'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* #Wannan labarin zai iya daukar wani salo na musamman duk abin da za aji ayi nazarin ba sabo bane.... Paid book 01 Yau rana ce na musamman ga Aliyu Muhammad Jadda, wato Tafida yau ranar al'ummar jahar Borno zasu tabbatar da shi a matsayin halattaccen Gwamnar jahar Borno, wanda yayi daidai da haihuwar da nayi. Kallon Nurse din nayi da take nad'e yaran na ce mata. "Macen ce babba ko namijin?" Cikin girmamawa ta ce min. "Ranki shi daɗe, Macen ce babba." Ajiyar zuciya na sauke tare da faɗin. "Ya Allah nayi tawassali da sunayenka tsarkaka Ubangiji ka bani ikon tunkarar yakin da nake shirin gudanar da ita, Ya Allah na rokeka a sarari da boye ka bani ikon yakar Aliyu Tafida har sai na kai shi kasa " Turo kofar dakin aka yi na zuba mishi idanu, ko kiftawa bana yi, "Inuwar!" Shiru yayi bai karasa ba, na kauda kaina ina kallon inda ake gyara Yaran, domin ina haihuwa sai da suka gama gyara min jikina sannan suka koma kan Yaran. Takowa yayi har inda nake zaune fuskarshi dauke da murmushi ya shafa kwantaccen sumar kanshi yana reading fuskana. Dauke kai nayi tare da cewa. "Harkalla ya faɗa!" Da wani irin sauri ya d'ago kai yana kallona. "Hala baka ji ba ne? Harkalla ya faɗa!" "A'a Hadiyyah kada muyi haka dake!" Zabura nayi wanda ban san ina da karfin na ce mishi. "Kace me? Kace me? Harkalla ya faɗa nace Tafida! Gasu can ba daya ba biyu na baka na gama!" Cikin masifar da yake dauke da ita wanda nayi imani da Allah ba zai daina ba koda kuwa kasa zata rufe masa idanu ne ya ce min. "Ke kin isa ne ki ce zaki ja dani? Saura awa uku na saka doka da oda baki isa ba wallahi, kuma ki ji da kyau babu wanda ya isa rabaki da Yarana ki ajiye wani harkalla ai kin fara kenan First Lady!" Ya faɗa yana sakar min muguwar murmushi, nima haka ce a kan fuskana. A hankali na zuro da kafata kasa, naji na tsaya daidai akan kafata. Ban ce mishi cikanka ba, na nufi inda kayana suke na cire doguwar abaya na shiga ban daki na watsa ruwa na gyara jikina,sannan na fito zuwa dakin an gama shirya Yaran. Yana tsaye akansu ba zan iya bayyana yadda yake jin Yaran a ranshi ba, amma nasani kamar yadda maza da yawa suke amfani da Yaran mace domin juya akalarta ni yanzu Aliyu Tafida yana hannuna ne da Yaranshi. Sai da na gama shiri tsaf sannan na nufi wurin akwatin kayanmu na ciro tsohuwar ajiya na nufi inda Yaran suke na ajiye mishi. "Wannan shine karshen Yarjejeniyar da muka yi, na sauke nauyin da Allah ya bani, kai ma sai ka yi adalci ka sauke nauyin da yake kanka!" Bude takardar yayi ya kalle ni dakyau. Ganin na shafi kumatun Yarinyar da take barci cikin kaya pink! Ya rike hannuna. "Diyyah me kike so na gayawa Duniya? Yau za a rantsar da ni! Yau kin haifa min Yara har biyu Diyyah ko don albarkacin Yaran nan ki hakura mu daidaita kanku waye zai rike mana su? Diyyah na taso babu uwa na sha faman rayuwa don Allah ki!" "Na rantse da Allah! Wanda babu wani sarki bayan shi ba zan zauna da kai ba, ai mun gama maganar nan tun wata bakwai baya me zai saka a dawo da shi. Tafida ka bukaci haka ni kuma na maka laifi ne? Ni da kai auren an yi bamu son juna, ni va irin matar da kake ba ne, Tafida zuwa yanzu ya dace mu fuskanci rayuwarmu Yara ne gasu nan na baka su don Allah kada mu samu matsala akan haka! Ana jirana a waje Allah ya tayaka rikon al'ummar Borno da kewayensa, Ubangiji yasa daga nan har matakin shugaban kasa. Na gode sosai!" Na juya a hankali ina jin hawaye na shirin zuba min. "Ummu me kike so na gayawa Abbana da Inna?" Cak na tsaya tare saka bayan hannu na goge hawaye da yake zuba min. "Abba adalin Uba ne, Inna dattijuwa ce me hangen nesa. Sun bani tabbacin wata rana zan tsaya na kwaci yancina amma babu wanda ya bani tabbacin zan cigaba da zama cikin kaskantacciyar rayuwa! Ni Yar mace ce, Kwantai ce sannan ni yar tuwo-tuwo ne, baka gajeruwa me sufar kwado, mummuna yar kabilar Babur...." Ji nayi ya toshe min bakina ta baya. "Ya isa haka! Ya isa haka!" Ya faɗa yana haki Idanunshi ya kad'a jajjur fuskarshi ita kanta tayi jar ne sosai. "Ki min uzuri bayan gama bikin rantsuwa zan zauna dake!" Kallonshi nayi shekeke! Dariya ya kwace min nace mishi. "Ni ce zaka zauna da ni? Ka manta ne na tuna maka? Ka manta kace baka ga ranar da zaka zauna da ni domin Sulhu ba? Ko ka manta ne ka ce min tunda Abba ya auro maka ni zaka dauke ni kamar takalmin ka ce idanu lokacin da kaji bukatar kayi ado zaka shure ni yadda kake so? Ko ka manta da cewa ni din nan dai gajeruwa jahila yar kananun mutane ce! Ni da Allah ya halicce ni ne domin kawai ka biya bukatarka baka fatan ka haɗa iri da ni! Ga mata." "Ya isa haka!" Ya faɗa da mugun karfi da yasa ni ja da baya! "Me yasa tuntuni baki fito da wannan nufin ba sai yanzu? Me yasa? Ke kiyi duk abon da kike so wallahi babu shegen da ya isa ya sani sake ki kada ki ga ina bin ki, ki tsammaci don ina tsoron ki ne!" "Ai kuwa har abada ba zan sake zama a inuwar mutum irinka ba, wallahi billahi azim na gama zama da kai kana da damar cin mutuncina daga har ranar da zaka fara aiki ni kuma zan tabbatar na baka mamaki!" Na juya zan fita ya riko hannuna. "Ba kida hankali ne?" Ya faɗa da karfi. "Daga turu nake karewar rashin mutunci!" Na fisge hannuna,na barshi sake da baki. Kuma ina fatan na bar Tafida kenan har abada, haɗiye kukan da taso min nayi sannan na gyara tafiyata a hankali har harabar asibitin motar da aka kawo ni asibiti na nufa. "Na san ni mai laifi ne a gare ki, amma ba zaki tausayawa waɗannan bayin Allah ba? Basu da laifi ko ɗaya na san kin fahimci haka, don Allah kada ki sani kara jin tsanar wata mace." Dariya abin ya bani. Na juya tare da murmushi. "Sai me? Ai ba yau ka fara tsanar mace ba, ko so kake na gayawa duniya cewa Mutumin da zai zama wani abu a gare su yana jin tsanar Uwar da ta haife shi?" Rintsa idanunshi yayi ya bude a kaina yana kallon yadda na juya abina, zan bar Tafida na har abada amma dole ya fahimci girma da soyayyar Uwa ya gane cewa ita uwa ba abin yarwa ba ce. Kamar wani gigitacce ya riko hannuna yana faɗin. "Gaya min me kike so nayi?" Shiru nayi kafin na tura baki don da dama ya zama dabi'ata na watsa hannuna na ce mishi. "Ohon ka, duk abin da ka gadama kayi Tafida. Kai yanzu ai gwamnatin ne idan kaso zaka iya sakawa a kashe ko a kyale rayuwarka ce ba tawa ba!" Na fada zan juya ya riko hannuna kamar zai zube a ƙasa. "Gaya min me zanyi na sha azabar rashin Uwa kada Yarana Tarihi ya maimaita kanshi!" Dafe kirjina nayi da naji suna zuui-zuui wafce hannuna da ya rike nayi tare da nufar motar da sauri n shiga ya maza ya rike ni. "Tafida wallahi idan baka kyale ni sai na falla maka mari!" Na fada da kausassiyar murya da tasa shi tilas ya kyale ni,na rufe kofar motar. "Muje mudansir!" Babu uwar da zata haifi d'a ta bar shi a ranar farkon da ta haife shi, babu uwar da zata so ta juya tabar danta a halin yana bukatar ta. Sai dai na san haka da nayi shine mafita. Jinjina kaina nayi da jikin motar har muka isa unguwarmu bolari market can karshen layin anan gidanmu yake, a hankali Mudansir ya sulala hancin motar har kofar gidanmu, sai da ya ce min. "Hajiya mun iso!" Na juya da kaina ina kallon kofar gidan, kamar yadda nasan gidan yana nan a yadda yake babu sauyi, Kawu gwani na hango ya fito yana waya. A hankali na janye idanuna daga kanshi, "Hajiya mun iso!" "Tow!" Nace a sanyayye ina jin kamar na rabu da bukar ne na haifi abu, Kawu gwani a wannan lokacin kamar fama min sabon b'acin rai ne, kamar nace mu juya sai na fasa. "Hajiya ko na maida ki asibitin ne?" "A'a Mudan na gode sosai!" Na bude motar zan fita ya kuma jefo min wata maganar fa ta sani jin numfashina kamar zai fita. "Hajiya Ummu, ina ga barin yaran nan a hannun Oga Tafida ba mafita ba ne, duk abin da zao faru a tsaya akan juna. Su bayin Allah ne da basu ba basu gani ba." Shiru nayi kafin na kakaro murmushin karfin hali da kwarin gwiwa nace mishi. "Na gode da shawara!" Sannan na bude motar na barshi da dinbin mamakina. Eh kowa ma mamakina zai ji amma ni ba wani abu ne kawai na zaɓi haka ne don rama abin da nake ganin shi ne daidai, a lokacin da Tafida yake azabtar dani hakuri ake bani ana nuna min cewa idan na kashe auren kowa zai tabbatar da bani da mafadi. "Ke ina cikin?" D'ago kai nayi na kalle shi kafin ma kauda kaina ina faɗin. "Suna asibiti!" Na furta tare da nufar hanyar cikin gidan, shanye da mamaki ya rufa min baya, "Ummu kina da hankali kuwa? Ina Yaron da kika haifa!" A matuƙar gajiye na nufi ɓangarenmu, na fada cikin gidan da sallama. "Aunty Ummu?" Yan matan da suke taya Mama aiki suka faɗa. Mama da take dama gasarar kunu ta leko tana kallon yadda nake tafiya a hankali. "Ina cikin yake?" "Suna asibiti?" "Kamar ya suna asibiti?" Ta kuma wurga min tambayar. A gajiye na ce mata. "Mama na haihu dazun da asuba!" Sake kwaryan hannunta tayi cikin mamaki ta ce. "Kin fara hadiyar kwaya ne?" "Mama nima abin da na gani kenan!" Ya faɗa daga bayana! Takaici yasa na wuce zuwa dakin Mama. "Ke Badi'a kawo min bokiti a kwashe mata ruwan zafin nan, a sake daura wani!" Ta fadi haka tana fitowa daga zauren girkin. "Mama" "Kawu gwani je ka, kada Hajiya Balkisu ta ganka." "Amma " "jeka kawai!" Ta fada tana me shigowa dakin ganin yadda na kwanta tare da lumshe idanuna yasa ta shafa kaina tana faɗin. "Me yasa kika bar Yaronki?" D'ago kai nayi idanuna cike da kwalla nace mata. "Kin ce min ba zaki bani mafita na yaki da Aliyu ba? Kin kara da cewa zaki tsaya min a gabana da bayana, don Allah Mama kada ki ce kome." Kura min idanu tayi kafin ta ce min. "Ina nufin zan baki duk wani goyan bayana amma ba ina nufi ki ajiye Yaronki a hannun shi ba, idan shine ya bukaci haka shi kenan." Girgiza mata kai nayi tare da cewa. "Ni ce na zaɓi haka!" Kura min idanu tayi ina iya hango kwantaccen b'acin rai a cikin idanunta, murmusa min tayi sannan ta juya zuwa waje, can ta dawo da kunu a hannunta ta ce min. "Tashi ki sha." Babu musu Na amsa tare da kafa kai sai da na sha rabi sannan ta ce min. "Tashi ki sauya kaya an kwashe miki ruwan zafin ganyen Dalbejiua ne da ba a samu ba yasa kika jima!" Ta shige can kuryan dakinta na bita da kallo tarkace ta fara fitowa da shi, tana me cire su a leda, tana kallona na cire kayana, sannan na daura zanin da ta ajiye min sabo ne fil. Na dauka na daura ta ce min. "Ki duba sif akwai hijabi sabo ki dauka daga yau sun zama kayan wankinki da jego, sannan ki gaya mishi za a zo dauka miki kayanki na sawa!" "Tow amma kin san yau za a rantsar da shi?" Na fada mata ina kokarin fita daga dakin. Ta ce min. "Na sani mana Ummu! Aliyu Muhammad Jadda Tafida zaɓaɓɓen gwamnar jahar Borno ba!" Fita nayi domin na fahimci Mama tana fusace, kuma idan na sake nayi magana zanci Ubana! Ina fitowa waje ana kawo ganyen Dalbejiya. Ban daki na wuce, itama ta fito tana faɗin. "Sannu Sa'adu." Ya amsa ta shiga gyara ganyen sannan ta biyo ni ban daki, tunda kannena suke haihuwa ba ita take musu biki ba, domin Mama yar kasuwa ce kuma bata da lokacin da zata zauna musu daga Biu take dauko me zama a gidansu, har su yi arba'in amma ni dake yar gata ce na samu wannan damar. Shigowa ban dakin tayi tare da saka ganyen a cikin ruwan da yake tiriri. Ta yayyafa min a kafana sannan ta kuma diba ta zuba a karo na biyu. Karo na uku ta shiga yafa min ruwan sosai tana yi tana dauke kanta yadda ta ga ina jin dadin saukar ruwan a jikina. "An miki dinki ne?" "Eh!" Bata kuma cewa kome ba,ta cigaba da min wankar sai da ta kwashe rabin bawon sannan ta fito daga ban dakin ta hada min sauran kayan wanka ta kai min, ta tab'a ruwan bawon ta saka min gishiri a ciki ta ce min. " Shiga ki zauna!" Ba musu na zauna a cikin ruwan, ina cizon bakina. Sannan ta fita can ta kuma kawo min ruwan zafi da na kara wanka da shi sosai,lokacin da na fito ji nayi kamar an zare min duk wani gajiyar da yake jikina. "Ummu ashe an sauka lafiya?" Inji Jamila, murmusa mata nayi na wuce dakin. "Mama ina Yaron yake?" "Yana asibiti bai da lafiya." Idanuna ne ya cika da kwalla wato ita uwa wata tsani ce da ba kowa yake hawa ba, take ta gyara abin da na aikata da wani abu na daban, "Sa'adu ka kira min Yusuf yazo maza ya yanka min talotalona dama ya ishe ni!" Ta fada tana wucewa kitchen, dake gidan Mama baya rabuwa da masu sayan abinci yanxu haka kunu aka yi da kosai da alale na safiya. "Zakiya kina kwab'a dan waken ne?" "Eh Mama." Ta fada daga cikin ɗakinsu, "Tow ai waken da yake kan wuta ya nuna, ga Kwai ma na sauke miki!" "Mama Ina Uwani ne?" "Ta kai marden kayan miya ba!" Ina daki aka shigo min da alale da manja da yaji cikin kula har yana tiriri, ga kwai guda shida akai, ga kunun tsamiya da ta kuma dama min, "ki duba sif din akwai kayan Ummu Kulsum ki dauka mana!" Na juya na dauko kayan Ummu Kulsum na shiga kokarin sakawa. "Mama nonon yana zuba!" Banza tayi da ni. Juyawa nayi naga tana janyo wani bokiti no secret, ta ajiye min dambun kaza ce ta ajiye sai wani kwano samira shake da yajin kalwa, kafin kace me dakin ya dauki alamar jego. "Zauna ci, ki kwanta." Baya da kura. Kasa tsayuwa yayi ya nufi cikin asibitin, ya kalli Nurse dinda suke dakin kamar gulma suke,suna ganinshi kowacce ta kama gabanta. Wayarshi ya ciro ya kira Yayarshi."Maryam ki zo maza asibiti Ummu ta haihu." Kafin wani lokaci labarin haihuwar ya karade familyn Aliyu Tafida, kafin karfe takwas asibitin ya cika da yan Barka, sai dai duk wanda yazo ya ga Yaran turus yake yi idan yaji uwar Yara ta barsu. Shi dai a saninshi ba a tab'a yin haka ba, amma kamar kaddaranshi ce yake bibiyarshi yasa haka ya kuma faruwa da Yaranshi. Idanunshi ya lumshe yana jin yadda Inna take salati. "Innalillahi'wa'inna'ilaihi'raji'un, Tafida lallai kin tunawa kanki asiri! Yanzu ke Tafida abin da kika yiwa yaron nan Ummu Hadiyyah kin kyauta kenan? Yaron nan Ummu Hadiyyah ta gama shan wahala dake shine zaki saka mata da wulakanci? Tafida ki ji tsoron Allah wallahi halinki bai da kyau!" A fusace Tafida ya kalli Inna da ya fahimci har duniya ta nad'e ba zata daina mai da shi mace ba, ta kuma daina mai da mace namiji ba ya haɗiye takaici ya kalli Hajja Gana ya ce mata. "Hajja gaanah ki gayawa yar uwarki don Allah yta shiga gaba Ummu Hadiyyah ta amshi Yaran nan wallahi kukansu hana ni sakat yaƙe!" Domin ya fahimci zuwa yanzu babu wanda zai tsaya mishi mahaifinsa da yaji labarin yaki zuwa asibitin ma, kuma yaki magana ma, Yayunshi maza da mata kowa sai cewa yake Allah ya kyauta yanzu ya fahimci suna shirin juya mishi baya, Kallon Maryam yayi da ta dauki Macen da bata da yawan kuka ta ce mishi. "Tafida kasan lokaci yana tafiya, kuma!" Zuba mata idanu yayi kafin ya ce mata. "I wishing da mafarki nake da na farka! Zafi biyu nake ciki." Ƙarar da wayar shi tayi ne ya saka shi. Kallon wayarshi yayi wanda an kira yafi sau saba'in ya kuma juya ya kalli Jariran da suke kyankyara kuka ji yayi kamar duk duniya babu wanda aka tab'a tubewa mutuncinsa aka watsa a titi kamarshi tsinkayo muryan Hajja Gaanah yayi tana faɗin. "ABIN DA KIKA SHUKA, SHINE ZAKI GIRBA MARA KUNYAR KARYA ANAN KIKA CEWA annah Yaron nan Ummu Hadiyyah tana haifa miki Yara xaki kawo masu kula da su daga can ƙasar arna su musu irin tarbiyyar da kike so kai Yaron nan Ummu Hadiyyah dan halak." Kasa yayi da kai daidai kira na saba'in da daya yana shigo mishi. "Ki dauka kada ki saka a fasa rantsar dake a matsayin gwamna." Safiyudeen ya gani a hankali ya dauki wayar. "Saura awa uku, ga kayanka ya iso kana ina ne?" "Ina cikin tashin hankali, Ummu Hadiyyah ta haihu ta bar min Yaran!" "Innalillahi'wa'inna'ilaihi'raji'un! Me yayi zafi Tafida!" "I don't know!" "Ka sani Aliyu Tafida ka sani Aliyu kasan me yasa ta barka!" "Ya zanyi tow yaran suna kuka sun ki amsar kome!" "Yanzu ina Inna da Abba?" "Abba yaki cewa kome! In fact ya ce kada na kawo mishi su gida, na san yadda zan yi!" "Gani a hanya" wasa wasa tunda Safiyudeen yazo ake tufka da warwara har Safiyudeen ya iso, ga Yaran sun fara galabaita da kuka, Hajja Gaanah tana kallon yadda Aliyu yayi wujiga-wujiga domin tashin hankali, a cikin Yan uwansa Maryam ce kawai a tare da shi. "Inna don Allah ku kai Yaran nan, ni zan kai Aliyu ta shirya lokaci yana ta tafiya!" A fusace ta b'alla mishi harara Hajja Gaanah tayi ta juya cikin Yaren shuwa ta ce mishi. "Yar banza ba kince ke ba zaki zauna da shi ba? Kin zata ke ce kawai mara mutumci? Anan kika ce ko yaron nan Ummu Hadiyyah ya haihu ba zai bawa Yaranka nono ba, don uwaka ba zan saka dan uwana ya je ba, ka ja mana abin kunya ana bikin rantsar da Gwamna amma tana asibiti tana cutar da marayan Allah, Anya Aliyu kina tsoron haduwa da Allah? Ka ga ni daga nan ina gama bikin zan koma garin mu can miki da mugun nufinki Gara da Yaron nan Ummu Hadiyyah ya bar ka Yaranka ki je can mara kunyar karya. Ni dai ba zan tafi na kara zubar da mutuncin na ba!" Ta fada tana kauda kai. Kwanciya nayi amma na kasa jin dadin rayuwata, ita uwa a kodayaushe Uwa ce na haihu a rayuwata amma na ajiye Yaran a can tow me yasa na bar mishi Yaran? Me yasa ban kwaso abina ba? Lumshe idanuna nayi wanda ba barci nayi ba, amma fa ina cikin tashin hankali. Har kusan karfe sha daya da naji gabana yana faduwa, karfe sha biyu za'a rantsar da shi amma tow waye ya sani ko ya tafi abin shi ya bar min Yaran a can? Ban san yadda aka yi ba sai ji nayi na tashi zaune ina zare idanu. Idan kuma Aliyu ya kaiwa Hajiya Shuwa Yarana fa? Kenan Sa'adiya ce zata ci gaba da yadda taso a kaina da Yarana kenan? Shigowa Mama tayi ta kalle ni. "Lafiya?" "Kaina yake ciwo!" Na mata karya, don naci karya na kwana da yunwa na gayawa Mama cewa Yarana nake tunanin kada su fada hannun Shuwa da Yarta. Tab'e baki tayi ta janyo locker gadon ta ciro Panadol ta ajiye min ta fita, karfe sha biyu saura minti ashirin, naji hayaniya a gidanmu da Unguwar bakiɗaya, sai da naji kamar zuciyata zata diro waje........ For more info... 08130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *🚫 Gargadi da kashedi! Wannan labarin hakkin Mallakar Mai_Dambu ce! A kiyayye tab'a abin da ba naka ba kuskure ne kowa yayi nashi🔞* FATAN ALKHAIRI GA DUK WATA SINGLE MOTHER WANNAN LITTAFIN NAKU NE💕🌺 Paid book _Zuwa yanzu na fahimci nayi kuskuren barwa Tafida Yarana tabbas kowacce mace ba ce ta cancanci zama uwa sai wacce Allah ya so ta da rahama_ 02 Mikewa nayi jikina yana rawa domin haka kawai nake ji kamar Aliyu ne da tawagarsa suka biyo sawuna. Shigowa dakin Mama tayi tana faɗin. "Bismillah ku shigo mana!" Tun kafin ya iso kamshin turarensa ya cika dakin gabana sai dukan uku uku yake, yana baya safiyyudeen yana rike da baby macen domin daga yanayin abin daukansu na fahimci haka, komawa bakin gadon nayi na zauna tare da saka hijab dina. Cikin wani munafukin na nutsuwa ya zauna yana sunkuyar da kai wanda a da can wani gani gani yakewa dakin idan muka zo, sai yau naga akasin haka. "Mama don Allah ki ce ta amshi yaran wallahi an kusan!" "A'a ba sai kun had'a ni da Alla ba ai bata kyauta ba, kawo su ku tafi kada a makara." Ta amshi yar hannun Safiyyudeen din ta kwantar da ita sannan ta mika hannu ta amshi Namijin da yake kwance a faddadar kirjin shi. "Don Allah ki roke ta, ta koma kafin ayi bikin shiga gidan gwamnati!" Ya fada yana mikewa cikin sanyin halin da ban san yaushe ya dauko shi ba yo ai ba halinsa ba. Kasa-kasa nace. "Sai dai a kai gawata gidanka, wallahi ba xan koma ba!" Nasan zai ji kuma bakiɗaya ma nasan zasu ji, na dauke kai kamar bani nayi maganar ba. Wayar Safiyyudeen ne yayi kara ya ga Mahmud tsaki yayi yana faɗin. "Muje!" Dakyar ya iya fita yana jin kamar an sauke mishi nauyin da yake kanshi. A gurguje suka nufi filin da za a rantsar da shi, daga shi har Safiyyudeen babu me damar magana hankalin kowa a tashe yake domin gani suke kamar an mishi wani ne. Gyara murya alkalin alkalai yayi sannan ta shiga maimaita alqawarin da rantsuwa da Aliyu Muhammad Jadda zai dauka, ya sha fararen kaya kanshi sanye da wata bakar hular zanna Bukar da tasha aiki me kyau, ana gama rantsar da shi ya shiga motar gwamnati kamar yadda kowani gwamna yake. A fusace Mama ta nuna min Yatsa, "kada ki sake fushina ya kwace akanki, kika sake raina ya b'aci zaki ga ba daidai ba" a matuƙar tsorace na hadiye duk abin nake ji na koma na nutsu tare da kame kaina Mama bata daukar reni tana cikin iyaye marasa daukar iskancin Yaransu. Fita tayi amma bakiɗaya ranta a b'ace yake haka ta hado ruwan zafi ta kawo dakin Allah Sarki Uwa me dad'i, hatta sabulun wanka ta hada, "Assalamualaikum, Hadiza ashe an kawo Yaran?" Inji Umma, murmushi tayi tana me faɗin. "Eh gasu nan zan wanke su." Waye bai san halin Umma ba wurin had'a wuri da son bin didigi, "Kai Hadiza ina laifin ki ce ni ko Yaya wata tazo ta wanke Ummu Hadiyya da jarirai ke da kanki zaki yi haka?" Cikin ko in kula ta ce mata mata. "Yanzu aka min jika abin cikin kwai, yafi kwai dad'i!" Daga haka Umma tayi turus, "Allah ya huci zuciyarki!" "Ai ba fada ba ne!" Mama ta fada tana cirewa Macen kaya, ta fara shafe ta da lalle da ta kwab'a da tazargaje, ta maida ita cikin abin ɗauka ta rufeta, sannan ta koma wurin wurin namijin shima haka ta shafe shi tas, har lokacin Umma ta gagara jan kafa ta bar dakin. Domin bata tab'a kawowa Mama zata gaya magana haka na. "Ummu babu inda yake miki ciwo?" Girgiza mata kai nayi sannan ta juya yana faɗin. "Sannu da arziki ashe har yan biyu ne." Gyada kai nayi a kunyance, fita tayi can bayan fitarta Mama ta dalla min harara. "Wallahi da kin sake wani ya san bar mishi Yaran kika yi da na sab'a miki!" Shiru nayi ban ce kome ba, saboda nasan zata iya nad'a min duka wallahi. Tana rufe bakinta sai ga makota sun fara shigowa. "ashe Ummu Hadiyyarmu ta sauka lafiya?" Murmushi Mama tayi domin Mama me Jama'a ce kuma Allah ya bata jama'a don haka ta ce musu "Eh wallahi!" Ta nuna musu Yaran da take gyara su, yadda Mama take hidima kawai ya saka ni jin tabbas ta jima tana shiri ba na wasa ba, domin tsakaninta da Allah take kome, kafin zuwa azhar gidanmu ya cika da yan barka da yan Allah ya sanya alkhairi. Wato a a tayani murnar samun nasarar da Tafida yayi har yau an rantsar da shi. Murmushi nake domin basu san me ke faruwa ba, da an buga ni a jarida. "Assalamualaikum!" Mama da take tsakar gidan ta amsa tana faɗin. "Malam Mudan!" "Na'am Mama, ga kayan Hajiya Ummu da wayarta." "Masha Allah, ka kyauta wallahi!" Zata amshi kayan Zakiya da itama shigowar kenan daga kofar gida ta amshi kayan tana faɗin. "Mun gode, Mudan yanxu dai zaka koma Government House kenan?" "A'a Hajiya Zakiya ina nan daram a tare da Hajiya Ummu!" "Lallai na zata can zaka koma ai." Dariya yayi yana faɗin. "A'a babu inda zani!" "Mudan kyale magananiya ga abincin nan!" "Hajiya Mama kin san gidan ana ta hidima Hajiya Maryam ta haɗa min kayan naci abinci." "Tow shi kenan." Sallama yayi na leko ina faɗin. "Mudan ka rufe min store dina!" "In sha Allah" ya fada yana me barin gidan. Mika min jakata Zakiya tai na na amsa ina bude jakar,wayata ce Samsung series X ina kunnawa na ga babu charger. "Zakiya?" Na kirata. "Na'am Aunty Ummu!" "Don Allah bude akwatin nan akwai power Bank a ciki bani!" "Tow!" Ya zuge akwatin na ciro, ta mika min ina sakawa a charger kamar abin munafunci sai ga kiran Tafida. Kamar ba zan dauka ba. Jin wayar tana ta ringing ban dauka ba, ta shigo dakin. "Kanki daya kuwa? Ba kiranki ake ba?" "Ayya Mama kin ga abin da nake yi basu mama nake fa!" Na fada kamar zanyi kuka, "kowa rai ya amfana baya ga me shi ne!" Daga haka ta fita wayar ya kuma ruri. Dauka nayi a fusace na ce mishi. "Me kake bukata?" "Ko ki kira ni!" "Akan me zan kira ka meye matsalata da kai da har zan damu kaina da kiranka!" Murmushi yayi sannan ya ce min. "Matsala ai babba ce tsakanina da ke, dama na kira naji yaushe zaki dawo ayi suna a government!" Ya fada a cikin sanyin murya da ni bako ne a gare ni. "Da bance ka zo ka ɗauke kayanka da ka kawo min ba?" Wani shiru yayi kamar baya rike da wayar na cigaba da cewa. "Idan ka sake raina ya b'aci kotu ce zata raba ni da kai." "Ummu Hadiyya duk akan me yayi zafi?" "Na gaya maka zama da kai ne ya kare ka fahimta mana!" "Ummu Hadiyya ni fa ban san me nayi kika dauka da zafi har haka ba." "Zaka sani daga baya!" Na kashe wayar har yanzu wani irin b'acin rai nake ji domin kaf wayata babu wanda ya kira ni a gidansu Aliyu Tafida ya min barka haka ya tabbatar min suna tare da Dan uwansu da Yar uwarsu, kuma nasan koda ina gidan haka zasu cigaba da harkansu babu wanda ya damu da ni. Murmushin takaici nayi ina kallon Yaran, wayata tayi ƙara dauka nayi ganin Kulsum. "Aunty Ummu Hadiyya ashe kin sauka." "Hmm eh Kulsum!" "Wayyo Allah nan nesa bata maganin kusa kamar nayi tsuntsuwa na zo na ga Aunty baby da Jaririnta kin san ma a ina na gani?" "Sai kin fada tsikallazi!" " A status din Mai girma gwamna, ya saka tare da cewa My beautiful kids from first lady!" Tab'e baki nayi ina cewa. "Sai dai wata faisi ladyn ba dai jinin Baburawa ba!" "Kai Aunty Baby!" "Meye nayi? Daga fadar gaskiya wallahi kuwa zai aiko min da takardana!" "Ba ruwana!" Jin ana kiran wayar nace mata. "Kashe Father inlaws yana kirana!" "Tow Maman twins daga Aunty Baby zuwa Maman twins!" Tana kashewa ina daukar kiranshi. "Abba kayi hakuri!" "Yarinyata ke xan bawa hakuri ashe babu wanda ya zo ganinki? Babu abin da aka kawo miki? Yarinyata wacce irin rayuwa kike yi ne haka? Kin ga haka abokiyar zamanki take yi ne?" Kafin nayi magana Hajja Ganaah ta ce mishi. "A'a Jadda kar ki ga laifin Yaron nan Hadiyya mutum ce guda, Yaron yana da kawaici kawai iskancin yan gidanka ne su ya dace kiyi musu fada ba Yaron nan Hadiyya ba, kuma kin ga hankalin kowa ya tafi wurin bikin rantsar da Tafida shi yasa aka manta.", ai kuwa ina ji ya juya mata kanuri shiru yayi domin a fusace yake, "Ga sako nan na turo zuwa an jima xan zo da kaina.;" "Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana, Allah ya biya da gidan Aljanna!" "Zan zo na ga yaran kin ji!" Nan ya shiga bani hakuri dama fa haka yake, Tafida da laifi shi da bada hakuri. "A'a Abba wallahi babu kome!" Kai mutumin nan da girma yake. "Na gode sosai! Allah ya muku albarka sai na zo!" Haka muka yi sallama na ajiye wayar kenan sai ga Kiran Aunty Maryam na dauka. "Ashe kin sauka lafiya!" "Eh wallahi!" "Tow sannu!" Ta fada a dakile kafin ta rufe baki na ce mata. "Yawwa!" Na kashe wayar, sake kirana tayi na dauka tare da cewa. "Kin yi mantuwa?" "Ban yi mantuwa ba, kada ki ga don Abba yana wani ji da ke ki dauka wata tsiya ce, domin talaka bai iya samun wuri ba!" Dariya nayi irin na cusa haushi nace mata. "Ke Yayar Aliyu ce shi yasa ba xan gaya miki me zafi ba, amma idan da gaske kina tare da dan uwanki don Allah ki ce mishi kafin faduwar rana zuwa hudowar na gobe ya sauke igiyoyin da ya zame mishi alak'ak'ai ya huta kuma ku huta da bakar kaddara!" Kafin ta gaya min abin da zai hana ni barci na katse kiran tare da sakata a blacklisted kowa ya huta, nasan ba irina suke bukata ba, shi yasa duk abin Tafida yayi min basu gani asalima gani suke kamar an tauye mishi hakkinsa na aura mishi. "Mama Amarya ga wata a kori kura da kaya wai an kawowa Aunty Hadiyya ne!" Shiru nayi ina zare idanu, bankado labule tayi na fara kokarin ajiye Jaririna zan mike. "Ban fahimci me Yaron nan yake faɗa ba?" "Dama-dama, Abban babansu twins ne ya ce za a kawo kayan abinci." Wani kallo ta zuba min na fara rantsuwa. "Wallahi ban roka ba." "Kada ki tara min mutane." Ta ja mayafinta, ta yafa sannan ta ce min. "Kika sake wani abu ya dawo daga hukuncinki wallahi zan saka kafar wando daya dake." Hadiye yawu nayi na wuce ban dakin da yake cikin dakinta na dawo dakin na tsiyayyi ruwan flast na wuce, Tabbas Abba ya turo da kayan abinci, babu abin da babu kama giron kunu, buhun sugar, katon din madara da Ovaltine, shinkafa, alkama, man gyada manja, da Naira dubu hamsin, wai a gaya min gobe za a kawo nama. Koda aka shigo da kayan, Hajiya Balki da Umma suka shigo. A fuskar Hajiya Balki da na hango sanyi na gaisheta. Cikin kulawa ta ce min. "Sai gashi har biyu kika haifa da kanki?" Komawa kujera nayi na zauna, domin girman Hajiya daban ne. "Kin zama Maman Yan biyu, bana nan tun asuba muka tafi gidan Taima kin san abin sai a hankali zama yaki dad'i kuma Babanku yaki magana akai shi yasa naje tun lokacin ina can. Ina dawowa Kawu Gwani yake gaya min kin haihu. Ikon Allah muna ta al'ajabin wannan cikin naki ashe kyautar Allah ne awurin." "Ya su Taima din da Yaranta?" "Suna lafiya, al'amarin sai a hankali uwar mijin taki a zauna lafiya yanxu haka dakyar aka shawo kanta!" Naji babu dad'i sai dai ita sharri haka take, "Allah ya kyauta ya daidaita tsakaninsu." "Amin Ummu ki yafe mana, sannan ki zauna a dakin Mijinki wallahi Allah ne ya d'aga darajarki amma tabbas halin ki da na mahaifiyarku abin koyi ne!" A hankali na d'ago kai na kalleta kafin ta ajiye Yaran ta ce min. "Daga yau zan cigaba da musu wanka, jin Yaran nake kamar Yaran kawu gwani!" Hawaye ne ya cika min idanuna. Nasan Allah ya haɗa ni da kawu gwani tun farko amma da Allah bai nufa ba haka kome ya tafi da tarin zunubi marasa dad'i, "Ba kome Ummi!" Yadda Yaranta suke kiranta. Har zata fita Mama ta shigo da ruwan wankan Yaran. Ta ce mata."kiyiwa ma mijinki da kishiyarki ni zan yiwa Y'ata." Murmushi Mama tayi tana faɗin. "Oho wato ke nan me gudun dangi har zaki guji miji da kishiya ki gyara yarki!" Abin da daure kai yaushe Mama da Ummi suka shirya? Wai meke faruwa ne a gidanmu waye zai gaya min wannan labarin? Ummu Rooman, tabbas ita ce zata bani labari haka Ummi ta kwashe ruwa ta kai ban daki ta saka na fito tayi min wanka tas, har da jijiiga min cikina sai ga jini da yake damuna. Kafin na fito ta koma bangarenta, ina ga girkin daren da tayiwa Baba shi aka zuba min yaji man shanu gijib, aka Mahira ta kawo, sai sannan ta ga Yaran dake irin yaran nan ne masu rawan kai, amma.tana tsoron Ummi, ta shiga daukar Yaran a hoto sannan ta daura a story dinta, da faɗin. *Alhamdulillahi Masha Allah tuburkallah, Yaran mai girma Gwamna Aliyu Muhammad Jadda Bro Tafida!* Kafin wani lokaci an cika mata waya da kira ana tambayarta da gaske Matarshi ta haihu? Komawa Whatsp tayi ta ce Yes Aunty Baby ta haihu. Ta faɗa tana murmushi. "Aunty Baby ni fa xan iya dawowa nan da dama saboda Yaran nan, wai ma ya sunansu ne?" "Mahira kina babbar Uwa ina ruwana da su!" "Ok bari mu zabi suna masu dadi!" mama da take shafe su da turare ta ce mana. "Oho garin saye sayen suna sai kun sakawa Yara suna cokali!" Dariya Mahira tayi tana faɗin. "Wannan sunanshi Mufid ita kuma Mufidah. " "Oho idan kunso ku saka musu muzuru da magege!" "Kai Mama kishinki yayi yawa!" "Idan ban yi waje dasu ba ku ba dame ni da maganar kishi!" Ta fita tana murmushi. "Aunty Baby kiyi hakuri ban shigo ba na tafi school ne kuma na dawo na kama aiki kiyi hakuri!" "Ba kome Mahira!" Shigowa Mama tayi da tukunyar miya, ta ajiye ta zubawa Mahira tace. "Ki kaiwa Umminku da Umma!" "Tow Aunty Baby sai gobe don karatu nake sosai mun kusan Exam!" "Allah ya bada sa'a!" "Amin Ya Allah!" Ta fada tana me barin dakin, zuba min nawa tayi can su Zakiya da Uwani suka shigo. Suka baje a dakinta. Nan muka shiga hira, muna haka Baba yayi sallama. Duk suka mike tare da komawa can gefe, ciki ya shigo yana faɗin. "Haka kawai naji ina cikin farin ciki ashe Ummu Hadiyya ce ya sauka, Masha Allah Alhamdulillahi Ubangiji me kyauta da kari." Ya taka har bakin gadon ya dauki yaran yana musu addu'a. "Wato kun zo ayi bikin Babanku ko?" Kaina a sunkuye ya kalle ni kafin ya ce min. "Sannu Ummu!" Ni dai kaina a sunkuye. "Dazun Alhaji Muhammad Jadda yake gaya min, Ummu Hadiyya ta sauka sai da na kusan shigowa gari yake gaya min yana ta bani hakuri yanxu ma yace bayan Isha yana hanya. "Tow Masha Allah!" Haka ya gama maganar sannan ya ajiye su ya fita after kamar minti talatin sai ga Amiru da katon leda, gasashen kaza ne har uku inji Baba. "Amma Alhaji ko? Zai gamu da ni!" Ta fada tana me faɗin.."Uwani dauko min tire da flat." Fita Uwani tayi sai gata da su, ta baje mana sannan ta zuba min nawa naci sosai don ma bakina ba dad'i. Wurin karfe takwas sai ga Sako Baba ya turo a gayawa Mama Alhaji Muhammad Jadda yazo. Sai da tayiwa yaran addu'a sannan ta dauki daya Zakiya ta ɗauki namijin, Uwani da katon tire an saka ruwa da kayan sha. Aka kai musu Yaran, dake ya saba duk inda zai shiga da Kannen shi nan guda biyu. Ba'agwe da Abbalawan, sune suka amshi Yaran yana zaune a kusa Baba da ya ajiye mishi kayan marmari gabanshi. "Ina Yarinyata ba wurin wadannan naxo ba!" Abba yana cikin mutane masu dattako da daraja, shi hankaka ne mai da dan wani naka, kuma har yau haka yake. "Bari na kirata!" mama ta kuma fita muka tawo tare na sha uban lafayya. Ina shigowa na zube zan gaida shi ya ce min. "Kul koma kan kujera, danyen jiki ne dake zauna a sama, Hajiya shigo mata da takalminta!" Kallon Abba Mama tayi yayi murmushi ya ce mata. "ki shigo da shi mana!" Haka ta fita ta kawo takalmin, ya ajiye min sannan ta cewa Abba. "Alhaji baka bukatar wani abu ne?" "A'a Hadiza me zan bukata yau ango nake nayi sabuwar Amarya shar ke da Balki da Yahanasu na ja muku layi." Ai kuwa farlon aka saka dariya ta fita tana murmushi, "Alhaji Bulama kayi dacen mata, haka nake mafarkin Aliyu ya dace da Hadiyya,matukar wancar matar da ta fita ita ta haifi Hadiyya tabbas Aliyu ya dace. Alhaji ka bawa Ummu Hadiyya hakuri na sani,.kuma nasan zata cigaba da yi. Murmushi Baba yayi ya ce mishi. "Alhaji sha'anin Yaranmu sai Allah amma nasan zuwa yanzu kome ya wuce ai, tunda gashi har da zuri'a." Wai ma tukun bikon Aliyu aka zo yi wato gani nan sakarya shine da zo a bani hakuri ban gama nazarin haka ba naji Abbanshi yana faɗin. "Nayi mata alkawarin kuma zan sauka akan alkawarina ba, Allah ya mata albarka ta kuma cika yar halak, ta nuna min ita haifafiya ce, Ummu Hadiyya ki tsaya akan kalamanki Allah zai tsaya miki, zan kuma koma gefe na zuba idanu. Idan Aliyu Tafida yayi nasara akanki zan baki boye kaina idan kika kai shi kasa da shi da yan barandanshi nayi miki alkawarin tsaya miki kai da fata, amma ki sani sai kin zama jajjurtacciya akan kome da kowa, Alhaji Bulama kayi hakuri amma akwai banbanci da can baya da yanxu domin ina bayanta ne a yanzu. Wannan shine dalilin zuwa ta. "Na zata kome ya wuce Alhaji!" Girgiza kai yayi yana faɗin. "Yanzu ne mafarin.... Anya Alhaji Muhammad Jadda Uban Aliyu Tafida ne kuwa.... Me yayi zafi har da zai hada kai da Matar dansa? 🥺 08130269641YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 03 Duk da dai ban san dalilin Abba nayi haka ba, amma naji a jikina tabbas ko Abba da Baba su tsaya min ba, wannan shine karshen zamana da Tafida domin a duk lokacin da na tuna abun ya faru a baya tabbas Tafida yana buƙatar space me girman gaske, yana bukatar na bashi wuri ya sha iska, don haka na sunkuyar da kaina kasa, har Abbanshi ya gama bamu hakuri ya cewa Baba. "Ka kira Mamanta su maida su daki." Ya fada yana kallon Yaran da yake jin wani kaunarsu kamar ya tafi da su. "Tow Alhaji Muhammad, ayi ta hakuri dai domin shi rayuwar bakiɗaya akan hakuri yake." Haka ya kira Mama a waya suka tawo suka dauki Yaran ni kuma nayiwa Abba da Baba da yan uwan Abba sallama, koda muka koma dakin Mama ruwan zafi ta had'a min na danyen gasarar kunu da ta zuba sugar da garin yaji, ta dauko min namar da Baba ya kawo ta kara dumamin, sannan ta ajiye min tana faɗin. "Kafin ki kwanta ki sha ana bukatar yaran su wadata da ruwan nono kafin gari ya waye." Gyada kai nayi na cire kayan jikina, sannan na maida wanda na saka dazun na fara shan ruwan zafin ina cin namar, hira suke tun ina jinsu har barci yayi gaba da ni, dake na manta da wayata ban kashe ta ba, wurin karfe daya na dare naji wayar na ƙara, a matuƙar gajiye na dauki kiran. "Ya kike?" "Gaskiya ka shiga hakkina akan me zaka kira ni daidai irin wannan lokacin? Fisabiilillahi baka gane kana cutar da rayuwa ne? Ka je Allah yana nan baya barci." Na kashe wayar bakiɗaya na kwanta. Dakyar nayi barci don ma Mama tana dakinsu Zakiya. *Aliyu Tafida* Yau duk wani hayaniya da aka yi tare da bidiri a kasan ranshi Ummu Hadiyya ce, domin a matuƙar dame yake ya rasa yadda zai yi ne, amma dake Allah ya daura mishi zurfin ciki da juriya yasa bai wani nuna damuwa ba, amma tsakani da Allah yana hautsine akan abinda Ummu Hadiyya take nima, wunin yau bai da nutsuwa ga bikin da aka yi, bayan rantsar da shi. Duk yadda yaso ya yi magana Safiyyudeen ya hana shi, koda ya kira Ummu Hadiyya ma yana cikin mota zasu koma gida ne su uku Tafida, Safiyyudeen da Mahmud. "Ummu!" "Tafida zuwa karfe biyu na rana zan zo na hada maka kayanka!" "Deen!" "Na'am!" "Ka wuce da ni gidansu Hadiyya!" "Dare yayi kai ka gaya min tun karfe daya na daren jiya take abu daya yanzu ta samu zata huta kace a tafi a tadda ita kai ka ce baka tab'a sanin haka Mata suke shan azabar haihuwa ba, ka san me? Allah yana sonka da rahama ne har ya nuna maka yadda mace take nakuda." "Amma me yasa.!" Kafin ya kai Aya Safiyyudeen ya dakatar da shi da cewa. "Kada ka manta yanzu kai ne gwamnar Jahar Borno wai ma Tafida yaushe ka fara kananun magana?" "Tun ranar da aka aura mishi wancan me siffar dodon wasan Yara!" Inji Mahmud, kalamansa sun yiwa Aliyu zafi saboda ya san cewa shi ya bada damar haka amma bai taɓa kawowa zai iya cin mutuncin Ummu a gabansa haka ya basu damar fadar abin da yayi musu. "Wannan wacce irin hauka ne? Taya zaka fadi haka?" Inji Safiyyudeen yana tuki. "Kambu da kai nayi? Dan shigigi ko ance babu wanda bai san halinka ba ne." "Gara ni ba munafiki ne ne, gara ni bani da fuska biyu idan har bana son Abu bana wahalar da kowa sannu shugaban munafukai. " "Kai ya isa haka, don Allah meye haka ne? Tun muna Yara kuke wannan haukar har yau baku gane gaskiya kun girma ba ne!" "Shi zaka gaypawa dan matsiyata!" "Na gode sosai tunda arzikin ba ubanka yake rabawa nace ya manta da gidanmu ba, gara na zauna a tsiya da na zama me irin halinka!" "Zanci bura uban mutum!" Ya fada da karfi haka yasa bakiɗaya suka yi shiru. Wato shi Safiyyudeen kokari yake ya hana Tafida fadar sirrinsu yayi da Mahmud yake son yaji meke faruwa tsakanin Tafida da Ummu. Dukansu abokan Tafida ne tun suna Yara shi yasa kaf duniya bai da sama da su, amma don sirri da tattauanawa me muhimmanci bai da sama da Safiyyudeen domin shi Deen irin mutanen nan ne masu zafi da fada, yanxu sai ya iya kwaabewa ayi dambe da shi babu ruwan shi. Yayinda Mahmud baka tab'a sanin halinshi idan ka cire jaraban bin mata tow magana ya kare duk suna da kirki sai dai tsakanin Mahmud da Safiyyudeen shirinsu na lokaci ƙalilan ne zuwa wani lokaci sun hautsine don shi Mahmud yana da wani irin dabi'u saurin gori da nunawa yafi kowa yayinda Safiyyudeen bai da irin wannan halin sam, sannan shi kanshi Tafida yasan halinsu ya san abin kowanensu zai aikata. Kuma dukkansu babu wanda yake jin zai rabu da shi don halinsa sai dai kai ka rabu da Tafida don kanka. Sai da aka fara sauke Mahmud a gida ya tsaya a gefen motar ya ce. "Allah ya isana duk wanda yayi gulmana!" "Kai can ci ubanka!" "Na dai faɗa!" Ya juya tare da shiga get din gidansa. Murmushi Safiyyudeen yayi ya ja motar suka yi gaba. Tafida ya kwantar da kanshi. "Deen me yasa kake hanani magana!" Banza yayi mishi tare da mai da idanunshi kan hanya, wannan halin na Deen yana matuƙar burge Tafida domin Deen Allah ya mishi baiwar iya shariya musu ka tambaye shi abin da yasan ka sani ba zaka kulaka ba sai dai ya bawa banza ajiyarka banbancinshi da Mahmud shi a kodayaushe cikin zargi yake ana munafuncinsa. Sai da ya shigar da shi cikin gidan Mahaifinsa security da masu tsaron da suka hana binsu suka taso tare da lullube su. "Aliyu!" Juyawa yayi yana kallon Deen yana da kyau ka mutuntata darajar Ummu Hadiyya ko babu kome yanzu an zama d'aya, idan da hali kada ka bawa kowa damar cin mutuncinta, yarinyar nan ta rufa maka asiri sama da yadda zamu rufa maka, ta boyewa duniya waye kai ta kuma maida ka mutum sama da kasa, don Allah ko ba don ita ba ko don albarkacin Yaranka ka girmama lamarinta, ba ina gaya maka haka don akwai wani abu ba, kai mutum ne da yayi approaching siyasa yanxu kada ayi amfani da abinda ka aikata akanta ayi kokarin b'ata maka siyasar ka." "Nagode sosai Deen in sha Allah zan kiyaye kuma ina son idan na samu lokaci zamu je gidansu." Murmushi Deen yayi ya ce mishi. "Sai da safe!" Daga haka Aliyu ya fito a motar ya cewa Security din. "Ku Kai shi gida!" "Yes sir!" Suka fada tare da bin motar Deen. A hankali yake takawa jikinshi na matukar mishi ciwo, ya shiga har cikin gidan ya samu babu kowa bangarenshi ya nufa ya samu Sa'adiyya tana zaune waya a hannunta, sanye take cikin kyakkyawar shigar kayan barci. Sau daya ya kalleta sannan ya dauke kai kamar bai dangata ba. "Ya Tafida!" Kallonta yayi kafin ya ce mata. "Au kina nan ne ashe?" "Zaman jiranka nake?" "Ni kuma? Ai da kin kwanta abinki!" "Wani irin kwanta na gama shirin na tayaka murnan samu nasarar zama Gwanma kace nayi barci." Yadda take surutu ba karamin haushi yake bashi ba, Sa'adiyya ita ce irin choice dinsa amma yawan maganarta yasa yake jin babu dad'i akanta ta bude baki zata yi magana ya ce mata. "Please na gaji hutawa zan yi!" Ya wuce dakinsa wanda yake kusa da na Ummu Hadiyya, sai yanzu yaji bakiɗaya kome ya tsaya mishi. Gabanshi ya shiga faduwa da gaske Ummu Hadiyya tafiya tayi? Kurawa dakinta idanun yayi sannan ta wuce dakinsa, duk yadda yaso ya samu hutu ya kasa dole dakin Hadiyya ya dawo ya kwanta. Kamshin turarenta da yake cike a dakin kamar yanzu ta saka ya sashi lumshe idanu. Yana kwance a wurin har aka kira sallah asuba, dakyar ya tashi yayi sallah anan ya baje bai farka ba sai wurin karfe daya na rana. Shima kiran sallah azhar ya farka. Ban dakinta ya nufa yayi wanka sannan ya dauro babban towel dinta. Ya nufi waje sake da baki Sa'adiyya tayi da take waya da kawarta ganinnshi daure da Towel din Hadiyya, bata san lokacin da ta kashe wayar hannunta ba. "Tafida meye haka? Ko tsari babu." Banza yayi mata ya wuce dakinsa, tana biyo bayanshi ya ce mata ya ce mata "Get out!" Juyawa tayi babu shiri, tasan ba karamin aiki bane ya maketa kamar zata yi kuka ta kira Uwarta. "Ammi anya kuwa mun samu Tadda yadda muke so kuwa?" Ta fada kwalla na cika mata idanu. "Kul ki sake fadar haka ki zo muyi maganar mu biyu ban da waya." Kashe wayar tayi tana jin wani zafi da kishin Tafida a ranta, bata gaya masa ba ta shirya ta nufi cikin gidan. Shi kan yasan abincin gidan tunda Ummu ta bar gidan shi kenan ta kare mishi. Don haka ya nufi bangaren Inna sanye yake da gezner skyblue shaddar har wani sheki take takalmin kafarshi hafcove ne na kamfanin Dolce de Gabbana, sai hular da ya murza akanshi tangaran ce tayi bala'in mishi kyau. Ta babbar kofar gidan ya shiga cikin gidan, kamshin turarensa ya sanarda yan gidan da masu aikin gidan ga Tafida nan ya shigo, wani uwar gud'a da Mama indo ta buga yasa shi sake fuskar shi. Ta shiga mishi kirari. "Mama indo bakya gajiya ne?" Dariya tayi tana faɗin. "an gaida Uban Yan biyu, Uban Mutanen Borno. " Hannu ya saka aljuhunsa bai san iya adadin abin da ya ciro ba ya mika mata, ya wuce sai godiya take. Yana barin wurinsu ya haɗe rai kamar bashi ba, ya nufi bangaren Abbanshi. Da sallama ya shiga farlour ya samu Yayunsa maza suna zaune a kasa Abbansu yana kan kujera. Cikin nutsuwa ya zauna bayan yayi sallama. "Ina kwana Abba!" "Lafiya lau, ya aka ji da Jama'a?" "Alhamdulillahi!" Ya fada yana sosa giransa ya kalli Yayunsa cikin dan sake fuska. "Ina kwana ya Abubakar? Ina kwana Ya Umar!" "Lafiya lau Mai girma gwamna!" Murmushi yayi suka su bakiɗayansu. "Aliyu!" Alhaji Muhammad Jadda ya kira sunansa"Na'am Abba!" "Jiya Allah ya nufa an rantsar da kai a matsayin Gwamnan jihar Borno ko?" Cikin nutsuwa ya gyara zaman shi. "Eh Abba." "Masha Allah!" Abban ya furta a hankali, sannan ya ce mishi. "Nasihata gare ka ka ji tsoron Allah, ka tuna abun da ka dauka na kamar matsayin senata ba ne a baya, ba matsayin wakilin shugaban kasa ba ne, Aliyu ka tuna nauyi ne na al'ummar jahar Borno bakiɗaya, ya zaka ji idan Allah ya tsayar da kai karkashin alarshinsa yana tambayarka shin ka sauke nauyin da ya daura maka?" Sake sunkuyar da kai yayi yana jin wani irin yanayi yana rab'arshi. "Aliyu ni mutum ne da nayi aikin gwamnati tun daga matakin karamar hukuma har zuwa matakin federal nayi gwagwarmayar da yan boko da yan siyasa, kuma an waye da ni lafiya Aliyu kada ka shiga rigar gwamnati ta yi abinda zai saka ni jin kunyar kaina da a Mutanen da suka yarda da ni! Aliyu shugabanci yana da matukar wahala, na rike shugabancin jami'o'in kasar nan, na rike shugaban jami'a, na rike shugabancin hukumar zab'e, na zama me baiwa shugaban kasa shawara, nayi aiki da ofishin jakadanci, Alhamdulillahi duk wannan aikin da nayi ban tab'a dukiyar gwamnati da na Al'umma ba, Aliyu kada ka sake wani ya tab'a dukiyar al'umma da saninka ba tare da ka janye shi a tafiyar ka ba. Aliyu zuwa yanzu zaka ga masoya da makiya ka tuna da abokan da kuka tashi tun Yaranta kada duniya ta sa ka manta da su. A cikin hakkinka kayi kyauta kayi sadaka kada ka tab'a hakkin Al'umma, kada ka yarda wani ya baka shawarar gina kanka domin masifa ce idan kayi hakuri, wannan albashin da ake biyanka ya ishe ka kai da iyalinka da sauran dangi. Aliyu yan uwanka da sauran dangi kada don ka samu duniya ka manta da su, Aliyu kada don ka zama wani abu ka manta da kamsuna salawati, babu babban tashin hankali kamar kayi ta wasa da Allah, domin daga nan ne ake fahimtar waye mutum, Aliyu ka rike Allah cikin lamarin ka Allah zai tsaya maka kana nan ko baka nan, babu wanda ya isa cutar da kai face Allah ya rubuta a kaddaranka! Aliyu bakiɗaya shekarunka Arba'in ne cif a duniya kada ka yarda ka lalata alakarka da Allah, domin shine abu mafi muni da tashin hankali. Abubakar Umar ku zama shaidana ba bawa Aliyu Shawara akan rayuwa da mulki, Allah kana ganin na sauke nauyin da yake kaina. Duk abinda yayi na sauke nawa, saura shi ya sauke nauyin da Allah ya daura mishi, Allah ta tayaka riko, ka ga dai yadda kuka yi da Alhaji Mansur Goza!" Yayunsa ma suka mishi nasiha kafin suka shiga taya shi murnar samun karuwa da yayi na haihuwar da aka mishi, abinci aka kawo mishi daga ɓangaren Inna. Anan ya ci yana faɗin. "Gaskiya Inna tayi kokari." "Yawwa ya batun suna ne kayiwa Yaran suna ne?" Gabanshi ne ya fadi yana kallon Abbanshi. "Ban yi musu suna ba, rabona da su tun jiya." Ya zaci fada daga Abbanshi sai ya ga akasin haka ya nuna ma bai damu ba. "Yaushe zamu je a gansu? Ko zasu dawo ne?" Umar ya tambaye shi, "Hmm ban sani ba ko zata zo ayi suna anan ko a can zata yi sunan." "Abba baka ce kome ba?" Inji Ya Abubakar, "da aka yi me?" Ya tambaye su, "Akan matar Tafida, za ayi sunan ne nan ko a can?" "Ya je ya same ta a can su shawararsu." Shiru Tafida yayi domin ya fara shakkar Abbansu nan, don haka ya mike jiki a sanyaye ta nufi bangaren Inna ya shiga ya gaida ita tana karyawa Ita da Yar uwarta. "Tafida kin kira Yaron nan Hadiyya?" Zama yayi yana kallon Hajja Ganaah ya ce mata. "Ban kira ta ba!" "Baki kira Yaron nan Hadiyya ba? Anya Tafida kina tsoron haduwarki da Allah Yaron nan ya haifa miki Yara biyu shi ne ba zaki kira shi amma Tafida zaki ci mutum har buzunsa." Gajiya yayi da maganar Hajja Ganaah ga Inna taki cewa Uffan, haka ya ƙara saka shi cikin tashin. Muryan Deen yaji yana dariya a tsakar gida Hajiya Kaltuma tana faɗin. "Yanzu fa kuna tarewa a government house ba zamu kara ganin ku ba, sai an cika wasu takardu da sharuddan ko?" Dariya yayi ya ce mata. "Baba ina ba muda inda yafi nan, don haka ki kwantar da hankalinki. Muna nan fa babu inda yallabai zai koma." "Masha Allah, sai gashi an samu karuwa bana nan wallahi daren jiya na dawo!" "Ba kome Allah ya raya mana su tafarkin addinin Muslunci." "Naji ance ya shigo cikin gidan nan ko?" "Eh!" Hajiya Kaltuma Amarya Abbansu ce kafin ita akwai Hajiya Hawwa tana nan itace Uwargidan Alhaji Muhammad Jadda, sai dai dukkanninsu Mahaifiyarsu Tafida ita ce Babba amma aka samu rabuwa, tana Njamaina na kasar Chadi. "Inna baki ce kome ba?" Harara ta watsa mishi ta ce mishi. "Ke Tafida ki fita idanuna na rufe wallahi kika sake raina ya b'aci sai na miki shegen duka." "Assalamualaikum! Dama nasan za ayi haka kazo wurin uwargida sarautar mata ne?" "Hmm!" Ya fada yana mikewa ya ce . "Muje ka kai ni gidansu wancan yarinyar!" "Wacce kenan?" A hazuke ya dannawa Deen zagi. "Bana son kutma uba, Black gidansu zaka kai ni!" "Ai kuwa ban san hanyar gidansu ba!" A fusace ya sa kai zai fita Deen ya riko shi. "Kada ka sake ka fita wani ya kai ka gidansu Ummu a wannan lokacin, ka san waye kai yanzu? Ya kamata ka iyawa kanka haba don Allah, wai me Ummu ta tsare maka ne?" Buge hannu Deen yayi yana faɗin. "Zanci ubanka wallahi xan maka rashin mutunci ni zata hada da iyayena?" Ya fada da karfi, "matsalarka kenan baka da hakuri, kowa ya raina matarka saboda a gaban kowa zaka ci zarafinta." "Safiyyudeen zan maka rashin mutunci wallahi!" Ya fada cikin fada kafin ya daura da cewa. "Don ina binta ba yana nufin ina sonta ba ne, Yarana ma da ta zuba min zan je na amso su wallahi na fasa bar mata su, har Ni zata hada da iyayena!" Kafin kace kwabo an taru a tsakar gidan, ran Alhaji Muhammad Jadda ya kara b'aci amma yayi murmushi irin nasu na manya ya kalli Hajiya Kaltuma ya ce mata. "Dole sai ya biya abin da yayi Kaltuma." "Aliyu bai da laifi fa, har yau ina kan bakana da ace lokacin da ya rasa Uwa Inna tana nan da zai samu sauƙin haka, kai ka yanke hukuncin rabuwa da Aisha, sannan ka kwace shi kasan illar da ka mishi? Ka saka ya tashi mara hakuri, Eh Aliyu yana da zurfin ciki domin babu wanda yasan irin ukubar da ya sha a hannu Hawwa da shuwa, don haka bai tab'a gayawa kowa ga damuwarshi ba, akan Ummu Hadiyya ne baya iya hakuri, akan Ummu Hadiyya ne baya boye b'acin ransa, domin duk abin da ya faru kai ne sila, ban da Allah ya taimaka Uwarshi bata barci a kanshi har yan uwansa ai da abin da Aliyu zai zama sai yafi haka tow Allah baya barci kuma shi ba azzalumin sarki ba ne. " ta fadi haka tana fitowa waje, ganin yadda aka tsatssya yasa ta cewa. "Da alamu matsalar gabanku bai ishe ku ba ko ? Har sai kun kara da na Tafida!" Tuni kowa ya watse, ta shiga dakin har lokacin bai daina fada da masifa ba. "Deeni kyale shi ya je, tunda har Ummu Hadiyya ta iya tsallake Yaranta a gadon haihuwa babu abin da zai bata mamaki ko tsoro ya je ya tunkare ta, har yaushe zaka girma Baba Ali? Yaushe zaka yi hankali? Tow zuwa yanzu Borno da Al'ummar borno suna kanka sai ka cigaba daga inda ka tsaya, Amma hargowa da hargagi ba zai kara maka kome ba, sai dariyar waɗanda basu son kayi gaba. " daga haka ta juya ta bar dakin Inna, a can bangaren Shuwa daurawa suke suna kuncewa domin Aliyu dai irin mutanen nan ne da yau aka yi aiki kansu gobe zai iya yin sanyi ko ya lalace. Don haka koda Samha ta gaya mata Ya Tafida yana can yana fada akan Ummu taki zaman dakinta tayi jego wani murmushi ya kwace mata, "Alhamdulillahi ta nan muka yi nasara......🤔YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 04 "Ke tashi aikinmu yayi kyau!" Girgiza kai Yarta Sa'adiyya tayi tana faɗin. "Ba dai akan Tafida ba, na san waye shi na kuma san me yake yi a cikin kashi goma na aikinmu dakyar daya yake kama shi, tow bari na gaya miki a dakinta ma ya kwana karewa kenan kin ga kenan babu batun wani aiki yayi kyau. Ni na gaji da zubawa yan iska kudi ki nimo wata hanya amma Tafida baya cikin mazan da asiri ko tsafi zai kama su, domin nayi imani da Allah kaf gidan nan babu wanda ya kai shi ibada da tsayuwar dare, lalacewa da ake kallon yayi yafi wadanda ake musu kallon kintsatsu sannan ke kanki shaida ce yadda na gama lalacewa da bin maza ina amsar kudi tow Tafida a idanunku yake mutumin banza amma a zahirin gaskiya yafi kowa samun Allah, sannan ban da sharrin da muka mishi bana jin har akwai abin da zai kama Tafida tunda kowa ya ga abin da ya faru hatta matarshi ta gani amma ta kare tana zama da shi a haka ne dai ki nimo wani hanya idan har haka zai saka ya rabu da ita wallahi bar ganin yana ihu na rantse da Allah son da yake mata ya wuce baki ya faɗa, domin kuwa na gani akan idanuna." "Ke kada ki mai dani yar iska, kina nufin Aliyu yana son wancan bakar Yarinyar?" "Kwarai da gaske, baya sonta zai dinga hawa kanta yana sauka? Baya sonta zai dirka mata ciki? Baya sonta zai haukace ta ce ta dawo dakinta tayi suna? Jiya fa har na shirya zan bishi ya ce kada na sake yaga kafata a wurin bikin rantsar da shi tunda bai min alƙawarin nice first lady ba, gaya min wacece First Lady?" "Ke mana, ai ya gayawa Babanki tuntuni ke zai bawa wannan matsayin." "A'a ba dai haka aka yi ba, sai dai idan kune kuka roka min ya bani!" "Ke ki min shiru yarinyar da kike magana akai ko jami'a bata shiga ba balle ayi maganar wani matsayi. Nasan nan duniya babu wata first lady sai ke!" Mikewa tayi zata fita domin ita kan Sa'adiyya bata jin zuwa yanzu zasu sake samun kan Tafida don yayi gaba. "Ina zaki bamu gama magana ba!" Juyawa tayi idanunta cike da kwala ta ce mata. "Watannin baya kin san dalilin da yasa Tafida ya kora Hadiyya gida?" Girgiza kai tayi tana kallon yarta da take ciki da mamaki. " murmushi Sa'adiyya tayi tana faɗin. "Nice nan na saci kudinsa na yi amfani da shi, kuma nasan bayan shi da Hadiyya babu wanda yasan inda yake ajiye kuɗi, na kwashi sauran na kai dakinta na boye." Goge hawaye tayi tana kallon Hajiya shuwa da kyau, "amma kin san me? Da yazo yana bincike na ce ban sani tunda ban san inda yake ajiyar ba, hmm kiran Hadiyya yayi ya ce ta tafi gidansu sai ya zo da kanshi. Bayan yasan ko me zai ajiye ba zata tab'a dauka ba. Tana barin gidan ya turke ni sai da na gaya mishi gaskiya ya kyale ni kin san me ya ce min? Kin ga wancan yarinyar da muke renata ko me na ajiye idan ban ce ta ɗauka ba da shi da banza daya ne, wallahi kin yi na karshe kada ki sake raina ya kuma b'aci wallahi kika sake na kuma kama ki sai na wulakanta ki!," murmushi tayi tana share kwalla ta cigaba da kallon Hajiya Shuwa. "Kina tsammanin zan kyale ni ne idan ya gano abubuwan da nake aikatawa na son rai!" Daga haka ta juya huci Hajiya Shuwa take tana jin lallai koda zata yi yawo tsirara sai yarta ta zama first lady na Maiduguri. --- *Ummu Hadiyya* Cikin barci naji wayata tana kara, a hankali na lallubeta na saka a kunne. "Assalamualaikum!" "Waalaikumun salam, Ummu Hadiyya!" Bude idanuna cikin nauyin barci nace. "Na'am?" "Maman Ilham ce, gamu a unguwarku ban san inda xan fara ba ne!" Tashi nayi zaune nace mata. "Aunty Saimah! Ki ce a nuna miki gidansu Aunty Baby'sMama kitchens!" "Ok!" Tashi nayi zaune ina me tattara sumar kaina, domin na wanke dazun da safe, na saka ribom na kama shi, sannan na shiga ban daki na kama ruwa na fito, ina kokarin zama naji sallamarta. "Assalamualaikum! Ikon Allah matar nan ashe har kin haihu? Ni da nace ki gaya min idan haihuwar tazo muje asibiti." Murmushi nayi ina sosa kaina, ina kallon Yaran. "Ikon Allah dama biyu ne Abban Ilham yaki gaya min, lallai zai sani." Ta fada tana shigowa dakin. "Aunty Saima zauna mana!" Na fada ina kokarin saka hijab xan fito waje. "Idan ta ni ce koma ki zauna sai da naci abinci kafin na fito kin san ba don rantsar da Tafida ba ni da borno sai kin haihu!" "A'a bari a kawo miki ruwa!" Haka na fito na samu Uwani ce a tsakar gida tana tattan kunun yamma. "Uwani ki had'a min kome ina da bakuwa!" "Tow Aunty Baby!" Na koma ciki, ina hada faɗin. "Kawai sai kuka ji labari ba!" "Wai kawai ashe ke da Aliyu kuka tawo asibiti!" "Eh wallahi kin san Hajiya Kaltuma bata gari tafi bikin yar Yayarta kuma kin san hidima baya karewa a familynta. Kin ga Inna kuma girma ya cimmata town waye zan kira a wannan daren?" "Hajiya Hawwa da Shuwa fa!" Murmushi nayi bance kome ba domin bana fatan na fadi kome har abada tsakanina da su idanu. "A'a kawai Ni ce nace muje asibitin idan ban haihuwa ba a nimo su." "Amma Ummu baki dauki kasada ba?" "Salamun alekum!" "Uwani oho Assalamualaikum ake fada fa!" "Tunda kin gane ba shi kenan ba, ke dai akwai son gyarawa mutum abu!" Dake abokiyar wasata ce yar Kanin Mama ce na kuwa ce mata. "Ai kuwa kina yin kuskure zan gaya miki katuwa kawai!" "Eh na yarda ke kuma Yar mitsila!" Dama can tun fil azal haka muke da ita. Ta juya tana kallon Yaran ta ce min. "Allah yasa kada kuyi halin Aunty Babyn roba!" "Allah ya taro mana ke!" Na fada ta juya ta gaida Aunty Saimah. Dalilin shiririnta Uwani aka share batun haihuwa, muna cikin hira sai ga Yayun Aliyu mata da biyu, Aunty Maryam da Aunty Rukayya, kallon Maman Ilham suka yi. "Eh ba dai Ya Abubakar ya baki labari ba ?" "Eh ai kunsan haihuwa da mutuwa bata boyiwa kafin ya gaya min makotana daga Abuja suka kirani suna min barka ashe har IG an daura yaran Baby'sMama kitchens." Tab'e baki Aunty Rukayya tayi tana latsa wayarta. "Ina wuninku!" Na gaishe su, a lalace suka amsa. Ban damu ba itama kuma Maman Ilham abin ya bata haushi tuni ta hade rai, ta dauki zobo tana sha. Taki mika musu Yaran. "Uwani!" Na kirata. "Aunty Baby gani nan ba sai kin fada ba, the first lady of Borno state." Kallon juna muka yi da Maman Ilham muka saka dariya. "Wato Uwani nan taku yar gari ce." Shigowa tayi da katon ture ta ajiye musu cikin zolaya ta ce min. "Banda mugun hali irin naki, kiri-kiri kin hanani ganin kyakkyawar mijinki, ki rage kishi, sai dai ya kashe shi da soyayya da shagwab'a. Don Allah kada ki saka yaje office yana kasa aikin al'umma." "Uwani zanyi zagi!" Tab'e baki tai tana faɗin. "Idan kin zage ni ma kin yi a bawo, domin nice zan shiga gidan mai girma Gwamna a ta uku!" Ko su Aunty Rukayya da Maryam basu yi niyyar dariya ba, suka kwashe da dariya. Yarinya ce Uwani amma ta iya mu'amala da mutane ga kayan saka dariya. "Kada ki damu indai tafida ne kamar kin ganshi."inji Maman Ilham, murmushi tayi ta fita kamar ba zasu sha ruwan ba suka sha Aunty Rukayya ta ce min. "Sai mun roka ne zaki bamu Yaran!" "Amma a bisa alada ba ita ya dace ta mika muku Yaran ba" ta fada tana mikewa ta dauko yaran ta basu. "Ikon Allah! Maryam yaran nan kamar lokacin da Hajiya ta haifi Tafida sak-sak da shi,.ina da hoton har yau." "Wai ni kuna jin labarin Hajiya kuwa?" Inji Maman Ilham, kallona suka yi suna jiran karin bayani. "Baby ya labarin Hajiya?" Hmm kusan wacece Hajiya? Mahaifiyarsu ce fa, idanuna ne suka cika da kwalla na ce mata. "Hajiya tana lafiya sai dai kuma bata jin dadi gaskiya." Na fada ina dauke kaina. "Allah ya bata lafiya!" "Amin Ya Allah!" Na fada bayan sun hade baki sun mata fatan sauki, hira suke jefi-jefi Mama tayi sallama ta shigo. "Oyoyo Mamana!" Dakin ta shigo tana me sallama. " Sannu ku da zuwa. Uwani baki kawo musu alele ba sai kayan ruwa ba kome a gabansu baya akwai alele da dan wake da doya da kwai maza a kawo musu ga babba me shiririnta da ta kasa magana, a zuba musu farfesun kajin nan maza don me Alhaji da Babanku suka kawo ba don a ciyar da masu zuwa Barka ba, maza a kawo musu abincin." Ta fada tana me kallona. "Kin ci abinci? Jego ba zai yiwu ba sai ciki ya dauka musamman wancan cinye du din don yafi yar uwarsa cin abinci. Maza hada shayin kisha." "Mama nasha fa bakina ne ba dad'i." "Ayya Ummuna daure kisha idan baki ginu ba, ba zaki iya daukar wani laluran nan kusa ba, amma idan kika ginu nan da wata shekara wani labrin ake." Mamaki ne ya maka su yadda suka ga Mama tana ritita ni, haka Uwani ta shigo musu da abinci, tana ajiye musu Mahira tana kawo min tuwon alkama miyar kuka danya wacce aka daketa kamar karkashi ta sha kayan kamshi, ta ajiye." "Aunty Baby Yan grp suna gaida ke, wai sun yi kewarki don Allah yaushe zaki cigaba da sanwata alfaharina!" "Ke Mahira yafi can kyaleta da wayarnan!" Dariya tayi tana faɗin. "Sweetheart kuna barci ko? Sai kun tashi xan zo muyi wasa;" "Sai ki hada har da kasa da yashi a bude muku fili Sabuwar uwa ta fara hauka!" Ta fita tana dariya, duk kin Allah aunty Rukayya sai gashi ta sake suna cin abinci hankali kwance. Fita Mama tayi ta bamu wuri can sai gata da wani kofi dauke da dafaffen madara. "Mama yanxu nasha tea." "Ungo naki, gyaran jiki babu ruwansa da kin sha ko baki sha ba, maza sha." Haka na amsa ina kallon madaran har mai mai yake yi kamar zan yi kuka na fara sha. "Wallahi kin more, irin wannan kulawar waye zai samu ji yadda Mamanki take kulawa dake!" Inji Maman Ilham, dariya nayi kaina a kasa na sha rabin madaran na ajiye. "Kin san nice Babba kannena duk ba ita tayi musu jego ba, asalima ba a dauko wanka a gidan nan, nice dai nazo da kaina!" "Assalamualaikum Mama ga sako daga Baba wai dafawa Aunty Ummu Baby!" "Sai dai Uwar baby yanxu ta tashi daga baby ta koma Uwar baby." Murmushi Aunty Maryam tayi tana faɗin. "Kanwarki nan akwai abin dariya!" "Uwani ba, ai ba ita ɗaya ba ce a kofar shiga kun wuce wata tana sayar da abinci a shago. Zakiya kenan Yaranta ne anan suke zaune abinci suke sayarwa idan sun yi aure ko kafin su yi aure za a kawo mata wasu." Ware idanun suka yi. "Kamar Ya?" "Kusan dake mu talakawa ne amma muna da burin mu cigaba idan har zaki iya hakuri ki kuma kame kanki zaki nime kudi Mama bata da matsalar kome, yanxu ita Uwani public health ta karanta, kuma next year zata gama, tana abinci da safe na karyawa an fara maganar aurenta idan tayi aure Akwai kanwaart zata zo ta fara karatu da sayar da abinci." "Kuma ya batun kayan daki?" Dariya nayi ina na saka hijab na dauki Mufidah da take dan rigima na bata ruwa ta sha sannan na bata nono. " kayan dakina waye yayi min? Ita tayi min haka suka kayan dakinsu da kome hatta garan da zata miki na shekara daya duk ita ce! Ai mace ce me kamar maza." Na fadi haka ne saboda yadda suke ganin kamar nauyi aka daurawa Dan uwansu. "Ummu ni gas cook ɗinki nan Amma ba a Nigeria aka saya ba?" "Eh kanina Ahmad da yake Turkiyya ya gani ya turo min na tura mishi kudin ya kawo min an karshe hatta kayan kitchen dina da furniture duk a can muka saya." "Amma aka ce mana Abbanmu ne yayi!" "Wai da gaske?" Inji Maman Ilham, murmushi nayi nace mata. "A'a kayana ne da Uwata tayi min da guminta domin yar kasuwa ce kuma a gidanta nake sayar da abinci." "Amma mu kuwa aka gaya mana duk abin da aka kawo miki Abba yayi miki!" "Eh zasu fadi haka saboda yadda Abba ya dauke ni kamar yarsa!" "A bar wannan zancen yaushe zaki koma domin mun fi son ayi suna a can!" Murmushi nayi ina kallon Aunty Rukayya da tayi maganar nace mata. "Ina ga mun magana maganar nan da shi ai, ba zan koma gidan Aliyu ba, ai yanzu ya isa matakin da yake bukata suna kuma zaku iya zuwa ku dauki Yaran ku tafi dasu babu matsala, amma yadda na dawo dakin Uwata babu me fitar dani sai gawata!" Na fada ina murmushi. "Wai me yayi zafi ne? Naga dai kuna zaune lafiya zaki dauko tashin hankali, daga haihuwa da rantsarwa sai ya zama tashin hankali da niman rabuwa yanzu haka yana can yana ta faɗa." Cikin girmamawa nace mata. "Ko me zai yi yayi kawai amma na zan koma ba." "Kamar ya ba zaki koma ba?" "Akan me kike tambayarta? Kada ta koma ya ce anjima idan yazo zaki bashi Yaranshi." Gyara zama nayi da kyau nace musu. "Ku bari na hada muku har da kayansu ku tafi da su!" Na mike tsam na fara hada kayansu tsaf, sannan na ajiye musu. "Gasu nan, idan kun isa ku ce ina jiran sakonshi." "Ummu Hadiyya ban san ki da wannan halin ba!" Murmushi nayi mata nace mata. "Maman Ilham, baki sanni da wannan halin ba, amma yanxu zaki sani ai sun san waye Tafida don haka su dauke Yaranshi su kai mishi bani daga cikin Matan da namiji zai yiwa barazana da Yara kafin na same su sai da na shekara ashirin da takwas, kafin Allah ya kawo shi kin ga na haife su ina da shekaru talatin, gara a kai mishi Yaransa." Duk sai jikinsu yayi sanyi. "Amma me yasa tuntuni baki bukaci haka ba?" "Yo ina nake da yancin yin haka yanxu da nake da Yanci ba gashi nayi ba." Kiran wayar Aunty Rukayya akayi ta kalle Aunty Maryam ta ce . "Kin ganshi nan!" "Sai ki dauka ai!" "Daukar wayar tayi tana faɗin. "Ayya Tafida kayi hakuri mana!" "Ina karamar mara kunyar?" Mika min wayar tayi na saka ta a handsfree. "Ina jinka!" Na fada a dake. "Meye nufinki? Ki zubar min da mutuncina a gari ko me?" Dauke kai nayi gefe nace mishi. "Yo na ga ba mutuncin ne da kai ba, gara na watsar da sauran a titi kowa ya huta!" "Hadiyya!" "Na'am Uban A'isha!" "Akan me zaki sakawa Yata sunan A'isha? Na gaya miki bani da lokacin zuwa ne nayi masu huduba, maza ki biyo su Rukayya su kawo ki gida idan na haka ba raina zai b'aci." Kamar bai ji haushin abin da na fada mishi ba nace mishi. "Na rantse da Allah, ba zan dawo ba kuma na gaya maka kafin na barbad'a da sauran mutuncinka, ka sake ni ma gaya maka!" Tass naji an dauke ni da mari a zafaffe na d'ago kai, Mama ce a tsaye jikinta yana rawa. "Kika ce me?" Ban dawo daga wancan marin ba ta kara min wani sai da naji bana ji sosai. " mama ki gaya min meye zan yi da Aliyu? Me xan yi da zuri'arsa? Mutumin da ya ke kyamar uwarsa? Alhamdulillahi da Ya bani Uwa irin ki da ta tsaya min ta hana ni kuka amma kiyi hakuri na rantse da Allah ko a lahira bana fatan tashi a matsayin matar Aliyu Tafida na gaji da auren shi Gara ki kashe ni da ki ce na koma gidan Aliyu domin ni nasan makara zaki tura ta dauko ni. Duk da ina son Yarana Amma na hakura a kai mishi Yaransa na yafe su, yaji yadda ake ji idan da gayya Hajiya ta tafi ta barshi a tsummar goyo yaji yadda take ji shima ai Ubane kuma yasan Uwarsu tana raye don haka a kai mishi Yaransa, kuma wallahi yana ji ki gaya mishi aurena da shi ƙaddara ce, Mama bana son na bude miki cikina amma gashi yana jina idan karya nake mishi, Aliyu baka ce min idan na gama nayi har sata ko bin maza na ciyar da kaina ba? Ko baka gaya min cewa na tafi wurin Wanda ya aure maka ni ya ciyar dani, ba don kasan kai kafara ba da ka musanta Yaran nan ba naka bane karya ne?..........(Tirkshi 500₦ kawai fa na bukata🤔 domin warware wannan rikata-rikatan)YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 05 Cikin sheshakar kuka na ce mata, "ki gaya min akwai abin da ya fi haka muni saboda kawai Miji baya kaunarka yace ka fita ka bi maza ko kayi sata bai dame shi ba? Mama gasu nan a gaban idanunsu yake cin zarafina sun tab'a dakatar shi? Addu'a nayi tayi ba dare ba rana Allah ya ara min ranar da zan mara ashe cancanci a dafa min ba? Yana ji tunda ya iya cewa ba don shi ya fara tarayya dani ba, da ya ce cikinsu Mufidah ba nashi ba ne, amma babu yadda zai musanta hatta a gaban jama'a da danginsa ya gaya musu idan na gaji da kafata zan tafi tow na bar mishi gidan shi don Allah ku kyale ni na huta." Jikin Mama kamar an watsa mata ruwan sanyi haka ta fita, Aunty Rukayya suka kasa magana kowacce kanta a kasa, kafin suka mike. "A dai yi hakuri kome na duniyar nan dan hakuri ne!" "Da yake a jikin bishiya na fado, Ni yar talaka mara galihu, shi yasa da yayi babu me ce mishi ya daina domin shi d'a ne da Uwa ta haife shi ni kuma mahaukaciya ta haife ni " girgiza kai Maman Ilham tayi tana faɗin. "Ko daya kina da ikon niman hakkinki ma, babu me dakatar dake da nasan haka ne wallahi ba zan fara zuwa ba domin ban isa da wannan abin kunyar ba Ummu Hadiyya Allah ya huci zuciyarki." Daga haka ta ajiye min kuɗi fa ban san nawa ba ne, suka min sallama suka fita. A tsakar gida suka samu Mama tana lissafin an kawo mata wake. "Har kun fito?" Ta tambaye su da sakin fuska. A kunyance Maman Ilham ta ce mata. "Eh Mama, zamu tafi!" "Tow mun gode fa!" Ta musu godiya, abun mamaki yake bawa Aunty Rukayya suka fita dake gulma na cinta ta cewa Aunty Maryam!" "Ban gane yarinyar nan Uwarta kasuwanci kawai take yi ne ko da wani abu?" "Yar kasuwa ce kuma kin san ai muslunta tayi shi yasa bata damu da sauran abubuwan da matan hausawa da kanuri suke ba, ita niman kudi kawai ta iya." "Amma kuma idan har ita ta yi tarbiyyar Ummu Hadiyya da alamu ta samu tarbiyya me kyau tunda har kowa yasan cewa Ummu Hadiyya tana da kirki ta ina Tafida ya rasa na shi tarbiyyar da har ya iya ci mata mutunci kuna gani kun kasa magana!" "Hmmm!" Inji Aunty Maryam da tasan kome domin har gidan take zuwa taci mutuncin Ummu ta ce mata. "Wallahi ki bari kawai, amma abin bai yi dadi ba!" Haka suka isa gidan Babansu domin Tafida yayi kira ya kai goma babu wanda ya ɗauka, yana ganinsu ya mike. "Ina Yarana?" "Ai Gara ka cire rai akan Yaran domin Ummu ta rantse ba zata dawo ba, idan kuma ka nace kaje ka dauki Yaranka ta ce." "Wani irin hauka ne wannan?" Ya fada a harzuke. "Zafin kanka ba zai hana kome ba, abu mafi alkhairi ka sauke girman kai ka nime sulhu babu abin da yake kawo zaman lafiya kamar sulhu." Inji Safiyyudeen. "Akan me zan nime sulhu da ita me na mata?" "Kai zamu tambaya." Kamar ya fasa ihu ya kurawa Safiyyudeen idanu. "Me kake bukata?" "An jima zamu gidansu muje da kayan Barka idan muka je kada ka sake ka b'ata min aikina!" Suna cikin tattaunawa yan party dinsu suka tawo tare da Mr Abdullahi deputy suka iso gidan, aka bude musu babban parlour baki, suka zauna aka fara taya juna murna kafin suka shiga tattaunawa akan abin da ya kawo su. Safiyyudeen yana tare da shi yana kokarin kwantar mishi da hankali, tare da aron bakinsa yana cin albasa har aka gama meeting din suka tafi. Ya kalli Safiyyudeen ya ce mishi. "Deen me yasa ka hanani magana!" Murmushi yayi ya ce mishi. "Ranka a fusace yake, idan aka ja maganar kwamishinonin nan laifin Ummu zai shafe su." Murmushin takaici yayi yana me kwantar da bayanshi a jikin kujeran parlour din ya ce mata. "Na cancanci haka daga Ummu?" Girgiza kai Safiyyudeen yayi yana faɗin. "Ko kaɗan, sai dai itama tayi haka ne domin niman yanci." Kankance idanunshi yayi yana kallon Safiyyudeen. "Dama bata da yanci ne?" "A wurinka fa bata da yanci ita da da baiwa daya ce, sannan duk abinda ya fada baka musu ba shin laifi ne don Ummu ta nime Yanci?" Kurawa juna idanu suka yi. Kafin ya cewa Safiyyudeen. "Na ga ai ba wani abu ba ne ko?" "A wurinka da wurin kowa naka ba wani abu ba ne, amma a wurina da ita wani abu ne, idan da Ummu ta zauna tow tabbas zaka kashe ta ne da takaici domin kuwa akan Yaranka ma zaka kara dagula mata lissafi, amma akan kanta da ta zabi barinka da Yaranka ina ga ya kamata ka fahimci ba kowani mutane bane ake cutar da shi yayi hakuri akwai masu iya shanye kome kamar Ummu tayi hakuri yanzu da tace ba zata hakura ba ya kamata kai ka sauko da kanka!" "Never!" Ya furta kamar zai mangare Deen da yake bashi shawara. Kiran wayar Deen aka yi ya mike yana faɗin. "Zan je na dawo Madam tana niman dan saurayinta." tsaki yayi ya ce mishi. "Banza wawa me rami daya ni biyu ne gare ni!" "Gaskiya kan gara kai ni daya ne idan ta rufe ramin asirina ne zai tonu!" Ya fita yana dariya. "Sai me idan bata dawo ba, ina da wani ramin wallahi kuma a yanzu zan tafi kodumo!" "Aikin kenan Hajiri!" "Yes!" Ya fada yana dariya, a kofar gidan suka hadu da Mahmud, "Har ka iso?" "Eh wallahi!" Suka mikawa juna hannu sannan suka yi sallama. Mahmud ya shiga yana mu Tafida zaune yana kallon wakcyarshi. "Mai girma gwamna da kanshi me aminai biyu ango yar baka mijin yar fara!" Kiran wayarshi aka yi ya dauka ya kara a kunnenshi. "Don Allah don darajar Iyayenka kada ku tasa maganar Ummu!" "Ok Kanin Ubana, Bagwai." Ya kashe wayar, yana murmushi. "Yallabai kana dai sane da ina jiran appointment dina!" Murmushi Tafida yayi yana faɗin. "In sha Allah ina sane da kai!" "Yaushe zamu je ganin Madam da Yara ne?" Girgiza kai yayi yana faɗin. "Sai na samu lokaci!" "Allah ya kai mu. Haka suka yi ta hira har lokacin sallah yayi, a daren ranar suka nufi gidansu Hadiyya. *Ummu Hadiyya* Tunda rana da abin nan ya faru Mama bata kuma min magana ba, nima kuma ban takaleta ba gudun kada samu matsala sai dai naga kamar jikinta yayi sanyi bayan sallah Isha ina shan kunu aka yi sallama daga yadda naji Muryan Baba nasan Tafida yazo don haka na gyara zamana, ina saka hijab mama tana sallah, suka shigo dakin. Dake akwai wadataccen haske da ni suka fara arba, kallo daya nayi musu na dauke kaina. "Sannunku da zuwa Yaya Deen!" "Barka dai mai jego akwai kunun kanwa?" "Eh har da yajin kunu, ya aka ji da Jama'a da hidima!" "Alhamdulillahi!!" Ya fada yana kallon Yaran da aka nad'e su cikin shawal. Sallama Mama tayi suka gaisa sannan ta mike ta basu yaran, sannan ta fita ta kawo musu abinci tuwon laushi da miyar kuka, sai kayan yaji da farfesu. Kunya ya hana tafida nutsiwa kamar ya nutse domin bai zata zai ga Mama a dakin ba, a hankali Deen ya ce. "Ni fa Hajiya Ummu nayi missing abincinki don haka ci zan yi wallahi!" "Bani nayi wannan ba, my Chef My Master ita tayi Mama wannan girkin!" Murmushi yayi ya ja kwanon ya wanke hannunshi kafin ya fara cin tuwon laushi da yaji tuki, sai miyar kuka da yasha namar rago, yana ci yana gyada kai. "Dole na turo Sadika ta dauki course domin na yarda Mama ita karshe ce." Murmushi yayi, kan tafida yana sunkuye ya saka yaran a gaba yana kallonsu. Sai da Deen ya ci ya koshi sannan ya ce mata."gaskiya ba don kada nayi abin kunya ba da nace miki ayi parkinge dinsu zuwa gida ayi min dumame wallahi!" Zungure shi Tafida yayi yana hararanshi. Can aka fara shigowa daki ana gaida Tafida sai da Baba ya fito ya tsawatar domin har makota sun fara shigowa. "Malam Ummu ko nace Hajiya Ummu Hadiyya, nazo ne akan batun taron suna domin yallabai zai tafi umara ibada!" Tab'e baki nayi nace musu. "Ku yi taronku a can family house dinsu ni zan yi nawa anan!" A zafaffe ya d'ago kai yana kallona, nayi kamar ban ganshi ba."amma da kinyi hakuri an hadu anyi ba, zai fi kwanciyar hankali da nutsuwa." "Waye ya aike Ni? Na je gidan tafida nayi suna, wai kawai ka bashi shawara na janye igiyar da aka zarga mishi da ya takura mai don Allah!" Wasa wasa tun karfe takwas muke tukawa har sai da goma tayi bamu cimma matsaya guda ba, na kafe suma sun kafe. "Idan ya dage sai nazo anyi suna ga Yaranshi dama Yaranshi ne ba nawa ba." "Ok ba xan karbi yaran ba, kuma ba zan sake ki ba za ayi sunan yadda kika ce amma ki sani wallahi babu shegen da ya isa raba auren nan zan nuna miki iyakarki a garin nan da ni kike wasan." Wani dan iskan dariya nayi nace mishi. "Ai kuwa sai dai na zauna da aurenka da na koma gidanka mu zuba mu gani Allah ya bamu sa'a." Tun daga ranar kowa ya fahimci ai babu zaman lafiya Mama tayi tayi na koma naki, kowa kai hatta dangin Aliyu sun zo amma na zuba musu idanu suka gama magana nayi murmushi kawai. Haka muka cinye kwanakin har ana jibi suna saniya daya da raguna biyu aka kawo, Ummu Kulsum da Ummu Rooman sun zo, aka ana gobe suna sai ga Hajiya da Kanwarta Umma Yaanah a gidanmu suka sauka. Ta ga Yaran kamar tayi kuka ta kalle ni cikin rarrashi ta ce min. "Allah ya miki albarka, amma a yafewa Babana banki a hukunta shi ba amma kada a ce za a rabu dashi wallahi bai kyauta ba bana bayanshi don Allah kada a rabu da shi." Matar tana da mutunci ba zan iya mata musu ba amma nace mata. "Kiyi hakuri sai na duba yiwuwar zamana dashi." Haka ta hakura har aka yi suna a daren sunan ya turo akan dauke ni da yara suna wani gidan shi aka taa daukar mu hoto, ana gamawa ya karbi tukin motar har mun hau kan hanya ya ce min. "Ke ba kowa ba sai ninkin ake kina batawa mutane rai, na barki dai ki yi wanka idan kuka gama ki dawo dakinki!" Juyawa nayi na kalle shi ina murmushi na ce mishi. "Ina ga ya kamata na gaya maka gaskiya don na lura baka fahimta sosai. Ba xan dawo gidanka ba. Kuma idan kace zaka min dole zan baka mamaki!" A fusace ya ce min . "Allah ya baki sa'a!" "Ai ya bani Uban A'isha Baban Muhammad!" Na fada daidai ya iso kofar gidanmu. "Ni da kai Allah ya bamu sa'a!" Na fada ina kara rungume Yarana, fitowa yayi ya dauki Mufid ina rike da Mufidah har cikin gidan, kada ku dauka wani abin arziki muke yi tsakanina da shi gasawa juna magana muke, domin kuwa ya hau dokin zuciya, har cikin gidan ya shiga anan ya ga Hajiya dauke kai yayi bayan ya gaidata sama sama, Mama tayi mishi nasiha da mishi fatan alkhairi da nuna mishi ya manta wani nauyi da ya kasa saukewa, bai ce kome ba yana zaune ya turo min text. "Ki ce mata tazo ina son ganinta!" Cike da mamaki nake kallon Tafida Mahaifiyarsa ce fa? Innalillahi wa innalihir rajouna! Hadiye kukan da yazo min nayi ina kallon Hajiya cikin tausayi ya saka kai ya fita, "Hajiya tana son ganinki ya ce!" "Tow!" Ya fada cikin sanyin murya sannan ta mike ta bi bayanshi, kuka na saka har da shasheka. "Mama Uwarsa ce fa!" Girgiza kai tayi tana kallona, "Uwar da ta haife shi! Mama Aliyu ya halaka!" Girgiza kai tayi tana faɗin. "Kul koda wasa uban Yaranki ne addu'a yake bukata." "A'a Mama son rai ne irin nashi, Aliyu son kanshi yayi yawa ba zan iya zama da shi ba, duk me sabawa Iyaye yana tare da fushin Allah........'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book *Assalamualaikum don Allah kada a tura payment ta GTBANK babu network zan saka Opay dina* 06 Madadin Mama ta taya ni jin haushin abin da yayi sai ta koma tana bani laifin da cewa. "Aliyu bai da laifi me yasa ke baki ja shi a jikin kin nuna mishi girma da hakkin Uwa ba? Me yasa baki gaya mishi azabar Allah akan wanda ya watsar da iyayenshi ba? Kawai kina tsammanin Aliyu zai gyaru ne domin yafi kowa? Ke ya kamata ki nuna mishi hanya!" Sake baki nayi ina kallon Mama hala ta manta mazan zamanin yau ba irin mazansu na da ba ne, "Aliyu kamar yaro yake ko nace duk wani namiji kamar yaro yake." Ganin yadda fuskana ya sauya ta ce min. "Bakya jin dadin magana ta ko?" "A'a!" Na fada a sanyaye, Mama bata yarda tayi mana goyon kawai ba, ta ja mu a jikinta sosai. Cikin hade rai yake wani kaukauda kai tare da kunkuni yana faɗin. "Kin san yanayin da ake ciki kin zo taya?" Yadda zaka fahimci lamarin uwa sai Allah ita ya dace ta tsaya a sama amma ta kaskantar da kanta cikin yanayi na rarrashi ta ce mishi. "Ayya gadanga kusar yaki kayi hakuri, na zo ganin likita ne!" Ta fada da dan rawan jiki. "Tow gaskiya ki koma idan kin ganshi!" Cikin kulawa irin na d'a da uwa ta kalle shi tana faɗin. "Gobe in sha Allah zan koma!" "Anan zaki kwana?" Ya tambaye ta idanunshi bude. "Saboda nan yafi kusa da asibiti ne!" Shiru yayi kafin ya ce mata. "Ki zo mu tafi za a duba ki." "Tow Ummu Hadiyya ta ce zata raka ni!" A yadda ya fahimce ta tana son lallai su tafi da ita Ummu Hadiyya ne, don haka ya barwa kanshi haka matsayin damar da zai sake magana da Ummu ta dawo dakinta. "Tow sai dai mu tafi yau gobe ta same ki a can! Domin ina sauri ne." "Tow bari na dauko kayana!" Ta shiga cikin gidan, can sai gata ta fito tare da Maman Hadiyya, har wurin motar ta rakata, shima cikin girmamawa yake kara godiya wa Mama. Ina kwance Mama ta shigo, tana faɗin. "Ke ni banga kome da Tafiya yayiwa Mamanshi ba, kece dai mai gurguwar fahimta." Shiru nayi ina me gyara kwanciyar Mufeedah tare da mata addu'a, sannan na kwanta. Washi gari da safe ina farkawa da sakon Tafida na fara cin karo. *Inuwar alli! Mahmud zai zo daukarki!* ban kula shi ba nayi wanka na gyara jikina sosai, sannan na dauko wata English wax na saka me yakuwa, sai babban mayafin da lullube kaina bayan na karya d'an kwali. A hankali na zaro takalmin lefena grey colour da jakarshi kasancewar Mayafina ma grey colour ne. Domin akwai a jikin zanin. A hankali na kalli kaina a mirror dakin, fuskana tayi kyau da alamun jego ya amshe ni. "Ke dai ta wurin saibi kece za a bawa lambar yabo, fisabiilillahi ke ba yarinya ba amma kullum kece a karshen shiri." Inji Mama da ta shigo dakin. "Ga Nana jikar Hajiya Amina zaku tafi tare!" Ta dasa aya tana kallona, domin kuwa ban yi mamakin kallon da take min ba, "duk zuwa asibitin ne ya kawo wannan shigar?" Kallon kaina nayi kafin nace mata. "Kin san zan kai Mufidah ta ga likitan idanu! Kuma kin san yadda al'amarin yake ana ganina tagajam magajan za a fara surutai a kaina!" Na fada karamin murmushi tayi sannan ta ce min. "Na fahimta Allah ya tsare!" Haka muka fito ni da yaran, dakin Baba muka fara shiga na gaishe shi sannan ya ga Yaran yayi musu addu'a, kafin na wuce bangaren Ummi da Umma. Sannan na fito, ina zuwa waje na samu har Mahmud din ya iso, wani haɗe rai nayi na nufi bayan motar na shiga na cewa Nana. "Ki shiga gaba!" Murmushi yayi yana me jan motar bayan mun shiga. Kin yarda nayi na zauna inda zai na kallona, na koma gefe na zauna ina kallon gefen hanya. "Hajiya Ummu ya kwana biyu, da fatan ba ayi fushi da rashin zuwanmu ni da Madam ba ko?" Magana yaƙe son nayi da shi, amma fir naki ma cigaba da kallon gefen hanya, asibitin koyarwa na garin Maiduguri muka nufa, tun kafin mu isa inda suke security suka tari motarmu. Sam haka bai min ba, amma na share ni ban tab'a mafarkin irin wannan rayuwar ba. Tun kafin na isa inda suke manyan staff na asibitin suka yi ta fitowa ana min Barka da zuwa, MD na asibitin ya amshi Mufidah, yayinda mataimakinshi ya amshi Mufid a bayan Nana. Muka shiga cikin asibitin bayanshi na hango yana duba marasa lafiya. "Ina Hajiya?" Na tambayi Safiyyudeen. "Tana office din MD." "Tow ka kai ni wurinta!" Kasa yayi da murya yana faɗin. "Akwai yan jarida sosai, sannan wannan abin kin ga kowa zai dauka yazo ziyarar bazata ne so please ki ɗan kame kanki!" "Jinyar mahaifiyarshi sai ya siyasantar da shi sannan zai samu yadda D sVo? Anya kai mutumin kirki ne? Idan da kai mutumin kirki ne ba zaka zo ya siyasantar da jinyar mahaifiyarshi ba, ka je kuyi yadda kuke so da nasan zuwana ba zai yi amfani ba tow babu me kawo ni nan!" Na juya zan fita daga bayana Tafida ya ce min. "My Love kin iso ne?" Wani kululun bakinciki ne ya cika ni, na juya ina kallonshi fuskana dauke da murmushin takaici. "Ih yallabai!" "Muje mu ga marasa lafiya!" Kallonshi nayi ido cikin ido. "Hmm bar min wannan kallon my love!" Takaici ne ya kama ni. "Muje!" Kafin nayi magana ya riko hannuna, wai Tafsstida ya haukace ne? Taya zai na irin wannan abin kunyar a gaban jama'a. Sai daukar mu hoto ake yana ta washe baki shi nan ga gwani. Muna tafiya ina duba agogona, har zamu wuce office din MD. "Na gaji ba ziyara na kawo ba, wurin Hajiya nazo." Murmushi yxyayi yana faɗin. "Yarinya kenan, ai Hajiya tuni ta tsufa a garinta, domin tun jiya daj dare ta ga likitan aka sallame ya yau da safe. " a hankali naji kamar numfashina zai bar gangan jikina. "Mahaifiyarka cewa kuwa?" Murmushi yayi yana faɗin. "Idanun media yana kanmu, nayi kokarin nayi rayuwa ko babu ke a cikin kwanakin nan, amma na fahimci mutane suna yawan tambayana shin da gaske muna tare? Ni kuma ina son nayi amfani da hakan domin na nunawa duniya ina tare da yar ƙaramar guntuwar matata.." ya fada yana zungure ni, yadda ake daukar hotonmu yasa na buge hannunshi ina dariya. "Wannan abin ba sabo ba ne. Amma kuma i think yazo karshe, zan bar Aliyu Tafida amma taya? Haka muka zaga asibitin aka kuma kai ni office din MD, na zauna na bawa Yara nono sannan aka kawo mana abinci bakinciki da b'acin rai ya hanani kallon ko abincin ma, Nana ce taci sosai har tana faɗin. "Aunty Baby na kwashi abincin na tawo da shi gida?" Daidai shigowar Aliyu dakin. "Idan kina so ba, ki dauka ." Na fada a hankali ina kauda kaina. "Bata ci bane?" "Eh!" Idanunshi naji a kaina, ta mike a hankali ta fito waje. Tunda ta fita yake son magana amma naki kula shi. Wayata na duba zan dauka babu ita babu labarinta. "Wayarki kike nima?" Y ajiye min akan cinyata. "Ina son mu samu lokaci na gaya miki waye ni." "Ai ban bukata ba!" "Ummu Diyyah!" "Zan tafi!" Na mike a hankali, "Ummu!" "Don Allah ka bar ni na tafi!" "Yaushe zaki dawo dakinki?" Dauke kai nayi tare da cewa. "Ina son zan tafi gida!" "Ki bani lokaci!" "Ka dauki duk lokacin da yayi maka Malam bada case!" Shiru yayi yana kallon yadda nake kokarin daukar Yaran bakiɗaya ya amshi Mufid yana faɗin. "Hajiya ta isa lafiya!" Boyayen ajiyar zuciya na sauke, tare da cewa "ban tambaye ka ba!" Daga haka na wuce ina me nufar kofar fita. jin shi nayi ya fisgo ni yana me faɗin. "Idanun duniya yana kanmu, ina ta kokarin nayi yadda ba zan cutar dake ba ki saurare ni!" Yadda yayi maganar kamar ba shi ba. A hankali na dan kara tsawona na ce mishi. "Duk yadda kayi duk daya ne Tafida kuskure na shine shiga rayuwarka, kuma cikin ruwan sanyi na fita ina ga karama gidahumar yar Mace me ya rage? Na ce me ya rage?" Kasa magana yayi yana kallona. "Zan tafi nace na sake maimata maka!" "Muje a ajiye ki!" Ban san ni ba ko kalaman da nake amfani da su yana tab'a shi, amma nasan shi da taurin kai ba zai damu ba. Haka na wuce yana me bin bayana, har wurin motar Mahmoud. Lokacin da na isa wurin motar Nana ta buɗe shi kuma yana rike da Mufid ni kuma Mufidah tana hannuna, shiga motar nayi ya kalle ni. "Ki cire number na a blacklisted kin ji!" Yadda yayi maganar sai da na d'ago shi nace mishi. "Yaushe ka zama haka? Na zata har yau hayakin na kanka bai sauka ba." "Ku huta lafuya." Ya fada min yana me rufe min kofar motar, dauke kai nayi ina kallon can gefe guda. Muna barin asibitin Mahmoud ya fara magana amma nayi banza da shi, tunda babu dalilin da zai saka yana min9ps7dzas magana son ranshi, ganin yayi naki cewa cikanka yasa shi yin shiru da bakinshi. A kofar gida ya tsaya na fito tare da Nana, ban kalli inda yake ba balle ya saka ran zan mishi magana. "Yan mata ga sakonki!" Ya mika mata irin ledar abincin. "Aunty Baby!" "Karba!" Amsa tayi na wuce na barta, muna shiga cikin gidan na samu mutane a cikin gidanmu. "Lafiya?" "Ummu yanxu muka kalle ki a hoto!" Inji Mahira, murmushi nayi da bai kai zuci ba, na wuce zuwa dakin ina ajiye Mufidah Nana ta shigo tana faɗin. "yau gani ga gwamna!" "Don Allah!" Inji Zakiya, "wallahi kada ki ganshi wai Aunty Baby ta cab'a!" Suka kama ihu kowa yana jin ina ma shi ne, matsalar da ake samu kenan a rayuwarmu baka san yadda mutum ya sha azaba ba, kawai burinka ina kai ne a wurin. Ni yanzu na daina damun kaina da rayuwar wani domin akwai abin tsoro a cikinsa. Ina zaune Mama ta shigo ta kawo min abinci. Sauka nayi kasa na zauna akan pillow ina sauke ajiyar zuciya. "Aunty Baby ga abincin nan;" "a'a na koshi nima yanzu zanci nawa, ki gaida Mamanmu, "zata ji!" Har zata tafi nace mata. "Zo nan Nana!" Na bude jakata na ciro kudi dubu biyar na mika mata, ta amsa tana godiya, har tana kara nunawa Mama. Murmushi Mama tayi tana faɗin. "Kai Masha Allah kawata yau a wurinku xan kwana sai kudinmu ya kare zan dawo nan!" Dariya tayi tana me barin dakin. Ina cikin abincin Mama ta ce min. "Ya jikin Hajiyar?" "Da sauki sosai, har ta koma gida!" " Yau kuma?" "A'a tun jiya ta ga likitan ashe fitarsu ya kaita Asibitin." Na cigaba da cin abincin. "Tow idan kika yi arba'in zaki koma dakinki ne?" Hadiye abincin bakina nayi ina kallon yadda take kallona cikin damuwa. "Mama kin gaji da ni ne?" "A'a Ummu ban gaji dake ba, bana son a fahimci cewa kina son ki kashe aurenki ne, zai zame min abin kunya ne!" Ta fada cikin sigar lallashi. "Mama na gaji ne!" "Har yau baki dauki auren ibada ba ne?" "Na dauka amma akan Tafida na fahimci babu amfanin yin ibadar da kasan babu lada a cikinsa. Ki fahimce ni!" "Na fahimce ki amma ke yanxu ba abin kunya bane ace kin samu damar hawa sama lokaci guda a ji kin dirko kasa? Ummu ba zan hanaki rayuwarki ba, amma zawarci yana da nashi kalubalen fa." Ban san me yasa iyayenmu suke hango mutuwar auren mace kamar tonuwar asirinsu ne. "Yanzu kin ga Taima duk da halin da take ciki Hajiya Balkisu bata mata fatan kashe auren, balle kuma Samira duk yadda take fuskanta matsala Umma taki yarda da maganar mutuwar aure, ina tsoron kada ayi ta." Hawaye ne ya zubo min tabbas Mama bata yi kuskure ba, amma kuma mai da ni rayuwar Aliyu Tafida shine mafi girman kuskuren da zata aikata! "Yanxu ki duba Yaranku haka zaki barsu? Ina ga ya kamata ki koyawa kanki zama mace kuma jaruma ba wacce zata gudu ta bar sauran aikinta ba. Da ace shekarun baya na samu wnada ya min wannan karatun da ban baro gidan mijina na auri Bulama ba. Amma dake rabon su Ummu Kulsum da Ummu Rooman yasa dole na hakuri da kome na dawo nan, kuma ina zani? Anan nake da sauran Rayuwa. Kiyi hakuri kada ki kashe aurenki akan abin da bai da hujja, dayawan iyaye mata muna hakura da abun da muke dashi ne domin ku, kuma sai ki ga kome ya wuce." Kasa magana nayi domin wani abu da naji ya tsaya min a kirji wanda ya kasa wucewa kasa yana tsaye a wuyana, hawayen da nake dannewa ya zubo min tabbas, idan na fahimci mama da kyau burinta na koma gidan Tafida. "Kiyi hakuri kin ji!" Ta kuma fada ban san lokacin da kuka ya kwace min ba, kaina a sunkuye na ce mata. "Me yasa? Me yasa kika bari aka bashi aurena? Me yasa ko don bani da gata ne? Mama nima mutum ce kamar kowa nima ina son farin ciki. Idan na koma gidan Aliyu har abada bani da fata da farin ciki sai dai nayi rayuwa domin Yarana. Amma shi kenan idan aka kawo miki gawata kada ki zargi Aliyu." Na tashi ina me nufi ban daki. Jikinta yayi sanyi domin kuwa gani yadda nake kuka yana tab'a mata rai, idan har ta bar ni za iya cigaba da zaginta na ta bar ni na kaso aurena, amma kuma farin cikina yana gaba da kome tow me zata cewa Mutane? Da ko a gidana nake tasan magana zasu cigaba da yi. Koda na fito na samu bata dakin tana ɗaya dakin, sai da naji dariya na fahimci aminiyarta ce tazo wato Hajiya Amina. "Hajiya Amina shigo." Suka shigo dakin bakiɗaya, "ke Ummu dubu ashirin da biyar kuka bawa Nana fa, a cikin ledar abincin da dubu ashirin kin ganshi yayi mata yawa wallahi!" "A'a rabonta ne fa bani na bata ba, Babansu Mufidah ya bata!" "Amma!" "Kai Amina sai kace wacce aka bata miliyan don Allah ki sawa ranki nutsuwa rabonta ne!" Zama suka yi ta kalli Hajiya Amina tace mata. "Gata nan ban san meye ribar da zata ci ba, idan ta kashe aurenta. Don Allah ki fahimtar da ita illar zawarci." Kallona Hajiya Amina tayi kafin ta ce mata. "Kada mu ga laifinta, bayan kema kin san yanayin da suka zauna da Yaron nan, bana fatan Ummu Hadiyya ta dawo gidan nan, amma maganar gaskiya shine ta nimawa kanta yanci, sannan shi yaron kin ga danginshi sun damu da ita ko kula da ita? Kin ga Hajiya Hadiza mu kowa Yaranmu kwatan kansu kada ki maida ita lusara mana kishiya take da shi fa, yar uwarsa kuma Yar dangi na zata an wuce wannan zamanin da mace zata zauna zaman alfarma, Ummu ki ja zarenki da kyau ki nunawa danginsa kema mutum ce kada ki zama.wacce Tafida zai naja yadda so!". "Wai Amina me yasa kike biye mata ne?" "Na gaya miki tabawa kawata a gidan take aikin tuwo, ita ta ke bani duk labarin abinda yake faruwa ban da Allah ya nufa Ummu Hadiyya tana da nisan kwana aka ce miki bakinciki bai isa kashe ta ba har lahira kawai idan kin ganta a damuwa tayi hakuri ta zauna gudun kada aurenta ya mutu a mata gori ko?" Ta juya tana murmushi ta ce mata. "idan kika so yarki babu wnada zai wulakantata idan kika juya mata baya, akwai irin Aliyu dayawa zasu ta wulakantatta shawara na gare ki, ki barta ta tsaya da kafarta ko kuma kina ji kina gani wata rana za a kawo miki gawarta, ban san me yasa mu iyaye muke tsoron mutuwar auren Yaranmu ba, idan don maganar mutane ne da zawarci tow kinyi kuskure...... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *Assalamualaikum don Allah kada a tura payment ta GTBANK babu network zan saka Opay dina* Paid book 07 Shirun Mama babu alkhairi a cikinsa, domin kuwa girman Hajiya Amina take gani yasa tayi shiru wanda nasan Hajiya Amina tana barin gidan Mama ba zata daura maganarta. Don haka na ce mata "Mama Amina zan koma." Ba iya ita ba hatta Mama naga mamakina a fuskarta. "Zaki koma fa?" Suka tambaye ni bakinsu a haɗe, cikin wani irin shashekar kuka na ce musu. "Eh zan koma!" "Ummu babu inda zaki kome, ranki baya son gidan Tafida yanzu idan kika koma kamar cutarwa ne ga rayuwarki!" "Babu abin da zai same ni!" Na fada ina kuka, sai kallona Mama take ita dai bata ce min dole ba, amma kuma a ranta tasan bata kyauta min ba. "Kiyi tunani Hajiya Hadiza tunda kika haifi Ummu ta tab'a miki musu? Duk abin da kike ce shi take miki, akwai hisabi a tsakaninmu da Yaranmu." "Hajiya Amina ni fa bance mata dole ba, kin ga na mata magana ne?" Ta fada kamar ranta ya b'aci, murmushi Hajiya Amina tayi tana faɗin. "Shi kenan, Ummu ki yi duk abin da ya dace. Wanda zai gyara miki yau ɗinki da domin kuwa shi rayuwarki na gaba. Ita mahaifiyarki!" Sai kuma tayi shiru tana kallona kafin ta mike tana faɗin. "Allah yasa haka shine mafi alkhairi! Ni zan tafi." "Amina kamar ranki ya b'aci?" "A'a raina ba zai b'aci ba, Ummu Hadiyya yarki ce ni kuma makociyarki ce kina da yadda zaki yi da ita. Ni kuma babu yadda zaki yi da ni, sannan ina ga mu bar zancen nan kawai Ummu Hadiyya mun gode sosai fa, kamar kin san ina niman kudi ido a rufe, sai an jimanku!" Ta saka kai ta fita nasan Mama Amina ranta ya b'aci sosai, tana fita ko minti goma ba ayi ba, Mama ta sabi mayafinta tana faɗin. "Amina ita ce bangon da nake jingina na ji dadi, ita ɗaya take tayani kuka lokacin kuka, gara na shirya kafin a fara mana dariya." "Sai kin dawo!" Na fada ina jijiga Mufid. "Kawo shi na goya shi!" Goya shi tayi suka fita, hawayen da suke ta zuba min na goge, ban san ta kuma dawowa ba sai ce min tayi. "Kuka ba zai miki magani ba Ummu Yaran nan zaki duba, ya rayuwarsu zata kasance idan baki tare da mahaifinsu. Dama Allah ya baki kada kiyi wasa da shi wurin lalata aurenki, Allah ya buda miki kika gidan aurenki ma bai saka kin rasa kome ba shawara nake baki fa ban ce dole ba." Share hawaye nayi ina kallon Mama da ina ga kamar dole take min na koma gidan Tafida, fita tayi tana faɗin "kowa rai ya amfana baya ga mai shi ne." Kamar Tafida yana jiran ta fita sai ga kiranshi. Kallon wayar nayi kafin na dauka. Dariyarshi na ji tare da yan iskan abokan shi. "Ummu!" "Hmm!" "Uwar gida Sarautar Mata, dama na kira na gaya miki ko zaki samu lokaci zuwa wata sati zamu je Umra da ke!" "Tafida!" "Na'am Matar so!" "Bana son aurenka! Kayi hakuri ka rabu da ni." "Amma Ummu baki ga kamar yayi sauri ace mun rabu da juna duka-duka shekarar mu nawa da auren da zamu rabu da juna?" "Ai ko kwana ɗaya ne nace ba zan zauna ba!" "Ba zaki zauna da ni ba, tow me nake miki da kike jin haushina." "Ba kayi kome ba, ba zaka tab'a min kome ba saboda bana bukatarka yasa nake son rabuwa da kai." "Ummu Hadiyya kin ga ina ganin girman Iyayenmu yasa nake bin ki cikin lumana idan kika bari wani abu ya taso ba zan miki da dadi ba!" "Ni dama bana son ka min dad'i" daga haka na kashe wayar ina ganin yana ta turo sako amma fir naki budewa. Tunda na fahimci ni ce matsalarshi na saka a raina zan rabu da shi, amma shi ya kasa fahimtar haka. ** SA'ADIYYA. Amarya Tafida wacce suka sha alwashin dole ta zama first lady, ana ta gyara ciki da waje domin tun barin Ummu Hadiyya gidan har yau bata gane kan kusar yakinta ba, duk wani abin da suke karbowa na barbadawa da turarawa, bai yi tasiri akan Kusar yaki ba domin kuwa yana da matukar taurin kai, sannan Tafida duk rashin jin shi ya tsare salloli biyar nan baya wasa da su, Allah yayi alƙawarin kuma yana cikata akan wadanda ya daukawa, shi yasa duk haukarsu baya tab'a sh, sai da suyi ta asara wanda kowa yasan bata da dad'i. Tunda aka rantsar da shi bakiɗaya yan uwanshi da yan daki daya da waɗanda suke yan uba, suka kara shigewa Sa'adiyya wacce ita basu ne a gabanta ba, ga gidan nan dai Ummu ta bari sai me? Tafida ne kuma babu hadin kai yaƙi kulata ma, tana zaune a parlournta tana shan fruit Wanda ya sha kayan Mata, aka kirata a waya. Dauka tai tana yatsina fuska. "Tanko shi dade, Hajiya Larai ce shugaban Mata, na kira na tayaki murna sannan na tuna miki da alƙawarin da kika mana!" Wani haɗe rai tayi tana faɗin. "Tow ai bamu shiga gidan gwamnati ba ko?" Ta tambaye ta, sannan ta kara da cewa. "Idan muka shiga xan kira ki!" "Yawwa haka ne kan, Hajiya ko kin ga abin da yake faruwa Mai girma gwamna da wata mata da Yaranta hala kishiyarki ce ko?" Wani irin dauke wuta Sa'adiyya tayi kafin ta ce mata. "Ban gane ba?" Ta fada da sauri, "Eh tow ki duba zaki ga ana ta daura hoton a media! Sai an jima" matar ta kashe wayar, sororo tayi tana bin wayar da yake hannunta da idanun. Jikinta yana rawa ta buɗe data, abin da ta fara gani shine sakon da arewa fashion trending suka turo na *Mrs Tafida Mama's Kitchen! Long live Mr and Mrs Tafida!* Jikinta yana kerma ta shiga duba notifications hoton Tafida da Ummu ne, a yadda aka yi ta daura hoton zaka ɗauka soyayya ake zubawa a asibiti amma a zahirin gaskiya, rigimarsu da suka.fara ce take yawo a tsakaninsu yayinda media suka kafa hujja da cewa soyayya ce kawai.. a wani page da ta ga wata tana faɗin. *OMG maza kyawawa sun iya karewa a jikin Mata munana ba mamaki yayi breaking heart din kyawawan Mata Allah ya jarabce shi da auren wannan yar karamar yarinyar!* a kasar comments din aka rubuta. _Ke dalla ba yarinya ba ce, dakyar idan ya bata shekaru me yawa domin nasanta a dan gaba damu take Aunty Baby! Akwai mutunci da kirki* still yarinyar farko ta kara cewa *Amma ance su biyu ne ko?* *Eh su biyu ne akwai Amaryanta idan kika ganta wallahi sai ki dauka aunty Baby Yar aikinta ce saboda kyau da haduwa amma ki ga yadda ya kare* sai a lokacin Sa'adiyya ta sake murmushi, karamar wayarta ta dauka ta kira wani number. "Zan ajiye maka sako ta Whatsp! Kasan yadda zaka yi ka ruguza abin da ake daurawa a social media! Zan turo maka 20k!" "Ki nime wani yayi miki aikin ba zan yi ba" aka fada mata, tasan matsalarshi da maganar kuɗi. "Ok 50k!" "A'a bana bukata!" "Zan baka 150k yayi!" Ta fada a hankali, "tow ba damuwa bari mu tashi kura!" "Yawwa nasan zaka iya!" Ta kashe wayar tana me ɗaukar screen shot ta tura mishi ta Whatsp. _Kin san bana aikin banza ko? Don haka turo na miki aikin da zai zama trending!_ _Na sani! Sannan idan da hali ka karyata abin da ake fada na soyayya suke ! Ka gaya musu gaskiya Ummu ba zata dawo rayuwar Tafida ba aurensu mutuwa zai yi suna haka ne don hankalin mutane ya kau akansu! Zan kara maka idan har ka girgiza media!_ take ta tura mishi dubu dari da hamsin din. Tana jiran aiki domin tasan smarty matuƙar yace zai yi aiki tow babu me hana shi a duniya. Bayan awa guda aka yi ta kiranta, ana tambayarta. "Sa'adiyya kin ga meke faruwa kuwa?" Dake tasan me ta kulla ko a jikinta. "Me ya faru?" "Hmm ke dai duba!" Bude data tai kamar da gaske ta ga abin da ya daura da cewa! *Labarin da ake ta damun kowa soyayya soyayya! Hmm soyayya for ma foot! To karya ce!* anan yayi ta rubutu akan wasu hotunan Ummu Hadiyya, da tafida. Yayi magana marasa dadi da kyau akan Ummu Hadiyya da Tafida. tare da kafa hujjar idan ana ganin karya ne a bincika Ummu bata tare da Tafida yanzu haka tana jiran takardan sakinta ne. Wannan abin ya saka mutane suka fara kokwanto akan maganrshi. Yayinda wasu suka yi ta zaginshi suna mishi mugun fata da Allah ya sakawa Ummu da Tafida. Dariya tayi sannan ta karawa Smarty wasu kudadden, ta kashe wayar tana kad'a kafarta musamman inda Yaron ya rubuta. *Allah Sarki Uwar marayu gatan mai iyaye! Turmin tsakar gida shaluguden mahassada! Kin yi naki kin yi na me karamin karfi! Hajiya Sa'adiyya Aliyu Tafida! Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana! Madara mai kama da nono* wannan kalaman sun tsaya mata a rai! Sai kallon kanta take a wayarta. Tana murmushi ita yanzu idan da smarty ba zata kashe wa wani dan iska kudi ba, shi kadai zai yi draging kome out! Bayan la'asar aka yi sallama tana kwance bata tashi a wurin da take ba. Aunty Rukayya ce tare da yarta Naziha. Ita fa sun fara damunta daga ranar da aka tabbatar da Tafida ne ya ci zabe suka hanata sakat, amma dake makira ce mikewa tayi tana murmushi ta ce musu. "Aunty Ruky ke ce!" "Eh wallahi mun zo ganin Alhaji ne na ce bari na zo na gaishe ki!" "Ina wuni!" Naziha ta gaida ta sama sama, domin Allah bai had'a jininsu ba. "Mammy bari na shiga cikin gida!" "Au baku shiga ba ne?" Inji Sa'adiyya, "eh yanzu shigowarmu!" Aunty Rukayya take fada, "Ayya!" Ta fada fita yarinyar tayi, Aunty Rukayya kuwa tayi ta zuba tun da suka shigo bata kira an kawo mata ko ruwa ba, suna zaune aka kirata. Cikin dauki da murna ta ce mata. "Tow sai kun iso!" "Laraba!" Da sauri matar ta fito tana faɗin. "na'am hajiya!" "Yawwa maza a gyara parlour ki ce Rose ta hada kayan ciye-ciye ga matar mai taimakin gwamna nan zuwa da Yaranta!" "An gama Hajiya!" "Masha Allah yau gidan da baki kenan! Ai da sun fada da wuri ko abinci da anyi musu!" "Eh ba kome haka ma yayi" ta nufi dakinta tana hararan Aunty Rukayya, dake bata san meke faruwa ba. Ta tsaya aka gyara parlour sannan aka jera musu abin tabawa. Kafin karfe shida bakin sun iso, nata so Aunty Rukayya ta zauna ba, amma haka ta share suka yi ta ina zaka saka ina zaka ajiye da iyalin mataimakin Gwamna. Sai bayan Isha suka tafi shima lokacin Tafida ya shigo suka kara gaisawa, sannan suka rako su. Juyawa suka yi cikin gidan Aunty Rukayya ta shiga tattara abubuwan da aka sakawa baki tana zubawa a wani leda abin ya bawa Sa'adiyya haushi. A cikin gidan kuwa tunda Alhaji Muhammad Jadda ya ga Naziha ya tambaye ta. "Ina Mamanki?" "Tana can bangaren Uncle Tafida!" Jinjina kai yayi yana faɗin. "Ai haka yayi!" Yana sane da abin da suke ya zuba musu idanun ne kafin Allah ya hukunta su daidai da laifinsu. Ko da yayi magana za su ce yana bayan Ummu ne Gara ya zuba musu idanun tukun indai shuwa ce Allah zai kawo karshen abin da suke yi. Har aka yi sallah Magariba bata shigo ba sai bayan sallah ta shigo sama sama suka gaisa. "Naziha muje gida dare yayi!" "Tow!" Ta fada tana kallon Alhaji Muhammad Jadda, "Abba Allah ya baka lafiya, zamu tafi!" "Ku gaida yaran da mai gidan!" Suka fito da sauri tana faɗin. "Zai ji in sha Allah!" A kofar dakin Inna suka tsaya"tsohuwa zamu tafi ban samu shigowa ba!" "Ai kai kud'a me kwadayi ne ban yi mamaki dan baka shigo ba, a gaida Yaran!" Dariya ta yiwa mutanen gidan sallama suka bar gidan domin Tafida ya bada motar da za a kaita gida. Shiga dakinta tayi tare da kiran Uwarta. "Mommy na gaji! Wallahi na gaji haba don Allah akan shi aka fara zama gwamna ne? Ace kai da gidanka ya zama kamar gidan gandu, kowa zuwa yake bakin arziki ma sai anyi ta shige musu!" "Kiyi hakuri lokaci ne zai tabbatar da haka, ina sane da kome. Sannan kiyi amfani da ruwan nan fa da hayakin da turaren" "Shi kenan!" Ta kashe wayar, ban daki ta shiga tayi wanka da ruwan rubutun tayi turaren da kome sannan ta wuce kitchen ta dafa mishi indomie aka barbad'a kayan aiki kafin ta wuce dakinshi, yana ta aiki a laptop. Karatun Sheikh abdurrahman sudais yake tashi a wayarshi. Ta kawo ta ajiye mishi, "sannu da hutawa!" "Yawwa!" Ya fada yana aikinshi. "Ga abinci!" "Me kika dafa?" "Indomie ne!" Ta fada tana kallonshi. "Barshi kawai xan sha tea!" Ya fada yana me cigaba da aikin. "Na hado maka?" "A'a ina aiki idan na gama zan sha!" Ya fada yana ta aikinsa kamar ta fashe da kuka tana zaune a wurin har barci ya fara daukarta, ya mike ya haɗa tea sannan ya bude drower dinsa, soyayyen nama ne da dambun nama, ya zuba a wani flat ya dauki bread guntu ne ma jiya Deen ya saya musu. A hankali yake ci yana jin dandanon kayan haɗin abincin Ummu, daukar tea din yayi da kayanshi ya kai parlour sannan ya dawo ya dauki wayarshi ya koma parlourn. Yana shan tea yana me kiran Ummu. Sai da ta kusan yankewa ta dauka da "hello! Waye?" "Kiyi tunani Ummu Hadiyya me kyau ga dambuna ya kare waye zai min irin naki?" Kashe wayar aka yi, ya kira yaji wayar a kashe bakiɗaya. A can dakin kuwa yana jin motsin fitarshi ta farka tare da bin shi ta makale tana me saka kunnenta. Jin sunan Ummu abin ya bata mamaki, wannan wacce irin masifa ce haka? Tana Barka an rabu da bukar ashe an haifi habu. Kwafa tayi tana me barin jikin kofar ta kwanta karshe barcin da bata yi ba kenan har sai.da ya shigo a saninta shi din yana da bukatar mace a koda yaushe, amma sai ta ga tun barin Ummu Hadiyya gidan ya rage sosai asalima tana zuwa dakin zai dauki pillow ya shimfida bargo ya kwanta a kasa. Wannan abin ya mata ciwo ko yana mata ciwo kamar wacce tayi mishi wani abu bakiɗaya ya janye daga kulawar da yake bata. Dakyar barci yayi gaba da ita cikin takaici. *** "Waye ya kiraki a wannan daren!" Kallon Mama nayi kafin nace mata. "Tafida!" Sannan na gyara kwanciyana. "Yaron nan yana ta kokarin ya ga kun daidaita amma kin ki ban san wani irin taurin kai yake damunki ba, amma ba xan daina gaya miki gaskiya ba domin kuwa shi ne gatan da zan miki." Kasa magana nayi ina kallon gefen da take kwance, a hankali naji alamar barci ya ɗauke ta. Gyara kwanciya nayi ina son na tuna me yasa na rasa wanda zai tsaya min akan abinda Tafida yayi min? Me yasa Mama take niman juya min baya? Me nayi da zafi haka da kowa yake ganin kada na rabu da Tafida. - Sunana Ummu Hadiyya a sanina ni agola ce Mama ta auri Baba Alhaji Bulama bayan ta yaye ni. Alhaji Bulama yana da mata biyu da Mama uku Hajiya Balkisu ita ce uwar gida kuma me manyan Yara dakinta tana da yara biyar, Ahmad Bakura yana aiki a abuja yana da mata daya da Yara biyu, sai Muhammad sani Kawu Gwani sai Salman Bamai, sai Safina wacce ake kira Taima..... N500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *Assalamualaikum don Allah kada a tura payment ta GTBANK babu network zan saka Opay dina* Paid book 08 Sai Saratu wacce ake kira Kwaise, ita ce autarsu. A gaban Hajiya Balkisu akwai Yar kaninta wanda ya rasu ya barta wato Mahira Hajiya Balkisu wato Ummi ita ta fito ƙabilar barebari ce wato kanuri kamar Hajiya Bulama Hajiya Balkisu tana da zafin kishi shi yasa kome nata ya banbanta da na kowa hatta Yaranta ba yarda su tafi . Sai Hajiya Karima wacce muke kiranta Umma, Yaranta uku duk mata ne , kuma kowacce tana gidan, Sadika, ita ce babba yaranta hudu, sai Asiyah tana da yara biyu sai Azizah ita ce har yau Allah bai bata haihuwa ba, dukkansu ukun nan suna aure cikin manyan ahali. Mama ce matar Baba ta uku, lokacin da aurenta ya mutu ta bar garinsu tazo wurin Kanin Mahaifin ta zauna. Mama yar kabilar Baburawa ce. Anyiwa Mama auren dole ne da Babana wanda ya kasance malamin makarantan secondry school, Babana ya so Mama amma saboda kiyayar da take mishi taki zama, haka yasa dole aka raba auren lokacin ban wuce wata goma a duniya ba, shine ta dawo garin Maiduguri wurin Kanin Babanta da zama, matar kanin Babanta Mama Yahanasu gidanta cike yake da Jama'a kasancewarta tana sana'ar sayar da abinci a bakin kasuwar Monday market, wuni ake ana shiga da fita. Anan suka hadu da Alhaji Bulama, wanda ya nuna soyayyarshi a gareta kuma ba a wani sha wahala ba ta amince mishi. Manya suka shiga cikin maganar, haka aka yi daurin auren ta tare, kasancewar ta san dadin niman kudi bata yarda ta aure shi ba sai da ta ce mishi zata fara sana'arta, shi kuma a bangaren Alhaji Bulama abin da ya kara bashi sha'awa da Mama ta gama secondry school, haka yasa shi kara bata kwarin gwiwa ta fida poly tayi diploma, wanda ta fara shi tana da cikin Ummu Kulsum, har aka haifeta ni a lokacin ina wurin Hajiya Yahanasu, duk da ban wani girma sosai ba, sai dai ina da matukar wayo a lokacin, bayan shekaru biyar a lokacin ina da shekara bakwai a duniya na koma gaban Mama, sakamakon rasuwar Hajiya Yahanasu, da Babana yaso amsata amma fir taki amincewa haka yasa saboda kaunar da yake mata ya hakura na zauna a hannunta, Mama uwa ce da ta tsaya min a ko ina, duk da kuwa ina shan gori a wurin yaran gidan amma haka bai hanata nuna musu ina da gata ba, ban san babana ba amma a yadda nake jin tana bada labarin Babana yana da rufin asiri. Har tana fadawa mutane yadda duk bayan wata shida yake min aike ita ce ta hana saboda bata son kome daga gare shi. Duk yaran gidanmu suna da ilmi. Hatta kannena suna da kokari idan ka cire ni, duk yadda naso nayi karatu domin Mama dai ba tayan baya ba ce a ilimi, sannan tana aiki da local government. A lokacin Mama ta fara deciding fara yin abincin sayarwa saboda ta fara amma ta ajiye sakamakon aikinta, kuma tana sayan kayan abinci tana rabawa ma'aikata karshen wata su bata kudinta. Tunda muka fara abin karyawa na sayarwa idan muka tashi tun 4:30am muka fara aiki ba zamu koma.ba sai karfe sha daya na dare sakamakon yadda ake wuni sayar da abinci,ana sauke abinci karfe shida na safe, kafin karfe bakwai na safe ya kare an daura na rana. Ni zan tafi makaranta ita Mama aiki. Sannan akwai masu mana aikin wake-wake da daura abincin rana saboda zan dawo, ina da shekaru goma a duniya Mama ta sake min ragamar girkin abincin sayarwa tare da bani damar na cigaba da kula da kome tana lissafi, ba don kome ba sai yadda ta fahimci ƙwaƙwalwata bata iya gane kome sai sarrafa tukunya da kayan abinci, Mama tayi kokarin nayi karatu amma Allah ya gani bana ja bana iya kome ban san kome ba idan ba girki ba, tayi min nasiha har dukana sai da tayi amma ban fahimci kome ba. Alhaji Bulama da kanshi ya dakatar da ita ya ce ta yiwu bani da wani abin da zan amfana ne a can, sai ta saka ni a high Islam, na fara gara shi kan ba laifi na maida hankali sosai. Sannan a unguwar mu ina zuwa tahafiz kada ku sha mamaki yadda nake iya karatun Alqur'ani amma boko kamar zan mutu ko hala ban da rabo ne cikinshi. Mu hudu Mama ta haifa Ni ce babba sai Ummu Kulsum, sai Ummu Rumana, sai Ahmad domin Ahmad biyu ne a gidan mu, Baba Bulama yana da rufin asiri sosai, domin babu abin matanshi da yara suka nima suka rasa, Ummi wato Hajiya Balkisu turare take sayarwa shine sana'arta Umma kuwa yar zaman banza ce, sai gulma bata da aikin. Akwai wani abu da nake kara jin dadi da tausayinsa a raina farkon dawowata gidan yadda Yaran gidan suka tsane ni, idan na cire Sadika wacce ta girme ni sosai, amma Asiya,Azizah, Taima, duk sa'o'i muje sai Yaran riko da Ummi da Kuma suke daukowa, saboda ni da Baba ya bar Mama ta dauko ni. Suna irin na cin mutuncin da cin fuska babu wanda ba a saka min a gidan ba, an saka min yar duna jikar masu daddawa, Mama ta tsaya kai da fata ita da Baba da Kawu Gwani wanda Allah ya haɗa jininmu, suka kashe sunan. Bayan nan aka sake saka min African queen, Kai har sai da sunan ya fita waje Baba ya samu me unguwarmu aka kashe sunan, sai da aka saka min suna yafi kala goma Mama da Baba suna kashewa domin akwia wani yaro me suna Farouk da ya saka min cinnaka baki san na gida ba, sunan har makarantarmu ya tafi, Mama ta wanke kafarta har gidan iyayen Yaron ta ce bata yarda ba. Shine aka dawo aka saka min Baby. Kun san dalilin, kasancewata yar karama domin bani da girma sannan ni baka ce ina da dan auki sakamakon yadda Mama take fada ai ni bakwaini ce shi yasa nake da karamin jiki. A lokacin da na cika shekaru goma sha biyar, ina dab da gama high islam. A wannan lokacin Baba ya bude gadon sayar da Abinci ya ce min yaga ina da kokari na cigaba da sana'a. Haka na cigaba har muka yi sauka,.inda na kara kankaro mutunciwa Mama, domin idan ka cire mazan gidan duk sun sauke Matan ne sai a hankali domin suna da shegen kyau fa farin fata. Wannan kyan nasu yasa suke min izgilanci bai taɓa damuna ba, domin bani nayi kaina ba, abu daya na sani duk da wannan kyan nasu kafin su saka suturar da nake sakawa sai an shekara, ba wai ko lokacin bikin sallah ba a'a, akwai wata bayarabiya da take zuwa daga Lagos, wurin aikin Mama take duk karshen wata uku tana zuwa ta kawo kayan sayarwa daga kwatano haka yasa Mama take saya mana kaya, Mama har Kano wani lokaci tana zuwa ta sayo mana kaya ta ajiye a gidan Hajiya Amina sai dare yayi ta saka ni da su Ummu Kulsum da Ummu Rooman mu je mu kwaso kayan, wani ma daga can muke kaiwa wurin tela wata yar kalaba me suna Maman Chioma, haka yasa duk iskancin yan matan suke d'aga min kafa, kuma babu yadda suka iya dani, koda nazo na gama high Islam na kara rungumar, gashi mun shaku da kawu gwani wanda haka yasa aka.fara zargin soyayya muke. A wurin aikinsu aka kawo tallar wani makarantar girki, kafin ya dawo ya saya min Form ya cika min sannan ya kawowa Mama ta gani, ban ji dadi ba amma kuma ganin shine ya kawo min na mai da hankali na shiga makarantar, tabbas akwai inda zaka rena kanka, domin ina shiga makarantar na hadin gwiwa wasu mutanen kasar waje ne, larabawa da turawa, sai Hajja Yaana wacce ta bukaci so tayata budewa, ita din Yar shehun Borno ce. Haka yasa muka mai da hankalinmu. Shekara daya muka yi akan girki amma kafin na gama na samu satifiket a bangarori na makarantar da dama, saboda kwazona da mai da hankali akan abinda ya shafe ni, haka yasa muna gamawa na kara mai da hankali na rike baiwata gam. Ana haka aka yi bikin Bakura da Sadika. Muka sha biki sosai amma sai da aka yi ta girma domin kawai Baba ya dauki hidimar abinci ya bamu, karshe sai da Mama ta dauki kayan abincin ta maidawa Baba case ya mutu, sai dai Baba da yayi walima mune muka hada mishi kome sannan muka samu kanmu. Haka rayuwar gidan yake. A hankali aka yi ta bikin yan matan gidan har aka zo ɓangarenmu. A lokacin ne aka yi bikin Ummu Kulsum da Ummu Rooman, hankalin Mama ya tashi domin lokacin da Baba yayi maganar hada ni da kawu gwani hankalin Hajiya Balkisu ya tashi inda tace ko a fada auren ko ta tsine mishi albarka, haka ya bar ni ya auri wata yarinya Mariya, bayan nan aka yi auren Salman Bamai, babu kowa sai yayan rikon Umma da Ummi. Nasan Mama tana cikin damuwa amma Allah ya gani ba ni ce na hana kaina miji ba, domin ana haka nayi ta samu manema sai sun zo zasu gudu, wani ma sai anyi maganar aure rimi-rimi har manyan sun shiga an kawo sadaki za a fasa, sau uku ana haka kawai sai na daina bawa kowa fuska. Akwai wani taro da aka yi a unguwarmu, wanda ya janyo aka yi ta zuwa sayan abincin, maza ne guda uku suka shigo shagon abincin nasan dayan yana yawan sayan abinci da safe. "Barka dai Hajiya kwana biyu bana ganinka!" "Aunty Baby nayi tafiya ne!" Dariya nayi ina faɗin. "Har da kai a cikin masu kirana aunty!" "Eh mana!" Ya fada cikin dariya. "Me za a zuba maka!" "Shinkafa da wake, da soyayyen kifi ayi min hadin kullum dai!" Shinkafa da wake yake saya, sai salat da kifi, sai tsimi. Haka kullum yake saya kuma za ayi mishi takeaway guda ɗaya. "Jamilu anan nake cika cikina!" "Hmm na ga alama!" Ya fada yana bin inda nake da kallo. "Me za a saka maka ka fada?" "Idan akwai tuwon alkama miyar kuka! Sai mana wani iri suke da shi!" "Aunty Baby wani irin nama kuke da shi!" "Akwai na kaza, na rago da na saniya!" " A saka min kirjin kaza!" "Tow!" Shigowa Uwani tayi tana faɗin. "Aunty Baby an gama dan waken da alalen!" "Tow zo ki mika musu, na dauko." Shigowa tayi ta mika musu na shiga cikin gidan na kwaso kayan na kawo. Ina kawowa kuwa aka.fara shigowa ana karban abinci, Mudan yana ta zuwa yana kaiwa kasuwa musamman wadanda suka yi booking. " "Alawan anan suke abincin ne?" "A cikin gidan nan mana, gidansu ne kuma ko yaushe ka zo zaka samu abinci da dumi. Babu abinda basu sayarwa domin local food ne amma kuma luxury restaurant ne da sai ka jijjiga aljuhunka!" Ya fada yana shan ruwan tsimin. "Aunty Baby a bani takeaway na ga kudin abincin!" Ya mika mata kuɗin su bakidaya. "Na gode sosai!" Na saka mishi wanda yayi guzirinsa, haka rayuwata take tafiya. Sannan a gefe guda wannan Jamilun a nan yake karyawa, abincin rana da na yamma da Uwani take yi. Wasa gaske sai gashi yana niman shigo min da zancen soyayya. Duk yadda na kaucewa soyayyarshi haka ya takura min, ban san ya aka yi ba wata juma'a bayan an sako masallaci ina ta fama da almajirai da wani ya saya musu abinci ina raba musu, dan gaba da mu, ana daurin aure ne. Unguwar an cika sannan wasu na ta shigowa na sayan abinci, sannan duk ranar juma'a an fi yin abinci dayawa saboda sadaka. Sannan an fi cika gaskiya. Kaina yayi zafi ina fama da jama'a. "Assalamualaikum ina niman Aunty Baby!" "Na'am gani nan!" Na d'ago ina kallonta. "Jidda ki fito mana da shegiya karuwa!" Kallon wacce aka kira da jidda nayi na ce Mata. "Ki ce musu tayi hakuri zuwa gobe yau ina da jama'a ne!" Ihu ta wajen tayi ta fara zage zage da cin mutuncina, ban kulata ba sai da na ga haukar tayi yawa na fito an cika ga yan aurin aure sun fito ana ta tsayawa. Zakiya da bata da hakuri ta nufe su na riko hannunta. "Uwani ita ɗaya ce kyale su!" "Baiwar Allah ban san wacece ke ba, amma kiyi hakuri idan na b'ata miiki rai." Na juya riko rigana tayi ta baya. Na juya zan kwashe da mari sai kuma na fasa musamman yadda na ga an cika a wurin ana bata rashin gaskiya. "idan akan Alhaji Jamilu ne ki je bana bukatar shi, domin bai isa da ke kuma kin nunawa duniya cewa ke mahaukaciya ce, wacce ta fi karfin Mijinta. Ban tab'a rigima da kowa ba a unguwar nan tun tashina, idan don shi ne ba zaki mai da ni karya yar uwarki ba, ki je da Mijinki Allah ya baku zaman lafiya!" Na juya ina me komawa shago, rintsa idanuna nayi,ina kallon mutumin a cikin idanuna wanda girmanshi da kwarjininsa ya hana ni marinta, "Malam Inuwa wacce yarinyar nan?" "Agolan Bulama ce." "Amma tana da tarbiyya sosai!" "Ai don ma baka zauna da ita ba ne, yarinya ce matuƙar hankali da sanin ya kamata." "Hmm ko ban zauna da ita ba zan bada labarin haka a gaba, yadda ta d'aga hannu zata mare ta kallonta nayi ta sauke hannun. Irin wannan yarinyar nake ta nimawa Tafida wacce ta san idanun da darajar na gaba, Alhamdulillahi na samo mishi ita." Kwana biyu a tsakanin muna cin abincin dare aka kira ni wai Jamilu yana kirana, na san ina son nayi aure duk da ba wani jimawa nayi kawai hankalin Mama da yake tashi ne yasa nake ganin gara nayi auren, tunda na fita yake bani hakuri amma ban ce mishi kome ba,.yana gamawa na ce mishi. "Kayi hakuri kawai, Allah ya baka wacce ta fini." Na juya na koma gida, ni a zatona zai bar ni ne a'a haka ya cigaba da zuwa shigona. Bana kula shi abinci yake zuwa ya saya ya tafi. Bayan kamar wata biyu ya daina daga nan na sakawa raina hakuri babu amfanin saka kaina hakuri da mai da kome ba kome ba, duka-duka shekarunta ashirin da biyar ne zuwa da shida kawai ganin kannena duk sun yi aure yasa Mama take cikin damuwa. A duk shekara akwai wani Alhaji Mu'azu yana daukar nauyin girka abincin bude baki da na asuba ana rabawa sadaka. Sai da ya rage wata daya za fara azumi Allah ya mishi rasuwa, a wurin rasuwa mabukata ke ta kukan rashin da aka musu, bayan anyi jana'izar shi wasu daga cikin Yaranshi suka dauki nauyin abincin kamar yadda Babansu yake yi, bayan sun gama kome da aka share makoki suka ce sun fasa. Domin basu gayawa mana sun fasa ba sai da azumi ya rage saura sati biyu a lokacin yake bada kudin kayan abincin wata guda. Abin ya dame ni sosai domin raina yayi masifar b'aci, ana cikin wannan yanayin aka ce an samu wani ya dauki nauyin abincin. Kuma yazo yana wurin Baba. Sai a lokacin Mama take ta zolayata. "Ummu ina zaki kai son kuɗi ne haka?" "Allah Mama ba wai don kudin da nake samu ba ne kawai sadakar yana da amfani. Sannan ina shan addu'a a wurin Mutane." "Allah yasa mu dace!" "Amin nace mata!" "Hadiza!" Muka tsinkayo muryan Baba yana kiranta, mikewa tayi ta fita can ta kuma dawowa suka fita da shi. Koda ta dawo ban kuma bin ta kanta ba, sai dai na ga ta fita zuwa gidan Mama Amina. Ban san me ya faru ba na ga dai sun dawo tare suka tasani a daki ana ta min wani irin bayani da ban gane kanshi ba. Ni lissafi idan ba na abinci ba ai gani nake kamar bata lokaci ne. Ni dai washi gari na shiga kasuwa nayi sayayya sosai sannan na dawo muka ci aiki kamar ba gobe. Har ana gobe za a fara azumi bamu daina aikin ba, da yamma muna busar waje aka shigo mana da nama, wai Alhaji da ya dauki nauyin abincin azumi ne ya turo da namar, ni dai haka muka gyara aka saka a firji, washi gari aka fara azumi duk fadin duniya muka yi kunu da kosai, sai shinkafa da mita wanda yaji nama. Idan aka gama muna sakawa makota da mutanen gidanmu, duk da Mama ta gaya min nayi harkan gabana kada na damu da kowa nayi abin da na ga xan iya shi yasa ban tab'a kallon yan gidan mu a cikin rayuwata ba. Duniyata da Uwata da kannena sune a gabana domin ko lokacin da kanina Ahmad ya samu scholarship ba karamin artabu aka yi ba wai Baba yana fifita yan dakinmu. Haka ya zuba musu ido. Ahmad ya tashi a tsakaninmu duk abinda ya gani na hidimar gida da kome sai ya kira ya gaya min sannan ta tura min ta facebook din Uwani domin ni dai irin wannan haukar bai dame ni ba, sai daga baya wani zuwan shi hutu ya zo min da waya waya. Anan yake turo min da kayan kitchen mu kuma da mama muna tura mishi kudi, idan ya saya dayawa sai ta turo min ra cargo. Idan aka kawo gidan Hajiya Amina muke kaiwa tana da extra daki da take zuba min shirgina. Hatta kayan gado a can ya saya min aka kawo min. Sannan a gidanmu ana ganin duk wahalar da nake yi ba mamaki idan bikina ya tashi nauyin zamu daurawa Baba shi yasa ake yawan samun rigima akai