haka, cikin muryar rarrashi Dr yace " matar ka tana lafiya munyi duk abin da ya kama ta muyi, harta wankin ciki duka munyi mata, yanzu haka barci take yi allura muka mata nan da awa 4 zata farka, ku kwantar da hankalin ku, babu wani wani matsala zata farka lafiya insha Allah." Rubutu ya ɗanyi a jikin wani dan paper ya mika wa Aslam gashi wannan magunguna ne zaka siyo mata na jini sunfi yawa aciki wanda zata din ga sha ba sai mun mata Karin jini ba idan tasha wadannan magungunan amsa Aslam yayi suka yi ma Dr godiya sannan suka fito Asmah ta shiga dakin da aka kwantar da zee shi kuma ya tafi pharmacy dan siyo magunguna. Bayan ya dawo ya samu Asmah zaune a kan kujera hannunta cikin na zee dake ta sharar barci, ajiyar zuciya ya sauke ganin ta dawo daga suman da tayi yanzu barci take sai lokacin tunanin kiran su mummy ya fado mai, take kuwa ya lalubi waya ya kira Mami, kan kace kwabo asibiti ya cika da yan uwa, sai bayan isha'e zee ta farka kuma alhmdllh jikin da sauki sai dai Dr yace bazai sallame ta ba sai zuwa gobe, Mami da Asmah ne suka kwana a Asibiti, shi kuma Aslam ya tafi gida a gurin mai gadi ya samu little har ma yayi barci abin shi cikin net a kan dan karamin gadon dake dakin mai gadi, me gadi kamar ya gaya mai halin da dad ke ciki sai kuma kawai ya share, A cen general hospital kuwa bayan sun kai Dad asibiti, cikin gaggawa a kayi cikin emergency dashi aka bashi gado,wadan da suka kawo shi wucewa suka yi bayan sun sanar wa likitocin cewa tsintar shi suka yi yayi accident a bakin hanya da alama mota ce ta buge shi kuma mai motar ya gudu.jin haka yasa akayi banza dashi tun da babu wanda zai tsaya mishi, sai bayan isha'e daker dai aka samu wani likita mai dan tausayi ya kula shi, jikin shi aka duba cikin sa'a aka samu wayar shi, a kulle wayar take hakan yasa aka cire daya daga cikin sim uku dake wayar aka saka a wani wayar take lambobi guda uku suka bayyana. Daughter, wife, Brother, ganin, haka yasa suka San duk wadannan makusantan shi ne, wani je ya bada shawaran a kira Brother saboda shi namiji ne zaifi matan saurin fahimtar lamari, Alhaji Abdur-rahman na zaune a falon shi yana hutawa shida matar shi kira ya shigo wayar shi, sunan daya gani ya matukar bashi mamaki kwarai sanin irin bakin zuciya na kanin nashi yasan sarai a yadda suka yi rabuwan baran baran karya ne ya neme shi nan kusa sai dai idan shine ya gaji ya neme shi, ajiye mamakin shi a gefe yayi ya daga wayar, maimakon ya tsinkayi muryar ƙanin nashi kamar yadda ya sakankance zai ji sai ya tsinkayi muryar wannan Dr , a gurguje ya sanar dashi abin da ke faruwa da me wannan lambar Alhaji Abdur-rahman yasha mamakin jin cewa a Nigeria ne ƙanin nashi yayi hatsari har ake neman shi a general hospital, jiki a sanyaye ya amsa wa Dr da cewa gashi nan zuwa nan da 20 minutes, suna ajiye wayar Mom ya kira yake tambayar ta ina Dad nan take ce mashi rabon da shi tun jiya, take ya sanar mata da abinda ke faruwa aiko dai hankali ba karamin tashi yayi ba nan ta fashe mashi da kuka a waya, daker ya dan rarrashe ta sama sama ya tashi ya kamo hanyar asibiti, sai da Alhaji Abdur-rahman ya iso ya bude ma Dad file yayi duk abin da ya kamata yayi sannan Dr din suka taba shi. Dad ya nakasa iya nasaka dan gaba daya kafafun shi sun samu karaya bibbiyu ga kuma hannun shi na dama, banda uban ciwukan daya jijji ga kanshi daya fashe , fuskar shi ta canja kamanni lokaci guda haƙora ukun sama dana kasa duk sun zube sai wawakeken giɓi, su karan Kansu litocin sun tausaya mai kuma sun jinjina ma taurin ranshi da bai mutu ba duk da tarin ciwukan daya ji. Abinka da harkar nera suna gaya wa Alhaji Abdur-rahman akwai karaya za'ayi gyara yace a bashi Dad ya zai canza mai asibitin ba bata lokaci kuwa akayi cike ciken komai aka saka shi a. Ambulance sai asibitin da zee ke kwance.A cikin daren aka yi ma Dad ɗauri dan tsananin azaba harda su kashi a wando suma kuwa yayi yafi so uku yana farfaɗowa, gashi baisan ya kira Allah ba, sai tsala ihu yake yi kamar wani Arne, ranar gaba ɗaya asibitin sai da akasan da zaman Dad masu tausayi nayi masu dariya nayi, su Asmah da Mami ma sun sami labari duk da basu san ko wanene bane kwarai sun tausaya mai, Alhaji Abdur-rahman ne kaiɗai yake ta kai kawo akan shi har zuwa safe, sai da yaga komai ya daidai ta har barcin azaba ya kwashe Dad sannan ya yi sallama da likitoci da niyar zai je gida ya huta, zuwa anjima zai dawo, da safe wuraren karfe 7 Aslam ya iso asibiti,kusa da motar Alhaji Abdur-rahman yayi fakin ba tare da sani cewa motar shi bace, fito wa yayi ya zagayo ya buɗe ɗaya gefen ya dauki little juyowan da zai yi daidai lokacin Alhaji Abdur-rahman ya iso wajen fakin din domin shiga ɗaukar motarshi, kallon mamaki suka shiga bin juna da shi, Aslam na tunanin to waya gaya mishi zee na asibiti don shi a tunanin shi zee yazo dubawa, shi kuma yana tunanin ya akayi Aslam yasan Dad na asibitin nan to ko shima Dr ya kira shi, Aslam ya ƙarasa ya bashi hannu sukayi musabaha, Dad yace "Ya mukaji da wannan iftila'il kuma." Ba tare da ya fahimci komai ba yace "Sai godiyan Allah, amma jikin da sauƙi sosai Alhaji don Dr ma yace yau zai bamu sallama." Alhaji Abdur-rahman cikin mamaki "sallama Kuma! wa za'a ba sallama?" Aslam yace "Ita mana." "Ita wa?" Ya tambaya, Aslam shima abin ya fara ɗaure mishi kai dan haka yace " Ita Zainab ɗin." Zaro ido Alhaji Abdur-rahman yayi cikin kaɗuwa yace "kana nufin kace min Zainab na kwance a wannan asibitin ita ma?" Aslam yace "eh Alhaji ai na dauka ma ita kazo duba wa." Maimakon ya bashi amsa sai "innalillahi wainnailaihi rajiun ya shiga maimaita wa." Can kuma yace "Muje ka kaini wajen ta na duba ta meye ya same ta." Suna tafe Aslam ke gaya mishi ai ta samu miscarriage ne, Alhaji yace "subhanallahi garin yaya." Shiru ya danyi kamar bazai gaya mishi ba sai kuma wata zuciyar ta umarce shi daya faɗa domin barin kashi a ciki baya maganin yunwa, tuno kawai abin da ya faru don faɗawa Alhaji sai da yaji zuciyar shi ta dauki zafi dan sanyin data ɗan yi tuni ya gushe. Bai yi ƙasa a gwuiwa ya kwashe komai ya shiga gaya mishi, tunkan Aslam ya kai karshe Alhaji wata uwar burki ya taka tare da juyowa hankali tashe yace "Kana nufin Abdus-salam yaje gidan ka ajiya har yayi sanadin zubewar cikin jikin Zainab." Kasa bashi amsa Aslam yayi dan wani irin tukukin bakin ciki yake ji a ranshi. "Innalillahi wainnailaihi rajiun, Allah wadaran naka ya lalace, gaskiya Abdus-salam baiyi wa kanshi adalci ba dama na gaya mishi wani rabon karfi gareshi kisa yake, to shi Allah ma yaso shi bai mutu ba amma kuma da wannan halin daya shiga ai gara mutuwa." Kallon rashin fahimta Aslam ya shiga binshi dashi, ganin haka yasa ya kwashe duk abin da ke faruwa tun da ga daren jiya da aka kira shi a waya daga general hospital zuwa wayewar garin yau, ko ɗar Aslam baiji a ranshi sai ma cewa da yayi "Allah kyauta Allah ya kiyaye na gaba." Sun tarad da su jugum jugum kamar wa'inda aka aikowa da saƙon mutuwa, Asmah da Mami na zaune a bakin daya extra bed ɗin dake ɗakin, zee kuma na zaune a bakin nata bed din rike da cup din tea a hannun ta idanunta sunyi jajur alamar taci kuka ta ba uku lada, ganin wan mahaifin nata yasa ta sake fashewa da kukan da da'ker su Mami suka samu tayi shiru, shima direct gareta ya isa ya zauna a kusan da ita tare da kamo hannayenta ya rike cikin nashi, yana bin ta da wani irin kallon tausaya wa, cikin tsananin kuka tace "Abba dan Allah ka gaya min gaskiya da gaske Dad shine mahaifina shiya haifeni, Abba Dad kullum ikirarin shi yana sona yafi kowa sona a duniya amma wlh ni soyayyar shi ni batai mini rana ba, tun da har ya kasa bani farin ciki, ya kasa barina na zauna da mijina domin na sami Aljannahta aƙarƙashinsa, Abba Dad yayi sanadin da cikin jiki na ya fita, shin wannan wane irin sone?." Ta karashe da wani irin matsanancin kuka, jikinshi ya jawota ya rungume, Asmah da Mami tuni zuciyar su ta daɗa karyewa ji suka kamar su taya ta kuka, Aslam kam taɓe baki yayi ya dauke idanunshi daga garesu, daker Alhaji Abdur-rahman ya samu ya lallɓa zee ya samu ta tsagaita kukan ta, cikin kwantar da hankali yace "Kiyi hakuri Zainab ko wani bawa da kalar jarabtar da ubangiji yake mishi a rayuwar shi ta duniya, ke da mahaifin ki jarabtar ku iri ɗaya ne, shi kece jarabtarshi, kema shine jarabtar ki, kiyi hakuri ki daina jin kamar cewa ba shi ya haife ki ba, tabbas shi ya haifeki, amma Allah ya jarabce shi da wani irin makauniyar soyayya akan ki, wanda a karshe shine yayi sanadin nakasan shi." Nan kuma ya kwashe duk abin da ke faruwa da Dad ya sanar mata, kan kace kwabo ta kara birkicewa, sai kuka take tana kiran dadin ta, karshe ma ta tsige Karin ruwan dake hannunta tace ita gurin dadin ta zata tafi, wai a haka ma Alhaji Abdur-rahman bai gaya musu irin raunukar daya samu ba daga ita har Aslam ɗin kawai ce musu yayi, yayi hatsari, ba shiri Alhaji yasa aka kira Dr ya duba ta, a take ya rubuta mata sallama ma gaba ɗaya kawai, Alhaji Abdur-rahman yace Aslam ya kaita gida, aiko ta ƙeƙashe ƙasa babu inda zata je sai taga dadin ta, dan dole suka dunguma zuwa ɗakin da aka kwantar dashi,da taimakin wani dr abokin Aslma don ɗakin ba'a bari a shiga Aslam baiyi niyar zuwa ba kawai dan yana jin nauyin Alhaji Abdur-rahman ne amma ba dan Allah yaje ba dan ko kaɗan baiji tausayin Dad ba kwata kwata mutumin ya sire mai, gani yake ma alhakin su ne ya kama shi na zuwa da yayi bagatatan