COPY N COMPILED BY ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS WASAPP 08066360176 FOR MORE 馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰 *SANADIN KIDNAPPING* 馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰 *ZAHRA SURBAJO* *亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲* *Kirkirarren labarine,banyishi dan wani ko wataba,dan haka akiyayi juyamin shi ta kowacce siga,duk wanda yayi na barshi da Allah* *Gani Allah ya nufa nazo muku da wani sabon karatun,littafine daya kunshi abun tausayi,Yaudara,Nishadi,fadakarwa,uwa uba zazzafar soyayya,kubiyoni cikinshi kusha mamaki,dan da yardar ubangiji,babu kamarsa ajerin littattafaina,takowacce siga,comnents dinku shi ze bani kwarin guiwar yinshi akan lokaci,kubiyo yarnufawa domin jin wainar da zaa toya,#nice de dinnan Surbajo for life* *1-2* "Who is he?"ya tambaya cikin kakkausar muryar dake nuna tsananin tashin hankali da bacin ran da yake ciki. jiki na bari,wanda aka tambaya ya matsa kusa dashi ya duka yace. "Sir,He is a contract killer,he can do anything for Morney" "Oh God,how can we find him now"ya fadi yana yamutsa gashin kansa. "Sir the solution is,we have to be very smart first ,dan mutum ne shi me hatsari in aka nuna masa karfin mulki ze iya kashe Sanaya kuma ya gudu batare da anganshi ba" Se a lokacin matar dake zaune a gefe tana ta shirgan kuka,tace cikin kukan. "Alhaji,ni ba komai nakejiba,se Sanaya,nawane milyan dari,kayiwa girman Allah kabasu su sakomin yata,kana ganin Yadda hankalin Munaya yatashi sabida rashin yaruwarta" Shuru yayi yana kallonta,zuwacan yace. "Ba naki bada kudin bane,kawai inaso naji muryarta ne,to kuma sunki bata wayar tai mgn,amma tunda hakane zan basu,hajiya ki kwantar da hankalinki" Dubansa yakai gurin me tsaron lafiyarsa yace cikin kakkausar murya. "After given them the Ransom Morney,you guys i want you to find the person who was behind this kidnapping,if you find him chop him in to tiny pieces,so that no one can recognize him,this is an order"ya fadi cikin kakkausar murya.yana kaiwa nan ya fice Daga falon kamar kububuwa. Da sauri me tsaron lafiyar tashi ya bishi a baya. Ita kuma hajiya mikewa tayi ta nufi dakin Munaya domin ta rarrasheta ta samu taci abinci. *DAJIN KUDARU* Wani babban dajine me manyan dutsuna,da bishiyoyi,ga duhu,kwata kwata dajin beda kyan gani ko a ido ne,dajin na kan hanyar pambegua zuwa Saminaka. Wasu gungun matasa ne zaune cikin wani kogon dutse,sunkai su ashirin dukansu babu alamar imani atattare dasu,inka cire daya daga cikinsu wanda ke zaune can gefe rike da bindiga ya takure, Wata kyakkyawar budurwace zaune a tsakiyarsu sun daureta se kuka takeyi,ko suturar jikinta kawai ka kalla kasan yar manyan masu kudice. Wani bakin mutum ne mummuna rike da kwalbar giya ya nufeta yana tangadi,sharab ya zube agabanta yana dariya,Hannu yakai ya shafo fuskarta yace. "kaga wata jar fulawa,gaskiya ko babanki ya bada kudin bazan sakekiba,sena huta ajikinki"yayi maganar cikin muryar maye, Hannu yasa yana kokarin shafo boobs dinta,ayko a zafafe wannan matashin yataso ya iso gabanshi ya ture yarinyar daga kusa dashi yace cikin bacin rai. "haba oga ya zaka bata mana ayki,bafa daukota mukayi dan haka ba,kawai mun 蓷aukotane dan kudi,to meyasa kakeso kaci mutuncinta?" Dariya ogan yayi sannan yace. "kaga shegen yaro,Wlh wannan fulawar se na mata ban ruwa koda so biyune kan ta bar gurinnan," Gabadaya sauran dariya suka kwashe da ita,shiko matashin shuru yayi yana binsu da ido,yayinda ita kuma yarinyar ta tsananta kukanta jin abun da ogan yace. "Wannan ba daidai bane,kuma wlh hakan bame yiwuwa bane,babu wanda ya isa cikinku ya taba mutuncin wannan yariyar matukar ina numfashi"cewar saurayin cikin kakkausar murya. Wani ne daga cikin sauran yataso da sauri yazo gurin saurayin yace. "Haba Safwan kasha kwayane,ka tunafa taimako ka nema agurina na kawoka gurin oga,dan kasamu kudin biyawa mahaifiyarka kudin operation din da zaa yimata,shine dan rainin wayo har oga na fadi kana fadi wlh kashiga hankalinka"yafadi yana me nunashi da yatsa. Cikin matsanancin fushi,yace. "Don't point your fingers at me or else i will cut them,ina danasanin haduwa dakai hafizu,kar ka kara fushina kasa na saukeshi akanka" Sanin halin safwan na bakar zuciyane yasa hafiz jan bakinshi yayi shuru. Sauran dayake abuge suke ba wanda yay mgn,guri safwan yasamu yana huci. Jan duwawu yarinyar ta dunga yi har tazo kusa da safwan din,Bayanshi taje ta lafe,tana hawaye. Waigowa yayi yana kallonta,sosai tabashi tausayi,hannu yasa yacire mata plasta din da suka rufe mata bakin. Muje zuwa. Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Fatima Abubakar Radda,kina da guri na musamman a zuciyata,ina sonki ina kaunarki,Allah ya dauwamarmin dake cikin farinciki har iya karshen rayuwarki,ya raya mana zuria,Wannan littaffin gaba dayanshi sadaukarwane gareki* *Auta Inna ibrahim kime😝,ina gaisuwa* *3-4* Lumshe ido tayi tana ci gaba da kallonshi hawaye nabin fuskarta. Daure fuska yayi dan shifa beson raini kuma karma wataran su hadu ta tona masa asiri,dan kallon yayi yawa. Hannu yasa yaja rawanin dake kan wuyanshi ya rufefuskarsa,Tsab Sanaya ta fahimci manufarsa,ita ko bakomai yasa take kallonsaba,sedan ganin gashi dan iska amman yasan daraja da mutuncin yamace. Haka suka zauna zugum zugum,har dare yayi,da yake Safwan beyi bacci ba yana gadin sanaya shiyasa da dare yayi yakwanta tunda sauran sun tashi daga baccin buguwar da sukayi. Oga Jagan shine sunan shugaban kungiyartasu,Jagan mutumne mara imani,beda tausayi ko kadan,inyamurine daga Delta state, Ya gagari akamashine sabida tsabar asirin dake tattare dashi,amman babu wani state da jagan beje yayi barna ba,contract killer ne shi na sosai,kuma gwanine gurin yin kidnapping, Haduwarshi da Safwan tasamo asaline daga abokin safwan din Hafiz,wanda ya kasance yaron jagan dinne kuma unguwarsu daya da Safwan. Mahaifin Safwan ya rasu da jimawa,dagashi se kanwarsa kawai iyayensu suka haifa,suna zaune a unguwar tudun wada dake kaduna.to kwatsam se Allah ya dorawa mahaifiyarsu,ciwon cancer ta nono, Sun kashe kudi sosai gameda ciwon har mashin dinshi ya siyar amman suk da haka abun ya faskara. Safwan yayi karatu tundaga primary har zuwa matakin degree akarkashin jagorancin mahaifiyarshi shiyasa yashiga damuwa dan yakasa taimaka mata shima,dan ko ayki bedashi. Alhaji Khabeer Umar, shine Mahaifin Sanaya,wanda ya kasance kuma shine zababben gomnan jihar Kaduna na wannan lokaci. Mutum ne shi da beda tausayin na kasa dashi ko kadan,kanshi kawai yasani da iyalinshi. Cikin ikon Allah se Safwan yasamu Aykin share office din gomna,da taimakon takardunshi,shima yasha wuya kan yasamu, Sede Alhaji Khabeer irin mugayen gomnonin nanne masu kin biyan albashi akan lokaci,wani sain ma har na wata biyar rikewa yake be biyaba. Matsalar da Safwan ya fara fuskanta kenan dan ga mahaifiyarshi kwance a gida ba kudin zuwa koda ganin likitane, Hakannw yasa ya yanke shawarar tuntubar gomnan aduk sanda ya ganshi. Yau monday da wuri gomna ya iso office dinshi,sabida akwai wasu yan kwangila daze sawa hannu, Safwan yana sane yaki yin aykinsa da sauri dan so yake yaga gomnan dan inde yasake yafita kan ya shigo to bazaa barshi yashigo gurinsa ba. Shigowar gomnan keda wuya shida mukarrabansa,Safwan ya nufeshi,da Sauri masu tsaron lafiyarshi suka dakatar dashi. Cikin kuka safwan yadaga murya yana rokon gomna. "Don girman Allah ranka yadade kayi mana albashi haka,wlh mahaifiyatace ke gida zata mutu sabida ciwon cancer gashi babu kudin zuwa Asibiti" Tasowa gomna yayi cike da izza yazo gaban safwan din,yasa hannu ya kifeshi da mari,sannan yace. "in uwarka ta mutu ba damuwata bace,tunda ba tawa uwar bace,da rayuwar uwarka da mutuwarta ni agurina bata da bambanci da ta karen dake gararamba a titi,bazan biyaka albashi ba,baya ga haka ma na sallameka a ayki,wawa dan matsiyata kawai" Safwan akwai zuciya,haka yashiga dambe da masu gadin gomnan,har yasamu ya isa gareshi,janshi yayi da karfi ta yadda suka hada goshi,a haka safwan yace. "Kare irinka,be isa ya ambaci sunan mahaifiyataba,dan haka ko tanzu daka ambata nasan da taka kake ba tawa ba,kuma albashina dole ka biya ni dan bana yiwa karnuka ayki abanza"yana kaiwa nan yasakeshi taga taga gomna yayi kamar ze fadi daga bisani ya tsaya kam. Tsananin mamakin karfin hali da jarumtar safwan ce tasa gomna kasa bada umarnin a kamashi,koda securities suka bi bayanshi zasu kama,da Sauri gomnan ya tsaida su. "Ku barshi,zamu gana watarana"cewar gomna yana murmushin mugunta,shide safwan ko kallonsu beyiba,yasa kai yafice daga office din zuciyarshi na tafasa. Ba komai yasa gomna yace akyale safwan ba,sedan tausayinshi da yaji,dan yasan bakin talaucine ya rufe masa ido har yaci mutuncinsa haka, Bayan sati guda da faruwar lamarin,jikin mahaifiyarshi ya tsananta dan zuwa yanzu har tsutsotsi ke fita a nonon. Haka zasu sata agaba shida kanwarshi rahama suna kuka,ga wani arnen wari dake fita ajikinta. Haka suke kula da ita,kwatsam se Safwan ya hadu da hafixu,inda ya karanta masa damuwarsa ya bukaci daya ranta masa kudin daze kai ummanshi Asibiti. "karka damu safwan,munada kungiya me kawo mana kudi shafshaf,in kanaso zan kaika gurin oganmu ya taimaka maka,sede da sharadi baa fita acikin kungiyar dan in kace zaka fita kasheka oga zesa ayi" Da yake soyayyar mahaifiyarshi ta rufe masa ido,kai tsaye ya amince da sharadin,ayko hafizu yasadashi da ogansu jagan. Hannu bibbiyu suka karbeshi,dan lokacin suna gab da fita wani opretion ne,dubu dari oga jagan yaba safwan,akan yaje yakai ummansa asibitin yazo su fita operation din. Dan dadi har kuka safwan yayi haka yazo yadauki,Umman da Rahama zuwa asibitin Barau Dikko dake unguwar rimi kaduna. Be baro gurinba seda yaga ummansa ta samu kulawar data dace,dan likitocin sun shaida masa sede yakaita shika dake zaria,su zasu kula da ira na iya yaune kawai. Bayan Safwan ya koma gurinsu oga jafan,da.misalin karfe hudu na yamma,suka fita operation din, Airport suka nufa,domin Ranar ne yaran me girma gomna,twins munayada sanaya ke dawowa daga kasar England . Sunyi shiri na musamman,dan haka tawagar masu dauko yaran na zuwa,sukuma suka bude musu wuta,kan wani lokaci sega gawarwakin yansanda akasa. Da gudu twins din suka fice daga mota,kasancewar dare yafarayi dan magribane lokacin kuma gurin ba haske. Sanaya gudu take ko waige batayi,seji tayi taci karo da mutum,Safwan ne tsaye agurin,dan duk kashe kashen da akayi babu shi agurin,oga jafanne yace yatsaya agurin in wani yazo guduwa ya kamashi, Sanaya na ganin safwan da gudu tayi bayanshi tana kuka tana fadin. "Don Allah kataimakeni zasu kasheni" Murmushi yayi gamida jan hannunta ba musu tabishi,wata mota yasata aciki sannan shima yashiga yatada motar ta fice da gudu daga airport din,yana fita dakarun sojoji na isowa, Su jagan dakyar suka sha,sojojin basu rutsasu ba,jin jiniya na tashine yasa munaya fitowa daga inda ta boye,tana neman sanaya amman bata ganta ba. Shiko safwan ko motar ɗayasa sanaya ciki ta oga jagan ce shi yabashi for emmergency,danhaka daita tay amfani gurin guduwa da sanaya. Ganin bebi hanyar gida da ita bane yasa tafara ihu,ayko parking yayi kamin yakai marabar jos ya fita yasa igiya ya daureta ya manna mata plasta abaki. Da yake kan akai maraba akwai checking point na sojojine yasa yadanna kan motar ta cikin daji,yadunga tafiya cikin duhun dajin har yafado kan titin daze kaika pambegua,tafiya yake aguje sosai dan haka be jimaba yazo pambeguan dauke kan motar yayi yafara bin daji dan can gaba akwai checking point,da taimakon wayar da sukeyi dasu oga jagan ya isa mahadar tasu lafiya dansu tuni sun jima da isa. Ba karamin jin dadi sukayiba sanda suka ganshi da sanaya,dan da sun dauka sunyi fitar banza ne. Acan kaduna ko tuni ankai munaya gida,ansa matakan tsaro akoina dan neman sanaya,hankalin gomna in yayi dubu ya tashi dana iyalinshi,sabida ba abinda yakeso arayuwarshi kamar sanaya itace farincikinshi. A wannan yanayinne yasamu kira daga oga jagan akan cewa yarsa na hannunsu se ya bada ransom morney milyan dari. Wannan shine abinda ya faru abaya,labarin ze dora muje zuwa surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Autah Inna ibrahim kime🤣😜wlh dadin kiran sunanki nakeyi me babies face😝* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *5-6* Safwan baccinshi yake cikin kwanciyar hankali. Sanaya lallabowa tayi ta matso inda yake kwance,ta dora kanta agadon bayanshi,tana feeling much comfortable in yana kusa da ita duk wani tsoro na kaucewa,dan ita fyade ne bataso ta gwammace ta mutu da hakan ta faru da ita,to ta fahimci baze bari ayi mata ba. tana kwantar da kanta wani bacci yayi awon gaba da ita. Oga jagan duk abinda ke faruwa akan idonshine,ganin tayi baccine yasa ya mike yanufi inda take, daukarta yayi cak,se wani lungu acikin kogon dutsen,ya ajiyeta,yana ajiyeta ta farka,zatayi kuka ya rufe mata baki da plasta. Nanfa yafara rabata da kayanta,da yake sanaya akwai manyan boobs to sune sukafi daukar hankalin oga jagan,jikinshi har bari yakai gurin son fito dasu daga cikin bra din jikinta. Sanaya naji na gani bata da ikon hanashi domin adaure take, Bayyanar boobs dinta awajene yasake dagawa jagan hankali,da sauri ya nutsa fuskarshi a tsakankaninsu,wata sassanyar ajiyar zuciya yasaki sanda yaji laushinsu. Safwan nacan kwance kamar wanda aka tsikara ya farka,,waige waige yafara yana neman sanaya. Ganin bata agurinne yasa yamike zumbur ya dauki bindigarshi yafara zagaye cikin kogon dutsen,duk sauran matasan se dariya suke masa. Yana cikin zagaye gurinne ya iso inda oga jagan yake shida sanaya.zuwa lokacin har ya fara cire kayan jikinshi. Itako boobs dinta sunyi jajawur sabida matsasu da oga jagan yadunga yi,se zafi suke mata. Idon safwan na sauka kan boobs dinta da suri ya runtse ido,ya furta. "Noooooooooooooooooo¡!!!!!!!!!!!"wanda sabida karajinshi har kogon dutsen seda ya dauka duka. Da