na. Azumi yana kawai goma da safe na je gaida Baba yake gaya min. "Hajiyar tuwo da miya, bayan tarawi akwai bakon da zaki yi don Allah a tsaya a mutunta shi kamar yadda na san ki da halin ƙarammaci!" "In sha Allah Baba!" Daga nan na dawo daki ko Mama ban gayawa ba, haka muka yi ta aiki bani da kuzari, bayan ana sha ruwa ina kwance yaro ya shigo . "Aunty Baby ana sallama da ke!" "Tow gani nan zuwa!" Na fada ina kwance. "Tashi ki je mana!" "Tow Mama!" Ma fada ina jin damuwa, haka na shirya na fita akan zan musu iso zuwa parlourn baki. Ina fita na hango su a jikin Motarsu, domin nace haka ne saboda dayannsu da ma gani cikin motar karasawa nayi zan musu sallama daya ya ce min. "Kanwata don Allah ki shiga gidan can ki kira mana Ummu Hadiyya!" Sai naji na diririce, baki na yana rawa na ce musu. "Ai ai ni ce!" Yana latsa waya ne bai san lokacin da ya d'aga kai yana kallona ba. Karewa kunna torching wayar yayi yana haska ni daga kasa har sama kafin suka kwashe da dariya, su biyu shi wanda yayi min magana bai yi dariya ba, sai cewa yake. "Meye haka Tafida Mahmoud Meye na biye shi kuna dariya." Idanuna ne suka cika da kwalla san lokacin da hawaye ya zubo min ba. Ina tsaye sai dariya suka tare da faɗin. "Wai Tafida kayi kamuwa wai ina ruwan kashi da rai! Ka ga hancinta kuwa ina ruwan mitsil!" Wani irin kuka ne ya zo min. Har jikina yana rawa, na juya xan tafi shi wanda ya haska ni ya ce min. "ke Ummu kike? Tow ki gayawa Mutumin da ya zo gidanku idan ya sake zuwa ki ce ni tafida ban miki ba." "Dalla me yasa kake yin haka ne? Mahaifinka ne fa kake cewa mutumin da yazo kamar wani sa'anka!" "Deen babu ruwanka da ni, ya ga Yan mata kalar gari a hada ni da wata kucaka wacce bata da bambancin da yar kauye. Idan kai haka ka shirya rayuwarka ni tawa da banbanci.... #500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 09 "Kyale shi Tafida idan kana niman bagidaje ka samu Deen ai magana ya ƙare, banza ko shi aka hada da wannan me magana busashen kifi ba yarda zai yi ba, don Allah duba ta kamar wacce aka gama rabon halitta aka manta da ita sai daga baya aka yi karo-karo..." Bangaje kafadarshi mutumin da yake musu fada yayi yana faɗin. "Sannu Ubangiji da ya iya tsara halittar kowa!" "Kada dai ka fita musulunci don na lura ba Tafida aka turo ganin yar baby ba kai ne" ya kwashe da dariya, yana.nuna Deen din. "Kanwata" ko sauraronsu ban yi ba na nufi gidan a zaune na durkusa na fashe da wani irin kuka, na kai minti ashirin a wurin kafin na mike zuwa cikin gida sai da na wanke fuskana, sannan na shiga dakin Mama na ce mata. "Na dawo Mama" na fada zan fita daga dakin. "Ya kuka yi?" Na ji ta tambaye ni. Bakina yana rawa dake ban saba mata musu ba na ce mata. "Allah yasa haka shine mafi alkhairi!" "Alhamdulillahi Ubangiji ya tabbatar da alkhairi." Juyawa nayi zan fita ta ce min. "Ummu Hadiyya Yaron yayi miki?" A hankali na kara juyawa hawaye na zuba min. Na ce mata "hm!" "Ki kwantar da hankalinki in sha Allah lokaci yayi da zaki tafi dakinki,masu ganin ba zaki yi aure ba su sha mamaki." Hawaye ne ya kara zubo min Mama bata damu da nawa damuwar ba bukatattar nayi aure ta huta da maganar har yau na ki aure. Bani manta lokacin da Ummu Rooman ta haihu ranar sunan da muka je gidan sunan haka wasu daga cikin dangin Mama suka yi ta min magana wai ina nan ina ruwan idanun. "Ina zata yi aure tana jin kudi na shigo mata, sannan har da laifin Hadiza da ta rike mata kan maciji tana wasa da wutsiyarshi." Ni dai ban ce kome ba, haka suka gama mita wai naki aure. Haka na shiga dakinmu. Na kwanta sai na fahimci barcin ba zai min ba, kawai na tashi ma nufi waje nayi alola na zo na gabatar da sallah nafilla, ban tab'a ganin daren da yayi min tsawo kamar wannan daren ba, sam barci ya kaura ce min, domin har karfe biyu da rabi yayi muka daura abincin sahur bana jin ko gyangyadi, haka na yi ta aiki har muka gama hudu saura Mudan yazo yayi ta fita da shi ana rabawa mutane. Uwani ta lura da bani da kuzari ta ce min. "Aunty Baby ko zan zubo miki tuwon ne?" "A'a zan sha lipton ya isa!" Haka muka yi sahur sannan muka kama aiki sai da aka yi sallah asuba muka kwanta, musamman ni wurin karfe daya na farka. Dakin Mama na nufa da na leka na ganta da Aminiyarta, "Mama Amina ina kwana?" "Lafiya lau Ummu kin tashi lafiya, sai nake jin abin arziki Allah ya tabbatar da alkhairi!" Gyada kai nayi kawai na dawo dakinmu na kwanta. Ban san me suke ta yi ba sai dai azumi na da goma sha biyar suka sake dawowa, da yamma bayan sallah la'asar. Tunda aka gaya min na kasa fitowa, Mama ta ce min. "Wai baki ji baki kika yi ba?" "Na ji!" Na saka hijabi na fito a parlour Baba na same su dake yana gida, "gaida da shi na fara yi sannan na gaishe su, ashe yau har da Babansu suka zo!" Hadiye yawu nayi domin na ga shi daya ne. Babu abokanshi. "Kasan yayi dan majalisar wakilai kafin ya dawo, ko nace suka dawo da shi yanxu yana tare da shugaban kasa ne, Alhaji Bulama ka ganshi talatin da bakwai yake so nake ya samu macen da zata rufa mishi asiri, yar mutanen kirki wacce zata haska mishi gidanshi da na Yaranshi. Shi yasa na ce maka xan turo shi ya ganta, jiya nayi magana da shi ya ce min na tambayi Yarinyar shi tayi mishi sai dai wai ita ta ce bata amince ba!" Mutumin ya zuba min idanun da nayi kasa da kaina, ina jin kwalla na cika min idanu. "Ummu ce ta ce bai mata ba? Amma yadda nasan Ummu ba zata fadi haka ba, domin ranar da suka zo Mahaifiyarta tace min ta amince sai dai ko a tsakaninsu, Alhaji Muhammad Jadda bani na haifi Ummu ba amma wallahi a gaban Allah zan yi shaidar ta tun tana yarinyar bata musu da babba matukar kace mata yi nan zata bi nan, duk cikin Yaran gidan nan babu me hakurinta. Amma idan kuna ganin haka akwai matsala Allah ya zab'awa kowa abin da yafi alkhairi, domin kada muzo ana kace nace, sannan da Yarana da na haifa ne suka fada mishi haka na rantse da azumin bakina zan ce maka zasu aikata amma Ummu nayi mata shaidar da ko a bakin mutuwa nake xan bada labarinta." Baba wani irin mutum ne haka? Baba ya yarda dani sama da yarda da yayiwa Yaranshi. "A'a Alhaji Bulama ni naga fitila a gidanka, kuma ba zan tab'a barin shi ba sai ya haska min gidan Tafida, Yarinyar tashi ku tafi ku gaisa!" Ya fada yana kallona cikin kauna da soyayya. Haka na fita na nufi zaure. Ya fito cikin isa da kasaita. Kallona yayi ya ga na had'a kaina da bango. Yana tsaye kafin ya ce min. "Kika sake kika aure ne hmmm, da kafarki zaki gudu!" Kaina yana kasa nace mishi. "Ni Y'ace mai tarbiyya!" "Yar Mace ba? Yar tuwo-tuwo ba jahila irinki ake kira da fitila. Ita Babarki.." a lokacin na d'ago kai na kalle shi kamar xan yi kuka nace mishi. "Ina ganin darajar iyaye ko ba nawa ba, sannan kada ka sake ka zagar min mahaifiya, domin nasan darajarta tunda har uban riko na yayi min shaidar da ko a gaban Allah zai iya vada shaida Kaina haka ma yabwadata, kada haukarka ya ja ka zagar min mahaifiya domin na san darajarsu. Daga kalamanka na fahimci rufa maka asiri aka yi domin shigowarka gidan nan baka isa ba, baka da ikon shigowa wannan gidan gidan dattawan arziki ne da suka san tarbiyyar kansu da na yaransu. Bance ka zauna da ni dole ba amma kada ka zagar min iyaye domin suna da daraja sosai." "Me kike nufi?" "Ban nufin kome sai dai na gaya maka ko wuta suka ce na shiga xan amsa musu da harshen tarbiyya nace musu na amince kuma xan bi yadda suka ce. Domin na kara musu godiyar abin da suka yi min na zuwata duniya, ba kowa yake fahimtar haka ba sai daliban islamiyya wadanda suka samu tarbiyya suka koshi." "Ke!" Ya buga min tsawa, da sai da cikina ya kad'a. "Ni ne bansan darajar iyaye ba?" Ya fada tare da dukan bangon inda nake tsaye? Baya na ja tare da rintsa idanuna. "Na amince da aurenki, amma ina baki shawara ki sayo likkafaninki ki zo min gidan dashi yadda ko kin mutu ba sai an sha wuyar saya a wani wurin ba." Ni dai ban ce mishi kome ba, domin na lura kalamai na sun yi zafi muna tsaye muka jiyo muryan iyaye mazan, sake fuska yayi yana faɗin. "Gobe za a kawo miki kayan azumi da kayan sallah. Na gode sosai da amincewarki!" Ni dai ban ce kome ba domin na lura mugun dan wasan kwaikwayo ne. Haka suka tafi gida suka bar ni da ciwon kai. Har aka sha ruwa ban dawo nutsuwata ba, washi gari kuwa sai ga sako da kaya niki-niki kamar hauka,aka ce min yana waje sanye yake da blue jeans sai rigarshi red shirt, me guntun hannu, sai yanxu na ga dalilin da yasa yake hauka ashe Allah yayi halitta, sai na rena kaina na fita har inda yake na tsaya tare da sallama. Bai amsa ba ya ce min. "Nasan baki saba shan abin da na kawo ba kada a sayar domin ayi wani uzuri da shi, don Yasan getto area sun iya rayuwar reni. Akwai manyan atamfofi da lace maybe tunda kike baki tab'a sakawa ba,na so na saya gwal amma akace ku Yaran talakawa ai baku wani san darajar gwal ba!" Murmushi nayi na zaro yatsun hannuna, ina gyara zaman zoban hannuna guda biyu na gwal ne. "Wannan ka gayawa wanda ya gaya maka, ni Ummu zanin da nake shiga aikin tuwo-tuwo da shi super wax ce. Tun kafin a haifi uwar me sabulu balbela take da farinta, kayanka ka tsaya a baka su kai ne ma xan tausayawa da alamu arzikin da kake da shi na hucin gadi ne, jikan dan karuna!" Kasa magana yayi musamman yadda na rama cin mutuncin da yayi min, a fusace ya shiga motar shi ya bar unguwarmu. Kayan da ya kawo ko daya ban tab'a ba, kuma ban bari an tab'a ba, bai kuma zuwa ba. *Aliyu Tafida Jadda* Ya taso cikin wani irin rayuwa ne, mara dadi ko nace mara sukuni. Sakamakon irin gidansu. Shine ya na biyar a cikin gidansu. Hajiya Aisha itace mahaifiyarsu wacce suke kira Hajiya, yan uwa ne da Alhaji Muhammad Jadda, aka yi auren zumunta. Duk da suna son juna sosai haka bai hana Alhaji Muhammad karo mata kishiya ba, A haka suke zauna lafiya da Hajiya Baraka wacce ta boye halinta saboda Alhaji Muhammad Jadda bai dauki renin hankalin ba gidanshi akwai zaman lafiya. Alhaji yana da kanne biyu, Alhaji Nura sai Alhaji Saleh. Suna zaune a gida ɗaya bakiɗaya. Tun basu yi aure ba suke tare wa da Hajiya take daukar nauyinsu. Ma'ana cin da wasu abubuwan gidan, Alhaji Nura yayi aure inda ya auri wata Shuwa. Shi kuma Alhaji Saleh ya auri bafulata daga Yobe mai suna Zainab, sai dai haduwar gidan ya janyo wani gagarumin tashin hankali, domin bakidaya suka hadewa Hajiya kai, fadar yau daban na gobe daban ba kowa ya hadassa haka ba, sai zuwan Shuwa. Tana bin malamai sosai amma tafi ƙarfi wurin munafunci da makirci, da ita shi take hada Hajiya rigima da matan gidan. Wani tashin hankali da ya faru kuwa ba wani abu ba ne ya haifar da haka sai lokacin da Barakatu ta haife danta Khamil, wanda hajiya ce tsaye akan kome, Yaron bai amsa suna ba ya koma anan aka ce Hajiya ta kashe Yaron, duk da a lokacin Yaranta biyar, Abubakar, Umar, Rukayya, Maryam sai goyon Aliyu da bai wuce wata tara ba. Jin wannan lamarin iyayen Barakatu suka ce basu yarda ba, haka suka yi ta rigima har za a kai kotu, Alhaji kamar wanda ake ingiza shi ya sake Hajiya, ita kuma jin haushin haka ta ajiye mishi Aliyu, anyi juyin duniya nan ta amshi Yaron tace ba zata amsa ba, kada yaron ya mutu ace shima kashe shi tayi, haka Hajiya ta tsallaka Yaron da bai da laifi ta bar shi, a lokacin Abubakar ya bar makaranta yana kula da Aliyu, wanda Barakatu ta sako Yaron a gaba, saboda tsnar da tayi mishi. Wata rana Shuwa tayi bakuwa ta ga Aliyu ya mata kyau amma kuma cikin wahala gashi karami sosai. Kallon Shuwa tayi tana faɗin. "Ke Shuwa wannan yaron fa zaki more shi dauke shi ko gyara shi babu wanda zai fi ki moranshi!" "Ke ban haifa ba, ba zanyi wahalar dan wata ba!" Dariya matar tayi tana faɗin. "Kin manta sunana ne Rabi me idanun mikiya! Wallahi Yaron nan akwai kashin arziki a jikinshi na rantse kuma ki saka a bincika miki." Da wannan Shuwa ta fara kula Aliyu wanda Alhaji Nura yake gayawa Yayanshi abin da Shuwa take yi, Alhaji yaji dadi kamar me. Haka yayi ta mata hidima a lokacin kuma kishin Barakatu ya dawo kan Shuwa. Duk da tana rike da Tafida amma babu zancen tarbiyya domin dai tarbiyya yayi gabar Aliyu yayi yamma, sannan ta cusa mishi kiyayar iyayenshi daga Alhaji har Hajiya wacce ta auri wani dan kasuwa a Chadi. Haka Aliyu ya taso da tsanar Hajiya domin yana ma jin maganar Alhaji wani lokacin. A hankali ya fara bin Yaran unguwa yana yan sace-sace, nan ma sai da Alhaji yayi da gaske, sannan ya bar wannan halin. Bayan an gama haka ne ya fara bin yan bangan siyasa ko secondry school bai gama ba, tan Alhaji ya b'aci a lokacin ya dauke shi zuwa sudan wurin wani abokinsa. Anan ya samu nutsuwa sai dai Aliyu Tafida ya taso bai da kunya bai san girman kowa ba, abin da ya sani ka tab'a shi zai tab'a ka. A duniya bai da abokai sama da Deen da Mahmoud, domin kuwa sune suka taso tun Yarantarsu, Deen iyayenshi talakawa ne, sab'anin Mahmoud da iyayenshi suke da kudi sosai, sai dai a duniya babu abokin sirrin Tafida kamar Deen domin me zasu yi babu me jin abin da ya faru a bakin Deen sab'anin Mahmoud da bakinshi kamar reza. Dukkansu Deen ya fisu tarbiyya sosai domin yana bala'in tsoron iyayenshi, shi yasa da suka ga zai lalace irin na Yaran masu kuɗi Babban ya tura shi bodin school, kamar yadda aka tura tafida Sudan, sai Mahmoud ne yake gararanba a unguwarsu, haka yasa ya lalace amma idan baka sani ba sai ka zata bai aikata kome tun yana secondry school yake bin mata, da suka gama Tafida yazo hutu Deen ya zo shima anan suka kara haduwa, yayi kokarin bayyana musu sabbin abokan da yayi, kai tsaye Aliyu Tafida ya ce mishi. "Waɗannan yan iskan zan tsaya ina abota dasu, kaga ina da ra'ayi ni ba zan iya mu'amala da su ba, ka fahimta." Shima Deen yana tare da Tafida, amma Mahmoud gani yake Deen yake zuga Tafida. A lokacin gwamnatin jahar Borno ta bawa Yara masu kokari scholarship a cikinsu har da Deen. Kuma ikon Allah an tura su Sudan. Ba karamin dad'i Tafida ya ji ba, a rayuwar Tafida Deen yayi yaki sama da yadda ba a zato, domin kuwa ya saka shi akan hanya, daga wasa da ibada rashin mutunci duk sai da Deen ya raba shi da su, Deen bai kara wasa da damarshi ba sai da ya ga Aliyu yana kiran mahaifinsa sau uku, duk da Alhaji Muhammad Jadda yayi wasa da damarshi na tsayawa a matsayin Uba, Amma Deen ya nunawa Aliyu illar rashin tarbiyyar da yake nunawa mahaifinsa. Wani bin har fada suke yi. Wani abin da yake karawa Deen kaunar Aliyu bai taɓa mishi gori ba, a'a gani yake kome na Allah . Sai dai inda Deen ya kasa nasara akan Aliyu shine mahaifiyarshi, a duk lokacin da ya fara mishi zancenta tow sai sun yi kwana uku basa magana sannan Aliyu yayi ta zazzaɓi kenan. Haka yasa Deen ya daina mishi zancenta domin baya kaunarta. Asalin kinta yake kamar zai mutu. Haka suka gama karatunsu na degree inda Deen ya karanci kimiyyar kera-kere. Yayinda Aliyu Tafida ya karanci kimiyyar siyasa, domin kuwa haka kawai Allah ya daura mishi burin siyasa yana da shekaru ashirin da daya ya hada degree shi da Deen dinsa,suka dawo a lokacin Mahmoud yake kawo musu zancen Yan mata. Dariya Aliyu yayi ya ce mishi.."kai mace take damu ni nan mace bata gama!" Deen ya ce mishi. "In sha Allah ba xan yi aure ba sai na hada degree na biyu zan duba macen da ta dace da ni!" "Kai Malam sai ka tsufa baka yi aure ba kenan!" Inji Mahmoud kyale shi suka.yi, samari biyun nan komawa jami'ar Maiduguri suka yi inda suka sake fitowa da wasu kwalayen degree na biyu, a lokacin Idanun Aliyu ya fada kan siyasa, saboda yayi wani aiki a majalisar wakilai na Nijeriya, a nan suka hadu da Alhaji Mansur Goza, mutumin nan shaidani ne. Hajiya Aisha. Tasan tayi laifi na barin Aliyu, amma matar nan bata tab'a kwanciya ba tare da ta mikawa Allah sunayen Yaranta ba, bata tare dasu amma saboda tashin hankalin ta barsu a baya bata barci sosai, sai ta mike tsaye ita ce sadaka ita ce ta saka ayi musu sauka, a lokacin da taji labarin Tafida yana hannun Shuwa, saura kiris ta kauce Hanya Allah ya taimaka ta dawo kan hanya, matar nan mijinta yana da rufin asiri,domin sai da ya kara biya mata aikin hajji. Ta je tai ta addu'a Allah ta kare mata Yaranta. Hajiya bata tare da su amma tana jin Allah yana kare mata Yaranta. Haka suka shekara ashirin bata saka su a idanun ba. Sai wani rasuwa da aka yi a family tazo ta'aziya. Taga yaranta wanda ta zame musu baki. Tayi kokarin danne zuciyarta, domin bata ga wani abu me muni a tare dasu ba, sai dai Yaran sam bata gabansu. Haka ta dawo tayi ta kuka tana gayawa Allah lamarinta, bayan shekara daya ne sai ga Yaran su hudu suka zo mata, tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa hatta makota sai da suka zo tayata murna. Kishiyarta ma kamar tai yaya don murna domin ta kwashe yaran kishiyar duk ta riƙe, kwanan su biyu anan suke gaya mata an saka bikinsu Maryam da Rukayya zasu koma. Tayi murna sosai bayan tafiyarsu mijinta ya bata kuɗi suka yi sayayyar kayan aure, mota guda aka kai gidan Inna aka ajiye da bikin taso haka tayi gayyar mutane aka sha biki, Alhaji Muhammad Jadda ya kuma tsaya sosai akan Uwar Yaranshi, domin sun so cin mutuncinta.ya ce bai yarda ba ko babu yara kanwarshi ne, bayan gama biki yaje har chadi, yayiwa Mijinta godiya da irin dawainiyya da yayi dasu. Aliyu ya fada harkan siyasa, duk da Alhaji bai so ba, haka Shuwa tai ta zuga shi ai Alhaji baya son cigaban shi ne da yan dakinsune, da Yawan Baraka ne da tuni ya tsaya musu, haka ya ƙara rura wutar kiyayar iyayenshi a ranshi, daga ƙarshe sai Alhaji ya zuba musu idanun domin yasan ana zuga Aliyu a gefe. Ya fara da wakilin matasa na unguwarsu ya samu damar rike muƙamin kansila da goyan bayan Mansur Goza, ana gama wannan shekarun ya samu Chairman na karamar hukumar borno, a lokacin ya rike kudi kamar hauka. Kwatsam Alhaji Mansur Goza ya kara janyo shi harkan ya saka har ya samu takarar dan majalisar jahar,babu yadda ba ayi yayi aure ba amma fir yaki. Addu'ar Hajiya yana bibiyarshi ta ko ina haka yasa bayan shekara hudu ya samu damar zama ɗan majalisar wakilai, a lokacin yana da shekaru talatin da biyu. Anan lissafin ya fara kwacewa Tafida domin kuwa bai da kunya bai da kalamai abin da ya fito bakinshi yake yabawa kowa. Ga dan iskar renin hankalin. Rigimarsu ta fara ne lokacin da Alhaji Mansur Goza ya fara takura mishi da ya bashi kudi da yayi mishi kaza shi kuwa ya fara gajiya yace ba zai yi ba, ai kuwa dake ya fishi sanin siyasa yasa aka dawo da shi, aka yi ta rigima wanda ta ja har aka kore shi a aiki. Haka bai isa ba sai da Mansur Goza ya fara farautar rayuwar Aliyu Tafida. Domin sau biyu ana rutsa shi har da wani sara aka mishi a gadon bayanshi. Anan ne Alhaji Muhammad Jadda ya kai karar Mansur Goza har Fadar shehun Borno. Lokacin sakataren shugaban kasa yazo gaida Mai martaba, aka case nan Alhaji Muhammad Jadda ya juya turanci aka yi ta bugawa kada ku manta Alhaji Mansur Goza irin jahilan yan siyasan nan ne da basu da wani ilmi kawai ana amfani ne da sunan siyasar. Aikuwa abinka da renon Ingila mai martaba da suka yi gwagwarmaya tare da Alhaji suka tsaya aka yi magana Mansur Goza ya ce ya cire hannun shi akan Aliyu ko ciwo yayi a kama shi, haka yasa Sakataren shugaban kasa ya cewa Alhaji Muhammad Jadda ya ce mishi. "Aliyu yana da matasa iya su kadai zasu iya tsaya mishi amma yanxu domin kara karfaffa mishi gwiwa zan shigar da batun shi ga shugaban kasa!" "Dr Mandara ni bana son harkan ne!" "Shi yasa aka yi ta binka, amma ka ki tunda ka haife siyasa sai hakuri amma yanxu ma zan kira shugaban kasa na gaya mishi dama tun kwanan baya yace yana niman matashin da zai kira musu jama'a." Duk da Alhaji bai so ba haka yayi musu fatan Alkhairi. Haka Aliyu ya kara tafiya siyasa kuma Allah ya mishi nasibi. Hajiya shuwa tana da yarta wacce ta boye ta, mai suna Sa'adiyya, yarinyar ana zargin ma bata da Uba, amma haka Hajiya shuwa ta boye ta, domin tasan zata zame mata makami mai linzamin. A lokacin da Aliyu ya fara samun kyakkyawan rayuwa dama a gabanta yake a lokacin ta dawo da yarinyar kuma kowa ya amshi yarinyar saboda yadda Hajiya shuwa ta saka aka tarbiyyar da ita. Tana da hankali a idanun da mu'amala amma shaidaniya ce kamar Uwarta, sannan kashewa yarinyar kudi take kamar bala'i, a lokacin da ta gama tsara Aliyu Tafida ya kai inda ya dace gashi a matsayin da ya dace su more shi sai ga Alhaji Muhammad Jadda ya sako batun ya sama mishi mata, wanda bai mata dad'i ba, da Aliyu ya gaya mata yaga yarinyar bata mishi ba hakuri tai ta bashi tana cewa. "Naso yadda na sha wahalarka, ga kanwarka Sa'adiyya nasan zaku yi farin ciki da had'a ku!" Dama can Sa'adiyya tayi mishi ta ko ina amma ganin abin da Alhaji ya Kunno yasa aka yi ta artabu da yan uwanshi musamman da ya gaya musu irin Ummu.... *** *Ummu Hadiyya* Ban san meye shirinsu Mama ba, amma kuwa naga har Kano suka yi ta tafi sannan ga Karami da yake ta aiko da kaya wanda ashe Mama tayiwa Ummu Kulsum magana anata sayan kaya a Turkiyya. Aka sallah yazo aka yi bikin sallah aka wuce a lokacin aka fara hidimar bikina wanda ashe an saka tun cikin azumi, ko yan gidan babu wnada ya sani daga Mama sai Hajiya Amina aka yi ta hidima wanda aka saka goshin sallah layya. A lokacin na firgita sosai domin rashin mutuncin Aliyu bai bari ba, biki saura sati biyu aka kawo kayan aure da aka yi min shi a wulakance saboda ganin ai ni yar talakawa ce, sai dai ganin irin kayan karban da aka basu tare da tukwaici yasa Aunty Yaana ta koma ta gayawa Alhaji Muhammad Jadda abin da ya faru, an kawo kayan da kwana hudu aka.sake kawo wanda yafi na farko Baba yayi ta fada ya ce shi ba sayar da ni zai yi ba. Domin an saka bikin da gaggawa. Alhaji Muhammad Jadda yayi ta bashi hakuri, tare da niman alfarmar kada a kawo ni da kome, anan ne na ga amfanin Mama tace ai ba ta san da haka ba, kayan fa an riga da ayin min..... N500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 10 Shi dai Alhaji Muhammad Jadda bai so haka, domin shi gani yake auren da aka basu baka karamin alfarma aka yi musu ba, bikin na kara matsowa abubuwa suna kara fito domin kuwa shi dai wanda ake kira da ango tunda ya koma Abuja ba kara jin motsinsa ba, wata juma'a ina lissafin kudin abinci aka, ban d'ago kai ba don naji muryan Yara ne. "Aunty Baby kina da bako a waje!" "Tow gani nan zuwa!" Don a tunanina shi ne ya zo. Shiri nayi domin yau ba zan yarda ya gaya min magana na kyale shi. Haka na mike na daura mayafi kan gown din jikina. Na fito daga cikin gidan, abin mamaki ba shi ne wani ne da ban gane shi ba. Na isa har inda yake cikin mutumtawa na gaida shi. "Barka dai!" "Yawwa Hajiya Ummu Hadiyya!" Shiru nayi kafin na ce mishi. "Ban gane ka ba." "Eh gaskiya ba zaki gane ni ba, da farko sunana Mahmoud abokin Tafida wanda zaki aure a yan kwanaki da suka rage. " "Ai na fahimta! Da Fatah lafiya ko!" "Eh tow lafiyar kenan shi yasa nazo na taimaka miki kada ki dauka nima azzalumi ne!" Sai yanzu abin ya fado min dashi ranar suka yi ta min dariya. Murmushi nayi kafin na ce mishi. "Ina jinka!" "Dama ina son na gaya miki ne, ki dakatar da iyayenki akan aurenki da Tafida domin ba mutumin kirki ba ne." Shiru nayi fuskata dauke da murmushin takaici na ce mishi. "Tow yanzu me kake so nayi?" "Yawwa Ummu ni ina son ki fasa aurenshi ne, sannan zan yiwa Iyayena magana su zo don na ga ke yar mutunci ce, kin san darajar iyayenki!" Cike da mamaki nake kallonshi abokinsa ne kut da kut yazo yake sararshi wani irin abota ce haka? "To na gode sosai da shawararka, amma ina son ka sani iyayena ba kananun mutane ba ne, idan suka ji labarin nan zasu iya min fada ni kuma duk abin da za ayi min fada bana fatan ya faru, na gode sosai maganar zaka turo manyanka bari na tuna maka haramun ne nima a cikin nima, hadisi ne ingantaccen daga Bukhari da Muslim, na Barka lafiya." Na juya zuwa cikin gida, "Aliyu ne?" "A'a" kallona Mama tayi tana son magana amma sai ta share tana me cigaba da aikinta. Tun bikin saura kwanaki biyar nayiwa duk kwastamomina sallama tare da gaya musu aure zan yi ga Kanwata Uwani zata cigaba daga inda na tsaya, sun yi fatan alkhairi, wasu ma washi gari sai ga shi ana ta turo min gudummawarsu, ban san yan gidanmu sun fitar da anko ba. Sai daren da aka kawo min kayan da zan saka na zuwa dinner ne oho can suka sani. Abin mamaki wannan gayen da wanda yayi musu magana ranar zuwansu na farko suka zo ya kawo min kayan. Dake ni da Uwani muka fita, ita ta amshi kayan. "Hajiya Ummu ni sunana Deen shi kuma wannan.." "Mahmoud ko?" Na tambaye shi, a dan razane shi Mahmoud din ya kalle ni. "Ya aka yi kika san sunanshi." Murmushi nayi nace mishi. "farkon zuwanku!" Gyada kai yayi ya ce min. "haka ne kiyi hakuri wakili zai zo amma sai ana jibi biki!" "Ba kome na gode! Sai an jimarku!" Na juya na koma gida domin tunda aka saka bikin na rage saka manyan hijab wanda yake nuna kankantatta. "Deen gayen nan ya samu mace, asalin yar dakar idan kana jin mace yar dakar yarinyar nan ce. Idan ya sake ya rabu da ita ni zan shiga na fita na aureta domin irinsu Ummu Hadiyya ba matan su Tafida ba ne." Sake baki Deen yai yana kallon Mahmoud. "Kana nufin zaka iya cin amanarshi kenan!" "Idan ya bani kofar haka zanci domin shima yaci Amanar iyayenshi wurin amsar zabinsu!" Naushi Deen ya kai mishi me karfin da sai da ya fasa mishi baki. Dariya yayi yana faɗin. "Ko zaka kashe ni wallahi ba zan barwa Aliyu Ummu ba domin matsiyaci ne da bai san darajar Iyaye ba, idan ka isa ka dakatar da ni." "In sha Allah, matukar ina Numfashi ba zan tab'a barin Aliyu ya rabu da Ummu ba matuƙar ina raye sai na kare martabar Aurensu ko haka zai zama karshen rayuwata." Dariya Mahmoud ya cigaba da yi yana faɗin. "Muje bingo! Amma ka sani matukar kudi na aiki sai na raba su dama daya tak nake nima na bawa kowa mamaki! Tafida Tafida kowa tafida kowa Tafida kowa tafida kowa, Nasara Tafida iyaye na gari Tafida wife material Tafida, Aboki irinka tafida , degree da Masters Tafida. Ni ne koma baya babu wanda yake fadar Mahmoud." "A'a Mahmoud muna sonka kada ka lalata mana abotarmu ta yaranta don Allah kada ka zama me son kai!" "Wani irin kuna sona? Kai ka raba Ni da yardan tafida baya shawara da ni bata gaya min kome akanshi, sai dai na ji kuna tattaunawa a sirri. Haka shine abota? Haka shine aminta? Dama an fada abota ta mutane uku tow akwai munafiki a cikinsu kuma ba kowa ba ne sai kai!" Ya share gefen bakinshi da ya fashe yana faɗin. "Na jima da sanin kome kuka saka a gaba sai kunyi nasara, kai kana aiki a state University Maiduguri, shi yana tare da shugaban kasa, ni kuma Uwar me kuka mai dani?" Ya fada da karfi Deen sai yaji kamar da gaske sun yiwa Mahmoud kuskure. "Mahmoud babu wanda yaki ka, Mahmoud ka san ba karfi iyayena suke da shi ba, wannan matakin da nake Allah da gwamnatin jahar Borno suka kawo ni wurin, wallahi ban tab'a maka kallon wanda ya gaza ba, Please na haɗaka da Allah kada ka shiga wannan zabin da Abba yayi mishi wallahi Tafida yana buƙatar mace ta gari, kai kanka kasan gidansu ba barin shi suka yi haka kawai ba don Allah mu taya Hajiya karkato da hankalinshi" yadda Deen yake magiya ya ce mishi. "Ya wuce na hakura! Na bar zancen." Ajiyar zuciya Deen ya sauke, sannan Mahmoud yasan ko mutuwa yayi Deen ba zai tab'a fitar da maganar nan ba domin mutum ne mai mugun sirri da zurfin ciki. Duk wani abun da ake na al'adar kanuri babu wanda ba ayi mana ba, Baba ya tafi har wurin Mahaifina ya gaya mishi kome da kuma Maganar auren da cewa za a kawo daurin auren wurinshi. Cikin girmama lamarin juna, sannan ya dauko kudi kusan miliyan daya ya bawa Baba Bulama ya ce mishi. "tun daga ranar da aka haifeta nake ajiyar shi nasan mace ce kuma Yar hidima ce wannan ku kara da shi, sannan akwai kayan gara. Domin nasan kabilar da tayi aure cikinsu mutane ne masu matukar girmama lamarin Gara!" Duk da Baba Bulama so hana shi, amma yaki. "Ita ce daya tal min a duniya don ma Hadiza ta hanani ita, na gode sosai da irin dawainiyya da kayi min wallahi ka biya ni, amma don Allah ka turo min mijin na zaga da shi wurin yan uwnaa!" A take Baba ya kira Alhaji ya gaya mishi har ya haɗa su da Baban suka yi magana, Alhaji ya jaddada mishi gobe tafida zai zo kuwa. Sannan Baba Bulama ya ce mishi. "Zasu zo tare da Ummun In sha Allah!" Koda Baba ya dawo haka ya sami Mama da maganar, bata ki ba ta gaya min, na dauki kayana kala biyu domin Baba ya ce na kwana a can ranar daurin Aure za a wuce da ni gidana. Mama kan bata so haka ba amma yadda Baba Bulama ya fada bata kauce zancenshi, haka ni da Uwani muka shirya domin ban yi a raina Aliyu zai zo ba. Haka na kwana ina juya zancen, da safe wurin karfe takwas sai ga sallamarsu har cikin gida suka shiga suka gaida Baba dasu Ummi da Umma, yan matan da suka.fara zuwa hidimar bikin da yan uwan Mama sai aka fara surutu dama wannan Ummu zata aura. Lokacin da ya iso part dinmu ya samu Mama tana ta lissafin kayan abin da za a sayo a kasuwa. Cikin sakin fuska Deen yake gaida kowa yana me godiya da fatan Alkhairi. Shi kan ina hango shi ta window yadda yake yiwa Mama wani irin kallo irin na renin hankali. "Aliyu kake ko? " ta nuna Deen girgixa kai yayi yana murmushi yana nuna tafida da ya sunkuyar da kai kamar mutumin kirki, "Allah ya shiga lamarinku bakiɗaya ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyiba! Ku tafi kada rana tayi muku!" Ta fada tana me kallon Uwani da ta fito dauke da jakarmu. "Uwani maza ta fito ku tafi!" Ina jinsu, sai da Uwani ta kara kirana na fito ina me zama a kusa da ita. "Mama!" "Meye kuma Ummu? Bana sallame ki ba!" A hankali na gyada kai zan yi magana kuka ya kwace min. "Mama idan nayi miki wani laifi don Allah ki yafe min, ki saka min albarka kamar yadda Mahaifiyar Nana Mariam ta saka mata don Allah ki albarkaci rayuwata da yawun bakinki, Mama don Allah ki yafe ." Cikin dauriya ta ce min. "In sha Allah ko kare kika rike Ummu sai ya miki biyayya sai ya soki domin Allah yana son masu biyayya ni kuma me zance bayan wanda kika min, Ummu idan har yawun bakina zai zama albarka da alkhairi in sha Allah babu abin da zaki tab'a Allah bai albarka ce shi ba, Ummu Hadiyya in sha Allah ba zaki tab'a baya ba sai gaba, kiyiwa aurenki biyayya ki kuma rike shi Ibada Allah zai cike miki duk wani gurbin da zaki rasa Ummu Hadiyya in sha Allah ba zaki tab'a danasanin auren nan ba, ko zaki yi na lokaci ƙalilan ne. Aliyu ga amanar Ummu Hadiyya, sannan zan gaya maka gaskiya idan ka sake wani abu ya rabaka da ita ba zan mata dole ba zan tsaya mata gabanta da bayanta, kai kanka da danginka xaku yi alfahari da samunta a matsayin Mata da suruka. Sannan ban da duka" d'ago kai yayi da sauri yana kallon Mama. "Eh ban da duka na fada maka, ka dake ta wallahi sai na rama mata." Sai kuma ta sake yar dariya kafin ta shafa kaina tana faɗin. "Gudaliyya ba zata yi abin da za a dake ta ba sai dai a rashin sani. Ku je Allah ya muku albarka!" Ina kuka haka muka bar gidan cike da soyayyar mahaifiyata itama ina barin gidan sai share kwalla take, tunda muka dauki hanya Deen yake tsokanata. "Yau naga shagwab'e Hajiya Ummu ba naji kina da kanne ba, Yan mata ina kune kannenta?" Tab'e baki Uwani tayi tana faɗin. "Idan shagwab'e Aunty Baby ya motsa ina ga ko yaron da aka yaye ya salama mata, ina dalili ya sani jin kishinta!" Uwani bata da mutunci, amma tana da kirki. Garin Biu. Anan Babana yake kasancewar shi, dan kabilar Babura ne, lokacin da muka isa gidan wanda Uwani ta sani amma ni ban sani ba, domin ban tab'a zuwa ba. Babban gida ne me cike da ahali. Lokacin da muka iso kofar gidan da jama'a tun kafin motar ta tsaya sai ga Babana ya taso yana me murmushi, anan na fahimci yanayin jikina daga gare shine, don ma shekaru sun ja. Bakine amma dogo kasancewar ni kuma Yar guntuwa, siriri ne amma kana ganinshi ka ga wanda ya wadatu da rayuwa me kyau. "Ummu Hadiyya;" ya bude motar cike da farin ciki da zumudin ganina. "Yarinyar da ta aka tafi da ita tana tsumar goyo yau gata mijin da zata aura ya kawo min ita. " ya fada cikin farin ciki da raha. Fitowa Deen yayi shi da Aliyu suka gaida shi, sannan muka shiga cikin bayan mutane na ta mika mana gaisuwa, sannan wasu sun ji labarin ai wanda yar shi zata aura wakilin shugaban kasa ne, Babana shine Sarkin noman biyu. Domin tun daga zauren gidanmu zaka fahimci Babana attajiri ne, don alkama ce aka yi ta jerata ya kai buhu sama da arba'in har sai da ta tab'a silif din zauren, da muka shiga babban parlour shi, ridine a cikin buhu har sai da ta cinye rabin parlour. Cikin murmushi ya ce mana. "Parlour yayi kaɗan ko? Tow ya za ayi store ya cika da kayan abinci, shi yasa aka saka wasu nan." Sannan ya kalli Tafida da yake ta kallon hoton parlour, kafin ya saukar da idanunshi ƙasa. "Yarona sannunka da kokari." Kafin ya ce min. "Tashi muje cikin gidan ki gaida iyayenki!" Haka muka shiga cikin gidan, a hanya na ga ana ta wucewa da tire manya-manyan ana wucewa parlour Baba da shi, dakin Uwargidanshi muka nufa tana ganina ta mike. "Ikon Allah! Yau ga Ummuna Hadiyya a gidan nan!" Murmushi nayi nan aka yi ta shigowa ana min Barka da zuwa ashe ni yar gata ce, na tuna lokacin da na tab'a tambayar Mama Ubana ta mare ni. Haka suka cika min gabana da abinci, Uwani tana tab'awa ta gudu gidansu. Bayan nayi sallah aka ce naje parlour Baba na tafi, nan baba yayi min nasiha tare da su Aliyu, wai zasu tafi. Bawan Allah nan da kokari yake domin kajin gida guda biyar manyan zakaru sai zabbi guda biyar da katon toron agwagwa ya saka musu sai madaran saniya danye da galan din zuma. Ya saka aka hada musu. Har wurin mota muka rako su bayan sun gaida yan gidan tare da bin gidajen Yan uwan Baba ya gaishe su. Cikin gidan na koma. Baba ya ce na zo parlourn shi muka ta hira, yana bani labarin kanshi da hotonsa lokacin yana aikin gwamnati. Da kuma dalilin rabuwarsu da Mama. Na sha kuka domin Babana yana son Mama har gobe, sannan yadda yake nuna min haka daga kalamansa na fahimta, yayi aure aure amma Allah bai bashi haihuwa ba sai akan Mama ita kuma bata sonshi haka Allah ya ƙaddara aka haife ni. Sannan ya ce min. "Duk abinda nake nima dominki nake yi. Kaf wannan hatsain da kome naki ne. Ni ban da wata bukata na dai ajiye su ne ko wata rana zaki zo ko ce min kina son wani abu, sai na fahimci Hadiza ta toshe wannan hanyar da zaki nime abu a wurina. Alhamdulillahi da bata miki rikon uwar wani ba, ta rene ki a matsayin nata amma naji ba dad'i da kika ki karatun boko!" Sosa kaina nayi ina dariya. Sallah ya tashe ni na tafi cikin gidan, abin da na fahimta suma gidan hidimar bikina ake, da dare sai sha biyu ya rako ni dakin Mamawo, uwargidansa na kwanta. Tun asubar fari aka fara hidima, bayan nayi sallah asuba aka ce naje yana kirana, ina zuwa ya zuba min kaya ya ce min. "Sunce aurin aure karfe sha daya ne ina son mu tafi ne yanzu domin mahaifiyarki ta bukaci a kai ki wurinta!" Girgiza kai nayi nace mishi. "Na rayu a gabanta, yau daya ta bar ni ka raka ni ka ji!" Na fada ina kallonshi hawaye ya cika min idanuna. "Tow taya ni zabar kayan da zan saka to!" Wata farar gizne na nuna mishi wanda ya sha aikin hannu, ya ce min. "Shi kenan!" Haka na fito ina jin shi yana fadawa Mamawo. "Idan an daura auren zan gaya muku sai ku taso! Ina Ummu Hadiyya!" Na fito ina faɗin. "Na'am baba!" "Yawwa babu abun da kike bukata ko? Mamanku zata baki sako zamu tafi Allah ya miki albarka." Gyada kai nayi kaina a kasa. "Allah ya tsare!" "Amin Ya Allah " suka fita, ina komawa ciki wata yar Kanwar Baba suka zo da Mai lalle, ta zauna da min ja hannu da kafa, yarinyar me suna Raliya ta ce min. "Aunty Ummu an miki kitso kuwa?" Girgiza kai nayi. "Zan iya bude kan?" Ya tambaye ni, murmushi nayi na ce mata. "Aljanuna zasu tashi!" Dariya yayi tana faɗin. "Sai mu musu turaren barkono!" Zame hular kaina tayi tana faɗin. "Masha Allah!" Ba kome ya saka ta fadar haka ba, sai yawan gashin da Allah ya min wanda na fahimci zuriar Babana ne na gado, domin Babana gashi har wutar shi alamar genen dinsu yana da karfi. Itama Raliya tana da gashin. "Yanzu haka zamu kai ki babu gyaran gashi wannan amarya da kayan ban mamaki kike! Bari na kira Bintu me gyaran gashi ta gyara kan nan!" Ta fada tana zungure kaina!" Can sai ga matar tazo sai dai ba wuta. "Mamawo a saka mai a inji a gyara mata gashinta!" "Ki kira Sama'ila ya tashi injin akwai mai ai ko jiya da ita aka kwana!" Man wanke kai aka saka domin ta tambaye ni relax nace mata a'a don haka man gyaran gashi aka dauko na kayan auren Raliya sai mamaki nake ina son magana ta hanani. "Zan gayawa Baba Malam zai mai da min wasu balle ma idan auren yazo zai min wasu kayan, kema ai an bada kudin kayanki tun da aka fadi maganar aurenki idan zamu kai ki za a kawo kayan." Murmushi nayi domin na fahimci Babana yana son ganin farin cikin duk wnada yake tare da shi. Kafin karfe goma an wanke min an ja min gashin, sannan na gaban goshina aka gyara min su tass. --- A Maiduguri tunda Aliyu suka dawo yake wani niman hanyar rigima, Deen ya kyale shi yayi yadda yake so, a parlour Hajiya shuwa suka hadu shi da su Maryam da Rukayya,sai zuga shi suke akan kada ya sararawa Yarinyar. "Yar matsiyata kin ga wani gidan da muka je ban da noma babu abinda ake yi!" "Ayya My Son bana son abin da kike yi, tunda Alhaji ne ya zab'a maka ita haka zamu riketa hannu bibbiyu." "Haba Mama waye zai yi farin ciki wannan auren ga Sa'adiyya Yar dangi waye zai ji dadin auren Aliyu da yarinyar kabilu ne fa!" "Allah yasawa auren albarka!" "Ya kike son kawar da zancen Sa'adiyya idan aka kwana biyu dole ya auri wacce muke so, wallahi ba zamu tsaya muna kallon ki gama wahalar shi wata can ta more shi, ko Hajiya albarka abin da kika yiwa Aliyu Allah ne kaɗai zai biyaki!" Inji Rukayya. Haka suka gama zuga Aliyu ita Shuwa tana dai gefe amma ranta yayi dubu ya b'aci, tunda Deen ya shigo da kayan da aka basu Alhaji yake kara jadaddawa Deen ya taya shi rikon auren Aliyu ya saka idanun a kanshi. Biki me sunan biki aka yi a gidansu Aliyu, a ranar asabar al'ummar musulmi suka shaida auren Aliyu da Ummu. Wanda ya samu halartar manya mutane, yan siyasa, mai martaba shehun Borno, a wurin aurin auren Baba Bulama ya gabatar da Baban Hadiyya ga Abban Aliyu abin mamaki, sai gashi ashe abokai ne da suka yi barewa College, sai kuma lamarin ya koma na zumunci, aka yi ta tattaunawa har shi kanshi Shehun Borno ya san Baban Hadiyya Alhaji Kabir Biu. An yi daurin aure an tashi taron lafiya. - Tun karfe daya na rana, aka gama shirya kome tare da zabar mata hudu da zasu rako ni. Sai Raliya Uwani haka muka taso har da Mamawo da karfe shida muka iso sannan aka sake shirya tafiyar aka kawo ni gidansu Aliyu da yake Polo..... N500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 11 Zan iya cewa dukkaninmu a wannan duniyar muna da kalubalenmu, sannan kowani mutum da nashi ƙaddaran nawa shine ya hankad'oni duniyar Tafida, tun kafin mu iso an gyara inda zamu zauna da abincin da zamu ci babu abin da muka nime tunda muka iso domin wasu mata biyu daya me yawan fara'a ce, tana da matsakaicin jiki. Sai daya da babu yabo babu fallasa, suka yi ta hidima damu sannan a bangaren guda akwai wasu mata biyu da suke ta shiga da fita. Wanda suka juya harshe shuwa, don ma akwai masu ji musamman Kulsum da take auren shuwa, a take ta fara shan jinin jikinta tana kallona. "Aunty Baby wannan dangin Mijinki suna maraba dake kuwa?" Bance kome ba kaina a sunkuye. Haka suka fita babu abinda muka tab'a sai sallah da muka yi Rooman ce ta kira Kulsum tana tambayarta batun dinner da aka shirya ashe ita mijinta can ya wuce da ita. Mu kuma nan an bar mu a zube babu wanda ya kara mana maganar fita wani wurin. Shi da yan uwansa suke shirya abinsu lokacin da muka shigo lokacin suka fita wurin shagalinsu, inda suka maida wata wai me suna Sa'adiyya a matsayin Amarya. --- "Mahmoud ina Deen yake?" "Hmm ina zan sani na kira ya ki ɗauka!" Tsaki yayi yana zaune a cikin motar, gefenshi Sa'adiyya ce ta cab'a kwalliya. "Muje idan kace zakai ta jiran Deen ranka ne zai b'aci muje next wifydinmu!" Inji Mahmoud, haka suka fito a motar rike da hannun juna, har cikin hall din. Inda yake cike da jama'a. Anyi hidima sosai, duk da haka hankalinsa baya kwance ya kira Deen ya kai sau dari amma bai dauka ba, karshe kashe wayar yayi abinsa. Rooman tana ganin abin da yake faruwa ta ja mijinta suka bar wurin sai fada yake tayi, ita kan bata ce kome ba. "Fisabiilillahi a rasa wanda za a bawa Aunty Baby sai wannan dan iskan Yaron mara mutunci wanda kowa yasan.kaf garin nan bai da da'a kaf gidansu babu wanda yake da bakin mutane kamar Yaron nan, rashin auren Baby ba yana nufin rayuwarta zata kare a haka ba ne Allah ya gani naji zafin wannan auren yaron nan bai da kunya." Ita kan bata ce kome ba,.har suka iso gidansu Aliyu. "Bappa zan kwana Please!" "Idan aka samu matsala ki kira ni don Baby zan barki amma.da wani ne ba zan barki ba!" Ita kan godiya tayi mishi tare da shiga cikin gidan, da taimakon Uwani ta shiga cikin inda muke, tana faɗin."Ban tab'a ganin aure irin naki ba, wallahi taya ga Amarya anan wata ta zama ke a can? Idan baya sonki me yasa zai yarda a aura mishi ke wannan cin mutuncin da me yayi kama?" Turo kofar dakin aka yi daya matar me fara ce ta ce mata. "Ba ance babu dinner ba?" Zata yi magana nayi saurin dukar gefen cikinta. Ashe matar ta lura. Murmushi tayi ta ce mata. "Anyi dinner ne?" Kallona Rooman tayi tana me kallon matar ta girgiza kai tayi. "Ba zaki fada ba kenan?" "Tow me zance? Amarya anan ango a can da wata mace? Yayata ce fa?" Rufe bakinta nayi bayan na cire mayafin . "Ya isa haka!" Na rungumeta domin kuka zata yi. "Me yasa daga kawo ki sai tozarci?" Inji Kulsum. "Don Allah ki bar maganar nan, don Allah?" Nasan zan ga abin da yafi haka amma bana son tashin hankali. "Kuyi min alƙawarin Mama ba zata ji ba!" "Munyi!" Suka fada har da Raliya da Uwani. Don iya su suka tsaya min. "Don Allah Hajiya a bar maganar nan ba wani abu ba ne da zai zama babba a wannan lokacin. Don Allah!" Na fada ina kallonta. Murmushi tai sannan ta ce min. "Sunana Hajiya Kaltuma nice Amaryan Alhaji Muhammad Jadda, na ji dadi da Aliyu ya same ki a matsayin Matarshi, amma ban ji dadin abin da ya faru ba. Kiyi hakuri da abin da zai biyo baya amma nima uwa ce ina da Yaran da na rike ba xan so ayi.musu abin da aka miki ba, sai da safe." Haka ta fita tare da barin dakin, rufe kofar nayi na zauna a jikin kofar na hade kaina da gwiwata, "Aunty Baby!" D'ago musu hannu nayi nace musu. "Ku kwanta kawai!" Na cigaba da zama a wurin. Ban san me nake ji ba amma har karfe daya na dare lokacin da suka dawo ina zaune a banki kofar dakin. Can naji ana ta fada a cikin gidan bakiɗaya, tashi Kulsum tayi tana me kallona har lokacin ina zaune. "Baki kwanta ba ne?" "Bana jin barci ne!" "Meke faruwa?" "Ban sani ba!" Tsaki tayi ta kwanta domin muna jin hayaniyar amma da kusan shuwa ake yinsa. Kuma muryan na mace ce ba namiji ba. Ban daki na shiga nayi alola na fito na gabatar da sallah ina sallah naji ana buga kofar wurin karfe uku da wani abu. Haka na yi sallama na bude kofar. Gabana ne ya fadi nayi baya ina hadiye yawun bakina. "Fito munafika!" A hankali na ja kofar domin yayi maganar yadda iya ni zanji. Cafko hannuna yayi tare da fitar dani daga cikin gidan, wurin motar shi ya kai ni ya wurga ni cikin motar ya shiga. "Ke jakar ina ce? Ke wacce irin dakikiya ce dabba mara hankali? Matsuyaciya mara hankali har kin isa ki hada ni da mahaifina? Wallahi kika sake kuskuren shiga tsakanina da shi mutuncinki wawuya sakarya dabba kawai" tunda ya fara zagina kaina a sunkuye yake ban iya motsawa ba domin ji nake duniyar tana min yawo. "fita min a mota tinkiya kawai!" Wani irin zazzaɓi ne ya rufe ni, Dakyar na bude motar na fito jikina yana rawa, ga sanyin alfijir da ya fara ketowa wanda ya haɗa min wani irin zazzaɓi da tashin tsigar jikina. Dakyar na koma dakin, ban iya kuka ba domin na nime kukan na rasa. Har aka kira sallah asuba ina zaune a wurin Dakyar na tashi nayi na koma na kwanta bayan na tashi Kulsum. Tun da na kwanta ban farka ba, sai karfe biyu na rana. "Amma lafiya dai ko?" Hajiya Kaltuma ta tambaye ni bayan na farka. "Lafiya lau!" Na fada ina gyara zama. "An kai miki ruwa ki shiga kiyi wanka. " haka na tashi jikina babu kwari, na wuce nayi wanka da alolan azahar na fito nayi sallah aka kawo min kaya na sakanOllfaya. Ina zaune aka kawo min abinci,kaɗan naci domin bani da dandano a bakina. Haka na ci na bar sauran, yamma can aka fara hidimar biki sosai a gidan, yan gidan mu duk sun iso dama tun bayan daurin auren aka kawo gara da yasa èduxl k masu adawa da lamarin a jikinsu yayi sanyi, a da can shi yaso ya kama haya ne amma Abbanshi ya hana ya ce ya fara xama a gidan ya ga yanayin zamanmu, dangin Mama da yan uwa babana sun zo a kai ni cikin gidan wurin Abba, bawan Allah nan dattijon kwarai ne, domin ya amshe ni hannu bibiyu sannan ya hada ni da matanshi biyu hajiya Salamatu da Hajiya Kaltuma. Sannan aka fito dani aka yi budar kai. Anyi hidima sosai wnada yasa abin da Mama tayi ita da Mijinta da Mahaifina ya kashe karfin zukatar yan uwansa. Sannan aka dauke ni zuwa bangaren da zamu zauna wanda tunda aka yi jere babu wanda ya kara shiga sai yau da za a mai dani bangare na. Anyi hoto ko nace ni nayi nawa da yan uwana da abokan arziki, shi yayi na shi tare da yan uwanshi, da kuma yarinyar da Rooman take nuna min ita a matsayin amarya da aka yi dinner da ita. Ban yi mamaki ba ai kowa yasan cewa ni ba irin kalarshi ba ce, yadda take narkewa a jikinshi yasa na kara jin tausayin me yasa na kawo kaina lahira, a gefe guda wasu yan mata da bansan su ba, suka zo har inda nake daya ta koma bayana tana faɗin. "Na baki shawara? Tun wuri ki bi yan uwanki gida, domin nan gidan sai ki roki mutuwa ma!" Idanuna ne ya cika da kwalla, kaina a kasa har suka gama iskancinsu ban ce kome ba, kiran sallah yasa aka fara watsewa aka wuce da ni dakina wanda kayan da Mama ta zuba na san Allah kaɗai zai biya ta, haka na sake wanka na sauya kayana. Sannan a hankali yan uwana da kannena suka yi ta watsewa. Ya rage ni daya kamar rai, tun ina saka ran jin motsin wani har na daina na mike tare da rufe kofar dakin na kwanta, duk tsayin ranar yau bana jin nayi shi cikin farin ciki da walwala ba tare da abin da Tafida yayi min bai fado min ba. Haka na zauna a cikin dakin har dare yayi sosai. Kafin nayi alola na kwanta, sama-sama nayi ta jin dariya da karfi tare da yan hayaniya. Ciwon da kaina yake yasa na tashi a hankali na nufi kofar dakin, bude kofar nayi, a hankali na maida tare da rufewa, na juya na koma gadon na kwanta. Ina jin kamar nayi kuka ne ko nayi meye oho, Tafida ne da yarinyar sai Mahmoud da yake ta kallon tv, asalin abin da ake a tv wani american film ne mara kyan gani. "Ya Aliyu kaga gayen abin da zai yi gaskiya nayi missing wannan Film din!" "Kai tashi ka tafi gida, kema tashi na raka ki." Ya fada yana kashe tv din. "Kai fa dan iska ne, ya muna kallo zaka kashe ma ko zaka shiga wurin wancan abin ne?" Inji Mahmoud. "Ove my death body, ku tashi ku tafi kada mai gidan nan ya san kuna nan ku sake jangwalo min wani magana!" Mikewa suka yi Sa'adiyya ta ce mishi. "Kayi min alƙawarin ni daya ce naka, kuma kace zaka aure ni kada ka ci amanata. Domin na rena wancan yarinyar." Tsaki yayi yana nuna mata hanya, duk suka fita, sai da suka fita sho Tafida ya raka Sa'adiyya Mahmoud ya bishi da sauri yana faɗin. "Man na manta wayata fa!" "Ok jeka nima zan lallaba Saadih kafin na shiga gidan!" Ganin yadda Tafida ya bashi damar shiga cikin gidansa babu wani abu ya bashi damar nufar gidan. Yana zuwa kofar Ummu ya nufa dama bai wani manta kome ba, buga kofar yayi. Jin yadda ake buga kofar yasa na ce. "Waye?" "Zo ki karba!" Yadda akayi maganar ban kawo ba Tafida ba ne, yasa na bude kofar. Turo kai zai yi na ja kofar da karfi. "Lafiya?" Murmushi yayi yana faɗin. "Har yanzu ba zaki hakura da zama da shi ba? Kin san ina yake? Yana tare da yarinyar da yake fatar ya aura suna can suna." Ya tsaya yana kare min kallo daya daga kasa har sama, rufe kofar nayi da karfi tare da rintsa idanuna. "Ummu Hadiyya ina me baki shawara idan ma ba zaki rabu da Aliyu ba, me zai hana mu ji dadinmu." Komawa tsakiyar gadona nayi na dunkule wuri guda na fashe da kuka, wacce irin masifa ce Wannan. Haka ya gaji ya tafi ban ma san tafiyarshi ba. A hankali ya shigo zai wuce cikin gidan, turus yayi yana kallon Tafida da Sa'adiyya wacce take wani narkewa tana kuka. "Ke wuce kafin na karya kafarki!" Inji Umar da yazo gidan sakamakon Attack din Abba da ya tashi aka kira shi domin maganin asthmar shi ya ƙare, da sauri ta wuce cikin gidansu. "Wai yaushe xaka yi hankali ne? Aliyu me kake son zama ne? Fisabiilillahi a daren farko ma sai ka cutar da kanka? Tow wallahi bari na gaya maka idan Abba ya samu labarin abin da kake yi ko wallahi babu ruwa mutumin banza kawai." Ko cikanka bai ce mishi ba ya wuce abin sa. Yana shiga ya kalli kofar dakin Ummu ya kai wa kofar naushi, ya wuce. Jin irin bugun da aka yiwa kofar yasa ni tsayar da kukan da nake yi, jin an wuce na sauke ajiyar zuciya. Kwana yayi yana shirin yadda zai yi Ummu domin kuwa ta shiga rayuwarshi. Washi gari. Tunda nayi sallah asuba na kwanta ban kuma farkawa ba, sai karfe daya na tashi nayi alola da wanka na fito na shirya cikin wata material, ina daura dan kwali naji muryansu Kulsum, da sauri na gama na yaga mayafi na fito. "Aunty Baby irin wannan barci ko!" Ware idanu nayi Taima da tazo tare dasu, ta saka dariya tana faɗin. "Bari muga ko tafiyarta ya sauya ko tana dingishi!" "Bana son iskanci! Wannan ai rashin kunya ce" na fada ina dauke kaina. Kayan hidimar girki ne da aka zuba su a cikin cantaine daban daban, suka shiga kitchen suna jera min. Kullar abinci muka gani, Kulsum ta buɗe doya da kwai ce tayi sanyi sai kunun alkama da farfesun kaji. "Mun zo miki da abinci fa! Ga wani kuma!" Ya nuna kullar da na bude. "Ina kewar abincin Mamana!" Na fita parlour na ja na fara ci a hankali, ina lumshe idanuna. Su kuma suka ci wanda suka samu, muna cikin gyara gidan aka sake shigo da abinci, muka karba da fara'a tare da godiya, mun wani likis, sannan suka tafi, can wurin La'asar daga cikin gidansu aka fara shigowa ana gaisawa, duk da nasan an kawo musu nasu kayan garan haka na shiga cikin na dibo musu tsatsafa, nakiya, dubulan tawaita da cin-cin da gereba, da duk wani kayan da aka kawo min na shake musu tire da shi, na koma na dauko ruwa da lemon gora na ajiye musu. "Wai Sannu da kokari!" Suka yi ta fada, can da suka gama zamansu suka mike tare da tambayata. "Babu leda ne mu juye" "akwai "kitchen na koma na dauko musu ledan na kawo musu, sannan na juye musu. Tun ranar da aka yi wuni ban kuma saka shi a idanun ba, haka na cika kwanaki uku babu labarinsa amma cikin gidan ana kawo min abinci da kome, na gaji da zaman haka yasa da safe Nabila yar rikon Hajiya Kaltuma da ta kawo min abin karyawa. "Don Allah ko zan bi ki na gaida mutanen gidan da Abba?" Murmushi tayi tana faɗin. "Dama Hajiya ta fada tace zaki shigo gaida Abba." Ta fada min tana faɗin. "Muje!" "Tow bari na saka hijab ba!" Na shiga cikin dakin na saka hijab dina sabo ne dal, a cikin kayan da Babana ya turo min. Tana gaba ina baya tun daga tsakar gidan nake gaida masu aikin gidan, suna amsawa da Mamaki, wanda ni dai ban san dalilin haka ba, har muka isa parlour Hajiya Kaltuma muka gaisa."Nayi tsammanin zamu shigo tare da Aliyu ne?" Sai aka bar ni da zare idanu, ina yake don ban san me zance ba. "Tashi muje parlour Abbanku!" "Tow!" Na amsa mata, sannan na mike na bi bayanta har zuwa parlourn shi. Yara mazan na zaune sun zage shi har da Aliyun, "Barka da hutawa Abba!" "Yawwa Ummu Hadiyya! Barka dai da fatan kin tashi lafiya!" "Alhamdulillahi!" "Ki mishi ya jiki bai ji dadi ba!" Inji Hajiya Kaltuma Ta fada min. "Ayya sannu ya jikin, Ubangiji ya baka lafiya yasa zakkar jiki ne." "Amin Ya Allah, ya bakunta?" Ya tambaye ni yana kallon Aliyu da ya hade rai. "Alhamdulillah!" "An jima za a kawo miki cefane ba sai kin jira an girki daga nan ba, ki fada idan an kawo miki ki ci! Domin yar Sarkin noman ba zata zauna jiran matan gidan ba, Mahaifinki mutumin kirki ne, shi yasa kika san hukunci da idanu. Babanki ya rike house captain makaranta, ya kula da mu yan jahar Borno, duk wani dalibi idan akace daga Maiduguri yake tow ya dauke mu kamar danginsa. Idan kika dauki halin Alhaji Kabir Biu tow nayi imani da Allah babu wanda ya isa cimmaki amma sai kin koyo jarumta irin nashi." Gyada kai nake kawai, babu abin dadi kamar ka ji ana gaya maka waye mahaifinka. Mikewa Aliyu yayi ya fita, "kana karawa Borno masu, tashi na kai ki wurin Inna da Salamatu!" Haka na mike na bita har parlour sayar mata ba yabo ba fallasa muka gaisa, sannan na fito muka karasa parlour inda, matar tana da kirki tunda ma shiga take ajiye min abinci da wanda na sani da wanda ban sani ba, haka da zan dawo na samu an hade min su cas na dawo dasu. Gabana ne ya fadi ganinshi zaune a parlourna ya daura daya akan ɗaya, dauke kai nayi na nufi kitchen na ajiye abin jikina yana bani kamar ya biyo ni ban gama tunanin haka ba naji ya shake min wuya da hijab dina. "Idan na kara ganin wannan mummunar fuskar naki a waje da sunan kin je gaida Abba sai na lahanta miki shi yadda ba zaki more shi da dadi ba! Kina jina!" Ya daka min tsawa. "Eh na ji!" Na fada ina kokuwa da numfashi. "Wawuya kawai!" Ya juya yana me fita, zubewa nayi a wurin ina rike wuyana, wani irin kuka ya zo min wanda ban kawo zan iya shi a yau ba, kuka nake. Sai da na gaji na mike zuwa dakina. Ina zaune a wurin naji ana ta magana sama-sama, fitowa nayi ina kallon ikon Allah. Kayan garana ake fita da shi buhun-hunan shinkafa da duk abinda aka kawo min ina kallonshi yana fitar da shi. "Kina da abinda zaki ce ne?" Juyawa nayi daki da sauri. Sai bayan fitarsu na fito zuwa kitchen din na samu buhun shinkafa daya kwalin taliya biyu sai jakan simo da sauran tarkace. Hawaye ne ya zubo min. Ina cikin gyara kitchen din aka kawo kayan cefene, ma zauna na fara gyarawa zan saka a firji sai gashi tare da Yarinyar nan, "Ya Tafida kayan abincin nan ina ga sai mun kai shekara bamu nemi abinci ba, gaskiya kana ji da Kuma sosai." "Hmm! Shiga ki raba kayan ki kai mata rabi." Haka ta shigo tana me bangaje ni. "Ya Tafida kace ta matsa min. Dama ina yar talle da samun irin wannan kayan!" Hadiye yawu nayi na koma gefe sai da ta dibi kome sama da rabi sannan ta fita da shi tana wani shegen dariya. Sauran na dauka na saka a firji, na fito da kayan aiki na fara kokarin daukar girki. "Su fooder za a fara dafa su kaji babu a gidan Uwalle da Uballe!" Inji Yarinyar kenan, sai na rasa bakin magana, ban kulata ba ta shigo kitchen din. "nan gidana ne, Yayun tafida da shi Tafida ni suke burin na aure shi!" "Tow ni ina ruwana! Wannan matsalar naku ne ba nawa ba." Kada ku dad'a kada ku kara, yarinyar nan ta fita tana ihu tare da fashewa da kuka. Ta nufi bangarensu, ba ita ba hatta Tafida da Uwarta suka tawo. Tana kuka kamar ranta zai fita, "Me kika mata?" "Me na mata kamar ya?" Na tambayi Mahaifiyarta da ta min tambayar. "Nace me kika mata?" Ta daka min tsawa. "Tow dama nayi mata wani abu ne? Ni ban mata kome ba gata nan!" "Ke Sa'adiyya me ta miki?" "Marina tayi tare da cewa har abada ni da Tafida sai dai naga nesa!" "Marinta kika yi?" Matar ta shigo zata rufe ni da duka, Hajiya Kaltuma da bamu san da zuwanta ba tace. "Kul Hindatu shuwa, kika sake kika tab'a musu yar mutane sai kin gane Alhaji Muhammad Jadda baya wasa da duk abinda yake na shi." "Amma Hajiya baki ga rashin kunya tayi ba, taya don iskanci zata mari Sa'adiyya har tana cewa wai ba zan tab'a auren sa'adi ba? Na bari ne Hajiya ta gama nata nayi mata nawa wallahi sai kin gane baki da hankali, wawuya wacce iyayenta suka gaji da ita." Yadda yake cin zarafina ya sani zamewa kasa. "Tow wallahi xan gayawa Alhaji abin da kake aikatawa hauka ne abin har ka isa ka zagi iyayen kai ba a gaji da mugun halinka ba, mara kunya wanda bai san darajar iyayenshi ba" yasan Hajiya Kaltuma bata da dad'i itama, "kuma kema Shuwa zan gayawa Alhaji ya muku iyaka da gidan tafida ." Haka tayi musu tas suka fita ta kuwa gayawa Abba, ranshi ya b'aci ya kira Abban tsakiya mijin Hajiya Shuwa ya buga mishi kashdi wanda ya sa shi dole ya gargadeta. Ashe al'amarin ya zaga ko ina na yan gidan, ranar da na cika sati Aunty Rukayya tazo da Yaranta. Ina kitchen ina wanke kayan abincin da Tafida da Sa'adiyya suka b'ata domin bayan gama fadar Abba, tafida yazo har dakina, ya murde min hannuna sai da yayi ƙara, ya ce min. "Ina son na illata ki ne? Tow wallahi ki nisanci Abbana idan kika kara barin yayi min magana akanki, zan baki abinda ba zaki iya amsa ba!" Ya tunkude ni na fadi goshina ya bugu da karfen gas dina, ai kuwa ya fashe. Tun ranar da naga haka na rufawa kaina asiri, ina dauke kai akan me suke yi, idan na fito na same su a parlour rufawa kaina asiri nake na shige dakin naki fitowa ai ba hauka nake da zan yarda ya fara saka hannunshi a jikina ba, ta ko wani hanya niman yadda zai ci zarafina Sa'adiyya take. Shi kuma biye mata yake kamar bai da lissafi. Na gama wanke kayan kenan naji Muryan yara, na fito kawai yaran nan suka fasa ihu tare da fita da gudu, ban san me ya faru ba amma dai zan ce abin ya bani mamaki, can sai gasu Aunty Rukayya da Tafida da Sa'adiyya,dauke da wani yaro da ya fadi yana kuka Yaran suka koma bayan Tafida. "Ke mike musu?" Kasa magana nayi ina me jin wani iri abu a raina. "Me tayi muku?" "Kama tayi mana da zombies shine muka gudu!" Wani irin dariya suka saka tare da nuna ni, Sa'adiyya har da yin alamar yadda zombies suke tafiya tana dariya. "Eh dama tayi kama da zombies don ma she always look ugliest!" Kaina a sunkuye hawaye na zuba min kamar an bude pampo...... #500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 12 Duk da naki karatun boko, hakan ba yana nufin ban san me wasu kalmomin turanci ba ne, hada na d'ago kai ina kallonsu. A hankali na juya zuwa dakina, na rufe kofar na cigaba da kuka. Suka cigaba da dariyarsu, can ina zaune naji yana buga kofar dakin tashi nayi na bude kofar ina kallonshi. "Uban waye ya baki izinin rufe min store din gidana?" Hadiye yawu nayi na rab'a gefenshi ya firgo ni. "Ba magana nake miki ba?" "Zan je na bude ne!" "Good!" Haka na bude ya shiga ya kwalawa Aunty Rukayya kira. "Aunty Ruky!" Shigowa tayi ta wuce ni zan fita Yaranta suka shigo suna daya Yaron yana ganin glass cup din da na wanke kawai ya dauka yana fadawa daya Yaron. "Ayman dauka mu sha ruwa a cikinsu;" "A'a sai dai mu fasa muji ko na gaske nan!" Kafin na ankara sun maka kofinanan da kasa shi kake tuss, suka kuwa kwashe da dariya suna faɗin. "La da gaske ne fa! Dauko sauran!" Nayi maza na tare su. "A'a kada ku kara domin zan muku bulala!" Na fada ina d'aga su. Ai kuwa Yaran suka saka ihu. Ban kula su ba na saka kayana a sama. "Wai don Allah me suka miki ne?" Inji Aunty Rukayya tana me cika bakinta da kayan garana, ashe diba mata yake yi har da kayan abinci. "Kayana suke fasa min, taya zan kyale su." "Lallai ma har kin samu bakin magana, kayan da waye bai san cewa Abba ne." "Wannan kayan hatta tsinke Uwata ce ta saya min, don haka ba xan bari a lalata min su ba." "Tafida kazo Matarka tana min rashin kunya" fitowa yayi ya mika mata wani bokiti cike da kayan duk abinda suka diba. "Me ya faru?" Nan ta labarta mishi abin da ya faru. Ganin ban kula su ba ina gyara inda kwalbar ya fashe, yasa shi kamo jelar gashina bakiɗaya ya d'ago ni. "Kika ce kayan Uwarki ce ya saya miki? Ko an gaya miki ban san Abba ya ce kada a kawo ki da kome ba ne." Irin kallon da nake mishi yasan ba kallon tsoro ba ne kallon kiyayya ce zalla. "Dani da kai ita, duk zamu hadu a fadar Allah kuma fadar karshe, Allah zai bin min hakkina kamar yadda zai fara hisabi daga kan dabbobi zuwa kan mutane!" Kamar wanda na gaya mishi wani magana me zafi ya sake Ni yana kallona, na gyara zaman hular kaina. Janyo glass cups din yayi ya fasa su bakiɗaya. "Kina da abin da zaki iya ?" Girgiza kai nayi, "wata rana tarihi zai maimaita kansa in sha Allah!" Na fada tare da nufar kofar dakina, ban san ya aka yi ba ni dai bude idanuna nayi na ganni a parlour Abba, bayana yana min wani azabar zafi. "Me ya faru?" "Sannu Ummu Hadiyya,.sannu Yaron nan Allah ya baka lafiya." Kokarin tashi nayi amma na kasa haka na koma na kwanta. Abin da na iya tunawa shine kamar an buga ni da kofar dakin da zan shiga daga nan ban san kome ba. "Kin tashi!" Abba da ya fito dakinsa ya fada min. " me ya faru?" Na tambaye shi. "Kaltuma d'aga idan zata iya zama!" Dakyar na tashi zaune dakin ya cika bakiɗaya har da Hajiya Salamatu. "Nura kai da Saleh ina son ku zama shaida Hindu ta fitar min da yarta a gidan. Sannan idan na kuma ganinta a cikin gidan nan kotu ce zata raba ni da ita, na biyu Tafida ba xan maka baki ba amma in sha Allah, sai ka zo nan kana rokon nayi maka alfarma a karo na biyu ina dauke kai. Na uku daga yau kada na kara ganin kafar Rukayya da Yaranta bakiɗaya a cikin gidan nan sai idan ni ne na bukaci haka, wannan shine hukuncina wanda haka bai mishi ba yana da damar kai ni kotu!" Sannan ya juya yana kallon Nabila ya ce mata. "Allah ya miki albarka da kika ga kome a idanunki, Ubangiji ya saka ki a cikin amintattun bayinsa." "Amin Alhaji!" Inji Hajiya Kaltuma, sannan aka watse. Rike ni Nabila tayi na koma bangarena bayan Abba ya bani hakuri, a hanya take gaya min abin da ya faru. "Na shigo na kawo miki sakon Inna kawai na ga Sa'adiyya ta tokare ki ta baya sai da kika bugu da kofarki, ga kuma Aunty Rukayya da kayan abinci shine na koma na kira Hajiyarmu tazo ta gani ta kira Abba, sannu." "Yawwa!" Tun da na koma na gyara gidan na kwanta ji nake kamar na bar gidan domin na gaji a yan kwanakin nan da nayi, ba karamin kullata na Tafida yayi ba. Satina biyu layya ya karato, ban yi wani zumudi ba, ina dai zaune ne amma bana jin dadin rayuwata. Idan na shiga cikin gidan hatta yan aikin gidan basu kula ni ko na gaishe su basu amsawa, sannan ban da Hajiya Kaltuma da Inna babu me shiga harkata. Ana gobe arfa Alhaji ya kirani na je na gaida shi domin tun da na fara girki na ware wani kula me kyan gaske ina kai mishi abinci, ina shiga na samu abincin rana da na kai yake ci. Hajiya Salamatu tana gefenshi. Cikin nutsuwa na gaida ita. Ta amsa sama-sama. "Barka da hutawa Abba!" "Yawwa Ummu Hadiyya! Ga wancan kayan ki dauka na sallah ne, jiya na bawa Salamatu ta sayo miki!" A hankali na kalleta na ce mata. "Allah ya saka da alkhairi Mama, Ubangiji ya duba bayanki da gabanki na gode sosai." A yau na ga murmushinta, tana faɗin. "Amin Ya Allah!" Na dauki kayan ina jin wani irin dad'i na d'ago kai idanuna cike da kwalla na ce mishi. "Ni ne da godiya Ummu ni ya dace nayi godiya ni zan miki godiya!" "Alhaji na fara jin kishin yarinyar nan ka ware ta a cikin Yaran gidan nan!" Kallonta yayi kafin ya ce mata.."ke kanki kin san Aliyu yana niman mace da zata iya hakuri da shi ko? Ke kanki kin san Sharif da Alfah sun fi Aliyu saukin kai ko? Ke kanki kin so da Sharif ne ya samu Ummu saboda nagartatta don haka ki bar ni nayi mata godiya." Tabbas taso da Sharif ne ya samu Ummu domin haka kawai taji yarinyar ta mata amma kasancewar basu shiri da Tafida ta gargadi Yaranta babu ruwansu da Ummu kada taji wani abu ya fito baya. Amma yau yadda ta ga farin ciki a idanun Yarinyar yasa take jin yarinyar tayi mata, amma ba zata shiga hidimarta ba. "Na gode sosai!" Na mike na bar musu wurin suka yi ta hira sama-sama. Wurin Hajiya Kaltuma na shiga na nuna mata, ta tayani murna sannan na kaiwa Inna itama murna ta tayani, kafin na wuce bangarenmu takalman mutane na gani da sallama na shiga Deen ne sai Mahmoud da Oga da kanshi. Gabana ne ya fadi na gaisu sannan na wuce zuwa dakina. Ina cikin dakin na ji yana faɗin. "Ke!!!" "Tafida meye haka ina laifin Ummu?" "Uwar wa ta haifa!" "Mutumtawa na da dad'i!" "Kai dai ka cika tsugudidi!" Fitowa nayi ina kallonshi. "Babu abinci ne?" "Akwai!" Na fada ina nufar kitchen din. "Amma me yasa ka mai da gidanka kamar wani Barack?" "Bana son iyayi da ka gudu baka zo bikina ba, ban maka magana ba na maka uzuri ne yanzu kayi min maganar banza zamu doku ne!" Abincin na zuba na shiga kawo musu dama tuwo ne miyar egusi, na kawo ina jera musu har na gama zan tafi ya ce min. "Wai dama kin dafa ba zaki bani bane?" "Kayi hakuri!" "Mtseew!" Dukar kafadarshi Deen yai yana faɗin. "Ka kula ita rayuwa ba a mata haka!" Haka na barsu suka cinye abincin shi bai ci ba, ganin yadda suke santi ya shi mikewa ya fita can gidan Hajiya shuwa ya amso abinci a parlour ya ga Sa'adiyya ware idanu yayi yana faɗin. "Saadi yaushe kika zo?" Tura baki tayi tana faɗin. "Tunda dama na hanaka sakewa da matarka shi yasa har nayi laifi na zata nayi abin da zai faranta maka ne ashe ban sani ba nice nake ta hauka." "Ya isa ki yi hakuri idan na dawo zamu yi magana! Abincina na zo dauka!" Cikin kwarkwasa ta dauko mishi abincin ya dauka ya fita da shi. Har zuwa parlourn. "Tafida kira min Ummu wannan abincin wallahi ta cancanci na biya shi." "Ke!!" Ya kara kwala min kira, haka na fito ina faɗin. "Gani nan!" "Ga dan iskan da yake kiranki!" Ya nuna Deen shi kuma yana cin jollop din shinkafa, "Hajiya Ummu ga shi ba yawwa!" "A'a na gode!" Na ki amsa tsaki yayi yana faɗin. "Kasan yaran matsiyata haka suke." "In sha Allah ba zan kuma zuwa gidanka ba idan zaka cigaba da cin mutuncinta." "Tow Allah ya baka hakuri." Haka suka ajiye min kudin har da Mahmoud na dauka na wuce ina jin b'acin rai. Haka suka yi hira har lokacin sallah yayi suka fita na shiga kitchen din na yi jallop din cus-cus sai sauce din kayan ciki. Na ajiye a kitchen din. Ina sallah la'asar naji hayaniyarsu ban fito ba sai da naji ya fara kwala min kira da ke, na fito ina kallonshi. "Bar kallona da idanun kamar na Mayu Mahmud ne yake jin yunwa akwai abincin?" Hadiye yawu nayi ina gyada kai, na shiga kitchen din na dauko katon kula na ajiye musu. "Ke wai haka zasu na cin abinci ko dan irin ruwan sanyi babu!" "Kayi hakuri!" Na fada na rasa ne xan musu kawai sai na duba firji din na ga babu kome, na fito waje tare da cewa. "Babu kayan haɗin zobo ne shi yasa ban yi ba!" "Ni zan nimo miki!" Kai mishi duka Deen yayi ya mike. "Hajiya Ummu bani list na sayo!" Haka na shiga daki na rubuta mishi, na kawo tsaki Tafida yayi yana cigaba da kallonshi. Fita yayi bayan minti talatin sai gashi dauke da kaya niki-niki, na ware fruit din na markadesu na tacce, sannan na dauki sugar da na narka shi yayi ja kaɗan na zuba, kafin na rufe shi ina me kawo kankara na zuba a kai. Na dauka na kai parlourn na ajiye musu. Ashe wai kallon kwallon suke tsakanin Real Madrid da Barcelona! Ni dai na barsu nan na dawo dakina. Kafin karfe bakwai na dare sun cinye abincin. Haka suka bar gidan, da safe da zai tafi masallaci ya buga min kofa "ke jiranki nake!" Fitowa nayi. "Yau anan zasu sha ruwa saura ki musu kwauron abinci!" "In sha Allah haka ba zai faru ba!" Tsaki yayi ya fita. Ina idar da sallah na fito na wanke shinkafar tuwo na barta a kwando, na gyara gidan nayi wanka na shiga daki, karfe daya na rana na ji anata hira fitowa nayi na ga Aunty Maryam ce, yaronta nata buga remote din tv a kasa yadda basu ce mishi bari ba, nima ban ce mishi bari ba. Na gaishe ta amma taki amsawa na wuce kitchen na fara aiki, Yaron ya shigo yana kallona ya kai hannunshi tare da ɗaukar wuka. "Kai Amir ajiye wukar nan!" Ya faɗa.."yau muguntar ce ta motsa ba zaki ce mishi ya ajiye kada ya jima kanshi ciwo ba!" Amsar wukar nayi na ajiye na cigaba da aiki, kullun tuwon masata na juye a bokiti na fito da ita tare da saka hijab. Na shiga cikin gidan. "Hajiya Barka da ibada Nabila bata nan ko?" "Kina son wani abu ne!" "Dama masa zan yi!" "Harira!" Me wanke-wanken gidan.."Na'am Hajiya !" "Karbi bokitin ki kaiwa Ummu markade!" Wani irin kallon banza tayi min kafin ta ce mata. "Hajiya ina aiki!" "Kina aiki?" "Eh!" "Yayi kyau daga aikin ki wuce gidan Ubanki!" "A'a Hajiya ba ayi haka ba, inji Tabawa. "ke amsa kuyi hakuri Hajiya, Ummu kema ki yi hakuri Maza amsa ki tafi!" Ko furucin da Hajiya Kaltuma tayi amfani da shi yasa bakiɗaya suka razana, fitowa Hajiya Salamatu tayi tana tambayar Hajiya Kaltuma, ta gaya mata ai kuwa ta hade rai tana faɗin. "Ina sane da iskancinsu ko kayan abincin da take kawowa Alhaji abinci ware shi ake ba a wanke ake mai da mata yan iskan Yara zaku yi akan abincin ku." Ni dai ban ce kome ba, haka yarinyar ta dawo jikinta yayi sanyi, ta ce min. "don Allah kiyi hakuri, wallahi Hajiya Shuwa ce tace idan muka kula ki zata saka a kore mu,." "Ba kome." na wuce abina, haka na hada kullun zafin garin yasa kafin wani lokaci har ya tashi, na daura farfesu sai shinkafa da miya, haka nayi masar tass na gama aikin sannan na yi duk abinda ya dace na koma dakina nayi wanka, ina gama wanka ana kawo kayan cefenrm abincin sallah, haka na fito ana shan ruwa na jera musu kayan abincin sannan na koma daki nayi sallah. Ina idarwa Nabila tana shigowa ta kawo min abinci na hada mata abincin cikin gida aka tafi da shi nace mata. "don Allah ki zo na baki aiki mana." "Tow!" Haka ta kai ta dawo na bata aiki kayan yin cake ne da donut. Tana kawo min na bata masar Harira ta kai mata, wato tun da nayi sallah isha na shiga kitchen ban fito ba sai karfe daya da rabi,don har sun watse wurin takwas Deen ya tafi sha daya Mahmoud ya tafi ni daya kamar mayya nayi aikin nan, har da miyar abincin sallah duk rage aikin. Ina fitowa na same su a parlour shi da sa'adi ban kalli inda suke ba na wuce. Daki ashe ina shiga daki ta wuce kitchen din ta dibi Cake da donut. Kamar an aiko ni na fito na samu zata fita na saka hannu na amshi abuna babu kunya ta wuce ta bar gidan don dama shi ya tashi daga parlour shine zata shiga ta kwashe min wahalata. Haka yasa da na maida na rufe kitchen din na wuce daki nayi wanka na kwanta. Asuban fari na tashi da aiki ina da babban kurfo na fito da shi na daura tuwon shinkafa, haka na cigaba da aiki har gari yayi haske aka fara tafiya Idi. Ban je ba domin aikina amma naji haushi ina tuka tuwo ta shigo sanye da Hijab fari sol, tana gyara zaman madubinta. Fitowa yayi sanye da farar shadda tass, sau daya na kalle su na cigaba da aikina, haka suka fita. Kafin su dawo na gama tuwon na kwashe na dauki na cikin gidan na kai na hada da kayan abincin da nayi da zobo, ni ba waya ba domin ina ji a lokacin bikin aka sace min nawa, ina zaune ina kallon abincinsu Mama. Wurin karfe sha daya sai ga Mudan ban san lokacin da nayi ta murna ba. "Kai Aunty Baby sai kace mun shekara bamu hadu ba." "Kira min Mamana!" Kiranta yayi muka sha waya har da kukana. "Kasan Allah kafin gwamnan a wurina sannan bari na duba daki zan baka kudi ka sayo min waya kayi welcome back din layina. Sai ka kawo min jibi." Haka na hada mishi abinci ya ci na bashi dubu sha hudu. "Kai Aunty Baby ana rike waya irin su Samsung kina kawo kudin me torching." Shigowa suka yi da abokanshi. "Sannunku!" Ko inda Mudan yake bai kalla ba, "Ni dai ka saya min koma meye." "Gaskiya Aunty Baby ba zan saya miki waya me torching ba." Ya fada yana mikewa, a lokacin muke gaisawa dasu Mahmoud, na koma kitchen na hada mishi abincin Mama. " Ni dai don Allah ka sayo min sannan akwai katin dan kasana a wurin Mama kayi welcome back da shi!" Sai da ya tafi na koma cikin, na fara kawo musu abincin ina jerewa sannan da na gama na koma dakina na barsu, dake ina gamawa nayi wanka na saka atamfa me ratsin fari, "Aunty Ummu kizo Abba yana kiranki!" Farin mayafi yafa fito, idanun Mahmoud yana kaina. "Amaryan mu na ga kwalliyar nan, kuma na biya da sahalewar Tafida!" Tsaki tafida yayi yana faɗin . "Banza ka daina haɗa ni da yarinyar nan!" Yana gefe bai ci abincin ba, kallon Mahmoud Deen yayi, yaga yadda yake murna. Sai yaji ya rena Tafida sam bai san ciwon kanshi ba. Ina shiga cikin gidan kowa na tsaye Abba ya cewa Nabila. "Dauko mata kujera!" "A"a Abba nan ma yayi!" "Zauna dai!" Haka na zauna ina kallon namar. "Wancan na daron naki ne, ke daya da danginki. Babban daron kenan. Wannan kuma na tafida ne duk yadda yaso yayi da shi. Sai akwia kai da fata za a gyara a kawo miki. Salamatu bata goran sallah ta da kuma na tukwaicin abincin sallah." "Ai kuwa Alhaji yarinyar nan bata jin bata nime wani a tayata aiki ba kawai sai ganin tuwo muka yi." Inji Hajiya Kaltuma tana fada. "Mace ce ai, kuma ta nuna daga inda ta fito ba a koya mata son jikin irin nasu Farida ba!" Inji Hajiya Salamatu."Allah yasaka da alkhairi na gode Abba, na gode Mama na gode Umma. Sannunku da aiki sannunku da kokari Allah ya jibanci alamarinku!" "Amin Ya Allah!" Duk suka fada , na mike aka biyo ni da kayan naman nan, na nuna inda za a ajiye min na koma daki na cire kayana na shiga aiki da chopping butch. Ina cikin aikin ya shigo kamar zai yi kwallo da kayan shi da sa'adi ce, "saka hannu ki dauka muje." Ta tafasa bance musu ba balle ta kone, suka dauki namarshi suka tafida da shi. "Don Allah ayi ya yi kyau domin zan tafi da shi ne wa abokan aikina!" Sai anan na fahimci. Ashe zai koma ne, ni dai nawa na raba kashi uku na soya nayi dambu, sauran naman na saka a firji kwana biyu aka dauka ana aikin layya ranar na biyu Mudan yazo min da na gida, na zuba mishi nashi da na su Mama har da danyen nama, ya kai musu na bada nasu kulsum. Su Deen sun shiga na zuba musu nama da cakes, tunda Deen yaci tafida yazo musu da wanda aka mishi har ya fara dumm, ya cewa Tafida."waye yayi maka wannan aikin? Gashi yana son lalacewa!" "Bari nima dazun da naci naji ya fara yauki!" Na flat din gaban Mahmoud ya daukan yana sakawa a bakinshi. "A ina kuka samo wannan?" "Ji dan iska Ummu ce ta bamu!" Mahmoud ya dauke naman ya zuba a aljuhun wandonsa, cire namar yayi ya bar musu a wurin yana jan tsaki, wani dabara ce ta zo mishi ya juye na ta ya tafi da shi ita kuma.tasan yadda xata yi dasu. Bai kuma bin ta kansu ba. A daren da zai tafi ya shiga kitchen din ni nazo shan ruwa na samu yana juye min nama na. Inda yake ban kalla ba dake babu kunya a ranshi ya juye washi gari ya bar garin babu ko sallama. Bayan tafiyar shi na fito na dauki namar nan don har dambun ya juye ya tafi da su ban ce kome ba tow me zance nasan a can zai rabawa abokai ne tun da naji yana faɗa mata. Haka na nutsu na gyara wanda aka mishi ya dawo hayacinsa na juye a roba na bashi zan na miya da shi. Kannena sun zo min yawon sallah, har a cikin gidan anyi musu alkhairi. Bayan tafiyarsu na cigaba da yadda na saba. Bayan tafiyarshi na samu sassauci, domin dai babu shi. Amma yan uwansa mata sun tsane ni. Wata na daya cur Mahaifiyarshi tazo. Wayyo Allah na matar nan tana da kirki. Tunda taxo a cikin Yaranta babu wnada ya tab'a kawo abinci domin ta ci gashi tazo da kanwarsu Sabirah. Haka na ware mata kulla masu kyau, ina saka mata abincin. Yadda na daukaki lamarinta yasa ta kasa boye soyayyarta a gare ni,.ban san waye ya gaya masa ba amma ya kirani ta wayar Mahmoud ya kawo min wayar, yadda yake zagina da cin mutuncina bai saka ma jira ya kashe wayar ba. Na kashe na bawa Yara suka kaiwa Mahmud din. Kwananta goma ta tafi, bayan na mata abinda na ga xan iya domin Hajiya Kaltuma ta gaya min cewa. "Ki kyautata mata don Allah, tana bukatar kulawar Yaranta amma kamar wanda aka shiga tsakaninsu ai kin gani Dakyar suka zo ganinta." Na kwana ina juya lamarin nan tausayinta ya cika min rai. Shi yasa da zata tafi har da turmin zani na hada mata kala biyu nace mata inji Tafida ya kira wai na bata. Murmushi tayi irin na manya yasan Yaranta basu bata ba, tasan Yadda ya kullace ta ba zai bata ba. Amma haka tayi ta godiya, na bata dubu goma sabira na bata kala uku a wanda Mama tayi min, tow Allah na tuba Ina da sutura kamar me, domin Sif dina har babu inda xan saka kaya. Haka muka yi ta turawa sai da na kwashi wata hudu sannan ya dawo a lokacin abincin mu ya kare saura kaɗan ne. Dama baci yake ba ciyar da mutane ya bani damar nayi da shi. Sai da na gama nazarin yadda xan yi zan gaya mishi da ya fito zai fita nace mishi. "Hmmm kayan abinci ya kare fa!" Kankance idanunshi yayi yana faɗin. "ina ruwana? Ni na ajiye ki? Idan kin so ki yi sata ko ki bi maza ki ciyar da kanki, ko kuma ko tafi wanda ya aure min ke ya baki abinci." Duk yadda nake kokarin danne zuciyata amma sai da tayi rauni na zuba mishi idanu. Kafin na koma daki na zauna.... #500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 13 Na jima kafin na iya hadiye kome na kira Mama, domin nasan tana da kayan abinci. "Ummu Hadiyya!" Kuka ne ya tunkuro min na d'aga kaina sama ina hadiye kukan na ce mata. "Yaya Aliyu ya bani kudin cefane, shine nace a ware kayan abinci!" "Ina kika kai kayan garanki?" Ta tambaye ni a rude, hadiye kukan nayi na ce mata. "Kin san yana can Abuja ne tow ya ce shi ba zai dauki kayan garana ba, gara ya bani kudi na saya mishi. Kin ji ba wai na kayan garan ba ne, Yawwa mama ki hada min da garin dan wanke." Jim tayi kafin ta ce min. "Shi kenan zan turo miki sai ko bani kudina don kin san bana son wasa da dukiya. Yawwa akwai kudinki da Babanki ya baki na rike amma dai naga rikewar bai da wani amfani a wurina Uwani zata kawo miki." "Tow shi kenan!" Na fada mata, a hankali naji damuwata ya kare, amma kuma yanayin da nake ciki bana jin damuwar zata kare min. "Assalamualaikum! Aunty Baby gashi nan!" Ta ajiye min abinci murmushi nayi nace mata. "Nabila na gode, yau bana jin dadi ne shi yasa ban daura abincin rana ba." "Ayya haka ne!" Daga nan ta fita, ina zaune a wurin domin kunya nake ji na fada kayan abincinmu ya kare, wurin La'asar sai ga Mudan da Uwani sun kawo min kayan abincin. "Ku saka min a kitchen, zan kai store!" Zama Uwani tayi tana faɗin. "Aunty Baby baki da lafiya ne?" "Zazzaɓi nake ji!" "Gashi inji Mama!" Ta mika min kuɗi. Na duba dayawa na cire dubu uku na bata,.sannan na bawa Mudan ma ina kokarin mikewa Tafida ya shigo yana jin su Uwani na gaishe shi ya ki amsawa. Kamar ma bai ji ba ya wuce. "Jaraba kai Mudan muje kafin ya fara mana koran kare!" "Allah ya yaye miki!" Na fada ina rakasu har bakin gate, na dawo parlour na ganshi zaune a wurin kudina yana kallona. "Kin fara satan ne?" A hankali na kai hannu xan ɗauki kudin ya rigani dauka. "Ko ba tambayarki nake ba?" Nan ma shiru nayi ina Kallonshi. "Bakinki baya magana ne?" Na juya xan tafi ya ja rigana sai da ya yage ta gefe. Mikewa yayi yana kallona, hadiye yawu nayi na ce mishi."ka kyale ni don Allah!" Tura min kuɗi yayi yana faɗin. "Karbi kazamin kudinki waye ya sani ko abokan hulda ne suka turo!" "Zaka maimaita haka a gaban Ubangiji!" Buge min baki yayi yana hayayako min. "Wallahi idan baka daina kokarin dukana ba zai gayawa Alhaji domin ni ba baiwarka bace!" Na rab'a gefenshi ya finciko ni ya dawo da ni gabanshi. "Idan na zane ki uban me zaki yi?" "Ai kaji abin da Mamana ta fada maka zata ramin, ka gwada ka gani." Ganin yadda nake maganar da kwarin gwiwa yasa shi ture ni na fadi kan kujerar parlour. Haka na cigaba da ganin kayan bakinciki domin kuwa saboda mugunta karo yawan mutanen da suke zuwa cin abincin yayi. Na rasa yadda zan dakatar da haka amma ina kamar zuga shi nake, haka nake hakuri da shi, ban tab'a gayawa kowa ba domin nasan wata rana sai labari. Ana haka Mahmoud ya sako ni a gaba da zuwa, sai ya san Tafida ya fita zai zo zauna a parlour wai yana kallo, sannan duk abin da zan dafa haka zai rena ya ce shi abu kaza zan yi mishi, na gaji da haka ranar ya same ni akan tsini ya ce min. "Ummu yau ina son Dan wake da dafaffen kwai!" " ba xan yi ba." Na fada ina me shigewa dakina, domin nima yau taliya naci d miya, tunda na shiga daki ban kuma fitowa. Sai da naji ana doka kofar dakin na fito ina kallon Tafida ne. "Zo ki wuce ki daura mishi dan wake da kwai!" "Garin Dan wake na ya kare kuma baka yi cefenen ba!" Na fada ina me juyawa dakin ya ci kwalar rigana ya fito da ni. "Wuce kafin na tattakaki!" Buge hannunshi nayi, Mahmoud din ya ce. "No kyale ta na saka Sa'adiyya zata min!" Yadda ya fada a sanyaye zaka ɗauka wani abin arziki ne, a kan idanunshi Tafida yayi ta cin mutuncina. Yana gamawa suka fita na koma dakina, haka yayi ta hada ni rigima da Tafida shima bai gane ba, ga cikin gidansu an hade min kai idan na cire Hajiya Kaltuma da Hajiya Salamatu, suma harkan su ya ishe su basu san meke faruwa ba. - "Yanzu kai Tafida tsakani da Allah zancen Mahmoud ka dauka har kake iƙirarin sake Ummu saboda taki gaida Umar ko Abubakar ko?" "Ban gane ba?" Ya fada idanunshi bude. "zaka gane idan lokacin ya kure maka, ka rabu da Mahmoud ka kula da matarka Tafida wallahi idan ka gyara alakarka da Ummu sai kafi kowa moran aurenka Tafida kada lokaci yayi kace kana niman masu tayaka." "Bana son haka Allah ya min tsari da niman wani alfarma a wurin wancan yarinyar baka mummuna me kamar da yan kasan wuta." "Eh tafi wnada ya gagarawa Iyayenshi alfarma ya zauna da ita haka!" "Deen gorin tarbiyya xaka min!" "Na gaya maka ka dakatar da shigar Mahmoud gidanka ka sanshi kuma kasan waye shi akan mata, ni wallahi ko kai da na yarda da kai zai yi matukar wahala na kyale ka kana shigar min gida. Balle har ka zauna da sunan kallon ball. Manzon Allah yayi alƙawarin baya tare da mazan da basu kishin matansu idan kana son ka zama daya daga cikinsu Allah ya baka sa'a " "Yanzu kana nufin zaka iya hana ni shiga gidanka?" "Wallahi ba zan tab'a barinka ka zauna a parlour mata ta ba, domin kai abinka ka rena baka dauke shi da daraja ba shi wani yake son ko yayya ne ya samu." "Ina ruwana kai idan taso na shiga gidan na same ta da kato akanta wallahi zan iya kauda kai na wuce." "Wacce irin kiyayya kake mata ne Aliyu?" "Kawai na tsaneta ne daga kasar zuciyata." Mamaki ya kama Deen jin furucin Aliyu, "tow Allah yasa kada kayi tunanin cutar da ita!"tsaki yayi ya bar office din Deen. Satin shi biyu amma na sha azaba kamar idan ya tafi kada ya kuma dawowa. Bayan tafiyar shi da kwana biyu ne sai ga Aunty Maryam da Rukayya, ita Aunty Maryam bata da matsala sosai kamar Aunty Rukayya, tunda suka shigo muka gaisa sama-sama suka fita sannan suka bar min yaransu ban yarda nayi abinda Yaran zasu yi kuka ba. Yadda na saka musu abinci haka suka yi kaca-kaca da parlourn ban damu ba kayana ne dai na kwashe kada a lalata min. Haka suka gama harkansu suka tafi cikin gidan. Ban san me ke faruwa a cikin gidan ba, sai da Abba ya turo a kirani na je na samu an taru a parlournshi na gaida su. Na nime wuri na zauna. "Alhamdulillahi." Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya fara da addu'a, "Daman abin da yasa na tara ku Aliyu bai da lafiya, na tura dan abokina ya duba shi yana asibiti." *Allah yasa ya mutu!* wani bangare na zuciyata ya furta haka, kamar ana ji ni, na rike bakina. "Ummu zaki tafi ke da Umar." Ban iya d'ago kai ba, haka na cigaba da sunkuyar da kai har aka gama taron. Kafin na tafi Hajiya Kaltuma ta turo min kayan cefene. Nayi miya sannan na soya kaza tare da dambu nayi mishi, sai cin-cin da cake. Domin ita ta sani nayi haka ina tsoron kada nayi ace wani abu. Haka kwana biyu a tsakanin muka wuce abuja, da gaske bai da lafiya abin mamaki Deen da Mahmoud mun same su a can, jikina yayi sanyi domin yadda ake son shi. Bai da lafiya sosai, domin baya gane wanda yake kanshi. Deen ya ce na zauna a asibitin ba zan koma gida ba, shi ya kai min kome na gida. Tunda Mahmoud ya ga na zo yaki tafiya ya tare a gidan baki daya a tunaninshi zan dawo gidan ya samu kaina. Sai aka yi rashin dace Deen ya harbo jirginshi, haka na cigaba da zama har tsawon kwanaki biyu, ya fara dawowa hankalinsa. Sannan suka bar garin tunda ya ganni yake wani haɗe rai. Ni kuwa ko a jikina tunda na fahimci ni ne baya bukata. Kwanansa uku aka sallame shi, sai dai har lokacin jikinshi babu kwari, tunda muka dawo gidan yan dubaiyya suke zuwa gaishe shi. Wani abun tashin hankalin shine yadda nake wuni a tsaye bani da ikon zama zai kwala min kira duk da wannan zaman da nake bai saka Tafida cin abincin da xan girka ba, asalima zuwa mishi ake yi Ni kuma nawa haka zan ta girkawa ana cinyewa. Ana haka Sa'adiyya tazo, tunda na ganta na zuba mata idanun, tana zuwa ta amshi ragamar girkin gidan tsakanina dasu idanun. A hankali na lura zaman jinya ya fara wuce gona da iri, domin kusan a dakinshi take kwana, wata safiya ina dakina a kwance naji ana buga kofar gidan, na tashi na je na bude Deen ne da Abba. Kamar na nutse a kasa domin nasan Sa'adiyya tana dakin Tafida. "Abba! Sannunku da zuwa anan kuka kwana? Ku shigo!" Na fada ina jin kamar na saka hannu a kaina nayi ta ihu. "Bari na taso shi!" Na fada ina nufar dakin, ina shiga na same su cikin wani irin yanayi da duk me Imani abin da zai zo ranshi zargi ne, na buga kafarshi ya bude idanu a gajiye. "Ka zo Abba ya zo, sannan ita ta zauna a dakin kada ta fito domin kimarka zata zuba a idanun mahaifinka." Kafin na fita daga dakin, dafe goshi yayi tare da ture Sa'adiyya wallahi bai yi kome da ita ba, duk da Burinta yayi wani abu da ita amma shi bai tab'a ketare iyakar Allah ba yau ma don tace bata da lafiya ne, shi yasa har ta haura gadon ta kwanta a jikinshi. Sannan akwai wani abu da ya kasa ganewa da zaran ta nufe shi da wani shaidanin turarenta yake jin bai da ikon sarrafa kanshi. Jallabiyar shi ya saka ya fito waje, Ni kuma na shiga kitchen na fara aikin ina ta Addu'a Allah yasa kada ta fito don na lura yar iska ce. Dankalin turawa na soya da sauce din kwai, sai garin kunun tsamiya da na dama, na fito da shi parlourn sannan na koma ina daura abincin rana tuwon semo ne miyar kubewa busashe da na hada da miyar kazar nan, nayi kome na kwashe a leda, a ranar Tafida ya fara cin abincina don yaga idanun Abba, sai kallon Deen yake wanda yake murmushi yana faɗin. "Abba ya kamata a dafawa Ummu ta buɗe katon shagon abincin, domin ni dai Allah ya gani yarinyar da zata saka surukarka zata zo koyan girki wurin Ummu." "Safiyyudeen bakina yana kewar abincin Ummu, kai idan ta gama jinyarka, maza ka tura min ita gida domin bakina da cikina suna kewar abincin ta." "Ai Abba ta dawo kenan sai dai ayi hakuri." Haka suka yi ta santi, haka suka ci na zo na kwashe kayan na kai kitchen sannan na dawo na wuce daki nayi wanka na saka kaya, na fito muka kara gaisawa da Abba, shima dakinsa ya wuce yayi wanka tare da zubawa Sa'adiyya warning kada ta fito. Sai wurin karfe uku su Abba suka tafi, ya ja Deen gefe ya gaya mishi abin da yake faruwa. Sake baki Deen yai idanunshi sun yi jajjur. "Idan ka sake hauka ya kwashe ka, ka sake Ummu Hadiyya. In sha Allah zan aureta tunda baka bukatarta a rayuwarka ka sake ta ka ga ikon Allah!" "Deen!" "Eh zan mata da abotarmu, alakarmu zan aure ta a matsayin da duk tazo min kuma zan yanke mu'amala da kai saboda ex-wife dinka ce kada ka ketare min iyakata, sai ka zauna da ƙaruwar da take biyo namiji har gidan aurenshi akan idanun Matarshi, idan da kasan wacece yarinyar nan ko hada numfashi da ita ba zaka yi ba, Aliyu na gaya maka gaskiya ne domin ba zan koma baya ina cin dudduniyarka ba! Ka sani ba iya kanka kake jefawa bala'i ba innocent soul din da kake jefawa masifa shine tashin hankali, Tafida zina ko kusantarta masifa ce balle kuma Allah ya baka mace ta gari da take kara kame kanta, idan da yau duk abinda zaka yi iya kanka zai tsaya da sauki idan ita wani yayi attempt dinta saboda ka kusanci zina kayi mata adalci? " "Amma kasan ban tab'a zina ba ko?" "Taya xan sani bayan ka ajiye mace a dakinka kuna kwana daki daya, ita matarka ta sunna ka mai da ita hoto, kamar yadda kake da lafiya da kuzari haka take da shi kai ba Jahili ba amma kafin jahili jahilci zan gayawa Abbanka yasan irin ukubar da kake ganawa Ummu, tunda kai ka tashi daga sahun mutanen kirki ka koma sahun kasikai azzalumai masu cutar matayensu da danginsu." "Deen " dakatar da shi yayi yana faɗin. "Ban gama ba, ita yarinya har abada ba zaka tab'a samun biyunta ba, ta rufa maka asiri ta saka ka boye macen da ta zo mata dadiranci sannan kayi tsammanin yarinyar nan har yau bata isa ta baka abinci ka ci ba, Yarinyar da ta rufa maka asiri idan wata ce tona maka asiri zata yi a gaban mahaifinka, amma ta nunawa maka kai mutumin kirki ne abin da ta gani ba zai hana ta rufa maka asiri ba, Ummu Hadiyya mace ce ya kuma me tarbiyyar da ake bukata don Allah idan ba xaka zauna da ita ba da kayi ta bata wahala ka sakota ni zan zauna da ita Daga haka ya bar shi sake, sai dai yadda ya fadi haka sai yaji ranshi ya b'aci ba fa akan Ummu ba a'a shi kawai babban matsalarshi aibanta Saadi baby da yayi, bayan tafiyarsu ne ya shigo ya dauki abinci ya kai mata dakin, tana murmushi ta ce mishi. "Abba ya tafi ne?" "Eh ki koma gida yau, zaman ya isa haka!" "Ya Ali!" "Nace ki koma gida!" Jin haka yasa ya shiga hada kayanta tana kuka. "a yau xan koma Maiduguri!" Kallon agogon dakin yayi yana shafa kansa. "Zuwa gobe ki wuce!" Sannan ya fita, har dare bai kuma yin wani abu ba asalima ban san ya suka kare ba, washi gari da sassafe naji tana ta kuka tare da surutai, domin cikin dare da na fito na dibi tea saboda muran da yake damuna a parlour na ganshi ya kwanta, na dauke kai nayi kitchen. Ko bayan tafiyarta ban yi abin karyawa da wuri ba, domin nasan iya cikina ne. Sai wurin sha daya na dumama tuwon jiya naci, da rana nayi shinkafa da wake, na ci tare da barin sauran zuwa dare don nasan baya shigowa sai da barcin, haka muka cigaba da rayuwa babu me shiga harkan wani sai dai akwai wata yarinyar me suna Tina da ta dame mu da zuwa, idan tazo tun safe sai ta kai har karfe goma kafin ta tafi, na farko Ita ba musulma ba balle nace ba wani abu. Sai dai dake ban bata fuska ba. Tana zaune zama take a parlour idan yana gida suka yi hira, haka zata gayyato kawayenta sun mai da ni mai girkinsu. Sannan ban isa na ce yau ina ciwo ba domin Tafida da bai da uzuri yanzu sai ya fara fada. A hiransu na fahimci Babanta kusan gwamnati ne, sannan yana da kusanci da shugaban kasa, bayan nan Baban Tina Yana son Tafida musamman da yasan waye Uban Tafida, haka yasa shi kara son shi. Sannan wani abu da ya yarinyar tana da hankali da nutsuwa matsalarta shine yadda ta maida ni mai girkinsu. Ranar wata Juma'a ina dan wake tazo, tana buga kofa naje na bude mata, "Amarya yau na zo miki da wani abu canka?" Murmushi nayi nace mata. "Kin ga na bar abinci akan wuta shigo!" Har ga Allah na gaji sosai, kamar na gudu gida haka nake ji, kwashe dan waken nayi na zuba a ruwa na karasa sauran jifan. "kin ga wannan wata kawata ce a kamfanin Maggi star, wai za ayi girki na gasa arewa da kudu shine na amsa miki Form!" Kallont nayi bakina sake."kika amsa min?" "Eh mana taya xan biya ki hidimar da kike mana, kin ga har da kyauta na san Amarya You Are the best, kuma abincinki ko uban waye yaci zai sara miki, manyan masu girki ake gayyata shine na gayawa Aliyos yace babu ruwanshi." Murmushi nayi tare da cewa. "Tow bari na gani xan gayawa Alhajinmu!" "Yawwa next week za a kira ku!" Ta mika min takardan yarinyar nan ba karamin kudi ta kashe ba, sai naji kunya ya kama ni. "dubu dari uku kudin shiga gasar!" "Kina tsammanin baki fi karfin haka bane?" "Na gode!" Na fada bayan na ajiye takarda na nufi daki na ji bakiɗaya kunyarta ya ishe ni. Na fito na zuba mata abinci, tana ci dai ga Tafida na shiga kitchen na dauke mishi takardan na ajiye mishi. "Me yasa kika kashe kudinki tina akan inuwar alli, ina ruwan kukun guntaye, don Allah dube ta da kaɗan tafi Mug tsawo!" "Aliyos wannan cin fuska ne." "I'm just joking ne fa!" "Wannan ba joking bane mock dinta kake, maybe a idanunka ne kake kallonta haka, amma tana da mutunci da sanin darajar kowa tunda nake zuwa bata tab'a gajiya da ni ba, sannan ko ya na kawo mutane zasu ji dadin zuwan Please bayan ni kada ka kara cin zarafinta haka, domin ni idan aka min zan iya mutuwa balle ita da haka.bai dame ta ba which mean ta saba da cin fuskarka. Addininku ya bawa mata kariya, ya kuma girmamasu. Sannan ya nuna musu muhimmancin mutanen, kai kana da kirki da mutunci amma Matarka ta wuce tunanin ka, da ce ni ce kai na sameta har abada ba xan yi wasa da damar da na samu ba, ita kamar haske ce a gidanka a lokacin darkness, tana da kirki Please ko ba yanzu ba kada ka taba yarda wani abu ya rabaka da ita don ba zaka tab'a samun kamarta ba" kasa magana yayi yana jin tinah har ta gama suka yi hira ta bar gidan, ina zaune ya d'aga labulen ya watsa min takardun yana faɗin. "Idan ma asiri kike yiwa mutane tow ki daina domin wallahi xan miki ba dad'i.... *Ni jikar na tsalle kwad'o yace. inji Aunty Hadiza 🤣😂 Tafida baka jin magana wallahi asiri kuma dai!* #500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 14 Hadiye yawu nayi ina kallonshi, kafin na ce mishi. "Kayi hakuri idan kace ma kada na shiga gasar zan hakura da shi!" Wani wulakantaccen kallo ya zuba min yana me kara shigowa cikin dakin. "Da kiyi da kada ki yi daya ne a wurina ko a kwalar rigana, ke idan kin son ki tafi tsirara babu abinda ya dame ni." "Na gode!" Na fadi haka tunda na samu wannan damar nayi alkawarin zan yiwa Aliyu biyayya koda kuwa zan rasa rayuwata ne, don na kara gane wasu daman baka tab'a samunsu haka kawai sai ta wani dalili me karfi dalilin kuwa shine auren Tafida, don haka na yarda da cewa Allah yana tare da ni shine wannan damar yazo min, bayan fitar shi na kira Mamana na gaya mata abinda yake faruwa, Abinda ta fara tambayata. "Mijinki ya amince?" "Eh ya amince!" "Tow ki kira Babanshi ki gaya mishi sannan ki gayawa Babanki da Babanku Bulama!" "Tow Mama!" Haka kuwa nayi na gayawa Abba yayi min addu'a sosai, sannan na kira Baba Bulama na gaya mishi, ya tambaye ni Aliyu ya amince nace eh, sannan yayi min addu'a. Can na kira Babana sai da muka yi dogon hira har katina ya kare sai gashi ya kuma kirana. "Babana!" "Na'am Ummuna!" Ya fada yana murmushi. "Dama wani gasar girkin zamani ne aka saya min Form din shine na ce bari na gaya maka ayi min addu'a." "Masha Allah Mijinki ya amince?" "Eh ya amince!" "Tow ya za ayi shi zai na kai ki ko kece xaki na zuwa don nasan ke bakuwa ce a abuja!" "Eh gaskiya yana fita da wuri ni kuma ban san yadda xan na fita ba." "Tow shi kenan zan nime shi muyi magana!" "Tow Baba!" Haka muka yi sallama, bayan Isha ina zaune na ji ana buga kofar gidan, zuwa nayi na bude Sa'adiyya ce, ban yi mamaki ba na bude mata kofar ta shiga tana yatsina fuska. Ban ce mata kome ba, wurin karfe goma ya shigo gidan ina dakina, buga kofar yayi na tashi na buɗe. "Uban waye ya ce ki hada ni da wadancan tsofi ukun!" "Kayi hakuri na gaya musu ne amma ba zan ƙara ba." "Sakarya kawai!" Ya fara tijaran da ya saba, koda yake kwana biyu bai yi ba amma yau kamar jira yake Sa'adiyya ta dirko gidan, haka ya gama ina bashi hakuri yana kara tinzura karshe na makale jikin bango kamar zai dake ni, yana gamawa ya fita. "Ya Aliy!" "Sa'adi yaushe kika zo?" "Dazun nan man!" Washi gari Tina tazo ta amshi Form din ta ga ban cika ba, ware idanu tai tare da cewa. "Aliyos bai cika miki ba ne?" "Eh kin san yana busy!" Amsa tayi ta buɗe jakarta. "Amma naji kamar kina mura!" Na tambaye ta. "Eh jiya nasha ice cream ne!" "Bari na dafa miki ruwan zafi da yar farfesu!" "Amarya bar shi na koshi!" Ya fada tana kallon dakin Tafida da Sa'adiyya ta fito. "Wacece ita?" "Yar uwarsa ce daga Maiduguri!" Dauke kai tayi tana wani haɗe rai. Kitchen na nufa na hada mata kayan kamshi ma dafa mata shayi, sannan akwai sauran nama da yake sayowa na mata farfesu me ruwa ruwa. "Amarya ya kamata ace kina da babban frij, wanda zaki na ajiye kayan abinci. Ba sai kullum za a na girki ba!" "Tow Tina!" Na zauna, ta mika min takardan har ta cike wurin girki ne ta ce min. "Zaki dauki na gargajiya ne domin an fi samun na sa'a akanshi." "Duk wanda kika zab'a min zan amsa!" Ina jin motsin Sa'adiyya a kitchen, har ta gama abin da take ta fito ta wuce dakinshi, dama ya tafi aiki. Kitchen na shiga nayi mana shinkafa da miya sai salat. "Amarya zaki kashe ni da dad'i." Haka muka wuni da dare aka zo daukarta, ta tafi da takardan, weekend bata zo ba duk sai na damu domin tun ranar Alhamis juma'a asabar da lahadi bata zo ba, yammacin Lahadi ina zaune ya shigo dakin yana me tsayawa a kaina. "Ki saka kaya ina jiranki a waje! Kuma kada ki sake ki saka min burma-burman kaya." "Tow!" Na fada sannan na mike, kayana na duba babu wanda yayi yadda yake so, sai kayan dinner da aka min shi bubu ne na saka tare da daura zani akan rigar. Sannan na dauki dan kwalin na kafa dauri. Mayafi fari na saka da takalmi fari saboda lacce din fari ne tas, kwali da man baki na saka fuskana kuwa sama-sama na shafa mishi hoda, na fito. A parlour na same shi da Sa'adi, kwashewa da dariya tayi tana faɗin. "Yau an saka a cuci maza kenan! Don wannan boons din ba naki ba ne!" Yana jin mu bai ce kome ba, haka na tsaya kaina a sunkuye. Domin naga yana shan abu ne da itama shi take sha. Mikewa yayi yana faɗin. "Muje!" Haka na bi bayanshi, abin mamaki a harabar unguwar muka samu Mahmoud ya zo, yana idanunshi kur a kaina. Parking yayi a gefen motar Tafida ya fito yana kallona. "Man ina zaku?" "Kasan yar gidan Mr Kayemi Tina ita ce yau take birthday ta ce na zo mata da wannan abin!" Murmushi Mahmoud yayi ya ce mishi. "Ko na raka ku ne?" "Me zai hana sai ka tawo da Sa'adi!" "Ba dai a motatta ba, domin na tsani yarinyar nan bata da kamun kai!" Ya fada yana hade rai. "Please mana!" Ya fada yana nufar motarshi. "Na gaya miki gaskiya! Ke tauraruwa ce a cikin taurari, haskenki daban yake shi yasa zan biku na kare martabarki kada wasu , su kallar min ke!" Ya fada yana rike da mayafina, kwace mayafin nayi kafin Tafida ya juyo ya ganmu. "Man bari na shiga na mata magana." Kin yarda nayi mu hada idanu, har na shiga motar, muka bar gidan yadda Tafida yayi ta min kashedi kada na je nayi rawan kai, abubuwa iri-iri babu wanda bai min ba. ** Lokacin da Mahmoud ya shiga ya samu Sa'adiyya ta shiga dakin Ummu zata saka abu. Kamar ance ya d'aga labulen kawai ya ganta tana niman inda zata saka abin. "Da kuwa naci Ubanki, munafika fito kafin na takaki." Yadda ya hauro mata yasa tayi baya, ya amshe layyar ya jefa a toilet ya tura ruwa. "Yar iska kika sake gobe na same ki a gidan nan sai na baki mamaki, kuma ki shirya mu bi bayansu jaka kawai!" Haka ta fita jikinta a sanyaye, ta shirya suka fita, tasha zagi da harara. Har gidansu Tina. Lokacin da muka isa ana yiwa Tina kwalliya, janyo ni tayi tana faɗin. "Itama ayi mata amarya ce!" Murmushi nayi kawai,"shine baki gaya min zaki yi bikin Birthday dinki ba!" "Amarya ba zan so kiyi aikin wahala ba!" Ta fada tana murmushi ana gama mata aka yi min kwalliyar dan daidai. Ba yawwa ba hayaniya, a tare muka fito bayan an dauke mu hotuna muka zo wurin Birthday dake mayafina yana kafadana. Idanun Mahmoud yana kaina, duk inda nayi yana bina da idanu. Sa'adiyya abin ya d'aga mata hankali musamman yadda Tina take hada ni da kawayenta, take gaya musu ai ni matar Aliyos ne, haka suka yi ta taya ni murna tare da bani labarin kirkinsa. Haka aka tashi taron wurin karfe goma sha daya, na gaji don ma ban yi sake Sallah ya kwace min ba, don da nace zan yi sallah sake kiran me kwalliyar tayi bayan na idar da sallah ta gyara min fuskana. A hanya muna dawowa yake gasa min magana. Ni dai ban kula shi ba, don barci nake ji. Ban san me ya hau kanshi ba, amma yadda yake gaya min magana yasa na kauda kaina kamar bana jin shi, Sa'adiyya da ta rigamu dawowa ita da Mahmoud suna parlour muka shigo. Daki na shige ban kalle su ba, na kwanta don na gaji sosai. Washi gari da sassafe naji motsin ana jan akwati. Ban fito ba sai sha daya gidan babu kowa na fito daga ni sai riga da wando na barci da na saka da asuba, na fere dankali na fara soya naji ana buga kofar gidan da kirana. "Amarya!" Da sauri ba saka hijab da yake jikin kofar kitchen na fito. "kin manta ne?" "Na gaji ne har nayi barci ." "Shirya mu tafi!" "Ban karya ba!" "No need zan miki takeaway!" Haka na shirya sannan na saka doguwar riga da mayafi na nad'e kaina, muka fita ita ce ta kai ni har inda zamu yi taro na kwana uku. Tana kai ni ciki tace zata kawo min abinci. Ta tafi ta cika alkawarinta, ana fitowa tana mika min abinci. "Kin san na makara muje na ajiye ki!" Haka ta kawo ni gida, "ki zo muci mana!" "A'a na gode!" Ta tafi ina shiga cikin gidan, hadiye yawu nayi domin Mahmoud na gani zaune ya zuba min idanu. Wuce shi nayi na nufi dakina, ina shiga na rufe kofar na zauna tare da fara cin abinci na. "Ummu Hadiyya! Ina son ki bani damar miki bayani yadda zaki fahimce ni, Ummu ina kaunarki ni bana son muyi kazamar alaka ki amince min na tsaya miki, Aliyu ya sake ki mu gina rayuwarmu na jima ina niman mace irinki." Idan gidan zai amsa tow na amsawa Mahmoud ya gama haukarshi ko waje wunin ranar ban fito ba, washi gari da safe ina fitowa na ganshi zaune daga shi sai gajeren wando, dakin na koma na zauna. Can ina zaune na ga abin bana kare bane zan tafi wurin taro na fito nayi abin karyawa haka ya zo ya tsaya a kaina yana ta min magana ban kula shi ba, abin da nayi niyya da ya sake yayi min wani shirme man gyada xan watsa mishi. Sai bai fara ba, har ya bar wurin na gama kome na shirya na fito zan tafi Tina ta zo muka tafi a bakinta najin Aliyu da shugaban kasa sun yi tafiya zuwa Morocco. Haka yasa na fahimci shi yasa Mahmoud yake damuna, kuma da alamu tafiyar ya sati guda ce, don haka tana kai ni nace mata. "Ni naga gidanku yafi kusa da nan, me zai hana kawai na dawo gidanku da zama kafin mu gama taron!" " Da gaske?" "Allah da gaske!" "Tow shi kenan!" Nayi haka ne domin gujewa sharrin shaidan, ana tashi muka dawo tare ta jira na kwashi kayana muka bar gidan, dana san gida daya muke kwana wallahi da ban zauna har haka ba, haka na koma gidansu Tina da zama ban tab'a ganin mutane masu mutuncinsu ba, sun girmama ni da mutuntatta ni, kannenta da Yayunta da matan yayunta kamar su goya ni, abinci kuwa dani ake girkawa Yarbawa karshe ne a girki sai suka ga nima ba a bar ni a baya ba, ai kuwa suka shiga cewa Ayawo a bude mana restaurants a garin nan, a wurin taron ma Ni daya ce yar arewa. Haka muka yi taron kafin muka fara zuwa girki, anan na ga Hajja yar Shehun Borno, ai kuwa ta ji dadi domin tana cikin alkalan gasar. Kowa na gabatar da kanshi nima na gabatar da kaina da inda na fito. Cikin jin dadi ta ce min. "kenan ke yar borno ce amma nasan yan borno turare aka sansu da shi, ba abinci ba." Cikin girmamawa na ce mata. "Dukka muna da shi turare da abinci!" Murmushi tayi tana mana fatan Alkhairi, tunda muka fara gasar girkin nan bana barci, ina kiran Mama tare da tambayarta, sallah dare kuwa na kara akan nada, girkin zai dauke mu kwana sha hudu. Ashe Mahmoud ya kira Tafida ya gaya mishi bana dawowa gida, da kamar zai ce ina ruwanshi sai yayi tsaki yace mishi. "Tana tare da Tina k zauna abinka kafin na dawo!" "Wallahi na zata wani wurin ta tafi!" Tsaki yayi yana faɗin. "Tow ina ruwana taje duk inda yayi mata ita ta sani ba ni ba." "Ban gane ba!" Kamar wanda aka tsira mishi allura ya fara magana, har da rantsuwa ko kato ya gani akan Ummu zai iya dauke kai don ba zai ji kome ba don baya kaunarta gara mutuwa sai dubu da zaman da yake da Ummu. "Tow ka sake ta mana tunda abin ya kai haka." "Ba zan sake ta ba domin Alhaji zai iya tsine min albarka. "Ita kuma bai dame ka ba idan ta bi wani namijin?" "Ita ta sani tunda yar talle ce ta saba da tsalle tsallensu da maza a waje kai ka dame ni!" Kashe wayar yayi murmushi Mahmoud yayi ya nufi dakin Ummu da ya ɓalla dazun, ya dauki bra dinta da pant, dinta ya runguma yana me sakawa a fuskarshi kamshin turaren miski yake shaka. "Kamar yadda kamshin nan yake Allah yasa kome na jikinki haka yake Aliyu na rantse da Allah sai na baka mamaki!" Kwananmu tara Tina ta gaya min zai dawo ranar, daga wurin gasar gida ta kawo ni, ina shiga gida Babana ya kira ni yana tambayata ya nake da abinda nake yi, na gaya mishi akwai me kai ni, "ki turo account dinki zan turo miki zakkar da na cire ne na ware miki naki!" "Babana na gode in sha Allah zan turo!" Muna gamawa na tura mishi, ashe a can gida Maiduguri ana saka gasar mu bayan sallah isha, yan uwa da abokan arziki, kowa yana gani a tv NTA Maiduguri suna sakawa, wanda hajja ta dauki nauyin shi tare da Maggi star. Wasa wasa Yan uwa Aliyu abin bai musu dadi ba, domin gani suke ban cancanci shiga gasar ba, Shuwa kamar ta mutu don bakinciki, Abba kuwa ana isha yake dawowa yana me zama a jikin tv, yana kallon girke-girken. Sai bayan Isha Aliyu ya shigo gidan, tunda na ce mishi. "Barka da hanya ka dawo lafiya?" "Da ban dawo ba zaki ganni?" "Ayi hakuri! Masifatu!" Inji Mahmoud yana shigowa cikin gidan, basu wuri nayi na koma kitchen, ina dafa jollop din taliya, ina gamawa na zuba a kula na barshi a kitchen din na shige dakina. Bayan ya huta ne ya fito ya samu Mahmoud ya dauki abinci ya baza a tire, har ta fara ci. "kai bana son iskanci, gidana ne zaka zo ka juye abinci kana ci sonka!" "Ai naga baka damu da girkin ta bane shi yasa na juye idan kana so Bismillah!" Ba musu ya sauka ya fara ci ko cokali bai dauka ba, haka suka cinye ya nufi kitchen ya dauki tukunyar ya juye sauran ya fito suka cinye. Washi gari na fito na kwaba fanke, na koma daki kafin karfe shida ya tashi na koma na fara soyawa ina gamawa na dama kunu na tafi wanka. Nasan Mahmoud baya nan, sai dai ina fitowa na samu an sha kudin saura kaɗan a kasan kofi, fanke kuwa na rantse da Allah daya aka bar min. Raina ya b'aci haka juya abincin nan aka juye tas yau kuma an kara min haka. Haka yasa ban ce kome ba na kira tinah na ce ta zo min da abinci don Allah. Da abincin tazo min muka wuce wurin gasar na karya a motarta. A hankali na fahimci wannan abin da ake min ya fara yawa, daga ni sai Tafida a gidan bayan shi ko Mahmoud naga baya nan yazo da alamu ya tafi gida, kwatsam Ranar asabar da safe na gama soya kosai, na shiga daki na fito ko ya dauka wanka na shiga kawai na zo na samu ya zauna yana cin kosan da kunu sauri sauri yana gudun kada na kama shi, juywa nayi dakin na barshi ya ci. Yana gamawa na ji motsin ya bar gidan. Tun daga lokacin ban kara yin abu iya cikina ba, sai na yi dayawa amma bai gane ba idan nayi dayawa sai ya kwashe ya tafi da shi, ranar da muka gama gasarmu, da ranar wani kunu nayi wanda ake yi da shinkafar tuwo, madara kilo, kimba, kanunfari, citta, da manshanu da sugar. Domin a cikin kwanakin nan da kuma yi ni daya ce ban maimaita abinci ba, kuma yau da nayi wannan bakiɗaya hankalin Alkalan yayi kaina. Tunda na wanke shinkafar tuwo na zuba da ruwa me yawa, sannan na zuba kayan kamshi kafin na barci yayi ta nuna ina ganin ya nuna sosai na bude na kara dama shi, sannan na kara masa ruwan dumi ya sake. Na rufe shi kafin na dauko garin madaran na fara zubawa ina damawa, sai da ya hadu tas sannan na sauke na zuba sugar na juya shi, sannan na zuba a yan kananun bowl da cokali na zuba manshanu a kai ba jera inda kowa zai dauka. Tunda na gama na wanke kayan na koma gefe ina goge hannuna. A yau aka bamu damar magana tare da nuna mana inda zamu zauna, Alkalai na cin abincin mu, suna mana tambaya. Wani dan china da yake cikin alkalan ya ce min. "Wannan abincin naki ban tab'a ci ba sai yau! Sannan dayawanku da kuka tsallake zagaye na biyu kun sake maimata girki ke kuma tunda kika fara baki maimaita ba me yasa haka!" Rike abin maganar nayi na sake murmushi, sannan na fadi sunan makarantar Yar shehun Borno inda na samu diploma a girki abin da suka koya mana da kuma ni kaina tun ina shekara goma nake koyan girki , sannan muna yin abincin sayarwa wanda a rana guda muna abinci sama da kala biyar zuwa shiga, haka yasa na kara sanin yadda zan kaucewa maimaici. Sannan na gaya musu iya abincin gargajiya da nayi ba arewa ne, ban dauko wani abu daga kudu ba, masa, dan wake, sinasir, kindirmo da dambunshi, tuwon alkama, fumkasau, dambun cus-cus, biski, da sauransu. Karshe na rufe da wannan girkin. Sun jinjina min hadin aka fara fitar da sunayen wadanda suka yi nasara ban kawo zan yi nasara ba, haka yasa ana gamawa hira damu aka fara kiran waɗanda basu yi nasara ba ana basu shaidar kwarewarsu, a cikin mu goma aka sallam shida, ya rage saura huɗu. Na hudun sha fara kira aka bata kyauta. Sannan aka kira na uku namiji ne, sai na biyu na miji ne, sai gaba na ya fara bugawa. Lokacin da alkalan suka kira na biyu zuba min idanun suka yi yadda na kasa nutsuwa, na rasa waye zai tsaya min a lokacin. Tina ce ta fito wurin ta rike hannuna. Hawaye ya zubo min. "ba gani a tare dake ba, zaki iya na gaya miki yanzu zasu kira ki!" Lokacin da suka kira suna na, kawai ban san lokacin da na zube ina me sujada ba, domin sun tabbatar da cewa idan nayi nasara akwai wasu kamfanoni da zasu dauke ni nayi musu talla sannan akwai gasar girki na duniya a garin dubai wanda za ayi December, ni ce zan wakilci Nijeriya da jahar Borno. Yadda nai sujada nan ina tashi da kuka na tashi Tina ta rike min hannu muka je aka bani lambar yabo da kuma kyautar miliyan biyar. Kuka nake idan na tuna irin kokarin Mama akan girkin. Sai na rasa abin cewa haka aka tashi taron. "Kai shegen sama ina ka boya ne?" "A wannan lokacin da yarinyar nan tayi nasara ya dace ace kai ne a gefenta, amma Tafida ka barwa Tinah matsayinka, Haba Aliyu Haba Aliyu me yasa ne haka? Me yasa ko ina sai ka nuna baka kaunar Ummu, me tayi maka da zafi haka? Aliyu Allah yana sonka ne ya baka Ummu amma wallahi muna nan dayawa da muke addu'ar Allah ya bamu mata nagari, Aliyu har cikin raina nake son zamanka da ita, yanzu ka ga yadda take kuka tana bukatar wani a gefenta iyayenta ko mijinta, amma ta rasa kowa sai wata da bata hada kome da ita ba zata tsaya mata abin nan duk Najeriya ake kallo haba Aliyu abokan aikina dayawa sai da suka fadi cewa ina mijinta yake ba an ce matar aure ba ce, haba Aliyu, don Allah don soyayyarka da Annabi Muhammad ka saketa kaji ka sake ta don Allah tayi wani auren ko zata samu wanda zai kula da ita!" Nan ya hau fada tare da gayawa Deen cewa. "Ina da nayi tafiya na bar mata Mahmoud ya na kaita wurin tattarawa tayi ta koma gidansu Tina shi yasa na barta da Tinan!" "Mahmoud ka barwa Ummu yana kaita wurin ? Tafida anya mutane ne aka haifeka? Kai da kanka kasan Mahmoud ko bunsuru ya ganshi ya barshi shine zaka ce ka bar mishi yar mutane Innalillahi, gara da ta bar gidan Allah ya mata albarka ya bata yadda zata yi amma tabbas Allah sai ya saka mata domin nayi Imani da wanda rayuwata da mutuwata take hannunshi Mahmoud ya mata akunyaci yasa ta bar gidan Wayyo Allah kai dai Allah ya wadaran halinka, duk amintatta da Mahmoud ba zan bar mishi ajiyar mace ba kai mace ko ta kare balle macen mutum ba zan barwa Mahmoud ba, kai bari na gaya maka ko macen alade ba zan taba barwa Mahmoud ba balle macen bil adam wacce ta hada sura da zati irin na Hadiyya wallahi ba zan bar masa ita a gida ɗaya ba ko a mota daya ba zan bari ba, kayi a hankali da rayuwa idan kasan fitar rana baka san inda zai fadi ba....... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 15 "Wallahi baka yiwa kanka da rayuwarka adalci ba, kasan waye Mahmoud? Koda yake ba mamaki kai da shi kwarya sama ce ta daki na kasa, amma nasan haka kawai ba zan barwa Mahmoud diya mace baliga ba, idan baka sonta fine amma barin Mahmoud a jikin mace baliga masifa ce kuma na gaya maka gaskiya tunda kai dan banza ne!" "Ya ishe ka zagina!" "Hmm wata rana zaka yi kuka da fatan Ummu ta saurare ka." "Allah ya min tsari kada ya nuna min wannan ranar ya raba ni da mugun ji da mugun gani!" Duk wani masoyina ya kirani a waya anyi min fatan Alkhairi, na rasa inda Deen ya samu number na sai gashi ya kira har da fatan alkhairi. Haka na samu damar shiga cikin mutane, a wannan lokacin na ga kokarin shi na yarda ya kai ni irin tarurruka da aka yi ta yi akan nasarar da muka samu, sai dai abin da ya fara damuna yadda kiri-kiri yake gaya musu ai kawai girkin na iya amma ai kaina babu kome a cikinsa sai yadda ake abinci. Kusan sai naji abin ya fara fitar min a rai, ya zamana ko taro ne bana son zuwa sai ya saka ni a gaba da dariya. Ana haka kwatsam tafiya ta kama shi Maiduguri, ya tafi da safe da yamma sai ga Mahmoud tunda na ganshi ta window naki bude kofar, yayi kiran duniyar nan naki budewa nayi kamar ma bana gidan. Kawai ya kira Tafida ya gaya mishi ai yazo bana nan. Aikuwa ya fara fada kamar ya shigo wayar. ** Deen yana jinshi bai ce kome ba, saukar wayarshi yayi ya turawa Mahmoud sako. *Kabar gidan Tafida kafin na shiga wurin Mahaifinsa na gaya mishi yadda kake kokarin niman Yar Mutane!* Sakon na shiga ko minti ɗaya ba ayi ba sai ga kiran Mahmoud. "Zan ci abu kazan-kazan Ubanka Ni zaka mayar dan iska nace maka ina niman matar aure ne!!" "Kai ka sani idan kaso kada ka bar wurin sauran Alhaji zai ji da shi." Ya kashe wayar. "Kai da waye?" "Ni da wani dan akuya ne da yake bin matar wani jaki shine na mishi kashedi ya biyo ni!" "Shi mijin dakikin ina ne da yana zaune wani na niman Matarshi?" "Ai bayi da banbanci da maloho irinka, da ka bar Ummu Hadiyya a abuja har wani yana ce maka matarka bata nan? Anya Tafida tsinuwar Annabi ba zai kama ka ba kuwa? Tow zan gayawa Abba domin iya adalci nayi maka ina tsoron kada wata rana wani ya keta alfarmarta saboda kai " "ban gane ba kana nufin Mahmoud yana niman Ummu?" "Ni na gaya maka? Rufa min asiri wallahi ban isa ba!" "Lashe bakinshi yayi yana faɗin. "Tow shi kenan!" Kwananshi biyu a Maiduguri da zai dawo tare da Deen suka zo saboda akwai wani workshop da zasu yi, tafida yaso ya sauka a gidan amma yaki, ya ce." Zan na zuwa cin abincin dare dai!" Da haka kuwa aka bar zancen, an bawa Tafida kaya amma yaki ikon Allah da Deen ya shiga yin sallama da Abba ya bashi kayan ya zo min da shi. Nayi murna domin kusan kayan Mama ce ta turo min, haka na gyara abuna na cigaba da mana girki. Kullum na kira Babana ko Abba nasiha suke min tare da tambayana ko akwai abinda nake so, nace musu a'a babu kyautar da Abba yake bani har mamaki yake sani jin ga Babana ma haka, Mama itama nayi hakuri na zauna . Baba Bulama shima ba karamin kokari yake ba, abin da na kara fahimtar iyayena da na Tafida suna son mu zauna a inuwa guda amma shi fa yaki sam yaki maganar a zauna. Haka lokaci ya tura har muka fara kusantar watan azumi, wanda yasani jin kamar nayi kuka don ina son nayi azumi a Maiduguri, haka muka fara azumi ranar da aka ɗauki azumi daya ranar ya shigo dakin ya ce min. "Ke ki shirya Babanki ya ji zan tafi Umara ya biya miki!" "Babana?" "A"a Babana!" Ya fada yana watsa min harara, haka na saka hijab muka tafi aka mana kome har da passport, muna dawowa muka samu Tinah, murna kamar zai yi yaya ta kawo min kaya ne , wai ashe ta tafi Dubai ne sai gata da kaya niki-niki, tsaki yayi yana faɗin. "Tina kina bata yarinyar nan da kyauta fa,.ni bani da halin yi mata abinda kuke mata ke friend dinki!" "Aliyos ba zaka gane ba ne, Ummu tana da kirki shi yasa bana jin zan iya samun abu ban bata ba." Dogayen riguna kala uku sai takalma heel , masu kyau kafa hudu da jakunansu. Sai wani Musulmin lace me kyau kala biyu, "Gashi kin zo muna azumi me zan miki?" "Tafiya xan yi idan za a sha ruwa xan zo!" Haka na rakata ina ta godiya, har zata shiga Mota ta ce min. "Akwai wata yar ghana tana sayar da mai da sabulu xan karba miki." Dariya nayi nace mata "a'a bana son bleaching!" "No ba zai kara miki haske ba amma zai gyara miki fata!" "Tow shi kenan amma zamu tafi Umara duk da bai gaya min lokacin ba!" "Zan kawo miki an jima! Ni dai turaren Maiduguri nake so ga gidan ki nan mutum ya rasa wani irin kamshi yake yi!" "Kai Tina zan a kawo miki!" Haka muka yi sallama ta tafi,na shiga aiki kamar kafafuna zasu yanke. Ana shan ruwa Tina ta kawo min kayan na ciro mata kula masu kyau na zuba abinci a ciki ta tafi da su don saurayinta ya kawo ta, an fara azumi da kwana bakwai muka bar Nigeria zuwa Saudiyya. Lokacin da na ganni a dakin Ka'aba sai da nayi kuka nayi kuka nayi farinciki nayi addu'a na kai kuka na wurin Allah. Sai da aka sha ruwa na koma hotel dinmu, hmm Tafida tunda muka yi wanka muka tafi harami ban kara ganinshi ba, wasa gaske sai da muka sati Daya na ganshi tare da Sa'adiyya. Kallo daya nayi musu na dauke kai, ko ya sha jinin jikinshi ne, da asuba lokacin Sahoor sai gashi. Sau daya na kalli inda yake na kauda kai. Koda muka yi Sahoor kowa kama gabanshi yayi, na nufi masallaci, shi kuma yana me budar hotel din da ya sauya dukkanmu a nan haramin muke, haka ma da muka tafi Madina, sau na ganshi sai na dauke kaina, lokacin da naje rauhda. Anan ne naji kuka ya zo min, na tafi gaban Kabarin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, na zauna cikin kuka nace. "Ya Rasulullahi, ka sauke dukkanin sakonka ka yanta mu daga duhu zuwa haske ka cire mana rigar jahilci ka saka mana naka me haske da kamshi, Ya Rasulullahi kace muyiwa Mazajenmu biyayya su kuma su riƙe mu da adalci Ya Rasulullah na kawo kukana gare ka." Ban sani ba ko damuwar Tafida da ne yasa nake surutai ko bakinciki ne yasa nake jin kamar ban isa kome ba,amma zamana a rauhda yasa ni jin sauki da kuma surutai da nayi tayi sai naji kamar na yantu na samu sauki a zuciyata, na roki Allah ya cire min tashin hankali da damuwar Tafida. Har muka gama umara, sannan muka yi sayayya wanda ana jibi zamu bar maka yazo ya watsa min kudi na kalle shi nayi murmushi tare da cewa. "Ni bana bukata, ita wacce ka dauko ka kai mata ta fini bukatarshi ita tana jiran naka ne ni wanda iyaye suka bani ya ishe ni!" Ware idanu yayi tare da shigowa dakin zai hayayako min nace mishi."ina azumi bana faɗa!" Ina fadar haka ya dakata. "ina dakin Allah bana son na tafi na bar zunubi, kaima ina maka fatan shiryar Allah. Domin ka b'ata da yawa." Na fada ina me shigewa ban daki, wanka nayi tare da alola na fita nayi sayayya a kantin da naje sayayya, nayi ta sayan kananun kaya, Allah ya taimaka ina dan iya fahimtar larabci saboda mun yi tajewid, haka na gama sayyana lafiya lau na fito. Har nuna ni larabawa ke yi wai sun sha mamaki da nake iya fahimtar larabci da kuma kokarin da nayi. Turare na sayawa Abba biyu Babana biyu. baba bulama biyu sai Hajiya Kaltuma da Hajiya Salamatu, sai Maman Tafida da na saya mata kaya itama, ina dawowa na same shi a bakin kofar dakina. "Ga kudin nan Abba ya turo na baki wai na kayan sallah ki ne!" Saka hannu nayi na amsa ina faɗin. "Allah ya ƙara mishi lafiya da nisan kwana!" Na shige abina ina me rufe kofar, zama nayi ina nazarin kudin nan idan na canza shi Maman Tafida ya dace na bawa tai ko jari da shi ne gaskiya matar tana bukatar taimako sosai. Ranar da muka bar Makka muka wuce jidda, ina kallon tsiyarsu. Jirgin Maiduguri muka hau amma zai sauke mutane a Kano, haka muka bar kasar cike da kewarshi. Mun isa Kano, daga nan ban kara ganin Sa'adiyya ba, murmushi nayi domin naga sai lokacin ya nutsu da bai da nutsuwa bakiɗaya, haka muka taso bayan mun sha ruwa muka iso Maiduguri Deen yazo ya dauko mu, sai tsiya yake mana wai mu gaya mishi gaskiya ko mun dauko dan Makka da Madinah ne! Ni dai ban ce kome ba, ban san wani irin mutum ne Tafida ba, amma bai iya boyewa Deen matsalarshi. Domin anan ma gaya mishi yayi tare da Sa'adiyya suka tafi Umaran, bayan sallah nan zai gabatar da ita a wurin Alhaji . "Yayi kyau ai, amma ka sani yadda ka saba lalata da ita a waje idan ka shiga cikin gidan ya." "Bana son iskanci wallahi ban tab'a wuce gona da iri ba, iya kata." Sai juyawa muka haɗa idanun ganin murmushin da yake kan fuskana ina sauraron karatun Alqur'ani, domin akwai earpies, shiru yayi yana faɗin."ashe tana jin abu ne!" "In sha Allah sai Allah ya saka mata!" Kafin mu isa gida sunyi fada kaca-kaca kamar zasu daku,. Har cikin gidan Deen ya dauka min kaya, ina jin yana faɗin. "Muje na ajiye miki zan tafi wurin budurwata!" "Kai ba zaka ɗauka min kayana ba!" "Saboda tsine min Ammah tayi?" "Hmm Dan iska!" "Ni bana wuce iyakar Allah!" Ya fada yana shigar da kayanmu, ni kuma na wuce cikin gida, dakin Inna na fara shiga ina faɗin. "Hajiya Innata gani nan!" "Ummu kai ne kazo!" "Eh nice Innata!" "Sannunka Yaron nan Ummu sannu da zuwa!" " yawa Inna! Da fatan an sha ruwa lafiya, mun same ku lafiya?" "Alhamdulillahi, ya Tafida take?" Murmushi nayi ina faɗin. "Duk muna Lafiya!" Sannan na mata sallama na wuce wurin Hajiya Salamatu na gaidata, ta ji dadi sosai. Ina fita na shiga dakin Hajiya Kaltuma, Uwar dakina nan na bararraje muka sha hira kafin na wuce wurin Abba, wasa wasa zai da muka share awa biyu hiran da nasiha yake min. Sannan nayi mishi sai da safe na.dawo bangarena. Dakina da gidan na ga an share min shi tas an goge an gyara ko ina, wanka nayi da ruwa me dumi ina fitowa nayi sallah Magariba da Isha na bi lafiyar gado, da zan yi sahur nayi wani mafarki me ban Mamki, Tafida ne ruwa yake tafiya da shi Ikon Allah hajiyarsu tayi kokarin janyo shi amma ina ruwan yaci karfinsa, ban san ya aka yi na fada ruwn ba na shakka wuyarshi, amma wasu mata da bansan su ba suka hanamu fita, wani katon maciji ya fasa kai yana bude baki, ganin haka yasa nayi ta jan Tafida amma Macijin nan yana bin mu, duk wanda ya nufe mu xan ga macijin nan ya nufe shi baki bude da wannan tashin hankali na farka jikina yana rawa. Ban daki na shiga nayi alola sannan na nufi parlour yana zaune shi da Sa'adiyya, ban yi mamaki ba don naga yana cin abinci, sai hira suke abin su zuwana Umaran nan na koyo shan shayi na fito da dauke da kofin tea domin jiya bayan dawowa na daga cikin gidan Deen ya buga mana kofa ya bashi yace. "Kai bawa Ummu na ta ne!" Don har da Nama yana zuwa ya ajiye min a bakin kofar, wani ikon Allah ban tab'a jin nayi magana akan Abinda yake min ba, haka kwanaki suka zo suka wuce , aka zo bikin sallah nayi abinci na kai, anyi sallah da kwana biyu kamar an bashi ina kwance a dogon kujera ya shigo yana faɗin. "Idan kin gadama ki shirya muje ki ga yan gidanku!" "Da gaske?" Na tambaye shi, "Ni abokin wasanki ne?" Yadda yayi min maganar na fahimci babu wasa da sauri na shiga daki sai ga Ni dauke da katon akwati, na tsarabarsu dama na cirewa Abba da na yan gidan, sannan na daura laffaya. Ina jan akwatin haka muka fita, a waje muka samu Deen ashe har da shi gaban motar ya shiga, "Ummu inji Ammah wai ta gode, abincin sallah sai sun cinye suka hanani. Gashi ko abokaina ban yi musu kome ba, don Allah na kawo cefenen ki musu girki wancan yarinyar ba zata iya fitar dani kunya ba!" "Ka turo ta mana muyi tare sai kace mata tazo na tayata babu dad'i tana matar da zaka aura amma ce ka kawo min abincin da zaka ba abokanka, sannan gasu Jalila ba zaka basu su maka ba?" "Ammah zata min sinasir, Jalila me ta iya ban da iyayi." "Shi kenan!" Na fada ina dariya, haka muka isa gidanmu, Wayyo dadi tunda muka shiga cikin gidan, na nufi parlour Baba na gaishe shi tare da Tafida, sannan na wuce wurin bangaren Ummi na gaida ta ita da Umma kafin na wuce bangaren mu, ina shiga na ga irin kallon da Tafida yake yiwa bangaren mu, kamar ya ga kashi. Mama kuwa sai hidima take mishi, Deen sai godiya yake mata. A yau nakara jin wani irin tsanar Tafida, domin babu dan da za a yiwa iyayenshi haka ya ji dadi. Ko ruwa bai sha ba ashe bani daya abin ya dama ba,.har da Deen. Suna gama gaisawa ya fita Deen ya zauna yaci abinda aka ajiye musu, ya ce mata. "Mamanmu ni fa zan tafi da kayan dadin nan wallahi!" " za a zuba maka ka tafi da shi!" Nan ya sake narkewa da murna, ita kanta Mama ta ji dadin Deen domin ta fahimci abokin Aliyu ne na amana. Bayan ya gama ya fita nima muka yi ta hira, na tura mata tsaraban ina mata bayani, ta amsa tayi godiya ta kuma ce zata raba gobe in sha Allah, "maza tashi ku tafi Allah ya miki albarka." "Amin Mamana " haka ta zuba min kayan ciye-ciye, na fito da shi, anan take gaya min ai Uwani ta tafi sallah gida , nayi fatan Allah ya dawo da ita lafiya haka muka bar gidan, tun a mota Deen yake faɗin. "Ummu Mamana ta ce min zata baki kayan dadina!" "Da dai kayi hakuri muje gida na diba maka!" "A'a gudun kada a sake samun dan fashin da yake juye nama ya kuma juye min kayan dadina ne wallahi ba zan yarda ba!" Ashe ya gaya mishi ya juye min nama, mutum sam babu sirri koda yake na lura tsakaninsu su biyun nan babu sirri suna gayawa juna kome, idan ka cire Mahmoud da basu irin wannan maganar da shi. Koda muka dawo na diba mishi nashi ya tafi, na bari a kitchen ina fitowa na samu ya dibo ya zuba a flat suna ci da Sa'adiyya sai santi take. Washi gari na kara kiran Mama na gaya mata ina son turaren wuta zan kaiwa Tina da yan uwanta da kawayenta, ta ce zata saya min a wurin Ummi. Kwana biyu Abba ya ce na shirya Tafida zai kai ni Biu. Haka na roki Hajiya Kaltuma ta bani aron Nabila muka shiga kasuwa nayiwa Babana sayayya, muka yi cin-cin da cake. Sai nama wanda Abba ya bamu na sallah na soya na saka rabi a firji domin a zaman shekara kusan daya na gano lagon Tafida yana son nama kamar yayi hauka, zai iya cin nama da bread ya sha ruwa ya koshi, don haka na saka mishi wani a langa tsirara. Da kanshi da rakiyar Deen ya kai ni har kofar gidanmu, wannan karon an karbe shi a matsayin d'a ne da zai tafi ba karamin hidima aka mishi ba, Babana har kudin mai ya bashi ya mishi alkawarin zai saka a kawo ni har gida, haka kuwa aka yi na kwana biyu a garin Biu, mahaifina da danginsa kamar su lashe ni domin duk abinda na kawo ya saka an rabawa dangi kaf sai kaɗan Mamawo ta ajiye mishi, nima da zan dawo kamar wacce nace musu bani da kayan abinci, kuka, kubewa busashe, barkono, albasa, daddawa, garin kunu me kyau, kai tsaraba sai da aka cika min bayan mota da shi, kaji kuwa yanka min su aka yo aka gyara aka fasa ƙanƙara a kai, domin nace dambu zan yi. Mun iso da la'asar ban huta ba na hada wuta na daura dambu. Ya kwana washi gari na tuke shi tass. Alhaji ya kara turo min da nama danye yace na soyawa Tafida, haka na dafa na soya shi cikin langa tsirara, Mama tayi min cin-cin da kayan ciye-ciye sosai domin wannan karon mota zamu bi, sai da na gyara gidana na cirewa yan gidan tsarabansu ana gobe zamu tafi da dare Aunty Rukayya ta zo, ina jin yana gayawa mata shi ya gaji da bin shi da zan yi yayi magana Abba ya fara faɗa. Shine ta shigo dakin ina zaune da littafin addu'a. "Ummu Hadiyya ki gayawa Abba ba zaki bishi ba, don ai wannan takura ne ke baki ji kunya ki bishi ba." D'ago kai nayi na kalleta kafin nace mata. "Aunty Rukayya ke me zai hana ki samu Abban da kanki!" "Ni sa'anki ne?" "A'a na gaya miki abin da ba zaki iya ba tow nima ba zan iya ba, ba haka aka koya min ba, ba a nuna min musu da babba ba!" Fita tayi jikinta a sake, can ya shigo.ya fara zagina ina ga Sa'adiyya tana parlourn don naji muryanta Aunty Rukayya tana bata labarin har ya gama ban d'ago kai na kalle shi ba, yana fita na rufe kofata. Jin Muryan Deen yasa ni fita muka gaisa nace mishi. "Don Allah ina son magana da kai idan da hali!" "Ok!" Ya tashi muka fita waje mika mishi kudi nayi nace mishi. "Don Allah ga number Mamanshi ka tura mata kudin nan, " "ke kika yi niyya ko tambayarki tayi?" Murmushi nayi nace mishi, "Bata tambaye ni ba idan ka canza a tura mata don Allah!" "Allah ya tsare gabanki da bayanki, lallai na yarda akwai abinda Abba ya hango ne." Amsa yayi ya saka a aljuhun shi, koda ya koma ciki share shi Tafida yayi wai akan ya kula ni hala, shi kuwa dan ya kular da shi sai dariya yake irin na niman fada.. da fada suka rabu, washi gari muka bar Maiduguri da assuban fari ana kiran assalatu, wannan dawowar da nayi abuja ya saka ni jin na tsani kome na duniyar nan, ya sakani cikin tsoro da wani irin fargaba. Domin kuwa Tafida ya barni ina rayuwa kamar bani da yanci. Tunda muka dawo Mahmoud ya saka ni a gaba ko a ina ya samu numberta kullum sako kullum kiran waya, idan nayi blocking dinsa zai kuma kirana da wani layin. Tun ina daurewa har wata rana kira Deen ina kuka na gaya mishi Mahmoud ya dame ni, don Allah ya saka baki Tafida ya sake ni, har abuja Deen.yazo Ashe ya nimo Mahmoud ne ya mishi dan banza duka, ina wannan bai ishe Mahmoud ba sai da ya saka Tafida ya dawo dashi gidan wai da sunan jinya...............Babban al'amari ne.... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 16 Tunda Mahmoud ya dawo gidan da jinya, na shiga wani irin takura wanda tunda nake ban tab'a ganin irinsa ba, dama gidan daki biyu kuma kowanne da bandaki a cikinsa sai ban daki a parlour haka yasa ko su tinah a ban dakin waje suke yin uzurinsu, ni kuma ina dakina shi ma Tafida haka, sannan a yan kwanakin nan ina fita taron kafin Onga haka yasa bani da lokacin da zan huta sai asbar da lahadi, wanda bakiɗaya Mahmoud zama yake a parlour har na kasa fita, idan na fita kitchen duk motsina idanunshi yana kaina, wuraren Kirsimeti, Tina ta dawo daga course din da ta tafi, tunda tazo na karanci fuskarta ganin Mahmoud bai mata. Bata nuna min ba har ta tafi. Washi gari Tafida yana office dinsa ta shiga Hannunta harde a kirjinta. "Aliyu Tafida!" "Yes My Love sannu da zuwa zauna." "No tambaya daya nazo maka zuwa biyu!" D'ago kai yayi ya zuba mata idanun ta sake murmushi. "Meye alakarka da gayen nan da yake gidanka?" "Abokina ne tun na yaranta!" "Babu kada blood related da shi?" "Ko daya na gaya miki tare muka taso?" "Kai muslumin kwarai ne kuwa?" Kura mata idanu yayi cikin gajiya da maganarta. "Ban fahimta ba?" Ya tambaye ta. "Addinin Musulunci ya ce ka ƙare darajar Matarka da kimarta, sannan kada ku bari waɗanda basu da related daku su zauna a cikin gidajenku, gujewa haduwar Baligi da baliga, a Suratu Nur da Suratu Nisa'i Allah ya rarrabe hukunce-hukunce akan matayenku da Yaranku da Yan uwanku mata da yan uwan Iyayenku mata da maza haka ne?" Zama tai a kujeran office din tana murmushi ganin yadda yake zaro idanu. "Sannan na ga wasu daga Islamic scholar irin Malik, Abuhanifa, Bukhari da Muslim sun kawo hadisai Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, akan matayenku da abokan." "Tinah go to the point, ki daina dukar Tanti bayan ga jaki." "Last abinda na gani a wani hadisin wani mutum ya zo wurin Manzon Allah yake gaya mishi yafi kowa kishi." "Tina na gaji gaya min me fitar da ni a musulunci? Da kike tambaya ta anya ni Muslim ne?" "Wancan gayen da ka bari a cikin gidanka haramun ne domin idan yayi yunkurin rape Ummu fa?" Hadiye yawu yayi makwat. "Kina hauka ne? Taya Mahmoud zai aikata haka, abokina ne. Kuma bai da inda zai yi jinya sai gidana!" "Bana hauka amma idan ya tab'a Ummu zan tabbatar da daga kai har shi kun yi danasani na rantse maka da Allah!" Ta mike tare da fita tana me buga kofar office din. Tsaki yayi ya kira Number Mahmoud a kashe.. ** Dama jiya nayi azumi Alhamis, wanda yasa na shigo da wuka dakina da su lemo da safe naje dauka ina sauri zan yi abin karyawa, wukar ta fadi ban tsaya dauka ba na nufi kitchen na fara daura abin karyawa, domin Tafida, ina gamawa na wuce daki na bar musu ina jin suna karyawa har Mahmoud din yana fada mishi. "Yau xan tafi fa!" "A'a ka bari ka warware bakiɗaya." "A'a zaka iya dawowa ka samu na tafi don na warke!" Y fada daga nan ban kuma sanin ya suka kare ba, ina gama karyawa na kwanta abuna, sai wurin karfe goma na farka na shiga ban daki nayi wanka, ina fitowa na daure da Babban towel. Na nufi wurin kayana da yake kan gado, turo kofar aka yi na juya da sauri Mahmoud tsirara haihuwar Uwarshi da ubanshi da sauri na juya tare da ɗaukar hijab dina na fara kokarin sakawa, ji nayi an cira ni sama tare da watsa ni kan gado. Na fasa wata irin ƙara. Nan ya shiga kokarin cire min hijab dina, muka shiga kokuwa da shi har Allah ya bani sa'a na ture shi tare da tashi da sauri xan fita ya riko kafana, ya ja ni na fadi towel din jikina ya so ya fadi. Na rike da karfi idanuna.ya kai kan wukar nan cikin sauri na ja wukar na yanki gefen hannunshi da ita da sauri ya sake ni yana faɗin. "Kika yanke ni?" "Idan ka iso gare ni sai na kashe ka!" Na fada ina kauda kaina daga gare shi, hijab Dina yana can ƙasa. "Ummu ki yarda mu yi wanann al'amarin cikin sauki hada jikina da ke yasa ina ta xubar da ruwan sha'awar na gaya miki ba zan cutar dake ba, zan rage miki aikin da wancan lusarin ya kasa ne shine kika yanke ni!" Ya nufo ni da sauri kara rike wukar nayi ina nuna mishi, abinka da namiji yana zaune ya buge wukar da karfi wanda yayi sanadin faduwata, jan towel din yayi da karfi ya zame kasa. "ashe ba gizo nake gani ba,.sune a tsaye waw!" Ya kai hannu zai tab'a min na daddage na gwara mishi goshina a fuskarshi abin da yayi sanadin faduwarshi da gudu na shiga ban daki, towel din ya fadi can na rufe kofar da key. Na zube a ban dakin ina wani irin kuka, shi kuwa sai buga kofar ban dakin yake amma naki budewa. Haushi yau ya samu dama amma Ummu ta hana shi yasa shi dukar kofar toilet din da kafarshi, sannan ya fita yana faɗin. "Duk ranar da na kama ki sai na cika kudirina a kanki!" Ban tab'a shiga tashin hankali a rayuwata irin wannan lokacin ba, na ji garin Abuja ya min zafi, naji bakiɗaya kome ya min zafi na tsani kaina na tsani Aliyu da ya kawo ni. Nayi kuka kamar raina zai bar gangan jikina. Sai da nayi awa uku a ban daki kafin na fito na gyara banyi tare da hada kayana bakiɗaya, karfe uku saura ne, na fito parlour ya b'aci da jini haka na goge tare da saka turaren wuta, sannan na sauke salolin kaina, na kwanta a dakin saboda tashin hankali ko ruwa ban kai bakina ba wunin ranar, koda Tafida ya dawo bai bi kaina ba, tunda ya leka kitchen ya ga babu alamar abinci ya yi wanka ya fita a gidan bai kara dawowa ba sai goman dare. Washi gari tun karfe biyar na asuba na bar gidan, yana can ko ya tashi ko bai tashi ba, abin da na sani na bar gidanshi kome zai faru sai dai ya faru, karfe shida muka bar Abuja, na kashe wayata. Tun lokacin ban kuma samun nutsuwa ba, sai karfe sha biyu da muka iso Bauchi, daga nan muka nufi fataskun, wurin karfe hudu muka yi sallah azahar da la'asar, sannan muka dauki hanyar Maiduguri, wanda shima koda muka isa bakin get an rufe, domin karfe bakwai muka isa, anan muka kwana. ** Abuja Tunda yayi sallah asuba sama-sama yake jin motsi daga baya barci yayi gaba da shi, bai farka ba sai karfe takwas, ya duba agogo wayar shi, da sauri ya nufi ban daki yayi wanka sannan ya fito ya shirya tsaf, haka kawai yake jin gidan kamar babu kowa don haka ya fito parlour ya daidai ne babu abin ya sauya, bai nemi abin karyawa ba ya fita, a office ya tura aka kawo mishi abin karyawa duk da haka ya ci ne amma dan sabo da yayi da abincin ta yasa shi fahimtar ita gwana ce a wurin girki. Yau yayi alƙawarin sai ya ci abincin dare. Lokacin da ya dawo gida bai ga alamar tayi abinci ba anan ne ya fahimci ba ta gidan ne fa, ya kira Tinah ya tambaye ta Ummu tana tare da ita ne? Ta ce a'a bata zo ba, zufa ne ya karyo mishi, ya kara kiran Tinah ko wasa take mishi nan ta rantse idan bai yarda ba yazo gidansu. Sannan itama ta gwada kiran Ummu wayar a kashe. Ta gaya mishi Deen ya kira ya gaya mishi Ummu ta b'ata. "Wacce irin magana ce haka? Ummu ta b'ata kamar wata yar kaza?" "Wallahi na gaya maka da gaske Ummu bata nan!" Shiru yayi kafin ya ce mishi. "Ka tambayi Tinah?" "Eh basu tare!" "In sha Allah tana hanyar gida, domin nasan wacce irin mutum ce ba zata tsaya a wani wurin ba gida zata tawo, sannan nima zan tafi gate na jira zuwanta." "Don Allah kada ka gayawa Alhajinmu idan ka same ta ka gaya min " "Ok!" Haka suka yi sallama amma hankalinsa yayi dubu ta tashi, domin wannan shine karon farko da yaji tashin hankali da rikicewa, ba tare da ya fahimci haka ba, ya kira Deen yana tambayar shi ko an dace. Amma shiru Deen kuwa haka yayi ta bin tasha yana niman Ummu , daga karshe ya samu labarin akwai wasu motoccin da aka tare ba zasu shigo ba sai gobe, tafiya yayi can ya zauna, har tsakiyar dare Tafida bai kyale shi ba, karshe sai da suka yi fada ya cewa Tafida. "Dan iska kasan ka damu da ita kayi ta shuka mata rashin mutunci, banza dan iska!" "Ni fa bana gida na barta da Mahmoud ne zai bar gari bayan nan shima na nime shi ban same shi ba wallahi ban mata kome ba tow dama me nake mata idan ba sharri zaka min ba." Kusan kwana zaune suka yi shi da Deen, asuban fari aka bude kofar, Deen ya shiga bin motoccin da suke parke. Ina sallah naji ana tambayar wacce Ummu Hadiyya, sai buga jikina nayi alamar nice, wata matar kusa dani ta ce musu. "Kamar gata tana sallah tayi alama!" "Mai gida gata nan an same ta." Sai da nayi sallama gabana ya fadi ba dai Tafida ba ne, a hankali na d'ago kaina ina kallon Deen a cikin dan duhu-duhu. "Ummu Hadiyya!" "Na'am!" Na amsa ina mikewa, "Malam sauke min kayanta zamu wuce!" Haka suka taso ni a gaba na nuna musu kayana, Deen ya dauka ya saka min a motar shi, baya ya bude min na shiga na zauna. Sai lokacin kuka yazo min. "Ina zan kai ki?" "Wurin Ammah!" Kallona yayi ta glass din motar, sannan ya cigaba da tuki. Gidansu ya kai ni, wurin Mamanshi. Tunda na shiga dakinta nake kuka, "ya isa haka mana Ummu kanki zai yi ciwo!" "Kyaleta tayi idan tayi zata ji sauki, zata kuma manta da kome, idan bta yi ba zai zame mata ciwo a ranta har zuwa mutuwarta barta tayi kukanta shi kuka ba ragwanta ba ne, jarumtace da juriya ke kawo shi duk wanda zai yi kuka zai manta abun da aka mishi, barta ta rage nauyin da yake ranta haka kadai zai bata damar fuskantar wacece ita wacce duniyar take raye!" Nayi kukan da ko a gaban Mama ba zan iya shi ba,haka yasa Deen ya zuba min idanun yana me tambayata. "Tafida ne ko Mahmoud?" Da sauri na kalle shi ina tsannanta kukana tare da girgiza kai. "Gaya min waye ne a cikinsu?" Cikin shashekar kuka na ce mishi. "Na barsu da Allah!" Jin haka ya kira sunana kamar zai yi kuka. "Kika ce kin bar wa Allah?" Gyada kai nayi, bayan na zauna tare da dunkulewa wuri guda, na cusa kaina a tsakanin cinyoyina. "Ummu me kike so?" "Kace tafida ya sake ni, kafin wata rana na wayi gari a wulakance." "In sha Allah ba zaki wulakanta ba." Inji Ammah, bayan Deen babu wanda yasan ina Maiduguri, kai washi gari sai ga Tafida, a wannan abin na hango sanyi a tare da shi, nan yayi ta bawa Ammah hakuri yana fada mata bai san me ya faru ba, don Allah ta rufa mishi asiri kada Abbanshi yasan yazo. Abu daya Ammah tace mishi. "Zan yi hakuri amma ka sani dole zan na turo wani zuwa Abuja ya ga irin zaman da kuke ko na gaya Alhaji Muhammad Jadda!" A kade ya ce mata. "Ban gane ba Ammah?" "Nufina tunda kana tara yan iska a gidanka zan gayawa Alhaji Muhammad Jadda, cewa ka mai da gidanka hotel wurin saukar yan iska, sannan ya je ya ga irin zaman tozarci da kake da Ummu Hadiyya!" Kamar zai kwanta a kasa ya ce. "Wallahi daga yau zan zauna lafiya da Ummu lafiya!" "Ban yarda ba, nasan waye kai da taurin kai!" "Na rantse da Allah." Ba wasa Ammah ta fara wanke shi kamar yadda Deen ya gaya mata, a ranar sai da yaji kunya ya kama shi. Haka ta ce mishi ya tafi ya bata wuri ta ma fasa na koma wurinshi, kawai zata kai ni wurin Abbanshi ne. Kamar yayi hauka domin san Abbanshi ya mishi alkawarin. Duk ranar da Ummu tazo da kukan ya zalince ta har abada bashi ba kara aure ko na wacce mace ce, balle Sa'adiyya shi yasa yake shakkar Abbansu yaji labarin nan, sannan yasan kome na shi zai koma baya ne. ** Tun daga Maiduguri har jibiya na garin Katsina suka isa. Can wani kauyen jibiyar suka shiga ciki. Shafa kasar yayi da yake katon tire yana shafa farin gemunsa. "Yaron nan tun fil azal babu aikinku da yake kama shi, har abada ba zai kama shi ba domin Uwarshi tana tsaye akanshi, yana biye muku ne saboda kece kika tsaya mishi da abinci lokacin da yake jin yunwa. Sannan na kara gaya miki kaf duniya babu wanda ya isa mishi wani abu domin Uwarshi tana sauke numfashinta ne da bugun zuciyarta. Hindu ko?" Ya kuma tambayarta sannan ya gyara zama yana kallon Sa'adiyya. "Bari naga muku gaskiya, ƙaddaran yarki yana kusa da shine, amma shi ƙaddaranshi yarinyar ce, kuma kin san me? Shi din babban mutum ne nan gaban, zata iya aurenshi taci arzikin shi amma... lokaci ne zai gaya muku haka bokaye malamai irina, ba zasu iya muku kome ba domin Tafida kainuwa ne dashen Allah, zaki iya zama da shi domin ki ci arzikin shi amma ba wai yadda kike tsammani, idan zaki yi nasara sai dai akan Yan uwan shi da yan gidan amma akan Tafida. " wannan abin ya d'aga mata hankali. Don haka ta sauke ajiyar zuciya, tana faɗin. "Tow yanzu zamu tafi daga baya mu dawo." "Zaki tafi Nijar ne, a can za a hadaki da wani boka wanda kafin ya miki aiki sai ya kwanta da yarki," dariya yayi ya fada mata siffar matar da ta gaya mata bokan da kome sannan ya shafa kan tirenshi yana faɗin. "Kaf duniya babu wanda zai miki aiki ya kama Tafida na rantse da Allah, sannan idan kika sake yarki ta kwanta da shi, daga ranar ko auren Tafida sai ya mata wahala, gara ta samu kan yan uwanshi su saka shi a gaba yadda zai kula da lamarinta amma kika bari wani ya kwanta da ita kusa da Tafida ma ba zata samu tsayawa ba." Kai karewa sai da ya gaya mata kome hatta fadar Ummu da Tafida, ya ce mata yanzu haka Tafida yana Maiduguri, sannan Ummu tana gidan abokin Tafida idan karya ne ta kira Tafida zai gaya mata. Ai kuwa kamar yankar wuka.haka ta kira shi ta gaya mata yana Maiduguri sun samu matsala ne da Ummu, bayan ta mishi fatan Allah ya daidaita su. Ta kashe wayar tana kallon malamin ya gyara zama.ya ce mata."abin da yasa Tafida ya biyo ta saboda Ubanshi yace masa matukar Ummu ta kawo karan shi har abada ba zai auri yarki ba, ƙaddaran yarki tana kusa shi ban san me zai faru ba amma ki koma lokaci na zuba da zai auri yarki kada ki sake ki rasa damarki na moran arzikin da kika tsaya ya ginu ta sanadin ki.... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* Paid book 17 Ammah tayiwa Tafida wulakncin da bai tab'a zata ba, domin ta kuma rantse matuƙar bai gyara ba Abba zai ji, kwananmu biyar muka juya Abuja, Ammah tai min nasiha tare da nuna min na rungumi Aurena nayi hakuri kada na dogara da shi, Ammah bata san tuni na wuce wannan matakin ba, sannan ta ce tsakaninsu da su Deen su hadu a wurin aiki, wai a haka ban gaya mata kome ba, sannan ta ce mana tana nan zuwa kada muyi tsammanin zata gaya mana ranar zuwa zamu ganta ne kamar diran yesu, sannan ko kallon banza ya min nayi mata magana zata tambaye shi Hujja, haka muka isa Abuja lafiya lau. Sai dai muna isa madadin ya gyara halinsa sai ya karo rashin mutunci sama da baya ma, iskanci da tozarci sai naji me yasa ma na tafi Maiduguri, kullum ina cikin kuka da tashin hankali, domin na fahimci Tafida indai ba Abba ba ne zai zauna a gidanmu babu dalilin da zai saka ya kyale ni. Yadda yake zabura idan yana fada sai na koma da baya domin kamar zai buge ni haka yake ji, dalilin da yasa na kama kaina na kara nutsuwa, dayawan mutane suna faɗin idan aure yana sauya mutum wani ikon Allah sai gashi gidan na cire class da nake aiki a wurin koyar da girki na yi wani irin sanyi wanda ko magana kai yi min zan iya samun kaina da jin tsoronka. Dama can halina ne rashin son hayaniya da kwaranniyya, haka ya ƙara samar min da wata irin nutsuwa, wasa wasa kamfanin da suka dauke ni aiki suka tab'a gayyatatta nayi zuwa Lagos, akan wani festival na girke-girken Africa. Yana kwance a parlour na shigo gidan a gajiye ya amsa Sallama da nayi bai amsa ba, ni dai ban sani ba na ajiye jakata na shiga kitchen, a gurguje nayi na gama taliya da miya amma yau nayi mamakin yadda na same shi a gidan. haka na shiga dakina nayi wanka kakarinsa na ji, na fito yana ta amai yana rike cikinsa. "Subhanalillahi Ya Tafida naka da lafiya ne?" Gyada kai yayi yana amai, haka na dauko abin mofin da parka na kwashe sannan na gyara mishi inda ya bata. Hadiye yawu nayi tare da zazzare idanu. "Ko zaka tashi ka cire kayanka, na wanke maka su ka b'ata su." "Ummu ba zan iya tashi ba!" Ware idanu nayi cikin tashin hankali. "Ba zaka.." matsawa nayi na dafe goshinsa rau yana kuna da zazzaɓi. "Bari na cire maka!" Na fara ƙoƙarin cire mishi amma na kasa, abun da na sani tafida dogo ne me kauri da fadi, sannan duk wannan kokarin da nake kallona kawai yake ganin yadda nake kokarin cire mishi rigar na kasa sai shawagi nake a gabanshi, ya sa shi cewa. "Tsaya na gwada" a hankali ya cire rigar sau daya na kalli kirjinsa wanda yake cire da wasu irin gargasa, sai ji nayi jikina yana rawa, na tattara rigar na bar wurin dakina na wuce na zuba a banɗakin na shiga wankewa. Bayan na gama na fito na samu yana rawan sanyi. "Muje na taimaka maka " haka na isa gabanshi Dakyar ya mike muka tafi dakinshi amma ji nake kamar na dauke shi yadda ya sake min ragamar jikinshi. Haka ya zube a saman gadonshi, na gyara mishi kwanciya. "Me zaka ci?" Na tambaye shi, "Babu!" "A'a ba zaka zauna da ciwo haka ba!" A wannan lokacin na tsaya sosai akan shi domin nice dai a kusa da shi. Sai da ya kwashe kwana shida, har Tinah tazo tana tambayata ya maganar tafiya wata sati kuma an ji ni shiru. "Kin ga Ya Tafida bai da lafiya, ba dad'i na tafi na barshi idan lokacin tafiyar yayi bai warke ba su yi hakuri ciwo na gaba da kome, kuma ban gaya mishi ba kin ga kenan dole na hakura." "Amma" saurin dakatar da ita nayi ta hanyar cewa. "Ki bar maganar bani da ra'ayi a tafiyar ne shi yasa na tsaya jinyarshi." Duk tozarci da yake min ta sani amma tayi mamakin yadda na hakura da nawa damar da na samu saboda jinyarshi. "Matan aure kenan kuna da kirki da sadaukar da kome domin mazajenku" murmushi nayi na ina faɗin. "Aure ba abin wasa ba ne, idan kayi wasa da aure Allah ba zai Barka ba, kada ka cutar da aure domin shi ne mafi girman kuskuren da ake aikatawa, sannan shi auren Ibada ce bakiɗayansa." Ashe duk hiranmu yana ji, domin ya fita wajen wurin Motarshi, ta window kitchen yake jin mu. "Amma Ummu kina son mijinki ko?" Kallonta nayi a rayuwata bana jin akwai tambayar da take matukar bani wahala kamar kina son Mijinki, shiru nayi na ce mata. "Dama nace miki bana sonshi ne? Mijina ne kuma Yayana,sannan kuma dan uwa ne a musulunci." "Ba wanann tambayar na miki ba, domin na sansu shin kina sonshi na soyayya da rayuwa?" Shiru nayi ina kallon sama kafin na ce mata. "Wannan tambayar naki yayi tsauri dayawa bani wuri na wuce " dariya ta saka min tana faɗin. "silly girl!" Haka muka gama abincin rana alale da kunu muka dawo parlour, sai lokacin ya shigo yaga muna cin abincin. "Ya Tafida na kawo maka daki ne?" Na tambaye shi ina mikewa, "A a anan yayi kawo min nan!" Zan iya cewa a kwanakin da nayi ina jinyarshi, na sha azaba domin taimaka mishi ya saka kaya ma aiki ne. Wani abun da ya kara bani tsoro, shine yadda jikinshi yake tare da kai hannun shi cikina ko ya ya tab'a min kirji, ganin haka na fara baya baya, idan yace na rike shi nayi ta ɗan jan baya kenan ina dan nazarin taimaka mishi. Zama yayi yana faɗin. "Kada ki cigaba da tambayarta wasu abubuwan, Please." "Kana tsoron kada tace bata sonka ne? Ai na hango ka shi yasa nayi mata tambayar, yanzu ma ba haka ba maganar tafiyarta Lagos ka ware ka barta ta je!" "Zamuje tare!" "Ka fara sonta ne?" "Ina ga wannan ba matsalarki ba ne! Na sota ko na kita choice dina ne!" Haka na kawo mishi abinci na wuce dakinsa na dauko maganin anan na lura da dakin yayi datti na zauna na gama cin abincin sannan nace mata. ,"bari na duba dakinshi!" Na shiga duk da naga yadda ya kafe ni da idanun haka yasa na shiga da sauri na shiga gyarawa. "Tana da kirki da sanin ya kamata, matarka ce kana da damar gyara kome." "Jira ni mu fita tare zan tafi asibiti!" Ya fada mata yana me nufar dakin, na zage ina wanke ban dakin na ji shi a kaina yana gyaran murya, da sauri na d'ago kai. "Wanka xan yi ko zaki bani wuri!" Ya fada yana wani haɗe rai. "Ba damuwa na" na fada da sauri ina barin ban dakin, wanka yayi yana kara jin zazzaɓin yana dawo mishi. Sannan ya fito ya shirya muna tare da ita a parlour. Ya fito cikin farin material na maza, rigar kenan wandon Black kaftani ne me ɗaukar idanu, duk da ya rame amma kyan shi ya kara fitowa sosai. "Zan tafi amma maganar tafiyar tana nan?" "Ba zan samu zuwa ba!" Na fada mata ina murmushi, fita tayi yana bin bayanta, asibitin a unguwar yake ta kai shi ta wuce shi kuma ya wuce cikin asibitin. Yana shiga suka hadu da likitan dake sun san juna. Haka ya shiga ya zauna Abokin yana kallonshi ya ce mishi. "Ya jikin naka?" "Da sauki amma kuma!" Gyara zama yayi yana faɗin. "A yan kwanakin nan ina fama da matsanancin bukatar mace, abin da ban tab'a ji ba." "Ina Madam take!" Gyara zama yayi kafin ya shafa kanshi. "Matsalar daga ita ce, tunda ta fara kulawa da lafiyata nake jin kamar akwai wani abu a tare da ita, da tana kusanto ni zan ji kamar na tab'a kirjinta." "Aliyu kasan matsalarka tun wancan jinyar da kai. Kana bukatar mace kuma itama mace ce." "Habib ba wai naki ba ne, a yadda nake ji kamar idan na same ta zan iya rabata gida biyu ne, ita kuma tayi kankantar da ina ga ko wucewa ba zan iya ba,.shi yasa idan na samu dama nake son na auri Sa'adiyya!" Kallonshi yayi kafin ya ce mishi. "Tafida kenan Ita matarka da kake ganin ba zata iya da kai ba, irinsu ne suke bada mamaki, sannan xan baka magani da zai rage maka zazzaɓin ita Sa'adiyya babbar mace yaushe zaka aurota!" Jingina yayi da kujeran yana murmushi ya ce mishi. "Abba yaki amincewa!" "Ya kyauta wallahi!" Ya cigaba da rubutu. "Kafin kayi magana akan mutum ka fara sanin waye shi, ita Yarinyar da ka rena ba zata iya daukarka ba, ka bincika ka ji tarihinta? Sannan ita wacce zata dauke ka kaji wacece ita? Aliyu kada ka so kanka dayawa, duk wata mace tana daukar bukatar namiji daidai da yadda yazo mata kai kuma ɗan kutumar abin da Malam ya hana fada kana gaya min ba zata dauke ka ba,kai din banza abinka da bai kai a matsayin wanda zai fito ta bakin mace ba." Ganin tozarcin Habib yasa shi ya kama dariya, yana kallon shi. "Ita mace matukar ba kai ne ka lalata ba, babu abin da zaka rasa a tare da ita balle kuma irin matarka ka kamar kayan hada abinci suke idan babu su babu dandanon ba zaka gane haka ba sai ranar da ka ajiye su zuwa biyu anan zaka fahimci haka." "Ni rubuta min magani na fita kafin ka lalata min tarbiyyar da nake da shi!" Tsaki Dr Habib yayi ya rubuta mishi magani, sannan ya fito ya saya kana ya bar asibitin, a hankali yake tafiya har ya ya isa gidan. Ina wanka na ji ana buga kofar da sauri na gama na fito, tare da saka Hijab kato, naxo na bude kofar yana tsaye. "Uban me kike nake ta buga kofar gidan?" "Kayi hakuri wanka nake?" "Wankan baki asarar ruwa kenan ko yayi ma kamar bai yi ba! Ke ki daina wannan wahalar domin ba wani burgewa zaki yi ba " kasa nayi da kaina na matsa ya shiga na wuce ban daki, sai kaji kamar gaskiya ya fada ko nayi wankar ai ba fatar xan sake ba. Hadiye yawu nayi domin dai ba zan yi bleaching saboda shi ba. Haka na dauraye jikina na fito zuwa dakina. Ina tsaye daure da Towel ina niman kayan da zan saka ya shigo dakin. " da sauri na juya abinda ya faru kwanakin baya ya dawo min da sauri na ja da baya, kallona yayi daga sama zuwa kasa idanun shi ya dauka kan kafaffuna, gyada kai yayi kafin ya tako har zuwa inda nake ni kuma ina komawa da baya. "Nazo ganin me yasa nake jin na tab'a kirjinki!" Baya nayi da sauri ina me k'amkame towel din kamar xan yi kuka. "Cire towel din na ganki da kyau!" Girgiza mishi kai nayi ina kokarin gudu zuwa banɗaki sai ji nayi ya saka min kafa na fadi can, takowa yayi yana kokarin mikewa ya damke towel din da karfi ya raba ni da kasa, kan gadon ya wurgani sai da gadon yayi wani irin ƙara, "don Allah kada ka min haka!" "Kada ki bata min lokaci kawai kallon abin zan yi na wuce!" Ya janye towel din da karfin tsiya rintsa idanuna nayi da ƙarfi, idanunshi a kan kirjina zuwa cikina. Hannunshi ya kai kan cinyata ya fara kokarin kallon gefen dama da hagu, kafin ya kai hannunshi tsakanin cinyoyina, da sauri na rike hannunshi ina jin kamar na fashe da kuka. "Don Allah kada ka min haka!" "Ke kamar takalmina ne, na saka shi lokacin da yayi min don haka na zo na yi gwajin takalmi ne naji ko zan shure shi duk lokacin da na shirya!" Mikewa nayi tare da ture shi ya janyo kafana tare da min rufa bayan ya danne hannayena da na shi. "Kada ki saka ni nayi abin da ban yi niyya ba nazo na gaya miki ne gobe zamu tafi Lagos don haka daki ɗaya zamu kwana. Daga yau kuma kin daina kwanan ke daya dai dakina wannan shine karshen abin da zan gaya miki."ya fada yana me kai hannunshi cikin wani irin yanayi da ban san shi ba, yana min tafiyar tsutsa akan cikina. "Don Allah ka bari, ka ji don Allah ka daina bana so." Hannunshi naji a wani wurin da nan zata ba, rintsa idanuna nayi ina ji kamar numfashina zai bar gangan jikina. A hankali jikina ya dauki rawa ban san lokacin da na fashe da kuka ba. "Don Allah nace ka daina!" Na fada da karfi wanda ya dawo da shi hayacinsa. Da sauri ya cire hannunshi da ya b'ata share min yayi a jikina na fashe da kuka, haka.ya mike ya bar dakin, tunda ya fita anan wurin ya bar ni cikin tashin hankali. Ban yarda na kuma haduwa da shi ba, washi gari ma haka ya saka ni a gaba muka bar Abuja zuwa Lagos sai dai har lokacin bani da nutsuwata, kuma shima ya gane haka. Sau dayawa Sa'adiyya tana son yayi mata, amma yake ki, idan bai yi ba kwana take tana juyi a gado, Sa'adiyya ita ce dalilin ciwonsa na farko na biyu nan ma haka domin akwai wani gidan cin abinci da suke yawan haduwa, duk da ya hanata zuwa gidanshi, haka bai haka shi kama mata daki anan garin Abujan ba, idan suka hadu tayi ta jarababshi da ya matseta shi kuma yana gudun abin da xai faru don yasan haramun ne. Haka zai jagwalgwalata, har sai yaga ta nutsu, ba zai ce ba amma tabbas akwai abin da ta bashi da jikinshi baya so wanda ya haifar mishi da rashin lafiya domin wani irin jaraba yake ji amma wani ikon Allah duk da haka baya nimanta, na wannan karon da yaji abin sau biyu yana ganin likitan shi yana bashi shawara, na karshen ne ya gaya mishi ya nime Ummu su daidaita amma karshe ya kare da hakan. Tafida ya ci alwashin sai ya biya bukatarshi kafin ya ji a ranshi yana da wata bukatar domin duk abinda Sa'adiyya take saka shi yu duk ya ajiye akan Ummu zai sauke. Koda muka isa lagos Tafida bai boye min ba, jikina yake so ya tab'a na shiga tashin hankali kamar zan gudu haka na daure, daki daya muke kwana ina kasa yana gado.amma zan farka naji ya mai da ni sama. "Shiii! Zan koya miki yadda ake gudanar da kome ne! Da zaran kin zama yar hannu ba ki da matsala! Don ma kina da tsafta jikinki bai da wari ko karni!" Kuka na saka mishi haka yayi ta jagwalgwalani, kafin ya kyale ni. "Ya nasan kin ji dadi ko? Nasan kin ji kamar na cigaba!" Tattara kayana nayi na shiga ban daki nayi wanka na fito na kwanta a kasa. Idan nace bana takura ai nayi karya Tafida ya saka min damuwa har sai da ta kai cikin dare bana barci domin yadda zai lallabo ya tashe ni, kai ranar da muka cika kwana uku, zazzaɓin shi ya dawo ina jin bai tashe ni ba sai kakarinsa naji na farka ina me nufarshi. Kunna wutar dakin nayi na ganshi yayi rubda ciki. "Sannu Meke damunka?" "Kina guduna ne fa, shine ciwon ya tashi!" "Ban gane ba?" Na tambaye shi. Nan ya warware min ji nayi kirjina yana dokuwa, kamar zuciyata zata dirko nayi baya. "Me kake nufi? Ni." Dake bukatar shi ce ya manta da kiyayya da kome ya fara kokarin niman abin da zai kara da shi ya min tijara, kasa hakuri nayi na koma can inda nake kwanciya na kashe wutar dakin na kwanta. "Kada ki manta Mala'iku zasu ta tsine miki har gari ya waye domin kin kauracewa shimfidar Mijinki! Sannan zan gayawa Abba ya sani idan na mutu kece!" Kasa magana nayi ina kallon shi a cikin duhu, ya tako kamar wani dan kwayya ya nufe ni. "Kin gani kamar zan mutu kada na.mutu a wannan yanayin!" Banza nayi da shi zan tashi ya riko jelar kitsona ya wuce da ni kan gadon. Kamar wanda aka cire mishi ciwon ne ko jin yadda nake kuka yasa shi cire hannunshi a jikina, ya koma ya kwanta yana juyi karshe ya tashi ya bude jakarshi ya hadiye wasu magani ba ruwa ya kwanta. Ni dai kwanan zaune nayi. Bayan minti talatin na ji ya fara barci. Nima kwanciyar nayi a wurin, bamu farka ba sai da gari ya waye tas, wani ikon Allah sai gamu manne da juna, bude ido nayi na ganni cikin jikinshi da sauri na tashi zaune ina kokarin ganin na bar shi ya kalle ni a wulakance. "Iskanci zaki min? Ko fyade kika so min?" Hadiye yawun bakina anyi na rasa me zance mishi, a hankali na zare jikina daga nashi na sauka akan gadon na wuce ban daki nayi wanka da alolan shima wanka yayi da alolan ya fito daure da Towel a kugunsa, lokacin har na gama saka kaya. Yau juma'a babu abin da zasu yi sai asabar da Litinin. Don haka ina gama shiryawa na saka abayan zan fita ya ce min. "Ina zaki da safe nan garin akwai ruwa?" "Zan je na karya ne!" "Ki zauna za a kawo dakin!" Ya fada yana saka wandon shi naki yarda mu hada idanu. "Dawo nace!" Haka na dawo na zauna, cire towel yayi yana shirinsa, yana gamawa ya kuna wayarshi nan na ga yana me murmushi. Wayar ya kanga a kunnenshi ya manta da ni bakiɗaya daga yadda yake wayar na fahimci da rukayya yake magana, "Laraba zamu dawo ke kuma kizo juma'a." Kallona yayi ya ce. "Kina kallona kamar mayya ni manyan idanunki nan tsoro suke bani wallahi! Yanzu za a kawo abinci." Sunkuyar da kai nayi ban kula shi ba. Haka aka kawo min abinci har dakin na karya , washi gari asabar muka je taron, Litinin da Talata duk an yi, na dawo da tarin kyautttuka. Na kira Mama da Abba na gaya musu sannan na kira Baba Bulama da Babana na gaya musu. Ranar Laraba muka dawo Alhamis na wuni aiki ranar juma'a, sai ga Rukayya da yaranta biyu. Nayi kokarin koyawa kaina dauke kai akan abinda bai shafe ni ba, kuma Alhamdulillahi Allah ya ba Ni saa domin naki kula iskancin Yaran balle na Uwarsu, yadda ta ga dan uwanta yayi laushi sai da ta xage ni wai na karbi asiri xan mallake musu dan uwa. A hankali fa kome ya fara cabe min abin da ya rage ya dawo, kwananta uku Sa'adiyya tazo sai da naji kamar na kashe kaina don bakinciki domin duk ta inda zasu saka min damuwa suna aikatawa, abu daya na sani zuwa wurin koyarwa tayi tasiri bana ganin abinsu kayana kuwa har na dawo na samu anyi min kaca-kaca da shi. Kwana biyu ban ga Tinah ba sai da tayi kwanan biyar sai gata da wasu kawayenta na amshe shi da farin ciki, na kawo musu abin tabawa. "Iyawo mun zo za ayi bikin wannan kin ganta!" Ta nuna min ita sannan ta cigaba da cewa. "Tana son turaren wuta, da irin wanda kike amfani da shi, sannan za ayi mata cake." "Tow ki gaya mata za a yi amma turaren wuta daga gida zaa kawo kamar na nawa take so?" Tana gayawa kawar tace ita . "Ni ko na dubu dari biyar ne." Kiran Mama nayi muka gaisa na gaya mata, ta kaiwa Ummi wayar na fada mata abin da ake bukata, ai kafin wani lokaci ta turo account na kara mata bayanin ni nawa har da humra da kwalaca, duk aka hada mata aka tura kuɗin, sai lokacin Aunty Rukayya ta fito tana kallonmu,jin muna maganar kuɗi. Sama-sama suka gaisa da Tinah sauran kayan aka bar min aikin. Sannan na raka su. Ita yarinyar da zata yi aure ta bani kyautar dubu hamsin. Na dawo na ajiye a kitchen. Abin mamaki sai gashi tsakanin rukayya da Sa'adiyya ba a san waye ya dauke kudin ba, ni dai ban yi magana ba, na barwa Allah don sune a wahale. Shi ma Tafida ashe a wannan dan yanayin da gidan ya karu sata ake ta mishi dakinsa, wannan lokacin ko bera albarka, sati guda aka.dauka sai ga turare ban yarda na kawo gida ba, Tina ta amsa musu ni kuma na amso kayan da Mama ta hado min na kawo. Haka lokacin bikin yayi muka sha aikin cake da kawo sauran gida, akan idanun Tafida na ajiye a kitchen shima ya shiga dauka aka rasa waye ya dauka. "Ummu!" Ya daka min tsawa, ina sallah ya kara kiran Amir ya ce mishi. Ina sallah, ina idarwa ban yi addu'a ba, na fito . "Ina abin da kika kawo?" "Ai kana gani a kitchen na ajiye!" "Rukayya, Sa'adiyya Ummu tana shigowa dukkanku biyu kun shiga kitchen din wacece ta dauki abin da aka ajiye." Fashewa da kuka Rukayya tayi wai ya daura mata sata, dama ta lura na gama da shi. Abin haushi ban san lokacin da na fara fada ba wanda nasan tunda nake ban tab'a yin shi ba. "Na gaji ban isa na fita ba xan samu an bincike min kayana, ban isa na ajiye za a dauka min. Ranar can dubu hamsin na ajiye saboda dakina ban isa ajiya ba za a bincike min na saka a kitchen haka narasa kudina, Allah ya isa min ban yafe ba, domin hakkina ne gumina ne duk.wanda yaci sai mun tsaya Allah ya karba min abina a ranar da bamu da shi." "Kudinki yana wurin Umminmu, cake din ma ita ta dauka!" Juyawa Sa'adiyya tayi tana me nufar dakin Tafida ta saka kayana ta fito tana faɗin. "Ni dai babu shegen da zai ajiye abu na dauka ko na dakinka da ake dauka ita Yar uwarka zaka tambaya." Bakiɗaya muka barta a wurin kunya kamar zata nutse, ai kuwa washi gari ya haɗa mata kayanta kudina na wurinta fir taki bani, nima ban mata magana ba. Ashe gurmi ne a aka shirya bayan tafiyarta aka kira shi aka gaya mishi bikin Sharif wanda za ayi shi wata me kamawa.... *SAURA 3 PAGE NA GAMA FREE PAGE! ANZARTA KI BIYA KADA A BAKI LABARI* 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga number da zaku tura naku payment din : +227 84 50 64 76 Nana A'ishah maradi'YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML* *Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!* Paid book 18 Ashe ana can suna ta tattaunawa yadda idan nazo bikin zasu min tozarci, ni anan ban sani ba sai da Nabila ta kira ni take gaya min abin da yake faruwa, ban ce mata kome ba nayi dariya kawai domin nasan ina da gaskiya kuma Allah yana tare da mai gaskiya na babu abinda zai tsorata ni. A bangaren shi kuwa babu abinda ya sauya domin ya rantse sai ya mai da ni yar iska, haka yasa na ki yarda, sai gashi ya dawo da rashin mutuncina, haka na zuba mishi idanun tunda babu Allah cikin sha'aninsa. Ina ga idan na bashi damar ya samu yadda yake so iskanci sai wanda ya ci Uban na da, haka yasa nayi bala'i kama kaina, abin sai ya zama kamar renin hankali daga gareshi, amma na zuba mishi idanu don na fahimci waye Tafida me taka, don haka tun kafin ya fara min horon yunwa na saka kaina sayan kayan abinci, na ajiye. Kamar na san haka zai faru abinci yana karewa na gaya mishi, murmushi yayi yana faɗin. "Ba zan iya cigaba da ciyar da mummunar halitta irinki ba, gara dai a kira gida a roke su kamar yadda aka saba wai ma tsaya!" Ya fada yana mikewa. Bayan nayi kadan ya rike kugunsa yana faɗin. "ina kudin da kike samu?" Hadiye yawu nayi ban iya bashi amsa ba. "Ba tambayarki nake ba ne?" Zubewa nayi akan gwiwata na fashe da kuka, tunda nake a rayuwata Mama sau daya tayi min tsawa amma Tafida bai da aiki sai min fada da cin mutuncina. "Ko kina turawa wancan Matar ne tana tuwo-tuwo..." a yadda na d'ago kai a fusace ya sa shi ma bai karasa abin da yake bakin shi ba, murmushi yayi yana faɗin. "Kin san zafin Iyaye ashe!" "Saboda ni ba jahila ba ce, kuma ba dabba ba ce. Saboda sanin zafin Iyaye yasa nake zaune da kai ai baka isa ka..." Shake wuyata yayi tare da hada ni da bango, saboda azabar zafi ko kuka na kasa sai lumshe idanu, ja na yayi har cikin dakin, yana faɗin. "yau zan koya miki hankali, wallahi baki isa na ciyar dake sannan ki na min rashin mutunci ba!" Ya fada yana kokarin yi abinda ya saka kanshi. Sai dai me yana kai ga cimma buƙatarsa ya samu ina bakonmu na mata, kamar ya rufe ni da duka. Haka ya bar ni a wurin hawaye na cigaba da zubarwa, na sha kukana sosai sannan na tashi a hankali na shige ban daki nayi gyara jikina. Kitchen na shiga na hada tea na juye zan fito na ganshi a bakin kofar. Baya nayi ya shigo ya amshi tea din yana faɗin. "Idan kika sake na gano inda kike kai kudinki sai na lalata miki in da bakyso na shiga.." na rab'a gefenshi na wuce, ni yanxu bana mamakin abin da zai min domin duk abinda zai aikatawa baya danasani. Haka nayi ta maneji da irin halin Tafida gara ka zauna babu aure, domin haka kawai zai kwaso min abokan aikinsa su kwana na ciyar da su, su tafi ko kuma ya zo da yan mata hadaddun irin yan iska-yan iskan su kwana nayi musu hidima, su tafi akwai wata yarinya da tazo ta kwana, sai dai hatta bakin dakina sai da nayi mishi wankan tsarki domin karni da wani irin wari yake, ko sati ba ayi na ta sake zuwa min, tsakani da Allah nace tayi amfani da ban dakin parlour, abin ya bata haushi, ni ko a jikina domin nasan ba wani abu bane cuta nake gudun dauka. Ashe ta gaya mishi, cikin hayagagga yazo zai min tijara na dauki wayata na kira Abba. "Barka dai Abba, ya gida." Juyawa yayi ya kalli Yarinyar ya riko hannunta ya ce ta tafi kawai. Dawowa yayi ya samu har lokacin muna magana ne, bayan na gama na kalle shi. "Da ace abin da kake min zan gaya mishi, ni nasan hatta inda kake gadaran kana aiki sai an sallame ka, Tafida mu zauna mu fahimci juna shine muradin iyayenmu!" Wani shegen dariyar ya saka yana nuna ni. "Ke ni ne zan zauna mu fahimci juna? Ni ne zan zauna dake muyi sulhu don kawai na kyautatawa wancan mutumin!" "Abin da kake aikatawa idan Allah ya baka nisan kwana sai Yaranka sun maka, ka kyautatawa iyaye ma ya aka kare, balle kuma ka saka su bakinciki. Babban damuwa kada ka gurbata min zuriar da zan samu da kai da mugun dabi'unka, domin idan haka ya faru ni ne zan wahala tun haduwana da kai ban huta ba, zuwa yanzu ma ban huta ba na girma lokacin da ya dace na huta fitinarka ya sani na kasa barci. Kai ba yaro ba ne, saboda irin wannan kazamar rayuwar naka laifinka yaso ya shafe ni, in sha Allah na kusan gama contract din da nake na abinci, daga nan ba zan kuma dawowa rayuwarka ba, amma ka sani Allah ba azzalumin sarki bane sai wanda ya zalunci kasan har yau ina gayawa Allah idan zama na da kai alkhairi ne Ubangiji ya daidaita mu idan babu alkhairi Ubangiji ya kawo sanadin da zamu rabu ba tare da mun cutar da juna ba, sannan abu na gaba da zan kara tunatar da kai shine duk abinda na maka don Allah kada ka zagi Mahaifana domin bayin Allah nan sun yi matukar kokari akan tarbiyya da suka bani, bai dace yadda nake ganin darajar ahalinka kai ka gaza ganin darajar nawa ba, sai abu na karshe ina son na tuna maka ni ba yarka ba ce, da zaka na mangare ni son ranka, kana da Yayu mata da kanne idan ka cigaba da haka zan gayawa Abba da iyayena su shiga wannan lamarin tunda na fahimci baka gane karatun, gida naka ne duk wanda ka kawo daya ne, shi zina kamar bashi ce." Na fada ina kuka domin zuwa yanzu idan na tuna abinda ya faru sai naji kamar zuciyata zata buga,, idan na tuna saboda Tafida Mahmoud yaso keta min haddi sai naji na tsani zama da shi, haka yasa na kara raba kaina da Tafida. Ana haka sai ga Ammah abin ya bamu mamaki, koda yake Uwa ce ta gari, bata yarda tazo hannu haka ba sai da tayi min kayan abinci, tunda tazo na gyara mata dakina, ni kuma a daren ranar na koma dakin Tafida da kwana, ina kasa yana sama. Daga shi har ni kowa harkan gabanshi yake, sannan shi ya lura da yadda nake kyamar gadonshi. Abin mamaki yake bashi don ya rasa gane me yasa bana son na kwanta a gadon, sannan yana kara tinzura idan ina baya baya da abin da zai saka na tab'a ba, kwanan Ammah uku ta bar gidan, a daren na koma dakina. Sai dai albarkacin Ammah ya saya mana kayan abinci, kai Tafida mugun dan wasan kwaikwayo ne, domin har da cewa. "Ummu Hadiyya maza rubuto min kayan abincinmu nan da ya ƙare." "Ai kayan abinci da saurin karewa yake, don ma baku samun baki akai-akai ba ne." "Eh sai dai ranar juma'a tana yin abincin sadaka, nace tana yi." "Masha Allah Tafida girma yazo Ubangiji ya dafa maka!" Dariya abin ya bani yadda bai ji kunyar gatta karya ba. Nima ban yi musu ba domin na fahimci mutuncinsa yake kankarowa. Bayan tafiyar Ammah ba laifi abinci dai gashi nan sai yadda aka yi da shi, Ni haka bai dame ni ba domin nasan yana karewa iskancinsa zai dawo sabo dal. Bikin Sharif da ya karato ana ta shiri, na kira Hajiya Kaltuma na tambaye ta meye shirin da ake murmushi tayi tana faɗin. "Ki ware duk abinda Allah ya baki, ki basu idan kuma zaki mana su cake da kayan ciye-ciye ne muna murna." "Tow shi kenan!" Na fada mata ina murna, a inda muke hidimar girki akwai wani dan Senegal yana kawo kayan maza da mata, haka na sayi Senegal lace, me kyau sannan na gayawa Tinah batun bikin ai kuwa tayi tsalle ta dire har da ita zamu zo. Don haka na kira Hajiya na ce mata ina son ankon da za ayi a turo min Abuja har guda biyu. "Ke Ummu kayan nan kala shida ne Abbanku ya saya miki dukka don yace Mijinki matsolo ne bai zama dole ya saya miki ba." Dariya muka saka na gaya mata wacce take so, na.tura kudi aka saya mata sannan aka turo min dasu har da nawa Tinah ta kai ɗinki bakiɗaya. A nan Abuja na sayi kayan aikin da xan yi sannan ana saura sati muka bar Abuja, Tinah zata zo saura kwanaki hudu. Mun sauka lafiya akai ta murna, dake iskar dare muka yi washi gari na hada tsaraba na kai cikin gida, na bawa Hajiya nata sannan na wuce wurin Inna tana gani na ta ce. "Yaron kirki kun iso lafiya? Ina tafida take?" Murmushi nayi nace mata. "yana barci amma nasan zai shigo." Na ajiye mata tsarabarta na fita, sannan na wuce wurin Hajiya Kaltuma na gaidata sannan na ajiye mata nata, dakin Hajiya Salamatu na shiga duk yaran na zaune, suna cin abinci na gaida ta. "Mutanen Abuja, har an iso kenan!" "Eh Hajiya, ga wannan tsaraba ce. Wannan kuma gudunmawa ta ce ayi hakuri babu yawa." Amsa tayi tana faɗin. "Ikon Allah me yawan kenan, Ummu ashe kina koyar da girki ne a can?" Cikin girmamawa na ce mata. "eh amma na kusan kammala dake na wa'adi ne idan na gama shi kenan." "Allah ya dafa miki, ya kuma baki sa'a." "Amin Hajiya bari na gaida Abba!" Na dauki na shi kayan na fitar da shi, "Gaye nan ya samu mace fa, amma yake biyewa duniya yana mata iskanci." Inji Alfah Kanin Sharif. "Eh ya samu mace ga Allah, kuma irin matan nan ne na rufin asiri, Allah ya sa nima tawa tana da wannan halin!" "Amin Ya Allah. Ai naso lokacin da Alhaji ya kawo batun wa kai ya nimawa yarinyar domin tana da tarbiyya da hankali, ku kalli bata dauke ni a matsayin da suka dauke ni ba, yadda take mutuntatta ni yafi min kome dad'i, Allah ya mata albarka!" Ta fada tana murmushi. Da naje parlour Abba nan aka zuba min abin karyawa, ina ci ina bashi labarin wurin aikina. "Ai na gaya miki, nan gaba sai wata jami'an ta dauke ki aikin girki kafin nan ki nimo min takardunki!" Zare idanun na fara ina sosa kai nace mishi"Abba ni fa na tsani karatun boko ne!" Ware idanu yayi yana rike baki ya ce min. "Yau naga wacce bata kaunar boko, idan Mijinki ya zama.wani fa?" "Sai ya auri yar boko, tunda ni gaskiya bani gane kome na bokon nan!" Dariya abin ya bashi bayan na tab'a abincin na dauki tsarabarshi na bashi ina cewa. "Ba yawa wannan kuma gudummawata ce!" Na mika mishi, kamar da wasa Sai gashi Abba yayi ta min addu'a, kwanakin da suka biyo baya, ana ta shiri ne sosai. Ranar da aka fara biki a gkdansu amarya nima na fara nawa shirin aikin, a daren ranar Tinah ta iso na kaita har parlour Alhaji da su Hajiya, sun ji dadi sosai. Washi gari na kaita gidanmu muka wuni, sannan muka dawo ita da Sa'adiyya wani gani-gani sukewa Juna, abokinta ta biyo, amma sai zuwan ya koma nawa. Ana gobe daurin aure Abba ya kira ni. A gabansu Hajiya ya ce musu. "Ku ji da naku aikin ku bawa Ummu nawa aikin!" Mutane masu matukar kirki da mutunci suka ce. "yawwa gara da ka hada Ummu da aiki mu.ma mu ji da namu!" Haka ya aka bani aikin na shiga kitchen na amso kome na wuce bangarena, sannan aka turo min Nabila da Na'ima da kawayensu. Da Tinah muka daura aikin pepper chick. Muka kuma hada miyar jollop, washi gari muka tashi aiki kamar ba gobe yan matan nan da su muka ci Uban aiki, abinci ya kusan sauka kawai sai ga Aunty Rukayya da flat. Zata bude tukunyar Tinah da bagwaren hausarta ta ce mata. "Look me kake so?" "Abinci zan diba!" "Ba zaka saka ba, ina kake lokacin da muke aiki sai kazo kai me cin abinci!" Jin maganar Tinah yasa ni fitowa a daki ganin rukayya yasa na fahimci inda zancen ya nufa na ce mata. "Ki je ki tambayi Abba kosu Hajiya abincin nan na Abba ne." "Eh nasan na shine na zo diba, ko ban isa ba ne?" "Gaskiya kin isa amma.ba zaki diba ba." Na fada ina gyara wutar. Fita tayi fuuu, sai ga ta tare da Maryam da Safiya Matar Ya Umar. "Ke yar uban waye da zaki hana abincin? Na kira Tafida ma yazo ya diba mana. Dama ina cike da ke yar iska mara kunya!" Inji Maryam, ban tanka musu ba, Tinah zata shiga na rike hannunta ina girgiza mata kai. Shigowar Tafida da Deen yasa na dauke kai ina cigaba da gyara murhun. Nan suka gaya mishi abinda yake faruwa. Ba don Allah yasa yazo da Deen ba ban san me Tafida zai min ba. Domin shi da Tinah kamar zasu bugu yana gaya mata ita bakuwa ce kada tayi wani abu da zai saka mutuncinta ya zube nan ta.kara harzuka. "Zuba musu abincin!" Ya fada yana takowa gabana. "Ba zata zuba ba, abinci na Alhaji ne su je su same shi ko matanshi, ai gaskiya ta fada dake su masu dangi ne shine akazo cin mutuncinta! Ba zata zuba ba!" Inji Deen, "Kai ya ishe ku Ummu Matata ce! Babu Dan iskan da ya isa shiga tsakanin mu." "Ni kuma Ummu kanwata ce babu shegen da zai ci zarafinta na kyale dan kutumar." Ai ba sai ga Tafida da Deen zasu bawa hammata isa. Da gudu nabila da Na'ima suka kai labari cikin gidan, Alhaji da zai wuce wurin daurin aure ya shigo har cikin gidan yana kallon yadda na shiga tsakaninsu. "Wai ni don Allah ya kuke so nayi ne? Abotarku na.tsawon shekaru zaku lalata saboda ni? Idan abinci ne gashi can su diba yadda suke so abu daya na sani Allah zai kamani da hakkin cin amana, ba yau na fara hidimar abinci ba, amma ba zaku yi fada saboda ni ba don Allah!" "Allah ya maka albarka Safiyyudeen! Allah ya tsare bayanka da gabanka. Abinci ni nan na bawa Ummu tayi min domin gudun fitinarku na bata, Aniyarku zata bi ku abin da kuke mata Allah sai ya bi mata hakkinta. Inda ake zuga ku ." "Abba don Allah kayi hakuri!" Murmushi yayi ya kalli Tinah ya bata hakuri cikin harshen Ingilishi, daga nan ya fita ya ce a kwashe mishi abincinsa a kai mishi cikin gidan. Haka kuwa aka yi na dauki sabin kullolina na alfarma na zuba pepper chick din, sannan na koma daki muka shirya shiga aikin cake, muna gama kwabi na bar musu na buga donut, kafin wani lokaci har na gama na kai shi rana. A can bangaren Shuwa kuwa daura su tayi akan keken bera, tai ta zuga su tana gaya musu abin da ba shi ba ne. Karfe hudu na yamma muka gama sannan muka shiga cikin gidan bayan mun yi wanka . Dakin Inna muka shiga naga dasu Rukayya ko minti goma bamu yi ba muka fita na cewa Tina. "Mu koma bangarenmu!" "Ok!" Muka dawo, ko minti ɗaya bamu yi ba sai ga mata yuiuuuu. Hayaniyarsu ta fito da ni daga cikin kitchen na je diban abinci. "Lafiya?" Wucewa dakina Rukayya tayi tana faɗin. "bincike zamu yi bari na fara da dakinta!" "Ban gane ba?" "Shigar ku dakin nan, aka nime kudi aka rasa kuma.a inda kika zauna kudin yake!" Dariya nayi nace musu. "Bismillah!" Na koma kitchen din ina diban. "Innalillahi na gaya muku ita ce haka zuwana Abuja ta hada ni da dan uwana wai ina mishi sata, bayan ita ce take shiga dakinsa. " ba tare da na fahimci me suke nufi ba, matan nan suka rufe ni da duka, wanda ihun Tinah ya janyo hankalin mutane cikin gidan har da Tafida da suke kofar gidan, suka shigo ni kan ai na suma. Abba babh takalmi a kafarshi ya shigo parlour lokacin kowaccensu ta gudu sun bar gidan bakiɗaya. Tinah sai kuka take tana rungume. "Abba ka saka Tafida ya sake Ummu, Abba don Allah ka ce ya sake Ummu ba matar shi ba ce kashe ta zasu yi shi da Yan uwansa. Abba Tafida bayan son Ummu don Allah ka ce ya sake ta ni xan aureta!" Inji Alfah da ya shigo hankalinsa a tashe, ruwa akayi ta watsa min, kafin na sauke ajiyar zuciya. "Wallahi ban dauka ba, wallahi ban tab'a sata ba, ban iya daukar abin wani ba." Na shiga fada ina ihu, durkusawa yayi a gabana, ya janyo Ni jikinshi. "Allah sai ya saka miki, Allah sai ya bi miki hakkinki, nayi kuskuren barwa dabba ke bayan ke ce kika dace da samun mutum na gari na bawa Dabba rikonki!" "Tina rikota zuwa bangaren Kaltuma!" Ya tashi yana me kallon Tafida. "Ina son takardanta nan da awa daya!" Mai da hannunshi baya yayi yana me sunkuyar da kanshi. "kayi hakuri amma ba xan iya sake ta ba, ina son Matata!" "Tass!" Ya kifa mishi mari, duk da bana cikin hayacina sai da na juya ina kallon shi yadda ya zube akan gwiwarshi. A farkon rayuwata da naji wani irin mahaukacin matsayinsa me hade da kaunarshi da ban san yaushe ya min bazata ba. Abba sai kara marinshi nace mishi. "Don soyayyarka da Annabi Muhammad, kayi hakuri." Na isa gabanshi ina me durkusawa. "Don Allah kayi hakuri, laifina ne da ban je dakin ba, haka ba zai faru ba." "Ya sake ki tow!" Daga ni har Tafida muka kalli Abban. "Abba ina son mijina!" A fusace ya fita daga ɓangaren bakiɗaya, Deen ma ya saka kai ya fita, Mahmoud da shima ranshi ya b'aci ya fita daga gidan bakiɗaya, cikin Motarshi ya shiga yayi da dukar motar yana ihu, Tina ma fita tayi tana share hawayen da yake zuba mata. "Idan haka matanku suke da kashe kansu tabbas Ummu ta cancanci farin ciki a rayuwarta." T fadawa Deen da yake kokarin fita a gidan, "ina zaki?" "Somewhere!" "Muje ki zaga gari!" Ta shiga motar tana me bude pose dinta. Ta ga kome nata tayi murmushi. "Muje ga wannan ka bawa Ummu Atm dinta ne jiya network ɗin bankin mu yaki bani hadinka, shine ta bani Atm dinta. Me irin wannan kudin ne zai dauki dubu biyu!" Ya fada tana murmushin takaici. "Ummu bata da matsala shine dai matsalar Ummu sannan ya sake yan uwanshi suna wulakantatta!""shi ya wulakantatta ba su ba, da ya girmama ta babu me mata iskancin nan!" Bayan fitar kowa na koma gefe ina me hada kaina da gwiwata, wani irin kuka nake me cin rai a karon farko da na kara jefa rayuwata akan Tafida, "kiyi hakuri!" Naji muryanshi, "nayi hakuri? Kace nayi hakuri naji zan yi ko babu kome ka bani hakuri da kanka amma ka sani daga ranar da na gaji ne babu me tankwara Ni!" Na rarrafa na shiga ban daki nayi wanka da ruwan zafi zazzaɓi ya rufe ni, haka aka yi bikin nan ba dadi. Washi gari ranar budar kai, ban yarda na fita ba kayan abin da nayi na bada aka kai, ina kwance Tafida ya shigo ya zauna a bakin gadon. "Wai ba zaki iya fita ba ne?" Kallonshi nayi kafin na ce mishi. "ina tinah?" "Tana wurinsu Inna!" Haka na mike na gyara zaman dan kwalina, na fita ina me yafa mayafi. A hankali na nufi cikin gidan, na samu ana ta hidima. Wurin wucewa naji wasu kawayen Maryam suka ce. "Ita ce ta dauki dubu biyu aka mata duka!" "Eh ita ce fa! Anyi mugun hali ga baki kamar zunubi ga sata" Kallon Tafida nayi da yake murmushin mugunta. Zan yi ya rike hannuna. "Me yasa kayi min haka?" "Saboda kin cewa Abba kina sona, Ni kuma nayi alkawarin sai na cusa miki bakin ciki ta ko ina!" Ji nayi numfashina yana son fita daga gangan jikina. A hankali na durkusa a wurin ina jin kamar bakiɗaya mutanen ke fada min magana. Dafe kaina nayi da karfi nace. "Ni ba barauniya ba ce!" Na fashe da kuka kokari nake nayi numfashi, dafe kirjina nayi ina wani irin haki, kafin nan na zame akan kafata. Kokuwa nake da numfashi amma yaki bani hadinka. Iya abinda zan iya cewa naji shine. "Ka daukota ne ku kashe ta? Ka daukota ku tozartani? " rike hannun Abba nayi nace. "Ka kai ni gidanmu don....." daga nan bana ce na san me ya faru ba, wannan abin da ya faru yasa Abba yayiwa Rukayya da Maryam Allah ya isa, bai yafe musu ba, shi kuma Tafida Abba ya rantse sai ya mai da shi zero percent. Abin ba dad'i ita Hajiya Salamatu haushi ya hanata magana domin an lalata mata bikin danta. Kwana na biyu asibiti, na farka saboda yadda jinina ya haura sosai, likitan sai fada yaƙe. Akan an barni da damuwa lokacin da Mama tazo gaida ni tayi ta min nasiha nayi hakuri na rage damuwa a raina, hmm bata san me ake min ba, domin daga wannan lokacin na hadu da mugun hawan jini........... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML* *Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!* Paid book 19 Kallon Mama nake bakina kamar an daura min dutse, na lumshe idanu ina son yin kuka amma na kasa, na juya na kalleta kafin nace mata. "idan kika ji labarin mutuwata, ba dad'i ya kashe ni ba damuwa ce, idan na rayu kuma ki taimaka ki min Alfarma daya!" Jikinta ne yayi sanyi, kaina na dafe ina jin kamar zuciyata zata fita waje saboda bugawa. A hankali na juya na kalleta na ce mata. "Me yasa baki tab'a tambayata meke faruwa a gidan aurena ba?" Na sha mamaki da naji amsar da ta bani wanda ban yi mamakin fitar shi daga bakinta ba, "Idan na tambaye ki meye ribana? Na tambaye akan me? Kowa yasan kina zauna lafiya tow akan me zan tafi lafiyar aurenki, Ummu indai ba so kike a zage ni ace na kashe miki aure ba, ki rufa min asiri ki zauna lafiya wannan wacce irin rayuwa ce? Daga tambayarki kin ga kudi zaki yanki jiki ko fadi!" Ware idanu nayi akan Mama. "waye ya gaya miki haka? Sharrin sata suka daura min fa!" "A'a Ummu yayar Mijinki ta gaya min Ummu bakya son zaman lafiya." Kallon ta nayi kafin na fashe da kuka, ina yi ina yada kaina saboda yadda kirjina yake zafi da ciwo. "Ke kika haife ni kin san abinda xan yi da wanda ba zan yi ba, a tsawon rayuwata ban taba kawo miki kara ko nayi musu da wani ba, me yasa yau daya don an gaya miki abu kaina zaki amsa? Me yasa baki jira ki tambaye ni ba? Indai ke kika gagara min adalci a duniyan nan waye zai min adalci? Zan tafi wurin Babana na gaya mishi." Anan na ga ta ɗan yi jim kafin ta ce min. "Ai maganar ba sai ta kai wurin Malam ba,.akan abin da bai taka kara ya karya ba, kiyi hakuri tow zan cigaba da miki addu'a!" Da wannan tayi ta kwantar min da hankali, har nayi shiru na zuba mata idanu, kullum Tafida da Abbansu suna hanya, amma ni ko sau daya ban taba mishi magana ba, kwananmu goma aka sallame ni, gidana na dawo na cigaba da jinya duk da ana dawowa da ni Mama ta wuce gidanta, sannan wani abin da ya kara cin tuwo a kwarya yadda Tafida baya ganin girman Mama, har gara Deen yana girmamata. Shi yasa nima nake girmama Ammah. Sai da muka kwashe sati uku muka koma abuja, sai dai nayi mugun fita barkan Tafida, ban da aikin da aka dauke ni ba zan kara bin shi ba, haka a hankali nayi ta fuskantar kalubale daga danginsa, ana haka aka sake wani bikin ban je ba, sannan tun dawowarmu Tinah ta dauke kafarta ashe sun yi fada kaca-kaca da Tafida tun a Maiduguri, tayi mishi alkawarin sai ta saka ya bar inda yake samun kuɗi kamar hauka, da shi yake saka shi jin shi wani ne, lokacin da ta gaya min murmushi nayi na ce mata. "Ina kika yi sanadin da ya bar aikin bashi kika yiwa ba, ni kika yiwa ki barshi yayi aikinsa Allah ta bashi Sa'a duk abinda ya gadama yayi."tunda na hadu da laluran nake gudun abin da zai d'ago min shi,.sannan bana son tashin hankali bakiɗaya gani nake kamar xan mutu yadda nake fama da ciwon. A hankali lokaci yayi ta gudu ana haka har watan azumi ya cimma na, a lokacin na gama aikin da aka dauke ni, ai kuwa na ce sai Maiduguri, dake kusan wata bakwai babu me kula dan uwansa, don nayi kokarin koyawa kaina shanye iskancin, sai dai mafi girman kuskuren da zuciyata tayi min fadawa soyayyar Tafida. Wani irin mahaukacin sonshi nake kamar zan yi hauka, idan nace ban fada jarabawa ba nayi karya haka yasa nake rufe kaina a ban daki nayi ta kuka, tun ranar Monday na shiga tattara kayana, yana gani bai min magana ba, nima kuma ban ce mishi kome ba. Sai bayan Isha na same shi a parlour. "Barka da hutawa!" "Yawwa yar gajeruwa, au ashe likita ya ce zuciyarki zata buga!" Ya fada yana murmushi. "Dama ina son na koma gida!" "Ban yi niyyar ki koma ba!" "Shi kenan!" Na fada daga haka na koma na cigaba da zama abina, na zata maganar ta wuce tunda ya ce min bai yi niyya ba. Kawai sai ga kiran Mama tayi ta fada akan me zance zan dawo Maiduguri, fada kamar ta ari baki ta kara, Abba ma ya kiranki ya tambaye ni ko akwai matsala ne. Nace mishi kawai zan dawo ne, na gaji shiru yayi kafin ya ce min. "shi kenan ki hada kayanki Alfah zai zo ya dauke ki!" Ajiyar na sauke ina me jin kamar anyi min albishir da gidan Aljanna. Nayi ta mishi godiya, sati daya da maganar ya kirani yace na shirya gobe za a zo a dauke ni. Yadda muka mai da Tafida gefe ba karamin zafi yayi mishi, ina kwance ya fado dakina, tashi nayi xan zauna ya nufo ni. "Me yasa kika rena ni? Ni nake aurenki ko Abbana? Gaya min me yasa?" Ya hauro gadon ya da karfi ya fisgo ni na fara ƙoƙarin kwace kaina, "Tafida bana son tashin hankali, don Allah ka kyale ni!" "Akan me xan kyale ki bayan kina kallona lusari ban iska kiyi abu na yi magana ba, ace bani da kirki bani da mutunci!" "Tow don Allah meye nayi maka? Na gaji da fitinarka zan tafi inda nake da gata da galihu.." "ai nan baki da shi? Tow bari na gyara miki zama!" Kuka na saka mishi ina rokon shi don Allah kada ya min haka, amma bai ji ba cikin shashekar kuka na rike hannunshi domin bakiɗaya karfi yake son gwada min. "Don kaunarka da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ban san me akan wannan lamarin ba kada ka illata min rayuwa bayan ba son zama da ni kake ba!" Ina bai jin kira, ni dai nasan irin yadda ya zuba min karfi kamar jikan ilaya dan mai karfi, babu yadda xan kwaci kaina amma tabbas abubuwa da suka biyo baya, ban san yadda zan fade su ba, domin.nafi girmama fyade Tafida yayi min cikin mugunta da zalunci irin na ranshi. Haka ya ci mutuncina son ranshi. Sannan ya tashi a kaina yana me jan tsaki. Ya saka wandon shi ya bar dakin, dakyar na rarrafa zuwa ban daki nayi wanka tare da gasa jikina da nake jin kamar ba jikina yake ba, fatana kawai gari ya waye na bar garin Abuja. Kwana nayi ban yi barci asuban fari na hada kayana na fitar parlour wurin karfe biyar Alfah ya shigo yayi ta buga kofa, zazzaɓin da ya rufe Ni na lallaba na fito na bude mishi. "Kayi hakuri Alfa!" "Ba kome ina kayanki!" Na nuna mishi, sai lokacin Tafida ya fito ranshi a bala'in haɗe. "Kai haka ake zaka wani shigo gidan mutane da tsakiyar dare haka!" Dake basu shiri shi da Yaran Hajiya Salamatu. "Ayi hakuri!" Ya fada yana daukar jakata yana me barin parlourn, fisgo ni yayi yana me kallon fuskana. "Ki ka sake wani reni ya kara shiga tsakaninmu, sai na bi ta wannan hanyar sau goma wannan sau daya nayi tow idan kika bari na waiwaye ki abin ba zai mana dad'i ba." Tabbas duk macen da aka yiwa fyade matukar bata gigice ba, tow ciwon yana iya zama har cikin kwal-kwalwarta abin da ya faru da ni kenan amma ban gigice ba, sai dai wani irin tsoron tafida ya dasu a zuciyata, wanda ya ja na fara kuka yana ce min "shiii!" Na hadiye kukan kamar ba ni ba. "Ki kama kanki, shi kanina ne kada wani ya gaya miki cewa akwai wasa a tsakaninku, ki mai da kanki wata sakarai! Kina ji na!" Ya daka min tsawa, k'amkame jikina nayi tare da gyada mishi kai. "Yayi kyau maza muje ki shiga motar!" A hankali nake tafiya saboda yadda nake gogan wurin har cikin raina nake jin zafi, hawaye ne yake zuba ina sauke ajiyar zuciya. "Kukan na uban me kike yi?" Share idanuna nayi da sauri ina faɗin. "na daina!" Burina kawai na bar ganinnshi. "Ya tafiyarki ya sauya!" Ji nayi kafaffuna na rawa kamar ba su dauke ni ba. Fisgo ni yayi ya saka Ni a bayan motar yana faɗin. "Ki kula da kanki!" Gyada kai nayi ina kallon kasa. Motar na barin kofar gidan ya sauke ajiyar zuciya, idan haka aure yake tabbas ya tabbata asararre wanda ya bar damarshi tun farko. Zai barta ne kawai ta tafi don Abba yayi magana amma ba don haka ba, idan ya sakata a gaba sai ya ga abinda yake dadi a jikinta..(Ji dan iska mugu 🙄😒) Tunda muka dauki hanya nake sauke ajiyar zuciya, sai da muka bar Abuja zazzaɓi ya kuma rufe ni, yadda nake rawan sanyi yasa Alfah kashe ac motar, sannan ya yi parking ya ciro min panado ya bani na amsa ina godiya. Bayan na sha yace min. "Ki kwanta ki huta!" Haka na kwanta a bayan motar, tuni barci me nauyi yayi gaba da ni. Ban farka ba sai da ya tashe ni, wurin karfe daya na rana, a lokacin muna fataskum zare idanun nayi ina son nayi magana. "Ga abinci ki ci, zuwa anan da karfe hudu zamu shiga Maiduguri." "Tashi motr sama kayi?" Na tambaye shi ina bude abincin. "A'a gudu nayi kawai!" A hankali na fara cin abincin har muka bar fataskum, a yanxu na tabbatar da ba tashi yake sama ba, irin matasan nan ne masu mugun gudu, Alfah akwai wasa sa rayuwa kamar yadda ya fada karfe hudu cib yayi mana a garin Maiduguri. Wani wawan ajiyar zuciya na sauke ganina a gidan. Abba da kanshi ya tarbe mu, a nutse na gyara tafiya ta duk da ba karamin wahala nake sha ba, na gaida su . "Ummu baki da lafiya ne?" Yake nayi ina faɗin. "Bana jin dadi ne amma da sauki!" "Allah ya baki lafiya!" "Amin Ya Allah!!" Na wuce bangarena a hankali kamar kazar da kwai ya fashe mata, ina shiga ruwan zafi na daura na jira ya tafasa, na jure a flast na nufi dakina da shi, na zuba a bawo na a zauna sai lokacin kuka ya zo min ina yi ina karawa, sai da ruwan ya huce na fita, na kara wanka na sha magani nayi sallah, sannan na kwanta ban farka ba sai karfe bakwai ashe har Nabila sai da ta shigo yafi sau nawa, Alfah yake gayawa Mamansu ai bani da lafiya, haka yasa Alhaji ya saka lallai a kai ni asibiti, gudun abin kunya na ki yarda, haka nayi ta jinya a hankali na manta da wani Tafida can. Haka na bude sabon shafin rayuwa, satina biyu aka fara azumi na nutsu sosai nayi rabon kayan azumi har garin Babana na je da kaina a cikin azumin yana uku sai da nayi aka kai azumi goma na dawo na nutsu nayi kyau, na dawo da kwana uku sai ga Tafida, sai da naji kamar xan yi hauka, kome da nake yi a tsorace nake yin sa, sai dai zuwanshi ya zo min da ban mamaki domin kici-kicin ya hana Saadi shigo mana, ranar da ya zo nayi aiki na gaji, cikin dare ina kwance naji yana lallubena janye jikina nayi tare da matsawa can. "Ke meye haka?" "Na gaji sosai don Allah kayi hakuri!" "Ni mayunwacci ne daga lokacin da na bukaci abinci ci kawai nake son yi na tashi idan zaki bani hakkina a dadin rai ki bani ko na saka karfi na rusa kofar da take rufen nan!" Yadda yayi maganar yasa na mika wuya salin Alin, ina kuka ina jin yadda yake murzani son ranshi, ba zance nasan wani abu bayan nan ba, amma tabbas Tafida ya kashe kome nashi a zuciyata. Yana gamawa ya mike ya fita abinsa. Yau ma Dakyar na kai kaina ban daki nayi wanka da Tsarki na kwanta, wani sabon zazzabin ne ya rufe ni, da asuba bayan mun gama Sahoor ya kara shigowa, a nan ne fa na fashe da kuka wiwi, amma kukana bai hana shi biyan bukatarshi ba. "Idan zaki daina kuka ki daina domin ke da takalmina kallo daya nake muku zan shure ki lokacin da yayi min na bar ki lokacin da ya min." Nayi kuka har naji anya Allah yana amsar addu'ata kuwa. Haka ya share sati daya ya koma a wannan kwanakin ba karamin azaba na ci ba, ga aiki ga hidimar shi da abokanshi. Akwai wani abu da ban gane ba shine duk mu'amalata da Tafida da wani abu yake kusantatta. Irin robar da yan iska suke amfani da shi. Tun abin yana min ciwo har ya daina na saka ido kawai. Ana jibi sallah ya dawo na gyara jikina ta hanyar Hajiya Kaltuma, domin kawai jikinta ya bata akwai wani abu da yake kawo Tafida Maiduguri babu dalili, bata tambaye ni ba amma yadda ya ga na kare wancan lokacin yasa ta da kanta ta hada min magani masu kyau ta bani yana gab da zuwa, ta ce maza nayi ta sha kada nayi wasa da su. Haka nayi ta sha,ashe ita taji shuwa da Yarta suna hiran Tafida ya zama munafiki bayan yace babu abinda zai yi da Ummu shi ne ya munafunce su ya zaga yana shagali da Matarshi. Wanann abin yasa ta jin bari ta taimakawa Ummu itama. Ya shigo gari ana shan ruwa bawan Allah nan ruwa kawai ya sha yayi sallah sannan ya shigo min daki da gajeren wando. Ganin yadda nayi na razana ya sa shi sassauta min murya yana faɗin. "Zan miki a hankali!" Kamar yadda ya fada haka yayi sai dai abubuwan da Hajiya Kaltuma ta bani yasa shi kauce alkawarinsa kamar bashi ba yadda yake abin da wasu yan kananun magana yasa ni fahimtar maganin yayi kyau. Bayan ya gama ya sauka ya shiga yayi wanka a ban dakina, ya fito yana faɗin. "Ke anan zan kwana a hada min kayan abinci na!" "Tow!" Ina jan hancina, ban daki na shiga nayi wanka sannan na nufi kitchen na hado abincin zuwa dakin ya zauna ya ci sannan ya huta kafin ya shirya ya tafi sallah tarawe. Bayan ya dawo ya kuma fita da abinci waje. Suka ci bai dawo ba sai karfe goma sha ɗaya, har na fara barci ya shigo min, sai da gabana ya fadi. Fita yayi sai gashi da kayan barcinsa yazo ya kwanta a bayana, bai nemi wani abu ba don yaga yadda nake dan kerma a gabanshi. Bayana ya sumbata, yana faɗin. "Kwanta babu abinda zan miki, sai asuba zaki bani kafi shayi." Ban yi wani barcin kirki ba, tunda mutumin nan ya maida ni tuwon laushi. Ranar jajiberin sallah, yana gidan bai fita ba a tare muka yi ta fama, wurin karfe daya na dare, kashe kome yayi yana faɗin. "malama muje barci naje ji!" Haka na bar kome na kwanta, don gulma mutumin nan har da min tausa, ai shi ba zai yi aikin banza ba yana ganin na huta ya fanshe aikinsa, haka muka yi bikin sallah ni dai bana jin wani dadin zaman shi saboda jaraba. Sati daya ya koma, bayan na ji rigimar su da Sa'adi, ban yi farin ciki ba domin kuwa har parlourna Hajiya Shuwa ta biyo ni tayi min tijara wai bokana yayi nasara amma na shirya ko bai auri Sa'adiyya ba zai zo da wata ai, me ilimi gogayya wacce ta fiki wayewa. Ko inda take ban kalla ba na cigaba da harkan gabana. Lokaci ya tura sosai ba zato ba tsammani kawai sai matar Sharif ta haihu, a lokacin aka sakani a gabana da habaici da magana,ko ta kansu ban bi ba na bawa Maijego gudummawata na bar gidan, daga nan na zo nayi shawara na bude online business dina, yayinda muka yi da Mudan zai na min deliver. Wasa wasa Sai gashi gidajen abinci sun fara gayyatatta ina zuwa na musu dan karamin program, haka yasa na zama sananniya, ai kuwa na koma yar kasuwa kamar me ina cake ina abinci sannan ana oda sosai, abin dariya sai ga Rukayya ta fara abincin itama online, wasa wasa Sai gashi ana son abincina haka suka yi ta sake min habaici da sharri kala-kala, dake akwai kyakkyawar manufa a raina. Kawai ina zaune wani zuwan da Tafida yayi, yana kallon kwallo. "Ummu ki barwa Rukayya online business dinki nan!" "Ban gane ba?" "Eh ina nufin ki daina sayar da abincin nan da kike yi na Baby's Mama kitchen!" "Fisabiilillahi;" "ba zaki bari ba kenan?" "Gaskiya ba xan bari ba domin da shi na dogara idan." "Ba zaki iya ba kenan!" "Zan gayawa Abba ya ji abin da kike nufi da ni!" Ina saka Abba cikin maganar ya bar zancen, ashe sun same shi da zancen ne ko zai iya hana ni, ni kuwa naki. Ba karamin haushina suke ji ba, ana haka Aunty Maryam ta haihu, tana haihuwa da kwana biyu na je barka na kai mata dubu goma, ko zama ban yi ba na bar gidan, sai ana jibi suna ya kirani wai Maryam ta ce wai ni zan mata abincin suna naje, shafawa idanuna toka nayi nace su kawo idan tana bukata ni ba zanje suna nuna ni a matsayin barauniyar su ba. Na zata zuciya zasu yi sai naga ba haka ba, washi gari sai ga kayan girki, duk abinda aka kawo a bai kai ba,haka na kwashi kayan mu na musu abinci me kyau. Kawai nayi ne domin bana son ayi shi a babu isashe. Da aka zo dauka Rukayya ce, naga ta fito da babban kula ta diba, ya kai gidan shuwa. Ko kallo bata ishe ni ba ina ruwana, ana kai abincin Aunty Maryam ta kirani bayan na dauka nace mata. "An fita bakwai lafiya?" "Lafiya lau! Ya abincin haka? Ko Rukayya ta diba ba ne?" "Hmm wato dama kin kawo min ne da nufin na dafa ace na sace na boye ko?" "Ba haka ba ne, abincin ne kamar an diba!" "Ok ki tambayi yar uwarki!" Na kashe wayar, ina jan tsaki. A can kuwa zagina suka yi tayi wai nayi abincin na kwashe dake Allah ba azzalumin sarki bane sai ga Sa'adiyya ta fasa mata taya a gaban jama'a, ta ce mata. "Aunty Rukayya abincin ki yana bayan Motar Mama." Shiru tayi tana wani zare idanun. A shekara na uku da auren mu ne ya samu goyan bayan manyan dattijan borno, masu political powerful na arewa bakiɗaya suka goya mishi baya, aka fara hidimar yawon zabe, ni bai gaya min na domin a lokacin abin ya zo ne da maganar shi da Sa'adiyya wanda ya saka ni a gaba da fitina da wulakanci wai yana zargin nice nake hana Abba amincewa, a lokacin yanayin ya sauya min da sabon ƙaddara, domin haka kawai na fara wani irin ciwon da ta sa na bar duk wani abin da nake, na nutsu wuri guda, tun karshen shekarar na fara haka kullum ina fama da magani har na shiga sabon shekara, da ya gaji da ganina kwance ya saka ni a gaba muka tafi asibiti, gwajin farko aka tabbatar da cikin wata uku ne daram a jikina, hmm! Sai ga Tafida ya tashi hankalinsa domin ana maganar aurenshi da Sa'adiyya ne, haka muka fito yayi, y kalle ni da kyau. "Yaushe cikin nan ya shiga? Ina kina ganin nake saka condom! Ba don ni na fara koya miki ba da wallahi sai na musanta cikin nan nawa ne!" Rintsa idanuna nayi, naji kamar xan mutu, bayan mun isa gida bawan Allah nan bai huta na, yayi ta shige da ficce lallai zai zubda cikin jikina, a wannan yanayin aka yi bikin Mahmoud da Deen kusan sati guda ne a tsakaninsu. Ban samu damar zuwa ba, domin duk inda Tafida yaji zai samu magani sai ya kawo min ya tsaya a kaina na sha, wani hukuncin Ubangiji magani dai shi ake kira Daram ko jiri bana ji, duk abinda ya kawo zan sha domin ni kaina na kawo aurena ya zo karshe da Tafida. Haka aka yi ta fama ganin cikin ko nasha magani bana kome sai ya kai Ni asibiti wai a cire cikin, likitan yana min scanning ya gano yan biyu ne kwance mahaifata, nasiha yayi mana ya ce mana. "Cikin nan yan biyu ne, kana da damar da zaka iya zubarwa baka san arzikinsu ba, sannan kai ne ake tsammanin zama gwamnan jihar Borno, don Allah kayi hakuri ka barsu! Daga kansu sai ka ajiye haihuwar ma domin cikin ya shiga wata hudu idan aka tab'a za a iya rasa uwar da yaran ma!" Jin haka ya sa shi hakura amma shi kansa yana ganin da zaran ya zaman gwamna zai rabu da ni. Haka muka dawo gida cikin sanyin jiki, daga nan ya fara fito min da abin da yake shiryawa, cikina yana wata bakwai aka yi bikinsu da Sa'adiyya, akwia wani abu da idan kace Allah zai amsa maka, rawan kai da na kafa da Tafida yayi lokacin sai da na taba farkawa da wani irin ciwon ciki kamar haihuwa, ana gobe daurin aure a asibiti na kwana, a wannan lokaci yan uwanshi suka yi ta fitar da abinda yake ransu na idan na haihu zai rabu da ni ya kwace yaranshi, Abba kuwa ya ce . "A duk lokacin da kika samu dama, zan rike miki kan maciji kiyi wasa da bindin yadda ranki yake so," haka ma Inna ta goya min ba, kwana ɗaya nayi aka sallame ni washi gari da ya dace ango ya fito da kaudi sai ga Mutumin ya fito daga bangarenshi kamar ruwa yayiwa zakara duka........... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76YAR MACE....🌺 *Mai_Dambu* *Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML* *Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!* Paid book Last free Page 20 Da mamaki yazo ya zauna a gefena, ina rike da hisnulmuslim, ina karanta addu'o'i domin Inna ta ce min domin samun Yara na gari masu nutsuwa na rike azkar, kusan abinka da gajeruwar mace. Cikin ta fito sosai, haka yasa nake yawan saka hijab ba dare ba rana, yau ma ina zaune ya zo ya zauna a gefena. "Ummuna!" Abin mamaki batar nono a kirjin budurwa, da mamaki na kalle shi kafin nace mishi. "Wani abu ne?" "A'a kawai ina son magani me bani da lafiya!" "Ai ho, Allah ya sawwaka ka tafi wurin Sa'adiyya zata baka ni maganin da yake nan na masu ciki ne sai wanda da kake kawo min don cikin ya zu...." rufe min baki yayi yana girgiza kai. "Kada ki tuna min shirmen da nayi, Allah ya sauke ki lafiya ayi shagalin suna a government house!" Shiru nayi kafin nace mishi. "Ni can zan shiga gidan gwamnati? Ka manta ina haihuwa zaka dauke Yaranka kai da Sa'adiyya da masu renon da zaka kawo daga kasar waje ni kuma na tafi na samu yanci!" Mikewa yayi yana faɗin. "Wasa nake miki!" Murmushi nayi na cigaba da azkar dina. "Babyyyyyy!" Naji Muryan Amarya me maganar sugar. Kafin ya amsa ta diro dakin kamar daga sama. "Haba masoyi!" Wani irin kallon banza yayi mata daga sama har kasa. Ya daka mata wani shegen tsawan da ya razana ni, na dafe cikina. "Don Allah ku fita likita ya hanani jin hayaniya saboda lafiyata!" Juyowa yayi yana faɗin. "Sorry My uwar biyu, bari na ji da wannan mara kunyar." Ya saka kai ya fita ta bishi, da rarrafe na nufi kofar dakina, na rufe na daina jin hayaniyarsu kome ta haɗa su oho. Wasa wasa rikici ya balle a tsakanin Ango da Amarya, babban al'amari fa, yadda kowa ya dauki laifin ya daura min wani nayi musu asiri. Shi Tafida ya kafe babu asirin da nayi musu ita ce asirinta ya tonu. Yan uwansa da suke ciki daya Musamman matan suka juya bakiɗaya suka koma wurin Sa'adi, sai ya zama daga ni sai halina. Ana haka Naziha ta fara shigo min. Idan suka zo dake akwai sauran hidimar da ake yi ba a gama ba. Amma Tafida yayi tsalle yace an gama biki a gidanshi. Abin dariya ina kwance da cikina kowa yasan yadda masu ciki suke fama da yan kananun cututtuka. "Ke tashi!" Ya fada min, kallonshi nayi kafin na gyara kwanciyata. "Ni don Allah ka kyale ni naci abinci ne bai fada min ba!" "Tashi nace!" Ya buga min tsawa, haka na tashi ina nishi. "Saka hijab ɗinki!" Ba musu na dauka na saka, ya kalli kafana da suka kumbura. "Muje!" Ya fada min a harzuke, haka na fito a hankali ina tafiya har waje ya shiga bangaren Sa'adi, yadda suka fito kowa ranshi a dagule yasa ni kame kaina. "Ke Ummu fito daga baya nan!" "Ni dai don Allah ka kyale ni, wallahi gaban nan hana ni sakewa yake kuma hajijiya nake gani." Zare idanun yayi kamar zai fasa ihu. "Zauna zauna!" Ya fada yana hararan Saadi. Shiga motar yayi daidai lokacin da Shuwa ta fito da gudu. "Ina zaka kai min y'a wato rashin mutuncin da ake fada kana yiwa matarka da iyayenta shine zaka fara a kaina?" "Zan kaita a mata gwajin cutar kanjamau ne saboda na sayi rariya mai yoyo. Batun rashin mutunci kuwa tunda kuka bani sauran gardawa ai kin san abin da zai faru, idan har Mahaifina zai zaba min alewar da yake nad'e cikin ledarshi a killace cikin muhallinsa nayi shakukatin bangaro da shi gaya min me zai faru da zabina da ta zama kamar rijiya kowani guga ke fadawa cikins. Hajiya Hindu ke a tunaninki abin burgewa ne Uwa irinki ta sake kiwon akuyarta kowani bunsuru ya barbareta? Ok na ji rashin mutunci da nayiwa iyayen Ummu Hadiyya kece kika jagoranci haka kin dauka ni irin Kawu ne da ake bashi manta uwa?" Zai sake magana na bude motar na fara amai, dama nasan haka ne zai faru matuƙar ban huta ba, daga cikin abinci na fito tow abinda zai faru shine amai da mutuwar jiki. "Sannu-,sannu!!" Yayi min sannu ya fi sau goma, sannan ya bude bayan motar ya ciro ruwan gora ya bani, na wanke bakina. "sannu Maman Twins na dauko ki ko?" Shiga motar yayi ya bar Hajiya Hindu tsaye kamar gunki, tsaki yayi ya ja motar da sauri yana kallona ta madubi. "Sannun kin ji!" "Tafida amma kasan zaka tozarta ni me yasa ka aure ni?" "Ita da tasan zan tozartatta me yasa ta aure Ni? Ko kin manta sau nawa kika zo bangaren mu a lokacin tana amarya?" "Akan me yasa zaka dauko kishiya kana cin zarafina a gabanta." X "Sau nawa naci zarafinta a gabanki? An gaya miki zan kyale ki ne don kawai ga ki yar gwal? Tambayeta yadda na sameta a daren farko da na.." "innalillahi wainnalihir rajouna! Na shiga uku na lalace, ni dai don Allah ku daina irin wannan maganar a kunnen Yarana!" "Ok okay! Suna jin mu ko?" Ya tambaye ni a dame, daga haka yayi shiru sai ita ce ta cigaba, kamar xan yi kuka sai da ya daka mata tsawa, tayi shiru asibitin da nake zuwa awo mutumin da yace kada mu cire cikin nan nake zuwa awo bakiɗaya staff na asibitin sun sanni. Koda ya isa sai da na kai minti goma kafin na fito a hankali, duk yadda nake tafiya a hankali Tafida bina yake a nutse, yana min sannu yafi baki dubu. Kallonshi nayi yadda yayi sanyi daga jiya zuwa yau. "Kai ma ka huta da sannun nan!" "A'a Ummuna!" Ya fada yana bina har muka shiga cikin asibitin office din Dr muka isa, dukkanmu uku muka shiga. "Maman unborn twins kece a tafe ai sai ranar juma'a zaki dawo,?mu ga yanayin kwanciyarsu!" "Dama akwai matsala ne Dr Sagir?" "Eh kasan dake biyu ne daya ya kwanta daya kuma yana zaune, idan tayi sa'a lokacin haihuwarsu daya yana fita daya zai juya, idan aka samu matsala kuma wanda xai juya ba sai anyi aikinsa!" "Zauna Ummu, ai dole lamarin nan a hada da addu'a!" "Ranka ya dade zabe na ta karatowa!" Tsaki yayi yana faɗin. "Duk kome ya fita kaina wallahi, na gaji bakiɗaya!" "Allah ya tabbatar da alkhairi! Lafiya dai?" Ya tambaye mu yana kallon Sa'adiyya. "Lafiyar kenan test din HIV zaka mana, bakiɗaya ." "Tow!" Ya ce yana kallonmu, "amma ita Maman unborn twins lafiyarta lau, domin tana da kyakkyawar record a files dinmu." Gyara zama yayi yana faɗin. "ka ga wanann amarya ta ce." Ya juya yana zabga mata harara, kafin ya juya yana kallon Dr Sagir, "Ka mana gwajin bakiɗaya saboda Yarana kada su ɗauki wani cuta!" Tashi yayi ya bude wani drower ya fara ciro files dinmu ya mika mishi yana faɗin. "wannan file dinta ne da Yaranta da suke cikinta. Lafiyarta lau idan muka cire jininta da yake hawa. Bata da matsalar kome!" Kallon Dr Sagir yayi ya ce mishi. "ita wannan a gwada ta domin ina son kada ta shafa mana!" Wayar office din ya dauka ya kira Nurse can sai gasu har su biyu. Suka gaishe ni sannan suka wuce suka dibi jininsa na Sa'adiyya ce zata musu taurin kai ya daka mata tsawa, sannan ta tsaya aka diba nata. "Fadila ki kawowa Maman unborn twins, fruits." "Ok Dr!" Suka fita, Dr Sagir ya ce min. "Ina samun barci kuwa?" "Eh tow gani nan dai!" "Wani abu ya same ya ne?" "Bata samun barci ne cikin dare, haka yasa jininta yake hawa! Amma zan bata wani magani tana sha zata samu barci!" "Dr Sagir! Ya zanyi na kula da su ita da Yaranmu!" Kallona Dr yayi zai magana Fadila ta kawo min wani bowl da fruit. "Aunty Ummu gashi nan!" Amsa nayi ina faɗin. "na gode Yaya Sagir!" Kallona Tafida yayi yana faɗin. "Kun san juna ne?" "Eh bata gaya maka ba ne?" Ya kalle ni, yana murmushi, "Babanta Yayan Babana ne, sannan a hannun Babanta na tashi wannan asibitin ma shi ya gina min, a can Biu ma akwai daya asibitin duk sati a can nake spent weekend dina!" Juyawa Tafida yayi yana kallona, kafin ya juya ga Dr Sagir yana faɗin. "Ai zurfin ciki ne da ita!" Ni ma dai ban san dan uwana ba ne, sai da na fara awo idan nazo matukar ya san na zo zai ce na shiga nurse su duba ni a gabanshi. Lokacin da ya gaya min dangatarkarmu, ban yarda ba sai da ya kira Babana ya gaya mishi ai wurinsu nake awo, ya bani wayar muka gaisa da Babana, bayan mun gama wayar na ce mishi. "Don Allah kada ka gaya mishi abin da ya faru kaji, ka ga idan." "Ni likita ne, kuma na rantse da boye sirrin kowa kamar nawa!" Ko baya asibitin nazo za a gaya mishi, haka zai tawo yazo ya duba ni. "Sannu ko zaki kwanta ne?" Girgiza kai nayi ina faɗin. "A'a kawai xan mike kafana ne!" Tashi yayi ya dauko wani stool har biyu ya kawo gabana, ya saka min na gyara zamana, ina jingina. "Kina cin abinci kuwa?" Gyada kai nayi ina faɗin. "Eh!" Ina zaune a wurin Nurse Fadila ya shigo tana faɗin. "Dr an kawo maka sako daga jimeta!" "Ki zuba kankara a ciki a damawa Ummu Hadiyya a kawo!" "Tow Dr Sagir!" Ta fita. "Ummu bari a kawo miki madara da dafafe ne daga Yola aka kawo min." Mamaki ne ya kama Tafida. "Wannan kulawar fa?" "Kanwata ce!" Gyada kai yayi, ina zaune aka kawo madaran a wani bowl, na fara sha a hankalin ina gyada kai. "Ya Sagir! Wata sati xan kawo maka sako a kaiwa Baba da Mamawo!" "Allah ya kai mu!" Ina sha aka kawo result dinsu, yana gama dubawa ya kalle shi. "Babu wani abu sai dai ciwon sanyi, Ita take dashi zan dauraku akan Magani ita kan Ummu ba zan bata magani ba saboda bata da kome, idan kana son a haifa maka Yara da lafiya sai kun yi treatment din ciwon sanyinku!" "Idan kuma aka samu matsala fa!" "Yaran zasu iya mutuwa, ko a haife su da ciwon idanun ko suma da ciwon mafi akasari ana haifan Yara da ciwon ." "A'a rubuta mana maganin da zamu sha." Ni kuma ya haɗa min chocolate da wani kwali ya mika min. "Nauyinki yayi kasa, ki sha kafin ki dawo ban da skiping abinci, duk abinda kike so ki ci saboda idan babu nauyi tow yaran zasu samu matsalar domin yunwa zai kama su!" Wayyo Allah na, tuni Tafida ya rikice mana, tun a asibitin yake min sannu har muka iso gida ta wuce bangarensu. Ni kam Kayan ya kai kitchen ya zuba ai a firji. Ni kan kayan Dr Sagir ya haɗa min nake ci da abinci. Washi gari Abba ya aiko da cefene, Tafida ya shigo ya same ni ina shan ice cream, "ko zaki zo ki raba kayan nan ne?" Girgixa kai nayi ina faɗin. "Ta raba kawai!" "Tashi nace!" Yadda yayi maganar a dake na tashi a hankali, na nufi tsakar gidan na raba, kome na nuna mishi ya dauki nawa ya kai min. "Kaji nan ka cire guda hudu da danyen nama nayi maka dambu!" Zare idanun yayi yana faɗin. "Amma baki da lafiya fa!" Murmushi nayi ban ce mishi kome ba, na saka ya kira min Harira muka fara aikin kafin karfe shida na yamma na gama,na bawa Harira nata tayi ta godiya da wani abu tayi wanka. Sai ga yarinyar nan ta dawo tana min wanke-wanke da shara da gyaran gida, ni kuma ina girki a daddafe Tafida yayi kwana biyar ya dirko dakina da sunan ya gama kwanakin kenan. Tunda na ga haka na rufawa kaina asiri da nuna mishi ina fama da kaina, na zata zai yi hakuri ne sai naga ashe ba haka bane, jarababshi ta kawo shi kamar bai da mace a gidan. Kwana biyu bai waiwaye ni ba amma yau da ya waiwaya sai da naji kamar abin cikin zai fito bakiɗaya. Washi gari tun asuba naji ana ta buge buge da fada. Sallah nayi na koma na kwanta, ashe fada aka yi ya maketa, karshe aka kai sharia gaban Abba, ya ce ai babu ruwanshi. Sai gashi an fara ganin laifina dama nasan kome ya faru Ni ce, ina fama da kaina aka ce na sace mata girki a kwanakinta . Ban damu ba na zuba musu idanu. Cikina yana wata takwas Kanwarshi Sabirah ta rasu wurin haihuwa. Dama hanya nake nima rasuwar ya bani na tafi na bi yan gaisuwa. Na bar masa Matarshi a lokacin sun tafi yawon campaign, tunda na isa a matuƙar wahale, haka ta tsaya a kaina duk da itama bata da lafiya, ba karamin tausayi ta bani ba Allah yasa nazo da kudi, Yaranta mata kamar ba Uwarsu ba. Tafida baya gari lokacin da ya dawo yaji labarin na tafi ranshi ya b'aci . Yana kirana na ce mishi. "Kazo ka ɗauke ni kawai idan kayi niyya!" Kamar wanda na bashi umarni ranar addu'ar bakwai ya shigo cikin gidan. Ina zaune a wurin suyar masa, ya shigo ya zabga min harara. "Wannan uban nisan kika kwaso katon cikinki salon ki haifa min Yara a gefen titi ko? Ummu baki gane condition dinki bane? Fisabiilillahi idan wani abu ya same ku fa? Kin san yadda aka yi na dauki kwanaki ina zulumi? Idan wani abu ya same ki ba zan yafewa kaina ba, kuma wallahi ki daina min shishigi!" Kuma kada kuyi tsammanin a kebe yake maganar nan. Deen yana bayanshi yana murmushi. "Ummu don Allah a me kika bashi ya zama bita-zaizai haka?" Yana dariya. Ni kan kunya ya kama ni, na tashi da kyar ina faɗin. "ku shiga Hajiya tana ciki, zan kawo muku abincin karyawa." Riko hannuna yayi yana faɗin. "a'a muje ki zauna ki huta waye ya sani ko tun zuwanki kike musu aiki!" Ya fada yana hararata. Har cikin dakin na kai su suka zauna suna gaida Hajiya na fita na fara hada abincin yan uwansu da suke abokan wasa Sai tsiya suke min. "Ummu gaya mana gaskiya me kika bashi ya sha!" Dariya nayi na zuba musu kunu da masar. Na kai dakin, sannan na fito na dauki miyar da haka kawai nayi tun jiya ina fatan kada ya bani kunya Tafida yaki zuwa. Cikin hukuncin Allah sai gasu da safe sun shigo ashe tun daren jiya suka shigo. Sai nafi Hajiya Murna, kallonshi take cike da so da kauna. Bai tab'a zuwa ba ko wancan zuwa da yan uwansa suka zo bai zo ba. Yana cin abinci Rukayya ta shiga. "Tafida bamu da kudin mota. Ko zaka taimaka mana ne?" "Rukky ina zaki kai kudi ne? Ina baki kudi amma kamar ina baki kasa? Fisabiilillahi." "Shi kenan kada ka bani ka kunyata Ni a gaban makiyana!" Murmushi nai tare da barin dakin ta ja tsaki. "Bana son haka, kada ki d'aga min hankalin matatta jininta ya hau." "Sannu yaushe ta samu zama a ranka!" "Aunty Rukayya kefa babba ce! Yarinyar nan tana mutuntatta ki sai zubda mutuncinki kike akan idanunta!" Inji Deen. "Hmm!" Dake tana son Abu a hannun Tafida kuma tasan matukar yana tare da Deen baya barinshi haka sai ya saka yayi mata. Shigowa nayi da kofin tea har biyu na ajiye musu. "Gashi babu dambu nasan kana so da bread!" Murmushi yayi yana faɗin. "akwai sauran na ai na zo da shi!" Mika min key motar yayi ya ce. "Je ki dauko min!" Make kafadarshi Deen yayi yana faɗin. "Sannu uban yan son zuciya, tunda muka shigo take shiga da fita, dan banza zata kuma fita har waje tayi wani aikin!" Karban key din yai ya fita. "Ayya Yayana da ka bari na tafi na dauko!" Haka ya share ni, ya dauko bokitin, yana kawowa na zuba mishi na raba biyu na bawa Hajiya tayi ta godiya. Bayan la'asar aka yi addu'a, tun da yazo muka kebe na mishi magana akan Hajiya itama bata da lafiya. Ya share ni. Jan hancina nayi ya d'ago kai yana kallona. "Yaran Dady kun ga zata fara ko? Ni dai ban mata kome ba kawai ita ce dai da rikicinta." Ai kuwa na fashe da kuka, "ya isa me kike so?" "Abinci da kulawa kaga mijinta yanzu baya raye sannan Yarann sabira zata rike su a rage mata dawainiyya!" Sosai goshinsa yayi yana faɗin. "hmm! Naji!" Ya fada yana mikewa. Ya dawo gabana ya durkusa yana kallon cikina. "Yarana kuna kewata ko?" Ya fada yana shafa cikin. "Zan kawo Nanny har biyu su taya ki reno, domin naga ke baki da lokacin kula dasu. Sannan ba zasu sha nono ba saboda!" "Saboda ni yar karamar gajeruwar mace ko?" "No ba haka ba ne!" Hmm Tafida ba zai tab'a canjawa ba. Haka na gayawa raina ba zai canja ba. Haka muka kwana da zan fita ya mika min kuɗi yace min. "Wannan ki bawa Hajiya, wannan kuma ki bawa Rukky!" "Allah ya saka da alkhairi!" Na fita na nufi cikin gidan, na samu suna ta mita. Mika musu kudin nayi na nufi Hajiya na mika mata nata, na ciro wanda na riko mata na mika mata. "Hajiya xan bisu ya ce, Allah ya ƙara miki hakuri!" Godiya take min kamar ta durkusa min. Muna haka ya shigo ta kalle shi a raunanane ta ce mishi. "Allah ya saka da alkhairi! Na gode Allah ya biya maka bukatarka na alkhairi ya baka sa'a da nasara akan abinda kake nima, ka rike Ummu mace ce ta gari tana da mutunci kuma ta fito daga gidan da ya dace kayi hakuri Baba Ali kayi hakuri da yan uwanka kai ne karami kai ne babba Allah ya baka matsayin ne don ya jaraba imaninka!" "Amin Amin Amin!" Deen yake faɗa yana kara fada "Tafida ni gaskiya ku xan bi ke bashi kudinsa" inji Aunty Maryam, itama Rukayya, haka ta hakura amma ta ki bada kudin, ya ce musu. "Kada ku takura mata domin ni gaskiya muje tasha nayi shatar mota ku tafi ni kwanciya nake son tayi saboda Yarana." Ai kuwa tashar ya kai su tare da ɗaukar musu mota nasu iya su, haka muka bar garin cike da kewar Hajiya. Maryam bata so ba don haka ta gayawa drive yayi ta bibiyar su Tafida. Haka kuwa aka yi duk inda aka tsaya sai sun tsaya domin ayi musu abinda ake min. Haka muka shigo Maiduguri ya kai su gidajensu. Lokacin da muka dawo Abba da kanshi ya zo gaida ni, nayi ta dariya ina faɗin. "Abba na dawo babu tsaraba!" "A'a da kika dawo lafiya ma ai arziki ne!" Haka ya gama gaida ni ya fita. Bayan na dawo na zata zan huta ashe ba haka ba domin kuwa Sa'adiyya da Uwarta suka saka ni a gaba, na farko cikin ya hanani barci, haka yasa cikin dare zan ga Sa'adiyya ta shigo dakina tsirara musamman idan baya gari, ganin haka na fara daina barci nima sai na maida hankali wurin raya daren, amma a haka nake jin kamar na bar gidan. A hankali na je na gayawa Mama ranar a naje awo nace Sagir ya kai ni gida, lokacin da muka isa Mama ranta ya b'aci don bata son alaka.da nake da yan uwan Babana. Da na kwanta ina nishi. "Mama bana son tashin hankali, amma ina ganin ya dace ki tsaya min na samu yancina, Mama gidan Tafida jin shi nake kamar wuta ake hura min wura min." "Nayi miki alkawarin tsaya miki gabanki da bayanki, amma dole kiyi hakuri." Wannan shine karo na uku da take min alƙawarin. Sai yamma da suka dawo campaign yazo ya dauke ni, yana ta Godiya. "Wai Ummu meye matsalarki ne?" Ya kalle ni yadda na lalace!" "Zaman gidan ne bana so." Shafa kaina yayi yana shiru kafin muna isa ya raka ni cikin gidan, sannan ya wuce wurin Abba, ban san me ye matsalar ba sai dai tun ranar ya fara kawo min ruwa a goran swan yana kawo min, ashe rubutu ake da Farin zuma ana wankewa da ruwan zam-zam. Tunda na fara sha barci ya fara zuwa min, ina hutawa shima ya rage yawan tafiyarshi, sannan cikin dare zai dawo ya kwana a gida domin lafiyar cikina. Ana haka zabe yazo aka yi cikin kwanciyar hankali aka fara na shugaban kasa, sati biyu a tsakani aka.yi na gwamnonin. A nan Borno Tafida da wani Yaron Alhaji Mansur Goza aka yi takarar kuma Allah ya ba Tafida sa'a. Koda yake Sa'adi ta fita campaign amma ni ko waje ban fita ba, wani labari me dad'i shine yadda yan ƙaramar hukumar biu suka zaɓi Tafida saboda yana aurena. Tun daga nan Tafida ya kara ganina da kima. Tun da aka fitar da sakamakon nake nakuda a tsaye, mun yi sintirin asibiti har na gaji. Haka muka hakura jiran ciwon. Wani abin mamaki kiri-kiri yan uwanshi da wanda suke uba daya suka koma gindin Sa'adiyya, musamman yadda ta fita campaign sai suke ganin ai ita tafi dacewa da zama First Lady, ni dama bai dame Ni ba ina dalili. Tinah ta kirani tana taya ni murna, a wannan lokacin Abba hakuri yake bani domin tunda aka ce shi yasa ci ya dan rage bani lokacinsa. A haka Shuwa tana ganin kamar sun shiga tsakaninmu ne. A hankali kome ya zo karshe zuwa daren da za a kawo ni asibiti, yaso ya gayawa yan gidan nace a'a muje kawai. A lokacin da muka je Dr Sagir baya nan. Nabila ne a daren har wurin asuba kafin Allah ya sauke ni lafiya.. **** Dawo labari Ajiyar zuciya na sauke ina jan kukan da y zo min, "Wai Ummu saboda nace ki koma dakinki kike wannan kukan? Ummu idan don haka ne Ummu ki zauna muna goga kafada da kugu wuri guda, kowa yana dakinsa yana rufawa kanshi asiri ke zaki tona min asiri a saka ni a gaba da habaici da gori?" A hankali na bude idanu na kalleta, kafin nayi magana ta dasa da cewa. "Ba zan takura miki ba, amma ki sani har abada ba zan tab'a farin ciki ba idan kika kashe aurenki!" Tashi nayi zaune idanuna sun yi fulu-fulu, don kumburi gashi babu barcin da nayi, hasken da nake gani ya fara daukewa a hankali na dunguro daga gadon ai kuwa ta sake salati....... *Wash hannuna! Anan na kawo karshen free Page na labarin Ummu da Tafida! Hmmm Ga Ummu Hadiyya ga Tafida mai girma Gwamna! Wannan ba labarin soyayya ba ne kamar yadda kuke gani labarin gidan aure ne da yadda ake gwagwarmayar gidan aure. Yes ba labarin da zan cika ku da soyayya kiss! Sex scene da sauransu wani bangare ne na wata rayu idan har soyayya zata biyo baya tow ba mamaki farin ciki zata wanzu a zukatan masu hakuri da Imani! Ina labarin Mahmoud? Shin ya hakura da kudirinsa ko har yau yana bibiyar motsin Ummu! Shin Ummu zata hakura ta koma dakinta ko zata rabu da Tafida kamar yadda ta ce! Shin Tafida zai sake ta kuwa ko zai cigaba da riketa kamar yadda ya fada, Mahmoud zai samu biyan bukatarshi akan Ummu kuwa! Ya Tafiyar Sa'adiyya da Yan uwan Mijinta? Shin zasu dawo jikin Ummu? Ya Mahaifiyar Tafida Ummu zata iya dawowa Hajiya dan ta kuwa? SHIN AKWAI SOYAYYA? INDAI AKWAI SHIN WAYE ZAI iya amayar da nashi don.a koma sabuwar duniya! Tafida zai iya rike Borno kuwa a matsayinsa na gwamna! Sa'adi ta saka smarty ya lalata fake soyayyar Ummu da Tafida shin wai me zai faru? Hmmm wannan labarin ko? Ban yi kome ba domin idan tafiya yayi tafiya gumurzu zai fito rikici da soyayya zai jagoranci Yar Mace, wacece Yar macen nan ne?......* TAFIDA UMMU DEEN MAHMOUD SA'ADIYYA ...... ALL IN YAR MACE kowa da kuka gani zai taka nashi matsayin don haka ku biyo alkalamin Uwar Muwaddah Ammyn Anum! Mai rikon Walid 😂🐐🤣 500 NE MALAMA IDAN KIKA GA LABARIN NAN A WAJE TOW SATOWA AKA YI Yawwa na gaya muku na kudi ne.. Zan tafi hutu sai Friday zan cigaba in sha Allah.... 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76https://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw *R&U BAG's GALLERY! Wai da gaske kun manta ne na gaya muku? Tow R&U ta kara dawo muku da kayan ado da kawwa wanda Ummu First Lady take amfani da su, tow dai Ummu tace na gaya muku a sirrince! Kawo kunnunku 🙉 a wannan R&U BAG's GALLERY babu abinda babu domin kamar kanti kwari ne a gidanki! Muna da kaya irinsu Atamfa, lace, shadda! Karewa dai har da lefe, kayan fadar kishiya, kayan Fitar suna na mai jego, kayan toshi na wanda saurayi zai kaiwa budurwa! Waya miyar sai a mota, muna bada dai-dai har da sari ku shiga domin tabbatarwa idanunku* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Innalillahi wainnalihir rajouna! Ummu!" Ta kira sunana da karfi tare da nufo kaina, tana salati wannan salatin ya tashi Uwani daga barcin da suke ita da Zakiya, suka shigo dakin da gudu. Ganin yadda Mama take kokarin d'ago ni amma jikinta ya mutu, ita kanta zaune take akan gwiwarta. Da gudu Uwani ta fita tare da nufar waje tayi ya buga kofar Baba, ai kuwa suka tawo tare ganin halin da nake ciki ya fita yana salati ya taso kawu gwani. Aka fita da ni zuwa asibitin Dr Sagir. Har gari ya waye Dr Sagir yana kaina. Sai da garin ya fara haske ya nufi waje yana kallon Baba. "Don Allah kada a shiga da kanta zata farka!" "In sha Allah!" Sai lokacin suka nufi massalaci, bayan sun yi sallah Baba da Kawu Gwani suka dawo gida, Uwani ta hada abin karyawa aka saka a basket aka kawo asibiti. Ban farka ba sai karfe biyu na rana, Tafida na gani zaune a gabana yana ta jijjiga Mufidah da take rigima. Ajiyar zuciya na sannan na fara yunkurin tashi ya ce min. "Da dai kin jira a zo a duba ki!" Ya fita da Yarinyar a kafadarshi, can kuwa sai gashi tare da Dr Sagir, yana tsaye a kanmu ana duba ni. "Ummu!" "Hmm!" "Yanzu ya kike ji?" "Kan dai yana ciwo!" "Sannu bari a kara miki alluran kiyi barci ko zai daina!" "Sallah zan yi!" "Ok?" Ya fada yana kallon Fadila. "Ko zaki cire mata ruwan!" Haka ta cire min ruwan. Na tashi zaune ajiye Mufidah yayi ya ce. "Kawo hannunki!" "Bar shi kawai!" Na fada ina dauke kaina, zungure min kai yayi yana faɗin. "Oya tashi kada ki saka a ji labarin Tafida ya ajiye mukaminsa ya tare asibiti." Dago fararen idanuna nayi ina kallonshi. "Kasan me?" Girgiza kai yayi yana faɗin."kasan me?" Yayi wani iri da bakinshi, "ka fita bana son ganinka!" Na fada ina kokarin mikewa,na fada ina kauda kaina. "Akan me?" A hankali na sauke kafana kasa, na saka takalmin da na gani a dakin. A hankali jiri ya nime kada ni, yayi maza ya rike ni. "Ki kula!" Ture shi nayi tare da bin jikin gadon zuwa bangon dakin. "Ki bari na rike ki mana!" "Ka tafi nace!" Na fada ina bude ban dakin na shiga. Tunda na shiga na jima a ban dakin, kafin na fito. Yana tsaye kamar an dasa shi, "nace ka tafi!" "Me yasa kike ture ni daga jikinki!" "Saboda bana son ganinka." Daga haka na nufi inda ya shimfida min abin sallah, wani irin b'acin rai nake ji kanshi. Haka nayi sallah ina sallah kuka nake, domin na fahimci yana nan har yanzu. Koda na idar hade kaina da gwiwata nayi na cigaba da kuka. Shigowar Abba da Babana tare da baba bulama, yasa shi mikewa yana me gaida su. "Ummu lafiya kike kuka kuma?" Cak kukan ya tsaya min sakamakon muryan Babana da na ji, "babu kome!" " akan me zaki ce babu kome bayan Muryanki har waje!" "Baba kayi min addu'a na mutu!" A wani irin razane Tafida ya nufo ni, "kada ka zo inda nake!" Na fada ina kara k'amkame jikina. "Kada kazo don Allah ka tafi nace bana son ganinka don Allah!" Yadda nake maganar yasa bakiɗaya iyayenmu suka shiga kallona musamman Babana. "Kul na kara jin haka, Mijinki kike kora haka." "Kyaleta Alhaji Kabiru tayi ba mamaki bata son ganinshi ne! Jeka." Inji Abbanshi, "ina zai je? Idan bai zauna kusa da ita ba a ina zai zauna? Matarshi ce Jadda kyale ta bana son fitina irina su na mata." Babana ya fada, shigowan Doctor Sagir yasa suka fita. "Ummu tashi ki kwanta!" "Kyaleta na ga gudun ruwnata! Ummu ki gaya min me nayi miki da zafi kike min irin wannan tozarcin?" D'ago kai nayi zan yi magana a hankali naji bakiɗaya duhu ya mamaye idanuna. Ji nayi na tafi bakiɗaya can nesa nake jin kamar ana kiran sunana daga nan ban kuma sanin me yake faruwa ba. Daga asibiti gida ya wuce a matuƙar fusace, a parlour ya samu Sa'adiyya ta cab'a kwalliya, ta mike cikin tarairaya tana faɗin. "Welcome back His Excellency!" Dama haushin Ummu ta b'ata mishi rai ya zuba mata idanun. So yake ya gano inda Sa'adiyya ta fi Ummu. So yake ya hango, "hancinki yana da kyau amma da yazo nan dai yayi tukunya, ita kuma hancinta premature ne saboda yanayinta da bata da girman jiki, haihuwa daya tayi amma kamar yar shekara shida ke idan kika haihu sai dai a bude kofar gida domin zaki koma kamar saniyar hud'a" kamar bashi yayi maganar ba, ya wuce dakinsa daren jiya fa sun kwana lafiya,har yau garin Allah da ya waye amma yanzu ji yadda ya banka mata bakar magana. Yana shiga dakinsa ya zauna shiru, tabbas idan bai yi da gaske ba yana ji yana gani Ummu zata subuce mishi. Babu abinda ya kara b'ata mishi rai kamar yadda Dr Sagir ya ce mishi. *Ranka ya dade! Idan da hali ka daina zuwa ganinta domin jininta mun samu ya sauke jiya har zuwa yau, yanzu tana ganinka jininta ya kuma hawa muna tsoron kada ya tab'a mata zuciya nayi tunani kodan Yaranka!* Shi fa yanzu tunda Ummu ta haifa mishi yara yake ji kamar kaf duniya babu abinda za'a ce ya kasa amincewa. Ajiyar zuciya ya sauke yana jin wayarshi tana tsiwa amma bai d'aga ba. Sake kiran aka yi ya dauka yana faɗin. "Deen!" "Naje asibitin baka nan!" "Deen Ummu bata son ganina!" "Kamar ya?" "Wallahi Ummu taki jini na ban san me nayi mata da zafi ba! Don Allah ka san me na mata?" "Kai da kake tare da ita baka san me ka mata ba, sai ni da nake waje zan sani kai dai ka binciki kanka!" Zare hular kanshi yayi yana faɗin. "Na rantse maka ban san me nayi mata ba, yarinyar nan ko ana saura kwanaki ta haihu sai da ta min dambu yanzu dambu ya kare, sannan miyar da take yi ta ajiye yanxu babu, wallahi rabona da naci abinci me dadi na manta!" "Ok yanxu saboda yunwar cikinka kake son Ummu ta dawo?" Deen ya tambaye shi, "Tow ya kake son nace? Yarinyar nan tasan yadda nake son zama da ita fisabiilillahi ita!" "Tafida tambayarka nake saboda yunwar cikinka kake son ta dawo?" "Eh a'a!" "Ok akan me kake son ta dawo?" "Har ga Allah akwai nutsuwr da nake samu a tare da ita ne, sannan." "Aliyu na fito maka zahiri mutum? Tow ai lamarinka idan dai akan haka ne Ummu ba zata dawo ba, domin abu biyu ya bayyana a maganarka! Na farko don kasan kaf duniya abincinta zaka ci cikin natsuwa da yarda da kai, na biyu ita ce macen da ka fara sani, sannan ta rike maka darajarkanta. Idan akan wannan ne tow kayi hakuri Ummu zai yiwu ta dawo gare ka!" "Deen dole ta dawo ai tana jin maganar iyayenta da manya!" "Nayi maka alkawarin idan ta dawo don dole sai nayi azumin kaffara na wata gudu!" Ai kuwa ya fara masifa kamar Deen din yana gabanshi. "Ban da iskanci taya na kiraka ka gaya min magana, Ummu kanwarka ce da zaka tsaya kana min munafunci munafuki waye ya sani ko kai kake zugata." "Eh ni nake zuga ta nace kada ta sake ta dawo gidanka mutumin kawai!" "Ni kake gayawa Magana kasan da wanda kake magana?" "Da wanann mara jin maganar me shegen taurin kai da rashin kunya Tafida nake nufi da kai nake magana Look ka ajiye iskanci kayi facing reality dinku." Tsaki yayi ya ajiye wayar Ummu zata ga iskanci Umara zai tafi ma da Sa'adiyya. Kiran Mahmoud yayi ya gaya mishi abinda yake bukata da kuma rigimarsu da Ummu, cikin takaici da baƙin ciki. "Wallahi da ni ne saketa zan yi haba da girmanka da darajarka sai wani baka wahala take kamar ta samu wani danta! Ka yarda kwallon managoro ka huta da kud'a." "Ai kasan Alhaji ba zai yarda na sake ta ba nima ai na gaji wallahi!" "Ok shi kenan zan yi abinda ya dace." Daga haka suka kashe wayar. Mahmoud. A lokacin da Tafida ya kira shi, yana parlourn gidanshi ne, yar aikin matarshi ya saka a gaba yake ta lalata da ita. Jin kiran Tafida bai saka ya tsagaita wuta ba, sai da ya gaya mishi rigimarshi da Ummu tuni ya zare. Kallon yarinyar yayi yana hango yanayinta da Ummu, dama abinda ya sa shi fara lalata yarinyar kenan yanayinta kamar Ummu bata da tsawo gata yar siririya. Shafa fuskarta yayi yana faɗin "ki nutsu mu mori juna, babu abin da zai faru." Ya cigaba da abin da yake yi. Da sauri ya sauka akan yarinyar yana me nufar ban daki, Maza fita kada na same ki a dakina!" Ya shiga yayi wanka idan har Tafida basu shirya da Ummu ba tabbas abin da zai faru saki zata bugata idan ya sake ta haka zai bashi damar niman soyayyarta. Murmushi yayi a karo na uku yana ban dakin ya gama ya fito, ya shirya sake kiran Tafida yayi cikin kame-kame ya ce mishi. "Naji kana cewa Ummu bata da lafiya ko?" "Eh tana asibiti!" Ya fada mishi. "Ok dama zan kai Madam ne ta gaishe ta!" "Ba damuwa!" Ya faɗa, murmushi yayi yana faɗin. "Shege Allah yasa kun rabu kenan har abada." Ya fada yana shiryawa sannan ya fito daga dakin cikin shigar kananun kaya ya nufi bangaren iyayenshi. "Ammyn zan tafi na duba matar Tafida bata da lafiya?" "Allah ya bata lafiya, sannan ina Yarinyar nan take ne ba halin na tura ta wurinku aiki sai ta tafi nata yawon!" Cikin ko in kula ya ce mata. "Oho ni ai na jima da gaya muku bana bukatar yar aiki amma kuka ƙi yaran da ko an dauke su basu da wani aiki sai rashin ji!" "Ni dai ka rufa min asiri kada na ji kada na gani wani abu ya sami yar mutane, aiki na dauke ta kuma marainiya ce bata da kowa sai yar Uwarta don Allah kada labarin da nake ji a waje ya zo gidana!" Inji Hajiya Haulatu, mahaifiyar Mahmoud, saboda tasan halin danta kud'a baka haramun ne, cikin borin kunya ya ce mata. "Fisabiilillahi Ammyn da ace Rayyan ne ba zaki fadi haka ba, sai ni saboda kawai abin da mutane suke fada " yadda yake maganar zuciyarshi na tsannanta bugawa domin tabbas idan ya sake Ammyn tasan yana lalata da yarinyar me suna Khairat ya mutu ya lalace domin sai ta masifar bata mishi rai. "Ni xan tafi Allah yana gani!" Ya fada yana kokarin barin dakin, shigowar Khairat din ta nime wuri ta zauna. A hankali kallonta Hajiya Haulatu tayi a tsannake. "Ke Khairat daga ina kike?" "Ammyn na tsaya wanke kayan Aunty ne!" Shiru Hajiya Haulatu tayi tana faɗin. "Allah ya kyauta!" Zama yayi cikin motarshi yayi shiru, gabanshi yana tsannanta bugawa. Domin lissafinshi sai yanxu ya zo mishi dole ya iya takunshi idan ba haka ba duk ranar da Ammyn ta samu labarin abinda yake sai ya yi danasanin. Shi kuma abin da zai bata mishi ran iyayenshi yake gudu, yasa yake mamakin yadda Tafida bai dauki iyayenshi da daraja ba, shi ai ko Iyayenshi yanka namar jikinshi suke ba zai tab'a kinsu ba. Balle shi Tafida hatta rike Matarshi iyayenshi suke mishi. Tsaki yai yana jan Motarshi. Koda ya isa asibitin Mama ya samu dakin tana jijiga Mufid da yake rikici. "Sannu Mama ya me jikin?" "Da sauki Malam Mahmoud! Ya mutanen gidan?" "Suna lafiya!" Ya fada yana zama a kujeran dakin, turo kofar dakin aka yi Deen ne dauke da basket da bakar jakar leda. Wani haɗe rai yayi yana me gajeruwar sallama. "Sannu Malam Safiyyudeen! Sannu da kokari." "Yawwa Mama, Mufidah tayi barci ko?" "Eh tayi Mufid din ne dai yake rikici uwar bata cikin nutsuwarta balle ta basu nono." "Ai lalura ce, Dr Sagir ya ce min yawan rikicinsu har da yunwa shine na kawo musu madaran gwangwani a fara basu kafin uwar ta samu lafiya!" "Allah ya saka da alkhairi!" Sannan ya ajiye mata basket din abincin yana faɗin. "sakon Ammah ne wannan!" "Kai Masha Allah mun gode Allah ya saka da alkhairi!" "Amin Ya Allah!" "Kazo ne?" "Eh ya kake?" "Alhamdulillahi? Tow Mama zan tafi idan ta farka a gaya mata Ammah tana gaishe ta." "In sha Allah!" Inji Mama, "Mahmoud sai mun sake haduwa!" "Ok nima fita xan yi!" Shima yayiwa Mama sallama suka fito. "ban gane ba ne, Matar Tafida ce ko Matar Safiyyudeen? Domin naga hidimar kamar na matarka ko kana zaga Tafida ne?" Dariya Safiyyudeen yayi yana faɗin. "Allah ya min tsari da kallon abincin da guba ne a gare ni, Ni Deen Allah ya haramta min shiga gonar wasu. Iya nawa ya wadatar da ni." Mahmoud zai kara magana Deen ya ce mishi. "Shawara daya zan baka, kada ka sake Tafida ya samu labarin ka tab'a kokarin hakewa Matarshi, don na lura akan Ummu zai iya taka uban kowa ya kwana lafiya!" Fisgo shi Mahmoud yayi yana faɗin. "A ina ka ji labarin nan?" Dariya Safiyyudeen yayi yana faɗin. "Ka zata kowa banza ne irinka?" "Ummu ce ta gaya maka?" "Baiwar Allah ta rufa maka asiri a yawon barbadarka ka gayawa mutane aka gaya min." Fuskarshi ya maida kamar ta yara ya nuna shi da yatsa yana faɗin. "na gaya maka duk ranar da ya samu labarin hatta yankaka tayi domin ta zare mutuncinta, Wayyo!" Deen ya rike bakinshi. "Ta kare maka!" Ya fita daga kofar ward din yana me nufar inda Motarshi take, yana shiga motar ya zauna yana tuna wanda ya gaya mishi. Wani Yaronsu ne mai suna alguburo, Yaron shi yake kawowa Mahmoud matan banza tow ya kai masa wata yarinyar yayi kome da ita amma yaki biya shine yarinyar tayi ta kiran Alguburo tana gaya mishi magana ya kashe wayar kashe ta biyo shi tana mishi tijara, Deen ya kashe rigimar ta hanyar tura mata kudin Mahmoud da yake wurinsa, domin suna hada kudi haka kawai ana sadaka da shi kuma Deen yake haɗawa. Shine Deen yake yiwa Yaron fada. Ya ce mishi. "Fisabiilillah kai kaga wannan rayuwar da kuke ya dace? Baka tunanin za a yiwa iyalanku haka!" "Oga Deen wallahi ba aikina bane Oga Mahmoud yake tura ni na dauko su,sannan gaskiya ku saka idanun akan Matanku da kannenku domin Oga Mahmoud bai da kyau haka lokacin da ya nime matar Oga Tafida shine ta yanke shi a cikin don Allah ka saka idanun akan kanwarka Jalilah domin ya sha fada min duk wani abu me kyau da daraja kune kuka hada, sannan akwai wata mata da bansan wacce ita ba,tana da alaƙa da ku suna tare da ita gaskiya ban san ta ba domin baya waya da ita a gabana. Idan zai yi ma baya yarda na fahimci wacce ita!" Tun daga ranar kiri-kiri Deen ya hana Jalilah zaman gidansu ya mai da ita gidanshi sannan ya mata wani irin kashedin da tasan tabbas zai aikata domin yace koda wasa ya samu tana da alaƙa da Mahmoud wallahi sai ya kashe ta har lahira kuma ba zai nadama ba. Tana mugun tsoronshi Matarshi ma ya hana ta alaka da Matar Mahmoud domin itama Matar ba wani tarbiyyar ce da ita ba. Shi yasa a wannan lokacin baya bukatar Tafida ya ce zai yi wani abu da Mahmoud zai fahimci ainihin abinda yake faruwa a tsakaninsu da Ummu. Domin yin haka kamar bada kofa ne,yasan waye Mahmoud yasan idan yasaka abu a gabanshi sai ya cimma, sai dai bai kai Tafida tijara ba, shi fatan shi kada Tafida ya gano abin da yake faruwa, duk ranar da haka ya faru a yadda ya fahimci Tafida ya fara gano amfanin Ummu a rayuwarsa tow gaba yana fatar idan har ya fahimci wacece Ummu a rayuwarshi anan ne zai tsaya mishi da yakin dawo da ita. -- Shafa kai Mahmoud yayi yana kallon Motar Deen da ya fitar da ita daga asibitin. Murmushi yayi yana faɗin. "Deen baka isa raba ni da abinda nake so ba. Ummu Hadiyya mallakar zuciyata ce, tabbas idan ban samu Ummu ba to sai dai Mutuwa nayi matukar ina raye Ummu tawa ce." Haka ya nufi wurin Motarshi ya shiga, ya nufi office din hukumar mahajjata, yayi duk abinda zai yi sannan ya kira Tafida ya gaya masa ya gama kome. --- *TAFIDA* Juyawa abincin yake yana kallonshi kafin ya ajiye cokalin, ya mike tare da nufar cikin gidan. Kowa yana ta sha'aninsa. Parlourn Abba ya nufa da sallama ya shiga cikin parlour. Zama yayi yana kallon abincin Abba. "Sannu Abba!" "Yawwa Tafida!" Abba ya amsa mishi. "Yaushe zaka tare a gidanka na gwamnati?" Shafa kanshi yayi yana faɗin. "Ina jiran Ummu ne?" "Ai tow shi kenan ai!" Gyara zama yayi yana faɗin. "Abba dama nazo ka saka baki!" "Baki a ina?" Cike mamaki Tafida yake kallon Abba. "Akan lamarina da Ummu, Abba ta kusan arba'in ta dawo dakinta haka." "Wannan tsakaninka ne da ita idan ta ce zata dawo ai shi kenan sai fatan Alkhairi." "Abba ba zata dawo ba!" "Ai haba?" Yadda Abba ya mai da lamarin wasa yasa Tafida ya harzuka. "Abba!" "Kaga lokacin da na nima maka ita ka aike ni ne? Daga lokacin da aka bata aurenta nayi maka wani abu ne acikin gidanka? Aliyu ka je kai da matarka da kake so babu ruwana." Cikin haushi da zafin rai kamar zai fasa ihu. "Shi kenan idan na dawo daga Umara xan bata abin da take so " ya mike ya fita daga dakin a fusace, har yana kwallo da butar karfen Abba. Sunkuyar da kai Abba yayi idanunshi yana cika da kwalla. "Ya Allah kai ka bani Aliyu ya Allah kada ka kawo sanadin da zai rabu da yarinyar nan, Ya Allah kada ka sani nayi kuka akan Aliyu, Ya Allah ka shirya Aliyu tafarkin addinin Muslunci, Ya Allah ina jin ciwo da zafi Ya Allah kada ka.dauki rayuwata Aliyu bai shiryu! Ya Allah!" Ya fada a raunanane, har ga Allah Aliyu shine rauninsa. "In sha Allah Ubangiji zai amshi addu'arka, Allah ya shirya mu bakiɗaya!" Inji Hajiya Salamatu da ta zo ta zauna a gefenshi. Zata iya cewa ita ce silar lalacewar Tafida, ita ce ta raba shi da Uwarshi, amma bata tab'a zaton lalacewarshi zata kai har haka ba, ta godewa Allah da bata wanke hannunta da datti ba, domin a lokacin har Hajiya Shuwa tana faɗin ya saubanta rayuwarshi tow ba ayi ba kenan. "Duk yan uwansa suna cikin nutsuwa, da kwanciyar hankali amma shi da ya kasa rike mace daya ne da rigimar auren Mace biyu, hmm!" "Allah ya taya shi riko!" ** *SA'ADIYYA" "Ni wallahi ba xan iya rashin mutunci Tafida ba, haba fisabiilillahi wai yau matarshi ta fini kyau!" Tsaki shuwa tayi tana zaga dakin, "shegen Yaro duk yadda nake kashe kudina amma dan banza babu abinda yake aiki akanshi. " "Hmm ai na gaya miki mutanen kudinki suke ci fa." Wayarta ta janyo tana me kiran wani Malaminta da yayi mata aikin da aka matso da maganar auren Sa'adiyya aka ayi akan lokaci. "Malam yaron nan fa sai kara haukace mana yake wallahi, yarinyar ya bar gidan yanxu haka." "Ok rike wayar da fatan kina da kudi a wayar!" "Akwai malam!" Ya fada tana ajiyar zuciya. Tana rike da wayar har bayan minti goma ya ce mata. "Shuwa Yaron nan Uwarshi tana akan shi, Ubanshi yana kanshi. Yarinyar kuwa tun kafin ta haihu muka yi aiki akanta amma ya warware kuma yaron ya warware shuwa Yaron nan ya san me kike bukata a gare shi, idan kika matsa dayawa zai iya baki mamaki!" "Tow Malam maganar Matarshi fa?" Ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin. "Zan saka aljanu su kara dagula al'amarin amma akwai aikin da xan yi shine a rufe bakin yarinyar yadda ba zata tab'a amince ta dawo dakin ta ba. Amma maganar gaskiya wannan aikin yana bukatar kudi, sannan kafin nan ki tabbatar an nimo miki kudin da ya fito hannun Kuturu da wanda ya fito hannun makaho da wanda ya fito hannun Bebe, da wanda ya fito hannun kurma, ki hada bakiɗaya ki saya mana kifi tarwada me rai a saka a abu a kawo min Allah ya bamu sa'a!" "Tirkashi taya haka zai faru? " dariya yayi ya ce mata. "Kin ce yarki ta zauna a gidan ko? Kuturu yana da kuturta kuma mutane suna kyamarshi, makaho mutane na tausayarshi. Saboda makantashi. Ita yarinyar zata tayi ta kyamar komawa gidan shi, shi kuma zai ta tausayin yarki. Sannan yarinya zata zama kurma bata jin maganar kowa, sannan zata yi shiru da bakinta kamar bebiya yadda kowaye ya mata maganar ta koma dakin mijinta ba zata tab'a sauraronshi ba koda Uwarta ce. Idan har aiki zaki yi fa dole ki nimo kayan nan idan ba haka ba labarin da nake baki yarki tana gab da rasa Mijinta, sannan ki gaya mata ta kiyaye kanta domin ita ce zata lalata mana aiki kuma aikin mu idan muka yi miki kin san abin da yake karya shi? " "A'a ban sani ba Malam!" Murmushi yayi ya fada mata. "Ki gaya mata ta tsaya a inda take matuƙar bata nutsu ba, yarinyar zata dawo ba zato ba tsammani!" A fusace shuwa ta juya ga Yarta tana mata wani irin kallo. "Sannan Malam wacce hanya ke karya aikin?" "Sai kin zo min da kayan aikin!" Ya kashe wayar, hannu ta daura a kai tana jin kamar ta fasa ihu. "Yanzu kika sake aikin nan ya kuma lalacewa kamar wancan na aurenki wallahi sai na miki baki, ba zai yiwu tun da kuruciyata ake gaya min akwai wanda gidan da zan yi mulki da dan gidan yazo nazo ki raba Ni da wannan damar baki isa ba wallahi kika sake wannan aikin ya lalace sai na miki baki." Gyada kai tayi tana jin kamar tayi kuka, wancan aikin da suke maganar ya lalace kuwa an ce tana shiga dakin Ummu tsirara tana zagaye gadonta tow ba makawa Ummu ko ta bar gidan ko tayi hauka. Shine lokacin Ummu ta fara jin kamar idan tana gidan kamar zata yi hauka har tafida ya amso mata rubutu. Zuwa yanzu shirinsu akan Ummu ba karamin aiki bane domin su a ganinsu, kin dawowar da tayi yana daga cikin aikinsu da suka yi. ** *UMMU* Ban farka ba sai dare na farka wanka nayi nayi sallah, sannan na ci abinci naji bakiɗaya kamar an cire min ciwon kan da yake damuna. "Mama sannu!" Na fada mata tana shan kunu. "Yawwa Ummu, ya jikin naki?" Murmushi nayi ina faɗin ."da sauki sosai Mama, babu ciwon kan sai gajiya da rashin kuzari. " "Allah ya ƙara afwa!" Shigowa Doctor Sagir yayi yana faɗin. "Gawa taki rami!" "Sai na gayawa Babagaji!" "Mama ya me jiki?" "Da sauki!" "Da sauki!" "Baki tambayi kishiyar da angon ba!" "Na huta da yen-yen, da wasu muryansu a shake!" Murmushi yayi yana faɗin. "Kai Mama kina jin murya me dad'i!" Dariya tayi, "Sister ya jikin naki?" Ya dauki abin gwanji ya gwada kirjina, sannan ya gwada jinina. "Gobe zaki koma gida, sannan ban da cin gishiri banda amfani da ruwan zafi fa, ki raba kanki da tunani. Addu'a shi ne babban mafita ayi yawaita azkar ban da yawan tunani kin ga Baba yana cikin damuwa yanxu haka ya rasa yadda zai don Allah ki daina saka damuwa a ranki ko don mahaifin ki!" Sunkuyar da kai nayi ban ce kome ba, a sanyayye na d'ago kai ina son tambayarshi. "Shima bai da lafiya ne?" Saka hannu yayi a aljuhun rigarshi. "No zai iya kamuwa da ciwon ne matuƙar kina kwance kin san ke daya ya mallaka idan aka ce mishi ga halin da kike ci shima girma ya hau kanshi kwanciya zai yi ki tuna ko don shi You need to survive..... *Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML* *Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!