ya musu asarar ciki. Alhaji Abdur-rahman ne gaba yana rike da hannun zee sai Aslam dasu Mami biye dashi, dukkannin su saida zuciyar su ta girgiza da ganin yadda Dad ya koma cikin abin da baifi awa ashirin da huɗu ba, wani gigitaccen ƙara zee ta saki tare da durkushe wa a gaban bed ɗin da Dad ke kwance, Asmah ma tuni ta fashe da kuka hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ba, wai mutumin daya zo jiya ya nemi wulakansu haka, lallai Allah ba abin wasa bane, Mami ma sai dauke kwalla takeyi, na tausayin zee da mahaifin ta, Aslam kam take idanunshi suka kala sukayi jajur, duk yadda yake jin haushin Dad a zuciyar shi sai da ya tausaya mai, lallai ɗan Adam ba'a bakin komai yake ba, ganin yadda zee ke kururwa tana kuka, yasa Dr saurin basu umarnin su fita su bar mara lafiya shi kaiɗai kar su bata musu aiki, daƙer Aslam ya janyeta daga ɗakin, koda suka fito yace tazo ya kaita gida tayi wanka ƙin yarda tayi ta tafi, Asmah ma sarkin tausayi cewa tayi zata zauna tare da zee, ya kada dambu taliya amma suka ƙi bin shi, karshe shi da Mami ne kawai suka bar asibitin mami ta wuce da little can family hause dan zaman asibiti bai kamace shi ba. A nan suka wuni tare a asibiti sallah kawai ke tada su, daga inda suke zaune, sai bayan la'asa Alhaji Abdur-rahman ya musu abinci daga gida sa, , daga ita har Asmah babu wanda ya kalli inda abincin yake, saidai nan kuma Dad ya farka daga alluran barcin da aka mishi, sun so shiga su ganshi amma Dr ya hana ganin sun matsa yasa da'ker ya bar Alhaji Abdur-rahman ya shiga, ya samu Dad idanunshi a bude harass sai dai hawaye kawai yake zirararwa, ya tausaya mai amma hakan bai hana shi rufeshi da fada ba ya kuma sanar dashi abin da zuwan shi gidan Aslam a jiya ya janyo, karshe kuma ya daura da nasiha,daga yadda Dad ke kuka yana Neman gafarar shi,shi kamshi ya tabbatar yayi nadama sosai harda cewa a kira zee da Aslam ya nemi gafarar su, Alhaji Abdur-rahman ya hana tare da cewa taya bari ya kara samun sauki tukun, daga karshe ya koma barci saboda karfin magungunan da aka bashi yanzu bayan farkawanshi. Bayan isha'e Aslam da Abba da Alhaji baba suka zo asibe ko za a basuyi ba Alhaji Abdur-rahman shima ya dawo da ta masallaci . Mami ne data koma gida ta labarta wa Abba abun da ke faruwa shine fa ya sanar wa su daddy da Alhaji baba sun tausaya matuka duk da sunji tsiyar daya tafka Allah ya kama shi. Bayan sun gaggaisa Alhaji Abdur-rahman yace bari yaje yaji daga bakin Dr ko zasu iya shiga su ganshi dan ɗazu jikin da sauƙi, kafin ma ya kai ga tafiya wata nurse ta nufosu da sauri tana haki, dukkan su ido suka zuba mata zuciyoyin su na tsistsin kewa, tace "wacece zee da Alhaji Abdur-rahman da Aslam da karima a cikin ku." Zabura zee dake rungume jikin Asmah tayi ta mike, Aslam ne ya bata amsa da "gamu nan duka." Tace "Dr yace kuzo maza patient ɗin ku yana son ganin ku da gaggawa." Da sauri kuwa suka rufa mata baya dukkansu zuwa ɗakin, Dr ɗaya suka samu da nurse ɗaya akan Dad suna faman bashi taimakon da zasu iya, kimanin mintuna ashirin kenan da farkawanshi, tunda ya farka jikin shi ya ƙara rikice gaba ɗaya sai dai bakin shi bai mutu ba sunan zee da Aslam, Alhaji Abdur-rahman da karima, kawai yake kira a wahalce, ganin yanayin da yake ciki ne kawai yasa Dr ya zare mai karin ruwan da jini da duk wani na'ura dake jikin sa dan jikin shi ha bashi wannan mutumin kam da'ker zai kai labari, hakan daya gani yasa ya aikin nurse dinnan ta kira mutanen da yake nema watakila wasiyya zai bayar, da gudu zee ta karasa gaban shi tana wani irin kuka, mai ban tausayi, da'ker yace "Zainab mutuwa zanyi, ki yafe min." Ciki kuka tace "dadi na baza ka mutu ba in sha Allah zaka warke zafin ciwo ne yasa kake ganin kamar ajalin ka yazo." Murmushi yayi wanda ba kowa bane zai fahimci hakan saboda yadda fuskar shi tayi dameji, yace "mutuwa zanyi Zainab ni nasan abin da na hango, ina mijin ki yake." Aslam dake tsaye daga can baya idanunshi jajur ya karaso gaban Dad, kallon shi Dad yayi ya mika hannunshi guda mai lafiya ya kama hannun Aslam ya manna dana zee dake tsaye kusa da shi cikin maganar shi irin ta marasa lafiya sosai wanda sai mutum ya kasa kunne yake iya gane mai yake fada yace "Aslam kayafe min, nasan na cutar da kai na yi sanadin da ka rasa gudan jikin ka, amma dan Allah karka kulla ceni komai nakeyi akan soyayyar Zainab ce, itace jarabtata duniya tunda na haifeta nake bata wa mutane da yawa rai akan ta indai ita zatai dariya, Allah ya rarabceni da makahon so akan Zainab, kuma har yanzu dana ke kan gabar barin duniya daidai da kwayar zarra banji ɗigo na sonta ya ragu a zuciya ta, ga amanar Zainab nan na bar maka Aslam, duk duniya babu wanda take so sama da kai dan Allah ka kula min da ita ko bayan rai na, dan Allah badan halina ba." kafin ya samu daman kara cewa wani abu tuni harshen shi ya karye sai magana yake yi amma babu mai fahimtar shi, tuni zee ta ƙara ruɗewa tare da fashe da wani irin kuka ta faɗa jikin shi ganin haka yasa Aslam janyeta da karfi tana fisgewa ya fice da ita daga ɗakin, Asmah ma dake kuka Abba ya rike hannun ta ya fice da ita waje,Alhaji Abdur-rahman ne ya masto gare shi yana sharar kwallah ya kama hannun shi ya rike gam yana cewa "dan uwana insha Allah baza ka mutu ba, zaka tashin akan kafafun ka zafin ciwo ne." Alhaji baba dake tsaye gefe yana kallon yanayin Dad ya tabbatar wannan kam yana kan gaba, matsowa yayi gare shi ya shiga laƙaba mishi Kalmar shahada, Allah sarki Dad kasa.kamawa yayi sai ya bude baki zai kama kuma maganar ya sarƙe, karshe idanun shi ya shiga kafewa kumfa na fitowa daga bakin shi, take kuma jikin shi ya fara sakewa a hankali kuma kanshi ya karye gefe............. Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen} Page 131 Mutuwar Dad ya girgiza zukatan mutane da dama, duk wanda ya tuna abin da ya faru kafin awa ashirin da hudu da suka shude, sai ya kara tsarkake lamarin ubangiji ya kuma kara tabbatar wa lallai rai ba'a bakin komai yake ba, lokacin da labarin rasuwar Dad ya riski zee kusan zaucewa tayi, take ta fisge daga rikon da Aslam ya mata ta nufi ɗakin da gawar Dad kwance da mahaukacin gudu, tana yin arba da gawar Dad take ta yanke jiki ta faɗi sumammiya. kwanan keso Dad yayi saboda da daddare ya cika. Washe gari Karfe tara Mom ta iso a birkice , bata yarda cewa Dad ya rasu ba saida tayi arba da shi kwance baya motsi lulluɓe da farin alawayyo, take ta ƙara birkicewa ta shiga zunduma ihu tana kururuwa da birgima kamar wata arniya maimakon ta mishi addu'a, rarrashin duniya an mata taƙi ta haƙura har aka gaji aka yi kyale ta, masu zagi da alawadai nayi masu tausayi nayi. Karfe goma daidai aka kai Dad makwancin shi na gaskiya, Aslam da duk wani makusancin shi sun halarci jana'izan Dad, tare dashi aka cigaba da karɓan gaisuwa a gidan alhaji Abdur-rahman. Har aka kai Dad aka watse zee bata cikin hayyacin ta, dan tunda ta sume aka kwashe ta aka sake bata gado a asibitin, likitoci suka duƙufa a kanta har aka samu ta farfaɗo, koda ta farfaɗo zabure zabure ta shiga yi tana ihu ce ihu ce lamarin kamar da bugun aljanu ganin haka yasa likita ya zunduma mata alluran barci mai karfin gaske, sai da Dad ya kwana ya wuni a kushewa sannan ta farko,cikin hukuncin ubangiji ta farka cikin hayyacinta sai dai kuma ruwan hawaye ya kasa ƙafewa a idanun ta, a ranar Dr ya bata sallama direct Aslam ya wuce da ita gidan Alhaji Abdur-rahman aka cigaba da zaman makoki tare da ita, duk yan gidan su Aslam sunje sunyi gaisuwa tun daga kan su mummy har su batool da mazajen su, Aslam da Asmah kam kullum nan suke wuni shi yana falon Alhaji Abdur-rahman ana karbar gaisuwa dashi ita kuma tana tare da zee tana kwantar mata da hankali, har zuwa ranar da akayi addu'an fidda'u na kwana uku. Sai da zee tayi kwana bakwai sannan Aslam ya dauko ta, har zuwa lokacin mutuwar Dad nanan daram a ranta, sai dai tayi amfani da shawarar da Asmah ke bata a kulkum ta daina yi mai kuka sai dai in abin ya ciyo ta tayi ta hawaye tana mai addu'a domin tasan shine abin da yafi buƙata a halin yanzu, part guda aka ware wa Mom a gidan Alhaji Abdur-rahman a nan take zaman takaban ta, Allah sarki Dad tasa ta ƙare wasu har sun manta dashi sai wa'inda ya zame wa dole kamar dai zee da Mom da Alhaji Abdur-rahman. Bayan wata daya da rasuwan Dad, zaman lafiya tsakanin Asmah da zee sai abin da ya ƙaru, zuwa lokacin zee ta koma asalin zee ɗin ta, tayi laushi ta kara miƙa wuya ga lamarin ubangiji, ta dau hakuri da dangana akan rashin mahaifin ta, idan ta tuna shi sai dai kawai ta mishi addu'a, Aslam ma ya dena yi mata wasu abubuwan da yake mata zuwa yanzu dan ba karamin tausayi take bashi ba , musamman idan ya tuna da wasiyyan da mahaifin ta ya bashi da kuma amanar ta daya damƙa a hannnun shi a lakacin yana kan gargarar barin duniya. A bangaren Asmah yau ta wayi gari cikin wani irin yanayi mara daɗi tun cikin dare ta ke jin cikin ta na wani motsi kamar akwai abu mai rai a ciki,dama takanji haka lokaci lokaci cikin kwanakin nan tana sharewa amma na yau sai yayi yawa gashi Aslam ba'a dakin ta yake ba, tun cikin daren tayi ta kiran wayar shi amma yaki shiga, haka ta zauna ta dafe cikin ta tana ta kuka, idan taji motsin yayi yawa sai ta shiga karanta ayatulkursiyu ta tofa, ta firgita ainun da lamarin kafin safiya duk ta fice daga hayyacin ta, kwanaki da cikin ta keta kumbura taje asibiti taga likita, Dr Aysha ta mata duk wani tambayoyi