♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 ᗩՏᕼᗩᑎTY LOVE. # WORK OF FICTION. # ADVENTURE. # DESTINY. # ROMANCE. # HEARTBREAK. # HOT LOVE. # MYSTREY. # Royalty. ⚠︎: 𝑊𝑎𝑛𝑛𝑎𝑛 𝑙𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑖𝑟𝑘𝑖𝑟𝑎𝑟𝑟𝑒𝑛 𝑙𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖 𝑛𝑒. 𝐵𝑎𝑛𝑦𝑖 𝑠ℎ𝑖 𝑑𝑎𝑛 𝑐𝑖𝑛 𝑧𝑎𝑟𝑎𝑓𝑖𝑛 𝑤𝑎𝑛𝑖 𝑘𝑜 𝑤𝑎𝑡𝑎 𝑏𝑎. 𝐷𝑢𝑘 𝑤𝑎𝑛𝑑𝑎 𝑦𝑎𝑔𝑎 𝑦𝑎 𝑔𝑖 𝑑𝑎𝑖-𝑑𝑎𝑖 𝑑𝑎 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎𝑟 𝑠𝑎 𝑎𝑟𝑎𝑠ℎ𝑖 𝑛𝑒. ________________❦︎_________________ 𝐴𝑙ℎ𝑎𝑚𝑑𝑢𝑙𝑙𝑖𝑙𝑎ℎ ,𝑑𝑢𝑘𝑘𝑎𝑛 𝑦𝑎𝑏𝑜 𝑑𝑎 𝑔𝑜𝑑𝑖𝑦𝑎 𝑠𝑢𝑛 𝑡𝑎𝑏𝑏𝑎 𝑔𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ. 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑘𝑎 𝑘'𝑎𝑟𝑎𝑤𝑎 𝑚𝑎𝑛𝑧𝑜𝑛 𝑚𝑢 𝐴𝑛𝑛𝑎𝑏𝑖 Muhammad (𝑆.𝑊.𝐴)𝑑𝑎𝑗𝑎𝑟𝑎. 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑘'𝑎𝑟𝑏𝑖 𝑖𝑏𝑎𝑑𝑢𝑛 𝑚𝑢,𝑦𝑎𝑠𝑎 𝑚𝑢𝑛𝑎 𝑑𝑎𝑔𝑎 𝑐𝑖𝑘𝑖𝑛 𝑏𝑎𝑦𝑖𝑛 𝑠𝑎 𝑑𝑎 𝑠𝑢𝑘𝑎 𝑠𝑎𝑚𝑢 𝑟𝑎𝑏𝑜 𝑚𝑎𝑖 𝑔𝑖𝑟𝑚𝑎 𝑐𝑖𝑘𝑖𝑛 𝑤𝑎𝑛𝑛𝑎𝑛 𝑤𝑎𝑡𝑎 𝑚𝑎𝑖 𝐴𝑙𝑏𝑎𝑟𝑘𝑎. 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑚𝑎𝑖𝑚𝑎𝑖𝑡𝑎 𝑚𝑎𝑛𝑎. ❤︎ EID MUBARAK ❤︎ ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 1/5. YEMEEN. NIGER 2005. Bansan taya zan iya kwatanta muku yanayin rayuwar mu ba a wannan lokacin. Muna rayuwa ne can wani yanki dake cikin YEMEN Niger. Buzaye ne mu rayuwa muna yinta cikin kwanciyar hankali da Annushuwa. K'aramin kauye ne inda muke amma Allah ya hore mana jindaɗin rayuwa. Nasan zaku ce me ku ke dashi?. Yaruwa muna yinta cikin y'anci da kaunar junan mu. Kunsan mu buzaye yanda muke rayuwa. Bani da wasu shekaru a wannan lokacin dan shekarata 7. Zan sheda irin matsanancin kauna da iyayena da kuma mutanen kauyen mu kewa juna. D'an kowa na kowane. Muna da matsanancin had'in kai. Wannan kad'ai ya isa mu samu kwanciyar hankali. Duk inda aka ga wani abu dazai kawo mana cikas cikin kauye za'a had'u a tattauna dan samun masalah. Daga ni sai iyayena da nake matuƙar kauna. A duniya bani da wasu masoya daya wuce su. Na taso cikin gata, kauna da soyayya. Bamu da wani ilimi mai zurfi saboda yanayin rayuwar mu. Amma akwai tarbiya. Sannan duk alhamulis da juma'a har zuwa ranan lahadi mahaifina yana tara yara nan k'ofar gidanmu bakin bishiyar Mangoro da tun tasowa ta na tarar da ita. Zai ta bamu tatsuniyoyi da kuma labarai masu Jan hankali musamman na yankin kudu. Abbu na yana yawan cewa shi ba haifeffen d'an Yemen bane. Hasali ma shi dan gudun hijirane shida Innati sun baro k'asar su ta haihuwa ne saboda irin mulki na zalunci . Bansan kuma me yasa ba sam basa son fad'an wace k'asa ce asalin k'asarmu. Duk sanda na kawo zanchen sai su kauce baza su bani amsa ba. Innati tana yawan cewa "Nadeeyah akwai wata k'asa da zakiyi alfahari da ita banda wannan da ki ka buɗe ido ki ka ganki a ciki?, wancan k'asar ba k'asa bace da za'ayi alfahari ko kwantace da ita , k'asar ki ita ce nan YEMEEN kar ki manta wannan" Idan Abbu yana bamu labarin irin zaluncin da ake k'asar saboda mulki ba k'aramin tsoro abun yake bamu ba. A koda yaushe yana samana tsoron Allah da kuma gudun cin zarafin wani ko na misk'ala zarratan . Yakan ce duk abunda wani zaiyi muku dan zalinci ku barshi da Allah zai isar muku a duk inda kuke. Addu'a wadda aka zalunta karbabbiyace domin Allah baya yafe hakk'in wani kan wani sai in shi mutum yace ya yafe masa. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Mummunan kaddarar da ban taɓa tunanin zata same ni cikin kuruciya ta ba ita ce ta same mu a daren yau. Hayaniya da kuma ihuce-ihuce mutanen rugar mu ta farkar dani daga barcin da nake mai nauyi jikin Innati. Cikin barci na farka ina kallon Abbu dake tsaye bak'in k'ofar d'akin mu yana k'ok'arin rufeta cikin firgici. Tunda na taso ba'a tab'a rufe k'ofar ba sai yau. Sai dai a saki asabari da zai rufe ko ina. Tunda na taso wannan al'ada ce da mutanen kauyen mu ke yi saboda halin rayuwa. Bamu da asibiti ko masallaci, ko makaranta. Dalilin da yasa bama rufe k'ofa dan wani zai iya neman taimako cikin gaggawa. Da y'ar muryar ta ta wanda ya tashi daga barci nake kallon Abbu dake tsaye jikin k'ofa cikin matsanancin tashin hankalin da ban taɓa ganin sa a ciki ba. Kallon Innati nayi data k'ara rungume ni tsam cikin k'irjin ta itama dai tashin hankalin ne kwance kan fuskarta kaman na Abbu. "Abbu, Innati ihun mene haka naji mutane suna yi?" Da sauri ya k'araso inda muke ya durkusa. Hannu ya tura cikin rawanin sa ya fito da wata sarka kaman ta zinare. D'aura min ita ya yi yana kallon Innati da naga hawaye masu zafi sun biyu kuncin ta. K'asan rigata ya tura sarkar sai kuma ya kunce gashin kaina da Innati ta nade min shi tsakiyar kaina kaman gammo. Shekara 5 nake amma za kayi mamakin yawan gashi na da kuma tsayin sa gashi baki sid'ik. Har wajen gwiwar kafata yake zuwa. Shi yasa duk bayan wata Innati ke rage min tsayin sa. Da ita da Abbu na rasa wana biyo gurin gashi. Danma Abbu bai cika buɗe fuska ba kullum nad'e yake da rawani ya rufe fuskarsa sai idonsa kawai ka ke gani. Idan kaga ya kwance rawanin to cikin d'aki yake daga shi sai ni da Innati idan kuwa ya kwance har kitso nake masa naita ja masa kai dan gashin sa har gadon baya yake kwanciya. To itama Innati haka. Abun tambayar shi ne meke faruwa ne? Wannan sarkar fa?. Goshi na ya sumbata idan sa tab cike da hawaye yace "Nadeeyah duk wani bayani da zanyi miki yanzu baza ki fuskanta ba saboda k'arancin shekarunki, amma ina so ki riƙe wannan sarkar da kyau, duk runtsi karki yarda wannan sarkar. Babu wani lokaci da zan iya yi miki bayani da zaki fuskanta, amma kar ki manta a koda yaushe muna tare dake" Shar naga hawaye sun biyu kuncinsa. Galala na tsaya ina kallon sa .sheshshek'ar kukan Innati ya d'auke min hankali na juya ina kallonta. Cikin rashin wayo da yarinta na rungume Innati na riƙo hannun Abbu shima na jawosa na rungume su kan kirjina. Hannun Innati ,Abbu ya kama yana mata murmushi. Ihuce-ihuce da guje-guje da nake ji na mutanen karkarar mu ya yi yawa ga sawon kaman dokuna . A hanzarce Abbu ya miƙe ya kama hannun Innati da nawa k'ofar da yake b'ulla tacan bayan Sahara ya buɗe. K'ofar kaman boyyayyir hanya ce da Abbu ke yawan bi idan yana san kad'ai cewa cikin sirri. Binsu kawai nake har yanzu na kasa fuskantar komai. Babu zato muka ji wata murya mai kaushi da cikin tsantsan larabci da ban iya shi sosai ba lokacin sai kuma k'arar dokuna a bayan mu. Wani irin fisgata Abbu ya yi ya sab'a kan kafad'a ya riƙe hannun Innati muka hau gudu bana wasa ba. Gudu muke mutanen suna biye damu har sun kusa kamomu. saboda nike fuskarta su ya bani damar ganin mutanen dake binmu kan dokuna sanye da kaya bak'ake sun rufe fuska da bakin abu. Kayan dake jikinsu kaman irin kayan nan na yaki irin wanda Abbu ke bamu labari. (Armour ). Wasu riƙe da takobi wasu kuma riƙe da mashi. Cikin wanda ke riƙe da mashin naga wani ya saita Abbu kafin nayi wani yunƙuri ya saki mashin ya tawo da mugun gudu . Wani irin slow naga abun ya tawo na saki gigitacciyar k'ara ina kiran Abbu. Amma sai dai me Innati naga kawai ta fisge daga hannu Abbu ta tare mashin daya nufushi a guje ya huda saitin k'irji ta ya wuce. A take ta zube a k'asa tana tarin jini. Matsanancin kuka na fashe dashi ina kallon Innati dake kallon na ina sab'e kan k'afad'ar Abbu da murmushi kan leben ta dake motsi kaman mai magana. Ganin da nayi Abbu kaman bazai tsaya ba sai sharara gudu yake ga Innati can kwance a k'asa cikin jini. Na fara buge -buge zan kwace ina kiran Innati cikin matsanancin kuka. Wani mashin suka k'ara harbowa Abbu ya yi maza ya kauce cikin zafin nama ya shige cikin ciyayi muka samu damar b'ace musu. Saida muka yi y'ar tafiya mai nisa mun shiga cikin dajin sosai babu alamun ana binmu sannan Abbu ya tsaya gindin wata katuwar bishiya. Sauke ni ya yi yana haki ya jingina jikin bishiyar. Duk da cewar dare ne amma hasken farin wata ya haske sararin samaniya kana ganin komai tar. Sannan ina da wata baiwa koman duhun dare da nisan abu tar nake ganin sa kaman rana. Dalilin da yasa na iya hango mutanen da suka shigo cikin jejin da k'afafuwansu babu dokunan. Rigar Abbu na kama ina nuna masa da hannu. A firgice naga yana kallon inda na nuna masa d'an waige-waige ya yi ya jani da sauri ya tura tsakanin wasu ciyayi. Rawanin dake kansa ya cire ya nade fuskata dashi sai ido na kawai. Ido na zuba masa ina kallon fuskar sa dake d'igar da hawaye da sai alokacin ma na lura dasu. Wani kuka ne ya k'ara zuwarmun mai k'arfi dan nasan kukan me Abbu yake. Sunan Innati na fara kira ina kuka sosai shima Abbu duk yanda yake daurewa kar ya yi kuka mai sauti kasa jurewa ya yi ya fashe da kuka mai k'arfi jikinsa na girgiza. Durkusawa ya yi gabana yana sharemin hawaye murya a raunane yace "Nadeeyah zanje na d'auko Innati kinji ko?, idan na tafi ki irga d'aya zuwa uku sai kibi nan " Doguwar hanya ya nunamin mai tsayi daga can nesa kanajin k'arar teku. "Kibi nan har sai kin bulle bakin gaba ki samu guri ki buya har sai na dawo da Innati kinji ko. Ki buya kar ki fito ko kinji motsi sai in na kira sunanki wanda ni kaɗai da Innatin ki muke kiran ki dashi. Gayamin sunan" Murya na rawa nace "SULTANAAH" Murmushi Abbu ya yi ya kama fuskta yana kallona hawaye kwance kan kuncinsa " kar ki manta har sai kinji wannan sunan zaki fito kinji SULTANAAH " Shar hawaye suka k'ara wanke min fuska. Me yasa nake ji kaman sallama ce Abbu shima yakemin?. Goshina dake nade ya sumbata ya miƙe tsaye . "Ina sanki SULTANAAH, INNATIN ki na sanki. A shirye muke mu bada rayuwar mu dan ceton ki. Muna tare dake a koda yaushe " Saki na ya yi da sauri kafin nayi wani yunƙuri ya kwasa da gudu ya koma hanyar da muka biyo. Gursheken kuka nake ina k'ok'arin danne bakina. Saboda baiwar da nake da ita na samu ganin Abbu har ya b'ace daga ido na kafin ya fice daga dajin ya juyo yana kallon duhun sa bak'insa na motsi na karanta kalman da yake cewa. "MY SULTANAAH" Murmushi ya yi mai had'e da kuka ya juya da sauri ya fice ba tare da yaci karo da mutanen dake nemanmu ba. Kuka nake sosai na kasa motsawa daga inda nake har suka k'araso inda nake b'oye. Ido na runtse ina jin motsin su daf da inda nake . Wai su waye wad'annan mutanen mai suke so?, mai muka yi musu da suka tarwatsa mana duk wani farin cikinmu cikin d'an k'ank'anin lokaci? . Ina jinsu suka gama zagaye- zagayen suka dumfaro inda nake boye bayan ciyayi. Numfashi na d'auke na k'ara damke ido na tsaya kam rungume da k'irjina dake bugawa. Muryar su naji a kaina da sauri na buɗe ido na na zaro su waje ina shirin kwasa da gudu. Abun mamaki gasu dai a gaban nawa amma babu wani alamu da yake nuni da sun ganni. Ga d'aya kusa dani kaman zai tab'a ni. Baya naja da sauri ina kallon su dafe da kirji. Babu alun ya ganni ya juya da sauran mutanen sa suka koma inda suka fito. Me hakan ke nufi? Gani gasu amma basu ganni ba?. Iska naji ta d'an kad'a mai sanyi har saida na k'ank'ame jiki. Wooshh naji iskar tabi bayan kunne na sai kuma naji kaman magana. "SULTANAAH nan" A firgice na juya bayana dan ganin wanda ya yi maganan. Wayan babu kowa. Matsanancin tsoro ya k'ara kamani. Iskar ta k'ara kad'awa wajen saitin kunnena na dama ta wuce Wosshh na k'ara jin wata maganan kaman daga cikin Iskar ma take fita. "Nan SULTANAAH " A guje na kwasa hanyar da Abbu ya nunamin yace nabi tun d'azu na kasa bi. Gudu nake ina kiran Abbu da Innati ban tsaya ba sai da na fara hango hasken ruwa da farin wata ya haske na k'ara kaimi dan sai nake ji kaman sawun mutum ne bayana idan na juya kuma bana ganin kowa. Sai dana kai bakin tekun na samu guri na zauna ina maida numfashi. Waige-waige nake ta inda zan hango mab'oya amma babu sai cikin ciyayin dana fito. Sawun k'afafuwa da naji na mutane na yowa inda nake na miƙe a sukkuwanne da y'an kafuwana ina neman hanyar tsira sai gasu sun bullo. Ajiyar zuciya na sauke mai k'arfi ina kallon wasu daga cikin mutanen kauyen mu da yara dana shedasu a take. A guje na nufe su ina kira hakan yasa suka juyo kaina. Ido waje FAHIMA ta nufoni tana kira kaman yanda nake kiranta. Rungume juna kuma yi duk da k'arancin shekarun mu nida ita sai kayi mamaki irin matsanancin k'awance da muke. Cikin kuka tace " sun kashe Mama da Baffa, sun kashe kowa. Su waye wad'annan mutanen?, me suke su a tare damu?" Kuka muke sosai abun tausayi sauran yaran suka matso muka rungume juna. Mun jima a haka na d'ago don na k'irga mu nawane. Mu biyar ne yaran sai manya mace da namiji mutum biyu dana gane su. Babu zato mukaji k'arar dawakai. Gaba d'ayan mu yaran muka rude muka fashe da kuka a hanzarce Ma'auratan suka kamamu muka hau gudu bana wasa ba. Saidai duk wannan gudun da muke a banza dan saida wad'annan mutanen suka tadda mu. Zagaye mu suka yi da dawakai. Julde da matarsa Azima suka kamamu suka rungume dan bamu kariya. Hannun FAHIMA na riƙe muka cigaba da zubda hawaye don mun tabbatar muma mutuwar mu tazo kaman sauran mutanen mu. INNATI da ABBU na. Ko yana raye ko shina sun kasheshi? Gaba d'ayansu suka sakko daga kan dokin suka kewaye mu. Magana suka fara tsakanin su cikin yaran da bama fuskanta sosai.