gudu ya nufi oga jagan sede kan yakarasa sauran matasan sun taso sun rikeshi. Duk yadda yaso subarshi sun hana shi,gashi yana kallon yadda boobs din sanaya keshan tsotsoagurin oga jagan yana imagining ace Kanwarsace Rahama awannan yanayin yazeyi. Wani kukan kura yayi ya kwace daga rukon da suka masa,nanfa yashiga kaimusu duka ta koina, Fada ake bana wasaba,safwan dukansu yake suna ramawa amman dayake azuciye yake ko ji baya yi. kan wani lokaci tuni,ya musu likis,wani irin tsalle yayi wanda har se da yayi tambul asama sannan ya dira akan gadon oga jagan. Hannu yasa ya kamo hannayen dake matsa boobs di ya banƙaresu baya jikake kas,sun karye🤣 Dagashi yayi ya mikar ashi ya rike kanshi yadunga bugawa ajikin dutsen seda ya tabbatar da babu wani sauran hakori da yayi saura abakin sannan ya kyaleshi. Hannu yasa ya kinkimi sanaya yasata akan kafadarshi,ya dauki bindigarshi,yayi nufin ficewa daga kogon da ita oga jaganne wanda yake cikin mawuyacin hali dakyar ya iya furta. "Don't let him go free"Ayko nanfa sauran yaran suka mike suka dauki bindigoginsu,suka mara masa baya. Gudu yake da Sanaya akafadarshi,yayinda yaran oga jagan keta harbi da bindiga,tsananin karar harbinne ya haddasawa sanaya sumewa, hak yake gudu da ita,hannunshi daya yana harbi dashi, Duk wanda yasan dajin kudaru yasan dajine da har yanzu akwai ragowar mugayennamun daji dasukai saura aciki. Safwan bedamu da kallon gabanshiba bayanshi kawai yake kallo yana harbi. cikin saa wani daga cikin yaran oga jagan yasameshi da harsashi akafa, Dagashi har sanayan wanwar sukai akasa,azabar da yaji bazata misaltuba,kwance yake rike da kafarshi,daidai lokacin akayi wata walkiya. Idonshine ya hango masa sanaya kwance kasan wata shirgegiyar kasa,ta fasa kai tana shirin yin kalaci da sanaya,wacce alokacin tafarka daga suman datayi ganin macijitarne yasa tasake komawa suman,a raina nace tokode irin abunnan na kanawa tayi damacan wato likimo🤣😝. Wayyo safwa,waigawa yayi ya hango yaran oga jagan sunkusa tarad dasu,wanda yasan in suka zo kasheshi zasuyi su tafi da sanaya,suyi abunda suka ga dama da ita Tofa,ga sanaya kasan macijiya kasa,ga harbi a kafar safwan ga yaran jagan sunkusa cinmusu,koya zata kasance? Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Ruqayya Hassan gaskiya kinsani nishadi,narasa bakin gode miki,Allah yasakamiki da alkhairi yasa kifi haka,Allah ya bani ikon kwatanta abunda kikamin,ngd ngd ngd,ilove you so much more my sis,just keep burning the light,the sky is your limit,#me laya kiyayi me zamani♥♥♥♥♥* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *7-8* Waige waige kawai yakeyi yama rasa abunyi,hannunshine ya sauka kan wani dutse kato,ay beyi kasa aguiwaba ya dauki dutsen Be saukeshiba se akan macijiyar,take kan macijiyar ya fashe,jini ya zuba jikin sanaya,wanda yasanya ta farfado. Ganin gawar macijiyar ajikintane yas ta kwalla wata kara wacce ta sanya yaran oga jagan fahimtar inda su sanayan suke, Ganin sun nufo gurinne yasanya Safwan yamike da kafa daya yana dingisa dayar ya dauki sanaya wacce gaba daya afirgice take,yaci gaba da gudu da ita. Tuni yaran jagan suka hange shi,dan haka mara musu baya sukayi, Haka sukai ta gudu cikin dajin Allah,har suka iso bakin wani kogon dutsen,ayko safwan wuf yayi ya fada ciki,batare da tunanin koma meye aciki ba. Suna shiga ya sauke sanaya suka labe ajikin dutsen,yaran jaganne suka karaso gurin,daidai bakin kofar shiga kogon suka tsaya,suna nemansu. Sanaya jin wani tayi me sanyi yana bi mata kafa,ayko azabure tafara diddire kafar,gamida daka wani uban tsalle ta makale kafadar safwan ta kankameshi jikinta na bari. Hannu yasa ya gyara mata zama ajikinshi gamida tallafe mazaunanta gudun karta fado🙊. Sanaya sake shigewa jikinshi tayi dan sanyin dake gurin yayi yawa harma yafi na waje,hakanne yasa ta dora kanta akan kafadarshi gamida sakala hannunta awuyanshi. Hakanne yabawa kirjinsu damar haduwa irinta no gab,Safwan jin da yayi abu me laushi na taba kirjinshine yasa yakai hannu danjin komeye,an be zaci boobs din Sanaya bane. Yana kai hannu da sauri yasaki,sabida fahimtar ko meye da yayi,itako sarkin tsoro batamasan yayiba,addua kawai take akan Allah yafiddasu. Yaran jagan sunkusa awa guda agurin,sannan suka wuce,jin motsin wucewarsune yasa Safwan fitowa daga ramin koramar da ya shiga batare da yasani ba,wanda da yayi gaba ba makawa cikin ruwa zasu fada.shiyasa sanyi yayi yawa agurin. Cikin sanda yake tafiya,dauke da sarkin tsoro dake kankame ajikinshi,Sannu a hankali yake tafiya zuwa lokacin jiri yafara daukarsa sabida raunin kafarsa,jinine kawai ke fita,har yafara barin cikin duhuwar dajin,yafara zuwa gurin gonaki. wani ginin daki guda daya ya gani a cikin wata gona wadda yasan na masu gonarne suka gina sabida in sunzo aykin gonar. mukulli yagani ajikin kofar sanda ya isa bakin dakin,so yayi yasauke sanaya dan ya samu damar balla mukullin amman inna kankamo🤣 fafur taki sauka,karshema kuka tasa tana fadin. "wlh bazan sauka ba,nide bazan saukaba" Harda kara makalkalewa,kyaleta yayi ahaka yayi iya dabararsa ya bude kofar,suka shige. maida kofar yayi ya kulle,sannan yafara laluben abinda ke cikin dakin. Wayarshice tai kara,wanda dagashi har sanaya seda suka firgita,wanda shi sam bema dauka wayar n jikinshi ba,dakyar yaciro wayar,yaga rahama ce ke kira. Dakyar ya dauka,yana dauka yaji ta rushe da kuka tana fadin. "Yaya safwan kazo umma zata mutu,wayyo Allah na shifa uku don Allah kazo" Tashin hankali baasa maka rana,zaman dabaro safwan yayi,wasu hawaye na biyo fuskarsa,cikin kuka yace. "Rahama,bazan iya zuwa ba wlh yanzu haka harbine na bindiga a kafata,gashi ina guri me hatsarin gaske,don Allah kisawa umma wayar akunnanta nai mgn da ita bazata mutu ba da yardar Allah" Umma dake cikin mawuyacin hali,dama tunda taji Rahama ta ambaci sunanshi take mata alama data bata wayar. Samata wayar tayi akunne tana kuka, Dakyar umman ta furta "Safwanullah kana ina?" cikin kuka Safwan yafara yimata bayani,br boye mata komaiba ya sanar da ita duk abinda ya aykata. Cike da tausayin halin da ya jefa kanshi sabida soyayyarta tace masa. "Karka damu safwan,ni Allah yayi ba rayayyibace,yar mutane daka dauko lfy kayi kokarin sadata da iyayanta lfy,karka bari acutar musu da ya,na yafe maka dana,Allah yayi maka albarka,ka kula da rahama,safwan daka aykata mummunan ayki dan sama muku abinci gwanda kabari yunwa ta kasheku,kamin alkawarin maida yarinyar nan gida"ta karasa mgn cikin haki daya taso mata. Tunda ta fara mgn safwan ke kuka sanaya na tayashi dan tanajin duk abinda umman ke fadi. "Umma naimiki alkawarin maidata gida cikin koshin lfy,karki mutu umma da safe zanzi nakaiki asibitin shikan don Allah umna ki rayu damu karki tafi ki barmu" "Allah yay muku albarka"itacr kalmar data fito abakin umman,safwan najin sanda take kalmar shahada,zuwacan yaji sautin ihun rahama na kiran doctor ko baa fada masa ba yasan umma ta amsa kiran Allah. Sharaf ya zube ajikin sanaya dake nanike da jikinshi wacce inbanda kukan tausayinshi babu abinda takeyi,koda ta tabashi babu numfashi atattare dashi. Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Aisha Yar'aduwa natayaki murnar kammala book dinki me suna matar babana,Allah yakara basira sis naji dadin sadaukarmin dashi da kikayi ba kadanba,Allah yasaka da alkhairi yasa kifi haka,banji dadin cewa kindena book da kikayiba,pls sisto aduba kokenmu aci gaba😭😭😭* *marubuciyar kawalli surbajo da marubuciyar beautiful zahra,naga books dinku ngd Allah yasaka da alkhairi yasa zumuncinmu ya dore,ngd sosai,ana mugun tare* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *9-10* Ihu sanaya tayi tashiga jijjigashi,amman ko motsi bayayi,wayarshi ta dauka ta kunna fitila ta haska dakin ba ruwa babu alamarsa. Kuka take kashirban harda majina,tsoronta kar ya mutu ya barta,tunanine ya fado mata na cewa itafa doctor ce,hakanne yasa da sauri ta duka ta hade bakinsu guri guda ta shiga hura masa iska. Sannu a hankali iskar ke shiga huhunsa ba jimawa yafara numfashi sama sama har numfashin ya daidaita,sam sanaya bata lura ya fara numfashi fa,ta dukufa gurin hura masa iska,jin taki dainawane yasa shima data hura ya huro mata,saurarawa tayi taji daga ina aka huro mata,sake yi yayi danta kauda tantama, Dagowa tayi tana kallonshi gamida gyara gashin kanta me uban yawan daya musu rumfa sanda ta dukar da kanta. Da sauri ta mike cike dajin kunya,shiko ya kasa koda mikewar halin rasuwar mahaifiyarshi shi ke damunsa,ga ciwon kafarsa dake damunsa. Yana kwance inbanda hawaye ba abinda yakeyi,tabbas rayuwarsu nacikin wani hali na rashin ummansu, Sanaya shuru tayi itama tana tayashi kukan,idonta ne ya sauka kan kirjinta,wata wawiyar kara ta saki gamida sa hannu ta kare. Duk bidirin da akeyi se yanzu ta lura da babu riga ajikinta,gaba daya kunyace ta kamata,ashe haka ya daukota daga gurin oga jagan batare daya dauko mata rigar taba. Safwan kallo ya bita dashi gamida mikewa dakyar ya zare rigar jikinshi ya mika mata. Da sauri ta amsa ta saka,har lokacin bata dena jin kunyarba. Haka suka kwana dashi da ita adakin,a takure,yayinda ita tasha baccinta,shiko yana zaune kafa tasashi agaba Da garin Allah ya wayene,sanaya ta lura da wukake masu kama da aska dake rataye ajikin bangon dakin,da sauri ta saukosu,dukda bata da garanti gameda tsabtarsu amman yazama dole ta taimaka masa dan yasamu sassauci. Alokacin bacci ya fara daukarshi,matsawa tayi kusa dashi ta kafa kafar dake ciwo,tashiga kokarin ciro masa bulƙet din da aka harbeshi, Azabar data ratsashine yasashi yatashi afirgice,da sauri ta dago tana dubanshi,fahintar abunda takeyi yasa ya koma ya kwanta ya runtse idonshi ita kuma taci gaba. Wayyo azaba haka safwan ya daure,ita sanayan dake cirowan itace ke kukan,ahaka tasamu ta ciro masa da kyar. jini ne yafara zubowa da sauri ta yagi kasan rigar data saka,ta daure masa kafar, wani zazzafan zazzabine ya rufeshi,rasa yadda sanaya zatayi tayi,gashi tana tsoron bude kofar,karta bude taci karo da wani abun. Dataga de ba sarki se Allah dole ta bude,safiyace itatuwa se kadawa sukeyi, ahankali tasa kanta waje. Ganin ba kowane yasa ta fice daga dakin gamida jawo kofar. ta fara tafiya kenan taji sautin tahowar mota,da sauri ta boye bayan wata bishiya, Bin mitar tayi da kallo se taga tayi parking,ba jimawa se taga na ciki sun fito sun bude bayan boot sun fito da ghana must go guda biyu sun ajiye agurin,gamida kiran waya dataga dayan yayi. "Hello,ga kudin fansar sanayan nan ankawo,dan haka kuyi hanzarin sakota don Allah muna bakin titi muna jiranta"yana kaiwa nan ya kashe wayar,suka juya suka nufi mota. Da gudu sanaya ta fito zata bisu,se kuma ta tuno da Safwan,tsayawa tayi chak,tana kallonsu har suka bace. Jikinta na bari ta isa gurin kudin,da kyar ta iya daukar jakunkunan,ta ruga zuwa dakin da safwan yake. A firgice ta shiga dakin ta maida kofar ta rufe se zare ido,take. Dagowa yayi da kyar yana kallonta,gamida mikewa da kyar. A rude tai masa bayanin komai,shuru kawai yayi yana tunanin abinda ya hanata binsu bayan tasan ita suke nema. Haka suka wuni gurin bame cewa kowa komai,har yamma tayi hankalin safwan nagurin gawar ummanshi,da rahama,ga yunwa da sukeji shida sanaya. wani buhu yagani cikin dakin da sauri yasata ta bude srga dankalin hausa aciki. ay daga shi har ita haka suka haushi da ci ba kakkautawa. Suna tsaka Da cinr suka fara jiyo karar harbi gamida karar helikwafta a sama a firgice sanaya ke kallon safwan wanda shi ko ajikinshi. Tawagar gomnane dama yacr in jamian tsaro sukaji shuru baa sakotaba subude wuta, Kamin wani lokaci tuni ankamo yaran jagan dashi kanshi,koda aka nemi sanaya,cewa sukai safwan yamata fyade kuma ya gudu da ita. Afkawa jamian tsaron sukayi cikin dajin nemansu kokadan basu kawo suna cikin wancan dakin da suke hangowa ba Acan daki ko fada akeyi tsakanin sanaya da safwan. "kifita kibi yan uwanki"cewar safwan cikin fushi. "don Allah ka kyaleni,wlg bazan ita tafiya na barka ba,kana bukatar taimako,pls kabarni tare dakai" "bana bukatar taimakon ki ki fice kawai nace" Kuka tasa masa tana rokonsa yabarta amman fafur yaki yarda,daga karshema wurgata waje yayi da kudin uban nata ya kulle kofar. Komawa yayi ya kwanta yana cigaba da kukan rashin ummansa,hadarine ya taso me karfi iska se kadawa takeyi,ba jimawa ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya. Wundon dakin a bude yake dan haka feshin ruwa na shigowa,yayi iyayinsa ya kulleshi tacikin dakin avbun ya gagar dan haka bude kofar yayi da nufin kulle wundon.Sanaya yagani t saye cikin ruwa ya mata shegen duka se kuka takeyi. Sosai ta bashi mamaki,kulle wundon yayi sannan yasa hannu ta janyota zuwa cikin dakin ita da kudin. muje zuwa. Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *My Humy luv ga gaisuwarki,ina sonki irin sosai dinnan,ina yinki sisto Allah yabarmin ke kijima ki karko,Allah yakara basira Surbajonkice for life♥♥♥pls kimana typing🙏😝😝in yaso ni nayi me wuyar wato posting😜* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *11-12* Sumi sumi ta shige dakin se digar ruwa takeyi,guri ta samu ta tsuguna. Haka kawai ran safwan yadunga masa daci sabida dukanta da ruwan yayi. "Baki da hankaline zaki tsaya awaje ruwa na dukanki?"ya tambaya rai abace. Jikinta har bari yake ta duka agabansa tace. "Don Allah kayi hakuri,kaine ka koreni ni kuma bazan iya tafiya na barka ba,kuma alkawari kayiwa umma cewa har gida zaka maidani lfy,"tayi mgnr hawaye nabin fuskarta. Shuru yayi yana kallonta,wato ya fahimci yarinyar irin tabani kaga sarkinnance,wato shagwababbiya ta ajin farko,dan ya lura kuka ba wani abu bane me wuya agurinta. Maganartace ta dawo dashi daga tunanin da ya tafi. "In har ka yarda bazan cutar dakai ba kabani aron wayarka inyi kiradon Allah" Ba tare dayayidogon tunani ba yamiko mata wayar. jikinta na bari,ta amsa tasaka number munaya,ta jima tana ringing kamin munaya ta dauka. "karki kira sunana ko kiyi ihun murna,sanaya ce"cewar sanaya. Zumbur munaya tamike zaune,ji take kamar amafarki,sanaya na kiranta,cikin kuka da zakuwa tace. "My Sweetheart kina inane don Allah?" "Ba shi zaki tambaya ba,yanzude nan da awa biyu inason ganinki a cikin dajin kudaru,kitahomin da abinci da kayan sawa both maza da mata,sannan kitahomin da first aid box da drip da da da da😊" "are you mad sanaya how can i do so,ni na kawo kaina halaka,,pls tell me ina kike ina kuma gayen da ya miki fyaden?" Sosai batun yaba Sanaya mamaki,amman setace mata. "in har da gaske kina sona,kizo kisameni kamar yadda nace,inkuma kika bari wani yasan munyi mgn nidake babu yafiya har abada"kit ta kashe wayar tana share hawaye. Munaya tuntsurowa tayi daga kan gado ba shiri,da yake doguwar rigace ajikinta takalmi kawai ta zira,ta dauki key din motarta,cikin sanda ta nufi dakin sanaya,ta dauki kayanta tasa ajaka,sannan ta fito ta nufi part din yan ayki,abinci tasa suka hada mata me rai da lfy,a kuloli. Daki ta koma ta dauko first aid box din sannan ta nufi parking space,bude motar tayi ta zuba kayan aciki sannan ta shiga ta tada. Masu tsaron lafiyartane suka nufoto da gudu,da sauri ta dakatar dasu da cewa. "gidan naigbours dinmu zan shiga,no need ku biyoni"tana kaiwa nan taja ta fice a gidan da mahaukacin gudu. Lekawa sukayi sukaga tadau wata hanyar dabam,da gudu suka kira dad dinta suka sanar dashi, Ayko gurin sakkowa daga stairs har gangarowa yayi sabida tsabar kidima,tsawa yadunga dakawa masu tsarin gidan,inda yabasu umarnin binta abaya. Munaya gudu take bana wasa ba,dan tuni ta tsaya awani pharmacy tasai sauran kayan,gamuda kayan mazan da sanaya ta bukata. Tafiyar awa daya da rabice ta sadata da dajin,da yake yamma ce yasa tashiga cike dajin tsoro. Wayar da sanaya ta kiratata shiga kira,nanfa sukaita mata kwatance,tasha wuya kan ta gano wannan daki. parking tayi ta fito taje ta fara kwankwasa kofar gamida kiran sunan sanaya. Da gudu sanaya ta bude kofar ta rungumeta tana kuka. cikin dakin suka shiga inda safwan ke kwance kafa ta kumbura tayi suntum😭 Cike da mamaki munaya ke kallonsu. "sanaya waye shi,me kukeyi anan?" "Shine wanda ya ceceni daga halaka,nan shine inda muka fake"daga haka ta kwashe komai daya faru ta shaida mata. Sosai munaya take kuka na tausayin safwan,shide kallonsu kawai yakw,yana mamakin tsananin kamanninsu. Abincin sanaya ta fito dashi,ta taimakawa safwan yatashi,ta shiga bashi abaki,tana hawaye,cin abincin yake ayunwace,har seda ya koshi. Munaya dakw gefe tuni ta fara kukan tausayin yaruwartata,dan duba daya taimata ta gane ta fada tarkon son wanda bedace tasoba. seda yaci ya koshi,sannan suka hadu su biyu sukai masa dressing kafar tasa yasha azaba,dan har ihu seda yayi,munaya ce karfin aykin dan sanaya inbanda kuka ba abinda takeyi. Allurar bacci munaya tai masa,sannan ta daura masa drip,tuni ya bingire agurin yana bacci. da sauri munaya ta kama hannun sanaya tace "to taso mu tafi gida,sanaya nan gurin bedace dame matsayi irin naki ba" "wlh sis bazan fito adajinnanba hat se ranar da hero yaji sauki,da kanshi ze kawoni gida dan haka kitafi kawai ngd da taimakonsa da kikayi" Duk yadda munaya taso tafiya da sanaya dole ta hakura ta tafi ta barsu, A hanya taci karo da wanda aka turo nemanta dan haka rankayawa sukai zuwa gida tare. Muje zuwa surbajo for life. [08:57, 1/6/2018] ‪+234 813 454 0705‬: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Where are you my other half🗣Hauwau Muhammad Danjuma N,B,S,?here is your page,thanks for the visit,i hope you arrived home safely,Surbajo love you so much,always remember this my sweetheart,Don"t cry in Love coz 4 whom u r crying does not deserve ur tears & the person who deserves it will never let u cry!!!ana uhibbuki hubban shadidan,my suruka(Amaryar yusuf)♥♥♥♥♥♥♥♥♥🤝* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *13-14* Haka sanaya taci gaba da kulawa da safwan,tare da taimakon munaya dake kawo mata ziyara a boye. ko kadan kulawar sanaya bata burge safwan,shi burinshi yasamu sauki ya maida ita gaban iyayenta kamar yadda yayiwa mahaifiyarshi alkawari. Kimanin sati guda kenan,jamian tsaro kullum cikin neman safwan suke da sanaya,amman koda wasa basu gansu ba. Zuwa lokacin kafar safwan tayi sauki,dingishi kawai yakeyi shima ba sosai bane. Sanaya ce zaune ta takure agefe tana kallan safwan yana waya da rahama,sosai yake burgeta,musamman dan karamin bakinshi,kamar ba namiji ba. Batai auneba har ya kamata tana kallonshi,da sauri ta dauke ido ta fara soshe soshe alamun jin kunya. Mikewa yayi ya dauki jakunkunan kudin,ya fitar dasu waje sannan ya leko yace mata batare daya kalleta ba. "uwar yan kallon kwaf,seki fito mutafi" Mikewa tayi jiki asanyaye dan ko be fada mata ba tasan gida ze maida ita. fitowa tayi tana turobaki gaba,tana shirin yin kuka, shiko ko ajikinsa haka ya dauki kudin suka kama hanyar da zata sadasu da bakin titi, sundan jima suna tafiya kan suzo bakin titin,shatar mota ya daukar musu zuwa kaduna,har lokacin sanaya bakinta a ture yake. Sun iso kaduna lfy,inda kai tsaye unguwar rimi suka nufa inda anan gidan nasu da sukafi rayuwa aciki yake. isarsu tayi daidai da fitowar gomna zashi gidan gomnati dake kashim ibrahim house. Sanaya ce ta fito sannan safwan,akan idon mahaifinta hakan ta faru,a gigice,yacewa direba ya faka. Tun kan agama tsaida motar ya fice,dama tuni masu tsaron gidan sun kama safwan, da gudu sanaya tayi jikin mahaifinta tana kuka,runfumeta yayi kam kamar zaa kwace masa ita. Janta yayi zuwa cikin gida,yayinda yabada umarnin a shigo da safwan. Nanfa hayaniya ta kaure,dan safwan ware kwanji yayi ya kwace daga rukon da aka masa. takawa yayi yaje gaban gomnan,ya finciki hannun sanaya,ya kamo na gomnan yasa aciki yace afusace. "Banyi fatan,sake saka a idona ba firauna,ga yarka nan nadawo maka da ita cikin aminci,ashawarce kadunga adana duk abinka dakasan yanada muhimmanci,dan nan gaba in na dauka bazan dawo dashi ba" Daukeshi da mari gomnan yayi,sannan yace cikin fushi. "dama kaine karen daya ketawa yata mutunci?kaine karen,daya hana iyalina sukuni?dole na hukuntaka daidai da abinda ka aykata" "karnukan zasu kara yawa,da zaran nazo gidanka akaro na biyu na kara yin haushi"cewar safwan,ya juya a fusace ze bar gurin. "hey dakata dan samari,ay ban sallamekaba,zaka bar gurinnan ne kawai idan nai maka umarni"cewar gomna. Batare daya waigoba ya bashi amsa. "sanda nazo ba umarninka nabiba,dan haka zan koma vatare dana jira umarninkaba,in kuma akwai wanda kake tunanin ze tsaidani inason ganinshi" Nuni gomna yayi da hannu kawai,ay kan kace kwabo tuni sojoji sunyi kan safwan. Da wata razananniyar kara sanaya tace musu. "ku dakata!!!!!" Cak suka tsaya,takawa tayi taje gurin safwan din,tana zubar hawaye,ta duka agabansa tace. "kai namijine safwan,kayi rawar gani a rayuwata,bazan taba mancewa dakaiba,don Allah ka manta da abinda ya faru,sabida kar ko nan gaba in nemi alfarma agurinka ka kasa yimin sabida laifin babana,katafi cikin aminci babu me tabaka" Shuru yayi yana kallonta,daga karshe yasa kai ya fice daga gidan batare da kowa ya tankashi ba. mikewa tayi da gudu ta nufi jikin mahaifinta tana kuka,rungumeta yayi,ya nufi cikin gidan da ita,mahaifiyartace ra taso da gudu ta rungumeta,tana hawayen farinciki. Kamin wani lokaci tuni gida ya cika da yan uwa da abokan arziki sunzo tayasu murna,ba abinda yafi va gomna mamaki kamar ganin kudin da aka dawo masa dasu baa taba ba. Acikin masu zuwa murna harda Shaheed yaron abokin daddy,wanda aka tsaida mgnr aure tsakaninshi da sanaya,sabida son juna da sukeyi. Ada un akace ga shaheed,sanaya rasa inda zata sa kanta takeyi dan murna,dan so tari kan yafito daga mota,tuni ta isa gareshi. Sabanin yau,da tanajin muryarshi ta lumshe ido alamun bacci takeyi. Shigowa yayi cike da murna,gaba daya yayi baki ya fada sabida rashin sanaya,ko yanzu ma doguwar rigace kawai ajikinshi ya nƴfo gidan. Kusa da ita yaje ya zauna yana kallon yadda ta dan rame gamida yin duhu,jiyayi ranshi ya baci,gamida tausayinta daya kamashi. hannu yasa ya shafo kanta,ya furta a hankali. "i miss you my pretty,nagodewa Allah da kika dawo cikin koshin lfy" duk abinda yake sanaya najinshi Tade yi shuru ne,dan ita yanzu ko kallonshi bata son yi🤔 muje zuwa kuyi hakuri na rashin jina tsawon lokaci, nayi bakine daga gida,so na basu dukka lokutanane,yanzu zaku ci gaba da ganina akan kari ngd Surbajo for life [08:57, 1/6/2018] ‪+234 813 454 0705‬: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Gaida me gaisheka ko baze amsa ba,my Bilyn shantali,wannan shafin nakine,ngd sosai da yadda kike bin rubutuna kuma kike fahimtar bambacin dake tsakanin nawa dana saura,ina sonki bily Allah yabarmu tare* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *15-16* Haka ya gaji da zaman jiran ta farka ya tafi,amman badan ransa yasoba. Yana fita ta farka,tabi bayanshi da kallo,runtse ido tayi hawaye nabiyo fuskarta,na tausayinshi,dan tasan yana sonta,ita kuma yanxu ba sonshi aranta. Safwan yana barin gidan gidansu ya nufa,inda yasamu kawunnans na kauye sune sukazo suka sallaci gawar ummansa suka mata sutura. Yau sadakar bakwai shiyasa yasamesu a kofar gidan,suna ganinshi sukayo kanshi da tambayoyi. "safwanu ina ka shiga tsawon wannan lokacin?"cewar kawunsa. Kasa mgn yayi kawai se yasa kuka,nanfa sukayo kanshi da rarrashi,dan sosi ya basu tausyi. Rahama na ganinshi da gudu tajeta rungumeshi,tana kuka,ranar mutuwar sbuwa ta dawo. Koda aka rkashi kabarin umman be baro gurinba se da magrib,yana ta kuka gamida yi mata addua. Haka rayuwa taita tafiya har akayi sadakar arbain din ummansa,yana fita yayi aykin karfi dan yakawowa rahama abinci ko kadan be barinta da yunwa. A nashi bangaren kuma gomna yasha alwashin se yaga bayan safwan,dan beci bulus ba,yanajin tsanar safwan a zuciyarshi kamar yadda bawa ya tsni mutuwa. Sanaya rabuwarta da safwan yasa ta koma so silent,in banda tunaninshi ba abinda takeyi,a nsu tunanin iyayenta da gaske ne safwan yamata fyade,shiyas mummyn ta ta maida hankali gurin dirka mata magunguna domin rufuwar asirinsu Sanaya ce rike da wayarta,ta buga uban tagumi,tanaso ta tuno wani abu. zuwa can naga tayi saurin fara danna numbobi a wayar tata,ba number kowa tasa ba seta safwan. wacce ta jima da haddaceta tun suna daji. bugu daya biyu ya daga. "slm wa ke mgn"ya fada batare da damuwar komaiba. Jin muryarshi ne ya haddasa mata bugun zuciya,da kyar ta iya cewa. "Hero sanaya ce"ta fada a tsorace. Mamakine ya kamashi,na inda ta samu number shi. batare da mamakin komai ba yace. "oh sanaya,sannunki ykk" Tunda sanaya take bata taba jin bakin da ya kira sunanta daidai ba kamar safwan,runtse ido tayi wani farinciki na ratsa ta. "lfy launake,ya dadin hakurun umma?" "mun gode Allah" "Allah yajikanta" "Amin" Shuru ne yabiyo bayan hakan. zuwa can de ta sake cewa. "ina rahama?" "Tana gida"ya bata amsa. sake rage murya tayi sannan tacd. "kai kuma kana ina?" "ina gurin kasuwanci na" "wanne irin kasuwanci"ta tambaya . Tambayoyinta sun fara isarshi dan haka cemata yayi. "ngd ko sanaya,se anjima"kan tayi mgn ya kashe wayarshi. kifewa tayi akan gado tana share hawaye,tabbas tasan safwan baya sonta,amman ita kuma shine rayuwarta,zatayi duk me yiwuwa wajen ganin ta mallakeshi🤔 Tana kwance tana kukanne kuran shaheed ya shigo wayarta,a fusace ta dauki wayar tace. "To uban yan naci,me kake nema kuma?" ita kanta batasan sanda mgnr ta fita a bakinta bs,shiko shaheed wayarcr ta kusa faduwa a hannunsa sabida tsabar kudima da jin sunan data kira shi. "Sanaya nine uban yannacin?"ya tambaya. "Eh"ta bashi amsa gamida kashe wayarta. Jirine ya soma dibar shaheed da sauri ya nemi guri ya zauna,tashin hankalin daya shiga baze faduba dama shi ya lura tunda sanaya ta dawo gaba daya ta sauya masa,dan haka ze yiwa dad dinshi mgn ayi saurin yi musu aure,dan yana tsoron rasata. Ba comments a whatsapp,but Facebook abun se godiyar Allah su sunayi sosai. muje zuwa surbajo for life [11:11, 1/6/2018] ‪+234 813 454 0705‬: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *AUNTY RUMAISA LAGOS,MACE ME FARAR ZUCIYA DA KYAWUN NIYA,A MASOYANA INNACE DAYA TO TABBAS ZAN AMBACEKI A BIYU,SHAWARWARINKI GARENI SUNAMIN DADI,KUMA IN NABI SUNA MIN RANA,INA SONKI SOSAI AUNTY NA,ALLAH YA RAYA MANA ZURIA,YABAR MU TARE DA MAZAJENMU CIKIN SO DA AMINCI,LOVE YOU SIS WITH ALL MY HEART♥♥♥♥♥♥♥♥♥* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *17-18* Sanaya ranar wuni tayi kulle adakinta tana kuka dan safwan ya kashe mata waya. Shaheed ko Allah Allah yake dad dinshi ya dawoya sanar dashi aje nema masa auran snaya cikin satinnan,tunda sun kwashi tsawon shekaru uku suna soyayya. Mahaifin shaheed na dawowa ya tare shi da maganar,murmushi kawai yayi yace. "son ba ko kunya wai aure yakeso,to karka damu bari zuwa gobe se in shiga gurin dad dinta muyi maganar " Murnace ta kama shaheed rungume dad din nas yayi,yana masa godiya,dan shi dama yafiso ayi auran inma laifi yay mata ya rarrashi abarsa sanda ya dorata akan cinyarshi. Washe gari da safe,dad din shaheed yaje gurin gomna,sun tattauna gameda auran tunda dama kowa yasan suna soyayya. Kamar yadda shaheed ya bukata,haka aka saka wato nan da sati guda. Bayan sun rabu ne gomna ya shiga bangaren mtarshi inda yasmeta zaune dasu sanaya suna hira. Be damuba yafara maganar data kawoshi. "hajiya kinji mutananki ko,sanaya da shaheed yanzu sun fara mgnr auransu,dan yanzu mahaifinsa yabar gidannan shaheed ya matsa akan a daura auranshi da sanaya cikin satin nan to nasan da amincewarta shiyasa na amince a daura din" "WHAT!!!!"cewar sanaya da taji maganar kamar saukar aradu. azabure ta mike tana kuka tana faɗin. "no daddy bazan aureshi ba,ko na aureshi ze sakenine,kafa tuna dad safwan yarigadaya batamin rayuwa,wlh ba namijin dazega mutuncina mtukar bashidin daya yimin fyaden ba,dan haka wlh banason shaheed inkuma kamin dole wlh sena kashe kaina"tana kaiwa nan ta juya ta shige dakinta tana kuka