* #Mai_Dambudhttps://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw *R&U BAG's GALLERY! Wai da gaske kun manta ne na gaya muku? Tow R&U ta kara dawo muku da kayan ado da kawwa wanda Ummu First Lady take amfani da su, tow dai Ummu tace na gaya muku a sirrince! Kawo kunnunku 🙉 a wannan R&U BAG's GALLERY babu abinda babu domin kamar kanti kwari ne a gidanki! Muna da kaya irinsu Atamfa, lace, shadda! Karewa dai har da lefe, kayan fadar kishiya, kayan Fitar suna na mai jego, kayan toshi na wanda saurayi zai kaiwa budurwa! Waya miyar sai a mota, muna bada dai-dai har da sari ku shiga domin tabbatarwa idanunku* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Hajiya Aisha!* Kallonta kawarta tayi ta kuma kalli kishiyar Hajiya Aishan wato Balaraba. "Wallahi Shatu ba zan yi kafarta ba Y'ayanki shiga tsakaninku aka yi, yanzu ya dace ki mori ribar Haihuwa amma ce kin barwa duniya su! Balaraba wannan abin ya dace kuwa?" Girgiza kai tayi tana faɗin. "Gaskiya abu bai yi dadi ba, kuma bata da lafiya sosai amma suka manta da ita!" Murmushi tayi me sanyi ta ce musu. "Basu manta da ni ba, tafiyar da nayi na barsu lokacin da suke buƙatar kulawata yasa suke jin babu dad'i amma nasan suna sane da ni!" Shigowar wasu Yara ne yan mata, Umma Marka ta mika Baban Yaron me suna Hafiz wayar Hajiya kai. "Hafizu kira min Ummu Hadiyya!" Hajiya bata so ba, amma babu yadda ta iya domin bata son su ce tana da taurin kai don sun damu da ita. Ai kuwa kira daya zuwa biyu ya shiga. "Hallo! Ummu Hadiyya ce?" Can cikin sanyin murya ta ce . "Eh Ni ce!" "Fisabiilillahi Ummu Hadiyya, ke da muke saka ran zaki gyara kome shine kika bari aka dawo da Hajiya Shatu? Bata da lafiya sosai tana kwance kome bata yiwa kanta, kada ki manta kema Uwace ban gaya miki haka don na muzanta miki amma ta saka rai akanki zaki gyara tsakaninta da Yaranta, Hadiyya ki yi wani abu domin kin san danta da Yaranta suna da halin taimaka mata don Allah ki yi wani abu kada ta mutu a wannan yanayin don Allah na zuba gwiwata a kasa ina rokon arziki." "Umma Marka ko?" "Eh Ni ce!" Ta fada da sauri, "ki ce tayi hakuri ta ba ni lokaci zuwa nan da gobe Allah ya taimaka mana y bamu sa'a!" "Amin Ya Allah! Ubangiji ya shiga lamarinki ya sakawa Yaranki tausayinki da jin kanki!" "Amin Ya Allah! Umma Marka ki bata hakuri in sha Allah zata samu lafiya!" "Tow Allah ya miki albarka ya bawa Yaranku ikon miki biyayya!" "Amin!" Kashe wayar Umma Marka tayi tana kallon Hajiya Shatu. "Yanzu ba gashi ba!" "Ai Aliyu ne yana jin na koma zai ta faɗa!" "Tsoron shi kike ji? Gwamna kika haifa fa? Daya maaikacin banki daya dan kasuwa me kike bukata kuma ko a jikinshi ai kin huta!" Gyada kai tayi tana hango rigimar Tafida. "Allah yasa mu dace!" Duk suka ce mata "Amin!" ** *Ummu Hadiyya* Kallona Mama tayi tana faɗin, "Kin san dai gobe za a sallame ki, kike bukata saka kanki cikin wani damuwar?" Kallonta nayi kafin na kurbi kunun da yake kofin da dan zafinsa. "Na sani!" "Tow Allah ya kyauta!" "Amin!" Na furta ina kallon Mufid da yake ta wasa shi daya Mufidah tana bayan Mama. "Mama me yasa Yara suke kin iyayensu bayan sun sha wuyarsu?" Girgiza kai tayi tana faɗin. "Daga Iyaye har Yaran akwai soyayya mai zafi da sanyi a tsakaninsu, matukar uwar ta shayar da dan na tsawon wata daya zuwa goma lokacin da ya fara gane dadin nono har abada soyayyar nan ba zata tab'a karewa ba. Sai dai idan shiga tsakani aka yi!" Ajiyar zuciya na sauke ina tuna irin laulayin da nayi sannan nazo nayi ta fama da matsanancin ciwo har na haihu amma ace Tafida da Yan uwanshi sun manta da hakkin Uwarsu. "Wani abu ne?" "A'a!" Na fada ina shan kunu. So nake Mama ta bar dakin amma kamar ta sani taki fita, muna haka sai ga Ummi tazo ita da Mahirah ta dauki Mufid tana faɗin. "My love gaya min gaskiya mintsini nawa Mamanmu tayi maka don na lura tafi son Mufidah akanka!" "Me xanyi da me kukan banja!" "Mamanmu cefenen yau babu nama haka zaki yi miyar kuka lami!" "Yau naga tijara a wurin iyayenta zamani Hajiya Balkisu idan zaku tafi ki tafi da shi na baki shi!" "Alhaji Bulama sai ya rushe kanshi don kada ya ga shi fari ne ya zata zan koma bayanshi nafi son Dan bakin mijina!" "Mahirah kin ji dai danki ban da masauki!" "Wannan hade kai kuka mishi don kunya dan beauty!" Haka suka yi ta hira da tsokanar Mufid una dariya, bayan sun gama suka mana sallama domin Kawu Gwani ya kawo su kuma ya dawo yana jiransu. Na rasa gane kan Gayen nan bakiɗaya yaki ko shigowa gaida ni. tare suka fita da Mama ta raka su na dauki wayata ina kallon waye xan kira! Deen wata zuciya ta gaya min sai naga kuma bai dace ba sai na kira Baban Ilham wato Umar. Bayan mun gaisa sama-sama nace mishi. Kawai sai na rasa me xan gaya mishi sai nace mishi. "Ina son magana da Maman Ilham ne!" "Ok tana zuwa zata kiraki!" Kashe wayar nayi ina cewa na gode. *Abba* abin da wani bangare na zuciyata ya sanar min kenan, kiranshi nayi a hankali na fara magana da shi cikin nutsuwa, ina kuma tuna mishi girman hakkin Uwa da aka tauyewa Hajiya idan ta musu a wannan yanayin yana da hali bai taimaka mata ba, Allah sai ya musu hisabi. Na gyara zamana da kyau. "Abba idan wannan shine horon da zaka yiwa Hajiya tabbas a tsawon shekaru sama da talatin ta horu, kai ko a kotu ce iya hukuncin da Alkali zai mata tsawon shekaru goma ne zuwa sha biyar amma Abba ita tsawon shekaru sama da talatin tana amsar hukuncin laifin da bata aikata ba, sannan Abba taya uwa me kaunar yaranta zata manta da su, Hajiya bata taɓa mantawa da Yaranta ba, ba iyawarka yasa yaran suke cikin amincin Allah ba, tana can gefe tana tayaka rikonsu nasan na wucd makadi da rawa amma a duba lamarin a tura a daukota kai dan uwanta ne ko babu aure gidanka gidanta ne, ko bata zauna a gidanka ba a nima mata inda zata zauna kayi hakuri da abin da na fada, amma nayi mata gobe zata ji yadda muka yi." Sannan nayi mishi sallama ina jin kamar na sauke nauyin da yaƙe kaina. Tunda na fara wayar kaina yake sunkuye ban san Mama ta shigo ba sai da na d'ago kai na kalleta. "Me yasa ba zaki koma dakinki ba, idan kin san kina gefe guda kuma zaki saka ayi?" Murmushi nayi ina faɗin. "Ba zaki gane ba, komawana dakina bai da nasaba da haka Mama ki min fatan Alkhairi Ubangiji yasa haka shine mafi alkhairi!" Bata ce kome ba, ta wuce ya kwantar da Mufidah. Muna jira jefi jefi, nasan a ranta bata jin dadin yadda na kafe, amma saboda laluran da nake fama da shi yasa ta kyale ni. --- *Abba* Tunda suka gama waya da Ummu ya ji kamar kanshi zai fashe, shima yana da kaso me girma na raba A'isha da Yaranta. Zazzafar huci ya fesar, ya dauki wayarshi ya kira Umar cikin abin da bai wuce minti talatin ba ya hada kan Yaranshi. "Abba lafiya ka tara mu?" Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce musu. "Mahaifiyarku ba lafiya!" "Abba ba Tafida ya Kaita asibiti ba?" Inji Rukayya. "Ke uwa ce kina da Yara maza da mata, idan suka miki abin da kuka yiwa Mahaifiyarku zaki ji dadi?" Hadiye yawu tayi. "Amma Abba ita ta tafi ta bar mu fa!" Inji Maryam. "Karuwa ce ita?" Da sauri suka d'ago kai suna kallonshi. A tare suka girgiza kai, "tow ita wacce? Bayan ta bar ku?" "Matar wani ce! Kuma ba zai yiwu ta tafi da mu ba." Inji Abubakar, "me yasa kika watsa da ita? Baku tunanin wata rana Yaranku zasu watsarku? Kusan nauyin da yake kanku na ta? Tafida ka ji tsoron Allah, kana son mulkinka ya tafi maka yadda kake bukata? Ka juya ga mahaifiyarka, idan kana son kayi yadda kake so ka koma gare ta. Manyan masu laifi na duniya Allah ya amshi addu'ar iyayensu bai hukuta su ba, sai bayan ran iyayensu kada ka rasa wannan damar dukkanku kuna da damar kyautatta mata idan ta rasu a wannan lokacin ko bana muku fatan amma kuma wallahi Allah sai ya girgiza duniyarku!" Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya cigaba da cewa. "Umarni na baku!" "In sha Allah!" Suka fada bakiɗaya suna masu kallon juna, "Umar gidan da yake kusa da naka a gyara shi, Tafida ka tura motar asibiti a daukota gobe nan, Abubakar Yaya Babba kai nake son ka tsaya kome a kawo min na asibitin na gani." "In sha Allah!" "Maryam ki amshi kudi a hannun Tafida ki sayi kayan abinci ki kawo min na gani a kai mata. Rukayya zan baki kudi a saka mata kome a cikin gidanta!" "In sha Allah!" Ya sake kallon Rukayya. "Na sanki da son rai, na sanki da son kai, zan baki kudin iya abin da zaki sayo idan aka samu matsala xan bala'in baki mamaki, ina sane da satar da kika yi abuja, ina sane da sharrin da kika kullawa Ummu, ina sane da kome. Wallahi kika sake wani abu ya faru da abin da na baki ki saya sai na saka an rufe min ke tunda kin zama bera!" Tsoro ne ya kamata domin Abba baya fadar magana bai cika ba, "in sha Allah zan kula!" Ta fada muryanta yana rawa. "Ku je!" Duk suka mike banda Tafida da yake zaune yayi kicin-kicin da fuska. "Uban masu gida muje!" "Babu inda zanje Abba ka shiga maganata da Ummu!" Murmushi irin na manya Abba yayi ya ce mishi. "Ina ruwa na? Kaga Tafida ka tafi wurin hidimarka!" "Abba kayi wani abu wallahi na gaji da abin da ake min ka saka baki a dawo min da mata." "Idan naki fa Mr Governor!" Ranshi ya kara b'aci, "wallahi ba zan tab'a sake ta ba sai dai ta zauna da aurena." "Akwai kotun Muslunci ai!" Mikewa yayi fuuuu ya bar parlour. Yana fita Abba ya saka dariya kamar ba yau da safe yake cewa idan ya dawo Umara zai sake ta ba yanzu ya dawo ya ce ya fasa sakin. "Ja'iri!" Kiran Deen Abba yayi ya ce bayan Isha yana nimanshi. Haka kuwa ya faru bayan Isha sai ga Deen ya zo. Bayan sun gaisa Abba ya mika mishi fura da nono, amsa yayi yana sha yana zuba santi. "Deen na kiraka ne akan Abokinka!" Gyara zama Deen yayi yana ajiye furan. "Sha kada ka damu" cigaba da sha yayi. A hankali Abba ya warware mishi yadda suka yi da Ummu akan Hajiya. Abba bai kai karshe ba Deen ya ce mishi. "Yarinyar nan yar aljanna ce kuma a aljannan First Class take!" Murmushi Abba yayi yana faɗin. "Na yarda da abin da ka fada, Ummu yar Aljanna ce. Yanzu abin da nake son naji daga gare ka shin kana ganin na shiga maganar Ummu da Tafida?" Gyara zama Deen yayi sannan ya ce mishi. "Abba zan yi farin ciki idan Ummu ta dawo gidan Tafida, amma kafin yau ka fara bincikan me yasa Ummu ta dage bazata koma gare shi ba, idan kayi haka ka mata adalci. Tafida yana buƙatar space sosai ya gane su waye a tare da shi lokacin da bai da kome ya kuma fahimci me ake kira zafi da dadin dandano rasa abin da kake da shi. Tafida ya ga lallai yana ji yana gani zai rasa abinda yake ganin na shi ne, Abba idan da Ummu Kanwata ce da muke uwa daya Uba daya. Wallahi Billahi azim, sai na saka Tafida ya rasa yadda zai yi domin sai na toshe duk wani hanyar da zai ganta ko ya mata magana, na fadi haka ne a matsayina na abokin shi amininsa, sannan ban yi haka da wata manufa ba, na san kai Uba ne kuma zaka.ji babu dadi a kalmai na amma adalci kake magana akai. Ka bar Tafida ya nime Ummu a karo na biyu. Idan ya fadi kuskuren shi ne, ya kada shi idan yayi nasara halayyarshi ce ya sauya. Yanzu nauyi uku ne akan shi na farko Al'ummar Borno na biyu Mahaifiyarsa, na uku Ummu Hadiyya ka barshi yayi ta fama kamar yadda ya iya fita yakin niman zaben gwamna haka zai fito yakin niman dawowar Ummu ni da kai mu koma gefe mu taya shi da addu'a, Tafida ba yaro ba ne da kullum sai an rike hannunshi a da can Yaro ne da bawa Ummu a yanzu kuwa tunda ya iya ajiye wata macen tow ba makawa yasan abin da yake mishi ciwo, don haka ka kyale shi ka zuba mishi idanu kamar yadda kace kana jin kunyar Yarinyar ka kyale shi kada ya zubar maka da sauran kunyar a duniya idan akwai yarinyar da ta cancanci kira da mace ta gari Ummu ce domin ta shanye duk wani abin Tafida. Kuma bata tab'a kai karar shi gida da wurinka ba, Abba ana barin halas don kunya, ka barta indai har tana gidan iyayenta ta iya tuna maka hakkin Hajiya tow Wallahi bata bukatar a takurata, sannan ciwonta yana kokarin tab'a mata zuciya ne, bata tab'a gayawa wani matsalarta ba, kada a takurata ta ga kamar don ta hada zuri'a da Tafida yasa ake mata haka, don Allah." Murmushi Abba yayi yana kallon Deen ya ce mishi. "Ina niman alfarma daya Deen!" Murmushi Deen yayi yana faɗin. "Abba ni danka ne har abada ba zan tab'a juyawa bukatarka baya ba!" "Ka zauna da Tafida koda bana raye ka zama dan uwa, Uba, Uwa, kamar shakikinsa!" "Abba kana raye in sha Allah zan zauna da shi!" "Na gode da ban yanke hukuncin kai tsaye ba, na kiraka na san zaka fini sanin wani abu na gode sosai Deen!" "Ba kome Abba!" Sun yi hira sama sama sannan yayiwa Abba sai da safe ya nufi bangaren Tafida, ya buga kofa. "Ka shigo!" Shiga yayi ya same shi ya zauna rashe-rashe, yana kallon abincin da Sa'adiyya ta girka. "Zauna kaci!" "Allah ya rufa min asiri, abincin Ummu ne nake iya ci zuciya daya salon a saka min wani abu!" "Bana son tashin hankali!" Inji Tafida yana kallon abincin. "Wai me yasa na zaka koma bangarenku ba,.nan bangaren Ummu ne fa!" "Me zai hana ka ɗauke ni ka mai dani bangarenmu tunda na kanwarka ne nan din!" "Allah ya baka hakuri!" "Mtseew!" Ya ja tsaki yana hararan abincin. "Muje ka raka ni asibiti!" "Waye ba lafiya?" Sake baki Tafida yayi yana kallon Deen da yayi tambayar hankalinsa kwance. "Ni ne ban da lafiya!" "Allah ya baka lafiya ka tafi Sa'adiyya ta baka magani!" "Idan zaka tashi muje naji me yarinyar can ta dauke ni muje idan ba zaka ba naje da kaina!" "Allah ya huci zuciyarka, gaskiya ba inda zani!" Ya mike zai fita, "Ok zan je da kaina!" "Better!" Inji Deen yana kunshe dariyarshi, haka suka rabu, Tafida ya nufi asibitin, Deen yana biye da shi don yadda yake tukin hauka kada ya ja musu magana kuma ya hana kowa binsa. A hargitse yayi parking motar ya shiga asibitin, ana ta gaishe shi bai kula kowa ba. *UMMU* Ina shan magani na ji an banko kofar dakin, ba ni ba hatta Mama sai da ta firgita. Rintsa idanuna nayi na bude shi akan Tafida. "Mama!" "Na'am Aliyu!" "Kin tambaye ta yaushe zata dawo dakinta!" Shan ruwa nayi abina domin nasan ita kanta bata da amsar tambayar da ya ce ta min. "Ummu!" "Akan me yasa ka dame ni ne? Kai kace ina haihuwa zaka bani damar nayi rayuwata ni ɗaya dauke Yaranka idan don sune zaka dame ni!" Na fada ina hade rai, tashi Mama tayi zata fita ya ce mata. "Don Allah ki tsaya ta saurare ni!" "Bari na baku wuri!" Fita tayi ya ja kujera yana faɗin. "Nayi kokarin koyawa kaina dauke kai akanki, amma na lura zaki mai dani dan iska ne!" "Wannan matsalarka ce ba nawa ba, na gaya maka ba yau ba ni idan na tsaya akan kalamai na ba zan tab'a sauka ba kace karya nake!" "Ummu ki dawo dakinki!" "Baka mummuna gajeruwar mace, yar Mace, yar talakawa ko ba haka ba? Ni bani da gata sai Allah amma ba xan tab'a komawa gidanka ba kaje na yafe maka amma gidanka ku kare kalau da danginka." Sake baki yayi yana faɗin. "Ummu Hadiyya!" "Na'am!" "Ki koma dakinki umarni na ne!" "Ba zan koma ba, idan ka dage kuwa na koma zan tafi inda ba zaka kara jina ba!" Na fada ina sauka a gadon. "Kina nufin zaki bar ni kenan?" "Ai dama tuni na barwa masu kaya kayansu, su yi sama sama da shi!" "Ummu ni Mijinki ne nake baki umarni!" "Kai ma baka ji umarnin Allah da na iyayenka ba, sai me don ban ji naka ba, Mallam idan ka tafi gida ka aiko min Deen da sakina. Na fara zawarci!" Mikewa yayi cikin wani irin zafin nama ya fisgo ni. "Idan na sake ki Allah ya tsine min ke babu shegen da zai shiga min gonata ko waye sai na kashe shi!" "Hmmm! Na gaya maka gaskiya kenan na gama zama da kai!" Kafin ya bar dakin muyi fada kaca-kaca, abin har mamaki yake bashi yaushe bakina ya bude da har na iya fada haka, bai yarda nice nayi fadar ba koda ya fita tsayawa yayi jim kafin ya bar asibitin. Domin na gaya mishi na bashi nan da kwana hudu ya sallame ni ko ya ga tijara. Fadar da muka yi sai naji kamar an sauke min wani irin nauyi da yake kaina da zuciyata, Mama kuwa bata min magana ba, domin tana jin yadda muka yi fadar tana jin yana faɗin yaushe bakina ya bude haka har na ke maida mishi maganarshi. Na kuwa gaya mishi tun lokacin da na fahimci bani da mai tsaya min sai Allah, bakina ya buɗe. Wannan maganar ya bashi haushi, inda yace ina nunawa Allah yana tare da shi wato shi shaidanune a tare da shi ba Allah ba! Ni kuwa nace mishi abin da ya min a zamanmu na yafe mishi idan kuma na cuce shi Allah ya saka mishi, shine ya bar dakin a fusace. Washi gari Doctor Sagir ya sallame ni da magani masu yawa, sannan ya bani shawarar yadda zan kula da lafiyata, Mudan ya kawo mu har gida, sannan muka shiga makota da abokan arziki na ta zuwa min gaisuwa, haka ko a cikin gidan Matar kawu gwani ma ta shigo suka gaishe ni. Tuwon alkama Ummi ta kawo min, miyar yauki, naci na koshi nayi wanka na kwanta bayan na sha magani. Tuni barci yayi gaba da ni ban farka ba sai azhar, Allah ya zo yaran ana basu madara kuma ana hada musu da nono,sun sha sun koshi sai wasa suke, bayan nayi sallah ma ka basu nono suka sha. Wurin karfe biyar na Yamma Abba ya kirani ya min ya jiki sannan ya gaya min abin da yake tafiya nayi godiya sosai. Hajiya an kawo ta kuka kai tsaye asibitin Doctor Sagir aka kaita, sosai suka tsaya akanta da kulawa ashe ciwon sugar ne, nan da nan aka daurata akan Magani. Sosai nake samun kulawa daga ɓangaren Mama da Ummi. Sai Mama Amina kafin mu yada wanka tuni nayi wani kiba har da kumatu, cikina kuwa Mama ta sani nayi ta matse shi saboda kada tumbi ya zauna min, tunda muka bar asibiti ban kara jin labarin Tafida ba gashi har muna niman sati biyu da dawowa gida, amma babu labarinsa. *** *TAFIDA* Tafiyarshi Umara daga shi sai Sa'adiyya, duk da sun zo Umaran amma kuma bawan Allah nan niman shi tayi ta rasa kuma ai dama ba daki daya suka sauka ba, haka yasa ta fara zargin ko ya zo da mace ne Umrah kamar yadda yayiwa Ummu ai kuwa shaidan ya kawata mata kome Tafida da mace yazo Umaran bayan ita..... *Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML* *Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!* #Mai_Dambuhttps://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw *R&U BAG's GALLERY! Wai da gaske kun manta ne na gaya muku? Tow R&U ta kara dawo muku da kayan ado da kawwa wanda Ummu First Lady take amfani da su, tow dai Ummu tace na gaya muku a sirrince! Kawo kunnunku 🙉 a wannan R&U BAG's GALLERY babu abinda babu domin kamar kanti kwari ne a gidanki! Muna da kaya irinsu Atamfa, lace, shadda! Karewa dai har da lefe, kayan fadar kishiya, kayan Fitar suna na mai jego, kayan toshi na wanda saurayi zai kaiwa budurwa! Waya miyar sai a mota, muna bada dai-dai har da sari ku shiga domin tabbatarwa idanunku* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Sa'adiyya* Bata taɓa sanin cewa tana da zafin kishi ba sai yau, babu Tafida babu me kama da shi yana can hotel da karuwan da ya kawo, wani irin kuka ta saka tana me daura hannu akanta, wiwi take kuka kamar ranta zai fita, tayi kuka har ta godewa Allah ta kuma yi rantsuwa matukar ta ga Tafida da mace sai ta kashe ta, haka yasa ta fita daga masaukin ta nufi waje, tafiya take tana bin mutane da idanun ko zata yi sa'an haduwa da Tafida amma bata same shi ba, babu me kama da shi. Banda asara bata da wani amfani zuwanta Umaran don ba ibada take ba. Shi kuwa Tafida dawowa yayi harami da zama yana jin kamar duk inda zai zauna babu inda ya kai wurin dad'i, abu na farko da yake zuwa mishi a rai Ummu ba zai taba mantawa ba zuwan da Ummu anan ta tab'a ganinsu da SA'ADIYYA amma ta dauke kai kamar bata gansu ba. Wata balarabiya ce ta ajiye jakarta tana mishi larabci, a hankali ya amsa mata kasancewar a sudan da yayi karatu kuma sai ka nazarci harshen larabci kafin ka fara karatu infact yana jin luggatul Arabia. Ai kuwa kamar ta ga dan uwanta suka shiga larabci tana tambayar shi shima Balarabe ne ya ce mata a'a daga Afrika yake. "Allah ya tona maka asiri karuwa ma dauko!" Ta yi maganar da karfi, tana nufar balarabiya, mikewa yayi yana fadawa balarabiyar zai tafi dama yana jiran Matarshi ce. Ya finciko Sa'adi da take ihu tana tutture shi tana ihu. Bai san lokacin da ya kifa mata mari ba, ai kuwa tayi tsit. "Ki wuce muje jaka!" Ya fada a matuƙar fusace, sannan yayi gaba mutane sai kallonsu suke musamman tsirarun hausan can, tun tana daurewa har ta kasa tana bin shi tana kuka. Masaukinsa ya wuce ta shige dakinta. Ta kira Uwarta tana kuka wiwi da kyar ta iya gaya mata marin da yayi mata. Kashe wayar tayi ta kira Tafida, da yake wanka bai san tana kiran ba har ya gama ya fito yana zaune ya ga kiran. Dauka yayi yana faɗin. "Lafiya?" "Me tayi maka ka mare ta?" "Da alamu baku mata tarbiyya yadda ya dace ba ne, sannan bata san girma da daraja irin na mijin aure ba." "Kai din tarbiyyar ce da kai!" "Koma dai me zaki ce ni nan renonki ne, ai kin san bani da tarbiyyar kika bani aurenta marasa tarbiyya ne suka hadu kin ga ai ba wani abu bane tayi min na mata!" "Aliyu!" "Me zan miki?" "Idan ka sake taɓa min Y'a sai na maka ka kotu!" "Allah ko? Ashe kuwa yanzu zan fara dukanta idan kin so ba kotu ba kuliya zaki hada ni da shi. Babu ruwanki da gidana ita yarki ce ni surukinki ne!" Daga haka ya kashe wayar yana tsaki, shi fa babu wanda ya isa mishi ganganci ya kyale. Yana gama jin haushin shuwa da Yarta ya kira Ummu. "Hello waye wrong number!" "Ke!" "Waye kai Malam?" Ta tambaye shi, yadda tayi tambayar a wani sanyayye da shagwab'a, yanayin maganarta amma shi gani yake kamar da gayyya tayi mishi wannan maganar. "Ummu Hadiyya!" " Ai kai ne?" "Eh!!" Ya bata amsa yana shafa kanshi. "Idan na dawo ki bani lokaci na zo mu tattauna kin ji!" "Akan sakina ne?" "Ummu Hadiyya!" "Ni ba sake ki zan yi ba, ki dawo dakinki!" "Ba zan dawo ba fa." "Me yasa baki jin magana Ummu?" "Ayya ai kuwa koya nayi!" "Daga waye?" "Oho!" "Tow yayi tunda oho ya koya miki mugun abu!" "Hmm zan kwanta kaina yana ciwo;" "Ummu!" "Don Allah ka kyale ni!" Ta kashe wayar. Bin wayar yayi da idanun kamar yana son hango Ummu ta wayar. Kiran sallah ya katse mishi kallon wayar ya shirya ya fita, a bakin kofar dakinshi ya ganta. Wani matsiyacin kallo ya watsa mata. "Ina zaka wallahi sai na bika?" Magana yaƙe son yayi amma kamar an rufe mishi baki ya dauke kai kamar bai san tana wurin ba, ya wuce haka ta biyo shi yana tafiya tana bin bayanshi. Sai kallonsu ake. Har massalaci ya wuce bangaren maza ita kuma ta wuce bangaren mata, tunda ya shiga Masallacin bai fito ba sai da aka yi sallah isha sannan ya fito a bakin kofar ta ganta tsaye. Kamar bai san tana wurin ba ya wuce abinshi haka ta bi bayanshi. Haka suka iso hotel din ya wuce restaurant ya zabi abinci, bai kulata ba ya amsa mata suka juya, ita nan tana bin shi ne don ta ga wacce ta biyo shi, girgiza kai yayi yana tafiya, har ya wuce dakinsa ya ajiye mata abinci. A bakin kofar dakinta, yana shiga dakinsa ya ajiye abincin ya zauna yana me hade hannunsa biyu wuri guda. Wayarshi da ya bari a parlour ya ɗauka a hankali ya shiga niman number Abba don har ga Allah yasan Abba kadai Ummu zata saurara. "Assalamualaikum Abba!" "Tafida dare yayi!" "Eh na sani amma zan tuna maka maganar Ummu ne!" "Ikon Allah Aliyu dama nayi maka alkawarin zan shiga maganarku ne?" "Amma Abba!" "Kasan bani da lafiya kuwa?!" "Innalillahi sannu Allah ya baka lafiya, yaushe xaka samu Ummun?" "Kai sai da safe!" Abba ya kashe wayar, bin wayar yayi da sauri yana kallonta. Nan ma ya kara kiran Ummu. Sai da ya kusan tsinkewa ta dauka. "Wai don Allah waye kai ne ka dame ni?" "Allah ya baki hakuri Ummu ya Yaranmu?" "Yaranka dai ni kuma na isa na haifi kyawawan Yara irinsu ne jiki duk baki kamar bayan tunku..." "Kin ga ban kira ki muyi rigima ba, na kira ki na tambaye ki yaushe zaki koma dakinki!" "Ni dai ba zan koma ba!" "Me yasa kike min haka ne?" "Me yasa ba xan maka haka ba? Tafida ka fita idanuna na rufe ko na maka rashin mutunci!" Ai kuwa ya hau shima ganin zai fara mata hayagagga yasa ta kashe wayar bakiɗaya. Takaici kamar ya ciji kanshi, yana cikin wannan takaicin Sa'adiyya tayi ta buga mishi kofa. "Uban me zan miki?" "Na ji kana magana da mace ne shi yasa na ke buga kofar kada a dauko karuwa!" Kuri yayiwa kofar tabbas yarinyar nan ta ga gadon barcinsa. "Idan na dauko ƙaruwar ai ba sabon abu bane. Tunda kema kin tab'a harkan kenan!" Wayyo Allah na, ji tayi kamar zata hadiye ranta. "Zargina kake?" "A'a ni bana zargi a rayuwata sai dai na gaya maka abin da kake aikatawa, sannan ba xan yi zargi na lalata aurenmu ba, wai na tuna miki kin tab'a biyo ni muka kwana gado daya, kika ce nayi miki!" Wani irin dukar kofar tayi, ya sake murmushi yana kallon kofar tabbas shi a duniya babu wanda zai cinye shi da baki domin Allah ya bashi baiwar magana sannan bata isa ta gaya mishi magana ya kyale ta ba ko da kuwa kwaya yake sha. Washi gari tun karfe uku ya nufi harami yayi dawafi, ya tsaya gaban dakin Ka'aba yayi addu'a sosai. A karon farko da yaji yana son yayi iyayenshi da Yaranshi da zamansu da Ummu, sannan ya kuma mika lamarinsa da na mukamin da ya samu,sai dai duk da haka ji yake kamar yayi missing wani abu me muhimmanci a rayuwarsa, duk addu'ar da yayi amma yana jin kamar akwai wani wawakeken rami a zuciyarsa da bai cika, Sa'adiyya da yake ganin itace zata kawo sanadin farin cikinsa ashe ba haka ba ne. Gashi tun ba aje ko ina ba ya fara gajiya da halinta. Ita kuwa Ummu yar renin hankali ce fisabiilillahi akan me zata wani dauki zafi ai ya dace tayi hakuri ta dawo dakinta, don ta samu yana damuwa da ita, tsaki yayi can kuma ya tsaya kafin ya samu wuri ya zauna yana kallon dakin Ka'aba haka yana ganin lokacin yadda tayi ta dawafi yana ganin yadda take kuka sai ji yayi tsigar jikinshi ya mike yarrr "ko me ya sata kuka?" Ya tambayi kanshi, tsaki yayi a karo na biyu yana faɗin. "Ta cika sakalci haka kawai ma kuka take kamar cry baby!" Ya fada shi daya kafin ya ware manyan idanunshi yana murmushi ya ce . "Yanzu da ta zama Maama ya zata daina kuka ko zata cigaba?" "Barka da asuba!" Wani ya fada mishi yana murmushi, zama mutumin yayi Tafida ya mika mishi hannu suka yi musabaha. "Yawwa Barka dai!" Suka yiwa juna murmushi. "Ban gane ba?" "Eh nima na ganka ne kawai sai na ga kana murmushi kana magana kai ɗaya, nace Allah yasa ba Madam bace ta hada maka kafi Malam!" Shafa kai Tafida yayi yana kallon Mutumin ya ce mishi. "Eh wallahi tana can rigima take ji, na bita taki saukowa hala so take taji na rataye kaina." "A'a baka bita ba dai, ita mace yar riritata ce da zamu yi hakuri da halinsu tabbas da tuni an manta da wuri, ni da ka gani mata na hudu kuma kowacce ina zaune da ita da halinta mutum daya ce take bani ciwon kai, kuma kaf dangina da duk wani na kusa dani sonta yake saboda halinta da kirkinta. Sai dai har yau sama da shekaru goma sha biyu Allah bai bata haihuwa itace Uwargidana, amma kasan me? Duk matan da nake aure a bayanta sun haihu. Ba don na tsaya akanta ni da Mahaifiyata ba wallahi da tuni bana tare da ita,saboda fitinar mutane kai sai da ta kai ta kowa na rantse da Allah duk wacce ta mata gorin haihuwa na gama zama da mace har abada, idan kuma kai dangina ne na datse alakarmu da shi, Alhamdulillahi Ubangiji ya ga nufina ya kuma bani ikon samun galaba akan kowa domin ina sonta ina kaunarta ban yarda wani ya tozarta min ita ba, ni nasan darajarta ni nasan amfaninta a rayuwata idan ba bari ya wani ya tozarta min ita ni nayi asara, Ina kuma girmama duk wani abin da zai fito daga gare ta. Yanzu haka Umaran da muka zo a tare da ita muka zo da Amaryata." Bakiɗaya Tafida kallon Mutumin yake gabanshi yana tsannanta bugawa, a hankali ya cewa Mutumin. "Gaskiya ka mata adalci ka kuma hana wani ya tozaratta, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyiba itama ta ga nata rabon!" "Amin Ya Allah! Bari na shiga na sake alola, Sunana Alhaji Junaid Yashi, daga jahar Bauchi." Mika mishi hannu Tafida yayi yana faɗin. "Aliyu Muhammad Jadda Tafida!" Shiru Alhaji Junaid Yashi yayi yana faɗin. "Kamar nasan sunan nan amma na manta inda na sanshi." "Haka ne Allah yake lamarinsa, sai ka.ga kasan abu amma sai ka iya manta inda kansan shi zan shi, zan tafi masallaci nima!" Suka rabu kowa ya kama hanyar shi, akwai wani darasin da bai tab'a tsinta ba sai yau labarin Matar Alhaji Junaid Yashi ya tsaya mishi a rai, ya rantse ba zai dauki duk wacce ta mata gori ba, sannan ba zai zauna da duk wanda ya wulakanta mishi mata ba, "kut!" Ya fada yana jin aranshi wannan kuskure ne, ai wannan kuskure ne taya don an yi mata laifi zai hukunta wanda bai ji ba bai gani ba. Tsaki yayi yana faɗin. "Ummu dole ki dawo dakinki wallahi!" ** *Abba* Zuwa yanzu Abba ya kara fahimtar waye Tafida, domin Ummu tana ta kan bayyana musu asalin siffarsa. Inda yake ƙara godewa Allah yadda Tafida bai bar kowa ba, bai kyale duk wani wanda yake ganin zai iya kyalewa. Shi yanzu abin da yake ganin zai taimakawa Tafida zai yi ba wanda zai kara nisanta shi da Tafida ba, don haka ya kira wani abokinsa babban Malami ne, wanda shi yake taimaka mishi da wani abu addu'a da sauran su, sannan akan Tafida ma Malam Zailani yayi ƙoƙarinsa domin shi ta bawa Abba shawaran kada ya sake ya bar Tafida ya fara auren Saadiyyah, wannan shine babban abin da zai yi danasani. Bayan sun gaisa ya ce masa. "Malam Zailani! Barka da asuba!" "Alhamdulillahi Alhaji Muhammad Jadda, ina ka boye mana mai girma Gwamna!" "Yana Umara malam kayi hakuri nayi maka laifi Yarinyar nan ta haihu ban gaya maka ba!" Murmushi yayi yana faɗin. "Hasken gidanka da na gaya maka ya fara bayyana ba, baka yi laifi ba nima bana kasar yau sati guda da dawowata!" "Masha Allah! Ya hanya da fatan ka dawo lafiya." "Alhamdulillahi, sai godiyar Ubangiji, lafiya tayi karanci. Amma da sauki." Sannu Abba yayi ta mishi sannan ya cewa Abba. "Ina jinka bakinka da magana!" Nan Abba ya gaya mishi kome, shiru yayi kafin ya ce mishi. "Aliyu bawan Allah! Kamar yadda na gaya maka gaskiya kuma kamr yadda na gan shi a cikin Yaranka bakiɗaya shi na musamman ne, Aliyu gadanga kusar yaki. Alhaji Muhammad Jadda, Aliyu yana tare da makiya dayawa, Aliyu yana tare da makiya kadan da suka bayyana kansu basu da illa kamar wanda suka boye kansu. Alhaji Muhammad Jadda, tun yanxu ka fara sadaka kayi yanka a zubda jini, a ciyar da miskinai da mabukata. A rabawa Yara fura da nono, a basu alawa da gyada da aya. A basu bakinsu ya amsa da Allah ya biya bukata, kasan inda kaddara ta kai shi. Wuri ne da ko yana da marasa imani da nutsuwa suka gina, Allah kuma ya kawo wanda yake bukata a cikin bayinsa. Alhaji Muhammad Jadda,kada ku tilastawa Yarinyar dawowa ita da kanta zata ga yiwar haka." "Batun Yaran fa! Ina tsoron kada a kara samu irin Aliyu a cikinsu." "A'a wannan lamarin Ubangiji ne, Aliyu yana tare da kariyar Allah. Yaran a kawo min su da Mahaifiyarsu." "In sha Allah!" Godiya sosai Abba yayi sannan suka yi sallama. Shiru Abba yayi kafin ya kira Deen duk da garin yayi sassafe ya ce mishi. "Ina son don Allah ka je gidansu Ummu zan kira Alhaji Bulama na gaya mishi ka kai su gidan Malam Zailani." "In sha Allah Abba bari na shirya!" "Allah ya maka albarka!" "Amin Ya Allah!" Kashe wayar yayi ya kira Alhaji Bulama ya gaya mishi zai turo Deen ya kai Ummu da yara a duba su. Tow ya ce mishi. Suka yi sallama. ** *UMMU!* Ina kwance Mama ta shigo tana faɗin, "Yaran nan ki shirya su yanzu haka Baban Tafida ya kira Alhaji wai ku shirya zaku fita." Gabana ne ya fadi na ce mata. "Lafiya kuwa?" Harara ta watsa min, "ina zan sani, Ummu ki koma dakinki na gaya miki." "Don Allah Mama kamar kin gaji da ni!" Ware idanu tayi tana faɗin, "lallai fa! Gajiya kan ai na gaji da ke." "Ni kuwa Mama don Allah me nayi da zafi?" Ware min yatsunta tayi tana faɗin. "Kaniyarki kika min, idan nazo sai na fasa miki baki!" Tura baki nayi ina faɗin. "Don Allah yaushe mutum zai samu nutsuwa ace kai da Mamanka amma tana gaya maka ta gaji da kai, gaskiya ba ayi min adalci." Mafificin gefen gadon ta dauka zata buga min na fada toilet da gudu, ina dariyar. "Ja'ira dole ki koma dakinki" wanka nayi na fito na samu tana yiwa yaran tea na hada na sha, sannan na dauki Mufid da aka gama mishi wankan na gyara shi, kafin ta miko min Mufidah itama na gyara mata jikinta, kayansu na saka musu iri daya, sannan na kalli Mama. "ko za a kira min Nana!" "Tow bari na tura a kirata" haka Mama ta fita aka kira Nana, tana zuwa ta gaishe ni. "aunty Baby! Kawo Mufid yau mun b'ata da Mufidah!" "Yau kuma!" Ta amshi shi muka fita ina kallon Uwani tana faɗin. "ke dai Aunty Baby gaskiya kin takura mana, Mama ta koma gidan Mijinta!" Ta fada tana komawa Bayan Mama. "Bani da lokacinki!" Na saka kai muka fita ina faɗin. "Mama sai mun dawo!" Sai da na fara shiga bangaren Ummi muka gaisa sannan na tafi Bangaren Umma. "Wai ke yaushe zaki koma dakinki ne?" Shiru nayi Nana yarinyar ce amma nayi mamakin yadda ta bata amsa. "Hajiya Umma yan rakiya take nima, idan zaki shiga cikinsu mu saka ki a list!" "Yar banza mara kunya ke kan Amina tana da aiki." "Oho dai ai aikin naku ne, idan tayi nata a cikin gidan ku kuma yan yad'awa kun karasa mata Aunty Baby muje ki gaida sweet Bulama!" Make ta nayi, ina hararanta muka fita, to suna wasan jika da kaka, su gaya mata magana ta gaya musu musamman Umma da bata ganin zarrau sai ta tsinka, a parlour baba muka hadu da Deen. "ina kwana baba!" "Lafiya Lau uwar Yan biyu, Amarya ta ya dai kike wani murmushi ko soyayyar mu ta naira goma ce ta motsa!" "Kai ina Sweet Alhaji Bulama, ka ga nayi kama da mai soyayyar Naira goma indai ba class zaka zubda min ba." Sake Baki Deen yayi yana kallon Nana yar yarinyar da bata wuce cikin cokali ba. "tow ku je kasan gidan Malam Zailani akwai a jama'a, ke kuma Amaryata zan kawo miki Naira gomanki har gida na tambayi Malam Yakubu nawa yake baki ne!" Dariya tayi tana me faɗin. "Shi kenan!" Deen yana gaba da nake gaishe shi, Nana tana bayana. Baya na shiga ita ta shiga gaba. "Ya Madam Yaya Deen!" "Tana lafiya itama kwana biyu nan bata jin dadi!" "Allah ya bata lafiya!" "Amin Ya Allah!" Ya fada yana jan Motarshi, "Ummu ya maganar abokina ne?" "Wa kenan?" Murmushi yayi yana faɗin. "Baban twins!" Hade rai nayi ina faɗin. "Shi ya turo ka?" "Ko daya bai turo ni ba, ina me son na baki hakuri ne!" "Hmm ya wuce kawai ya bashi shawara ya sauke nauyin da yake kanshi ya huta." "Tow Allah ya kawo mana mafita!" Daga haka yayi shiru don ya fahimci bana son maganar tayi nisa yasa nace ya sauke nauyin ya huta, kuma maganar gaskiya ban ga abin burgewa na sake jiki kana tattaunawa da abokin mijinka ba, indai ba dole ba. Gaskiya ba haka na ga Mama tana yi ba kuma ba zan ɗauki al'adar wasu na daurawa kaina ba. Tun kafin mu isa kofar gidan, na fahimci inda muka zo domin akwai motoci sun kai bakwai a kofar gidan, kuma ba kananun ba irin na alfarma na manyan mutane. Parking Deen yayi ya kashe motar muka fito, zauren gidan muka shiga, mutane ne suna zaune a gaban wani dattijo fari kyakkyawa da shi, "Safiyyudeen! Rabona da kai tun kafin aurenka yau gashi domin yiwa Aliyu hidima ka kara zuwa!" "Haka ne malam barka da asuba!" "Barka dai, Ummu Hadiyya!" "Na'am!" Na amsa a hankali, koda yake ban yi mamakin yadda ya kira sunana ba. "Ku shiga wancan parlour bari na sallame su" haka muka shiga dakin, Deen y amshi Mufidah da nake rike da ita. Yana kallon yadda take barci. Dukkan mu shiru muka yi aka rasa me magana a cikinmu, bayan minti goma aka kawo mana abin karyawa, Nana ce ta ci daga ni har Deen bamu ci ba. "Barkanku" ya fada yana shigowa dakin. "Yawwa malam" Deen ya fada yana mikewa, nima haka. "Zauna abinki!" Zama muka yi ya kalli Deen. "Amintarku da Yarda ku, abin burgewa ne kai dai ka cigaba da tsayawa a gefenshi, domin kalubalenku tafi ta kowa girma, ita wannan nata me sauki ne kai ne za ayi ƙoƙarin ganin an cimma nasara akanku. Ban da iyayenku mata suna hana idanunsu barci a kanku ai da tuni an murkushe alakarku. Tow Allah ya hada ne kamar yadda ya haɗa na Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama da Abubakar haka ya haɗa naka da na Aliyu! Kaf duniya baya jin kunyar kowa sama da kai." Sannan ya zauna yana murmushi ya cigaba da cewa. "Kanata samun promotion saboda Aliyu ka ki tafiya ka ki amincewa, kai mutum ne me matukar muhimmanci a rayuwar Tafida!" Kunya duk ya lullube Deen, domin yaƙi yarda wani yasan da haka, har kona takardan yayi kada wani ya gani, baya son barin Tafida a wannan yanayin da bai tsaya da kafarshi ba. "Yaushe zaki koma dakinki?" Ware idanu nayi bakina yana rawa. "Ummu Hadiyya yaushe zaki koma dakinki?" Hawaye ne ya shiga zuba min. A hankali ya ciro goro a aljuhun babban rigarshi ya fara ci yana faɗin. "ba kuka zaki min ba, Deen cirewa yarinyar nan rigar jikinta, kema cire mishi rigar jikinsa. " "Idan ke da Deen kuka nisanci Tafida garkuwar da yake da shi ya rasa, ban ce ko ne kuke kare shi ba, sai dai kowani mutum da irin baiwar da Allah ya masa, Tafida yana da shi amma naku da ya hadu da nashi Allah ya saka mishi albarka, kuna kyautatawa iyayenku da nashi, wannan albarkan da suke samunku yana rab'anshi. Idan kuka matsa s jikinshi wannan darajar da yake ci zai rufe kamar yadda ake saka toka akan fa a, Tafida zai rushe kuma za ayi nasara a akanshi, ku tsaya mishi Deen ka kula da hannun damanka." Ya fada yana jan wani allon karfe ya fara rubutu a jikinsa da zuma, murmushi yayi sannan ya kalli Nana. "Sarkin tsiwa. Shekarunki nawa?" "Sha uku!" "Masha Allah! Ubangiji ya albarkaci rayuwarki!" "Amin Ya Allah!" Kuma amsa bakiɗaya. Goran zam-zam ya dauka ya dibi ruwan ya wanke rubutun ya ce mana. "Bani namijin domin Alhaji Muhammad Jadda yana tsoron kada su gaji mahaifinsu!" Ya fada yana kallona, Deen ya mika mishi Mufid. "Tafida bai kyauta ba, amma qaddara ta riga fata, idan aka yi hakuri. Kuma sai kome ya zama tarihi." "A'a Malam ban da Tafida, a barshi ya san ciwon kanshi." Murmushi yayi yana faɗin. "Deen kamar ka koma bayan Ummu!" Dariya yayi yana faɗin. "Kanwata ce duk da naga tana fushi da ni!" Shafe Mufid yayi da ruwan rubutun ya dura mishi haka yiwa macen ma. ** *TAFIDA* Tare kofar tayi tana huci, kamar wata macijiya. "Bani hanya na wuce kada na rasa sallah azhar!" "Hakkina zaka bani....https://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw *R&U BAG's GALLERY! Wai da gaske kun manta ne na gaya muku? Tow R&U ta kara dawo muku da kayan ado da kawwa wanda Ummu First Lady take amfani da su, tow dai Ummu tace na gaya muku a sirrince! Kawo kunnunku 🙉 a wannan R&U BAG's GALLERY babu abinda babu domin kamar kanti kwari ne a gidanki! Muna da kaya irinsu Atamfa, lace, shadda! Karewa dai har da lefe, kayan fadar kishiya, kayan Fitar suna na mai jego, kayan toshi na wanda saurayi zai kaiwa budurwa! Waya miyar sai a mota, muna bada dai-dai har da sari ku shiga domin tabbatarwa idanunku* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Hakki?" Ya tambaye ta, kafin ya fara duba aljuhun rigarshi da wandon shi yana niman hakkinta. Inda ya ajiye amma bai gani ya d'ago kai fuskarshi babu annuri ya ce mata. "Matsa ki bani hanya na wuce!" Ciki ciki ta ce mishi. "babu inda zan matsa ka bani hakkina kawai!" "Ba zan bayar ba, ke din wani hakkin ne dake, bakiɗaya mace babu dandano kina tsaye mace amma a zahirin cikinki gara a baka dafaffen kaza mara hadi, domin zaka ci shi haka da akan ke." "Wannan matsalarka ce, ita matarka da ka iya ci meye banbancinta da ni?" Kallon renin hankali yayi mata daga sama har kasa ya ce mata. "Ita ni na fara yanka kazar na fige sannan na dafa da hannuna babu wnada ya taya ni daga gefe. Kin ga ba tare da ajinamota da gishiri ba. Na cinye kazata, kuma har yau marmarin kazata nake!" Ya wuce ta abinshi yana jin ranshi fess. "Allah zai saka min!" D'aga kafada yayi yana faɗin. "Can miki!" Idan tana jin asalin zaman doya da manja tow kuwa shi suke da Tafida, domin bawan Allah nan baya kunya ya gaya mata magana anyhow. Ranar da suka cika sati biyu suka fara shirin dawowa gida, sannan ya shiga manyan store yayi ta sayayya kamar hauka Yaranshi da Ummu kawai su yakewa sayayya, yana gamawa ya wuce gida. A bakin kofarshi ya hango Sa'adi. Murmushi yayi mata yana faɗin. "Matar Governor!" Banza tayi mishi tana faɗin, "Aliyu ka bani hakkina mana, tun ranar da ka kai ni asibiti baka kuma bani hakkina ba ana maganar wata kusan uku." Gyara tsayuwarshi yayi da kyau sai kuma ya shiga cikin dakinshi yana faɗin. "Ke hala Aljanu ne dake masu jaraba?" "A"a Ifriqai nake dasu ba Aljanu ba!" Banke kofar yayi yana faɗin. "Ki je can ni bani da lafiya, basir yana damuna!" Shiru tayi kamar zata yi kuka tayi ta buga kofar Amma yaki. *** *Ummu Hadiyya* Tun lokacin da muka dawo daga gidan Malam Zailani, maganar da muka yi ya tsaya min a rai. Amma na tattara ba ajiye a gefe Tafida ba kamar sauran mutane ba ne, da zan sake waiwayarshi cikin sauki, dole ina bukatar sanin halin rayuwa da kuma yadda mata irina suke tafiyar da mutum irin Tafida, ba wai ban san halin Tafida ba ne, sai dai bana fatan na koma mishi har ga Allah domin yan uwanshi ba kaunata suke ba, gara na rufawa kaina asiri. Nayi zurfi cikin tunani wayata tayi ƙara, Hajiya na gani cikin farin ciki na dauka ina faɗin. "Hajiyata!" "Na'am yata, bayan ƙoƙarin da kika yi amma kin kasa zuwa duba Mamanki? Kodai baki son na miki maganar Baba Ali ne?" "A'a Hajiya ban samu fita ba ne, amma idan na samu fita zan zo in sha Allah." "Allah ya nufa na gode sosai, Allah ya miki albarka, yasa kema Yaranki su miki abinda kike mana, Ummu Hadiyya Ubangiji ya shirya bayanki da gabanki na gode sosai!" Idanuna ne suka cika da kwalla tabbas Hajiya ta gama min kome irin wannan addu'ar. "Amin Ya Allah, Amin Ya Allah, Allah ya baki lafiya Hajiya." Na fada kamar xan yi kuka don bana son yadda suke min godiya. Kashe wayar nayi ina sauke ajiyar zuciya. Na kalli Yarana sai naji sanyi a raina tabbas Allah ya min ni'ima da ba kowa yake da shi ba. Alhamdulillahi da wannan damar da Allah ya bani. *Shuwa* A gaban Malamin take kamar zata yi kuka ya ce mata. "Ita yarinyar a tsaye ake kansu, na gaya miki sai an tashi tsaye domin ko muna aiki zamu samu masu warwaresu." Idanunta sun kad'a jajjur ta ce mishi. "Malam babban tashin hankalina shine uwarshi ta dawo taya zan samu biyan bukatana!" Zane yayi kafin ya d'ago kai yana kallonta kafin ya ce mata. "Yarinyar ta dawo da ita, sannan babu wata hanyar da zamu iya kulla wani abu, sai mun samu hanya." Ya cigaba da zane kafin ya d'ago da mamaki ya kalleta ya cigaba da cewa. "Akwai hanya amma ba nan kusa ba, abu daya zan gaya miki shine ga wannan hayakin ki tabbatar an saka ya sha shima dan banza yana da taurin kai, wannan kuma a jefa a rijiya mu ga me zai faru nan gaba! Tabbas hanya biyu ne na farko ki tabbatar ranar da ya dawo ranshi a bace yake na biyu kuma gaskiya za a iya rasa rayuwar wani ko.wata akan aikin idan kuma kina ganin haka zai zama mafita to!" "A'a ban da kisa Malam, a barshi xan san yadda zan yi da shi." Zufa ne ya karyo mata, kafin ta ce mishi. "Allah yasa a dace domin yaron nan na sha fama akanshi yanzu da zan huta amma kowa yana niman hanani! Yan uwansa da nake amfani dasu ma sun fara ja da baya." Murmushi ya yi ya ce mata. "Ga wanann ki tabbatar kin saka musu, ba zasu tab'a miki gardama ba, sannan zasu zama masu miki biyayya!" Kudi ta zuba mishi, tana godiya ta fito. --- Tunda tasan abin da ta kulla, ta nufi bangaren Abba da ta dawo tana me kai karar Tafida. Domin idan ta fara da Abba tafida na zuwa Abba ya mishi magana zai fusata. Tana komawa bangarenta ta kira Saadiyyah, ta gaya mata duk rintsi kada su tawo Najeriya bata fusata Tafida ba. Ita kuma yayi mata alkawarin haka zai faru. Shirin da Shuwa take ba karamin shiri bane don haka ta kira Rukayya domin tasan ita ce zata fi bata haɗin kai, don haka tayi amfani da ita ta kirata da sunan ranar da Tafida zai dawo ta zo su yi abinci, dake bata da lissafi Allah ya zuba mata kwadiya, don ko Maryam bata gayawa gudun kada maryam ta mata faɗa, haka ta ki faɗa. Aikuwa Ana gobe zasu dawo Shuwa da kanta ta shiga bangaren Saadiyyah ta gyara mata, sannan ta koma bangaren Ummu da tasan dole ta nan sai fara shigowa, haka yasa ya turara bangaren tas. Da kyakkyawar shirinta, haka kuwa ya faru tun a jidda ta fara mishi tijara, bai kulata ba domin burinsa kawai ya isa ya nufi wurin Ummu da Yaransa. Don haka yaki yarda ya amsa mata domin kada ta yarda ta fusata shi lokaci zuwa lokaci yana murmushi, don na karamin dad'i yake ji ba, koda suka bar Saudiya a jirgi ma magana take gaya mishi. Har su iso garin Maiduguri Allah yasa sun iso da dare, don haka ba tare da ya damu ba ya kalli Mahmoud ya ce mishi. "Ka wuce da ita gida! Ni zan tafi ganin Ummu!" Ya kan wasu akwatina guda biyu. "Tow na zata gida zaka wuce!" Wani shu'umin murmushi dariya Sa'adiyya tayi, tana faɗin. "Allah yasa rawan kan da ake yi akan Ummu ya koma upside down" banza yayi mata bai yarda ya kula ta ba zai shiga motar Deen ta ce mishi. "Da alamu dai gudu abin kunyar da aka aikata yasa ana ƙoƙarin rufa-rufa, waye ya sani ko yaran ba jininka ba ne!" Cak ya tsaya kamar an dasa shi a wurin ya kasa gaba ya kasa baya. "Waye ya sani ko bayan kai akwai mata yi tunda ai kafin kai akwai wani a gidansu da yake sonta!" Ta shige motar da gudu, wani irin tafasa ranshi yake tunda ya shiga motar, jikinshi yake kyarma, asalin yarinyar ta san spot din da ya dace ta buga ta koma buga yadda ya dace, "wuce da ni gida na ci Uban Yarinyar nan." "Kayi hakuri ka fara kai musu kayan!" "Wuce da ni gidan kawai!" Yasan yadda ya fusata nan, ba zai saurare shi ba, don haka bai yarda ya kai shi gidan ba, ya wuce da shi gidan Malam Zailani. Ai kuwa yayi ta fada kamar zai daki Deen yaki kuma fitowa, Malam da kanshi ya tawo har wurin motar. "Aliyu!" "Sannu Malam!" "Allah ya tayaka riko tunda ba zaka samu shigowa ba, ina jiranka Allah ya tsare hanya." Bai ce kome ba shi dai burinsa ya isa gidan, Deen bai ji dadi ba haka ya ja motar ya bar gidan Malam. Har ga Allah Malam Zailani tausayin Tafida yake ji, domin zuciyarshi ita ce matsalarshi. Lokacin da suka isa ko parking Deen bai gama ba, ya fita daga motar ya nufi bangaren Shuwa don yasan Sa'adiyya tana can, yana shiga cikin fusata ya shiga kwallo da Sa'adiyya, yadda yake dukanta zaka ɗauka Allah ne ya aiko shi yana faɗin. "Ke din banza karuwan banza kin isa ki kama kafar Ummu yarinyar da ta kare rayuwarta da mutuncinta zaki zaga. Ke karuwa da maza suka gama hawa da sauka akanki zaki zagar min.mata da tafiki daraja." Bai damu ihun da Shuwa take ba ya mata duka har yana ture shuwa. Sannan ya bar bangaren jikinshi yana wani irin rawa domin bai tab'a jin fushi irin na yau ba, riko hannunshi Abba yayi kamar zai yi kuka ya kai shi parlourn shi ya ajiye shi tare da bashi ruwa, yana.sha yana haki domin babu abin da ya mishi kamar sheganta mishi Yaranshi a duniya bai da sama da su. Gumsar ruwan sanyi Inna tai ta fesa mishi, ya sauke wata ajiyar zuciya me karfi a kai akai. "Tafida!" D'ago kai yayi yana kallon Abba kafin ya ce mishi. "Yaushe Ummu zata dawo?" "Sai lokacin da kayi hankali ka koyi sanin darajar iyaye da Macen aurenka, ku zama shaida na raba Aliyu Tafida da Ummu sai ranar da yayi hankali!" Ya juya ya koma dakinshi, ya rufe kofar ya zauna a bakin gadon shi. Baya son yayiwa Tafida kuka amma tabbas deeply inside dinsa yana jin rauni a ranshi dama haka Ummu tayi hakuri da shi. Waye ya sani ko har dukanta yayi Allah Sarki Yar Mutane. Kiran Malam Zailani yayi ya gaya mishi a hankali yake kuka kamar karamin Yaro ya ce mishi. "Malam Tafida yana son fin karfina ji nake kamar na mutu da takaici,na rasa yadda zan yi da shi." "Alhaji Muhammad kenan, ka daina kukan nan kada ya tab'a shi!" "Ba shi nakewa kuka ba." "Kada ka damu, ka godewa Allah yadda ya tsaya a haka bai zama wanda zai na janyo maka magana daga waje ba, zan zamu cigaba da addu'a." Rarrashin abba Malam Zailani yayi, sannan suka yi sallama. Dakyar Deen ya saka shi a gaba har bangaren Ummu ya kwanta yana jin kamar zuciyarshi zata buga musamman yadda Abba ya haramta mishi maganar Ummu! A daren bayan tafiyar Deen ya kira Ummu Hadiyya, "ki kira Abba ki ce zaki dawo gidana!" Dariya tayi tana faɗin. "Allah Sarki Malam Tafida, da fatan ka dawo gida lafiya! Ai kai yanxu yayana ne don haka babu maganar dawowa!" "Ummu me yasa ba zaki dawo dakinki?" "Saboda bana son aurenka bana sonka bana kaunar na bude idanunka, Tafida bana sonka bana son aurenka ka rabu da ni na samu Lafiya!" "Naji amma ki gaya min me yasa kika tsane ni?" "Kai baka san dalilin tsanarka ba, ba kasan dalilin da yar baka mummunar me siffar goron bobo ta tsane ka ba, ka manta dalilin da yar Mace yar matsiyata. Yar mace me sayar da tuwo a kofar gidansu ba.." kamar zai fasa ihu ya ce mata. "Dama kina rike da wadannan kalaman na zata ya wuce tunda between ni dake ba wani abu ba ne don an samu ire-iren waɗannan stuffs din shine kike ta threating din kike wani d'aga min kai, Ummu ki cigaba da zama da aurena tunda ba zaki dawo ba, kina nufin ni Aliyu Muhammad Jadda Tafida na kira ki ina baki hakuri tow baki isa ba, har yau baki kai macen da zan bude bakina na baki hakuri, ki zauna a gidanku ." "Ba zaka tab'a sauyawa ba, ina bakincikin rashin samawa Yarana Uba na gari, na fada rayuwarka Idan ka gadama ka cigaba da rike auren har ranar da zaka ji labarin na mutu sai kayi murna, ba zaka sauya ba ba zaka tab'a sauyawa ba!" Ta fada tana jan hancinta. Kashe wayar tayi ya bi wayar da idanun, bai san lokacin da ya maka wayar da kasa ba ya mike tare da nufar dakinsa. *Ummu Hadiyya!* Ni a tunina da lissafina Tafida zai sauya ashe ba haka ba ne, domin bai sauya ba kuma babu al'amar zai sauya. Kowa damuwarshi na koma dakina amma basu san Tafida ba, hawaye ne ya zuba min, na share da bayan hannuna shigowa Mama tayi da ta kawo min namar da Baba ya kawo. Ganin yadda nake kuka yasa ta zama tana faɗin. "Kuka kuma?" A yadda tayi maganar a tausashe yasa ni na sake fashewa da kuka na kalleta cikin kuka na ce mata. "Don Allah ki bar ni na koma wurin Babana!" Kallona tayi bata iya magana ba, "wani abu ne ya faru?" "Kawai zan tafi nesa da nan ne!" "Kun yi fada da shi ne?" Cikin sheshakar kuka na ce mata. "Don Allah kada ki ce min na koma ki ni na koma can wurin Babana!" Yadda nake rokonta yasa ta kasa magana, bakiɗaya. "Me ya faru?" "Kawai na gaji ne na gaji na gaji wallahi gawata zaki gani na gaji na kai matakin da bana son kome sai nutsuwa!" Murmushi tayi tana faɗin. "Dakinki ne wurin da zaki huta, ki koma dakinki ki kara sa yakin da kika fara!" "Me yasa ba zaki gane halin da nake ciki ba, me yasa kike ƙoƙarin ganin ko zan cutu sai na koma ga Tafida? Mama Tafida ba mutum ba ne, ni ba zan iya gyara shi ba, don Allah ki bar ni na tafi!" Yadda nake kuka har da jan zuciya. Bakiɗaya ji nayi zuciyata tana zafi, tashi tayi ta bar ni a dakin. Bayan fitarta ko minti talatin bata yi ba sai ga sakonshi. _Idan kina burin na sake ki ne ki auri Mutumin gidanku, kin yi kuskure ba zan tab'a sake ki ba har abada gara na ga mutuwata da naga aurenki da wani mara kunya don ina bin ki shine zaki rena ni! Don haka ki zauna har ki rube!_ Hawaye ne ya zubo min kamar an bude pampo, a daren na kira Mudan. "Aunty Baby lafiya?" "Ana kiran sallah farko ka zo don Allah zamu yi tafiya ne!" "Aunty Baby lafiya kuwa!" "Kayi min alƙawarin haka!" Ina cikin wayar Baba Bulama ya shigo shi da Mama, kashe wayar nayi suka rufe ni da fada kafin suka daura da nasiha, kafin suka kira Babana, shima ya nuna min b'acin ranshi. Ashe bayan ya turo min sakon shine Tafida ya kira Babana ya gaya mishi ni da Abbanshi mun hade mishi kai, shi kuma Babana ya kira Baba Bulama ya ce maza na koma dakina. Daren ranar ban iya barci ba, domin ji nake kamar zan mutu kafin gari ya waye. A daren na hada kayanmu ni da Yarana, na saka Babban jaka sannan tun cikin daren na kira shi na bashi kayanmu, asubar fari muka bar Maiduguri, bayan na ajiye musu wayata, Bauchi na saka ya kai ni, ya juya duk yadda yaso ya fahimci halin da nake ci naki, domin sai karfe sha biyu muka shiga Bauchi. Kai tsaye na wuce inda motar da yake zuwa Lagos, don na fahimci Mudan ba zai tafi ba, haka na je na samu ana kiran motar Lagos da ya fito daga Yola,ina zaune har ya iso na biya kudin Abuja, Mudan yana nan ina sane don yaki tafiya. Haka motarmu ya tashi, ya fito yayi ta bin mu kafin ya juya ya koma Maiduguri. Number Tinah da na dauka a takarda na duba, Ban tab'a sanin Yan biyuna suna da farin jini ba, sai da mutanen motar suka yi ta daukarsu wannan ya dauka wannan ya mikawa wannan, har muka isa jos, Yaran suna hannun mutane, ni dai addu'a nake tofa musu. Bayan mun huta karfe shida na dare bayan nayi sallah muka bar Jos, karfe sha biyu muka isa Abuja, dare yayi don haka a tashan na zauna aka bani wani daki da aka tara kaya, sai a lokacin nake jin me yasa na bar gida, dakyar yarana suka yi barci. Kiran sallah farko nayi sallah asuba, sannan na fito na amshi aron wayar wani mutum na kira Tinah. Har wayar ta yanke bata dauka ba, na sake kiranta a karo na uku ta dauka tana faɗin. "Waye ne? A daren nan!" "Gari ya waye yan mata, ki saka a zo a dauke ni don Allah kada ki fadawa kowa daga Maiduguri!" "Ummu kece!" "Eh nice!" "A'a gani nan zuwa a wani tasha kike?" Na tambayi mutum na gaya mata. "Gani nan ki jirani Please!" Kashe wayar tayi, wurin karfe shida da rabi sai gata da kiran waya ta iso,amsar Yaran tayi tana me rungumar Mufidah tayi tana faɗin. "Ummu!" Sai hawaye sharrr, cikin kuka nace mata. "Babu wnada ya damu da ni, n bar Tafida na huta amma ban huta ba, Tinah ya zan yi." "Shiga Mota muje!" Ta saka yaran a baya, sannan ta dawo ta saka kayanmu, muka bar tashan bayan ta bawa mutumin da ya bani aron waya dubu biyar, yayi ta godiya. Ganin yadda nake kuka sosai, taka motar take da mugun gudu, ranta yana sosuwa. "Gaskiya har yanzu Northeast basu fahimci Muslunci kamar yadda Annabinsu kawo da hukunce-hukuncen addini akan aure da kuma pillar da zasu rike auren! Ana." Shiru tayi tana jin zafi tasan wannan da kasar turawa ne da tuni an bindige auren, tsaki tayi yafi sau uku. "Yaranki masu kyau da haduwa!" Ni dai kuka na cigaba da yi ban kuma amsa mata ba, koda muka isa gidansu ruwan wanka ta hada min, nayi wanka tayiwa Yaran, ta shirya su tana faɗin. "gaskiya yaran nan sun girman fa!"..... #Mai_Dambuhttps://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw *R&U BAG's GALLERY! Wai da gaske kun manta ne na gaya muku? Tow R&U ta kara dawo muku da kayan ado da kawwa wanda Ummu First Lady take amfani da su, tow dai Ummu tace na gaya muku a sirrince! Kawo kunnunku 🙉 a wannan R&U BAG's GALLERY babu abinda babu domin kamar kanti kwari ne a gidanki! Muna da kaya irinsu Atamfa, lace, shadda! Karewa dai har da lefe, kayan fadar kishiya, kayan Fitar suna na mai jego, kayan toshi na wanda saurayi zai kaiwa budurwa! Waya miyar sai a mota, muna bada dai-dai har da sari ku shiga domin tabbatarwa idanunku* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Hakki?" Ya tambaye ta, kafin ya fara duba aljuhun rigarshi da wandon shi yana niman hakkinta. Inda ya ajiye amma bai gani ya d'ago kai fuskarshi babu annuri ya ce mata. "Matsa ki bani hanya na wuce!" Ciki ciki ta ce mishi. "babu inda zan matsa ka bani hakkina kawai!" "Ba zan bayar ba, ke din wani hakkin ne dake, bakiɗaya mace babu dandano kina tsaye mace amma a zahirin cikinki gara a baka dafaffen kaza mara hadi, domin zaka ci shi haka da akan ke." "Wannan matsalarka ce, ita matarka da ka iya ci meye banbancinta da ni?" Kallon renin hankali yayi mata daga sama har kasa ya ce mata. "Ita ni na fara yanka kazar na fige sannan na dafa da hannuna babu wnada ya taya ni daga gefe. Kin ga ba tare da ajinamota da gishiri ba. Na cinye kazata, kuma har yau marmarin kazata nake!" Ya wuce ta abinshi yana jin ranshi fess. "Allah zai saka min!" D'aga kafada yayi yana faɗin. "Can miki!" Idan tana jin asalin zaman doya da manja tow kuwa shi suke da Tafida, domin bawan Allah nan baya kunya ya gaya mata magana anyhow. Ranar da suka cika sati biyu suka fara shirin dawowa gida, sannan ya shiga manyan store yayi ta sayayya kamar hauka Yaranshi da Ummu kawai su yakewa sayayya, yana gamawa ya wuce gida. A bakin kofarshi ya hango Sa'adi. Murmushi yayi mata yana faɗin. "Matar Governor!" Banza tayi mishi tana faɗin, "Aliyu ka bani hakkina mana, tun ranar da ka kai ni asibiti baka kuma bani hakkina ba ana maganar wata kusan uku." Gyara tsayuwarshi yayi da kyau sai kuma ya shiga cikin dakinshi yana faɗin. "Ke hala Aljanu ne dake masu jaraba?" "A"a Ifriqai nake dasu ba Aljanu ba!" Banke kofar yayi yana faɗin. "Ki je can ni bani da lafiya, basir yana damuna!" Shiru tayi kamar zata yi kuka tayi ta buga kofar Amma yaki. *** *Ummu Hadiyya* Tun lokacin da muka dawo daga gidan Malam Zailani, maganar da muka yi ya tsaya min a rai. Amma na tattara ba ajiye a gefe Tafida ba kamar sauran mutane ba ne, da zan sake waiwayarshi cikin sauki, dole ina bukatar sanin halin rayuwa da kuma yadda mata irina suke tafiyar da mutum irin Tafida, ba wai ban san halin Tafida ba ne, sai dai bana fatan na koma mishi har ga Allah domin yan uwanshi ba kaunata suke ba, gara na rufawa kaina asiri. Nayi zurfi cikin tunani wayata tayi ƙara, Hajiya na gani cikin farin ciki na dauka ina faɗin. "Hajiyata!" "Na'am yata, bayan ƙoƙarin da kika yi amma kin kasa zuwa duba Mamanki? Kodai baki son na miki maganar Baba Ali ne?" "A'a Hajiya ban samu fita ba ne, amma idan na samu fita zan zo in sha Allah." "Allah ya nufa na gode sosai, Allah ya miki albarka, yasa kema Yaranki su miki abinda kike mana, Ummu Hadiyya Ubangiji ya shirya bayanki da gabanki na gode sosai!" Idanuna ne suka cika da kwalla tabbas Hajiya ta gama min kome irin wannan addu'ar. "Amin Ya Allah, Amin Ya Allah, Allah ya baki lafiya Hajiya." Na fada kamar xan yi kuka don bana son yadda suke min godiya. Kashe wayar nayi ina sauke ajiyar zuciya. Na kalli Yarana sai naji sanyi a raina tabbas Allah ya min ni'ima da ba kowa yake da shi ba. Alhamdulillahi da wannan damar da Allah ya bani. *Shuwa* A gaban Malamin take kamar zata yi kuka ya ce mata. "Ita yarinyar a tsaye ake kansu, na gaya miki sai an tashi tsaye domin ko muna aiki zamu samu masu warwaresu." Idanunta sun kad'a jajjur ta ce mishi. "Malam babban tashin hankalina shine uwarshi ta dawo taya zan samu biyan bukatana!" Zane yayi kafin ya d'ago kai yana kallonta kafin ya ce mata. "Yarinyar ta dawo da ita, sannan babu wata hanyar da zamu iya kulla wani abu, sai mun samu hanya." Ya cigaba da zane kafin ya d'ago da mamaki ya kalleta ya cigaba da cewa. "Akwai hanya amma ba nan kusa ba, abu daya zan gaya miki shine ga wannan hayakin ki tabbatar an saka ya sha shima dan banza yana da taurin kai, wannan kuma a jefa a rijiya mu ga me zai faru nan gaba! Tabbas hanya biyu ne na farko ki tabbatar ranar da ya dawo ranshi a bace yake na biyu kuma gaskiya za a iya rasa rayuwar wani ko.wata akan aikin idan kuma kina ganin haka zai zama mafita to!" "A'a ban da kisa Malam, a barshi xan san yadda zan yi da shi." Zufa ne ya karyo mata, kafin ta ce mishi. "Allah yasa a dace domin yaron nan na sha fama akanshi yanzu da zan huta amma kowa yana niman hanani! Yan uwansa da nake amfani dasu ma sun fara ja da baya." Murmushi ya yi ya ce mata. "Ga wanann ki tabbatar kin saka musu, ba zasu tab'a miki gardama ba, sannan zasu zama masu miki biyayya!" Kudi ta zuba mishi, tana godiya ta fito. --- Tunda tasan abin da ta kulla, ta nufi bangaren Abba da ta dawo tana me kai karar Tafida. Domin idan ta fara da Abba tafida na zuwa Abba ya mishi magana zai fusata. Tana komawa bangarenta ta kira Saadiyyah, ta gaya mata duk rintsi kada su tawo Najeriya bata fusata Tafida ba. Ita kuma yayi mata alkawarin haka zai faru. Shirin da Shuwa take ba karamin shiri bane don haka ta kira Rukayya domin tasan ita ce zata fi bata haɗin kai, don haka tayi amfani da ita ta kirata da sunan ranar da Tafida zai dawo ta zo su yi abinci, dake bata da lissafi Allah ya zuba mata kwadiya, don ko Maryam bata gayawa gudun kada maryam ta mata faɗa, haka ta ki faɗa. Aikuwa Ana gobe zasu dawo Shuwa da kanta ta shiga bangaren Saadiyyah ta gyara mata, sannan ta koma bangaren Ummu da tasan dole ta nan sai fara shigowa, haka yasa ya turara bangaren tas. Da kyakkyawar shirinta, haka kuwa ya faru tun a jidda ta fara mishi tijara, bai kulata ba domin burinsa kawai ya isa ya nufi wurin Ummu da Yaransa. Don haka yaki yarda ya amsa mata domin kada ta yarda ta fusata shi lokaci zuwa lokaci yana murmushi, don na karamin dad'i yake ji ba, koda suka bar Saudiya a jirgi ma magana take gaya mishi. Har su iso garin Maiduguri Allah yasa sun iso da dare, don haka ba tare da ya damu ba ya kalli Mahmoud ya ce mishi. "Ka wuce da ita gida! Ni zan tafi ganin Ummu!" Ya kan wasu akwatina guda biyu. "Tow na zata gida zaka wuce!" Wani shu'umin murmushi dariya Sa'adiyya tayi, tana faɗin. "Allah yasa rawan kan da ake yi akan Ummu ya koma upside down" banza yayi mata bai yarda ya kula ta ba zai shiga motar Deen ta ce mishi. "Da alamu dai gudu abin kunyar da aka aikata yasa ana ƙoƙarin rufa-rufa, waye ya sani ko yaran ba jininka ba ne!" Cak ya tsaya kamar an dasa shi a wurin ya kasa gaba ya kasa baya. "Waye ya sani ko bayan kai akwai mata yi tunda ai kafin kai akwai wani a gidansu da yake sonta!" Ta shige motar da gudu, wani irin tafasa ranshi yake tunda ya shiga motar, jikinshi yake kyarma, asalin yarinyar ta san spot din da ya dace ta buga ta koma buga yadda ya dace, "wuce da ni gida na ci Uban Yarinyar nan." "Kayi hakuri ka fara kai musu kayan!" "Wuce da ni gidan kawai!" Yasan yadda ya fusata nan, ba zai saurare shi ba, don haka bai yarda ya kai shi gidan ba, ya wuce da shi gidan Malam Zailani. Ai kuwa yayi ta fada kamar zai daki Deen yaki kuma fitowa, Malam da kanshi ya tawo har wurin motar. "Aliyu!" "Sannu Malam!" "Allah ya tayaka riko tunda ba zaka samu shigowa ba, ina jiranka Allah ya tsare hanya." Bai ce kome ba shi dai burinsa ya isa gidan, Deen bai ji dadi ba haka ya ja motar ya bar gidan Malam. Har ga Allah Malam Zailani tausayin Tafida yake ji, domin zuciyarshi ita ce matsalarshi. Lokacin da suka isa ko parking Deen bai gama ba, ya fita daga motar ya nufi bangaren Shuwa don yasan Sa'adiyya tana can, yana shiga cikin fusata ya shiga kwallo da Sa'adiyya, yadda yake dukanta zaka ɗauka Allah ne ya aiko shi yana faɗin. "Ke din banza karuwan banza kin isa ki kama kafar Ummu yarinyar da ta kare rayuwarta da mutuncinta zaki zaga. Ke karuwa da maza suka gama hawa da sauka akanki zaki zagar min.mata da tafiki daraja." Bai damu ihun da Shuwa take ba ya mata duka har yana ture shuwa. Sannan ya bar bangaren jikinshi yana wani irin rawa domin bai tab'a jin fushi irin na yau ba, riko hannunshi Abba yayi kamar zai yi kuka ya kai shi parlourn shi ya ajiye shi tare da bashi ruwa, yana.sha yana haki domin babu abin da ya mishi kamar sheganta mishi Yaranshi a duniya bai da sama da su. Gumsar ruwan sanyi Inna tai ta fesa mishi, ya sauke wata ajiyar zuciya me karfi a kai akai. "Tafida!" D'ago kai yayi yana kallon Abba kafin ya ce mishi. "Yaushe Ummu zata dawo?" "Sai lokacin da kayi hankali ka koyi sanin darajar iyaye da Macen aurenka, ku zama shaida na raba Aliyu Tafida da Ummu sai ranar da yayi hankali!" Ya juya ya koma dakinshi, ya rufe kofar ya zauna a bakin gadon shi. Baya son yayiwa Tafida kuka amma tabbas deeply inside dinsa yana jin rauni a ranshi dama haka Ummu tayi hakuri da shi. Waye ya sani ko har dukanta yayi Allah Sarki Yar Mutane. Kiran Malam Zailani yayi ya gaya mishi a hankali yake kuka kamar karamin Yaro ya ce mishi. "Malam Tafida yana son fin karfina ji nake kamar na mutu da takaici,na rasa yadda zan yi da shi." "Alhaji Muhammad kenan, ka daina kukan nan kada ya tab'a shi!" "Ba shi nakewa kuka ba." "Kada ka damu, ka godewa Allah yadda ya tsaya a haka bai zama wanda zai na janyo maka magana daga waje ba, zan zamu cigaba da addu'a." Rarrashin abba Malam Zailani yayi, sannan suka yi sallama. Dakyar Deen ya saka shi a gaba har bangaren Ummu ya kwanta yana jin kamar zuciyarshi zata buga musamman yadda Abba ya haramta mishi maganar Ummu! A daren bayan tafiyar Deen ya kira Ummu Hadiyya, "ki kira Abba ki ce zaki dawo gidana!" Dariya tayi tana faɗin. "Allah Sarki Malam Tafida, da fatan ka dawo gida lafiya! Ai kai yanxu yayana ne don haka babu maganar dawowa!" "Ummu me yasa ba zaki dawo dakinki?" "Saboda bana son aurenka bana sonka bana kaunar na bude idanunka, Tafida bana sonka bana son aurenka ka rabu da ni na samu Lafiya!" "Naji amma ki gaya min me yasa kika tsane ni?" "Kai baka san dalilin tsanarka ba, ba kasan dalilin da yar baka mummunar me siffar goron bobo ta tsane ka ba, ka manta dalilin da yar Mace yar matsiyata. Yar mace me sayar da tuwo a kofar gidansu ba.." kamar zai fasa ihu ya ce mata. "Dama kina rike da wadannan kalaman na zata ya wuce tunda between ni dake ba wani abu ba ne don an samu ire-iren waɗannan stuffs din shine kike ta threating din kike wani d'aga min kai, Ummu ki cigaba da zama da aurena tunda ba zaki dawo ba, kina nufin ni Aliyu Muhammad Jadda Tafida na kira ki ina baki hakuri tow baki isa ba, har yau baki kai macen da zan bude bakina na baki hakuri, ki zauna a gidanku ." "Ba zaka tab'a sauyawa ba, ina bakincikin rashin samawa Yarana Uba na gari, na fada rayuwarka Idan ka gadama ka cigaba da rike auren har ranar da zaka ji labarin na mutu sai kayi murna, ba zaka sauya ba ba zaka tab'a sauyawa ba!" Ta fada tana jan hancinta. Kashe wayar tayi ya bi wayar da idanun, bai san lokacin da ya maka wayar da kasa ba ya mike tare da nufar dakinsa. *Ummu Hadiyya!* Ni a tunina da lissafina Tafida zai sauya ashe ba haka ba ne, domin bai sauya ba kuma babu al'amar zai sauya. Kowa damuwarshi na koma dakina amma basu san Tafida ba, hawaye ne ya zuba min, na share da bayan hannuna shigowa Mama tayi da ta kawo min namar da Baba ya kawo. Ganin yadda nake kuka yasa ta zama tana faɗin. "Kuka kuma?" A yadda tayi maganar a tausashe yasa ni na sake fashewa da kuka na kalleta cikin kuka na ce mata. "Don Allah ki bar ni na koma wurin Babana!" Kallona tayi bata iya magana ba, "wani abu ne ya faru?" "Kawai zan tafi nesa da nan ne!" "Kun yi fada da shi ne?" Cikin sheshakar kuka na ce mata. "Don Allah kada ki ce min na koma ki ni na koma can wurin Babana!" Yadda nake rokonta yasa ta kasa magana, bakiɗaya. "Me ya faru?" "Kawai na gaji ne na gaji na gaji wallahi gawata zaki gani na gaji na kai matakin da bana son kome sai nutsuwa!" Murmushi tayi tana faɗin. "Dakinki ne wurin da zaki huta, ki koma dakinki ki kara sa yakin da kika fara!" "Me yasa ba zaki gane halin da nake ciki ba, me yasa kike ƙoƙarin ganin ko zan cutu sai na koma ga Tafida? Mama Tafida ba mutum ba ne, ni ba zan iya gyara shi ba, don Allah ki bar ni na tafi!" Yadda nake kuka har da jan zuciya. Bakiɗaya ji nayi zuciyata tana zafi, tashi tayi ta bar ni a dakin. Bayan fitarta ko minti talatin bata yi ba sai ga sakonshi. _Idan kina burin na sake ki ne ki auri Mutumin gidanku, kin yi kuskure ba zan tab'a sake ki ba har abada gara na ga mutuwata da naga aurenki da wani mara kunya don ina bin ki shine zaki rena ni! Don haka ki zauna har ki rube!_ Hawaye ne ya zubo min kamar an bude pampo, a daren na kira Mudan. "Aunty Baby lafiya?" "Ana kiran sallah farko ka zo don Allah zamu yi tafiya ne!" "Aunty Baby lafiya kuwa!" "Kayi min alƙawarin haka!" Ina cikin wayar Baba Bulama ya shigo shi da Mama, kashe wayar nayi suka rufe ni da fada kafin suka daura da nasiha, kafin suka kira Babana, shima ya nuna min b'acin ranshi. Ashe bayan ya turo min sakon shine Tafida ya kira Babana ya gaya mishi ni da Abbanshi mun hade mishi kai, shi kuma Babana ya kira Baba Bulama ya ce maza na koma dakina. Daren ranar ban iya barci ba, domin ji nake kamar zan mutu kafin gari ya waye. A daren na hada kayanmu ni da Yarana, na saka Babban jaka sannan tun cikin daren na kira shi na bashi kayanmu, asubar fari muka bar Maiduguri, bayan na ajiye musu wayata, Bauchi na saka ya kai ni, ya juya duk yadda yaso ya fahimci halin da nake ci naki, domin sai karfe sha biyu muka shiga Bauchi. Kai tsaye na wuce inda motar da yake zuwa Lagos, don na fahimci Mudan ba zai tafi ba, haka na je na samu ana kiran motar Lagos da ya fito daga Yola,ina zaune har ya iso na biya kudin Abuja, Mudan yana nan ina sane don yaki tafiya. Haka motarmu ya tashi, ya fito yayi ta bin mu kafin ya juya ya koma Maiduguri. Number Tinah da na dauka a takarda na duba, Ban tab'a sanin Yan biyuna suna da farin jini ba, sai da mutanen motar suka yi ta daukarsu wannan ya dauka wannan ya mikawa wannan, har muka isa jos, Yaran suna hannun mutane, ni dai addu'a nake tofa musu. Bayan mun huta karfe shida na dare bayan nayi sallah muka bar Jos, karfe sha biyu muka isa Abuja, dare yayi don haka a tashan na zauna aka bani wani daki da aka tara kaya, sai a lokacin nake jin me yasa na bar gida, dakyar yarana suka yi barci. Kiran sallah farko nayi sallah asuba, sannan na fito na amshi aron wayar wani mutum na kira Tinah. Har wayar ta yanke bata dauka ba, na sake kiranta a karo na uku ta dauka tana faɗin. "Waye ne? A daren nan!" "Gari ya waye yan mata, ki saka a zo a dauke ni don Allah kada ki fadawa kowa daga Maiduguri!" "Ummu kece!" "Eh nice!" "A'a gani nan zuwa a wani tasha kike?" Na tambayi mutum na gaya mata. "Gani nan ki jirani Please!" Kashe wayar tayi, wurin karfe shida da rabi sai gata da kiran waya ta iso,amsar Yaran tayi tana me rungumar Mufidah tayi tana faɗin. "Ummu!" Sai hawaye sharrr, cikin kuka nace mata. "Babu wnada ya damu da ni, n bar Tafida na huta amma ban huta ba, Tinah ya zan yi." "Shiga Mota muje!" Ta saka yaran a baya, sannan ta dawo ta saka kayanmu, muka bar tashan bayan ta bawa mutumin da ya bani aron waya dubu biyar, yayi ta godiya. Ganin yadda nake kuka sosai, taka motar take da mugun gudu, ranta yana sosuwa. "Gaskiya har yanzu Northeast basu fahimci Muslunci kamar yadda Annabinsu kawo da hukunce-hukuncen addini akan aure da kuma pillar da zasu rike auren! Ana." Shiru tayi tana jin zafi tasan wannan da kasar turawa ne da tuni an bindige auren, tsaki tayi yafi sau uku. "Yaranki masu kyau da haduwa!" Ni dai kuka na cigaba da yi ban kuma amsa mata ba, koda muka isa gidansu ruwan wanka ta hada min, nayi wanka tayiwa Yaran, ta shirya su tana faɗin. "gaskiya yaran nan sun girman fa!"..... #Mai_Dambu🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Tea ta hada min me kauri, da soyayyen kwai da bread ta kawo min dakin, na sha kaɗan na ajiye na wanke bakina na zo na kwanta, a madadin barci sai naji hankalina yayi bala'in tashi, kamar nayi kuka na tashi zaune. Shigowa Tina tayi tana faɗin, "na zata kin kwanta ne? Ashe kina zaune har yanzu!" "Hankalina ne ya koma gida sai nake ganin kamar ban kyauta ba!" Murmushi tayi tana faɗin. "Eh da haka gaskiya amma kuma ki daina jin ba dad'i akan yancin kai! Tunda ba cin kai bane ki danne zuciyarki na wani lokaci ne zaki saba, kasancewar baki saba da barin Mama ba ne ban da aure!" Yadda take gaya min kalmomin masu kwantar da hankali yasa na iya rike zuciyata amma tabbas ban tab'a nisa da gida ba. Haka yasa na kwanta barci yayi gaba da ni. Ta rage mana karfin ac ta fita. Cikin fushi ta nemi wuri ta zauna tana jin kamar ta kama Tafida tayi ta caka kan dan banza da kasa, gayen nan bai da mutunci ko na kwandala. ** *BAYA DA KURAA.* Barin Ummu gidan Mama bata sani ba, domin kuwa tana can bangaren Baba Bulama, sai ya tafi masallaci mace take dawowa bangarenta. Haka ya faru da Mama itama Baba Bulama yana tafiya massalaci, ta fito itama ta nufi bangarenta, sai tana shiga dakin Baba Ummu babu Yaranta, gabanta ne ya fadi don tasan Ummu Hadiyya guduwa tayi hala biu ta wuce, don haka ta share bata kuma bin zancen Ummu ba ai tasan duk inda zata ce ba bai wuce wurin Babanta, ban daki ta shiga tayi alola tazo ta gabatar da sallah, tana idarwa wayar Ummu da yake dauke da apps na islamic calendar, ya fara kiran sallah, ware idanu tayi tana sake addu'ar da take. Ta nufi gadon tana me ɗaukar wayar "tabbas wayar Ummu ce!" Rasa nutsuwa tayi ta gagara zama, ta nufi bangaren Baba Bulama, haka ya dawo daga massalaci ya same tana zarya a cikin parlourn shi. "Lafiya Hadiza?" "Ummu Hadiyya tana gudu! Domin da wurin Ubanta ta tafi ba zata bar min wayarta ba, barin wayarta yana nufin ta tafin kenan kamar yadda ta fada zata tafi idan na ce dole ta koma Innalillahi wainnalihir rajouna! Ya Allah na tuba." Zube akan kujeran parlour, da tasan da gaske Ummu take ba zata cigaba da takura mata ba, "bari na gama na kira Alhaji Kabiru!" Haka kuwa ya kira Baban Ummu ya gaya tambaye shi ko Ummu Hadiyya tazo, ya ce bata zo ba, amma zai ta zuba idanun jiranta. Abu kamar wasa sai ga shi har rana tayi, babu labarin Ummu Hadiyya. Biu ma Babanta har gidan yan uwansa ya bincika ko ta sauka a can, wurin karfe uku na yamma Baba Bulama ya kira Alhaji Muhammad Jadda ya gaya mishi halin da ake ciki, da wani irin damuwa ya amsa. "Kuma bata tafi da wayarta ba?" "Gashi nan babu wani abu da ta bari na alamar tana nan kusa, don ta kwashe kayanta da na yaranta, ina ga akan maganar da muka yi fa Yaron nan Aliyu ne, muka ci ta koma shine ya bar gidan, Alhaji don Allah ka fahimce ni, a dakatar da maganar komen tunda ka ga lokacin da aka nemi auren bata bada matsala ba, yanzu kuwa ya dace mu mata adalci mu barta don kanta kada muce zamu tirsassa mata a haifi d'a mara idanun!" "In sha Allah, ba zai kara magana ba. Ummu tayi kokari tunda tayi wannan fushi dole mu bata lokaci ta huce don kanta." Haka aka bar maganar ko Tafida bai sani ba, kuma ko da wasa bai gayawa wani halin da ake ciki ba. Domin yana son Tafida ya fuskanci al'umma, amma hankalin kowa ya tashi, Abba ya kira Malam Zailani ya gaya mishi ya ce ya bashi lokaci, bai kuma kiran shi ba sai wurin karfe goma na dare, ya kira Abba yana murmushi. "Ku kyaleta ta huta, in sha Allah tana cikin kyakkyawar hannu babu abin da zai faru, zata dawo idan lokacin yayi, ayi ta hakuri." Abu kamar wasa Ummu ta b'ace a garin Maiduguri babu ita babu labarinta, Mudan bai yarda yaje gidansu Ummu ba, sannan itama Mama ta roki Baba Bulama ya bar maganar akan Ummu tafiya tayi, haka kuwa ranar Alhamis Ummu ta bar gidan, washi gari Juma'a Tafida ya kama aiki tare da gayyatar masu ruwa da tsaki na jahar, suka yi meeting washi gari asabar ma meeting suka ayi, ranar lahadi ya dawo gidan gwamnati shi daya, sai da ya samu nutsuwa ya kira Ummu. Amma bata dauka asalima Mama ce ke daukar kiran, take ya shiga wasi-wasi ba dai lamarin ya kai Mama ta kwace wayar Ummu ba, murmushi yayi yana kara godewa Allah da ya bashi suruka irin Mama, yasan zai yi wahala bata dawo da ummu ba don ya lura da Mama irin iyayen da can baya ne, wani fadaddar murmushi yana kara jin kaunar kanshi da kuma samun Mama da yayi tana sonshi. Sai dai kuma da ya kara kiran wayar ita ce dai ta dauka, yaso ya tambaye ta ama sai ya tsinci kansa da jin nauyinta, haka ya gama kame-kame ya kashe wayar, ranar Monday da safe ya kara kira Mama ta dauka anan ne ya fara jin wani abu yana faruwa, gaishe ta yayi tare da kashe wayar, sannan yana tsaye Deen ya kira shi yana gaya mishi, ga masu taimaka mishi shiryawa su zo, ya ce tow. Yana zaune tunda ya fito wanka yake mamakin meke faruwa. Haka suka shigo security suka musu iso aka kawo wanda ya taimaka mishi ya shirya, abin ka da dan gaye kin saka babban riga yayi asalima kayan kamar dinki senetor outfits aka masa. Yana sakawa kayan suka mishi das, kasancewar kayan blue black ne sai ya fito da Asalinsa da kyawun surarshi. Lokacin da ya fito wani kwarjini yayiwa ilahirin masu take mishi baya, yana tafiya suna bin sa har inda motarshi yake, Deen ya kira cikin sanyin murya ya ce mishi. "Bangaren Ummu a kara gaya mata shi don Allah, ba don na kai ba a saka abin bukatar Yara yadda zasu sake." "An gama You're his Excellency!" "Ka kira ni da Tafida ko Aliyu zai fi min wannan sunan." Shiru Deen yayi yana nazarin muryanshi kafin ya ce mishi. "Kana lafiya kuwa?" "Ina fa Deen na kira Ummu tun jiya Mamanta take dauka ban san me ya faru ba don Allah ka bincika min!" "An gama angon Ummu mijin Sa'adiyya!" Shan mur yayi yana me kallon gefen hanya har suka isa office, cikin satin bakiɗaya bai zauna ba sai ranar Juma'a da Abba ya kira shi, ya tafi har gidan bayan sallah juma'a yan unguwarsu kuwa cika suka yi suna kallonshi. Shiga yayi gidan domin ya saka an tsayar da motar daga dan nesa da gidan ne. A hankali ya zubawa tsohon bangarenshi idanun, yana tuno wasu lokuta da yake zuwa ya samu tana aiki a wurin, haka kawai yaga kamar tana zaune tana wanki, kurawa wurin idanun yayi yana ƙara jin wani abu yana taso mishi daga tafin kafarshi wanda ya janyo mishi kaikayi ba tare da yasan dalilin ba, har tsakiyar kanshi. Lumshe idanu yayi rabonshi da mace tun ranar da Ummu ta fara nakuda, yasan shi ya zungure mata haihuwar, domin yasan wunin ranar tana kwace dakyar take aiki, amma ya nace cikin dare duk da yadda take magiya da gaya mishi cikinta yana ciwo da maranta, ya shafawa idanunshi toka, y biya bukatarshi saboda son rai. "Ya dai?" Mahmoud da ya shigo gidan ya tambaye shi, "lafiya lau!" Ya nufi cikin gidan Mahmoud yana biye da shi, da wasu manya-manyan foodflask, gaida Tafida ake yana amsawa a nutsu har cikin parlour Abba, ya zauna yana gaida Abba da Yayunsa. Mahmoud ya gaida su tare da ajiye a Abba kular abincin yana faɗin. "Gashi nan ba yawa na gidan gona na ne na saka aka yankasu." "Allah yayi albarka, na gode Mahmoud!" "Bari na gaida Inna!" Ya fita waje, Abba ya bi Mahmoud da idanun yana mishi addu'a. Kallon Tafida yayi yana faɗin. "Ya aiki da alumma?" "Alhamdulillahi Abba!" Ya fada yana murmushi. Mika mishi Mug yayi da dafaffen madara yana faɗin. "sha wannan kafin kaci wani abu!" Amsa yayi yana faɗin. "Abba amma naga damina bata yi ba!" "Eh daga Yola aka kawo min." Ya kurba yana gyad'a kai, "Naji labarin ka kama aiki? Tow Allah ya baka sa'a yasa ka fara da hannun dama kenan!" "Amin Ya Allah!" Ya fada, kallon Abubakar da Umar sannan ya ce musu. "Ko waninku zai kira min Saleh da Matarshi da yar rikonsu?" Mikewa Umar yayi ya fita ya kira Samha ya gayawa mata sakon Abba, da gudu yarinyar ta fita, can kuwa sai ga Shuwa da mijinta tare da Sa'adiyya, bayan Abba ya a buɗe taron da addu'a ya ce musu. "Tafida ga Sa'adiyya yau da safe tazo tana rokon na kiraka ka maida ta dakinta, tayi kuskure don Allah ayi hakuri." Gyada kai Shuwa tayi tana faɗin. "ayi hakuri dai Alhaji a kara hakuri ni ban san me yasa bata jin magana ba, amma zan yi magana da Kanina Ubanta ya tsawatar mata domin ai aure ba abin wasa ba ne balle miji irin naki mijin marainiya, yadda take bawa Tafida hakuri tare da Uwarta shi kuwa ya ce musu. "Abba na ji sai dai ku zama shaida duk ranar da ta kara zagar min Yara wallahi na gama aurenta domin igiya ukun zan sake bakiɗaya na gaya muku gaskiya." "In sha Allah haka ba zai faru ba!" Inji Shuwa tana share idanun. Domin yanxu ne ya dace ta janyo Tafida jikinta, ya kara moranshi sosai. Haka Abba ya haɗa su yayi musu nasiha, Tafida yana ta jira yaji Abba ya kira komensu da Ummu amma shiru wannan abin ya d'aga mishi hankali, "Abba Ummu fa?" Ba Sa'adiyya hatta shuwa sai da ta girgiza tana jin wani irin bakinciki yana lallubeta. "Ummu?" Abba ya tambaye shi, sai kuma yayi murmushi yana faɗin. "Zata dawo amma ba yanzu ba, ta baka damar cin amarcinka kafin ta dawo!" "Innalillahi wainnalihir rajoun, Abba." "Hindu ki hada mata kayanta idan zai tafi zasu tafi tare." "Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana, mun gode sosai." Ta mike tana hararan inda Tafida yake, tana fita Abba ya wanke shi tas akan kuma ko bayan ranshi bai yarda ya tirsassa Ummu ta dawo gare shi ba sai dai idan ita ta bukaci haka, kuma idan ta ce ba zata zauna da shi ba ya sawwake mata, " idan kuma naji labarin ka kara kiran iyayen Ummu da sunan su mata magana ta koma ban yafe maka ba har abada!" Jin haka ya sashi jan bakinshi yayi shiru, amma Allah ya gani Abba ya mishi iyaka da Ummu, yana zaune a wurin har aka yi mangariba shi kan sa bai san me yake ji ba, bayan isha suka bar gidan ranshi a dagule, ya kira Ummu babu labarin wayarta ma baya shi, haka yayi ta trying. Alhaji Saleh da ya koma bangarenshi ya gayawa Hindu abin da ya faru. Ai kamar su tika rawa, nan ta kara jan Sa'adiyya a jiki ta gaya mata abin da zata yi. Haka suka iso gidan tunda suka fita a motar take hango daya side din da ya sha gyara ko ake kan gyaranshi ta ce mishi. "Can wurina ne?" Wani matsiyacin kallo ya watsa mata ya wuce, haka ta bishi tana faɗin. "Ina magana ka ki kula ni ko na kira Abba na gaya mishi abin da kake min ne?" Banza ya bawa ajiyar ta domin yana mata kallon mahaukaciya wacce bata da cikakken hankali da nutsuwa. Ganin hankalinta daya da na akuya ya tsaya tare da juyawa ya nuna mata daya side din bai kai inda ake gyaran kyau ba, ya ce mata. "Can naki ne." "Ni ne zan zauna a can da bai da bambanci da akulkin kaza, karya kenan wallahi!" Zuba mata idanun yayi kamar zai magana sai ya kuma wuce bangarenshi ya bude da sallama ya shiga, haka ya biyo shi itama, juyawa yayi yana kallonta kafin ya ce mata. "Ko zaki fita!" "Ni ba fa xan tafi can ba, haka kawai ina gani wuri me kyau ace na koma wancan me kama da kangon na zauna." Zuba mata idanu yayi, ya juya ba tare da ya ce mata cikanki ba, haka ya wuce ciki ya rufe kofar, yanayin tsarin gidan akwai babban parlour da ya hada sassan uku, sannan shi kanshi zai iya shiga kowani bangare ba tare da ya fita ba. A can babban kitchen aka fara shigo da abinci ana jerawa a parlour, lokacin Tafida ya fito alamu yayi wanka ya sauya kayane, waya yake cikin yanayin damuwa ya ce mishi. "Ok kawai ka same ni a office, zai fi dacewa da maganar amma zaka iya zuwa ba matsala. Yana zaune a parlourn aka kira shi ana gaya mishi yayi baki. Ya ce musu. "Su shigo!" Kashe wayar yayi yana kallon Sa'adiyya. "Ki wuce bangarenki bana son Magana!" "Karuwa za'a kawo maka da kake tsoron kada na ganta?" Lumshe idanu yayi yana jin maganar, kafin fitowarsu Abba yasa shi yayi mishi alƙawarin duk abin da Sa'adiyya zata yi, tow kada ya tab'a lafiyarta, ko yayi wani abu idan har ya iya zama da ita tow shi yasan me zai iya mishi. "Tashi ki tafi, ina da baki ne." "Babu inda zani na gaya miki." "Ok!" Haka kuwa ta zauna kyam, yana murmushi ya dauki wayarshi ya kira Number Shuwa. "Hindu!" Yadda ya kira sunanta babu girmamawa yasata harzuka. "Ki gayawa yarki da alamu tana shirin miki kafar angulu don haka ki gaya mata ko kuma wani Babban al'amari ya faru!" "Bata wayar!" Sakawa yayi a handsfree! "Tashi don ubanki yar iska mara kunya, ke wacce irin mutum ce? Kina ganin yadda kowa yake lallaba Ummu ke ba abin koyo ba ne a wurinki! Wallahi na rantse da Allah wani abu ya kara faruwa sai na miki rashin mutunci." Mika mishi wayar tayi tana faɗin. "Zan tafi to!" Ta fita a kofar suka hadu da Mahmoud, dauke kai yayi yana wuce ta, Tsaki tayi tana me kallon Deen da yake murmushi domin shi dai yarinyar nan bai ga wani abun burgewa a tare da ita ba, ikin hura mata kai ya ce. "First Lady, ya ake ciki ne yaushe zaki fara aiki?" Yake tayi domin tana mugun ganin girman Deen ta ce mishi. "Sai lokacin da Habibi ya amince!" "Tow Allah ya nuna mana." "Amin Ya Allah!" Ta juya tana tafiya ita nan ga yar gayu, shi ganinta yake kamar wata yar tasha. Dariya ce ta so kwace mishi ya shiga bangaren Tafida ya samu duk suna kan table shi suke jira, yana zuwa ya kalli Abincin. Fruit ya diba yana sha a nutse yana faɗin. "Ni fa fruit ya ishe ni, ba zan kara cin abincin gidanka ba, sai Ummu ta dawo haka zai saka na zo naci abinci hankali kwance."🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Mama* Abin duniya ya dame ta, don haka ta yanken shawaran zuwa biu ko boye Ummu babanta yayi domin yanzu ta fara gajiya da tafiyarta sati daya babu labari idan har Tafida ya cigaba da kiranta zata iya abin kunya duk yadda ya kai da ganin girmanta. Haka yasa ta shirya ranar asabar ta nemi iznin a wurin mijinta, ta wuce Biu gidan Yayarta ta sauka, tana me niman wuri ta huta. "Hadiza meke faruwa ne? Wancan satin Kabiru yazo akan yana niman Ummu, nace mishi bata nan yaki yarda sai da ya shigo da kanshi, abin ya daure min kai!" Zaro idanun tayi zufa na karyo mata. "Da gaske Ummu bata nan garin?" "Wallahi bata nan, domin ni da shi haka muka yi ta bin gidajen Yan uwa da abokan arziki, amma babu labarin Ummu!" "Innalillahi me na aikata? Kada dai Ummu saboda matsalar aurenta ta gudu?" Ta fada tana hadiye yawun tashin hankali. "Ban gane ba, wani abu ne ya faru?" Nan ta labarta mata yadda Ummu take ta kin komawa gidanta, cikin takaici da bakinciki Mama Lami ta rufe ta da faɗa, kamar zata dake tana me nuna mata sakarcinta na kin bawa Ummu damar fadar abin da yake damunta. "Shi ba ga shi can da Matarshi ba, ke da yake sallamamiya ce shine zaki tilasta mata ta koma dakinta, bayan ita tasan Meke faruwa a gidanta." "Tow ya zanyi zan bar Ummu ne ta cigaba da zama aurenta ya mutu, yaron nan binta yake yana bata hakuri!" "Naci Uwar hakuri na kwana, ke dai wallahi baki da hali ace Danka ma ba zaka iya taimakawa rayuwarshi ba, kin zama kyandir kashe kai haska wasu, a gaskiya Ummu bata dace da Uwa irinki ba domin a madadin ki zame mata sanyin idaniya kin zame mata tashin hankali, ki saurare ta ma abu ya gagara. Idan da sauran Yaranki ne zaki saurare su, shi yasa ake cewa Ina son Yarana eh na yarda ina sonsu idan naki su ina da wanda ya fisu ne, shi yanzu ba yana tare da iyayen shi ba ke kuma kin kora naki dawa. Idan Allah yasa aka ganta ta dawo wurin Ubanta ta zauna ai shi bai gaji da ita ba, ke da kike gudun abin kunya kada ace yarki ta kaso aurenta kina bin bayanta, su da suke fadar me zasu baki? Duk wanda yayiwa ƙaddaran wani dariya ya jira tashi ƙaddaran amma karfi da yaji kin saka yarki ta bazama duniya don Allah meye ribar haka? Meye amfanin abin da kuka aikata!" Yadda take fadar sai ga Mama har da kuka wiwi. "Ki gane wani abu duk abin da zaka yi mutane sai sun rena maka, mafi alkhairi kayi wanda Allah zai yarda da kai, kada saboda abin da wasu zasu fada muna tauye hakkin Yaranmu, mutane basu fasa fadar abin da suka yi biyayya ba, tun fil azal suke faɗa kuma haka zasu rayu akan fadar duk abinda yayi musu don haka wannan ya zame miki izina akan masu irin halinki, ita Allah ya huci zuciyarta ta dawo gida, domin ita aka yiwa laifi dole mu tsaya mu jira dawowanta." Mama Lami tayi fada sosai kuma laifin Mama ta gani da Mama bata nuna ta gaji da Ummu ba ai babu inda xata. Haka lamarin ya rincabe, daga gidan Mama Lami gidan Baban Ummu ta nufa, nan ma babu labari anan Mamawo tayi ta mata faɗa da yar nasiha akan abin da ya faru, wanda bata boye musu ba shi kan Baban Ummu barin su yayi ya koma dakinshi abin duniya ya dame shi, bai taɓa danasani irin na yau ba, yaki yarda ya fito bar Mama ta bar gidan, Mamawo ta shiga dakinshi ta ganshi zaune. "Malam hakuri zaka yi, in sha Allah Ummu tana kyakkyawar hannun." Kwanan Mama daya ta bar Biu, tun mota take share kwalla, domin har ga Allah tayi babban kuskure. ** *TAFIDA* Dakyar suka gama meeting din da suke ga ganawa da mutane da kuma zuwa majalisar jahar da zai yi, babban damuwar shi Deen da ya ce mishi Akwai matsala, domin Deen yana zuwa gidan bai yarda ya shiga cikin ba, Uwani ya kira ya tambayeta Ummu. Shiru tayi kafin ta ce mishi. "maganar gaskiya Ummu babu wanda ya san inda take? Har yau da nake maka maganar nan ana nimanta!" Shiru yayi kafin ya ce mata. "ban gane ba kina nufin Ummu an nime ta ba a ganta ba?" "Eh wallahi wayarta ta bari a gida kawai!" "Yaran fa?" "Hm tana tare da Yaranta!" Shiru yayi kafin ya jinjina kai yana faɗin. "Na gode! Amma gidansu Tafida an sami labarin kuwa?" "Eh tow naji Mama tana cewa an gaya Abbanshi amma ban sani ba ko shi yasan abinda yake faruwa, ni nasan wacece Aunty Baby ba zata tab'a barin mijinta haka kawai bayan ta jima bata yi aure ba, kawai akwai abin da aka mata ne." Lumshe idanu yayi yana gyada mata kai. "Abubuwa dayawa, amma kuma lamarin mata da miji sai Allah, kada mu zake su babu kunya!"da wannan suka yi sallama, tun ranar juma'a yake son gayawa Tafida amma kamar Mahmoud yasan akwai wani abu a kasa ya tattare yana nanikewa Tafida, haka shima Tafida kamar ya zare saboda tashin hankali. Shi kanshi Deen ya rasa yadda zai fuskanci Tafida da zancen kawai sai ya share shi ya nime labarin da kanshi, sannan Deen yayi kokarin bibiyar duk wani tasha da hotonta amma babu labarinta. Bayan sallah isha ba tare da sanin kowa ba, Tafida ya ja Motarshi tare da zuba kashedi kada abishi. Kai tsaye gidansu Ummu ya nufa, babu wanda ya san shine don an dauke wutar unguwar babu haske, shi kanshi bai ji dadin yadda yake tafiya a cikin duhun ba, bai ce kome ba ya nufi gidansu Ummu garin wucewa cikin rashin dace ya fada kwata, Wayyo Allah cikin wani tashin hankali da dimuwa ya mike yana jin wani irin wari da hamami, kamar zai yi amai haka al'ummarshi take rayuwa? Waye wakilin mazabarsu waye dan kwangilar. Haka ya wuce wurin Motarshi yana me barin unguwar, government house ya nufa, yana shiga ya hadu da Sa'adi, bai ko kalleta ba ya wuce side dinsa yayi wanka ya kai sau goma. Kafin ya daina jin warin da yake yi, daki yayi ya fito, yana zama ya ƙara kiran layin Ummu yana jin wani irin abu, har lokacin wayarshi a kashe. Kiran Deen yayi cikin gajiya ya ce mishi. "Deen meke faruwa ne?" Shiru Deen yayi kafin ya ce mishi. "Ka je gidansu Ummu ba zan iya baka labarin nan ba, domin laifinka ne kome Ummu tayi ba, da baka mata abin da kayi ba da yau kana cikin nutsuwa bayan abin da kayi bai isa ba sai da ka hada ta da iyayenta. Alhamdulillahi sai ka je ka ji me ke faruwa nayi ina yina sauran ya rage naka!" Jininshi ne ya fara tafasa yana ji kamar ya bude idanun ya ga gari ya waye amma ina ya kasa wannan hakurin, Kiran Number Baba Bulama yayi cikin sanyi jiki yake gaishe shi duk da rawan da jikinshi yake, "Baba meke faruwa ne? Kusan sati biyu ina niman Ummu bata daukar wayar, don Allah wani abu ya faru ne?" "Aliyu bamu ga Ummu ba, sannan abin tashin hankalin bamu san inda take ba. Muna da yakinin Ummu tana cikin amincin Allah, amma kafin yau meye tsakaninta da kai da taki dawowa gidanka? Yarinyar nan tana gabana tsawon shekaru bata tab'a kafewa bata son abu ba sai akanka ta ce bata son gidanka ban san me ka mata ba, amma koma meye ba zamu daura maka laifi ba domin kuwa bata gaya mana ba" A hankali yaji tsoron kada dai Ummu tana rike da duk abinda suka faru ne yasa taki dawowa daga karshe ta gudu,, wani abu yaji ya daki zuciyarshi tunda yake bai tab'a jin tsoro irin na yau ba, idan dai Ummu zata hukunta shi da laifin da yayi mata ne tow kuwa kwananshi ya kare, muryan shi na rawa ya ce. "Don Allah Baba kada ka tambaye ni kome. Ina Ummu take, kayi min rai ina bukatarta ne." "Aliyu na gaya maka gaskiya Ummu bata tare damu, ka je duk inda zaka, kayi bincike iya yadda ya dace, amma maganar gaskiya Ummu ta b'ata. Bamu san inda take ba." "Innalillahi wainnalihir rajoun, Na shiga uku!" Ya furta yana kashe wayar, a daren ya kira Kwamishin Yan sanda da duk wani me ruwa da tsaki, tare da Deen aka fara bin tasha amma babu labarin Ummu kai a takaice har ƙarfe uku na dare, ana niman Ummu. Wannan barci barawo bai dace Tafida ba. Lokacin da Abba yaji labarin Tafida ya hautsina garin Maiduguri ana niman Ummu, sujada yayi tare da d'ago hannu sama yana zabga kirariwa Ubangiji. Hajiya ma lokacin da labarin ya iso kunnanta, hawayen Farin ciki da bakin ciki take. Domin tasan kaf duniya ban da Ummu babu wacce zata jure halin Tafida ba tare da Mutane sun shiga tsakaninsu. Ai kuwa tana son yin Azumi amma ta gagara dole ta dafa abinci na sadaka ana ta rabawa mabukata. Haka lamarin ya kasance, lokacin da Shuwa ta ji labarin b'atar Ummu da Yaranta, kiran Malaminta tayi tana faɗin. "malam aiki kayi mana me zafi haka? Domin Yarinyar nan an nime ta an rasa." Murmushi yayi yana faɗin. "Ifiritu kaezuzu ne ya ɗauke ta da cika Umarnina, ya tsallaka da ita bangon duniya Ummu ta tafi kenan har abada, ba zata kara waiwayar gida ba har abada." Nan ya cigaba da cika shuwa da karya da kuma gaya mata wannan aikin da ya mata sai da ya kashe sama da dubu dari uku, domin ifiritu kaezuzu harijin ifiritu ne baya aiki sai ya kwanta da matan aljanu guda tari cak, saboda kada ya ji sha'awaar mace ya fasa aiki don rauninsa kenan, don haka Shuwa ta tura mishi dubu dari hudu. Wasa wasa Tafida yana tsaye ne, amma ya zabge kamar bishiyar da aka wanke mata rasanta. Kallon Abba yake da yasaka shi a gaba yana mishi fada. "Ayi haka akan Ummu ka daina zuwa office sai dai kawai kayi ta yawo a gari, Al'umma suka zabe ka ba Ummu ba, ka tsayar da hankalinka akan Mutane ." Bai ce kome ba har Abba ya gama sannan a hankali ya mike yana faɗin. "Na ji Abba!" Ya bar parlourn, yana fita ya fada Motarshi. "Ghali wuce da ni Biu!" "A daren nan?" "Muje babu abinda zai faru!" Haka suka dauki hanyar biu. Basu isa ba sai karfe biyu na dare, a kofar gidan Baban Ummu suka tsaya, a tsohuwar daren nan ya buga gidan Baban Ummu. Sai da suka buga sau uku Baban Ummu ya fito yana faɗin. "waye ne a wannan daren?" "Aliyu Tafida ne!" "A wannan daren?" "Eh Baba!" Bude musu kofar aka yi ya shiga parlour da a can baya yake renawa da kallon talauci ne yasa aka ki gyara parlour, yau sai yaji bakiɗaya babu inda yafi mishi dadin zama kamar parlourn. "Barka da dare Baba!" "Yawwa Aliyu kai ne ashe!" "Eh Baba!" Gyara zaman shi a kasa Baba ya ce mishi. "Ka koma kujeran yafi kasan nan!" "A'a nan ya ishe ma Baba!" "Meke tafe da kai?" "Ummu nazo dauka?" "An gaya maka Ummu tana nan ne?" D'ago kai yayi yana kallon Baba. "Bata so nan ba, idan baka yarda ba ka shiga cikin gidan ka duba!" Dafe kai yayi yana faɗin Innalillahi wainnalihir rajou, abin da yake nanatawa kenan, kafin ya mike yana faɗin."zan tafi nimanta." Kaman hadin baki Baban Ummu ma fada ya mishi, idanunshi ya kad'a jajjur, sai huci yake yana kara jin tsanar duk wanda ya taya shi wulakanta Ummu, yaji ya tsani kowa. Haka a daren ya dawo Maiduguri ana shiga gida ana shiga sallah asuba, haka ya tafi masallaci ana ta jajjanta mishi domin ana ganin, abin kamar saka hannu ne. Da gari ya waye ya tafi office, da wuri ya dawo ya rufe kanshi a daki, bai taɓa jin b'acin rai irin wannan ba Ummu ta b'ata ita da Yaranshi ina suke ne.....🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Dama da take cewa zata tafi idan bai kyaleta ba da gaske ne dama? Shi ya dauka tana mishi barazana ne don ya kyale ta ashe har cikin ranta da gaske take, tunda Sa'adiyya taji labarin Tafiyar Ummu, ta saka Tafida a gaba da rashin mutunci kala kala, wanda ya ja dole ya zuba mata idanu, a lokacin da Mahmoud yaji labarin zama yayi yana nazarin yadda zai shiga tsakaninsu. Ya jima yana nazarin abin, duk da lamarin duniya kome ya faru idanun jama'a da yan jarida yana kan kowa haka Yan jarida suka fara rubutu akan b'atar Ummu yayinda su suke cewa. *Me yasa Ummu Hadiyya Matar Gwamna Aliyu Muhammad Jadda ta gudu? Ko dama can tana da wani saurayin ne ta bishi?" Wannan al'amarin ya saka Tafida tashin hankali inda ya saka aka kawo dan jaridar cikin fushi yayi kanshi Deen ya rike shi yana faɗin. "Me yasa zaka fusata? Su je su ta fadar abin da ya musu! Calm down my Friend fada ba naka ba ne, idan kayi da shi akwai gidajen Jaridun da nayi Imani da Allah biyansu aka yi su tunziraka, by now Ummu ba ita bace rauninka balle har ka yi hukuncin don an fadi maganar banza, koma ka zauna." Deen ya kalli gayen Matashi ne wanda bai wuce shekaru ashirin da biyar ba, ya ja kujera ya zauna gayen yana tsaye. "Ga kujera ka zauna!" "a'a nan ma ya ishe ni!" Murmushi Deen yayi ya ce mishi. "Jarida tana fitowa aka turo min, ina gani na ce a bincika min waye kai da inda kake waye mahaifinka, sai naga ashe dan bautar ƙasa ne daga Kaduna, na kuma saka an bibiye har garinku da ungimuwarku, ka fito tudun Wada layin yan kosai, kusa da masallacin Izala!" Zubewa Yaron yayi tare da sunkuyar da kai jikinshi yana rawa. Deen ya sake murmushi. "Mahaifinka tsohon drive ne, kafin yayi hatsari Mahaifiyarka tana sayar da kamun kunu da itacce,kana da kanwa tana sayar da awara da koko da la'asar. Da da dare tana abinci kamar taliya ko?" Ya tambaye shi yana nuna shi da yatsa. Kuka gayen ya fashe da shi. "Look ban san Tafida zai kawo ka ba,domin ni na gama nawa abin da zan gaya maka shine ka sake nuna Tafida da Yatsa." Murmushi yayi yana faɗin. "Ba bincike zan yi ba hukunci zan yi kada ka yi tunanin nafi Tafida sauki! Ni nan jekariyarshi, na kara jin kayi rubutu ka kuka da abinda zai faru tashi ka tafi" kuka gayen yake yana bashi hakuri ya ce mishi. "Lukman muna da halin tab'a kowa amma kafin muyi magana, mu fara duba waye wanda zamu tab'a waye yake tare da shi. Nasan akan kudin da zai kare aka baka, kayi a hankali da rayuwarka! Su waɗanda suka saka ka wannan aikin su fuskanci Tafida ido da ido shine zasu cika maza, ban da muna lissafi da na shafe labarinka daga Kaduna! Tunda ka iya rubutu baka iya nazari ba ka kira Mamanka, ka ji ya jikin Babanka yake out of my sign!" Mikewa yayi da sauri yana ta buga godiya yana kuka, wannan masifar da me yayi kama, "Me yasa ka kyale shi?" "Kana da hauka ne? Niman hanya ta kowani fuska a lalata maka suna, matukar ina raye zan zama Inuwarka in sha Allah idan ka ga abu ya same ka haka Allah ya rubuta zai faru da kai, tun fil azal amma ina tare da kai babu abin da zan taba bari ya same ka. Ka ajiye Ummu a gefe duk inda take tana kallonka, ka fuskanci al'ummar da suka zab'e ka!" Deen ya mike yana faɗin. "Kasan Allah ka rame wallahi!" Ya fada yana bude wani basket da yazo da shi zuba mishi abinci yayi yana faɗin. "Maza ci!" "Deen na koshi!" "Sha kunun!" Amsa yayi ya fara sha a hankalin, yana sauke ajiyar zuciya. "Deen bana barci!" "Ba zaka iya barci ba domin zuciyarka tana ga Ummu!" "Ba fa wasa nake ba!" "Saboda girman kai yasa ba zaka iya fitar da shaukinka ba kada a rena mai girma Gwamna!" Banza yayi da Deen yana faɗin. "ka kyautawa kanka da kayi shiru!" Bayan sun gama Deen ya kwashe kayanshi yana faɗin, "zan tafi wurin aikina! Idan an tashi ka kira ni zan zo daukarka mu fita wani wurin." "Tow na gode!" "Aliyu ka fuskanci al'ummarka kada ka kara tasa zancen b'atar Ummu ko da kuwa da ni ne, na gaya maka " "na ji Deen!" "Mai kan kwakwa!" Ya fada yana barin office din. Yana zuba kayan abincin a motarshi ya kira wani abokinsa wanda lauya ne da ya daukawa Deen, mutumin Bayarabe ne, ya gaya mishi ya jira shi gashi nan zuwa, yana zuwa ya samu lauyar da wasu lauyoyi uku. "Mr Safiyyudeen ka iso!?" "Eh na iso ka biyo ni!" Ba tare da sanin Tafida ba,Deen ya tafi har gidan Alhaji Mansur Goza, da yake wajen garin Maiduguri. Da lauyoyi, lokacin da suka tafi ganin Lukman ya kara tabbatar mishi aikin Alhaji Mansur ne, "Kai me ya kawo ka nan? Kana son ka mutu ne?" Ciro madubin idanunshi yayi yana hure Madubin yana faɗin. "Waye ya gaya maka mun zo nan ne mu daya kalli sama!" Wata karamar jirgin sama ce irin ta yara amma shi wannan da tambarin sojoji. " sannan wannan madubin akwai abin ɗauka. Kasan me? Kayi rigimarka kamar yadda kaso ya zame maka kamar Jela shi kuma yaki. Ni masanin kimiya ne ba iya kimiyya ba hatta yadda ake haɗa mugayen sinadarai irin abin shan da yake hannunka na san kansu. Na fahimci lissafinka baya ja, ka turo yaro ba gaya masa waye mu, na kuma kara bashi shawara ya tsaya a gefe. Yaron nan da Tafida suna bayan kulawa ne, musamman mutuncin Tafida da iyalinsa. Idan ka sake wani abu ya kuma faruwa Lauya ajiye takardan yarjejeniyar sulhu idan wani abu ya kara faruwa ku zama shaidana allon kalla zan saka akfta min katon hotonka a manna a gari kowa yana gani na rantse da Allah, ka kara gwadawa ka gani!" Haka lauyoyi suka bashi takardan saka hannun yaki sakawa. Mika mishi wayar aka yi ta bayanshi ya dauka. "ga wasu jami'an tsaro a kofar gida zasu shigo! Wai zasu yi bincike ka san da su?" Kallon Deen yayi ya d'aga mishi gira daya yana faɗin. "Zaka saka hannu ko sai sun shiga cikin gidan sun binciko abin da kake boyewa? Tun muna Yara na gayaws Tafida ya girma ya zama babban Mutum ni zan zame masa jekariya duk abin da nake zan saka idanuna akanshi, kasan me yasa ban damu da sauran abin da yake ba, iya zama a tare a shi wani arziki ne na musamman. Ka zama mutumin kirki yadda kowa zai yi koyi da halinka, saka hannu ko su shiga wannan dakin da kake boye shi!" Saka hannun yayi jikinshi yana wani irin rawa, domin wallahi bai tab'a sanin akwai wanda yafi Tafida rashin mutunci ba, hadiye yawu yayi ya saka hannu. "ka kyautawa kanka!" Ya amshi takardan yana faɗin. "daga yau babu ruwanka da Tafida!" "Idan ni ka raba dani da shi sauran da suke kokarin ganin ya gaza fa!" Murmushi Deen yayi yana faɗin. "Kada ka damu yadda na iya tsamo ka sauran zan iya tsamo su kamar yadda ake tsamo nama a cikin miya!" "Kada tsoron rayuwarka ne? Ko baka da wani fata ne?" "Tsoron me zanji? Ko mutuwa nayi akwai Mahmoud, sannan fata na daya na tashi da Tafida a karkashin alrshin Ubangiji ka fahimta, ni ba kare ba ne da kudi zai sauya min rayuwa!" Daga haka ya kalli Lukman. "Zaka zo mu tafi ne ko zaka zauna da shi?" Mikewa yayi yana kallon Alhaji Mansur Goza. Shima tashi matsalar tafi ƙarfin ya kula shi, "Ya batun jami'an da suke kofar gidana!" "Ai tuni sun kara gaba!" Deen da mutanenshi suka bar gidan Gonan. Deen da Deputy suka tsaya sosai akan Tafida, domin aikin jaha guda a halin da Tafida yake ciki ba karamin al'amari ba ne, bakiɗaya ya tsinke ya fita hayyacinsa, gani yake kamar wayewar gari za a ce an ga gawar Ummu da Yaranshi, amma babu labarin, ranar da Ummu ta cika sati uku da kanshi ya tafi gidan Malam Zailani ta taimakawan Deen. Tunda ya isa gidan ya zauna yana me sunkuyar da kanshi. Murmushi Malam Zailani yayi yana faɗin. "matarka da Yaranka Lafiyarsu lau!" D'ago kai yayi yana kallon Malam Zailani idanunshi jajjar har kana ganin kwalla yana taruwa. Murmushi yayi a karo na uku. "Da kyau jekariya ba gari, ka kasance da shi zuciyarshi take sarrafa shi da kwakwalwarshi. Yarinyar lafiyarta lau ita da Yaranka, matsalarka girman kai ka amshi laifinka zata iya sassauta maka!" D'ago kai yayi yana faɗin. "Akan me zan amshi laifin da ban san nayi ba?" "Akan me kake barin zuciyarka take ciwo? Gaba kaɗan zaka fara kuka kana rike kirjinka!" Ya fada yana murmushi, ya cigaba da cewa."koda yake akwai dole Kanwar naki zata saka ka fadi laifinka da bakinka, yanzu aikin al'ummar borno ya dace ka fuskanta, domin kada Ummu ta zama rauninka yadda zaka kasa tabuka kome!" Yadda Malam Zailani yake mishi magana yana rubutu ya ce mishi. "Kai yanxu idan ka bari Ummu ta dawo ba kyautawa mutane dayawa ba, ka nuna baka damu da tafiyarta ba ta haka ne zaka fahimci meke faruwa." Haka yayi shiru har zuwa wani lokaci kafin ya wanke rubutun ya mika mishi. "Kai ce maka aka yi rashin barcin nan da baka yi kawai tunanin Ummu ne? Ko daya don ma Mahaifiyarka tana tsaye kanka daga nan ka wuce ka duba ta." Gyada kai yayi yana kallon kasa, haka Malam yayi ta mishi nasiha tare da nuna mishi kuskuren shi na rashin kyautatawa Iyaye. Sannan suka baro gidan wurin Hajiya, suka wuce anan suka zauna har dare haka kawai Tafida ya ji baya son barin gidan. "Deen jeka zan kwana anan!" "Alhamdulillahi shi kenan, Hajiya zan tafi sai da safe." Har waje ya rako shi, "Deen unguwarsu basu da wuta sannan akwai wuraren da ba su da kyau ina gaya maka ranar na je na fad'a kwata kada ka ji wari da nake don Allah gobe a tuna min ." "In sha Allah!" Suna tsaye Deen ya tura sako wa security. Kafin su yi sallama unguwar ya samu bakoncin hukumar tsaro, "zan tafi Tafida! Ka gaida Madam!" "Yawwa zasu ji ita kuma Sa'adi baby fa!" Danna mishi ashar Tafida yayi ya juya cikin gidan. Dariya Deen yake yana karawa. A parlourn Hajiya ya kwanta ta ce mishi. "Zo ka shiga daki ka kwanta!" "Hajiya nan ya ishe ni!" "Shi kenan!" Ya fada yadda tayi maganar sai yaji bai ji dadin haka ba, mikewa ya nufi cikin dakin ya kwanta a gadonta, ita kuma ta zauna a kujeran dakin rike da casbi, mikewa tai ta kashe wutar dakin ta koma ta zauna, tun yana iya hangota a dan hasken da yake ratsa dakin, har barci yayi gaba da shi. Tana zaune a wurin jin saukar ajiyar zuciya yasa ta haska shi da torching ta. Hawaye yake zubarwa yana barci. Tashi tayi ta koma gefenshi tayi tana tofa mishi addu'a, a hankali hawayen ya daina zuba. Mikewa tayi ta nufi banɗakin da yake cikin dakin tai alola tazo ta shimfida abin sallah. Matar nan raba dare tayi tana gayawa Allah kukan da danta yaƙe, tun karfe sha biyu take ganawa da Ubangiji bata tsaya ba dai karfe hudu cif, ta cigaba da addu'a bayan tayi sallah. Ita kanta bata san iya adadin raka'o'in da tayi ba. Allah ya daidaita Tafida da Ummu wannan shine fatanta, tuj wurin karfe daya aka buga bindiga haka ma hudu na asuba da rabi aka kara bugawa. Kallonshi tayi tana me shafa fuskarshi. "Babana tashi ka tafi sallah!" "Ummu!" Ya furta a hankali. Murmushi tayi tana kara jin tausayinshi ta shafa kanshi. "Babana tashi ka tafi sallah asuba!" Bude idanun yayi yana kallon Hajiya idanunshi sun kad'a jajjur. A hankali ya tashi, ya nufi banɗaki alola yayi ya nufi waje, da jagorancin jami'an tsaro ya isa masallacin, abin sai ya bawa yan unguwar Mamaki Tafida a unguwarsu. Matsa mishi aka yi akan ya shiga sahun bayan liman, cikin sassanyar murya yace musu. "Bismillah." Ya tsaya a sawun baya tare da mutane da yawa, ana idar da sallah, kowa yayi tsammanin zai fita ne, abin mamaki sai aka ga yana zaune yana azkar, kusa a shi Abubakar ya dawo ya zauna yana murmushi. Mika mishi hannu yayi suka yi musabaha, wani abin mamaki bakiɗaya masu sallah aka kasa fita. Can Limamin ya fara addu'a da bayani da kuma rokon alfarman abubuwan bukatar da suke so kasancewar Unguwar sabuwa ce. Bayan sun gama ya kalli Liman ya ce mishi. "Ku hada kwamiti na yan unguwa ka bawa Yayana sakonku, idan ma baku same shi ba, ku kai sakon wurin Hajiyata zata iso muku da shi har wurina, tafiya ce ta ratso ni nan, na gode sosai da mutumtawa ku taya mu aiki gwamnati ba zata manta da ku ba, na gode sosai da bani damar sallah a cikinku!" Suma godiya suke suna kara jin dadin ciki ashe haka suke basu da girman kai. Sannan ya musu sallama ya koma gidan hajiya, ya samu ta hada mishi abin karyawa tea ne, a gurguje ya sha yana me faɗin. "Deen zai zo amsa min abincin rana!" "Kai ba zaka zo ba ne?" Yake yayi Abubakar ya ce mata. "uzuri yake da shi, Hajiya nima a saka min tea din!" Ya shigo parlourn yana kallon Tafida da yake kurban tea. Bai shanye ba zai mike ta rike hannunshi. "sunnar Annabi ne cin kome a nutse, zauna kada ka kware." Zama yayi yana hura tea din amsar kofin tayi ta d'aga mishi shanyi. "Hajiya Tafida ba yaro ba ne fa, haka kawai kina sakalta shi. Akwai kanwarshi fa Sabirah." Murmushi tayi tana faɗin. "eh dama ina son na dauko yaranta, tow ku naje jira na ji me zaku ce!" "Hajiya da a dauko miki su in sha Allah zan tura Deen!" "Shi Deen bai da aikin yi ne sai..." "Assalamualaikum, ya na iya Hajiya Tafida ya mai dani dan dakon shi." Ya shigo parlour shima yana faɗin. "Kai Jama'a, Tafida ga yaran can a waje suna jiranka zasu ga gwamna!" Ya zauna yana me karban kofin hannun Tafida, "Tow Ya fada yana jin kamar an yantashi agogon hannunshi ya kalla wato sun jima a masallaci, don har bakwai da minti goma sha biyar. Wajen ya nufa ya samu suna ta hayaniya, bude kofar yayi ya zuba musu ido. "La wallahi shine!" Fitowa yayi ya dan duka kaɗan yana kallonsu. "Kuna jina ko! Tow sunana Tafida ku yi karatu sosai domin ku zama gwamna kuma!" Ihu yaran suka yi. Ya kara ce musu. "Ku zama mutanen kirki masu yarda da kansu, ina makarantarku yake?" Nuna mishi hanyar suka yi suna ta murna, ya saka su a gaba security suka take mishi baya har makarantar, Firamare me hade da secondry school, shiga yayi kafin kace me an baza ga gwamna da kanshi a makarantun. A hankali yake bin yaran har cikin makarantar, office din principal ya nufa mutum daya ne a office din, "kai daya ne?" "A'a yallabai akwai wasu a staff office." Ya fada yana fitowa, suka nufi office din mata biyu ne sai namiji daya, fitowa yayi suka biyo shi, bakin gate ya dawo ya tsaya yaran suna biye da shi, sai tambaya suke mishi. "Gwamna kana yin wasa kuwa?" "Kai dalla can waye ya gaya maka yana wasa baka ganshi babba bane?" "Ina wasa mana, har da wurin wasa na bude a gidana " turbune fuska yaron yayi yana faɗin. "Hala ma har da keke kana hawa!" Rike dariyarshi yayi yana faɗin. "Matori ina har da keke nake da shi!" Matori security dinsa ne gyada kai yayi yana faɗin. "Eh har da doki duk akwai a gidan!" "Laaa kace kana da rago ma!" "Eh har da kaza ma da biri duk yana dasu!" Hankalinsa yana kan get, a hankali ya ga malaman makarantar suna shigowa, kowa ya sha jinin jikinshi. Sai da suka gama zuwa har karfe takwas a haka kuma ake tsaren lati. "Kai zo nan!" Ya kira daya daga cikin masu tsaron latin, "me yasa kake tsaron lati?" "Ni timekeeper ne, aikina na kula da lokaci, an saka ni tare su ne don sun makara." "Su kuma malaman fa?" Kallon Malam yayi yaron sannan ya sunkuyar da kanshi, a hankali ya saka yaron a gaba har office din principal, ya shiga malamai na take mishi baya. Jami'an tsaro na bayansu. Tsayawa yayi yana kallon Malamai da daliban! "Na ji kunya sosai da naga dalibai suna riga malamai zuwa makaranta, a yau naji matukar kunya yadda malamai suka mai da kansu makararu. Amma ba kome Matori daukar min sunan kowa zai ga sakamakonsa wadannan mutanen da na samu a dauki sunansu a farko sauran kuma su zo daga baya, a cikin gari kuke ba a kauye ba balle kuce abin hawa ne baku samu ba." Daga haka ya dauko daga inda yake tsaye ya nufi Yaran nan suke tsaye ya ce musu. "Za a saka muku kayan wasa kuma har da doki da ragon nan" suka yi ta murna. A hankali ya juya motar Deen ya gani aka bude mishi ya shiga. "Deen me ya maka mata nayi musu!" "Ba fada ba zagi ka ka fara nad'a kwamitin nad'a kwamishinonin kafin ka hukunta su!" " idan na yi haka meye zai biyo baya, wadanda ka samu a cikin makarantar a kara musu matsayi daga principal har headmaster a maida su kauye a barsu da matsayinsu, sannan ka nad'a jami'a na musamman suna kai musu ziyarar bazata." Har gidan ya kawo shi da zai fita ya ce mishi. "Unguwarsu Ummu dole sai ka nad'a kwamishinonin za a fuskanci unguwar!" "Na gode sosai Deen.!" "Ni ne da godiya!" Haka suka yi sallama Tafida ya shiga cikin gidan, ya samu Sa'adiyya tana cike dam, bai kulata ba ya wuce dakinshi yayi wanka ya fito masu taimaka mishi shiryawa suka taimaka mishi, yana gamawa ya nufi inda jakarshi yake ya dauka yana me fitowa, "Ka dawo baka karya ba. Kuma zaka fita!" "Na koshi." "Inda ka kwana ta baka abinci ne bayan dadirancin da kuka yi!" Kura mata idanu yayi kafin ya sake murmushi, ya fita daga ɓangaren. Deen yayi gaskiya da ya ce mishi. "Sa'adiyya ta dawo, kada ka ɗauka zasu kyale ka ne haka. Kayi kokarin ganin ka nisanta kanka da abincin gidanka idan ba Ummu ce zata dafa ba, nasan duk ranar da Ummu ta diro gidanka abincin da zaka ci na musamman ne!" Da wannan ya ke kin abincin gidansa ya gwammace yaci na gidan Deen ko na Ammah. Abin da Tafida ya fara yi, shine nad'a kwamitin zabar kwamishinonin, a cikin sati biyu aka kawo mishi shi kuma ya zabi wanda suka dace da shi ya turawa Deen ya gani, shi kuma ya kara mishi da Mahmoud. Ya turo mishi ta email yana gani ya kira shi. "wallahi ka kyauta min na manta da shi bakiɗaya!" "Kada ka damu ka godewa Allah da nake tare da kai, dan banza irinka bai cancanci kanwata Ummu ba!" "Na gode!" Sannan ya tura mutanen da ya zab'a zuwa ga majalisar dokokin jahar Borno, a zaman da tayi wata Laraba ta bukaci duk waɗanda aka tura sunansu Mahmoud bai sani ba, sai da Rayyan kaninsa yaji labarin ya kira shi baya gari ya gaya mishi. Ya sha mamaki domin a tuanninsa Tafida ya more shi yaki biyanshi, shi kuwa Deen yasan wannan abin yana damun Mahmoud, domin yana ganin kyashin Tafida da kishin Tafida akwayar idanun Mahmoud. Sannan Yaron Mahmoud Alguburo yana turawa Deen bayanai anan yake tsintar wasu abin, shi Tafida zuciyar shi daya bai san wainar da ake toyawa ba, haka yasa yake ta kome na shi. A lissafin Mahmoud ba haka yaso ba, damuwarshi a bashi SSG, amma ya kare a Kwamishina, a gefe guda kuwa Alhaji Ahmed Bamanga, tsohon ma'aikacin gwamnati ne ta rike matakai dayawa, Abba da kanshi ya tafi har gidan Mutumin ya roke shi ya taya tafida aiki. Kuma Ya amince babu wani tirjiya. Koda Abba ya bawa Deen sunan Alhaji Ahmed Bamanga, ya ce yayi bincike akanshi, wani ikon Allah sai ga bayanai na alkhairi akan shi haka yasa Deen ya bawa Tafida sunanshi aka.kuwa kira shi Majalisa aka rantsar da shi. Deen da Abba suna tare da Tafida aikin da suke yiwa Tafida ban da Allah babu wanda ya sani, haka yasa Abba yana gefe idanunshi yana kan danshi. Sannan ko lokacin da Tafida ya tura sunayen kwamishinonin wa Deen sai da ya turawa Abba shi kuma ya ce ya naziri da kyau Tafida ya manta da wani na musamman. A hankali ya fahimci Mahmoud aka mance. *Ummu*🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Ummu* Mamana ta tsaya min a raina, kawai karfin hali nake amma na kasa, Tina ta fahimci haka sai ta dauke ni muka tafi garin Mamanta Ibadan wayyo Allah na, Mutanen nan akwai mutumci da sanin ya kamata da Tinah take bawa Mamanta labarin abin da ya faru. Zuba min idanun tayi kafin ta ce min. "Kina son komawa gida ko baki so?" Idanuna ne suka cika da kwalla Tina ta ce mata. "Mamy ki barta mana." Murmushi tayi tana faɗin. "Yan arewa suna da kirki da akida, sannan basu yarda d'ansu ko yarsu ya nuna gazawarsu akan zamantakewar da suka daura su akai ba, musamman Mace ana son tayi hakuri da duk wani abu da zai faru da ita, ta kasance me juriya da tawakalli, ba laifi ba ne don ku kaucewa abin bai miki ba amma ki kara hakuri akan wanda kike yi ki zama jaruma!" Kusan wani abun mamaki Maman Tina musulma ce, asalin Malama ce a kungiyar Fowam, rikakkiyar Yar da'awa ce. Haka Kanin Tinah me suna Muhammad Musulmi ne kuma irin dan ahlil sunnah ne. Tayi min nasiha tare da nuna min sakamakon masu hakuri inda take bani labarin Baban Tinah da ita sunyi aure ne na zumunta, lokacin da ita da shi suna Kiristoci, zuwansu arewa a Kano suka hadu da mutanen kirki, daga nan mutumci da zumunci haka yasa ta musulunta duk da a familynsu akwai masu sallah amma su Babansu ya ware kanshi, tana musulunta kuwa Yan uwan Babansu wnada wasu su manyan malamai ne, suka bukaci Mijin ya musulunta shi kuma gidansu pastor ne Babanshi, ya ce ba zai sauka akan akan addinin iyayenshi ba, danginta kuwa suka ce ba zasu barta ta zauna da shi haramun ne a musulun, akwai wani kanin Babanta yana koyarwa a Madinah da kanshi yazo ya dauke ta, bayan sun rabu da mijinta cikin salama, ya kwashi yaranshi a lokacin bata san da cikin Muhammad ba, sai da suka tafi can ta fara laulayi, aka gayawa Babansu Tina ya ce eh nashine kuma ya amsa, idan ta haihu sai ta bashi Yaron ai kuwa Kanin Babanta ya ce babu wannan zancen. Haka ya cigaba da rayuwa har ta haihu sannan ta mai da hankali aka rayuwarta da na Yaronta, yan uwansa kuwa babu ranar da ba zata saka su cikin addu'a ba, haka yasa ba a rufe shekara biyu ba Yaran suka saka uban sai da ya nima musu hanyar da zasu na jin labarin Uwar. Na tausaya musu shi yasa Idan Tinah tana yin wani abu yadda ka san wacce Muslunci ya haifa ashe haka yana da nasaba da mahaifiyarta ce. Tunda muka zo sai na ware na zama kamar yar gida, domin Mamansu tana jin hausa, a yadda take gaya min ta zauna a kano, sannan kuma a Madina ta zauna da Hausawa haka yasa take jin Hausa sosai, sannan har kwana gobe Mijinta yana ranta, tana jiran ko zai dawo gare ta. Sai yanzu na kara fahimtar wani abu guda daya. Idan mace tana son Mijinta idanunta rufewa yake. Amma ni a bangarena ban san me nake ji akan Tafida ba, amma tabbas na ajiye lissafinsa. Mufidah da Mufid kuwa tsakanina da su nono, yaran gwanin ban sha'awa duk inda suka shiga sai an hado su da kyaututtukan kudi da kaya sabi. A hankali muka samu wata guda, nayi kyau nayi kiba. Muna aikin cake, sai ga Tinah ta shigo tana faɗin. "Ke Mijinki dai ya hana mutane sakat a Maiduguri." Kallonta nayi tare da son jin ba'asi. Mika min wayar tayi tana karanto min abin da ake faɗa. "Allah ya kyauta!" Na wuce zan koma kan aikina. "Ummu ko zaki koma ne?" Idanuna ne suka cika da kwalla. "Ba haka ba ne, kawai ban san me zan yi ba ne." Kawai na fashe da kuka. Zama tayi ta kalli masu aikin ta nuna musu hanya, fita suka yi ta ja kujeran ta zauna. "Yanzu ya dace ki huce, ina son ki koma ga Aliyu amma dole ki koyawa kanki yadda zaki kwaci kanki ko kin koma Maiduguri abu daya ne ki tsaya akan kalamanki, sannan idan kuma ba zaki koma ba duk daya ne a yanzu da baki gida nasan kina komawa tow ba shakka kowa zai mai da hankali ne akanki, don haka ki saka a ranki zaki iya tunkarar kowa akan ra'ayinki." Gyada kai nayi ina jin abin da take fada min, "ku gama cake muje wani wurin!" Gyada kai nayi, haka muka yi cake din da ita bayan mun gama, nayi wanka na bawa Yan biyu nono sannan muka bar gidan, shopping muka tafi don Yaran kan sai da ta jibga musu kaya kamar bata san darajarsu ba, nawa kuwa English wear ne, tayi ta zuba min. "Mijinki dan duniya ne, ina son mace mara kunya, ke kuma kina da kunya da addini shi yasa ba zaki iya abin da yake so ba." Hade rai nayi nace mata. "ina ruwana to!" "Hmm! Zaki sani ai!" Ya fada tana ciro wani night gown. "Wannan zai dace dake!" "Ke Tinah kada ki mai da ni yar iska!" " ina fa zan mai dake yar iska bayan wanda Tafida yayi!" Share ta nayi, muka gama sayayya har zamu tafi ta ja ni wani bangare gajerun wandona ne, haka ta diba min kamar na yan mata, haka sake kwasar kayan. "Na gaji!" Nace mata, "Ni kada ki dame ni da mita!" Haka muka bar shagon. Lokacin da muka dawo gida, ta zuba kayan a dakinta. Washi gari wani shagon yan Indonesiya muka je na Spa aka fara gyara min jiki, ita da kanta ta ce musu. Wata guda zan yi ana kawo ni domin jikina tayi kyau sannan su hada min har man shafawa. Haka kuwa ya faru kullum muna hanya. ** *Tafida" Wani kallon renin hankalin yake mata, yana zaune a tsakiyar gadonshi ya nutsu akan aikin da yake amma lokaci zuwa lokaci yana zame abin da yake yana kallon hotonshi da Ummu daren ranar suna. Banko kofar dakin aka yi ya zuba mata idanu kuru daga ita sai wani lalatacen rigar barci. A da can baya yafi kowa kwadayi da son jikinta, amma a yanzu tun ranar da ya fahimci bata da kamun kai, shi da ma ace hatsari aka samu aka mata fyade zai dauki haka a matsayin ƙaddara, duk da gyaran da aka mata amma shi ba dan iska ba ne, akan Ummu ya fahimci yadda mata suke, shi ya fara dandana zumarta haka yasa shi fahimtar wacece Sa'adi baby. "Ka bani hakkina, na gaji da kallonka da idanun idan kuma ba zaka bani hakkina ba wallahi zan kira Abba ya san me muke ciki!" Murmushi yayi ya ce mata. "idan na shiga ba zan gamsu ba ne, ke kofar garinki a bude take, ni kuma so nake na shiga inda xan ji a matse da kyar nake tura kaina." Wani ware idanu tayi tare da fashewa da kuka tana faɗin. "wallahi sai ka bani hakkina!" "Akan me zan baki hakkinki?" Ya tambaye ta yana murmushi. "Don Allah Tafida ka bani hakkina!" "Gaskiya ba zan wahalar da kaina ba na zo ke ki ji dadi ni na sha wuya!" Zubewa tayi tana kuka da rokonshi, amma yayi banza da ita. "Idan don Ummu kake wannan abin ka ji wallahi har abada ba zata tab'a dawowa, don haka ka shirya zama da ni!" Sauka yayi a gadon ya tako har inda take yana murmushi, kafin ya fisgota tare da d'agota suna kallon juna. "Me kuka yiwa Ummu!" "Ban sani na ka nimo da kanka!" Ta fada tana kuka, turata gadon yayi cikin gajiya da halinta ya ce mata. "Zaki gaya min ko sai na wulakanta ki?" "Haka da kake kana tsammanin zai baka damar ganin Ummu ne? Ai kai da ita har abada hakkina kuwa idan baka bani anan ba zaka bani a lahira!" Ta fada zata sauka a gadon ya fisgota, da karfin tsiya ya nimeta, tun tana kokarin kwatar kanta har ta kasa ta shiga zuba ihu da salati tana rokonshi, amma Tafida bai kyale ta ba sai da ya ga ta daina motsin kirki, bai taɓa jin b'acin rai irin na yau ba domin sai da ya girgiza Hq dinta yadda kafarta sai da ya gagara ɗaukarta. "Na baki daga nan zuwa awa ashirin da hudu ki fada min abin da kuka yiwa Ummu ko na baki mamaki!" Ita kan da take cikin tashin hankali gabanta kamar an watsa mata barkono, shi ma ban daki ya shiga yayi wanka yana ganin kazamtar da ya kwaso jikinta, wanka yayi ya wanke jikinshi da ruwan zafi, akwai wani abu da ya dauka yadda Ummu take amfani da gishiri a ruwan dumi ya sha ganinta idan ta shiga ban daki, ko idan sun shiga tare cikin dare bayan ya turmusheta, kuma yana yawan jin labarin gishiri yana kashe wasu ƙwayoyin cuta, don haka yayi amfani da shi wurin wanke jikinshi. _Haka da kake kana tsammani zai baka damar ganin Ummu ne?