akan alamomin ciki tace bata jin ko daya, kuma duk watan duniya al'ada takeyi, duk wani test daya kamata tayi, tayi harda su scanning babu komai, kwantar mata da hankali Dr tayi tace ba komai kawai tumbi bi ne, ta kiyaye cin abubuwa masu maiko da kitse kuma ta ringa motsa jiki zai baje insha Allah, koda taji haka sai ta tattara lamarin ta watsar kawai tunda dai ita ba ciwo yake mata ba, kuma ma ba wani shegen girma yayi ba itace kawai take ganin abinta sai ko Aslam shi da yake mijin ta , amma idan ba mutum kallon kurulla ya mata ba bazai ga komai ba, shine kuma cikin wannan week ɗin ta farajin motsi motsi a cikin nata, tana dai daurewa tana basarwa don ko Aslam bata fadawa ba, sai dai tayi ta addu'a tana rokon Allah koma menene ya yaye mata, har aka kira sallan assalatu idanun ta biyu bata rintsa ba, da'ker ta lallaɓa tayi sallah, tana idarwa ta farajin kamar ana yaki a cikin har in ta taba tanajin motsin a hannun ta, wayar ta ta dauka ta sake gwada kiran Aslam still bai shiga ganin haka yasa ta juya akalar kiran ta zuwa numbar mummy dama abin da ya hana kiran ta tun jiya dare ne dan karta ɗaga mata hankali, mummy nakan dardumu da asuba tana lazumi taji wayar ta na ringing kamar ta share haka kawai taji zuciyar ta na azalzalan ta akan ko baza ta dauka ba ta duba, ganin sunan Asmah na yawo a saman screen din wayar yasa taji gaban ta ya fadi, a fili ta furta "Asma'u da wannan farar safiyar Allah dai yasa lafiya." Ɗaga kiran tayi ta kara a kunne tare da yin sallama, cikin shehsheka taji muryar Asmah na amsa mata sallama, cikin dan tashin hankali jin Asmah kamar kuka taje tace "subhanallahi! Asma'u mekefaruwa, meya sameki waya taɓa ki?" Dan ita duk a tunanin ta cikin Aslam da zee ne wani ya saka ta kuka a Cikin kuka take ba Mummy labarin abin da ta kwana ji a cikin ta yau, mummy karan kanta abin yadan tsorata ta, wani tunanin ya faɗo mata a rai da sauri ta kauda shi tare da yin istigfari a zuciya, cikin sanyin jiki tace "Ina Aslam ɗin yake to?" Tace "yana ɗakin anty zee yau a can yake kuma tun cikin dare nake ta ta kiran shi wayar shi yaki shiga." Katse kiran mummy tayi tare da cewa "Ina zuwa." Lambar Aslam ta shiga kira itama cikin rashin sa'a yaki shiga, ganin zai bata mata lokaci yasa ta shiga shirya wa dan tafiya gidan Aslam taje taga halin da marainiyar Allah take ciki. A waya ta sanar ma daddy abin dake faruwa shi kanshi lamarin ya daure mishi kai, baiyi kasa a gwuiwa ba yace ta shirya ya kaita, minti 30 ya dauke su zuwa gidan Aslam, har zuwa lokacin Aslam na part ɗin zee dan koda ya dawo masallaci can ya koma da nufin yayi shiri ya sallame ta gaba ɗaya sai ya koma part ɗin Asmah, horn din motar su mummy da kuma ƙaran bude get da mai gadi yayi shiya janyo hankalin shi, yana tsaye gaban mirror yana shirwaya zee na gefen shi tana taimaka mai, kallon juna suka yi da mamaki fal fuskokin su, waye da wannan sanyin safiyar a gidan su, kasa hakuri yayi ya karasa bakin windo ya daga labule ya leka zaro idanu yayi lakacin da yayi arba da motar Daddy kafin ya gama mamaki yaga Mummy ta fito ta nufi part din Asmah, da sauri ya saki labuleb ya juyo ya kalli zee data ke nan tsaye tana jiran taji su waye, yace cikin dan tashin hankali "Daddy da Mummy ne fa." Cikin kaɗuwa tace " A gidan nan da sassafe? To duk yadda akayi ba lafiya." Bai tsaya jin me zata ce ba ya zira jallabiya ya fice da sauri ganin haka yasa ta rufa mishi baya. A can kuryan ɗaki Mummy ta same ta durkushe tana hawaye da sauri ta karasa ta dago ta, ganin mummy yasa ta fashe da kuka, rarrashinta Mummy ta shiga yi "yi shiru Asma'u ya isa haka, yanzu zamuje asibiti insha Allah koma mai ke ciki zasuyi scanning mu gani, asibitin Dr nasidi zamuje babban likitan mata me kuma yana da wankin ido imma jinnu ne ko sihiri zai gane." Kasancewar sanye take da hijabin da tayi sallah yasa mummy kamo hannun ta kawai suka nufi kofar fita, daidai nan Aslam ya iso da sauri zee na biye da shi, ɗaga ido mummy tayi ta musu kallo daya sai taji wani haushin su ya tirnike ta suna can suna soyayya sun bar mata yarinya ita kadai zata mutu a banza ita fa shi yasa auren mai mata bai taba birgeta ba, sama sama ta amsa gaisuwar su, ta wuce su rike da hannun Asmah dole suka matsa mata a hanya, ganin yadda ran ta ke a bace, daddy na hango su ya fito ya bude musu gidan baya, zaunar da ita tayi tare da rufe mata kofar ta zagaya ta shiga mazaunin ta nada suka dauki hanyar asibitin Dr nasidi dake kwangila, suna fita Aslam na fitowa, hankalin shi gaba daya ya tashi dafe kai yayi ya shiga karanto innalillahi wainnailaihi rajiun, ganin haka yasa zee nufar dakin ta da gudu ta dauko makullin mota bata tsaya mai bayani ba ta shiga ta tayar ganin haka yasa shima yayi sauri ya fada ta bi bayan su mummy cikin sa'a ta cim musu saboda traffic light daya tsayar da su, koda suka iso asibitin sun taradda da layi duk da likita bai karaso ba sai Karfe takwas, duk wani zirga zirgan da za'ayi na bude file da sauran su Aslam ne yayi, so yake ya tambayi meke damun Asmah amma yana Shakkar mummy ganin yadda fuskar ta ke daure, kasa jurewa yayi ya nufi ta inda yasan zai iya sanin sauki, wurin daddy, a nan yake jin mekefaruwa, aiko dai hankalin shi ba karamin ta shiga yi ba haryaso yafi Asma'un shiga rudu, takwas daidai Dr nasidi ya iso, mutane da yawa ke gabansu amma kasancewar akwai sanayya a tsananin su, ɗan wani tsohon abokin daddy ne yasa aka musu wuru wuru wanda ba'a rabuwa dashi a Nigeria suka shiga, yana gama jin bayanin ta daga bakin Mummy kallo daya ya mata yasan lamarin ta akwai saka hannun mutanen ta a ciki, amma bai gaya musu haka ba, scanning ya fara mata take ciki ya bayyana yaya uku rerass da ransu da lafiyan su yan wata shida har an gama halittan su, bai basu bayanin komai ba saida ya gama daidai ta komai, duk wani abin da ya kamata ya mata yayi, ya bata duk wani taimako da ya dace sai da ya tabbatar yanzu komai normal, sannan ya nemi ganin mijin ta a office din shi, jiki a sanyaye Aslam ya tafi don tunda daddy ya gaya mai mekefaruwa jikin shi yayi sanyi, musabaha sukayi da Dr nasidi shima matashi ne dan akalla zasuzo tsara da Aslam din, dan da alama ma sunsan juna, bayan Dr ya nuna mai wurin zama ya zauna, farin takarda ya mika mishi tare da cewa " Da farko dai zan fara da cewa Congratulation Mr Aslam." Ya fada yana sakin kayataccen murmushi, kamar wani gaula haka ya tsaya yana kallon shi, zaka rantse baijin yaren da Dr nasidi keyi ne,ganin bai amsa faifan ba yasa Dr sake cewa "karbi mana dan uwa." Kamar mara jini a jiki haka ya miƙa jhannu shi nya karɓa,koda ya karba bai iya budewa ba sai rike wa yayi gam kamar wanda aka ba tikikin shiga Aljannah, Dr ganin bai bude ba yasa yace ka "Bude mana." Ba musu kuwa ya warware faifan ya fara binshi da idanu, wani irin yam yam yam haka ya ringa ji yana ratsa tsakanin kanshi da zuciyar shi, tabbas ba barci yake yi ba idanun shi biyu amma kuma abinda yake gani a rubuce jikin faifan ne yasa yake gani kamar mafarki yake, bayani ne akan cikin Asmah watannin Cikin da matsalar Cikin da kuma saka hannun Dr akan tabbatar da cewa yayi duk abin da ya dace yanzu komai nomal abu daya ne babu adadin babies din wannan kuma ya bar musu su jira ranar haihuwa, yana gama karanrawa dago kai yayi yace "Dr a mafarki muke ko a ido biyu?" Dariya Dr ya kwashe dashi, indai irin wadan nan bankauran ne ya saba gamo da su iri iri amma nayau na Aslam ya bashi dariya sosai, cikin zolaya yace "ko nadan mare ka ne sai ka tabbatar" ga mamakin shi saiji yayi Aslam yace "eh Dr pls ka mareni kozan dawo cikin duniya ta." Sai kuma hawayen farin ciki shaaa wanda shi karan kanshi Aslam din baisan wanda suka zubo ba, can kuma ya mike ya kaima Dr nasidi runguma,yana zuba mishi godiya, shikam dai Dr dariya yake yi, yana kara yimai congrat, lokacin daya fito daga wurin Dr zee da mummy suna dakin da aka ba Asmah bed rest na awa uku, daddy ne kawai a wajen daga yadda ya hango Aslam yana tafe da kuzarin shi fuskar shi a washe dauke da madaukakin farin ciki ba kamar yadda ya tafi ba yasa tun kan ta karaso ya mike ya tare shi, shima ganin haka yana zuwa kawai ya fada jikin Daddy ya rungume shi gagam cikin farin ciki ya shiga cewa "Alhmdllh daddy husnah tana dauke da ciki na, Ashe ciki ne da ita daddy har na tsawon wata shida bamu sani ba." Cike da mamaki daddy yace "Ciki fa kace Aslam, wane irin ciki, kodai baka ji da kyau bane." Yace "wlh daddy naji da kyau haka Dr ya fada kuma ya bani bayanin komai a rubuce." Da sauri ya sake shi tare da mika mishi faifan da Dr ya bashi, daddy na gama karanrawa ya fuskanci gabass ya daga hannu ya shiga jerowa ubangiji kirari, mutane sai kallon su suke yi, abinka da Nigeria, suko ko a jikin su basu san ma suna yi ba, zaro waya Aslam yayi tare da cewa "daddy bari na kira umminmu na sanar mata." Hana shi daddy yayi ta hanyar kama hannunshi suka nufi dakin da su mummy ke ciki. Asmah na kwance tana maida barcin da bata samuyi jiya ba,zee na zaune a kujeran dake gabanta ta zuba tagumi yayinda mummy keta safa da marwa ta kasa zaune ta kasa tsaye jira kawai take Aslam ya dawo daga wurin Dr taji menene ke damun Asma'un ta, suna shiga ta dakata tare da juyowa da sauri ta kalli Aslam cikin yanayin damuwa tace "me Dr yace?" Bai iya amsata ba sai wani irin kyakkyawan murmushi daya ke binta dashi, daga ita har zee sororo suka tsaya suna kallon shi, daddy ne da har yanzu faifan nan ke