me tsuma zuciya. wani gumine yashiga karyowa gomna,safwan ya cuce shi,cuta tahar abada taya ze iya yafe masa. "Alhaji batun sanaya abun adubane fa,kasan fa budurcin mace shine mutuncinta dana iyayenta agurin miji da danginsa,pls kayi nazri sosai kar muzo muna dana sani"cewar mummy. Shide yakasa mgn gumi kawai yakeyi dan ko giyar wake yasha baze bari sanaya ta auri safwan ba,inde shine ubanta. Alamura sun cabe gaba daya dan yanzu sanaya kwananta biyu kenan kwance adakinta tarufe kofar baci basha,gaba daya ta fita hayyacinta. Hankalin iyayenta duk yatashi ba ma kamar gomna tsoronshi kar yunwa da damuwa ta kashemishi sanayarsa. Masu balla kofa ya kira suka balla kofar, a kwance suka hangota ko numfashi batayi,dagudu dad ya sungumeta,zuwamota mummy da munaya nabinshi. Da sauri excorde dinshi suka bude musu motar,tuni jiniya ta fara tashi,suka fice a dari,zuwa asibitin Garden City. Duk abun da ya dace shi aka mata,inda binciken farko yabada tabbacin jininta ya hau,sosai snnan damuwa tayi yawa a zuciyarta wanda gab take dahatsarin kamuwa da ciwon zuciya. Kukane kawai gomna beyiba,amma mummy da munaya sunyi kuka har sun gaji. Safwan ya gama cutar dasu,cuta ta har abada haka kawai suke maimaitawa. Shaheed besan wainar da ake toyawa ba se yau dayaje gidan aka sanar dashi ay mutan gidan na Asibiti. kai tsaye asibitin ya nufa,inda ya samu kowa jugum jugum ana jiran farkowar sanaya. Ayko suna zaune ta farka. "wlh banason shaheed bazan aureshiba,inko aka takuramin sena kashe kaina,na tsaneshi bana kaunarshi"itace kalmar dasanaya ta farka da ita akan bakinta. A gigice shaheed ya mike yana ja da baya yana fadin "No,no, no, sanaya kina sona duniya ma tasan hakan........"ji kake sharab ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme, wayyo tashin hankali baa sa maka rana gomna ko takalmi babu akafarsa 🤣haka yake daba kafar akasa, Emmergency aka shiga da shaheed rai a hannun Allah,itako sanaya bata masan anayi ba dan ci gaba tayi da fadin batasonshin cikin mayen ciwo. muje zuwa Surbajo for life 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* *Sometimes I forget 2 say hi, sometimes I forget to reply,sometimes my msg doesn reach u, but it doesn"t mean I forget u. I"m just giving u time to Miss me😊 AUNTY ASMAU ABDULLAHI SHAREEF YAKO AND AUNTY ALIYA SHAREEF GAMBO YAKO,YOU GUYS I LOVE YOU IRIN SOSAI DINNAN♥♥♥♥♥♥♥🙈* *Dedicated to fatima Abubakar Radda* *19-20* Kan kace me an dukufa gurin ceto ran shaheed,dakyar akasamu numfashinshi yadawo shima seda taimakon oxygen. Do kyar security din dad suka lallabeshi yasa takalmi,se masifa yake tayi. Sanaya ko allurar bacci aka mata dan ta daina cewa batason shaheed. tuni labari ya isarwa iyayensa tuni suka garzayo asibitin domin kawo masa agaji. Sun kidima da ganin halin da dan nasu yake ciki,mumynshi in banda kuka ba abinda takeyi. Munaya ko tausayin shaheed yafi komai sata kuka,dan tasan irin son da yakewa sanaya ba na wasa bane. Bayan kwana biyu dukansu sun dan murmure,hakanne yasa daddy sawa asallamesu in yaso doctor yaje gida yaci gaba da duba su. Batan an sallamesunne yasa aje azo masa dasafwan in yayitaurin kai,su babballasa su kawo shi. Allah sarki bawan Allah yanacan gurin da yake faskare,yaga motoci kamar ana yaki dan harda igwa🤣. "ka bimu muje cikin aminci inba haka ba wlh se mun harbeka,me girma gomna ne keson ganinka"cewar daya daga cikin wainda aka turo. Ba musu safwan yabisu dan dama yanaso yamasa warning na karshe😳 Har cikin falon gidan suka shigar dashi,yayi mamakin ganin kowa zaune yana kallonsa. Sanaya na ganinshi ta rushe da kuka,sabida tuno sharrin data mushi. "meyasa kayiwa sanaya fyade?" jin tambayar yayi kamar daga sama da sauri ya waiga yana kallon gomnan. "tambayarka nake ko baka ji vane?"ya maimaita. "katambayeta ni ban yi mata fyade ba,ay gatanan tana jinmu"cewar safwan. "Sanaya,waye ya miki fyade?"gomna ya tambayeta batare da wasa ba. kukanta ne ya karu inda cikin kukan tace. "Daddy safwan ne yamin,wlh har so goma yana maimaitawa"t karasa maganar cikinkuka inda taci gaba da cewa. "ka cuceni safwan,ka lalatamin rayuwa,kasa nida shaheed mun haramta ga juna dan ko na aureshi baze ga mutuncina ba,dan haka yazamemaka dole ka aureni tunda kaine ka fara Sanina"ta karasa maganar cikin gunji kuka. A zabure safwan ya mike,ya nunata da dan yatsa yacr cikin fushi. "naga alamun kamar yadda tsohonki yake dan giya kema kin fara korawa,agidan ubankine ni safwan nai miki fyade,wlh ki shiga taitayinki ni ba saan wasanki bane" "wlh kaine,kuma dole ka aureni a hakan,in banda kaddara ma ni mezanti dakai kazamima irinka"cewar sanaya cikin kuka. wata cafka yakai mata inda ya shako wuyan rigarta sega sanaya a sama ya ruketa da hannun daya,dan masifa hancinshi har budewa yake,yace. "kin gama rabarwa atiti ne yasa kikeso ni na kwashi saura ko,to bari kiji ni nafi karfin ragowar wani,kuma wlh ko na aureki sanaya,senasa kin mance da waye ubanki,karuwa kawai"cillar da ita yayi,sanaya fitsari ne kawai batayiba dan tsananin tsoro. "Nan gidanane dan samari ba naka ba,kuranka nayi dan na baka umarni,yazama dole kayi daya aciki,ko ka auri yata daka lalata ko kuma nasa atsareka anan na tura karti guda goma gidanku su yagalgalamin kanwarka kamar yadda kayi wa tawa yar,wlh ba wasa nakeba"cewar gomna yana huci. kuyi hakuri da wannan abubuwanne se ahankali surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SANADIN KIDNAPPING* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *ZAHRA SURBAJO* 🙏🙏🙏🙏🙏🙏🙏🙏 *Don Allah kuyi hakuri na jina shuru da kukayi,wlh inada babban uzurine,daya sha kaina,ina fatan zakumin uzurin* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda♥* *21-22* Shuru safwan yayi yana kallon sanaya,cikin matsanancin mamakin sharrin da ta masa. Se yanzu yayi danasanin saninta a rayuwarshi,wasu hawayene masu dumikebin fuskarsa,dan yasan sabida kansa baze so ya tarwatsa rayuwar kanwarsa ba,uwa uba anashi ganin,da yakai rahama gidan miji ba cikakkiyar budurwa ba to gwamma shi yadauki second hand din koda hakan zeyi sanadin salwantar numfashinshi. Zubewa yayi akan guiwowinsa yana kuka ya rike kafafun gomnan,yace. "zan auri yarka domin kare mutuncin kanwata,bana son yarka bana kaunarta,na fada maka ne dan ka tabbatar da cewa kiyayya ba abunda bata sawa,dan haka in har ni kakeson na aureta to ka daura mana auran yanzu,dan wlh ya wuce yanzu bazan aureta ba,koda kuwa da naman jikina zaa dunga yin miya a gidanka kullum"ya karasa maganar cikin dakewar murya. "kai dalla malam dakata,ubanwaye saanka anan,kabar ganin fa ina kyaleka,wlh ba tsoronka nake jiba,akwai lokacin da zakayi nadamaraykata min duk abinda kayi,kasan duk wanda ya rigaka dakwana dole ze rigaka tashi,yata ni nake da ikon saka ranar auranta ba kaiba dan haka bazan daura auran yanzu ba" mikewa safwan yayi yace "to naji,sede ka manta da cewa,sanayace yarka ba niba,kana daiko akanta amman banda ni,dan mulkin naka ba inda aka rubuta se gomnan jihaya amince dan jihar zeyi aure,kamar yaɗdana fada da farkoin na fita yanzu wlh bazan aureta Ba"yana kaiwa nan ya juya Ze bar falon. Dawani mahaukacin gudu sanaya tazo tasha gabanshi har tana haki,sabida adan zamanta dashi ta fahimci shi kaifi dayane,inde ya fadi abu ti tabbas seya aykata, ruko shi tayi tana kuka tace. "Don Allah kar ka tafi,ka bari adaura auran yanzu"da sauri ta waiga gurin dad dinta tace cikin kuka. "dad inde da gaske kana son farincikina toka Daura aure na yanzu anan gurin," "Sanaya..."cewar dad "dad"ta katse shi da hanzari. shiko safwan ko ajikinshi,so yake ta bashi guri kawai yawuce. Ganinfa da gaske sanaya take ne yasa dad Yin abinda ta bukata badan shi yasobane. Shide shaheed dake zaune kamar gawa inbanda kuka ba abinda yake. Haka abban shaheed yayiwa sanaya wakilci sannan gomna yayiwa safwan aka daura kan sadaki dubu dari dahamsin . an daura aure lfy,sanaya se murna take,ana gama daura auren taje gaban daddynta tace cikin kuka. "daddy kuyi hakuri,zan sanar daku gaskiya,wlhsafwan beyimin fyade ba,kawai sonshine ya kama zuciyata ta yadda bazan iya hakuri dashi ba,ina son safwan dad fiye da raina,shaheed kayi hakuri,wlh nakasa jurewa ne" Azabure kowa ya mike yana kallonta,cikin fushi dad yasa hannu ya dauketada mari,sannan cikin fushi yanufi safwan. "nasan kunnenka yaji maka,cewa ba gaskiya bane sharrin data maka,dan haka yi hanzarin sakarmin ita yanzu dan baku dace da ita va" Murmushi safwan yayi,ya mika hannu ya kamo sanaya suka tsaya gaban dad yadubeta yace "Kina sona da gaske ko?" kai kamar na kadangarw haka tashiga gyada shi. murmushi yasakeyi Sannan yakai dubansa gun gomna yace. "Baba a tayamu da addua dan nima.gaskiya ina son matata"yana kaiw nan yaja hannunta suka fice daga falon. "sanaya in kika bi karen nan na tsmeki acikin yyana,bani bake har abada"cewar gomna kamr zeyi kuka. Sanaya ko hawaye kawai takeyi dan tasan yanzu safwan yafi iyayenta iko da ita,dan haka ko waigowa bata yiba,tabi safwan suka fice daga gidan. tofa muje zuwa. Surbajo for life. *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *23-24* Har suka fice get safwan be saki sanaya ba,janta yake iya karfinshi. Mahaifinta ganin sun fitane yasa ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme,sabida in akwai abinda ya tsana a rayuwarsa to be wuce safwan. Da gudu aka kwashe shu zuwa asibiti,rai a hannun Allah. Koda likitoci suka dubasa tuni jininsa ya hau over dan haka taimakon da yadace suka shiga yimasa. Safwan da sanaya ko suna fita ya saki hannunta,yaci gaba da tafiyarshi kai kace ba tafiyarsu daya ba. Binshi take kamar bindi,dan batasan manufarsa rayin hakanba. Ɗankwalin kanta ta kwance ta rufa ajikinta,dan ko mayafi babu a tare da ita. Safwan tafiyarshi kawai yakeyi,dan ko sisi bashi dashi dazasu hau mota.sanaya taga ta kanta,dan tun daga malali,har zuwa tudun wada kaduna akafa sukayi ta. sanaya har jiri ke dibarta dan tunda tazo duniya bata taba yin irintaba,gashi sauri yake kamar ze tashi sama,haka ta dunga falla gudu tana binshi dan kar ya bace mata. Gurin inno me icce dake gangaren bolar layin ƙosai ya nufa,yana zuwa gatarinshi ya dauka yaci gaba da faskarenshi. Agurin akwai wani tsohon tankin mota da aka ajiye kusa da shagon deluwa me mangoro dan haka sanaya can ta nufa ta zauna tana kallon yadda yake faskaren. Hawayene kebin fuskarta,na tausayin kanta,sanda takai dubanta kan kafar deluwa sannan ta dubi tata kafar,sosai ta deluwa tafita ta kyn gani, Safwan be dena faskarenba se gefin magrib,sanaya na kallo inno tabashi dubu uku kudin aykinshi,fuskarshi kawai ta kalla tasan yana tsaka da murnar samun kudin. Suna sallama da inno ya juya ya dau hanyar tafiya,batare dayayiwa sanaya magana ba,da sauri ta mike tabi bayanshi. wani gida sanaya taga ya danna kai ciki,me kama da akurki a gurinta,da sauri itama tabishi. Rahama ce ta taso da saurinta tana fadin. "Sannu da zuwa yaya,ya ayki?" Murmushin da sanaya bata taba gani safwan yayi ba,shi taga yayiwa rahama,gamida cewa. "lafiya lau kanwata,ya zaman kadaici?" murmushi rahama tayi,se alokacin ta hangi sanaya dake rakube a bayanshi,da sauri ta kalleshi tace. "yaya bakuwa mukayine?" be kulata ba illa wucewa da yayi ya dauki buta yayi alwala,yazo ya fice masallaci. jiki a sanyaye rahama ta matso gurin sanaya,kirkiro murmushi tayi gamida cewa. "sannu da zuwa bakuwa,tafiyarku daya da yayana ko?" murmushi sanaya itama tayi gamida cewa. "yauwa rahama,tafiyarmu daya dashi" Mamakine ya kama rahama najin sunanta a bakin sanaya,tunda taga safwan be kira sunan ta ba bare tace anan taji. Hakade ta jata zuwa ɗakinta,ruwa ta bata tai alwala,ba abinda yafi ba rahama mamaki,kamar ganin suturar jikin sanaya,wani leshine da kwanaki taga irinshi gurin jummai dillaliya 400k, kwata kwata rahama ta kasa sakin jiki da sanaya,har zuwa sanda ta zubo musu abinci,suka ci rahama dari dari takeyi ta kosa safwan yadawo gidan. sanaya ko tana gama cin abinci ta bingire a gurin s bacci,sadaf sadaf rahama ta mike tafice daga dakin,kofar gida taje ta tsaya Bata jimaba yadawo gidan,yasameta a waje,ayko faɗa yarufeta dashi,dukar dakai tayi tacr kasa kasa. "ba dole in fito ba kaje ka dauko budurwa kamar yar aljanu dan kyau kazo ka ajiyeta a gida bakamin bayanin ko ita wacece ba," Murmushi yayi yacr. "wlh rahama kin bani da tsoro,yanzu macen ma tsoronta kikeji" dariya tayi gamida kama hannunshi suka juya zuw cikin gidan. a tsakar gida ya zauna kan tabarmar data shimfida masa. abinci yaci tukuna,sannan bayan ya gama,ya kwashe duk abinda ya faru yafadamata. Idon rahama kamar goruba tace. "yaya kana nufin wannan yar gomnan garinnance Kuma matarka?" tsaki yayi gamida cewa. "to meye aciki na mamaki,da har kike wni zaro ido?" Bata kulashiba da gudu ta mike ta koma dkinta tana karewa snya kallo cike da tsananin mamaki,dan ita ko me ayki. Gidan gomna bata tabazaton ganinta ba ko a mafarki bre yarshi. muje zuwa nifa Allah ya sni thanks dinna ce ta fama bana so nafiso ayi sharhi shine ke bani kwarin guiwar yin wani akan lokaci Surbajo for life. January 15 at 9:19pm · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Haba yan amanar surbajo,wato zahra surbajo novel group,don Allah ku dunga hakuri kunji,koda nice nai muku laifi don Allah kudena cewa left shine masalaha,bare in wanine yay muku,danni de nidaku mutu ka raba,dan duk wacce ta fita sena dawo da ita,duk da banfiye zuwa online ba yanzu amman inde nazo nasamu ba wata tofa zan dawo dake don haka don Allah kuyi hakuri da juna,in kuka rushe nima na rushe ,kusha kuruminku register ta kiran suna zan muku sabida tsaro * *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *25-26* Sanaya jin mutum akantane yasa ta farka,wata kara tasaki na razana da gnin inda take,dan ta manta tabiyo safwn gidansu,azatonta saceta aka sakeyi Jin ihun tane yasa safwan dake waje shiga dkin da gudu,rahama ko mannewa tayi da bango dan itama a tsorace take,dan bata san abind yasa sanaya yin ihu ba. Sanaya