_ wadannan kalaman sun yi tasiri a ranshi da zuciyarsa bai san lokacin da yayi wankar a gurguje ya fita ba, yana zuwa ya samu bata dakin, bangarenta ya nufa, banko kofar yayi yana samu tana waya, kashe wayar tayi tana kallenshi, yadda ya zuba mata idanun ya bata tsoro. Rufe kofar yayi da key ya nufe ta yana faɗin. "Zaki gaya min inda kuka kai Ummu ko sai na aikaki lahira!" Ya shiga kokarin niman wani abu da zai shake ta, ganin haka ta runtuma ban daki a guje. Kafa ya saka mata, ta fadi ta fasa ihu ya take ta yana faɗin. "zaki gaya min ko sai na karya kafarki?" "Zan fada maka!" "Ina jinki! Ina kuka kai min matata da Yarana?" Wayarta da ta saka a handsfree daga can aka ce. "Sa'adiyya Lafiya?" "Abba zai kashe ni, don Allah ku kawo min a gaji!" "Tafida idan ka sake ka mata wani abu sai na baka mamaki domin sai na maka iyaka da Ummu har karshen rayuwarka, mace daya ka gaza riketa taya zaka rike mata biyu, Sa'adiyya ki yi hakuri Kaltuma tana zuwa!" Ajiyar zuciya ta sake tana kukan munafunci, kashe wayar yayi, a tunaninta zai kyale ta ne, ai kuwa ya hade kanta da jikin gadon ji kake. "Kummm!" Ya bar dakin ta fashe da kuka, washi gari kuwa Hajiya Kaltuma tazo, ta ganta ras sai ma yan iskar kawaye da suka cika gidan, ganin haka yasa ta kira Tafida da yake office, domin da ta kira Saadiyyah kin daukar wayar tayi sai da ta kira Abba ta gaya mishi ya kirata ya gaya mata ga Hajiya Kaltuma. Tana gaya mishi ya bar abin yi yazo gidan. Tana ganinshi ta mike tana da murmushi. "Babangida! Kai ne haka?" Murmushi yayi yana shafa kanshi. "Hajiyar Abba muje ina Innata?" "Ai baka da kirki tunda ka dawo nan ka barsu ita da yar uwanta zasu zo gobna has!" Dariya yayi ya mata jagora har bangaren shi waya yayi aka fara kawo mata abinci da abin sha, kafin wani lokaci gabanta ya cika da abinci . "Ina zan kai abinci haka? Allah ya yi albarka " ruwa ta sha tana kallonshi yadda ya faɗa. "Tafida!" Kallonta yayi kafin ya sunkuyar da kai. "Ka daina saurin hasala idan Sa'adiyya tana maka abu ka koyawa kanka hakuri." "Hajiya tasan kome akan Ummu, Hajiya sune!" "Duk mun sani Ummu tana nan, amma kayi hakuri." "Hajiya Ya zanyi? Ummu taki ta bayyana kanta ita kuma wancan yar iskar yarinyar tana sane!" "Kana son Ummu ne!" Numfashi ya sauke a hankali yana dafe kanshi. "Allah yana sane da kai!" Jinjina kai yayi, "Kasan Hajiya Turai?" Gyada kai yayi yana kallonta. Rasa yadda zata mishi magana tayi kafin ta ce mishi. "Kasan yar rikon Inna ce, tayi aure a Yola." "Eh Hajiya na sani amma na manta saboda bata zuwa akai akai." "Alhaji bai kiraka bane?" "A'a!" "Ya Aisha Fa?" Girgiza kai yayi ya kagu ya ji me zata ce, "Tow Allah ya kyauta ka tafi wurin Ya Aisha zata gaya maka meke faruwa!" "Hajiya gaya min me ya faru Ummu ne wani abu ya same ta!" Yadda ta birkice da tambayoyi yasa ta fahimtar, Tafida yana ganiyar kaunar Ummu! "Aure zaka yi!" Zubur ya mike yana me girgiza mata kai. "Akan me? Nace muku ina sha'awar wata mace ce? Ni Ummu nake bukata a rayuwata idan babu ita zan ajiye kome na tafi niman Matata!" " zauna Tafida! Shima Alhaji babu yadda ya iya ne, da yana da yadda zai yi ba zai amsa ba, ta baka auren Yarta son zo tare." "A ce mata ni Aliyu Muhammad Jadda Bana son Yarta ni matata ta wadace ni ko Saadiyyah jiran dawowar Ummu nake amma bata bukatar zama da ni! Hajiya ki gaya musu ni Tafida bana bukatar yarinyarta." Yadda Tafida ya gigice zaka ɗauka mutuwa aka kawo mishi. Amma ina ita kanta Hajiya Kaltuma bata da yadda ta iya haka ta bar gidan, Deen ya kira yana gaya mishi abin da yake faruwa. Yazo maza su tafi gidan Abba domin al'amarin ya wuce lissafinsa. *Mama* Zubawa Mudan idanun tayi ta rasa me zata ce mishi, dakyar ta dauki wayarta ta kira Baba Bulama. "Alhaji don Allah ka zo gida ka ji...... (Kuyi hakuri Maybe na kara muku wani update din yanxu ina busy ne...)🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Mudan Duk sai yaji kunyar duniya ta rufe shi. Har zuwa lokacin da Baba Bulama ya iso, kan Mudan a sunkuye yake bai d'ago ba saboda tsabar kunya da jin ina kasa zata bude ya shige cikinsa. Bai tab'a danasani irin yau ba, "Mudansiru me ya faru?" Baba Bulama ya tambaye shi. Kamar wanda yayi sata muryan shi yana rawa ya ce mishi. "Ni ne na dauki Aunty Baby daga nan na kaita Bauchi." "Kasan inda take a Bauchi ne?" Cikin rawan murya da rudewa. "Wurin motar lagos ta tafi bata yarda na kaita ba yadda aka yi na sani bin bayan napep din da ta shiga nayi na gano inda ta nufa." Cikin rikicewa Mama ta ce. "Ban gane ba?" "Ba a Bauchi ta tsaya ba babbar motar nan ta shiga zuwa lagos!" Wani irin zufa ne ya shiga karyo mata daga ko ina na jikinta rawa yake. A hankali ta fashe da kuka don ita ta jefa Ummu a wannan yanayin, "Alhaji ni ne na cillata cikin wannan yanayin, ta gaya min na fuskance ta amma naki, na dage gidanta zata koma!" "Kiyi hakuri zan saka a cigaba da saukar qura'ani Allah zai dawo mana da ita. Allah ya kyauta jeka ka ji!" Haka ya mike yana ta basu hakuri suna nuna mishi babu kome, bayan ya tashi Mama ya cigaba da kuka domin zuwa yanzu yan unguwa sun fahimci Ummu ta b'ata, haka ma Umma sai magana take yada mata a wasa. *** *Tafida!* A parlour Abba suka hadu bakidaya, tunda ya shiga cikin gidan Deen sai tausarshi yake da kalmai amma ya kasa nutsuwa, a tsakar gida suka hadu da Hajiya Turai. Ta ci sunanta Turai domin fara ce tas kamar baturiya, tare da wata baturiyar Yarta, ga kyau kamar tayi kanta abin ya haduwa yarinyar biyu Ubanta Fulanin Yola ne kuma fari Uwarta shuwa ce, abin ya mata yawa wai shege da hauka. Tsabar kanshi yayi zafi bai ma ganta, parlourn Abba ya fada kamar an wurgo shi, a tsakiyar dakin yayi musu sallama. "Abba na ji sakonka!" Jan shi Deen yayi ya zauna. "Baka da kai ne?" "Ina take da kai ta shigowa mutane kai sannan tayi sallama,wannan hali naki Tafida bai da kyau ki daina wannan abin bai dace ba!" Hajja Ganaah yayi idanu. "Inna ki ce ta daina mai da ni na mace!" "Idan naki fa? Kin zo kina mana ihu!" Shiru yayi yana jin takaici, shigowar Turai da yarta Asiya yasa shi kallonsu. "Ashe Tafida ne haka ko gaisuwa babu!" Banza yayi da ita, shi yake abinshi Deen ne da jin kunya. "Ki zauna!" Zama duk aka yi sannan aka gaisa da juna, kafin Abba ya bukaci ta maimaita abin da yazo da shi, nan kuwa ta faɗa. Kallon Abba Tafida yayi ya juya kanshi yana kallon Yarinyar ya ce mata. "Kanwata, ina da matar nake jira, kada ki fada dayawa, domin ni inuwar giginya ne. Wacce nake jira ita ɗaya ce zata sha dadin inuwata. Daga kanta na gama aure ki je ki auri wanda yake sonki ni tawa ta ishe ni!" "Tafida!" Deen ya rike shi, "Ba karya da gaske bana sonta ne, babu macen da nake muradi da son zama da ita sama da Ummu, ko na aureta ba adalci xan mata ba." Daga haka ya mike zai fita, "Har yau baka cancanci zama da Ummu ba, domin baka san darajar Ummu ba, kana niman Ummu ne don bukatar kanka." A matuƙar gajiye ya juya ga Abba da yake wannan maganar ya koma gabanshi. "Abba ka bani dama ta biyu, ka bani dama na gyara zamana da Ummu!" "Idan na baka dama ita ta ce bata bukatar zama da kai fa?" Lumshe idanu yayi ya bude, gwiwar shi a ƙasa. " zan amshi ƙaddarata a duk yadda ta zo min, zan rungume ta hannu bibiyu sannan zan zama Adali akan kaina da ita din." Tsakanin d'a da mahaifi sai Allah, Tafida ya narkawa da Abba zuciya, "ka je Allah ya bayyanata!" Tashi yayi zai fita Hajiya Turai ta ce mishi. "Asiya yar uwarka ce, idan da hali ka bata aiki mana!" Bai bata amsa ba ya bar parlour. "Ya jadda baka ce kome ba!" "Turai kina ji ya ce Matarshi yake so, shi yasa nace miki ni ba zan kuma saka Tafida ya kara aure ba domin na sha ciwon kai akan Ummu, yanzu kuwa ban isa ba" kamar tayi kuka ta ce mishi.."Ko bai aureta ba ai Kanwarshi ce zata zauna a wurinshi." Haka aka bar zancen Baba Bulama ya kira suka kara tattauna akan batun Ummu. Sannan ya kashe wayar ya cewa Inna. "Maganar yarinyar nan ne, ana ta samun haske akanta!" "Allah ya bayyana wannan yaron yana ganin rayuwa waye ya sani ko matar saleh ne ta tura shi ya bi duniya." "Allah ya kyauta!" "Amin Ya Allah!" -- A kofar gidansu ya nime faduwa sai da Deen ya rungume shi. "Kai ni gidan Hajiya!" "Tow!" Haka ya wuce da shi. "Na kira Doctor ne?" "Bar shi kawai!" Haka ya wuce ga shi gidan Hajiya, security sun cika unguwar, Deen yana rike da shi har parlour Hajiya. Kwanciya yayi yana haki, "Babana ya dai?" "Hajiya wai auren wata yarinya aka bashi " "Asiya ko?" "Eh!" "Na gaya mata ta fara nimanshi ya ga yarinyar ni ba zan mishi dole ba." "Eh ya gaya musu gaskiya baya sonta!" "Alhamdulillahi! Tunda ya gaya musu! Tow shine ya koma haka?' "muna fitowa ne ya nemi faduwa a kasa." Murmushi tayi tana faɗin. "Allah ya baka lafiya kai Deen Allah ya baka ladan aikinka." D'ago kai Tafida yai yana faɗin. "Hajiya ni fa?" "Allah ya baka lafiya mana ai baka da lafiya ne!" "She Deen din me yayi da sai an mishi addu'ar lada!" "Tow dan hassada ashe kuma ba ciwo kake ba. Tashi ka zauna ka hana Allah bani ladan da ake min fatan samu, kai dai Tafida bakinciki ka dayawa yake yanxu don Allah ladan kake wa mita har da tashi zaune!" Ita kan Hajiya tana kallonsu fadar nasu gwanin ban sha'awa. Komawa yayi ya kwanta dole Deen ya kira Deen Sagir yazo ya duba shi, sosai yayi mamakin yadda jininshi ya haura. "Yallabai meke damunka haka?" "Kanwarka ta gudu ta bar gari, gaya min idan jini na bai haura ba ina zan cusa kaina." Girgiza kai Sagir yayi yana faɗin. "Allah ya baka hakuri ya daidaita tsakaninku!" Lumshe idanun yayi yana faɗin. "Amin Ya Allah! Ubangiji ka raba ni da yan sa'ido, masu farin ciki da halin da na shiga!" "Wallahi ba Amin ba!" Deen ya fada yana dariya. Haka suka yi ta drama har Sagir ya tafi. A gidan Hajiya Tafida ya rage dare dake Doctor Sagir ya bashi magani har da na barci, sannan Deen ya rako shi gida, har cikin gidan ya rako shi. Washi gari. Bai fita office ba domin jikin ya matsa mishi, Saadiyyah tana can bangarenta bata san bai da lafiya ba, haka Deen da Sagir suke ta shige sai yamma da su Abba suka zo aka san halin da yake ciki, a lokacin ta fito zata je mishi tijara ta ga motar gida, a tunaninta Ummu ce ta dawo hankalinta a tashe ta nufi bangarenshi. A parlour ta samu yana kwance da karin ruwa a hannunshi. "Dama baka da lafiya ne?" Bude idanun yayi ya kalleta, hankalinta kwance sai kiba take. "Taya kuna gida ɗaya Sa'adiyya ace Mijinki bai da lafiya baki sani ba?" Kame-kame ta fara tana zare idanu. "ban gaya mata ba ne!" Mikawa Deen kunun da Hajiya ta dama mishi tayi. "Sannu da kokari Hajiya!" "Yawwa kafin ruwan ya kare yayi daidai shan shi ba." "Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana!" "Amin Ya Allah!" Wayar shi da yake hannun Deen ya karba yana faɗin. "Deen bani na gwada kiran Tinah kona abuja! Haka kawai nake jin like Tina tana tare da Ummu." "Wacece ita?" Hajiya ta tambaye shi da sauri don a wannan yanayin bata ki ta ga Ummu ba, ta roke ta ta zauna da danta idan ma ta kama har kwanciya tayi. "Kanwarshi ce tazo bikinshi ma." Kiran layin Tinah yayi ya saka a kunne. "Titina!" "Yes Aliyos ya kwana dayawa!" "Sai godiya!" "Teeminatina! Alfarma nake nima a wurinki" "Tafida ina jinka!" "Idan Ummu tana tare da ke ki ce mata tayi hakuri ta kawo min Yarana mu gana ina kyautata zaton rayuwata ya zo karshe!" "Ban gane ba!" Kwarewa yayi Deen ya kwace wayar yana faɗin. " idan tana tare da ke ki ce mata ta dawo kowa ya damu da halin da take ciki. Please." Kiran Doctor Sagir akayi domin tari yake tayi kamar zai mutu, haka Sagir yazo da kayan aiki aka saka mishi abin numfashi, Hankalin Hajiya yayi mugun tashi. Karshe dai asibitin da yake cikin gidan gwamnati aka wuce da shi, ba iya Doctor Sagir ba har da wasu likitocin suka zo daga babban Asibiti tare da Kwamishinan lafiya da aka nad'a. Duk suka rufa akanshi, Maryam da Rukayya sun tawo, hankalinsu a tashe har yayunsa maza. "Yaya Jadda kayi wani abu!" Deen ya kalli Abba cikin kwantar da hankali ya ce mishi. "Zan tafi da wayarshi zuwa gobe da yamma zan shigo inda in sha Allah akwai wani ganawa da zan yi da wasu turawa idan na sake na rasa ganawar yau Tafida zai rasa wani babban abu ne bana son a rasa abin." "Tow! Allah ya baku sa'a!" Inji Abba, babu wnada ya iya mishi magana har ya bar gidan, kiran Layin Tinah yayi tana dauka ya ce mata. "Kina ina ne a abuja?" "Look ban san inda Ummu take ba!" Shashekar kuka yaji yayi yar dariyar takaici ya ce mata. "Bata wayar!" "Nace maka!" "Bata wayar nace!" Ya daka mata tsawa, "ok!" "Ummu!" Kukanta kawai ya ji ya ce mata. "Kina ina ne?" "Ibadan!" "Ok ki shirya kome dare xan kira Aliyu Tafida yana cikin wani irin yanayi bamu sani ba zai tashi ko zai mutu, ba zan ce ki dawo gare shi ba amma ki kawo mishi yaranshi." "Kazo ka ɗauke mu! Ka ji don Allah ka zo ka kai ni wurin Mamana!" "Good girl gani Safiyyudeen nan tafe!" Ya kashe wayar a lokacin yayi booking flight to abuja, karfe shida suka bar Maiduguri. Wurin goma yana zaune a airport din sai lokacin ya samu jirgin Ibadan. "Ummu* Tunda tafida ya kira yana tari domin ni ce na dauka, ta bar wayar a dakin yana kira ni kuma na dauka, da sauri na fito waje na mika mata wayar nayi na ji tana kiran sunanshi, sai na kasa tafiya. Sakawa da Handsfree tana magana da shi, ban san lokacin da na kura mata idanun ba. Da farko na zata drama ce sai da naji Deen ya amsa yana mata magiyar idan muna tare ban san lokacin da na fashe da kuka ba. Domin ba karamin tashin hankali na shiga ba da yace na kawo mishi Yaranshi. Kuka nake ina jin a raina ban mishi adalci ba, da ni yake rigima ba da Yaranshi ba. Na saka yaran a rigimarmu! Haka na shiga haɗa kayanmu. Tana taya ni murmushi take tana faɗin. "Zaki koma ne?" Girgiza kai nayi na ce mata. "Yaranshi suna da hakkin ganinshi!" "Good amma dole ki koma ga Tafida kina buƙatarshi yana bukatarki." Shiru na mata, har na gama a ranar nayi sallama da mutanen gidan, wurin karfe daya Deen ya kira ya ce ya iso yana airport zai jira mu. A daren muka isa airport din, ta rike hannuna "Please ki nutsu ki yanke hukuncin da ya dace dake, kina buƙatar nutsuwa sosai, amma the best solution ki koma ga Tafida. Akwai abin da sai kin koma zaki kara ganewa." Hawaye ne yake zuba min nayi ta mata godiya. Muna isa Deen ya iso yana hararanta. "Kina da hankali zaki rike matar mutane? Sai na mare ki!" Ya nuna mata yatsa. "Shi mijin da gaske ya shirya zama da ita ne?" Kamar ya mangare ta ya kalleta. "Ka ce yayi hakuri kada ya mutu ga kayarsa nan dama tashi ce." Kaina a sunkuye ya ce min. "kin kyauta da kika tsallake har nan, idan gudun hijiran zaki yi me zai saka ki zo nan ga gidana." Ya fada da Yaren Babura, "Kayi hakuri!" Na fada, amsar kayan yayi ya mana booking jirgin kano, a daren muka wuce cike da kewar juna. Karfe uku na asuba muka sauka kano. Karfe shida bayan sallah asuba jirgin yan kasuwa da suka zo jiya yau zasu koma da safe, muka isa karfe takwas ya mana a gidanmu. Mama tana zaune akan abin sallah, ta ji ihun yara suka faɗin. "Oyoyo Aunty Baby!" Sai naji kunyar yadda na gudu ya kama ni, dakin Baba Bulama na shiga na zube a kan gwiwata, na fashe da kuka. "Alhamdulillahi Barka da zuwa Ummu Hadiyya, Allah ya miki albarka kin zo lokacin da ya dace, kai kuma Deen Allah ya tsarkake lahiranka da duniyarka!" "Amin Ya Allah! Zan tafi Baba don Allah kada ku gaya musu ni na dawo da ita." "Ummu Hadiyya!" Juyawa nayi ina kallon Mama da Ummi. "Allah ya shirya ki ke da zuri'arki, me yasa zaki tafi ba zaki min yadda xan gane ba?" Kuka nake itama tana share kwalla. Deen ya mana sallama ya tafi aka bar nida su Mama, can Mam Amina tazo bata san me ke faruwa ba, saboda bata gari tayi tafiya tsawon wata biyu. Tana jin haka ta shigo ya cewa Mama. "Tunda Allah ya nufa an dawo da ita, tow maganar kome babu shi, ta fahimci kanta da rayuwarta garin gudun b'acin suna ki rasa yarki!" "In sha Allah!" Basu rufe baki ba, Rukayya da Sa'adiyya suka shigo. "Maman Ummu Hadiyya ko?" Mama ta gyara tsayuwarta da kyau. "Tow ki gayawa yarki da ta tafi yawon karuwanci kada ta sake ta dawo rayuwar mijina idan ba haka ba sai na wulakanta rayuwarta kare sai yafi ta daraja!" Fitowa nayi na kalleta kafin na ce mata. "Karuwanci ba tambarin gidanmu ba ne, tunda ban bi na miji har gidan aurenshi ba. Kuma ki tambayi Tafida da kyau ba yar iska ya aura ba domin a bai kai ni asibiti gwajin a duba lafiyata ba, idan don Tafida ne ki je na bar miki shi ki kwad'a shi ki ci." "Kika fadi haka Ummu har kina da bakin fadar haka!" Inji rukayya. "Ina ganin girmanki saboda dan uwanki, ki fita mana a gida kafin na saka a muku a tule!" Ummun da suka sani ba ni ba ce rashin mutunci nayi musu suka fita da kunya, sannan na zauna na cigaba da kukana, "Ita yar uwanshi ce, ba zan taba samun nutsuwa a cikin gidan ba domin basu kaunata." "Bama zaki koma ba su je can su ci kansu!" Ɓangaren Mama na wuce na karya sannan aka yiwa Yara wanka, na kwanta sai barci. Can wurin karfe daya naji tana faɗin. "Mun gode, amma Hajiya kiyi hakuri ba zan bada yarinyata ga Tafida ba domin dazun Rukayya da Matarsa sun zo nan suka ci Mutuncinmu, nima ina son abata na bar halas don kunya ne amma yanzu ko shekara dubu zata yi babu miji zai fi min kwanciyar hankali na ganta haka da ace tana can babu kwanciyar hankali.....🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Duk da abin da Tafida yayi min, sai naji sam Mama bata kyautawa Hajiya ba, ina jin yadda Hajiya take kara kaskantar da kanta wannan matar akan Tafida tana ganin jarabawa. Ban gama tsinkewa da Lamarin Mama ba sai da naji tana faɗin. "Hajiya idan Matarsa bata da hankali, rukayya sai ta biye mata su zo taiwa Ummu Hadiyya tijara? Na zata duk wani kiyayya zai kare tunda ga zuriar a tsakaninsu amma abin kamar wanda bana sonshi." "Kiyi hakuri Maman Ummu na sani anyi laifi, amma a kara hakuri haka ba zai sake faruwa ba." "A'a Hajiya na san duk abin da ya faru ki fahimci halin da Ummu take ciki, shi da ke da Mahaifinsa kuna buƙatar Ummu, yan uwansa basu bukatar Ummu idan da yau Tafida da Yan uwansa suna da bukatar Ummu tow da na gani a kasa, shi a cire shi ya shiga damuwa rashin Ummu amma saboda kiyayya irinta dangin miji babu wanda ya zo da sunan ganin yaranshi, idan na fahimta ba Ummu ne basu bukata Tafidar ne baya gabansu sannan Ummu ta haifa masa Yara abin da yake musu zai koma kan Yaran Ummu!" D'ago kai Hajiya tayi cike da mamaki taya Maman Ummu ta hararo abin da take tunani. "Hajiya abin da na faɗa gaskiya ne, kiyi hakuri idan ya samu lafiya ya sawwake mata kowa ya huta su rike nasu dan uwan ni zan rike nawa Yar, aure ne mun fasa an janye." Hajiya cikin sanyin murya tace mata. "Maman Ummu kin san dan yau ka haife shi baka haifi halinsa ba!" "Haka ne Hajiya amma kiyi hakuri ni tun ranar da Ummu ta bar gidan nan na fita a sawun iyayen da suke tursasa Yaransu, a yanzu ina tsaye ne akan Y'ata, Hajiya ni ina da sauki akan Ummu saboda ba ita ɗaya na haifa ba, idan Mahaifinta yasan da haka ni ban san me zance muku ba, kuyi hakuri ya sawwake mata ai tayi kukan zama da shi a cikin ukubar rayuwa yanxu da ya zama wajibi ta raba da shi ai tayi. A da can ban sani ba, a yanzu da na sani ina sonta ina gudun kada wata rana a kawo min gawarta. Hakuri da muke basu ba wai tsoron kada su rasa auren ba ne a'a muka koya musu ne suyi hakuri akan Yaransu. Idan har muka cire amsar bukatarsu da kukansu wata rana gawarsu za a kawo mana, don Allah ki fahimce ni, ina son na tsaya mata ne a matsayina na Uwar Yar mace." "Maman Ummu na fahimce ki, ita Ummun xan iya ganinta!" "Tana cikin dakin!" Mama ta mike ta bata hanya, shigowa Hajiya tayi, ya zauna tana murmushin yake. Ina tsaye na kasa motsi bakina rawa yake. "Zauna Ummu!" Zama nayi kaina a sunkuye. "Suna barci ko?" "Eh Hajiyata!" "Kiyi hakuri na san Mamanki ta dauka da zafi, amma kiyi hakuri Tafida ya sauya dayawa mafi girman sauyawar da ban tab'a gani ba. Nasan an yi miki kuskure amma ni nazo bada hakuri ne, tun da na ganki nasan yanzu bani da aufi ko mutuwa nayi Tafida yana da wacce zata tsaya mishi zata kuma mishi addu'a, ban kara yarda ba sai da na zauna dake sai naga ashe duk addu'ar da nake Allah ya jima da amsa min su, Ummu Hadiyya haka kawai nake miki kallon wacce ta amshi tarbiyyar Tafida saboda hakurin da kika yi na zama da shi a wannan baudadden halin nashi, kuma kika boye kome nashi baki tab'a gayawa wani ga halin da kike ciki ba, kawai don ki rufa mishi asiri, wannan kin fi karfin na kiraki matar Tafida sai dai Magajiyata. Domin kiyi abubuwa da bakina ba zai iya furta su ba, Ummu Hadiyya ina me kara baki hakuri zan ta zuwa kullum domin bikonki don ina son ki kasance da Tafida har zuwa lokacin da Allah ya diba muku. Amma maganar saki Mamanki tayi hakuri ba zan iya goyan bayan Tafida ya sake ki ba, da na ga saki a tsakaninku gara a wayi gari bana raye!" Da wani irin sauri na d'ago kai ina kallon Hajiya wacce murmushi ke kwance akan fuskarta. "Mahaifiyarki tana da gaskiya da mutunci da wata ne ba zata kula ni ba kuma ba zata bari na ganki ba, amma ta bari na ganku. Ki yi hakuri ki kuma saka a ranki kece hasken gidan Tafida." Duk sai na rikice na rasa me zance mata, Hajiya ta saye ni da kalamanta wanda nake jin kamar wani abu yana zaburana nace mata zan bita, amma ba zan iya watsawa Mama kasa a idanuna ba, bayan gudun da nayi yanxu aji nace xan koma gidan Tafida. Mama sai ta hallaka ni da duka kawai gara na hakura naga lokacin da Mama ta diba min ni yanxu wani shakkar Mama nake ji. "zan tafi Ummu idan kin samu lokaci ki zo ki ganshi!" Hadiye yawu nayi a raina nace. *Cab Hajiya zaki saka Mama tayi min dukar sakwaran shege.* motsi Mufidah tayi ta kalle ni, dauko yarinyar nayi na mika mata, ta rungume tana faɗin. "Fuskarta kamar na Tafida yana Yaro, gashi nan ya girma ya zama.gwamna!" Ni dai ban ce kome ba, a hankali ta mika min ita tana min alama na kwantar da ita. Haka kuwa nayi, aikuwa ta koma barci ta ce. "Ba farkawa tayi bakiɗaya ba, ba kuma nono take so ba ta farka ne taji kina kusa da ita ne!" Gyada kai nayi. Haka ta fito Mama tana wurin kwashe abinci. "Hajiya gashi na zuba miki, zaki tafi?" "A'a Maman Ummu ai tunda naga kawata da mijina naji na koshi, bari na tafi. Na gode!" "Tow a kasa miki a kaiws mutanen asibitin mana!" Fadadda murmushi tayi tana faɗin. "Ba zan ki amsa ba, nasan zai ci idan yaji daga gare ki ne!" Fita Mama tayi ta shiga dakin yan mata ta dauko babban kula me kyau ta zuba abinci, ta saka farfesu a kananun kulolin, sannan ta mika min muka fita, "Ummu na gode sosai!" "Hajiya ba kome, ki gaishe shi da jiki Allah ya d'aga kafadarshi. Kada ya manta al'umma suna jiranshi." Na fada mata a hankali, bayan ta shiga motar ta ce min. "Ke fa?" Damke hannayena nayi ina kallon kasa. "Na fahimce ki Ummu ba zan so ki sabawa iyayenki ba, amma Tafida yana nan yana jiranki!" Shiru nayi ban iya bata amsa ba, har suka bar unguwarmu da ake ta aikin gyara ungwar, cikin gida na dawo jikina a mace, kallo daya Mama tayi min ta dauke kai na wuce daki, ina cire hijab ya banko dakin. "Ina jin kalaman da Mahaifiyarshi tayi amfani da shi wurin rarrashinki, wai ke don Ubanki ba guduwa kika yi ba don nace ki koma? Meye kike nufi da ni da zaki fara tafiya kamar kazar da kwai ya fashe mata?" Cikin tsoro da tashin hankali na ce mata. "Allah Mama ni ban yi wani abu, kuma ban ce mata zan koma ba na rantse da Allah!" "Ke Ummu zan ci abu kazan kazan Ubanki, kada ki ga kin yi min abu ban tanka miki ba zanci Ubanki na rantse da Allah, na ji labarin kin bukaci zuwa ganin Tafida sai na taka wuyarki idan Yaranshi ne suzo su ɗauki kayansu. Yar banza mara kunya da baki son zama da shi hatta ni na sani da kalamanki da motsinki, amma yanzu da kika ji labarin zai mutu har kin bayyana saboda kin mai da ni yar iska na ga shegen da zai fitar min dake zuwa gidan Tafida zai na ci mutuncinku, ita ai Uwace akan me zata bar yaranta suna juyata an gaya miki ni zan ɗauki wannnan iskanci ne ta kuma zuwa wallahi sai na tura can kauyen Ubanki ki zauna a can naga dan iskar da ya isa dawo dake. Ko ance miki ban san me nake yi ba ne, tow ya isa haka ki kame kanki ko naci ubanki!" Tunda naji haka na rufawa kaina asiri, na nutsu ban san kuma me zance mata ba, na dai san tunda tayi haka tow ba makawa akwai wata a kasa. Abinci Uwani ta kawo min na fara ci, ta ce min. "Ki nutsu ki fahimci Mama, tunda kika bar gidan nan ta sauya daga yadda kika santa, a yanzu zata yi fadar nan ne domin darajarki idan ta kama ma auren ya mutu kada ki ce mata kome, tasan me take yi, kuma zata tsaya miki in sha Allah ita tayi alqawarin haka!" Haka yasa nayi bala'in nutsuwa tsoron Mama ya kara lullube ni. Kayan da nazo da shi na ja na fara budewa ga akwatin da Tinah tayi min tsaraba, budewa nayi na fara ciro kayan Mama ta shigo tana kallon Abincin.."Me ya hana ki cin abincin?" "Mama da zafi ne idan ya huce xan ci." Na fada ina cire kayan ciki ina ware tsarabarsu Mama. "Wai ma tukun gidan Uban waye kika je?" "Mama ina Ibadan wurin Tinah kawata din nan na abuja!" Ajiyar zuciya ta sauke, tana faɗin. "Kada ki kara min irin wannan abin da kika yi duk inda kika san zaki je ki gaya min na baki shawara!" Kallonta nayi kafin nace mata. "A lokacin kin ki saurarona ne!" "A yanzu xan saurare ki gaya min me wancan dan banza yayi miki?" "Mama ya wuce fa!" "Ai ba zaki gaya min ba!" "Idan na gaya miki zaki cigaba da tsanarshi ko don albarkacin su Mufid a kyale shi haka." Harara ta watsa min tana faɗin. "Allah ya kyauta!" Sai da na cire mata nata kason da turaren Baba Bulama, sannan na ware na mutanen gidan, wayarta da take gefen gado ta fara ƙara. Dauka nayi na bata ta saka a kunne. "Alhaji lafiya!" "Lafiya lau gani nan zuwa da Alhaji Kabiru." "Tow shi kenan!" Ajiye wayar tayi ta gaya min Babana yana zuwa. "Mama shima yayi fushi ko?" "Uwaki ban sani ba;" ta wuce waje kafin wani lokaci an kia abinci da ruwa da kome ni kuma nayiwa su Mufid wanka na shirya su, sannan na watsa tare da alola na fito na saka kaya na tadda sallah, a lokacin suka iso, Shigowa dakin Mama tayi ta dauki Yaran ta kai musu, ina idar da sallah tana kara shigowa. "Ki je can ki same shi, kuma wallahi kika sake kika bani kunya sai na zaune ki, domin na lura shi ta alakarsu yake da Uban Tafida ni kuma kece a gabana." Gyada kai nayi tare da barin dakin, koda na nufi parlour gabana ne yayi ta faduwa na rasa me ke min dadi, tsoro da fargaba yasa na kasa shiga, "eh tsayuwar me kike yi?" Inji Ummi da ta zo zata wuce. Taima tana bayanta. "Shiga" ta daka min tsawa, da sauri na shiga da sallama. "Ke kuma ki wuce wurin Maman Ummu gani nan zuwa." Ta wuce bangarenta, ni tunda na shiga da sallama na zube a gaban Babana. Murmushi yayi yana faɗin. "Bulama Yarka tana tsoron karya!" "A dai yi hakuri Alhaji!" "Tow Allah ya zauna da su lafiya, kiyi hakuri kowa hakuri ake akan zaman auren nan, yaushe zaki koma?" "Baba kayi hakuri ba zan koma ba don Allah!" Yadda nayi maganar yasa shi murmushi ya ce min."tow ba damuwa Allah ya yi albarka." Amin nace a raina, sannan ya min nasiha sosai kafin ya sallame ni, murmushi yayi ya cewa Baba Bulama. "Me kake ganin akan wannan lamarin?" "Alhaji a bar yarinyar tayi ra'ayin kanta, idan har yadda nake ji ne akan zamansu tow Ummu tana buƙatar nutsuwa sosai, Alhaji Muhammad Jadda mutanen kirki ne, amma iyalinsa basu da kirki don Allah kada aminta da alaƙarku yasa ka tauye mata hakkinta ka barta ita da mahaifiyarta su yi wannan yakin!" Haka Babana ya mishi sallama akan ya bar mishi wuka da nama,.kome ya taso a gaya mishi. *** *TAFIDA* Lokacin da Hajiya ta dawo an cika a dakin yana jingine da bango Deen yana rike mishi da bowl na fruit. Ta shigo dakin tana me kallon rukayya, wuce su tayi sai da ta ajiye basket din ta nufi Rukayya ta kifa mata mari, sai da dakin ya dauka. Sannan ta kara kifa mata mari. "Tashi ki bar gidan nan ko na miki baki ki lalace!" Tashi tayi jikinta yana rawa, zata fita ta ce mata. "Hajiya me nayi don Allah?" "Zaki fito ko sai na hada ki da Allah!" Da sauri ta fita ta juya ga Sa'adiyya. "Ba ni na auro ki ba, amma ki saka kafarki ki koma wurin uwarki domin idan na ganki a cikin gidan nan sai ya sake ki har uku gara ya zauna babu mace da ya cigaba da zama dake!" Da sauri Sa'adiyya ta fita babu wanda ya ce mata cikanki. Abincin da ta zo da shi ta buɗe. "Hajiya kin je gidansu Ummu ne?" Murmushi tayi tana faɗin. "eh Safiyyudeen!" "Yau kan zanci abincin Mamanta!" "Ummu ta dawo ne?" "Eh ta dawo Tafida!" Murmushi yayi yana faɗin. "Shi ne baku gaya min ba!" "Tow ba gashi ka sani ba!" Abinci Hajiya ta zuba musu Maryam ta ce mata. "Hajiya akan me zaku mari Rukayya sannan ki kori Sa'adiyya?". Duk suka zuba mata idanu. "basu da hankali ne!" "Akan Ummu kenan don sun gaya min sun je gidan!" Zuba mata idanun Hajiya tayi tana mamakin yadda take shirin bin bayansu Rukayya. "Eh wani abu ne?" "Amma Hajiya yarinyar da ta gudu bata son zama da shi ne ake wannan hukuncin." "Eh saboda ita ne, da yau kun saka Tafida akan hanyan kun kaunaci Tafida Ummu ba zata yi tunanin barin shi ba, amma daga ke har rukayya kun mai da min Yaro saniyar tatsarku bukatar ranku yake kawo shi ga Tafida. Babu ruwanku da Yaranshi me yake ciki kawai kun samu wanda ya dauke muku bukatarku, shi kuma nashi bukatar ko oho, maza fita ki bisu Allah yana gani ban tab'a kin ku ba, amma akan Tafida sai inda karfina ya kare, ita Ummu zata dawo gare shi ko kuwa bana raye zata tallafe shi kamar yadda ta saba. Ku kuma ku je Allah ya kyauta!" Domin Mama ta gaya mata magana da yasa take jin ba zata iya kara barin Tafida ya rasa Ummu ba, koda kuwa haka zai zama ajalinta, ana cikin wannan yanayin Deen ya shigo, suka gaisa ya zauna yana korafi. "Hajiya tunda ya fara aiki bawan Allah nan ya manta da ni ya manta da matsayina, abu daya ya sani ya saka a kawo min aiki ya koma gefe ya cigaba da harkansu shi da Deen ban san bai da lafiya ba, tsabar wulakanci ban san Ummu bata gari ba sai da ya saka ana bincike, Hajiya tambaye shi me yasa zasu juya min baya?" Ya fada kamar zai yi kuka, "Kai tafi can ban manta da kai ba,aiki ya maka yawa nima aiki ya min yawa bamu da lokacin haduwa sai dare, Deen da kake gani shi nake gayawa Abubuwa masu muhimmanci ya rike min lokutansu sunan ina gwamna ne amma wallahi bani da lokacin kaina sai dare!" "Eh haka ne kinji ba Hajiya wai yana bawa Deen Abu masu muhimmanci ya rike shi." Cika cokali Deen yayi da abinci yana ci ya ce mishi. "ka taya shi murna Ummu ta dawo namu da kai yanzu bikon Ummu!" "Da gaske?" "Kwarai da gaske!" "Masha Allah amma an san daga in take?" "Ko ina Ummu ta je, nayi Imani da Allah ba zata je inda zai zama wani abu else." "Eh haka ne kuma, Alhamdulillahi." Suka ci-gaba da hira. ** *SA'ADIYYA* Sa'adiyya bata saduda ba, kiran Smarty tayi ta gaya mishi rubutun da zai yi, sai da ya ji tsoron ya ce mata. "Gaskiya Hajiya na wannan aikin da hatsari!" "kayi kada ka damu zan tsaya maka, kuma akwai wanda zai wanke ka." Haka tai ta zuga shi har ya amsa mata ta bashi kudi me yawan gaske. Sannan ta zuba idanu. A cikin kasa da awa 24 yaron nan ya birkita social media, wanda ya janyo cece ku ce, dama Wayar Tafida yana hannun Deen ya gani, don haka da kanshi ministry of Information technology, ya tsaya a babban hall dinsu ya zuba musu idanu. "On behalf of Borno state Government! Na zo ne a binciko min Yaron da yake rubutu na.baku awa biyu!" Ya kalli agogon hannun shi ya sakar musu murmushi ya cigaba da cewa. "Lokacin ku ya fara, idan kuka yi fail hmm! Ku saka a ranku aikinku nan amma kuma matsayinku zai ragu! A nimo min gurayen 2011 to 2013 maza ku fara aiki time dinku ya fara." Fitowa wasu matasa suka yi aka ajiye musu computer sannan ya koma gefe ya zauna, wasu dalibai masu sanin makaman aiki suma suka fito. Dayan su ya d'aga hannu ya ce." Yallabai wata uku da suka wuce na datsi IG din mataimakin IG na kasa, saboda ina son na dauko ni aikin yan sanda, Yallabai aikin da ka basu a cikin awa biyu ni zan maka shi a minti talatin! Idan an amince ni kawai aikin dan sanda nake so a dauke ni!" "Kai ku dakata, meye sunanka!" "Jabir Adam!" "Ku bashi!" Mika mishi computer aka yi ya zauna tare da cewa. "Yallabai ka saka lokaci!" "Lokacinka ya fara!" "A dakata!" Kallon MD na ministry din yayi yana faɗin. "Lafiya!" "Yallabai daga fadar abu sai a biye mishi! Ka mata yayi a fara jaraba shi tukun." Dariya yaron yayi ya ce mishi. "Tow ;" kafin mutumin ya cigaba da magana Yaron nan ya shige kan wayar MD tare da kwashe kome na shi na account dinsa.. "Yallabai ka ce mishi ya bude satar shi!" "Bude!" Ba musu ya bude datar. "Sunanka Haruna Gambo, kana da account uku, daya First bank. Daya UBA, kana da kudi a kowani account ka duba nawa ne a cikin suka rage, sannan kana da wasu hotona da wani shafi na musamman!" "Kai don Allah rufe ba shi muke bukata ba, kawai kamo min wancan dan iskan!" "Yallabai ya kwashe min kome a bankina!" " zan dawo dasu amma ka sani sai ka fanshe su!" Ya koma kan Smarty. "Yaron yana cikin Maiduguri state University." "Taya ka gano haka!" "Wayarshi Samsung series X ce, sannan location dinsa a bude yake." Wasa wasa Sai ga Yaron nan ya kamo dan banza, Deen ya tura sako tun da ya fara bayani, har da hotonshi aka binciko! "Yallabai me yasa ba za a saka hukuma ba?" Inji Jabir Adam, "Hukuma ta kama shi zata mishi dukar mutuwa ce, ni kuma ina son na ganshi ne zai gana da me girma Gwamna! Sannan daga yau kun zama team na musamman! Shugaban Team din kai ne, zaku yi aiki da mai girma Gwamna a office dinsa. Dakyau Mazaje kun yi abinda ya dace." "Mun gode sosai sir!" "Matukar zasu yi aiki a special team! Me ya dace da ku?" "Dark web!" "Daga yau kuyi kokarin saka idanun akan socila median Mai girma gwamna! Kun gane MD? Ku zaku zame masa security ne a duk lokacin da haka ya faru, ina bukatar bayani, albashinku zai fara ne daga ranar ashirin da daya ga wata MD su baka number account dinsu. Ka turo min kamar yadda nace wannan team ya zama sirri ko abokan aikinku bana sonsu sani, idan ka sake naji labarin Dark web ya fito." Murmushi yayi yana faɗin kad'a hannunshi. Ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin, "Yanzu dai lahu a gare mu, mu kame harshen mu da zukatanmu fitar da sunan team din nan daidai yake da ka kwabe wando kayi tsirara!" "Inji MD, dake kusan matasa ne shine magidanci sai suka yi na'am da kome kuma dama basu dayawa su goma ne. * *Ummu* Kiran wayata da turo min sako kala kala yasa na fara jin kamar zan mutu, a lokacin Mahira take gayawa Mama da ta shiga wurinsu domin Ummi ta dawo da Taima, sakamakon jin jajjircewa Mama a kaina, sai ta ga ashe ita ma irin kuskuren Mama.take shirin aikatawa. Shine ta kira Mama take gaya mata halin da ake ciki, suke tattaunawa ita kuma Mahira ta fito tan gaya musu abin da ya faru. Ai kuwa akan kafarta ta shigo dakin ganin yadda na cusa kaina a tsakanin cinyoyina ina kuka me cin rai. " idan suka kashe ki Yaranki ne da asara. Kashe wayar ki bani!" Cikin kuka na nuna mata wayar da na buga da kasa. Dauka tayi ta saka a wardrobe. "Mahaifinki Bai tab'a zina ba,.nima ban yi ba har abada ba zaki yi ba kuma ban zagi masu yi ba addu'ar shiriya nayi musu gaya min me zai saka ki yi? Idan duniya bata yarda dake ba ni na yarda dake." "Nima na yarda da Mata ta......🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 D'ago kai nayi ina kallon Tafida da yake tsaye, yayi wani irin rama, cikin kuka na ce mishi. "ka tafi ka tafi bana son ganinka ka tafi don Allah, mama ki gaya mishi don Allah ya tafi bana son ganinshi." Na fada ina kuka don na gaji, takowa yayi har gaban Mama ya zube akan gwiwarshi. "Nayi mata laifi, na hantare ta, na cutar da ita na wulakantata, nayi mata cin zarafin da ban sha'awan ko makiyana a mishi. Mama gaya min me zan yi don na fashi kaina a wurin Ummu? Nayi kuskure nayi kuskure nayi kuskure nayi kuskure. Na rantse da Allah Sarkin sarakuna, nayi mata kuskure." Bakiɗaya sai jikin Mama yayiwa wani irin sanyi, ta kira sunan shi a hankali kafin ta ce mishi. "yau da ka gaya min kayi kuskure na yarda kana bukatar Ummu, amma kayi hakuri yan uwanka basu bukatarta!" "A'a Mama ni nake auren Ummu ba su ba, Mama ni zan zauna da Ummu ba su ba, Mama don ni daya Allah ya halicci Ummu Mama don Allah ki bani ita a karo na biyu, da kanki zaki bada shaidar haka!" "Kayi hakuri Hajiya Aisha ma tazo nace mata tayi hakuri Ummu Hadiyya bata da baki idan na barta da danginka zasu kashe min ita ne." Kasa zama yayi ya kasa tsaye. Ya kara zubewa a gaban Mama ya ce mata. "Na rantse ba zan kara barin Ummu tayi kuka ba na rantse!" Ya fada yana haɗa hannunsa wuri guda. "Ka je zan duba lamarin!" Kallona yayi ya ce. "na rantse ba zan bari ko kud'a ya tab'a ki ba!" "Kana haka ne domin buƙatar kanka, ka gaya min bani da amfani a gare ka balle ga rayuwaryka, Mama idan na koma ma." "Ki min shiru!" Mikewa nayi na bar su yanata magiya, ban daki na shiga na zauna tare da fashewa da kuka. Abun ya min nauyi yadda yake bada hakuri sai naji ba zan iya jure ganinshi haka ba, a ban dakin na zauna har na daina jin muryanshi, kafin na fito ban samu Mama a dakin ba, alola nayi na gabatar da sallah. *Shuwa* Shuwa ce ke kaiwa da komowa take ta kira Malaminta ya fi sau goma daga jiya zuwa yau amma dan iska yaki ɗauka, kallon Sa'adiyya tayi kamar zata zage ta. Sai kuma ta fasa cikin takaici ta rufe ta da duka tana faɗin. "Ni zaki kunyata? Ni zaki ci mutuncina ki tafi har gidansu kishiyarki, zaki tafi ki ci mutuncinta dake yar iska ce ke! Tir da halinki." Ta fada tana haki ranta yayi bala'in b'aci domin bata zaci maganar da Makamin ya fada bogi ba ne sai yanzu. "Na rantse Hajiya Aisha ba zata tab'a moran Yaranta ba, na rantse da Allah musamman Aliyu!" Yadda take cika baki zaka rantse da Allah zata aikata ko idan tayi wani abu zata samu nasara. Ita kan Sa'adiyya kuka take da takaici tana jin tana ganin zata rasa Tafida. *Tafida* Dakyar Deen ya kawo shi domin yaki kawo shi, ya ce mishi ya fuskanci matsalarshi ya ajiye batun Ummu, amma ina zuciyarshi ta gama nauyi, kwantar da kai yayi yana dafe kanshi da yake bala'in sara mishi, "Deen ina ga zan rasa Ummu har abada, Mahaifiyarta taki dawo min ita, Deen ya zan yi?" "Kayi hakuri! Abin da nake gaya maka kenan, kowani mutum da nashi amfanin yau ga Ummu da bata da wani amfani a gare ka, kana son ta dawo gareks amma abu ya ci tura, Ummu da kake renawa ita ce Allah ya nuna mata maka itama mutum ce kuma baka san iya baiwar da Allah ya mata ba, Tafida wannan ya zame maka izina." Hawaye na zuba mishi ya share yana faɗin. "Deen ka zage ni ko ba kome ya ji a raina ina da me gaya min gaskiya, Deen a ce kaf yan uwana babu wanda ya damu da halin da nake ciki sai Hajiya da Abba suka damu da ni, kowa kanshi ya sani sai dai nayi musu hidima, Deen ya zan yi? Kowa kansa ya sani." "Tun farko kai ka nuna Ummu bata da amfani a rayuwarka, da ka ja ta a jiki yan uwanka ba zasu mai da kai abin da suka mai da kai ba, sun mai da kai wawa kowa ya more ka ya koma gefe, Tafida ina jin haushin yadda babu wanda ya tab'a tambayar Ya Yaranka sai su zo da nasu yaran fisabiilillahi wannan wacce irin rayuwa ce, wato idan na fahimci wani abu kawai babu me son kayi gaba gara ka zauna kana bautarsu. Kayi hakuri yan uwanka ne dole yasa nake magana!" Haka ya mai da shi gidan Hajiya, nasiha da Hajiya tayi ya mishi tana nuna mishi muhimmanci yarda da ƙaddara yasa shi samun nutsuwa ya kwana a gidan, washi gari Deen ya zo daukar shi don yace zai koma office. Haka ya koma office zuciyarshi babu sukuni, idan ka ganshi sai ka zubar da hawaye. Alfarma daya Mama ta mishi. Duk ranar Juma'a ta ce yana turowa ana daukar mishi Yaranshi suna wuni a wurinsa. Abba kuwa jin labarin abin da ya faru, akan kafarshi ya maida Sa'adiyya. Yace ai babu saki babu yaji, bayan komawarta Hajiya turai itama ta ce Asiyah ta koma gidan da zama yadda zata na taimaka mishi, shi kuwa ganin haka yayi amfani da Asiyah don cusguwa Sa'adi. Yadda yake fita da ita ko ya ce mata ta fito su zaga gidan, wannan abun ya fara damun Sa'adi kamar zata yi hauka. Ai itama ta ji yadda mata suke ji, nan ta fara zirga-zirgan kai kara nan ma Abba ya ce tayi hakuri aiki Asiyah take taya Tafida,ai lokacin Ummu da take mata haka bata kawo kara ba haka ta shanye itama ta koya daga Ummu, bakin ciki yasa ta jin kamar zata mutu, a bangaren Tafida ya rungume lamarin rayuwarshi domin ya fahimci Ummu bata da iko da kanta sai abin da Mahaifiyarta ta ce mata, Hajiya ma tana zuwa kullum ta gaida Ummu sannan ta roke ta alfarman yaushe zata dawo. Bata iya magana sai dai tayi ta wasa da yatsunta Hajiya bata sare ba. *Ummu* Zan iya cewa Mama tayi tsaya akan kalamanta, kuma ta tsaya min sai dai a kwanakin nan Mahmoud ya matsa min da zuwa, yau ne zuwan shi na biyu don haka naki fita, Mama tace min. "Ba naji ance Abokin Babansu Mufidah ya zo ba?" "Kyale shi Mama da Yaya Deen ne zan fita wannan na tsani ganin fuskarshi ma!" "Hmm idan muka sako ya kawo ki fa?" "Mama babu sakon da zai kawo min domin." "Ba kyau wulakanci, tashi ki je abokin Tafida ba abin wulakantawa ba ne!" Ban so ba haka na fito na same shi sanye da babban kaya. "Malam me kake bukata da ni?" "Malama Ummu ina sonki, kuma ina me baki shawara ki rabu da tafida domin ba sonki yake ba, amfani da ke zai yi ya wuce abinshi! Sannan ya cigaba daga inda ya tsaya kada ki manta, yan uwanshi basu sonki ni kuma duniyata a bude take na so ki." Murmushi nayi sannan na ce mishi. "Ko mutuwa Tafida yayi bana fatan na auri wani na shi balle kai, don haka ka b'ace min da gani mara kunya mara tsoron Allah, Allah ya tozartaka kamar yadda tab'a min aurena, Allah ya kunyata ka, kamar yadda ka kunyatani." Daga haka na bar shi tsaye ranshi a b'ace. Bai kara zuwa ba sai dai yana yawan turo min sako bana gogeda na shiga tara su domin zasu min amfani. * Yan uwan Aliyu sun dauka da zafi, sosai fiye da yadda ake zaton, sai kananun magana suke har da wanda basu daki daya suma sun dauka da zafi abin da ya kawo haka zuwan watan azumi da ya gabato, A tunaninsu Tafida zai sake bakin aljuhu sai suka ga wannan lokacin shiru suke ji, Abba ne ya musu rabonshi, a wannan azumin ya biyawa Hajija da Abba Umara, Sai Inna da Hajja Ganaah ya ce su je can su ta mai da larabawa maza mata, mata kuma maza, sai abincin sadaka da ya kaiwa Mama da kanshi ranar da aka kai azumi biyu, ranar a gidan ya sha ruwa.da zai tafi ya dauki Mufid da bai yi barci ba, ya fita da shi, "Ko zaki zo ki karbe shi!" Kallon Mama nayi naga tana nata hidimar ban amsa ba, sai da ya kara maimaita maganar ta amsa da cewa. "Ka je zata zo" fita yayi ta zuba min idanun. "Ki je!" Tashi nayi na saka hijab din sallah mama na fita, a zaure ya tsaya. "Bani shi tow!" "Zan baki shi don Allah ko zaki raka ni nan wajen ba nisa!" "A'a babu inda zan je!" "Please baki nayi zamu je ki gaida su don Allah!" "Babu inda zaki ka rufa min asiri kada ka ja min fada a wurin Mama!" "Ok na fahimce ki idan Mama bata gari zaki iya raka ni kenan!" "A'a Tafida ka rabu da ni kada ka kara cillani cikin matsala." "Ok ba zaki.je ba!" Ganin yana jan maganar na juya xan koma cikin gidan ya riko hannuna. "Ki fahimce ni ina bukatarki a kusa dani!" "Ni dai don Allah ka kyale ni!" Mika min Yaron yayi sannan ya tako gabana yana fadin. "Allah ya huci zuciyarki! Don Allah ki dawo dakinki!" "Ka tafi wurin Mama babu ruwana!" Haka na bar shi tsaye rashin da zuciyarshi kewa suke. Ya rasa yadda zai yi kamar yayi hauka, haka suka bar gidan washi gari ya aiko Deen da shaidar zuwa Umara, tayi murna sosai amma indai don kome ne gaskiya ba zan koma ba haka ta gayawa Deen ta cigaba cewa. "Ina son Tafida ya gane yan uwan shi basu bukatar Ummu idan ya dage karshe rayuka zasu B'aci kaga ba zan yarda a ci mutuncinta ina gani ban dauki mataki ba, da ace yan uwansa suna sonta da zan hakura." Murmushi Deen yayi kafin ya ce mata. "Mama a wannan duniyar ma, Manzon Allah har ya gama rayuwarshi dai da aka samu wanda suka ki bin shi duk da sun san gaskiya ya kawo musu, Mama idan kika ce lallai sai wasu sun so Ummu baki yiwa Tafida adalci ba, amma Ummu yarki ce kina da iko akanta amma ki sani a kasa yaushe addu'ar zabin alkhairi muke fata, nasan yanzu Tafida yayi laushi wallahi ba Ummu ba wani ma ba zai wulakanta ba, kuma ba zai tab'a bari a wulakanta ba, Mama zuwa yanzu ta dace ki gane darajar yarki a wurin Tafida shi gwamna ne, wanda ake mishi tayin mata a kullum.amma ya hakura da bukatarshi yana jiran Matarshi daga gare ki, amma a haka ki ce na zata koma ba, duk abin da kika ji ba a kai wanda na gani ba, amma yau naga tarin soyayyar Ummu a idanun Tafida, na ka kauna mara iyaka a cikin kwayar idanunshi, na san Allah yake da ikon sauya mutum ba mutum ba, sai dai a wannan karon Allah ya bawa Ummu sa'a ta sauya Tafida. Ummu ta sauya Tafida ta sauya tunanin shi da duniyarshi, Mama idan kika bincike ta itama tana bukatar mijinta hakuri ne da kawaici irin naki da kika tarbiyyarta da ita a kai Mama ki gane ba kowa ba ne a duniyar nan lallai zai soka wanda suka so ka ka musu halaccin mai da musu soyayyarsu ko da bayawa ne."ba ita Maman ba hatta ni sai da Deen ya kashe min jiki da kalamanshi, a hankali ya mike yana mana bankwana, hankalina ya tashi amma haka na boye damuwata a raina na kuma yi alkawarin ba zan kara zubda hawayena ba, duk yadda tayi daya ne da Tafida zan zauna ba da Yan uwanshi ba.....🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Bayan na shigo gidan Mama tayi ta kiran Yan'uwa da abokan arziki tana gaya musu abin da ya same ta na alkhairi. Kafin wani lokaci mu ma gidanmu kowa yasan Mama zata umara, amma maganar gaskiya bata ce kome akan komawa gidan Tafida ba, ban san waye ya gayawa Dangin Tafida kawai sai ga kiran Maryam koda na dauka ina jinta. "Wato asirin da Maman Samha take cewa kun yiwa Tafida gaskiya ne ko? Tow wallahi ku dawo da takardan Umaran da ya baku ko na.baki mamaki." "Maryam ni bana faɗa a cikin azumi idan kun cika yan halak ku hana Tafida yau zuwa shan ruwa, sannan ku ce kada ya zo yaci abin da na dafa mishi domin kuwa zan saka mishi, makale mata, manne mata, dan katafi, mallaka, tare da bita zai zai, ku hana shi zuwa fa domin idan ya sha ruwa zan bashi kafi shayi ma." "Ummu kin ci Abu zan Ubanki tsinanniya yar matsayata!" "Eh na yarda aje a haka, yanzu ya dace ku kwantar da hankalinku duniyar sannu wanku ba zai tab'a cika ba sai da jinin Baburawa, Allah Sarki bawan Allah ya gano inda arziki sai rawan kafa yake, idan na kore shi ta tafi gida likitoci su ta saka mishi ruwa, ku tanadi maganin hawan jini matukar na dawo sai dai wasu baku ba, mtsee!" Na kashe wayar ina jan tsaki, kallon Mama nayi da take tsaye a bakin kofar dakin. "Ni bana son tashin hankali Ummu, Tafida yan uwanshi ba zasu barki haka, fitinarsu tai yawa, ki kira min Deen ya zona fasa zuwa Umaran." "Mama bafa su suka biya miki ba, shi ya biya miki taya zaki mai da kyautar da yayi miki bayan Allah baya son haka, idan yan uwan Tafida ne ba zasu fasa ba haka suke, hassada da kyashi halinsu ne!" "Ke kina son Mijinki?" Kaina a kasa na rasa amsar da xan bata, dai nayi shiru don nasan babu amsar da xan bata. "Nace kina son Mijinki ne?" Ban yarda na amsa mata ba, murmushi tayi sannan ta fita, ajiyar zuciya na dauke ina jin kamar na tsira. Ina kwance bayan azhar ya turo min sakon. _Ummu xan zo na sha ruwa!* gyada kai nayi kamar yana ganina, tashi nayi na nufi tsakar gida. "Mama Babansu Mufidah zai zo shan ruwa!" Juyawa tayi tana kallona. "Ko kiranshi kika yi?" "A'a wallahi ban kira shi ba." "Ki shiga store akwai kayan abinci, ki daura mishi duk abinda ya dace!" Abinka da an kwana biyu ba a shiga office ba, na shiga store din na fara aiki, kamar me domin akwai gas me kai hudu, tunda na shiga da Mufid a bayana, Mufidah tana bayan uwani Yarana sun yi wayo don ma naji Mama tana fadin Allah ya raba ni da kunika domin alamu ya nuna kazamin goyo nake. Wato ina goyo ina period, kafin a fara azumin nan sai da nayi kwana huɗu ina wanka aka fara azumi haka na nufi idan aka kusan gama azumi ma xan kara yi, ina gyara wanke kaza ta shigo tana faɗin. "Ke ga wayarki tana ta kara!" Amsa nayi ina faɗin. "Na gode!" "Ni fa ba gudun lamarinki da Tafida nake ba, ke rawan jiki shi rawan jiki, ga shi dama baki yi wani abu na kula da Yaran nan ba, idan ban yi da gaske ba, ciki zaki kara daukowa don haka ki gaya mishi nace sai bayan layya zaki koma dakinki, ki je can naga shegen da zai tab'a min ke! Kafin nan Yaranki sun ƙara wayo wata takwasi zuwa tara tunda yanzu suna da wata biyar ko?" Sai na rasa farin ciki zan yi ko bakincikin sai na tsinci kaina da juyawa na kalli Mama amma kuma ban ce mata kome, watanni uku ban gaba fa mama take magana a kai, sai ban ce kome ba, iya abin da na tsinci kaina da furtawa. "Allah ya saka da alkhairi! Ya baki lafiya da nisan kwana, ya kuma kai ki Umaran ya dawo dake lafiya!" "Amin Ya Allah!" Ban yarda nayi wani farin ciki can ba, na cigaba da aikina. Haka na gama. Ana dabda shan ruwa, koma daki na bawa Yarana nono suka sha, sannan na shiga nayi wanka na gyara su tas, na fito na hada musu madara suna sha suka kwanta, wayata ce tayi ƙara na dauka, ganin bakon number ne yasa na ɗauka na kara a kunnena. "Ummu, ina me kara baki shawara ki amince da bukatata, Ummu yan uwan Tafida ba zasu barki ba." "Deen meye matsalarka da ni ne?" "Ummu! Dalla yi min shiru banza dan iska Dan akuya xan gayawa Tafida na gaji da halinka!" "Kafin nan ki saka Tafida ya sake yaron da ya saka aka kama, domin kuwa abin zai faru ba zai yi kyauta ba." "Barazana kake min ne?"."na gaya miki dai!" Kashe wayar nayi na barshi ina cikin tunanin wani Yaro Tafida yasa aka kama, aka kira sallah, na saka doguwar riga na tadda sallah. Ina zaune a wurin, ina kokarin mikewa na fito na yi bude baki aka dauke wuta, daga yadda aka dauke wutar jikina y bani Tafida tana hanya a gurguje na sha kunun gyada da kosai, bayan minti talatin sai gashi dakin Kawu Gwani na zaune muka kai abincin, shi yana wurin Baba suna tattaunawa. Bayan ya gama ya shiga ya gaida Mama, sannan ya fito don tana mishi godiya ne ya fito yana murmushi. Dakin zauren ya nufa, can na biyo shi da Mufidah da ta farka, ina shiga dakin ana kawo wuta, baya dakin amma ga kamshin turarensa. Juyawar da xan yi na ganshi tsaye a bayan kofar, ya harde hannunshi a kirjinshi. Sunkuyar da kai nayi ina faɗin. "Kazo ka ci kada ya wuce!" Kwaikwayo na yayi yana rufe kofar. Kallonshi nayi da sauri. " ba abincin bane damuwata, ki taimaka bawan Allah!" "Tafida ka rufa min asiri ni na yar iska ba ne!" Jan kumatuna yayi yana faɗin.."tow zauna ki bani na ci sai na tafi kada na lalataki." Haka na cigaba da zuba mishi abinci bayan ya zauna a bayana, juyawa da zan yi na sauka akan cinyarsa da jikinshi. "Ummu Hadiyya karya ni zaki yi?" "Kai ne fa ka zauna a wurin!" "Uwata kin ga abin da akewa Shalelenki ko!" Ya fada yana wasa da Mufidah. Ajiye abincin nayi xan mike ya ajiye Mufidah, ya riko gam. Tare da sakar min wani irin huci me zafi sanyi sanyi, ya matse ni sosai. "Ina kewarki Ummu!" "Kayi hakuri bayan layya tace zan dawo!" "Gaskiya yayi nisa, ina zan kai bukatata!" "Don Allah ka rufa min asiri kada ka ja min magana." Juyar da ni yayi yana kallon fuskata. A hankali ya sumbaci goshina. "Har ga Allah wata uku nan gaba, wallahi zan lalace!" "Tow ya xan maka? Na gaya maka ga abinda ta ce amma ba yarda ba!" Rungume Ni yayi yana shinshinar wuyata, "please a dawo bayan sallah wallahi ba zan iya jiran har bayan babban sallah ba." "Tow kayi yadda kake so shi kenan!" "Yadda nake son haka za ayi!" Ya shiga sumbatar wuyana zuwa kirjina, rike shi nayi na fara faɗin. "Don Allah ka ci abinci!" "Bafa abincin da xan ci!" Ya cigaba da abinda yake, haka kawai nake jin jikina yana wani irin Yummmmm, da sauri na kwace kaina, bai tab'a min abin da yake min yanxu ba, sai na kasa jurewa, bude idanu yayi a kaina. "Ki min adalci ki barni na samu nutsuwa dake!" "Tafida ni ina jin tsoro Mama tace zan iya samun ciki shi yasa ba zan koma ba sai Yarana sun yi kwari!" "Allah ba zan shiga ba na miki alƙawari." Yadda yake lallaba ni da kalamai yasa nayi shiru, tare da kasa cewa kome, domin yadda yaƙe min a da can baya bai tab'a min ba, kuma ni ba zance haka shi ne wani sinadari na musamman a aure sai yanzu da yake biya min karatunsa. Kukan Mufidah ya katse mishi abinda yake yi, ya zuba mata idanun yana faɗin. "Uwata ya zaki min haka? Gaya min laifi nayi da ba a son na huta a jikin Mama?" Kwace kaina nayi na tashi a jikinshi na koma can gefe ina gyara zaman rigana, nayi ina matukar jin kunya. Abincinshi ya a hankali yake ci yana kallona. "Gaskiya wata uku nan gaba yayi min yawa bayan sallah shi ne abin da na yanke!" "Tow ka same ta ka gaya mata ni babu ruwana!" Na zata zai hasala ne, sai na ga ya ce min. "Ummu ina matukar jin kunya mama ba zan iya ce mata haka ba, da Abbana ne ko Hajiyata wallahi sai sun rage, amma ba zan iya kallon Mama nace mata watanni sun min yawa ba, Mama tayi kokari da ta bani ke a karo na biyu, ina tsoron kada wani abu ya faru ta kwace min ke har abada, mutuwa xan yi!" Murmushi nayi kafin na ce . "Ba zaka mutu ba, kawai zaka sha ciwon kai ne!" "Ummu!" Ya kai hannunshi fuskana. "Ki yafe min abin da na miki?" Hannuna na kai saman nashi nace mishi, "Aliyun da na sani ba haka yake ba!" "Ki ce kin yafe min!" "Na yafe maka Daadin yan biyu!" Sai nake ga kamar da can Tafida yana sona kawai iskancinsa ne yasa yake ta tsula min tsiya, haka ya gama cin abincin ya tafi, na raka shi har bakin kofar, ya ce min yana zuwa ne nan kafin Hajiya ta dawo, don a can wurinta da wurin Deen yake cikin abinci har zai tafi na ce mishi. "Ni Ko akwai yaron da ka saka aka kama shi ne?" Kallona yayi kafin ya ce. "Eh wani abu ne!" "Ka sake shi!" "Za a tura shi hannun hukuma!" "Ka sake shi nace, saboda yana cikin mutanen da suka kaad'a kuriar zabarka, babu amfanin rike shi." Murmushi yayi ya ce min. "Zan saka a sake shi, amma kuma dole na tauna aya tsakuwa taji tsoro, waye ya gaya miki!" "Ka tafi sai da safe ka samu kayi sallah tarawee!" Na koma cikin gida, yana barin gidan kofar gidan kiran Deen yayi ya ce mishi. "Taya Ummu tasan da batun yaron nan?" "Ban sani ba wallahi!" Shiru yayi kafin ya ce . "Wani yana niman shiga tsakaninmu kenan!" "A'a ba haka ba ne, maybe an gaya mata ne domin ta roke ka alfarman sake Yaron!" "Ai na gaya maka ba zan waiwaiyi Yaron ba, sai na ga abin da ya faru tsakanina da Ummu, zata kome shi kuma ɗan iska ku ci Ubanshi gobe a mika shi kotu!" "An gama!" Lokacin da ya isa gidan, ya samu yan uwansa da matan yayunsa da matan Sharif wai Sa'adiyya ta hada musu bude baƙi, kallo daya yayi musu ya wuce bangaren shi, Tashi tayi ta biyo shi, wayarshi tana kunne a hankali ya ce mata. "Baki kyauta min ba, naso na sha madaran nan amma kika hanani, me yasa?" Daga can Ummu ta ce mishi. "Saboda kai kato ne, kada ka shanyewa Yarana abincinsu!" "Tow ai ni ma yaro ne, "gaskiya babu adalci a wanann lamarin, duk ranar da kika dawo zamu tafi honeymoon!" "Yarana jarirai ne!" Saadiya Ji tayi kamar an dasata a wurin shi kuwa da bai san tana nan ba, ya ce mata. "Ki gyara min gashinki nan, da wancan wurin sannan na shanun nan a gyara min domin ina nan daram zan dawo fage na!" "Kai ni fa na gaji da kai ka bari dai na tafi na samo wani bazawarin tunda kaima kayi auren!" "Ummu zan fasa miki baki, na gaya miki idan kina son numfashina ya tsaya ki fara kiran saki, zan daujee bakinki nan!" "Hmm! Ai gaskiya ne!" Jan kofar dakin da aka yi girummmm ya sa shi juyawa, bai ga kowa ba,ya cigaba da sake zantuttukar da yake jin nishsdi akansu, bayan ya gama wayar, ne yayi kamar ana ihu ko kara ne cire babban rigarshi yayi ya fita, Saadiya ya gani tana ta hauka tare da fashe-fashe. "Meye haka?" "Tunda ta fito daga ɓangarenka take wannan abin borin. Murmushi yayi yana faɗin. "Ok tow Allah ya bata sa'a gwamnati bata san asara ba, duk abin da kika fasa ki sani zaki biya shi, su a tunaninsu zai bada hakuri ne sai suka ga wani salon rashin mutunci. "Na san abin da kuke aikatawa kyale ku nayi, don wacce ta fasa abin da tayi niyya ta rena mahaliccinta, Ummu kuwa ku saka ranku ta dawo, wani dan iska ya kara shiga tsakaninmu sai na saka an daure shi har ya mutu, kai wani shegen ya kara shiga harkar Ummu wallahi ko ciki daya muka fito sai na saka an wulakanta min shege, mugun kallo aka mata sai na tozarta mutu, don haka ki gama haukarki Ummu zata dawo wacce kika ji muna waya ita ce zata dawo dakin ta, sannan duk wanda ya san.ya biya wani yaci mutuncin aurena sai na lalata mishi lissafisa." Yadda yake bala'i yasa suka fara daukar kayansu daya bayan daya suna barin wurin dama, ya kalli Maryam cikin masifa da tijaran da ya ajiye kwana biyu ya ce mata. "Wallahi idan kuka tab'a min Uwar Yarana sai na baku mamaki!" Daga haka ya wuce abinsa cikin gidan. Ko yau Baba Nura da yazo daga Damaturu sai da ya gaya mishi kada ya sake ya zama irin Abba da kome za aayi ya tsayawa Matarshi itace shi, kafin ya zama gwamna take tare da shi, sannan ta shanye duk wani abin da yake mata, ya tsaya da gaske ya ga ya bata kariya, kada ya ga kamar abin wasa ne wannan abin da yake faruwa sak abin da aka yiwa MAHAIFIYARSU ce don haka ya tsaya kada yayi saken da zai yi danasani. *Hajiya* A kasa me tsarki kuwa bata daina gayawa Allah lamarinta ba, musamman Tafida da Ummu fata take Allah ya daidaita su, idan suka hadu da Abba dariya yake mata ya tsokaneta da cewa. "Idan don Tafida da Ummu ne ki barwa Rabbil Ka'aba, yasan abin da zai yi da alamarinsu!" Murmushi tayi tana faɗin. "Ban sare ba, ina gaya mishi ne domin yasan ban daina rokon rahama da jikai ga Tafida ba." "Allah ya tabbatar da alkhairi!" "Amin Ya Allah!" ** *Deen* "Ba zaka gaya min waye ya saka ka ba? Kai ku ci kaniyarshi!" Ganin zasu cigaba da mishi dukar da kullum sai sun mishi kamar jaki. Ya kalli Deen cikin tashin hankali ya ce mishi. "Idan na gaya maka zaka kyale ni?" "Zan kyale ka!" "Da gaske?!" "Eh!" Cikin tashin hankali ya ce mishi. "wasu mutane biyu ne daya Sa'adiyya matar gwamna ce namijin ne ban san waye ba, don Allah ka taimaka min." "Zan kai ka kotu a hukuntaka, idan ka fito zaka min aiki kuma zan tsaya maka kayi karatu ka ji!" Cikin kuka ya ce mishi. "Na gode sosai!" Daga haka aka fitar da shi zuwa office din Yan sanda. Washi gari aka wuce da shi kotu. Duk abinda ake tuhumi yaron ya amince, don haka aka hukunta shi tare da gargadin na gaba su kiyayye aka tura shi gidan gyaran hali. *** *Ummu* Ranar goma sha biyu ga watan Ramadan su Mama suka nufi kasa me tsarki, sai da ta min Gargadi akan na kama kaina kada na sake Tafida yayi min dadin baki, na barshi wani abu ya haɗa mu na hakura akwai gyaran da zata min kada na sake wani abu ya faru don ranta zai b'aci, sannan ga wani tsoro da ya kama ni, don haka na rufawa kaina asiri, bayan na rakota, muna dawowa Tafida ya kira ni. Tsoro yasa na kasa daukar wayar don gani nake kamar Mama tana kallona. Sake kiran wayata yayi na dauka jikina yana rawa. "Me yasa ba zaki dauki wayata ba, Hajiya da Abba gobe zasu dawo!" "Kaga don Allah ka kyale ni, kada ka ja Mama tace ta fasa dawowarmu!" Dariya ya saka yana faɗin. "Ina hanyar zuwa bude wani titi. Deen zai zo ya kawo ki da abin bude bakina." "Tafida masifa kake son jaza min ne? Don Allah ka rufa min asiri!" "Ni kuma ki tona min asiri ina yawo abu a hannu ke zo ki bani hakkina!" "Tafida yaushe ka lalace ban sani ba.......🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Innalillahi wainnalihir rajou! Don Allah ka rufa min asiri azumi nake ni ban saba da wannan sabon halin naka ba sai an jima!" Ina jin yana dariyar shakiyanci. "yarinya ki gama kimtsa min kanki na gaya miki, dama Mama ce ta min karan tsaye, yau kuma ki tabbatar tare zamu kwana!" Kashe wayar nayi ina zare idanu. Ba zan iya maganar Tafida da ba, tunda muka dawo sai na kasa kome domin nasan tunda ya ce haka ne tow haka ne na san waye shi akan ra'ayinsa. Shiru nayi ina zare idanu kamar nayi karya. ** *Asiyah* "Mummy da gaske Matarshi zata dawo, Wallahi na rasa yadda xan yi domin ni dai yayi min, sannan ba a office dinsa nake aiki ba a tare da wani abokanshi nake aiki. Gaskiya Mummy kiyi wani abu ko ni nayi wani abu!" Ajiyar zuciya Uwar tayi ta kafin ta cewa Asiya ta waya. "Na gaya miki Tafida shu'umi ne, sannan ba zamu tab'a nasara akanshi ba haka kawai sai dai ko idan zamu jaraba makirci shine kawai mafita!" "Kamar ya kenan?" Murmushi Uwar tayi ta waya tana faɗin. "Kwantar da hankalinki, ina yanzu kina gidanshi ne?" "Eh Mummy!" "Shi kenan, ki tunzira matar gidan ta miki wani abu yadda zaki shigo gidan kenan, dole sai mun hau matakala ta kanta yadda zata bamu kofar shigowa gidan!" "Allah Mummy?" "Da gaske nake gaya miki, zaki shiga gidan Tafida kamar yadda shuwa ta shigo da jakar yarta haka kema zaki shigo mishi!" "Wayyo Allah Mummy shi yasa nake sonki, yanzu ki gaya min yadda xan yi?" "Yanzu kafin matar shi ta dawo nake son ke maganarki tayi karfi, idan har muka sake yarinyar ta dawo baki shiga ba tow har abada ba zaki tab'a shiga gidan Tafida, domin yarinyar a shirye take, haka Uwarta ma!" Sannan ta daura yarta akan hanyar da ya dace. Ta kara da cewa , "wawuya ce, tana ganin haka zata haukace ta fara kiranki da sunayen banza, ni kuma zan yi magana a lokacin." Ajiyar zuciya ta sauke tana faɗin. "Na gode sosai Mamana!" *** Tunda na gama birgima na tashi, saboda yadda Tafida yake gaya min abin da yake bukata na bude baki, na shiga ba baji ba gani, kafin karfe shida na gama. Sannan ka kira Uwani na fara lallabata domin tun shida saura Tafida ya tabbatar min yana hanyar dawowa Maiduguri, Deen zai zo ya kawo ni gidanshi ba na gwamnati ba. Na fara kame-kame. "Babansu Mufidah yace ki tafi ko?" "Eh amma na rasa yadda zan yi! Don Allah ki rufa min asiri, wallahi na rasa yadda xan yi da shi ya dage kuma Mama ta ce." "Wayyo Allah Aunty Baby Allah ya baki irin mijin da nake fata!" Inji Zakiya da ta shigo dakin. "Meye?" "Eh mana domin ya rakashe ya tura keyar Mama Umara" suka kwashe da dariya, fita Uwani tai ta dauki jakar goyanmu ta zuba kayan barcin da nazo dashi kala daya, sai na su Mufidah. "Ba don kada Mama ta zargi wani abu ba da ba hada miki kayanki sai ana gobe zata dawo ki dawo gidan nan, kina da hakuri gaskiya. Irin su Mama ne da a sawun mutanen farko ta fito tow za a sha wahala ita kafin ta fahimci Yesu Almasihu Annabi ne ba dan Allah ba! Maza ki gyara! Aunty Baby kema kamar tsohuwa fisabiilillahi ko irin maganin matan nan ba zaki na sha a boye ba, haba don Allah." Sai gani da zare idanu, ina sosa kai tsaki tayi ta bar dakin, store ta shigo ta dauki kwai da lipton, ta fasa sannan ta jika lipton din, ta matse min tana faɗin. "Lokacin da Ummu Rooman take wanka idan mama ta wuce dakin Baba shegiya mijinta yana zuwa ganinsu zata jika ta sha, idan ta raka shi waje. Yarinyar nan tantiriya ce wallahi Aunty Baby na ga kokarin, yadda Ummu Kulsum tayi ta kashe arna da sunan wanka lokacin da muka je mata kwana biyu. Yadda kuka san me ciwon idanun na fata kyafkyafta idanu. Yarinyar ta bani tsoro da ta mika min kwai na sha. "Zan yi amai!" "Mtseew yar kauye!" Ta kama hancina ta matse tare da dura min ruwan sannan ta dauko lemon tsami rabi ta cusa min a bakina, haka nayi ta taunawa har na hadiye, na wuce ban daki da gudu ina wanke bakina. "Aikin kenan!" Ta fada tana ciro dabino ta fara cire hancinsa, tana jefawa a cikin ruwan zafi. "Aunty Baby wannan sai kin dawo ke da kanki zaki ce Excellency ya bani kujeran aikin hajji!" Fita nayi ina faɗin. "Allah ya kawo miji mu mika ki, kafin ki fara sayar da kayan mata!" Haka na wuce daki ina jin kamar nayi amai, na daure, yarinyar nan ana kiran sallah ta dura min kwai, haka nayi ta jin zuciyata kamar zai tashi, can da na sha ruwa sosai sai na nemi kome na rasa, wanka na cab tare da zuba kayan kamshin a jaka, domin ya ce min Deen ne zai zo ɗauka ta. Ina sallah na zauna naci abinci a gurguje, kiran wayarshi yasa na tsaya na dauki wayar. "Da kaina nazo bana son Deen ya rigani kallon kwalliyar da kika min, gani a parlour Alhaji!" Murmushi nayi na mike ina faɗin. "Tow!" Yadda nayi maganar sai da ya kwaikwaya. Bude jakata nayi na dauki kayan kamshina na fara shafawa ina mirza nan ina shafa wannan. Kafin kace kobo dakin Mama ya kidime da kamshi, sannan na fito na kira Sa'idu ya kai min abincin waje, wurin drive, ya bashi aka saka a mota, ni kuma na nufi parlour Baba Bulama na gaida shi. Na mishi Barka da shan ruwa, bayan na fito shima Tafida ya mishi magana zai tafi, addu'a Baba Bulama yayi mana, ina tsaye rungume da Mufidah Mufid yana bayana. Amsar Yarinyar yayi yana faɗin. "Yaushe zaki girma?" Kallonshi nayi ina mamaki. "Eh mana, shirunki yayi yawa ko dan irin hiran nan baki iyawa da ni a waya, balle kuma nace muyi chat a Whatsp!" "Hmm!" Hannunshi ya kai ya hana da nawa, yana faɗin. "Hmm! Yana min dadi idan kika ce, haka yana nufin akwai maganar da ba zaki iya fada ba kawai kin barwa zuciyarki." Kallon shi nayi, "Ka Amshi baka mummunar siffa nan? Ka amshi inuwar Bobo!" A hankali ya sunkuyo da kanshi ya kai bakinshi kan nawa, ya sumbaci bakina. "Ina son lips ɗinki! Da wannan kwayar idanun da babu tsoro a cikinsa sai kunya da kawaici!" Kasa nayi da kaina, ina faɗin. "Daga karshe ka karbi yar karama gajeruwar mace!" Bakinshi ya kai daidai kunne na, "akwai tazara tsakanin fuska da kasa. Shi kasa yafi fuska alfanu! Shi yasa never judge book, saboda bangonshi." A zaure muka tsaya. "Wannan tafidar da yake gabanki, ba wancan me cewa gyara min zan shiga gona ba ne, wannan manomi ne kuma makiyayi ne, sannan dan Gwari ne da ya san darajar kome, wannan ya san darajar tsirai har su yi yabanya, wannan Tafidan ya san amfanin kiwon yadda zasu ta yaɗuwa, wannan Tafidan ya san amfanin kayan Gwari yadda ba su lalace ba, ya iya matse lemo har sai ya zubda ruwa face-face!" Ya fada yana murmushin shuumanci!. Wani rufe idanu nayi tare da faɗin. "Don Allah kada ka mai she ni yar iska ka zauna kana yanko min magana gundun -gundun!" Wurin motar muka isa aka bude mana, na shiga shima ya shiga daya bangaren. Karban Mufid yayi yana me kwanta da shi, shima a kafadarshi. "Kina tsammanin!" Rufe mishi baki nayi ina faɗin. "Don Allah!" "Don Allah!" Tura baki nayi ina faɗin. "Meye matsalarka da murya ta ce tayi karama ne?" Girgiza kai yayi yana faɗin. "tana min dadi ne? Kin tuna ranar da muka zo? A ranar da aka ce don Allah ki kira Ummu Hadiyya a gidan can!" Juyar da kaina nayi ina kallon titi! Unguwar da muka je sabon unguwa ce babu kowa, wani gida muka nufa tun daga bakin get din gidan na fahimci Tafida ya yi ne domin hutawa. Sannan bayan son hayaniya. Gidan yayi kyau ga shuke-shuke da aka zagaye gidan da shi. Ko ina ka shiga gwanin ban sha'awa. Allah yasa shigar da nayi ta lullube ni, Deen ne ya fito yana tsaki.."Dan iska namamajo dalla zan tafi, Ummu cin amana don ya tura mama Umara kika biyo shi xan gayawa Mama ai!" Ya wuce wurin Motarshi yana me shiga. "Gobe Friday kayi handling wasu abubuwa akwai maganar project na Bama nan, sai ka tura min ta email dina." "Ok! Drive din zamu tafi da shi ne?" "Eh tow me zai min!" Ya fada yana jan hannuna. "Ummu shiga bari nayi mishi nasiha domin ba kai ne da shi ba kamae sigari." Shiga nayi na barsu a wurin. "Tafida ka dawo da Ummu rayuwarka a karo na biyu, Tafida idan ka yiwa Ummu wani abu bayan ta yarda da kai Allah zai saka mata, Tafida a cire son zuciya idan wata ce da aka gaya mata baka da lafiya ba zata dawo ba, amma dake tana sonka tana buƙatar ka ga Yaranka ta dawo Tafida ja ji tsoron Allah kada ka cutar da Ummu wallahi babu ruwanta yarinyar tana sonka ne domin Allah!" "Kayi min uzuri idan na kauce hanya, idan nayi kuskure kada ku juya min baya ku tsaya tare da ni haka zai saka na fahimci abin da na aikata ni, xan yi kokarin gyarawa! Na gode sosai Deen!" Murmushi yayi yana faɗin. "Kai kai kada ka ce zaka rungume ni ba Ummu ba ce ni ne nan Safiyyudeen!" "Banza gardi kawai!" "A dai bita a hankali tana da karamin goyo!" Dariya ya saka suka tafa, Tafida yana tsaye har ya bar gidan shi da Drive, kofar gidan security ne dauke da manyan makamai. Sannan ya shigo parlour ya samu ina bawa Mufidah Nono, zama yayi yana kallon Mufid da yake barci. Murmushi yake yana kallon yadda nake bata nono tana sha a hankalin. Hannunta ya shafa da ta dunkule ta daura a saman nonon. "Ummu nonuwar kananun amma kuma ji yadda take sha kamar an bude mata pampo!" Ya fada yana shafa saman maman, kallonshi nayi kafin na cire hannunshi a hankali, wanda nake jin duminsa har cikin raina. Sake mai da hannun yayi yana murmushi. "Sau nawa suke shan nono cikin dare?" "Ya danganta da madaran da suka sha, ne!" "Yanzu haka zaki kara musu madaran ne?" "Sai zuwa sha daya xan basu suna sha bai wuce su sha nono sau daya ba." Gyada kai yayi yana faɗin. "Tow nima a samin na sha?" Zare idanun nayi kafin na rufe mishi baki. "Ka daina Please!" "Ka daina Please!" Ya fada yana dariya. Barci tayi na cire ta a nonon, sannan na kwantar da ita. Barci yayi gaba da ita zama nayi a gabanshi na zuba mishi abinci ya fara ci, muna hira yana har ya gama cin abincin, ya ce min. "Muje mu ga gidan, idan na gama shekaru takwas, nan zan dawo da ku na zauna part uku ne, daya nawa daya naki daya kuma." "Na Sa'adiyya!" Janyo ni yayi jikinshi yana faɗin. "Saadiya bata cikin matan da xan saka a gidan nan, sannan mata masu daraja xan ajiye anan gidan, daya part din na Hajiyata da Yarana, Hajiya tayi wahala damu, duk da bata zauna da mu ba amma tayi dawainiyya damu a zuciyarta, ban gane haka ba sai da kika bar min Yaran nan a gadon asibiti, na fahimci kukan yaran da yadda nayi ta kukan niman a gaji ban samu ba, ranar nayi nadama amma ban san nayi ba sai daga baya. Kin zame mini Futu'atulkhair! A duk lokacin da nayi wani abu na tuna zan gan kin zame min Qurratul-Ayn, Ummu Hadiyya duniyata ba zata tab'a cika ba sai dake, sai dake sai dake!" Juyawa nayi ina kallonshi. "Ni ba yar kowa ba, ni!" Sumbatar bakina yayi yana rike kaina. Ban san lokacin da na kai hannuna duka biyu na rikon kanshi ba, mun kwashe sama da minti sha biyar kafin ya had'e goshinmu. "Nayi kuskuren da na bari aka yi ta cin zarafinki, ji nake kamar nayi kuka idan na tuna an cutar dake saboda ni, sai naga ashe ban cancanci zama mutum ba, Ummu Hadiyya!" Duk sai na diririce na rasa me ke min dadi, "zaki zauna da ni a haka?" Gyada mishi kai nayi, a hankali ya riko hannuna muka cigaba da zaga gidan. "Hmm! Ban saba barinsu, su daya ba!" "Ok muje mu dauko su!" Haka muka dawo na dauke Mufid ya dauki Mufidah. "Me kike son nayi idan kika dawo?" Kallonshi nayi kafin na sake murmushi na ce mishi. "Duk tsannani duk dad'i kada ka manta da ni da Yaranka da Hajiya tare da Abba muna bukatarka!" Na fada ina kallonshi. "Wannan shine bukatarki?" "Ba bukata bane fata ce idan ka cika min ita, zan yi hakuri akan kome idan ka juya mana baya, zan tafi inda ba zaka kara ganina ba, ko Yaranka tunda mune baka bukata." Riko hannuna yayi sosai. "Kice mutuwata taku kenan?" Girgiza kai nayi ina faɗin. "Ba zaka mutu ba, zan Barka da mutanen da ka zaba ne?" "Idan kuma Hajiya da Abba na zab'a fa!" "Hakkina ne na tayaka musu biyayya!" Jan kumatuna yayi bayan ya cire hannunshi cikin nawa yana faɗin. "ji min wayo, ke da Deen kuna kwashe min lada wallahi!" Murmushi nayi muka cigaba da zaga gidan. "Ummu Hadiyya!" "Na'am!" Na tsaya ina kallonshi. " Ko kin dawo, don Allah kada ki biyewa kowa zamana kike, ba zaman kowa ba sannan kiyi hakuri da duk abinda zaki gani, Ummu Hadiyya nauyi ya karu a kaina. Sannan babu wata first lady sai ke, sai dai maganar gaskiya idan ba dole ba, gaskiya ba zaki na fita ba domin Allah ya gani ina da zafin kishi, iya Deen na yarda zaki na magana da shi, kada ko da wasa na ga kin yi wani magana da Mahmoud raina zai b'aci sosai. Please kada ki zama yadda kowa zai na bada labarin yadda kike, Ummu kishinki nake ji. Gani nake kamar nayi wani sab'o , Ummu idan na ji wani ya fadi suranki ko kwalliyarki wallahi sai na kashe dan banza!" Wani irin tsoro ne ya kama ni, idan ya ji labarin Mahmoud ya tab'a kokarin yi min fyade fa? Janye hannuna nayi baya ina hadiye yawun bakina, ina kara kame hannuna. "Da gaske nake! Ji nake kamar na haukace, ke ba zan barki ki zama kamar sauran matan gwamnoni da zaki ta yawo anyhow Ummu ni Matar gida nake so ba matar ado ba, idan don ado ne ki yi hakuri da kaina zan na shirya mana tafiya, ina sonki a kusa da ni ne, ki bani abinci idan ba dawo gida na samu me ce min Barka da dawowa, ina son idan na kwaso gajiyata ina da wacce zata min tausa. Ko zafin kai da damuwa ina dawowa na samu wacce zata tsaya a kusa dani don Allah ki yi hakuri kada ki ce zaki zabi burgewa a kan nawa rayuwar...... someone is confessing 😜🏃🏻‍♀️.........🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Kada ki ce zaki dauki burgewa akan nawa rayuwar ni da Yarana muna bukatar Uwa a cikin gidan nan, don Allah ki mana alfarman ki zauna a gida, ina matukar kishinki!" Ya fada yana kamo hannuna, ji nayi kamar zan yi kuka wani ya fada min abin da yake ranshi wanin ma Tafida da kamar wuya gurguwa da auren nesa. Kasa magana nayi ya kai ni wani daki yana faɗin. "Wannan shine dakina, yayi kyau ko na sauya domin dakuna uku ne a nan bangaren, naki dakuna hudu saboda baki da wasu laluran. Bangaren dayan kuma akwai dakuna uku shima kamar nawa." "Duk yaushe ka yi gidan nan?" Hannunshi ya kai gefen fuskata. Yana murmushi ya ce talla aka kawo min lokacin muna abuja, shine na gayawa Deen ya shi kuma ya gayawa Abba. Kafin na turo kudin ma Abba ya biya sai na maidawa Abba kudinsa, amma kin san me? Ko da aka zo saka sunan mamallakin gidan Abba sunanki ya saka." Murmushi nayi sai na kasa magana, ya fito dani zuwa daya dakin yana cewa. "Duk wani abu na gidan Deen ya zuba min su." "Saboda baka da lokaci ne?" Gyada min kai yayi yana jan hancina. "Bani da lokacin da xan zauna nayi ta wannan aikin, shi da Matarshi da kanwarshi Jalilah suka min wannan aikin." Murmushi yayi yana faɗin. "Ina tsoron kada wata rana na juyawa Deen baya." "Idan haka ya faru zai maka uzuri! Domin shi ma'abocin uzuri ne!" Murmushi yayi wanda tunda muka fara zaga gidan shine akan fuskarshi, muna gama zaga cikin gidan ya ce min. "Muje ki ga bangarenki!" "Na gaji sallah isha zan yi na kwanta jikina duk ciwo yake!" "Wai ki ce zan yi tausa kenan?" Ya fada yana kashe min ido daya, parlourn muka dawo muka shimfida abin sallah, ya shiga bandakin parlour yayi alola nima anan nayi alola, shi ya jamu sallah isha da tarawee, muna idarwa na kasa hakuri nace mishi. "Kayi sauka ne kai ma?" Saboda yadda yake jan kira'a. Addu'a ya shafa yana faɗin. "Eh nayi na fara a Nijeriya zuwana Sudan Deen ya saka ni a gaba sai da na hada sittin hankalinsa ya kwanta. " "Gaskiya ya kyauta mana!" Jan kumatuna yayi yana faɗin. "kwarai kuwa ya kyauta min tunda Allah ya haɗa ni da Hafiza!" Janyo ni yayi muka kwanta a parlourn ina jikinshi kwance. D'ago kai nayi ina kallonshi. "Yan mata bar kallona, ni naki ne duk wacce zata zo tow sudinki zata samu;" rufe fuskana nayi a kirjinshi ina dariya. "Naji kamshin turaren Tina a jikinki dazun gaya min yadda kika gudu daga garina." A hankali na warware mishi kome, murmushi yayi yana faɗin. "Yarinyar nan baki da tausayi!" Ya tashi zaune, "Ni sau nawa ka tausaya min?" Na tambaye shi, "kishin yadda Abba yake sonki, yake kuma damuwa da ke yasa ni jin haushi, taya ni da ya dace ya bawa kulawa ya koma nawa Yar mage kulawa!" Ya fada ina kallonshi. "Ni ce ma mage?" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Yes ke magena ce, idan ban yi kishin magena ba waye zan yi kishi. Ke magena ni muzurunki!" Ya fada yana rungume ni, dariya nayi ina kara k'amkame shi. "yaushe zaki min dambu ne?" Kallon bakinshi nayi na matsa a hankali na kai bakina, janyo ni nayi na zauna a jikinshi muna fuskarta juna. "Duk lokacin da kake bukata kazo ka ɗauka." Bakina ya kama da hakorinsa. A hankali ya sake yana faɗin. " Ba zata zaki min kuka ne kamar crybaby!" "Dake ka saba ganin kuka a idanuna ba!" Wayarshi ce tayi ƙara ya duba Mahmoud ya gani dauka yayi yana faɗin. "ya dai?" "Tafida dama na kira ne zamu zo da madam ku gaisa!" "Bana nan wallahi idan na dawo zan gaya maka sai ku zo mu sha ruwa tare" "ok na gode amma kana ina ne?" *Ka koyi boye mana kome hatta ni bana bukatar sanin privacy dinka!* inji Deen ya gaya mishi. "Eh tow bana kusa gaskiya!" "Tow ba damuwa, ko kana tare da yar baka ce?" "Me kace?" Ya tambaye shi a fusace. "yar baka nace ko kana tare da ita ne?" "Daga yau kada na kara jin ka ambaci Ummu da wanann sunan, Mata ta ce kuma Uwar Yarana, idan kuma ka sake raina zai b'aci zan yi hukunci." "Tow kayi hakuri na ga dai a bakinka naji!" "Eh a bakina ka ji na tab'a aibanta matarka? Ko na tab'a baka shawara ka cutar da ita?" "Tafida kayi hakuri ban san ranka zai b'aci ba, amma yaushe ka fara sonta?" Wani ashar ya lailayo ya maka mishi take ya kashe wayar domin Allah ya gani yana bala'in shakkar Tafida. Jifa da wayar yayi, na bi wayar da sauri na dauko ina faɗin. "Ji kamar an ce min yar wuta." Na shiga duba wayar ina kallonshi. "ka godewa Allah da wayar bata fashe ba!" Na mika mishi wayar ina rike hannunshi, shafa bayan hannun nake. "Kada ka damu tun ina Yarinyar na taso da kushen mutane, wannan ba sabon abu ba ne." "Ummu idan baki yafe min ba Allah sai ya kona ni!" "Ba zai kona ni saboda na bawa kare da dokin damar cin zarafinki." Kwantar da kaina nayi a gefen kafadarshi, ina murmushi. Na fahimci Tafida ya sauya sosai, amma tijara yana nan babu abinda ya bari, wurin sha daya na dare ya haɗawa Yaran madara, muka basu, sannan nayi musu wanka da ruwan dumi. Kafin muka wuce dakin na kwantar da su, ban daki ya shiga ya jima kafin ya fito daure da Towel. "Taso muje!" "A'a jeka kawai!" Zuwa yayi ya dauke ni cak, sai ban dakin, ya sauke ni yana faɗin. "Kina tsammanin zaki kwanta min a haka ne!" Kayan ya shiga cire min, yana faɗin. "Malama babu bakin magana ne!" Ya cire rigar ya ajiye can gefe, sai pant da bra! Juyo ni yayi na rufe idanuna. "Cancadi, wannan bra din yayi min kyau, gaskiya ina son irinsu." Ya kai hannu yana ɓalle pin din. Ni dai bance mishi kome ba yana gamawa ya kai hannun kan abin da yake jan hankalinsa. (😡😒 Ni rashin mutuncin Tafida ya fara isata.) Ban iya lokacin da muka dauka a banɗakin ba, amma tabbas naji kamar yau na fara haduwa da d'a namiji, koda muka dawo daki sha biyu ta wuce, a bangaren Tafida kuwa tunda muka dawo dakin, ya makale min domin ba zance wani abu, ina jin labarin ayu amma yau naga makwafin ayu. Ban san yadda xan fada ba, amma tunda ya manne min bawan Allah nan daga ni har shi idanunmu biyu har aka kira sallah farko. Yana makale a jikina yana jin kamar zan kwace na gudu. A hankali yake bin kome tun kiran sallah farko, farko yake jan tafiyar a hankali cikin sanyi da kulawa, ban tab'a sanin halinshi na zahiri ba sai yau, yau ya fito min a mutum dinsa, na kuma fahimci waye shi. Kallon fuskarshi nayi cikin rawan murya na ce mishi. "Yallabai!" Bude idanunshi da suka ji ja ya zuba min. "asuba tayi kada mu rasa sahur!" Kamar dama jiran maganata yake kafin na rufe baki ya shiga aikin da ban san yana da karfin yinsa ba. Ni dai a hannunshi na ji a jikina, sai da na fashe da kuka saboda yadda ya fita hayacinsa haka yasa ni jin kamar Tafida baya mu'amalar aure da Sa'adiyya, domin da yanayi da kuzarinsa ba xai yi yawa kuma ya dauki lokaci haka ba, sai da muka kusan makara ya kyale ni, kasa tafiya nayi domin kafaffuna kamar ba zasu dauke ni ba, haka ya riko ni zuwa banɗaki nayi wanka asalima zama nayi cikin ruwan dumin, a gurguje na fito na samu ya hada min tea mika min yayi da zafi-zafi na sha sannan ya ce min! "Sannu kin ji!" Dake ina bakin gadon daure da towel, kasa kallonshi nayi ina gama sha ya mika min farfesun jiya, kafin ya wuce yayi wanka sannan ya fito shima yayi sahur. Ganin ina bawa Yaran nono ya dawo bayana ya zauna tare da saka hannunshi dukka biyu a kasan cikina. "Ina tumbin?" Murmushi nayi nace mishi. "Ya koma!" Shiru yayi kafin ya sumbaci dokin wuyata. Muna zaune a wurin aka sake kiran sallah, amsa Mufid yayi ya kwantar da shi sannan ya amshi Mufidah ma, kafin ya ciro min doguwar rigana, muka yi raka'atul fijr. Muna idarwa ana shiga sallah asuba, a tare muka yi sallah, bayan mun idar mun jima muna addu'a, da azkar sai da rana ya fara fitowa na rarrafa domin sai yanzu na ji kafar ya min tsami. Gadon na hau na kwanta don wallahi jikina ciwo yake, musamman yadda ya makale yaki kome don rashin kirki, na juya xan harare shi. Ware idanun yayi yana faɗin. "me nayi kuma ake hararana da alamu ana zagina a rai kenan, tow na yafe miki, yar aljannata!" Kwanciya nayi ya dawo bakin gadon ya zauna tare da rike hannuna yana murzawa, murmushi muke sakarwa juna, a hankali barci yayi gaba da ni, shima gadon ya hau ya kwanta a bayana, tare da janyo ni jikinshi. Ban da azumi babu abin da zai hana shi komawa ruwa shi ya san abin da ya ji ya kuma tab'a ya ji. A hankali shima barci yayi gaba da shi, wato ranar Tafida tun kafin yau ya mikawa Deputy koma ya ce mishi sai Monday. *** A bangaren Mama tunda ta sauka ta kira uwani suka gaisa ta ce mata. "Ina Ummu!" "Yaronta bai da lafiya, sun kai shi asibiti ita da Deen wayarta kuma kin san tun tafiyarta ta saba barin shi a gida!" "Tow Masha Allah idan na samu lokaci zan na kiranku, yanzu lokaci ne na ibada a kwanakin karshe xan mika lamarin Ummu da naku ga Ubangiji, in sha Allah kafin na dawo zan yi addu'a sosai Ubangiji ya kawo miki miji na gari mijin marainiya kin ji Uwanina!" "Tow Uwata sai kin dawo Allah ya baki ikon mana addu'a!" Suka yi sallama. Mama tana son Uwani sosai irin so na gaskiya nan takewa Uwani yarinyar ma tana son Mama. Haka Mama da ta kira Baba Bulama shima ya gaya mata ai Ummu danta bai da lafiya ne, ganin duk bakinsu daya yasa Mama ta yarda, bata san cin amanarta suka yi ba. *** Karfe daya da rabi na farka, na samu yaran an musu wanka sai wasa suke da junansu, idan ba mafarki ba ina ga har nono Tafida ya ciro ya basu amma dake barci ya ci karfina ban iya bude idanun ba. "sleep beauty!" Make hannunshi nayi ina faɗin. "Kai da Yaranka sai da kuka shanye min nono ko?" Na fada ina gyara zaman rigar jikina. "Ayya sun tashi na rasa yadda xan yi shi ne na gyara ki na basu kowanne ya kama, suna gama sha na dama masu madara suka sha, kin ga har wanka nayi musu!" "Yaushe ka dawo Nanny!" "Taso na hada miki ruwan wanka kin ji!" Tashi nayi na ga yaran aka wani abin wasan Yara. Yana tsaye yana kad'awa Mufidah da take bangala mishi baki, na zo na rungume shi ta baya, karatu Tinah. "Good afternoon My Yallabai!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin. "Qurratul-Ayn! Kin tashi lafiya?" Juya mishi idanun nayi na wuce banɗaki, na leko yana tsaye inda na barshi. "Baby bani jakata akwai brush da toothpaste!" "Akwai sabi na bude mana!" Murmushi nayi na ce mishi. "Ban gani ba!" "Don Allah ki rike wannan muryan taki, wallahi ban shirya yin sittuna ba!" Ya shigo ban dakin ya dauka tare da matsa min. "fita kafin ka karya mana azumi!" Na fada a sanyaye. "Idan aka ga na suma kece wallahi!" Murmushi nayi na rufe ban dakin nayi wanka sosai, sannan na fito, shi da Yaranshi suna can parlour, na gyara jikina kafin na fito, muryanshi da naji da Deen yasa na koma dakin, sai kuma na saka Babban hijab na fito na gaishe da Deen, sai Hararata yake yana faɗin. "Ke bana ce kada ki fito ba!" "Ka ji guntun dan iska, ita Kanwata ce yayar Jalila ce, ka saka Ammah ce ta haife ta dan iska kawai! Ummu ina fatan bai miki kome ba ko?" Ya tambaye shi yana nad'e hannun rigarshi. Dariya suka bani na girgiza kai ina faɗin. "Bai min kome ba! Ya Sadika tana lafiya ta kusan sauka kan yanzu ko!" "Eh wallahi ina kyautata zaton karshen watan ko farkon sabon wata!" "Allah ya raba lafiya! Yallabai kitchen nake son shiga na maka aikin kafin na tafi!" "Ba fa zaki tafi yau ba, sai wata sati!" Rufe bakina nayi da hannayena, wani irin tsoron Mama ya dirka min kamar an wurgo dutse daga sama. "Ka rufa min asiri!" Murmushi yayi ya ce min. "Allah da gaske wayar mana na saka an sace shi a can Saudiya amma fa za a dawo mata da shi, kiyi hakuri Alhaji Bulama da Babanki sun sani, hankalin Mama ya kasu gida biyu tana ibada kuma kafin faruwar haka tayi waya da Mijinta da kuma Uwani, ki fahimci wani abu ina son mu kasance tare shi yasa na zabi haka amma kiyi hakuri da abin da nayi, wallahi bani da zabi ne ina son na zauna da ke na wasu kwanaki kafin ta dawo Please!" Hawaye ne ya zubo min. "Yanzu kawai don ka zauna da ni sai ka sakata a zullumi bata yi magana da kowa ba." "Mama ba irin sauran iyaye ba ne, Mama tayi magana da kowa kafin na saka.aka dauke wayar amma bari Deen ja ce yarinyar ta maida mata wayarta." Juyawa nayi zan koma dakin ya ce min. "Ki shirya zan mai dake gidan!" Yadda yayi maganar sai naji hankalina ya tashi, haka na wuce dakin na zauna ina jin kuka yana zuwa min. "Kana burge ni Tafida, kai tsaye kake lamarinka. Na ji dadi da kake fadar gaskiya ba ƙaramin aiki bane fadarta." "Deen tafiya zata yi fa!" "Ba zata tafi ba, yanzu ka je kace ta shirya zaka fita. Sallah juma'a zaka ajiye ta a gidansu!" Ya kuwa mike, ya nufi dakin Deen sai dariya yake mishi yana wasa da Yaran kaunar da yakewa Iyayen Yaran ya shafi yaran sosai, don yana jinsu kamar na shi. A bakin gadon na zauna ina shashekar kuka, domin nasan ba wani sauyawan da yayi, yayi min laifi kamata yayi yazo ya rarrashe ni amma yace wai na shirya zai ajiye ni a gida, wato yaci moriyar ganga, duk sai naji na tsani kaina da ban biyo shi ba da ba zai min haka ba, haka na cigaba da kuka, ban kawo a raina zai zo din ba sai gashi ya turo kofar, wani irin sanyi naji ya tsirga min, na d'ago kai ina kallonshi shima kallona yaƙe. "Allah ya huci zuciyarki, nayi laifi a yafe min dama can ni tsohon mai laifi ne, kuma na kara aikata bayan laifi ayi hakuri ba zan kuma ba." Ban kalle shi ba, na cigaba da share kwalla da yake zuba min, "Tow tunda ba zaki min magana ba, bari na hada kayanki na kai ki gida!" "Dama ka kawo ni ne ka min koran kare!" *Yes i hit the point!" Narke min yayi cikin rarrashi ya ce min. "a'a tashi na kai ki gida don Allah, wannan abin da nayi ina jin kunyar kallon idanunki!" Ya fada yana me durkusawa a gabana ya zuba hannunshi akan cinyoyina. "Ni dai kada garin son zama dani kayi ta aikata kuskure bayan kuskure, ka rufa min asiri kada kayi wani abin da zai tab'a rayuwarmu bakiɗaya." Na fada ina kuka, "ita mahaifiyata ce, dole naji wani abu na ga kamar ba sona kake ba, dama can na san Babu so kawai muradi ne ta zuciya...." hannunshi ya saka ya rufe min bakina. "Don Allah ki daina fadar haka wallahi bana jin dadi, nima Uwata ce, yanzu haka na saka za a maida mata wayarta ba zan kara wasa da rayuwar wani saboda ke ba, amma kiyi hakuri ba zan kara ba kin ji!" Gyada kai nayi ina share hawayen da yake zuba min. "Kiyi hakuri xan tafi sallah kada na makara!" "Allah ya tsare muje na tayaka shirya." Gaban closed din shi muka nufa na cire mishi wani babban kaya shadda ce fara sal, sai hular da zai haka da kayan, sai takalmi da links zamana da shi a abuja, baya saka babban kaya dai ranar Juma'a. Amma kusa na haddace shigarshi. Yadda yaga ina taya shi saka kayanshi ba tare da na damu ba, ya ce min."Ina tunanin ko idan kika dawo na barki a nan ne ba sai kin je government house!" Shafa kumatunshi nayi ina faɗin. "Duk yadda kace yallabai na!" Jan hancina yayi yana faɗin. "An gama yarinyar nan hancinki Mufid ya dauka. Mufidah nawa!" Ya fada yana haɗe rai. Dariya nayi ina faɗin. "Kuma laifi ne don haka ya faru?" "Kawai dai kishi nake da kika raba shi Abba ya dauki hancinki Ita Uwata kika barta da irin nawa hancin!" "Ba ka ga yadda yaran suka zamo kalanka ba!" "Hmm kuma haka ne kin fini gaskiya!" Ya fada yana rike hannuna, "ki so ni koda dan ne, ni dai nasan ina miki mahaukacin so ne! Ummu Hadiyya ina sonki sosai, irin son da nake jin ban yiwa kowa irinsa ba." Girgiza kai nayi ina faɗin. "'Lokaci yana tafi kace fada zaka je sallah!" "Eh anan nake zuwa tunda na zama gwamnanku!" Jan kumatunshi nayi ina faɗin. "Ka kyauta!" "Gobe asabar zamu shiga Biu ki shirya da wuri fa." Kallenshi nayi kafin na ce mishi. "Gobe kace amma kana ce min na shirya da wuri!" Na fada ina yaƙe. Mika mishi hular da yake hannuna nayi ya kansa ya kafa, wurin turaren shi na nufa na ciro na fara fesa mishi yana murmushi. "Na gode zan tafi mai xan sayo miki!" "Duk abin da ka gani ya maka kyau ina so nima zan min kyau!" "Hmm ji nake kamar kada na tafi!" "Muje maza Yayana yana jiranka, ka wani bar mishi renon Yaranka!" Muka fito ina gefenshi, "Nanny sannu da kokari ka ji!" "Kam uban can ni ne Nanny?" Deen ya fada da karfi yana nuna kanshi. "Lallai tafiya daga dan iska sai kai, a rashin mutunci ni zaka kalli tsabar idanuna kace min Nanny ka ɗauke ni dan daudu ne!" Yadda Deen yake tijara sai naga sam haka bai damu Tafida ba, asalima sumbatar goshin yaran yayi yana faɗin. "Kuyi hakuri Abbanku yana ta ihu, sai na dawo Yarann Daadi da Abba! Idan ka gama basu dariya muje don Allah!" Wayarshi ce tai ƙara ya kalla yana sake tsaki yayi ya ce. "Deen ya zan yi da Asiya ne?" "Ina ruwan sly Queen!" Juyowa yayi ya kalle ni, "wata cousin dina ce!" " ka gaya mata me kama fatalwa kin san an bashi mace dan iska ya ce baya so!" "Deen kada ka ja min bala'i don Allah!" "Yaya Deen kace dama can amanata kuke ci?" "A'a ban dani dan iska dai yake cin amanarki!" Ya nuna tafida da hannu, "Ka aurota!" Na fada zan juya, "Ni fa ba dan iska ba ne, kuma abu daya gare ni kin ga ya wuce daya ne? Da zaki ce na aurota!" "Yallabai ko bance ka aurota ba, wajibi ne auren mata sama da daya, Allah ya baka budi da rufin asiri in dai ba son zuciya ba, ai kana da damar rike mu mata hudu!" "Ummu Hadiyya ki fita idanuna na rufe. Auren ce miki aka yi da sauki ne da shi da zan rike mace sama da daya Hadiyya ki fito Ki gaya min bakya bukatar zama da ni mana!" Murmushi nayi na wuce shi don nasan ya cika haka suka fita, a waje ya amsa wayar yana me bude mata tsohon littafinsa na tijara, jin tana kuka yasa shi sasauatawa ya tambaye ta me ya faru, bai karasa ji ba ya kashe wayar ya nufi massalaci yana zargin Deen da hada mishi husuma me Deen zai yi ban da dariya. Bayan fitarsu nayi alola na zo nayi sallah, sannan na kunna wayata na kira Uwani na gaya mata ba zan dawo ba, ta ce min ai Baba ya gaya mata. Murmushi nayi sannan na kashe wayar na ja Yarana muka shiga kitchen, mamakin yadda aka zuba kome na zamani nayi, ina cikin aiki wurin karfe biyu da arba'in da biyar, ya kira ni. "Ummu Hadiyya! Akwai matsala!" "Ina tare da kai babu wata matsala gaya min me nene?" Daga can na ji Deen yana faɗin. "wallahi billahi azim ba zata zauna a inda Ummu take ba, ka kaita gidan Abba ko ko gidan Hajiya ba zata zauna ba, Ummu tana buƙatar ka kana bukatar Ummu, meye amfanin kebewan da kayi ba don ku huta ba ne, Yaran nan wallahi ban da suna shn mama da na rabaku dasu, ko ka kaita gidan Maryam amma ban da Ummu." "Wai me ke faruwa ne?" Kashe wayar yayi. Mamaki ya kara kamani na kira Tafida, "zan kira ki!" Kashe wayar yayi.. ** A can kuwa Abin da ya faru, Asiyah ta sab'a lamba, domin ta tabo Saadiya a daidai lokacin da take cike da Tafida, abun da ya faru kuwa, tun da Tafida ya bar gidan bai gaya mata zai tafi bude sabon titi a wani kauye ba, take cika take batsewa domin a bakin yan gulmanta take jin labarin, har dare aka sha ruwa babu Tafida, ta kira Deen lokacin yana waya da ya gama ya kashe wayar domin shi dai bai da amsar da zai bata, wurin karfe hudu na asuba kamar ance ta fito ta hango Asiyah ta fito kamar daga ɓangaren Tafida, haka yasa ta kara kallon sosai ganin ta ga sun sake rungumar juna, kafin ta wuce inda take zama, tana ganin ya shiga Mota ya bar gidan. Jikinta yana tsuma kawai ta fito da gudu lokacin Asiya ta shiga bangaren da take ta rufe kofarta, komawa tayi ta shirya har karfe daya na rana Asiya bata fito ba, sai wurin karfe biyu ta fito. Ai kuwa Sa'adiyya tayi wuf da ita tayi ta bugata da kasa, tana bata kashi. Sannan ya yakushe mata fuska tana ihu karuwa kwartuwa me bin mijin wasu. Yadda kuka san mahaukaciya haka aka dauke Sa'adi baby akan Asiyah, duk abin ba dadin gani. Da ta samu ta shige dakinta ta kira Tafida tana kuka, shiri tayi amma bata zata wannan me kalar samudawan zata mata mugun duka haka ba, sai gashi ta yakushe mata fuska, sai da tayi kukan bakin ciki, bayan sallah juma'a Tafida yazo gidan ganin har lokacin Sa'adiyya tana ihun sai ta kashe Asiyah yasa Tafida kallon Deen. "Ku sake ta ku je!" Suna barin wurin ya nufeta. Aikuwa farar shaddan jikinshi ta damke wuyar rigarsa da ta yaga har kasa. "gaya min me nayi maka zaka ci amanata, ashe karuwa ka ajiye a gidanka, shine ka hanani hakkina, wallahi ba zan yarda ba muje ka bani hakkina nima na haihu kamar Ummu." "Kin ga nan ba kamar da can baya bane, ko ina akwai jami'an tsaro Please mu shiga daga cikin gidan!" Dake tana ganin girman Deen haka suka shiga rarrashinta da tambayar me ya faru bakincikin ya hanata fadar abin da ya faru sai kuka da rantsuwar matukar bai d'aga Asiyah a gidan ba zai samu gawarta, dakyar Deen ya kwantar da rigimarta, sannan yazo ya ga Asiyah sai da yaji babu dad'i. Yarinyar fuskarta ya kumbura. Shine yake tunanin ya kawo ta wurin Ummu ta yi jinya, Deen yace karya kenan. Ba zai yiwu lokacin da ya samu zai kula da kanshi da iyalinsa yace zai karawa kanshi yan sa'ido ba, don haka yasan yadda zai yi da ita...... #Tafida #Deen #Ummu #Sa'adiya #Asiyah #Mahmoud🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Kada ki ce zaki dauki burgewa akan nawa rayuwar ni da Yarana muna bukatar Uwa a cikin gidan nan, don Allah ki mana alfarman ki zauna a gida, ina matukar kishinki!" Ya fada yana kamo hannuna, ji nayi kamar zan yi kuka wani ya fada min abin da yake ranshi wanin ma Tafida da kamar wuya gurguwa da auren nesa. Kasa magana nayi ya kai ni wani daki yana faɗin. "Wannan shine dakina, yayi kyau ko na sauya domin dakuna uku ne a nan bangaren, naki dakuna hudu saboda baki da wasu laluran. Bangaren dayan kuma akwai dakuna uku shima kamar nawa." "Duk yaushe ka yi gidan nan?" Hannunshi ya kai gefen fuskata. Yana murmushi ya ce talla aka kawo min lokacin muna abuja, shine na gayawa Deen ya shi kuma ya gayawa Abba. Kafin na turo kudin ma Abba ya biya sai na maidawa Abba kudinsa, amma kin san me? Ko da aka zo saka sunan mamallakin gidan Abba sunanki ya saka." Murmushi nayi sai na kasa magana, ya fito dani zuwa daya dakin yana cewa. "Duk wani abu na gidan Deen ya zuba min su." "Saboda baka da lokaci ne?" Gyada min kai yayi yana jan hancina. "Bani da lokacin da xan zauna nayi ta wannan aikin, shi da Matarshi da kanwarshi Jalilah suka min wannan aikin." Murmushi yayi yana faɗin. "Ina tsoron kada wata rana na juyawa Deen baya." "Idan haka ya faru zai maka uzuri! Domin shi ma'abocin uzuri ne!" Murmushi yayi wanda tunda muka fara zaga gidan shine akan fuskarshi, muna gama zaga cikin gidan ya ce min. "Muje ki ga bangarenki!" "Na gaji sallah isha zan yi na kwanta jikina duk ciwo yake!" "Wai ki ce zan yi tausa kenan?" Ya fada yana kashe min ido daya, parlourn muka dawo muka shimfida abin sallah, ya shiga bandakin parlour yayi alola nima anan nayi alola, shi ya jamu sallah isha da tarawee, muna idarwa na kasa hakuri nace mishi. "Kayi sauka ne kai ma?" Saboda yadda yake jan kira'a. Addu'a ya shafa yana faɗin. "Eh nayi na fara a Nijeriya zuwana Sudan Deen ya saka ni a gaba sai da na hada sittin hankalinsa ya kwanta. " "Gaskiya ya kyauta mana!" Jan kumatuna yayi yana faɗin. "kwarai kuwa ya kyauta min tunda Allah ya haɗa ni da Hafiza!" Janyo ni yayi muka kwanta a parlourn ina jikinshi kwance. D'ago kai nayi ina kallonshi. "Yan mata bar kallona, ni naki ne duk wacce zata zo tow sudinki zata samu;" rufe fuskana nayi a kirjinshi ina dariya. "Naji kamshin turaren Tina a jikinki dazun gaya min yadda kika gudu daga garina." A hankali na warware mishi kome, murmushi yayi yana faɗin. "Yarinyar nan baki da tausayi!" Ya tashi zaune, "Ni sau nawa ka tausaya min?" Na tambaye shi, "kishin yadda Abba yake sonki, yake kuma damuwa da ke yasa ni jin haushi, taya ni da ya dace ya bawa kulawa ya koma nawa Yar mage kulawa!" Ya fada ina kallonshi. "Ni ce ma mage?" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Yes ke magena ce, idan ban yi kishin magena ba waye zan yi kishi. Ke magena ni muzurunki!" Ya fada yana rungume ni, dariya nayi ina kara k'amkame shi. "yaushe zaki min dambu ne?" Kallon bakinshi nayi na matsa a hankali na kai bakina, janyo ni nayi na zauna a jikinshi muna fuskarta juna. "Duk lokacin da kake bukata kazo ka ɗauka." Bakina ya kama da hakorinsa. A hankali ya sake yana faɗin. " Ba zata zaki min kuka ne kamar crybaby!" "Dake ka saba ganin kuka a idanuna ba!" Wayarshi ce tayi ƙara ya duba Mahmoud ya gani dauka yayi yana faɗin. "ya dai?" "Tafida dama na kira ne zamu zo da madam ku gaisa!" "Bana nan wallahi idan na dawo zan gaya maka sai ku zo mu sha ruwa tare" "ok na gode amma kana ina ne?" *Ka koyi boye mana kome hatta ni bana bukatar sanin privacy dinka!* inji Deen ya gaya mishi. "Eh tow bana kusa gaskiya!" "Tow ba damuwa, ko kana tare da yar baka ce?" "Me kace?" Ya tambaye shi a fusace. "yar baka nace ko kana tare da ita ne?" "Daga yau kada na kara jin ka ambaci Ummu da wanann sunan, Mata ta ce kuma Uwar Yarana, idan kuma ka sake raina zai b'aci zan yi hukunci." "Tow kayi hakuri na ga dai a bakinka naji!" "Eh a bakina ka ji na tab'a aibanta matarka? Ko na tab'a baka shawara ka cutar da ita?" "Tafida kayi hakuri ban san ranka zai b'aci ba, amma yaushe ka fara sonta?" Wani ashar ya lailayo ya maka mishi take ya kashe wayar domin Allah ya gani yana bala'in shakkar Tafida. Jifa da wayar yayi, na bi wayar da sauri na dauko ina faɗin. "Ji kamar an ce min yar wuta." Na shiga duba wayar ina kallonshi. "ka godewa Allah da wayar bata fashe ba!" Na mika mishi wayar ina rike hannunshi, shafa bayan hannun nake. "Kada ka damu tun ina Yarinyar na taso da kushen mutane, wannan ba sabon abu ba ne." "Ummu idan baki yafe min ba Allah sai ya kona ni!" "Ba zai kona ni saboda na bawa kare da dokin damar cin zarafinki." Kwantar da kaina nayi a gefen kafadarshi, ina murmushi. Na fahimci Tafida ya sauya sosai, amma tijara yana nan babu abinda ya bari, wurin sha daya na dare ya haɗawa Yaran madara, muka basu, sannan nayi musu wanka da ruwan dumi. Kafin muka wuce dakin na kwantar da su, ban daki ya shiga ya jima kafin ya fito daure da Towel. "Taso muje!" "A'a jeka kawai!" Zuwa yayi ya dauke ni cak, sai ban dakin, ya sauke ni yana faɗin. "Kina tsammanin zaki kwanta min a haka ne!" Kayan ya shiga cire min, yana faɗin. "Malama babu bakin magana ne!" Ya cire rigar ya ajiye can gefe, sai pant da bra! Juyo ni yayi na rufe idanuna. "Cancadi, wannan bra din yayi min kyau, gaskiya ina son irinsu." Ya kai hannu yana ɓalle pin din. Ni dai bance mishi kome ba yana gamawa ya kai hannun kan abin da yake jan hankalinsa. (😡😒 Ni rashin mutuncin Tafida ya fara isata.) Ban iya lokacin da muka dauka a banɗakin ba, amma tabbas naji kamar yau na fara haduwa da d'a namiji, koda muka dawo daki sha biyu ta wuce, a bangaren Tafida kuwa tunda muka dawo dakin, ya makale min domin ba zance wani abu, ina jin labarin ayu amma yau naga makwafin ayu. Ban san yadda xan fada ba, amma tunda ya manne min bawan Allah nan daga ni har shi idanunmu biyu har aka kira sallah farko. Yana makale a jikina yana jin kamar zan kwace na gudu. A hankali yake bin kome tun kiran sallah farko, farko yake jan tafiyar a hankali cikin sanyi da kulawa, ban tab'a sanin halinshi na zahiri ba sai yau, yau ya fito min a mutum dinsa, na kuma fahimci waye shi. Kallon fuskarshi nayi cikin rawan murya na ce mishi. "Yallabai!" Bude idanunshi da suka ji ja ya zuba min. "asuba tayi kada mu rasa sahur!" Kamar dama jiran maganata yake kafin na rufe baki ya shiga aikin da ban san yana da karfin yinsa ba. Ni dai a hannunshi na ji a jikina, sai da na fashe da kuka saboda yadda ya fita hayacinsa haka yasa ni jin kamar Tafida baya mu'amalar aure da Sa'adiyya, domin da yanayi da kuzarinsa ba xai yi yawa kuma ya dauki lokaci haka ba, sai da muka kusan makara ya kyale ni, kasa tafiya nayi domin kafaffuna kamar ba zasu dauke ni ba, haka ya riko ni zuwa banɗaki nayi wanka asalima zama nayi cikin ruwan dumin, a gurguje na fito na samu ya hada min tea mika min yayi da zafi-zafi na sha sannan ya ce min! "Sannu kin ji!" Dake ina bakin gadon daure da towel, kasa kallonshi nayi ina gama sha ya mika min farfesun jiya, kafin ya wuce yayi wanka sannan ya fito shima yayi sahur. Ganin ina bawa Yaran nono ya dawo bayana ya zauna tare da saka hannunshi dukka biyu a kasan cikina. "Ina tumbin?" Murmushi nayi nace mishi. "Ya koma!" Shiru yayi kafin ya sumbaci dokin wuyata. Muna zaune a wurin aka sake kiran sallah, amsa Mufid yayi ya kwantar da shi sannan ya amshi Mufidah ma, kafin ya ciro min doguwar rigana, muka yi raka'atul fijr. Muna idarwa ana shiga sallah asuba, a tare muka yi sallah, bayan mun idar mun jima muna addu'a, da azkar sai da rana ya fara fitowa na rarrafa domin sai yanzu na ji kafar ya min tsami. Gadon na hau na kwanta don wallahi jikina ciwo yake, musamman yadda ya makale yaki kome don rashin kirki, na juya xan harare shi. Ware idanun yayi yana faɗin. "me nayi kuma ake hararana da alamu ana zagina a rai kenan, tow na yafe miki, yar aljannata!" Kwanciya nayi ya dawo bakin gadon ya zauna tare da rike hannuna yana murzawa, murmushi muke sakarwa juna, a hankali barci yayi gaba da ni, shima gadon ya hau ya kwanta a bayana, tare da janyo ni jikinshi. Ban da azumi babu abin da zai hana shi komawa ruwa shi ya san abin da ya ji ya kuma tab'a ya ji. A hankali shima barci yayi gaba da shi, wato ranar Tafida tun kafin yau ya mikawa Deputy koma ya ce mishi sai Monday. *** A bangaren Mama tunda ta sauka ta kira uwani suka gaisa ta ce mata. "Ina Ummu!" "Yaronta bai da lafiya, sun kai shi asibiti ita da Deen wayarta kuma kin san tun tafiyarta ta saba barin shi a gida!" "Tow Masha Allah idan na samu lokaci zan na kiranku, yanzu lokaci ne na ibada a kwanakin karshe xan mika lamarin Ummu da naku ga Ubangiji, in sha Allah kafin na dawo zan yi addu'a sosai Ubangiji ya kawo miki miji na gari mijin marainiya kin ji Uwanina!" "Tow Uwata sai kin dawo Allah ya baki ikon mana addu'a!" Suka yi sallama. Mama tana son Uwani sosai irin so na gaskiya nan takewa Uwani yarinyar ma tana son Mama. Haka Mama da ta kira Baba Bulama shima ya gaya mata ai Ummu danta bai da lafiya ne, ganin duk bakinsu daya yasa Mama ta yarda, bata san cin amanarta suka yi ba. *** Karfe daya da rabi na farka, na samu yaran an musu wanka sai wasa suke da junansu, idan ba mafarki ba ina ga har nono Tafida ya ciro ya basu amma dake barci ya ci karfina ban iya bude idanun ba. "sleep beauty!" Make hannunshi nayi ina faɗin. "Kai da Yaranka sai da kuka shanye min nono ko?" Na fada ina gyara zaman rigar jikina. "Ayya sun tashi na rasa yadda xan yi shi ne na gyara ki na basu kowanne ya kama, suna gama sha na dama masu madara suka sha, kin ga har wanka nayi musu!" "Yaushe ka dawo Nanny!" "Taso na hada miki ruwan wanka kin ji!" Tashi nayi na ga yaran aka wani abin wasan Yara. Yana tsaye yana kad'awa Mufidah da take bangala mishi baki, na zo na rungume shi ta baya, karatu Tinah. "Good afternoon My Yallabai!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin. "Qurratul-Ayn! Kin tashi lafiya?" Juya mishi idanun nayi na wuce banɗaki, na leko yana tsaye inda na barshi. "Baby bani jakata akwai brush da toothpaste!" "Akwai sabi na bude mana!" Murmushi nayi na ce mishi. "Ban gani ba!" "Don Allah ki rike wannan muryan taki, wallahi ban shirya yin sittuna ba!" Ya shigo ban dakin ya dauka tare da matsa min. "fita kafin ka karya mana azumi!" Na fada a sanyaye. "Idan aka ga na suma kece wallahi!" Murmushi nayi na rufe ban dakin nayi wanka sosai, sannan na fito, shi da Yaranshi suna can parlour, na gyara jikina kafin na fito, muryanshi da naji da Deen yasa na koma dakin, sai kuma na saka Babban hijab na fito na gaishe da Deen, sai Hararata yake yana faɗin. "Ke bana ce kada ki fito ba!" "Ka ji guntun dan iska, ita Kanwata ce yayar Jalila ce, ka saka Ammah ce ta haife ta dan iska kawai! Ummu ina fatan bai miki kome ba ko?" Ya tambaye shi yana nad'e hannun rigarshi. Dariya suka bani na girgiza kai ina faɗin. "Bai min kome ba! Ya Sadika tana lafiya ta kusan sauka kan yanzu ko!" "Eh wallahi ina kyautata zaton karshen watan ko farkon sabon wata!" "Allah ya raba lafiya! Yallabai kitchen nake son shiga na maka aikin kafin na tafi!" "Ba fa zaki tafi yau ba, sai wata sati!" Rufe bakina nayi da hannayena, wani irin tsoron Mama ya dirka min kamar an wurgo dutse daga sama. "Ka rufa min asiri!" Murmushi yayi ya ce min. "Allah da gaske wayar mana na saka an sace shi a can Saudiya amma fa za a dawo mata da shi, kiyi hakuri Alhaji Bulama da Babanki sun sani, hankalin Mama ya kasu gida biyu tana ibada kuma kafin faruwar haka tayi waya da Mijinta da kuma Uwani, ki fahimci wani abu ina son mu kasance tare shi yasa na zabi haka amma kiyi hakuri da abin da nayi, wallahi bani da zabi ne ina son na zauna da ke na wasu kwanaki kafin ta dawo Please!" Hawaye ne ya zubo min. "Yanzu kawai don ka zauna da ni sai ka sakata a zullumi bata yi magana da kowa ba." "Mama ba irin sauran iyaye ba ne, Mama tayi magana da kowa kafin na saka.aka dauke wayar amma bari Deen ja ce yarinyar ta maida mata wayarta." Juyawa nayi zan koma dakin ya ce min. "Ki shirya zan mai dake gidan!" Yadda yayi maganar sai naji hankalina ya tashi, haka na wuce dakin na zauna ina jin kuka yana zuwa min. "Kana burge ni Tafida, kai tsaye kake lamarinka. Na ji dadi da kake fadar gaskiya ba ƙaramin aiki bane fadarta." "Deen tafiya zata yi fa!" "Ba zata tafi ba, yanzu ka je kace ta shirya zaka fita. Sallah juma'a zaka ajiye ta a gidansu!" Ya kuwa mike, ya nufi dakin Deen sai dariya yake mishi yana wasa da Yaran kaunar da yakewa Iyayen Yaran ya shafi yaran sosai, don yana jinsu kamar na shi. A bakin gadon na zauna ina shashekar kuka, domin nasan ba wani sauyawan da yayi, yayi min laifi kamata yayi yazo ya rarrashe ni amma yace wai na shirya zai ajiye ni a gida, wato yaci moriyar ganga, duk sai naji na tsani kaina da ban biyo shi ba da ba zai min haka ba, haka na cigaba da kuka, ban kawo a raina zai zo din ba sai gashi ya turo kofar, wani irin sanyi naji ya tsirga min, na d'ago kai ina kallonshi shima kallona yaƙe. "Allah ya huci zuciyarki, nayi laifi a yafe min dama can ni tsohon mai laifi ne, kuma na kara aikata bayan laifi ayi hakuri ba zan kuma ba." Ban kalle shi ba, na cigaba da share kwalla da yake zuba min, "Tow tunda ba zaki min magana ba, bari na hada kayanki na kai ki gida!" "Dama ka kawo ni ne ka min koran kare!" *Yes i hit the point!" Narke min yayi cikin rarrashi ya ce min. "a'a tashi na kai ki gida don Allah, wannan abin da nayi ina jin kunyar kallon idanunki!" Ya fada yana me durkusawa a gabana ya zuba hannunshi akan cinyoyina. "Ni dai kada garin son zama dani kayi ta aikata kuskure bayan kuskure, ka rufa min asiri kada kayi wani abin da zai tab'a rayuwarmu bakiɗaya." Na fada ina kuka, "ita mahaifiyata ce, dole naji wani abu na ga kamar ba sona kake ba, dama can na san Babu so kawai muradi ne ta zuciya...." hannunshi ya saka ya rufe min bakina. "Don Allah ki daina fadar haka wallahi bana jin dadi, nima Uwata ce, yanzu haka na saka za a maida mata wayarta ba zan kara wasa da rayuwar wani saboda ke ba, amma kiyi hakuri ba zan kara ba kin ji!" Gyada kai nayi ina share hawayen da yake zuba min. "Kiyi hakuri xan tafi sallah kada na makara!" "Allah ya tsare muje na tayaka shirya." Gaban closed din shi muka nufa na cire mishi wani babban kaya shadda ce fara sal, sai hular da zai haka da kayan, sai takalmi da links zamana da shi a abuja, baya saka babban kaya dai ranar Juma'a. Amma kusa na haddace shigarshi. Yadda yaga ina taya shi saka kayanshi ba tare da na damu ba, ya ce min."Ina tunanin ko idan kika dawo na barki a nan ne ba sai kin je government house!" Shafa kumatunshi nayi ina faɗin. "Duk yadda kace yallabai na!" Jan hancina yayi yana faɗin. "An gama yarinyar nan hancinki Mufid ya dauka. Mufidah nawa!" Ya fada yana haɗe rai. Dariya nayi ina faɗin. "Kuma laifi ne don haka ya faru?" "Kawai dai kishi nake da kika raba shi Abba ya dauki hancinki Ita Uwata kika barta da irin nawa hancin!" "Ba ka ga yadda yaran suka zamo kalanka ba!" "Hmm kuma haka ne kin fini gaskiya!" Ya fada yana rike hannuna, "ki so ni koda dan ne, ni dai nasan ina miki mahaukacin so ne! Ummu Hadiyya ina sonki sosai, irin son da nake jin ban yiwa kowa irinsa ba." Girgiza kai nayi ina faɗin. "'Lokaci yana tafi kace fada zaka je sallah!" "Eh anan nake zuwa tunda na zama gwamnanku!" Jan kumatunshi nayi ina faɗin. "Ka kyauta!" "Gobe asabar zamu shiga Biu ki shirya da wuri fa." Kallenshi nayi kafin na ce mishi. "Gobe kace amma kana ce min na shirya da wuri!" Na fada ina yaƙe. Mika mishi hular da yake hannuna nayi ya kansa ya kafa, wurin turaren shi na nufa na ciro na fara fesa mishi yana murmushi. "Na gode zan tafi mai xan sayo miki!" "Duk abin da ka gani ya maka kyau ina so nima zan min kyau!" "Hmm ji nake kamar kada na tafi!" "Muje maza Yayana yana jiranka, ka wani bar mishi renon Yaranka!" Muka fito ina gefenshi, "Nanny sannu da kokari ka ji!" "Kam uban can ni ne Nanny?" Deen ya fada da karfi yana nuna kanshi. "Lallai tafiya daga dan iska sai kai, a rashin mutunci ni zaka kalli tsabar idanuna kace min Nanny ka ɗauke ni dan daudu ne!" Yadda Deen yake tijara sai naga sam haka bai damu Tafida ba, asalima sumbatar goshin yaran yayi yana faɗin. "Kuyi hakuri Abbanku yana ta ihu, sai na dawo Yarann Daadi da Abba! Idan ka gama basu dariya muje don Allah!" Wayarshi ce tai ƙara ya kalla yana sake tsaki yayi ya ce. "Deen ya zan yi da Asiya ne?" "Ina ruwan sly Queen!" Juyowa yayi ya kalle ni, "wata cousin dina ce!" " ka gaya mata me kama fatalwa kin san an bashi mace dan iska ya ce baya so!" "Deen kada ka ja min bala'i don Allah!" "Yaya Deen kace dama can amanata kuke ci?" "A'a ban dani dan iska dai yake cin amanarki!" Ya nuna tafida da hannu, "Ka aurota!" Na fada zan juya, "Ni fa ba dan iska ba ne, kuma abu daya gare ni kin ga ya wuce daya ne? Da zaki ce na aurota!" "Yallabai ko bance ka aurota ba, wajibi ne auren mata sama da daya, Allah ya baka budi da rufin asiri in dai ba son zuciya ba, ai kana da damar rike mu mata hudu!" "Ummu Hadiyya ki fita idanuna na rufe. Auren ce miki aka yi da sauki ne da shi da zan rike mace sama da daya Hadiyya ki fito Ki gaya min bakya bukatar zama da ni mana!" Murmushi nayi na wuce shi don nasan ya cika haka suka fita, a waje ya amsa wayar yana me bude mata tsohon littafinsa na tijara, jin tana kuka yasa shi sasauatawa ya tambaye ta me ya faru, bai karasa ji ba ya kashe wayar ya nufi massalaci yana zargin Deen da hada mishi husuma me Deen zai yi ban da dariya. Bayan fitarsu nayi alola na zo nayi sallah, sannan na kunna wayata na kira Uwani na gaya mata ba zan dawo ba, ta ce min ai Baba ya gaya mata. Murmushi nayi sannan na kashe wayar na ja Yarana muka shiga kitchen, mamakin yadda aka zuba kome na zamani nayi, ina cikin aiki wurin karfe biyu da arba'in da biyar, ya kira ni. "Ummu Hadiyya! Akwai matsala!" "Ina tare da kai babu wata matsala gaya min me nene?" Daga can na ji Deen yana faɗin. "wallahi billahi azim ba zata zauna a inda Ummu take ba, ka kaita gidan Abba ko ko gidan Hajiya ba zata zauna ba, Ummu tana buƙatar ka kana bukatar Ummu, meye amfanin kebewan da kayi ba don ku huta ba ne, Yaran nan wallahi ban da suna shn mama da na rabaku dasu, ko ka kaita gidan Maryam amma ban da Ummu." "Wai me ke faruwa ne?" Kashe wayar yayi. Mamaki ya kara kamani na kira Tafida, "zan kira ki!" Kashe wayar yayi.. ** A can kuwa Abin da ya faru, Asiyah ta sab'a lamba, domin ta tabo Saadiya a daidai lokacin da take cike da Tafida, abun da ya faru kuwa, tun da Tafida ya bar gidan bai gaya mata zai tafi bude sabon titi a wani kauye ba, take cika take batsewa domin a bakin yan gulmanta take jin labarin, har dare aka sha ruwa babu Tafida, ta kira Deen lokacin yana waya da ya gama ya kashe wayar domin shi dai bai da amsar da zai bata, wurin karfe hudu na asuba kamar ance ta fito ta hango Asiyah ta fito kamar daga ɓangaren Tafida, haka yasa ta kara kallon sosai ganin ta ga sun sake rungumar juna, kafin ta wuce inda take zama, tana ganin ya shiga Mota ya bar gidan. Jikinta yana tsuma kawai ta fito da gudu lokacin Asiya ta shiga bangaren da take ta rufe kofarta, komawa tayi ta shirya har karfe daya na rana Asiya bata fito ba, sai wurin karfe biyu ta fito. Ai kuwa Sa'adiyya tayi wuf da ita tayi ta bugata da kasa, tana bata kashi. Sannan ya yakushe mata fuska tana ihu karuwa kwartuwa me bin mijin wasu. Yadda kuka san mahaukaciya haka aka dauke Sa'adi baby akan Asiyah, duk abin ba dadin gani. Da ta samu ta shige dakinta ta kira Tafida tana kuka, shiri tayi amma bata zata wannan me kalar samudawan zata mata mugun duka haka ba, sai gashi ta yakushe mata fuska, sai da tayi kukan bakin ciki, bayan sallah juma'a Tafida yazo gidan ganin har lokacin Sa'adiyya tana ihun sai ta kashe Asiyah yasa Tafida kallon Deen. "Ku sake ta ku je!" Suna barin wurin ya nufeta. Aikuwa farar shaddan jikinshi ta damke wuyar rigarsa da ta yaga har kasa. "gaya min me nayi maka zaka ci amanata, ashe karuwa ka ajiye a gidanka, shine ka hanani hakkina, wallahi ba zan yarda ba muje ka bani hakkina nima na haihu kamar Ummu." "Kin ga nan ba kamar da can baya bane, ko ina akwai jami'an tsaro Please mu shiga daga cikin gidan!" Dake tana ganin girman Deen haka suka shiga rarrashinta da tambayar me ya faru bakincikin ya hanata fadar abin da ya faru sai kuka da rantsuwar matukar bai d'aga Asiyah a gidan ba zai samu gawarta, dakyar Deen ya kwantar da rigimarta, sannan yazo ya ga Asiyah sai da yaji babu dad'i. Yarinyar fuskarta ya kumbura. Shine yake tunanin ya kawo ta wurin Ummu ta yi jinya, Deen yace karya kenan. Ba zai yiwu lokacin da ya samu zai kula da kanshi da iyalinsa yace zai karawa kanshi yan sa'ido ba, don haka yasan yadda zai yi da ita...... #Tafida #Deen #Ummu #Sa'adiya #Asiyah #Mahmoud🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Kada ki ce zaki dauki burgewa akan nawa rayuwar ni da Yarana muna bukatar Uwa a cikin gidan nan, don Allah ki mana alfarman ki zauna a gida, ina matukar kishinki!" Ya fada yana kamo hannuna, ji nayi kamar zan yi kuka wani ya fada min abin da yake ranshi wanin ma Tafida da kamar wuya gurguwa da auren nesa. Kasa magana nayi ya kai ni wani daki yana faɗin. "Wannan shine dakina, yayi kyau ko na sauya domin dakuna uku ne a nan bangaren, naki dakuna hudu saboda baki da wasu laluran. Bangaren dayan kuma akwai dakuna uku shima kamar nawa." "Duk yaushe ka yi gidan nan?" Hannunshi ya kai gefen fuskata. Yana murmushi ya ce talla aka kawo min lokacin muna abuja, shine na gayawa Deen ya shi kuma ya gayawa Abba. Kafin na turo kudin ma Abba ya biya sai na maidawa Abba kudinsa, amma kin san me? Ko da aka zo saka sunan mamallakin gidan Abba sunanki ya saka." Murmushi nayi sai na kasa magana, ya fito dani zuwa daya dakin yana cewa. "Duk wani abu na gidan Deen ya zuba min su." "Saboda baka da lokaci ne?" Gyada min kai yayi yana jan hancina. "Bani da lokacin da xan zauna nayi ta wannan aikin, shi da Matarshi da kanwarshi Jalilah suka min wannan aikin." Murmushi yayi yana faɗin. "Ina tsoron kada wata rana na juyawa Deen baya." "Idan haka ya faru zai maka uzuri! Domin shi ma'abocin uzuri ne!" Murmushi yayi wanda tunda muka fara zaga gidan shine akan fuskarshi, muna gama zaga cikin gidan ya ce min. "Muje ki ga bangarenki!" "Na gaji sallah isha zan yi na kwanta jikina duk ciwo yake!" "Wai ki ce zan yi tausa kenan?" Ya fada yana kashe min ido daya, parlourn muka dawo muka shimfida abin sallah, ya shiga bandakin parlour yayi alola nima anan nayi alola, shi ya jamu sallah isha da tarawee, muna idarwa na kasa hakuri nace mishi. "Kayi sauka ne kai ma?" Saboda yadda yake jan kira'a. Addu'a ya shafa yana faɗin. "Eh nayi na fara a Nijeriya zuwana Sudan Deen ya saka ni a gaba sai da na hada sittin hankalinsa ya kwanta. " "Gaskiya ya kyauta mana!" Jan kumatuna yayi yana faɗin. "kwarai kuwa ya kyauta min tunda Allah ya haɗa ni da Hafiza!" Janyo ni yayi muka kwanta a parlourn ina jikinshi kwance. D'ago kai nayi ina kallonshi. "Yan mata bar kallona, ni naki ne duk wacce zata zo tow sudinki zata samu;" rufe fuskana nayi a kirjinshi ina dariya. "Naji kamshin turaren Tina a jikinki dazun gaya min yadda kika gudu daga garina." A hankali na warware mishi kome, murmushi yayi yana faɗin. "Yarinyar nan baki da tausayi!" Ya tashi zaune, "Ni sau nawa ka tausaya min?" Na tambaye shi, "kishin yadda Abba yake sonki, yake kuma damuwa da ke yasa ni jin haushi, taya ni da ya dace ya bawa kulawa ya koma nawa Yar mage kulawa!" Ya fada ina kallonshi. "Ni ce ma mage?" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Yes ke magena ce, idan ban yi kishin magena ba waye zan yi kishi. Ke magena ni muzurunki!" Ya fada yana rungume ni, dariya nayi ina kara k'amkame shi. "yaushe zaki min dambu ne?" Kallon bakinshi nayi na matsa a hankali na kai bakina, janyo ni nayi na zauna a jikinshi muna fuskarta juna. "Duk lokacin da kake bukata kazo ka ɗauka." Bakina ya kama da hakorinsa. A hankali ya sake yana faɗin. " Ba zata zaki min kuka ne kamar crybaby!" "Dake ka saba ganin kuka a idanuna ba!" Wayarshi ce tayi ƙara ya duba Mahmoud ya gani dauka yayi yana faɗin. "ya dai?" "Tafida dama na kira ne zamu zo da madam ku gaisa!" "Bana nan wallahi idan na dawo zan gaya maka sai ku zo mu sha ruwa tare" "ok na gode amma kana ina ne?" *Ka koyi boye mana kome hatta ni bana bukatar sanin privacy dinka!