(LARABCI) Wanda nake tunanin shine ogan nasu ya matso sosai gabanmu yana kallon fuskarmu d'aya bayan daya. K'ara k'ank'ame juna mukayi hawaye na cigaba da ambaliya kan fuskarmu. Yana zuwa kaina naga ya zubamin idon duk na rude Azeema ta k'ara b'oyeni cikin k'irjin ta. Wajen sakan biyu yana kallona duk da fuskata a rufe take sai idona kawai da ake gani.sai kuma ya juya wajen y'an uwansa suka fara magana cikin harshen su. "Ya zamuyi da wad'annan yaran ne?, banga alamun akwai yarinyar da aka ce mu kashe ba. Ina tunanin ya b'oye ta cikin dajin nan. " Na kusa dashi ya yi saurin cewa " To su wad'annan d'in fa mu barsu kenan? Gwanda suma a kashe su kawai kaman sauran. Dama ai cewa aka yi kar mubar kowa da rai, babba ko yaro. Kaga muna da kaso mai tsoka musamman idan muka bada shedar nasarar kashe yarinyar da masu bata kariyar" Jim ya yi yana juya maganan shi cikin ransa kafin yaja dogon numfashi ya fesar. " yara ne wannan. Enough with the killings. Abunda za'ayi mu sasu jirgi sun zama bayi. Wannan ce shekarar da masarautar Egypt ke daukan bayi dan haka sai mu basu su a matsayin gudunmawa. Kasan irin tsanani na wannan masarauta idan aka shiga ba'a fita sai dai a fito da gawar ka. Hakan shi ne mafita kawai sai su k'are rayuwar su a can matsayin bayi" Kai suka jinjina gaba d'aya amincewa da maganan sa. Juyowa suka yi kanmu muka k'ara had'a ido dashi sai kawai naji saukar duka tsakiyar kaina a take na zube k'asa kafin na rufe ido naga FAHIMA da sauran yaran uku ,Azima da julde suma sun zube k'asa a sume sakamakon dukan da suka yiwa kowa a kai. Idona na gab da rufewa naji an kira sunana cikin kunne kaman rad'a "SULTANAAH" bayan mutumin naso naga wasu irin kwayar ido masu hasken gaske ga alamun gashi mai tsawo baki sid'ik na kad'awa kaman iska. Runtse ido nayi na k'ara buɗewa don sai nake tunanin ko dukan da sukayi min ne yasa na fara ganin ba dai-dai ba. Har ila lokacin wannan kwayar idon dake lekowa ta bayan mutumin tana nan d'auke da gashin ido mai tsayin gaske. Sai kawai naga kaman mutanen sun zube k'asa suna kururuwa daga nan ban k'ara sanin komai ba ido na ya rufe ruff. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 ASHANTY LOVE. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 5/10. ❤︎ EID MUBARAK ❤︎ 18YRS LATER. EGYPT. Bazan iya ce muku ga yanda aka yi muka tsinci kanmu cikin wannan k'asa ba k'ark'ashin wannan masarauta ta zalunci. Mun farka ne kawai mun ganmu anan kewaye da masu tsaro(Gaurds). Tunda muka shigo wannan masarauta aka rabamu kowa da b'angaren daya ke aiki. Tun ranan kuma ban k'ara saka Julde da Azima a ido na ba da sauran yaran da muke tare. Uwar d'akina da nake gurin ta Mama Maria ita ke cemin suna can wani b'angare cikin masarautar saboda girman ta da kuma rashin y'anci da bayi basu dashi basu isa su fita ba sai in aiken su aka yi. Yau tsawon shekara goma sha takwas ban taɓa fita daga masarautar nan ba bare nasan ya rayuwar waje take. Muna can b'angaren bayi dake k'arkashin k'asa. Bamu rasa ciba bare sutura don nikam Allah yaso ni da arziƙi uwar d'akina wato Mama MARIA ita keda ragamar girkin Sarki da sarauniya da y'ay'an su. Ita ke musu wanki da sauran wasu abubuwa daya dangance su. Babban abun mamakin shine tun ranan da muka tsinci kanmu cikin wannan k'asar na daina wannan ganin da nake cikin duhu. Har zuwa yau kuma na kasa tantance abunda na gani ranan bakin teku kafin na suma. Shin idon da na gani da kuma sillin gashin da naga yana kad'awa cikin iska gaskiya ne ko kuma imagination d'ina ne?. To amma kiran da naji ana munfa da sunan da babu wanda ya san shi sai iyayena fa?. Allah ne kad'ai masani. Nima kuma tunda na mallaki hankalin kaina na watsar da komai bana son ma na tuna wannan bak'ar rana da baza ta tab'a gogewa a kwanyar kai na ba sai ranan da zan koma ga mahallicina. A yanzu bani da komai sai wannan sarkar da Abbu ya bani. Duk lokacin da nake begen su zan d'auko sarkar ina kallon ta ina kuka. Ganin yanda sarkar ke sani cikin damuwa sosai Mama Maria ta sani na cire sarkar na ada nata. Ta hanani daukan ta sai dai in babu idon ta. Kuma hakan da tayi ya yaye min damuwar rashin su matuƙa. Mama Maria babbar macece balarabiyar Egypt. Tana da aure da yara biyu, halin rayuwa yasa ta karb'i aiki cikin masarautar kuma Allah ya taimake ta macece ita mai gaskiya da amana ,dalilin da yasa sarki da sarauniya suka yarda da ita d'ari bisa d'ari. Duk irin wannan bauta da take musu basu amince da fitarta daga masarauta ba sai lokaci zuwa lokaci. Wato sai idan abu mai muhimmanci ya taso. Tace hakan ya yi mata matsawar mijin ta da yaranta zasu ci, su sha su kuma saka sutura mai kyau. Babu laifi gaskiya ana bata albashi mai tsoka. Har mamaki nake idan naga yanda take yin komai saboda y'ay'an ta. Wata rana haka zan zauna nayi ta kuka idan na tuna Abbu da Innati. Zamana da Mama Maria yana d'an debemin kewar rashin su dan ta d'auke ni tamkar yarda ta haifa. Ta koyamin larabci duk da nima ina ji amma ba sosai ba. Yanzu idan na juye harshe baza kace nasan wani abu waishi hausa ba. Kusan mutanen da muke wannan b'angaren d'ai-da'i kune ban koyawa hausa ba. Wasu sun d'an iya wasu kuma har yanzu sun kasa cikin su harda Mama Maria da bata iya sosai ba harta sunana NADEEYAH bata iya furta shi sai kawai ta samin NADINE da harshen su. Duk wanda ya sanni anan da sunan da yake kirana dashi kenan. Bayan wannan kuma sai harshen nasara da muke makaranta shi nan b'angaren mu akwai dogari (Gaurd) na musamman dake koyar damu turanci don ya zama kaman doka ne mutum ya koya saboda gudun had'uwa da wani daga cikin masu Mulki. A yanda nake ji sunfi yin turanci a kan harshen su mai dad'i yaran Manzon mu Annabi Muhammad (S.A.W) saboda y'an boko ne. Kaf cikin su jinin sarautar basu cika zama ba a nan sai kasashen waje. Shi yasa ma ilimin addinin ya yi musu k'arancin. Ina da shekara goma sha bakwai cikin masarautar Egypt KING SAIFULMULK da QUEEN AIRA suka sauka daga kan kujerar Mulki suka d'ora d'ansu da naji anawa lak'abi da EZKE'IL wasu suce AZRAH. A yanda naji ana labarin sa mutum ne shi mai masifar had'arin gaske. Bashi da imani bashi da tausayi. Maganan Mama Maria a koda yaushe nayi hankali koda wasa kar na bari hanya ta had'ani dashi. Kai ko hanya nabi naji ana labarin sa tace na chanza wata. Ranan nad'in nashi kaf cikin mu babu wanda ya runtsa. Yanda muka ga rana haka muka ga dare. Wuni mukayi muna aiki babu kama hannun yaro. Musamman ma mu da muke b'angaren girki. Mama Maria har ciwo tayi saboda gajiya ga kuma girma dake k'ara kamata. Da yawa wasu abubuwan nike yinsu nace ta huta. Shi yasa aikin ya zame min jiki, Idan ka cire ciwon jiki da kai babu wani bayan hakan. A ranan ne zan iya cewa muka fito daga b'angaren mu ,muka mik'a abinci wajen da ake ajiyewa a shiga dashi cikin masarauta. Tunda ake fita dashi ban taɓa karb'a na fito da dashi ba hasalima nan gurin mu dogarai ke shigowa su kwasa suyi waje da su. D'ai-da'i kun rana ne Mama Maria ke fita da abincin da kanta bata tab'a cewa nazo muje tare ba. Wajen had'a kayan ne muka had'u da Fahima. Rungume juna muka yi cikin matsanancin farin cikin ganin juna. Harna fidda ran k'ara ganin ta sai gashi Allah ya had'amu. Tun daga ranan muke d'an satar jiki muna haɗuwa. Ita tana can b'angaren masu wanki. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Yau ya kama ranan weekend. Tun dare Mama Maria ke kwance zazzabi mai zafi ya rufeta. Da kyar ta iya yin sallan Asuba don ko karatun Qur'ani da take koya min duk bayan sallan asuba kasawa tayi yau. Na shiga cikin matsanancin damuwa da ciwon nata hankalina duk ya tashi. Idan itama ta mutu bani da kowa yanzu a duniya sai ita. Ina yin salla na miƙe da sauri na fito katon kitchen d'in dake nan kaman gari masu aiki nata kai kawo sai kayi tunanin kasuwace. Da sauri na fara bin kayan ganye dake ciki kwanduna ina dubawa har Allah ya taimake ni na samo ganyan lemon. Shayi na had'a mata da ganyen da y'ay'an coffee. Cikin y'ar k'aramar butar shayi ta silver na juye na d'ora kan plates da d'an k'aramin kofin butar. Ragowar abincin da aka kawo daga masarauta nabi da sauri ina d'an duba abu mai dan ruwa-ruwa. Kayan abinci ne gasu nan sunfi kala ashirin. Nama ne , kaza ce ,kifi ne, snacks ,kayan ganyayyaki ,fruits ne gasu dai bila adadin dan wasu ma ko tab'asu ba'a yiba. Haka kullum zamu dage mu girka a dawo da rabin abinci ba'a tab'a ba. Shi yasa babu yunwa mukam a gurinmu kaman sauran b'angarorin. Dan muna ci mu koshi har sai mun ture. Kaza na hango katuwar gaske kan wani plate an shak'e da abubuwan ci wasu ma baka sanin mene. Da sauri na d'auki plate na yanka k'azar na d'ora a kai na kwashi romanta da yawa na zuba na hada da d'an snacks na koma d'akin mu da sauri. A tsaye na tadda Mama Maria tana ta rawar jiki da babban d'anta da kanwar sa dake binsa. Huzaifa da Jalila. Kaya suke sa mata suna ganina fuskarsu su ta cika da fara'a. Ajiye kayan nayi cike da farin cikin ganin su nace "Huzaifa , Jalila. Marhabanbikum, kaifal hal?" A tare suka bani asma " Alhamdulillahi, kaifa Anty?munzo tafiya da Mama ne saboda yanayin jikin ta, zata koma gida ta d'anyi jinyar ta acan har Allah ya bata lafiya" Ido na zaro tuni ruwa sun fara cika su. Idan suka tafi da ita zanyi zaman kad'aici. Babu yanda zanyi haka na taimaka musu muka shirya Mama Maria ina k'ok'arin hana kaina kuka. Duk abunda nake nasan Mama Maria na kallo na tasan kuma dakiya ce kawai nake saboda babu yanda zanyi. Muna gama shirya ta Jalila ta kwashi kayanta suka rik'e ta zasu fita da ita. Hannuna ta kama ta tallafo fuskata. Hawayen da nake ta k'ok'arin riƙewa suka tawo shar kan kuncina. Murmushi ta yi na wanda ke jin jiki tace. "Ki kwantar da hankalin ki Nadine, da zarar na warke zan dawo kinsan babu yanda za'ayi nayi nesa dake sai in ta kama dole ne. Yanzun ma naso tafiyar dake ban samu wannan alfarmar ba saboda King SAIFULMULK da QUEEN AIRA basa k'asa sai EZKE'IL. Kinsan wane AZRAH yanzu ma da kyar ya amince wa Huzaifa da Jalila su d'auke ni saida ya ganni cikin matsanancin hali tukun. Nadine ki kula da kan ki har sanda xan dawo kar kiyi wani abu da zai jawo hankalin EMPEROR AZRAH kan ki don Allah Nadine" Ina kuka na d'aga mata kai. Ba yau ta saba tafiya ta barni ba. Duk inda zata je kuma bata wuce kwana biyu ,yau d'inne kawai nake jin kaman wani abu na shirin faruwa idan ta tafi ta barni. Huzaifa da Jalila suka hau dariya suna tsokana ta dole na ware muka fito nayi musu rakiya har bakin k'ofar mu. Ban bar bak'in k'ofa ba saida suka b'acewa ido na na sauke ajiyar zuciya mai k'arfi na koma ciki. Ranan wuni nayi babu kuzari. Harta Fahima data saci hanya tazo muyi hira sai gajiya tayi ta tafi dan duk abunda tace sai dai na bita da eh,ko A'a. Kwana biyu da tafiyar Mama Maria na kasa warware wa. Duk abunda nake ina yinsa babu kuzari. Wajen la'asar yau na fito dauke da kwando dana zubo kayan ganye daga lambu dake can bayanmu. Azeemah dake aikin Mama Maria duk lokacin da bata nan ta aike ni na deb'o mata. Tafiya nake ina y'ar wak'a ta larabci da Mama Maria ta koyamin duk kewar ta ta dame ni. Bansa ya akayi ba na fito wani katon Garden dake nan gari guda ga wasu irin bishiyu masu masifar kyau da suka k'awata gurin an kuma kewaye gurin da kujerun glass da aka yiwa ado da furanni masu kyan gaske. Turus na tsaya ina kallon aljanna duniya. Ban taɓa sanin da akwai gurin nan ba sai yanzu. Can gefen sa wani irin kwami ne dake zubda wani irin ruwa mai shegen haske kaman madara ga wasu irin fulawoyi dake zuba cikin sa da wani irn kamshi da kukan tsuntsaye masu masifar kyau dake shawagi a gurin. Nikam ya aka yi bansan da wannan aljannr duniyar ba duk tsawon zamana cikin wannan masarautar?. Dube-dube na fara ina tunanin hanyar dana biyo ta kawo ni nan. Chak idon nawa ya tsaya kan wata hallita mai masifar kyan gaske. Tubarakalla MashaAllah, hak'ika babu abun yabo da bauta sai Allah. Bayansa kawai na gani nasan cewa koma wane wannan ba k'aramin kyakkyawan mutm bane. Dogone mai faffaɗan kirjin duk da bayan nasa kawai nake iya gani yanayin zubin halittar sa ya nuna shi d'in maji k'arfi ne. Gashin kansa dake tufke tsakiyar bayan sa nabi da kallo baki sid'ik dashi har tsakiyar bayansa duk da ya tufke shi. Wata irin tsayuwa ya yi bak'in kwamin dake zubda ruwa hannun sa goye a bayan sa ga wata irin tsuntsuwa mai masifar kyau kan k'afad'ar sa. Kayan jikinsa riga da wando farare kaman na Pakistan mara nauyi nabi da kallo da basuyi nuni da shi ko wani mai muk'ami bane cikin masarautar. Murmushi nayi a raina nace ai dole ma na kulla k'awance dashi kodan saboda kyansa duk da ban taɓa ganin sa ba cikin masarautar. Wata kila sabon d'auka ne cikin bayin da aka d'auka satin daya wuce. A hanzarce na k'asara inda yake tsaye cikin sand'a . Ashe yaji ni dan a wani irin slow ya juyo inda nake. Kalu'innalillahi. Chak numfashi na ya d'auke sanda nayi arba da kyakkyawar fuskarsa. Tunda na taso tsawon rayuwa ta naji yanda ake zuzuta kyau na, amma wannan bawon Allahn ni ba komai bace a kansa. Ban taɓa ganin mutum mai tsananin kyau kaman sa ba ,duk da ba fita nake ba nasan ko na fita da wuya a samu mutum mai masifar kyan sa. Wata kila ma yafi EMPEROR EZKE'IL kyau kaman yanda naji ana zuzuta kyawun nasa. Murmushi nayi mai kama da yak'e nayi tsuru-tsuru dani kaman wadda aka kamata tana sata. Kwayar idansa dake bak'a sid'ik da ita ya zubamin ya d'aga cikakkiyar girarsa guda d'aya da suka kusa had'ewa . Cikin inda-inda da rashin sanin abun fad'a nace da larabci. "Assalamu'alaikum. Ya kke?, hala kai sabon d'auka ne anan?" Shiru bai bani amsa ba sai idon sa daya zubamin ga uban kwarjini da yake dashi kaman na zura a guje amma na dake don ina son gwada damata. To ko bayajin larabci?. Kai na gyad'a na juya harshe da turanci nace. "Hey are you knew?" Nan madai shiru bai bani amsa ba. Na fara tsarguwa da kallon da yakemin zuciya ta tace ki kama gaban ki Nadine. Shawarar zuciya ta na d'auka na juya da sauri zan tafi sai kuma wata zuciyar tace ki gargade shi ya yi hankali cikin masarautar nan ya iya takun sa. Juyowa nayi da sauri na fara magana ina yi da larabci ina had'awa da turanci kai harma da Hausa tsabar yanda na rud'e da kwarjinin sa. "Kayi hankali cikin masarautar nan idan kai sabo ne. Tunda har ka shigo masarautar nan nasan kasan wane KING AZRAH. Ba sai na tsaya ina maka dogon bayanin rashin mutuncin sa da rashin Imanin saba,amma dai kayi hankali da takun ka dan mugun mutum ne mai kan agwagwa, mummuna mai katon ciki. Nasan yanda ake cewa yana da kyau ko yatsan ka bazai kama ba...." 