ko ido a rufe take ta faman buge buge na neman hanyar gudu,da sauri safwan ya isa gareta akayi katari ko ta fado kirjinsa. Rungumeta yayi tsaf a jikinshi,tuni sanaya ta dwo cikin hayyacinta dan jikin safwan ta jima d haddace yadda yanayinsa yake,dan haka bata bukatar karin bayanin ko waye ya rungumeta. kwantar da kanta tayi akan kirjinshi,tana maida numfashi,kasancewarta shagwababbiyane yasa bata dena kukan kasa kasa ba. yawan gashin kan sanaya ba safwan ba hatta rahama seda ta yi mamakinsa,dan gaba daya ya rufemata rabin bayanta, Hannu safwan yasa ya yaye mata gashin da ya rufe mata ido,yadan sunkuyo daidai kunnanta yace a tausashe. "me aka miki ne?" sinne kai tayi gamida yan soshe soshe na alamun taji kunya,. kara matseta yayi ajikin shi yace. "oya tell me,whats wrong with you?" A kunyace tace. "Nothing" "are you sure?"ya tambaya. "very sure"ta bashi amsa. Har alokcin be saketa ba,seda yaga ta ntsu sosai,yana sakinta,ya juya ze fice a dakin,ji yayi an ruko shi,kan ya juyo ita ta karaso gabanshi. langabe kai tayi,ta kureshi da idanuwanta masu kama dana ashwairiyya,shima binta yayi da ido,tabe baki tayi alamun kuka tace. "tsoron dakin nakeyi fa,kuma naga zaka fita ka barmu mu biyu" Yasan zaa rina,dan ya fahimci shine abund ya firgitata dazu, "to ya kike so nayi muku,munan shine inda muka saba rayuwa,so mu be bamu tsoro"ya bata amsa. sakalo tayi tana kallonshi,dan ta fahimci akwai alamun bacin rai agame da amsar tashi. "Allah ya baka hakuri ni ba nufina kenan ba"tace tana share hawaye sakinshi tayi ta koma gefe ta takure, sa kai yayi ya fice,adakin. Rahama cr ta karaso gurin sanaya tacr "kiyi shuru kinji ba abinda ze sameki da yardar Allah ki kwanta kiyi bacci" murmushi sanaya tayi gamida kwantawar kamar yadda rahama ta bukata. itama rahaman kwanciya tayi abinta kan wani lokacu tuni tayi baccinta,sanaya ko idonta biyu, ga aladar berayen gidan su safwan se cikin dare suke shagalinsu,dan haka yanzunma farawarsu kenan. tim sanaya taji abu ya fado mata akanta,da sauri tamike,ta haska fitilar wayarta,wani rusheshen berane tagani yana kada bindinsa, Wayyo sanaya,mikewa tayi tsaye tana ta guje gujenta,sabida berayen sunkai shida a tsakar dakin. Rahama ga nauyin bacci sam batasan wainar da ake toyawa ba,sanaya se kuka take jikinta na bari, Safwan daga dakinshi yajiyo karar guje guje,da kuma sautin kuka,da sauri ya fito daga dakinshi,yana fitowa ya fahimci daga inda karar ke fitowa,da sauri yaje ya tura kofar gamida haskawa da torchlight din hannunshi beraye n yaga suna guje guje tare da sanaya,wacce hatta zanin jikinta ya kwance,daga ita se pant sabida ita dama ba gwanar saka underwear bace. Fararan cinyoyinta a waje se sheki suke,tayi gumi kashirban tana kuka. A karo na farko da wani tausayinta me tsanani ya kamashi,da sauri yaje gurinta,yasa hannu ya dagata sama, da sauri ta kankameshi tana fadin. "don Allah kataimakamin wlh bana kyamar gidanku amman wainnan halittun zasu hallakani" bece mata komai ba ya juya ya fice da ita dauke a hannunshi, Dakinshi yakaita,wanda shi akwai gado me rumfa aciki,dade sauran kayan afanin gida haka,sabida shine dakin ummansu kan ta rasu,Rahama ta guji dakin ne sabida tuno umma da takeyi aduk sanda ta kwanta aciki,babu yadda safwan beyi da itaba amman fafur taki aminta da dakin,shiyasa shi yake kwana aciki ita kuma ya bar mata nashi. Kan gadon yaje ya dora sanaya,sannan ya koma ya rufewa rahama dakin shima yadawo ya rufe nashi. Rawar sanyi sanaya takeyi sabida rigarta data jike da gumi batare da tunanin komai ba ta cire rigar ta cillar sannan ta shige cikin bargon nan irin na fulani me ruwan toka.wani dumi taji ya ratsata, Safwan hawa gadon yayi shima sannan ya gyara net din dake jiki gudun haurowar berayen dan ko adakin nashi akwaisu. bude bargon yayi da nufin ya rufa shima,arba yayi da boobs din sanaya da rabinsu basa cikin bra din,sunyi tirtsi tirtsi suna kallonshi, wani abune kemasa yawo ajiki wanda yarasa ko menene,daurewa yayi ya kwanta amman idonsa na kansu. A zatonshi tayi bacci ne, sede yana kwanciya ta mirgino jikinshi,ta dora kirjinta akan nashi,tacr cikin dasasshiyar murya. "sanyi nakeji,pls ka rungumeni" Shuru yayi kawai,dan shi kadai Yasan yanayin da yake ciki awannan lokacin,hannu yasa yaja bargon ya rufesu sannan ya gyara mata kwanciya ajikinshi ta yadda zataji dadin baccin. muje zuwa Surbajo for life. January 16 at 9:38am · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *ESHA MUSTAPHA, ALLAH YA SAUKEKI LFY,YADDA YA SHIGA ANA DARIYA ALLAH YASA YAFITA ANA DARIYAR ,DAKE DA SAURAN MATA MASU CIKI ALLAH YA SAUKEKU LFY DOMIN ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI AMEEN,KEDA UNBORN SURUKATA KULLUM KUNA RAINA,ALLAH YA KAWO MANA ITA LFY,IN KUMA SIRUKINE SHIMA MUNA MASA FATAN ISOWA CIKIN DUNIYA LFY, * *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *27-28* In banda juyi ba abinda safwan yakeyi,tudun boobs din sanaya akan kirjinshi sosai ya jefashi a wani hali. Ita ko batama san yanayi ba,dan ita agurinta yau tafi kowacce rana dadi agurinta,tunda gata kan kirjin mijinta tana bacci hadi da mafarkai masu dadi. cikin dabara yakamata ya kwantar da ita akan gadon ze zame jikinshi anata ne yaji carab ta rikeshi. fitila ya haska,abun dariya ya bashi domin dan karamin bakintane ta cuno shi gaba alamun anmata ba daidai ba,koda ya duba har lokacin baccinta takeyi, Kwanciya yayi yaja musu bargon,Ranar de safwan gadin dare yayi domin sanaya seda ta sake shigewa jikinshi cikin dare. Da asuba atare suka tashi,dubanshi yakai fuskarta da ta dago tana kallonshi yayin da tayi dare dare akan shi , A hankali ya furta. "to ay seki daga jakin da kika samu haka ko tunda gari ya waye" murmushi tayi wanda ya kara kawata fuskarta tace cikin shagwaba. "wanne irin jaki kuma,sede katifa,dan nan akwai dadin bacci"ta dora kanta akan kirjinshi. "Au nine ma katifar,wlh kinyi da da" "ba gwanda katifa ba,da jakin da kace,ay nama fada maka suna me dadi" Sake kudundunewa tayi ajikinshi, safwan lamarin nata yafara tsoratashi dan ya fahimci sam bata da kunya,alamun ta saba harka da maza kenan, "to naji tashi muje muyi sallah kar lokaci ya kure" Da kyar ta tashi,shima seda ta gama juye juyenta akanshi sannan ta diro kasa tana mika. Binta yayi dana mujiya,ganin yadda hips dinta ya cika kamar ze fashe,wani miyau ne me dumi ya hadiye da sauri,ita ko tafiya ta fara yi zata fita a dakin a haka yadda take takunta kai kace nickiminaj ce har shape din jikin. Da sauri safwan yazo gurinta ya damkota,yace cikin fada. "ke mufa nan ba america bace ko london,bare ki dauka agabar teku kike,dan haka ki nemi kayanki kisa kan ki fita ehe kinji na fada miki" cuno baki tayi gaba ta fara dira kafa,tana fadin. "nifa a gidanmu Allah bana sa kaya sede in nayi wanka," "Au haka kike musu sagade sagade da wainnan kitba kitban cinyoyi atsakar gidan?" Dariya abun yaba sanaya,musamman datakai dubanta kan hips dinta taga ya ɗora hannunsa akai batare daya saniba. Dariyartace tasa ya farga da abinda ya aykata da sauri ya cire hannunsa,gamida sosa kai dan yaji kunya sosai,ficewa yayi adakin yana fadin. "wlh kika fito ahaka nidake ne" Koda safwan yaje toilet seda ya hada da wankan tsarki,dan bidirin da sanaya tasashi jiya babba ne, ita ko Walldrop dinshi ta nufa ta bude ta shiga neman kayan daze mata daidai wani jeans tasamu irin weezy dinnan da wata riga bodyhug ta saka abunka da mace me cikar halitta tsaf suka amshi jikinta,wandonne yay mata tsayi amman kasancewar pencil ne ksan se kawai yayi tattara daga kasan. ficewa tayi tsakar gidan inda ta samu rahama ta dora ruwan zafi akan murhu. "Sannu da fitowa aunty na"cewar rahama tana murmushi. harara sanaya ta watsa mata gamida cewa. "hold your sannu da fitowa i don't want it,jiya kinajin beraye zasu cinyeni baki tashiba,se brother dinkine yazo ya ceceni dan haka mun bata " Rahama ta kasa mgn,in banda dariya ba abinda takeyi,buta sanaya ta dauka ta wuce toilet tana murmushi. kunu da kosai Rahama ta shirya musu,bayan sunyi wanka sanaya kayan safwan ta sake sawa,duk da rahama ta bata nata amman taki sakawa. Suna zaune suna shan kokon,safwan se harara yake zubawa sanaya akan sa masa kaya da tayi,ita ko ko ajikinta , Suna gamawa Rahamace ta gyara ko ina,sannan ta dawo suka shiga hira da sanaya,safwan mikewa yayi yacewa rahama. "zan shiga bacci in azhar yayi kizo ki tasheni kuma ku rage hayaniya"yana gama mgnr ya wuce dakinshi. Murmushi sanaya tayi ita da rahama,bayan tafiyarshi ba jimawa sanaya ma ta mike tacewa rahama. "sis zanje na taya yayanki baccin inyaso kya tashemu gabadaya" "to auntyna afito lfy" shigewa dakin tayi,inda ta hangeshi kwance dagashi se boxsize yayi daidai akan gado yanaso yayi bacci,dan ko kadan beyi zaton zata shigo ba. Tun kan yayi mgn,yaga ta cire wandonshi da tasaka,dan dama ya isheta,rigarma cirewa tayi,sannan ra nufeshi sanye da pant da bra da sauri ya dakatar da ita da cewa. "ke nifa ba dan iska bane,taya dan tsabar iskanci zaki wani biyoni daki da ranar nan gatse gatse" turo baki tayi gamida cewa. "nima baccin zanyi" "dan zakiyi bacci kuma shine dan iskanci sekin biyoni,sbida tsbar bakida kunya shine harda cire kaya" "naga kaima kacire ba gwanda nuba ma hrda bra nasa kai ina taka bra din, " "agidan ubanwa kika taba ganin namiji da bra?" "ko bakwa sa bra ay kuna saka singlet amadadinta dan haka ba laifi aciki danna kirata da bra,kuma ma kai wainnan manyan nonuwan naka Allah ko bra din kasa seta yimaka daidai"da yake safwan irin mazan nanne murdaddu kamar salman khan,shiyasa sanaya tace haka. Tun kan safwan yay mgn ta wuceshi taje ta hye kan gadon ta zauna ta kure kirjinshi da ido. "ke wannan kallon na menene nifa ba hariji bane wlh" "Ayko ni harijace"ta bashi amsa tana wasa d harshenta. zaro ido yayi waje yana kallonta,can kasan makoshinshi yace. "da gaske?" kai ta gyada masa. Shuru yayi kamar ruwa yacishi, "to ka kwanta man ni kabarni a zaune" "dole sena kwanta zaki kwanta?" "eh mana ko kamanta kaine katifata"bata jira ya bata ams ba ta turashi baya ta haye kan kirjinshi. Safwan shuru yayi dan abun yafi karfin tunaninshi, itako sanaya bakomai yasa sanaya take masa rashin kunyarba srdan yakara yadda da cewa itadin second hand dince kamr yadda yake tunani,ta haka zata koyar dashi sonta a secondhand din inyaso duk ranar daya gano gaskiya ya mutuntata. Shikuma tunaninshi so yake yamata muguntar da ko yace tazo gurinshi gobe bazata zo ba muje zuwa. Surbajo for life. January 17 at 1:56pm · Public aysm" *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *ESHA MUSTAPHA, ALLAH YA SAUKEKI LFY,YADDA YA SHIGA ANA DARIYA ALLAH YASA YAFITA ANA DARIYAR ,DAKE DA SAURAN MATA MASU CIKI ALLAH YA SAUKEKU LFY DOMIN ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI AMEEN,KEDA UNBORN SURUKATA KULLUM KUNA RAINA,ALLAH YA KAWO MANA ITA LFY,IN KUMA SIRUKINE SHIMA MUNA MASA FATAN ISOWA CIKIN DUNIYA LFY, * *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *27-28* In banda juyi ba abinda safwan yakeyi,tudun boobs din sanaya akan kirjinshi sosai ya jefashi a wani hali. Ita ko batama san yanayi ba,dan ita agurinta yau tafi kowacce rana dadi agurinta,tunda gata kan kirjin mijinta tana bacci hadi da mafarkai masu dadi. cikin dabara yakamata ya kwantar da ita akan gadon ze zame jikinshi anata ne yaji carab ta rikeshi. fitila ya haska,abun dariya ya bashi domin dan karamin bakintane ta cuno shi gaba alamun anmata ba daidai ba,koda ya duba har lokacin baccinta takeyi, Kwanciya yayi yaja musu bargon,Ranar de safwan gadin dare yayi domin sanaya seda ta sake shigewa jikinshi cikin dare. Da asuba atare suka tashi,dubanshi yakai fuskarta da ta dago tana kallonshi yayin da tayi dare dare akan shi , A hankali ya furta. "to ay seki daga jakin da kika samu haka ko tunda gari ya waye" murmushi tayi wanda ya kara kawata fuskarta tace cikin shagwaba. "wanne irin jaki kuma,sede katifa,dan nan akwai dadin bacci"ta dora kanta akan kirjinshi. "Au nine ma katifar,wlh kinyi da da" "ba gwanda katifa ba,da jakin da kace,ay nama fada maka suna me dadi" Sake kudundunewa tayi ajikinshi, safwan lamarin nata yafara tsoratashi dan ya fahimci sam bata da kunya,alamun ta saba harka da maza kenan, "to naji tashi muje muyi sallah kar lokaci ya kure" Da kyar ta tashi,shima seda ta gama juye juyenta akanshi sannan ta diro kasa tana mika. Binta yayi dana mujiya,ganin yadda hips dinta ya cika kamar ze fashe,wani miyau ne me dumi ya hadiye da sauri,ita ko tafiya ta fara yi zata fita a dakin a haka yadda take takunta kai kace nickiminaj ce har shape din jikin. Da sauri safwan yazo gurinta ya damkota,yace cikin fada. "ke mufa nan ba america bace ko london,bare ki dauka agabar teku kike,dan haka ki nemi kayanki kisa kan ki fita ehe kinji na fada miki" cuno baki tayi gaba ta fara dira kafa,tana fadin. "nifa a gidanmu Allah bana sa kaya sede in nayi wanka," "Au haka kike musu sagade sagade da wainnan kitba kitban cinyoyi atsakar gidan?" Dariya abun yaba sanaya,musamman datakai dubanta kan hips dinta taga ya ɗora hannunsa akai batare daya saniba. Dariyartace tasa ya farga da abinda ya aykata da sauri ya cire hannunsa,gamida sosa kai dan yaji kunya sosai,ficewa yayi adakin yana fadin. "wlh kika fito ahaka nidake ne" Koda safwan yaje toilet seda ya hada da wankan tsarki,dan bidirin da sanaya tasashi jiya babba ne, ita ko Walldrop dinshi ta nufa ta bude ta shiga neman kayan daze mata daidai wani jeans tasamu irin weezy dinnan da wata riga bodyhug ta saka abunka da mace me cikar halitta tsaf suka amshi jikinta,wandonne yay mata tsayi amman kasancewar pencil ne ksan se kawai yayi tattara daga kasan. ficewa tayi tsakar gidan inda ta samu rahama ta dora ruwan zafi akan murhu. "Sannu da fitowa aunty na"cewar rahama tana murmushi. harara sanaya ta watsa mata gamida cewa. "hold your sannu da fitowa i don't want it,jiya kinajin beraye zasu cinyeni baki tashiba,se brother dinkine yazo ya ceceni dan