hannu shi ya miƙa mata tare da cewa, "Dr yace nan da wata hudu amaryar ki zata iso sai ki fara shiri." Bata bi takan zancen daddy ba dan a halin yanzu bata shi take ba, tun kafin ta gama karanta bayanin dake rubuce ta zube a gurin ta shiga gabatar da shujudul-shukur, tana dagowa kuma ta rungume Aslam tana hawayen farin ciki ta shiga ce, "Alhmdllh! Alhmdllh! Alhmdllh ala kulli halin Allah kun gode maka." Aslam kam murna kan murna wai yau shine Mummy ta rungume kai da alama dai idanunta sun rufe ne bata san shita rungume ba, shi yanzu ko bindiga za'a saka mai aka, yaushe zai iya tuna when last ya kiji a jikin mahaifiyar tashi, zee ma tayi farin ciki sosai dan koda ta samu cikin ta na biyu bata yi irin farin cikin da tayi a yanzu da bayyanar cikin Asmah ba. Tun a asibitin suka shiga buge bugen waya suna gaya wa yan uwa da abokan arziki, baga Aslam ba baga mummy ba kai har daddy ba'a barshi a baya ba wannan karon, tunda Aslam da daddy suka shigo dakin ta farka, sai dai bata bude idanun ta ba,duka abin da ke faruwa a kunnen ta, hawaye ne kawai ke ziraro wa daga idanunta ba tare da kowa ya kula ba, suna can suna ta murna da buge bugen waya, kan kace kwabo kuwa tuni asibiti ya fara cika da yan uwa kwace ce musu akayi asman ta haihu, daddy tafiya yayi bayan komai ya lafa ya bar mummy idan anyi sallama Aslam ya maido ta, Dr ganin sunyi yawa adakin yasa yace su fita zuwa waje a bata dama ta huta nan da awa biyu ma zai basu sallama su tafi gida gaba daya, duk fita sukayi a dakin aka barta ta huta kamar yadda Dr ya bukata, Aslam ne bayan Dr ya tafi ya lallabo ya koma dakin ba tare da kowa ya kula da shi ba, tun dazu yake ta neman wannan daman na samu ya kebe da ita ya zama shine mutum na farko da zai fara yi mata wannan albishir din, a kujeran sake facing dinta ya zauna tare da kama hannayenta ya rike, ya tsirawa fuskar ta idanu yana kallonta, haweye da yaga yana zirarowa a hankali ta gefen fuskar ta ne ta tabbatar mai da idanun ta biyu, murmushi ya saki a hankali cikin rada yace "Bazan hanaki zubar da hawaye ba husnah ta, ki zubar da abinki nasan na farin ciki ne dan nima na zubar da nawa." A hankali ta ware idanuwan ta akan fuskar shi, tace "Ya Aslam da gaske ne, abin da nake ji kuna fada cewa wai ina dauke da juna biyu har na tsawon wata shidda, kenan nima zan haihu kamar kowacce mace." Girgiza mata kai ya shiga yi cike da karfafa gwuiwa yace "kwarai husnah kina dauke da ciki Dr ya tabbatar mana da haka, insha Allahu very soon zaki haihu ki zama uwa kamar ko wacce mace." Mikewa tayi zaune ta fada jikin shi ta rungume shi ta fashe da kuka tare da cewa "Ahmdllh alakulli halin Allah mun gode maka, wlh zuciya har yanzu ta Gaza daukar lamarin da sauki ji nake kamar zata fashe tsabar farin ciki." Murmushi yayi yace "Haka Allah yake lamarin sa, mahakurci dama ance shine nawadaci wata rana." Kamar yadda Dr yayi alkawari awa biyu kawai suka kara ya basu sallama tare da bata magungunan da zata ta amfani dashi na nasara dana musulunci, suka dunguma zuwa gida,ranar Asmah ta kara tabbatar lallai ita yar gata ce, sai tururuwan zuwa gaishe ta akeyi ana taya ta murna, tare da al'ajabin yadda lamarin ubangiji ya kasancewa, wadan da ke nisa kuwa sai kiran waya akeyi har daga dangin mahaifanta itama. Kamar jira cikin yake yi a gano shi, ko sati ba'a rufe ba ta kama wani irin laulayi mai zafin gaske, duk abinda ya kamata ace tayi su tun ciki na karamin batayi ba sai yanzu, take kuma cikin ya fara wani irin girma yana fitowa fili da kadan da kadan kafin ta rufe wata daya da bayyanar shi ya fito rass ya zama wani tukeke kamar dan wata tara ba bakwai ba, ga laulayi daya sakata a gaba ba dama ta ci abinci sai amai ba dama ta shaki abin da bai mata ba sai amai , tuni ta koma abin tausayi duk wanda ya ganta sai yaji kamar ya zubar mata da hawaye,da kanta tace ta barma zee kwanan ta sai ta haihu, kafin wata na takwas girman cikin ya fara basu tsoro,kuma duk bayan sati biyu Duke zuwa asibitin Dr nasidi yace musu ba komai normal ne karsu damu, wannan suke samun relief, tana shiga watan haihuwa mummy tace ya tattarota ya dawo da ita gaban ta dan ita tsoro take ji,kar nakuda ya taso mata gida babu wani babba daga ita sai zee kuma dukansu bawai sun san kan abin sosai bane, shima bai musa ba haka nan ya kaita, aka koma aka zura sa sarautar Allah idanu kowa ya dukufa da addu'a ba dare ba rana, Aslam har masallatai da makarantun islamiyya yake bi yana bada saraka akan lamarin, Asmah kam tana jin jiki ba kadan ba ko tashi bata iyawa ita kadai cikin rinjayanta yakeyi sosai, ta dena zuwa awo sai shi Dr ya biyo ta gida ya duba ta, yana kuma kara kwantar masu da hankalin akan cewa komai na tafiya yadda ya kamata su dai kawai su dage da addu'a, har ta fita wata na tara shiru haihuwa zaizo bai zoba tun suna saka rai yau gobe jibi amma shiru kake ji wai malam yaci shirya yasha ruwa, mummy kam tuni ta rufe fita ko ina, Aslam ma kullum a gidan yake wuni kwana ne kawai bai taba yi ba haka zai saka ta a gaba yana taimaka mata suyi ta zagaye gidan suna exercise. Ranar da cikin ya shifa wata na goma sha daya ta wayi gari garau ranar dan har wani karfi takeji na musamman ba kamar kullum ba, dan ranar har mikewa da kanta takeyi kuma tayi exercise sosai da kanta ranar ba tare da ta jira Aslam ba, koda ta gama exercise din ta a falo ta samu mummy, sannu Mummy ta mata har tana tsokanar ta da cewa in ta haihu sai ta Zane babyn dan ya wahalar mata da ƴarta ya shige cike ya nemi guri ya kwanta to dai a kwai ranar ƙin dillanci, tana murmushi tace "mummy bari na watsa ruwa na dawo." Koda ta shiga dakin da aka ware mata a ƙasa tube dogon rigar ta na robaroba tayi ta daura zanin mummy babba ta shiga toilet, ita karan kanta tana mamakin karfin da lafiyar da take ji yau a jikin ta wanda rabon da taji irin shi tun kafin baiyanar cikin ta, tsugunawa tayi da niyyar yin fitsari, ji tayi marar ta yadan daure kasa mikewa tayi daga tsugunan da tayi, cikin abin da baifi minti biyu ba taji wani irin nishi mai mugun karfi ya taso mata daga tsakiyar bayan ta, kafin tayi wani yinkuro sai ji tayi wani abu na kokarin rasto kasan ta ya fito duk da bata san ko menene ba ta tsorata ainun kwala kiran sunan mummy tayi da mugun karfi, mummy dake falo bata kai ga tashi ba a gigice ta mike ta nufin dakin da Asmah ta shiga dan yin wanka ko kafin ta karasa toilet din har baby daya ya fado, da sauri mummy ta ta karasa ta tallabo ta tana fadin "subhanallahi." Ina! Asmah bata san inda kanta yake ba kafin ta kai ga kara cewa a wani abu wani babyn ya kuma fadowa, bata gama mamaki dayan ma ya fito fit tare da mabiya a lokaci guda..... ba editing ayi hakuri Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ FREE BOOK {Nasaukar da wannan book ɗin ga duk wacce ta rasa hahaifiya Allah kajiƙan iyayen nu.} Page 132 Wani irin haihuwa Asma'u tayi mai ban mamaki gaba d'aya da tasowar na'kudan da haihuwar tayi shine cikin abinda baifi minti biyar ba, tsabar rud'ewa mummy rasa me ya kamata tayi, tayi ,kukan jinjiran daya karad'e kunnenta ne ya yasa ta dawo cikin hayyacinta da wani irin sauri ta fice daga toilet d'in jakar da suka had'a kayan haihuwa ta bud'e, zazzage shi tayi ta d'auki kwalin reza da sauri ta koma toilet d'in, yanke cibiyan tayi ta d'auki zanin ta da Asmah ta rataye ta raba shi uku ta nad'esu a ciki ta kaisu kan bed ta jere su, ta koma toilet d'in, heater d'in ruwan zafi ta kunna ta daidaita shi cikin abin da baifi awa d'aya ba mummy ta gama gyara Asmah da babies d'inta ba tare da kowa a gidan ya sani ba,Asmah tuna barcin gajiya ya kwashe ta babies d'in ma da suka ji ruwan zafi shiru sukayi basu sake kuka ba tunda suka yi tunda sukayi na fadowa duniya wanda yake wajibi. Sai da ta tabbatar komai ya daidai ta sannan ta d'auki wayar ta daddy tafara kira, dan shaida wa wannan daddad'an labarin mai dauke da abin al'ajabi, yana zaune a office ya ga kiran mummy ya shigo sai da gabanshi yadan fad'i kasancewar yasan ya barta da mai lalura a gida , da sauri ya d'aga dan dama shima yana jiran ya d'an samu saukin aiki ne ya kira su yaji ya Asman take, haka yakeyi kusan duk inya fita bayan wasu y'an awanni sai ya kira yaji ya take, ko amsa sallaman ta na kirki baiyi ba ya shiga tambayar ta Asmah da lafiyar ta, murmushi tayi mai sauti tare da cewa "To daddyn Asma'u kyakkyawan labari, amma sai an bani goron albishir." Jin yadda take ta sakin murmushi yasa ya tabbatar lallai abin mai girma ne, cikin d'an yanayin za'kuwa yace "fad'i duk abin da kike so zan baki." Tace "ka tabbatar." Yace "In kina so sai na rantse." Tace "ba sai ka ranste ba, goro na shine (No kishiya in my hause)." Dariya yayi yace "har kullum kedai zancen ki kenen, kuma na sha fad'a miki tunda kuruciyar mu kin isheni riga da wando rayuwar duniya A'isha ta." Dad'i taji ya mamaye mata zuciya cikin yanayin farin cikin da take ciki a yau tace "nagode sosai mijina abin alfaharina." Yace "yanzu dai duk ba wannan ba, ki Adana min wad'an nan dad'ad'an kalaman naki sai na dawo gida, fad'a min albishir dina dan wallahi na 'kagu naji." Dariya ta shiga yi mai, cikin son taja mai rai, sai da taga ya koma rok'on ta cikin marairaice murya kamar zaiyi kuka, sannan tace "Asma'u ta haihu." Zaro ido yayi tare da cewa "wacce Asma'un, kee! A'isha bana son irin wannan tsokanar, dan Allah." Tace "wallahi ta haihu kuma yaya uku rerass." Nan fa Daddy ya k'ara yarda cewa lallai