'NADINE ' Zuciya ta ta kirani da k'arfi. Chak na tsaya da b'ab'atun da nake Ina zare ido. Wani irin kallo naga yana min da naji hanjin cikina sun kad'a. Shikenan na b'ata damata nasan zama abokiyar sa. Nasan yana min kallon mahaukaciya na tsaya ina ta b'ab'atu bana ko Jan numfashi daga haɗuwa da mutum bansan waye ba?.A guje na juya a sittin na bar gurin cikin matsanancin kunya. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 ASHANTY LOVE. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 11/15. Ban tsaya da gudun ba don burin kunya saida na tabbatar na sadu da sashen mu. Kitchen na nufa kai tsaye na ajiye kayan lambun dana deb'o kan kanta na durkusa ina haki hannuna dafe da k'irjina dake bugawa. Muryar Mama Azeema naji a kai na d'ago da sauri ina kallon ta da murmushi kan fuskata dani kaina na rasa dalilin sa. "Ina ki ka shiga tun d'azu ki deb'omin kayan lambu kawai?" Y'ar dariya nayi mai kama da yak'e nace "Yi hak'uri Mama Azeema bansan zan dad'e haka ba. Na tawo ne na kauce hanya na b'ata " Ido ta zubamin tana jiran k'arin bayani. Idan nace mata na had'u da wani hanyar dawowa ta zata ce babu wani b'ata da nayi da sani na ne. Ni ko yama sunan sa? Allah yasa gobe mu had'u na tambaye shi. Kai na sosa nayi saurin kawar da kaina daga kallon tuhuma da takemin. "Wlh Mama Azeema b'ata nayi. Gani kawai nayi na bulle wani Garden mai shegen kyau. Ban taɓa sanin da akwai shi ba ,koda yake ba fita nake bane shi yasa babu lallai nasan dashi." Ido waje naga tana kallona kafin ta kama hannu na da sauri taja ni gabanta. "Me naji kina cewa Nadine?,kinsan inda ki ka tsinci kan ki kuwa?, wa ki ka gani a gurin ?,kin had'u da wani" Kai na girgiza ina kallon fuskarta dake d'auke da tashi hankali k'arara. "Babu wanda na haɗu dashi Mama Azeema amma me yasa naga kin shiga damuwa" "Saboda wannan gurin b'angaren Sarakai ne . King Azrah yasa aka gina shi bayan nad'in sa. Babu wani bawa daya isa ya shiga gurin har saida iznin sa. Ko da ace ka shiga gurin ne cikin rashin sani sai ka karb'i hukunci. Akwai bayi da dama da suka samu b'atan hanya irin ki har yau babu wanda ya k'ara jin labarin su" Shiru tayi tana maida numfashi na zuba mata ido ina tunanin mutumin dana had'u dashi cikin garden d'in. Suturar jikinsa na tuna da bata da banbanci da kayanmu na bayi. Mu mata muna sanye ne da doguwar riga mai d'an fad'i daga kasa wajen kugu an dan tattare ta kad'an ya zama kaman sket, sai saman rigar wajen k'irji da mad'aurai gudu uku. Rigar mai three quarter d'in hannu ce. Su kuma maza suna sanye ne da riga da wando ruwan toka mu kuma farare. Rigar kaman Y'ar Pakistan ce da wandon ta. Sai hula ko dan hankici da zamu daura a ka ga duk mai so. Ance ko wane b'angare da irin kalan kayan su. Mu namu b'angaren kalan namu kenan. Ba'a chanzawa sai in ana cikin d'aki ko kuma ranan da babu aiki. Nikam ina dasu wajen kala goma da Mama Maria ke sawa ana d'inka min duk lokacin da aka samu yadi mai kyau. Tunanina ne ya tsaya kan cewa shima bawan ne amma ba b'angaren mu ba. Yanzu haka ko shike kula da garden d'in shi yasa kayan sa suke farare kal . Gum nayi da baki na ban k'ara cewa komai ba na wuce na kamata aikin ina na taimaka mata da yanka kayan lambun dana kwaso. Har muka gama tunani na na kan wannan mutumin Mai Kyau. Sunan dana rad'a masa kenan. Saboda rashin Mama Maria nina fita da abincin da taimakon Mama Azeema da sauran mutane da muke abinci tare muka kai can inda ake ajiyewa. Shi kanshi gurin d'aukan abinci idan kaje kaman karka fita saboda kyau. Komai Allah ya wadata su dashi dole kuwa suyi abunda suka ga dama. Allah ya kyauta. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Tsawon kwana biyu kenan da haɗuwa ta da wannan bawan Allah har yau kuma ban k'ara sashi cikin ido naba. Sai naji duk babu dad'i na saddakar cewa bazan k'ara ganin saba. Duk irin kashedi da Mama Azeema tayi min akan garden d'in nan ban fasa satar hanya ba nabi ko Allah zaisa na ganshi ta wajen don tunani na yafi k'arfafa ne a nan yake nashi aikin, amma sai naje na gama zagaye ne ban ga ko inuwar sa ba. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Qur'anin dake hannuna na ina bitar karatun da muka yi da Mama Maria na rufe sakamakon bugun k'ofar da naji ana yiwa k'ofarmu. Agogon dake mak'ale jikin bango na kalla. Karfe shida da rabi ya nuna. To waye haka yanzu da sassafen nan?. Ko aiki bama farawa sai bakwai dan su kansu wanda muke yiwa bautar basa tashi sai wajen d'aya na rana sannan za'a kwashi abincin su nasafe a kai musu lokacin mun kusa sauke na rana. Kunga abunda yasa bama zama da yunwa. Qur'anin na ajiye da sauri na tashi na ajiye gefe saboda bugun k'ofar ya yi yawa. K'ofar na nufa a hanzarce ina cewa gani nan. Da rawar jiki na buɗe k'ofar dan ganin masu wannan bugun. Matsanancin bugawa k'irjina ya yi ganin Royal Gaurd(dakarun Sarki na musamman) ba'a ganin su sai in mutum ya yi laifi. Laifin ma mai girma da zaisa King Azrah ya turosu da kanshi suzo su tafi da mutum. Ganin su babbar musifa ce. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Me ya kawo su k'ofar mu? Me nayi?. Ko an gano ina zuwa Garden d'in ne a b'oye? bugun K'ofar da suke ya fito da Mama Azeema da sauran mutanen dake nan b'angaren namu. Ina kallon yanda tashin hankali ya bayyana k'arara kan fuskar Mama Azeema da sauran Mutane gashi basu isa su tunkaro inda suke ba ko saji ba'a sin zuwan su nan. Tashin hankalin dasu Mama Azeema suka shiga ba komai bane kan wanda nake ciki. Kad'an ya rage ban saki fitsari ba har wani gumi ke kyetomin tsabar firgici. Kallon su nake jiki na, na rawa na fara k'ok'arin buɗe baki nayi magana suka rigani da firgitacciyar murya d'aya daga cikin su ya yi magana. "Anty NADINE ?" (kece Nadine?) Jikina na rawa na d'aga kai dan bazan iya basu amsa ba ji nake kaman na fashe da kuka. Kallon juna suka yi suka k'ara kallo na kafin d'ayan ya cigaba da cewa "Ana buƙatar ki cikin masarauta yanzu-yanzu" Wani irin kullewa cikina ya yi naji kamn zan kifa saboda firgici. Nashiga Uka ni NADINE. Mama Maria kizo ki cece ni. Me nayi yau ake nemana cikin masarauta? Tsawon shekara goma sha takwas ban taɓa takawa cikin taba ko wani guri makamancin ta bare nayi laifin da za'a nemi cikin ta. Idan ka cire garden d'in nan. Shima kuma bana shiga saidai na kewaya shi tunda tunda katangar sa da wani irin glass aka yi shi. Kai ko King SAIFULMULK da QUEEN AIRA basu san da zamana gurin Mama Maria ba. Inma sun sani to sun manta dani dan ina bin duk wasu dokoki saboda gujewa wannan rana. Maganan su ta katsemun tunani "Ki hanzarta kina tsaye. Umarni ne daga EMPEROR AZRAH " Wai ai tuni naji fitsarin da nake riƙewa yana k'ok'arin kufcewa a guje na juya na koma d'aki. Tsawar su naji bayana sunyi tunanin ko guduwa zanyi. To in gudu inje ina?. Da gudu na fad'a d'an banɗakin mu dake cikin d'akin da muka kewaye shi da labule. Ina jin sawun tafiyar su bayana suna ganin na shige suka ja tunga bakin k'ofa suka tsaya suna jirana. Saida na rage marata na fito jiki a salube ina kallon su kaina. Wasu d'irka-d'irka dasu jiki duk a murmurd'e. Ga wasu kaya da suka sa na yak'i dake k'ara firgita mutane. Gaba nayi suka rufamin baya. Ina fitowa na iske su Mama Azeema da sauran mutane tsaye k'ofar d'akin namu. Tana ganin na fito ta tawo da sauri ta rungume ni tana kuka. "Me ki ka yi Nadine? Me ki ka yi da har King Azrah ya turo a tafi dake?" Murya ta na rawa nace "nima ban sani ba Mama Azeema. Ke shedace babu inda nake zuwa cikin masarautar nan" Kai kawai ta d'aga hawaye na bin fuskarta. Tsawa suka daka min "Wuce muje mana kina b'ata mana lokaci " A sanyaye Mama Azeema ta sake ni na wuce ina sharar hawaye kasan zuciya ta ina kiran Mama Maria. Da ace tana nan nasan sai inda k'arfi ta ya k'are wajen ganin ta hana sun tafi dani. Inma bata hana sun tafi da niba to tabbas babu makawa tare zamu tafi da ita. Kome zan tarar kuma cikin masarautar da ban taɓa taka k'afata cikin taba?? ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 ASHANTY LOVE. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 16/20. Tafiya nake ina sharar hawaye suna biya dani. Tunanin mak'omata cikin wannan masarautar nake. Tsawon minti hud'u muka dauƙa muna tafiya kafin na fara hango tangamemen ginin daya raba mu da cikin masarautar. Dakarune kewaye da ita ta ko ina tun daga farkon ta har k'arshen katangar da baka ganin sa. Ajiyar zuciya na sauke mai k'arfi zuciya ta fal tsoron abunda zan tarar. Da sauri naga sun wuce ni zuwa bakin k'ofar suna wa katon Gaurd dake gadinta magana. Shi kaɗai ma ya isa yasa ka juya da gudu tun kafin ka k'arasa. Katon gate d'in suka buɗe da aka yi da zallar Crystal stones. Baki na hangame na tsaya chak ina kallon wannan masarauta kaman aljanna duniya. Hak'ika babu abun yabo da bauta sai Allah. Shike bayarwa kuma shike hanawa ga wanda yaso.Gaskiya dole su shagala da duniyar da Allah ya basu su manta cewa zasu koma gareshi. Ji nayi kawai sun tankad'ani nayi taga-taga kaman zan fad'i Allah ya taimake ni na tsaya da k'afafuna. Tsawa suka daka min "Wuce mana kinja kin tsaya. Ko kinsan illar barin KING AZRAH zaman jira?" Bance komai ba na cigaba da tafiya bansan inda zanyi ba don yaune karo na na farko dana shigo cikin wannan Palace. Lura da hakan da suka yi suka k'ara wuce ni na cigaba da binsu a baya. Katon gini muka shiga mai masifar kyan gaske da doguwar hanya kaman corrido. Shima saida muka yi y'ar tafiya sannan muka bulle wani irin Garden mai tsananin kyau dayafi na b'angaren mu. Ta cikin sa muka shiga sai gamu mun bullo Royal Palace. Ido waje nake kallon ginin. Kunne nayi baki nayi. Sosai na zama y'ar kyaune na hangame baki ina kallo. Tankamemen falo muka shiga da ke dauke da kujerun gold da garden cikinsa kai harma da kwani na ruwa a tsakiyar sa ga wasu tattaburu farare dake shawagi kansa. MashaAllah hak'ika Allah ya basu duniya saura lahirar su kuma. Glass staircase dake can k'arshen falon ya kewaye shi ta ko ina suna nufa na rufa musu baya. Kaman dai yanda ko ina yake zagaye da dakaru haka shima falon yake tun. Saboda yawan benen saida na gaji na d'an yunƙura zan hutu suka k'ara dakamin tsawa na miƙe da sauri na cigaba da binsu. Ajiyar zuciya naja mai k'arfi na dafe gefen cikina ganin mun kawo k'arshen benen. Kai wannan wahala da yawa take. Mutum in mai k'iba ne ai cikin kwana biyu zai ya zazzage gaba d'ayan sa. Hanya muka bi doguwa nan ma kaman corrido mai d'auke da kofofi wajen shida ko wacce a gark'ame da matakan tsaron a bakin ta. K'ofar dake tsakiya warda tafi ko wace girma da kyau tana fuskantar mu ,mu ka tsaya. Kai na d'aga ina kallon jibgegiyar k'ofar da aka yi kaman da gold sai shek'i take saman ta an rubuta EMPEROR EZKE'IL CHAMBER da stone's na crystals abun sai ya k'ara armashi sosai. Dakurun dake zube gaban k'ofar na maida hankali kai ina kallo cikina na bada sauti saboda matsanancin tsoro. Sai yanzu nake jin irin bugun da zuciyata take da mugun gudu kaman zata tsaga kirjina ta fito. Gyaran murya d'aya daga cikin dakarun da suka titsiyoni nan ya yi nayi saurin maida hankali ina kallon su. Kai ya jinjina ganin na maida hankali ina sauraran shi ya fara magana. "Idan an buɗe kin shiga kar ki kuskura ki d'aga kan ki har sai ya baki umarnin hakan. Ki kiyaye kallon sa ba tare da izni ba kinji ko" Sakato na tsaya ina kallon Gaurd d'in. Wane irin abu ne kuma haka? Tsawa ya dakamin "Kinji abunda nace?" Da sauri na d'aga kai cikin firgici. Kai ya d'aga ya juya. Ina kallo yaja numfashi mai k'arfi kafin ya d'aga hannu ya buga k'ofa sau biyu ya koma baya ya wani k'ame ko motsin kirki baya yi kaman an zare masa laka bashi kad'ai ba gaba d'aya dakurun sun k'ara k'amewa kaman basu numfashi. Tun daga nan na fara hango makomata. Tsawon minti goma muna tsaye babu alamun za'a amsa bugun k'ofa bare a buɗe. Kafafuwan har sun fara gazawa na fara k'ok'arin sunkuyawa sai kawai naji wata irin murya mai shegen gard'i da sanyi gata so, so Deep tayi magana daga cikin d'akin a kasalance kaman wanda maganan kewa wuya. "Minnnn ?" (Waye?) Ai tuni hanjin cikina suka k'ara kad'awa na gyara tsayuwata da sauri kaman yanda naga dakarun sunyi. Jiki na rawa ya bashi amsa. "Mune KING AZRAH. sakon da kace a kawo maka gashi mun tawo dashi" Sak'o? Ban ma isa a kirani da mutum ba kenan?. Nan ma dai sai da ya d'auki sama da wajen minti goma kafin ya bada amsa. Wannan wace irin rayuwa ce?. Wace irin isa ce wannan?wai shin da mai kuɗi da mulki, arziƙi ,talaka duk ba d'aya suke ba gurin Allah?. Me yasa wasu mutanen idan sunga Allah ya basu duniya sai su dinga ganin kaman sunfi kowane?. Bafa dabara ko iyawa tasa Allah ya basu wannan matsayin ba. Duk wani abu da zai samu bawa a wannan duniyar jarabawa ce a gareshi. Wani zata kaishi wuta wani ta kaishi Aljanna. Ga wad'an da suka fifita duniyar su kenan a kan laharir su. Sun manta cewa duniyar nan ba komai bace. Maganan gaskiya iya fusata nayi. Wannan wulaƙanci ya yi yawa. Yasa an kawoni ba tare da nasan abunda nayi ba. Nazo kuma sai iko yake