haka mun bata " Rahama ta kasa mgn,in banda dariya ba abinda takeyi,buta sanaya ta dauka ta wuce toilet tana murmushi. kunu da kosai Rahama ta shirya musu,bayan sunyi wanka sanaya kayan safwan ta sake sawa,duk da rahama ta bata nata amman taki sakawa. Suna zaune suna shan kokon,safwan se harara yake zubawa sanaya akan sa masa kaya da tayi,ita ko ko ajikinta , Suna gamawa Rahamace ta gyara ko ina,sannan ta dawo suka shiga hira da sanaya,safwan mikewa yayi yacewa rahama. "zan shiga bacci in azhar yayi kizo ki tasheni kuma ku rage hayaniya"yana gama mgnr ya wuce dakinshi. Murmushi sanaya tayi ita da rahama,bayan tafiyarshi ba jimawa sanaya ma ta mike tacewa rahama. "sis zanje na taya yayanki baccin inyaso kya tashemu gabadaya" "to auntyna afito lfy" shigewa dakin tayi,inda ta hangeshi kwance dagashi se boxsize yayi daidai akan gado yanaso yayi bacci,dan ko kadan beyi zaton zata shigo ba. Tun kan yayi mgn,yaga ta cire wandonshi da tasaka,dan dama ya isheta,rigarma cirewa tayi,sannan ra nufeshi sanye da pant da bra da sauri ya dakatar da ita da cewa. "ke nifa ba dan iska bane,taya dan tsabar iskanci zaki wani biyoni daki da ranar nan gatse gatse" turo baki tayi gamida cewa. "nima baccin zanyi" "dan zakiyi bacci kuma shine dan iskanci sekin biyoni,sbida tsbar bakida kunya shine harda cire kaya" "naga kaima kacire ba gwanda nuba ma hrda bra nasa kai ina taka bra din, " "agidan ubanwa kika taba ganin namiji da bra?" "ko bakwa sa bra ay kuna saka singlet amadadinta dan haka ba laifi aciki danna kirata da bra,kuma ma kai wainnan manyan nonuwan naka Allah ko bra din kasa seta yimaka daidai"da yake safwan irin mazan nanne murdaddu kamar salman khan,shiyasa sanaya tace haka. Tun kan safwan yay mgn ta wuceshi taje ta hye kan gadon ta zauna ta kure kirjinshi da ido. "ke wannan kallon na menene nifa ba hariji bane wlh" "Ayko ni harijace"ta bashi amsa tana wasa d harshenta. zaro ido yayi waje yana kallonta,can kasan makoshinshi yace. "da gaske?" kai ta gyada masa. Shuru yayi kamar ruwa yacishi, "to ka kwanta man ni kabarni a zaune" "dole sena kwanta zaki kwanta?" "eh mana ko kamanta kaine katifata"bata jira ya bata ams ba ta turashi baya ta haye kan kirjinshi. Safwan shuru yayi dan abun yafi karfin tunaninshi, itako sanaya bakomai yasa sanaya take masa rashin kunyarba srdan yakara yadda da cewa itadin second hand dince kamr yadda yake tunani,ta haka zata koyar dashi sonta a secondhand din inyaso duk ranar daya gano gaskiya ya mutuntata. Shikuma tunaninshi so yake yamata muguntar da ko yace tazo gurinshi gobe bazata zo ba muje zuwa. Surbajo for life. January 17 at 1:56pm · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *FIDDAH SOKOTO (MATAR AYMAN ME FITSARIN TSAYE,A BOOK DIN UMMU AYMANA)(KISHIYATA )DUK DA HAKA INA YINKI TA IRO,ALLAH YABARMU TARE ALLAH KUMA YAKAIMU RANAR AURANKI MU GIRGIZA UKU,MU KWASHI SHOKI,DAGA NAN HAR SOKOTO SAUTIN MURYATA ARANAR,LOVE YOU DEAR IRIN SOSAI DINNAN * * just for you salma b,add with this * *Dedicated to fatima Abubakar Radda* *29-30* Haka suka kwanta sanaya se shafa kirjinshi takeyi. Shuru kawai yayi yana sauraronta,sosai hakan ke daga masa hankali. Da kyar ya iya ce mata. "ba kince bacci zakiyi ba,?" kara matsarsa tayi gamida cewa cikin muryar daukar hankali. "eh to ay baka sani bane" "baccin ma se an saki?" "eh mana," "kmar ya to?" "kamar yadda nake saka baccin kaima" "ok to jirani"sauka yay a gadon yaje ya kulle kofar sannan ya dawo gareta bayan ya cire kubar jikin kofar. yana hawa gadon,sanaya ta fara zare idanuwa. Murmushi yayi wanda da an gani ansan na muguntane. Kwantar da ita yayi akan gadon sannan ya dora rabin jikinshi akanta ya sakar mata nauyi,sega sanaya na nishi. wasa da gashin kanta ya fara,gamida hura mata iska a kunne, tuni ta fara lumshe ido, Haka de ya Shiga batar mata da hankali da salon shi,sanda hannunshi ya sauka kan na shanunta daga ita har shi seda sukai suma na wucin gadin. Sannu a hankali ya fara murzasu,cikin salo me rikitarwa,sanaya ko ta jima da hawa online dan haka har sake tutturo masa su takeyi. ay safwan,dayaga sakon na mata dadi,ay se ya sauya salo,yakoma murza boobs din iya karfinshi. wayyo sanaya,azaba ta isheta so take ta kwaci kanta amman ina ya danne ta tayi ihu tana kunyar rahama tajiyo, ay kan wani lokaci tuni hawaye ya cika fuskarta kuka take harda majina, shiko be dena ba seda ya gaji dan kanshi ya saketa,ay dagudu ta diro dags kan gadon tana kuka. boobs dinta zafi suke mata bana wasa ba sun ja jawur abunka da farar mace. agurin ta durkushe tans ta kuka. dariya safwan yayi yace. "ya zo mana muyi baccin ko kin fasa?" harara tabishi da ita da jajayen idanuwanta,mikewa tayi da kyar ta dauki kayan data cire dazu ta mayar,sannan ta dauki kubar taje ta bude kofar ta fice tana sharar hawaye. Bayan fitartane karatun ta natsu yazo masa ya fahimci be kyauta ba abinda ya mata, ita ko dakin rahama ta koma ta nemi guri ta kwanta tana jinyar kirjinta,da ya fara yimata ciwo. Koda rahama taga tana kuka bata bi baasi ba,dan tasan tsakaninsune, Safwan ya kasa baccin kaya yasaka ya fito zuwagurin sanaya,inda ya sameta kwance ta dafe kirji tana kuka rarrashinta yashiga yi amman taki yin shuru,se tureshi takeyi daga kus da ita. "kefa kikace nasaki bacci"ya fada cikin sigar zolaya. Harara ta watsa mishi sannan tace. "ko a asibitin dawanau na kano kake kwana ay yakamata kasan cewa boobs ba kayan wanki bane" Dariyr da yake boyew ce ta fito,ayko yana dariyar tan a dukanshi. "Yar renin wayo su turawan da kika gama rabarwa kyauta ay baku musu kukan zafiba seni,da kece kika sani bani na bukata ba" maganar ta sosa ran sanaya amman seta daure ta bashi amsa. "suma ba kyauta na basu ba,kudi suka biya,kaga ko kare da kudinsa,"ta karasa maganar tana dariya. Sosai amsar tata ta kona ran safwan dan haka mikewa yayi fuuuuu ya fice a gidan gaba daya lamarin gomna ko seda yasha kare karen ruwa sannan yadawo normal,kullum da tunanin taya ze raba auran sanaya da safwan yake,dan baze amince ya hada zuria da matsiyaci irin safwan ba. muje zuwa surbajo for life January 19 at 2:11am · Public aysm" *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Kumin afuwar rashin jina,nayi rashin lfy ne,wanda se yanzu nadan samu sauki,* *Akwai wainda kuka turomin sakon karta kwana a etisalat dina,bayan munyi waya daku, Maman Abba kd,masoyan zahra group,Khadeeja umar muhammad,naga sakwanninku masu dadi da faranta zuciyar duk wanda aka yiwa,barinma adduoin dake ciki,banda bakin gode muku,sede ince Allah amin,kuma Allah ya sadaku cikin rahamarsa ngd sosai,ana tare irin sosai dinnan * *Auta Inna Ibrahim Kime,ke tawace ko banyi godiya ba,we are still together for ever * *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *31-32* Har dare safwan be shigo gidanba se karfe tara na dare. lokacin sanaya najin bacci amman taki yi kuma ta hana rahama yi sabida gudun beraye. A tsakar gida ya samesu,inda rahama taimasa sannu da zuwa,yana amsawa dakinshi ya shige, Rahama dariya fushin nashi ya bata,juyawa tayi ta dauko abincinshi,taba sanaya tace. "aunty ga abincin yaya ki tafi masa dashi,ni zanje na kwanta seda safenku"bata jira taji komaiba ta juya ta nufi dakinta,tana shiga ta turo kofar. tsam sanaya ta mike ta dauki kayan abincin ta nufi dakin. A tsakar daki ta sameshi zaune yayi rasherashe yana rubutu a wata takarda. da sallamarta ta karasa kusa dashi,ta ajiye kwanukan abincin,sannan ta maida idonta kan takardar da yake rubutun aciki. Gabanta ne yayi wata mummunar faduwa azabure ta mike tsaye tana salati. masu karatu kuma nasan kun zaburan Da sauri ya dago yana dubanta,itako se tsuma takeyi,da kyar tace. "Haba Hero don Allah form din NDA fa naga kana cikewa,nufinka aykin soja zaka shiga?" tsaki yayi gamida maida hankalinshi kanta yace. "Eh shi zanyi,koko laifi ne?" "ba laifi bane,gani nayi baka shiga soja ba ma ka shahara gurin iya mugunta ina ga kuma ka shiga wanda wlh nasan duk abinda aka koya maka na mugunta acan akaina zaka fara gwadawa"ta karasa maganar cikin kuka. Sosai batun nata ya bashi dariya,ayko ya shiga yimata dariya,seda ya gaji dan Kanshi sannan ya tsagaita,yace "Jita don Allah harda wani tabe baki tana kuka daga cike form inaga kuma ace sanye cikin uniform din kika ganni dauke da bindiga,na setaki,ranar kuma inaga fashewa zakiyi"yaci gaba da yi mata dariya. ita ko har lokacin bata dena kuka ba,harda majina. Seda ya gama cike form din tsaf yaje ya adana,sannan yazo ya zauna yafara cin abincin. Sanaya na tsaye se goge kwalla takeyi kawai,dan yau tana ganin ko bacci bazata iya yiba. Be kulata ba,dan ya fahimci yarinyar akwai shagwaba harda ta banza,tunda form din NDA yasata kuka inaga kuma ganinshi tayi janye da igwa. yana gamawa ya wanke baki,yaje ya haye kan gado yayi daidai abunsa,yafi awa kwance amman sanaya bata da niyyar dena kukan bare tazo ta kwanta. Sakkowa yayi tsam yazo ya dauketa gabadayanta yaje ya kwantar daita akan gadon. Har zuwa lokacin kukan take. Kureta yayi da ido yana kallon yadda hawaye ke zarya a fuskarta wacce tuni ta rine tayi ja. Jawota yayi jikinshi,sannan yace a sanyaye,dan ya fahimci sanaya batason zafin nashi, "Sanaya me yasa kike da yawan kuka ne haka?me kike tsoro a zamantowata soja?" "ni kukan bansan yana zuwa ba ay,ni in ka zama soja zalina zaka dunga ci,kamar yadda kamin dazu da safe"ta karasa maganar cikin kuka. Murmushi yayi ya janyota jikinshi yace. "kiyi hkr ko dazu ma kin damenine shiyasa nai miki haka,amman bazan sake ba kinji ko,kimin fatan alkhairi,ko kinfi so naci gaba da faskaran karfina ya kare acan?" Girgiza kai tayi,tana murmushi. Nande yayta rarrashinta har seda tayi shuru,sukayi bacci tana kan kirjinshi. Haka rayuwarsu taci gaba da tafiya,tuni safwan yazaga da sanaya gun danginsa na kauye dana birni,kowa na kaunarta sabida kyawawan dabiunta. tunda safwan yayi submiting na form din yake jiran ranar da zaa kirasu yin exam. Dama ko form din se masa akayi wani aminin babansu,da yake Tsohon sojane,shine yasai masa form din. Rayuwarsu se godiyar Allah,amman baduk abinda suka nema suke samuba. Sanaya na kewar family dinta,sede duk wanda ta kira a waya be dauka har munaya. Abunda bata saniba shine gomna ne yasa Allah ya isa ga duk wanda ya nemi sanaya ko kuma ita ta nemeshi ya amsa,shiyasa basa daukar wayarta. Abun na damunta,ga safwan ba irin mazan da zaka zauna ka fada musu damuwarka bane,shiyasa sede tajabakinta tayi shuru. Yau ne aka bukaci ganin su safwan a Nda dan haka da wuri ya shirya ya wuce domin yin exam muje zuwa Surbajo for life. January 26 at 10:11am · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Kuyi hakuri banajin dadine shiyasa kukejin shuru * *Aunty Hassana Tanko Atk kaduna,wannan shafin nakine kiyi yadda kikeso dashi,Allah yabar zumunci yasa mu gama da duniya lafiya Ameen,* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *33-34* Ranar sanaya wuni tayi kamar mara lfy,sabida zullumi,daga karshe da taga hakan bazata mata ba mikewa tayi taje ta dauro alwala tazo tafara nafila tana rokon Allah akan Allah yasa safwan ya fadi jarabawar . Be dawo gida ba seda laasar,agajiye yake sosai,yana shigowa da sanaya yafara cin karo wacce ta kureshi da ido kamar ace ar ta arta a guje. Murmushi yayi ya karasa gurinta yace. "wannan kallon fa mrs safwan,ko duk na tsoron ince naci exam dinne?" Shuru tayi tana me ci gaba da kallonshi,abun dariya ya bashi,dan ya fahimci har lokacin a tsorace ma take. wuceta yayi abunshi,sede duk inda ya gilma idon sanaya na kanshi,tana binshi da kallo. Wanka ya shiga yana fitowa still kallonshi takeyi,ajiye bokitin yayi yana murmushi ya nufeta. Yana zuwa janta yayi zuwa dakinshi,se tirjewa take ita bazata bishi ba, A haka har suka shiga dakin. zama yayi kan kujera,sannan ya dorata akan cinyarshi akaro na farko. Ware ido kawai sanaya takeyi, Hannu yasa ya gyara mata gashin da ke kokarin rufe mata fuska,sannan ya janyota ta kwanta a jikinshi yasa hannu yarungumeta. "Inaso ki bani aron hankalinki,kinji sanaya ta"cewar safwan cike da tattali. Kai kawai ta gyada masa,hakan ne yabashi damar ci gaba da cewa. "Abunda na miki rannan ba zalinci bane,horo ne,na mikine sabida kibarni na huta,inaso kicire tsoron aykin da nake nema a ranki,kimin addua,ko so kike in samu aykin a kasheni gurin yaki?" A zabure ta mike daga jikinshi tasa hannu ta rufe mishi baki tana kuka take fadin. "Bazaka mutu ba hero,pls kadena fadin abunda ze tarwatsa zuciyata,wlh bazaka mutu ba"ta karasa maganar cikin matsanancin kukan da yaba safwan matukar mamaki. Cikin kankanin lokaci har ta fice daga natsuwarta sabida kuka,yayi rarrashi amman taki yin shuru,budar bakinta se sake cewa tayi. "Bazaka mutuba,ya kakeso inyi da rayuwata bayan ranka,iyayena da dangina sun gujeni sabida kawai inasonka,banida kowa sekai,zuciyata ta zabi rabuwa da kowa inde zan kasance tare dakai,bana burin kabar duniya,batare da kai da daddyna kunso juna ba,Safwan ina sonka,ina kaunarka,banuda buri a rayuwata da yawuce naji irin wainnan kalmomin daga bakinka" Tana kaiwa nan ta mike zata bar kan cinyarshi,wawiyar rungumar da yayi matane tasa ta tsorata,dan ta aza dukanta zeyi. Runguma yayi mata bata wasa ba ji yakw kamar zaa kwace masa ita. cikin hawaye yace. "Sanaya ni mutum ne me tsananin kishi,Keda bakinki kin bani tabbacin kin kwanta da wasu mazan,wannan abun shi yake wahal da zuciyata,bawai sonki ne bana yiba,kishinki ne yafi son da nake miki,kiyi hakuri sanaya,komai ze daidaita,amman dad dinki honestly speaking bana sonshi bana kaunarshi kamar yadda kinfi kowa sanin shima baya kaunata,dan gashi kin da yakemin harke ya shafa" Shuru kawai sanaya tayi dan bata da abun cewa,se addua. haka safwan yayta rarrashinta har ta dena kukan da yawancinshi na shagwabane. mikewa yayi domin yasa kaya,bin jikinshi sanaya tayi da kallo,gaba daya a murde yake cikinshi har wani layi layi yayi, Mikewa tayi tana murmushi,ta isa gabanshi,dariya tafara yi,cike da mamaki