tsokanar shi take, duk da yasan cikin Asmah ya wuce watan haihuwa bai taba bata haihuwa yau ba, saboda garau ya baro ta gida baiga wani alamar nak'uda a tare da ita ba, kuma da fitar shi da kiran wayar mummy tace mai Asmah ta haihu duk baifi awa biyu ba, jin shi shiru yasa mummy katse kiran ta, tasan dole zai kira kokuma ya biyo baya dan ya tabbatar, bayan daddy Ummi ce next da mummy ta kira sannan Mami, duk wanda ta gaya wa Asmah ta haihu sai ya karya ta, Mami ma ko katse wayar basuyi ba sai gata a part d'in mummy da ta diro kamar daga sama, tana tabbatar wa kuwa ta shiga murna tana hamdala kamar ta taka rawa dan farin ciki a wani bangaren kuma tana al'ajabin yadda wannan lamarin ya kasance, can kuma ta shiga kiran su batool d'aya bayan d'aya tana fad'a musu. Mummy da kanta ta je ta sanar wa hajiya mama da alhaji baba, aiko tare suka dawo part din ta da hajiya mama, kan kace kobo magana ya karad'e family Asmah ta haihu yan uku, duk wannan bidirin Aslam bai da labari dan mummy bata kira shi ba Mami kuma tayi tunanin mummy ta gaya mai shi yasa bata kira shi ba. Ya gama shirin shi na tafiya office kenan suna sallama da zee yana ce mata zai biya yaga jikin Asmah kafin ya tafi, ita kuma tana bashi sallahun gaisuwa wayar shi tayi ringing, Amir ne mai kiran hakan yasa bai bata lokaci ba wajen daga wa, daga can bangaren Amir yace "angon k'arni angon k'arni congratulation d'an uwa, yanzu Abba ke kira na wai Asmah ta sauka, gaskiya baka da kirki shine ka kasa kira na sai Abba ne ke gaya min." Duk wannan surutan na Amir tuni Aslam ya dena fahimtar shi dan karshe ma dauke wayar yayi daga kunnen shi yana sake maimai ta kalaman Amir, wai Asmah ta sauka, sai ya rasa ma wani irin sauka yake nufi to, bai gama wannan mamakin ba wani kiran ya sake shigo wa daga Dr bash shima dai congrat yake mai, wannan karan dai dakatar da Amir yayi da cewa "kai dan uban ka yi min dalla² wacece ta haihu wai kuke ta rigar rigen kira na zaku rudar dani." Daga cen bangaran Dr bash yace "wai kai a komai saika saka iskacin ne? kana da wata mata Asma'u ne banda Asmah bamu sani ba, nima ina hospital yanzu teema ke kirana wai Asmah ta haihu yan uku yanzu Mami ta kira ta itama ." Duk wannan bayanin na bash ma iska yake yi, dan tuni Aslam ya katse kiran ya nufi gurin mota cikin sassarfa yama manta tsaye suke da zee da little sai da yaga sun biyo bayan shi, bai amsa tambayar da zee ke mai na cewa meke faruwa ba sai cewa yayi ta shigo su tafi. A tare suka iso da Daddy, bayan sunyi parking gaisawa suka tsaya yi har kasa zee ta tsuguna ta gaida da daddy a mutumce shima cike da kulawa ya amsa mata tare da kamo hannu little mikewa tayi ta nufi part fin Mummy inda tasan Asmah take, gaisawa sukayi da Aslam bayan tafiyar zee, daddy yace "baka tafi office d'in ba bayàn wannan uwar lattin da kayi, har kullum kai baza ka canza ka daina wasa da aikin ka ba. Wanan inda a wani wajen kake aiki ba gida ba da tuni sun manta sun Dade da korar ka." Yana Sosa keya yace "Ayi hakuri daddy wlh wani labari naji mai kama da almara shine na biyo dan na tabbatar." Daddy yace "Au harda kai takira Ashe , to mu karasa ciki muga zahiri." Falon mummy cike da mutane tuni batool, da Khadijah, sun karaso kowacce da danta yayan sun zama yan samari dan suna neman shekara bibbiyu kenan, ga hajiya mama ga Mami ga Abba ga kamal ga ya Rabi'ah kai falo dai cike da mutane ga kuma makota ga kawayen mummy na kusa, zee na shiga batool ta d'ebe ta ta watsar tare da maida kai gefe har gobe bata kaunar zee duk da kuwa irin yadda zee din ke nuna mata kulawa, Mami ce ta fara mata lale da barka tana ga uwar yan uku ta karaso, itama wurin mamin ta nufa dan a nan taga fuska, a mutumce ta gaggaisa da mutanen falon gaba daya harda su batool daya kamata ace su suka gaishe ta, yadda tayi gaisuwar a mutunce haka suka amsa mata da kulawa suna yi mata barka masu tsokanar ta nayi irin su hajiya mama da Mami, ita dai amsa barkan kawai takeyi ba tare da tasan na menene ba, cikin haka Aslam da daddy sukayi sallama nan kuma aka shiga wani sabon gaisuwar da barka barka ,daddy yace "wai kuna nufin da gaske ne kenan Asma'u ta haihu." Hajiya mama tace "kwarai kuwa d'an nan ga zahiri kana gani, Allah ya amshi addu'a ya kawo wa yarinya abu cikin sauki haka lamarin gwanin dad'i." Daddy yace "Allahu akabar Allah muna gode maka daka amshi addu'an mu, ina dan tselan uwan yake na zuzzuge shi da carbi ladan wahalar min da y'a da yayi duk da dai a karshe an rabu kalau." Mummy tace "d'an tselan uwa ko yan tselan uwa, suna ciki suna baccin gajiya, to an zaunu a ciki wata goma sha d'aya fa." Zaro ido daddy yayi yace "wai kina nufin da gaske ukun ne ba zolayata dama kike yi ba." Yadda yayin ne gaba d'aya ya basu dariya suka shiga darawa. kamal ne ya budo hotonsu da Khadijah ta dauka d'azu da ta shiga ganin su ya mik'a wa daddy, kabbara da kirari daddy ya shiga jerowa ubangiji yana kara gode mai a bisa wannan gagarumin kyauta daya basu, first in history a zuri'ar su, an haifi y'an uku, yana kara kallon su yace "to wai wasu iri ne naga dai wannan mai d'an kumatuttukan nan kamar fanke, kamar macece." Ya fada yana pointing d'aya daga cikin su a jikin screen din faskeken wayar kamal, dariya duk suka saka mummy tace "wato itace amaryar tawa kenan ko? To duka yan mata ne kwantar da hankalin ka, sai ka darje." Aslam kam tunda suka shigo falon yaga an shiga haya baya ya samu ya lallaba yashige dakin Asmah ba tare da kowa ya kula da shi ba, suna kwance daga ita har yaran barci suke yi, tunda ya tura kofar ya hango su, zuciyar shi ta shiga dukan uku uku ji yake kamar a kan iska yake tafiya lokacin da yake karasawa gaban gadon dukewa yayi ya zuba musu ido kamar bai ko keftawa kamar wanda ya warke makanta kokuma wanda bai taba ganin jarirai ba, a fili ya furta "yanzu wadannan duka nawa ne ni Aslam, duka nan mallakina ne." Sai kuma yaji hawaye farin ciki ya ziraro mishi, durkusawa yayi a gurin ya gabatar da sujudulsh- shukur, yana dagowa ya koma gaban yara ya tsura musu idanu yarane kyakkyawan gaske kamar y'ay'an larabawa kama suke yi sak da juna kamar an tsaga kara manya dasu kamar ba yan uku ba, a hankalin ya ringa ba kowacce peck a goshi yana yi mata addu'a yana tofawa, sai da ya gama dasu ya maida kallon shi kan Asmah tana kwance tayi fiyaut da ita, wani irin haiba da annuri yake gani yana fitowa daga fuskar ta, sai ya ga ta wani kara mishi kyau sosai a idanun shi, karasawa yayi daidai saitin face din ta, a hankalin ya shiga saukar da kanshi yana son ya subaci labbanta da yaga sun kari yi mai wani pink kamar ta shafa jambaki, bai kai ga hade bakin nasu ba mummy ta turo kofar ta shigo da sauri ya janye fuskar shi, amma abinka da mara gaskiya ganin yadda yayi wuri wuri yasa ta harbo shi a kallo daya, daure face tayi tace "To bismillah faruwa da iyawa, to tun wuri bari na gaya maka bazan laminci wannan iya shegen ba, idan na dauki na Amir naka kam bazan dauka ba danshi na mishi uzirin ita kadai gareshi kai kuwa fa? Wai da yaushe ma ka tsallakemu a falo ka shigo nan." Ta karashe maganar cikin tsatstsare shi da idanun ta, Sosa keya ya shiga yi yana yan kame kame, tace "maza ka fice min da gani,ka karasa kama Dr iso yazo zai duba su ita da yaran." Dr nasidi ya duba ta sosai ya mata dinki danta samu tear sai da ya tabbatar babu wani sauran matsala sannan ya rubuta mata magunguna, ya duba yaran suma sannan aka fitar dasu aka ba kowa ya dauka cike da farin ciki sai hotona ake musu wasu na daurawa a media masu sakawa a status nayi masu tura a Facebook nayi kai harda su tiktok da Insta sai da kamal ya daura, (yan dama ta biyu fans masu yin tiktok a hya kallo lahiya😂 in kunyi kwa dauko mana mu gani muma.) Asmah taga gata iya gata a wajen yan uwa da abokan arziki ko ta ina tururuwan zuwa mata barka akeyi harda ma wa'inda ba dangin iya ba na baba irin su AyshaNalado😁 kula kuwa ta kawane bangare samun shi take yi baga mummy da daddy baga Mami da Abba ba kai har su Alhaji baba ba'a bari a baya ba, Ummi kam tun kwana uku da haihuwa ta iso kuma a part mummy ta sauka wannan karon dan karma tayi nisa da yaran, kafin ranar suna ya zagayo ta murmure tayi wani irin fresh ta dawo yar cakwai cakwai da ita asalin Asma'un ta babu wanda zai ce itace ta haifi y'ay'a har uku a cikin ta, zee da Aslam kam kullum sai mummy ta koresu suke tafiya dan in suka zo tun safe sai sukai sha daya a gidan hatta little ba'a barshi a baya ba son yaran yake kamar kamar me da an dauke su zaice a bashi kannen shi idan anki ya saka rigima wata ran sai mummy ta make shi dake ita fire fire ce bata daukar fitsara, sai da daddy yaga abin yayi yawa ya taka ma Aslam birki shine suke wucewa tara, ana gobe suna zahra ta iso ita ma da babyn ta dake gudu ko ina, tana daukan yaran tace "um lallai yara kunzo inda ake neman ku, Asmah da y'ay'an kanta wai aiko zaku sha kula aradu." Ranar suna tun da farar safiya gida ya fara daukar harama. Kowa a k'age yake da yaji sunan da Aslam ya saka wa y'ay'an shi dan an kad'a an raya yaki fad'a duk wanda ya tambaye shi cewa yake sai ranar suna, dan rashin ta ido har Alhaji baba daya tambaye kin fad'a mai yayi. Hatta Asmah bata sani ba daga shi sai zee suka san sunan yaran, aiko abin ya matukar kayatar lokacin da liman ya baiyana sunan yaran, mummy ce da Mami da kuma Ummi, aiko abin yama su mummy dad'i kamar me Aslam yasha ruwan albarka ranar kamar ba gobe. Haka akaci