* inji Deen ya gaya mishi. "Eh tow bana kusa gaskiya!" "Tow ba damuwa, ko kana tare da yar baka ce?" "Me kace?" Ya tambaye shi a fusace. "yar baka nace ko kana tare da ita ne?" "Daga yau kada na kara jin ka ambaci Ummu da wanann sunan, Mata ta ce kuma Uwar Yarana, idan kuma ka sake raina zai b'aci zan yi hukunci." "Tow kayi hakuri na ga dai a bakinka naji!" "Eh a bakina ka ji na tab'a aibanta matarka? Ko na tab'a baka shawara ka cutar da ita?" "Tafida kayi hakuri ban san ranka zai b'aci ba, amma yaushe ka fara sonta?" Wani ashar ya lailayo ya maka mishi take ya kashe wayar domin Allah ya gani yana bala'in shakkar Tafida. Jifa da wayar yayi, na bi wayar da sauri na dauko ina faɗin. "Ji kamar an ce min yar wuta." Na shiga duba wayar ina kallonshi. "ka godewa Allah da wayar bata fashe ba!" Na mika mishi wayar ina rike hannunshi, shafa bayan hannun nake. "Kada ka damu tun ina Yarinyar na taso da kushen mutane, wannan ba sabon abu ba ne." "Ummu idan baki yafe min ba Allah sai ya kona ni!" "Ba zai kona ni saboda na bawa kare da dokin damar cin zarafinki." Kwantar da kaina nayi a gefen kafadarshi, ina murmushi. Na fahimci Tafida ya sauya sosai, amma tijara yana nan babu abinda ya bari, wurin sha daya na dare ya haɗawa Yaran madara, muka basu, sannan nayi musu wanka da ruwan dumi. Kafin muka wuce dakin na kwantar da su, ban daki ya shiga ya jima kafin ya fito daure da Towel. "Taso muje!" "A'a jeka kawai!" Zuwa yayi ya dauke ni cak, sai ban dakin, ya sauke ni yana faɗin. "Kina tsammanin zaki kwanta min a haka ne!" Kayan ya shiga cire min, yana faɗin. "Malama babu bakin magana ne!" Ya cire rigar ya ajiye can gefe, sai pant da bra! Juyo ni yayi na rufe idanuna. "Cancadi, wannan bra din yayi min kyau, gaskiya ina son irinsu." Ya kai hannu yana ɓalle pin din. Ni dai bance mishi kome ba yana gamawa ya kai hannun kan abin da yake jan hankalinsa. (😡😒 Ni rashin mutuncin Tafida ya fara isata.) Ban iya lokacin da muka dauka a banɗakin ba, amma tabbas naji kamar yau na fara haduwa da d'a namiji, koda muka dawo daki sha biyu ta wuce, a bangaren Tafida kuwa tunda muka dawo dakin, ya makale min domin ba zance wani abu, ina jin labarin ayu amma yau naga makwafin ayu. Ban san yadda xan fada ba, amma tunda ya manne min bawan Allah nan daga ni har shi idanunmu biyu har aka kira sallah farko. Yana makale a jikina yana jin kamar zan kwace na gudu. A hankali yake bin kome tun kiran sallah farko, farko yake jan tafiyar a hankali cikin sanyi da kulawa, ban tab'a sanin halinshi na zahiri ba sai yau, yau ya fito min a mutum dinsa, na kuma fahimci waye shi. Kallon fuskarshi nayi cikin rawan murya na ce mishi. "Yallabai!" Bude idanunshi da suka ji ja ya zuba min. "asuba tayi kada mu rasa sahur!" Kamar dama jiran maganata yake kafin na rufe baki ya shiga aikin da ban san yana da karfin yinsa ba. Ni dai a hannunshi na ji a jikina, sai da na fashe da kuka saboda yadda ya fita hayacinsa haka yasa ni jin kamar Tafida baya mu'amalar aure da Sa'adiyya, domin da yanayi da kuzarinsa ba xai yi yawa kuma ya dauki lokaci haka ba, sai da muka kusan makara ya kyale ni, kasa tafiya nayi domin kafaffuna kamar ba zasu dauke ni ba, haka ya riko ni zuwa banɗaki nayi wanka asalima zama nayi cikin ruwan dumin, a gurguje na fito na samu ya hada min tea mika min yayi da zafi-zafi na sha sannan ya ce min! "Sannu kin ji!" Dake ina bakin gadon daure da towel, kasa kallonshi nayi ina gama sha ya mika min farfesun jiya, kafin ya wuce yayi wanka sannan ya fito shima yayi sahur. Ganin ina bawa Yaran nono ya dawo bayana ya zauna tare da saka hannunshi dukka biyu a kasan cikina. "Ina tumbin?" Murmushi nayi nace mishi. "Ya koma!" Shiru yayi kafin ya sumbaci dokin wuyata. Muna zaune a wurin aka sake kiran sallah, amsa Mufid yayi ya kwantar da shi sannan ya amshi Mufidah ma, kafin ya ciro min doguwar rigana, muka yi raka'atul fijr. Muna idarwa ana shiga sallah asuba, a tare muka yi sallah, bayan mun idar mun jima muna addu'a, da azkar sai da rana ya fara fitowa na rarrafa domin sai yanzu na ji kafar ya min tsami. Gadon na hau na kwanta don wallahi jikina ciwo yake, musamman yadda ya makale yaki kome don rashin kirki, na juya xan harare shi. Ware idanun yayi yana faɗin. "me nayi kuma ake hararana da alamu ana zagina a rai kenan, tow na yafe miki, yar aljannata!" Kwanciya nayi ya dawo bakin gadon ya zauna tare da rike hannuna yana murzawa, murmushi muke sakarwa juna, a hankali barci yayi gaba da ni, shima gadon ya hau ya kwanta a bayana, tare da janyo ni jikinshi. Ban da azumi babu abin da zai hana shi komawa ruwa shi ya san abin da ya ji ya kuma tab'a ya ji. A hankali shima barci yayi gaba da shi, wato ranar Tafida tun kafin yau ya mikawa Deputy koma ya ce mishi sai Monday. *** A bangaren Mama tunda ta sauka ta kira uwani suka gaisa ta ce mata. "Ina Ummu!" "Yaronta bai da lafiya, sun kai shi asibiti ita da Deen wayarta kuma kin san tun tafiyarta ta saba barin shi a gida!" "Tow Masha Allah idan na samu lokaci zan na kiranku, yanzu lokaci ne na ibada a kwanakin karshe xan mika lamarin Ummu da naku ga Ubangiji, in sha Allah kafin na dawo zan yi addu'a sosai Ubangiji ya kawo miki miji na gari mijin marainiya kin ji Uwanina!" "Tow Uwata sai kin dawo Allah ya baki ikon mana addu'a!" Suka yi sallama. Mama tana son Uwani sosai irin so na gaskiya nan takewa Uwani yarinyar ma tana son Mama. Haka Mama da ta kira Baba Bulama shima ya gaya mata ai Ummu danta bai da lafiya ne, ganin duk bakinsu daya yasa Mama ta yarda, bata san cin amanarta suka yi ba. *** Karfe daya da rabi na farka, na samu yaran an musu wanka sai wasa suke da junansu, idan ba mafarki ba ina ga har nono Tafida ya ciro ya basu amma dake barci ya ci karfina ban iya bude idanun ba. "sleep beauty!" Make hannunshi nayi ina faɗin. "Kai da Yaranka sai da kuka shanye min nono ko?" Na fada ina gyara zaman rigar jikina. "Ayya sun tashi na rasa yadda xan yi shi ne na gyara ki na basu kowanne ya kama, suna gama sha na dama masu madara suka sha, kin ga har wanka nayi musu!" "Yaushe ka dawo Nanny!" "Taso na hada miki ruwan wanka kin ji!" Tashi nayi na ga yaran aka wani abin wasan Yara. Yana tsaye yana kad'awa Mufidah da take bangala mishi baki, na zo na rungume shi ta baya, karatu Tinah. "Good afternoon My Yallabai!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin. "Qurratul-Ayn! Kin tashi lafiya?" Juya mishi idanun nayi na wuce banɗaki, na leko yana tsaye inda na barshi. "Baby bani jakata akwai brush da toothpaste!" "Akwai sabi na bude mana!" Murmushi nayi na ce mishi. "Ban gani ba!" "Don Allah ki rike wannan muryan taki, wallahi ban shirya yin sittuna ba!" Ya shigo ban dakin ya dauka tare da matsa min. "fita kafin ka karya mana azumi!" Na fada a sanyaye. "Idan aka ga na suma kece wallahi!" Murmushi nayi na rufe ban dakin nayi wanka sosai, sannan na fito, shi da Yaranshi suna can parlour, na gyara jikina kafin na fito, muryanshi da naji da Deen yasa na koma dakin, sai kuma na saka Babban hijab na fito na gaishe da Deen, sai Hararata yake yana faɗin. "Ke bana ce kada ki fito ba!" "Ka ji guntun dan iska, ita Kanwata ce yayar Jalila ce, ka saka Ammah ce ta haife ta dan iska kawai! Ummu ina fatan bai miki kome ba ko?" Ya tambaye shi yana nad'e hannun rigarshi. Dariya suka bani na girgiza kai ina faɗin. "Bai min kome ba! Ya Sadika tana lafiya ta kusan sauka kan yanzu ko!" "Eh wallahi ina kyautata zaton karshen watan ko farkon sabon wata!" "Allah ya raba lafiya! Yallabai kitchen nake son shiga na maka aikin kafin na tafi!" "Ba fa zaki tafi yau ba, sai wata sati!" Rufe bakina nayi da hannayena, wani irin tsoron Mama ya dirka min kamar an wurgo dutse daga sama. "Ka rufa min asiri!" Murmushi yayi ya ce min. "Allah da gaske wayar mana na saka an sace shi a can Saudiya amma fa za a dawo mata da shi, kiyi hakuri Alhaji Bulama da Babanki sun sani, hankalin Mama ya kasu gida biyu tana ibada kuma kafin faruwar haka tayi waya da Mijinta da kuma Uwani, ki fahimci wani abu ina son mu kasance tare shi yasa na zabi haka amma kiyi hakuri da abin da nayi, wallahi bani da zabi ne ina son na zauna da ke na wasu kwanaki kafin ta dawo Please!" Hawaye ne ya zubo min. "Yanzu kawai don ka zauna da ni sai ka sakata a zullumi bata yi magana da kowa ba." "Mama ba irin sauran iyaye ba ne, Mama tayi magana da kowa kafin na saka.aka dauke wayar amma bari Deen ja ce yarinyar ta maida mata wayarta." Juyawa nayi zan koma dakin ya ce min. "Ki shirya zan mai dake gidan!" Yadda yayi maganar sai naji hankalina ya tashi, haka na wuce dakin na zauna ina jin kuka yana zuwa min. "Kana burge ni Tafida, kai tsaye kake lamarinka. Na ji dadi da kake fadar gaskiya ba ƙaramin aiki bane fadarta." "Deen tafiya zata yi fa!" "Ba zata tafi ba, yanzu ka je kace ta shirya zaka fita. Sallah juma'a zaka ajiye ta a gidansu!" Ya kuwa mike, ya nufi dakin Deen sai dariya yake mishi yana wasa da Yaran kaunar da yakewa Iyayen Yaran ya shafi yaran sosai, don yana jinsu kamar na shi. A bakin gadon na zauna ina shashekar kuka, domin nasan ba wani sauyawan da yayi, yayi min laifi kamata yayi yazo ya rarrashe ni amma yace wai na shirya zai ajiye ni a gida, wato yaci moriyar ganga, duk sai naji na tsani kaina da ban biyo shi ba da ba zai min haka ba, haka na cigaba da kuka, ban kawo a raina zai zo din ba sai gashi ya turo kofar, wani irin sanyi naji ya tsirga min, na d'ago kai ina kallonshi shima kallona yaƙe. "Allah ya huci zuciyarki, nayi laifi a yafe min dama can ni tsohon mai laifi ne, kuma na kara aikata bayan laifi ayi hakuri ba zan kuma ba." Ban kalle shi ba, na cigaba da share kwalla da yake zuba min, "Tow tunda ba zaki min magana ba, bari na hada kayanki na kai ki gida!" "Dama ka kawo ni ne ka min koran kare!" *Yes i hit the point!" Narke min yayi cikin rarrashi ya ce min. "a'a tashi na kai ki gida don Allah, wannan abin da nayi ina jin kunyar kallon idanunki!" Ya fada yana me durkusawa a gabana ya zuba hannunshi akan cinyoyina. "Ni dai kada garin son zama dani kayi ta aikata kuskure bayan kuskure, ka rufa min asiri kada kayi wani abin da zai tab'a rayuwarmu bakiɗaya." Na fada ina kuka, "ita mahaifiyata ce, dole naji wani abu na ga kamar ba sona kake ba, dama can na san Babu so kawai muradi ne ta zuciya...." hannunshi ya saka ya rufe min bakina. "Don Allah ki daina fadar haka wallahi bana jin dadi, nima Uwata ce, yanzu haka na saka za a maida mata wayarta ba zan kara wasa da rayuwar wani saboda ke ba, amma kiyi hakuri ba zan kara ba kin ji!" Gyada kai nayi ina share hawayen da yake zuba min. "Kiyi hakuri xan tafi sallah kada na makara!" "Allah ya tsare muje na tayaka shirya." Gaban closed din shi muka nufa na cire mishi wani babban kaya shadda ce fara sal, sai hular da zai haka da kayan, sai takalmi da links zamana da shi a abuja, baya saka babban kaya dai ranar Juma'a. Amma kusa na haddace shigarshi. Yadda yaga ina taya shi saka kayanshi ba tare da na damu ba, ya ce min."Ina tunanin ko idan kika dawo na barki a nan ne ba sai kin je government house!" Shafa kumatunshi nayi ina faɗin. "Duk yadda kace yallabai na!" Jan hancina yayi yana faɗin. "An gama yarinyar nan hancinki Mufid ya dauka. Mufidah nawa!" Ya fada yana haɗe rai. Dariya nayi ina faɗin. "Kuma laifi ne don haka ya faru?" "Kawai dai kishi nake da kika raba shi Abba ya dauki hancinki Ita Uwata kika barta da irin nawa hancin!" "Ba ka ga yadda yaran suka zamo kalanka ba!" "Hmm kuma haka ne kin fini gaskiya!" Ya fada yana rike hannuna, "ki so ni koda dan ne, ni dai nasan ina miki mahaukacin so ne! Ummu Hadiyya ina sonki sosai, irin son da nake jin ban yiwa kowa irinsa ba." Girgiza kai nayi ina faɗin. "'Lokaci yana tafi kace fada zaka je sallah!" "Eh anan nake zuwa tunda na zama gwamnanku!" Jan kumatunshi nayi ina faɗin. "Ka kyauta!" "Gobe asabar zamu shiga Biu ki shirya da wuri fa." Kallenshi nayi kafin na ce mishi. "Gobe kace amma kana ce min na shirya da wuri!" Na fada ina yaƙe. Mika mishi hular da yake hannuna nayi ya kansa ya kafa, wurin turaren shi na nufa na ciro na fara fesa mishi yana murmushi. "Na gode zan tafi mai xan sayo miki!" "Duk abin da ka gani ya maka kyau ina so nima zan min kyau!" "Hmm ji nake kamar kada na tafi!" "Muje maza Yayana yana jiranka, ka wani bar mishi renon Yaranka!" Muka fito ina gefenshi, "Nanny sannu da kokari ka ji!" "Kam uban can ni ne Nanny?" Deen ya fada da karfi yana nuna kanshi. "Lallai tafiya daga dan iska sai kai, a rashin mutunci ni zaka kalli tsabar idanuna kace min Nanny ka ɗauke ni dan daudu ne!" Yadda Deen yake tijara sai naga sam haka bai damu Tafida ba, asalima sumbatar goshin yaran yayi yana faɗin. "Kuyi hakuri Abbanku yana ta ihu, sai na dawo Yarann Daadi da Abba! Idan ka gama basu dariya muje don Allah!" Wayarshi ce tai ƙara ya kalla yana sake tsaki yayi ya ce. "Deen ya zan yi da Asiya ne?" "Ina ruwan sly Queen!" Juyowa yayi ya kalle ni, "wata cousin dina ce!" " ka gaya mata me kama fatalwa kin san an bashi mace dan iska ya ce baya so!" "Deen kada ka ja min bala'i don Allah!" "Yaya Deen kace dama can amanata kuke ci?" "A'a ban dani dan iska dai yake cin amanarki!" Ya nuna tafida da hannu, "Ka aurota!" Na fada zan juya, "Ni fa ba dan iska ba ne, kuma abu daya gare ni kin ga ya wuce daya ne? Da zaki ce na aurota!" "Yallabai ko bance ka aurota ba, wajibi ne auren mata sama da daya, Allah ya baka budi da rufin asiri in dai ba son zuciya ba, ai kana da damar rike mu mata hudu!" "Ummu Hadiyya ki fita idanuna na rufe. Auren ce miki aka yi da sauki ne da shi da zan rike mace sama da daya Hadiyya ki fito Ki gaya min bakya bukatar zama da ni mana!" Murmushi nayi na wuce shi don nasan ya cika haka suka fita, a waje ya amsa wayar yana me bude mata tsohon littafinsa na tijara, jin tana kuka yasa shi sasauatawa ya tambaye ta me ya faru, bai karasa ji ba ya kashe wayar ya nufi massalaci yana zargin Deen da hada mishi husuma me Deen zai yi ban da dariya. Bayan fitarsu nayi alola na zo nayi sallah, sannan na kunna wayata na kira Uwani na gaya mata ba zan dawo ba, ta ce min ai Baba ya gaya mata. Murmushi nayi sannan na kashe wayar na ja Yarana muka shiga kitchen, mamakin yadda aka zuba kome na zamani nayi, ina cikin aiki wurin karfe biyu da arba'in da biyar, ya kira ni. "Ummu Hadiyya! Akwai matsala!" "Ina tare da kai babu wata matsala gaya min me nene?" Daga can na ji Deen yana faɗin. "wallahi billahi azim ba zata zauna a inda Ummu take ba, ka kaita gidan Abba ko ko gidan Hajiya ba zata zauna ba, Ummu tana buƙatar ka kana bukatar Ummu, meye amfanin kebewan da kayi ba don ku huta ba ne, Yaran nan wallahi ban da suna shn mama da na rabaku dasu, ko ka kaita gidan Maryam amma ban da Ummu." "Wai me ke faruwa ne?" Kashe wayar yayi. Mamaki ya kara kamani na kira Tafida, "zan kira ki!" Kashe wayar yayi.. ** A can kuwa Abin da ya faru, Asiyah ta sab'a lamba, domin ta tabo Saadiya a daidai lokacin da take cike da Tafida, abun da ya faru kuwa, tun da Tafida ya bar gidan bai gaya mata zai tafi bude sabon titi a wani kauye ba, take cika take batsewa domin a bakin yan gulmanta take jin labarin, har dare aka sha ruwa babu Tafida, ta kira Deen lokacin yana waya da ya gama ya kashe wayar domin shi dai bai da amsar da zai bata, wurin karfe hudu na asuba kamar ance ta fito ta hango Asiyah ta fito kamar daga ɓangaren Tafida, haka yasa ta kara kallon sosai ganin ta ga sun sake rungumar juna, kafin ta wuce inda take zama, tana ganin ya shiga Mota ya bar gidan. Jikinta yana tsuma kawai ta fito da gudu lokacin Asiya ta shiga bangaren da take ta rufe kofarta, komawa tayi ta shirya har karfe daya na rana Asiya bata fito ba, sai wurin karfe biyu ta fito. Ai kuwa Sa'adiyya tayi wuf da ita tayi ta bugata da kasa, tana bata kashi. Sannan ya yakushe mata fuska tana ihu karuwa kwartuwa me bin mijin wasu. Yadda kuka san mahaukaciya haka aka dauke Sa'adi baby akan Asiyah, duk abin ba dadin gani. Da ta samu ta shige dakinta ta kira Tafida tana kuka, shiri tayi amma bata zata wannan me kalar samudawan zata mata mugun duka haka ba, sai gashi ta yakushe mata fuska, sai da tayi kukan bakin ciki, bayan sallah juma'a Tafida yazo gidan ganin har lokacin Sa'adiyya tana ihun sai ta kashe Asiyah yasa Tafida kallon Deen. "Ku sake ta ku je!" Suna barin wurin ya nufeta. Aikuwa farar shaddan jikinshi ta damke wuyar rigarsa da ta yaga har kasa. "gaya min me nayi maka zaka ci amanata, ashe karuwa ka ajiye a gidanka, shine ka hanani hakkina, wallahi ba zan yarda ba muje ka bani hakkina nima na haihu kamar Ummu." "Kin ga nan ba kamar da can baya bane, ko ina akwai jami'an tsaro Please mu shiga daga cikin gidan!" Dake tana ganin girman Deen haka suka shiga rarrashinta da tambayar me ya faru bakincikin ya hanata fadar abin da ya faru sai kuka da rantsuwar matukar bai d'aga Asiyah a gidan ba zai samu gawarta, dakyar Deen ya kwantar da rigimarta, sannan yazo ya ga Asiyah sai da yaji babu dad'i. Yarinyar fuskarta ya kumbura. Shine yake tunanin ya kawo ta wurin Ummu ta yi jinya, Deen yace karya kenan. Ba zai yiwu lokacin da ya samu zai kula da kanshi da iyalinsa yace zai karawa kanshi yan sa'ido ba, don haka yasan yadda zai yi da ita...... #Tafida #Deen #Ummu #Sa'adiya #Asiyah #Mahmoud🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Tafida* Kasa magana yayi yana kallon Deen baki sake. "Na tambaye ka wani abu?" Tafida ya tambaye shi, "ina jinka dan iya!" "Da ni da Ummu waye ka fi so a cikinmu?" Murmushi yayi yana faɗin. "Kai waye ya damu da kai, kato shirgeggen mutum irinka, nafi damuwa da Ummu akanka!" "Mtseew! Amma ita yarinyar!" "Indai ba cikin Hajiya kuka kwanta ba ka kara kira min sunan Yarinya sai na zage ka!" Tunda Deen ya fada mishi haka ya rufewa kanshi asiri, yana me lumshe idanunshi. "Yanzu me?" "Daman-daman!" "Kada ka fita idanuna sai na zage ka!" Haka suka isa gidan. Abba sun iso tun sha daya na safe, cikin nutsuwa da ya samu a kwana ɗaya, ya shiga gidan sai gaishe shi ake. Da fara'a a fuskarshi yake amsawa. Yana isa parlourn Abba ya samu su Maryam da Rukayya, cikin girmamawa ya zube a gaban Abba, tare da cire hular kanshi. "Gwamna da kanshi!" "Barka Abba ka sha hanya!" "Lallai Babangida ya kara girma, Deen me kake bawa Babana ne haka?" "Abba me zan bashi kuwa Ummu take cika mishi tumbi da daddar abinci, don bakinciki nace ya nima min daya kanwar Ummun gayen nan ya hade rai, gashi sai tara tsokaki yake kamar tsutsa!" "Abba kace ya fita idanuna!" "Tow kai Deen fita a idanunsa!" "Abba ina zan fita bayan yana auren kanwata! Bari na shiga wurin Ammah!" Ya mike yana gaida su Rukayya. Banza suka yi da shi kamar basu ji shi ba, "Man idan ka gama ka min magana, akwai sakon Ummu zan kai mata hannu to hannu, Abba ka kara yiwa Ummu godiya fa, Allah ya mata albarka yar aljanna!" Ya mannawa Rukayya da Maryam hauka. Ya fita suna gaisawa da Inna da take tambayar shi me ya faru da Asiyah Mamarta ta kira tana cewa. "Deen me ya samu wannan yaron Asiyah, Mamanshi ya kira ni yana ta cewa an kashe mishi fuskar Yaro, shine nace mishi nasan zaki zo!" Shiru yayi kafin ya ce mata. "Fada suka yi ita da Sa'adiyya amma da sauki tana asibiti!" "Na shiga uku ni jakan Umaru, Yaron nan Sa'adiyya ta fada ta'addanci ne? Ya daki mutum har gadon asibiti. Maza a kira min shuwa yazo ya ji abin da yaron nan ya aikata, Ita Tafida tana ina wannan abin ya faru?" "Baya gari Inna?" "Oho haka yasa ya kashe Yaron mutane, wannan masifar da me yayi kama da zai kashe yaron mutane." Yadda Inna take maida Sa'adiyya namiji yafi kome bawa Deen dariya, a nan ya barsu. Har parlourn Abba ta shiga da fada tana masifa, zuwa Tafida idanu. "me ya faru?" "Ina zata sani ita da bata gari." Inna ta kwace tambayar ta shiga rabto bayanin Saadiyyah zata kashe Asiyah tana asibiti, ciro wayar shi yayi da yayi kara. Sakon Barka da juma'a aka tura shi. Murmushi yayi yana kallon Inna da take ta bayanin yadda Sa'adiyya ta kashe Asiyah. "Inna da kike wannan maganar wai a kan idanunki aka yi ne?" "Ungo naka Mairamu nace ungo naka, ka fita idanuna munafiki, ko an gaya maka ban san kome ba ne wannan yarinyar Deen ta gaya min!" Murmushi Tafida yake yana faɗin. "Innata bayan sallah zaki fara zuwa wurin bita ajin bana ke da ni da Ummu Hadiyya da Hajiya Kaltuma zaku tafi, ki kira Yar uwarki Hajja Ganaah muje mu sauke farali." Bata son lokacin da ta fashe da kuka ba, tana faɗin" Alhamdulillahi! Allah na gode yau da yarinyar da Muhammad da Aisha suka haifa ta biya min aikin hajji, Allah ya saka ki gama da duniya lafiya ya rabaki da iyayenki lafiya!" Zani a hannu ta fito tana rangad'a gud'a tare da kiran Alhamdulillahi, maza a sayo gyada a rabawa Yara sadaka. Kallon Abba Tafida yayi yana faɗin. "Abba kasha Madina!" "Eh Aliyu na ji kamar kada na bar garin!" Murmushi yayi, sannan ya cigaba da cewa. "Yan uwanka sun kawo karanka!" "Tow Abba laifin me na aikata?" "Maryam ina jinki!" Nan ta shiga kame-kame kafin ta kawo zancen ya biyawa Maman Ummu Umrah amma ga Hajiya shuwa da ta sha wuyarshi, yanzu baya kyautata musu, sai Ummu da danginta. Murmushi yayi ya ce mishi. "Abba yanzu daga dawowarka hutawa ya dace kayi ba Muhawara ba!" "Eh haka ne amma me yasa kake musu rashin kunya? Yayunka ne fa!" Kura mishi idanun yayi har Abba ya kai Aya kafin ya ce mishi. "Abba ba zan taimaka musu ba, Abba kune kuka zama dole na muku hidima, su kuwa suna da wanda zai musu suna da Mazaje da ya xama wajibi akansu!" Yadda yake maganar Abba ya fahimci ranshi a b'ace yake. "Me suka maka!" Kasa magana yayi yana sauke numfashi, tunda yayi haka Abba yasan tabbas yafisu gaskiya. "Kai musu don Allah, Allah zai maka sakamakon alkhairi. Sannan kayi hakuri sosai na sani kai meyi ne kuma kana badawa ba tare da ka damu da jiya ka bada ba. Kayi hakuri kayi musu Allah zai tsarkake rayuwarka da zuri'arka!" Hakuri Abba yayi ta bashi yana rarrsshinsa. "Kana tare da Ummu ne yanzu?" D'ago kai yayi da idanunsa suka cika da kwalla ya ce mishi. "Eh ina tare da ita, kafin ta dawo." Murmushi Abba yayi hawaye na zuba musu dukkansu biyu, kuma suna murmushi, "Abba kuka kake?" Girgixa kai yayi yana faɗin."kukan farin ciki da jin dadi nake yi, yau gaka ga Ummu a tare. Ji nake kamar kome nawa ya cika yau gaka ga Ummu." Shima share kwalla yayi yana sunkuyar da kai a gaban Abba, yana murmushi ya ce. "Abba ina sonta sosai! Abba ban san wani irin so nake mata ba, Abba ina son Ummu sama da yadda nake jin bugun zuciyata. Abba ina sonta sosai, Abba ba zan yafewa duk wanda ya shiga tsakaninmu ba!" "In sha Allah babu me shiga tsakaninku duk wnada yayi ƙoƙarin shiga zai yi mummunar karshe, na roki Allah ya kare aurenka da Ummu duk wanda ya shiga cikin aurenku, sai yayi mummunar ƙarshe!" Yadda yake gayawa Tafida irin mugayen addu'ar da yayi yasa Rukayya tsoro don dama tana da mugun tsoro, Maryam ta razana amma bata yarda ta an ga haka a kan fuskar. Sai da suka gama hira tsakanin da da Uba, sannan ya juya kan Maryam yayi musu tas akan Umara da ya biyawa Maman Ummu, sannan ya ce su b'ace mishi daga parlour. Sun ji tsoro amma haka.suka nufi bangaren Shuwa suna ta zagin Tafida da jin haushin Abba yana goyawa Tafida baya. Anan ya sha ruwa yayi sallah Magariba, sannan ya baro gifab.. *UMMU* Tun fitarshi da kuma kiran da yayi min, yasa na tattara hankalina akan aikina da sauraron dawowarshi, ina gama aiki nayi wanka tare da Yarana, yau daya sai naji na gaji sosai, domin idan daya yayi barci zaka samu daya idanunshi biyu, haka nayi ta fama da su har na gama, mun fito ras kamar ba, na basu madara sun sha sannan na kara musu da nono, har aka sha ruwa babu labarin, bayan nayi sallah na kara gyara jikina, nasan yanzu yana hanya, dakin na kara gyara dakin nayi na shiga ban dakin duk da na gyara da nayi wanka sake gyara shi nayi, sannan na fito parlour na zauna kenan naji alamar ya dawo motar rakiyarshi. Bakin kofar na tsaya, yana turo kofar da sallama. Na kalle shi cikin kulawa ina amsa sallamarshi, "sannu da zuwa, barka ka sha hanya ya Ibada?" Zuba min idanun yayi yana murmushi, "Alhamdulillah na gaji." "Masha Allah, sannu sadauki!" Na riko hannunshi muka tafi har dakin shi, na zaunar da shi a bakin gadon, na fara cire mishi takalmin kafarshi da safar kafar, na wuce ban daki na hada mishi ruwan dumi, sannan na dawo na shiga cire mishi links da hular kanshi, sai babban rigar na cire ina fadin. "Sannu ka ji!" Wani shagwab'e min yayi na shafa kumatunshi. "Sannu kayi kokari Allah ya daura maka nauyin al'umma da kuruciyarka ai dole ka gaji!" Na taimaka mishi ya cire rigarshi, sannan na ja wandon shi ya sauka kasa ya rage daga shi sai boxes, na wuce gaba yana bina har ban dakin na kaishi. "Ummu ki taya ni mana!" Hannuna daya yana bayanshi ina shafa bayanshi. "Kayi xan zauna da Yaran!" "Eh gaskiya ne!" Na masa wayo na dawo waje,.na gyara dakin da kayan na fita inda ya nuna min dakin wanki na kai sannan na saka kayan a cikin injin wanki na zuwa kayan kumfa sannan na fito, a kayanshi na samo wasu kananun kaya wandon mara nauyi kamar na barci sai rigar itama haka, na fito da ita na fesa mishi turare, sannan na wuce waje na kara gyara inda zai ci abincin, ina gamawa na shiga dakin wankin na matse kayan sannan na koma dakin ya fito daure da towel, isa gabanshi nayi na amshi karamin towel din din na ce. "Yau ka wuni a gidan Abba ka je gidan Hajiya kuwa?" "Ban samu na je ba ko muje ne idan na gama!" "Hmm tace bani da kunya na kawo kaina tun ba a kawo ni ba!" " a dai taimaka muje!" "Ok kaci abincin!" "Hada a basket muje can muyi hira naci ma a can!" "Tow Yallabai!" Na shiga kitchen na hada kome na dawo na samu ya saka wannan kayan. "Na zata wasu zaka saka ba wannan ba?" "Bai dace da fita ba ko?" "Gaskiya kam !" Bude wurin kayan nayi na ciro mishi wani yadi coffee colour, na dauko hula milk da takalmi na ajiye mishi, na kara fesa mishi turare, muka nufi gidan hajiya bayan na sauya kayana, Wayyo Allah na, Hajiya rasa inda zata ajiye tayi dauko wancan ajiye wannan, bayan mun ci abinci aka yi ta hira, ina gefe jefi jefi ina kallonsu yadda suke hira. Murmushi nake kawai ina jin kamar nafi Tafida nutsuwa yaran kamar sun san suna wurin Hajiya sai wasa suke, ta dauki wannan ta ajiye wannan, a takaice na fahimci wani irin mahaukaciyar soyayyar da Hajiya takewa Tafida ya bambanta da sauran Yaranta, wannan soyayyar na hango shi akan Yarana, ko dan nishi suka yi sai ta ce min. "Ummu me ke damunta?" Yaran kamar sun santa sai kamata suke suna kokarin ja jikinta. Wurin karfe daya muka fara haraman gida, ja na daki Hajiya tayi tana kallona ta ce min. "Sabirah ta tafi, sai nake kallonki kamar sabirata ce, ga wanann kayan duk naki ne da na Yaranki, Auta yace min idan kika dawo zaki dauki Nana ko?" Wato yar sabira babban. "Eh na fadi haka tun bayan rasuwar Mamansu, in sha Allah zan dauke ta Hajiya." "Ummu hala baki gyara jiki ba kika dawo wurin Ali ko?" Kunya ce ta kama ni, murmushi tayi ta ce min. "Ga wannan kayan zauna.maza kisha tun shigowarku na dama miki, ga wannan sai da na tambaya ko yana da kyau kuma bai da illa. Suka tabbatar min larabawa na amfani da shi sosai, kada ki ji kunyata ni dawowarku tafi min kome dad'i, ban dai karba miki na." "Hajiya ya isa haka!" Don idan na fahimci Hajiya wato na cusawa. "Kin san yanxu cututtukan zamani ya yawaita shi yasa na amsa miki na sha kawai! Zan saka a miki zuma me kyau a kawo miki!" Matar nan so take danta ya kashe ni daren yau, fita tayi can dai gata da wani kofi Innalillahi wainnalihir rajou kankana ce da aka dama da madara da dabino da wulnut da kwakwa, ta ce min. "Ku sha tare da shi!" Ta ajiye min goran, haka na shanye tas sannan na fito Tafida yana harararmu. "Hajiya ban san iya adadin gulamta da kuka yi ba, Amma xan gaya wa Abba!" Haka muka bar gidan cikin farin ciki. A hanya ya dauke goran ya fara sha yana gyada kai. Har muka isa gida kaɗan na sha na bar sauran a firji, na kira Uwani muka yi hira. Sannan na kashe wayar. Bayan mun yi wanka Tafida ya ce bai san zancen barci ba, ga gajiya ga yanayin yadda na amshi kayan Hajiya. Wato ashe jiya wasa Tafida yayi min, yau kam ban san yadda xan fadi abin ba, domin sai da nayi danasanin amsar abin Hajiya. Na yakushe shi na ture shi na gantsara mishi cizo, karshe kuka nake har na tashi su Mufidah. Ya kyale ni na rarrashesu suka koma barci, .na gaji kafaffuna har rawa suke, "Aliyu ka kyale ni kada ka ji min ciwo, wallahi ba xan iya maka ba!" Shafa kaina yake yana faɗin. "Ke daya ce a duniyar Ali idan baki dauke ni ba, wacece zata dauke ni, Allah ka shigar da Ummu aljanna na karshe wurin daukaka, Ya Allah ka bar ni da Ummu tana feso min ruwan dumi face-face, Wayyo ni da na rabu da ke da nayi asara duniya da Lahira, Ummu me kika sha haka. Ummu me kika zuba me dad'i da gard'i haka. Ummu zan yi kuka wallahi kuka xan yi miki, Wayyo Allah na ji abin da yake zuba Ummu! Yar albarka, sannu zumata." Shi yake surutu ni nake ji kamar kasa ta buɗe na boya, wurin karfe uku ya matse ni yana haki, tare da sauke ajiyar zuciya. Jikina yayi laushi sosai, kuka na saka mishi domin har lokacin kafaffuna kamar ana zare min jijjiyonsu nake ji, sauke min kafaffuna yayi a lokacin naji wani irin sanyi ya tsarga min na fashe da kuka. Rungume ni yayi yana shafa bayana. "Kiyi hakuri wallahi ban san ya aka yi ba, sai xan kawo sai naji na kara kidimewa." "Jikina da kasana ciwo suke!" "Kiyi hakuri na sani zasu miki ciwo!" Ai kuwa na shiga rena mishi kukan shagwab'a yana rarrsshina har muka yi wanka muka fito, abu daya muke bamu yi barci ba, sai aikin rarrsshina yake, hudu da rabi muka yi sahur. Na koma na kwanta ya d'ago ni, kada ki kwanta ki jira abincin ya fada miki, ya jingina ni a jikinshi. Hawaye na zuba min don na gaji barci nake ji kawai. Rabona da barci tun Mama tana nan na kawo kaina wurin Tafida yana hanani barcin dare, muna zaune har aka shiga Masallacin na sake alola nazo na gabatar da sallah nafilla, kafin.muka yi sallah asuba, yau ko addu'a ban yi ba a nan na shiga barci, na gaji sosai. Duk da yaso muje Biu amma ganin yadda na gaji ya kyale ni, shima barcin ya kwanta bayan ya turawa Deen sakon. An fasa tafiya biu, barci muka ta yi har wurin karfe biyu saura wayarshi ce ya farkar da ni, ban bude idanu ba cikin barci na tashi na dauki wayar na saka a kunne ina faɗin. "Waye?" "Waye kike tambaya?" Dakyar na cije bakina saboda barcin da yake damuna na ce mata. "Yana barci idan ya farka zai kira ki, kin ji." "Ke wacece dama a wurinki yake kwana!" Fisge wayar yayi don ya fahimci ban gane wacce ta kira ba, janyo ni jikinshi yayi yana faɗin. "Ummu kwanta a nan, bashin barcin nan ba zai barki ba, sannu kin ji zo.ki kwanta Nur!" Ya fada yana bude min jikinshi, na kara kwanciya ina sauke ajiyar zuciya. Ganin har lokacin wayar tana nan ba a tsinke ba. Ya ce mata, "Ba nace a wuce dake Yola ba meye kuma kike bukata?" Daga can ta ce mishi. "Shi kenan dama na kira naji Ya kake kuma baka zo mun yi sallama ba." "Akwai matsala ne?" "No babu wata matsala!" "Ok bye!" Ya fada yana kashe wayar, duk ina jin shi sai na tsinci kaina, da jin wani irin farin ciki. "Murmushin kin kora min budurwa ko?" "Ni fa babu ruwana!" "Ni fa babu ruwana!" Ya fada yana jan hancina, a tare muka shiga wanka, muka gyara gidan a tare sannan muka yi kome ya ce min. "Yau Deen da wasu kwamishinonin guda goma zasu zo cin abinci, na ce Deen ya kawo miki Jalila." "Ok ba damuwa!" Ban tsaya jiran wani abu ba na shiga kitchen, ina cikin aiki Jalilah tazo muka fada aiki kafin karfe biyar har mun gama duk wani abu me ɗaukar lokaci. Kafin Magariba mun gama kome na kaita part dina na kara gyara gidan a cikin kayan da Hajiya ta bani akwai turaren wuta masu kyau, a cikin drower dakina na ga har da burne, na kai bangaren shi na saka turaren wuta. Na dawo na cab kwalliya, sannan muka zauna muna addu'a har aka kira sallah, kafin muka sha ruwa. Duk abincin mun jera musu sannan na dawo part dina. Jalilah sai murmushi take tana faɗin. "Aunty Baby! Girki a jininki yake, Aunty Baby idan kika dawo xan zo ina daukar karatu!" Murmushi nayi bayan Magariba suka zo aka ci abinci aka sha, har da Mahmoud sai raba idanun yake, basu har gidan nan ba sai karfe goma. domin Tafida ya aikin zai iya min yawa gobe, kasancewar suma gidansu akwai yan aiki yasa Deen ya bar min ita, dare nayi Tafida yazo ya dauke ni, muka nufi bangaren shi ai kuwa da kuka na isa dakinshi ina faɗin. "Kasan ba zan yarda ka min abinda kayi jiya ba, Gara na koma nabi Umarnin Mama... Murmushi yayi yana faɗin. "Yarinyar ai fa sai kiyi Mama tana can dakin Allah yana roka mana Ubangiji " mita nake yi yana dariya Tafida akwai mugunta a lamarinsa, haka muka yi ta rigima da shi, domin gaskiya wuni nake ina farsa wurin da ruwan zafi, Mama gayen nan bai gane dawar garin ba. ** *Mahmoud* Kamar zai yi hauka haka ya koma gida, ya kalli Matarshi Subaitu, bata da wani aiki daga kwalliya da zuwa bikin dangi yanzu ana azumi ne babu bikin da ake zuwa sai dai tayi kwalliya ayi ta hoto, sannan gefe guda daga ita har shi babu wanda yake da ra'ayin haihuwa. Ita ta ce idan ta haihu nonuwarta zasu kwanta sannan zata bude kasarta, shi kuma addu'ar da Ummu ta mishi yake tsoron kada ya fada kanshi. Parking yayi ya kashe motar Amma ya kasa sauka, Ummu yake son gani yadda Tafida ya samu nutsuwar nan ya san ba karamin dad'i yake kwasa a jikin Ummu ba, wayar shi ce tayi ƙara ya ja tsaki ya kashe, sannan ya sauka akan motar ya nufi bangaren Ammyn tana barci ya sani, bai shiga ba window dakin Khairat ya buga..🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Yadda ya buga window yasa Yarinyar tashi zaune, ta lallaba ta mike sannan ta fito ta kofar kitchen, kallonta yayi kafin ya shafa fuskarta yanayinta tana mishi kama d Ummu, idan har da gaske yana son Ummu dole yayi ta bibiyar Tafida amma taya? Sa'adiyya bata kashe mishi kirshiwar da yake ji. Zuwa yanzu Deen ya kara shiga tsakaninsu da Tafida yadda bai san me ke faruwa ba. Janyota yayi da karfin tsiya, yana nishi, "idan har kika sake wani ya san me zan aikatawa dake sai na yankaki!" Gyad'a kai tayi jikinta yana rawa, sannan ya jata har dakinshi ya ajiye ta sai da ya biya buƙatarshi kamar ba watan azumi ba sannan ya rakota ta shiga ta kitchen. Komawa yayi ya kwanta a dakinshi duk wani abu da yake na sa'a Tafida ne kan gaba a samunshi. Babu abin da zai d'aga ya ce yayi sa'a a kai wanda Tafida bai riga shi ba, haka yasa yake jin kamar ya gaza, akan me? Me yasa Tafida ya shi? Deen ma da yake kallon bai da kome sai ya lura yadda deen yake tare da Tafida shi ko rabin haka bai samu ba. *** *Asiya* A duk lokacin da wani yayi nasara a cikin rayuwarmu na yau da kullum, mutanen kirki da na banza suna kokarin shige mishi ne domin ace ai wane yana tare da su wane, Ita kanta Hajiya Turai rabonta da Maiduguri ta jima ko tazo bata tab'a zuwa gidan Inna balle wurinsu Abba, a da can baya ba wani shiri suke ba, domin tun suna Yara basu jituwa da Yaran Inna, kasancewar rashin kunyar da take da shi, Hajiya Turai Mahaifinta dan uwan Mahaifinsu Abba ne, mahaifinta a aikin soja ya rasu, kuma tun daga lokacin aka dawo da rikonta Inna kasancewar bata da y'a mace, abin sai yayiwa Inna dad'i. Sai dai zaman bata ba dad'i domin kullum fada suke da su Nuhu, wanda suke mata dukar fitar hankali sakamakon rashin kunyarta. A lokacin bata wuce shekaru goma ba,haka Inna tayi ta fama da ita. Har ta zama budurwa, dake dangin Mamanta suna zuwa ɗaukarta yan Yola ne, haka yasa suke gaya mata kada ta sake ta cigaba da zama da Inna zata iya sakawa danta ya aureta saboda kawai ta yi ta mata bauta haka yasa Turai d'aga hankalinta bayanta gama secondry, ta koma wurin kakarta na wurin Uwa jimeta. Inna taso Turai amma haka ya hakura da ita tun da bata da wani hujjar lallai sai ta rike ta, bayan komawarta Yola aka ture da zancen aurenta Alhaji Aliyu Jadda da kanshi ya je har Yola ya karbi aurenta ya kuma mata duk abinda uba yake yi, sannan ya dawo, tun daga nan tana zuwa lokaci zuwa lokaci, a hankali sai ta shafe shekaru goma bata zo ba, bayan rasuwar Alhaji Ali, tazo daga nan bata kara zuwa ba, sakamakon mijinta ya fatsama harkan kudi daga sama har kasa likafa ta cigaba, bayan wannan lokacin bata zuwa sai dai a je mata, kwatsam sai ga Allah ya daukaka aliyu ya zama gwamnan borno, duk Yaran biyar uku mata ne biyu maza mazan kuma sune manya, duk ta aurar dasu Asiya ce dai sai a hankali. Asiya irin yaran nan ne marasa tarbiyya, domin idan ka ajiye ta a wuri sai ta san yadda ta lalata maka wani abu me daraja, idan ana niman Yar iska aka samu Asiyah tow magana ya ƙare, Yarinyar ko akuya ta sallama mata a duniyar yan iska, babu abin da bata yi. Turai babban Burinta ta aurar da Asiya ba tare da ta damu ko tayi kyau ko kada tayi kyau ba, ana cikin wannan yanayin sai ga Labarin Aliyu ya zama gwamna, sai da suka bincika sosai akan Ummu dake Turai ta san sirrin bin malamai da bokaye, aka gaya mata Ummu da Tafida ba dai mutum ba sai Allah. Kuma zuciyar Tafida yana ga Ummu domin babu macen da zata iya samun shi, sai wani ikon Allah. Duk inda Turai ta shiga lamarin daya ne, aka gaya mata shuwa ma.tana can tana kafa yarta amma ko kallo basu isheshi ba, don haka ko da yarta zata shiga gidan sai dai wani ikon Allah ba dai da son ran Tafida ba, sai ga makircin da suka hada ta kuma hadu da fushin Saadiya. Lokacin da ta isa gida Turai ta ga yarta sai da taji ranta ya tab'u haka yasa ta kira Abba, bayan sun gaisa a nutse da jan zuciya ta warware mishi irin ta'asar da Sa'adiyya tayi musu, abun ya mata ciwo cikin sanyin murya ta ce mishi. "nasan da Baba Alhaji yana raye, sai ya kwatar mata hakkinta, amma ba kome Allah zai saka mata." "Kayi hakuri Turai, ni kaina ban zaci haka daga gare ta ba kuma ban san al'amarin ya kai har haka ba!" Yayi ta bata hakuri kamar zai aro baki ya ƙara. Amma tace ba kome, kashe wayar tayi ta kira kawarta ta gaya mata ta rasa yadda zata yiwa al'amarin Tafida. Shiru kawar tayi sannan ta ce mata. "Gaskiya ba za a rasa wanda zai iya mishi aikin ba ko da kuwa ana yi zai warware mu jaraba sa'aarmu. Gobe ki fito da karfe hudu domin zan kai ki bodar taraba da Kamaru akwai wani bamaguje a can in sha Allah za ayi nasara ai ki tawo tare da ita." "Na gode sosai kawata!" "Amma ki tawo da ita fa! Domin aikinsa haka yake sai ya ga yarinyar tukun akwai abin da zai mata kafin ayi nasara!" "Shi kenan zamu zo!" Haka suka ajiye wayar kuwa. Sannan ta sauke ajiyar zuciya.. ** *Ummu* Alkhairi yayiwa Jalila aka maida ta gida, ni kuma na tashi na fara aiki na gaji da cin dankalin turawa da doya, fanke na kwab'a sannan na ajiye shi yana tashi na fara soyawa, yau bakiɗaya abinci me sauki ne kunun fulawa da gyada nayi, sai jollop din taliya wanda yaji Aida special species, ```All spicess Jollof mix BBQ mix Thyme plus Garam masala Curry powder``| ```Special zobo Special yaji Spice kuli kuli Miyar kuka Miyar kubewa Special daddawa``` ```Garin masa/sinasir Garin alale da kosai Garin kunun tsamiya Garin kunun aya``` da farfesun kayan ciki wanda yaji Aida Special Speciess . Domin abin da na fahimta shine Tafida ya zuba kome tun kafin nazo, ya gama shirinsa kafin nazo. Sai na samu kwarin gwiwa yin duk girkin da na iya, fruit na markad'a nayi juice da shi, na hada na zuba a kofi babba na kara da ƙanƙara, na jera sannan na shiga wanka na gyara jikina, kananun kaya na saka na raba gashina gida biyu, na kitse su sannan na yafa mayafi, dab da kiran sallah naji karar motarshi. Murmushi nayi ina kallon agogon dakin, yarana na dauka bakiɗaya na fito da su parlour na saka su a kan kujerar parlour, na nufi bakin kofar yana budewa na rungume shi. "Oyoyo!" Dan sunkuyowa yayi yana sumbatar goshina, "Oyoyo Matata! Wannan wankar tun daga shan ruwa zan fara noma!" Da sauri na kwace jikina ina faɗin. "kada ka karya azuminka dai!" "Haba ina Aliyu Tafida ba zan karya azumi ba." Amsar kayan hannunshi nayi, "Tun da ka fita sai yanzu!" "Muje Ummu na gaji!" Raka shi daki nayi na taimaka mishi yayi wanka, yana fitowa ana shan ruwa, shiga dakin nayi da ruwan dumi da dabino na mika mishi. "Barka da shan ruwa!" "Yawwa Barka dai Ubangiji ya amshi ibadarmu!" "Amin Ya Allah!" Yana daure da towel ya sha ruwa na ciro mishi kayansa, ya saka su sannan ya riko hannuna muka sha ruwa a nutse kafin ya jamu sallah, muna idarwa muka ci abinci kadan sannan ya ja laptop dinsa ya fara aiki har aka yi isha, nan ma ya jamu sallah yana fadin. "Ina da aiki sosai idan kina jin barci ki je ki kwanta zan zo!" "Zan tayaka hira!" Haka muka yi ta hira muka kallon tafsiran malamai, can na kwashi Yaran na basu madara sannan nayi musu wanka na kwantarsu na tofe su da addu'a, na shiga nayi wanka wurin karfe sha daya, kayan barci na saka na shirya jikina sosai sannan na fita parlour na zauna, duk da hankalinsa yana kan aiki amma sai da ya d'ago a gurguje ya zuba min idanun, "Kin iya kashe mutum da shagali!" Ya kashe laptop din, ya bude min hannu, da sauri na nufe shi, ya rungume ni yana faɗin. "Zan saka ki kuka muje daki don na ga nan!" Rufe mishi baki nayi, "ai idan wannan kukan ne yanzu na fara. " Ina mishi wani irin kallo, wanda ban san yaushe na koya ba, Ya Salam Tafida ya tashi kaina a parlour ya goge min duk wani abin da nake ji, ya kuma sani jin lallai a duniyar nan bayan shi babu wani namiji. Haka yasa da kome ya lafa, ya min wayo ya kai ni daki, sannan muka yi wanka sai da ya ga mun kwanta barci yayi gaba da ni, ya dawo ya cigaba da aikinsa. Project ne mai muhimmanci, idan ya bari bai san yaushe zai gama ba, haka yasa shi ƙara mai da hankali, a bangaren Ummu yasan sarai idan ba kashe mata jiki yayi ba, ba zan tab'a tafiya nayi barci ba shi yasa ya min wayo ya sakata ni barci. Da asuba shi ya tashe ni, na tashi ban daki na nufa na wanke baki da alola na amshi tea na sha, ina kallonshi. Kashe min idanun yayi yana d'aga min gira. "ko muje second round ne?" "Hmm" na ce mishi, kallon agogon yayi karfe hudu da minti goma, jin hmm kawai da yayi ba sai ga Malam Ali ya sake turmushe ni a karo na biyu ba, bargon da ya fito da shi domin lullubuwa yana aiki, ya rufa mana, yana zaune a bayana. Yana shan tea din da ya kara hada mana, "Yaushe Mama zata dawo?" "Sallah da kwana hudu!" "Ya kamata na koma gida!" "Ni kuma waye zai kula da ni!" Kwantar da bayana nayi a kirjinshi ina faɗin. "Akwai saadiya!" "Idan kina son muyi fada ki daina kira min wata mace daga Hajiya sai Inna da Mufidah!" "Allah ya huci zuciyarka!" Na fada ina kurban tea. "Hmm!" Shafa mama na yayi yaji suna zubda ruwa. "Ummu don rowa hana ni sha kika fa!" " abincin yaran zan baka fisabiilillahi!" "Ni dai ki bani na sha!" "Zaka mai da ni ruwa ko?" Juyar da ni yayi ya fara sha kamar wani jinjiri. Dakyar na kwace ina jin jikina yana wani irin budewa, lasar wuyana ya fara har zuwa fuskata. "Lokaci yana tafi don Allah ka bari!" "Kiyi!" Sumbatar bakina yayi yana faɗin. "ba xan yi kome ba! Ba zan ketare iyakar Allah ba!" Ya matse ni a kirjinshi, ajiyar zuciya na sauke ina k'amkame shi, bayan an kira sallah na tsayar da cin abinci muka shiga wanka, muna fitowa nafilla muka yi sannan muka jira lokacin sallah yayi, muna sallah har rana ta fito. Kafin muka kwanta, kasancewar ranar Monday ne. Da kanshi ya tashi ya fada ban daki, ina jin motsin shi na mike na ciro mishi kayansa, na shiga haɗa mishi duk wani abu me muhimmanci kafin ya fito na hada kome, yana fitowa na taimaka mishi ya shirya sannan na amshi jakarshi nima na saka doguwar riga na kara shi har bakin motarshi, yana shiga ya d'aga min hannu. Ina shiga cikin gidan na fara aiki kafin sha daya na gama kome, sannan na kwanta. Ina barci wurin sha biyu aka yi ta buga kofar gidan. Bude idanun nayi na saka hijab na fito. Security ne. "Madam kina da baki sun ce su yan uwan His Excellency ne!" Murmushi nayi kafin nace mishi. "Tow su shigo nan da minti Talatin!" Rufe bangaren shi nayi na nufi bangarena da Yarana, sannan na gyara ko ina duk da nasan jiya mun gyara da Jalilah. Bayan minti talatin kuwa na fara jin hayaniyarsu. Ina zaune a parlourna na daura kafa daya akan ɗaya, doguwar Arabia gown ce, pink colour. Fuskata ba yabo fallasa. "Kutumar Uba! Gidan nan na ajiye ki?" Inji Sa'adiyya, murmushi nayi ina faɗin. "Ina kike so ya ajiye ni tow?" Maryam da Rukayya sun kasa magana. "Sai naci Ubanki sai kin gaya min waye ya tsaya miki!" Murmushi na sakar mata ina kallon bakin kofar. "Aliyu Muhammad Jadda Tafida ya tsaya min, ta Ikon Allah Barka da zuwa Mijina hasken rayuwata! Uban Aisha Baban Muhammad!" Cak Saadiya ta tsaya tana kallonshi jikinta yana rawa. "Abin da kika yiwa Asiyah ba a tsawatar miki ba kika zo zaki yiwa Ummu *ASIYA!* (Ba fa kowa ka isa ka tab'a ka kwana lafiya ba! Musamman heir din Tafida 😜🏃🏻‍♀️) *Shin ko kun san kayan kamshin da kayan zobo tare da duk wani dangin kayan abincin gargajiya da Ummu take amfani yana samuwa ne ta wurin Shaharariyar me kayan kamshi na AIDA spicess! Ina mata yan yayi ina masu abinci na online kayanku ya tsinke a gindin kaba, ga Hajiya Aida special spicess tazo mana da kayan girki na gargajiya da na zama kai Jama'a wata miyar sai a makota! Na gwada sauran ku gwada ina jiranku! Za a iya samun Aida spices ta wanann number:+234 806 968 1068 Whatsp siyan na gari mai da kudi gida! Hajiya ki zama yar gayu me sauki ne amma girkin yan gayu dai da Aida spicess*....🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 Wani irin numfashi ya sauke tare da rufe kofar parlour ina zaune a kujeran har lokacin. "Munafuka kiranshi kika yi? Annamimiya!" Murmushi nayi na ce mata. "Idan kina tsammanin idan da kiranshi nayi, kafin na kashe wayar ina ga da yasa an muku ba daidai ba, amma bani da lokacin kiran shi domin ya tsaya min don nasan ko baya nan babu abinda zaki iya min." Har lokacin yana jan wayar wuta ne da aka hada kayan electric na gidan, "Me xaka yi da shi? Ai babban kuskuren da ta so aikatawa bata aikata ba, kawai ka tattarata ta bar min gidana." Na fada ina mikewa daga kujeran. "Ke jinki wata jar wuya ce? Asirin da kuka yi don mallakanshi in sha Allah sai mun warware, wawuya me dangi arna!" Juyawa nayi kamar zan tanka mata amma na kyaleta, ko don Tafida Maryam ta cancanci na kyaleta, amma kuma zagin ya min zafi. Sai nayi baya kamar zan fadi, ya tare ni yana haɗa Sa'adiyya da bango. "kada ka illatatta kyaleta don Allah!" "Maryam ke da Rukayya mu bar min gidana kafin na saka a muku koran kare!" "Wai ka ji kunya, mune zaka biya mu wahalar da muka maka kana yaro shine bari ka ci zarafinmu, Tafida mun barwa Ummu kai, amma ki sani akwai karshen ki yana nan zuwa yana nan tafe zaki ga abinda zai faru alkadarinki yana nan zai karye wata rana." Haushin ba zai iya dukar Yayunsa ba, kawai ya rufe Sa'adiyya da duka, zuwa nayi na kwantar da Yaran. Na fito suna kokarin janye shi amma yaki barin dukarta sai da na zo na rungume shi ta baya, ina kiran sunanshi da karfi. "Don Allah ka daina dukarta haka, kada ka saka min tsoronka don Allah!" Na fada da karfi ina kara k'amkame shi. Yarda wayar yayi yana me bude musu kofarshi. "Ku fitan min a gida, ko na rufe idanuna na ci zarafinku!" Hanta suka yi waje tana sume, hankalinsu a tashe domin basu zaci tafida zai iya mata kafirin duka haka ba. Juyawa yayi yana kara rungume ni. Na fashe da kuka kamar zan bar jikinshi. "ya isa babu abinda zai faru in sha Allah baki yi kama da matar da xan saka ba, da na dake ki gara na wayi gari hannuna ya rube!" Kuka nake a hankali na d'ago kai ina kallonshi. "abinda Mama take gudu kenan, ko bama gida ɗaya ba zan huta ba!" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Zaki huta, nima nasan zaku huta!" Cikin shashekar kuka na kwantar da kaina a kirjinshi. "Ya aka yi kazo?" "Matori ya gaya min ga wasu sun zo zasu shiga, sun ce yan uwana ne su. Na kira wayarki baki d'aga ba, ashe har ya tambaye ki, shine mace maza a kawo ni na san Babu alkhairi a zuwansu." "Don Allah ka daina dukar mace haka zaka kashe ta ne?" Girgixa min kai yayi yana shafa bayana, "ba zan kashe ta ba, sai dai ta cigaba da min haka zata wahala." Har lokacin jikinsa bai daina b'ari ba, zaunar da shi nayi na daura kaina a kafadarshi, "Ina son zama dake har karshen rayuwata!" Damke hannunshi nayi cikin sanyin murya na ce. "Ina fatan daga yanzu har abada ina tare da kai!" Murmushi yayi yana faɗin. "Kiyi hakuri!" "Ya wuce kai zan bawa hakuri an d'agoka daga aikinka!" "Zan koma yanzu!" Haka ya koma bangarenshi ya sauka kaya, na raka shi ya shiga Mota suka koma office. Wunin ranar dakyar nayi shi cikin nutsuwar rai. Daga can gidan Abba ya wuce ya kai ƙara, lokacin da shida ta ga halin da yarta take ciki sai da ta fashe da kuka domin bata zaci haka daga Oga Aliyu ba, wani irin rigima aka yi ta fama da shi a cikin gidan Tafida ya rantse ba zata koma mishi gida na ya gaji da renon tinkiya. Maganar da yayi ta gayawa Shuwa yasata kuka sosai, rigimarsu taki karewa sai da aka kira Hajiya ta tsawatarwa Tafida cikin fushi ya ce mata. "Wallahi ta kara yunkurin tab'a min matata sai na yanke hannunta ku rubuta ku ajiye!" Ya juya ya bar gidan sai da ya dawo gida ya kura Deen yake bashi labarin abinda ya faru me zai yi ban da dariya Deen ya ce mishi. "Muna asibiti an kawo Sadika haihuwa!" "Kai Masha Allah, bari na gayawa Hajiya yanzu!" Ba karamin farinciki ya shiga ba, ya kira Hajiya ya gaya mata. Aiki ya koma amma bakiɗaya sai ya kasa nutsuwa. Can ya kira Ummu "babu wata matsala ko?" "Babu!" "Ummu Hadiyya!" "Na'am!" "Ki kara min hakuri kin ji!" "Akan me zan kara hakuri me kayi min? Ba kai ne matsalata ba, kuma bana fatan ka kara zame min matsala, ka fuskanci al'ummarka kada ka damu da ni, ba ni da matsala a har can!" Kashe wayar yayi yana sauke ajiyar zuciya. UMMU Ina gama waya da shi, sai ga kiran Maryam kin dauka nayi na rufe idanuna, can ta kara kira na dauka. "Ummu ki rubuta mi ajiye sai mun raba ki da Tafida, ki saka a ranki duk abin da ya same ki, mu ne tunda kika mallake mana dan uwa kika sa ya daki matarsa da danginta suka mishi kome!" "Alhamdulillahi tunda na yar kanwar Hajiya ba ce ya daka ai da sauki, Maryam ni ba zan ce zan rama abin da kika min, in sha Allah zaki gani a ƙwaryan cin tuwonki, ai kema gidan wani kike, nima Allah xai aiko masu rama min!" Na kashe wayar, Tafida ba shine matsalata ba, yan uwansa sune damuwata. Bayan na kashe wayar sai ga kiran Mahmoud. Haka yayi ya kiran wayata naki dauka, kira yayi da bakon number na ɗauka. "Kada ki kashe min kira, baki yi mamaki yadda su Rukayya suka zo ba? Kada ki damu ni na gaya musu! Ki kashe aurenki da Tafida zan baki kome na rayuwa zan tabbatar da na nime takarar da ta fi na Tafida domin na baki duk abinda kike so?" "Jahili kazami, fasiki matsiyaci na kasar wuta, in sha Allah Ubangiji yana nan yana maka shiri na musamman, Allah sai ya kunyata ka lokacin da baka zata ba! Mahmoud matukar ina raye zan yi murna da farin cikin ganin ka a wulakance, aurena da kimata da ka so tab'a Allah sai ya kawo masu tab'a naka, Allah sai ya kunyataka Mahmoud Allah ya isa tsakanina da kai, ba zan yafe maka ba albarkan azumin bakina!" Na kashe wayar ina kuka, idan na tuna abun da Mahmoud ya min ji nake kamar na mutu da takaici, yadda Mahmoud ya ga tsiraicina, Allah ka wulakanta shi. Wuni nayi ban daura kome ba,saboda kukan da nake, yana dawowa ya ganin a birkice, ai sai yafini shiga damuwa ya tambaye ni yafi sau goma, tow na goge kome na wayar bakiɗaya na tsani wayata. "Ummu idan aka abinda su rukayya suka miki ne, zan dauki mataki na gaya miki!" "Kaina je ciwo!" "Tashi muje gidan Hajiya mu sha ruwa, na ga yau baki yi kome ba!" Ban sauya kaya ba, haka na fita shima duk abinda nake mishi yau ban yi ba domin haushinsa nake ji, ai shi ya kawo Mahmoud ya wulakanta ni. Hannunshi ya kai zai tab'a ni, ma kauce. Ciki ciki na ce mishi. "Muje don Allah!" Daga haka na wuce sai ya tsaya yana kallon hannunshi kafin ya dunkule hannun. Ya fito ko a mota kin zama kusa da shi nayi ina can gefe hanya. "Gobe zan koma gida kada ka ce min a'a!" "Ummu amma ai ba haka muka yi da ke ba!" Sharrr naji hawaye na zuba min, ban tab'a ganin wanda bai iya jure tashin hankali irin Tafida ba, yadda ya shiga damuwa sai nake jin babu dad'i. Tambaya ta yake na gaya mishi me yayi min wallahi ba zai kara ba, har muka isa gidan Hajiya Hajiya kuka nake, yana rungume da Mufidah muka shiga gidan, tunda hajiya taji karan saren tasan yazo, murmushi ne a fuskarta tana me mana barka da zuwa sai dai ganin yadda nake kuka yasa ta zuba mishi idanu. Zubewa yayi akan gwiwarshi a kasa, "Hajiya ki min tsakani da su Rukayya zasu kashe min auren da na sha azabar dawowarshi Hajiya, ji nake zuciyata tana zafi don Allah Hajiya kiyi wani abu kafin su raba ni da Ummu!" Ya fada yana juya kanshi. Hajiya zuba min idanun tayi kafin tayi murmushi tana faɗin. "Ummuna Hadiyya!" D'ago kai nayi ina kallonta, "kiyi hakuri! Kin ganshi durkushe gabanki, ban san me ya faru ba, amma nasan su rukayya ba zasu raba ki da shi ba, ban ga tsoro akan abin da kika dauka ba, amma naga damuwa akan fuskarki, idan su Rukayya ne basu kara zuwa damunki, kin ji ko?" Gyada kai nayi kaina a kasa na ce mishi. "Ka tashi !" Kallona yayi kafin ya kara matsowa. "Kin hakura ba zaki tafi ba!" A sanyayye na kalle shi kafin na ce mishi. "Babu inda xan je sai ana jibi Mama zata dawo!" Na tashi da sauri na shige dakin Hajiya, murmushi tayi tana karban takwaranta. Zai yi magana ta dakata da shi. "Ka godewa Allah ta san darajar Manya, idan wata ce babu ruwanta da haka nake gaya maka ka samu mace na nunawa sa'a. Ka riketa gam domin ka sake ta subbce maka sai kayi jinyar da tafi ta dawo!" *** *Asiyah* Tafiya yankin azaba, shine Hajiya Turai da yarta da kawarta suka yi har wannan lokacin basu isa cikin dajin gyambu ba, sai wurin karfe biyu na rana suka isa dajin wanda tun kafin su isa suke hango alamar bokanci, wani takadaririn shaidani ne zaune wani fili fallau, a saman iska ya tankwashe kafarshi, gefenshi bukka ce a wurin gabanshi kayan tsafi ne gasu nan kamar hauka. "Aliyu Muhammad Jadda Tafida, kika kawo a saka shi ya auri yarki Asiyah, akwai haske bayan kin rasa wanda zai miki aikin nan yau gashi kin zo mana, aiki zai yi nasara amma ba yanzu ba ba yau ba domin ana azumi duk wasu shaidannun da zasu mana aiki suna daure, idan aka gama azumi yau saura kwana goma sha biyu ki dawo da ita. Nayi aikin da zai bata shi amma ku sani aikin nan ba zai kammala ba sai da amincewar matarshi! Ummu Hadiyya." "Matarshi kuwa?" "Ba a tambayata maza juya ku koma inda kuka fito." Haka suka juya hankalinsu a tashe, "kada ku damu tafiyar zata gajarce muku!" Daga haka suka cigaba da tafiya ko minti goma ba su ba, sai gasu a bakin hanyar da suka shiga dajin. Ajiyar zuciya suka sauke sannan suka koma motarsu. *** Ummu Har bayan shan ruwa ajiyar zuciya nake saukewa, duk sai ya rasa sukuninsa yayi ta bina da idanu har aka yi bude baki, massalaci ya tafi a can suka hadu da Abubakar, bayan sun su sallah, suka tawo gidan Hajiya tare, anan suka sha ruwa suna hira sama-sama, Hajiya take gaya masa abin da su Maryam suka yi. "Wai ni kam me kake yi da yarinyar nan ne tunda ya tabbatar baka bukatarta?" " A lokacin da narasa nono Shuwa ce ya bani kunu, a lokacin da narasa Uwata ita ce ta ɗauke ni duk da na taso da jin zafin Hajiya, haka bai hana ni ganin girman Hindu ba, tayi min abin da ba kowa yayi min ba, matsalar da aka samu ni ba zata juya ni ba ne, sannan ba zata saka ni nayi abinda ban yi niyya ba. Hindu so take ta kowani kusurwa ta mallake ni, amma Allah ya tsare ni ba tare da na yi kome ba, yarinyarta kuwa naso na zauna da ita watsar da kanta da tayi yasa na jingine ta. A da can baya idanuna basu bude ba, sai da Ummu ta bar min yaran na rasa wanda zai dauki Yaran ya rike min kowa gudu yake yana komowa gefe, daga nan na fahimci Ummu kaɗai zata zauna da Ni ba tare da ta guji wani abun da xan kara mata ba, a asibiti Hajiya nayi danasanin abin da na aikata. Yaran da aka haife su danyen jego wai Maryam take gaya min idan Uwarsu na zata rike su ba, sai dai na nimo wata mace ta shayar min dasu itama nata yaran sun ishe ta sannan danyen goyo ina zata kai su, Hajiya Maryam ta ce min na rabu da Ummu na kwace Yarana akan idanun Ummun aka yi gata nan da ranta, Hajiya na rasa wanda zan kira na ce ya rike min yaran kafin a gaban rantsarwa na rasa hatta Hindu cewa tayi ita ba zata iya ba, kowa gudun Yarana yayi Hajiya Allah ya sakawa da Deen alkhairi shi daya ne ya ce min, "Muje a kai mata idan bata amsa ba matarshi da Ammah zasu rike Yaran Hajiya ina jin yadda ake cewa Deen ya mallake ni, ba laifi matukar Deen da Haddiya zasu mallake ni tow ni zance don Allah su kara da bita zai zai, yadda ba zan tab'a bijire musu ba" ajiyar zuciya hajiya ta sauke tana kallon kofar dakin da Ummu take. "Hakurin da kayi da naka jarabawar, shine Allah ya baka mace ta gari wacce zata rungumi duk wani matsalarka, Tafida na gaya maka Ummu mutum ce ka riketa hannu bibiyu." Bayan shan ruwa a daki nayi tarawe, na kwanta. Shigowa tai tana faɗin. "Ummu ya dawo!" Kamar xan yi kuka na ce mata. "Hajiya ni a nan xan kwana!" Kallona tayi kafin ta ce min. "Ummu Hadiyya!" Ta zauna a gefen gadon tana faɗin. "kada ki hukunta shi da laifin da bai san ya aikata ba,kiyi hakuri kada ki kaurace mishi, har yau Ali yaaro ne, ki dauki haka domin sakarai ne idan kika bi na zuciya zai ji ina ma da yana tare da wata macen tunda kin juya mishi baya." Yadda Hajiya take gaya min kuskuren da zan tafka idan nace ba zan koma gidan Tafida ba, sai na tsinci kaina da mikewa ma gyara zaman mayafina, ina ne rungumar Mufid. "tow Hajiya na shirya;" na fada kaina a sunkuye. "Yawwa yar albarka maza jeki Allah ya miki albarka." Haka na fito yana kallonmu, duk sai ya susucewa yana faɗin. "Hajiya idan tace anan zata kwana a kyale ni nima zan kwana anan." Hararanshi tayi cikin harshen kanuri ta ce. "hala baka da lafiya ne ko? Maza ka wuce da ita ka rarrashita an gaya maka haka zai sama muku zaman lafiya ne? Dole sai da rarrashi da ban baki zata manta da wani abu maza ɗauketa ku tafi! Allah ya baku zaman lafiya!" "Amin Ya Allah!" Ya fada, wani kula ta dauka ta raka mu da shi, ina murmushi. "Hajiya baki gajiya ne?" "Har yau gani nake kamar dan Babyn nan da na bari a wata goma sha daya ne a gabana shi yasa bana jin gajiya!" Murmushi yayi yana faɗin. "Hajiya kada ki saka Ummu ta rena na ni!" Duddu ta zuba mishi tana faɗin. "Tafi can ja'iri!" Haka muka fito security suka amshi kular hannunta suna gaishe ta sai albarka take saka musu, muma muka mata sai da safe. Tunda muka bar gidan na kasa sake jiki da Tafida, ban sani ba ko haka shine irin nawa fushin amma na kasa sake jiki dashi , kuma shima da ya gane bai min dole ba, da muka isa gidan bangarena can na wuce ya zuba min idanun. Murmushi yayi yana faɗin. "Ran yan mata a b'ace yake." Haka ya kawo min Mufidah, ma gyara musu kwnanciya. "yau Ummu ban yi wanka ba, kin lalata ni kwana biyu ke kike min kome yau kuma kin ajiye subsidy din da kike min anya ba karshen rayuwata ba ne ya zo!" "Muje kayi wanka amma ni yau bana son hayaniya ne!" "Tow Yan matana!" Ban dakin na wuce ba hada mishi ruwan wanka zan fito ya tare ni. "Ki taimaka min muyi tare!" "Don Allah!" Na furta muryana yana rawa. "ok ba damuwa!" Na bashi hanya ya shige yayi wankar yana fitowa ya samu har na kashe wutar dakin ina kwance. Saka kaya ba ya hauro gadon ya kwanta a bayana, bai nime kome ba, amma kuma naji dadin haka domin zuciyata a cunkoshe yake da damuwa. Daga ni har shi babu wanda ya samu damar rintsawa saboda a kwanakin da muka yi ko ayu albarka, amma kuma hakan ya saka ni fahimtar wani abu shi mutum ne da baya iya takura maka a da can Tafida bai takura min ba ya bar ni sakaka kamar goyon gwauro . Haka muka kwana. *Hajiya* Da sassafe ta saka drive ya Kaita gidan Abba, tana shiga ta samu wanke wanke kowa na dakinsa. Kofar Inna ta nufa anan suka gaisa ta mata Barka da dawowa har suka tab'a hira kafin nan Hajiya ta fara gaya mata abinda ya kawo ta, shiru Inna tayi kafin ta ce mata. "Tow yanzu Yaron nan Sa'adiyya Mairamu ya ce Tafida da Ummu suka mishi duka cikin shi ma wata biyu ya zube, suna asibitin har yanzu Jadda bai ce kome ba. Kasan haka ya kama Yaron Asiya ya mishi duka aka ce fuskar Asiya kamar yayi karo da jirgin kasa, Ni lamarin Tafida bata bani mamaki amma Yaron nan Saadiya yasan Tafida yanzu hankalinta yana kan matanshi Ummu don haka ya dace ayi hakuri da juna amma Hindu ya ce ba a mishi adalci ba!" Ran Hajiya ya b'aci ta fara faɗa faɗa, abin da ya tashi yan gidan har Abba haka yasa kafin wani lokaci lamarin ya rincabe, domin itama Shuwa ta dawo gida daukar wasu kayan, aka yi ta bata kashi da bala'i.. Hajiya Tayi rantsuwa ko Saadiya ta daina shiga harkan Ummu ko kuma Hindu ta bude mata dakin zawarci domin a tsaye take akan Ummu ba Ummu ta haifa ba amma babu wanda ya isa taka Ummu, kuma Maryam da Rukayya idan suka sake zuwa wurin Ummu Allah ya isa bata yafe ba, tunda ta roke su akan su fita harkan Ummu amma sun ki! Sannan ta bar gidan. *Ummu* A hankali labarin na saka Tafida ya daki Saadiya cikinta ya zube, maganar nan har IG da wasu blogspot aka dinga yayyata ni, har facebook ana ta kai zancen, a lokacin Ummu Kulsum da Ummu Rooman, suka fi kowa maida martani, saboda Saadiya tana da kawaye fitinanne irinta, haka yasa suka yi ta saka hotonta da hotunan mu da Tafida, ana ta mana zagin zogale, Ni dai ban san meke faruwa ba sai da Mahirah ta gaya min ita da Aunty Saadika!" Sannan na san meke faruwa, musamman da aka alakanta zubda cikin da cewa don kada su mori tafida ne tunda nayi mishi asiri shi da Iyayenshi. Na sake fita hayacina, domin al'amarin ya girgiza ni kuka kawai nake ina jin kamar zan mutu, ranar da aka ɗauki azumi na ashirin da biyar ranar bakona yazo, haka ya ƙara min yawan rikici da fushi sama da kullum. Shi kanshi Tafida bayi da nutsuwa domin matar Deen ta haihuwa, kwana biyu da suka wuce, kuma ina kai musu abinci, haka yasa nake bala'in jin haushinsa, ranar da muka kai na tsaya waya da Mama da ta kira ni, nake gaya mata matar deen ta haihu na zo kawo mata abinci ne. Muka gaisa komawa gefe nayi na zauna security suna tsaye a gefe can, naji wasu mata suna faɗin. "Eh ita ce wallahi, ita ce ta saka Gwamna a corner ai kin san ba banza ba." Sallama nayi da Mama na juya ina kallonsu, biyu nurse ne sauran kuma irin masu zuwa ganin likita ne ko me oho, takawa nayi har gabansu. Na tsaya tare da murmushi na ce musu. "tazo ta same ni da mijina ne, kun san azabar da na sha kafin ya zama gwamna? Kun san sau nawa na kwana ina kuka? Sau nawa na kwana ina gayawa Allah kuka na? Kun sani ne? Kawai don kun gani da shi muna dariya ba yana nufin jin dadi muka samu ba, ba zaku gane halin da kowacce mace da mijinta ya zama wani abu ta fuskanta ba sai Allah ya kai mazajenku matakin nasara, kafin yau har hotuna an saka akan na gudu waye ta tanbaya me yasa na gudu? Kawai daga labari yazo sai ku zauna kuna bata lokacinku mtseew!" Na wuce , Deen da Tafida da suka zo wurin suna kallonmu, sai bayan tafiyata suka karasa wurin take matan suka mike. "Kuna wasa da abincinku ne ko? Kanwata ce idan na kara jin wani gulma asibitin zan saka hannu a rufe! Munafukan banza." Inji Deen. Tunda na shiga dakin muke hira da Jalilah da taxo itama. "Ni abincin Aunty Baby zanci!" "Allah baki isa ba, Ummu bani abincin nan kafin wannan mara kirkin su hadu da yayanta su cinye!" Mamanta kuwa sai dariya take mana. "Ina su yan biyu?" "Suna gidan Hajiya idan zan wuce zan amshi su!" Nan muka ta hira sama-sama har suka shigo sannan na tashi zan tafi ya ce min." Na sallame su Matori a motatta zamu tafi,!" "Tow!" Na fada ina jingina sai da ya gama muka fito gidan Hajiya ya wuce muka dauki Yaran muka nufi gidanmu, ganin yadda nake shan kamshi ya tattara ni ya ajiye a gefe, domin ya lura bana sallah tun da ya ga ban bishi sallah Magariba da Isha ba, da asuba ma haka sai ya share ya gane bana sallah ne, a haka ya kira wata Doctor Falmata ya shiga tambayeta me ke saka mata fushi da jin rigima, ta tambaye shi akwai ciki ne ya ce babu ta ce "amma tana haila ko?" "Eh ta fara tun shekaranjiya!" "Shima yana tunzira mace!" Taya ta gaya mishi abubuwan da suke kawo saurin fushi. Ya mata godiya ya kashe wayar. Ina kwance aka turo min sakon. _Kamar yadda kika yiwa Sa'adiyya sanadin cikinta In sha Allah Yaranki da kike alfahari da su sai kin rasasu in sha Allah_ wannan abin ya tashi hankalina. Da sauri na kwashe yaran na nufi bangarenshi cikin kuka na zube a gabanshi. "me yasa ka dake ta, me yasa Aliyu yanzu Yarana zasu amshi abin da basu aikata ba Wayyo Allah na, ya zan yi da rayuwata ne, tunda na tsallake maganar mama na biyo ka nake fuskarta tashin hankali.." amsar wayar yayi yana kallon rubutun. Kafin ya kira layin malam Zailani. "Baba Malam!" "Haidara na mutane Madina!" Ya sake murmushi yana faɗin. "Wani abu ne?" A hankali ya kara gaida shi kafin ya gaya mishi kome, dariya Malam yayi yana faɗin. "Ummu uwar matsorata, kyaleta kada ka nuna mata akwai babu wani abu, in sha Allah babu wanda ya isa ya same ku, idan ka ga wani abu ya faru ka saka cikin kaddaranku ce!" Dariya Malam yake yana kara zoyalarsu" domin shi dai bai ga abin tashin hankali ba, don haka ya ce mishi. "Gobe ayi yanka a raba sadaka! Akwai jarabawa bawa a daure a karba da hakuri haka shine cikar imani, Allah ya muku albarka sannan Ali kayi bincike da kyau, ka kuma gyara zamantakewarka da iyalinka haka zai sama kama nutsuwa amma abin sai godiyar Ubangiji!"........... ```All spicess Jollof mix BBQ mix Thyme plus Garam masala Curry powder``` ```Special zobo Special yaji Spice kuli kuli Miyar kuka Miyar kubewa Special daddawa``` ```Garin masa/sinasir Garin alale da kosai Garin kunun tsamiya Garin kunun aya``` *Shin ko kun san kayan kamshin da kayan zobo tare da duk wani dangin kayan abincin gargajiya da Ummu take amfani yana samuwa ne ta wurin Shaharariyar me kayan kamshi na AIDA spicess! Ina mata yan yayi ina masu abinci na online kayanku ya tsinke a gindin kaba, ga Hajiya Aida special spicess tazo mana da kayan girki na gargajiya da na zama kai Jama'a wata miyar sai a makota! Na gwada sauran ku gwada ina jiranku! Za a iya samun Aida spices ta wanann number:+234 806 968 1068 Whatsp siyan na gari mai da kudi gida! Hajiya ki zama yar gayu me sauki ne amma girkin yan gayu dai da Aida spicess*🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Ka gyara mu'amalarka da yan uwanka, akwai waɗanda ka manta da su a cikin yan uwanka, munyi magana da mahaifinka, yana da kyau ka janyo su a jiki kada ka nuna bambanci a tsakaninsu. Ayi sadaka domin ita maganin masifa ce duk wasu fitittunnu." "In sha Allah!" Inji Tafida, kashe wayar yayi yana kallona da nake kuka kamar an aiko min da mutuwa. "Ya Isa haka, ki je ki kwanta." D'ago kai nayi na zuba mishi idanu. "Kasan me suka ce?" "Gashi nan a rubuce, sannan idan kika razana haka yana nufin wani yana bibiyarki kenan!" Gabana ne ya fadi sai yanzu lissafin ya zo min Mahmoud, hannuna dukka biyu na saka a bakina. Wasu irin hawaye ne suka shiga wasan tsare a idanuna taya aka yi su Maryama suka zo nan gidan? Taya Mahmoud ya san ina tare da Tafida? Taya ya san ina gidan nan? A hankali na mike xan fita bayan na wauci wayata. "Tow me yasa kike kashe ni da wannan shiru da kukan naki ne? Me ye nayi miki da na cancanci kyautar azaba daga gare ki? Kin san yadda nake ji a raina a idan na ga ruwan hawaye na zuba a idanunki? Kin san yadda nake kuntatta a dalilin kukanki? Gaya min meye zan yi ki daina muka?" Ya fada da karfi yana girgixa ni. "Kai laifintu tuni hukuncin laifin nake amsa? Ban san yadda zan gaya maka ba amma da ciwo, da zafi da kuna ka bude idanunka a cikin tashin hankalin da nake ciki, ban aikata kome ba amma saboda mutum daya kullum da zullumi nake kwana saboda shi gani nake wata rana zaka iya juya min baya, nemi rabuwa da kai ba sai don dalili daya dalilin da wata rana zai iya kashe ni har mutuwata don Allah kada ka tambaye ni mai ya faru domin bani da Ansarta, sai dai daga ranar da ka tsinci gawata ka zurfaffa bincike domin tashin hankalin barina da kayi kowani kare da doki yana tozartani!" Da sauri ya sake ni cikin wani tashin hankali, muryan shi na rawa ya ce min. "Me ya faru? Me aka miki!" Durkusawa nayi ina sauke wani wahalallen ajiyar zuciya, saboda kirjina da yayi nauyi." Zan kwanta" na fada ina dafe kirjina, daukata yayi ya kwantar da ni, sannan ya kalli yaran da suke kananan kuka,Sagir ya kira sannan ya kira Kaninshi Sharif a karon farko a rayuwarsa y gaya mishi abin da zai mishi, juya kaina nake ina jin kamar numfashina zai iya daukewa na fara yunkurin tashi. Ta d'aga ni, ya zaunar da ni sannan ya tafi ya dauko min doguwar riga, domin kayan jikina kananunne. Yazo ya saka min a kan rigar sannan ya rufa min bargo, ina kwance a kishingide Sagir ya iso, ruwa ya saka min tare da allurai, kafin ya zauna yana tattaunawa shi da Tafida. Suna cikin haka Matori ya kira shi yace ga baki sun zo, "su shigo!" Hajiya ce Tafida ya dauko domin shi bai san waye zai dauko a wannan lokacin ba, kowa so yake ga bayanshi."Innalillahi wainnalihir rajou! Meke damunta?" Kallonta yayi kafin ya mike yana bata wuri ta zauna ya kalli Sharif. "Sharifai!" "Na'am!" "Ya Ummun da jiki?" " sauki sosai! Na gode sosai!" "Ba kome xan tafi!" "Da wuri haka? Dama akwai aikin da xan baka ko kana da free time?" "Ba damuwa Tafida!" "Yawwa muje!" Haka suka fita ya bashi sakon sannan ya tafi dama sadaka ce da yanka. Ya bar gidan yana godiya, kallon agogon hannun shi yayi kafin ya kira mahaucin da yake aikin yankan gidan Abba ya gaya mishi abin da yake bukata, sannan ya tura mishi kudin da Tafida ya turo ya mishi kuɗin da yawa, ya kuma rubuta a cikin sakon, *Ba yawwa ka sayi kankana da sauran!* Saniyar miliyan daya zai saya Tafida ya tura mishi miliyan biyu da rabi! Kiran wayar shi yayi ya ce mishi. "Saniya daya ka ce kuma ka turo!" "Kada ka damu ka saka mai da sauran sannan ka sha kankana domin nasan tun Muna yara akwai soyayya da kankana?" Murmushi yayi yana faɗin. "Kudin yayi yawa!" "A cikin albashina ne ba a cikin dukiyar al'umma ba!" "Alhamdulillahi Ubangiji ya ƙara dafa maka!" Daga haka suka yi sallama. A bangaren Tafida tunda Hajiya tazo shima ya narke bai da lafiya hararanshi tayi ta mai da hankalinta kan Ummu. ** *Mahmoud* A can ranar da yayi yunkurin yin fyade wa Ummu akwai wani abu da ya aikata da ya zame mishi majidadinsa! Kafin Ummu ta fito ya dauki wayarshi mai kiran Black berry, ya saita shi yadda zai ɗaukar mishi duk abin da ya faru. Haka yasa shi duk fadar da suka yi jan towel din Ummu da yayi ya ga tsiraicinta, yana nad'e cikin videon ya san Ummu ko zata mutu ba zata tab'a bashi kanta ba. Amma idan yayi amfani da videon yasan abin da yafi kanta sai ta bashi. Haka yasa kafin ya tura mata sakon ya fara kiranta yana faɗin. "ki duba wayarki na ga baki Whatsp na turo miki wani sako!" Bayan ta gani ya ga babu al'amarin ta kuma a online bayan ta ga sakon, sake tura mata yayi da abin da ya sake jifata cikin zullumi. Murmushi yayi yana faɗin.."Duk inda kika tafi kika dawo Ummu wannan dukiyar sai na tab'a naji yadda kike kema!" *** *Ummu* Wannan lokacin nafi sha'awaar mutuwa da rayuwata, sai nake ganin kamar barin umarnin Mama da nayi yasa ni nake fuskarta azabar rayuwa haka. Bude idanun nayi ma ganni a dakinshi. Yana zaune a gefena hannunshi cikin nawa. "Ya jikin naki?" Hadiye yawu nayi kafin na juya naga iya Mufidah ce a gefena. "Ina!" "Yana bayan Hajiya tazo tana kitchen!" Ajiyar zuciya na sauke, kafin na lumshe idanu. "Don Allah ka mai da ni gida!" "Na ji amma sai kin warke." "Amma na warke ai!" "Da saura!" Sai da ruwan ya kare ya cire min da kanshi sannan ya haɗa min ruwa nayi wanka, kafin na fito ya cire min kayan da zan saka, sannan na fito na shirya. "Ya jikin naki?" "Da sauki kan!" Haka na koma na kwanta, ya gayawa Sagir shi ya gaya mishi yadda xan mai da min wani ruwan. Kwana biyu ina kwance Hajiya ke min kome domin ta dawo kusa da ni, Yaran ma a wurinta suke. Haka yasa nima kome yazo min da sauri. Ana jibi sallah na matsa ya kai ni Biu, haka muka tafi Hajiya ta koma gida, an karbe da farin ciki. Haka na kwanta a kafadar Babana, yayi ta tambayata ko akwai wani abu ne? Na ce mishi babu. A daren ranar muka dawo gida. Washi gari Jajiberan sallah, muka tashi aikin sallah, wuni nayi ina aiki domin ba wani abu ba ne a wurina don ma yana ta min faɗa, na share shi kafin karfe biyu na rana na gama cin-cin da cake da nayi, sai soyayya da dambun nama da nayi kadan. Sai dai kuma a duk lokacin da na tuna da sakon Mahmoud ji nake kamar zan mutu, domin wani irin bugawa zuciyata take sau biyu ina kona cin-cin sai da Tafida yazo mun faɗa. Dakinshi na shiga nayi alola, sannan na duba abin da Hajiya ta bamu, na zo na sha wunin ranar shi nayi ta sha ina karawa da abubuwan da zai gyara min jiki. Tunda ya ga ina sallah, sai ya zama kamar ɗan Maraya yayi ta narke min kamar man shanu. Murmushi nake mishi domin ya cancanci nayi mishi murmushi. A hankali muka gama kome, sannan na wuce bangarena nayi wanka ina zaune wayata tana saman gado naji tayi ƙara. Tashi nayi na dauki wayar Tinah ce a hankali na dauka ina faɗin. "Tuba nake!" "Yar dad'i miji kin manta abokiyar gwagwarmaya!" "Kiyi hakuri Tinah ina cikin damuwa ne!" "Jikina ya bani!" Zama nayi a bakin gadon na rasa yadda xan mata bayani. Sai na mata karya tare da gaya mata abin da ya faru Mama ta tafi Umara na biyo tafida muna cin amanarta. Dariya yayi tana cewa, "normal ne ai!" Jin ta kawai nayi amma ba shine asalin abin da nake son gaya mata ba, wani irin tsoro yasa na yi shiru. Sallama muka yi sannan na kashe wayar, shiryawa nayi sosai sannan na wuce wurinsa da Yaran da suke rarrafe. Zama nayi ina kallonshi.. ajiyar zuciya na sauke ina kallon wani Turkiyya drama ada aka saka a MBC 4, yadda yaga na zubawa tv idanun yayi dariya. "Me kika fahimta!" "Matar ta gano mijinta da Aminiyarta suna cin amanarta, haka yasa ta dauki matakin tura kawar ta window!" "Hmm! Ni idan na kama mata ta, da abokina ba zan kashe su ba amma xan tabbatar da na basu sakamakon da sune zasu bukaci mutuwa da kansu. Sannan ki lura ita kawar har hoton kawar ta samu a wayar mijinta da kuma ita kawar, haka yasa ta tabbatar da mijinta yana cin amanarta. Mace ma kenan ta dauki wannan kasadar ina kuma namiji ai ina ga sai garin nan yayi min kad'an da shi kwarton domin wallahi sai na yanke mishi azzakarinsa! Ita kuma na rabu da ita na barta da Allah da haduwarta da shi." Hawaye ne ya zubo min yau naji na kara tsanar Mahmoud, "idan kuma aka ce ni na aikata?" Kallona yayi yana hararata. "Ba zan yarda ba domin babu alamar kin aikata wani abu don ni ne mutum na farko da na fara sanin darajarki. Ke nemi wata rigimar ban da wannan." Girgixa kai yayi yana faɗin. "Ban da jaraba irin taki har da kuka wai meye matsalar da batun cin amana haka kawai kina kukan banza yau zaki gaya min dalilinki nayi min bori babu gaira babu dalili!" Tura baki nayi na wuce kitchen na fara fito da kayan abincin bude baki, ina gamawa ana kiran sallah , addu'a yayi sannan ya shafa na taya shi, bude baki yayi ina kallonshi labarin Fim din nan ya tsaya min a rai, haka yasa har muka gama ban kara nutsuwa. Wayata ma bakiɗaya na kashe ta. A daren dakyar Tafida ya kyale ni, na kasa barci tunda muka fito wanka. Parlour na dawo na zauna, tare da kunna wayata domin yau kamar jira yake mu fito wanka ya kama barci. Yayi gaba da shi, shine na samu na fito, shima yana bukatar hutu. Wayata ce ta kawo, na tsura mata idanu. Sakonnin Mahmoud na fara gani hawaye ne ya cika min idanun na dafe goshina. *Zuwa yanzu ya dace ki bar Tafida! Domin idan na sake wannan fefen videon kujeransa da mutuncinsa duk zasu tafi! Waye zai damu da Fyade ne? Hmm! Kiyi tunani Ummu ki kashe aurenki kawai ina jiranki tunda ba zaki iya shagali da aurenki ba!* A hankali na wuce kitchen na rufe kofar na fashe da wani irin kuka, ina goge sakon wayar, layin na cire na karya shi sannan na tattaune shi na sha ruwa akai, wayar kuwa bani da wani mafita da ya wuce na wurgata a ruwa. Na zauna na fashe da kuka ina jin kamar xan kashe kaina don bakinciki. *** "Deen* Yana kwance tunda Matarshi ta dawo ya samu nutsuwa, wayarshi ce take kara a hankali ya janyota. "Hello!" "Yallabai akwai wani sako na tura maka ta email! Ya da kyau ka gani don Allah!" "Ok!" Ya fada yana kashe wayar. Ya cigaba da barcinsa. Da asuba da ya tashi sahur ya ga tuna, da sauri ya kunna wayar, sakon da aka turo mishi ya gani, a hankali ya fara dubawa. Jikinshi rawa ya dauka, yayi maza ya kira Number. "Kwaro me yasa baka gaya min ba?" "Yallabai ina cikin mutane ne, ba zai yiwu na gaya maka ba, yallabai His Excellency zaka fara covering ba sauran, nasan is not easy zakulo irin wannan abin, amma akwai matsala!" "Mahmoud!" Ya kira sunanshi. "Yes Sir nima abin nayi mamaki kenan, har sai yaushe zaka bayyana shi." "Bana son Ummu ta shiga tashin hankali ne, amma na jima da sanin yana bibiyarta na gode zan cigaba da tuntubarka." Ya kashe wayar, shiru yayi yana mamakin abokinsu yadda yake abin da ransa yaƙe so. Tashi yayi ya leka masu jego, bayan ya gansu yayi shiru yana kallonsu, Uwar da jaririnta. Murmushi yayi sannan ya fito waje, haka ya koma daki ya kwanta ya kira Number dazun. "Duk rintsi kada ka bayyana kanka, sai ka ji wani abu ya faru mara dadi kayi ƙoƙarin haduwa da Malam Zailani! Ka fahimci." "In sha Allah!" "Kai fa yallabai!" "Ba kome! Zan samu Mahmoud kada kayi gaggawan fitowa nasan Mahmoud!" *** *Tafida* A hankali yake shirinsa, kamar ruwa ya cinye shi, yau ya tashi da wani irin yana duk da kasancewar gobe sallah, kunna wayarshi yayi a yana jin wani irin sanyi har cikin cikinsa. Kallona yayi da nake kwance yau shi ya shirya duk da bayan sallah asuba Deen ya kira shi akan zai zo shi da Mahmoud! Haka yasa ya shirya a hankali ya juya yana kallon yadda nake kwance. "Yau ba zaki tashi ba ne?" A hankali na bude idanuna na kalle shi. "Kaina na bala'in ciwo!" "Ko na kira Dr Sagir ne?" "A'a ba sai ka kira shi ba, zan kwanta." Na fada ina rufe idanuna. "Deen ya kira ni tun dazun zasu zo da Mahmoud wai akwai maganar da za ayi har dake!" Ban san lokacin da na tashi zaune ba ina dafe kirjina. "Ni?" "Eh!" "Innalillahi wainnalihir rajou! Tow me ya faru?" Yadda na rikice ya da shi matsowa ya zauna a gefena. "Ke ba wani abu aka ce min yi ba, kai Allah ya shirya ki ." Kwantar da kai nayi a pillow na share shi naki magana, yanayin da na shiga Allah kaɗai yasa ni tun da nayi sahur nake gayawa Allah abin da Mahmoud ya min Allah ya saka min. Wayar Tafida ne yayi kara, ya ɗauka yana sakawa a kunne. "Innalillahi wainnalihir rajou! Ke dauko Yaran nan da kayansu, Deen!" Ya fada da sauri, tashi nayi zan mike wani irin duhu na gani a idanuna a hankali na ji nima na zube a wurin. Ban kara sanin me ya faru ba, tashin hankalin da Tafida ya shiga babu iyaka, Ummu ya kai Mota ya dawo ya dauki Yaran, ya kai su sannan ya kira Sharif ya gaya mishi ya dauko Hajiya ya kawo ta Asibiti. Da yake Sharif yana wurin rabon sadaka, haka yasa bai zo da wuri ba har dan wani lokaci, Hajiya tayi matukar razana musamman ganin halin da Tafida ya shiga bakiɗaya likitocin da suke kan Deen sun fi ashirin, an yi juyin duniya ya fita amma yace babu inda zai je, idanunshi yana kan Deen, hawaye na zuba mishi. Idan ya rasa Deen, har abada ba zai samu me cike mishi gurbin Deen ba, yana tsaye har aka fito da Deen wanda kanshi da da jikinshi aka yi masa sara kamar ba dan adam ba, an mishi dinki kamar wani kwarya. Fitowa yayi ya wuce waje, matar Deen da Ammah ya gani suna ta kuka, gidan Malam Zailani ya nufa. Duk da yau shi da kanshi yake tuki ga jami'an tsaro na binshi. A zauren karatu ya same shi zubewa yayi akan gwiwarshi. "Ka gaya min me yasa Deen?" "Me yasa Deen?" Malam ya tambaye shi, sai yayi murmushi ya ce mishi."wallahi ban tab'a istahara, na ji babban al'amari akan wasu ba sai akan ku ukun nan!" Murmushi yayi yana ƙara faɗin. "Istahara ba a ganin kome, amma daga ranar da na ganka da shi, na fahimci ba iya aboki yake maka ba, akwai Babban al'amari a tare da shi. Aliyu yanzu ya dace ka nutsu wanda yake tayaka yaki yana kwance ko? Duk wanda yayi wannan abin ba kai yake bibiya ba, abu me daraja yake bi a tare da kai. Mulkinka baya gaban wanda yayi haka!" "Taya ka sani?" "Saboda abin ya faru ne a akan idanun mutane dayawa, kenan ka ga babu bukatar sai na sani tunda ko ban je ba za a gaya min. " "Me ya dace nayi?" "Da farko ka dauki aikin da wasa ne? Kai banda Mahaifiyarka tana hana idanunta barci ai nimanka da ake sai ka kusan barin duniya zasu kyaleka. " Rufe fuskarsa yayi yana faɗin, "duk wnada yayiwa Deen haka sai na tabbatar da hukuma sun rataye shi." "Allah zaka roka ya tona asirinsa ba hukuma ba domin za a shekara ana nimansa ba a ganshi ba, ka ajiye a ranka yanzu ake lamarin kuma ba za a daina ba sai ko idan zaku mutu kai da Deen domin kuwa ka saka idanun akanshi don lamarin bai kare ba." Tashi yayi ya juya zai fita, "Ka godewa Allah, an zubar da jini yau, da kuma addu'a da ake kai, daga yau har ranar da zaka sauka akan kujeran ka tabbatar an yi sadaka ana rabawa mutane idan ta kama har da abinci ka bada ayi, Kasan inda kake kuwa? Wasu da jinin mutane suke bukatar zuwa wurin basu samu ba kai kuwa Allah ya d'aga darajarka, kana wasa." Fita yayi ya kira Sharif. "Zan tura maka kudi a sayi kayan abinci a raba sadaka!" Ya fada yana shiga motarshi, kifa kai yayi ya fashe da wani irin kuka. Domin bai tab'a ɗauka lamarin haka yake ba, Ummu da Deen suka cikin wani hali, hawaye ne yake zuba mishi, yau daya yaji ashe yana da rauni sosai haka. Wayarshi ya dauka ya kira Matori! "Matori a saka idanun akan Deen don Allah!" "An gama" duk sai ya kasa aikin, a hankali aka buga kofar ya d'ago kai Malam Zailani ya gani yana murmushi, sauke glass din motar yayi. "ungo wannan sannan ka fita a wurin tukin su ja ka." Amsa yayi, murmushi Malam yayi yana kara faɗin. "ka fita zasu kai ka, sannan ka godewa Allah da lamarin zo a haka." Fita yayi daga cikin security din ya shiga gabatar motar, sannan ya ja suka bar kofar gidan. *Malam Zailani* "In sha Allah Deen zaka tashi, nufinka na alkhairi da alkhairi da yake zuciyarka zaka tashi in sha Allah,... ```All spicess Jollof mix BBQ mix Thyme plus Garam masala Curry powder``` ```Special zobo Special yaji Spice kuli kuli Miyar kuka Miyar kubewa Special daddawa``` ```Garin masa/sinasir Garin alale da kosai Garin kunun tsamiya Garin kunun aya``` *Shin ko kun san kayan kamshin da kayan zobo tare da duk wani dangin kayan abincin gargajiya da Ummu take amfani yana samuwa ne ta wurin Shaharariyar me kayan kamshi na AIDA spicess! Ina mata yan yayi ina masu abinci na online kayanku ya tsinke a gindin kaba, ga Hajiya Aida special spicess tazo mana da kayan girki na gargajiya da na zama kai Jama'a wata miyar sai a makota! Na gwada sauran ku gwada ina jiranku! Za a iya samun Aida spices ta wanann number:+234 806 968 1068 Whatsp siyan na gari mai da kudi gida! Hajiya ki zama yar gayu me sauki ne amma girkin yan gayu dai da Aida spicess*🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 *Ummu* Karfe shida na yamma na farka, Uwani na gani a dakin tana ta shirya abin bude baki. "Aunty Baby kin farka?" Lumshe idanu nayi na bude, "yanzu Babansu Mufidah ya shigo." Kokarin tashi nayi ta ajiye abin hannunta, ta d'aga ni "na gode!" Karin ruwan dake hannun nawa na kalla kafin na kalli bakin kofar da ake kokarin shigowa. Hijab na janyo domin na saka Uwani ta taimaka min, shigowa yayi yaga muna saka hijab. "Mahmoud zai gaishe ki!" Kura masa ido nayi kafin na sunkuyar da kai, umarni ya basu suka shigo. Ban sake na d'ago kai ba, "Man ko dai Maman twins ta sake karban wasu twins ne?" Ban kalli fuskar Tafida amma yadda naji ya amsa ciki-ciki na fahimci maganar bata mishi ba, haka yasa na kara sunkuyar da kaina ƙasa. "Tow Allah ya baku lafiya!" "Amin Ya Allah!" Uwani ta fada tana mika min ruwan dumi, shima Tafida fita yayi. Ajiyar zuciya na sauke ina jin kamar na tsira daga Mahmoud. Ana bude baki Doctor Sagir ya shigo yana kallona, "Kashe kanki zaki yi ko? Wani irin damuwa ne da har jininki yana shirin tab'a zuciya. Idanuna ya cika da kwalla girgixa kai nayi, ina me hadiye yawun bakina, "kawai ciwon kai ne fa!" "Wai me ke damunki?" "Ba kome!" "Akwai mana Ummu waye zai ganki yace babu wani abu." Haka ya gama duba ni, sannan ya fita abinci aka kawo mana daga gidan Abba, a hankali na samu nayi sallah, sannan kwanta duk sai naji babu dad'i, washi gari aka tashi da bikin sallah, sai bayan sallah idi Abba da Baba suka zo, dama Deen mahaifinsu ya jima da rasuwa, Ammah ke faman fadi tashi. Yadda nayi azabar lalacewa yasa Abba da Babana suka yi ta min faɗa min ko ina da matsala ne nace musu babu kome, haka yasa Abba yace a kyale ni. Binsu nayi na ga Deen, sai da na kasa tsayuwa na fashe da kuka, haka kawai nake jin kamar akwai wani abu a wannan yanayin da muke ciki. Ga Matarshi da danyen jego, jarumar uwa irin Ammah tana tsaye akanshi idan ka cire jiya da tayi ta share kwalla. Komawa dakina nayi, na kwanta ina wani irin kuka, Deen ya bani tausayi. Haka lamarin ya kasance, a daren anan naji labarin za a tura shi abuja, domin zuciyar Tafida ya kasa nutsuwa da asibitin, a can asibitin da za akai shi akwai tsaro da kulawa, haka kuwa aka yi da shi a tafiyar suka wuce Abuja. *Mahmoud* Kifawa mutumin gabanshi mari yayi, kamar zai kashe lalata mishi fuska. Sai hakuri yake bashi kafin ya kyale shi. "Me yasa ka sare shi na tare da ka kashe shi ba? Kasan waye Tafida kuwa? Kasan waye shi kuwa? Yaron da kaf arewa babu mara kunyar da ya tsaya a ƙwaryan majalisa yayiwa yan majalisu rashin mutunci! Bari na gaya maka ka tabbatar da ka goge duk wani shaidar da za a gano ka, idan hali ka hada kayan Yaranka ku bar Maiduguri idan ka kara jin motsinka sai na kashe ka!" "Kayi hakuri! Amma akwai da yasan zaku hadu da Deen! Mun bibiye wayarshi bai dauka ba, asalima kiran baya shiga." "Ina wayar yaƙe?" Mika mishi yayi tare da kallon wayar duba wayar yayi ya ga babu duk wani abu me muhimmanci layin daya ne da aka rubuta Begger! Jinjina kai Mahmoud yayi yana faɗin. "an duba waye shi?" "Mun bibiye layin baya shiga, sannan da nace Cuna ya duba mana kome akan layin wallahi babu kome sai dai a wayar naji yana faɗin. Haka" ya kunna wayar sai ga Muryan Deen faɗin. "ka tabbatar da yi nisa da Maiduguri, sannan kada ka kara amfani da wayarka saboda nasan zasu bibiye IP codenka, idan ka ji labarin bana raye kada ka bayyana kanka, ka nutsu zata ji da kome. Ka bata kome tare da wasikar da na baka zasu nime Tafida ka kula da rayuwarka ka yi tunani idan kanwarka ce Ummu Hadiyya waye zai tsaya maka, sannan ka ji a ranka idan Aliyu ne Abokinka me zaka yi zaka kyale rayuwarshi ta lalace ne saboda kawai Mahmoud ya maka barazana, ka tabbatar ka yi record nima ina yi." Cikin fusata ya buga wayar a kasa, yana huci yana faɗin. "Ku nimo min Yaron a duk inda yake sai na kashe shi!" "Ai babu lamar shi a garin nan, domin mun yi kome don yaron ya fada tarkon mu amma babu alamarshi, idan na fahimci wani abu Deen tarko ya maka, ka duba wannan." Ya mika mishi wata takarda ya cigaba da cewa. "A lokacin da muke saran shi ya ce na baka." Amsa yayi yana kallon takardan kafin ya warware. _Kai mahaukaci! Ka sani yadda kake yiwa Ummu barazana! Na saka ka ka fada tarkona! Shi yasa na fito maka a mutum kai kuma dake jaki baka gane kome daga mata dai mata, baka iya lissafi irin na maza! Daga lokacin da kayi wani motsi! Mutane na suna kallonka! Kana motsi ban san wani irin yanayi zaka tsinci kanka ba! Mahmoud kana tab'a Ummu kai ma za a tab'a ka, domin na bada sako a bawa Ammyn na yadda kake lalata yar mutane! Kasan me? Duk motsin kowa yana sane musamman shashsha irinka. Ka hada hannu da mutane dayawa kowa ya juya baya saboda shakkar abin da zai faru, amma ka tab'a hijabin da ba naka ba! Ka duba Email dinka ka huta lafiya ko mutuwa nayi Ummu ta tsira idan kuma kana son Mahaifiyarka ta gano cewa kai din na musamman ne maza maza ka duba zaka ga abin mamaki kai jama'a duba_ _Flashing back!_ Ranar da Deen ya ware manyan masana akan cyber security ya dauko duk wani number da Tafida yake amfani da shi ya tafi har kamfanin Mtn ya karba, sannan ya kira Jabir Adam da dare. Bayan sun ci abinci ya mika mishi file yana faɗin. "Bana son kowa ya gane kai na musamman ne a gare ni! Wadannan numbers din, ka fahimci me nake nufi?" "Na fahimta amma maganar gaskiya sai dai ka ware laptop din da zan yi wannan aikin kasan muma ana bibiyarmu!" "Shi kenan gobe kazo ka amsa!" Haka Deen yayi bai tab'a yin abu bai gayawa Malam Zailani da Abba, su kuma suka mara mishi baya, haka yasa kome suna sane da shi, wasa gaske Deen ya saka idanu akan aikin a kaf numbers din babu matsala, sai number Sa'adiyya da Mahmoud da aka samu yawan kira a tsakaninsu da musayan sakonnin, tare da wasu bidiyo kazamai, a binciken ne ya suka hango videon da ya boye don razana Ummu, sannan shima Deen ya kara da wani irin bincike, a cikin gidan ya haɗa da masu yin aikin gidansu Mahmoud da drive da kome ya basu kudi me yawan gaske, tare da ce musu kawai su dauko mishi duk wani abu na tsiyar da Mahmoud yake, sannan kuma Deen ya kara bugan cikin Alguburo ya gaya mishi Mahmoud yana lalata yarinyar da take aiki a gidansu, haka yasa Deen yasa aka bibiyeta, da haka da hikima aka samu video daga ɓangarenta da kome, Deen ya shiga rayuwar Mahmoud ya zakulo kome, dama tun can yasan yana halinsa da son mata, a hankali ya cigaba da bibiyarshi, a lokacin da ya kara kama Mahmoud ya bar abin sai ya tab'a Ummu, kuma abin da ya faru kenan. Har zuwa shirin Deen da abin da cigaba da bibiyarshi da yake da abin da yake turawa Ummu,duk yana gani. Barazanar da yayiwa Ummu yasa shi fitar da kome, sannan ya kira Tafida wayewar garin jiya ya gaya mishi gasu nan zuwa tare da Mahmoud akan wani magana, sai gashi Mahmoud yasaka an bi motarshi an far mishi, wannan tashin hankalin yasa ya gayawa Jabir Adam ya gudu wurin Tinah, da ya gaya mata kome, amma ta saka idanun akan Mahmoud da Tafida, yanzu haka Jabir Adam yana garin Ibadan cikin tsaro, ita kuma Tinah tana Abuja tare da Tafida da Deen. --- A hankali Mahmoud ya duba wayarshi sako ne rututu, ta email dinsa a hankali videon ya bude na kan sunan Deen shine tsirara haihuwar Uwarshi da ubanshi, a kan Khairat, fita yayi yana jin zuciyarshi kamar zata buga. A kasar video ya ce mishi, _Akwai irinsa an tura kwafe dinsa kan wayar Ammyn hmm! Ban sani ba ko zata iya jure haka, kana kara motsi akan Ummu har gidan Tv za a turo kowa ya gani Mahmoud ko mutuwa nayi nasan baka isa taka Ummu da wannan abin ba, sai na saka ka biya abin da kayi don haka ni da kai Allah ya bawa me rabo sa'a ka sani ko mutuwa nayi ba zaka tab'a tsira ba sai an.kamaka don haka shawara ya rage naka kamar yadda kake da hannu haka nike da hannu akwai masu tsaya mana haka.ma Allah ya tsaya mana_ Shiru yayi kafin ya kalli yaranshi. "Ku bar garin nan, idan na matsa dayawa za a samu matsala kuje ta sha." Ya faɗa yana barin gidan, tabbas tunda Deen ya fada mishi ba makawa haka ne duk inda ya sake akwai matsala. Wani kira ne ya shigo mishi ya ɗauka. "Akwai nasara!" "Babu domin Safiyyudeen ba zai tab'a barin mu tab'a Tafida da iyalinsa ba, sai dai mu jira dama daya tal! Idan kuwa muka samu xan baka damar cimma matsaya ni na dauki nawa!" Daga can ajiyar zuciya aka sauke kafin ya ce mishi. "Kai da Hamza Safiyyudeen ya hana ku sakat ko? Idan ya mutu fa?" "Ba iya ni ba, kai da kake gefe sai mutuwarshi ya shafe ka, ka ajiye maganar tab'a Safiyyudeen domin Tafida mahaukaci ne daga kai har ni idan ya kamo mu, Borno yayi mana kaɗan." Ya kashe wayar yana tsaki. Tun daga ranar da aka sallame ni, ban kara kwana ɗaya ba sai gida. Kamar ban je ko ina ba, muna waya da Tafida lokaci zuwa lokaci da wayar Uwani don nawa wayar ta lalace. Sannan na gaya mishi na koma gida, don gidan ya min girma shima bai da nutsuwa yasa bai min magana ba, sati daya yayi ya dawo ya kama aiki, a can kuwa an canzawa Deen asibiti kafin Tafida ya bar garin, iya Tinah kadai take zuwa shima ba kasafai ba akwai masu kula da shi. Domin an b'adda kafa yadda ba za a bibiye shi ba. Tunda ya dawo bamu hadu ba, domin ya dawo da kwana ɗaya Mama ta dawo, kai murna kamar me amma zuciyata a razane nake, don kada a samu matsala wani ya labartawa Mama abinda nayi. Tsakanina da Tafida haduwa yayi wahala, aiki yake tsakaninsa da Allah, sai da aka yi sati uku cif kafin wata Juma'a yazo, cikin sanyin murya ya ce min.."ki roki Mama ki koma dakinki don Allah!" Tsoro yasa na kasa amsa mishi. "Tow ni zan mata magana tunda kina jin tsoro." "Gara kai ka mata magana!" A daren kafin ya tafi a zauren nan sai da ya lallabani yayi yadda yake so, amma ranshi a b'ace yake. Bai koma gida ba sai da ya kira Abba ya roke shi yayiwa Mama magana, shi kuma ya mishi alƙawarin zai yiwa Baba Bulama magana koda aka yiwa Mama magana bata ce kome ba, haka wata sati ya kuma shiga. An gama azumin sitta shawal, a lokacin na fara wani irin tsirfa, da zaben abinci. Bana son kamshin manja ko man gyad'a. Sam ban fahimci haka ba, abinci kuwa ina son mai yaji, duk zuciyata bata bani wani abu ba. Mufid ya fara wasu kananun rashin lafiya, wanda yasa dole na gayawa Tafida ya ce na tafi asibiti a duba shi, Mama ce ta mashi Yaron tana kallonshi tana sauraron wayar da muke da Tafida. "Tow shi kenan zan kai shi " na fada ina gyara daurin dan kwalina. "Kai Uwani manja nan nata bai da dad'i." Na wuce ban daki ina jin aman da ya taso min. Ka sake Mama tayi tana kallon yaron da yake fesa. Bakinta a sake tana kallona na amshi Yaron na fita ina mita a tsakar gida, itama fitowa tayi bakinta dauke da mamaki. Tsirta da yawun bakina nayi da ya yanko min kamar xan yi amai.... (Burinku ya cika kun kashe mama da mamaki ko?) ```All spicess Jollof mix BBQ mix Thyme plus Garam masala Curry powder``` ```Special zobo Special yaji Spice kuli kuli Miyar kuka Miyar kubewa Special daddawa``` ```Garin masa/sinasir Garin alale da kosai Garin kunun tsamiya Garin kunun aya``` *Shin ko kun san kayan kamshin da kayan zobo tare da duk wani dangin kayan abincin gargajiya da Ummu take amfani yana samuwa ne ta wurin Shaharariyar me kayan kamshi na AIDA spicess! Ina mata yan yayi ina masu abinci na online kayanku ya tsinke a gindin kaba, ga Hajiya Aida special spicess tazo mana da kayan girki na gargajiya da na zama kai Jama'a wata miyar sai a makota! Na gwada sauran ku gwada ina jiranku! Za a iya samun Aida spices ta wanann number:+234 806 968 1068 Whatsp siyan na gari mai da kudi gida! Hajiya ki zama yar gayu me sauki ne amma girkin yan gayu dai da Aida spicess*🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 "Gaskiya Uwani Allah zai kamaki da hakkina wannan wacce irin rayuwa ce, sam Manja nan bai da dad'i." "Kuma haka zaki dawo ki ci abincin da nayi da manja ban da gulma haka kawai ki hana ni kasuwancina!" Mama sai ta koma kakar wata mutummutumi, ni ban lura da halin ta ke ciki ba, nayi mata sallama saboda ya turo a dauke mu. *Mama* Idan hankalin Mama yayi dubu ya tashi, sannan wani abun da ta lura yadda Ummu take zumudi idan Tafida ya kira wayar Uwani, idan ma idanunta bai mata karya ba, har hiran dare suke, sau biyu tana kamata suna wayan dare, gyada kai take kawai tana tafa hannunta. "Uwani!" Ta kira ta, tana juye abincin sayarwa a babban kula, ta d'ago kai tana amsawa. "Na'am Mama" "Bayan tafiyata Umara tafida yana zuwa daukar Ummu ne?" A matuƙar razane ta zare idanu zuciyarta da Mama zata gani sai ta fahimci a razane take, amma ta boye tsoron tayi shiru kafin ta ce mata. " A'a, baya zuwa gaskiya ban ganshi ba." "Ba cewa nayi yana zuwa ba, baya turowa a dauke ta?" Uwani a matuƙar rude ta ce mata. "Gaskiya idan ba rashin lafiyar Deen ba gaskiya bai tab'a turowa a dauke ta ba, shima saboda Baba Sarkin noma ya zo ne!" Ajiyar zuciya ta sauke, bata kara magana ba, ita kan uwani tayi maza ta bar gidan, har wurin azhar tana baza idanun Ummu jiran Ummu, ai kuwa biyu da rabi sai gasu nan. *UMMU!* A matuƙar gajiye na dawo domin ina goye da Mufid, Mufidah tana hannuna na shiga gidan amsar Mufidah Mahira tayi tana min sannu. "yawwa!" Muka shige bangarenmu, har dakin Mama ta kai min ita, na zauna ina gaida Mama da take kan abin sallah. Sauke yaron nayi na wuce ban daki nayi alola, amma amai ya saka ni a gaba. Kura kofar idanun yayi ita ɗaya tasan yadda take ji. "A hankali na fito muka hada idanu. "Aman me kike yi haka Ummu?" Kallonta nayi shiru, mikewa tayi daga abin sallah ta bani wuri na dauki abin sallah. "Yaushe rabonki da bakonki!" Har na tadda kabbara, tambayar nan ya sani na wani juya a gigice. Murmushin takaici tayi tana kara kallona. "Yaranka wataninsu bakwai da wani abu, kai bana jin sun cika bakwai ma." Zubewa nayi a gabanta cikin tashin hankali da. "Mama ba abin da kike tsammani ba ne, ba ciki ba ne" na fada ina hadiye yawun bakina nayi, ai kuwa ya taso min da amai da sauri na koma ban daki na fara kwara amai, ba ma kome a cikina. "Don Ubanki zaki gaya min yaushe kika bashi kanki da kananun Yaranki?" Ya fada rike da muciya don na bata haushi, a gajiye da aman da nake, zare idanuna cikin tsoro na ce mata. "Don Allah kiyi hakuri!" "Zaki gaya min gaskiya ko sai naci Ubanki!" Ta daka min tsawar da yasa na fashe mata da kuka, domin yadda ta ja dagga zata maka min muciyar na ce mata. "Tun tafiyarki Umara ne, ya dauke ni wallahi ban san haka zai faru ba don Allah ki yi hakuri!" "Eyee binshi ma kika yi wato na hanaki farincikin rayuwa shine kika biye mishi yayi miki ciki Ummu Hadiyya? Ni kika watsawa kasa a idanun maza kira shi ya kwashe mu ba zaki zubar min da mutuncina ba, munafukar banza mara kunya!" Ta mika min wayarta cikin tsawa hannuna yana rawa na amsa, na fara saka number shi da na haddace. "Ni Ummu zaki mai da sakarai, har kin haddace number Mijinki! Maza kira shi!" Ina dial number shi sai gashi ya shiga, kashe kiran yayi na kara zare idanu hawaye na zuba min, na kara kira amma ina bai dauka ba, yadda Mama ta hayayakomin na manne da jikin bangon ban dakin, kamar yasan ina cikin wani tashin hankali ya kira ni. "Ummu ya jikin Babana?" Cikin shashekar kuka na ce mishi. "Don Allah kazo ka cece ni." "Kut da ban buga miki muciyar ba Ummu? Shine zai zo ya kwace shi yazo shima mara kunya ya gaya min dama dalilin biya min Umara kenan ban bashi ke ba ya dauke min ke ya dirka miki ciki!" Ta fada da karfi, "Wayyo Allah Mama don Allah kiyi hakuri gani nan zuwa!" Ai kuwa Mama ta cigaba da kurari tana fada kamar zata buge ni, kai na ga tashin hankalin da ban tab'a gani ba, ni sai ban damu da halin da nake ciki ba, yadda yake ta bata hakuri tana balbale shi da fada ya sani kuka, don wallahi tausayi yake bani. Juya tayi ta ce min m "wuce kiyi sallah ki shirya Yaranki, sai ki tafi Allah ya baku sa'a." Ta fita tana mita kamar zata aro baki ta kara, dakyar nayi sallah. *Ciki!* na furta a zuciyata, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, me yasa Tafida zai min haka, ban tab'a jin tausayin Yarana irin yau ba, a yanayin yadda mama takr magana Mufid ya sha nonon ciki ne, yasa ya fara kashi, ai kuwa ina idar da sallah yana shigowa unguwarmu daga karan saren dinsa. Ina zaune Mama ta shigo ta zabga min harara, tana faɗin " maza tattara kayanki gashi nan yazo ba xan iya abin kunya ba!" Shigowa gidan yayi gaisa da yan gidan da suke waje, da sallama ya shigo. Yadda yake tafiya a sanyayye yasa duk zafin ranta, sai taji tayi sanyi. Har cikin dakin suka shigo da shi, ta zauna a bakin gadon shi kuma ya zauna a bakin kofar dakin. "Aliyu ka kyauta min kenan?" Kasa d'ago kai yayi yana buga key din hannunshi a kasa, Mufidah da idanunta biyu ta ganshi tayi ta mika mishi hannu. "Wato ka tura ni Umara!" Kunya ce ta kama shi wanda bai tab'a jin irinta ba, "Sai ka ɗauke ku tafi Allah ya kyauta! Babanku ya gaya min kome!" D'agowa yayi da sauri yana faɗin. "a'a Mama ta zauna idan kika ji a ranki tayi mu tafi xan zo ɗaukarta!" Harara ta watsa mishi. "Eh ga tsohuwar banza ka cigaba da zuwa kuna rashin kunya a gabana ko? Ba dani ba wallahi oya maza ɗauketa ba zan iya ganin rashin kunyarku ba." "mama kiyi hakuri ba zan bishi ba, wallahi cewa suka yi ni ce na zubar mata da cikinta na rantse da Allah, zasu kashe ni ya zan yi da raina?" "Idan ya so ki mutu maza bani wuri " Abin da ya faru. Fitar Maman Ummu a dakin ta kira Alhaji Bulama tana fada Tafida yazo ta dirkawa Ummu ciki, ba tare da wani damuwa ba ya ce mata. "Alhamdulillahi kin ga ai dole ki bashi Matarshi idan dai ba ado zaki yi da ita ba, tun tafiyarki Umara ya dauke ta kuma ban hana shi ba, ban ga dalilin hana shi matarsa ba" "Alhaji da kai aka ci amanata?" "To don Allah wani amana aka ci? " Shiru tayi saboda yadda ya mai da abin wasa, daga karshe ya bata hakuri tare da mata bayani ta barsu kawai su tafi kafin mutanen gida su fahimci wani abu yana faruwa idan ma rana zata saka shi kenan, dake tana jin haushi tace su shirya kawai su tafi ba bata son ganinsu. Haka ta kashe wayar, tana gama haɗa kayanmu. Ganin yadda Tafida yake ta kallona a dame, yasa ta cewa. "Kai bana son munafunci ɗauketa ku bar min gida, lokacin da kika bi dadin kalamanshi ai kin manta da zan dawo ko zaki samu ciki sai da na gaya miki kanku rawa yake daga ke har shi, ki jira nasan abin da zan miki, jikinki yana rawa kika bashi ya dirka miki ciki ko tausayin wadannan bayin Allah da babu ruwansu baku ji ba, daga kai har ita kuka yi son ranku, maza ku bar min gida kafin a fara min gori tai kunika!" Daukar kayan yayi a bakin kofar gidan Matori ya amshi kayanmu, wasu mutane biyar suka shiga aka kwashe kayan da ya saura. Ina zaune a dakin ban fita ba ina kuka. "Zaki fita ko sai na karya kafarki munafukar banza!" "Amma don Allah a zubar da ci...." "Kauuuu!" Naji ta dauke ni da wani irin marin da ya fasa min hancina. "Da ana zubda ciki da naki zan fara zubarwa saboda bana son Ubanki amma haka na rungume ki har na haife ki ban tab'a tsanarki ba! Sakarya samodara! Fita min a gida kafin na tattaka ki!" Cikin kuka na fito a bakin kofar na same shi, yana kallona. Na rasa fahimtar haushi yake ji ko kuma bakin ciki yake ji, wani irin murmushi ya sakar min ya juya abinshi. "Aliyu!" "Na'am Mama!" Ya juyo yana kallonta kasa. "Na Barka da Allah idan ka cutar da ita, sannan ka saka idanun akanta kada ta zubar maka da ciki don sakarya ce bata da hankali! Duk wanda zai juyawa kyautar Allah baya sakarai ne Alhamdulillahi Ubangiji ya rabata da shi lafiya amma ka saka idanun kada ta zuvda maka ciki! Allah ya muku albarka!" "Allahummah Amin, Mungode sosai Mama Allah ya huci zuciyarki, kiyi hakuri da laifinmu ba zamu kara ba, na gode sosai Mama da gatan da kika min, na gode da bani Ummu a karo na biyu, na gode sosai na gode zan baki mamaki in sha Allah." Ya saka kai ya fita, "Idan kika kuskura wani abu ya samu cikinki da gayya Allah yana ganinki!" A hankali na fita daga cikin gidan. Ban san lokacin da kuka ya zo min ba, bai saurare ni ba ya bar gidan a mota na same shi, ya gyara kwanciyar Mufeedah ya amshi Mufid. "Na san tausayi yasa kika fada, zan kaisu gidan Hajiyata Doctor Falmata zata duba su." Kifa kaina nayi ina kuka har muka isa gidan Hajiya, ina jin shi yana waya da ita Doctor Falmata. A parlourn Hajiya na zube ina shashekar kuka. "Innalillahi wainnalihir rajou! Tafida mai ka mata kuma?" "Hajiya ban mata ba, Mama ce ta koro mu!" "Da tayi me?" "Da ta.." yadda na d'ago kai na kafe shi da idanun yasa shi cewa. "Kai Hajiya maganar nan da nauyi yake, amma za a yayesu Mufidah!" "Alhamdulillahi! Ubangiji ya raya su tafarkin addinin Muslunci, ita kuma ya sauke ta lafiya. Ya bata lafiyar shayarwa." Daukar yaran tayi tana sumbatar kansu. Haka nayi ta kuka tana rarrsshina tare da min nasiha, sannan ta ce min. "Gobe za a kawo su Nana kin ji, Asma'u zata zo ta zauna a wurinki! Ta rage miki aiki!" "Yar shekara bakwai ce zata taya ta aiki? Hmm idan zaku koma kawai wata sati ki dawo gidan, domin ummu ba zata zauna a government house ba!" "Allah ya nufa!" "Amin Hajiya! Amma zan tafi da Ummu Yaran yanzu za a zo a duba su!" Kaina ne ya fara ciwo na kwanta a kujerar, Hajiya ta nufi kitchen tana faɗin. "da kin shiga daki kuka kwanta ki huta!" Girgixa kai nayi, tana shiga ya dauke ni. "Ka sauke ni!" "Idan na ki fa!" Ya wuce da ni dakin Hajiya ya kwantar da ni. "Ya kike son nayi? So kike a zubar da cikin nan kenan?" Da sauri na bude idanun ina gyad'a kai. Girgixa min kai yayi yana faɗin. "Ban san yadda zan miki bayani ba, amma ina cikin farin ciki kamar na goyaki nayi ta yawo dake a garin nan! Kina dauke da cikina a karo na biyu! Lallai ni dan gata ne Allah yasa Deen zaki haifa min!" Sai a lokacin na ware idanuna akanshi, "Ni fa kawai a cire shi yaran nan abin a tausaya musu ne, basu kai shekara ba balle mu ce sun sha na shekara daya, wata bakwai fa gaskiya sai dai a cire cikin nan ba zan iya tashi biyu ba!!" Duk yadda zai fahimtar dani nima so nake na fahimtar da shi amma yaki nima, zuciya nayi na juya mishi baya. A wannan lokacin na fuskanci kawaici irin nashi bai yarda ya biye min ba, ina jin bayanin da likita tayi masu, tare da musu allura na tsawon kwanaki arba'in, sannan nima za a bani maganin da xan na sha na cigaba da basu nono. *** *Asiya* ``All spicess Jollof mix BBQ mix Thyme plus Garam masala Curry powder``` ```Special zobo Special yaji Spice kuli kuli Miyar kuka Miyar kubewa Special daddawa``` ```Garin masa/sinasir Garin alale da kosai Garin kunun tsamiya Garin kunun aya``` *Shin ko kun san kayan kamshin da kayan zobo tare da duk wani dangin kayan abincin gargajiya da Ummu take amfani yana samuwa ne ta wurin Shaharariyar me kayan kamshi na AIDA spicess! Ina mata yan yayi ina masu abinci na online kayanku ya tsinke a gindin kaba, ga Hajiya Aida special spicess tazo mana da kayan girki na gargajiya da na zama kai Jama'a wata miyar sai a makota! Na gwada sauran ku gwada ina jiranku! Za a iya samun Aida spices ta wanann number:+234 806 968 1068 Whatsp siyan na gari mai da kudi gida! Hajiya ki zama yar gayu me sauki ne amma girkin yan gayu dai da Aida spicess*41 *Kafin na fara zan soma da tayaki murna zagayowar shekarar haihuwarki Mom Sayyad da Noor! Allah ya albarkaci rayuwarki ya kawo yan uku in sha Allah a raba cake a kawo min nawa🎉🍧🍨🍦🍰🍮🎂🧁🍭🍬* *Asiyah* Kallonta bokon yayi yana nunata da yatsa, "Zaki auri Tafida! Ba makawa da amincewar matarshi, amma ki sani Tafida ba sauki cikin lamarinsa domin Allah yana kare shi, abu daya na sani babu abinda zai tab'a samunshi domin matarshi kadai zamu iya samun Matarshi saboda laluran juna biyun da take da shi." Murmushi yayi yana faɗin. " Itama ba dole ba ne, domin tun ranar da kika tafi nake aiki akanta, iyayenta da iyayenshi suna tsaye akansu! Akwai wani munafikin malamin da yake tsaye kan lamarinsu, nayi kokarin na razana malamin aljananuna talatin da biyar ya kona minsu da Yasin! Idan kika samu damar shiga gidansa ki tabbatar an had'aku gida! Sannan ita me uwa wawuya ce ki ja yaranta a jiki yadda zata sake da ita!" Buga kasa yayi yana faɗin. "Ba zaki tab'a nasara ba sai kin shiga jikinta domin suna son juna ita kuma yanzu cikin jikinta zai ta juya mata lissafi! Karbi wannan ki tabbatar ya shiga hannunta daga haka zata, amince!" Turai ta kalle shi da kyau tana faɗin. "Mai zamani kana nufin sai mun tafi har Maidugurin kenan?" "Da yare nawa zan gaya miki? Ke tashi ki asko min gashin gabanki maza!" Jikin asiya na rawa ta mike. Mika mata sabon reza a takardan ta ya yayi yana kallonta. "Maza cire dan kanfen ki asko sannan ki yanka jikinki da shi yadda zaki jini zai tab'a gashin!" Haka tayi yadda yace, sannan ya amshi gashin gabanta ya haɗa abinda zai hada ya kalleta. "Ki zuba a turarenki, ki tabbatarwa kin hadu da Tafida! Yadda kome zai tafi mana! Tashi maza gobe Laraba tabawa ranar samu ki bar garin nan da sassafe kada ki dake rana tafi zafi baki bar garin nan ba domin sa'arki tana gobe ne." Gyada kai take tana jin kamar ta auri Tafida ta gama. Kudi suka zuba mishi sannan suka juya zasu bar dajin. "Ke mace ce kuma karuwa kiyi amfani da karuwancinki wurin jan hankalinsa!" Gyada kai tayi ya kara sake murmushi ya ce mata. "Yana amincewa ki dawo nan akwai sauran aiki." Gyada kai tayi, suka bar dajin, Ajiyar zuciya Hajiya Turai ta sauke tana faɗin. "Matukar aka yi nasara to ba makawa, sai mun samo hanyar da zamu mallake Tafida bakiɗaya yadda wani ma ba zai more shi ba." "Mu fara samun kan Matarshi, Mama Matarshi ba da wasa ta kama shi ba, sannan duk shige-shigen Hajiya Hindu haka Tafida ya fi ƙarfinta kin ga kenan babu hanyar da zamu kanta." Haka suka fito sai da suka huta kafin suka bar garin, koda suka isa gida dare yayi drive suka sake sakawa a gaba, ya dauki Hanyar Maiduguri, bayan sun loda kayanta a motar. Wurin karfe tara suka bar Yola. Dake driven ya san hanya, sannan babu wasu ababen hawa a hanya. Ba karamin tafiya suka yi ba amma kuma cikin ikon Allah basu hadu da kome ba. *** *Ummu!* Daga ni har yaran magani da abubuwan gina jiki aka bamu, a wannan lokacin babu laulayi sosai dai tsirfa, bana cikin kowani abinci sai wanda na zab'a, gashi ko sati ban yi da dawowa ba Tafida suka Tafida Abuja, naso zuwa domin mun yi waya da Tinah take gaya min jikin Deen sai addu'a, kamar zan yi kuka domin a Tafida ne ya bar wayar a dakina ni kuma na dauka ina waya da shi. A tsaye yake jikin kofar ya harde hannunshi a kirjinsa. Yana murmushi ya ce min. "Zan sauya password, na ga ta yadda zaki takurawa wayar me girma Gwamna!" Ba wani abu ya fada ba, amma naji raina ya b'aci na ajiye mishi wayarshi na fashe da kuka. "Sannu shagwab'a, wato ga yar kwai da ba a mata magana. Hajiya xan gayawa ta daina riritaki!" "Ni ka rike wayarka ba xan kara ɗauka ba, don ka ga bani da amfani shine kake min wulakanci!" Dariya yayi yana faɗin. "Gaskiya ban ga wani amfanin da kike min ba!" Wayar ce tayi ƙara, na mika mishi zan fita rungume yayi ta baya yana daukar wayar ya saka a kunne. "Barka da dare Mama!" "Yawwa Barka da dare dai, ina Ummun take?" "Gata nan!" Ya saka min wayar a kunnena. Cikin kuka na ce mata. "Mama don Allah ya dawo da ni, sai saka ni kuka yake!" "Tow sannu Yar yaye da bata rena kuka, ki kira Ummu Kulsum ki gaida ta yarta ta kone, Ayya zan kirata amma Mama ba nida number ta ki ce Uwanina ta turo min zan kirata da layin hajiya." "Shi layin Mijinki fa? Ke bana son munafuncin, ina da uwani kuka munafunce ni!" Kashe wayar tayi na fara matsar kwalla sumbatar dokin wuyata yayi yana faɗin. "Idan ba rigima irin naki ba kiyi hakuri mana!" Haka yayi ta lallabani har na share na hakura, an turo min number da layin mama na kirata na mata ya me jiki, ta ce da sauki da gayya nayi ta hira da katinshi. Murmushi yake yana kallona don ya lura ba karamin aikina bane na fashe mishi da kuka, nima na rasa dalilin wannan shagwab'ar. Koda yake Hajiya ta daure min kugu, nayi yadda nake so, satinmu daya da dawowa itama ta dawo, da jikokinta, ni kuwa na kama su na rike abuna, haka ya ƙara min daraja a idanunta. Domin ta kwashe Yaranmu ta riƙe. Sharif tafida ya kira ya kai Nana Asma'u makaranta Humairah kan tayi karama da makarantar. Su Mufidah tsakanina dasu nono. Tunda suka tafi Abuja, na tare a bangaren Hajiya. Tow ta hanani aiki sannan ta dauko wata yar dan uwanta daga kauye tana aiki girki kuwa da kanta take mana. Ina kwance Nana Asma'u ta kawo min dan wake da mai da yaji, tashi nayi da sauri nace. "Hajiya na gode!" "Allah ya miki albarka!" Ta fada daga kitchen, Fanna ta ce mata. "Inna kina shagwab'a Ummu kamar yadda Tafida yake faɗa." "Eh nayi din!" Ta fada tana murmushi, hmm matar nan tayi domin goye take da Mufid da yake rigima ta ce mishi. "Ba fa zan sauke ka ba, na gaya maka sai taci ta koshi!" Ta fito min da gulli da ta yanyanka da tumatur da albasa ta matsa lemon tsami a ciki, ta ajiye min. "Allah Ubangiji ya tabbatar dake a cikin gidan Aljanna!" Na fada ina cin abincin bayan na juye gullin a cikin dan waken. Mufidah kan tana wasanta. "Hajiya !" "Na'am!" Ya bani hankalinta kaina. "Kiyi hakuri!" Haɗe rai tayi tana faɗin. "Ba Falmata ta ce ki rage yawan damuwa ba? Ko so kike na kira Babangida na gaya mishi kin sake tadda maganar!" Murmushi nayi nace mata. "Hajiya ba zaki iya gaya mishi ba, Hajiya kiyi hakuri su shigo ko sau daya ne, Ya Abubakar ya roki haka kiyi hakuri don Allah!" Na fada ina loda abincin a bakina. "Ke baki damu da kanki ba ne." "Hajiya ina dake ina da Allah!" Na fada ina kara loda abincin. Wayata ce tayi ƙara. Domin kafin ya tafi ya saya min amma don jaraba nace mishi. Don kada na dame shi da karban waya ya saya min ko? Tow wallahi ba zan yarda ba ni wayarshi nake so. Tow ya ce min ya tafi, *Sweetpie* na gani dauka nayi ina hade rai. "Sai yanzu ka gadaman kiranmu Daadi?" "Hmm baki tambayi Deen ba?" "Allah sarki ya jikin nashi?" "Alhamdulillahi yanzu haka zamu wuce da shi india ne, kuma kin san akwai wani hadin gwiwa da zamu yi tsakanin gwamnatin kasar da borno, ina son idan na je na samu ganawa da Ministan harkokin waje kasar, Ummu i need pray!" "Kana da Allah da Hajiya in sha Allah mun gama maka! Amma Daadi meye matsalar Yayana?" "Akwai aikin da zasu mishi a kwakwalwarshi ne zuwa dokin wuyarshi kin san ya auna arziki, sare kanshi suka so yi! Ummu ki taya mu da addu'a idan ayi aikin a dace!" "In sha Allah za a dace " mikawa Hajiya nayi suka gaisa tayi ta musu addu'a ina cewa Amin, bayan sun gama na amsa nayi mishi sallama kafin na ce mishi. "Yallabai Daadi, su zaso ganin Hajiya don Allah kayi hakuri!" "Ina wasa dake ne na saka doka ki karya min? Kada su shigo min gidana!" Murmushi Hajiya tayi ta bamu waje, kwalkwal nayi da idanuna, ai kuwa na fashe da kukan da yada shi dole ya janye mitarshi. "Ni gidan Mama xan wuce!" "In sha Allah kafarki sai ta makale a gidana!" "Kayi hakuri su zo su ganta mahaifiyarsu ce! "Hmm! Idan suka miki wani abu babu ruwana." "Na yarda!" "Allah ya miki albarka, ki shafa min babynDaadi!.dasu Babana da Mamana sannan sun gaya miki zasu zo dayawa kada ki sake ki shiga kitchen saboda wasu yan iska." "Zasu ji in sha Allah!" Haka muka yi sallama, ashe zuwan ba iya su Maryam ba ne, sun shiryawa zuwan. Kallon agogon parlour nayi, na kalli Mufidah tashi nayi na shiga kitchen Falmata tana faɗin. "Kai Maman Mufidah me zaki yi?" "Kayan cake nake bukata." "Daren nan?" Na ji muryan Hajiya. Gyad'a kai nayi ina faɗin. "Eh Hajiya!" "Ummu" "don Allah Hajiya!" Na fada kamar zan yi kuka, "shi kenan sai ki fada mana Me zamu taya ki?" Murmushi nayi na ce mata. "Hajiya Sakwara zamu yi gobe idan Allah ya kai mu!" "Sakwara da lafiyarki!" "Akwai abin dakawa na zamani!" Na fada ina mata dariya. Haka muka daura aikin cake da miyar egusi, kafin karfe sha daya mun rage aikin, Yarann duk sun yi barci Hajiya ta musu wanka ta kwanta dasu bayan tayi musu addu'a. Hankalina kwance muka gama rabin aikin, cake din sai sha biyu na gama, a lokacin muna waya da Tafida ban gaya mishi cake nake ba, sai da na gama na gaya mishi shiru yayi kafin ya ce min. "Bana ce banda aiki ba?" "Eh bakina yake jin kwadayi Malam!" "Allah ya shirya mara jin magana!" "Amin Malamina! Ina kewarka amma!" "Kiyi hakuri idan na dawo zan sake zuwa duba shi tare zamu zo!" "Hmm na gode" na fada ina murmushi. Haka muka cigaba da hira har barci yayi gaba da ni, Hajiya ta dauke wayar ta saka a charger, ta gyara min kwanciyata. Sannan ta fara sallah, Gudu nake sosai a cikin wani bakin daji, wata mace tana bina da wuka, zata caka haka yasa nayi ta gudu kamar xan tashi sama, sai tayi kamar zata caka min sai nayi mata nisa, garin gudu Na fada wani rami me cike da kwayoyi, Maryam da Saadiya da rukayya ke min dariya, suna zuba min kasa a kaina, ban san ya ka yi haske ya bayyana ta ramin me karfi da yasa dukkanmu , muka fasa ihu. Farkawa nayi Hajiya tana gefena tana tofa min addu'a. Haki nake kamar wacce taci Uban gudu. Mika min goran zam-zam da Malam Zailani ya bada a bani yayi na sha. "Ummu kin kwanta babu addu'a!" Hawaye ne ya cika min idanun nace mata. "Hajiya na manta ne ina waya da Daadi!" "Allah ya mana tsari da mugun ji da mugun gani, tashi kiyi alola ki zo kiyi sallah.." "tow Hajiya na!" Haka na sauko na wuce ban daki nayi alola sannan na dawo na samu ta ajiye min wani abin sallah, tare da kayana, ta wuce can tana nata haka nayi sallah na dake da addu'a gabana sai faduwa yaƙe. *Asiyah* Karfe biyar na asuba suka shigo gidan Abba, kowa yayi mamakin ganinta, domin a dakin Inna ta sauka, a bakin Inna ta ji labarin zuwansu Maryam gidan Tafida. Don haka yi kasa da Murya tana faɗin. "Inna don Allah na je dani, ina son ganin Yan biyun nan!" "Idan nabila zai tafi sai ka bishi, don na ji yana cewa har da Yaron gurin shuwa zai je samha da sadiya!" "Allah sarki zan je don Allah!" "Tow sai ka shirya!" Haka ta hada kome, nata tayi wanka bayan ya fito ya je ta gaida Hajiya Kaltuma ta gaya mata zata itama Gidan Ummu, tace shi kenan su shirya ai. Koda lokacin Tafiya yayi kwalliya ta cab'a kamar me shirin zuwa gasa. 