yake kallonta,yanaso yaga abunda takewa dariyar, Ba komai takewa dariya ba,se ganin yadda kirjinshi yayi tumbul tumbul kamar na mata. Beyi auneba se ji yayi ta taba da hannayenta tana dariya tace. "Wai hero meyasa nonuwa suka fito maka kai ba mace ba,jikinka duk ya wani murde ya tattare,tsokoki ko ta ina curi curi,"ta karasa maganar tana dariya still tana ci gaba da tabawa. Ajiye rigar hannunshi yayi yasa hannu ya matso da ita jikinshi,shima dariyar yake,hannu yasa akan mazaunanta duka biyun,yace cikin muryar da sanaya bata taba sanin yana da ita ba. "wlh nima inada tambayoyi da yawa,wai meyasa mazaunanki sukayi manya haka,kuma koya mutum ya taba se yaji hannunsji kamar ze bace aciki dan laushi,sannan kema ga kirjinki acike sosai,wai meye sirrinne"yayi tambayar sanda hannunshi ya sauka akan kirjin nata. Da gudu sanaya ta sakeshi ta ranta ana kare tana zaro idanuwa Dariya sosai abun yaba safwan,karasa shiryawa yayi yafice tsakar gidan,inda yasameta ita da rahama,tana ganinshi ta boye bayan rahama tana dariya. Shima ita yayi yasamu guri ya zauna yafara cin abincinshi. Haka rayuwar taci gaba da tafiya,safwan da sanaya,akwai fahimta a Tsakaninsu,sede koda wasa be taba shaawar hada shimfida da ita ba. Jarabawarsu ta fito inda cikin nasara yasamu yaci,dan haka yanzu shirin tafiya training yakeyi,sanaya duk tabi ta damu kanta. Acan gidan gomnati ko tuni munaya ta amarce sa angonta shaheed,shagali akayi bana wasa ba amarya ta tare agidanta daya gaji da haduwa. gomnane yayiwa shaheed auran huce takaici da munayar,bawai dan shaheed din ne ya bukata ba,amman girman dadsyn ne yasa ya amshi auran da hannu bibbiyu. Kamun safwan yatafi training seda yayi musu cefanan abincin da zasu ci har yadawo,sannan yabarmusu dubu goma a hannunsu,wanda yasamu kudinne ta hanyar faskaren dayakeyi ba dare ba rana. Cikin kuka suka rabu da sanaya,kuka bana wasaba,dakyar rahama ta rarrasota suka dawo gida dayake har NDA din suka rakashi muje zuwa Surbajo for life. January 30 at 9:59am · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *35-36* tunda safwan ya tafi sanaya ke cikin matsananciyar damuwa babu abunda take yi sai kewar shi gashi abubuwa sun taru sun mata yawa,Rahma bata zama a gida sabida makaranta da take zuwa,inta tafi sanaya ita kadai ke xama a gida ba abokin fira,gashi safwan ko wayar shi ta kira bata fiya samu ba,acikin dan kankanin lokaci sanaya har tayi baki ta rame Shi ma anashi bangaren safwan adan zaman da yayi tare da sanaya sosai yanzu yake jin kewar ta,musamman idan dare yayi,yana dai kawai daurewa ne a matsayin sa na namiji,amma tabbas yana kewar tattausan jikin sanaya musamman idan tana mashi shagwaba,Abokan nanshi sun sha tambayar shi akan meke damun shi sai dai yace ba komai,yana son kiran sanaya a waya,amma yasan idan ya kira da rigima zasu rabu,shiyasa sau tari ya gwammace ya kashe wayar shi, Toh!yau dai tura ta kai bango,domin yau shi da kanshi ya ke son yaji muryar sanaya,don haka Allah-Allah yake su tashi a wurin training domin ya kirata a waya Sanaya ce duke a gaban murhun itace,tana hura wuta da bakin ta sabida iccen yaki kamawa,idon ta gabaki daya yayi ja sabida hayaki,karar wayar tace ta dauki hankalinta zuwa daki,domin ta jima ba taji karar wayar ba,don danginta babu mai neman ta,safwan kuwa sati biyu kenan tana neman wayar sa amma bata samu ba Da kamar kar taje ta dauka,sai wata zuciyar tace taje ta dauka,mikewa tayi ta nufi daki,inda wayar keta kururuwa a kawo mata agaji,sanda taga sunan mai kiran nata har tuntubi tayi,ba kowa bane face safwan,hannunta har rawa yake yayin danna abun amsa kiran. "my mrs "cewar safwan cikin wata sassanyar murya,tunda sanaya taji muryarshi wasu hawayr masu dumi suka fara zubowa akan fuskar ta Tuni ta rushe masa da kuka,da kyar ta iya furta "My Hero................"maganar ta kaqare saboda kukan daya fi karfin ta Safwan dama yasan za'ayi haka,lumshe idon sa yayi yana jin yadda kukan sanaya ke taba zuciyar sa,bai yi gaggawar hanata yin kukan ba sanda ya bari tayi mai isarta,sannan yace,"oya fada min maiyafaru? kike kuka"cikin shagwaba sanaya tace ba kai bane "Nayi me?"cewar safwan cike da kulawa,kara shagwabewa sanaya tayi tace "ka tafi ka barni Rahma ma sai tayi tafiyar ta makaranta,tun safe sai karfe shida zata dawo,Ni kadai ake bari a gida,gashi wannan itacen ban iya amfani dashi ba kullum saina kone,kuma hayaki ya cika min ido,ta karasa maganar cikin kuka Tausayin ta ne ya kama safwan tabbas ya yarda sanya tana son shi,don da bata sonshi bazata jure duk wata wahala akan shi ba,a jiyar zuciya yayi sannan yace "kina aon na dawo ne?" da sauri sanaya tace kamar wani zai riga ta"eh wallahi ina son kadawo" "Inna dawo me zaki min?"safwan ya fada cikin sigar san dagawa sanaya hankali,"zan maka duk abunda kake so" "duk abunda nake so kika ce fa?"ya tambaya "eh wallahi My Hero zan maka duk abunda kake so indai zaka bari wurin kazo mu xauna tare a gida" Dariya safwan yayi kana daga bisani yace "har boobs dinki zaki barni na taba? " Sanaya jin maganar tayi tamkar saukar aradu,cikin rawar murya tace "a'a kayi zamanka kawai ba saika dawo ba tun da dama zalumcin daka koyo zaka zo kamin,ni dama shiyasa tun farko ban so kaje wurin ba"ta karasa maganar cikin kuka Dariya safwan yake yi acan inda yake zaune kamar zai kife,don kuruciyar sanaya na daya daga cikin abunda ke burgeshi da'ita,da kyar ya iya daurewa ya daina dariyar,yace "Haba mrs safwan nine fa?" "kai din" "aikuwa sai na dawo tunda bakya son zamana anan" "wallahi karka dawo kayi zaman ka" "Ahap ina nan tafe yau da daddare,haka dai ja'inja ta barke tsakanin sanaya da safwan yana sai ya dawo,ita kuma tana bazai dawo ba.shi ko safwan abun nema ya samu,haka yasa sanaya a gaba da tsokana,akan cewa yana nan tafe yau dinnan,ita kuwa sanaya kuka take har da majina akan bata son ya zo,safwan bai kyale sanaya ba,sai da yaga da gaske kukan take sannan ya kyaleta,suka shiga hirar arziki,be kyaleta va,sai da ya tabbatar duk wata damuwar da take ciki ta yaye,sanna suka yi sallama akan zai kirata da daddare Muje zuwa Surbajo for life February 18 at 9:48pm · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *NA DAWO DA YARDAR ALLAH,SEMUN GAMA* *Dedicated to My sweetheart Fatima Abubakar Radda(am sorry )* *37-38* Wuni sanaya tayi cikin firgici game da zuwan da yace zeyi,haka ta dunga abu salalo salalo. Koda Rahama tadawo daga makaranta haka ta sameta,bata tambayeta meke damunta ba dan tasan,kwanan zancan. Tun sanaya nasa ran zuwan safwan har tazo ta cire,dan tsawon sati guda kenan bezo dinba. Anashi bangaren safwan,ko dama tsokanarta yayi ba zuwan zeyiba, Haka rayuwar taita tafiya,har zuwa lokacin dasu safwan suka kammala taining kuma Allah ya bashi saa aka daukeshi. Be fadama sanaya ba,dan haka basusan ze dawo ba. Rahama ta tafi mkrnt,se sanaya kawai agida,ta gama girke ta shiga wanka,safwan yashigo gidan cikin sanda. karar ruwa yajiyo a bayi,sannan ga zanin sanaya rataye jikin kofar bayin hakan ne yasa yagane ta shiga wanka,ne. Kofar bayin yaje cikin sand,yasa hannu ya dauke zanin ya wurgashi,cikin ruwan dake gangarowa ta cikin bayin zuwa kwatar da suke wanke wanke da wanki. Yana wurgashi,yayi sauri ya shige dakinsu. Sanaya ta gma wankanta fes,ta mika hannu dan daukar zanin ta,sed wayam bashi ba alamar shi. Lekawa tayi seta ganshi yashe akasa take ta fahimci iska ce ta yardar mata dashi. bude kofar tayi,hannunta rufe da gabanta,ta falfala da gudu zuwa dakinta,danta suturta jikinta. Tana shiga ta nufi akwatin da safwan yase mata tana zuba kaya. zata duka kenan taji anriko mata boobs dinta ta baya,cikin wani salon da ya haddasa mata lumshe ido,arazane ta bude ido ta fara kokarin kwatar kanta sede safwan ba rukon wasa yay mata ba, Zata kurma ihu ne taji muryarshi,can kasan makoshi,yana fadin. "sweet wife nine" da sauri ta juyo tana kallonshi,sosai yayi baki ya rame gashi ko sajen fuskarshi yanzu babu,ya aske,binshi take da ido. yayinda shi kuma wata zazzafar shaawartace ke dawainiya,dashi,yayi danasanin yarda zaninta. Dan yasan ganin surartane yajefashi cikin yanayin da yake ciki. daukarta yayi cak yanufi kan gado da ita,se alokacin sanaya ta tuno ba kaya jikinta. Ayko nan fa dambe ya kaure tsakanin sojan da ya hango dan boko haram,da kuma talakan da ya hango,ana rabon kudi,kunga ko kowa zeyine bakin rai bakin fama. "Don Allah kabarni,naje nasa kayana,ba komaifa ajikina"cewar sanaya cikin kuka dan ta Kasa kwace kannata. "au da gaske ba kaya ajikin ki ?"cewar safwan sanda yasa hannu yana shafar hips dinta. Runtse ido tayi jikinta na bari,cikin kuka take cewa. "iskanci zakamin ko?" Lakuce mata hanci yayi,gamida nutsa fuskarshi tsakanin boobs dinta yace. "Babu kalmar iskanci tsakanin miji da mata,sede soyayya" "to ay kai baka taba sona ba,taya soyayya zata wanzu tsakaninmu?"cewar sanaya cikin raunanniyar murya. Hannu yasa ya dago kanta,ta yadda hakan yaba hancinsu damar haduwa,yafurta a hankali. "inasonki sanaya,son da bayan rahama da ummana babu wata diya mace dana taba yiwa irinshi" Kauda kanta tayi gefe ta furta, "baka sona hero,wlh baka sona,jikina kakeso,dan ka ganshi bayyane a fili,don Allah karka keta haddina matukar babu sona A ranka,me sona nyiwa tanajin kaina pls kabari har kafara sona,na rokeka" Ganin zata sauya mishi aniya ne yasa yayi hanzarin hada bakinshi da nata ya shiga ayka mata sako. Tun tana basarwarnan,har yazamto abun na mata dadin da yasa ta shiga mayar masa da martani. Sosai safwan ya iya sauke mace online,dan haka tuni sanaya ta lula bakin gaba, Har wani rukoshi take idan yadan yunkura,seda safwan ya tabbatar,da cewa she is ready to receive him,sannan ya cillar kwallonshi araga,cikin incewar Allah bayan ya karanta adduar da manzo S,A,W, ya koyar damu. wayyo Allah sanaya,wata razananniyar kara ta saki,gamida manna masa cizo a kirji,wanda shima zafin d yajine na cizon yasashi bude kofar,da karfi batare da yasani ba. Tun tana kukan najin muryarta harta koma ko motsi bata iyayi,tanajin yadda yake mata dalla dallah,hawaye kawai kebin fuskarta, Shiko garujen,cinye du,besan zuru ba,yi yake kamar ya samu inji,memakon ajiyo kukanta se kukanshi akeji,dan besan a inda yake chatting ba,facebook ne ko whatsapp,ko kuma togo? Fans abashi amsa. Muje zuwa gobe da safe da yardar Allah zaku kara ganin posting. Nasan zakuce surbajo ta sauya, sauyin na dolene,kumin afuwa. Surbajo for life. March 6 at 5:57pm · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Masoya na kuyi hkr don Allah, ina gani sakwanninku akoda yaushe na cigiyata da littafina,kuma inajin dadin hakan sosai,shiyasa na dauki aniyar ganin nayimasa zama daya domin ku,surbajon ce yanzu ba irin ta da ba,nauyi ne yadan karu wanda ke cinye duk lokacina dan haka kuyi hkr,bayan Sallah da yardar Allah akwai show me dadi,* *Zanyi amfani da wannan dama domin mika gaishe gaishena wanda suka faru abaya.* *Mrs mahmoud ina miko taaziyata game da rasuwar mahaifinki Allah yajikansa yasa aljanna ce makomarsa,Esha mustapha mama ta tafi mama ta dawo,Allah yajikan mahaifiyarki yasa aljannace makomarta,little mama da muka samu kuma Allah ya rayata bisa tafarkin tsira,Hafsat dahir jos Allah yajikan babyn mu ke kuma Allah ya baki lfy,ya maida alkhairiFiddah sokoto ta ayman bada kanki asare tunda ayman ya koroki yanzu iro ya dauka to ina miki adduar samun dauwamamman zaman lfy fiye da yadda ummu aymana ta samu agidan ayman,asha shayi lahiya ,kuna da yawa wasu har na manta sunan da akwai mutane biyu da suka haihu kwanaki a group dina na zahra surbajo novels,i think jamur yar baba na ciki,da maman zainab data haihu yarinyar ta koma,duka ina miko sakon taaziyata da taya murna,ngd* *mmn gidado,inna ibrahim kime,billyn shantali,minash,jidda abbas,hassan atk,salbiyya adam,fatima radda,esha mustapha,hafsat dahir,fidda,mrs mahmoud,salma b etc,you mean everything to me,* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *39-40* Hon suke mata akan ta tashi akan hanyar amman ina kojinsu batayi,ganin haka ne yasa sojoji fitowa dauke da bindigu sukayi setinta da su domin atunaninsu yar kunar bakin wake ce. Ganin bindigane yasa rahama dawowa hayyacinta,akidime ta ruga da gudu gurin sanaya da nufin daukarta su gudu. Bin ta sojojin sukayi dan koya mata hankali,dago sanaya tayi,wanda hakan yay daidai da waigowar me girma gomna dake cikin mota yana kallon meke faruwa. Ko a mafarki yaga sanaya dole ya ganeta sabida son da yake mata yafi gaban wasa,jikinshi har bari yake gurin bude motar ya fito, Da gudu ya nufe su yana kiran. "my baby sanaya" A razane sanaya ta farka tana bin shi da ido,hannu ta mika masa kamin ya karaso ta sake sumewa,yana zuwa rungumeta yayi yana kukan kiran sunanta, Se alokacin ya lura da cikin jikinta,ga jini dake zuba akidime ya dauketa sukai mota rahama nabin su abaya. Kai tsaye asibiti na musamman suka nufa da ita wanda tunkan su iso anyi waya dan haka komai ready sukawai ake jira. Ana gungurata agadon daukar marasa lafiya daddynta rike da hannunta yana kuka har suka karaso kofar labour room. dakatar dashi likitocin sukayi awaje sannan suka shige da ita. Duk abinda yadace shi sukai mata,yayinda awaje daddy yakasa tsaye ya kasa zaune kuka yinshi yake kamar yaro,dan wannan ne karo na farko daya taba ganin sanaya cikin mawuyacin hali. Cikin ikon Allah da taimakon kulawar likitoci ta haifo yaranta guda biyu duka maza,masu kama da mahaifinsu. Sede rayuwarsu na cikin danger dan babu isasshen jini ajikinsu daga su har mahaifiyarsu wacce batasan inda kanta yake ba. Sanda likitoci kema daddy bayani komawa yayi kamar dutse dan tsananin tausayi,taya zaace jariri ba jini,rasa abun yi yayi seda likitan ya sake mgn. "your Excellency ba bu isasshen lokaci zamuje lab aduba in akwai wanda zeyi daidai da su se asa musu" "ban amince asa musu jini wani ba,jikokina ne fa,muje aduba nawa in zeyi"cewar gomna yana share hawaye. Koda akaje lab jininsa donor ne dan haka beda matsalar