suna aka sid'e abin sai wanda ya gani, suna na gani na fad'a akayi abinci da abin sha enough anyi taron da a tarihin gidan ba'a taba yin taron daya kai wannan cika ba, dan yan dama ta biyu fans ma kawai mun ishi gayya, mu kusan dari hud'u muka zo kuma duk saida mukaci mukayi hani'an mani'an harda masu guzirin na dumame😅. Asmah da yara sun samu kaya bana wasa ba dan saida aka cika store biyu manya manya da kaya bana yaran ba bana uwar yaran ba, kudi kuma cash ta samu yafi miliyan biyar daga abokan Aslam na kusa dana nesa, banda masu transfer wannan kuma Allah kadai yasan adadin su, masha Allah yara kam sunyi goshi harda keya😂 . Second 2 d last page💃💃💃💃💃💃 luwaiiii Oum Ummeetarh 07041130088 💖DAMA TA BIYU💖 BY ~AYSHA NALADO~ {Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu} Paga 133 🔚🔚🔚🔚💃 Bayan taron suna ya watse baƙi na nesa dana kusa kowa ya koma gida lafiya, a nan family hause Asmah da babies ɗin ta suka ci gaba da zaman jego, basu canza wa yaran wani suna ba da sunan da suke kiran iyayen nasu suke kiran su, wato Mummy, Mami da Ummi. Suna samun kula sosai ta ko wane bangare,kafin arba'in yaran sun murmure sun murtuka wani uban ƙiba dumi dumi dasu gwanin sha'awa idan ka gansu zaka rantse yan 3 month ne, haka itama Asmah tayi wani irin kyau sahihi fatar ta ya ƙara haske da gogewa kamar wata balarabiyar masar idan ka ganta baza ka zata ma tayi aure ba balle har ta haifi ƴaƴa har uku , gyara take samu na musamman daga gurin mummy, abin ba'a cewa komai, tunda jini ya dauke mummy bata tsaya wata wata ba ta shiga gyara parta ciki da bai gyara kuwa bana wasa ba, a cewar ta wai tana da kishiya, dole sai ta tashi tsaye sosai akanta dan bata so ta zama bora a gurin miji, hankalin kwance take jegon ta don yaran kwata kwata basu da rigima madara suke sha basu damu da su sha nono ba, itama bata basu sai taga ya cika yana zuba ko ya fara mata ciwo sannan take basu, ko kuma mummy ta takura mata, Aslam kuwa ya zama abin tausayi kullum kafar shi na gidan ba dare ba rana, duk safiyar duniya sai yazo ya duba su kafin ya tafi aiki, haka ma da yamma idan ya dawo yaje gida ya huta zai sake dawowa tare da little dan shima yaron shegen kulaficin yaran gareshi, sai dare zai tafi,haka zai tasa yaran a gaba ya dauki wannan ya ajiye ya dauki wannan, tsakanin shi da Asmah kuwa sai gani sai hange, gaisuwa kadai ke hadasu, dan mummy ta kasa komai ta tsare idan sunyi doguwar fira to a waya ya kiranta, ba karamin wahaluwa yakeyi da rashin ta ba, duk da ga zee a gefen shi amma baya jin zata iya kashe mishi kishin Asmah, yana maneji sosai da ita yana rage zafi amma fa baya samun yadda yake so ko kaɗan, zee daidai da fruits bata san ta sha da sunan gyara ba, haka nan take kara zube, wai dan ma ana cin me kyau a sha mai kyau kenan da ba'asan ya abin zai kaya ba, kullum cikin lissafin kwanakin dawowar Asmah yake yi, ranar da suka cika kwana talatin da tara a gareshi kamar jajibarin karamar sallah haka yake ji, tuni ya saka an gyara mata part din ta tsab an share ko'ina an kyalkyale sai kamshi da sheki ke tashi, ya ware dakuna biyu ya gyara wa babies, daya an shakare musu shi da kayan wasa da kayan karatu da duk wani tarkace na yara,dayan kuma ya saka musu saitin baby beds da wardrobes har guda uku masu mugun kyau da tsada, ba karamin kudi ya narkar wa yaran nan ba dan harta kayan sawan su sai da ya ciccika musu wardrobes dinsu da shi , washe gari kuwa cike da zumuli ya farkar, tun da sassafe yaje gidan yana sauraren yaji Mummy tace yaje ya dawo ya dauke su shiru bata ce ba har lokacin tafiya aikin shi yayi, jiki a sanyaye ya tafi, ranar daga gurin aiki baije gida ba still nan ya dawo amma har yamma bata ce mai komai ba bai ma ga alamar ana wani shirin tafiyar su ba, haka ya karaci wunin shi a gidan har zuwa dare ba wani alamu, da zai tafi sau biyu yana ma mummy sallama tana cewa a gaida mutanen gida, karshe dai ya gaza hakuri yayi, yaga gara yaje ya tunawa mummy yau ne fa arba'in ɗin koda da wayau ne basai ya fito fili ba, har yakai bakin kofa ya dawo yana sose keya yace "mummy nace ba sai an turo kowa dan gyara ɗakin nata ba nasa duk an share an gyara mata shi tun jiya tunda naga yau ne zasu cika arba'in din." Hararan shi Mummy tayi tace "Waya saka? Da wa kukayi in suka yi kwana arba'in zasu dawo, to bari kaji bazan baka ƴata da kananan yara da basuyi kwari ba har uku, sai sunyi kara kwana biyu zasu dawo zuwa lokacin yaran sun yi kwari sosai." Ji yayi kamar mummy ta kwada mai guduma a kai,tsura mata idanu yayi kamar ranar ya fara ganin ta, harara ta kara watsa mai tace "meye kake kallo na kamar wata sabuwar halitta in kana da magana ne kayi ina jinka." Da sauri ya girgiza kai tare da cewa "ba komai mummy." Tace "to oya a gaida gida." Jiki a sanyaye ya fice, tun daga ranar yake ta zuba ido mummy tace ga ranar da zasu dawo shiru shiru har suna neman kwashe wata biyu, zuwa yayi ya samu Abba ya gaya mai, Asma'u tayi arba'in tun tuni mummy ta hana ta dawowa wai sai yara sunyi kwari, dariya Abba yayi yace "yanzu dai ƙaran mummy ka kawo min kenan ko? Kawai ka fito fili kace mummy ta rike maka mata." Zaro ido yayi tare da cewa "A'a Abba wlh ba haka nake nufi." Cikin dariya Abba yace "ɗan nema bari zan samu daddyn ka da maganar in sha Allah za'asan abin yi." Da taimakon Abba da daddy aka samu mummy da'ker ta bari Asmah ta koma ɗakin ta, ba haka taso ba taso ne sai sunyi wata uku cur sannan su koma, itama Asmah a nata ɓangaren kewan mijin ta take amma ko shi bata taba nunawa ba bare kuma mummy. Saka ranar komawar mummy tayi jibi, Aslam kamar ya taka rawa dan murna sai wani rawan jiki yake yi magana daya biyu Asmah, motsi kaɗan Asmah har sai da zee taji abin ya sosa mata zuciya, a cikin satin babu abinda Asmah take sai kai ziyara gidajen yan uwa, da abokan arziki, har gidan su batool da Khadijah da Amira duk taje, Allah sarki zahra ita kadai ce bata kusa. Ranar da mummy ta saka zasu dawo da sassafe yaje gidan wai yazo daukar su, mummy tace yaje ya dawo sai da daddare kamar yayi kuka, fushi yayi ya tafi yana surutai a zuciyar shi, harda su rantsuwa in suka koma basu ƙara zuwa gidan sai bayan wata biyar. Ko kafin ya dawo da daddare sun gama shirin su tsab shi kadai suke jira, ana isha'e kuwa sai gashi, already ta riga tayi sallama da kowa na gidan su Mami da Abba, hajiya mama Alhaji baba daddy duka ba wanda bata sallama ba, yana zuwa kawai da mummy suka ƙara sallama ya dauki mummy karama ita kuma ta goya Ummi ta dauki Mami a hannu suka tafi, suna isa zee tazo ta tarbe su da murnanr ta suka rungume juna cikin farin ciki gaskiya tayi kewar Asmah abokiyar zama ta gari, duk da kishin da ke dankare a ranta hakan bai hanata nuna mata zallar farin cikin ta da dawowar ta ba. Har part din ta, ta raka ta tana dauke da ummi data sauke daga bayan ta, little sai tsalle yake yi yana murna mummyn shi da ƙannen shi sun dawo, rungume shi tayi itama tana karajin son yaron a ranta duk da ta haifi nata ko kaɗan son da take ma yaron bai ragu a zuciyar ta ba sai ma karuwa da yayi, saboda yadda yake nuna son nata ƴaƴan shima, basu wani zaunar ba zee ta kama hannun little tace su tafi sai da safe yaron harda kuka Asmah tace " ki barshi mana anty zee yaro da ɗakin mummyn shi." Zee tace "ba yau ba anty Asmah sai kin gama cin amarci." Ta karashe zancen cikin zaulaya da ɗan murmushin ta na yake a fuskar ta, da sauri ta sa kai ta fice daga dakin, ko rakiya Aslam bai mata ba dan zumuɗi, Asmah ce tamai singnal da ido alamar yaje ya rakata mana, shima da idon ya mata alamar bazai je ba, hararan shi tayi ta haura sama dan ta watsa ruwa ta na shigewa ya maida kofar falon ya rufe da key alamar ya gama fita kenan, ya kwashe yaran ya kaisu dakin su ya kwantar tunda duk a koshe suke ya shiga jijjigasu ba bata lokaci kuwa suka yi barci, dama haka suke yi idan barci zasuyi a tare sukeyi haka ma kuka da daya yayi abu sai sauran su kama suma. Ta samu dakin ta fes sai kamshi ke tashi yasha gyara sosai an shimfede bed din da Sabon zanin gado fari kal mai shegen taushi,kayan ta, ta tube ta daura tawel ta shiga toilet ta watsa ruwa, tana fitowa, ta tsaya gaban mirror ta shafa mai tare da shafe jikin ta lungu da sako da turaren da mummy ta bata a dan kwalba yanzu da zata dawon tace tayi amfani dashi yau idan taje gida ita karan kanta kanshi turaren ya kashe mata jiki, lokaci guda ya saukar mata da kasala tare da wani irin feeling mai zafi dama ga gyara ta sha harda na fitar hankali ,kayan barci ta dauka masu kyau riga da wando irin na turawa ta saka tazura silifas d'in ta na d'aki ta doshi falo da nufin ta dubo Aslam da yara, wayam taga falon ba kowa, cike da mamaki ta karaso tsakiyar falon, sai kawai gani tayi an kashe wuta lokaci daya ko ina yayi dumɗum da duhu, ita uwar yan tsoro take hantar cikin ta ya kaɗa, ta fara jero addu'o'i, tare da laluben hanya, ji tayi an taɓa kafaɗar ta ta baya, kara ta saki tare da juyowa ta bayan, tana juyowa ta sake ji an kuma taɓa ta, taƙarƙarewa tayi zata zunduma ihu, da sauri ya saka hannu ya rufe mata baki, tare da rungumota gaba daya jikin shi, jin haka yasa ta shiga zazzare ido daidai nan kuma wutar falon ya dawo, sake mata baki yayi yana mata dariya, ganin shine yasa ta sauke wani nannauyan ajiyar zuciya tare da fashewa da kuka shagwaba tana dukan shi a kirji, hada hannayen ta yayi ya rike yana sunsunar jikin ta yana lumste idanu, ganin haka yasa ta shiga mustu