mana. Anya kuwa zan iya jure wannan isar? A kasalance naji ya yi maganan da saida na kasa kunne sosai naji. Cikin harshen nasara yanzu yace "Let her in" Kallo na gaurd d'in ya yi ya matsa k'ofar da sauri don ya buɗe yana cewa "Kar ki manta gargad'in da nayi miki. Kar ki d'aga kai har sai ya baki umarni" Ban bashi amsa ba na d'auke numfashi bayan buɗe k'ofar da ya yi duhun d'akin ya yi min sallama da wani irin kamshi da sanyi mai ratsa bargo da kashin mutum. Da kyar na d'aga kafata da suka yi nauyi na tura kai cikin d'akin bakina d'auke da siririyar sallama. Bana iya ganin komai saboda duhu sai y'ar fitilar dake can kan wata tebir katon gaske mara haske. Ido na buɗe sosai ina kallon kaman mutum ne zaune gaban tebir din ya d'an jingina dashi. Cikin duhun na fara bin kafafunsa da fitilar ta d'an haska min da kallo. Kaman wando ne na suit a jikin sa daya dan kama shi sai farar riga mai botira da kusan gaba d'ayan su a balle suke hannuwansa harde a kirji ya tattare hannun rigar zuwa gwiwar hannun nasa. Cigaba nayi da kallon nasa na d'aga ido na zuwa wuyan sa dake sanye da wata irin sarkar data kwanta kan faffaɗan kirjin sa dake a murd'e sai shining yake ga gashin kansa dake zube wajen kafad'unsa wasu sun zubo kan kirjin nasa sun kwanta. Ido na k'ara d'agawa zuwa dogon wuyan sa wajen Adam Apple nashi (makwalato) na cigaba wajen fuskar sa sai diff wutar ta d'auke gaba d'aya. Tuni na dawo cikin hayyaci na na tuna da gargad'in da aka yimin. Innalilllahi meke damuna na ne? Nashiga uku ni Nadine. Rarraba ido nake saboda matsanancin duhun d'akin baka ganin komai. A mugun hankali naji kaman takun tafiya na kasa kunne inda nake jin takun da baya fita kaman wanda ke sand'a sai kuma naji diff shima ya d'auke. Yanzu nake jin ciwon rashin ganina cikin duhun da banayi. Da Sam ban damu ba amma yanzu saboda wannan mugun naji ina ma ya dawo ko na samu naga abunda yake kar naje ya kashe ni a banza. A hanzarce na kai hannu na kare ido na saboda wani irin haske dal da dakin ya dauka lokaci d'aya. Murmushi (chuckling) naji anyi mai birkita lissafin mutum nayi saurin juyawa inda naji sautin. Sai da na kusa zubewa a k'asa lokacin da kwayar idon mu suka had'u jikina ya hau kyarma bansan sanda na d'aga hannuna na nuna saba. Yana zaune yanzu kan kujerar katon glass tebir irin ya dogara duka gwiwar hannun sa kanshi ya talleb'e hab'ar sa da yatsun sa daya had'a su guri d'aya. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Baza kuso kuga irin matsanancin tashin hankalin dana shiga ba wannan lokacin babu abunda ke yawo a kwanyar kaina sai kalmomin dana furta ranan kaman " 𝒎𝒖𝒈𝒖𝒏 𝒎𝒖𝒕𝒖𝒎 𝒏𝒆 𝒎𝒂𝒊 𝒌𝒂𝒏 𝒂𝒈𝒘𝒂𝒈𝒘𝒂 , 𝒎𝒖𝒎𝒎𝒖𝒏𝒂 𝒎𝒂𝒊 𝒌𝒂𝒕𝒐𝒏 𝒄𝒊𝒌𝒊, 𝒂𝒛𝒛𝒂𝒍𝒖𝒎𝒊 𝒎𝒂𝒓𝒂 𝒊𝒎𝒂𝒏𝒊" Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un shi ne King AZRAH. Shine na gama zagin sa kan idonsa cikin rashin sani duk da cewa wasu kalmomin da hausa na fad'e su. Na shiga Uku, Na shiga Uku. Da kyar na d'aga ido na na kalle shi har yanzu yananan yanda yake fuskarsa babu wani expression a kanta. Kwayar idansa da ke da girma gata baka sid'ik kaman midnight dake bada wani calm expression ya zubamin kaman mai ganin hanjin cikina. D'aga gira ya yi gefen bak'in sa shima ya d'aga (smirk) da alama tsoron sa da ya gani kwance kan fuskata ya bashi enjoyment. Magana ya yi a kasalance muryar sa a kausasashe "Masmik?" Saboda firgici na kasa bashi amsa sai kai kawai da nad'aga. Gira ya k'ara d'agawa da alama kaman yin hakan nature nashi ne. Da sauri yanzu nace murya na rawa "NADINE" A d'ai-da'i ce ya kira sunan nawa "NA-DI-NE.. hmm" Sunayen Allah kawai nake kira cikin raina da duk wata Addu'a data zo baki na. Murmushi ya k'arayi na lura da double dimples nashi a ko wane kunci. Tun daga sama har k'asa ya kalle ni sai kuma ya tashi daga zaunen da yake ya zagayo gaban tebir d'in ya zauna kaman yanda ya yi d'azu dana shigo. Kuttt na had'iye yawu ina kallon sa na matse kafafuwana dake rawa guri d'aya. A take yanayin fuskarsa ya chanza zuwa wani deadly calm expression. Magana ya fara da calm voice cikin harshen turanci " what is that you say?" Kuttt na k'ara had'iye wani yawun, naji kaman na juya a guje na fice. Ga mamakina sai naji yana maimaita abunda nace harda hausar da nayi. " Kayi hankali cikin masarautar nan idan kai sabo ne. Tunda har ka shigo masarautar nan nasan kasan wane KING AZRAH. Ba sai na tsaya ina maka dogon bayanin rashin mutuncin sa da rashin Imanin saba,amma dai kayi hankali da takun ka " Yana dasa aya na kusa zubewa k'asan gurin. Duk irin matsanancin sanyin na d'akin wanda tsab mutum zai daskare cikin sa zufa na had'a kaman wadda aka zubawa ruwa. Gashin kaina dana tufke shi a tsakiyar kai na d'ora hula a kan nawa ina jin yanda gumi ke biyowa ta cikin gashin yana bin wuyana da goshina. Shi kanshi gashin ya jike jagab. Ban gama shiga tashin hankali ba sai da naji ya k'ara magana yanzu da Hausa. "Ko kinsan tsawon lokacin dana d'auka ina koyan wannan yaren naki saboda na gane ma'anar kalman MAI KAN AGWAGWA DA KATON CIKI?" "You dare to insult me like that?, mene ma ki ka ce .Bani da Mutunci da Imani?, why not na nuna miki rashin Imanin nawa zahiri yanda zaki ji dad'in bada labari da kyau?, . You disrespect me in the worst way possible. I know you have being told not to look at me, amma gaki kina kallo na ido cikin ido?" Da azama na sauke ido na k'asa jikina na rawa kaman mazari. Wani murmushi naji ya k'ara yi da nasan babu alkhairi cikin sa. "So Nadine. Daga yau zaki zauna a nan don ki sheda rashin imani na da rashin mutunci na. Aikin ki ya dawo cikin masarauta daga yau. Know Dismiss.." Baima k'asara ba na juya a sukkuwanne na fice da mugun gudu daga d'akin. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 21/25. Bansan inda nake sa gaba ba saboda firgici saida na sadu da k'ofar da zata fitar dani daga cikin masarautar. Ajiyar zuciya naja mai k'arfi bayan na tsaya bak'in k'ofar na sunkuya rik'e da ciki ina maida numfashi. D'agowa nayi saboda idon da naji a kaina. Gaba d'aya hankalin dakarun yana kaina babu kuma wata alama da take nuna zasu buɗe min k'ofar na fita. Banyi k'asa a gwiwa ba na k'arasa ina kallon jibgegen Gaurd d'in dake tsaron k'ofar kaman yanda shima yake kallo na. Jarumta na aro na saita nutsuwa ta kafin nayi magana. "Uhmmm ka buɗe min k'ofar zan koma b'angaren mu" Kallo ya watsa min irin don't mess with me d'innan ya kauda kai gefe kaman da iska nake magana. Ai kuwa na k'ara tunzura a fusace na k'ara buɗe baki zanyi magana muryar mace ta katse numfashi na. A hanzarce na juya inda naji muryar. Kyakkyawar yarinyar ce da a kalla baza ta gaza haura shekaruna ba ashirin da hud'u ko biyar ba sanye da suit riga da wando da Air Bluetooth sakale a kunnen ta. Fuskarta dake d'auke da katon glass daya cinye rabin y'ar fuskar ta ta da babu wani annuri ko kaɗan a tare da ita. Bayanta wad'annan Gaurds d'inne yanayin ta ya nuna ita ce gaba dasu. Tsawa ta daka musu da kausassar murya tace "Me ki ke tunanin ki ke shirin yi?. You damn idiot gets her" A hanzarce suka yo kaina dan cika umarni nayi saurin d'aga musu hannu. "Kar wanda ya kuskura ya tab'a ni, zan tafi da kaina" Na fad'a cikin tsawa. Saurin gimtse baki nayi. Ni kaina bansan inda na samu wannan kwarin gwiwar ba har na iya yin magana cikin tsawa haka. Shiru gurin ya d'auka kaman anyi ruwa an d'auke. Kallon da naga dakarun nayi min na k'ara shiga damuwa matuƙa. Da alama babu wani mahaluki daya tab'a tsayawa ya yi ja-in-ja da ita a matsayin ta na mace. Ga dukkanin alamu kuma tana da matsayi mai girma wajen King Azrah da sahalewar sa take duk abunda taga dama. Da wani irin izza ta tako inda nake tsaye . Glass d'in dake fuskarta ta cire ta watsamin manyan blue eyes d'inta da suka k'ara fito da asalin kyanta. Da wani irin sinister voice ta fara magana "Kar kiyi tunani ko na sakan d'aya saboda Kin dawo aiki k'ark'ashin Azrah kiyi tunanin matsayi ki ka samu. Ke d'in baiwa ce kaman sauran bayi babu wani chanji ko mahaluki da zai chanza hakan matsawar kina numfashi cikin masarautar nan. Dan haka ki kiyaye harshen ki in har kina son ki cigaba da rayuwa dashi a doron k'asa. Your nothing but a slave so stay within your limit" Ta k'arasa maganan tana jifana da wani k'ask'antaccen kallo kafin ta mayar da glass d'in ta kan fuskar ta ,ta wuce da tafiyar izza wasu daga cikin masu tsaron suka rufa mata baya wasu suka tsaya don tafiya dani. Duk cikin kalamanta babu abunda nake juyawa cikin kwanyar kai na sai sunan King Azrah data kira gatsau babu sakayawa. Tun daga nan na tabbatar da lallai ita d'in macece mai babban matsayi a nan tunda har ta iya kiran sunan sa haka babu shakka babu komai. Tabbas ita d'in na daga cikin list d'ina da zan gujewa in har ina son zama cikin salama. 'Ya Allah babu abun bautawa da gaskiya sai kai, baka d'orawa bawan ka abunda bazai iya d'auka ba, ina rokon ka, ka bani ikon cinye wannan jarabawar.' Addu'ar dana tsinci kaina ina yi kenan k'asan zuciyata data sama min nutsuwa. Numfashi naja mai k'arfi cike da kwarin gwiwar daya ragemin na fara takawa a hankali ina kiran sunan Allah nutsuwa na ratsa dukkan gabban jikina. Sab'anin d'azu yanzu wata hanya muka bi y'ar siririya sai gamu mun bulle wajen bayi dake aiki cikin masarautar. Babu wani banbanci tsakanin b'angaren su da damu sai dai girma kawai. Guri ne har guri gari gudu ma'aikata nata kai kawo kace kasuwa ce. Bakin wata matacciyar k'ofa na hango budurwan nan tsaye da wasu mata sanye da kayan bayi. Muna k'arasawa ta fara magana cikin izza "Nan ne d'akin ki daga yau. Wad'annan zasu nuna miki aikin ki da kuma dokoki da zaki dinga bi. Dan haka ki kiyaye " Bata jira amsa ta ba ta wuce bayan ta flipping gashin ta baya. Ban d'auke ido na daga kanta ba harta b'acewa ido na. Saida ta b'ace sannan naji matan sun sauke wani gauran numfashi na maida hankali kansu. Babbar cikin su wadda nake tunanin za tayi Mama Maria ta matso kusa dani da murmushi d'auke kan fuskarta. " zo muje ya'ta. " D'akin ta buɗe muka shiga. Wani irin wari da k'ari ya yi min sallama. Da alama an dade ba'a yi amfani da d'akin ba ga wata uwar yana da kura a kursurwoyin d'akin. K'aramin dakine dake dauke da wani tsohon gadon karfe duk ya mutu gefe masai ne ya yi bakikkirin ga wasu uban kyenkyesai suna yawa. Duk rashin wadatar b'angaren mu yafi nan sau dubu. A take naji amai na taso mun. Tabbas na yarda koma wace wannan yarinyar bata kauna ta. Aiko mak'iyin ka baza kaso ya zauna cikin wannan a kurkin d'akin dake d'auke da abun cutar wa haka ba. Muryar matar naji tana magana da tsantsan tausayi cikin ta "Ke kuwa y'ar nan meya hadak'i Anita? Babu wanda yake so yaga ya shiga cikin bakin littafin ta don bata da mutunci. Tana da karfin iko cikin masarautar nan saboda alak'ar ta da King Azrah . Gashi naji ance ke sabuwa ce kuma King Azrah ya zabe ki da kanshi. Tabbas sai kin jure don Anita babu abunda baza tayi ba kan EMPEROR EZKE'IL . " Idan na fuskanci maganan ta Anita nasan King Azrah shima kuma yasan da hakan shi yasa take abunda taga dama?. To ni meya shafeni da hakan?. Kasa jure warin d'akin nayi na fito da sauri ina kakarin amai. Biyoni tayi tana d'an buga bayana ta cigaba da cewa " wannan d'akin babu wanda ke amfani dashi saboda kazantar sa. Ni kaina nayi mamaki danaga ta ce nan ne d'akin ki. Sai kinyi hak'uri zamu taya ki gyarawa muje na nuna miki wajen karb'an abinci da sauran b'angarori. Layher ku da'n fara gyara mata d'akin kafin mu dawo" Hannuna ta kama muka hau zagayawa tana nuna min b'angarori dake cikin gurin kafin daga karshe mu yada zango wajen cin abinci. Faranti ta dauka nima ta bani muka k'arasa gaban kanta da aka d'ora abinci . Wani irin fatan wake ne kaman gudawa sai wani ganye da farar shinkafa a gefe. Yatsina fuska nayi ina bin abincin da kallo. Tabbas indai wannan ne cimar da zan dinga ci kullum na hak'ura da cin abinci. Wannan ai in kanaci kullum sai ka mutu a banza. Kallon yanda matar ke deban abinci take babu wani damuwa a tattare da ita alamun sabo da cimar. A take naji ashe mu kan a aljanna muke dan gaskiya mun fisu wadata suda ma suke cikin masarautar kenan fa. Karb'an kwanon nawa tayi ta zubamin ganin na tsaya na kasa tab'uka komai. Ita ta d'auko mana abinci muka dawo k'ofar d'aki muka tarar da Layher har sun gama aikin. Shiga d'akin nayi da ya yi kal yanzu sai warin aizil yake har zanin gado suka dan shimfiɗa kan a kurkin gadon. "Kinga ya yi kyau ko?" Kai kawai na d'aga dan gaba d'aya bakina ya mutu tunanin Mama Maria da mak'omata kawai nake. Ko wane irin aiki ne zanyi tunda ba'a sanar dani ba har yanzu.? Matar da na san sunan ta a yanzu da Layher ke kira da Mamee suka yi min sallama suka fice nayi musu godiya. Numfashi naja mai k'arfi na zauna bakin gadon ina bin a kurkin d'akin da kallo. Hannuna na kai na ciro sark'a ta dake wuya na. Tun sanda Mama Maria ta cire min sark'ar ban k'ara sawaba sai bayan tafiyar ta. Shima kad'aici ne ya dameni na saka ta na tura kasan rigata. Sai nake ji kaman Abbu da Innati na tare dani a koda yaushe hakan yake d'an ya ye min damuwa. Kiran salla azahar da naji anayi na miƙe na fito dan neman fanfo nayi alwala. Karo mukaci da Layher tana k'ok'arin shigowa tayi saurin ja da baya. "Yauwa dama Mamee tace nazo na nuna miki inda fanfo yake sai ki samu bokiti da zaki dinga zuba ruwa kina kaiwa d'akin ki" Kai na d'aga mata na bita ina tunanin wannan wace irin rayuwa ce?. Wajen fanfo ta nunamin nayi alwala ta bani bokiti na d'ibi ruwa na wuce dashi d'aki. Saida nayi salla na d'auko flat d'in abinci na zuba masa ido kafin na runtse ido na tura shi da kyar. In badan ina jin yunwa ba babu abunda zaisa ni cin wannan abinci. To ranan dai haka na wuni cikin wannan a kurkin d'akin da tunani kala-kala da suka yimin kawanya. Har dare ina zuba ido ko za'a kirani naji matsayin aiki na ,amma shiru har nayi salla isha na takure kan gado bayan nayi Addu'a. Bazan iya cewa k'arfe nawa ba don babu agogo cikin d'akin amma nasan na dade banyi barci ba. Saida na daina jin motsin kowa da komai duk girman gurin ya yi tsit baza kace akwai dubban jama'a a gurin ba. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 26/30. Bansan sanda barci ya d'auke niba ,haka ban dade da fara barcin ba na farka a firgice kaman zan shid'e sakamakon ruwan k'ank'ara da naji an zubamin shi a ka. A firgice na farka ina maida numfashi jikina ya fara rawa a take wani irin sanyi mai ratsa bargon jiki ya yimin salla. Nasan babu makawa sai na kwanta ciwo dan sam bana shiri da sanyi. Maganan Anita naji a kaina " barci ki ke?,bakiga ta barci ba. Ki tashi maza ki fito ki same ni a waje. Azrah na neman " Bata jira abunda zance ba juya ta fice daga d'akin. Da ido na bita zuciya ta na suya. Wane irin wulaƙanci ne wannan kana barci a zuba maka ruwan k'ank'ara a jiki?. Da kyar na miƙe ina rawar dari saboda zazzabi daya rufeni lokaci guda hak'orana har kakkarwa suke. Da kyar na iya cire kayan jikina na tsaya ina tunanin to kayan da zansa fa tunda basu bari naje na deb'o ba. Kaman kuwa taji abunda nake cewa cikin zuci sai gata ta dawo riƙe da y'ar bakko na da nake ninke kayana a ciki. Tsayawa tayi tsakar d'akin tana k'aramin kallo. Tun daga kan jikakken gashin kaina daya bazu har zuwa gwiwar kafata ya zubo gaba d'aya ya rufe ni. Har zuwa k'afafuwana dana rufe da doguwar rigata dana kare k'irjina da ita. Allah kad'ai yasan abunda ke cikin ranta dan jefo min jakar tayi ta juya ta fice daga d'aki a fusace. Ajiyar zuciya naja mai k'arfi na sunkuya da kyar na buɗe jakar ina rawar d'ari na d'auko doguwar rigata na saka kan jikakkiyar shimita da underwear d'ina da suke a jik'e. Sosai nake jin zazzabi amma saboda gudun tashin hankali haka na daure na fito da kyar. Karo naci da ita bakin k'ofar sai cika take tana batsewa. Wani banzan kallo ta jefamin tana cire glass dake fuskarta. "Na d'auka ai zaki shekara ne a ciki baki fito ba?" Nidai ban bata amsa na sunkuyar da kai. Gashin kaina kuwa ya tawo yarr ya rufe min fuska saboda ban kama shi ba ina so ya bushe. A fusace naji ta k'ara magana "Shi kuma gashin iyayi ne yasa baza ki tufke shi ba kaman yanda ki ka saba? Ko din kinji nace Azrah na neman ki?. Oh kina so ne idan kinje ki ja hankalin sa da wannan shegen gashin naki mai kama dana Aljanu?" D'agowa nayi na zuba mata manyan ido na jin irin kazafin da takemin. Wannan aicin fuska ne ita bata ga yawan nata gashin ba sai nawa?. Allah na tuba me zanyi dashi?. Ita dai data d'orawa kanta wahala sai tayi ta yi ai. Shashasha kawai. Tsaki taja mai k'arfi ta wullo min wani hankici "Ki kama gashin ki. Y'ar neman suna kawai banza mai ido kaman na mujiya. Wlh ina dai naga miki kar ki kuskura ki kara yin wani abu gaban Azrah da har zai bada intereste a kan ki inba haka duk abunda ya same ki kiyi kuka da kan ki" Numfashi taja ta taune harshe kaman mai tunani kafin ta cigaba da cewa. "Za kije Chambers nashi ki had'a masa ruwan wanka cikin kwami. Akwai kayan had'awa komai cikin banɗaki. Da zarar kin gama ki fito kar ki kuskura ya ganki. Ni bansan ma dalilin da yasa yace dole sai ke zaki had'a masa bayan akwai mai yi" Ta k'arasa maganan tana jefana da muguwara harara. Hak'ika nayi Imanin da da wuk'a a kusa tsab zata dab'amin saboda kishi. Ita kuwa wannan wane irin so ne take masa haka?. Ta gamu da aiki kuwa babba. Da kanta ta kaini har b'angaren King Azrah ta zagaya dani ta bayan wata k'ofa sai gamu cikin wani dan garden da aka kewaye da glass tun daga sama har k'asan shi. Tsuntsaye nata shawagi a ciki daga k'arshen sa wata kifa ce katuwa mai girma ta silver. Wasu madannai ta danna jikin k'ofar ta buɗe kanta kafin ta kutsa kai ciki nima na bita. Banɗaki ne katon gaske tsakiyar sa kwami ne na wanka kaman swimming pool sai turi ruwan ciki yake yana fidda wani irin hayaki mai shegen kamshi. Zagaye da ruwan kuma wasu kujerune na crystals da d'an tebir d'insa mai shegen kyau an k'awata shi da furanni. Gaban wata drawer dake can jikin bango ta tsaya ta fito da wasu kwala masu kyan gaske da kaloli a cikin su. Kan tebir d'in ta ajiye ta juyo tana kallo. Da fad'a ta ce "Ni ki ke jira ne na kawo miki kayan?" Da sauri na matsa gaban tebir d'in ina k'ank'ame jiki saboda zazzab'i. Tsaki taja mai k'arfi ta fara nunamin kwalaben. Duk kayan had'a ruwan wankan ne ashe. Da wanda za'a zuba ruwan ya yi kala, da wanda zaiyi kamshi, da wanda zaisa ruwan ya dinga fidda hayak'i mai dad'in kamshi. Gasunan kala-kala na riƙe su a kaina saboda gudun aikata ba dai-dai. Tana gama yimin bayani ta juya ta fice tana cewa "Ki hanzarta kiyi ki fito ina jiran ki a waje. Ruwan dake cikin kwamin sai kin zubar dashi duka kin tara wani sannan ki kunna fanfon dake ciki ki tara wani kafin ki fara zuba kayan dana lissafa miki" Sakato na tsaya ina kallon k'ofar data fice kafin na tattaro ragowar k'arfin daya ragemin na k'arasa bakin kwamin. Yanzu ta ina zan fara zubarda ruwan nan fisabillahi banga wata hanya da take nuna da inda za'a buɗe ba ruwan ya fita. Rigata na tattare na dora k'afa kan kwamin na zauna kan abin. K'afata d'aya a waje daya cikin ruwan . Sosai na sunkuya ina laluben inda zan buɗe ruwan ya fita kaman wadda aka ja naji na kifa cikin ruwan wankan gaba d'aya. Y'ar k'ara na saki kafin na jini cikin ruwan gaba d'aya. Ashe zurfine dashi gashi ban iya ruwa ba. Babu shiri na fara kici-kicin ceton raina. Hannu kawai na gani mai shegen kyau dake dauke da zararan yatsu dogaye gwanin sha'awa . Ban tsaya duba wanda ya kawomin d'aukin ba na kama hannu da sauri ya jani kyee na fito daga cikin ruwan. Ba'a sake ni ba saida aka tabbatar na tsaya da k'afafuna sannan naji koma waye ya sakemin hannu. Ga hannu da shegen laushi kaman audiga kaman ba hannun mutum ba. Gashin kaina daya rufe mun fuska na fara k'ok'arin tattare shi na sak'ale bayan kunne na. Da farar riga da wando naci karo na wanka doguwa mai madauri ya kwance rigar gaba d'aya. K'irjina ya fara harbawa na fara d'aga kaina a mugun hankali kaman slow motion har zuwa kugun sa inda wandon ya tsaya. Yawu na had'iye kut na daga ido zuwa vline nashi da yabi cikin wanda sa mai tazuge zuwa shafefen cikin sa dake dauke da well difine 8 pack abs (muna ce musu guraye). Chak na tsaya da idona kan murdadden faffaɗan k'irjin sa dake uban shining. Wani irin yawu na k'ara had'iye da mugun k'arfi da ya yi sanadin daya saki murmushi(chuckling) . Da azama na k'arasa d'aga kaina muka had'a ido dashi da d'agaggiyar girar sa guda daya gashin kansa tufke tsakiyar kansa sai gefen fuskarsa da wasu suka kwanta har k'irjin sa. Wani irin komawa baya nayi zan kara fad'uwo nayi sauri dafe kwamin. Tashin hankalin dana ke ciki yasa zazzab'in da nake ma na nemeshi na rasa. Gira ya k'ara dagawa ganin yanda na kafeshi da ido. Muka zubawa juna ido na y'ar tsakanni kafin naji Deep voice nashi yana magana cike da kasala "Pervert"( y'ar iska kenan ko a hausan ce?😅) "For the 3rd time kin k'ara karya min doka?. Kina a matsayin baiwa amma kinga abunda bai kamata ki gani ba. So what kind of punishment ya kamace ki?" Wani irin matsowa ya yi naja baya cikin ruwan da sauri . Sunkuyawa ya yi ya d'ora hannuwansa kan kwamin ya d'an rankwafa yana kallo na tun daga sam har k'asa fuskarsa babu wani expression. Wajen minti biyu muka yi a tsaye a haka yana k'aramin kallo nayi duk iya bakin k'ok'ari na kar na kara kallon shi. "So tell me wane irin punishment ya kamace ki?, " Murya ta na rawa nace "Don Allah kayi hak'uri wlh ban sani ba" "Hmm. No you must be punish. You have seen me naked. So kema zaki cire naki kayan" A rude na dago kaina ido waje ina kallon fuskar sa da babu alamun wasa. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Komawa baya yi lazily ya zauna kan kujera ya wani bararraje. Gira ya d'aga da dakakkiyar murya yace "Don't keep me waiting. Strip" ( kar ki barni zaman jira. Cire kayan ki) Ya hayyu ya kayyum. Allah kaga halin da nake ciki wannan wace irin rayuwa ce?. Wai hala ko ya manta haramcin hakan ne? Me yasa yake abu kaman ba musulmi ba?. Wata irin tsawa ya dakamin. "You dare to disobey me?. Nace ki cire kayan ki" A yanzu kam matsanancin kuka na rushe dashi na durkushe cikin ruwan ina k'ara k'ank'ame jiki. Wlh bazan taba cire kayana ba sai dai ya yi duk abunda zaiyi. Mugu azzalumi mara imani. Fasikin banza da wofi. 😃 k'ak'a -k'ak'ara-k'ak'a. Bari na baku suspense ko🤣🤣🤣??. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Announcement. READ PLS👇. Littafin SULTANAAH PAID BOOK NE. 500 kacal🤌. Book 1 is free wanda shi muke yanzu. Idan mun kusa gama free pg zan bada ACCOUNT da number da zaku turo shedar biya. Wannan ne kad'ai Announcing da zaku samu so pls read. Bana so sai na gama free page a dinga tambaya dama paid book ne?. Nevertheless enjoy 😉 Chapter 31/35. A fusace naji ya taso na k'ara k'ank'ame jiki na d'ago dan inga abunda zaiyi. Da wani irin fushi ya miƙo hannu zai kamani sai ga Anita ta fad'o cikin banɗakin kama wadda aka wullo. A karo na farko da ta ceci rayuwata. Duk duniya a yanzu naji babu mace da nake gani da kima sai ita. Chak ya tsaya da abunda yake shirin yi bai juya ya kalleta bai kuma mayar da hannun saba. Nida ke kallon ta na samu ganin matsanancin b'acin ran dake kwance kan fuskarta. Mugun kallon da take jefana dashi bai hanani jin abunda nake jiba na ceton rayuwata da tayi. Da kyar ta iya buɗe baki tayi magana "I'm sorry King Azrah. Queen Aira ke buƙatar ka cikin gaggawa " Sai a lokacin ya ajiye hannun sa ya juya ya watsa mata kallo tayi saurin sunkuyar da kai. Ashe isa da takamar da take a bayan idonsa ne kawai?. Y'ar firgita nayi na k'ara ja baya cikin ruwan ganin ya maida hankalin sa kaina. Wani kallo ya watsomin da bazan iya tantance abunda ya kunsa ba. Rigar sa ya tattare ya kama mad'auran ya d'aure ta kafin ya k'ara jefana da wani last kallo ya juya cikin tafiyar izza yabi ta wata k'ofar ya fice. Ajiyar zuciya na sauke mai k'arfi bayan ficewar sa. K'ok'arin miƙewa na farayi cikin kwamin naji anyi min wata mahaukaciyar fisga an janyo ni da k'arfi an watso ni wajen kwamin. Ban gama jin zafin ba ta kama gashin kaina da iya k'arfin ta ta d'ago fuskarta na saki kara dan rik'o ne tayi min bana wasa ba. Tuni hawaye suka fara gudu kan fuskata. "Don ubanki me ki ke cikin kwamin wankan sa?, me yake shirin faruwa tsakanin ku?" Bata bari na bata amsa ba ta d'auke ni da mari. Saida ta jeramin uku masu zafi ta jani kee ta gashi kaman kayan wanki tayi waje dani ta jefar. Wajen kaina ta k'ara durkusawa ta kara fincikar kaina na d'ago ina kallon ta da fuskata da tayi jege-jege da ruwan hawaye. "Me nace miki?, ke mai taurin kai ko? Banga alama kina son rayuwar kiba .kin d'auka wasa nake ko?, za kici ubanki na k'ara ganin wani abu ya shiga tsakanin ki da Azrah sai kin kwammace mutuwar ki." A zafafe ta saki kan nawa goshi na ya bugu a k'asa. Tsaki naji taja mai k'arfi ta tsartar da yawu gefe ta wuce a fusace wasu daga cikin masu tsaron suka bita. Komawa nayi k'asan na kwanta dan sai naji kaman an d'auko katon dutse an d'oramin zazzab'i da nake ji dazu ya dawo ya rufeni ruf. Motsin Mamee naji da Layher suna k'ok'arin d'aga ni sai sannu sukemin. Had'uwa suka yi suka kamani suka kaini d'aki suka kwantar. Ina Mamee na k'ok'arin d'oramin dan hankici data cika a goshi daga nan kuma wani irin barcin wahala ya kwashe ni ban k'ara sanin abunda ya faru ba. ✿︎✿︎✿︎✿︎ WANI YANKI DAKE CIKIN EGYPT A firgice ta farka daga barcin da take tana salati. Jalila dake kwance kusa da ita ta tashi da saurin tana tambaya "Mama menene?, yauma kin k'ara yin mafarkin ne?" Ajiyar zuciya Maria taja mai k'arfi tana girgiza kai bata bata amsa ba saida ta k'arasa Addu'ar da take. Huzaifa da Baban sa Abu Khamis suka shigo d'akin jin muryar Jalilan. Da kallo Maria ta bisu kafin ta fara magana tana k'ok'arin miƙewa tsaye. "Jikina yana bani Nadine na cikin wani hali tana buƙata ta a kusa da ita." "Mama Don Allah kiyi hak'uri keda baki da lfy. Kinaji d'azu abunda Doc yace ana buƙatar ki samu hutu har tsawon wata biyu kafin ki koma bakin aiki. Abu ya riga da yaje ya sanar da King SAIFULMULK da QUEEN AIRA kuma suma sun amince da neman lafiyar taki. Nadine ba yarinya bace zata kula da kanta inshaAllahu babu abunda zai same ta nida Jalila zamu dinga zuwa a kai a kai muna dubu miki ita" Kai ta girgiza tana kallon Huzaifa "A'a Huzaifa yarinya nan marainiyar Allah tana buƙata ta a kusa da ita. Bata da kowa saini gashi nima nayi nesa da ita. Don Allah ku bari na koma Nadine zata kula dani kuma kunsa hakan" Cikin fushi Abu Khamis ya fara magana "Me yasa ne kinfi fifita yarinya nan sama da yaran ki. Su basu buƙatar ki sai ita kaɗai? Su wad'annan basu ne ki ka haifa a cikin ba. Mu bama buƙatar ki? Mu baki damu da halin da zamu shiga ba sai ita.?" Ajiyar zuciya Maria taja saiga hawaye shar sun biyu kuncin ta. Tunda Khamis ya yi mata magana haka tasan ransa ne a b'ace amma Khamis baya taba banbanta Nadine da yaransu. Shima yana d'aukan te kaman Y'ar da suka haifa a cikin su. Hannu sa ta kamo cikin muryar lallashi ta maijinya tace "Kayi hak'uri Abu Huzaifa. Kar ranka ya b'aci. Bacin ranka babban tashin hankali ne a gareni. Kayi hak'uri zan zauna daku har na samu lfy. A duniya babu wanda nake buƙata sama daku a duniya. Ana Uhibbak ya zauji" Numfashi yaja mai k'arfi ya had'asi gaba d'aya ya rungume ya kuma bi goshin su gaba d'aya ya sumbata. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Bani na farka ba sai wajen asuba shima Mamee ce ta tasheni nasha maganin na gargajiya data jik'a ta kawomim. Da kyar na iya kurban maganin dake da mugun d'aci ga bauri amma kuma ina sha cikin ikon Allah ko minti goma banyi ba cikakke na fara had'a zuba. Miƙewa nayi da taimakon ta naje na kuskure baki na d'auro alwala. A daddafe na jero sallolin dake kaina ina cikin sallan Layher ta dawo dauke da faranti na abinci. Na dauka zanga irin cimar su sai naga abinci ne mai rai da lafiya harda kaji da y'ay'an itatuwa. Zagewa nayi naci na koshi kamin na ture na samu guri na kwanta sai barci. Nayi mamaki da naga tun ranan Anita bata k'ara lekowa inda nake ba. Ban sani ba ko taji bani da lafiya ne ta sarara min na warke ta cigaba daga inda ta tsaya?. To amma shifa wancan azzalumin? Shima bai k'ara aikowa nazo ba duk ina ta jiran fuskantar hukuncin sa dan bazan manta kallon da ya yimin dake nuni da akwai unfinished business tsakanin mu. Alhamdulillahi yau naji kwari sosai dan har na dan fito na kamawa Mamee da Layher wani abu bayan na gama ne na d'an zagaya dan tunda na shigo ban taɓa fita ba. Wani d'an k'aramin Garden na bulle dake can baya . Da alama dai kaman ba'a cika amfani dashi ba duba da yanda komai ya bushe baya samun ruwa fulawoyin duk sun zube. Wani d'an k'aramin d'aki na hango kaman mab'oya ta tsuntsaye. D'akin na shiga duk da rashin kula da yake samu amma guri da aka kashe masa dukiya. Gaban windon d'akin na zauna kan kujera dake gefen sa ina kallon wajen sa. Wati irin iska mai dad'i dake saka nutsuwa ta fara kad'awa a hankali na ciro sark'a ta dake boye a wuyana na sumbace ta ina murmushi kafin na mayar da ita. Haka kawai nake jin nishaɗi da ni kaina bansan me yasa ba. Sannu a hankali na fara rera wak'a da larabci ina d'an jijjga kai gashin kaina dana tufke da hankici iska nata kad'ashi sai ga wata tsuntsuwa mai shegen kyau fara tas da ita ta sauka kan gwiwar k'afata . Murmushi nayi na mik'a hannu a hankali zan tab'a ta komai ya tsayamin chak. Tsuntsuwar data sauka kan k'afata ta tashi da sauri ta koma inda ta fito. Baiyi motsi ba baiyi sallama ba amma naji a jikina. Aura d'in sa daban take a ko ina duk inda yake ya fita daban cikin mutane. K'irjina ya harba da k'arfi na ja doguwar ajiyar zuciya na miƙe tsaye kafin na juyo a hankali na fuskance sa. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 36/40. Tsuntsuwar data sauka kan k'afata ta tashi da sauri ta koma inda ta fito. Baiyi motsi ba baiyi sallama ba amma naji a jikina. Aura d'in sa daban take duk inda yake ya fita daban cikin mutane. K'irjina ya harba da k'arfi na ja doguwar ajiyar zuciya kafin na juyo a hankali na fuskance sa. Wane irin mutum ne shi bakajin motsin sa bare takun sa mutum ne kaman aljanni. Duk da kasancewar nan guri ne dake public amma boyeyyen gurine da zaka iya kad'aicewa cikin sirri yanzu inda yazo ya sameni ina yin wani abu da bai kamata ace ya gani ba fa?. Da kwarin gwiwar dani kaina bansan ina da irin taba na fara magana a zafafe "Can you please not do that? Appear out of no where.? mutum sai dai ya ganka tsaye babu sallama babu komai inda ina chanza kaya ,ko ina yin kashi ko fitsari fa,ko wani abu makamancin hakan fa? " Saida na gama maganan ina maida numfashi na tuna irin muguwar katob'arar dana aikata k'irji na ya cigaba da bugawa kaman zuciya ta zata fito fili. Innalilllahi mena aikata haka?. Shida yake nesa dani ma nasan yana jin bugun zuciyata bare ni da take cikin jikina. Har zuwa lokacin yana tsaye tsakiyar d'akin sanye cikin kananan kaya. Dogon wando Jean's baki da farar riga daya balle mab'ellenta wajen guda hudu , hannun rigar ma ya tattare shi zuwa gwiwar hannun sa sai katuwar bak'ar jacket dake hannun sa mai hular gashi. Tsawon sakanni na cigaba da kallon sa ina jira ya aikata wani abu, dan nasan dole zai aikata. dole zai hukunta ni kaman yanda ya saba hukunta duk wani wanda ya karya doka. Fuskarsa dake very cold babu wani emotion ta firgita duk mai kallon ta. Kwayar idansa kad'ai ta isa tasa mutum sakin fitsari a wando yabi umarni cikin gaggawa. Kirjina ya cigaba dabugawa na had'a hannuwana guri d'aya dan hana kaina rawar jikin da naji kafafuna suna k'ok'arin yi. Gefe na na kalla ina neman hanyar da zan tseratar da rayuwata. Cikin azama na juyo da kallo na kansa. Saidai me inda yake tsaye babu shi yanzu banma k'arasa juyowar ba da kyau naji wuff anyi sama dani kaman iska kafin a had'ani da bango da mugun k'arfi saida bayana ya amsa. Kakari na fara saboda hannun sa daya sa ya shakemin wuya dashi ina kallon sa ya d'aga ni da hannu d'aya har saitin idan sa. Da karfin hali na fara k'ok'arin cirewa hannun sa dake shak'e da wuyana "I'm your king. You dare to speak to me like that?. Wacece ke da zaki gayamin what or what's not to do?, this is my kingdom. Ina da ikon da zanyi duk abunda naga dama dake. You dare to question me?, how dare you?. Who are you?" Sauran maganganun nasa suka yimin nisa saboda numfashi na da naji ya fara barazanar d'aukewa. Tuni idanuwa suka juya bayan kai na. Babu abunda yazo min a rai wannan lokacin sai Mama Maria. Ita kaɗai ce ta ragemin a duniya kaman yanda nima na rage mata. Bak'in ciki zan tafi na barta. Allah kad'ai yasan irin kuncin rayuwar dazata shiga idan na mutu a hannun wannan azzalumin. Kalman shahada na fara yi cikin raina dan na saddakar mutum zanyi. Babu zato ya sake ni na zube kasa ina mugun tari da Jan numfashi mai k'arfi kaman mai Asmah hannu na riƙe da wuya na. Duk da haka na ki bashi damar da yake ganin ya samu nasara a kaina. Da karaji da ihu nayi magana murya ta a shak'e. Na tsane shi, na tsane shi "Mugu Azulumi. Me ka ke so a tare dani?. Ka kyale n..." Maganan ta mak'ale saboda wani barin makauniya daya d'auke ni dashi saida naga wuta. Kunnena ya bada wani shuu naga wani duhu ya kaure kwayar ido na. D'akin gaba d'aya ya amsa k'arar marin. Hannu na mik'a zan dafe kuncina ya kama hannun nawa da k'arfi ya fisgoni na miƙe tsaye kafafuna na rawa. Yanda ya matse hannun nawa kaman zai K'arya yasa na k'ara sakin kara na dago da idona da hawaye ke ambaliya cikin sa na d'ora su kan fuskarsa da manya deep black eyes nashi suka fara jaa tsabar b'acin rai. "Don't you dare raise your voice at me, I'm your KING remember that. I cannot wait to make you my personal slave to boss around." Wani smirk ya saki ya hankad'ani na zube a k'asa . Na shiga uku ni NADINE. maganan Mama Maria a koda yaushe ita ce ' kiyi hankali karki kuskura koda wasa Azrah yasan da zaman ki cikin masarautar nan. Sai gashi banji maganan ta ba na kasance mara sa'a duk haɗuwa ta dashi babu sa'a a cikin ta' Maganan ta dawo dani daga duniyar tunanin dana lula na d'ago da sauri ina kallon sa "Ki fara barci da ido a buɗe miss Nadine. Baki da masaniyar abunda zai same ki ,because this is just the beginning " Yana dasa aya ya juya da tafiyar nan tashi ta izza ya fice daga d'akin. Hannuna daya murd'e na d'ora a ka na rushe da matsanancin kuka ina kiran MAMA MARIA. ✿︎✿︎✿︎✿︎ OMAN. MIDDLE EAST. THE PALACE. KING AL'HUSSAIN CHAMBER. "uhhhm, uhmmm" Sautin dake fita kenan cikin tafkeken d'akin daya karad'e ko ina. Magidancin balaraben mutum ne da a kalla zai haura shekara hamsin da biyar da magidanciyar mace da za tayi talatin da takwas zuwa da tara. Yanda suka yi nisa cikin wata duniyar daban baisa sun kula da zoben shi na gwal dake kan wani k'aramin tebir na zinare ya d'auki wani irin haske kaman fitila. Sai kuma diff ya d'auke a take zoben ya yi bak'ikki'rin kaman gawayi. Baza ka tab'a cewa zoben gwal bane. Can sai d'akin ya kaure da wata irin iska kaman guguwa. Za kayi mamaki idan nace komai a rufe yake rufe. Babu ta inda iska zata shiga. Wannan ne yaja hankalin King Al'hussain da Kuyangar sa ya tashi da sauri yana bin d'akin da kallo kafin idansa ya fad'a kan zoben da ya yi baki kaman bak'in murhu. Wani irin wuntsulawa ya yi ya fad'o daga kan gadon ya d'auko zubon cikin matsanancin mamaki yana duban sa. Meke nan yake gani?. K'afad'ar sa Aina ta dafa ta bayan sa sakaye da zanin gado kan k'irjin ta . Kafin ta kaiga magana ya buga mata tsawa. "Get out" Sanin halin Al'hussain dan haka bata musa ba ta tattare zanin ta cukwukuye a k'irji tayi waje abun ta. Tana fita ya koma kan gadon ya zauna yana duba zoben dake hannun sa zaman keda wuya iskar ta tsaya chak sai ga magana mai amo cikin d'akin. "Your highness" Bai daina kallon zubon ba ya fara magana "Me nake gani ? Mene amsar hakan?" Muryar ta bashi amsa da "Hak'ika abunda ka ke gani ya shugaba gaskiya ne. Wannan shedace dake nuni da cewar akwai jinin Al'HASSAN a doron k'asa, amma mun kasa gano inda Wannan gudan jini yake. Kaman yanda muke baka kariya haka zalika Wannan jinin na Al'HASSAN yana samun kariya daga irin mu. Kuma irin namu masu tsananin k'arfin Mulki . Dalilin da yasa mun kaso gano inda Wannan gudan jini yake bare mu gano mab'oyar sa" Wani irin tsawa Al'hussain ya daka cikin d'akin da k'araji yace "Wannan bashi ne damuwa taba. Taya aka yi jinin Al'HASSAN ke raye bayan an shedamin mutuwar su?. Hakan na nufin akwai wanda suka ha'inceni kenan?." "Tabbas haka ne ya shugaba, babu kuma wanda zamu tuhuma don gaba d'ayan su basu wanda ke raye cikin su. " Miƙewa ya yi cikin zafin rai ya hau safa da marwa tsakiyar d'akin kafin ya tsaya gaban wani katon enlargement hoto da aka rufe da glass. Za kayi matsanancin mamaki idan kaga hoton da suke su biyu. Tsananin kamar da suke babu ta yanda zaka banbance su. Komai nasu iri d'aya ne tun daga kan bak'in gashin su dogon fuskarsu da kuma kwayar idon su dake nan GOLDING BROWN. Hannu ya kai ya dora kan d'aya daga cikin su ya shafa kaman mai jimami can kuma ya dunkule hannu ya kai masa naushi. D'agowa ya yi ya zubawa hoton ido kaman yana magana da hoton. "Brother " ya kira sunan da wani irin disdain. Kaman wanda aka d'urawa kashi a baki. "Babu wani blood naka da zaiyi numfashi a doron k'asan nan matsawar ina raye. Duk abunda zai shiga tsakanin soyayya ta zanga bayan sa. NEELAM is mine. Zan cigaba da ganin bayan duk wanda zai rab'eta matsawar daga tsatson ka ya fito" A fusace ya juya yana kallon tsakar d'akin cikin karaji yace "Ku nemomin su duk inda suke a fad'in duniya " Iskar ta kad'a da k'arfi kafin kuma ta b'ace kaman an d'auke ruwa. Juyawa ya yi saman hoton ya mik'a hannu ya danna wani abu kaman mukunni fitila. Sai ga bangon ya rabe kaman kofa ya kutsa kai ciki. Ashe wani irin boyeyyen d'akine da yaci uwar wanda ya bari. Komai na d'akin da gwal aka yishi. Can saman makeken gadon na hango mace a kwance. Jin motsin yasa ta d'ago a hankali kafin ta juyo gaba d'aya wajen k'ofar. Hasbunallahu wa ni'imal wakil. Me NADINE keyi a nan tambayar da nayiwa kaina kenan?🤣. In banda shekaru da zata nunawa Nadine to da tabbas sai nace rufa ido tayi ta rigani zuwa.🤣 Babu abunda ta bari na Nadine in ka cire kwayar idon ta . Ita wannan kwayar idon ta bak'ace wuluk sab'anin Nadine nata kwayar idon Golding Brown ne kaman na Al'hussain . Tsakiyar d'akin ya tsaya rike da kugu yana kallon ta kaman yanda ta zuba masa. Sai a lokacin na samu damar k'are masa kallo. Duk cewar shekaru sunja amma lifayeyyen mutum ne mai tsananin kyau da kwarjini. Da alama yana kula da kanshi sosai don kyawun jikinsa ko wani saurayin Albarka. Komawa tayi ta kwanta ba tare da tace komai ba. Wani irin murmushi ya saki ya nufo gadon da sauri . Har ya d'aga k'afa zai hau gadon sai kuma ya tsaya kaman wanda ya tuna wani abu. Da sauri ya juya ya shige wata k'ofa . Bai jima ba ya fito d'aure da tawul a kugunsa yana goge lallausan gashin kansa daya sha gyara. Duk abunda yake bata juyo ba sai ma runtse idon ta da tayi. Feshe kanshi ya yi da turarurruka kafin ya afka kan gadon da saurin sa ya jata kaman wani maye ya matse cikin k'irjin sa yana shinshinan wuyatan kafin ya fara lashen wuyan kaman ya samu sweet. Wasu hawaye masu zafi suka biyo kuncin ta ta k'ara k'ank'ame ido. Tanaji yana juyata kaman waina babu alamu dake za tayi wani attempt na kwace kanta da alama kaman abune data saba dashi. Tayi-tayi iya yanda za tayi don kwatar kan nata amma babu nasara shi yasa ta fawwala Allah ya kawo mata agaji. A b'angaren Al'hussain ba'a cewa komai , bai damu da kukan da take ba sai ma zuba uban sumbatu da yake yana furta mata irin matsanancin son da yake mata zai iya yin komai indai a kanta ne. Wannan kalaman nasa suka k'ara sata rushewa da matsanancin kuka. Baibi ta kanta ba ya cigaba da bugunta kaman doki yana sakin layi. ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 41/45. Washegari na fito ina taya Mamee da Layher aiki da k'arfina. Sam ban bari maganganun sa sunyi tasiri a kaina. Shi ai ba Allah bane babu kuma abunda ya isa ya yimin sai abunda Allah ya rubuta zai same ni. Wanki na taya su muka yi sosai har wajen azahar. Muna gamawa muka yi alwala muka yi salla kafin mu nufi tebir d'in abinci. Kaman dai koda yaushe kowa ya d'auki plates nashi zuba cimar da babu sauyi. D'an kwana biyun nan da nayi ina cin abinci mai kyau yasa na manta da wannan cimar. Sai yanzu na tunama to daga ina wancan abincin ke zuwa?. Da kyar na iya d'aukan plate na kai hannu zan debi waken mai tsaron abincin tayi saurin tare ni. Hannu ta d'aga da sauri tace "A'a ke akwai naki abincin da aka ce na baki" Wani irin dad'i ne ya ratsa ni domin nayi tunanin abincin da ake kawomin ne. Sunkuyawa tayi ta d'auko plate k'ark'ashin gurin ta mik'o min. Harna miƙa hannu zan karb'a na tsaya ina kallon ta cike da mamaki. Ni take so naci wannan abincin?. Abincin ne aka barshi ya lalace don waken har wani irin doyi yake shinkafar kuwa da gani tayi yami su kansu ganyan dake kai sun yamushe. Gira ta d'aga tana kallo na ganin ban karb'i abincin ba ta saki murmushi mugunta. "Ki karb'a mana kinja kin tsaya kina kallo .umarni ne daga sama kin san kuma illar karya doka" Muryar Mamee naji da Layher kusa dani. "Haba ke kuwa .Ya zakice wannan abincin za taci?, abinci ya lalace ace shi zataci. Anyi adalci kenan? Ko so ki ke ya yi mata wata illar?" "Au to ni zaku tsaya kunawa kumfar baki?too ni ina ruwana?, nima umarni ne aka bani kuma nake bi don haka itama dole tabi umarni" Cece-kucen nasu ya yi min nisa don nayi zurfi cikin tunanin maganganun sa. Bansan cewa rashin Imanin nasa ya kai haka ba. Gwanda kawai na mutu nima ko na huta da wannan ukubar da nake ciki. A zafafe na juya na warce kwanon daga hannun ta taja mugun tsaki. Ban saurareta ba na wuce Mamee da Layher biye dani suna magana kar naci abincin nan. Duk wanda yace naci abincin nan to bashi da imani mugun mak'iyi nane. Wai danma basuji waye ba don nikam nasan bani da mak'iyi kaman shi. Guri na samu na zauna na tankwashe k'afa. Mamee tayi saurin sunkuyawa zata d'auke kwanon na riƙe da k'arfi na hanata d'auka dole ta hak'ura ta kyale ni amma sai magana sukemin ita da Layher nayiwa Allah kar naci abincin nan. Toshe kunnuwana nayi na rufe ido ina tunani. Badai burinsa yaga ya bak'anta min ba. To zanci abincin kowa ya huta dama kuma bani da kowa da zaiyi rashina sai Mama Maria. Numfashi naja mai k'arfi dan hana kwallan da naji ta cika min ido fitowa. Ido na buɗe na d'ora kan abincin kafin na mik'a hannu da sauri na deb'o abincin. Wani Numfashin na k'ara ja mai k'arfi kafin na d'auke numfashi saboda warin abincin daya dake ni. Da sauri na kai hannu baki bayan na k'ara runtse ido. Sakan d'aya ina k'ok'arin kai abincin baki cikin sakan d'ayan kuma naji wuff an warce abincin kaman iska sai kuma k'arar kwanon nawa da naji kaman anyi jifa dashi gurin gaba d'aya ya amsa. Kafin na kaiga buɗe idon nawa naji muryar sa cikin wani irin b'acin rai da k'araji "Wanene ya bata wannan abincin taci?,kare ce ita ?" Gurin ya d'auki wani irin shiru da azama na buɗe ido na don na tabbatar da abunda naji. Ban sauke idona a ko ina ba sai bayansa daya juyamin. Sanye yake cikin kananan kaya farare ya d'ora wata doguwar rigar sarauta bak'a da aka yiwa ado da gwal ba. K'afar sa sanye cikin wani flat takarmi mai rufe . Ya saki gashin kansa daya zubo har gadon bayan sa sai shek'i yake gashi bak'i sid'ik dashi. Mafarki nake ne?. Na kasa gane inda ya dosa. Tsawa ya k'ara dakawa gurin ya amsa saboda yanda gurin ya yi tsit kaman babu mahaluki a gurin. "Nace waye ya bata wannan abincin?" Jikin wannan mai kula da abincin na rawa ta matso gaban sa daga can nesa ta durkushe a k'asa. Cikin tsananin tashin hankali ta fara bada hak'uri tana neman gafara hawaye na ambaliya kan fuskarta. Wani irin kallo ya watsa mata kafin naji yace "Is she a dog?" Wani irin jijjiga kai tayi kaman zata karya wuya don kukan da take ya hanata magana. "To why zaki bata rotten food taci?" Shiru bata bashi amsa ba sai sheshshek'ar kukan ta dake tashi cikin gurin. Wani irin takawa ya yi gabanta zo kaga yanda ake ja baya a guje. Gabanta ya wani irin durkushe k'afa d'aya a gaba d'aya a baya ya dan gicciya. "D'auko abincin kici ina kallon ki" A guje ta rarrafa tabi abincin tana ci. Loma d'aya tayi kuwa ta fara sharara amai kaman zata amayo hanjin cikin ta. Nayi tunanin aman da tayi zai kyale ta sai naga sab'anin haka. Kallo naga ya watsawa Gaurds nashi dake biye dashi. Cikin azama mutum biyu suka matso suka rirrik'eta d'aya ya tsaya a gabanta suka hau d'ura mata abinci babu imani. Ko numfashi basu bari tana shak'a. Da sun dura mata sunga ta fara yunƙurin amai zasu toshe bakin da hancin sai ta had'iye su k'ara d'ura mata wani. Saida ta cinye abincin nan tass ta suka watsar da ita gefe ko numfashi bata iya ja mai k'arfi. Wannan abunda naga ya yi ya k'ara samin matsanancin tsoron sa. Bama ni kaɗai ba duk wanda yake gurin a mugun tsorace yake ko motsi mai kyau basa iyayi kan kowa na k'asa sai ni kaɗai dana kasa d'auke kaina daga kansa. Miƙewa ya yi daga durkushen da ya yi ya wani juyo inda nake zaune firgici yasa na k'asa motsawa dan ganin komai nake kaman a mafarki. Ido muka had'a na sakan biyu kafin ya juya ya wuce matakansa suka rufa masa baya. What just happened?. A me ya kamata ma d'auki abunda ya yi? Kula?,damuwa? Kai A'a. Dole akwai wani abu dana kasa ganowa a tattare dashi. Idan bashi ne yasa aka bani wannan abincin ba to waye?. Anita, zuciyata ta bani amsa kaman ance na d'aga kaina kuwa na hango ta can baya tsakanin gini babu wanda ya lura da ita saini. Kallon da takemin ya tsorata ni matuƙa nayi saurin kawar da kaina daga kallon ta dan sai nake ji kaman tana ganin hanjin cikina. Ihun Layher ne ya katse shirun da gurin ya d'auka ta fad'o kaina cikin matsanancin farin ciki tana tsalle kaman wadda aka yiwa albishir da aljanna. "Wayyo Allah yau naga King Azrah ido da ido kuma kece sanadin hakan. Ai kuwa babu wani..." Maganan ta ta ta mak'ale sakamakon kwadeta da Mamee tayi "Shashasha kawai sake da Allah taji da abunda ke damunta. Kin fara wannan tunanin naki na gaibu " Baki ta turo ta tashi tana sosa k'eya. Murmushi nayi na mik'e da sauri dan na bar gurin saboda idon Anita da nakeji a kaina kaman kaifin wuk'a. A hanzarce na bar gurin mutane sai bina suke da kallo kaman sunga sabon halitta. A guje na k'arasa shigewa d'akina na banko k'ofar. Jingina nayi jikinta ina maida numfashi. Ganin tunanin bazai fissheni ba na d'auro alwala na tada sallan azahar bayan na idar na zauna ina tulawar karatuna nutsuwa na ratsani ta ko ina. Duk wata damuwar da nake ciki ta ya ye a wannan lokacin babu kowa cikin raina sai anbaton Allah da Manzon sa sai kuma iyayena da Mama Maria. Ban tashi ba saida nayi sallan la'asar sannan na samu guri na kwanta tunda babu abunda zanyi. Har barci ya fara d'auka ta naji bugun k'ofa ta sama-sama ana kuma kiran sunana. Da sauri na tashi jin muryar Layher. Ina buɗe k'ofar ta kutso kai cikin farin ciki d'auke da kaya da muka wanke d'azu. "Can you imagine yau zamu shiga masarauta da kanmu?. Mamee tace muje mu kai kaya aiki ya yi mata yawa. Sauri muje na kagu na taka k'afata cikin ta. " Bata bani damar cewa A'a ba ta jani da sauri muka yi waje. Badan naso ba na bita muka nufi k'ofar shiga Palace sai zuba take tana tsalle kace yarince k'arama da aka bata alawa. Abun nata sai ya bani dariya duk damuwar da jimamin shigar da nake saida na dara. Muna zuwa bakin k'ofar babu wani musu suka buɗe mana muka shiga kodan sun ganmu da kaya ne niki-niki. Wani corrido mukabi mai shegen kyau dake cike da dakaru sai ga wata babbar mace ta bullo daga wata k'ofa . Tana ganinmu ta k'araso da sauri "Yauwa kun kawo kayan ko wanne da inda zaku sashi" Layher ta nuna tana d'aga kayan dake hannun ta ta nuna mata wata k'ofa "Ke nan zaki shiga ki shimfiɗa zanin gadon ke kuma" Ta juyo kaina " muje na nuna miki d'akin da zaki shimfiɗa na hannun ki" Da sauri ta wuce na bita da kallo Layher kuwa a hanzarce ta fad'a d'akin da aka nuna mata. Murmushi nayi na girgiza kai nabi matar da sauri ganin tasha kwana. Bakin wata k'ofa mai kyau na sameta tayi saurin d'agamin hannu nayi sauri. "Yauws ki shiga nan ki shimfiɗa kiyi ki fito" Ko amsa bata jira na bata ba ta wuce ta da sauri kaman walk'iya. Kai na girgiza na tura k'ofar a hankali bakina d'auke da y'ar sallama. Ya illlahi ,rabbil Alamin. Tsananin kyawun d'akin yasa na saki baki da hanci ina kallo. MashaAllah Allahumma arzukuni wanda yafi wannan a Aljanna. Duk irin kyawun d'akin babu abunda yafi daukan hankali na irin lafiyayyen abinci dake shak'e kan wani gold glass tebir. Ajiye kayan nayi na zauna gaban abincin ina tunanin yanda zan deba naci ba tare da an gane ba. Gefe-gefe na dinga bin ina daukan snacks, pie,cakes ,fruits, kaza da sauran su ina ci saida nayi kat na miƙe da sauri don shimfiɗa zanin gadon kan tafkeken gadon dake tsakiyar dakin an kewaye shi da net kaman labube tsakiyar cikin net din kuma wata dankareriyar chandler ce ta gold. Dole a shagala da duniyar kuwa. Hannuna na sule na juyo don fara aiki. Wani irin bugawa k'irjina ya yi na k'ame gurin a tsaye na kasa motsawa. Ido na kyefta na k'ara Kyefta wa don tabbatar da abunda nake gani. Hak'ika kuwa dai-dai na gani ba gamo bane. Tsaye yake a gabana daga shi sai tawol d'aure a kungunsa ruwa nabin jikinsa tun daga gashin kansa har zuwa fatar cikin sa. Kutt na had'iye yawu nabi wani ruwa daya tawo daga wuyansa a hankali yana gangarowa har zuwa bakin tawol d'in sa . Wani yawun na k'ara had'iyewaa ina kallon yanda ruwan ke bin Abs dinshi a mugun hankali suna shigewa cikin tawol nashi dake daure kan kugunsa. Baza kuso kuji matsanancin bugun da k'irjina keyi ba. 'Me ki ke yi haka Nadine kin kafe shi da ido salon yace your a creep and a Pervert?" Da azama na d'aga ido na na mayar kan fuskarsa da babu emotion. Girar nan a had'e ya daga guda d'aya . Ido cikin ido muke kallon juna ya buɗe baki a hankali lebbansa kawai suka yi motsi badan ina kallon saba bazanji mai yace ba "Are you done?, Pervert " Cike da burin kamani da ya yi ina kallon sa na sunkuyar da kaina katsa. Takunsa kawai naji banyi aune ba sai ji nayi kawai ya fisgo ni na fad'o jikinsa babu zato. Wani irin shock ya tsarga jikina a rude na fara k'ok'arin kwacewa ya rike hannu gam yana cewa "Don't you want to see me naked?, I will show you" A firgice nake girgiza masa kai kuka na shirin kwacemin gashin na k'asa bashi hak'uri kaman wadda aka d'aure bakin. Jana ya fara yi ina turjewa ganin ya nufi makeken gadon. Me yake shirin faruwa ne? Ban fargaba sai da naga ya fisgoni da mugun k'arfin ya jefa kan gadon. Laushin gadon baisa na manta tashin hankalin da nake ciki ba na tashi da mugun gudu na wuntsula d'aya b'arin. Tsayawa ya yi riƙe da kugu yana kallona da wani expression dana kasa ganewa wa. Shar naji hawaye sun biyu kuncina. Wace irin rayuwa ce wannan? Raping d'ina yake son yi saboda yaga ni ba komai bace bafe baiwar sa? Tsawan minti biyu muka d'auka a haka nida shi. Yana kallona ina kallonsa hawaye na gudu kan fuskata. Duk irin d'aci da tsanarsa da nake ni bazan bashi damar da zai samu galaba a kaina. Yunkurawa ya yi kaman zai tawo na kawa a guje nayi kofa. Ko tsakiyar d'akin ban jiba naji ya fisgoni yana cewa "Ina ki ke tunanin zuwa?, do you think you will get away with what you have being doing?, you must be punish for your wrongs doing " Jana ya cigaba da yi ina turjewa .ganin da nayi ya kusa cimma galaba a kaina mun kusa bakin gadon naga babu sarki sai Allah na haushi da duka da cizo ina kokawar kwace kaina ga wani irin kuka da nake mai gunji. Yanda kasan dutse nake duka harta zafin a jikina nake jinsa. Bai daina jana ba saida ya kaini bakin gadon ya wani fisgoni gaban sa sai a lokacin na samu damar ganin irin matsanancin b'acin rai dake kwance kan fuskarsa har wasu jijiyoyi ne suka fito raɗau kan goshin sa. "How dare you?, ni ki ke duka harda cizo? ,ni Azrah?" Hannuna dake ciki nasa ya k'ara matsewa kaman zai balla. Tuni wani fitsari ya kawomin ziyara kafafuwana suka fara saboda azaba. Da k'araji ya cigaba da magana "Tambayar ki nake ni ki ke duka?, do you think am nice?" Ya wani lankwasa hannun nawa kashin ya bada kara kass kaman wanda aka balla. Lu na tafi zan fad'i saboda azaba ya riƙe ni. Duk nayi jage-jage da ruwan hawaye da majina ga uwar zuba ta wahala dana had'a. Ganin ina neman sume masa ya wani wulli da hannun nawa ya kama gashin kaina da k'arfi ya d'ago kaina ina fuskantar da. Badan halin da nake ciki ba da tsab zan iya cewa bakin mu saura kiris ne bai had'e ba saboda yanda bakin nashi ke dabda nawa har ina jin hucin numfashin sa da kamshin mint breath nashi. Dishi-dishi na fara gani saboda matsar da ya yiwa gashin nawa kaman zai cire fatar kan gaba d'aya. Saman lebena na fara jin hucin maganan sa "Don't you dare repeat the same mistake. Am not nice. Next ki ka k'ara gigin abu makamancin haka I promise you sai kin kwammace mutuwar ki" Wani irin hankad'ani ya yi na tafi taga-taga zan fad'i Allah ya taimake ni na dafe kujera. Hannu dake uban zugi na tallafe da sauri ina kuka mai cin rai. "Get out of my sight" Yace da k'araji. A guje na juya na fice talleb'e da hannu na da nake tunanin ya karya. Ji kawai nayi naci karo da mutum .saboda k'arfi had'uwar tamu duk muka zube a k'asa. Da sauri na dago dan naga ko waye naga. Wata kyakkyawar yarinyar da bata wuce shekaru gona sha takwa ba. Sanye take da doguwar rigar da akayiwa surfani da gwal. Sai kanta data saka d'an k'aramin crown na DAIMON. Kallo d'aya zaka mata kaga KING AZRAH. A take na gane kanwar sace PRINCESS SOPHIE. Ance ta jima bata k'asar tun tana k'arama tana can UK. Ta dawo kenan?.. Miƙewa nayi cikin azama na wuce ta a guje ina kuka sosai. ✿︎✿︎✿︎✿︎ Da ido Princess Sophie ta bita. Wacece wannan kuma? Me ya same ta ta fito daga d'akin Brother tana kuka haka?. Kai ta girgiza ta shigo d'akin kaman koda yaushe tana nan bubbly baka tab'a ganin bacin