bawa kowa,seda aka dibi leda hudu ajikinshi, , biyu akasawa sanaya daya daya kuma akasawa babys din duk da basu shanye shi duka ba. Seda jinin ya kare sannan aka fito da babies din da se kuka suke. Rahama rasa inda zata zauna tayi don murna yayinda daddy shima baa barshi abaya ba gurin murnar samun karuwar. Sanaya se magrib ta farfado,sanda tai arba da daddy kuka ta rushe dashi,tana mika masa hannu da sauri yaje ya kama hannunta yana shafa kanta. Cikin kuka take fadin. "daddy ka yafemin,wlh son mijinane yafi karfin zuciyata kayi hkr" "haushin ki kawai nakeji baby na amman na jima da yafemiki,ki kwantar da hankalinki kinji,"cewar daddy cikin sigar rarrashi. "daddy nagode,saura safwan shima ka yafe mishi don Allah daddy" "taya zan yafewa wanda besan darajarki ba,kinsan aya na ganki kuwa inda ban zoba kinsan meze faru,no sanaya babu yafiya tsakanina da safwan he hurt me alot,and yoo too," Zata sake mgn ya zare hannunshi anata ya nufi gadon jariran dake ta faman cilla kafafunsu sama. Sosai yakejin son yaran azuciyarsa,duk da kamannun dasuke da safwan hakan be hanashi sonsu ba. Waya yayi gida ya sanar da mahaifiyarta da mubina,baa jimaba suka iso asibitin cike da kewar yar uwarsu. Tunda suka rungumeta sun kai minti goma basu sake ta ba dan murnar ganinta. Rahama ko nacan wajen dakin tana ta faman kiran safwan wanda ta gagara samunshi. Kwatsam se gani tayi yana kiranta,da sauri ta dauka tana fadin. "haba yaya ina kashiga irin haka,nemanka nake kamar zanyi hauka,yau wlh saura kiris sanaya ta mutu," Ji tayi alamun faduwa yayin da ta jiyo hayaniyar mutane awayar ana fadin. "Ku kira ambulace sagent safwan ya fadi," Agigice rahama ta mike tayi cikin dakin tana kuka , Arazane sanaya take binta da kallo inda ta kasa daurewa tace. "sister lafiyarki kuwa?" Cikin kuka tace. "aunty yayane nakirashi ina fada masa abinda ya faru dake nace yau saura kiris ki mutu be jira na karasa ba se ji nayi hayaniya agurin ana fadin wai akira ambulace ya fadi"ta karasa maganar tana kuka. wata irin kara sanaya tayi itama ta koma ta kwanta sharab,agigice ayi kanta sede ina ba numfashi jikinta. Daddy gurin gudun kiran doctor har faduwa yayi sabida rudewa . Doctor na gaba daddy na binshi abaya gudu suke amman daddy har hankadashi yakeyi,dan ya raina gudun nasa. Doctor be jira wata wata ba yasawa sanaya oxcygen, Duk wani taimakon gaggawa shi aka mata,inda akasamu ta farko,sede fa ta dage ala dole se ankaita gurin mijinta,hankalin daddy in yayi dubu ya tashi,ko kadan taki jin rarrashi,ita sede akaita gurin safwan. Shiko safwan yanacan rai ahannun Allah dan dan ji yayi rahama tace mishi sanaya ta mutu. Koda aka kaishi asibiti babu sauyi,dan ko numfashi bayayi. Rahama kuka tasa su daddy agaba itama tanayi akan ataimaki dan uwanta. Akaro na farko da daddy yaji tausayin wani abu da ya shafi safwan, Wayar babban sojan dake kula dasu safwan din ya kira,inda ya bukaci da asako safwan ajirgi zuwa kaduna yanzu yanzu. Cikin awa biyu an iso da safwan kaduna,karkashin rakiyar sojoji,ciki harda babban sojan. Ambulance ce ta daukoshi zuwa asibitin garden city dake kaduna. wayyo sanaya jin ance an iso dashi da kyar ta iya mikewa rahama da munaya suka riketa zuwa inda aka doroshi akan gadon daukar marasa lfy,yayinda duk jikinshi an daureshi da belt, Jiki na bari sanaya ta dora hannunta akanshi tana fadin, "hubby pls katashi,karkaimin haka,ban mutuba gani nan da raina harda yaranmu katashi kazo muje ka gansu"ta fadi tana kuka. Hmmm love magic ya wuce wasa,se gani sukayi safwan na motsi,gamida tari Da sauri aka karasa dashi dakin da yadace,wanda tunkan ashiga ya bude idonshi yana kallon sanaya hawaye nabin idonshi. Daddy komawa gefe yayi yana kallon sarautar Allah,danshi ko a film betaba ganin so irin wannan ba,se ayau ya yarda babu me rayuwa cikinsu in ya rasa dan uwansa,sosai ya gamsu da son da sukewa juna. Sanaya fafur taki daukar yaran bare ta gansu wai acewarta se safwan ya miko mata da hannunsa atare zasu gani Muje zuwa anjima. Surbajo for life. May 9 at 11:44am · Public *SANADIN KIDNAPPING* *ZAHRA SURBAJO* *Allah abin godiya masoya abun alfahari,kamar yau na bude group dina na facebook segashi yanzu kimanin mutane dubu dari da daya da dori ne aciki,ina alfahari daku ahlin group dina na facebook mazan ku da matanku,da zan iya lussafoku da ba abinda ze hanani yin hakan,daukacinku masu hankaline aciki,bakwa fada ko fadin bakar mgn wlh na shaideku,Allah yazaunar da masu auran cikinku lfy agidajensu,samari Allah ya kawo mace tagari,yanmata Allah ya kawo miji na gari,zawarawa kui hkr kui addua ga azuminan ya gabato,ku roki Allah duk damuwa ze yaye Allah ya aurar daku ga mazajen da suka san darajarku,maza abar ruwan ido mata adena jan aji(wulakanci),dan so nake kamun babbar sallah duk na aurar daku na huta ,Allah ya hadamu a aljanna cikin aminci,* Facebook@zahra muhammad surbajo Instergram@zahra_surbajo1 *Note:bana chartting inbox a facebook dan ko yanzu sakwannin dake jiran na karantasu sunfi dubu biyu,akwai wanda tunda na fara rubutu suka rubuto amman har yanzu Allah be bani ikon isa gurin ba,amin afuwa don Allah,wlh idona har ciwo yake in na fara dubawa,nafi yin chartting instergram,ko whatsapp,,taku har kullum surbajo* *Dedicated to Fatima Abubakar Radda* *41-42* Haka sukai jugum jugum suna jiran fitowar likita, Ba a basu damar ganisa ba seda ya warware tas,sedan abinda baa rasa ba sannan likita ya amince su ganshi. Sanaya ce agaba,suna shiga suka ganshi andan jingina masa filo abaya yadan kwanta,shigowarsu ce tasa ya zabura da sauri ya diro daga kan gadon ya nufi sanaya dake dingishi ta nufoshi, Da sauri ya karaso gurinta,ya duka agabanta,inda yasa hannu yadan daga zanin dake jikinta dan yaga me yasa sanayarsa dingishi,bega komaiba dan haka dago kai yayi yana dubanta,itama shi take kallo yayinda kowa na gurin su suke kallo. Idonshi ne ya sauka kan cikinta inda yaga babu komaiazabure ya mike yana fadin. "No!!!!No!!!!!!," Rungumota yayi jikinshi da karfi yana fadin. "Ina babyn mu yake sinaya,?me ya sameshi ko shiyasa rahama ta dauka kin mutu ne,?tell me," Rungumeshi tayi itama tana murmushi gamida hawaye tace. "hubby babynka be mutu ba,be salwanta ba,ammade badan taimakon Allah ta silar daddy ba da dagani har su mun zama yan gari a lahira"... Jan hannunshi tayi zasu fara tafiya,dukawa yayi ya dauketa cak dan baze juri ganin tana dinshi ba, Adaidai kofar fita suka ci karo da daddy dake tsaye yana kallonsu,safwan kallonshi yake cike da mamakin ganinshi agurin. Ahaka suka wuceshi,zuwa dakin da jariran suke. Sanda safwan yay arba da yayan sa kadan ya rage ya suntuma sanaya da kasa dan ya kosa ya isa garesu. Wayyo dadi,rasa inda zesa kanshi yayi dan farinciki dukawa yayi ya kwasosu gaba daya jikinshi,yana kuka,yaran ko sunyi kuri suna binshi da ido,mikawa sanaya yayi su yana fadin. "sinaya bantaba son abun kwatankwacin son da nake mikikeda yaran nan ba,inkika cire iyayena da rahama,sinaya babu abinda nakeso sama dake," Rungume juna sukayi suna kukan murna rungume da yaransu. Rahamace ta karaso gurin ta rungumesi itama tana fadin. "Allah mungode maka daka turo mahaifin sanaya ya ceci rayuwar sainnan family dayanzu wannan farincikin bamu ganshi ba". Waigowa safwan yayi yace. "bani labari mana rahama me yafarune?" Ba bata lokaci ta kwashe komai ta fada masa duk yadda akayi. Wasu hawayene kebin fuskarshi,bin yaran yake da kallo cike da danasani,wai jinin wanda ya tsana fiye da kowa yau shine ya gauraya dana yayansa,wanda da taimakon hakanne yasa suke araye yanzu,wani kukanne yasake kwace masa. Mikewa yayi ya nufi kofar fita inda ya nufi gurin da daddy yake tsaye. Yana zuwa zubewa yayi akan guiwowinsa yana kuka,yakasa mgn. Daddy binshi yayi da ido yayinda cikin zuciyarshi godiya yakewa Allah da ya bashi siriki kamar safwan, Sunfi minti talatin ahaka safwan bedena kukaba kuma yaki mgn,shima daddy haka. Daddy yagaza jure ganinsa yana kuka besan sanda ya mika hannu ya dagoshi ba da sauri safwan ya shige jikinshi yana kuka. Rungume juna sukai shima daddy harda kwalla seda ya fitar. Su sanaya da suka fito ganin abinda ke faruwa sosai sukaji dadi, Safwan zeyi mgn daddy ya rugashi da cewa. "komai ya wuce,kayafeni nine ummul abaisin faruwar komai,don Allah ka yafemin" "tsakanin uba da da babu neman gafara daddy komai kayi akaina daidaine"cewar safwan cike da kulawa. Ranar de kowa bakinshi yaki rufuwa,dan murna,. Ba abunda yaba kowa mamaki se sanda safwan ya gama yin huduba wa yaran,aka tambayeshi sunansu. Yace "dukansu sunan daddy na sa musu,dan shine sunan da yafi dacewa dasu su duka sabida muhimmiyar rawar da ya taka arayuwarsu," Daddy murmushi yayi,najin dadi. Aranar aka sallami love birds daga asibitin. Kai tsaye gidan su sanaya aka nufa da ita,dan mummy tace se anmata wankan jego. Safwan be musa ba,haka aka tafi da ita,can din harda shi da rahama. sanaya farincikinta be faduwa yau gata ta dawo gidansu bayan lokaci me tsayi. Sosai mummy ke kulawa da sanaya har akayi suna na gani na fada,safwan raguna hudu yayi kokarin yankawa yaran nasa da duka albashinshi. Babu yadda daddy beyi dashi ya bari ba amman fafur yaki. Haka akayi taro aka watse. Da yake safwan anbashi hutu gurin ayki hakan ya bashi damar wuni gidan daddy gurin sanyin idanuwansa. Se dare yake komawa gida. . Shaheed da,hisham ake kiran yaran,wanda kullum suke gurin daddy matukar yana gida. Daddy yayi yayi da safwan akan ya koma gidan da yabashi amman fafur yaki yace da kanshi yakeso ya gina gida. duk wata gudummawa in daddy yayi yunkurin yimasa amman fafur yaki amincewa. ganin baze amince bane yasa daddy batare da sanin safwan dinba,yasa aka kara masa girma sosai agurin ayki inda yake daukar albashin daya tasarma milyan guda. Saɗwan sosai yayi murna dan shi ya aza kwazanshine yasa aka dagashi Tuni yasai fili,dan haka ko batun komawar sanaya gida beyi,dan so yake se yagama ginin su tare agida. Sanaya tuni tayi arbain,bame ganinta yace tayi aurema bare akai ga batun haihuwa Sosai mummy ta gyarata,haka munaya ma baa barta abaya ba gurin kulawa da sanayar Tuni safwan ya koma bakin ayki sede waya kullum suna makale awaya shida babynsa. Yau watanni hudu kenan da haihuwar sinaya,tuni ginin safwan ya kammala,har saukar al'qurani anyima gidan,furnitures kawai ya rage azuba shima yafiso suje shida sanaya ta zaba. Yau da kewar sinaya ya tashi dan haka tun safe ya shirya ya rubuta pass da yake babbane ba bata lokaci aka bashi. Da azahar ya iso kaduna acikin motarshi,range rover wacce aka bashi sanda ya samu karin girma. Sanda ya iso gidan ba kowa daga masu ayki se sinaya,dan har yaran suna gidan munaya ta turo an kwashesu,mummy kuma taje taro abuja,daddy bayanan yana office. A falo ya sameta,da gudu ta nufoshi ta rugumeshi,dagata yayi cak yana shinshinata. Kukan shagwaba ta farayi masa. "oh baby ya akayi kuma,bakisan kin girma bane yanzu,kefa mamace" Turo baki tayi gaba gamida fara dukanshi abaya tana fadin. "shine tunda akayi kwana Ashirin da haihuwa baka zoba se yau wata hudu,wallahi mun bata ni saikeni" da gudu ya haura sama da ita inda dakinta yake. Kan gado ya dorata sannan yabi bayanta shima yadan kwanta ajikinta yace. "to me zanzo nayi,kullum daddy se ya kirani video call ya nunamin su twins,ke kuma muna waya dama de innazo zan dan samu abun tabawane to danazo,to kedince tunda kika haihu se leeking kike,sekace damuna"yakarasa maganar cikin tsokana yana mata dry. Kuka tasa mishi tana tureshi. da sauri ya hade bakinsu guri guda ya shiga mika mata sako. Wayyo abunka da anjima baa haduba. Yi suke kamar zasu cinye junansu.tuni sun jima da rabuwa da suturarsu. seda suka samu biyan bukatar juna sannan hankalinsu ya kwanta,kwance suke sanaya ta dora kanta jankirjinshi,se ajiyar numfashi sukeyi dago fuskarta safwan yayi yana murmushi yace. "komai naki ya sauya baby wlh har kinfi da dadi,meye sirrin," runtse ido sanaya tayi tana dariya tace. "jego" "Ayko inde jegone ke kawo hakan zan dage wajen ganin jego beyi nusa dake da yakai shekaru biyu ba" Duka takaimishi tana dariya. wanka suka shiga tare,inda sosai ya nuna mata kulawa. Bayan sun fito suka shirya,safwan da kanshi yamata kwalliya,sannan ya jata suka fice daga gidan, ba kadan sukai kyauba,abun burgewa. gurin saida kayan furnirures yakaita ta zabi komai aka hada guri guda,akasa a mota,yabasu key din gidan,yace suje su shirya musu kamin dare. daganan gurin kayan abinci ya nufa yasiya komai shima Ya biya yasa suka kai masa gida. sannan suka nufi gidan munaya,tana ganinsu tace cikin zolaya. "marasa kunya wato kun biyo yayanku ko?" Dariya safwan yayi yace"haka yake yayarmu ta minti biyar" Dariya dukansu sukayi. Sundan jima gidanta sannan suka kwashi yaransu zuwa yawon shan iska. Sosai sukaji dadin fitar safwan manne da sanayarsa. Da magrib,suka isa tsohon gidansu gurin rahama wanda tuni safwan yayiwa gidan kwaskwarima babu me cewa shine na da Sosai rahama taji dadin ganinsu su twins se nan nan take dasu. Basu jimaba,aka kirashi awaya cewa komai ya kammala na gidan,dan haka mukewa yayi yasa rahama ta dauki abinda takeso,suka rankaya gidan. wayyo aljannar duniya,komai na gidan ya hadu,ba abinda yafi basu shaawa irin dakin su twins yadda aka kawatashi da kayan wasanni. Rahama harda kukanta sanda taga duniyar da Allah ya sauya musu. Tuni yasa aka kawo kayan abinci,dan haka sanaya da rahama kitchen suka fada suka hada abinci me rai da lafiya. Can gidan su sanaya ko jin shurune yasa daddy kiran safwan anan ya shaida mushi aysufa sun tare agidansu sosai abun yaba daddy dariya,fatan alkahairi yay musu. Rayuwar tayi dadi duk kunci ya yaye Allah kenan me yanzu yanzu. *.Alhamdulillahi rabbil alamin* Anan sanadin kidnapping yazo karshe ,duk inda nai kuskure Allah kayafemin inda nai daidai Allah kabanu ladan. Semun hadu cikin sabon littafina me suna *TAMBAYA* Bayan sallah da yardar Allah. taku har kullum zahra muhammad mahmoud wacce kukafi sani da surbajo.