mutsun kwacewa, surar ta yayi bai dire a ko ina ba sai bed room ɗinshi, ya zaunar da ita a bakin gado. Fita yayi sai gashi da wani kwali mai kyau sai kalli yake yi mai dan girma an daure shi da wani zare zare mai shainshain abin gwanin birgewa, yana zuwa ya duka a gaban ta tare da mika mata kwalin yana sakar mata murmushi, da ido ta mishi alamar nata ne ya girgiza mata kai alamar eh,hannu tasa ta karba ji tayi kwalin da ɗan nauyi ajiyewa tayi a gefen ta, yace "kyauta ce ta musamman ki bude ki gani." Cike da zakuwan son ganin meke ciki ta shiga kwance zaren da aka kulle kwalin da shi, tana gama kwancewa ta saka hannu ta zare kwali na saman dan dama kife suke da juna, abin da ta gani acikin ya bayyane ya saka ta saurin zaro idanu waje da sauri kuma ta juyo ta kalle shi, sakar mata murmushi yayi tare da dage mata gira ɗaya,sake mai da idanun ta tayi kan kwalin, dan kwalelen gasashen kaza ne gashin injin sai maiko yake yi da tashin kamshi, tsintar muryar shi tayi yana cewa "kazar amarci ne na taho dashi kar ayi na wancen karon." Kallon shi tayi ta sakar mai hararan wasa tare da cewa "wani irin amarci Kuma." Yace "amarcin da zamu ci yau." Dariya tayi tare da cewa "yau naga sabon salo hammata a dryer." Yace "oh dariya ma na baki ko, yayi kyau." Kwafa yayi tare da cewa "yarinya in zaki ci ki rage zafi garama kici dan yau idan kika shiga hannun na hmm ." Ya karashe maganar yana girgiza kai tare da sakin wani shu'umin murmushi, wanda bata fahimci ko na menene. Tace "ai dole ma naci wannan kaza kaji yadda kamshi ke dukan hanci na wlh har miyau na ya tsinke daga gani wannan tashin special ne." Ta karashe maganar tana daukar ɗan wuƙa da fork dake gefen Kazan ta yaga ta kai baki, lumshe ido tayi tare da cewa "um! um! um! ummm! So yummy gaskiya ban taba cin gashi mai dadin wannan ba." Gutsirowa tayi takai bakin shi tare da cewa "ci kaji wlh shegen daɗi." Ya girgiza mata kai yana murmushi, dage kafaɗa tayi alamar kawa kanka, tana ci tana zuba santi a haka har taji ta koshi, ta rufe kwalin tare da cewa "um bari naje na saka a frige gobe na dumama abuna da safe." Ta mike da kwalin a hannu ta nufi kofa ji tayi caraf ya cafketa ta baya tare da yin sama da ita, cikin kunnen ta ya raɗa mata "ina zakije bayan kin cinye min kazata ai in kinga kin bar dakin nan biya na ka zata kika yi." Bai bata daman cewa komai ba yayi bed da ita, kwantar da ita yayi ya bita ya danne tare da haɗe bakin su ya shiga aika mata da wani irin tsadadden kiss na musamman, wanda ba a ko ina ake samun irin shi, ji tayi kanta na juyewa itama dama mai neman Kuka ne aka jefeshi da kashin awaki, caɓewa tayi itama ta shiga mayar mai da martani cikin nata salon mai birkita brain, tun daga wurin kiss daga ita har shi sun tabbatar sun missing din juna ba kaɗan ba, da wani irin sauri ya shiga zare kayan jikin ta yana cilli dasu, saidaya maida ta haihuwar uwarta sannan cikin wani irin salo na musamman ya shiga sarrafata tare da aika mata da zazafan romance ta ko'ina, babu inda bai lashe ya tsotse ba a jikin ta boobs din ta kuwa ranar tass ya musu duk cikar su ko tunawa da babies baiyi ba ya zuƴe musu dan ruwan nonon, a burkice yake gaba daya jinshi yau tare da husnar shi, yadda yake a birkicen ita ma haka take dan yadda yake sarrafata itama haka take sarrafashi, duk inda tasan zata taba taji dadi tabawa takeyi ido rufe, da tazo wurin sucking din shi ihu ya dinga yi yana wani irin sambatu,dan dai itama ba'a hayyacinta take ba da sai ta tsorata da yadda ya din ga yi ɗin, wani irin tsotsa take mishi kamar ta samu sweet duk da girman shi haka take zura bakin ta, tana up and down da shi ba tare da ta san ma tanayi ba, ganin zata haukata shi yasa yayi saurin maidata kasa ya saita Ak din shi ya danna kai, duk da irin jikewan da wurin yayi da irin ruwan ni'imar data kwararar bai sa Ak din shi ya wuce direct ba, a matse take gam kamar wacce aka like da super glue, da'ker ya samu ya shige ta daga shi har ita sun hada uban gumi, wai dan ma tana da wadataccen ni'ima kenan yana jinshi yayi saiti daidai a jikin ta ya hau aiki baji ba gani babu sararawa ko daga kafa, da zafi zafi yake gudanar da komai cikin fitar hayyacin, idanu a rintse duk yadda zaiyi ya hana kanshi ihu yayi amma ina! Ya kasa tuni ya ware yana zunduma ihu daɗi tare da wani irin gurnani kamar wanda ya hau iska, duk yadda zai kwatanta irin yanayin daɗin da zƙi da garɗin da yake kwasa da baki abin bazai kwatantu ba, sai da ya kwashe kusan 30 minutes sannan yayi realizing ita kam tuni tayi nata har so biyu, rungume ta yayi a tare suka shiga suke numfashi tare da share uban gumin daya ke tsatsafo masu ta ko wane kafan gashi kamar wanɗan da sukai gudun fanfalaki, ɗan hutawa yayi na mintuna sannan ya canza style tare da cin gaba da gashi, zuwa lokacin kam ta dawo hayyacinta dan ta samu gamsuwa cikakke, amma shi taga kamar ma wani ƙaimi aka ƙara masa, haka dai ta daure bata nuna gazawar ta ba har ya samu gamsuwa a karo na biyu, jin ya huta zai koma na uku yasa ta fara sheshsheƙan kuka dan wlh harga Allah ta gaji, a kunne ya rada mata "shiiii! Karki yi kuka mana kamar wata raguwa." Cikin shehsheka tace "ya Aslam ɗan Allah kayi hakuri wlh na giji barci nake ji." Dan dariya ƙete yayi yace. "wai tun yanzu,? Aiko dai ko rabi banyi ba, dan sai na fanshe kazar amarcina da kika cinye tsab sannan zan barki,idan naci sa'a kila na kara saito mana wasu yan ukun." Yana magana yana fara ci gaba da gashi, jin haka yasa ta fara kuka ƙasa ƙasa, aiko bai sarara mata ba saida ya sake round biyu kwarara sannan ya barta ganin da gaske ta gaji dan ko daga yatsa da'ker take yi duk ta galabai ta, kallon ta yayi yana murmushi yace "sannu kinji my hussy bari na haɗa miki ruwan gashi." Harara ta wurga mai tare da cewa cikin shagwaba "ba kai ba ko ya Aslam wlh kaida mummy sai na gaya mata muguntar da kamin daga dawowa ta." Zaro ido yayi alamar ya razana da zancen ta, cikin muryar rarrashi yace "ayya my husnah kiyi hakuri karki fada mata bazan sake ba I promise." Ya fada yana rike kunnen shi, shiru tayi bata bashi amsa ba ya sake cewa a marairai ce"kinji husnahta kin yafe min." Yadda yayi maganar sai ya bata tausayi rintse ido tayi saiga hawaye, gwalo ya mata a kai ba tare da ta sani ba ya matsa ya tallabota jikin shi, yana share mata hawaye,shi hada mata ruwan zafi ya gasata sosai ya mata wankan tsarki, ita ko sai ruwab shagwaba take zuba w tana langwabe wa shi Kuma yana aikin rarrashi, basu kwanta ba sai da suka dubo dakin yara, suna ta barcin su abinsu babu wacce ta farka, kamar jira suke iyayen su shiga aiko mummy ta fara farka wa sauran ma duk suka farka, suka Kuma saka kuka a tare,a rude yace "hussy ki basu nono." Tace "wani nono, ai babu ruwa ko ka manta ne." Madara ta haɗa musu fida uku, yana ba daya ta na biyu a haka har suka koshi suka koma barci, ajiyan zuciya ya sauke tare da kama hannun ta suka koma dakin ta da ke facing na barcin yaran. Da safe duk wani aiki daya san zai iya taya ta ya kama mata harda breakfast shiya hada musu, ita Kuma tama yaran wanka ta shirya su itama tayi suka karya, tunkan tamai maganar tafiya aiki ya sanar mata shifa ya dauki hutun sati daya saiya gama cin amarci, a daki ya wuni ranar ko zee da'ker ya leƙa ta saida tayi da gaske ya tafi, Kuma bawai ya kwale ta bane motsi kadan zai lalube ta, ita abin har ya fara bata tsoro to kodai yasha wani abu ne, har Allah Allah take yi dare yayi ya koma dakin zee, bayan isha'e kamar an mata bushara da Aljannah take ji wai dan zai tafi dakin zee, shi ko sai bata rai yake yi, dan kar tace mai ya tafi, aiko dai yayi a banza takwas da rabi nayi ta same shi falo zaune ya jere ƴaƴan shi gaba sai wasa yake musu yana ganin ta ya bata rai dan kar tace ya tafi ko a jikin ta, tace "honey 8 : 30 yayi fa kazo ka tafi zan rufe kofa." Yace "ohh korata ma kikeyi ko? Har kin gaji dani." A zuciyar ta tace ba dole ba daga yin dan tafiya na dawo ka zama wani jarabebben a cikin kwana ɗaya da yini kayi abu yafi sau goma, a fili Kuma tace "A'a wlh honey ni na isa na gaji dakai, ni asuwa." Cikin jin dadi yace "da gaske baki gaji ba hussy?" Ba tare da tunanin komai ba ta dage mai gira tare da cewa "Yes honey." Mikewa yayi fuskar shi a washe yaje "OK to bari na je." Har bakin kofa ta raka shi tana mai sai da safe har yayi nisa ta kira shi ya juyo ta mai kiss ta hura mai ya cabe cikin dadi, tura kofar ta tayi ta murza key jingina tayi da kofar tare da sauke nannauyan ajiayar zuciya,kwasan yayan ta tayi ɗay bayan daya ta kaisu daki su inda nan zasu kwana yau gaba daya harda ita, nono ta basu suka kasha suka kama barci, addu'a ta musuta tottofesu sannan ta fito da nufin taje nata dakin tayi wanka ta dawo dan baza tayi anan ba karmotsin ta ya tashe su, wankan ta tayi tayi shirin barcin ta , biyowa tayi ta falo domin ta kashe wuta da sauran su, kamar a mafarki taji ana dannan doorbell, bata yarda ba ta dauka kunnen ta ne, sai da ta sake jin na biyu sannan ta yarda,da dumbin mamaki ta isa wurin kofar ta leƙa ta wurin lekawa, Aslam ta hango sai fuskar shi wasai alamar yana cikin matsanancin farin ciki, sai da gabanta ya dan fadi "me Kuma ya dawo da shi ta tambayi kanta." Jiki ba kwari ta bude mishi kofar, shigowa yayi da sauri tare da caɓe ta ya daga sama ya shiga juyo da ita a tsakiyar falon, mamaki da tsoro ne suka kamata mustu mustun kwacewa ta shiga yi, ganin haka yasa ya sauke ta yana dariya , a mamakance