ranta. Kullum fuskarta dauke yake da murmushi. Tsakiyar d'akin ta same shi riƙe da kugu ya juyawa k'ofar baya hannun sa d'aya rike da goshin sa. Da sand'a ta k'arasa inda yake tayi tsalle ta d'ane shi tana dariya. Groaning ya yi yace "Baby get off" Kafad'a ta mak'ale kaman yana kallon ta tace "Sai ka gayamin Wacece wannan kyakkyawar da naga ta fito daga d'akin ka yanzu" "No one, get's off" "No one fa kace, amma me yasa na ganka cikin damuwa?" Da sauri ya sauke ta daga jikinsa. Yasan halin Sophie da shegen bin kwakwaf. Banɗakin daya fito ya koma ta bishi da kallo tana wani irin murmushi da ita kaɗai tasan ma'anar sa. ✿︎✿︎✿︎✿︎ A guje na shiga b'angarenmu ina mahaukacin kuka. Da Mamee naci karo tana tambaya ta meya faru ban bi ta kanta ba na kwasa da gudu na shige d'aki na banko k'ofar. Zamewa nayi na jingina jikinta ina kuka sosai. Tsanar sa tayi min wani irin katutu a kahon zuci. Hannuna dake zugi na kalla . Runtse ido nayi na kama gurin da nake tunanin gocewar k'ashi ce na lankwasa yace bas alamun ya koma dai-dai. Kad'an ne ban saki fitsari a zauna ba sai gunji dake fita daga bakina dana datse da hak'orana saboda matsanancin azaba. A yau d'innan zan bar cikin masarautar nan koman dare inshaAllahu . Bazan zauna yaci galaba a kaina ba. Tunda ya kwantanta yimin fyade to tabbas duk lokacin daya samu dama zai iya kwatanta hakan saboda yana da ikon yin hakan. Kamar wadda aka tsikara na tashi da sauri na d'auko jakata na had'a kayana cikin bako na tura k'ark'ashin gado na zauna ina zaman jiran lokaci na aiwatar da kudurina. TO FA. NADINE ZATA CIMMA NASARA KUWA? WANDA BASU BIYA BA SU FARA HANZARIN BIYA DON MUN KUSA IDA BOOK 1 INSHAALLAHU! ♔︎ ♔︎ 𝕊𝕌𝕃𝕋𝔸ℕ𝔸𝔸ℍ 𝒕𝒉𝒆 𝒖𝒏𝒌𝒏𝒐𝒘𝒏 𝒑𝒓𝒊𝒏𝒄𝒆𝒔𝒔 Ashanty love. ☆ ☆𝐈'𝐌 𝐀 𝐒𝐓☆𝐑☆ Chapter 46/50. Har bayan isha ina jin Mamee da Layher nata buga k'ofa ta amma nayi mursisi naki buɗewa dole suka hak'ura suka kyale ni. Tunda nayi sallan ishan na had'a kai da gwiwa ina zaman jiran lokaci. Haka na zauna nayi ta zuba ido da wasi-wasi ta yanda zanyi na fice ba tare da wani ya ganni ba. Kai ita kanta k'ofar da zata fiddani daga cikin masarautar ban sani ba. Tsawon shekaru nayi cikin ta ban taɓa taka k'afata waje ba. Da wannan tunane-tununanen barci ya kwashe ni ban fargaba. A firgice na farka sakamakon mafarki da nayi mai ban mamaki. Cikin mafarkin na ganni cikin wani d'aki mai masifar kyau da akayi shi da gwala-gwala. Kuma abun mamaki kaina nake kallo zaune kan gado kaman yanda itama ke kallo na. Murmushi tayi ta miƙo min hannu kafin naji ta kira sunana 'SULTANAAH'. A firgice na farka ina maida numfashi bakina d'auke da Addu'a. Wane irin mafarki ne wannan kuma?. Gani a zaune gani kuma a tsaye?. Kai na girgiza na yunƙura da sauri na tashi saboda jin yanda masarautar ta d'auki shiru alamun dare ya tsala sosai. Zama na gyara sosai ina tunanin ta inda zan fara. Ajiyar zuciya naja mai k'arfi na yunƙura da sauri na d'auki bakkona na mak'ale shi cikin k'irjina na nufi k'ofar a hankali ina Addu'a. Turus naja na tsaya bak'in k'ofar na kasa buɗewa saboda zuciya ta data ce 'idan ki ka tafi wane hali ki ke tunanin Mama Maria zata shiga?' .wannan tunanin ya kashemin gwiwa matuƙa na kasa motsi. Hak'ika idan na samu nasarar fita daga nan bansan inda zan fad'a ko hannun wanda zan fad'a ba. Duk rashin dad'in nan yafi dana fad'a hannun wani mugun da ban sani ba. Ko ba komai ina ci ,nasa sutura da gurin kwanciya. To idan na fita kuma fa?. Numfashi naja mai k'arfi na juya a sanyaye na koma na zauna ina tunanin Mama Maria. Inama dai ina da halin da zanje naga yanda take. Da na samu nutsuwa ko ya ya ne. K'ofar d'akin nawa naji an tab'a kaman ana laluben sai kuma naji an d'an bugata a hankali. Da sauri na miƙe tsaye ina kallon k'ofar. Waye kuma cikin daren nan? Ban gama tunanin ba aka bugu k'ofar a hankali amma sai gata ta balle . Ga dukkan alamu wanda ya daki k'ofar maji k'arfi ne duk da cewa k'ofar dama ba wata k'ofar kirki bace. Wasu mutane suka shigo cikin bak'aken kaya sun rufe fuska da bak'in abu. A razane na ja baya na buɗe baki zan kwala ihu d'aya daga cikin su ya k'araso cikin hanzari ya toshemin baki da hankici. A take naji numfashi ya d'auke na tafi lu na zube a k'asa. ANONYMOUS POV. Baya suka ja suna kallonta kafin d'aya daga cikin su ya fito waje ya yi fito. Saiga wata mace ta bullo daga mab'oya sanye cikin bak'aken kayan kaman nasu ta rufe fuska da mask. Tana shigowa d'akin kallo d'aya tayiwa Nadine dake yashe a k'asa tace "Ku fito da ita" Wani irin k'amewa suka yi ta juya zata fice daga d'akin har ta kai bak'in k'ofa ta juyo. "Ku had'o da wannan tsummar jakar ta ta" Baki suka had'a wajen cewa "aye captain " Juyawa tayi ta fice ta barsu suna kici-kicin d'auka Nadine. D'aya d'aga cikin su ya sab'ata a kafad'a D'aya kuma ya d'auke ki kayan nata. A biye suka fice da ita kaman yanda suka shigo a b'oye. Wata hanya dake k'arkashin k'asa suka bi mai tsayi sai gasu sun fito daga cikin masarautar ta can k'ofa baya. Dankareriyar motar da yarinyar ke jiransu suka jefa Nadine bayan booth da kayan ta kafin su buɗe motar su shiga baya . Matar dake ciki taja motar da mugun gudu suka bar gurin. NADINE POV. Ruwan sanyin da aka kwaramin shi ya yi sanadin farkawa ta na tashi firgice ina ihu amma baya fita saboda manne bakina da sukayi da salatif. Ban gama farfaɗowa daga sumanmen ruwan da suka shekamin ba naji an d'auke ni da mahaukacin mari da saida naga wuta a take habo ya b'allemin. Gashin kaina aka fincika da mugun k'arfi aka dago kaina. Dishi-dishin da nake gani baisa na gane wake tsugunne gabana ba saida na runtse ido na da k'arfi na buɗe sannan ganin nawa ya fara dawowa daidai. Fatar bakina na furta sunan Anita da babu sauti. Wani murmushi tayi mun na tsananin mugun da samun nasara "Me nace miki idan har ki ka sake yin abu da zaki ja hankalin Azrah kan ki?,yau Azrah saboda ke ya yiwa baiwa dana sata aiki hukunci?. Duk irin abunda nake bai taɓa d'aga kai ya nuna ba dai-dai bane sai a kan ki. Wacece ke? Ke ba kowa bace face baiwa kaman sauran bayi. Aina gaya miki idan hakan ta kasance sai kin kwammace mutuwar ki" Sosai hawaye ke gudu kan fuskata da nake jin b'arin data maren ya kumbura sumtum dan ido na guda d'aya bana gani dashi sosai. Bayan rufe min baki da sukayi harda hannu na da k'afafuwana suka d'aure. Wace irin kiyayya ce wannan? Me yasa ta kasa gane cewar King Azrah babu abunda ya had'ani dashi face tsantsan kiyayya?. Me yasa ta kasa gane kishin da take a kaina duk aikin banza take. Nikam me yasa bani da sa'a a rayuwata ne?. Had'uwa ta da KING AZRAH babu abunda ya jefani ciki sai masifa da tashin hankali. Lokacin da baisan da zamana ba ina rayuwa ta cikin kwanciyar hankali aikin da nake ba komai bane kan masifar da nake had'uwa ta dashi. Duk abunda ya sameni saboda shi ne. Miƙewa tayi tsaye tana murmushi sai a lokacin na samu damar ganin inda nake. Bakin teku mu ke. Yau garin babu haske ki taurari babu bare hasken wata. Ruwan ya yi bak'ikki'rin baka ganin komai yanzun ma saboda y'ar torch da suke haskawa ne yasa naga fuskarta. "Ku yi abunda nace daga bisani ku jetafa cikin tekun" A razane na ke kallonta ina girgiza kai ko zataji tausayi na amma sai ta juya abun bayan ta bini da wani last kallo ta wuce ta barni da wad'annan kartan mazan. Tana b'acewa suka juyo kaina suna wani sinister smile da mummunan fuskar su. Tuni na k'arawa kuka na gunji na fara Jan jiki nan k'asa. Ina jin dariyar su suna bina harda tafawa alamun hakan ya yi musu dad'i. Saida suka bari na wahala duk na kurje ciki da k'afafuwana sannan suka kama k'afata kee suka jani zuwa bakin tekun inda ruwa ke haurowa. Juyo dani sukayi d'aya ya hau kan ruwan cikina irin ya sani tsakiyar sa bawai zama ya yi ba. Kici-kici na fara ina gunjin kuka sosai sai dariya suke ya kawo hannu kan mad'aurin rigata zai warware. Sosai nake girgiza kai ina kuka na fitar hayyaci. Kiris ya rage ya kai hannu wata irin iska mai k'arfi ta kad'a sai wuff ta d'auke shi tayi jifa dashi can gefe. A rude na d'ago ina kallon d'an uwan nasa daya kai masa d'auki shima iskar ta d'auke sa tayi jifa dashi gefe. Da wani irin tsoro da firgici suka tashi da mugun gudu suka bar ni nan kwance ina neman d'auki. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Allah ka kawomin d'auki kaga halin da nake ciki. Ka tseratar da rayuwata daga nan. Wossh naji iskar ta kad'a saman kaina kafin naji sunana saitin kunne na dama "SULTANAAH " A guje na runtse ido ina kuka sosai . Na shiga uku ni NADINE. Flash rayuwata tamin sanda ina yarinya da nayi experiencing irin wannan abu na d'auka ba komai bane yarinta yasa naji kaman hakan ne. "SULTANAAH, kar ki damu ina tare dake a ko da yaushe. Buɗe idon ki bazan cuce ki ba" Maimakon nayi abunda naji sai na k'ara runtse ido ina furta duk Addu'ar data zo bakina. Tabbas yanzu na yarda nayi gamo tun ina yarinya wanda yarinta yasa na kasa gane hakan. Ji nayi kaman anyi sama dani cikin iska kaman hannu yasa ya d'auke ni. Jikina in banda kakkarwa babu abunda yake kafin naji an kwantar dani cikin zunzurutun yashi. Shiru ban k'ara jin wani motsi ba bayan hakan har wajen sakan uku. Jin babu wani motsi kusa dani na fara k'ok'arin buɗe ido. Kan wata kyakkyawar fuska mai tsananin kyau na sauke kwayar ido na dake durkushe kusa dani. Ido na zaro sosai ina k'ok'arin ja da baya. Wannan idon nasan wannan idon. Idon da nagani a bak'ar ranan da bazan tab'a gogewa a rayuwata ba. Ranan da narasa komai nawa na rasa farin ciki na . Ranan data janyo na shiga cikin k'angin rayuwa. Tsananin firgice yasa na sume. ✿︎✿︎✿︎✿︎ THE PALACE. A zafafe ya juyo kan dakarun sa dake tsaye tsakiyar fada sun durkushe kansu a k'asa. "What did you mean she's gone?" Murya na rawa d'aya daga cikin su yace "Mun duba kaf cikin masarautar nan bamu ganta ba. Har can b'angaren da take muka je suka ce rabun su da ita tun ranan da aka d'auko ta daga can. To sai kuma wata take ce mana ko taje wajen Maria ne duk da bata tab'a fita ba. Muka je gidan Maria dan mu duba itama bata can" Da wani irin zafin rai ya sauko daga kan karagar Mulkin sa da yake zaune. Kaman dai koda yaushe fararen kayane a jikinsa riga da wando sai ya dora wata shegiyar alkyabba doguwa da aka kwata da gwals mai madaurai ya had'a madauren gefen kugunsa ya kulle sai k'afar sa dake sanye cikin takarmi sau ciki flat anyi masa ado shima da gwal. Gashin kansa tufke tsakiyar kansa an tufke shi da wani irin band kaman zube dake dauke da crown. Kai tsaye ya damki wuyan Gaurd d'in dake masa bayani. Da grith teeth yace "Tell-me- ta ya aka yi ta iya fita daga nan ba tare da an ganta ba?, kuna me?" Da kyar Gaurd ya iya yin magana saboda shak'a ya yi masa bata wasa ba "Kayi hak'uri King Azrah kuskure aka samu" "Kuskure. Kana so kace min sakacin ku yasa ta gudu?, for the first time in history an samu wata ta iya guduwa daga masarautar nan under mai rolling?" Shiru fadar ta d'auka kace babu dubban mutane a cikin ta sai kakari da Gaurd d'in keyi yaji shak'a barzahu nayi masa sallamad Tun daga kan King SAIFULMULK, Queen Aira, PRINCESS SOPHIE da Kuma ANITA har zuwa the only one childhood best and brother d'in Azrah, General ALEE . Shi kaɗai yake iya tolerating Azrah idan yana cikin irin wannan yanayin. "Azrah" "Azrah" A zafafe ya yi wurgi da Guard d'in ya juyo kan ALEE dake kiransa. Murmushi Alee ya yi ganin ya samu nasara ya saki Gaurd d'in. Yau kaf masarautar babu wanda baisan Kings Azrah na cikin matsanancin bacin rai ba. Da wani irin k'araji Azrah yace yana kallon su "Find her, duk inda take ku nemomin ita fad'in duniyar nan. Kar ku kusura ku dawo babu ita , do not come back without her inba haka ba ku d'auki kan ku a matsayin matattu" Gaba d'aya suka amsa banda Anita dake ji kamn za tayi bingida zuciyar ta zata fashe saboda bak'in ciki. Tabbas zargin ta kan Azrah ya zama gaskiya. Yanzu saboda baiwa yake wannan abu haka. To idan yaji cewar tasa an kashe ta fa?. Kafin nan za tayi duk abunda za tayi ta nuna masa soyayyar ta. Babu wata mace data dace dashi sai ita. Saboda shi ta sadaukar da rayuwarta ta jindaɗi take k'arkashin sa matsayin mai bashi kariya duk saboda so. Bazai yiwu ace wata can k'ask'antacciya ta samu gurbi cikin zuciyarsa saba. " wai Wacece ne wannan baiwar da duk ka tada hankalin mutane haka Son?" Bai bawa mahaifin nashi amsa ba ya juya a fusace yabar fadar Alee ya bishi da sauri. Murmushi Sophie tayi ita dama tasan za'a rina. ✿︎✿︎✿︎✿︎ NIGERIA KANO TA DABO. "Wai wannan baiwar Allah barci take bata san nunzo bane?, ke baiwar Allah, baiwar Allah..." Sama sama nake ji...... Book 1 End. WAI SHIN BAI YI MUKU KAMA DA FARKON PAGE 2 NAMU BA ?🤔😂 . KAMAN YANDA SUKA BUD'E IDO SUKA GANSU K'ASAR EGYPT . GASHI YAU MUN TSINCE MU A 9IGER OO🤣🤣. YA BATUN KINGA AZRAH? ZAI GANO ASALIN ABUNDA YA SAMU NADINE? IDAN YA GANO INDA TAKE ZAI BITA NE KO A'A?WANE MATAKI ZAI D'AUKA?. NADINE ZATA SAN ASALINTA? SHIN ABBU DA INNATI IYAYEN TANE NA ASALI? MENENE ALAK'AR NADINE DA WANNAN MYSTREIOUS ABU DAKE BIBIYAR TA? YA LABARIN SOYAYYAR AZRAH DA NADINE ZATA KASANCE? Duk zamu samu amsoshin wad'annan tambaya idan mun shiga book 2 da yardar Allah. Nan muka kawo k'arshen BOOK 1 NA SULTANAAH. Wanda basu biya ba su hanzarta don kar ayi babu su littafin SULTANAAH Naira 500 ne kacal babu yawa. Ga duk mai son biya zai tuntub'eni a wannan number 👇 08140754777 Wanda suke sun biya zasu turo kuɗin su cikin wannan asusun bankin 👇 3078293374 Aisha Sani Danjuma First Bank A turo shedar biya ta wannan number 08140754777