tace "lafiya honey mai ka dawo yi," yace "na roko mana kwana ne gurin my luv yar albarka sati daya na tambaya amma tace ta bani biyu, wlh bakiji dadi ba kamar na goya ta dan farin ciki." Magana yake yi cike da tsantsar farin ciki, hannu ta daura akai tare da cewa "innalillahi wainnailaihi rajiun. Ya Aslam me yasa kayi haka." Bai damu da yanayin taba yace "saboda bamu gaji da juna ba, ko ba yanzu kika ce kema baki gaji dani ba to kamme zamu cuci kanmu ga hanya mafi sauki, roko mana ita nayi ta ara mana kwanakin ta Kuma ta bamu harda kari, naga ai ba haramun bane yin hakan ko?" Lokaci daya taji tausayin zee ya lullubeta har saida hawaye ya ziraro mata, ganin haka yasa ya cira ta sama ya nufi hanyar bed room yana cewa"nifa ba kuka na dawo kimin ba dawowa nayi muci gaba da shan amarcin mu, kin gane ko beb, bari ma na dumama miki sauran kazar ki ta jiya kici dan yau ma ba sauki." Jin hakan yasa ta fashe da kukan shagwaba tana cewa "ni bazan ci ko wani kaza ba wlh, Kuma daga yau na daina cin kaza a gidan nan." Dariya ya saka mata da haka suka shige bedroom din ya turo kofar da kafa, saura kadan ya buge min katon hancina ni mai dauko rahoto yau dai ban samu shiga bed room ba balle naga yadda wasan zai kaya, dan haka na lallaɓa na fito na nufi part din zee dan ganin yanayin da Mr Aslam ya barota. Duke take a bakin kofar falon kuka taje kamar ranta zai fita,ji takeyi zuciyar ta na mata wani irin ƙuna kamar zai kama da wuta,ta gama shirin ta tsab dan tarban miji kwalliya ta yi mishi mai rai da lafiya cikin kananan kaya sai kamshi take zubawa amma yana shigowa ko kallon kirki bai mata ba sai ma rokon ta da ya shiga yi akan ta bashi Aron kwanakin ta zaije dakin Asmah, sai wani zumudi yake yi yana rawar kafa kamar wanda ya shekara babu mace a tare da shi, ta riga ta sani son da yake ma Asmah ya dama wanda yake mata ya shanye yana nuna mata banbancin a bayyane gaskiya ta fara gajiya da wannan abubuwan ko kaɗan bata da matsala da Asmah da shine take da matsala Kuma idan har irin Wadannan abubuwan sukaci gaba da faruwa tabbas zai ɗarsa mata wani abu game da Asmah ita kuma bata fatan hakan domin Asmah ta mata abin da bata cancanci wani mumman kallo daga gareta ba ko yanzu ta tabbata shine ya shirya wannan abin ba tare da sanin Asmah ba don ta tabbata inda Asmah tasan zaiyi wannan abin baza ta taba bashi goyan baya ba, domin ita shaida ce akan jajircewan ta akanta lallai Asmah tana sonta fisabilillah, don haka ta gama yanke shawaran da take gani shine kaɗai mafita a gareta tunda wuri kafin Aslam ya haddasa mummunan gaba atsakanin su dan zuciyar ta ta fara kaiwa matakin da baza ta iya cin gaba da jure irin walannan abubuwan ba. A hankalin ta lallaba ta mike jiki ba kwari ta wuce bedroom dinta ta fada kan gado ta kwanta rigingine tana ci gaba da kukan ta bata san sanda barci barowa ya sace ta ba. Sati biyu cur ya kwashe a part din Asmah,kamar yadda zee tace ta bashi, a cikin kwanakin nan babu abin da suke yi sai shan amarci inji ta bakin shi, kwata kwata baya gajiya da husnar shi kullum daɗi take karamai ko wani lokaci cikin sha'awar ta yake, Asmah ba famar da bata yi ba ya koma wurin zee da yayi sati ɗaya amma ya shafa wa idanun shi toka karshe har fushi tayi da shi sukayi fada wai ko zaiti fushi ya tafi amma a banza dan haka kawai ta kyale shi tunda ai yayi rabi, Ita wlh kunyar zee ma take ji ga Kuma tausayin ta da take ji kamar kamar me tasha auna kanta a ma'aunin zee kawai sai taga baza ta taɓa iya jurewa idan ita ce, ita ko baiwar Allah koda wasa bata taba yarda ta nuna damuwar ta akan wannan lamarin ba, Aslam take so dan haka dole ta taya shi son abin da yake so idan har son da take mai na gaskiya ne , amma Kuma dole zata dauki mataki don ita zuciya bata da ƙashi. Ranar da ya cika sati biyu, sai gurin karfe goma dare ya tafi kamar bazai taɓi ba sai kwan gaba kwan baya yake yi, da murna ta tarbe shi taci gayunta kamar yadda ta saba ta rungume shi tana gaya mai irin yadda tayi kewar shi, dan da gasken fa taji kewar shi kamar kamar me, shi karan kanshi sai da ya tausaya mata lokacin da suka kasan ce tare, saida ta bari sun samu nutsuwa suna kwance kanta akan kirjin shi tace,"my luv." Yace "na'am my luv." Tace "so nake ne Naimi wata alfarma a wajen ka idan babu damuwa Kuma hakan bazai zama takurawa ba." Yace "ba komai my luv ki faɗi duk bukatar ki idan bai sabawa Shari'a ba, Kuma baifi karfina ba na miki alkawarin ko menene zan miki, domin na faran ta miki kamar yadda kika faran ta min."sauke jiyar zuciya tayi tace "baifi karfin ka ba insha Allah." Dan shiru suka yi gaba ɗaya shi yana sauraren ta ita Kuma tana tunanin yadda zata faɗi bukatar ta,ta yadda bazai mata wani gurguwar fahimta ba, can dai ta daure tace "Dan Allah da manzon sa, Aslam so nake ka raba nama gida da Asmah." Shiru yayi ya bai bata amsa ba da alama ma ya fada tunanin, dagowa tayi suka tsirawa juna idanu gyada mai kai tayi tace "dan Allah da manzon sa karkace A'a Kuma karka tambaye ni dalili." Ta karashe maganar hawaye na cika mata idanu, tausayin ta taji ya mamaye mishi zuciya take tsohuwar Zuma ta motsa yana son zee sosai itama don ita din zaɓin shi ce, amma fa ko rabin na Asmah baikai ba, yana adalci a tsakani su a komai amma banda gurin nuna soyayya, shi Kuma wannan kadai ne jarabtar shi, ganin hawaye ya fara wanke fuskar ta yasa yace "ya isa haka Zainab ki share hawayen ki zan miki abin da kike so shi kenan zaki koma gida na dake odoye yayi miki." Rungume shi tayi tana gyada kai, take ta shiga jero mai godiya ta kare da cewa dan Allah karya gayawa Asmah sai ranar da zata tare ɗin ya ko yi mata wannan alkawarin, tare da cewa tabar komai nata na nan a kwai komai acan gidan taje ta duba abin da bai mata ba sai a canza mata, wanda babu Kuma a siya a saka mata. Hakan ce kuwa ta kasance daga ita sai shi suke ta shirye shiryen su na komawan ta odoye ba tare da Asmah ko wani nashi ya sani ba har suka gama kwashe kayan sawan su a gidan Asmah bata sani ba, sai ranar da zata wuce da safe shida zee ɗin suka saka ta a gaba suna bata hakuri tare da gaya mata batun tashin, aiko kamar saukar aradu taji zancen, take ta daka tsallen albarka tace bata yarda ba, rarrashinta suka shiga yi amma taƙi kula ko daya daga cikin su, wasa wasa fa fushi tayi sosai dasu har su mummy ta kira takai karan su amma ba wanda ya goyi bayan ta sai dai a bata hakuri , tanaji tana gani zee ta bar gidan aranar tare da little koda take sallaman ta kin amsa ta tayi saima ficewa da tayi ta bar mata ɗakin ta shige wani ta ɓamo kofa ta murza key tana hawaye, itama zee jikin ta yayi bala'il sanyi ji take kamar ta fasa amma Kuma inta tuna mafita take neman musu ta yadda zaman lafiyar su zai dore sai taji zuciyar ta ta ƙarfafa, komai idan ana nesa nesa da juna yafi armashi, Kuma duk abin da Aslam zaiyi ma ɗaya, ɗaya baza ta gani ba bare taji haushi ai kazantar da baka gaji ba tsabtace inji hausawa, wannan shine mafarain rabuwar gida tsakanin zee da Asmah Kuma hakan ya taimaka ma zaman su sosai da sosai Asmah tayi fushi Kuma daga karshe da kanta ta sauko har taje taga gidan zee din ta saka mata albarka suka ci gaba da zumuncinsu kamar yan uwa ba kishiyoyi ba, wannan kenan. BAYAN SHEKARA GOMA Abubuwa da dama sun faru a cikin waɗan nan shekarun masu daɗi da marasa dadi, kadan daga cikin marasa dadin akwai mutuwar Alhaji baba da hajiya mama, wanda tsakanin su wata biyu ne kacal, cikin masu daɗi akwai haife haife da akayi sosai a cikin ɗan waɗan nan shekarun batool da zahra yayan su hudu hudu, Khadijah uku, Amira shidda, dan yan biyu ta jera har sau biyu bayan haihuwar daddy, kwanciyar hankalin da nutsuwa ya watada a cikin zuciyar Alhaji baba, yan matan mummy zuwa wanan lokacin sun zan manyan mata zumunci da shakuwar su kuwa kullum gaba yakeyi, kowacce ta tara zuri'a tana zaune lafiya a gidanta sai hamdala. Asmah kam zuwa wannan lokaci ta zama Babbar mace ƴaƴa sun baibaiyeta ta ko'ina tun daga haihuwar su mummy kofar haihuwa ta bude mata dan ko wata biyar yaran basu rufa ba wani cikin ya bayyana a jikin ta, ta haifi yan biyu kaza bayan su ta sake yin ƴan daɗɗaya sau uku sai kuma abin ya tsaya tsab kamar anyi ruwa an dauke,a bangaren zee ma zuwa wannan lokacin komai alhmdllh dan itama ta waye ta shigo gari Asmah ce data fahimci kamar batasan komai a bangaren ba ta saura ta akan hanya tare da wayar mata dakai babu hassada ko munafirci a ciki dan ita wlh tausayi zee ke bata kula tsakanin ta da Allah take sonta har zuciya, aiko dai zee ta ga gurin zama kama jiki tayi itama gyara takeyi sosai tunda ta fahimci yana da mahimmanci sosai ga mace musamman mai kishiya dan ta fahimce tashin gyara na daya daga cikin abin da yasa Aslam yafi fifita Asmah akanta, ta ƙara haihuwa itama y'ay'a biyu bayan little duk maza daya Dad da alhaji Abdur-rahman, Aslam ya samu kwanciyar hankali yayi wani ƙiba ya zama babban mutum matan shi kuwa Kansu a haɗe yake kamar yaya da ƙanwa, haka ma ƴaƴan su dan tuni su mummy suka koma hannun zee da zama little kuwa yana wajen Asmah dan shi na wajen ta dama,yaran idan ba ka sani ba baza ka iya tantance wa'inne ne na Asmah ba haka baza ka iya gane su waye na zee ba, zee suna kiranta da mammah kamar yadda sukaji little na kira Asmah suna kiran ta da mummy abin gwanin birgewa sai wanda ya gani masha Allahu lakuwata illaha billah..... Karshe Alhmdllh! Alhmdllh!! Alhmdllh!! Oum Ummeetarh 07041130088