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7642 *Ummu* Haka na wayi gari jikina ba karfi, Hajiya ta bani addu'a na sha, ta saka ni a gaba na ci abinci kaɗan. Hajiya duk ta damu, haka na daure na fara aiki fanna ta gyara min doya ta daura na shiga aiki akan lokaci, kafin karfe daya mun gama, ina wanka na ji hayaniyarsu, ban fito ba sai da na shirya cikin shigar alfarma, na kira Mama muka gaisa na gaya mata yadda nake ji a jikina. "Allah ya kawo miki mafita duk laulayin ne" haka muka ta hira sama sama, jin kira yasa na duba wayar Tafida da number kasar waje, murna na yi na ce mata. "Mama Daadi yana kirana. Kashe zan kiraki!" Murmushi tayi tana faɗin. "Ko kin kira ba zan dauka ba!" Ta kashe wayar, tana kashe wayar na dauki nashi da ya kira a karo na biyu. "Koda na bi Allah na ki Annabi idan ban bi ka ba, Allah sai ya nisanta ni da gidan Aljanna, Allah ya albarkaci nimanka da samunka, Ina kwana hasken rayuwata!" "Lafiya lau, mace mutum kin tashi lafiya, ya jiki jikin?" Shafa cikina nayi ina faɗin. "Alhamdulillahi Daadi!" Turo kofar dakin Hajiya aka yi, na d'ago kai ina kallon ta, ban santa ba amma kuma sai da naji gabana ya fadi tana rungume da Mufidah, tana murmushi. "Makullim aljannata yau gidan da baki." "Eh na sani shi yasa na kira kada wani ya tab'a min ke." Murmushi nayi nace mishi. "Na gode makullin aljannata, ina kewarka." "Ina kewarki wallahi!" "Nima haka Uban Yarana! Ina kewarka ba iya ni daya ba hatta Hajiya Yaranmu." "Yaushe zasu tafi?" "Hmm! Ai kwana zasu yi da wuni kaga ba batun tafiya!" "Ummu ! Bana son irin wannan wasar ki gaya musu nace kowa ya tattara ya bar min gida idan sun gaida Hajiya!" "Malam babu ruwana!" Na fada ina gyara zamana. "Kin ci abinci ma kuwa?" "Ya jikin Yayana?" "Da sauki kin ci abinci kuwa?" "Eh na ci yanzu zan kara wani" "Yawwa kafin na dawo naga kin koma katuwa!" "Allah ya dawo min da mai girma Gwamna lafiya!" "Allahummah Amin! Nayi missing ƙafafuwan da ake daura min a wuyana ana sosa min kaina tare da ihun dadi!" "Sai anjima ba zaka saka ni abin kunya ba!" Na kashe wayar, ina kallonta. "Ni sunana Asiyah! Nazo ganinsu Mufidah ne ashe bata da kiuya!" Kun san zuciyar Uwa haka kawai naji zuciyata tana rawa da girgiza akanta, amma nayi murmushi. Fitowa muka yi zuwa parlourn da yara suka fara birkita shi Hajiya tana rungume da Mufid, "Ummu kin fito?" Gyada kai nayi nace mata. "Eh hajiya na fito." Kallonsu Maryam nayi da suke muzurai. Nabila ta ce min. "Aunty Baby! Baki ganni bane?" "Allah Sarki yar room dina zo muje ki taya mu fito da abinci!" "Ummu dawo ki zauna ki barta da Fanna su yi aikin!" "A'a Hajiya zan iya fa!" "Kin san jikinki bai yi kwari ba, dawo kawai." "Kai Hajiya!" Wayar hannuna tayi ƙara. Dauka nayi ina fadin. "Aljannata ka sake kira ko?" "Eh gani a masauki ne shi yasa nake ta kiranki! Duniyata da fatan babu wani matsala ko don jikina yana bani wani irin abu!" Dariya nayi nace mishi. "sai na gayawa Hajiya kana niman excuse!" Na kalli Hajiya tare da mika mata ina dariya. "Hajiya ga autanki yana nimana da faɗa." " Babangida lafiyanka? Me tayi maka? Bana son rikici fa!" "Hajiya da bance a sako min ita a jirgi ba shine zaki ga laifina yarinyar nan kin daure mata kugu tana min rashin kunya ba xan yarda ba!" "Yanzu ka kira wani rashin kunya ta maka Babangida Allah yana ganinka ka daina cin Amanar yarinyar da babu ruwanta!" Kamar yana gani na wani narka fuskata ina gyada kai nace mata. "Hajiya ki ce mishi ya maida hankali abin da yaje yi, don yanzu sai ya ce yana jiran a tuna mishi." "Hajiya Ummu ta rena ni!" Ya fada da karfi ina murmushi. "Hajiya Ina son Ummu!" D'ago kai tayi tana murmushi ta ce mishi. "Aliyu ina son Ummu nima, ina sonka da Ummu ko bayan raina wani ya sakata kuka Allah ya saka shi kukan shima!" Sunkuyar da kai nayi ya ce mata. "Hajiya taji kunya ko?" "Eh gata nan tana murmushi." "Hajiya ki ce mata Tafida nata ne baki daya tun da muka sauka nake ganin mata da fuskarta, Hajiya ki ce mata na kosa na dawo da sauri na wuce kitchen, domin wayar tana kan handsfree ne. Haka suka yi ta waya da Hajiya yana gaya mata yadda yayi kewarmu. Daga Saadiya har mutanen sun cika da bakin ciki. Kallon Hajiya suke kawai har ta gama wayar ta mikawa Nabila. Maryam ta amsa tana faɗin, "Hajiya bari na mika mata mana!" Kallon da Hajiya tayi mata bayan ta bata wayar , yasata harzuka sosai amma ta hadiye haka. Ina hada zobo ta shigo kitchen din. Zata mika min wayar ta sake shi cikin zobon. Murmushi nayi mata na ciro shi a hankali na karkade shi, ina murmushi na cigaba da aikina! "Fanna don Allah dakin Hajiya wata tana charge a kashe wayar Hajiya ta fada cikin zobo!" Ware idanun Maryam tayi na sake mata murmushi ina yar dariya. "Kin zata kin dakile haduwarmu da shi ta waya ce? Yo ai wayata tana daki na ki kunna shi saboda nasan idan na fara wayar da shi ba xan mori kaina ba, hmm!" Na ja wani nishi me cike da kaunar mijina. "Maman Mufidah kin ga ina shiga ana kiran wayarki!" Dauka nayi na ce mata. "Na gode" na cigaba da aikina sannan na juye kome suka fita da shi Maryam tana tsaye wysrs Hajiya na dauka na zazzage kome na saka a cikin bugun shinkafa. Na wuce daki na hada wayar da Bluetooth, na rufe kofar dakin na fito, na koma kitchen ina jin wayar tana tsiwa na dauke ta ina faɗin. "Sahibul Khair!" "Ya wayar Hajiya ka kashe!" "A zobo ya faɗa!" "Kai Ummu taya kika jefa a cikinsa ko?" "Maman Mufidah Maryam bata da mutunci ina gani ta jefa wayar a zobo fa, sai na koma da baya." Inji Fanna. "Shiii!" Na saka hannuna a bakina. "Naji ai! Me yasa ?" "Ina sonka Tafida, basu ita su min kome ba sai ikon Allah! Tafida kai ne kadai zaka juya min baya nayi kuka a duniya babu me saka ni kuka sai kai!" "Ina sonki Yar bakar matata!" Dariya nayi nace mishi. "Saura ka ga kyawawan Mata ka juya min baya!" "Ai zahirin gaskiya duk kyamsu bai zama dole su yi kyam wancan wurin ba na gaya miki, akwai wani sirri a jikin bakar mace!" "Gaya min sirrin naji!" "Idan kana cinta ta iya fesa ruwa kamar pampo! " "Innalillahi wainnalihir rajou, Daadi haka ka koma?" "No ba haka na koma ba haka kika mai dani, ina cin mace ina jin kome a tsantsame, ina ci ina shan ruwan kauna, ke Ummu na gaya miki ke korama ce!" "Na gode da baka kirani corona ba!" "Allah Ummu zumarki akwai zaki da dad'i, a cikin mata dubu dakyar ake fitar da dari irinki, a darin nan sai an kara bincike a samo biyar masu irin dad'inkii, gaskiya Ummu ki san yadda zaki yi da ni, " "Tow na kai ka iya? Ka kashe wayar ka yi barci zaka.manta da kome. " "Ina zan manta da kome, ke ni fa abuna ya mike zarr, ke kawai yake bukata wallahi." "Ka rufa min asiri ina zaka ganni!" "Kwantar da hankalinki nan da kwanaki biyar ina gida ki addana min kanki!" Kamar wacce aka wurgota daga sama ta shigo kitchen din. Kallonta nayi Sadia dai ba zata tab'a hankali ba. "Ke ina mijina yake?" "Ya tafi koyan sallama!" Da ta lailayo ashar ta maka mana daga ni har shi, haushi ya kamani na rama muka yi ta zage-zage, kashe wayar yayi, Hajiya ta zo cikin tsawa ta ce min. "Ummu da hankalinki?" Fashe mata da kuka nayi na durkusa a wurin. "Wallahi idan Aliyu bai bani hakkina ba sai duniya tasan irin zalunci da yake min, nayi b'ari bai damu ba kuma bai bi ta kaina ba, fisabiilillahi akwai adalci cikin lamarin nan kuwa? Hajiya me nayi da yake gudun hada shimfida da ni, sai Ummu matar so? Tun daga ranar da nace ya bani hakkina ya wulakanta ni daga nan bai kara waiwayata ba, haka na zo ya dake ni bai kuma bin ta kaina ba, Hajiya me nayi mishi da zafi haka?" "Shi kenan je ki!" "Ke kuma barwa Fanna aikin je ki huta!" Na mike a hankali na wuce dakin Hajiya na kwanta. Ina kuka, kirana yayi kamar ya biyo wayar amma ya share bai ce min kome b dake tafiyar bai dauki wasu tawaga ba don Deen. Haka yasa na matsu ya dawo. Ina kwance Asiyah ta shigo dauke da Mufidah. "Kayi hakuri Ummu, ga wannan turaren wuta ne!" Ta miko min ledar na amsa. Amsa nayi ina murmushi, sai dai me ina bude ledar Sweet ne da su chocolate ni kuma cikin ya hanani cin zak'i. "Chocolate ne fa!" "Sorry duk na damu da yadda mahaukaciyar can ta miki ne ya rudar dani, bari na kawo miki." Ban iya mata magana ba, na amsa ta fita, bude drower nayi na daka ledar, can dai gata ta kawo min turaren wuta irin na Dubai din nan, godiya nayi mata sannan na saka drower. "Baki ci chocolate din ba!" "Eh xan ci bana son zak'i ne!" Zata yi magana Tafida ya kira ni. "Bana ce kada su zo min da wancar mahaukaciyar ba!" Murmushi nayi na gyara kwanciyata. "Daadi ba kome ya wuce kasan yanayin ne abu kaɗan ke tunzira Ni!" "Kiyi hakuri yanzu na saka Matori ya mai da ta gida!" "Mijina!" "Na'am Matata!" "Ina sonka! Ka dawo da wuri don Allah!" "Lallai yarinyar akwai shagali kenan!" "Sosai fa!" Daga haka na manta da wata Asiya a dakin, nayi ta zuba soyayyata. Idanuna ya rufe akan Tafida bana ji bana gani kuma bana iya jin wani zan kaunaci wani sama da Tafida, ina cikin wayar Hajiya ta shigo dauke da Dambu. "Babangida kashe wayar nan taci abinci!" "Hajiya xan iya yin wayar ina cikin abincin!" "Bana son sakarci kyale shi ki ci abincinki!" Ya kalli Asiyah. "Me kike yi anan?" "Ba kome" ta fada tana mikewa, abincin na fara ciki a hankali, Hajiya ta kalle ni ta ce min. "Me ta kawo miki, na ga ta wuce da leda har biyu!" Bude drower nayi na fito da shi. Dauka tayi ta wuce ban daki ta juye a cikin masai ta tura mishi ruwa. "Duk wanda zai soka rana tsaka bayan ka samu wani abu ba masoyi ba ne moranka ya zo yi, ita ta zo da Uwarta Tafida ya aureta, ina Ni a jikina babu alkhairi a zuwanta. Kada ki kara amsar abin da ya fito hannunsu, su ajiye idan na tashi xan ɗauke. Ummu ke kika sha wahalar dawo da murdadden mutumin nan zuwa me sanyin dabi'a taya ba zaki mori Mijinki ba sai wasu sun shigo miki rayuwa!" Murmushi nake ina mamakin Hajiya, ta cigaba da cewa. "Na yarda da ƙaddara amma ban yarda da ganganci ba! Akanki zan iya rabuwa da kowa Ummu Hadiyya, ina sonki da Aliyu ina son da mutuwa ce kawai zata shiga tsakaninku ba dan adam ba, Ummu kece hasken gidan Aliyu...... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7643 Kallon Hajiya nake sai naji na rasa mafita, kafin na ce mata. "Hajiya na gode!" Domin Hajiya tana saka ni jin wani irin abu a raina kamar ita ta haife ni, saboda karamcinta, haka na fito na samu Saadiya ta tafi, ban kula su ba, na shiga kitchen na kara yaji da mai don Hajiya ta saka min amma ni na fison na ganshi kaca-kaca. Ina fitowa ta ce. "Ummu yanzu yajin kika kara? Gaskiya Tafida zo ya kira Falmata ta duba ki don wannan yajin zai iya makantar da yaron cikinki!" "Ciki take da shi?" Daga Rukayya da tayi tambayar da Maryam kallona suka yi nace mata. "Hajiya kaɗan na saka maggi ne da na barbad'a ya sa yajin yayi haka, amma ai na daina cin yaji dayawa!" Na wuce daki na zauna na fara cin abincina, ina gamawa sai ga Rukayya kallo daya nayi mata na cigaba da lashe yajin da na kunso shi a leda. "Ummu!" Kallonta nayi kafin na ce mata ."wani abu ne?" "A'a dama ina son na roke ki ko da kayan Abinci ne, namu kayan abincin ya ƙare!" "Nima bani da iko da kayan abincin sai abinda Hajiya ya bani, ko ki kira Daadi a waya." Shiru tayi kafin ta ce min. "Hmm! Kiyi hakuri dai kin ji kanwata ki taimaka min, wallahi bani da kayan abinci a gida ni ko dubu hamsin ko bani aro kafin wata ya kare!" Sai na tuna kalaman Abba da ya ce min. *Rukayya ko duniya ka bata da kayan cikinta, sai ta nime ƙari domin bata da godiyar Ubangiji! Ta fi gane sata kamar bera!* Ganin zata dame ni na janyo locker gadon Hajiya na bude kudin da ya bani kafin ya tafi na raba biyu na kai ɗaya bangarena daya kuma na saka tunda a nan nake, idanunta yana kaiwa kan kudin ta ce min. "Allah yasa ki bani ko dubu saba'in hamsin ba zai ishe ni ba!" Tura drower din nayi na rufe na kalleta kafin na ce mata. "bari na tambaye shi!" "A'a kin san Aliyu bai da mutunci!" "Ina laifin ya gaya miki gaskiya!" Na fara kokarin kiran shi sai ga Maryam ta shigo, "uban me kike yi anan?" Hade rai tayi tana faɗin. "kudi zata bani tunda dan uwanmu ne yake tarawa yana bata." Kallon da Maryam tayi min ya sani dauke kaina. "Ki bata tun da ba daga gidan Magajiyar yan tuwo-tuwo kika kawo ba!" Murmushi nayi nace mata. "Wai ai tunda magajiyar yan tuwo-tuwo! Ta wanke ta bawa dan masu arziki, ai ta yi kokari." "Kokarin Ubanki? Me siffar karuwa, kin raba shi da Matarshi." "Eh gidana ta shigo, idan ban yi niyyar xamanta ba haka zai hankad'ata waje! Batun siffar karuwai da kika ce Alhamdulillah haka ma wani arziki ne tunda na wanke gindina na bashi ya sha kome ma daidai ne, gashi can a India amma nashi gindin ya gagara hakuri ni yake nima! Maryam idan kin cika yar halak ki hana Tafida cin gindina idan ya dawo sai na tabbatar da kishin da kike ba na kome ba ne saboda kaninki yana hawa da sauka kaina! Kuma kudi ban yi niyyar bayarwa ba indai ba satar da aka samu za ayi ba, ko kunya baku ji ba ni da ban tuna muku abin da kuka min ba kune zaku zage ni,ba kunya ba tsoron Allah yayi ta diban kayan garana yana baku, kuna ci dake babu kunya a ranku shine bari ku min rashin mutunci tow abi wani sarkin gidan Tafida yanzu na fara zama daram!" Na fada ina gyara zaman da nayi a gadon. Shigowa Fanna tayi tana faɗin. "Maman Mufidah, Hajiya tace na tambaye ki me kike so a zaki sha?" "Ki cewa Uwata duk abinda ta bani sha, sannan ki gaya mata nace ki min wainar fulawa ki yanka albasa da green pepper a fasa kwai fulawan dan kadan!" Na fada ina nufar ban daki na bar kofar a buɗe ina faɗin. "Allah ga kayata!" Na yi alola na fito, na shimfida abin sallah. Na tadda sallah sai lokacin suka bar dakin, da ne nayi hakuri yanzu ba zan yi hakuri ba kowa ya tab'a ni sai nayi magana. Haka na idar na kwashe kudin na boye, sannan na fito parlour, kamshin ya cika gidan bude window parlour nayi Asiyah tana kallona, na fita daga parlour zuwa bangarenshi, har zan tafi na dawo na cewa Fanna. "Idan kin gama ki kawo min abincin can!" "Tow!" Ta fada, tana goye da Mufid da yake ta wasa. Parlourn shi na dawo na kwanta kiranshi nayi muka shiga hira, kamar na janyo shi ta wayar kusan dukkan hiranmu akan Yaren daki ne, ina zaune sai ga Asiyah da Fanna. Ajiye abincin suka yi, na ce musu. "Na gode!" Fita Fanna tayi Asiyah tana kallon parlourn dauke kai nayi nace mata. "Kina buƙatar wani abu ne?" "A'a!" "Tow ku je!" Fita tayi jikinta a sanyaye, sannan na cigaba da. Wayata ita ta riko kunun don haka na ajiye shi, wainar fulawa naci a hankali kwance kunun na zubar da shi a kitchen din, kafin na shiga girki daidai bakina don Hajiya ta nutsu da Yaranta. Wurin ƙarfe uku sai gasu nan bangaren Aliyu wai sun zagayawa. "Ok zaku iya shiga!" Na fada hana suka gama ina kallon Rukayya ta fito da wasu abubuwan. "Bani!" Kallona Maryam tayi cike da takaici nace mata. "Ko ki bani ko na kira shi, na gaya mishi!" Ba musu ta ajiye ta bar parlourn, zasu fita suka ce min. "Ba zaki bude mana bangarenki ba ko iyayenki basu saka miki kome ba ne?" Murmushi nayi nace mata. "Ba zan buɗe ba domin ina tsoron halinku kada a dauke min abinda mijina ya saka min, sannan bana tunanin kun kai na byee muku!" Na cigaba da zama, a fusace Maryam tayo kaina. "Ba abin da zaki min na rantse matuƙar Abba da Hajiya da Tafida suna raye sai kin yi danasanin takura min!" Na fada ina kallonta. "Haka kawai don ina kyale ku zaku sani a gaba da fitina meye nayi muku? Meye na tsare muku idan Tafida ne kuyi duk yadda kuke so da shi amma ni ku fita a rayuwata don na lura baku jin maganar Iyayenku!" Na fada ina shigewa dakinsa na rufe kofar, na kwanta. Haka ina jin su suka bar parlourn ni kan don bakinciki barci nayi a bangarenshi can bayan la'asar na farka sakamakon mafarkin da nayi, Asiyah tana kuka. Haka na wuce nayi alola nayi sallah, sannan na wuce bangaren Hajiya. Na samu Asiyah tana goye da Mufid itama Hajiya tana mata dariya wai bata iya goyo ba. Murmushi nayi na zauna ina kallonsu. "Aunty Baby ina kika shiga ne?" "Ina can part din Daadi nayi missing dinsa ne!" "Kai Aunty Baby gwamna guda har yana da lokacin da zai zauna kuyi hira!" Jan iskar bakina nayi kafin nace mata. "Ba sauki auren gwamna, amma kuma idan akwai kauna tow zaku fahimci juna. Daadi idan na kasar ya bari ba ko Abuja ya tafi kwana biyu yake ya dawo, sannan duk inda zai je zai kwana a gida." "Aunty Baby baku irin fita yawo ne da shi?" Murmushi nayi kafin nace mata. "Ni ya gaya min cewa ni ina da daraja bai dawo dani domin na zama abin yawo ga duniya ba! Don Allah na zauna a gida idan ya dawo nace mishi barka da dawowa, na kuma kula da lamarinsa na cikin gida da danginsa wannan shine aikina!" Dariya Maryam da Rukayya suka saka suna faɗin. "Yarinya sorry for yourself! Ai ke dai sai gida, amma in sha Allah first lady tana nan zata dawo." Murmushi nayi nace mata.. "first lady a idanun duniya kamar hoto ne mara kala, first lady a idanun Tafida kamar mutum ne da ya tashi cutar makanta wanda ya fara gani a farko shine zai kasance da shi har abada!" Shiru tayi kafin na ce mata. "Ni ba duniya da abin cikinsa nake bukata ba, mijina yaso ni ya kuma kula da ni, ya isa min bana jin don ban isa ba na ji tsoron komawa da baya, Tun yana Tafida da farar kafarshi nake tare da shi. Idan yau Tafida Mata dubu zai kawo matukar musulunci bata haramta mishi ba yayi ya kawo wacce zata wanke mishi gwamnatinsa duk me sauki ne a gare ni!" "Ayya Rukyy ashe islamiyya tayi! Shi yasa nata san go da come ba!" Suka kwashe da dariya. Maganar yayi min zafi yau daya naji me yasa naki mai da hankali akan boko ma ne? "Eh islamiyya nayi shi yasa aka samu tazaran dabi'a tsakani na daku! Sannan Allah ya taimaka dukkanku babu wacce boko ya mata rana domin kuna zaune ne sai abin da aka baku gara ni ina da abinyi yi." Na fada ina dariya suma su ji yadda nake ji yan iska kawai sun dame ni. Ai kuwa suka fusata. Hajiya da take kitchen tace min. "Sannu Ummu ai kin yi kokarin kula dabbobi nan, na gaya musu gaskiya amma sunki ji su meye bokon ya musu rana ina kowacce biyo ki take tana cin arzikin yar islamiyya! Sannan daga Maryam har rukayyan babu wacce tayi makarantar gaba da secondry, suma ai daga secondry aka aurar dasu ha gara ke kin yi high islam!" Daga haka suka yi shiru basu kara magana ba, na godewa Allah da ya bani Hajiya a gefena idan ba haka ba takaici ya ishe ni. Haka suka gama iskancinsu har suka bar gidan. *Asiyah* Tunda suka bar gidan take cikin farinciki domin ita burinta na farko ya cika, ta bawa Ummu maganin kuma ta rike, sannan tsakanin Ummu da Saadiya babu shiri haka zai bata damar shiga jikin Ummu kafin ta samu biyan buƙatarta. Amma wani irin sauri aka yi har suka dawo ga juna. Har aka kawo su gida bata kula hiransu ba, tana jin su kamar zasu kashe Ummu a ranta tayi murmushi. Bayan sun sauka Nabilah ta ce mata. "ban san me Aunty Baby ta tsare musu ba suka tsaneta amma koma meye ai duk wanda zai zauna da naka ya maka kome kawai suna da wani irin ra'ayi ne!" "Ayya Allah ya daidaitasu!" Ta fada tana murmushi don ita nata shirin ya ci Uban na kowa. Tunda suka bar gidan Asiyah ta sake kama kafa da Inna yadda take mata yasa Inna take tausayinta, sannan a wurin Nabilah ta amshi number Ummu don ranar tana jin ta fada mata numberta. Haka yasa yasa ta jira itama ta amsa a wurin Nabilah. Bata taɓa gwada kira ba, don haka da yamma bayan sallah la'asar kwana biyu da dawowa ta kira Ummu, bayan sun gaisa ta ce mata. "Aunty Baby Asiyah ce!" "Ayya sannu Asiyah ya kike?" "Lafiya Lau, Aunty Ina Mufid Dina!" "Suna lafiya!" "Allah sarki na yi missing dinsa na kwana biyun nan aunty xan zo ki bani aron shi." "Wai babu ruwana Daadi zaki tambaya don baya bari a fita da su!" "Ayya Aunty Baby ki mishi magana mana!" "Sai dai ko idan ya dawo na mishi magana!" "Tow shi kenan," Haka Asiyah take kiran Ummu su gaisa sannan ta tambaye ta Yaran, har ranar da ta ga labarai Tafida ya dawo. Haka yasa ta kudiri aniyar ranar Lahadi da yamma ta kira Ummu. Bayan sun gaisa ta ce mata. "Aunty Baby zan zo an jima ganinsu Mufid!" "Tow shi kenan!" Murmushi tayi ta dauki turaren sannan ta goga, kafin ta yiwa Inna sallama ta bar gidan. *** *Ummu* Ance mai d'a wawa ne tow ya yarda a kaina musamman yadda Asiyah ta gama zagaye ni da kaunar Yarana, a hankali nake hango hankalin yarinyar, tausayinta da ban san yaushe na fara ji ba, ya cika min raina. Haka tayi ta kirana tana nuna min kaunar Yarana, amma ban yi wani abu akai ba sai dai ina matukar jin dadin haka. Kaina a saman cinyarshi, ya daka laptop a gefen kujeran da yake zaune yana aiki. "Ya naga yanayinki ya sauya?" "Daadi yarinyar nan tana da mutunci!" "Wacce kenan?" "Asiyah Yola!" Daure fuska yayi yana me aikinsa. "Daadi baka ce kome ba?" "Tow me kike tsammani nace dama? Don tana da kirki bari na fara rawa da girgiza Ummu ta yabi wata a gabana!" "Wuuh" na fada ina tashi zaune. "Allah ya baka hakuri, amma ya rayuwarka da haka?" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Yarinyar sona take, ni kuma nayi rejecting dinta, idan kina son karamin matsala sai na aurota!" Jan hancinsa nayi nace mishi. "Kai da bakinka ka gaya min ai ba don ni daya aka halicce ka ba, kai mijin mace hudu ne idan ka manta na tuna maka idan baka auri Asiyah ba zaka auro wata ai, don haka ni ban ga wani abu na laifi ba don mutum yana son Yaranka!" Na fada ina tura baki, ni har ga Allah na fada wallahi ban fada da wata manufa ba, haka yasa shima ya bar zancen. Can kuwa sai ga Nana Asma'u ta buga kofar da sallama. "Waalaikumunsalam!" "Mami kizo kin yi bakuwa!" "Tow gani nan zuwa!" Na fada ina mikewa, mai da ni yayi na zauna yana min wani irin kallo me tattare da zautarwa. "Amma kasan!" Janyo ni jikinshi yayi yana faɗin. "Hm! Wato don kin gaji dani ana cewa ga bakuwa shine kika tashi zubur!" "Me xan maka kuma dai? Me kake bukata?" Shiru yayi ya cigaba da aikinsa yana rike da ni, yau ne zai sake ni kai har dai da na shafe awa daya cif a jikinshi, ban san saa'da na fashe da kuka ba, sharewa yayi ya cigaba da aikinsa. "Daga yau idan kina tare da ni, wani yazo wurinki matukar ba daga danginki ba ne wallahi sai na b'ata miki rai, oya ki je ki sallame ta ki dawo nan, idan kuma kika bari na zo da kaina a gaban Hajiya xan ɗauke ki cak." Ina tashi na harare shi ina share hawayen da yake zuba min na ce mishi. "Ba zan dawo ba, ka jima ba ka ɗauke ni ba!" Bai ce zai min kome ba dan gyara zama yayi na fasa ihu tare da tsayawa cak, na zata zai biyo ni ne. Tab'e baki yayi yana faɗin. "Haukar tsufa rashin ganin jika!" Ya fada yana cigaba da aiki, ai kuwa na tura baki ina faɗin. "ba xan kara zuwa ba" na fita, murmushi yayi yana faɗin."yarinyar nan zan kama ki!" Duk wani burin shi naso ganin ya kyautatawa Ummu yana kokarin cika shi, asalima gani yake kamar bai mata yadda take so ko hakuri take da shi, a bangaren Mu'amala aure yasan tana kokarin daukar laluranshi kuma haka ya mishi dadi musamman yadda take jure bukatarshi, haka ya cigaba da aiki. - Na samu Asiyah a parlour Hajiya tana hira da yaran, sai tsalle suke akanta. Murmushi nayi itama ta sakar min murmushi. Muka shiga gaisawa Hajiya tana kitchen. Nana Asma'u da yaran suna ta wasa , shine ta zauna a cikinsu. "Aunty Baby Ya Ali ya ki barinki, kizo gashi nan xan tafi." "Allah sarki, mun gode kiyi hakuri na tsaya gyara mishi daki ne shi yasa." Nan muka shiga hira sama sama, ta fito da wasu kayan Yara, irinsu hankchef da sauransu da turaren Yara, masu kyau da tsada ta mika min daya blue daya pink! Har da ribom na kitso irin na yaran nan! "Duk su ɗaya?" "Ai Aunty Baby kin ji girma sai yaran kawai!" Ta fada murmushi nayi nace mata. "Gaskiya sun gode sosai, Mum dinsu tayi musu sayayya!" "Kai Aunty Baby babu yawa." Hajiya da bata kula mu ba, sai da na mata magana ta ce min. "Sun gode! Ummu bari na shiga sallah!" Ta wuce nasan Hajiya bata yarda da kayan ba, haka yasa na ki tab'awa na cewa Fanna. "Ya Fanna zo ki kai dakin Hajiya ki ajiye," "dake Yaran sun koma hannun Hajiya sai nima hidimarsu ta min sauki, haka ta dauka tana ta godiya itama, hira muka sha na manta da Tafida na can yana jirana. Ganin shiru ban dawo ba balle na saka mishi ruwan alola, sai gashi nan ya tawo don Tafida irin Alhaji ne haka kawai daga dawowarshi ya zo da wani butar karfe daga India wai ina zuba mishi ruwan alola da farko cewa nayi ko butar tsafi ce, hade rai yayi ya ce a'a na bokanci ne karewar tsafi don idan ya yanko magana kamar bashi ba, baya gajiya da bakar Magana. Tura kofar parlour yayi muka hada idanu, washe hakori nayi domin nasan ba mamaki ya kunyata ni.... *Ban so nayi magana ba amma bari na goge muku lissafin da wasu suke yi har da masu karanta bati! Labarin nan ba daga farko na dauke shi ba! Daga tsakiya na dauki labarin Ummu, kamar kowani marubuci yana da side din da yake daukar labarinshi! Tow ni daga ƙarshe karshen rikicin Ummu da Tafida na ɗauka! Labarin Ummu idan baso kuke na yanke labarin ba ku bar ni nayi abin da yake cikin labarin amma ko ina cewa ake ya labarin bai yi ba yo dama ai nasan ba zai yi ba, idan kuma kuna ganin na kammala shi kamar yadda ake tatsuniya ce daga wannan pagen din sai nace Alhamdulillahi! Don haka a bar ni nayi abin na tsara a labarin idan kuna ganin da matsala! Sai ku ajiye ku jira idan na kammala sai ku karanta amma bakiɗaya kuna dagula min lissafi! Sai nayi gabar kuce yamma zan yi me Ummu ta gani a kaidin kishiya da dangin Miji! Me Mahmoud yayi da za ace an gama sai na kama shi nace na bayyana asirinsa ya tonu gaskiya wannan shine short story, bayan da kanku kun san Deen yana kwance don Allah kuyi hakuri a bar ni nayi yadda na tsara sunan Mahmoud kuwa sai fa hakuri gaskiya don na tafi da labarin sosai. Ba zai yiwu a dakatar da jirgin kasa a gudun dubu dari uku a duk kowacce dakika dari da tamanin! A bar min kayana nayi sama sama da shi😀🏃🏻‍♀️* 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7644 "Karfe nawa?" Ya kalli agogon hannunshi, kafin na bashi amsa ta bashi amsar. "Shida saura minti goma!" "Ummu karfe nawa?" Juya idanun nayi na mike tare da cewa. "Dama dama na manta amma!" Na juya zan nufi dakin Hajiya da wani irin zafin nama ya cabkoni yayi sama dani. "Wayyo Allah Hajiya ki ce ya sauke ni!" Na fara ƙoƙarin kwace kaina. "Hajiya kada ki fito ɗaukarta nayi rashin jin Ummu yayi yawa!" "Sauke ta dan gidanku ka manta ciki ne da ita!" "Hajiya me yasa kike min haka!" "Hajiya ki ce ya sauke ni Allah xan bishi!" "Ai tace Allah sauke ta!" Ba musu ya dauke ni, yana zungure goshina. "Wayyo Allah zai fasa min kai Hajiya ki ce ya bari kada ya fasa min kai!" "Babangida baka jin magana kai ma." "Gaskiya kam Hajiya Daadi baya jin magana ki gaya mishi ya daina rashin ji!" Matse hannuna yayi tare da cewa. "Hajiya ki tafi kawai ki barmu don Allah ya gani zan baki kunya!" Ya fada yana kokarin rungume ni! Juyawa tayi ta bar wurin tana faɗin. "fitsarare!" Tana barin wurin nace mata. "Hajiya cin zalina zai yi!" "Ai kema rawannki yawa ce da ita!" Murmushi yai ya saka kaina a gaba muka wuce bangarenshi daga ni har shi mun manta da wata Asiyah, *Asiyah* shiru tayi tana kallon kofar. *Ummu* ta furta a kasan makoshinta, ji tayi idanunta sun cika da kwalla, tabbas zata gyara mata zama, mikewa tayi ta fita tana me kallon bangaren Tafida a hankali ta bar gidan, a hankali take tafiya ita ba damuwarta kawai Tafida yasan tana nan da rai. Kiran Mamanta tayi a waya. Kuka ta saka mata a hankali take kuka kamar zata shiga wayar. "Mama Tafida idanunshi akan Matarshi ya ke baya tunanin kowa yake ba sai ita, mahaifiyarshi da mahaifinsa damuwarsu Ummu basu tunanin ko me, idan ban samu Tafida gara na mutu, ni ban da amfani!" Uwar ta rasa yadda zata yi da ita ta ce mata tayi hakuri kome zai wuce. Haka tayi ta kuka har ta isa, koda ta isa kwanciya tayi a kan kujerar dakin Inna. Haka ya cigaba da murkususu. Har kusan asuba, saboda rashin barci da safe tana tashi da ciwon kai, haka ta fadi a wurin domin jiya tayi ta shan kayan maye amma basu sakata barci ba, sai a lokacin sai da ta farka ne ta ji jiri ya kwashe ta, a wurin ta zube salatin Inna ya taso yan gidan, aka kwashe ta zuwa asibiti. A ranar aka kira Mamanta. ** Sa'adiyya. Cikin tsananin zafin marin da Mahmoud ya kwashe ta da shi, yasa take kallon shi bakinta a sake ta ce mishi. "Mai nayi maka? Na gaya maka gaskiya ba zan kara ba, idan ka sake ka kara dukana sai na gayawa duniya waye kai! Na gaji ka hanani zaman lafiya a gidan aurena, ka bar ni na tafi nayi rayuwata, kada ka kara min magana ko na gayawa Mahaifiyarka abin da kake min, kana tsammanin." Shake wuyarta yayi yana faɗin. "Ni zaki yiwa rashin kunya? Sai kashe ki na kara ganinki a wurin nan sai na lalata miki kafa jaka!" Cikin kuka ta ce mishi. "Eh na yarda a haka amma ka sani ni aurena na tab'a, kuma a shirye nake na gyara tsakanina da mijina amma kai fa? Amanar Abokinka ka ci, kai baka samu Ummu ba ni ban samu Tafida ba, tun basu son zama da juna yanzu kuwa duk abin da muke Allah ta nuna mana cewa Ummu da Tafida ba me raba su, ka gama haukarka tun daga ranar da kace min ka kasa mata fyade na gane baka da ss'a har abada Ummu Hadiyya tayi maka nisa, ka bar nayi nawa rayuwar." Juyawa tayi zata tafi ya riko Hannunta cikin fushi ta juya ta watsa mishi harara. "Sake ni kafin na gaya maka magana, yadda ka cutar da igiyar aurena haka Allah zai tozartaka Mahmoud wallahi sai kayi danasanin abin da kayi. Azzalumi macuci! Na dawo daga karyanka ka dawo daga zalincika na daina na daina na daina ka bar ni kada ka kara shiga rayuwata idan kuma ka dame ni sai na gayawa kowa waye kai!" Daga haka ya bar gidan tana tafiya tana wani irin kuka, jin tayi ta tsani kanta, ba zata kara yarda ta rasa Tafida ba. Gara ta samu Alhaji ya bashi hakuri zata koma gidanta. Har ta fito bakin hanya ta tuna ta bar motarta a can, haka ta kara juyawa ta koma ta bude motar ta shiga, sannan ta bar unguwar gidan ta wuce, bangaren Abba ta wuce ta samu yana shan shayi, akan gwiwarta ta zube tana kuka me cin rai. Zuba mata idanun yayi kafin ya ce mata. "Halimatu gaya min me yake faruwa?" "Abba na shirya zama da Tafida ne,Abba ka bashi hakuri ya zauna da ni!" Murmushi yayi yana faɗin. "Tow ai Halimatu ke da Mijinki babu wanda ya isa shiga fadarku, sannan ni nayi alƙawarin shiryaki da Mijinki don haka ki je gobe zamu yi magana da shi!" Tayi ta godiya sannan ta fita tana share hawayenta. Ba zai ce Tafida ya rabu da ita ba, amma zai bashi shawara ya saka idanun akanta, don yasan duk wani takunsu akan Ummu. Sannan ga Asiyah. Shiru yayi yana jin labarin ciwonta da alakantashi da dawowa daga gidan Tafida. Yarinyar tunda Uwarta tazo take kuka ita dai Tafida take so, ya rasa yadda zai shawo kan rikicin Tafida. --- Tun safe ya gaya min zai dawo ya ci abinci, sannan zai je gidan Abba bayan sallah isha. Haka na gama hada kome, tunda ya dawo nake maida hankali akan abinda zai ci, ina gamawa naji kar'ar saren dinsa, murmushi nayi sannan na tsaya a bakin kofar ya buɗe ido hudu muka yi da shi. Yadda na ganshi rai a b'ace, "barka da dawo hasken rayuwata! Ubangiji ya ƙara maka hakuri da juriya, Allah ya ƙara maka lafiya da nisan kwana yadda zaka kula da mu, Allah ya jagoranci lamarinka!" "Ki bani Ruwa na sha!" Riko hannunshi nayi bai min musu ba, ya biyo ni ya zauna Kamar yadda nace mishi, na wuce kitchen na dibo ruwa na kawo mishi. "Kayi ta ambaton Allah yana tare da kai!" Karba yayi yana sha kafin ya juyar da kan shi. Zama nayi a dan nesa da shi, kaina a kasa zuwa yanzu na fahimci me ake kira da Shugabanci. Domin wani lokaci zai shigo ranshi a dagule tunda Deen ya samu matsalar nan, "Ummu!" "Na'am Baban Mufid" murmushi yayi yana faɗin. "Sadiya ta kai karar na wurin Abba, sannan ya bukaci na haɗaku a government house, tunda nan." Hankalina ne ya tashi na kura mishi idanun. "amma!" "Kada ki damu zan akwai bangarenki!" "Da nan ka dawo da ita tunda akwai fili sai ka sake daukar wani aikin, idan ka duba gaba mulki zai kare dole nan zamu dawo! A ce yau muna can muna nan duk ba yi ba ne, zaka iya fa na yarda da kai!" Kallona yayi kafin ya ce min. "Kina ganin babu takura?" "In sha Allah babu takura sannan ni mace ce, kuma Uwargidanka idan ban rike gidanka ina zan riƙe?" Jinjina kai yayi. "Amma kace min sai isha zaka gidan ya aka yi haka?" "Eh zan tafi don yarinyar nan bata da lafiya ma!" "Wacce!" "Kawarki!" Sai na rasa wacece. "Wacce take kawo miki kaya mana!" "Ai Asiyah! Allah sarki Allah ya bata lafiya!" Na fada domin ban san meke faruwa ba. Sai da yamma ya ce min n shirya muje asibitin bayan sallah Magariba. Haka na shirya ban dauki yaran ba, muka tafi asibitin tunda aka sanar da Gwamna zai zo asibitin ake kome cikin nutsuwa, tare muka zo dashi ina sanye da riga da skirt ne na saka hijab har kasa sai face mask da ya ce na saka, haka muka shiga asibitin, rike hannuna yayi muka shiga kowa sai kallonmu ake, ina ta son cire hannunshi a cikin nawa amma yaki, koda muka isa kofar dakin haka ya rike hannuna gam, muka shiga dakin da sallama. Kanta kwance akan cinyar Mamanta. Tashi zaune tayi tana faɗin. "Maman Mufidah!" Yadda ta kira sunana yasa gabana faduwa. "Hmm! Ya jikinki?" "Da sauki Ya Ali Barka da zuwa sannunku!" Ta fada Mamanta kuwa sai wani dauke kai take na bude baki na gaishe ta. "Ina wuni?" Kamar bata ji ba, sai da Yar ta ce mata. "Mammy baki ji tana gaishe dake bane?" "Oho da ni take na zata da ke take?" "Baby muje!" Ya riko hannuna. "Tafida tafiya zaka yi ba ka gaishe Ni ba?" "Akan me xan gaishe ki? Bayan Ummu ta gaishe ki, kika share ta tunda jikinta da sauki ai shi kenan!" Ya riko hannuna muka bar dakin. *Asiyah* A matuƙar hasale ta kalli Uwarta. "Meye sunan abinda kika aikata? Kin dauka haka zai samu cikin ruwan sanyi ne? Haka kawai bayan na gama shan azabar samunshi zaki tashi ki lalata min kome, wallahi." Hakuri ta shiga bata."kiyi hakuri haushin yarinyar nake ji, ban kara jin na tsaneta ba sai yanxu da na ganta wata abu kamar inuwar alli, gaskiya dole ki shiga cikin gidan Tafida a damma dake!" Girgiza kai tayi tana cewa. "Itace makullin gidan sau da ita xan shiga cikin gidan, idan babu ita ai ya zama aikin banza." "Haka ne amma kuma taya kike ganin xan kaunace ta a siyasance, ga tafi dan da girman kai kamar akanshi aka fara zama gwamna. " "Ko da ba akan shi aka fara ba, shi din nawa ne ni daya zan tabbatar da na mallake shi in and out dinsa yadda kowa na shi sai ya biyo bayana. ** Ummu Gidan Abba muka isa, zama muka yi yana shan kankana. "Ummu Hadiyya tunda kika koma kika manta da Abbanku!" "A'a Abba!" Yar dariya yayi kafin ya ce min. "Ummu laifi kan muna ta miki, ba wai don ba mu muka haife ki ba, a'a kawai ba yadda zamu yi ne." A hankali gabana ya fara faduwa. "Yarinyar nan Asiyah bata da lafiya, sannan dalilin ciwon shine Mijinki, tana son shi amma ni Na gaya musu gaskiya tuntuni na gaya musu." Kaina a kasa ban iya magana ba amma kuma ai bani za ayiwa kishiyar ba kishiyar Sa'adiyya ce za ayiwa magana! "Abba ni ai na gaya maka bana sonta akan me zaka ka daura min ita!" "Tsakani da Allah yarinyar nan tana fama da jinya kayi hakuri ka aureta!" Tashi yayi ya bar parlour yana faɗin na same shi a mota. A sanina wasu mazan farin ciki suke idan za a basu damar kara aure sai na kasa fahimtar Tafida, har muka koma gida fushi yake, sannan ya saka an gyara bangaren da Saadiya zata zauna, wani abu da na kara fahimta gara tafida yayi auren yadda kowa iya ruwa fidda kai, kowa tashi ta fishe shi, idan na mallake Tafida ne za a gani idan kuma halinsa ne kowa zai gani, haka yasa na sakawa a raina babu tashin hankali. Bangaren da Saadiya zata zauna aka fara aikin shi domin ya fadawa Abba cewa sai ya gyara wurin, batun Asiyah yarinyar nan tana shan wuya domin yadda ake bada labarin kamar zata mutu haka take ji akan tafida. Shi kuwa ya ce a'a, cikin wannan yanayin aka fara shirin sallah layya, a kwanakin goman zulhajji na hana idanuna barci saboda ina yawan mafarkin Asiyah tana kuka haka yasa naki komawa gaida ta, ina azumin kwanakin kuma kara rub'anya ayyukana. Ranar ina zaune da hantsi, "Ummu!" Naji ana min kiran mafarauta. Gabana ne ya fadi ina fitowa Maman Asiyah ce ta zube akan gwiwarta tana kuka. "Ni taimaka min kada na rasata ki saka Tafida ya aureta don Allah zata iya mutu!" Sake baki nayi na juya xan shiga cikin parlourna sai ji nayi kamar duhu ya lullube min idanuna............ 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7645 Ban san me ya faru ba, sai dai tabbas zuciyata tayi min nauyin da na kasa jure kukan Uwar Asiyah lokacin da na farka Hajiya da Mama ne a dakin, tashi xan yi Hajiya tace min. "ki kula Ummu!" Bude idanuna nayi naga dakin da nake, dafe goshina nayi ina kallon sama, na rasa gane me ke damuna, a hankali nake ambaton Allah,ina ji kamar akwai abin da nake bukatar fadar shi amma na kasa, so nake lallai na ji haka ya fita daga bakina amma na kasa fadarshi fashewa da kuka nayi, Mama da tafi kusa da ni ta ce min. "Ummu Hadiyya lafiya?" Girgiza kai nayi nayi ina jin kamar ana daure min zuciyata. "Mama d'aga ni!" Na fada a hankali, "ikon Allah! Tow " Hajiya ta fada tana mikewa, itama zuwa suka yi suka d'aga ni, na zauna ina kuka kamar raina zai fita. "Tow me aka miki?" "Mama ban sani ba amma don Allah ki ce ya aureta!" Na fada ina kuka me motsa rai, tare da dafe kirjina, saboda ji da nake kamar ana hura min zuciyata. "Ummu!" "Don Allah Hajiya, ki saka baki ya auri Asiyah." Kamar zata yi kuka haka take kallona. "Wannan abu bai yi ba." Ta furta sai wurin goma Mama ta bar asibiti, Sagir da ya duba Ni allura yayi min saboda yadda jini na yayi bala'in hawa. Sannan gashi ko magana nayi haki nake, Tafida da yazo ya ga halin da nake ciki Hajiya ta gaya mishi hankalinsa yayi bala'in tashi ya kura min idanun kafin ya ce min. "Me yasa?" Rike hannunshi nayi kamar zai gudu na ce mishi. "Ka aure ta don Allah!" Na fada ina juya kaina tare da dafe kirjina. "Ka aureta!" "Ummu kin san halin da nake ciki zaki kara min damuwa akan damuwa? Ummu Hadiyya!" "Hajiya ki ce ya amince don Allah!" Itama kuka take domin basu tab'a ganina cikin wannan halin ba, sai yayi ta kallona. Wasa wasa Sai gashi na fara ji kamar zan mutu, idan numfashina yayi ta shiga da fita. Haka Sagir da Fadilah suka kwana akaina, washi gari da safe yayi sammakon zuwa ya samu ina ta barci. "Aliyu!" "Na'am Hajiya!" "Ka auri yarinyar! Shine masalaha idan ba haka ba Ummu ce zata ta wahala idan kuma wani abu ya samu yar mutane ba zan iya yafewa kaina ba balle kai, sai kayi kokarin ganin kayi adalci." "Hajiya!" "Sai ka zab'a rayuwarta ko taurin zuciyarka" tashi tayi ta fita ya dawo bakin gadon ya zauna yana shafa kumatuna, bude ido nayi ina murmushi. Gabana ne ya fadi yadda naga yana hade min rai. "Zaka aureta?" "A'a ba zan iya ba! Ki tashi mu cigaba da zamanmu!" Ji nayi kamar ya shake ni, lumshe idanu nake a hankali tun ina iya hango shi har na daina hango shi. A tunaninshi barci nayi, shigowar Sagir ya ce mishi. " ta farka ne?" "Eh ta farka har ta koma ma!" Takowa yayi yana kallon yadda nake kwance, "wani irin komawa, ta sake suma ne fa!" Ya fada yana tab'a hannuna. "Suma kuma?" Fita yayi ya kwalawa nurse Fadilah kira, aka sake rufe kaina. Sai da suka dauki lokaci kafin aka samu na farfaɗo barci yayi gaba da ni. *Tafida* A wannan lokacin da Ummu tasan halin da yake ciki ba zata tab'a d'aga mishi hankali ba, ga Mahmoud da ya saka shi a gaba ya gaya mishi inda Deen yake jinya amma yaki karshe kin haduwa da Mahmoud din yaƙe sau uku yana niman izinin ganinshi amma yana hanawa, saboda kawai baya son magana ne, ta gefe guda Yan adawa musamman Alhaji Hamza Goza sun matukar saka shi a gaba, akwai wani abu da matukar baka isa matakin ba gani kake kamar karya ne, zuwa yanzu ya kara hango tashin hankalin da ya kara cusa kansa domin da sauki zama gwamna a wurinshi, sai dai abin da yake kan Gwamna da gwamnati ya sha kanshi, domin kuwa zuwa yanzu duk abinda zai yi sai ya sha kiran manyan mutane. Lumshe idanunshi yayi a hankali ya bude akan laptop din da yake office dinsa, wayar office dinsa ya dauka ya kira SSG suna gama wayar ya kashe can bayan minti talatin sai ga shi yazo. Zama yayi yana faɗin. "Yallabai!" "A'a ka kirani Aliyu! Kawu!" Inji Tafida. "A'a ai matsayi Allah ya baka!" "Duk da haka dai, kawu dama akan aikin kwangilar nan ne, mutane dayawa suna ta bukatar a basu, kawu kayi aikin gwamnati na tsawon shekaru, shin waye kake ganin za a bashi aikin nan babu matsala!" Shiru SSG yayi kafin ya ce mishi. "ina ga ka bawa Amaan Yusuf Mandara zai fi maka aiki akan sauran, shi yana iya saka dukiyarsu ma ayi daga baya a biya su." "Alhamdulillahi shi kenan, ka hada mana zama da shi." Turo kofar aka yi ya zubawa Mahmoud idanu. "Meye matsalarka da ni nake son ganinka kana hana ni? Nayi kokarin ganin na dauke kai ka gaya min me nayi maka kake hanani ganinka? Wai duk wannan sauyin na meye?" "Kawu jeka!" "Shi kenan!" Ya fita, kallon juna Tafida da Mahmoud suka yi, "zauna!" Zama yayi yana huci. "Meye matsalarka da ni?" Murmushi yayi ya ce mishi. "Babu kome kana da damuwa, aiki ya sha kanmu daga ni har kai bamu da lokacin kanmu, idan nace kullum zamu hadu akwai matsala gara muna haduwa jefi-jefi haka muka shirya da Deen zamu na haduwa idan muka tashi a aiki!" "Da baya nan ni ban cancanci muna haduwa ba ne? Wai ma ina ka kai Deen?" Kai tsaye ya ce mishi. "Wani wurin na daba, yadda rayuwarshi zata tsira." "Tafida me kake nufi da Ni ne? Tafida me kake boye min? Wato ni ne magananne a cikinku kome nawa kun sani ni ban san kome akanku ba!" Girgiza kai Tafida yayi sannan ya ce mishi." Kana da magana, bakinka baya shiru sannan ina kokarin kare Deen ne kada wani abu ya kara samunshi, a lokacin da ta dace yayi murnan Matarshi ta haihu, ko sunan yarshi bai gani aka farmake shi." Taune lips dinsa yayi cike da takaici ya cigaba da jinjina kai yana faɗin. "Ba zan yafewa wanda yayi min wannan abin ba, matuƙar zan ganinshi sai yayi." Murmushin takaici ya kara yi, yana mikewa, "Allah ya kyauta amma ana kan bincike ko?" "Eh nace a cigaba da bincike!" Ya hada kayanshi zai fita. "Zan tafi asibiti Ummu bata da lafiya!" "Tow Allah ya bata lafiya! Nima tafiya xan yi!" A tare suka fito, bakiɗaya jikin Mahmoud wani irin rawa yake, Motarshi ya fada yana jin kamar ba zai iya isa gidanshi ba. Kiran wani layi yayi yana faɗin, "Ka tabbatar kun nisanta kanku da nigeria, domin gwamna da kanshi ya saka a yi mishi bincike, idan aka kama ku babu ruwana." Ya kashe wayar sannan ya kira wani layi. "Ya ka samu labarin inda ya kai Deen?" "Gaskiya bani da tabbaci amma ina kyautata zaton India ya fara zuwa, kuma a tunanina Deen ya kai asibiti." Murmushi Mahmoud yayi ya ce mishi. "Shi kenan zan san yadda za ayi a nimo kwararru na musamman a tura hoton Deen can, kawai a gama da shi." ** Jabir Adam Kallon Tinah yayi yana faɗin. "Aunty babu lokaci, Yallabai Deen ayi ƙoƙarin dauke shi a can!" Ya fada yana cire abu a kunnenshi. "Me yasa!" Kunna mata muryan layin Mahmoud yayi. "Tow me kake tunani?" "A rena musu hankali!" "Tow shi kenan!" Kiran wanda Tafida ya bari yana kula da Deen Tina tayi suka yi magana, ta tanbaye shi ya aikin, ya gaya mata anyi nasara kuma Alhamdulillahi, tun washi gari ya farka. Amma baya asibitin ya tafi masallaci idan ya koma zasu yi magana. Godiya tayi mishi. Sannan ta kashe wayar, tana gayawa Jabir Adam. ** *Ummu* Tunda yazo nake ji kamar xan mutu, ganin har lokacin ban bude idanu ba yasa shi riko hannuna. "Me yasa kika min haka?" "Ka tafi ka ji!" "Ina zan je bayan ina da ke!" Hawaye ne ya zubo min nace mishi. "bana da ni, da kana da ni ba zaka tab'a juyawa bukatatta baya ba!" "Ummu! Ki yarda dani wannan ba mafita ba ne, bana son wani abu yayi hurt dinki please!" "Ka tafi gida!" Na fada xan juya mishi baya. Domin na fara haki. "Idan na amince zaki tashi daga jinyar nan?" Kallonshi nake idanuna cike da kwalla shima kuma nashi cike yake da kwallan. "Zan tashi yanzu ma mu tafi gida, xan bika na kwana a gefenka!" Shafa min kai yayi ya ce min. "Ummu kin rame sosai, me yake damunki ne?" "Ina jin wani irin tashin hankali ne daga zuciya ta, sai naji kamar zuciya ta zata fashe so nake kawai ka amince ka ce zaka aureta ko xan daina jin haka!" Kamar ya fashe da kuka ya ce min. "Wani yana cutar da zuciyarki ko?" Girgiza kai nayi ina faɗin.."rashin amincewarka shine yake cutar dani!" Kura min idanun yayi yana jin kamar zai yi kuka yace. "bayan nan akwai wani abu da kike bukata ne?" Hawaye ya zubo min, na dauki hannunshi na daura akan bugun zuciyata. "Ka ji yadda nake ji, ka ji abin da nake ji? Wallahi ji nake kamar kafin gari ya waye zan mutu!" "Me kike so nayi ki daina jin haka!" "Don Allah ka amince itama ta huta, Don Allah Aliyu!" Inji Mama tana bakin kofar dakin. Hawaye ne ya shiga zuba min. "Mama ina jin tsoro ne ne!" "Ba shi bane mafita ka amince muga abinda hali zayi!" Kamar ya fasa ihu ya ce mata.."Mama shi kenan zuwa an jima zan dawo!" Ya mike dafe kirjina nayi da yake wani irin tsalle. Juya kaina nake ina ji kamar zan mutu. "Tunda ba zaka iya taimakawa ba, don Allah ka sake ta." A razane ya kalli Mama. "ka sake ta don Allah, ka sake ta ka dauki abin da kake so." "Mama!" "Bukatar Ummu shine tayi farinciki taya zan ganta cikin wannan yanayin na zuba mata idanun? Ni fa uwa ce!" Ta fada a sanyaye, tari na fara ina rike kirjina. "Zo ka fita mara imani, ka je kada kayi abin da take so, Allah yana.." "Amince !" Ya fada yana zama a bakin gadon, tare da rike kanshi. "Na amince don Allah ku barmu da ita." Ya fada muryanshi yana rawa, juyawa yayi yana faɗin. "Zan aureta yayi miki!" A hankali na zube a wurin, ina jin ihunsu amma ban san me ke faruwa ba, hajiya kuka take tana jin kamar ta cire ciwon ta daurawa kanta, haka yasa ko gida bata zuwa. Addu'a kuwa babu wanda bata mata, sadaka da take na kuɗi da Abinci da take sakawa a dafa a rabawa mutane. Zai saka ka fahimci Hajiya tana mugun son Ummu. "Gaskiya baka da kirki!" "Ya xan yi Sagir!" "Ya kuwa zaka yi! Haka zaka saka idanun akan gidanka Ummu tana buƙatarka." *** Abba A gaban Malam Zailani yake zauna, kamar zai yi kuka ya ce mishi. "Alhaji! Aliyu yana kokari mutane ne basu da adalci, idan ka koma ka ce ya amince da bukatarta. Ya amince, auren yana cikin ƙaddaranta, ka bashi hakuri idan yana son ta samu lafiya dole sai ya amince, haka zai saka ta samu sauki da sassauci in sha Allah." "Na rasa yadda zan yi da Tafida!" "Ka kyalesu dta shi mana, Aliyun dai Aliyu ne sannan ba zai tab'a sauyawa daga yadda yake ba, don haka ga gidan shi nan su shigo Allah ya basu sa'a." "Tausayi nake ji kada yarinyar ta kara samun matsala da Aliyu!" "In sha Allah haka ba zai kara faruwa ba! Allah ya shiga lamarinsu........ 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7646 Tunda Tafida ya amsa shi kenan, ba a kara ganin Asiyah da Uwarta ba, koda Abba ya ji labarin sun koma Yola bai ce kome ba, da kanshi ya shirya zuwa Yola domin ya ji kome, kuma dama yasan karshen idan suka sami yadda suke so shi kenan, har abada ba zai tab'a barin wani ya cutar da Ummu ba, sai idan baya numfashi. Faruwar abin da kwana hudu ya isa Yola. A lokacin da Turai ta ganshi a gidan ta sha jinin jikinta. Kame kame ta fara yi tana son lallai tayi mishi bayani amma ko inda take bai kalla ba, ya kurbi ruwan goran da Alfah ya mika mishi domin tare suka zo. "Na zo ne nayi miki kashedi! Tunda kika watsar damu ban kara jin ko ganinki bayan rasuwar mahaifina, haka ba laifi ba ne don naji kina zumunci da masu zuwa wurinki!" Murmushi yayi yana kura mata idanu. "Tun kina yarinya nasan halinki, kuma ko ba a gaya min abin da ya faru na nasan zaki aikata kin zata haka kawai nake gefe akan Tafida. Ki gayawa Bokan da yayi aikin ya warware idan kuwa kina son ganin bakinciki ki tambayi Hindu, duk hidimar da tayi sanadiyar rikon Tafida ke babu Allah cikin sha'aninta gata ga Tafida, ba alfahari ba ni nasan Allah ba zai tab'a kunyata ni ba, domin kuwa na yarda da shi." Tunda ya fara magana ta firgita haka yasa shi sake murmushi. "Idan ma baku lalata ba, sharrinku zai dawo kanku!" Daga haka ya bar parlour tare da Alfah. Bayan fitar Abba Asiyah ta fito daga ita sai mini skirt da wani hafvest. Tana kallon Uwarta. "Mammy lafiya?" "Zan tafi wurin bokon nan ne yau din nan ba sai gobe ba!" Rausayar da kai yarinyar tayi tana faɗin. "Me kuma ya rage bayan ya amince zai aure ni!" "Ba shi bane mafita! Ya kara nimo mana hanya da zaki riko hannunshi!" "Kuma dai!" Asiyah ta fada tana saka takalminta. "Hm!" Uwar ta shige dakinta, ta bar Asiyah tana waya da wata kawarta ta zo musu da abar.. Abba ya bar Yola ya dawo gida don dama wuni ce bai da niyyar kwana sai abu na gaba da yayi dangin Mahaifinsu Asiyah da ya tafi wurin niman auren Asiyah a can, duk da mutanen suna da kirki su dai abu daya suka sani sun basu aure idan suka shirya a zo a daura auren don Allah ya gani tsoron fitinar Uwar Yarinyar suke ji. *** *Ummu* Bayan sati guda. Naji sauki sosai kamar ba ni ba, tun ranar da na cika kwana uku da fara jin sauki Tafida ya saka lallai aka sallame ni shi kawai Doctor Sagir ya cigaba da zuwa gida ana duba ni. Murmushi nayi ina jin yadda yake jan gashina, shi nan yana gyara min gashi na ya cukurkude. Bayan ya gama ya saka ban ya kama min su. Yana faɗin "kin san su Mama zasu zo ko?" Gyada kai nayi ina kwantar da kaina a kirjinshi. "Sadauki!";na fada ina kallonshi. "Na'am jaruma!" "Aikin gidan yayi sauri sosai!" "Eh haka kowa yake faɗa!" Ya fada yana basar da zancen. "Amma na ga kamar part biyu ne a haɗe?" Banza yayi min bai kula ni ba, haka yasa ban kara magana ba, kaya ya ciro min, na saka skirt din hannunshi ya kai ya shafi cikina yana faɗin. "Yarinyar nan yaushe zaki taimakawa bawan Allah? Ya shiga fadar zuma!" Ya fada can cikin kunnena. Ture shi nayi ina faɗin. "kai ja can ni yanzu murna nake Mamana zata zo ka kira min abin da zaka sake jika ni!" Langwabar da kai yayi yana faɗin. "A dai duba lamarin bawan Allah!" Share shi nayi na wuce abina na saka yar bra. Ina gamawa ina kallonshi ta madubi ya balle su haushi ya saka na ce mishi. "Allah ya shirya min kai..." hannunshi dukka biyu naji akan boons din, nayi kewarshi sosai ba zan iya juyawa bukatarsa baya ba, haka yasa na mai da kaina kirjinshi ina sauke ajiyar zuciya,don nayi kewarshi kamar hauka. Na azabtu kewarshi juyar da ni yayi tare da cewa. "Nayi Ummuna!" Gyada kai nayi ina jin wani abu na yawo a jikina. Haka ya shagaltar dani wannan lokacin, Aliyu namiji ne da yasan meye so, Aliyu ya iya jiyar da mace so, Aliyu ya shayar dani zumar da ba zan iya cewa ga yawan dadinsa ba. Amma dai daga ni shi har sai gamu muna wani irin kuka na farinciki da kuma kaunar juna. Ina kwance a jikinshi na ji wayata tana kara, dauka nayi a hankali. " Ummu Hadiyya!" "Na'am Mama kun iso ne?" "A'a ba zan samu zuwa na zan tafi Biu ne anyi mana rasuwa!" Da sauri na mike ina tambayarta. "Waye ya rasu?" "Munirah kanwar Rakiya!" "Allah ya mata rahama, Allah sarki jinya ya kare ki yiwa Zakiya ta'aziya, kafin na zo." "In sha Allah zata ji, idan mun dawo zamu saka lokaci mu zo mu ganki!" Gyad'a kai nayi ina jin kamar na bisu. "Allah ya dawo da ke lafiya sai kin dawo!" "Ki gaida Hajiya da Yaran ta kwace min mijina!" Murmushi nayi mata sannan na kashe wayar. "yau baka da aiki ne?" "Eh jibi layya!" " Hmm karfi da yaji ka hanani azumi;" shafa fuskana tayi yana faɗin. "kiyi hakuri wata shekara zaki yi!" "Hmm!" Wanka muka yi ya kalle ni. "Kina saka ci da addu'a sosai, da nasan kina da yawan Ibada, yanzu kuwa kin watsar, daga ni har ke muna raye ne cikin makiya, yana da kyau ki kara yawan ibada idan ma ba zaki iya sallah dare ba, yana da kyau, ko walaha ki rike, sannna ki kara mai da hankali akan sadaka domin ita maganin masifa ce." Shiru nayi kafin na ce mishi. "In sha Allah zan yi!" Daga haka na koma gadon na kwanta. "Kin yi alola ai?" "Eh nayi!" "Taso muyi sallah!" Ban mishi musu ba, na biye shi muka yi sallah, sannan ya jima yana mana addu'a kafin ya shafa, juyawa yayi ya kalle ni da na jingina kaina da gadon, barci nake. "Lazy girl!" Ya fada yana mikewa, daukata yayi ya gyara min kwanciyata, sannan ya zauna a gefena yana shafa hannuna da ya riƙe, yana zaune a wurin, ajiyar zuciya ya sauke. A hankali yayi ta jiyo hayaniyar masu aiki. Gyara kwanciyarshi yayi kusa dani, a hankali barci yayi gaba da ni. *Deen* Ance duk tsanani yana tare da sauki, anyi nasara aikinsa, sai dai tunda ya farka ya ga me kula da shi ya ce mishi. "Ina son barin kasar nan taya zan fita ba tare da matsala ba? Sannan ka gayawa wanda ya kawo ni baka san inda nake ba. Ina son na bar kasar nan yau zan karasa jinya a wani wurin." "Tow ina zaka sir!" Murmushi yayi ya ce mishi. "wata ƙasar!" Ya fada, yana kwance. "Amma ba zaka iya tafiya ba?" "Kada ka damu zan iya!" Deen ya sauka akan gadon. Jikinshi babu kwari, ya cigaba da cewa. "Yau nake son barin garin nan!" "Ok!" Haka mutumin ya fita Deen ya duba kayanshi, ya ga kome a cikinsa kafin mutumin ya dawo ya cire musu kayan majinyatar ya fita, yasan tunda ya rayu tabbas za a iya bibiyarshi. Kuma idan suka kama shi kashe shi zasu yi, duk wannan abin ana yi ne domin Tafida ba don Ummu ba ne, akwai abin da ya manta akan Tafida, ko lokacin da Tafida ya zama ɗan majalisa bai samu masu bibiyarshi ba, amma lokacin da mutanen suke sararshi yaji daya yana faɗin. _idan muka kashe wannan samun gurbin shiga rayuwar Tafida mai sauki ne, wannan shine kofar Tafida_ Shiru yayi lokacin da yayi nisa da asibitin, yasan zasu iya bibiyarshi don haka yayi wasa da hankali mutane kafin ya wuce inda ya hau jirgin Kashmir, akwai wani malaminsu wanda koyarwa ya kai shi Sudan, idan har yadda ya ji labarin ya bar sudan tow yana Kashmir ba makawa, don haka ya bi address din malamin, tafiya ce da suka kwana, da safe suka isa, ba tare da ya sha wuya ba, ya gano gidan kasancewar Malamin gidansu manyan mutane ne, yana fadar sunanshi aka kai shi har gidan Malami, cikin farin ciki Malamin ya karbe shi, nan suka gaisa kafin Deen ya bashi labarin abinda yake faruwa. "Gaskiya abin da zan gaya maka, shine ka koma ga Aliyu, idan ka cigaba da gudu zasu cimmaka, idan har kana son Aliyu ya samu nutsuwa ka boya a bayanshi yadda zaka kara zakulo mutanen da suke bibiyarshi!" "Naso haka amma ina tsoron kada haka ya zame min matsala ne!" "Ba zai zame maka matsala, abin da zaka yi zan nima maka ticker din gida, amma zan fara gayawa Aliyu" asalin layin da iya Deen yasan Tafida yake da shi babu number kowa Deen ya bawa Malam Anwar. * A can asibiti kuwa, wasu kartine majiya karfi, lafiyayyu kosasu suka isa asibitin tare da shaidawa shugaban asibitin sun zo sauyawa Deen asibiti daga gwamnatin jahar Borno. Ba musu aka kai su dakkn. Abin ya basu mamaki lokacin da aka samu babu Deen babu alamarshi, abin da ya d'aga musu hankali kenan suka fita niman shi kamar karanuka. *** *Ummu* Kallon Tafida nayi da yake ta barci, hankalinshi kwance. Ban daki na shiga nayi tsarki sannan na yi alola na fita, saboda sallah azhar da yayi, shima shafa mishi kai nayi ina faɗin. "Barka da rana yallabai!" Bude idanun yayi na sakar mishi murmushi. "Ummu!" "Na'am wayata a kashe take ko?" "Eh ka kashe hala!" Da sauri ya tashi zaune, ya bude drower din gadon ina kallonshi ya dauko wata Nokia, kunnata yana jin wani iri a jikinshi. Kurawa wayar idanun yayi, "wani abu ne?" "A'a kawai ji nayi kamar Deen yana cikin matsala!" "Lokacin sallah yayi kayi alola ka zo." Ihun Sa'adiyya ya sashi dafe kanshi, a hankali ya wuce ban daki tana ihu da nimanshi. Ina sallah naji ihunta kamar zata fasa gidan, ina idarwa nayi addu'a sannan na mike ina me barin dakin bayan na gyara inda muka kwanta. Bude kofar nayi kamar zata shige da ni, da sauri na bata hanya. "Ina yake? Akan me zaka min kishiya da yarinyar da ka gama isksmci da ita? Akan me zaka ci mutumcina?" Waje nayi ma barsu, sai dai ban yi nisa ba naji ya buga mata tsawa, sai da na diririce. Jikina yana rawa na wuce bangarena, na zube a parlour. Saadiya fitina ce bata kaunar zaman lafiya, ihunta da ke ki yasa na ji a raina dukanta Tafida yake, yadda jikina yake rawa na fito, ganinta nayi ta cukume mishi rigarshi a gaban Mutane, mamaki ne ya kashe ni don ga Hajiya a gefenta. "Sake shi ki tafi kafin a gama miki gyaranki!" Kamar arziki ta sake shi tana huci. "Ummu Hadiyya! Kina tsammanin kin samu wuri har da wani cikin ko? Tow nima zan dawo kuma sai nayi cikin nan na nuna miki babu abinda zaki yi min!" Murmushi nayi girgiza kai nayi ina faɗin. "Ina fatan ki dawo dakinki lafiya, ki zo ki ta haifa mishi yara masu kyau irin shi!" Na fada ina barin wurin, ban san me yasa naji a raina gara ta dawo, babu rana da ba zan ga takaici a fuskar Tafida ba. Gyalenta ta sab'a a kafadarta, yadda kasan yar tasha haka take ita bata da nutsuwa ne kawai amma mace ce sai dai rashin mutunci kawai. Ina kallonta ta window ta shiga cikin gidan tana dubawa, tana gamawa ta fito ta bangarena, tana kallon kofata sake labulen nayi, ina zaune naji ta bude kofar parlour. "Kuma Tafida ne ya zuba miki kayan gida haka?" "Eh!" "Kambu idan bai zuba min ba wallahi zai ga rashin mutunci!" Tashi nayi na shiga kitchen na kawo mata ruwa da juice. Na koma na zuba mata cin-cin da cake, wanda Fanna da Hajiya suka yi saboda bikin sallah, aka kawo min nawa. Ci ta fara tana zare idanu, "kuma don munafunci me yasa kika ce sai ya auro Asiyah? Ke yarinyar nan ban yarda da ita ba, kuma ban zo nan don mu hada kai ba na zo na miki kashedi ne idan kika sake ta kara shigowa da iskanci sai na hada dake da ita naci.." "Zo ki fita min a gida!" Ya daka mata tsawa, kusan Allah sai dariya take bani ina dannewa. Ta cika bakinta da cake ta ce mishi. "Kasan Allah babu inda zanje yawwa sai ka gaya min dalilin da yasa ka amince zaka auri wancan yar iskar yarinyar, ni ban isheka zama gaban mota ba? Ko an gaya maka i don't know what is going on? Look Tafida dole a fasa auren nan ko nayi muku rashin mutunci kuma a kammala min aikin gidana a zuba min irin kayan Ummu, sannan nima wurinka zan tare" dole na fashe da dariya don na fahimci babu amfanin tashin hankali akan irin saadi baby..... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opayar Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 47 Idan na ce muku yarinyar nan mahaukaciya ce, kada kuyi mamaki domin karfi da yaji bata da hankali. "Yawwa kayiwa Ummu ciki ni sai yaushe zaka min cikin nima?" Wulakantaccen kallo yayi mata yana nuna mata hanya, ta ce mishi. "Ba fa inda xan tafi na gaya maka!" Wucewa wurin kayan kallo yayi ta ga haikan wayar wuta zai dauka, da sauri ya fice a parlourn na kwashe da dariya, ina nuna shi da yatsa. "Ango ango!" Zuba min idanunshi da suka ji jajjur yayi, ganin yadda yake kallona na rike kunnena. "Kayi hakuri!" Na fada a hankali, takowa yayi ya gabana ya durkusa. "Ummu!" "Wannan lamarin ba na wasa ba ne" "na sani Daadi!" "Baki sani ba, don bake kike jin zafin ba ko?" Saka hannunshi nayi a kumatuna nace mishi. "Kayi hakuri!" " ba fushi nayi ba amma ya mata ki fahimci wani abu yarinyar nan bata da amfani a rayuwata!" Kallonshi nake wani dakika kafin nayi murmushi. "Idan akwai wanda zai ba da labarinka, daga Deen sai ni" na fada ina cizon bakina na kara kallonshi da kyau. "Har yau kina tuna abinda nayi miki ko?" Murmushi nayi ina girgixa kai. "Ai na manta da shi,domin nasan dole wata rana za'a iya tuna maka, amma Ni bana son a tuna maka don har abada ya wuce." Zama yayi yana kallon yadda nake wasa da wani zaren mayafin kayana. "Me yasa kike boye abin da yake damunki?" "Ni!" Na nuna mishi kaina kafin na girgiza kai ina faɗin. "Ni ba zan ajiye kome na tuna ba!" "Kina kullace da ni kenan har yau? Ummu shi yasa kika yi draging dina na auri Asiyah?" "Me kake fada ne? Ka ga ni ba haka nake nufi ba amma yana da kyau ka yarda da ƙaddara me kyau ko mara kyau sannan ni ban saka ka dole auren Asiya ba, abin da nake ji a raina ya wuce wasa, idan ba zaka auri Asiyah ba shi kenan amma ka daina zargina da turaka auren Asiyah!" Yadda ga na koma ina magana sanyi -sanyi ya sashi rike hannuna yana faɗin. "Ok shi kenan ya wuce, amma!" Shafa fuskarshi nayi nace mishi. "Fatana kayi mana adalci!" "Ki tafi dakina ki dauko min kayana ba zan iya fita da wannan kayan ba!" Murmushi nayi ina kallonshi. "Shi kenan." Zan tashi ya mai da ni yana cewa. "Koma ki zauna na fasa. Ni gobe arfa ko yau ne? Ciwonki ne yasa ni na daina azumin nan fa!" "Muje sauya kayanka!" Na fada ina me riko hannunshi. Muka fita tare, Sadiya na tsaye a ginin da yake yi, ware idanun yayi akanta bai tab'a ganin mutum mara jin magana irin sadiya ba. Bai kulata ba muka wuce ashe tana binmu. "Ke Ummu wai ke bakya gajiya da namiji ne? Abu daya ba zai tab'a gunduranki ba ne!" Ban kulata ba domin kamar bani da abin yi ne, har parlourn ta biyo mu. "Aliyu wai meye matsalarka da matsayina na first lady ne?" Duk da bai son kulata amma sai dai wannan karon zuba mata idanu yayi ya wuce dakinshi, tana tsaye a parlour ni ina kitchen, sai tijara take mishi. Ina cikin aikina naji, gudun kamar za a tashi gidan, dariya abin ya bani. Na fito na hango shi daga shi dai farin singlet da dogon wando. "Yanzu don Allah meye ribar haka?" "Ummu idan ba zaki iya saka baki Sadiya ta fita a rayuwata ba, ki daina nuna min baki damu da ni ba. Taya yarinyar nan zata na Abu kina dariya?" Ajiyar zuciya na sauke tare da cewa. "Tow kayi hakuri na zan kara mata dariya ba." Sai kuma na tsinci kaina da yin dariyar saboda yadda yake haki da masifa. "Wato ga mahaukaci nan?" Girgiza kai nayi xan yi magana muka ji kar'ar waya zubar da abin hannunshi yayi ya wuce dakin domin ni dai ban tab'a jin karar ba sai yau, yana shiga ya dauki wayar yana kallon number da yake kan kiran, kafin ya saka a kunnenshi. "Hello!" "Aliyu Muhammad Jadda!" "Malam!" Ya fada da dan karfi. "Aliyu kana nan ashe?" Nan suka shiga gaisawa, kafin ya gaya mishi abin da ya faru. "Ina Deen din?" "Gashi nan!" "Ya jikinka?" "Da sauki! Tunda abin ya zama haka, kokarin barin India, mu hadu a sudan wata sati!" "Shi kenan!" "Tafida ya za'a iyalina, akwai matsala akanka da iyalinka, babban damuwata na dawo koda ace ba xan iya muku kome ba!" "Deen ka bar India yau, ka wuce Sudan!" "In sha Allah!" Kashe wayar yayi ya juyo yana kallona. "Deen ne!" "Alhamdulillahi! Ya yake?" Zaunar da ni yayi yana faɗin. "Rayuwarshi tana cikin hatsari ne, saboda haka nace mishi ya nufi Sudan zaki raka Ni?" Gyada kai nayi ina faɗin. "ina ne ba xan bika ba!" Shafa kaina yayi, yana faɗin. "Ina cikin farinciki sosai amma bana son na nuna haka a waya gara na nuna mishi a zahiri!" "Allah sarki!" Na fada a hankali ina kallonshi yadda yake zama a gefena. -- Tuni aka saka lokacin auren Tafida da Asiyah, sai dai yadda Tafida yake hidimarshi a raina cewa nake gulma ce, domin maza dayawa irin wannan lamarin ya taso zaka rantse da Allah basu son auren daga baya ka ga yadda suke rawan jiki. Sannan ma ai ba wani abu ba ne, amma Tafida kamar an hada shi da mutuwarsa, haka aka yi bikin sallah layya wanda shine karo na farko da muka yi a matsayin Manyan ni matar gwamna da shi kanshi muka tafi massalaci, inda aka ware min gwanin ban sha'awa ni da Yarana har da Hajiya d Fanna bakiɗayanmu gidan Nana Asma'u da Humairah. Kwana biyu a tsakanin bayan sallah, yana wurin aiki su Maryam suka zo, ina bangaren Hajiya, dake ban san me ya sa ba ni dai na tattara kaso hamsin na zamana a cikin gidan wurin Hajiya nake zama, Hajiya bata da matsalar kome. Ina jin sallamarsu na mike daga kwance ta ce min. "Kwanta abinki ai ba baki ba ne a gidan!" "A'a Hajiya na tuna ya bani aiki nazo na kwanta." "Tow shi kenan!" Ta fada tana kallonsu, zama suka yi kamar wasu na kwarai. "Lafiya!" "Lafiya lau Hajiya, dama mun zo gaishe ki ne!" Suka yi shiru tasan dai ruwa baya tsami banza. "Na gode!" Ta mike zata dauki dan karamin dish da tabawa su Mufida abinci. "Hajiya dama akan maganar auren Autanki ne, shine muka ce ko zai bamu hada kayan amarya da sauran matanshi." "Ai tuni ya bawa Ummu Hadiyya da Kawarta! Baku da labari ne?" Ware idanu suka yi suna faɗin. "Hakika Hajiya ba a kyauta mana ba, muna yan uwan Tafida, taya za a bawa wasu hada kayanshi, musamman Ummu Hadiyya da kowa yasan ba zata hada abin arziki ba, idan ma bata hada abin da zai saka kowa b'acin rai." "Allah ko? Tunda haka ne gara na ga b'acin ran. Kaf duniya Tafida bai da sama da ku amma kuka kware mishi baya, don haka kowa ya tashi ya bani wuri." Kasa da Murya Rukayya tayi tana faɗin. "Hajiya ki kara hakuri, wannan karon zamu baki mamaki zamu jira shi ya dawo sai mu roke shi ya taimaka mana!" Bata kara magana ba, ta koma dakinta babu wani zancen ya bawa Ummu hada kaya, tasan ya basu cutar shi zasu yi ita kuma bata jin zata iya barinsu ne cutar da shi kamar yadda ta ji labarin suka yi lokacin auren Ummu, suna gidan har Magariba, girki ina gamawa na zuba na Hajiya na kai mata. "Assalamualaikum!" Suna jina suka ki amsa sallamar. Fanna da take tare da Yaran ta amsa, fitowa tayi tana faɗin. "Mami sannu da kokari." "Yawwa Aunty Fanna" abincin na mika mata, "a shafa min kan Mufida!" Dariya tayi tana faɗin. "Leka ki ga abinda take yi!" Lekawa nayi na ganta ita nan tana sallah, ta saka hijab tana ta kokarin mikewa, don ita tafi Mufid kokarin cewa zata tashi. "Fanna ki bi a hankali, Sayyada Mufidah tana sallah idan tayi addu'ar karba Allah zai yi!" Na fada ina barin kofar. "Aunty Baby dariya muka yi fa!" "Na dai gaya miki!" "Mami har da zaman tahiya tayi!" "Ai dole " muka yi ta dariya. 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Ina kowa bangarena, wanka nayi na shirya cikin wani material sannan na dauki abincin shi na kai mishi bangarenshi nayi ta jerawa haka nayi kafa uku. Sannan na rufe bangarena, na zauna a parlourn. Can kuwa sai gashi ya dawo, wurin Hajiya ya fada nufa, haka na gaya mishi, kafin ya fita ya fara zuwa wurinta ta saka mishi albarka ya tambaye ta bukatar da take da shi, meye matsalarta. Idan babu yayi mata dan hira sai ta mata sallama, zata saka mishi albarka. Idan ya dawo kada ya damu da ya gaji ya fara zuwa ya gaya mata ya dawo ya zauna su yi hira ita da kanta zata mishi magana. Bai so haka ba amma kuma sai naji a raina ina son yayi haka domin akwai wani albarka da alkhairi a tare da Uwa. Haka yasa idan ya je ya zauna suka gaisa nasiha take mishi kafin ta ce mishi maza ya tashi kada ya makara, yana dawowa ma zai shigo tana ganinshi zata fara cewa. "Baka huta ba ka shigo! Sannu" yana gaishe ta zata ce mishi"maza wuce kaci abinci ka tafi ka huta!" Haka zai rungume Yaranshi yana d'aga su. Irin wannan abin ne wata rana muna zaune a parlourn Hajiya ya gaidata zai fita Mufidah ta ga hotonshi an nuna shi a tv yarinyar nan ta rarrafa wurin tv tana ihu ita ga Babanta an nuna shi sai mika mishi hannu take wai ya dauke ta daga tv, dariya yayi ya dauke ta cak yana faɗin. "Mamana baki ganni bane? Ga danki nan Uwata!" Yayi ta cillata sama tana dariya, sannan ya dauki Mufid da shima yake dariyar, ya cilla shi sama yana faɗin. "Babana, ka zama super Man ka ji!" Haka yayi ta surutu. Hikima biyu nayi amfani da shi na farko Hajiya zata Ganshi kafin wasu su ganshi. Sannan yaranshi zai fita basu ganshi ba amma zai dawo zasu ganshi idan ya huta kafin su kwanta zai koma yayi musu hira ya basu lokacinsa har su yi barci. A hankali na cusa mishi wannan dabi'ar ba tare da ya sani ba, sannan nakan ware lokaci nace mishi ba zai ci abinci a bangarena ba, ya je yau yaci a wurin Hajiya. A hankali wasu abubuwan da suka faru a baya zasu na gushewa a zukatarsu. Idan na gaya mata yau a bangarenta zamu ci abinci da kanta take girki Hajiya ta girma amma irin mutanen nan ne masu kwarin kashi da himma, ga ibada kamar me ta yarda da akwai Allah kuma shi yake tsaye bisa kan alamarinta. Idan Hajiya tana mana nasiha sai ka rantse da Allah wasiyyar mutuwarta take bamu, haka yasa nake yawan son zama da ita. Yana shigowa parlour Hajiya ya same su zaune. "Barka da gida Hajiya!" "Barka dai dan albarka! Ya aiki ya aka ji da al'umma!" "Alhamdulillahi sai godiya, na gode sosai Hajiya ki cigaba da mana addu'a, akwai nasara amma kalubale yana zagaye damu!" "In sha Allah babu abin da yafi karfin Allah, Ubangiji ya ƙara dafa maka!" "Hajiya akwai kunun tsamiya nan ne?" "Eh amma na bawa Ummu da aka dama maka!" "Na gode Hajiyata!" "Yallabai barka da dawowa!" Inji Maryam.."Yawwa Maryam ya gida?" "Alhamdulillahi dama mun zo ne akan maganar hada lefe!" Yadda Hajiya ta rufe ta da faɗa ya bata mamaki. "Ya daga dawowarshi ko hutawa bai yi ba, zaki ce wani hada lefe? Na gaya miki ya bawa Ummu da kawarta!" "Tow Hajiya ya karba ya bamu, Ummu da take da duhun kai yaushe tasan kaya a laster!" "Tabbas Ummu tana da duhun kai shi yasa ba zan baku ba, gara na bata ta cinye kudin da na baku, Hajiya ki jawa Yaranki kunne wallahi idan suka bani haushi zan saka a daina barinsu zuwa kuma kayan aure ban yi niyyar baku ba." Yadda bawan Allah nan ya rufe idanu yana ta tijara sai abin ya baka mamaki kalma daya suka fada yake jin kamar an zarga mishi igiyar wuta a wuyarshi. Karshe da fushi ya bar bangaren Hajiya ita kuwa ta ce su bar mata gidanta. Ba zasu kashe mata Yaro ba, tunda babu mutunci cikin lamarinsu. Wannan abun ya kara b'ata musu rai, don haka suka bar gidan a fusace don dai sun san kudi kan Tafida zai zuba domin ko auren shi da Saadiya ya basu miliyan uku da rabi ne, amma suka yi ta shirme da sunan hada kaya duk da sun hada mata kayanta me kyau na fadar kishiya ce suka dauki dubu hamsin suka bawa Ummu wai tana da sauran kayan aure me zata yi da kaya gashi haihuwa zasu yi.. Yadda naji buga kofar gidan Hajiya na fahimci da zafinsa zai shigo, addu'ar da tafito bakina nake karantawa. "Assalamualaikum!" Yayi sallamar a fusace, abin da zai saka Tafida saukowa a wannan yanayin ba abu ne mai sauki ba, "Amin waalaikumunsalam! " na fada ina mikewa, yadda yake huci yasa na kara jin abin da zai yin ba kuskure ba ne, ina nufarshi sai da ya rage taku biyu a tsakaninmu, nayi kamar naci tuntube, na tafi zan fadi, da sauri ya tare ni tare da kiran sunana da karfi. "Ummu!" Tunda naji yayi min masauki a jikinshi na ce mishi. "Alhamdulillahi! Ai ka tare ni ai, babu abin da ya faru da ni. Lallai an bata maka rai su waye haka na ji dasu." Na mike ina bubuga hannuna tare da faɗin. "Ka gaya min su waye na ji dasu, gaskiya kana gama wannan shekarun hudun ba zaka kara tsayawa takara ba, kai ma ai mutum ne haka kawai za a saka maka ciwon kai waye shi?" Yadda na dage ina masifa na san ba daga waye ya dawo haka ba domin lokacin da ya dawo ina kallonshi ta window da fara'a a kan fuskarshi sannan ya juya yana kallon bangarenshi nasan yana dubawa ne ko na zo. "Drama Queen! Ni zaki mai da dan bulayi? Muje ki ji da ni. Sannan ki shirya kayanki zamu yi tafiya na kwana uku!" "Ba dai zaka gaya min me aka maka ba?" "Cab kuma Me zame zaki yi?" Nuna mishi kwanjina nai ina muzurai. "Zan aikata kome!" "Gaskiya ne yar karamar gajeruwar matata!" Na lura yana son fadar kalmar nan da zaran ya huce daga fushin da yake yi, murmushi nayi mishi ya kai bakinshi kamar zai hada da nawa har da rufe idanuna, bawan Allah nan ya cixan min hanci, ture shi nayi ina faɗin. "Kayiwa kanka ba zan tayaka kome ba!" Ina shafa hancin da ya ciza. "Gaskiya baka da imani, cinye min hanci zaka yi? Don Allah ji yadda idanuna ya cika da kwalla waye aka tab'a ciza akan hanci?" Na fada ina shafa hancin kai mutumin nan bai da dad'i, "Allah ya baki hakuri!" Murguda mishi baki nayi na bar shi anan, kurawa min idanun yayi shi sai yanzu ma.ya ga kayan jikina. Sake jakan aikin yayi faɗin. "Ummu zo ki dauke abuna na bar miki duka, amma don Allah ki bar juya min kugun nan wallahi sussucewa zan yi!" Juyawa nayi na kalle shi na kara da cewa. "Tunda ka cije ni akan hancina kayiwa kanka kowa ya kwanta a part dinsa." "What? Ni din banza ni din wofi waye ya gaya miki ni din wani ne ai ni bawan Allah ne kuma, Yaron gidanki Madam gaya min meye ya dace nayi domin wanke laifina ya mai girma mai shara'a!" Ya fada yana cire hular kanshi, ya wani haɗe hannu a gaba yana me sunkuyar da kai. Kallonshi nake kafin nace mishi. "Mai laifi ya amsa tuhumar da ake mishi?" D'ago kai yayi tare da yin fuska kamar ta mage ya wani kasa da Murya . "Ya mai girma me Shari'a na amshi laifina hannu bibbiyu?" "Anya ka amshi laifinka?" "Ya mai shara'a na amshi laifina hannu bibbiyu!" "Kotu me adalci zata yanke maka hukunci daidai da laifinka!" "Na'am ranki shi dade!" "Hukuncin shine ka sunkuyo da fuskarka sannan ka rufe idanunka!" Haka kuwa ya sunkuyar da fuskarshi daidai nawa, na sumbaci kumatunsa na kara da cewa. "Idan hukuncin baiwa me laifi dadi ba zai iya daukaka kara a kotun da yake gaban wancan dakin!" Na zuba a guje. Sake baki yayi yana faɗin. "Ya mai shara'a hukuncin yai kuma mai laifi ya amshi laifinsa sai dai zai daukaka kara ne idan ya sake aikata makamancin laifin da yayi!" Juyawa nayi ina me bude mishi hannu, idanuna cike da kwalla, zuwa yanzu na fahimci yadda nake dawainiyya da soyayyar mijina. Amma bana nufin tauye shi a kowani fuska, karasowa yayi ya shiga jiki yana me dukawa, "Kayi hakuri da rayuwa, ko yaya ka sami dama kasa kanka farinciki kada ka manta da saka kanka farinciki haka zai taimaka ainun wurin inganta lafiyarka! Duk wanda zai maka ba daidai ba zai yi ne don ya fusataka saboda an sanka a fusace zakina! Na sanka kai mai gaskiya ne kayi hakuri da kome kankantar b'acin rai kada ka nuna musu haka zai saka su cutar da zuciyarka." Na janye jikina sannan muka shiga daki, ya zauna a bakin gadon. "Kada ka manta gidan nan gaba kaɗan zai cika da mutane masu mabanbanta dabi'a, idan baka koyi sarrafa fushinka ba, wata rana har ni zaka hukunta da fushinka!" Kallona yayi da sauri, na gyada mishi kai. "Eh Haidar! Ni kaina ban tsira daga fushinka ba, waye zai tsira? Haidar duk duniya ko Hajiya zata nuna min ta haife ka ne ta kuma san waye kai, amma ni nafi kowa sanin waye gwamna Aliyu Tafida, ni zan kara bada shaida akanka. Ka yawaita azkar idan ka fusata. Ni nasan mijina mai addini ne da takawa amma fusatacce ne, sojan nawa, sannan kawo kunnenka na gaya maka waye ne kai!" Matsowa yayi na sumbaci kunnen tare da tsotsan kunnen nace mishi. "Kai ne kaɗai kake iya saka kuka, amma na dad'i!" ...... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opayar Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 48 Rungume ni yayi yana faɗin. "Duk wannan draman na meye?" Janye jikina nayi ina faɗin. "Malam sake ni muje kayi wanka!" Haka na taimaka mishi dama na cire mishi takalmi, ya mike na taya shi cire sauran kayan wanka ya shiga na gyara dakin, na fita na hado abincin shi na kawo dakin, na shigo na zauna yana fitowa na mike tare da amsar towel din hannunshi, na shiga taimaka mishi ya goge jikinsa 3qrt ya saka, sannan na zauna dashi na saka mishi rigarshi Armless ne, na zuba mishi abinci, ya sauka kasa yana ci yana kallona. "Kaci a nutse ka ji!" Ana yawan cewa bayan wuya sai dad'i, ga dadin amma bata zo mana da sauki ba, kamar ba Tafida da na sani ba. Ya sauya kamar wata halitta na daban. D'agowa yayi ya kalle ni, na kara mishi namar miyan yana ci yana kallona. "Ki yafe min!" Jan hancinsa nayi ina faɗin.. "Bakyau ana cin abinci ana magana, ba sunnah Manzon Allah ba ce!" Murmushi yayi yana dauke kwalla da yake son fitowa daga idanunshi. "Kana namiji kana share kwalla!" "Tsoro nake ji." Mamaki ya bani na ce mishi. "Tsoron me ni Ummu Hadiyya!" "Tsoro nake ji kada kina saka ni farin ciki ne amma a kasar ranki baki yafe min ba, ban san yadda zan kare da Rabbil Ka'aba ba." Jan kumatunshi nayi ina faɗin. "Ka bani tsoro wallahi ma zata wani abu ne can!" Na fada ina kallon yadda yake tsakuran abincin idan na bi na Tafida ba ci zai yi ba, haka na karbi cokalin nayi ta tura mishi, hararanshi nayi cikin haushi nace mishi. "Shi gulma dai babu kyau zaka ci amma ka tsaya kana wasa da cikinka an jima kace kana jin yinwa ko?" "Ummu!" Gatsine nayi mishi nace mishi. "Oya sha ruwa!" Karba yayi ya sha yana tsammanin na gama masifar ne na ce mishi. "Dazun kace na shirya zamu yi tafiya ka gayawa Abba da Hajiya ne?" Ware idanu yayi kafin ya ce min. "yanzu idan zan yi tafiya dake sai na nemi izninsu?" Ware idanu nayi tare da tafa hannu ina cewa. "Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama! Tafida." Na fada ina rike bakina "kai nufinka na tafi kada na gayawa kowa ko so kake kacewa Hajiya zamu yi tafiya da Ummu?" Na fada ina hararanshi. "Hmm tow meye aibun haka?" Girgiza kai nayi na ce mishi. "Babu aibu amma ka fahimce ni, dole ka nemi izninta." Na fada ina tattara kayan abincin. "Ummu ki min bayani don Allah taya xan yi kinga Deen baya nan balle na tambaye shi." "Ba zan maka bayani ba, sannan kada ka sake ka gaya mata zan bika sai ka ji me zata ce idan ka san me zaka gaya mata." Kanshi ne ya daure, bai ce uffan ba na bar mishi dakin, wayarshi ya dauko daga cikin jaka. Kiran layin yayi. "Deen ina son mu tawo da Ummu amma tace sai na tambayi Hajiya da Abba!" "Yaushe zaka girma? Ka tafi ka samu Hajiya ka ce mata, ka zo ta baka aron Ummu shima Abba haka zaka gaya masa!" "Kana nufin akan haka Ummu ta ki gaya min yadda zan yi?" "Tafi can!" Ya kashe wayar, ya fito tare da nufar bangaren Hajiya, ina dakina wanka zan shiga ina faɗin. "Fisabiilillahi taya don bani da kunya nace zan bi shi zuwa wani gari, sannan yana ganin haka shine daidai don Allah. Ace baka iya niman izinin ba" na cire rigar ina me zama haushi ya ishe ni. "Sam Tafida bai da ganewa!" -- Tsalle Mufid yake don bai yi barci ba, daukar shi yayi a cinyar Fanna yana faɗin. "Fanna yaron nan yana da wayo na Mufidah kuke gani!" Ya fada yana zama a kasa, tashi Fanna tayi ta bar parlourn tana faɗin. "Wayo kan ai yafi Mufida ita nata ne ya fito fili amma nashi irin na Aunty Baby ne ba zaka fahimci wayonta ba, sai idan lissafi ya hadaka da ita ko wani abu me muhimmanci." Gyada kai yake yana faɗin. "Hajiya kin ji fanna ko?" "Eh na ji ta kai!" Ta fada tana murmushi, "kayi hakuri da su Maryam!" "Tow ya xan yi da su? Allah ya kyauta ka basu hada lefen kada mu karawa Ummu bakin jini!" "Eh zan basu ki kira su, su amsa ta hannunta." "Haka yayi!" "A'a Hajiya haka bai yi ba, ku bar Aunty Baby ta hada kayan su zo su dauka idan ba haka ba zasu iya cewa bata basu kudi a wadace ba!" Inji Fanna tazo daukar wayarta da yake parlour. "Eh kuma haka ne don zasu iya haka!" Zama yayi sosai yana faɗin. "Na gode Fanna!" Ta bar su anan suna hira, kafin ya cewa Hajiya. "Hajiya hmm!" "Ina jinka!" "Dama-dama!" Kallonshi tayi da kyau. "Aliyu idan baka gaya min damuwarka ba waye zaka gayawa!" "Hajiya xan yi tafiya ne nake son Ummu ta raka ni, shine nazo tambayarki!" "Kai rawan jiki ita rawan kai, ku je ku taru ku barar da dan kyauta da Allah ya baku, babu inda zaka da ita!" Ta fada yana mikewa. "Allah Hajiya babu abinda zai same ta, don Allah ki bani aronta!" Yana bin bayanta, yadda yake rokonta yasa ta jin sanyi da dad'i a lokaci guda, "na amince amma wallahi ka kula kada wani abu ya samu lafiyar cikinta!" Rungume bayanta yayi yana faɗin. "Allah ya amintar dake rahamarsa Hajiyana!" "Amin Ya Allah Kusar yaki!" Da sauri ya bar parlour yana faɗin. "Hajiya a saka mu cikin sujadar nan da tahiya don Allah!" "Aliyu aikina kenan tun kafin na haifeka ban tab'a fasawa ba, kuma ba zan fasa ba, sai na daina numfashi." "Allah ya biyaki da gidan Aljanna mafi tsada da girma Allah ya hadaki makota da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama! Sai da safe Hajiyana!" Ya fita da sauri, sai kuma ya tsaya yana me rike kub'insa, murmushi yayi yana girgixa kai, kafin ya wuce part dinsa, a parlour ya same ni. Zaune a parlour ina sanye da riga da wando na barci, sake baki yayi yana kallon yadda na zauna ina shan fruit a hankali, lissafi ya fara da hannunshi yanzu kafin ya dawo har nayi wanka tow Anya Ummu ne ko kuma wata ce. "Mai shara'a yaushe kika yi wanka kika sake kaya har da gyaran gashi haka?" Dauke kaina nayi tare da kallon tv ina kallon tv, tasowa yayi ya nufi inda nake ya riko hannuna. "Ummu zaki kashe ni don Allah muje na baki labari!" Daukar grape nayi tare da kaiwa bakina. Rike hannuna yayi ya kai bakinshi. Yana taunawa tare da sumbatar yatsuna yana kallon yadda nake mishi shu'umin murmushi. Tafin hannuna ya sumbata, har zuwa fuskana a hankali yake gangarawa inda ba zan iya hana shi ba. Lumshe idanuna nayi, idan na tuna nan gaba kaɗan zamu cika gidan. Sai na ji hawaye ya cika min idanuna, yadda yake min haka zai musu yadda yake bin wani kafa da jikina yana lasa da tsotsa. Sai naji raina na b'aci, a take nayi ta jin me yasa na barshi ma zai ta kara aure. Abin da yake min yasa na watsar da tunanin da nake ina jin kwalla na zuba min domin kuwa Tafida ya gama kashe ni ya gama min raga-gara a duniyar kaunar shi, ban san ina kuka ba sai da naji ni a wata duniya. Na sake wata irin ƙara ina sake mika mishi kaina da rayuwata ba zan iya mishi jayayya ba, a kullum Tafida sabo yake dawon min, rungume shi yadda yake tafiyar da kome a a nutse yasa na rufe idanuna, duk da wnnan halin hura min iskar bakinshi. Bude idanuna nayi akanshi. "kin san yadda nake sonki?" Bakinshi na kama daga nan na toshe abin da zai fada domin nasan matuƙar zai fada kamar b'ata lokaci ne, haka muka yi ta gwagwarmayar, sai da muka nutsu ya gano a parlour muka yi wannan tabargazar.. "Darn it! Yarinyar nan zaki kashe ni, sai da kika saka na kasa jurewa." Ya zungure goshina. Murmushi nayi ina faɗin. "kwadayinka." Na fada ina sakala hannuna a wuyarshi. Jan wandonsa yayi sama, ya dauke ni zuwa dakinmu. "Har abada nan ne dakinmu, kuma bayan ke babu macen da zata shigo min shi." Ban daki ya wuce da ni, wanka muka yi, koda muka fito karamin towel yasaka yana goge min kai, cikin raha. "Ummu zan baki kudi kaya ki hada muku, miliyan goma tayi aiki?" "Eh yayi kai! Allah ya sanya alkhairi, amma me yasa baka bawa su Maryam ba?" "Saboda zasu iya bani kunya !" Murmushi nayi nace mishi. "Yadda ka yarda dani ka bani in sha Allah ba zan baka kunya ba!" Na fada ina sumbatar kirjinshi. "Na san da haka!" ** 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 ** Washi gari. Ina tashi sai da na yi abin karyawa na kaiwa Hajiya sannan na dawo na tashe shi muka karya, sannan ya shirya na raka shi har wurin Motarshi. "Kin ga na manta da passport dinki akan bedside da wayata please dauko min!" "To!" Na juya zuwa cikin gidan, shi kuma ya sauka ya nufi wurin Hajiya suka gaisa a tsaye, sannan ya dawo motar ya zauna, ina zuwa naga wayarshi tana haske, ban dauki kiran ba na kawo mishi tsaki yayi ya ce min. "Kin ga kin hada ni da fitina ko? Yan matan yanzu duk basu da kamun kai, kowacce ba zata iya zama kamar ke! Ki tabbatar kin shirya zuwa sha biyu za a zo daukarki zamu wuce Kano!" "Tow Baban Mufidah!" "Ke wannan sunan sai kace daga wancan unguwar!" "Eh getto area ba, ai unguwarmu ce." Na fada ina hade rai. "A'a ba nufi na ba kenan!" Zai sauka na rufe mishi motar har da rantse rantse ba haka yake nufi ba. "Kai wuce a shi kada ka sake ya dawo da kai aikin Al'umma zai tafi!" Cizon bakinshi yayi na kwashe da dariya ina d'aga mishi hannu. Ajiyar zuciya ya sauke, yana murmushi ya leko tare da d'aga min hannu. "Allah ya tsare!" Sannan na wuce na gaida Hajiya. "Yawwa ga taliyarki da wake da mai da yaji, nasan yanzu zaki ce zaki gyara gida ci sai ki tafi. "A'a bari na dawo Hajiya a rufe min ba zan jima ba!" Na fita da sauri sai da na gyara gidan tsaf, kafin na dawo na samu ba su Nana Asma'u da humairah. "Hajiya sun tafi makaranta ko?" "Eh dazun Alfah ya zo ya dauke su." "Allah sarki," na ce, ita kuma ta ce min. "Gaskiya Tafida ya kyauta da ya janyo Yaran Salamatu a jikinsa!" "Haka ne kan hajiya!" Watan shi uku da fara aiki ya ba bawa Sharif wani appointment na Borno state primary health, wannan yasa ko mi dare idan tafida ya kira shi zai d'aga. Sannan ya fadawa Deen ya mishi hanya ya samu ganawa da wasu kungiyar NGO, haka yasa bakiɗaya yan dakin suka bala'in girmama Tafida, ga Alfah shima yadda yaron yake da mugun saukin kai yasa Tafida tambayar Alhaji meye ra'ayin alfah. Tsaki Alhaji yayi yana faɗin. "Me ya wuce tafiya makarantar tukin jirgin sama, ai kasan da hankalina ba zan barshi ba don ba wai ban da kudin ba ne a'a Alfah yana da rawan kai ne." "Abba ka kyale shi idan haka ne bukatarshi ku bishi da addu'a kawai ni kuma zan yi iya bakin kokarina akan shi!" Akan wannan maganar suke don ya turawa Deen kome ya mishi, wannan abin ya faru. Dawowarsu Nana Asma'u ya roki tafida ko zai zo yana kaisu makaranta ne, da farko Mahaifiyarshi bata so, amma ganin duk wanda ya rabe Tafida a wannan lokacin baya rufe mishi kofa yasa Hajiya Salamatu ta hakuri. Murmushi nayi ina jin abin da Hajiya take cewa, wayata ce tayi ƙara na dauka Asiyah! Dauka nayi na mata sallama. "Maman Mufidah! Kiyi hakuri wallahi ban yi niyyar zuwa miki da wata manufa ba, sannan kin san ƙaddara da rabo wallahi ba nufina na." "Naji lafiya kika kira ni?" 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opayar Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 49 Shiru tayi kafin ta gyara murya tana faɗin. "Maman Mufidah idan aka miki abin da kika min zaki ji dad'i? Fisabiilillahi idan ke aka wa haka zaki ji dad'i?" "Ban gane me kike nufi ba? Ki gaya min yadda zan fahimta." Wani dariyar renin hankali tayi min kafin ta cigaba da cewa. "Fisabiilillahi kowa yasan cewa kin mallake Tafida da iyayenshi baya jin maganar kowa sai naki." "Da gaske? Wai ya aka yi ban gane da wuri ba gaskiya malamin da yayi min aikin nan ya cancanci na kara mishi wani abu yawwa yanxu kina ganin mallakar da na mishi ya isa ko bai isa ba?" Ashar ta auna min gangariya, na kuwa sake mata wani malalacin dariya na ce mata. "Yan mata kin ga ni ban san asirina ya kama Tafida ba, amma tabbas an zo inda zan kara yin wani hadin, sannan ki gaya min me ya faru?" Ban rufe baki ba tayi ta zagina tare da min miyagun alkaba'i ya dame ni ne? Ko kallon kashi bata ishe ni ba, na kashe wayar babu bukatar na d'aga hankalina akanta, kuma ban yi wani abu da zai saka ta fahimci naji haushi ba. Wayata ce tayi ƙara, ina dubawa naga wai kudi aka turo min daga Tafida, account dina bai taɓa amsar kudi me nauyi haka ba, ai kuwa tuni suka garkame dan iska. Kiranshi nayi, "Yallabai account din nan fa bai tab'a amsar irin wadannan makudan kudade, ka turo a kai ni banki don Allah!" "Babu inda zaki, ki jira Alfah zai zo ya amshi kome, kada ki sake ki bishi na gaya miki!" "In sha Allah!" Karfi da yaji tunda ya zama gwamna shi kenan aka haramta min fitar rana (😒) hararan wayar nayi har na dungurata can, sai ga wani kiran ya kara shigo min, dauka nayi na saka a kunnena na ce mishi. "Me kuma ya rage?" "Kada na ji labarin yazo ya ganki babu hijab don Allah ki rufe jikinki kada na mutu da kishinki!" "Uhm!" Na fada ina mamaki. "Tow ina dai gaya miki gaskiya ne" "Ni fa ina gidan Hajiya ne!" "Nace ki nime hijab kafin ranki yayi mugun b'aci!" "Tow amma ai kaninka ne!" Dafe kanshi yayi ya ce . "Ummu!" "Shi kenan zan saka na ji ba sai ka min ihu ba kasan bani da lafiyar zuciya!" Sassauta muryanshi yayi yana faɗin. "Shi yasa bana son tashin hankalinki, ki taimakawa bawan Allah ki saka hijab kin ji yar gatar Aliyu!" "In sha Allah!" Na fada, ina me fita a parlour Hajiya yana gayawa min abubuwan da Alfah zai tambaye ni, duk na hada sannan na dauko hijab dina, sakawa nayi na koma parlourn Hajiya. Bayan mintina Talatin sai gashi ya zo, na bashi kome da kome, sannan na mika mishi Atm. "Ka kaiwa Hajiya Kaltuma zamu yi magana da ita!" "Shi kenan!" Yana fita na kira ta muka gaisa. "Hajiya dama na turo Alfah da Atm kayan auren Tafida da namu na fadar kishiya, Hajiya ki yi duk abin da ya dace mu fita kunyarshi don Allah!" "In sha Allah zan baki mamaki!" Muka yiwu juna godiya domin matar nan tayi min halacci a zamana da Tafida. Kallon Hajiya nayi da ta dawo parlour tana dauke da Mufid. "Hajiya walaha kika yi?" "Eh" ta fada tana shafa addu'a. "Zan tafi na kwanta, Mufid ba zaka raka ni ba?" Kwanciya yayi a kirjin Hajiya!" Nayi fitatta kuwa nayi ban tsaya ba, ina shiga bangarena nima walahan nayi da na tuna abin da ya hada ni da Asiyah nayi ta addu'a da niman kariyar Allah da shi kanshi mijina.. da rana a bangaren Hajiya na ci abincin rana, na yamma na zo na mishi tuwon semo,miyar kuka da yaji kayan kamshi da dakakken nama. Na gyara jikina, sannan na zauna jiranshi. Yau da ya dawo babu matsala, sai dai kamar aiki yaƙe sosai da yayi wanka ya ci abinci ya kama aiki. Da na koma daki shafa'i da wutiri nayi, na jima ina addu'a don na gano a cikin gidan nice koma baya akan ibada, lokacin da na idar ban kara fitowa parlour ba, barcina nayi jin shiru-shiru yasa shi zuwa dakin ya samu, ina barci, bai tashe ni ba ya gyara min kwanciyata bayan ya dauke ni daga kasa. Na cigaba da barci, wurin karfe biyu ya kira Deen suka yi ta waya, yana gaya mishi kome kafin ya gaya mishi yana hanya. Deen yaji dadi. Kashe laptop din yayi ya wuce daki da shi, sannan ina kwance ya zo ya kwanta ta bayana, muka cigaba da barci sai bayan sallah asuba, muka turmushe juna, kasancewar yau din Juma'a ya ce min. "Bayan sallah juma'a zan turo a kai ki airport " "tow!" Yau bakiɗaya a bangaren Hajiya muka karya, inda tayi masa da miyar kayan ciki. Muka karyawa sai ga Abubakar da Umar, suka zo nan aka hadu aka karya. Sannan ya gaya musu tafiyarshi fatan Alkhairi suka mishi. Sannan suka gyara zama suna faɗin. "Aliyu dalilin zuwanmu akan Maryam da Rukayya ne, sun ce zasu hada kayan aure amma kaki basu? Sun gayawa Alhaji ya musu ba dad'i wai ka bawa Ummu sannan ka biyawa mahaifiyarta U...." "Bana!" Hajiya ta katse shi, idanunta a kaina da jikina yake rawa. Tashi yayi a inda yake zauna ya zo ya zauna a kusa dani tare da rike hannuna. "Duk hukuncin da na yanke ban tab'a jin nayi kuskure ba, ko soke tafiyarsu Inna aikin hajji akwai dalili, kuma Abba ya fahimci haka." Shiru yayi kafin ya rike hannuna cikin nashi yana faɗin. "Ba xan iya boye muku ba, ina jin Rukayya da Maryam kamar ba jini daya muka tsaga ba, domin nasan idan da suna da tattali duk abinda nake basu da yanzu sun hidimta min ba tare da na bukaci ko sisi ba, a wannan lokacin bana son have hada hidimar gida da ta mulki, ka gaya musu tsakanina dasu shine abin da bai taka kara ya ka..." rufe mishi baki nayi, "Su din dolenka ne, ni ba dole bace a rayuwarka, sannan bai zama wajibi ka rayu har mutuwa da ni ba, amma su fa?" "Kece dole na idan yau na fadi na mutu daga ke sai Abba zaku iya rike min Yarana babu tsana ko tsangwama amma kowa zai rike min su sai dai don abin da na bar musu sai kuma Deen na san ko bayan raina ne zai rike duk abinda na bar mishi bayan nan bana tunanin wani zai iya min wannan alfarman. Zan iya hakura da kowa na rike ki, me yasa lokacin da nake wulakantaki basu gyara min kuskure na ba? Sai yanzu da na fahimci gaskiya ke din alkhairi ce a gare ni? Ummu ki gane wani abu ba zan kara barin wani ya azabar da rayuwarmu matukar ina Numfashi, sannan ku gaya musu ba zan tab'a basu abin da zasu more ni ba, dan dai sammusu." Mikewa yayi yana faɗin. "Hajiya kiyi hakuri nasan dukkanmu Yaranki ne, amma duk cikinsu babu wanda bai sha nono ya koshi ba, ko shi yasa suke min haka, ni wanda aka watsar da rayuwata a tsakar.." "ya isa haka!" Na fada da karfi ina murmushin bakinciki. "Ya isa haka! Ya isa haka!!" Na rike kirjina da yayi min nauyi, karya da gaskiya, ina ajiye damuwa dayawa a raina domin kuwa zuwa yanzu na kasa sakewa na bar zuciyata ta huta. "Ummu!" D'ago kai nayi ina kallonshi. "Baka gane kuskuren da kake yi ba ne? Da nasan da wannan rigimar ba zan bada hada kayan ba, yanzu ma bata b'aci ba, Hajiya zan tura su amshi hada kayan." Nasan ita uwa ce sannan tana kokarin danne kaunar Yaranta, don ta kyautatta min ne, amma har a kasar ranta tana jin babu dad'i. Mikewa nayi zan fita ya riko ni. "Waye kika bawa aikin hada kayan?" "Hajiya Kaltuma!" "Shi kenan! Muje ki kwanta kafin nazo mu tafi!" Yadda Hajiya bata yi magana ba, ya kara saka min shakka akanta, don rauni irin na uwa dole zata so Yaranta su hade kai kome zasu yi daga cikinsu zasu gama kome. Tunda muka isa na zauna akan kujeran parlour na cusa kaina a tsakanin cinyoyina, kuka nake son nayi amma na kasa, haka nayi ta jin zafi a raina. Bai fita ba sai da ya ga na kwanta sannan ya fita. Nasan dan Adam ajizi ne, a bangaren Tafida kuwa kiran Hajiya Kaltuma yayi ya ce mata ya kara turo wasu kudin ta cire ta bawa Alhaji Maryam zata zo ta amsa. Bayan fitarshi wurin karfe sha biyu nayi wanka na shirya ina jin hayaniya da kukan Yaran, na kasa nutsuwa ihun Mufidah da kukan Mufid yana tab'a min zuciyata kamar zan mutu, saboda ban tab'a jin kukansu har haka ba. Tashi nayi naji mamakin yadda aka yi Tafida yake gidan nan domin na hango shi rungume da Yaran a kafadarshi. Idanunshi jajjur. Bude musu kofar nayi tare da kallonshi. "Kina jin kukansu baki fita ba? Why Ummu? Why??" Ya fada da karfi, "Kayi hakuri!" Mika min Mufidah yayi yana faɗin. "Duba su!" Yatsan Mufidah ne yayi ha, abin ka da farar fata, shi kuwa Mufid kamar faduwa yayi, muna tsaye Hajiya ta shigo a rikice. "Babangida!" "Hajiya ki je kawai! Nayi laifi sosai da na barsu a wurinki, da a wurin mahaifiyarsu suke, yar gurin Maryam bata isa ta cizan min Yarinya ba, sannan ta janyo min da daga kujera, kina ji kina gani yadda suka ce wasa ne kika dauka wasa ne ko ba kome ai kin turo Nana Asma'u ta kira Uwarsu? Hajiya na gane cewa ni ne kawai baku kauna akan sauran Yaranki ai baki shiru ni da kika watsar a tsakar!" "Me yasa baka jin magana Daadi?" "Dole nayi magana? Dole nayi magana kin isa ki hana ni magana ne? Ke ɗin wacece ? Da har xan yi magana da Uwata ki shiga tsakaninmu! Idan ina magana kika kara saka min baki sai na baki mamaki." Ya wuce a wurin ya barmu tsaye. "Ummu!" "Hajiya ba kome ya wuce!" Na fada mata, ina kara jin ba dad'i, nasan babu asirin da za a mata makirci ne kawai, da kuma son kai irin namu na iyaye wanda wasu daga cikin Yaransu suke juya musu lissafi kuma al'amarin ya tafi dai-dai. Daukar Mufid nayi na kai dakina sannan na wuce na kai Mufidah,na gyara kwanciyarsu. Wannan abin da ya faru na yarda Aliyun da na sani ya dawo, kamar mutum me barci ne,.kuma idan aka tashe ni zai zama tarnaki akan kowa,haka ya kasance da Tafida. Tafiyar da zamu yi karshe shi daya yayi tafiyarshi. Ban wani damu kaina ba, domin na ga kamar Maryam ta dawo gidan da zama ne ko sammako take yi, ni dai na rufawa kaina asiri na rungume Yarana, sannan ya rantse min matukar aka kuma ta sanadin kai su ɓangaren hajiya wallahi sai ya bani mamaki, har kiran Abba yayi ya gaya mishi. Hakuri ya bashi ni dai na zubawa Tafida idanun ba zan yarda muyi fada ba. ** 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 ** Bayan tafiyarshi, an yi ta rigima a cikin gidan, domin su bani haushi a gidan a parlourn Hajiya suke kawo kayan da suka hada na Asiyah da Sa'adiyya. Bai dame ni ba kayana da Hajiya Kaltuma take hada min tana kirana ta gaya min abin da ta saka da kuma yadda kome yake tafiya a hankali, babu amfanin gaggawa. Bayan mun gama waya da ita naji ana buga kofar gidan. "Idan gari ya waye ki je ki gaida ita, idan kika gama abinci ki kai mata, kada wani shege ya buga miki kofa ki bude domin na saka matori yayi gadin kofar, kada ki bude matukar ba Hajiya ba ce." Maganarshi ya dawo min, "waye?" Na fada a hankali. "Ummu Hadiyya!" Jin muryan Mamana yasa na fasa ihu na bude kofar ina murna. "sannunku da zuwa!" Na ga Hajiya a bayanta. Shigowa suka yi ba shiga kawo musu abincin, dake bangarena nake. "Sannunku Mama! D'annaku Hajiya Uwani zaki kwana min biyu?" "Allah ya rufa min asiri,bar ni na koma gidan Mamana!" Ta fada tana kallon Mama. Kitchen na koma na dauko musu kullum jollop din shinkafa da wake da nayi wnada yaji kifi sosai, na kaiwa Hajiya Hajiya koda yake ban shiga ba Humairah na bawa na juya abuna don naga parlourn da mata har da Maman Ilham, yanzu itama ta sauya min. Ban shiga ba na juya abuna. "Ummu!" Na'am Mama!" "Ina Yaran suke?" "Suna barci!" "Me yasa kika daina kaiwa Hajiya Aisha su?" "Mama ba laifina ba ne, shi yace idan na kai mata Yaranshi zai min ba daidai ba " "kin manta ita mahaifiyarshi ce?" "Mama a cire maganar Mahaifiyarsa ce ayi maganar gaskiya me yasa Tafida ya ce kada ta bari a kai Yaran can? Na farko a lissafina akwai abin da suka yiwa Yaran kuma basu dauki laifinsu ba, na biyu ana amfani da Yaran a cusawa Aunty Baby b'acin rai domin kowa yasan yadda zuciyar Uwa yake akan Yaranta, na uku ita Hajiya me yasa bata samu shi Tafida tayi magana da shi ba ta kira ki, kiyiwa Aunty Baby magana, kada ki manta a Musulunce Aunty Baby ta hada gaskiya, ba xai yiwu ta lalata aurenta don gyara kuskuren da wani ya aikata ba, ni fa ba zan yarda da wannan abin ba domin kuwa Allah kadai yasan meke faruwa." Inji Uwani, shiru Hajiya tayi kafin ta sauke ajiyar zuciya, ta fara kame-kame. "Wato Hajiya dan yau ka haife shi baka haifi halinsa ba ne, ni bana son naga ana cutar da Ummu, kuma nasan tana kokari akan hadin kan iyalina, tow ya xan yi? Sun ce na fifita Tafida da Matarshi don ya zama gwamna, sun ce na fi son Yayanshi don Ubansu gwamna ne, wallahi." Sake baki Mama tayi ni kan abincin na diba na koma gefe na fara ci a hankali. "Hajiya Aisha!" "Na'am Maman Ummu!" "Ina ga Ummu tayi kuskure shigowa rayuwar Tafida ko? Tunda yan uwansa basu bukatarta da Yaranta idan Aliyu ya dawo ki ce mishi don Allah ya sako min ita kada ya sake na zo da sunan na zo amsar Ummu!" "Maman Ummu mai yayi zafi suna son juna fa!" " Da bata hadu da shi ba ai tayi hakuri yanzu idan babu shi ma zata yi hakuri Ummu ta koma gida sai ta haihu zan san abin yi tashi Ummu!" Ta daka min tsawa. "Mama ki kira Tafida tukun;" wani irin kallo tayi min, "kina tsammanin kiran waya daya zai saka na sauya ne? Idan har akan idanun Mahaifiyarsa aka cutar mishi da Yaranshi gaya min waye zai baki kariya babu Tafida babu ni sai Allah!" "Mama!" Nuna min yatsa tayi, tare da bani umarnin na hada kayana, kiran Mudan tayi ta ce ya dawo. "Maman Ummu ke da na zata zaki gyara kome, kuma shine zaki lalata kome! A matsayinki na Uwa bai dace kiyi haka ba!" "Hajiya Aisha, bani bace da matsala kece me matsala, Yaranki sun zama sune a gaba kina bin bayansu, duk cikin Yarana babu wnada bana so, amma ki sani ba zan iya gani Yaranki su illata min yarinya ba, lokacin da aka yiwa Yaranshi kin nuna rashin jin dadin abin da suka yi? Amma kina cewa wai ba a kyauta ba." Kayana Uwani ta taya ni muka hada, sannan muka bar gidan, ashe burinsu Rukayya idan Mama ta tafi su kamani su min shegen duka sai aka yi dace Ubangiji ya sakawa Mama shakku akan abin da Hajiya tayi ta dauke ni, a ranar ta cewa Mudan. "Ka wuce da ita gidan Ubanta, idan har Aliyu ya shirya zama da Ummu zai saita gidansu, idan bai shirya ba a bar min y'ata ina sonta a haka! Wayarki ban ce ki kashe ba!" "Mama na fita ba da izininsa ba fa!" Na fada kamar xan yi kuka. "Jikina ne ya bani wani abu zai faru, ki tafi idan yana sonki zai zo zai kuma nime ki!" Haka na bar garin Maiduguri na tafi biu, lokacin da za ayi ta'addancinsu, sun aiki Matori, sai Malam Habu me yiwa flowers din gidan ban ruwa, ya hango su dauke da bulala zasu shiga part dina, ita Hajiya ta can dakinta abin duniya ya dame ta(wasu zasu mamaki kada kuyi mamaki abun ko sai godiya yadda wasu suke rasin mutunci kamar ba za a mutu ba!) Shi ya kira Matori da sauri a waya yana zuwa ya ga suna ta dukan kofar, sannan shi kanshi matori bai san Ummu bata gidan ba, don har cikin gidan Mudan ya shigo ya dauke su, haka yasa shi kiran Number Tafida da yake tambayarshi lafiyan Ummu da su Hajiya, kira daya yayi, Tafida ya kashe sannan ya kira. "Oga gasu yan uwanka can, da abun duka zasu daki Hajiya Karama!" Wani irin ashar ya lailayo ya maka mishi uban waye ya ce ya bar wurin , kashe wayar yayi ya kira Abba. Yana tsaka da cin abinci Aliyu ya dauke mishi dadin abincinsa. "Abba ka ga Yaranka zasu kashe min matata da cikin wata uku! Abba wallahi idan na dawo sai na kame yan iska na zuba su a gidan Yari! Abba Matata da Yarana suna cikin hatsari idan wani abu ya same su wallahi ba zan yarda ba!" Kashe wayar Abba yayi ya dafe goshinsa. *Aliyun dai Aliyu ne! Ba zai tab'a bari a tab'a mishi matarsa ba! Alhaji na maka misali da zaki a dawa! Ka tab'a ji namun dawa sun tab'a iyalin zaki? Idan har haka ne shi yake farauta ya kawowa iyalinsa ya koya musu kare kansu, ko mutuwa anyi zaka tuna da kalmaina duk inda yake zai tsaka akan iyalinsa! Wannan wata kyautace da Allah ya bashi, lokacin da bai zaci haka daga Allah ba, ba zai tab'a barin a nuna ta da yatsa ba.* bai gama tunani ba Tafida ya kara kiranshi. "Aliyu! Ka kwantar da hankalinka, bari na kira Alfah muje mu daukota!" Shine ya kashe wayarshi, ya fita yana kiran Hajiya Salamatu ina Yaranta, "Sharif ne yana ciki!" "Ce mishi ya fito ya kai ni gidan Tafida, su Maryam dauke da makamai zasu daki Matarshi!" "Ina Hajiya Aisha take da wannan abin zai faru?" Inji Hajiya Kaltuma, "ina na sani!" Sharif da yaji haka bai tsaya wani abu ba, ya fito suka tafi a hanya ya kira Alfah yana gaya mishi ya same shi a can gidan Tafida. Kusan a tare suka isa. Sun samu Rukayya tana buga kofar gidan, sun fasa glass din window. Waya Abba yayi ya kira Kwamishinan yan sanda. Suna zuwa ya ce masu. "Yan ta'adda ne sun zo zasu kashe Matar gidan...... 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 50 Abin mamaki Abba yasa aka kama su bakiɗaya, har da surakanshi biyu da Yaranshi mata biyu su hudu kenan, kawai saboda kishi da hassada lallai sai sun ga bayan Matar danshi da ciki. Laifi na farko laifi na biyu wasu yan ta'adda mata biyu sun yi ƙoƙarin kashe matar gwamna da Yaranta, laifi na uku shine shigowa gidan gwamnar jahar Borno ba bisa ka'ida ba dauke da makamai tsirara. Wannan abin ya girgiza kowa sannan shi da kanshi Abba yayi ta karanto shashin dokokin kasar nan akan abin da suka aikata. Da hukuncinsu, Hajiya da take tsaye ta kasa magana sai share kwalla take ta rasa yadda zata yi da yaran nan nata mata, sam babu tausayi da imani a ranta. Batun gaskiya ta kira Maman Ummu ne domin ta bawa Ummu Hadiyya hakuri, tana barinta ganin Yan jikokinta don Allah ya daura mata kaunar Yaran sai take ganin soyayyar da bata yiwa Aliyu ba ne takewa Yaran, sati daya da ya wuce Maryam tayi ta kiranta akan lallai ta saka baki Aliyu ya basu hada kayan auren amma ta gaya musu ya bawa Ummu don lokacin Allah ya gani bata kawo a ranta zai bawa Ummun ba, sannan koda ya bawa Ummu har Fanna tayi magana taji a ranta haka ma ba laifi, sai dai yadda ta ji Ummu ta bawa Hajiya Kaltuma hada kayan ya sosa mata rai, duk da Ummu tana bakin kokarinta wurin hada kan Yaranta sai gashi taji b'acin rai ita Yaranta basu mori tafida ba, ta dauka ta bawa Hajiya Kaltuma, shi yasa taki magana ko da Tafida ya ce su je su amsa, wannan abin ya kara b'ata musu rai amma suka share, gashi nan an basu kudin amma burinsu shine su san nawa aka bawa Ummu sannan me ake haɗawa Ummu. Ranar Samha kanwar Sa'adiyya ta je amsar abu a wurin Nabilah, take jin Hajiya Kaltuma tana waya da Ummu da irin abin da ta saya, gasu nan a daki, dake yarinyar ta kware a gulma ta nufi wurin Hajiya Shuwa ta gaya mata ita kuma ta kira Saadiyyah ta tambaye ta, Saadiya babu lissafi tayi ta dokawa Tafida kira amma yaki ɗauka ta tura mishi rashin kunyar da ta saba mishi, bai kulata ba haka yasa ta kira Rukayya ta wanke ta tas ta kuma ce mata tasan adadin kudin da ya tura wallahi suka makale mata kudinta sai sun gamu da ita, haka yasa duk suka sha jinin jikinsu. Jin labarin kayan Ummu suka yanke hukuncin a gidan Hajiya za a hada kayan, tunda sun mata alkawarin ba zasu kara batawa Aliyu rai ba, zasu kaunace shi kamar kullum, shine zuwansu na farko yar gidan Rukayya ta janyo Mufidah ta fado a kujeran Hajiya tana sallah, Fanna ta zo ta dauke tana Amir dan Rukayya yana faɗin. "Afnan ce ta janyo ta fadi!" Haka bai gama rufe baki ba Mufid da yake wasan shi ta gantsara mishi cizo, lokacin Maryam ta shigo parlour kenan daga kitchen, ta ga Fanna tana buge ma Afnan, "Fanna ya haka da zafi?" "Cizon Mufid tai bayan ta janyo Mufidah daga kujera!" Daidai Hajiya ta fito daga dakin kenan, "Mu gani!" Inji Maryam tana gani ta kyalkyale da dariya tana faɗin, ana koya mata jarunta ne, shi kuma an nuna mishi shi namiji ne ai Yara ne!" Ai kuwa Fanna ta hau bala'i tana masifa ta ce. "Wannan shine karo na biyu da kuka yi haka, duk lokacin da kika zo sai wani abu ya sami Yaran!" Tana fada tana jijiga Mufid, "To ai yara ne ni ban ga abin tashin hankali ba, da ake ta wani cece kuce." Shi kuma Tafida yazo ne domin maganar tafiyar shi da Ummu tow ya bawa Hajiya ajiyar wasu takardun Deen, yana zuwa bakin kofar yaji abin da suke fada karshe ma suka maida Fanna mahaukaciya Har Rukayya tana zungure goshin Mufidah da c. "Uwarsu ta maida mana Uwa Nanny, Yan banza masu idanu irin na zuriar da suka hada iri da arna, bar kallona don Uwarka!" "Wai me yasa kike haka ne, a madadin ku rarrashi yaran sai ku zauna kuna irin haka." "Hajiya ke kika mana alƙawarin babu bambanci tsakaninmu da Tafida, mu kuma zamu zauna da shi lafiya don Allah kada ki ce kome, idan kika yi magana zamu dauka goyan bayan Tafida kike, yara kuma sun yi laifi dole a hukunt..." turo kofar yayi a tunaninsu Ummu ce har rukayya tana faɗin. "Ku ji yar iska ta ji kukan Yaranta ita me yara wato zata nuna mana ita uwa.." maganar ce ta makale ganin Tafida ne a tsaye da sauri Hajiya ta nufi Fanna zata dauki Mufidah. "A'a Hajiya! Kada ki tab'a min Yarana, ba sai kin nuna min kin fi son su da ni ba. Idan na kintatta daidai tow kina tare da ni ne don daukakar da na samu amma bayan nan babu ruwanki da rayuwata, kaf duniya mutane uku suke sona a yadda nake bayansu babu kaso daya na soyayya ta a idanunki, amma Abba, Ummu, Deen, sune kaɗai mutanen da nasan suna kaunata ba tare da abin da nake tare da shi ba, kina tare da ni ne Hajiya domin darajarki amma Yaranki sune a gabanki, amma ni bana gabanki domin kuwa na gani a idanuna na kuma.." "Tafida baka san wasa ba ne? Yaran nan wasa suke da junansu " yadda ya zabura yasa Hajiya ta shiga tsakaninsu. "Da kin sake na tako inda kike sai na zubar miki da haƙora bar ganin kin girme ni sai na zane ki wallahi." Yadda yake shiga banan yake fita ba, sannan ya ce su fita mishi a gida ko ya basu mamaki. Duk da haka Hajiya bata wani nuna damuwarta ba, sai da ta ga ya tafi kuma ya hana Ummu kawo mata Yaran, ga Maryam da suka yi rigima da mijinta da kannen mijin, Uwar mijin ta goya musu baya da cewa bata isa ta raba mata kayan Yara ba, idan ita Uwarta ta kasa hada kansu taci karya bata isa ba, don suna hakuri da ita da mugun halinta waye zai iya zama da ita da wannan halinta, wannan abin ya bawa Maryam haushi ai kuwa tayi tsalle ita Yayar gwamna Tafida za a ci mutuncina, ta bar mata danta idan ta haifi dan halak ya aiko mata da takardanta don tana rufa mishi asiri. Ai kuwa Mijin ya ce bai san wannan zancen ba ba zata ci mutuncin Uwarshi ya kyaleta ba, ya sake ta tare da korata sannan ya kwace yar shi karamar. Ya korota, tunda ta dawo kullum suna kasuwa su hudu, don sun dan sadiya ba mutunci ne da ita ba, kiran Maman Ummu kuwa Hajiya bata son shirin Yaranta akan Ummu ba ita dai don jikokinta tayi kiran amma kuma ta lura Maman Ummu bata da sauki akan lamarinmu, kuma ba don ya tafi da ita ba da haka zasu cutar da Ummu, hawayen da ya zubo mata ta share. "Ina ga ba sai an kai wannan case din ga hukuma ba, matsalar cikin gida ne a magance shi a anan!" Yan sanda suka koma bawa Abba hakuri, a nan kuwa Tafida ya kira ya kai sau goma. Lokacin da suka nace da buga kofar gidan Hajiya ta ce musu. "Uwarta tazo ta dauke ta." Yadda Abba ya fusata yasa ta fadi abinda ya faru, tana tsoron kada ya kore ta a gidan Tafida bayan bata da inda ya fi nan, "ina baki shawara ki bar gidan nan a mutunce idan ba haka ba wata rana abinda kike ganin zaki iya tunkarar shi, shine zai tunkare ki, hankalinku ya kwanta Ummu ta bar dan uwanku, sai ku zuba ruwa ki sha, amma ku sani daga yau na cire ku cikin Yayana!" Ya kalli matar Uwar da Abubakar. "Ku kuma mazajenku zasu san yadda zasu yi da ku!" Daga haka ya juya zai fita, Hajiya ya ce mishi. "Kayi wani abu Ummu ta dawo idan ya dawo bata nan ban san yadda xan fuskance shi ba don Allah!" Murmushi yayi irin na manya ya ce mata. "Tafida kike so ba? Uwarta tayi namijin kokari da ta dauke Yarta kafin a cutar mata da ita, ni abin tambayar anan shin dama kin shiga jikinta ne domin ta janyo miki Tafida a gare ki ne ko? Domin kuwa ban da haka babu yadda za ayi ku hada kai da Yaranki da surakanki zaku kashe yar mutane cikin jikinta da Yaranta. In sha Allah Ummu kuka saka a gaba Allah sai ya saka mata in sha Allah!" Ya fada yana barin gidan. Duk sun ji haushin Abba saboda Ummu zai kai su wurin yan sanda. ** Tafiyar Tafida Sudan, tare da Ammah da Matar Deen sai Jalilah aka yi tafiyar yaso tafiya da Ummu amma ta bata mishi rai, akan me zata saka baki idan yana magana ta bala'in rena shi. Haka yasa ko ta tafi da ita, zai ta jin zafinta ne sai dai tun da ya bar gida ya rasa nutsuwarsa. Kuma ya kasa sake jiki su tattauna da Deen, ya gane halin da Tafida yake ciki, karshe sai ya rasa yadda zai mishi bayani akan Mahmoud, ya bar zancen tare da ganin wata rana zai gaya mishi. Sannan ya gayawa Tafida kudirinsa don yasan matukar yana tare da Tafida Mahmoud zai ta bibiyarshi. Haka suka ta shige da fice har Deen ya samu aikin koyarwa a kasar. Deen bai tab'a boyewa Tafida abu ba, sai wannan karon sai dai ya mishi hannunka mai sanda ya ce mishi. "Kada ka bari kowa yasan Ummu ce rauninka domin akwai masu jiran haka su yi amfani da rauninka! Sannan bana nan ka saka idanun akan dukiyar al'umma da ka dankawa Mahmoud. Kada ka sake ko da wasa ka barwa Mahmoud Ummu, ka saka idanu akan gidanka Ummu tana buƙatarka kuma tana buƙatar kulawarka, Tafida ka saka idanun akan Ummu don gaskiya wannan karon idan ka bata rawanka da tsalle ba zan iya saka baki ba." "Tow ya zanyi?" "Ya zaka yi? Dole kowa ya bar maka gidanka Hajiya kuwa kayi hakuri da ita ba kai kaɗai ta haifa ba dole zaka na ganin irin wannan lamarin, musamman da su Rukayya basu da lissafi!" Kamar zai fashe da kuka haka yake kallon Deen, ajiyar zuciya ya sauke yana jin kamar ya fasa ihu, haka suka rabu satin shi daya ya kira Number Ummu ya kai sau nawa kullum bata dauka, asalima sai yake ji kamar bata raye ne an boye shi, babu shiri ya bar sudan, ranar da ya dawo kai tsaye gida ya ya ce. Yana shiga ya ga window bangarenta a fashe, jikinshi ne ya fara bashi da matsala a hankali ya isa bangaren ya tab'a kofar yaji a rufe, "Aunty Baby!" Ya kira ta kamar yadda kowa ke kiranta, yaji shiru juyawa yayi yaga Rukayya ta fito hannunta ɗauke da manyan jakanka leda, hadiye yawu yayi ya kalleta daga sama har kasa. "Meye ya kawo ki gidana?" "Hajiya nazo dubawa bata da lafiya!" A hankali ya nufi bangaren Hajiya, ita kan da gudu ta bar gidan bayan ta kwashi kayan abinci da wasu kayan auren da suke hadawa. Yana shiga babu kowa a parlour. Ya nufi dakin Hajiya tun a bakin kofar dakin yaji muryan Fanna tana kuka. "Eh Allah bai bani haihuwa ba, kuma bawai baya sona ba ne, ya daura min ƙaddaran aure ke da yake sonki ai kin kasa zama a gidanki, sannan kin hana matar zama a gidan kin ga ashe bani da laifi, kuma da kike cewa kwadayi ya kawo ni, na fi karfin kwadayi gidan Tafida, zan bar muku gidan ku ci yadda ranku yake so hakkin Ummu sai ya tambaye ku!" Ta fada tare da bude kofar zata fita tana kuka, Hajiya tana ganin abin da suke amma ta kasa magana, kwana biyu nan da suke gidan abincinta da take ciki saboda diabetes dinta, Maryam ta hana sai dai ayi daya wai ai tuna tana shan magani zata iya cin kome. Daurewa take amma sugarta kasa yake a madadin yayi sama, "Maryam! Kada ku kore min Fanna ita take taimaka min da wasu abubuwan, Ummu bata nan balle naji sauki a gare ta. Idan kuma kuna son na mutu ne tow shi kenan!" "Hajiya ba fa abin da zai same ki domin Ummu asiri tayi miki, kuma ba zan yi kaffara ba tayi haka ne don rabamu da ke da Tafida." Bata yi magana ba, kallon juna Fanna da Tafida suka yi ya juya abinsa yana jin kamar yayi kuskure na yarda da Hajiya zata dawo gare shi. Lokacin da suka fito waje ya ce mata. "Ina Ummu?" Sunkuyar da kai Fanna tayi tana share kwalla da yake zuba mata. "Ina Ummuna?" "Ummu ta tafi mahaifiyarta ta tafi da ita!" Lumshe idanun yayi yana faɗin. "Na gode Fanna! Yanzu ki tafi gidan Abba ki zauna a can kafin ta dawo domin dawainiyyar zai mata yawa " "Na gode amma gaskiya ban da kai da yau na koma gida na gaji da halin Maryam Hajiya bata iya magana, sannan bata da lafiya. Gashi ba a gama abinci akan lokaci ga ciwonta yana kokarin tashi, don Allah ka kula da ita." " shi kenan!" Haka ya saka aka kai Fanna gidan Abba, bangaren shi ya nufa yayi kura alamar Ummu bata nan kenan, hadiye b'acin rai yayi ya shiga dakinshi ya ga zauna shiru, ya rasa me zai yi a hankali yake sauke ajiyar zuciya, bakiɗaya kome ya tsaya mishi ya fahimci yanzu Ummu gata ce a rayuwarshi sannan rashinta kamar asara ce a tare da shi. Haka yasa yayi ta nazari, ban daki ya shiga yayi wanka da alola sannan ya dawo , daki ya dauki kayanshi ya saka, kafin ya drower din da ya ajiye mata kuɗi ko tana da bukata, ya samu bata tab'a kome ba, dakinta ya nufa ta rubuta mishi sako ta ajiye a saman mirror. _Ina son zama da kai amma igiyar ƙaddara tana ta walagigi damu! Ina son zama da kai ina son kasancewa da kai! Amma danginka sune rike da makomar aurenmu! Kayi wani abu kafin dangina su fusata don Allah_ *~MatarAliyu~* Rike takardan yayi kamar hannun Ummu yake rike da ita, haka yasa yaji hankalinsa yayi bala'in tashi. ** *Ummu* Har ga Allah na saka rai Tafida zai zo gare ni, haka yasa koda muka sauka a dakin Mamawo, ban yarda da na sake jikina da gidan ba, don gani nake Tafida zai iya zuwa a kwana na daya amma ina sai gashi yau ina kwana na hudu, duk da kome aka min, sannan Yarana takas Babana ya ɗaukar min me kula da su wata babbar mace ce, bata tab'a haihuwa ba tana da kirki. Ni kuma aka bar ni da laulayin da na fara, me matukar wahala. Kana ganina kasan na ƙaramin wahala nake sha ba, har gida Baba ya kira Sagir shi yake zuwa ya duba ni, ranar da na cika kwana biyar na kalle shi. "Bro baka ji labarin ya dawo ba ne?" Kura min idanun yayi, "Ummu ya dawo jiya!" "Me yasa yaki zuwa duba ni? Ko ya daina sona ne?" "Me yasa kike fadar haka?" Ya jefa min tambayar da ya sani naji kamar zan yi kuka. "Nasan idan har ya dawo ya ga bana nan zai ta kira na, ni ban ma san inda na ajiye waya ta ba." Wani irin tausayi ne ya rufe shi . "Ummu Mijinki yana sonki kuma zai dawo gare ki!" "Ina jin tsoron kada ya rabu da ni ne, ina jin tsoro kada yace ba zai zauna da ni ba ne, Yaran mu uku da shi. Idan na bar mishi yaran zai kula da su amma bai da lokacin zaman gida. Bakiɗaya lokacinsa na al'umma ce " murmushi yayi yana faɗin. "idan na gaya miki gaskiya zaki yarda?" Gyada kai nayi ya sakar min murmushi yana faɗin. "yana sonki kuma yana can yana niman kwarin gwiwa da zai nime ki, Ummu Hadiyya baki cikin matan da mazansu zasu daina so domin kina da kyau da hali me sanyi wanda duk wanda ya zauna dake zai fahimci haka!" "Na gode sosai!" Gyada kai nayi ina faɗin. "me yasa danginsa basu sona?" Murmushi yayi yana faɗin. "Ra'ayinsu ne su so ki ko su ki. Sannan wayarki tana hannun Babanmu, idan kika kwantar da hankalinki zai baki!" Godiya nayi masa sannan ya fita, ina zaune a wurin cikin damuwa. ** Tafida bai ce musu cikanku ba, yana dawowa ya fuskanci aikinsa, yadda zaka san yana cike da b'acin rai, mutumin nan da kanshi yake bin aikin da yabawa yan kwangila, yana dubawa. Sannan ya saka aka kawo mishi wata motar da haɗaka mata karfe a gabanta, idan ya bada aikin gini, zuwa yake da motar ya daki ginin yana zubewa zai saka dan kwangila sai ya biya kudin da ya bada sannan ya cigaba da aiki. Wasa wasa Tafida ya tashi hankalin ma'aikata, domin sai baku tsammanin zuwan shi ba sai a ganshi, an dakatar da ma'aikata dayawa, ya kuma kori wasu musamman idan ya fahimci yadda kake aikinka. Sai gashi kowa ya shiga hankalinsa, a wannan lokacin hadda Mahmoud sai da Tafida ya zabga mishi mari a gaban jama'a, sakamakon kama shi da yayi yana lalata da wata ma'ikaciya, wacce yar bautar ƙasa ce da ta zo daga Edo, mari uku yayi mishi sai ya ga yadda Mahmoud yake mishi wani irin kallon reni, cikin fusata ya fara ɓalle botirin rigarshi na hannu da cire agogon hannunshi. Yana faɗin "kutumar Uba Ni kakewa wannan kallon?" "Anyi maka lusari kawai kanata hauka a gari, bayan Matarka da kake haukar akanta cin amanarka take da Abokin sirrinka, me zai saka na maka kallon mutumin da zai bani tsoro, idan baka yarda ba ga shi nan!" Ya nufi laptop dinshi ya danna sai ga hoton Ummu tsira... Daukar laptop din Tafida yayi wurgi da shi da ya fashe, cikin bala'in fushi da mugun kishi, Tafida ya rufe shi da mugun duka kamar zai kashe shi, yana hango Ummu ba kaya. Sai da aka janye shi daga jikin Mahmoud don ya kasa ko motsi, sannan ya ce. "Kun gani ne?" "A'a!" Huci yake kafin ya ce musu.." an kawo min report din cin hanci a cikin ma'aikatan nan, ku turawa EFCC." Ya juya yana kallon Mahmoud. "Ka soke ni ta baya, kasan da haka ka cigaba da kallona." Ya kai mishi naushi da kafa. "Deen kashe shi zan yi, itama Ummu Hadiyya na b da Allah." Mahmoud da ya farfaɗo yana dariya ya ce mishi. "Kana sake ta shi zai aureta, waye ya sani ko Yaran da kuke kira naku, na sune su biyun!". Sake kai mishi naushi yayi sai da ya sake suma. Kwashe kayanshi yayi ya bar office din. Yana shiga mota ya kifa kanshi yana jin kamar zai mutu. "Kai ni gidan Abba!" Haka suka wuce sauran motar suna bin shi, lokacin da ya isa rikice ya nufi bangaren Abba, ya zauna a gabanshi yana me fashewa da kuka, yana jin kamar zai mutu saboda zafin kishi. "Abba kai ka bani Ummu, Abba na dawo maka da ita, amma ka rubuta ka ajiye idan nayi idanun biyu da Safiyyudeen zan kashi, ita kuwa Ummu Haddiya Muhammad Kabir, na sake ta saki daya na yafe mata abin da tayi min kada ka ce zaka.min dole domin zan iya mutuwa. Zan mutu kada ka min dole!" Ya fada yana kuka. "Abba taya abokaina zasu ci amanata? Me nayiwa Deen zai kebe da matar sunnah ta..." Tass Abba ya wanke shi da mari, ya kara marin shi ya ce mishi. "Saki ya tabbata ka rabu da ita ko?" Murmushi yayi mishi ya dauki wayarshi ya kira number Malam Zailani ya kira ya gaya mishi Aliyu ya sake Ummu, sun jima yana magana. Kafin ya bashi shawara guda daya sannan ya ce mishi. "Aiki yana gabanka, ka ɗauketa tayi nisa da inda yake a yanxu zai kara gane faidarta, ka kyale shi da sauran yanzu zaka gane waye shi da kyau sannan ka gayawa Deen, amma yanzu Mahmoud zai san ya tab'a masu tsada." Kallon Tafida Abba yayi, ya kashe wayar ya kuma kiran Deen ya ce mishi. "Allah ya maka albarka, na gode sosai sai dai Tafida ya sake Ummu, burin danginsa ya cika burin Mahmoud ya cika, sauran bayanin zan turo maka ta email zan maka bayanin sauran aikin da baka rasa min ba!" Sannan ya sakewa Tafida murmushi ya ce mishi. "Sati me zuwa za a daura maka aure da Matan da danginka suke so, sannan Sa'adiyya zata dawo gyara mata bangaren ta, Tafida idan ka sake ka rabu da sauran matanka baka da hujja sai na tsamme hannuna akan. B'ace min jahili, dabba wanda sauran dabbobin suka fishi hankali ina sha Allah Ummu tayi maka nisa, da nasan cewa saboda Mahmoud zaka sake Ummu da na saka an baka guba kaci ka mutu, wanda baya kishin kasa idan Ummu ta ci amanarka kai me rufa mata asiri. Ko don Yaranka!" "Abba ya ce min ba Yarana bane?" Tasss Abba ya kara kifa mishi mari. "Fita min a gida, kafin na fusata na tsine maka, fita kafin na saka maka baki a kanka da rayuwarka!" "Abba me kake boye min!" "Fita kafin nayi maka maganar da zai dame ka." Fita yayi yana kuka wiwi, ya rasa me ya aikata, bai tab'a zama yana kuka haka ba sai yau da ya sake Ummu. Yana fita Abba ya Baban Ummu, bayan sun gaisa ya ce mishi. "Gobe ina hanya zaka bani y'ata fa!" "Alhaji Muhammad Jadda yarka ce, sagir zai kawo maka ita yana gari." "Na gode zata tafi Sudan ce ta haihu a can!.kayi hakuri Aliyu kasan!" Dariya Baban Ummu yayi yana faɗin. "Allah sarki ai dukkanmu, mun san haka Allah ya bawa zaman lafiya!" Haka suka rabu, bayan sun kashe wayar ya kira Deen ya gaya mish gata nan zuwa idan ya sake ya bari Tafida ya san tana wurinshi zai fusata. Sannan ya kira Malam Zailani da yake aiki kamar ba zai dauki wayar ba ya dauka. "Ina aikin wannan ublishin ne!" "A'a kyale shi, kyale shi Allah yana ganinsa, Ubangiji zai mata sakayya kada ka damu lokaci na zuwa, mu barshi da Allah, Malam kai kake gaya min haka yau kai zaka fusata haka" "Raina ne ya b'aci!" "Ka kyale shi, Allah yasa Yaron bai boye mana kome ba!" Da wannan suka yi sallama ** Ran malam Zailani ya b'aci kwarai ba a tab'a cin mutuncinsa irin wannan ba, tashin wani almajiransa yayi ya dauko kayan aikinsa bai cika aiki irin haka ba, sai idan an yi abin da ya fusata shi. Yau saboda Tafida da Ummu zai yi shi. Wata allon azurfa ce, ya fara rubutun yasin yana yi yana tari, yau Mahmoud ya takalo bala'i." Suna gama waya da Alhaji hawaye ya zuba mishi, haka yayi ta zubar da Hawaye ya kara kiran Abba ya ce mishi. "Kada ka amshi sakin ka ɗauketa kafin labarin yaje kunnenta." *** Zazzaɓi ne ya rufe ni, kamar zan suma duk da na sha magani, ina kwance Babana ya shigo ya ce na shirya na tafi da sagir. Haka na shirya muka bar gidan, ina jin kewar Mamawo, muna isa airport ya kai ni, a daren muka wuce Kano, daga can aka wuce da Ni khatum na sudan, da asuba muka isa Deen ne ya zo daukata, yana me ɗaukar Mufidah, yana kauda kanshi hawaye na zuba mishi, "kuka kake Yayana? Tafida ya juya min ko saboda danginsa ko?" Sai ya rasa bakin da zai min magana, taya zai gaya Ummu an sake ta. A can Maiduguri labarin ya karad'e ko ina, da har ya fado gidan Mama da safe tana aiki Ummu ta shiga tana murmushi ta ce mata. "Hadiza hala baki ji labarin, abin da ya faru ba Mijin Ummu ya kamata da laifin cin amanarshi!" Sake abin hannunta tayi tare da riƙe kirjinta.... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* ---------------------- 51 Kamar wacce aka farka da ita, Uwani ta fito waje da gudu tana faɗin. "Karya ne wallahi, karya ne Umma karya ne Ummu ba gaba da gaba ba ko ta baya sai an shirya. Mu Yaran rikon Mama bamu lalace ba sai yar cikin Mama, haba Hajiya Umma ba dai Ummu, ko a yan matancinta ba a kamata da waya tanayi da saurayi ba, balle ace alalace yau aureta!" Ta juya tana kallon Mama ta sake murmushi. "Kina nufin zata iya watsar da tarbiyyar da kika bamu ne? Idan kina tunanin haka tow wallahi ki ajiye domin kuwa akwai masu son ganin tashin hankalinki gara ki nuna musu muhimmancin Ummu akan kowa, idan ma abin kunya ce ai ba kanta farau ba balle nayi imani da Allah ba halinta ba ne." "Allah ya miki albarka Aishatu na, Hajiya Karima je ki, Allah ya shirya mana zuriar na haifa kin haifa, mun haifa ba zan miki wani abu ba, kuma ba zan tab'a miki suna ba, daga nan har karshen duniya kiyita bada labarin Ummu!" Daga haka Mama ta barta baki sake. Uwani ta ce mata, "je ki dadin abin kin haifa wallahi kowa zai ga abin da ya shuka!" Wai naa haka abin Tafida yayi kokarin kashe zancen da anga video dole ya kusan mutuwa, bai kara yarda ya fito ba ya boye kanshi yana jinyar zuciyarshi. Ya rasa inda zai cusa ransa yaji sanyi Deen da ya da ce ya nima ya kasa nimanshi tow me zai ce mishi? Haka yasa ya turawa Deputy kome ya cigaba da gudanar da kome. Sannan ya wuce wurin Tinah a Abuja, kwanansa uku bayan hmm balle uhmm, abin duk ya dame ta. "Aliyu ka saka ni a duhu meke faruwa ne?" D'ago manyan idanunshi yayi yana kallonta kafin ya ce mata. "Na saki Ummu!" Wato da ta yanko wani gundumemmen turanci me sirke da yarbanci ta lailaya mishi da Ash'aria da ko a Dictionary babu shi ta yanka mishi mai nauyi da tsada. Ta ce mishi, "ka iya rabuwa da Ummu waye zai zauna da kai baka rabu dashi ba. Mutumin banza." Kai Tafida yaji zagi har dodo sai da aka kira shi, shi yanzu da take zaginshi sai yake ganin kamar tana rage mishi dawainiyyar da yake kanshi ne bakiɗaya, tayi mishi zagin tsamar nama, sannan ta koma tana me fashewa da kuka. "Tunda ka iya haka babu amfanin zama da kai!" Ta tattara ta bar masaukin da yake. Tun da yayi kuka a wancan lokacin, bai sake kuka ba sai dai kukan zuciya, ana cewa maza basu kuka tafida yayi fa, shar-shar haka yayi. *** Abba Da kanshi ya je biu ya zauna ya warwarewa Alhaji Kabir biu abin da yake faruwa, Murmushi Baban Ummu yayi ya ce mishi. "Yanzu tunda ya sake ta, xan tura Uwarta ta kwaso kayanta don Allah ka saka a dawo da ita!" "Alhaji ka yi hakuri ta haihu lamarin yana bukatar shiru da rashin ganin Ummu da zaa yi zai saka mutane su bar zancen!" "Na sani ita bata san da haka ba ne?" "Bata sani ba!" Tsakanin da da mahaifi sai Allah, Baban Ummu yaji zafi sosai amma dake yaga dattakun da Abba yayi sai ya ce mishi. "Idan da hali ka saka a dawo da ita gida, ina son ta zauna ne anan idan kome ya wuce ta koma wurin mahaifiyarta." "Tow amma Alhaji Kabir kayi min Alfarma daya tal!" "Ina jinka!" "Don Allah kabar Ummu ta haihu!" Shiru yayi na wani lokaci kafin ya ce amma ya kamata Mahaifiyarta tasan da zancen nan!" "In sha Allah zata sani zanje da kaina ma na bata hakuri na kuma nemi alfarma a wurinta." A bangaren iyaye maza babu matsala. Haka Abba ya bar Biu lafiya lau, ya dawo gida. Washi gari kuwa da sassafe sai ga Maman Ummu a gidan, daga yadda Hajiya Salamatu da Hajiya Kaltuma suka karbe ta, yasa duk zafin kanta ta hakura ta fara da gaisawa kafin ta ce musu. "Ina son ganin Alhaji ne!" "Tow ko zaki isa dakin Inna sai yazo!" "Tow na matsala!" Suka nufi bangaren Inna, suka gaisa a nutse, Inna tayi ta bata hakuri murmushi Mama tayi kawai bata ce kome ba, suka je suka gayawa Abba sai gashi kuwa. A mutunce suka gaisa gami da ganin girman juna. A hankali ya ta fara magana cikin sanyin murya kafin ta d'ago kai ta ce mishi. "A ranar da Hajiya Aisha ta kira ni, naji labarin sun so dukan Ummu ne ko? To kuwa da sun daki bala'i. Ba ma wannan ba, Tafida ya saki Ummu ko?" "Eh!" "Ina shaidar?" "Bai rubuta ba!" Girgixa kai tayi ta ce mishi. "ina Ummu?" "Tana sudan?" "Akan me zata tafi ko bata san ya sake ta bane?" "Eh bata sani ba Hajiya!" "Tow ta dawo!" "Kin san Muslunci ya bata damar tayi idda dakinta, kuma babu idda shine nace ta haihu a can kafin nan abin da yake faruwa yayi sauki!" "Ina son Ummu ta dawo Alhaji nan da kwana biyu, y'ace fa ba baiwa ba. Idan na bari Ummu ta zauna a can kamar bata da galihu ne, ka duba lamarin kowani daya a gaban Iyayenshi yake jin shi mutum idan baya tare dasu gani yake kamar bai cika mutum ba, ka duba lamarin ka dawo min da Y'ata don Allah!" Sunkuyar da kai yayi yana kallon kasa. Mikewa tayi tana faɗin. "Kayi hakuri amma nima ina da hakki akan Y'ata ce, kuma abin da ya hada ya raba don Allah kada mu kai kanmu ga tashin hankali, don Allah ka duba lamarin ina bukatar Ummu da Yaranta Alhaji!" "In sha Allah zata dawo kamar yadda kika bukata!" Tayi musu sallama ta bar gidan, in sha Allah Ummu sai ta yi nasara a rayuwarta, Ummu sai ta zama mace mai daraja a yadda Tafida zai ta bin ta tana ganin bai mata ba. Lokacin da ta koma gida sai da ta rufe dakin tayi kuka me isarta, Burinta Ummu tayi aure nata tab'a hango kalubalen da zata fuskanta a gidan aurenta. Kawai tayi aure ta bar gabanta, tunda Ummu tayi aure bata huta ba. -- Rukayya da Maryam da suka ji labarin, kuwa kamar su zuba ruwa a kasa don murna, shi kenan sun huta da jaraba da nanikewa Ummu da tafida tafi sauran matan, lokacin da Hajiya taji labarin sai da jininta yayi bala'in yayi sama, cikin dare aka wuce da ita asibiti domin a banɗaki suka ganta ta fadi, bakinta ya koma gefe. Gefen jikinta yana son ya shanye. Ga asalin ciwonta ya tashi lokaci guda ciwo ya kwantar sosai, Yaran ne kanta. A lokacin da Alhaji ya zo ya ganta. "Gashi saura kwana uku auren Juma'a za a daura auren Aliyu da Asiyah." Shiru suka yi suna jin haushin Abba da yazo yana maganar wani auren Tafida da wani zance. Daga asibitin gidan Tafida ya nufa ya ga an gama kome, ai don ya cusa mishi bakinciki, ya sake kudi ya bawa Sharif ya ce mishi. "Sharifai don Allah a yi ƙoƙarin karasa kafin Alhamis zasu zo jeren kayan Asiya!" "In sha Allah Abba!" Ya bawa Sharif aikin kafin Alhamis an gama su paint an kawo duk abin da ake bukata an zuba. Sannan aka rufe anyi wannan aikin tsakanin talata da Laraba, a daren yau laraba kuwa sai ga motar kaya yazo aka kawo, gidan hauka irin na masu amfani da shirka har da binne-binne. Har ranar juma'a ana aiki, bangaren Sa'adiyya itama haka aka yi mata jere kawayen Mamanta dasu Maryam, a daren ranar ta riga amarya tarewa inda aka yi ta zage-zage tsakanin Sadiya da yan uwan Asiyah don an daura auren gobe zasu tawo, kafin washi garin nan ayi fada yakai sau goma a gidan. Koda suka iso ma sai da aka so bawa hammata iska, shima sai da aka yi da gaske Maryam da Rukayya sun bar Hajiya a can asibiti da Fanna da bata bar garin ba. Allah ya so Hajiya haka yaranta suka gudu da sunan zasu kai kayan aure. Lokacin da suka kaiwa Sa'adiyya nata da ta gani ai kuwa ta hau musu zagin wulakanci da kiransu barayi sun kwashe kudin sun saya musu kaya kamar na gwanjo. Ashe gara Saadiya nata me sauki ne, domin Asiya tana ganin kayan tayi tsalle tace ba zata karba ba don duk kayan ciki babu zanin dubu dari biyu da hamsin. Balle lace din dubu dari sai na dubu hamsin. Ana cikin wannan gurmin kawai Hajiya Kaltuma ta fito da kayan fadar kishiyar da aka yiwa Ummu, wani irin gud'a aka sake lokacin da aka fara fitar da kayan, Wayyo Allah matar nan ta san kan lakato masifa, ihu Asiyah take tana cewa bata yarda ba kayanta ne aka bawa Ummu, sannan Hajiya Salamatu ta kai kayan cikin dakin Abba ya ajiye sai Ummu ta haihu. ---- *Ummu* Ranar Juma'a muka iso da yamma, amma bamu shigo borno ba sai dare, har cikin gidan Abba ya rako ni, tare da bawa Baba Bulama hakuri da abin da ya faru, lokacin da na isa dakin Mama na zauna nayi zuru-zuru, murmushi tayi tana faɗin. "Me za a kawo miki?" "Tea kawai nake so!" Na fada a sanyaye, haka ta hada min na sha, wani abu da na fahimta yadda take nan-nan da ni na shanye ta ce min. "a kara miki ne?" "Eh!" Haka ta kara min, na sha daga nan na jingina ina gumi. "Shine abincinki?" Gyada mata kai nayi ta sake yar murmushi sannan ta ce min, "ki huta an jima zan yi magana da ke." Kawai sai naji hankalina ya tashi, bayan nayi wanka muka kwanta, ganin yadda barci yai gaba da ni bata kara min magana ba, dai ta bar ni da asuba bayan na tashi sallah asuba, nayi wanka da alola, sannan na gabarta da sallah nafilla kafin nayi sallah asuba, ina zaune a wurin har rana ya fara fitowa tare da ita, mikewa tayi ta sakawa su Zakiya da Uwani hannu. Kafin ta dawo dakin. Zama tayi tana murmushi kafin ta ce min. "Ina son ki gaya min me ya faru tsakaninki da abokan Tafida da har hoton tsiraicinki ya bayyana!" Gabana ne ya fadi dafe kirjina ina jin kamar zuciyata zata faso waje. "Mama!" "Gaya min kome yadda zan iya gano mafita!" Kuka na saka, bata hana ni ba sai ma bani labarin abin da ya faru da hujjar sakina da Tafida yayi, juyi dakin yake min, na fada jikinta ina haki hawayen da nake zuba min ya tsaya cak, a hankali na fara bata Labarin tun daga zuwansu niman, har zuwa aurenmu da irin bakar izayar da na sha a hannunsa, ina bata labarin kome ina kukan zuci, a hankali da nazo kan labarin Mahmoud na fashe da wani irin kuka me cike da hawaye. Na kalleta na ce mata. "Meye laifina don na boye cin zarafina da aka yi? Meye laifina bayan shi ya bawa kowa damar shiga jikinsa............... 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 52 Shafa bayana take tana gaya min kalmai masu dadi da kwantar da hankali, nayi kukan da nasan in sha Allah ba zan kara yi, Tafida ya sake ni saboda rashin mutunci. Tafida ya cire min yarda da tsammanin duk wani d'a namiji, ya samin shakku da tsoron mu'amala dasu, shafa bayana take tana faɗin. "Kiyi hakuri Allah yana tare da masu gaskiya! Allah ba zai kunyata ba, kin rufa musu asiri suka nime tona miki Allah ya rufa miki asiri duniya da lahira, ya kuma miki sutura duniya da lahira." Addu'ar da Mama take min yasa naji kaina kamar an yanke min duk wani bakincikin rayuwa, amma mutuwar aure da ciwo, domin kuwa sai da na kwanta asibiti domin jikina rikicewa yayi, sai da na sha. Bakiɗaya ji yayi ina ma zai iya da ya ajiye mukaminsa ya huta, ya rasa waye zai taya shi jimami. Tsawon kwanakin nan yayi shine cikin tashin hankali, shi yasa ya rufe wayarshi ko taron gwamnoni da za ayi na arewacin Nijeriya bai samu zuwa ba amma yasan mataimakinshi zai je, haka yasa ya cigaba da boya, sai dai wani hali Ummu take ciki? Me yake faruwa dole ya koma gida dole ya je yaji meke faruwa, ɗaya wayar shi ya ciro ya kunna ya ga sakon Deen. _Kana ina ne? Ina ka shiga? Me yasa kayi haka? Me yasa baka tambaye ni me ya faru ba? Aliyu kayi kuskure Ummu bata da nufin cin amanarka, Mahmoud yayi kokarin mata fyade ka kunna wayarka muyi magana_ Jikinshi na rawa ya kira kira Deen, layin bata shiga, gwada kiran layin gida yayi, ai kuwa ya dauka. "Safiyyudeen!" "Na'am Aliyu? Kana ina ne?" "Ina Abuja!" "Ok ka jira nima ina hanyar gidansu Tinah ne amma gani nan zuwa a ina kake nazo?" Nan ya gaya mishi inda yake. Sai da ya isa gidansu Tinah ya daukota suka zo Hotel din da yake, ya tara gashi yayi wani irin muni. Ko inda yake Tinah bata kalla ba, ta zauna a can tana shan ruwan da ta ganina dakin. "Why Tafida?" "Nuna min video yayi ya ce kuna cin amanata kai da Ummu!" Ya fada kanshi s sunkuye. Wani naushin takaici Deen ya zuba mishi a gefen fuskar shi, tayi ja kuwa domin sai da ya tintsira. "Jaki kawai! Ka kasa bawa Ummu tsaro hatta matsayin da kake da shi bata da tsaro, ka gaza fahimtar da ita, girma da halaccin da tayi maka. Ka kwana da Saadiya daki daya ita ba yar wani ba ce? Ka yi soyayyar banza da Yaran mutane anan Abuja, ka zata wayo kayiwa Allah? Sannan don zalunci hatta fita unguwa sai da ka hanata saboda kada abin da kayi ya faru da ita! Ni da kai na gaya maka cewa kada ka sake Mahmoud ya samu mafaka a gidanka, ka da ka yarda Mahmoud ya samu inda zai zauna a gidanka alaka da duk za ayi ayi shi a waje. Karewa Mahmoud domin ya rufawa kansa asiri ya haɗa wanann rigimar, Tun a niman auren Ummu Mahmoud ya fara tanadin yadda zai lalata shirin Abba akanka. Tun daga nan lokacin Mahmud ya fara bibiyar Ummu, kayi ta cin mutuncinta kai hatta daren aurenku sai da Mahmoud ya bi Ummu akan ta kashe aurenka zai aureta. Ganin taki yasa shi har Abuja bika dan iska na zane shi wai ashe dan iska irinka ya bashi mafaka a gidanshi. Ban gaya maka gaskiya don na.wanke kaina ba na gaya maka gaskiya don na wanke Ummu daga zargin da kake mata kada ka lalata mata suna, Sannan ko Abba yasan abin da ya faru, amma ka rufe idanunka ka sake Ummu! Abba ya ce ka bani shaidar sakin domin mahaifiyarta tana bukata, sannan don Allah daga yau kada ka kara nimana a cikin rayuwarka, in har zaka iya rufe idanu ka zarge ni da shiga gonarka har abada babu amfanin na zauna da mutum irinka!" "A'a Deen! Ba zan iya rubutawa ba!" Juyawa Deen yayi ya ce masa. "Shi kenan na isar da sako, Tinah muje na ajiye ki a gida yau zan koma Maiduguri!" "A'a muje ka kwana gobe sai kayi asubanci!" Ya dauki top dinsa ya fita ko ta kan Tafida da yake kiranshi bai bi ba, ya rabu da Tafida kenan na har abada, idan ya cigaba da zama da Tafida zai aikata mishi kome. Rike rigarshi Tinah tayi ta ce mishi. "Me yasa ka bayyana kanka idan ba taimakonshi kazo yi ba? Me yasa?" Murmushi bakinciki ya sakar mata ya ce mata. "Tinah ko mutuwa Tafida yayi Ummu ta haramta a gare ni, ba zan iya shiru na bar zancen bane, nayi mamaki da naji wai ni wancan dan iskar da na dauke shi kamar Hassan dina, yana zargina Tinah kin san yadda nake jin shi a raina kuwa? Ji nake kamar ciki daya muka kwanta! Gayen can ya sadaukar min da abin da ba zan iya sadaukar mishi. Tinah wancan gayen dan iska ne mara mutunci." Yadda yayi ta zagin Tafida, Tinah ta ce mishi. "Me zai hana ka rufe shi da duka?" Girgiza kai yayi yana faɗin. "Nayiwa Ammah alkawarin duka daya zan mishi, ba zan kara ba." "Tow ka yafe mishi aboki ne kawai zai iya maka abu ka yafe mishi matukar ya yiwa rayuwarka halacci a rayuwarka!" Cire madubin idanunshi yayi yana goge kwalla da ya zuba mishi. "Babana ya kasance drive babban mota ne" ya juya cikin dakin yana kallon Tafida. "Kaf unguwarmu Alhaji Muhammad Jadda kaɗai yake iya daukar abu ya bawa makota da mabukata! Babab Aliyu. Bayan haka ko a yaranshi Aliyu ne ya dauki wannan dabi'ar ya muku kyauta ba tare da kun tanbaye shi ba, unguwarmu ai kin ga shi unguwar masu kuɗi. Bayan rasuwar Babana rayuwa bata zo min da sauki ba lokacin muna ss2, wallahi abin da zamu ci ya gagare mu." Ya nemi wuri ya zauna yana juya kanshi, "Kannena mata biyu, Hajja da Jalilah, a lokacin matsi yasa Ammah kokarin tura Hajja aikatau, a lokacin na rasa waye zan gayawa ya hanata. Yan uwanmu kowa ya guje mu babu kowa, ana haka yarinyar nan ta fita dibo ruwa a gidansu Mahmoud." Cikin wani irin karfin hali ya d'ago yana kallon Tafida hawaye na zuba mishi sosai. "Wancan dan iskar gayen yana tsaye a kofar gidansu, ana dagga da shi ya tafi makaranta ya ga shigarta gidansu Mahmoud, tun yana tunanin zata fito domin Mahmoud amma shiru babu labarinta. Ganin haka ya saka ya kwasa da gudu ya shiga cikin gidan, bata inda ake diban ruwa, ashe tana shiga Babansu Mahmoud ya kirata yana." Kuka yake yana rufe fuskarshi. "Wai yaron nan don kutumar ubansa, ni yake zargi. Tinah koda ya shiga cikin gidan Mahmoud ya tafi makaranta, kai tsaye parlour Alhaji Abbas ya shiga ya samu mutimn nan ya saka Hajja a gaba tsirara. Mahaukacin nan bai yi tunanin kome ba, ya daki kan mutumin nan sai da ya suma, ya saka Hajja ta saka kayanta, bayan ya fito da ita da ruwan ya kawo gida. Ya samu ina mitan babu inda zata. Bai gaya min ba domin itama ya gargadeta kada ta gaya min. Haka tayi shiru, yadda yaga ina mita nan ya shiga min dariyar dole. Haka yasa ni a gaba sai da na gaya mishi. Abin da ya fada min cewa. Da akwai wanda yake son Hajja da aurar da ita aka yi, domin Hajja ta girma babu amfanin kaita aiki wani wurin, saboda ko babu kome zata tsira da rayuwarta da kimarta." Kuka Deen yake tafida ya mike tare da jingina da bango, wannan wacce irin abota ce haka. Take tambayar kanta. "Tinah kin zata a baki ya bani shawara? A'a yaron nan baya jin magana. Haka ya samu mahaifinsa da zancen abin da ya gani da kuma abin da Ammah take shirin aikatawa. Kasancewar baya jin magana tun muna Yara yasa mahaifinsa ce mishi zai yi kokarin ganin haka bai faru ba, muna zaune sai ga kayan abinci daga gidansu Tafida da cefane sannan shi Babansu da kanshi ya samu Ammah ya nimawa wani Yaron Abokinsa da yake aiki a London auren Hajja, a lokacin hajjar bata wuce sha uku ba, kuma da aka gayawa Iyayen Yaron suka ce dama suna niman y'ace suma gidansu duk maza ne idan ta shigo matsayin In-law ba zasu iya girmamata ba zasu so ta shigo a matsayin y'a a cikin gidan. Haka Tafida ya aurar da Hajja, tana nan a gidan mijinta da Yaranta hudu, maganar da nake miki Babban Yaronta ya shiga jami'a sunanshi Aliyu suna kiranshi jonior Tafida. Ya sani ya san tana nan, bata tashi gaya min ba sai da Aliyu ya bar Maiduguri wani zuwan da tayi ta gaya min abin da yayi mata, Tinah na kai ki da nisa, tun daga ranar da aka fara kawo mana abincin danye gida, har yau Alhaji Muhammad Jadda bai daina ba, muna cikin waec aka kawo form na scholarship committee na Borno, gidansu tafida aka kai, wurin Babanshi aka kawo saboda yana cikin manyan dattawan arewa. Koda aka bashi bai yi tunanin kowa ba sai ni, domin already ya biyawa Tafida makaranta a sudan. Saboda nayi wani shirme ni da Mahmoud, Deen ya wanke ni ya ce shi da Mahmoud suka aikata, aka rufe shi na dawo gida a daren Aka yi belinsa, yana zuwa gidan mu ya nufa ina kofar gida, sai da ya kai ni gaban Ammah ya dauke ni da mari. Ammah ki gaya mishi kada ya kara shiga sha'anin Mahmoud! Wallahi sai na karya mishi hannu da kafa ya zauna a wuri guda, da ace bana nan ya zaka yi da Jalilah kai na kuma ganinka tare da shi sai na maka dukan mutuwa, yiwa ammah sai da safe muka fito. Ya kalle ni ya ce min me zaka yi da kuke ni? Makarantar Jalilah zan biya kasan Hajja itama zaman wani take bata da shi balle ta bamu shi yasa Mahmoud ya ce na saci ragon. Nawa ne kudin? Dubu uku! Matsiyaci dubu uku yo ko a tsaye anan ina da dubu goma, dauka ka biya mata idan kana son kuɗi ka samu Malam bala yana min wani aiki, ba matsala zai na baka kada ka ji kome, Tinah wani irin aboki ya dauke ni? Tinah don kada nayi sata ya saka me musu bayin ruwa yana sayar mishi da karro, ake kawowa daga wasu jahohin, mutumin nan kasar kano ne, shi yake kawowa, Tinah Alhaji Muhammad Jadda ya fita hakkin Yaranshi tun daga kuruciya har girma domin har ni ya dauke nauyin karatuna, haka aka tura shi Sudan, daga ranar na fara bin malam bala kasuwar muna tare, har na samu scholarship na tafi Sudan nima, da kudin aka biya makarantar Jalilah, muka gama jami'a ni sai na koma kasuwar karo, tafida ya dauke takarduna ya mai da mu makaranta inda muka yi masters, a lokacin Jalilah ta ce zata shiga makaranta school of nursings borno, Tafida ya biya ban sani ba, don itama tafi sakewa dashi, sai da Ammah ta gaya min! Yanzu haka Brother dinsa Alfah yake sonta, amma na rantse miki da Allah ya mishi warning kada ya sake ya yaudare ta domin zai yanke mishi gabanshi ya ga yadda zai auri wata yar iska. Tinah farkon nimawa Tafida Mata ina tare da Babanshi, yana ganin Ummu ya ce min kai duba zata yiwa mahaukacin Abokinka? Ina ganin Ummu naji Tafida ya dace, na ce mishi na amince." Numfashi ya sauke yana kallon Tinah da take hawaye ya ce mata. "Akwai wani Malami mutumin Abba me sosai, lokacin da Tafida ya dauko rashin ji bani mantawa saboda kin.ga shi kome nashi kai tsaye yake a gaban Uban kowa, ni kuma ba zan iya yin haka ba saboda bani da confidence! Shi mahaifinsa mai kudi ne kuma babba ne ni talaka ne fut idan na ce zannyi wani abu tafida ma b zai bari ba zai ce zan saka Mamana cikin tashin hankali. Babansa ya kai ni wurin Malamin ya nuna mishi ni ya bashi labarin kome, murmushi Malamin yayi ce shiga tambayana ina bashi amsa, bayan wani lokaci ya ce min. Gobe na je, haka kuwa washi gari na koma yana ganina ya b'ata rai ya ce min. Kasan Tafida bai da matsala me yasa baka gaya min a gaban Babanshi ba? Me yasa ba zaka iya taimakawa wurin gyara dabi'arshi, yana sonka kuma zai yi kome domin ka, kayi mishi alfarma mana!!" Ya d'aga kai sama yana jin hawaye na zuba mishi. "Tun daga ranar na daura dammara akan Tafida. Tinah bana son tashin hankalinsa har yau da nake gaya miki akwai mutane dayawa, da suke son ganin bayan Tafida amma kasancewar muna da shi babu wanda ya isa ya mishi wani abu, wannan sara da sukar domin na cika alkawarin da na dauka na tsaya mishi, ga Yarinyar ta shigo rayuwarshi nasan hatta familynshi wasu basu dauketa mutum ba, saboda wannan dan iskan bai mutunta ba, Tinah da a ce ina son Ummu na gaya mishi gaskiya wallahi sai ya sake ta kome za ayi mishi ya aureta, Tafida yayi min min abubuwa dayawa, Mijin Hajja yaso wulakantata saboda zai kara aure nake gaya mishi, kin san kiran shi yayi a waya ya mishi warning tare da gaya mishi matuƙar ya sake ta yi kuka akan aurenshi sai ya biyo shi har London, ba kudin Tafida yasa nake manne da shi, sadaukarwa da yayi min ya wuce na fada, amma na hakura abotarmu, alakarmu, amintarmu na hakura da shi, zargina yaƙe zargina dan iskan nan yake ba kara ganinka a kofar gidansu sai naci mutuncinka, kayi sha'aninka nayi nawa, kuma ka nisanta kanka da Ummu Hadiyya, in sha Allah sai Allah ya bata wanda yafika, wanda zai kula da ita wanda zai sakata farinciki." Ya juya tare da barin dakin..... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 53 Yana share hawayen da yake zuba mishi. "Ba gama aikinka ba, idan har da gaske zaka biya halaccin da ya maka haka bai isa ba, kamata yayi kama dan iska kayi ta buga shi da kasa, amma magana irinta gaskiya ka dawo rayuwarshi ka taimaka mishi, ka saka shi a gaba ka maida shi borno yana bukatarka a yanzu kai ne kawai ka rage mishi." Inji Tinah, "Ma'anar abota sadaukarwa juna da kuma yarda da juna, nasan Tafida yayi kuskure amma kuma da kasan gaskiya me yasa baka gaya mishi ba?" "Saboda ina da kishi, Mahmoud yana da baki da iya wanke kanshi, sanadin haka na rasa abubuwa biyu masu daraja! Amma me yasa baka gaya min ba!" "Dalla ka yi min shiru waye ya kira ka? Nayi da kai ne? Kada ka sake shiga maganar mu!" Kiri-kiri suka mishi zagin kare dangi, tare da saka shi a gaba ya haɗa kaya, suka bar hotel din, abin mamaki sai gashi kafin su bar Abuja an shirya kamar basu ba. *** Ummu Ban san shirin Mama ba, amma kuma da alamu ta dauka da zafi, domin kuwa sawunta biyu gidansu Tafida, tare da gayawa Baba Bulama zata shigar da ƙaran Tafida, Baba Bulama ya kira Abba ya gaya mishi wasa gaske hankalin Abba ya tashi domin ya fuskanci Mama hakkina take son kwatar min, haka yasa Abba tura Tafida ya dauko mishi Tafida. Ni dai ban so fadar nan na Mama ba, domin ko ba kome mun zama abu daya da Tafida, haka yasa bana jin dadin kafewarta akan hakkina. Mama ta karawa Ummi kwarin gwiwa, domin kuwa sau biyu iyaye maza na zama ana bawa Mama hakuri ta ce akwai Magana sai Tafida ya zo! Na razana na tsorata da hukuncinta. Amma kuma ban yarda na nuna hakan ba. Kwana biyu a tsakani Baba bulama ya gaya mata su Abba da Babana suna hanya abinci tayi me kyau, ina kwance a dakin ta shigo ya same ni. "Ina ta fadi tashi dominki, don Allah ki bani kunya ta hanyar kyale tafida yayi yadda yake so dake." Ban ce mata kome ba, haka ta fita tana mita, ai kuwa ina kwance wayata tai ringing. Dauka nayi na saka a kunne idanuna lumshe. "Yar iska karuwa, asirinki ya tonu, in sha Allah kin rasa Tafida kenan, ni Maryam nayi miki rantsuwa da alkawarin ko tsafi kike da mutum kin gama zama da Tafida kenan. Wuuuu kinji kunya ashe ma yaran ba nashi bane!" "Rai dai Maryam kina da y'ay'a mata a gabanki Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce matukar aka jife ka da abin da baka.aikata na mutum bai tab'a gushewa sai ya biya abin da ya fada!" Na fada ina kashe wayar tabbas ko tafida ne autar maza na hakura da shi. Karfe uku da rabi duk muka taru a parlour Baba Bulama, kaina a sunkuyo Tafida yana gefe can ya rame kamar ba shi ba sai Deen da yake ta wasa da Mufidah. Aka bude taro da addu'a sannan Mama ta musu bayanin dalilin kiran kowa. Sannan ta kara da cewa. "Ni ban nime wani abu daga wurin Tafida ba,.abu daya ne shi da Ummu da Deen idan aka tashi su tayi asibiti a gwada jinin Deen idan yayi daidai da na Yaran na dauki alkawarin zan kai Ummu kotun Muslunci a yanke mata hukunci daidai da laifinta, idan kuma yayi daidai da na Aliyu, Wallahi sai kotu ta shiga cikin lamarin nan, domin ya batawa Yata suna!" Rike hannunta nayi cikin kuka nace mata. "Mama har da yayarshi kin ji abin da ta fada min!" Na kuna wayar suka ji irin abin da Maryam ta fada. "Kiyi hakuri dan uwansu ne kin bar musu, Allah ya baki wanda ya fishi." Hakuri aka shiga bawa Mama, tare da nuna kuskuren Tafida. Dakyar aka shawo kanta, ta rantse da Allah ta kuma jin ko ganin Aliyu ya shiga rayuwata ba gwamna yake ba, ko waye yake sai an jita da shi ya kyale mata y'a ya je yayi rayuwarshi, ya tafi bata son ganinshi da jin shi bata son kara ganin shi a rayuwar Ummu. Sannan ta numfasa tana faɗin. "Kema munafuka kada naji ka da na gani wallahi na ga abin da ya faru a baya sai na sallamaki ga Tafida ko kashe shi zasu yi da danginsa ku can ku karata!" Ta mike tana me barin dakin. "Alhaji Kabir biu baka ce kome ba?" Murmushi yayi ya ce masa. "Me zance? Mijinta ya dace yayi magana, ni bawa bada hakuri ne, ana kai zuciya nesa sannan ana bincike kafin hukunci gudu kada a sake fadawa matsala! Allah ya kawo mafita idan da sauran rabo sai ku ga sun daidaita idan kuma babu rabo sai dai yi zumunci! Amma duk da haka ba zanso haka ya faru ga rayuwar Ummu ba, dukkanku kuyi tunani da kyau kafin ku dauki matakin rabuwa! Allah shine shaidana ban san iya adadin tambayar da tayi ko tayi maka laifi ne kaki zuwa gare ta, kai ma naga kiranka amma lokacin tana kwance, abu ne yazo kamar jiftawar rai da mutuwa!" Sannan ya daura da nasiha kafin suka shiga tashi daya bayan daya, aka barmu iya mu uku. Mikewa nayi zan fita yayi maza ya sha gabana tare da rike hannuna. "Ki dawo na shirya gyara kome wallahi sharrin shaidan ne?" Murmushi nayi hawaye na zuba min na kauda kai na, na ce mishi. "Shaidan ko kai kanka? Ka manta sau nawa kayi ta barina da Mahmoud a cikin gidanka? Bata taɓa zargin wani abu ba? Ka tab'a tambayata lokacin da ka dauko Mahmoud me yasa ya bar gidan babu sallama? Ya ya faru na bar Abuja washi garin ranar na tawo Maiduguri?" Maza nayi a kujerar parlour na cigaba da kuka na d'ago kai, ina kallon Deen. "Me ka tambaye ranar da ka je nima na a gate? Tafida ne ko Mahmoud? Me nayi maka? Tafida ba zaka gane yadda nake ji na azbatu da kai ba sai idan an maka ko anyiwa Makusancinka da yake kusa da kai zaka fahimci nayi hakuri, wanda ba tsoro ba ne kawai naji zan iya ne, daga yau kada ka kara zuwa inda nake balle Yarana! " Na zube akan gwiwata cikin shashekar kuka na cigaba da cewa.."Don Allah na ce kada ka kara kusantar inda muke na roke ka da Allah ka tafi a rayuwata idan kuma ka kara takura min." Kallonshi nayi ido cikin ido nace mishi. "Zan kashe kaina daga ni har yaran mu baka damar shan iska!" Ba iya shi ba hatta Deen sai da ya mike tsaye.."Ummu Hadiyya!" "Bani da wani zabi ne, bani da yadda xan yi ne haka shine mafita na, idan yana son zaman lafiya ni da Yarana ya nisance mu don Allah. Nayi danaasnin aurenshi ya je ya cire min tunanin duk wani d'a namiji, ya saka min kallonsu bakiɗaya a matsayin karfe dukka karfe ne, bana tunanin akwai zinari da lu'ulu'u a cikinsu, don Allah ya tafi kada ya kara shiga rayuwata! Zan rayu na gina kaina na kuma tsaya da kaina ko babu kai zan zama mutum me yanci idan ina ganinka a cikin rayuwata." Daga haka na fita zuwa wurin Mama, na shiga daki na ci kuka har na koshi nayi gatsa. Ban san yadda suka kare ba, na san nayi mishi barazana kuma naji a raina ya ji yasan zan aikata tunda na faɗa yasan xan aikata. Kwantar da kujeran Deen yayi mishi, daga nan government house ya wuce da shi, a daren har drip. *** Tun da aka kai Amarya Asiyah babu ango babu labarinsa, haka yasa Saadiya tayi ta mata habaici tare da mata rashin arziki tana faɗin. "Mace idan ta kai mace ita bata tallar kanta sai dai ayi tallata, matar cushe bata daraja, nice nan mai girma Gwamna ya zab'a da kanshi. Ba wacce tayiwa kishiya asiri don a auro ta ba waye bai sani ba?" Daga can bangaren Asiyah ta ce mata. "Eh na yarda sai dai Uwata batayi zaman gadar Lagos ba, waye ya sani ko a can aka kwaso cikin wata!" Wayyo Allah kafin wani lokaci fada ya kaure a gidan, Hajiya da aka ce ba ason ana d'aga mata hankali, tana dakinta Maryam tana parlour da Fannah, suka ji ihun zage-zagen Sadiya, Hajiya da take kwance bakin ciki da hawaye yake zuba mata, tausayi kanta da makomar Tafida take hangowa, ta zama sanadin raba auren da ya janyota jikinshi, haka tayi ta kuka wanda tasan yawan yin shi kamar masifa ce a gareta. Ai kuwa a can parlour Maryam da guntun munafuncinta, ta fita Fanna kuwa babu abinda ya dame ta idan sun so su kashe kansu........ 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 54 Aikuwa tana isa wurin Sadiya tace mata. "Haba Sady me kike yi haka? Kin fi karfin yarinyar nan, da sai da aka hada da asiri!" Daga can cikin parlournta ta ce musu. "Shi yasa kika kashe aurenki, kin zo raba kwana da mu ba! Tow ga mu ga ke ga Tafidan sai ya baki abin da yake bamu mahaukaciya, banza wacce bata san ciwon kanta ba duk sai naci Ubanku!" A haukace Sady tayi kan Kofar Matori ya dakatar da ita, kiran Tafida yayi Deen ya dauki kiran yana tambayar shi lafiya nan ya gaya mishi abin da yake faruwa, wani irin tausayi Tafida ne ya cika mishi zuciya ya rasa yadda zai yi da Tafida don haka ya mike yana faɗin. "Ok gani nan zuwa ka saka idanun akan su." Haka ya kashe wayar , har zai ajiye wayar sai ya fasa ya tafi da shi a cikin aljuhunsa. Yana fita Tafida ya bude idanun shi yana jin wani abu yana kara tokare mishi wuya. Lumshe idanu yayi daga nan barci yayi gaba da shi. Me cike da mafarkai marasa dadi. Lokacin da Deen ya isa gidan ya samu suna tayiwa Juna gori, da zage. Kallon Maryam yayi yana faɗin. "Yanzu da girmanki kike tsaye ake wannan haukar?" Yadda ya daka musu tsawa yasa kowacce ta nutsu. "Kun yi daidai, sannan zance muku wallahi idan kuka sake kuka d'agawa Tafida hankali sai na baku mamaki, sannan ke Maryam baki da amfani kin yi ƙoƙarin raba Tafida da Ummu, amma ki sani da sannu Allah zai musu sakayya. Idan kuma na kara jin labarin tashin hankali sai na saka ya rabu da ku, yan iska mara sa kunya, ban da abin kunya me zai yi daku, marasa kamun kai." "Ni dai ba dani kake ka samu wacce kake yi da kai ina da kai da Ummu kuka ci amanarshi!" "Karya kike, yar kwaya waye bai san wacece ke ba, don Ubanki tun baa haife ki ba nake ganin deen da Tafida, shegiya yar kwaya sai kin bar gidan don Ubanki!" Inji Sady, da ta nufi kofar ai kuwa Asiyah ta sheke da dariya. Karshe Sady da Maryam suka bar wurin ya shiga wurin Hajiya, ya gaida ta tana kallonshi. "Ina Babangida?" "Yana can bai da lafiya ne!" "Kace yazo don Allah!" "In sha Allah zan kawo miki shi!" Tana haki ta ce mishi. "Na gode sosai! Ina zuba idanu!" "In sha Allah!" Haka ya gama dan zaman zai mike ta ce mishi. "Ummu ba zata dawo ba ko? Duk abin da yayi daidai ne, da ban goyi bayan Yarana ba da tana nan zaune da ko wadancan sun d'aga mishi hankali yana da inda za kwantar mishi da hankali, yanzu kuwa na bari ya rasata bakiɗaya, Ummu mutum ce da babu irinta." "Allah ya rufa asiri ya bamu yadda zamu yi, idan da rabon sake zama Allah ya huci zuciyarta." "Amin Ya Allah!" Inji Hajiya, yayi mata sallama ya bar gidan. Lokacin da ya dawo ya samu yana ta barci har lokacin bai farka ba, a gidan ya kwana a gabanshi har asuba Tafida ya farka ya ganshi jingine da kujera yana barci. Tashi yayi ya cire drip din ya cire duvet din da Deen ya lullube shi da ita, ya lullube Deen, sannan ya koma ya zauna. Gani yake kamar a mafarki kome ya tafi mishi. A lokacin da aka rantsar da shi an bashi jami'an tsaro mata, amma da yake bai da zaɓi na first lady yasa shi yayi rejecting dinsu, ya san da ya bar masu kula da Ummu da haka bai faru ba. Yasan cewa Mama tayi fushi, Ummu tayi mishi barazanar kashe kanta da Yaran, zai hakura da saka kanshi lallai sai ya ganta, abin da ya sani ba zai hakura da Ummu ba duk abinda zata yi zai shanye. Amma ba zai tab'a barinta ba. Dumin bargon ya tashi Deen ya d'ago kai yana kallon Tafida wanda yayi shiru, "Ka rage tunani dai, ka tuba ka koma ga Allah zai yayye maka damuwarka. Lokacin sallah yayi bari na wuce masallaci." Ya fada bayan ya shiga ban daki yayi alola. Sannan ya wuce masallaci, shima Masallacin ta tafi bayan yayi wanka da alola. Basu dawo ba sai da garin yayi haske. Suna tafiya Deen yana faɗin. "Kai barin kira Little Ammah Wayyo Allah na, ban kira ministan gida ba!" Ya fara niman wayarshi. Can ya zarota yana sauke ajiyar zuciya, ya kira Matarshi cikin saukin kai da rarrashi ya fara magana. "Ranki shi dade, Allah ya huci zuciyarki ai nan da nazo tarzoma na samu ya tashi!" "Ina Yaya Tafida?" Mika mishi wayar yana yana mishi magana a hankali. "Kada ka janyo min kwanan waje kayi magana a mutunce." "Hello Maman Mommy!" Ya fada a hankali, murmushi tayi ta amsa suka gaisa kafin ta ce mishi. "Yaya mijina yana hannunka, don Allah ya dawo gida lafiya kaga Yarinyarmu bata sanshi ba don Allah kada wani abu ya same shi" yadda take rokonshi sai yasa ya ji bakiɗaya ya rasa yadda zai yi da ranshi ya ce mata. "Kiyi hakuri zai dawo sati me zuwa da kaina zan rako shi!" "Na gode sosai!" Ya mika mishi wayar, sannan yayi gaba. "Me kika gaya mishi?" Ya tambaye ta babu wasa a muryanshi. "Kai meye laifinta? Dalla kashe wayar." Ya fada yana karasowa wurin. "Hakkina ne na kula da rayuwarka don haka ta fika gaskiya, mace irin Sadiqa ake bukata." "A'a kada ta kara min haka" ya fada yana kashe wayar. Yana shiga cikin gidan yana me cewa. "Yau ya dace ka koma office, yana da kyau ka koma." "Amma!" "Ka koma nace!" "Ok!" Haka ya bashi wuri ya shirya, kitchen din ya nufa ya dafa musu tea da sauce din kwai tare da toast bread, ya kawo dakin kusan tare suka karya shima Deen ya shirya. "Ni zan tafi bari na raka ka office!" Haka kuwa ya raka shi office din, sannan ya nufi wani gidan Mahmoud da yasan zuwa yanzu a can yake, har cikin gidan ya shiga bayan ya ɓalle gate din yayi parking motar Mahmoud ya gani, ya saka kai zuwa cikin gidan. A parlourn gidan ya ga kaya a zube a parlour har zuwa kofar dakin da ya hango a bude zama yayi, tun karfe takwas yake zaune a wurin har wurin karfe goma da rabi, kafin Mahmoud ya fito daga shi sai gajeren wando. Kallon juna suka yi Mahmoud ya juya zai koma ciki Deen ya ce mishi. "Kayya dawo ka zauna babu inda zaka! Na samu labarin an sake ka ashe karamin kwaro ne kai, kanka karama ce bata iya daukar hauka. Haka ma yayi amma nazo naci Ubanka ne." Sai kuma ya sake murmushi ya mike yana faɗin. "na manta ashe daga dattin zina ka fito, ga Deen a gabanka bai mutu ba. Allah ya wanke Ummu daga sharrinka, amma ka sani idan ka kara yin wani motsi ko?" Mikewa yayi yana murmushi ya ce mishi zan baka kyautar da ba zaka manta ba, koda yake nasan baka san wacece matarka ba." Ya juya ya bar parlourn. "Karfe goma da rabi! Waye ya damu da sanin a ina take tunda ta iya zuwa taron mata muslmai da bikin dangi, amma a nawa hasashen anya ba wani abu yake zagaye ba." Daga haka ya juyawa ya bar shi a nan tsaye yana me zare idanu. Yasan Matarshi tnaa aiki a banki sannan tana yawan zuwa bikin danginta, sannan bata wasa da aikinta. Kiran wayarta yayi ta dauka a hankali ta ce mishi. "Lafiya kake ina ka shiga?" "Kina ina?" "Gani a wurin aiki?" "Ok gani nan zuwa!" Ya kashe wayar. Ya shiga dakin da yake ya tashi yarinyar da ya kawo, ya shirya ya bar gidan ganin yadda Deen ya karya mishi gate ya b'ata mishi rai. Ya nufi bankin da take aiki, yana me kiranta a waya. Can kuwa sai gata ta fito tana faɗin. "Lafiya?" Ajiyar zuciya ya sauke sai ya ci mutuncin Deen. "Babu kome kawai nazo ganinki ne kin san na kwana biyu ban ganki ba yanzu zan wuce gida na huta!" "Ok na gode ina sonka!" "Nima haka!" Daga nan ta juya zuwa bankin. Tana murmushi "kayi karya ka more da yan mata ka ce ni ba zan more tawa rayuwar ba karya kake!" -- Lokacin da ya isa gidansu, ya samu ana ta rigima da Kanwar Baban Khairat Ammy ta kira akan tazo Khairat bata da lafiya, sun je asibiti aka mata test da sauransu kawai aka gano ciki ne da ita, babu yadda ba ayi ba ta fadi wanda yayi mata amma fir taki, sannan mahaifin Mahmoud ya ce a koreta kada ta bata musu suna Rayyan yaki yace sai Mamanta tazo ta gaya mata wanda ya mata cikin. Tana zuwa kuwa Khairat ta gaya musu, nan Ammy da Babansu suka ce karya ne, babu wannan zancen Mahmoud da ya tsaneta ne zai mata wani abu. Ana cikin rigimar ya zo koda ya ji labarin abinda ya faru ya kad'e rigarshi ya ce musu. "Me xan yi da wannan yarinyar fisabiilillahi ga yan mata nan a gari, ku basu kudin mota su bar gidan nan bana son ganinta ma!" Ya fada yana barin parlourn cikin kuka ya ce masa. "Allah sai ya wulakanta ahalinku bakiɗaya, Allah sai ya hanaka faricikin duniya da lahira. Ubangiji ya cire maka nutsuwa da kammala ya dawwamar da rigar zina a wuyarka yadda kare ma sai ya mata haushi!" "Ke tafi can ballagaza kina yarinya karama kika iya bawa namiji kanki zaki zo kina yiwa Muhammad ihu!" Inji Ammy, "Hajiya Allah zai saka mata, Allah zai bi mata hakkinta ba zamu gushe ba da kai kararku wurin Allah ba amma kun zalinci marainiya Allah ba xai barku ba sai kun tab'e, wannan abin da kuka mana ya bazu har karshen rayuwarku, kina da Yara mata da jikoki mata zaki dandana yadda nake ji domin ta rasa iyayenta ba ta rasa rayuwarta ba ne Allah ya isa mata, Allah ya isa mata." Ta mike tare da riko hannun. "Ku bata kudin da zai isheta zubar da cikin!" "Idan muka zubar da shi kun ribance mu, amma zata haife shi a raye domin ku ji a ranku ashe kuna da sauran iri!, daga haka suka bar gidan,Khairat yayi kuka sosai. "Mama mutuwa zanyi?" "Ba zaki mutu ba, zaki rayu ki ga karshensu!" Haka suka nufi hanyar waje, Rayyan ya tawo da sauri yana faɗin. "Maman Khairat!" Juyawa tayi tana faɗin. "Me zan maka?" "Dama hakuri xan baku nasan tunda Khairat ta fada bata yi karya ba, cikin na shine idan ta haifa ina so!" "Ku kashe shi? Ba zan iya baku kome daga Khairat ba Allah zai saka mata. amma Allah yana ganinku." Ta fada suna barin gidan. Juyawa Rayyan yayi ya samu Mahmoud na fada musu tafiyar da yayi, cikin fushi Rayyan ya kife da naushi, dambe ya kaure a tsakaninsu, sai da Iyayensu suka shiga tsakiyarsu. "In sha Allah sai ka yi mummunar karshe wallahi sai ka wulakanta a duniya kafin ka isa Lahira azzalumi fasiki! Macuci ku kuma kika goya mishi baya, wallahi sai kun yi danasanin haka!" Ya shige cikin dakinsa ya haɗa kayansa. "Ba zan iya ganin wannan baƙin cikin ba!" Ya fita ya bar gidan, yana jin kamar yayi kuka don takaici. Haka iyayen Mahmoud suka goya mishi baya, ganin haka ya basu labarin abin da Tafida ya mishi, haka yasa suka yi ta zagin Tafida da Deen,har da cewa ba zasu yi kyakkyawan karshe ba. Haba haka yayi mishi dadi yana ganin sun mishi gata, har cewa abotarsu tun na Yaranta suka lalata su je sun ci amanar abota Allah zai ci nasu. *** Ummu Akwai wani abu da na kara fahimta a tare da Mama shi ne, bata iya fushi ba kuma bata iya saukowa ba, yanayinta da yadda ta tsaya yasa ni kaina na cire Tafida a lissafina, ban cire soyayyar Tafida a zuciyata ba domin Allah shine shaidana ba zan iya cire soyayyar Aliyu a raina cikin sauki ba, akwai abin da idan ba shi ba babu namijin da nayiwa soyayya haka, kuma akan shi na rufe shi, bana jin akwai wanda zan so kamarshi, cire soyayyarshi ba abu me sauki bane, haka yasa na kasa yarda Tafida ya sake ni, kamar almara, ni ce na dawo gida a matsayin sakakiya, ni na bukaci haka a baya amma a yanzu sai nake ganin kamar ba zan iya daukar haka ba. Tinah ta kirani tayi ta bani hakuri murmushi nayi ban iya mata magana ba. Haka matar Deen itama godiya na musu kawai. Amma wani lokacin kuka nake nayi kamar laifina ne kome ya faru, kuma haka ne. Da na gaya mishi yadda yake son abokanshi nan zai iya cewa ba wani abu ba ne. "ki daina kuka haka, ciki ne da ke idan kika cika damuwa zaki samu matsala da lafiyarki, tabbas sakin aure ba a abu me sauki ba ne, da ina da halin maida hannun agogo baya ba zan bari haka ya faru dake Ummu. Na sani kowanni mutum da irin zanen ƙaddaran shi naki wannan ne kiyi yaki da zuciyarki in sha Allah, Ubangiji zai tallafi rayuwarki!" "Mama haka yaran zasu taso suma su yi agolanci? Idan na kai su gidan su yi irin rayuwar da yayi? Mama taya ba zan yi kuka ba, Mama gaya min kowa na zaune bisa kan Yaranshi ni me yasa nake walagigi a ƙaddaran aurena? Mama shi kenan!" Na fada cikin shashekar kuka. "Kafin yau ban yi tunanin kome ba, amma yanzu nayi tunanin makomar Yaranki da aurenki, sai dai ki sani ba zan lamunci ki koma gidan Tafida ba, idan don kome kike wannan kukan ki daina domin Tafida ba mijin aure ba ne idan bai kunsa miki bakin ciki ba zai kai ki lahira da kafarki, mutumin da ya zarge ki da lalata da abokinsa me aka yi da mutum irinsa, mutumin da bai da adalci kowa so yake ya cutar dake kawai don kin karbar shi a haka. Ban tab'a sanin ke sakarya ba ce sai yanxu idan zaki bude idanunki tow wallahi ki bude domin babu wani abun da zai miki kyau akan tafida mutumin da ya wulakanta ki bance kada ki koma ba balle ki ji haushina idan kin koma babu abin da ya dame ni idan sun cutar dake.https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 55 Yadda Mama take kokarin kula da ni yasa na rage damuwa sosai, domin kuwa ta tsaya min yadda ba zan bukaci kome ba, hatta asibiti sai da ta nima min kusa da gida, Taima tana shigowa muyi hira, har take kawon min yadda suka yi da mijinta, har ga Allah mijinta yana sonta sosai kawai Uwarshi ce matsala, shiru nayi ina kallonta. "Kina son Mijinki ne?" Gyada min kai tayi tana faɗin. "Ina sonshi Ummu shima sona yake. Kuma ya gaya min yanzu zamu bar Nijeriya ne saboda ya samu damar karo karatu a Italiya, kin ga kenan zamu samu sauƙin fitinar Mamansa." "Hmm! Haka ne tunda yana da bukatar ina ga ki bi mijinki Allah ya daidai ku, ya kuma baku hakurin zama da juna, sannan ki rike azkar, kina yawan sadaka ko ba yawa. Ki koma Yaranku hudu idan kika barsu zasu tashi cikin maraici, kina raye amma Yaranki zasu zama marayun dole. Kina ji kina gani wata zata lalata miki rayuwarsu." Na fada ina kauda kai ina kallon Mufidah da ta fara ƙoƙarin takawa kwana biyu nan, haka kawai zasu ta kiran sunan Babansu da *Da* daurewa nake bana kuka amma tabbas abin yana sosa min rai. "Ashe Mufidah ta fara takawa?" Inji Mama ta shigo dakin. "Eh wannan shine karo na biyu da ta gwada!" "A sayo sweet a raba sadaka Alhamdulillahi." Ta kunce habbar zaninta, ta fita tana bada aikan, tashi Taima tayi tana faɗin. "Na gode Ummu bari na koma!" "Tow ba kome Allah ta rufa asiri ya sa mu dace!" "Amin Ya Allah!" Ta fita na zauna shiru ina bukatar abin da zai rage min nauyin da nake ji, ina son na rage damuwa, koda Mama ta sake shigowa ta samu na b'ata shiru bata min magana ba, ta fita. ** "Ina zamu haka?" "Gida!" Deen ya fada mishi, yana tuki. "Me yasa?" Murmushi yayi ya cigaba da tuki." Saboda ka tara dabbobi suna aikin su na dabbobi a gidan kuma kasan Hajiya bata da lafiya, dole tana buƙatar hutu!" "Tow ni daya ta haifa?" "Ba kai ɗaya ta haifa ba amma kai take buƙatar zama a wurinka!" "Ka daina min shishigi!" "Nayi Dan iska da ban daina kula ka ba!" "Mutuwa xan yi?" "Ko baka mutu ba zaka wahala!" "Me ya dace nayiwa Mahmoud?" "Lokacin da na gaya maka hatsarin barin Mahmoud a gida me kace min? Dan iska yanzu da ya lalata maka kome ai ka ji dadi, kai kada ka kara min maganar Mahmoud don wallahi xan ci zarafinku." "Idan kuma na ki fa? Idan naki fa Deen ka fita idanuna, mahaukaci!" "Duk haukata ban kai ba domin da xan gaya maka wani abu haukacewa zaka yi sai an daureka a turu." Shiru yayi yana kallon gefen hanya. "Yanzu ne ya dace ka fuskanci rayuwarka a bangaren Al'umma kana ta kokarin sauke nauyin da yake kanka, sai dai a fuskanci gidanka! Matanka da ka ajiye basu bukatar kome sai lokacinka." "Ni fa duk bukatata akan Ummu suke bayan nan bana jin zan iya mu'amala da wata mace, na rantse da Allah Sarkin da babu wani sarkin sai shi ba zan iya samun nutsuwa a tare da su ba, Saadiya ce ko Asiyah yarinyar da kai kanka kasan bata da nutsuwa idan suka kawo min reni zan kora su wallahi!" "Wannan kuma shine karya zama daram me jego ta hau gado!" "Mtseew!" Ya ja tsaki. Suna dab da shiga cikin gidan suka ga wasu cikin security na gidan sun shiga cikin gidan da gudu. Bude musu kofar aka yi Deen ya tambayi daya daga cikin masu tsaron kofar gidan. "lafiya!" "Fada ake tsakanin su uku ." Lumshe idanunshi yayi yana me sake murmushin baƙin cikin. Amma kuma sai ya ga babu amfanin tashin hankalin, suna shiga suka samu ana jan Saadiya akan Asiyah, Maryma na gefe kanta a fashe jini na zuba ana ƙoƙarin daure mata shi, amma yaki tsayawa. "Kai sake ta!" Da sauri suka kyale Sa'adiyya. "Tashi akanta?" Ya daka mata tsawa, tashi tayi cikin sauri tana haki. "Wallahi kika kara zagina sai na miki wanda ya fi haka!" "An fada uwarki tayi zaman kasar gadan lagos an fada din!" "Ke kuma Yar kwaya, Uwarki bata gaya miki gaskiya ba ke ba yar Alhaji Sanda bace a yawon bin malamai ta samu cikinki, idan karya ne kirata har ubanki na sani." "Wayyo Allah na, idan na yarda Allah ya tsine min!" Ta dauki muciya ta nufi Saadiya da shi. Fitowa yayi daga motar, tana ganin shi ta sake muciyar ta fashe da kuka. Sa'adiyya kuwa tasan waye shi don haka bata samu ba, ta wuce tana faɗin. "Kema uwar Munafukai baki ga kome ba, har ni zaki ciwa Amana ki shiga wurin asiyah wallahi sai kin bar min gidan nan tunda ba gidan Mijinki ba ne! Ni ba Ummu Hadiyya ba ce, da zaki zo gidana kina niman shiga jikin kishiyata!" Ta wuce tana yarfe hannu. "Ku kaita asibiti!" Har lokacin Tafida bai ce musu kome ba, ya wuce bangaren Ummu, key din da yake wurinsa ya bude kofar da shi ya shiga ya zauna ko ina yayi datti. Dakinta ya wuce ya bude sai yake ganin kamar zai ganta a gaban Mirror dinta tana kwalliya. Shiga dakin yayi ya zauna a bakin gadon, yayi shiru, kanshi a kasa. Asibiti drive ya wuce da Maryam, sannan Deen ya wuce bangaren Hajiya ya same ta a parlour kwance, tana kuka don ta gaji da fitinar safe daban na dare daban yau kan ma har da Maryam a fadar nasu. "Tafida ya zo ko?" "Eh yana can bangaren Ummu!" "Allah sarki, Ubangiji ya bashi hakuri da juriya!" Ta fada tana jin kuka na zuwa mata, da sallama Ya shigo parlourn, ya nime wuri ya zauna kamar babu abin yake damunshi. "Aliyu ya kake?" "Lafiya lau Hajiya!" Ya fada yana kallon inda Fanna take ya ce mata. "sannu da kokari na gode!" "Nice da godiya, Allah ya shiga lamarinka!" "Amin Ya Allah!" "Aliyu ba zaka iya yin wani abu ka dawo da Ummu ba?" Inji Hajiya, dariya yayi yana faɗin. "Hajiya Ummu kuma? Hajiya kenan! Ummu sai dai wani me sunan Aliyu ba ni ba, domin duk yadda zan yi na fahimtar da ku girmanta da darajarta ai kun kasa fahimta, yanzu da ta bar ni ai kowa zai fahimci tana da amfani a rayuwata ko bata da amfani, a bar maganar Ummun nan kawai Allah ya baki lafiya." Daga haka ya bar zancen duk yadda taso ayi maganar amma fir yaki ya nuna mata ma shi ya hakura da Ummu har abada. Bakin nan ya mata ciwo tayi bakin ciki kamar me amma haka ta hakura, banda Allah ya bashi Deen a gefenshi waye zai tsaya mishi haka shi yasa yake ganin kamar ya rasa kome nashi da ya rasa Ummu. Haka kwanaki suke cigaba da tafiya, kome yana ta tafiya kamar babu abinda ya faru, satin Deen daya ya koma wurin aikinsa, Hana barin kasar Tafida yayi bala'in sauyawa, wancan masifaffen yakusashe mara mutunci nan dai shi ne, sannan ya zama kamar dodo, idan yana gidan babu damar fada yana barin gidan zasu ta hauka da rashin mutunci kamar ba mata ba, ana cikin wannan yanayin suka samu gayyatar zuwa bikin dan shugaban kasa, don haka ana bukatar duk wanda zai je da Matarshi. Bai da niyyar tafiya da su amma saboda baya son magana yasa shi kiransu parlournshi, yana zaune ya zuba musu wasu takardu ya ce . "Gida ko Abuja, duk wacce ta dauka abin da yayi daidai shi kenan!" Da sauri Asiyah ta dauki takardan gaban Saadiya. "Mahaukaciya, ba saba zuwa Abuja ba shine da daukar na gabana!" Gyaran murya yayi Saadiya tayi shiru ta ɗauka. Ai kuwa ta samu Abuja, ta wani kwashe da dariya. "Abuja!" Ya fada tana mika mishi takardan. "Bura uba! Idan na yarda shegiya nake wallahi ba zan yarda ba munafunci aka hada min!" "Waye zai hada miki munafunci ?" Inji Saadiya tana dariya tare da zaro idanu. "Annamimiya ba dake nake ba munafika yar Mace!" "Kutuma ina wasa dake ne jaka? Yar kwaya!" Ai kuwa suka kaure da fadar da suka saba. Kai masifa, tashi yayi ya nufi kofar fita ya rufe ya ja wayar wuta ya shiga zane su, bakiɗaya ya koma musu asalin Tafidan shi sai da ya musu ligis ya kara da cewa.."Wacce zata tafi ta shiga abujan na kara jin tari sai na ci kaniyar mutum. " da sauri suka bar parlour, suna fita waje suka hau fadar kamar kajin. Dafe goshinsa yayi yana jin kamar ya fasa ihu.j *** *Ummu* Ina kwance wayata ta fara ringing, dauka nayi ina me faɗin. "Titilayo!" "Ummu ina son ki hada ni da Mama Please!" "Ok!" Na tashi ina me fita waje na cewa Mama. "Tina ce akan layi?" Na mika mata, wani murmushi Mama ta sake tana amsa gaisuwarta. Kafin ta shiga jin abinda take fada fuskarta a sake ta kalle ni, tana murmushi. "Alhamdulillahi shi kenan a turo kome zata zo da yardan Allah!" Sannan ya juya tana faɗin. "Mama lafiya?" "Wai za'ayi bikin yar shugaban kasa ne, shine aka gayyaci kwararrun masu girki baiwar Allah nan, ta tuna dake!" "Ni kuma? A wannan yanayin?" "Kashe kanki zaki yi? Kina tsammanin dangin Tafida zasu bar shi ya dawo gare ki ne idan an yi magana akan cigabanki sai ki ce zaki iya wannan wacce irin masifa ce asiri Tafida ya miki ne? Dalla bani wuri tafiya babu fashi!" Dama na lura da zarar aka ce min nayi wani abu nace a'a zata fara cewa ai ina jiran Tafida ne, wannan abin yana sosa min rai, haka yasa na hakura na rufawa kaina asiri. "Zan je Mama!" Na fada ina jin kamar xan yi kuka. Bayan na koma na kira Tinah muka yi qmagana sosai, na ware na goge kayana dama uwani ta wanke min wasu. A cikin satin na bar Maiduguri bayan na sha nasiha a wurin Baba Bulama da Mama, na iso Abuja ta jirgi tinah ta dauke ni har gidansu na kwana, washi gari muka wuce fadar shugaban kasa, inda aka bamu tsare-tsaren da za'ayi yi dayawa chefs din da aka gayyata sai suka fara ja da baya, saboda sun sanni, abu daya nayi shine hade kanmu muka raba girkin yadda kowani team zasu yi, duk da daurewa nake amma bana jin dadin jikina. Haka nayi ta nuna musu ni ban san kome ba, saboda yadda nake ji na, sai Allah ya taimaka ban yi ta amai ba ko zubda yawu ba, sai dai bana cin abincin sam sai tea, haka yasa bana wasa da shi. Mu talatin ne masu girki da Ya Gunsa yar shehun Borno, ita ta tambaye ni yadda zamu yi na bata amsa tare da raba mu, yadda ba zamu taru akan abu daya ba. Ganin yadda na tsara mana kome sai aka ware mu kabilu uku, ni daga Borno da wata yar Abia, sai wani Bayo dan Abeokuta. A kasan kowannen mu akwai mutane goma goma, yadda kowa zai ji da jama'arsa, sannan aka ware mana kome. Sannan a kasar mutane goma akwai akalla mutane talatin, saboda yadda aikin zai mana kuma ya tafi dai-dai. Haka muka kwashe kwanaki biyar muna aiki ba ji ba gani sannan babu wanda zai ci abincin yayi tsammanin zai bashi matsala musamman ni da Ya Gunsa ta tsaya tana gabatar da ni ga wasu manyan mutane da masu gidajen abinci manya da hotel. Sai gashi mutane suna ta yaba min, ai kuwa ban yi wasa da wannan damar ba, na kara zage damtse nayi aiki sosai, kasancewata yar arewa kuma nayi abin bajinta muna gama aikin Ya Gunsa ta kira ni a waya wai na shirya zan tafi dinner, haka na ci kwalliya duk da lafayya ce sai dan hill da na saka sai tsiya suke min. "Hadiyya da gaske kana da Yaro?" Inji wata me suna bose. "Twins ma kuwa suna gida!" Na ji muryan Tinah. "Malama ke ake jira maza zo mu tafi!" Ta sha kwalliya kamar ita ce Amaryan, bin ta muka yi har inda motar ta yake na shiga ta rufe min, muka wuce inda ake taron ta mika musu gate pass. "Tunda abin na ya faru mun hadu da Aliyu kuwa?" "Manta da wannan zancen bai da amfani!" "Ummu yana da kyau ki gane cewa rabuwarku ba yana nufin ba zaku yi zumunci bane, ki gane mana!" Murmushi nayi domin bana jin zan yi magana. Har muka isa ita ɗaya take maganarta amma ni dai naki magana. Koda muka shiga cikin wurin rike hannuna tayi har wurin Ya Gunsa, ita kuma ta mike ta kai ni wurin Uwar Amarya aka gabatar da ni, sai jinjina min take,sannan muka dawo inda take na zauna wurin, muna xaune naga Tinah tana juye juye. "Lafiya kuwa?" "Lafiya lau!" Ta fada tana juyawa tare da mikewa. Ta nufi can ɓangaren Gwamnoni da matansu. Ban juya ba amma jikina ya bani akwai wani da yake kallona, kamar an ce na juya muka yi ido hudu da Tafida. Cizon bakina nayi kafin na mike a hankali, na cewa Ya Gunsa. "Bari ka shiga bayi!" "Ok ki bi wancan hanya zai kai ki bandakin!" "Na gode!" Na fada tare da nufar hanyar, a hankali ya mike shima ya bi hanyar. Tunda na shiga ni ban yi kome ba, ji nayi kamar zuciyata zata buga saboda yadda nake ji, kallon madubin ban dakin nayi kafin na wanke hannuna sannan na bude kofar na fito daga nesa na hango shi, abin mamaki ni na saka laffaya fari ne ke ratsin golden, shi kuma yana sanye da wata material cream color, kallo daya nayi mishi domin na wasu yan mata suna tawowa ina ga sun zo nasu uzirin, ganshi tsaye suka tsaya daga nesa, zan wuce ya ce min. "Ko babu kome akwai Yara a tsakaninmu sannan da izinin waye kika zo nan?" Banza nayi xan wuce ya riko laffayana sai da ya zame a kaina gashina da ya dauka har bayana ya bayyana. "Don Allah ka kyale ni kafin a fara zargina da na zo Abuja sheke aya ce!" Sake ni yayi yana kallona bakinshi a sake, har na fita daga ban dakin. Kafin ya wuce yan matan da suke mishi magana. Haka yayi ta kallona har na zauna, dole na saka kaina farin ciki, na cigaba da hirana da su Tinah, komawa yayi ya zauna wurinsa Saadiya ta ce mishi. "Ni dai Tinah nan ba karuwa ba ce kuwa? Sai kace karuwa don Allah dubi shigarta haushi take ba ni!" "Kin ga kuwa tun sanina da ita ban tab'a jin labarin ta bi saurayi gidansu ba,sai dai ya biyo ta gidan Ubanta!" Shiru tayi ta kalle shi a fusace. "Malam magana ka gaya min?" "Akan me zan gaya miki magana ai ke First Lady ce ba a gaya miki magana!"shiru tayi tana jin yadda yake zugata hmm Tafida bai da mutunci ko daya, ya zageta ya kuma gaya mata abin da take mafarkin zama, hmm lallai fa yana kallon yadda Ummu take dariya tana shan ruwa, ai kuwa ta kware bai san lokacin da ya mike yayi ta ratsa mutane ya isa wurin yana bubuga bayanta. "Are You okay? Sannu ajiye ruwan haka!" Ya fada yana buga bayana har lokacin. "Ka bari!" Na fada ina kokarin ture hannunshi. "Ki tsaya ya buga hannunki! Ranka ya dade ashe kazo?" Jinjina mata kai yayi yana kallon yadda nake goge jikina!" "Kambu Uban waye ya gayyace ki bikin nan...…...https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 56 "Wacece wannan mara tarbiyya?" Inji Ya Gunsa budar bakin Tinah ta ce mata. "Hala mahaukaciya ce ta shigo ba bisa ka'ida ba" zata kara magana Tafida yayi maza ya ce musu. "Muna tare da ita!" Ya fada yana kallona. "Kin ji daidai ko muje asibiti ne?" Yadda yayi magana muryanshi babu wasa."Malam don Allah ka barni haka!" Na mike zan bar gurin, kafa Saadiya ta saka min na tafi zan fadi yayi maza ya tare ni na zube a kirjinshi, bakiɗaya wurin sai da suka mike, kamar an ce a haska mana hasken fitilar wurin ni da shi, ina sauke ajiyar zuciya nayi ina faɗin. "Allah ya Nagode maka da ka tsare ni!" Na d'ago kaina muna kallon juna. Janye jikina nayi na bar shi tsaye a wurin, domin na gama zama a wurin kenan, wurin motar Tinah na tsaya ban koma cikin ba, ina tsaye a wurin, wani mota ce tayi parking, sau daya na d'ago kai na kalli motar na mai da shi na sunkuyar ina kallon hotonsu Mufidah da Mufid, na shagala sosai a kallonsu naji ance min. "Assalamualaikum kema kina cikin yan bikin ne?" Kasancewar Muryan mace ce, yasa na d'ago kai na bude baki a hankali na ce mata. "Eh ku shiga!" "Tow Yayana ne ya ce ko zan miki magana ki shiga cikin wai nan babu tsaro!" Kallonshi nayi naga ya wani haɗe rai. "Kada ki damu ina jiran wata ne yanzu zata fito!" Ban gama rufe baki ba sai ga Tinah da Tafida. "Gata nan!" Na nuna mata, murmushi tayi ta koma ta gaya mishi, har zasu bar wurin sai ya kalli Tinah. "Kada ku sake kurkuren barinta zama alone!" Kallonshi tayi tana mamakin yadda ya mata magana yana me rike da hannun matar. "Ummu wani abu ya hada ki da shi ne?" "A'a kawai sun ce ka shige ciki na ce musu ina jiranki ne shi kenan!" Ashe ganin yadda yayiwa Tinah magana yasa Tafida tsare hanyar da zai shiga cikin hall din. "Bamu hanya!" Inji matar. "Ban gane me ya hada ka da wancan me lafayyar ba?" Domin yasan maganar da yayiwa Tinah yana me juyawa yana kallon Ummu yasan akan Ummu ce. "Cewa yayi!" "Nadrah" ya furta a hankali, sai lokacin "Muje!" "Kai magana nake maka!" A hankali ya zuba mishi idanun kafin ya ce mishi. "Ka bani hanya na wuce!" "Waye kai!" "Ina da abin yi!" "She is my wife! Kada ka kara kuskuren da kayi!" "Idan har matar kace bai dace ka barta a wurin ba!" "Matarka? Matarka for my Foot yarinyar da ka saka Tafida? Ummu kake faɗa hahaha matar da ka kama da Abokinka!" "Ke ki iya harshenki! Kina mace kina ihu kamar mahaukaciya, Yaya muje!" "Nadrah, ki kira security su kula da yarinyar can kafin na fito!" "Ok Yaya!" Sannan ya rab'a zai wuce ya ce mishi. "Perfect thanks! Allah ya turo ni ne domin na samu abokiyar gwagwarmaya! Na gode da jin sweet words na ka sake ta, Mahaukaciya meye sunanta?" "Ni ba mahaukaciya ba ce, sunanta Ummu Hadiyya! Ni dai idan kaso ka sace ta ka tafi da ita!" Tas Tafida ya dauke ta da mari, har mu da muke kokarin shiga motar sai da muka tsaya. "Matata ce Ummu Hadiyya, kuma dauke take da cikina wata uku, Uwar Yarana ne Muhammad da Aisha, kada kayi kuskuren shiga tsakaninmu na gaya maka!" "Yaya don Allah mu tafi!" Bai amsawa Tafida ba ya wuce cikin hall din, da sassarfa ya isa wurin motar kafin ya iso na shiga na saka lock na juyar da kaina. Dafa motar yayi da karfi tare da kallona, "Tinah bude min kofar!" Ba musu ta bude ta inda yake bata taɓa ganin shi a irin wannan temper din ba, ya bala'in tsorata. Shiga yayi ya ja murfin motar ya rufe, ai kuwa na fara ƙoƙarin buɗe na tafita. "Kika sake kofar nan ta bude wallahi da kalma daya zan wuce dake Maiduguri gidana, kin san me nake nufi!" Ji nayi cikina yayi wani irin murdawa sai da na rike cikina. "Na kara ganin wani ya kula ki da iddana sai na baki mamaki, na miki adalci ne yasa ban ce zan furta kalmar kome ba, idan kika sake kuwa haka ya kara faruwa!" Wani murmushi yayi yana kallon yadda nake zufa. Abu naji kamar yana zuba a pant dina, na rike rigarshi da ƙarfi. "Zan mutu!" Na furta da karfi ina rike shi gam, "Tinah!" Ya kwala mata kira, bayan ta shiga. "Lafiya!" "Abu na zuba a jikina, mara na cikina Wayyo Allah na Mama!" "What! Ba dai bari zaki yi ba?" Ta fada tana kara da cewa. "Ka taka mota mu wuce asibiti!" Bai san iya adadin gudun da yayi ba, shin gudun ceton cikin ne ko ka ceton rayuwar Ummu, sun isa wani asibitin da yake can gaba da unguwar yan majalisu. Yadda yayi parking zaka fahimci baya cikin nutsuwarshi, ta ciki ya bude inda nake, ina jingine da set ɗin, ya fito ya bude tare da daukata, jini na zuba a jikina kamar an bude pampo. "Oh My God! Tana bleeding out!"ta fada da karfi, ganin takalminta zai bata wahala tuni ta watsar dasu tayi cikin asibitin tana ihu. Haka ya janyo nurse suka rufe akanmu. A hankali nake ganin Tafida bibiyu, kafin ka daina ma fahimtar kome, emergency aka wuce da ni, aka shiga bani taimakon gaggawa. Zama yayi yana kallon Tinah. "Dama bata da lafiya ne?" "Eh amma ni a tunanina laulayi ne!" Ta fada tana kallon kofar. "Allah ya bata lafiya!" "Amin!" Can sai ga nurse sun fito daga cikin ER ɗin, suna zuwa aka cigaba da abin da suke sai dai ana bukatar jini, haka ya tafi aka dibi nashi bayan an gwada jininshi, haka yasa tunda ya kwanta ya huta. "Doctor! Babu wani cigaba ko zamu gayawa sakatariya ce ta gayawa Yallabai?" Kallonta daya likitan yayi kafin ya ce mata. "Ku kirata tow!" Haka suka yi ta ƙoƙarin ganin Ummu ta farka amma abin ya ki, haka yasa suka kira Sakatariyar wacce ta ce gasu nan zuwa dama an tashi. Kamar minti goma sha biyar suka iso, mamaki ya cike Tinah sai dai bata yi mamaki ba, sauya kaya suka yi daga shi har matar suka shiga ER. "Me ake ciki?" "Doctor bari ne, amma gudan yaki fadowa duk da placenta din ya fita amma shi gudan yaki fadowa har yanzu. Kalaman Tafida ne yake yawo akanshi. _Matata ce da cikina_ bai gama nazarin kalaman ba maganar Sa'adiyya ya kara fado mishi. *Babu aure a tsakaninku tunda zarginta kake me zaka yi da Matar da abokanka ya kwanta da ita* murmushi yayi ya amshi kayan aikin da allurai, sannan ya yi duk abin da ake ya kalli Nadrah. "Ki mata aikin !" "Why Yaya?" "Kawai ki mata!" A hankali ta koma gaban Ummu ta zauna ta haska gabanshi sannan ya ce mata. "Sauki wancan!" Ya dauka tana jiranshi. "Ki saka mata a hankali, sai ya shiga zaki bude shi!" "Ok!" Haka ta dinga bin abinda yake faɗa, tana yin yadda ya ce har aka samu nasarar fitar da dan tayin, ya amsa a hannunta. "So cute! It's baby girl!" Ya fada idanunshi na cika da kwalla, shi ko b'arin ma ayi a gidanshi Allah bai nufa ba, shi yasa duk lokacin da aka samu matsalar b'ari shi yake aikin domin Allah ya jarabce shi da son haihuwa. Haka ya gama goge jikin dan tayin, sannan ya amshi wani farin kyalle aka nad'e shi, ya saka a cikin wani karamin kwali. Ya fito sai lokacin ya ga Tafida yana rike da kanshi. "Gentle Man!" Ya d'ago kai suka haɗa idanun suna kallon juna. "Gashi a kai ta a bisineta, Allah yasa me ceto ce! Uwar tana bukatar hutu!" Ya fadi haka yana juyawa. "Kai uban waye ya baka damar kallon Matata!" "Matar mai rabo dai! Ai wannan matar ta gaya min kun rabu." Ya fada yana murmushi, sannan ya juya. "Kai!" "Shiiii! Muna da marasa lafiya please ka iya sarrafa kanka mana!" Ya fada mishi yana murmushi. Irin na cusa haushin nan. "Ki nuna min inda take ba zata zauna a asibitin nan ba!" "Matsalata da kai baka da hakuri sam baka iya bin kome gentle ba, babu inda Ummu zata. Kai yanzu abin da kake shi zai saka Ummu ta fahimce ka? Kasan yadda zargi yake destroying aure ai? Sannan kana ta kokarin kara cusa mata kiyayyarka idan ka yarda da kanka ka yarda da matsayinka no need kayi ta shirme haka, idan Ummu taka ce har abada babu wanda zai burge ta sai kai, idan ba taka ba ce kana ji kana gani zata tafi ta shimfida rayuwarta da wani don Allah ka iya sarrafa kanka!" Ta fada tana jin haushi kamar ta mare shi, can Nadrah ta fito tana faɗin. "Mss ko zaki je ku yi magana da Doctor!" "Ok thank you!" Ta wuce tana kallon Tafida da yake ta huci, tab'e baki tayi tana cigaba da tafiyarta, Office din doctor din ta nufa da tambaya ta isa office din duk da dare ne amma yadda ake gudanar da ayyuka a cikin asibitin zaka dauka rana ce. Knocking tayi tana faɗin. "Excuse me! Zan iya shigowa?" "Yes!" Ya fada daga cikin office din. "Sannu da aiki!" Ta fada tana zama, "yawwa!" Ya fada shima yana aikin shi. Shiru ne ya ratsa tsakaninsu. "Kayi hakuri da abin da ya faru dazun!" Murmushi yayi sai da dimple point dinsa suka lubba. "Ba kome!" Ya cigaba da aikin kafin ya ce mata. "Bugun zuciyar Babyn ya daina bugawa tun safe which mean, tun safe ya mutu ina ga da zaki tambaye ta sau nawa ta ga discharge kafin faruwar haka? Sannan akwai damuwa da gajiya sun taimakawa cikin wurin lalacewa, sai ban san alakar da yake tsakaninku ba, but zuciyarta yana kumbura!" "Excuse me!" Ya fito ta hango Tafida da yake tsaye har zuwa lokacin. Kiranshi tayi da hannu, ya zo tana tsaye suka shiga cikin office din. "Mu shiga!" "Ba inda xan shiga!" "Kayi karya kenan!" Ta fada tana cikin fushi da b'acin rai, ta ja hannunshi har cikin office din, kallon juna suka yi kafin ya cigaba da aikinsa. "Doctor please ka mana bayanin daga farko!" Nan yayi musu bayani har inda ya tsaya ya juya musu kan computer dinshi yana nuna musu. "Wannan shine zuciyarta, likitocin mu na bangaren zuciya suka dauki wannan hoton, domin mun ga yadda jininta yake hawa babu control, mun zata ko gishiri ne yayi yawa a jininta sai muka ga ba haka bane, bugun zuciyarta ne yake bugawa sama da kima, shi yasa basu wanke mata cikin ba sai da nazo domin gujewa hatsari, ban san kome akan ciwon zuciya ba amma ina ga ya kamata ku kyaleta idan ba haka ba zaa iya rasata." Ya datse kalman bakinshi bawai don ya gama ba, sai dai abin da zai fada zai iya fusata Tafida sai ya share yana kallon yadda yayi shiru. "kana nufin idan aka daina takura mata zata samu lafiya?" Gyada kai yayi yana faɗin. "Akwai abinda take gani wnada yake daga mata hankali, include Kai kanka domin matarka ta gaya min baku tare why not ka rabu da ita idan kayi haka zata samu lafiya!" "Eh na rabu da ita ka aure ta." Murmushi yayi yana. "A yadda nake hango kishinta a idanunka, tabbas zaka iya warewa ka yi dambe don na ga kamar dan dambe ne kai. A lokacin da aka kawo ta nurse biyu da suke kanta sun ji tana cewa. Ni banci amanar aurenka ba, ka zarge ni Allah ya gani ina sonka amma zan hakura da kai ba don naso ba! Haka yana nufin idan da zaka gyara kuskurenka zaku koma rayuwarku na baya, sai dai ita zuciyar mace tana iya rike abu me kyau da mara kyau, kayi kokarin bata lokaci sosai ba wata daya ba, ba biyu ba, ba uku ba kai ba shekara ba ka bata shekaru biyar har zuwa goma, sannan ka hakura da wannan zafin kan. Kayi ƙoƙarin ganin ka dauke kai akanta yadda zata samu zuciyarta ya huta. Amma ka sani matukar ka cigaba da tafiyar da ita kana barin wani abu yana faruwa a tsakaninku zaka kashe ta ne. Mata dayawa suna mutuwa da tarin takaici da bakinciki, saboda damuwar da tayi yawa a ransu. Idan da zaka bata damar nutsuwa da kanta zata amshi kaddaranta, ko na bata magani matukar zaka na tinzura ta ba zata warke ba Please domin yaran da suke tsakaninku ka barta ta huta!" Gyad'a kai yake yana ji kamar yayi hauka ne ko kuka ne oho, a hankali ya mikawa Tinah takardan magani. "Ku saya mata zuwa gobe da yamma idan ta ji sauki zamu iya sallamarta. Wannan maganinta ne! Sannan wannan takardan na wani Doctor Amjad daga lagos yake zuwa Maiduguri ganin masu irin matsalarta, ba kowa nake bawa katinsa ba, sai wanda na ga ya dace, yana babban asibitin Maiduguri ne yana zuwa duk karshen wata." Gyada kai Tinah tayi tana . "Zata tafi ganinshi kenan?" "Eh saboda ya ga yadda zuciyar take ne, kuma zai taimaka mata kwarai wurin bata drugs masu kyau da kula da lafiyarta sai dai kuma zata yi hakuri sosai domin!" Ya kalli Tafida kafin ya yi Murmushi. "Kawai shi kenan zata ganshi kuma xan mishi bayani!" "Mun gode!" Tinah ta fada tana, murmushi suka fito daga office din, wayarshi ya dauka yayi ta kiran Layin da ya rubuta *worst than death Dr* tsaki yayi bai dauka ba ya tura mishi sako kome sannan ya kashe wayar shima yana nazarin matsalar Ummu. Idan har ya fahimci maganar Sa'adiyya tabbas akwai soyayya da yayi had'aka da kishi, sannan gajen hakurin Tafida, idan bai ya kara fahimtar maganar Saadiya, da sunanshi da ta fada ya gano Gwamnan Maiduguri ne, haka yasa ya tuna rigimar da ake ta gulmar matar gwamna da abokinsa sun aci amanarshi idan har Tafida ne da Ummu tabbas an zalince ta, sai duk yaji tausayi Ummu ya cika mishi zuciya amma baya ganin zai samu damar shiga domin Allah bai bashi haihuwa ba, amma baya jin zai iya raba soyayyar da ya hango a idanun Tafida. Sannan ko bai raba su ba yadda Ummu take maganar tana sonshi zai matukar wahala ta karbi soyayyar wani da namiji cikin sauki da dad'i, Allah ya daidaitasu kawai. Kudi Tinah ta biya da fadar sunan Ummu da kome aka cika mata file, Tafida ya kalleta cikin sanyin murya ya ce mata. "Nasan na lalata kome, bana son ta kara ganina ciwon ya zauna a jikinta, don Allah ki kula da ita, idan da hali ki zama shadow dina, yadda xan na sanin kome akanta ba sai na nime ta ba, please Tinah ki min wannan aikin Please girgiza kai Tinah tayi tana faɗin. "amma me yasa ka bari kome ya tafi a haka!" "Saboda tana bukatar hutawa, na cutar da ita amma ina son ta dawo gare ni ba tare da alfarma ko tausayi da jin kai ba, ta dawo don ni don ra'ayinta i know Ummu she love me har yau, amma bana son soyayyar ta cutar da ita ne, akwai abubuwan da idan tana tare da ni ba zan iya, amma idan ta nisance ni maybe zan iya don Allah ki kula da lta!" "Zan yi kokarin haka amma kasan mun yi nisa bai zama dole na san wani abu ba." "Na sani yadda ta sake da ke bata sake da kowa haka ba, zaki fini jin wani abu a tare da ita!" Haka yayi ta rokon Tinah da ta zauna da Ummu. Karshe babu yadda ta iya dole ta shiga lamarin Ummu ko don dawo da martabar ta na baya, dole ta taimaka.mata domin sanin ciwon kanta, ita ba zata tsayawa Aliyu ba domin kuwa yayi kuskure yanke hukunci cikin gaggawa zata tsayawa Ummu Hadiyya ne ta zama mutum itama kamar yadda take ganin son nasara a rayuwarta zata yi kokarin ganin haka ya faru, tana kallonshi ya shiga motar da aka zo daukar shi ya bar asibitin. "Aliyu kuskurenka zaka girba, idan har kai ne soyayyar Ummu tow ba makawa zaka zama ajalin Ummu, zan tsayawa Ummu ba zan kara barin kayi nasarar nakasa mata zuciya ba!" Ta koma cikin asibitin ER din ta isa ta ga Babu Ummu a wurin, wata nurse ta ga tafito daga dakin ta tambaye ta. "Don ina ina mara lafiya nan da tayi b'ari?" "Tana can dakin an tura ta can." "Ok na gode!" Ta nufi dakin, ta tura. Ta samu tana ta barci hankalinta kwance. *** Tafida A bakin kofar masaukin ya sami Saadiya tana dariya, ganinshi kawai da tayi duk jikinshi ya b'aci da jini ta ce mishi. "Allah yasa ba kisa ya fara ba!" Shiga cikin dakin yayi ta bashi, kamar dama jira yake ta shiga ya saka ki. Yayi ta marinta domin ranshi yayi bala'in b'aci, sai da ya mata mari ya kai sau goma har sai da hancinta ya fara zubar da jini, cikin kukan wahala ta ce mishi. "Don Allah kada ka lalata min fuska, kayi hakuri wallahi zan fita a rayuwarka na rantse da Allah ka kyale ni don Allah!" "Ba zaki fita cikin sauki ba, kamar yadda kika iya cin mutuncina da na ummu a gaban Jama'a haka nake fatan na ci naki. Kazama jaka kin zata zan cigaba da kwanciya da ke ne? Wanda nayi na Allah ya yafe min, yanzu ma ina tare dake ne domin biyan buƙatar kaina, idan na gama zan baki mamaki. Kamar yadda kika kunyata min Ummu sai na saka uwarki ta ji me yasa ta haife ki jaka mara tarbiyya!" Marin da yayi mata yasa mata wani irin tsoron shi haka yasa ta koma gefe can ta takure. "Zan cigaba da azabtar dake yadda zaki na rokona na sake ki, amma ina kin haka domin sai na saka ki cin kashin da kika yi, kun yi kuskure ke da Mahmoud da Kaltuma da Hamza Goza na shiga rayuwarmu da Ummu kuka cusa min kiyayyar Aurena........! What?😲 Wasa farin girki me kuka fahimta? Shin me zai faru gaba...... Something out like 🔥🔥🔥 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH 57 "Don Allah kayi hakuri, wallahi nima biyana aka yi ba da son raina ba ne. Hajiya Kaltuma ce." Gwara kanta yayi da bango. Ta fashe da wani irin kuka, tana nishi. "Gaya min me yasa?" "Ita ce wallahi ita ce!" "Ok tunda ba zaki yi magana ba, zamu koma gida!" "Tafida kada ka koma Hajiya Kaltuma!" Mari ya kwad'a mata sai da ta suma. "Wato shirinku ba iya kaina yake ba me yasa kuka had'a da Deen me yayi muku?" Ganin bata motsi ya sa shi, bude friji din dakin ya ciro ruwa me sanyi ya watsa mata, yana kallonta. "Ban san iya adadin bala'in da kuke shirya min ba!" "Wallahi babu." "Zaki fada ma." Ya tashi ban daki ya nufa yayi wanka ya zo ya same ta tana niman key din dakin, "yana hannu na." Fashewa tayi da kuka, "Ka kashe ni kawai." "Murmushi yayi yana haɗa kayanshi a cikin akwati. "Na zata kina da hankali na zata duk iskancinki ba zaki iya boyewa Mahaifiyarki ba ashe kema munafukar ce, ita Babbar munafukan tana cikin gidan tayi shiru kamar ba ita, sai tsula tsiyarta take." Murmushi yayi ya wurga mata hijab da nikaf, "ki rufe mummunar fuskarki! Nasan Mamanki da son abin duniya amma ba zata tab'a yarda tayi tarayya da wasu akan abinda take niman iko da shi ba, Mahmoud yana son Ummu ke kina son ki zauna da ni tow ita Uwar dabarku me take buƙata?" Girgiza kai take tana kuka. "Ai ba zan miki kome ba." Ya faɗa yana murmushi sannan ya ce mata. "Daga yau ba zaki kara magana ba, balle har ki bayyana shirina akansu don na san halinki!" Buga kofar aka yi ya kalleta yana murmushi. Zuwa yayi ya bude kofar ta fasa ihu. "Kun ga ai na gaya maku, ta haukace yanxu ma ihun da zata yi ta muku." Ya fada cikin tashin hankali. Haka suka shiga dakin ta fara ƙoƙarin gudu suka kamata tare da mata allurar da yasa ta fasa ihu, ta fadi. Ɗaukarta suka yi akan wuce da ita, Tafida mugu ne domin murmushi ya sake, yasan idan ya cigaba da haka ba zai tab'a samun yadda yake so ba, amma a yadda ya shirya yasan ya gama cabke ta. Kusan rabin kwana yai yana gayawa Allah lamarinsa tare da tuba, don yasan ya aikata abin da ranshi yake so, yanzu kuwa bai da wani hanya da ya wuce gano su waye suke bibiyarshi. A ranar da zai raka Deen ya ce mishi. "Kana tsammanin Mahmoud kaɗai yake son ganin bayanka? " murmushi Deen yayi yana girgixa mishi kai kafin ya cigaba da cewa. "Nayi ƙoƙarin gano waye a cikin gidanku yake da alaka da Mahmoud, sai Sa'adiyya tayi Cross mind dina, amma me da na tsannanta bincike sai na gano ba Saadiya ba ce a cikin gidanku take, tana cikin gidanku sannan ba Hindu ba ce domin kwanyar Hindu baya ja har haka." Murmushi yayi ya ce mishi. "Wannan sune kiraye-kirayen wayar Mahmoud da mutane biyu a cikin gidanku, na farko Saadiya ce, sai mai wannan number itama yana kiranta amma ita tafi kiran Saadiya sama da kiran Mahmoud, idan ka lura duk wayar da zata yi baya wuce minti uku zuwa biyar tafi yi da Saadiya. Domin tafiyarsu tafi zuwa dai-dai. Haka yasa nayi ta bibiyar number amma ban samu damar kira ba! Kafin ka Fara naka binciken ka san waye yake bibiyarka!" "Kai ma ba iya samun me number ba sai ni kaga ajiye zancen!" "Abin da ya sa na dage maka, Ummu tana buƙatar kariya a kowani fuska, sannan yana da kyau ka san waye a tare da kai, iyayenka ma! Kai ka fini damar bincike a ko ina kake a fadin Nigeria zaka iya bincike kuma ka samu yadda kake so amma ni, ina da limit dina da ban isa cross dinsa ba." Jin haka yasa shi karban bayanan, da fari bai damu ba sai da ya nutsu, ya kawo maganar Tafiya abujan nan, koda suka iso yana lura da yadda take tuttura sako tana goge sakon, shi kuma da yake yana da hanya ya saka aka bibiye sakonta, lokacin da ta shiga wanka wayar tana gefenshi ya ga ta saka. *Abokiyar mutuwa* daukar number yayi ya duba da wanda ya dauka na wancan binciken sai ya ga ya zauna daidai, sannan ya ajiye bai kulata ba, sakon Saadiya aka kawo mishi aka buga kofar, mikewa yayi ya fita ya amsa yana faɗin. "Yanzu aka kawo!" "Shi kenan!" Dawo cikin ya saka cikin aljuhunsa domin a drive ne, fita yayi ya barta a dakin yana me barin hotel bakiɗaya, gidansu Tinah ya wuce anan ya ga sakon da kome sannan ya gwada kiran number. Ai kuwa Hajiya Kaltuma ta dauka tana faɗin. "Mahmoud ma gaya maka idan ba zaka iya amfani da damarka na lalatawa Tafida da Deen suna ba, kada ka kirana. Tunda ka kasa ni zan ɗauki nawa matakin hakura ya kare, Tafida da Deen da Ummu sun hanaka sakewa ni zan yi maganinsu, tunda iyayenshi sun gaggara rabu da shi duk da rashin mutuncin da yake, zan yi yadda iyayenshi zasu mishi baki ya lalace, ma raba shi da Ummu amma kamar ƙara ƙarfin gwiwa nake mishi! Na raba auren Iyayen shi wai don ya lalace amma kamar taki na zuba mishi anya Aliyu ba Aljanu suke kare shi ba." Kashe wayar yayi ya jingina kanshi kan shi a dakin karban bakinsu Tinah, ta kalle shi. "Me kake bukata? Yanzu?" Bayan sun gama jin kome. "Tinah kwarin gwiwata Hadiyya ce, idan na rasa ba zan iya kome ba!" "Zaka iya mana! Dole sai da Ummu ne?" "Na sake jifa rayuwarta cikin hatsari kenan." Shiru Tinah tayi tana gyada kai kafin ta ce mishi. "Haka ne kuma, zan yi amfani da damar da nake da shi janyo su, zuwa duniyata." Wannan shine abin da ya faru, tabbas Deen Alkhairi ne a rayuwarshi, Deen na musamman ne rayuwarshi. Bai yarda sun hada tafiya da Saadiya ba tunda yasan matukar yadda aikinsa ya tafi akwai sauyi, don haka a ranar ya bar Abuja, tare da Tunawa Tinah ta kula da Ummu, kada ta kira Mama shi zai same ta da kanshi. Karfe daya na rana yayi mishi a gidan Mama, a dakin Mama yana kallon yan dagwai-dagwain Yaranshi, rungume su yayi sai yanzu yaji kaunar cikin da ya zube, hawayen da yake kokarin dannewa suka zubo mishi. Ita kanta Mama da ta shigo ganin yadda ya rungume Yaranshi sai taji ta karaya, wai meke faruwa ne a rayuwar Tafida da Ummu ne? Duk sai tausayinsu ya kama ta. "Kai ne a unguwarmu?" "Eh Mama nazo ganinsu ne, na gaya miki Ummu bata da lafiya a can abujan!" Yadda ta razana ya sa shi gyara zama yayi shiru yana karantar yanayinta duk da baya kallonta amma yadda take salati da jajjantawa yasa shi kasa da kai ya ce mata. "b'ari tayi, amma da sauki zuwa yamma za a sallame ta hala ko zuwa gobe su iso!" "Allah ya bata lafiya! Amma me ya kawo b'arin ba wani abu ya." "A'a bata jin dadi ne wanda ya haɗa da ciwon kai da ya haifar da b'arin!" Yayi shiru kafin ya ce mata. "Don Allah Mama kiyi hakuri, don Allah, ina son na kai Yaran su ga Hajiyata da bata da lafiya!" "Tafida kenan, kasan Ummu bata nan yasa ka zo daukar su ka jira idan ta dawo ka zo ka ɗauke su." "Mama ki yi hakuri yau daya tal, ki bani su zan dawo dasu zuwa dare!" "Allah ya kai mu!" Ta fada tana me shiga cikin dakin ta hado kayansu gwanin ban sha'awa a jaka ta mika mishi. Amsa yayi yana kallon yaran. "Uwani! Zo ki taya shi daukar Mufid ki barwa Zakiya aikin!" Ta fada tana fitowa daga dakin. "Tow Mama!" Ta shiga ta amshi Mufid suka fita, security suka amshi jakar, sai da ya saka Mufidah a cikin motar kafin ya shiga sannan ya koma gefen suka ya amshi Mufid ya saka ya juya ya cewa Uwani. "Don Allah kada ki gayawa Ummu!" Murmushi tayi tana girgixa kai. "Ba ayin haka da ni " ta shige cikin gidan, mutanen sun cika a kofar gidan, shi damuwarshi ya kawo shi ba ta mutane ba. Lokacin da ya isa gida kallon bangaren Saadiyyah yayi , ya sake murmushi sannan ya shiga wurin Hajiya tana parlour ita dasu Rukayya. Yana ganinsu ya hade rai daga bakin kofar ya kalli Hajiya yana faɗin. "Hajiya na dawo ya jikin naki?" "Da sauki sosai, ya aiki da fatan ka dawo lafiya!" "Alhamdulillahi! Hajiya Allah ya baki lafiya!" Ya fada yana me juyawa zai fita ta ce mishi. "Kawo min su na gansu mana!" Murmushi yayi ya ce mata. "A'a Hajiya idan aka musu wani abu zan iya fita a hankalina, kina son Yaranki nima ina son Yarana." Ya juya abinsa ya bar parlourn, Har ya fita ya kwallawa Fanna kira, fitowa tayi ya ce mata. "Me kike yi a wurin?" "Abinci nake dafawa su Maryam!" "Ok je ki!" Ya juya da Yaranshi suka nufi bangaren Sa'adiyya, bude mishi kofar aka yi yana shiga ya ajiye su a parlour ya nufi dakinta tana barci. Murmushi yayi ya nufe ta yana kallon fuskarta, fita yayi zuwa parlour ya dauke su. Sannan ya wuce bangaren Asiyah tana parlour kwance a kasa tayi mankas. Kallonta yayi yadda take ta barci yasa shi barin bangaren. Ya nufi nashi da yaran, Allah sarki Ummu ya tuna da kafin ya dawo an mishi kome an ajiye mishi, dakinshi ya kasu ya zuba musu tarkacen wasansu da suke gefen gadon dakinsa wanda Ummu bata tab'a ba, sannan ya shiga wanka yana fitowa ya duba jakarsu garin kunu ya gani ya shiga kitchen ya dama musu kamar yadda Ummu take, sannan ya saka a ruwa ya dawo parlour dakin, ya dauke su kamar kada ya rabu da su,haka ya shiga ya haɗa musu ruwan dumi yayi musu wanka ya sauya musu pampers ya basu kunun suka sha kafin ta dauke su bakudaya a kafadarshi yana jijjiga su, aka buga kofar parlour. "Shigo!" Fanna ce dauke da tire. Kallonta yayi yana faɗin. "Mai da shi Fanna a koshe nake!" "Ni da Hajiya muka maka wallahi babu wnada ya shiga cikin kitchen din ka ci kana bukatar Abinci, ga matanka ba hankali ne da su ba balle a samu wacce zata baka ruwa ka sha!" Murmushi yayi yana faɗin. "Na gode sosai!" Ya fada yana kara jijiga Yaran. "Ka amso su ne?" "Eh na kawowa Hajiya ce da zan tafi tace tana kewarsu naga da mutane a bangarenku kada su cutar min da Yarana ta ce nayi hakuri!" "Gaskiya ne da ace kayi hakuri gara ba ayi ba ma balle ayi wani ba da hakuri!" Murmushi yayi ya ce mata. "Na gode!" Sannan itama godiya tayi mishi tana me barin parlourn, haka ya wuni da Yaranshi, sannan ya dauke su ya mai da su, Yaran suma idan ka gansu sai burge ka musamman yadda ya saka matori yayi musu sayayya. Har lokacin Sa'adiyya bata farka ba, sai da ya koma ya tashe ta. Bude idanunta tayi tana kallonshi kafin abin da ya faru ya dawo mata, wani tsalle tayi tana faɗin. "Kayi min rai!" "Me ya faru?" "Ni dai kayi min rai! "Kin yi hauka ne? Me yake damunki?" Ihu tayi tana me zubewa a kasa tana bashi hakuri. Bakiɗaya ya nuna mata bai san kome ba, Fita yayi ya kira Maryam. Can kuwa suka dawo tana me rufe kofar.. "Don Allah ka sake ni na fasa aurenka!" Kallon Maryam yayi yana faɗin. "Me ya same ta?" "Ai tun tafiyarka bamu san me ya faru ba sai dai ko ita da kishiyarta idan sun yi fada." Dake babu wanda yasan yayi tariyar da ita, sannan ya dauke ta ne ba tare da ya bar al'amar bata gidan ba, sannan koda aka dawo da ita daga Abuja, kowa na ɓangaren shi babu wanda ya kawo ita ce ta dawo ita Asiyah tana can tana shaye-shayenta. Duk rashin jin ta, ta hakura da kome amma ta kasa hakura ta bar shaye-shaye. Ihun da take yasa kowa yayi tsammanin wani abu, ita dai Saadiya akan gaskiyarta take amma Tafida ya mai da ita mahaukaciyar dole. *** Ummu Karfe takwas na dare na farka, ina kallon Tinah da ta ajiye min abincin, domin bata jima da dawowa ba, taimaka min tayi na shiga ban daki, nayi wanka da tsarki na sauya kayan jikina. "Team dinku sun zo kina ta barci." "Allah sarki, na gode sosai!" "Kin yi waya da Mamana?" Na koma gadon na zauna ina haki, don jiri nake ji. "A'a!" "Ya kamata a gaya mata ai!" "Eh na yi kokarin haka!" Ta fada tana murmushi, mika min wayar tayi na amsa lokacin da kiran ya shiga. "Mamana!" Sai ka fashe da kuka, ina gaya mata cikin ya zube, nasiha tayi min tace min.." idan zaki iya dawowa ki tawo gobe ayi miki jinya da gyaran jiki!" "Tow Mama!" Na fada ina kuka, dariya Tinah take tana faɗin. "Crybaby!" Bayan mun gama waya nayi kuka sosai, har Tinah sai da ta turawa Tafida text ya kira ta. "eh gata nan tana kukan!" "Ok ki rarrashe ta please!" "Ban iya ba!" "Please!" "Tow!" "Ummu kiyi hakuri mana!" "Kina tare da Tafida ne?" "Eh amma ai kin san abokina ne ba zan iya kyale shi ba!" "Dole ki zab'a ko ni ko shi don ina tsoron kada ya biya ki, ki cutar da ni." Dariya tayi tana faɗin. "Kina da abin dariya, idan xan cutar dake da tuni nayi, domin kuwa na jima da sanin haka, amma yanzu bana jin zan iya cutar dake, ga wannan file din idan kin koma ki bawa wani ya duba miki, ba sai kin zo abuja ba, wannan kuma gudummawata ce na lokacin da baki samu damar zuwa gasar girki na duniya ba, ki yi nazari." Hawaye na ji yana zubo min, na kasa magana ina kallonta. "Bayan duk wannan abubuwan me yasa kika yi haka!" "Tun da naji kun rabu naga babu amfanin ki zauna ki karawa Mama nauyi, sai na saka aka dawo da videos dinki na baya, yadda zaki samu damar kara dawowa Baby Mama's Kitchen! " kuka nake ina girgixa mata kai. "Me yasa?" "Ni naji ina ra'ayin haka!" Dakyar naci abinci, sannan nayi ta kallon takardun ina dubawa. Har wurin sha daya muna tare da ita, kafin Dr ya shigo ya duba ni, a daren ya sallame ni. A gidansu Tinah na kwana, washi gari na bar Abuja da kyakkyawar sallama daga Ya Gunsa, da mata shugaban kasa, sannan na dawo gida. Tunda na dawo Mama take jinyar jikina, satina biyu na tafi ganin likitan da aka ce zan gani Dr Amjad, sai dai bai samu zuwa ba, wani likitan na gani fuskana da nikaf. Bayan ya gama rubuta min na amshi takardan na tafi na sayi maganin, sannan na bar asibitin. Na dawo gida, anan na shiga tattaunawa da Mama akan abin da Tinah ta kawo min, don saura kwana uku na fara zuwa wani babban hotel ina musu girki kafin lokacin shiga gasar yayi. "Ummu!" "Na'am!" "Ki ji tsoron Allah! Ki tuna Allah yana ganinki idan ke baki ganin shi, Ummu kada ki sake wani abu ya faru wnada zai janyo zubar mutuncinki!" Yadda Mama take min nasiha sai naji hankalina ya tashi ina jin kamar na fasa aikin, amma babu yadda na iya tunda na amsa kaina a sunkuye, bayan ta gama min nasiha na mata alkawarin zan kare kaina da mutuncina in sha Allah. ** Tafida. Hajiya Shuwa ce take kallon Saadiya wacce ta fita hayacinta abin tausayi, kamar ba Saadi pagal ba, kallon Tafida tayi ta ce mishi. "Da alamu jifar Saadiya aka yi domin nasan haka!" Murmushi yayi yana faɗin.."Allah ya kyauta!" "Amma idan kana cigaba da addu'a zata samu sauki." Kwafa tayi tana faɗin. "Wallahi ba zan yarda ba!" A ranshi ya ce. *Kada ki yarda ai magana ya kare* Haka tayi ta surutai har da fadar sunan Asiyah don tasan ita ce Ubanta ne boka. A lokacin da aka fara maganar Auren Tafida da Asiyah suka tafi can wani kauye kusa da Yola anan suka hadu da wani tsohon boka, bayan ta bada sunan Asiya ya buga ya buga sannan ya kalleta yana murmushi ya ce mata. "duk duniya babu wanda zai miki aiki ya kama Kishiyar yarki, face ni." Ya kwashe da dariya sannan ya ce mata. "Ni kuma ba zan yi ba domin na hango ina da gudan jini a rayuwata, Yarinyar nan Y'ata ce shekaru ashirin da biyu da suka wuce Uwarta tazo nayi mata aiki akan tamallake mijinta, na kwanta da ita ashe rabon Asiyah ne ki tafi ba zan yi nima kare Y'ata zan yi." "Ban fahimta ba!!" Sake maimaita mata bayanin yayi, yana washe hakori yana faɗin. "Jeki ba zaki tab'a samun nasara ba, domin kuna kokarin tashin masifa ce daga barci yarki ta ci amanar Mijinta, mafi munin cin amana maza wuce ki fita kada ki yi tsammanin zaki yi nasara domin Aliyu Tafida Aliyu ne idan ya tashi ban san daga inda zai fara farautar shi ba.." Ita kuma daga dawowarta ta gayawa Saadiya yau ta hadu da boka uban Asiyah, shi kenan ta samu abin gorantawa Asiya, dama ita Hajiya Turai tasan shuwa tun da jimawa, sakamakon mijin Turai ya nime Shuwa a lagos, don a lokacin tana da kyau da kuma jikin da yake jan hankalin yan maza haka. Haka Turai ta shiga ta fita sai da ta rabasu. Murmushi tayi tana kara jin tsanar Turai.. "Ni zan koma wurin Hajiya na ga ya jikin nata." Domin rana daya aka kawo su asibiti ita Sa'adi bangaren mahaukata aka kawo ta Tafida ya manna mata hauka karfi da yaji. *** Hajiya Kaltuma..... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 58 Idan Sa'adiyya tana hannunshi duk wani active dinta zai sani, ta hanyar amfani da wayarta, na biyu yadda zai saka Hajiya Kaltuma tonawa kanta asiri, sannan zuwa yanzu gidansu zai saka security a wajen gidan kamar yadda yaso yi amma Abba ya hana shi, shiru yayi yana nazarin abin. *Hajiya Kaltuma* D'ago idanu tai ta kalli kanta a madubi, shekaru ashirin da takwas. Baya mijinta shine darakta ma'aikatan ilimi ta Nijeriya, a duniyarta babu abinda ta sani sama kudi, koda yake kafin mijin Alhaji Armaya'u tai aure har sau biyu, inda ya auri mijinta na farko daga gombe kazamin me arziki ne, Maccudo Ibrahim Hamma, idan aka ce zaa yi lissafin masu arzikin noma da kiwo yana cikinsu, sai dai irin mazan nan ne masu son abu me kyau, ya hadu da Kaltuma ce wacce kaf duniya bata da kowa sai Hindu kanwarta ce, ciki daya tana bala'in son Hindu domin tasan kaf duniya babu wacce zata mora tayi arziki da ita kamar hindu, Hindu tafi Kaltuma kyau nesa ba kusa ba, amma kowacce tana da abin da zata iya da abinda ba zata iya ba, Hindu zata iya tsafi amma rashin imaninta bai kai tayi kisa ba, amma Kaltuma zata iya kashe kowa akan kuɗi. Alhaji Maccido Ibrahim Hamma, tunda ya ga Kaltuma wacce ta kasance sadaka yalla,.ya makale mata amma yarinyar nan ta gaya mishi gaskiya bata son shi ya ko fahimta, sai b'arin kudi yake mata, a lokacin duniya na kwance, Uwarsu me suna Ayyah tana son kuɗi don haka ta takurawa Kaltuma aka yi aure, aka kashe kudi aka yi biki irin na alfarma, tinda aka gama biki ango da amarya aka samu zaman lafiya, babu wanda ya kawo ana samun matsala a zamantakewar su.. har tsawon wata shida, kwatsam Alhaji Maccido Ibrahim Hamma ya fara Jinyar da ba a san kanshi kuma dama yana auren ya saki Matanshi biyu, daga baya ya dawo dasu amma bai shiga harkansu, wannan jinyar yasa suka shiga tashin hankali, suka yi ta kaiwa da komowa kafin sati ya ce ga garinku, mutuwar ta girgiza kowa musamman Matanshi sumar Kaltuma uku, har aka yi bakwai bata cikin hayacinta, sai da rokon Allah ta dawo daidai, aka raba gado wani abin tashin hankali na Kaltuma yafi na kowa yawa. Haka kowa yayi shiru ya bar zancen amma zalinci anyi shi. Bayan ta gama takaba ta hadu da Alhaji Bashir Ishaq darakta, soyayya kamar zasu cinye kansu, a lokacin Ayyah bata son Bashir Ishaq domin kuwa bai da wani arziki, haka suka wayi gari Ayyah ta shura bokiti, wannan yasa Hindu ta gudu domin gani take kamar Kaltuma zata cutar da ita, ta bi wasu ayarin karuwai zuwa Lagos(🤣😂😒 kada na kara jin kasar gadan lagos) a hankali ta bude idanun ta a cikin duniyar tantiran karuwai, ran Kaltuma ya ɓaci domin ba karamin buri taci akan Hindu ba. Kwatsam sai gata da cikin Alhaji Garba Yola (Mijin Hajiya Turai) anyi cikin ya zuba amma yaki, a cikin wannan yanayin mijin Kaltuma yayi hatsarin mota ya rasu dama ya saki Matarshi yar kano, ya kwace Yaranshi Kaltuma tayi ta gana musu azaba, yana mutuwa danginsa suka zo suka kwashe yaransu. Ana cikin wannan yanayin ta samo labarin Hindu shine ta je ta daukota ta haihu a gabanta, sannan ta cigaba da kula da su har suka hadu da Saleh,dalilin mutuwar Bashir Ishaq kuwa zuwa da yayi da abokinsa, Alhaji Muhammad Jadda, tun daga nan ta ji a ranta ta samu miji kawai ta saka aka kunce mishi birki mota tabi ta kanshi. Haka yasa ta cigaba da kula da lafiyar hindu da yarta. Wacce itama Kaltuma ta kashe ta, jin bakin cikin haka yasa Hindu ta gudu na tsawon shekaru biyar, kafin Kaltuma ta sake kamota a lokacin tazo, ta cigaba da zama, amma babu wanda ya san meke faruwa, domin kuwa bayan dawowar Hindu, Kaltuma ta haihu. Shine ta haife Yarta mace mai suna Sadiya, a lokacin tayi auren Hindu da Saleh tare da bata kyautar Saadiya da sunan ita ta haifa, ita kuma hindu tana shiga gidan Saleh bata samu haihuwa ba saboda mahaifa yasha gwagwarmaya. A lokacin da Hindu ta zo ta raba Hajiya da Salamatu, sannan ta kara shiga jikin Salamatu har ta yi nasarar bakanta Salamatu a idanun Yaran Hajiya ta b'ata Yaran hajiya a idanun salamatu, Kaltuma bata sha wuyar samun Alhaji, kasancewar ta iya takunta, shirin Kaltuma akan Tafida ya samu asali ne daga zuwan Mahaifiyar Nabilah take ganshi ita kuma irin matan nan ne da Allah ya musu baiwar gane gane, tana ganin haka ta gayawa Kaltuma shine dalilin shlgowarsu, tana ganin aliyu ta kai shi wurin Malaminta, ita ce ta san Aliyu zai zama wani abu saboda kokarin shuwa na son ganin ta guje mata kada ta cutar da ita , sai ta nuna mata ita fa ta shiryu ta daina ta'addanci, tana son tayi aure ko don rayuwar yar karamar yarta da bata wuce wata shida ba. Sannan ita mai gidan da suke take son aura idan kome ya tafi daidai ba zata zalunci kowa ba, sai dai duk wanda ya gano wacece ita zata ga kayanshi. Shuwa ta amince ta amshi bukatar Yayarta kuma cikin ikon Allah, ta samu Alhaji Muhammad Jadda ta aura, a lokacin Tafida yana da kusan shekaru bakwai domin da wayonshi tazo gidan, amma tasha wuya kafin ta samu ayi auren, sai dai shirinta na farko ya fara ne akan Hajiya domin da Hajiya tana gidan ba zata iya shiga ba, kasancewar idanun Hajiya yana kan Mijinta, yayinda ta kuma kokarin raba Aliyu da Hajiya don tasan matuƙar ba raba su tayi ba babu yadda zata yi ta samu Aliyu, wani abun da ta fahimta Aliyu Mahaifinsa yana bala'in sonshi da son duk wani abin da yake so. Haka yasa tayi ta nunawa kamar ba kome, amma idan ta samu dama nunawa take ana fifita Tafida akan sauran Yaran gidan, wanda babu wanda ya d'ago ta sai Hajiya Salamatu ita duk da rashin kulawarta akan kome sai dai ta fahimci Shuwa da Kishiyarta bakinsu daya haka yasa ta janyo Yaranta jikinta yadda wani bai isa yasan wani abu akan Yaranta sama da ita, a wannan bangaren tayiwa kanta rashin adalci domin da janyo su zata yi, amma ta ja nata ita ɗaya ita kuma Shuwa ta janyo su Maryam jikinta da Tafida. Haka yanayin yake tafiyar, duk yadda Kaltuma taso bakanta Tafida sai ta kasa samun damar haka domin Alhaji Muhammad Jadda baya ganin laifinsa. Tayi matukar kokarin ganin yadda zata raba shi da mahaifinsa amma abin ya faskara haka yasa tayi ta kokarin shiga jikinsa, amma fir yaki yana me juyawa kan Shuwa. A lokacin da ya kai yadda zasu more shi, Alhaji Muhammad Jadda ya kawo maganar auren shi da Ummu, kusan tafi kowa murna amma kamar ta mutu don bakinciki, don tayiwa Tafida tanadin tsiya ta aura mishi Saadiya da take hannun Maman Nabilah, sai dai kuma bata samu damar haka shine ta turo Saadiya gidan a sunan yar shuwa ce yar kaninta, wannan tsarin Hajiya Kaltuma ne, Saadiya ta samu yarda a wurin Tafida. Sai dai kuma yadda yake nunawa ba zai iya aurenta ba yafi kome mata ciwo, saboda tun fil azal Aliyu baya ra'ayin Sa'adi sai dai da yake baya jin magana sai yayi ta janta a jikinshi don ta bakanta ran Abbanshi, da yake ganin kamar yafi son Yaran Hajiya Salamatu akanshi domin magana ba magana ba zai ce Sharifai ya fishi hankali. Su kuma Yaran dakin Salamatu suna matukar son tafida saboda ko a makarantar ba a tab'a su, asalima girmama su ake yi saboda Yayansu. Lokacin da Hajiya Kaltuma ta gano alakar da yake tsakanin Mahmoud da Sa'adiyya, wani jahilin duka ta aka mishi, tare da cewa ya sani abin da ya samu a jikin yarta kamar rayuwarshi ce, don haka zai mata aiki shi kada ya zama kamar Deen da ya koma karen Tafida, haka yasa tayi ta kashe mishi kudi tana saka yayi abin da za a kama su da Tafida. Tabbas Tafida kafin zuwan shi Sudan ya so lalacewa Allah ya dubi zuciyar Iyayenshi. Sannan tayi ta kara nisanta Aliyu da Hajiya baya jin maganarta baya jin tausayin, ta hanyar nuna mishi ba wani abu ba ne, don ya ko Hajiya ai Allah ba zai kama shi da laifi ba, Hajiya tana ji tana gani yaronta ya kasa samun nutsuwa da ita. A zuwa yanzu shuwa ta haɗa kai da Alhaji Hamza Goza, wanda tasan shine kadai zai iya kalubalentar Tafida a yarda a kuma ce siyasa ne, sannan bata jin a ranta duk abinda take wata rana dubunta zai cika, shi yasa farkon Auren Tafida da Ummu ta janyo Ummu jikinta yadda zata na jin dadin gaya mata kome, sai aka yi rashin dace, Ummu zurfin cikinta yayi yawa, bata jin zata iya sakewa ta gaya maka abin da yake damunta, wannan abin ya hana sa Hajiya Kaltuma kasa cutar da Ummu. Ko abin da ya faru da Ummu ta sani domin a gabanta aka ayi yarjejeniyar sadiya Tafida, shi kuma Ummu sai dai ya kasa samun Nasara akan Ummu. Sannan tana da videon abin da ya faru, gudun kada tafida ya san tana cikin Mutanen da suke farautar rayuwarshi yasa ta boye nata, amma tabbas ta ajiye shi domin hujja. A yanzu mutane uku ne a target dinta, Alhaji Muhammad Jadda, wnada take kokarin tsara shi su tafi India wurin jinyar kafarshi, Tafida wanda tasan hankalinsa yanzu ya rabu gida biyu, sai Deen wnada shi tasan baya kasar, a gefe guda Abubakar Yayansu Tafida tana ta cusa mishi kiyayar da suka kasa nasara akan Tafida tana nuna mishi idan ma bai farka ba, tow ya farka domin kiri-kiri Alhaji Muhammad Jadda ya fifita Aliyu akansu, tayi tayi ta samu kan Umar sai aka yi dace shi bai da lokacin irin wannan abin domin hanyar da Tafida yayi mishi tun kafin ya zama gwamna yake cikin arzikinsa sannan ai ba kowa ake haifa don ya samu yadda yake so ba, tana fara magana yake cewa ta bar zancen Aliyu ya cancanci zama wani abu tunda Abba yaki siyasa ba laifi don Aliyu yayi, shi kuma Abubakar kasancewar shi me sanyi amma irin Mutanen nan da matukar suka samu wuri ba kananun munafukai ba ne,, dama haka yanayinsa yake, kuma kyashi yasa yake ganin kamar yadda ta fada haka ne. Haka yasa take kara munana mishi Tafida da Abba, me yasa ya nimawa Tafida Auren Ummu? Don yafi son shi, me yasa ya tsayawa Tafida ya zama gwamna saboda ya fi sonshi, su kamar ba haihuwarsu yayi ba, ya fifita tafida akansu. Hajiya Kaltuma shaidaniya ce da babu wanda zai yarda zata iya aikata wani abu saboda irin mutanen nan masu zafin nime, haka yasa ta dan b'ata cikin rububi. Duk da wannan abun da take, tana bala'in son Saadiya don ita ta mallaka, Mahaifin sadiya a Saudiya suka hadu ya tafi Umara shi kuma ɗan Bengaladash ne,.haka yasa suka kulla alaka har suka rabu bata san tana da cikin Sadiya ba, koda Maman Nabilah ta sani ta bata shawara a zubar amma taki, saboda bata taɓa haihuwa ba sai akan Sa'adiyya, ta kuma ji a ranta tana bala'in yarta guda daya nan, kamar tsoka daya a miya, Hatta karatu da kome ta kashewa Saadiya kudi tayi amma yarinyar nan dakyar ta gama diploma, ta kama iskanci kamar karya domin karya tafi Saadiya kunya, sai dai Babban kuskuren da tayi na barin Saadiya su kula yarjejeniyar raba Ummu da Tafida, Saboda Tafi da ya farka daga barcin da yake,.ta kuma fara ta kan Sa'adiyya. Wannan kenan! ** *Ummu* A kusan sati biyar kenan da barin da nayi, wanda yayi daidai da sati biyu da fara aikina a hotel din garin Maiduguri na girki, wani abu daya da yake damuna, yawan kumburi kafaffuna sai suyi ta kumburi, ina ga ko yawan tsayuwar da nake ne, amma abin yana damuna..... 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 59 Nafi bawa zuciyata yawan tsayuwar da nake ne, haka yasa na dan nime kujera na zauna ina kallon girkin da wasu samari uku da suke taya ni aiki. "Aunty Baby!" Daya daga cikin samarin nayi, ina kallon dayan yana tab'a shi. "Wai da gaske gwamnan garin nan ne Mijinki?" Murmushi na, na ce musu. "A'a!" "Aunty Baby ina da hotonku na last year fa gashi." Sauka nayi akan kujeran na nufi wurin abincin na juye, shiga kwashewa ina dauke kai na domin basu rabuwa da abin dariya. Haka na gama abincin aka wuce da shi wurin da ake sayarwa, sannan na dauki kayana na fita. Ina musu sallama, Saddam ya kalli abokinsa. "Da gaske Matarshi ce?" "Wallahi Maaruf Matarshi ce, don na kara gaya maka matar gwamna ce." "Shi ne nake jin ana gulmar a wurin MD. Ban da shima Gwamna bai da lissafi taya zai rabu da wannan abin. Mai daraja a kullum na kai abincin da ya rage gida Mamana sai tambaye ni waye yake girki nan ko nice? Hmmm bata san wata guruwa ce take aikin ba!" Muna isa gida na fita na gyara zaman nikaf dina, don garin yayi duhu kasancewar damina da aka shiga. Kusan kwanaki uku ana wani irin zafi me shiga jiki kamar kayi yawo tsirara, unguwarmu an shiga sallah babu jama'a sosai, haka yasa na shiga cikin gidan da sauri. Har ina tuntube domin an fara yayyafi ne, ajiyar zuciya na sauke lokacin da na shiga tsakar gidan mu, "sannunku da gida!" "Aunty Baby kin dawo lafiya?" Ajiye jakar nayi na dauki Mufid da yake wasa a saman gado. "My papa kana lafiya? Uwani lafiya lau?" Na fada ina kallon Mama da take sallah, tashi nayi na shiga ban dakin da yake cikin dakin nayi alola ma fito na tadda sallah. Ina idarwa Mama tana bawa Mufid abinci, "Mama Kulsum ta ce tana hanya tun safe bata iso ba ne?" Tab'e baki tayi tana faɗin. "Ta sauka gidan Uban Mijinta!" "Ai na zata anan ne masaukinta!" "Eh wai sai ta ga jikokinsa!" Ta fada tana bashi tuwon laushi miyar kubewa. "Mama!" "Na'am, ya ya dai?" "Kawai na gaji ne?" "Kwanta Uwani ta miki tausa!" "Tow!" Ai kuwa ta kira Uwani, ta shigo ta cab'a kwalliya zata hira, ruwa ya sauko kamar da bakin kwarya. "Mama kina kira na ne?" "Eh dama Ummu zaki yiwa tausa!" "Aikin kenan gaskiya Mama a sake lale ta koma gidan Aliyu kawai!" Kai mata duka nayi ta goce, "bana son tausar jeki kawai!" Tura baki tayi tana faɗin. "Wallahi bata san waye zata aura nan gaba ba, sannan shima kuma bata san meye matsalarshi ba, matsalar Tafida kishi ne idan tayi hakuri zai wuce. Kinga a ce tana gidanta zata samu masu kula da lamarinta Mama ko duba lamarin nan!" Shiru duk muka yi kafin ya cigaba da cewa. "Ban yi auren nan ba amma nasan wallahi ni ba zan iya matsawa a gidan aurena ba sai ya zama dole, ai Aunty Baby da Tafida sun zama ɗan juma da ɗan jumai, kamata yayi su kashe su rufe babu wanda ya sani amma lokaci guda kome ya tafi." Ta saka kai ta fita, "ki cigaba da addu'a, mu gayawa Allah kukanmu!" Ni dai bana jin akwai wata mafita akan Aliyu domin na yau ya saba min abinda yayi ba, da babu shi a rayuwata sai nake jin kamar sauki da sassauci da zan tarar zamanmu, kawai ka gaji da fitinar danginsa. Sallah isha nayi ban sake na ci wani abu ba sai bayan na idar, sannan na aka kawo min abinci na fara ci ina duba girkin mu na gobe idan Allah ya kai mu, ko da dare yayi na kwanta amma na kasa barci, sai juyi nake kusan karfe biyu na samu barci yayi gaba da ni. *** *Hajiya Kaltuma* Wani mari ta kifawa Shuwa sai da ta zube, ta kara binta da wani marin sai da ta kifa sosai, bakinta a fashe ta ce mata. "Kin ji zafi ne? Kin ji bakin ciki ne? Ki godewa Allah da bata san wacece ke ba, ina ganin da mutuwa zata yi, ina son nawa Yar kika kashe min, waye kike tsammanin ba zai iya daukar fansa ba? Idan kin isa ki samu Aliyu da kanshi ai shi ya kawo ta a haka!" Lumshe idanunta tayi tana murmushi, cikin muryanta me sanyi da ya bi jikinta wanda wannan sanyin nata yake kara jadaddawa mutane cewar ita mutuniyar kirki ce ta ce mata. "Aliyu ina mishi tanadin da zan bashi, a matsayinshi na surukina! Ke kuma kanwata ce da dole na gaya miki gaskiya idan Halimatu bata farka lafiya ba, Samha, Dalal, Muhammad. Zan basu kyautar shinkafar bera a matsayin abincin break." Ta fada tana murmushi irin wanda ake cusawa mutum tsoro me razanarwa da tabbatar da aikata wani abu. "Gaya min me kike buƙata don Allah ban da Yarana don Allah!" Ta fada tana kuka tare da haɗa hannunta tana kuka me ban tausayi, ita duk rashin mutuncinta, tasan limit dinta. Murmushin mugunta tayi mata. "Kinsan yadda zaki yi ta farka akwai magana a bakinta, domin an gaya min tana fadar cewa lafiyarta lau! Haka na nufin akwai wani abu a kasa." "Na ji me kike bukata?" Inji Hindu. "Ta dawo karkashin kulawar mu!" "An gama in sha Allah!" Yatsa biyu ta nuna mata idanunta. "Ina kallonki duk abinda zaki yi!" "Amma ciwon Saadiyyah turen Aljanu ne!" "Haka yasa nake kokarin na nima mata lafiya!" Ta fada babu wasa a maganarta. Sannan ta mike tana faɗin. "Na gaya miki, ki fahimci yadda zaki yi da ita ta bar asibitin ko kuma a jin wani labarin ba wannan ba." Ta fada tana barin wurin, wani irin tsoro ne ya kamata tayi ta kuka, Yaranta me suka yi? Da zasu fuskanci izayar Kaltuma? Zuwa yanzu ma bata isa ta ce zata d'aga mata murya ba. Domin a banza zata cutar da ita ciki da waje. Kuma gefen Kaltuma tasan duk abinda zata yi Hindu ba zata tab'a bude baki tayi magana ba, domin tun fil azal ta cusa mata tsoronta yadda ko tari tayi tasan me take nufi, duk iskancin Hindu tana da tsoro. Bambancinta da Kaltuma bata da tsoro ita kome nata a sanyayye take yin shi idan da zaka saka mata hannu a baki ba zaka yarda zata ciza ba, amma fa gara Shuwa Hindu da take hayagagga. ** Washi gari. Tun bayan sallah asuba, Hindu take ruwan bala'i ita a kira Aliyu a sauyawa Sa'adiyya asibiti, koda aka kira Aliyu wayar a kashe, haka yasa ta hana kowa sakat ta tashi hankalin kowa ta hana kowa hutawa, har majinyatar da suke bangaren. Wurin karfe goma aka samu damar kiran Tafida, aka gaya mishi. Ya ce musu kada a fara sauya mata asibiti a barta zai turo jami'an tsaro a kara killace first lady, a cigaba da kula da ita kawai. Gaya mata likitan yayi abin da Aliyu ya ce, ihu ta saka tana faɗin. "Wallahi sai kun bar min Y'ata!" Yadda take ihun yasa aka fitar ita saboda wasu masu laluran haukar suna kokarin tayata ihu. -- Aikin da yake gabanshi yasa bai san an shigo ba, domin ba karamin dauki babu dad'i aka yi kafin Mahmoud ya samu shiga cikin gidan Tafida ba, yana shigowa kuwa jami'an tsaro na biyo shi, d'ago kai yayi ya kalle su, murmushi yayi musu ya ce. "Ku je!" "Sir ya karya gate din?" "Ba kome ku je!" Fita suka yi, ya zubawa Tafida idanu. "Kana tsammanin na hakura da Ummu ne?" Bai ce mishi uffan ba, ya cigaba da aikinsa. "Tana girki a hotel ko? Waye ya sani ko..." juyawa yayi ya sake murmushi yana faɗin. "kada ka damu ko me take aikatawa ina nan kara sonta. Saboda Mahaifinta da Mahaifiyarta ba mutanen banza ba ne, haka zalika mahaifina da Mahaifiyata, ba mutanen banza ba ne, kai karewa ban tab'a jin ko a tarihin gwagwarmayar rayuwa Abba yayi abin da zai bata mishi suna ba, sannan ko a mafarki ba za a tab'a samun Uban da yake da tsoron Allah irinsa ba, ka ga kenan Alhamdulillahi da samun iyaye na gari, ina ga Abbi bai tab'a baka labarin na kama shi da Hajja kanwar Deen ba ko?" A fusace ya tako har inda Tafida ya ci kwalarshi yana huci. "Akuyanci a jininku yake fa, malam na san wacece na aura shi yasa yanxu ko a gidan karuwai xata yi aiki ina tayata murna." "Kada ka zagi iyayena! Kada ka sake ka zagi iyayena!" Ya d'aga hannu da niyyar kaiwa Tafida naushi, ya rike hannun. "kai ma kasan tun Muna yara ban tab'a tsoron fada ba, ni rigima da sayarta a jinina take, bari na maka dukan abin da ka aikawa Ummu!" Tafida yayi sama da shi ta buga da kasa. Yadda kasan dan dambe haka yayi ta sokawa Mahmoud duka kamar zai kashe shi. Sai da ya sumar dashi sannan ya watsa mishi ruwa bayan ya saka shi a gaba ya fita. Yana dingishi. Sai da ya bar unguwar sannan ya kira Tafida. "Ina tayaka murna, an jima za a gaya maka kyakkyawar labarin Daf ta murkushe waye ma?" Ya kwashe da dariya, shima Dariya Tafida yayi ya ce mishi. "Abokina! Ka fara tunanin kanka, kasan me yasa na hana a kamaka? Saboda bana son a zarge ni, sannan bana son a gano cewa akwai matsala a tarayyarmu shi yasa da kayi min iskanci na kyale ka, amma yanzu na tayaka murna kafin su masu shirin murkushe ta su yi aiki bari na baka labari me dadi, gobe an samu motar Mahmoud tsohon Kwamishina yayi hatsari motar ta kome" aikuwa Tafida na rufe baki wasu mutane da bakaken kaya, suka shiga motar, yana ihu yana kome. Ban daki Tafida ya shiga, ya sakarwa kanshi ruwan sanyi,.yana tuno yadda Ummu tayi ta kuka ranar da yazo daga abuja zai mai da ita ta, yana jin kukan a ranshi amma ya share wani irin yanayi ne haka ya ke ji sama da kullum, yana son Ummu amma me yasa mutane basu son zaman shi da Ummu? Sai da ya jika kayanshi sannan ya cire, ya ajiye sannan ya wuce dakin ya sauya kaya ya nufi bangaren Hajiya ya zauna yana kallon yadda take gyangyadi akan kujerar wheelchair. Tashi yayi ya dawo parlour yaran Maryam ne da suka.tafi wai gaida Saadiya. Bangaren Asiyah ya shiga ya ji bata parlour ya nufi dakinta. Kwalben syrup ne tana sha a hankali kwance. Murmushi yayi ya ɗan tab'a ta da sauri ta shiga tattarawa tana kokarin boyewa. "Ina zaki kai?" "Babu wai kada ka gani ne, ka ji haushi." "A'a ba zanji haushi ba saboda wannan path dinki ne da kika zab'a, ba nawa ba." Sunkuyar da kai yayi kafin ya ce mata. "Zan baki shawara daya ne idan kin ji tow, idan baki ji ba zan barki a yadda kika so amma xan daura ki akan wani layi daya. Kawo kunnenki!" Mika mishi tayi ya gaya mata shi ya haukar da saadiya, idan bata yarda ba ga wayar shi ta gani akwai video ɗin. Bude video yayi ya nuna mata a yadda kome ya faru, zubewa tayi akan gwiwarta. "Me kake so?" Murmushi yayi ya ce mata. "Good girl! Kada na kara ganin kwalaben syrup a gidana idan ba haka ba, ke xan hadaki da hukumar NDLA su kama min ke su rufe har abada." Fashewa da kuka tayi tana rokonshi da Allah ba zata kuma ba, ya gyara zama ya shiga mata tambayoyi tana bashi amsa, yana rubutawa a wayarshi har suka gama magana ya kalleta da kyauta kafin ya ce mata. "me yasa kuka yiwa Ummu asiri?" "Saboda na aure.ka ne?" Kwashe ta yayi da mari sai da ta zube. "Bana gaya miki bana sonki ba?" "Eh ka faɗa," "tow ana dole ne?" "Na tuba!" Ta fada tana kuka. "Me kike shiryawa keda Uwarki?" Girgiza kai tayi tana faɗin. "Na rantse da Allah bamu shirya kome ba, ni zamana a gidanka yafi min kome kwanciyar hankali!" D'aga hannu yayi kamar zai mare ta,.ta kame kanta tana faɗin. "Wallahi ban yi kome ba, sai dai akwai wani mutum da yake kirana a waya ya ce na bashi hadin kai zai na turo min syrup ban san waye ba ne kawai shima nayi mishi nashi aikin idan bukatar haka ta taso, Ni na san nayi.rashin ji kuma ina kai amma ba zan kuma cutar da wani ba, nayi alƙawarin haka tun bayan an daura min aurenka iya gaskiyar da na gaya maka kenan!" "Maza nawa kika yi mu'amala da su?" Wani irin tsoro ne ya cikata, ta rufe bakinta ta fashe da kuka ta ce mishi. "Bansan iya adadin su ba, don Allah kayi hakuri." Amsar wayarta yayi ya mike zai fita. "Asiya idan na gano kina cin amanata me xan miki?" Kai tsaye ta ce mishi. "Ka kashe ni domin bani da amfani!" Murmushi yayi yana faɗin. "Good girl!" Ya fita da wayar ..... 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 60 Har ya fita ya kuma dawowa da baya ya kalleta, "idan na kara zuwa na samu kina make, tow abin da zan aikata." Wani d'aga idanu yayi ya kalle ta, da sauri ta kwashe kwalaben ta kai ban daki, sannan ta fito tana sake fito da wasu tana zuwa ta zubar da syrup din, murmushi yayi yana faɗin. "Kina jin magana! Ke?" "Na'am!" Ta fada da sauri tana komawa can gefe, "waye ni?" "YA Tafida?" "Sai kuma me?" "Gwamnan Maiduguri!" "Kina nufin duk abin da na yi babu wanda zai damu ko?" Gyada kai tayi tana kara k'amkame jikinta. "Good girl! Dole ma na baki kyauta me kyau kina da babban kai, idan naji wani abu ya fita!" "Ka kashe ni kawai!" "Me yasa kike tunanin na kashe ki?" Zubewa tayi akan gwiwarta, "Mutuwar zata min sauki akan irin na Saadiya!" "Waw shi kenan yar albarka!" Ya saka kai ya fita ya barta nan tana kuka, ita dai yanzu ta hango matsalar auren Tafida, na farko bata same shi ba, na biyu bata samu nutsuwa da gidanta ba, na Uku ga Mamanta ta matsa mata tayi ciki, ko da Uban me zata yi ciki bayan kowa yasan yadda syrup yake lalata mahaifa. Bata mantawa wani rashin lafiyar da tayi sai da likitan yayi mata fada ta kiyaye mahaifarta zai iya lalacewa, amma taki ji domin ji take kamar karya yaƙe mata, mata sai da tayi ciki da wani saurayinta, aka zo cire cikin haka ya ciro da mahaifarta kamar zata mutu lokacin, ko uwar bata san me ya faru da ita ba, saboda sakaci irin na Uwarta, haka yasa tayi ta jinya daga asibiti zuwa gida, har ta warke. Hajiya Turai bata taɓa sanin haka ya faru ba, damuwata kada yarinyar ta bukaci wani abu duk da Allah ya horo mata amma a duniya ta tsani a tambaye ta kuɗi ko wani abu yanzu zata fara ruwan masifa, ita bata son ana tambayar kudi. --- A bangaren Tafida tunda ya amshi wayarta yayi ya bincike sosai, amma bai ga wani abu ba, haka yasa shi ya kyale wayar. Washi gari tun asuba Abba ya kira shi, yana ɗauka ya gaishe shi yana tambayar shi ya mutanen gidan. "Alhamdulillahi, Aliyu kana duba Ummu kuwa?" "Eh Abba!" "Kaltuma ta damu sosai akan Ummu da Yaran, ta ce jibi zata je duba su." "Allah sarki, gashi kuwa basu garin domin sun yi tafiya!" "Tow Masha Allah, Ubangiji ya dawo da su lafiya!" "Amin Ya Allah, idan ka samu lokaci kazo ina son magana da kai akan matarka!" "Tow ba damuwa Abba zan zo in sha Allah!" "Ya Asiyah?" "Tana lafiya!" Ya fada , "tow bari na barka haka kada na cinye maka lokaci!" Abba na ajiye wayar da sauri ya fito daga dakin shi ya nufi waje lokacin karfe biyar da minti arba'in da shida, shida tai mishi a kofar gidansu Ummu, a kofar gidan ya samu Alhaji Bulama. Gaishe shi yayi sannan ya ce mishi. "Nazo wurin Mama ne!" Tana cikin gidan bari na mata magana. " A tare suka shiga, security da suka biyo shi sun harde cikin bakaken kaya sai zare idanun suke. A parlourn Alhaji Bulama ya zauna yana jiran Mama can kuwa sai gata ta zo, har kasa ya gaishe ta. "Barka da asuba!" "Yawwa Barka dai!" Shiru yayi kafin ya ce mata. "Mama !" "Na'am!" Ya rasa yadda zai yi kafin ya ce mata. "Ba don buƙatar kaina ba, nazo ne nan girma da darajar Ummu, don Allah ki bani aronta." Kallonshi tayi iyakar kokarinta naso gano wani abu bata gani ba, murmushi tayi sannan ta ce mishi. "Na baka, amma kasan babu wani abu a tare da." "Na sani! Kawai ita zaki bani!" "Shi kenan! An jima kazo ka ɗauke ta." "Za a zo a dauke ta in sha Allah karfe tara na safen yau!" "Allah ya amince!" Daga haka yayi musu sallama, sannan ya juya ya bar gidan, sai da ya shiga motarshi sannan ya kira Deen yana ɗauka ya ce mishi. "Shegen sama ina ka ajiye Mahmoud?" "Yanzu ba shine matsalar ba, Kaltuma ta tambayi Abba ina Ummu take? Ni kuma na ce musu sun yi tafiya!" Dariya Deen yayi ya ce mishi. "A yanzu da kasan wacece ita, babu amfanin gudun ta domin zata iya fara farautar rayuwarka ne, sannan zata na bibiyar duk wanda ta san kana da alaka da shi, abin da zan maka shine mutanen da idan suka san mayye na gida, sukan dauki amanar dansu su bawa mayyen ka san me yasa suke haka?" "Saboda kare rayuwarshi, idan ka dauko Ummu Hadiyya ka hadata da Kaltuma, sannan itama Ummun ka saka security suna tare da ita sai ka rufe kofar barnan Kaltuma, idan kuma ka sake Kaltuma ta riga ka yanke hukuncin bibiyarka baka da lokacin da zaka iya taimakawa kanka balle Ummu, kashin bayan Kaltuma Mahmoud ne kuma ka.saka an rufe shi kaga kenan babu amfanin tai yaki ita yanzu babban damuwarta Yarta da Mahmoud sune suka dan sirrinta shi yasa zata fara kokarin fitar da kanta kafin kai ka fitar da ita." "Ina ga gara Ummu ta tafi wurin Mahaifinta zai fi sauki, Mahaukaciya ce Kaltuma tsawon shekaru talatin tana buga game a nutse gaya min yaushe zata sake ta rike Ummu kai kada ka manta Sa'adiyya tana nan ita ba me hankali ba, ita ba Mahaukaciya ba, idan na sake wani abuna me daraja ya isa hannunta zata iya amfani dashi wurin yaki da ni, kada ka manta siyasa na karanta idan na bada kofa kowa ma zai cutar da ni, aka cutar da Ummu kamar ni aka cutar." Har ya isa gida maganar yake, ɓangaren Asiyah ya shiga ya samu tana ta barci, maka mata duka yayi a cinya ta farka tana zare idanu. "Kin yi sallah?" Zare ido tayi tana kallon agogon dakin. "Yanzu zan yi?" Ta fada tana sauka a gadon, "ke!" "Na'am!" "Kina ma sallah kuwa?" "Ina yi amma ba kullum ba. Sallah safe nake da ta isha!" Shiru yayi yana kallon yadda take kokarin fadar gaskiya abu daya ya sani ba zai iya zama da Asiya ba, koda bata lalace ba ba zai iya ba Allah ya gani yana da mugun kishi, da yasa ko bazawara ba zai iya aura ba! Don idan ya tuna da ta mu'amalanci wani namijin mutuwa zai yi, "Kina azumi?" Girgiza kai tayi tana zare idanu. "Bar zare min ido nima idanun nan ina dasu, yi kasa da kai kafin na kwashe ki! Kuma na gaya miki daga yau sallah biyar nan dake za ayi shi, sakarya kawai haka ake zaman auren babu Allah cikinsa ai kamar tafiya a sahara ce babu ruwan sha. Don haka ya kara tabbatar mata da cewa matukar tana son zaman lafiya tana sallah, haka taje tai alolan kamar ta yara, ya tambaye ta. "raka'a nawa ake yi a sallah safe?" Shiru tayi tana kallon ƙasa. Cizon lips dinsa yayi kamar ya fashe da kuka, "Asiyah?" "Na'am!" Ta amsa mishi tana kallonshi, hawaye na zuba mata. "Baki san raka'a nawa ake a sallah asuba ba?" Gyada kai tayi tana wasa da hannunta. "Ok raka'a biyu ne!" "Tow na gode!" Haka ta shimfida abin sallah, sannan ta tadda sallah, yadda ta fara dungura sallar yasa shi girgiza babu karatu babu kome sallah kawai take bankawa kamar me shirin tashi sama. Kafin tayi sallama. "Ke aka ake sallah?" Sai ta diririce domin yadda ya mata maganar kamar zata suma ta ji. "Ina jinki haka ake sallah?" Fashewa da kuka tayi tana faɗin. "Wallahi ban iya ba, ban san yadda ake sallah ba don Allah ka yi hakuri zan gyara kada ka min fada, yana sani jin kamar na sha wani abu, na yi ta barci." Ba zai ce yana son Asiyah ba, amma tausayinta ya dame shi, abinda Maman Ummu Hadiyya tayi ba karamin kokari tayi ba na rike babbar yarta mace har tsawon 26yrs ba sauki a cikinsa, wani mahaukacin kaunar Ummu yana huddaa duk wani sako da lungu na zuciyarshi, Ummu ta cancanci ya sota ko don fadi tashin da Mama tayi akanta na bata tarbiyya, haka kawai yaji a duniya bai da wacce ya yarda da ita kamar Maman Ummu Hadiyya ba. Don haka ya fita yana hararan Asiyah, dakinshi ya nufa ya kirata, shiru yayi kafin ya ce mata. "Mama Ina son Ummu!.......(Hmm Allah mu tsaya sosai akan tarbiyyar yaranmu da gina su tafarkin addinin Muslunci, da ciwo sosai a wayi gari yarka bata san kome akan addini ba. Mu koya musu tun suna kanana domin su tashi da shi a jikinsu da jininsu. Allah ka shirya mana zuriarmu bakiɗaya..https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 61 "Eh Tafida kowa ma yasan kana son Ummu, amma me yasa rayuwar Ummu take samun tangard'a da kai? Kazo kace min na baka Ummu ni ai ba mahaukaciya ba ce,da zan ɗauki Ummu na mika maka don ban da lissafi, don Allah kada ka kara zuwa Ummu ta ce ba zata bika ba, kuma ban ga laifinta taya haka kawai bayan ka gama azabtar da zuciyarta zaka dibo jiki kace na baka Ummu irin ban san darajarta ba, Hmm kayi duk yadda kake so Amma ba zan baka Ummu ba idan ba baka Ummu kamar ban san ciwonta ba ne, gara nayi ta kallonta a gabana yafi sauki na baka ita, irin ga ka idan kace ayi ayi idan kace kada ayi eh kada ayi. Ina jin kunyarka ne saboda zuriar da yake tsakaninku, idan ba haka ba sai na mata terere, kada ka ƙara samun Alhaji Bulama da zancen Ummu, kasan kana sonta ka zargeta zata ci amanarka." Lumshe idanunshi yayi yana jin kamar yayi kuka. "Mama rayuwarta!" "Tun fil azal rayuwarta da ƙaddaranta a rubuce suke, idan ka nace zan yi kar'arka." Tana gama fadar haka ta kashe wayar, dafe kanshi yayi kamar yayi ta ihu, haka ya mike zuwa ban daki yayi wanka, yana shiryawa ya kira Deen yana gaya mishi yadda suka yi da Mama, murmushi Deen yayi yana . "Nasan haka zai faru. Mama tana da hakuri amma kuma ba zata yarda kai ta wasa da rayuwar Ummu ba, idan ka duba condition din Ummu bata bukatar damuwa ko kad'an. Don Allah ka kyaleta." "Na ji me zan yi don kada Kaltuma ta waiwaye su!" Ka gaya musu kana sane da wasu na bibiyar rayuwarka idan shi yasa baka son barin Saadiya domin kada a yi mata wani abu!" Shiru yayi kafin ya ce mishi. "A'a zan yi wani abu dai amma na fito na nuna haka, shima jefa na kusa da ni nayi cikin hatsari." Ya fada yana zuwa ruwa a kofin tea. "Tafida rayuwarka ita ce me muhimmanci!" Murmushi yayi yana faɗin. "Na san da haka!" "Ka kula don Allah!" "In sha Allah! Ka gaida Amma da Madam!" Ya kashe wayarshi. Kallon wayarshi yayi kafin ya lalubi number MD na hotel din da Ummu take aiki, wanda tun ranar da ta fara aiki aka.tura mishi numbersa, ya share don ya fahimci ita ta ce ta zabi hakan. Kiran shi yayi kamar ba zai dauka ba, sai ya ɗauka yana faɗin. "Hello waye? Aliyu Muhammad Jadda ne, ka sallami Ummu Hadiyya kafin ta fito daga cikin gidansu, Umarni ne!" "In sha Allah yallabai, yanzu ma!" Kashe wayar yayi ya kira Ummu Hadiyya. *Ummu Hadiyya* Duk da ina kokarin dauke kai akan kome amma wannan karon, da Mama ta ce min Tafida yazo ya ce ta bashi ni aro sai naga kamar ya rena ni ne, ko ya mai dani baiwarshi, idan ba haka ba me yake nufi da ni? Da zai ce lallai Mama ta bashi kamar irin bani da daraja,.tana faɗin na fashe da kuka ina faɗin. "Kuma sai na bishi mutumin nan da ya ce yana tantamar ko ina mummunar alaka da abokinsa bai tuna yadda ya same ni da kimata da darajata ba , shine ya zo nima na zaki ce mishi tow Mama idan baki bukatar na zauna da ke zan koma wurin Babana!" Na fada ina kuka, sai jikinta yayi sanyi domin har ina fahimtar haka, "Ya isa haka ba sai kin je ko ina ba, babu abinda zai kara faruwa." Ina cikin kukan ya kirata, abin bai bani mamaki ba amma kuma yadda ta wanke shi ya fi kome min dadi don haka na kwanta ina sauke ajiyar zuciya. Ina cikin damuwa sosai, ban gama fita daga wannan ba sai wani ya kuno min kai, kiran MD dinmu yasa na bude idanuna. Daukar kiran nayi na ce mishi. "Yallabai gani nan zuwa!" "No need, ki zauna kawai mun samu wani daga abuja!" "Laifin me nayi?" Shiru yayi kafin ya ce min. "Kin gane ko Ummu Hadiyya, ke matar aure ce kuma idan aka ga kina zuwa nan ba zaa yi tsammanin aiki kike ki tuna kina y'a mace sannan kuma duk wanda ya ji Mijinki ne His Excellency kin gane!" "Tabbas ban gane ba, wani ne ya maka barazana!" "A'a mutuncinki nake son karewa Please kada ki girmama al'amarin. Allah ya baki hakuri!" Ban san lokacin da na fashe da kuka, ina faɗin. "Tow me yasa?" Na kara fashewa da kuka me yasa sai ni? Shigowa Mama tayi tana kallon yadda nake kuka, raina yayi bala'in b'aci. "Kukan na me?" "An sallame ni a wurin aikina ne" "Allah ya haka shine mafi alkhairi!" Daga haka ta fita, sai yanzu na gane Mama itama bata murna da aikina. Haka yasa tunda na fara take mita ita bata ki na bude gidan abincina na kaina ba, amma wannan yawon da nake ita sam bai mata. Kwana biyu na kwashe ko waje ban leka ba, haka yasa na samu natsuwa amma kuma zuciyata a kuntacce nake, ** Tafida Duk yadda yaso ya rage aikin gabanshi, sai ya ga kamar kara tula mishi ake, ga shi yana son ganin Abba da ya ce ya zo, ko jiya sai da Malam Zailani ya kira shi, suka gaisa yake tambayarshi ya aiki , ya kuma tambaye shi Ummu daga nan ya ce ta cigaba da hakuri kome yayi tsannani maganinsa Allah, ajiyar zuciya ya sauke yana kallon hoton Yaranshi cikin so da kauna. Kiran Abba ne ya shigo mishi ya ɗauka. "Aliyu nace ina son ganinka, amma har yanzu shiru!" "Kayi hakuri Abba, in sha Allah bayan isha zan zo!" Ya fada yana jin alamar ana kiranshi. Fanna, gabanshi ne ya fadi ya ce. "Abba bari na amsa kiran Fanna!" Kashe wayar Abba yayi ya dauki na fanna. "Don Allah kayi kazo kazo don Allah, Hajiya ta fadi ban san me ya same ta ba!" "Ki fita waje ki gaya musu, kada ki bata lokaci." Ya fada da karfi, sannan ya fita da sauri, har yana tuntube, security na ganinshi suka bude mishi kofa ya shiga. Yadda yake musu magana yasa suka fahimci saurin da yake, a lokacin da suka isa gidan Hajiya babu kanta, haka suka wuce da ita asibiti. Aka shiga bata taimakon gaggawa, Allah cikin ikonsa ta farfaɗo. Ta samu barci, wannan abin ya faru Maryam tana gidan tana barcinta, domin rufe kofarta tayi saboda Hajiya ta mata faɗa akan ta koma dakinta kan Yaranta yafi zaman da suke a nan gidan Tafida, domin ba tsinanan kome take ba. Abin da ya faru kuwa har yasa Hajiya magana, Matar da mijinta ya aura bayan mutuwar aurensu, suka hadu da kannenta da wasu kannen mijin suka yiwa yarta Naziha shegen duka, wanda ya kai Yarinyar suma, da ya koma gida Matarshi ta ce rashin kunya ta mata, shi kuma ranshi ya b'aci ya sake yiwa Naziha dukan da yafi na da sai da ya karya mata hannu. Shine yarinyar ta kira Maman tana kuka, don Allah ta dawo zasu kashe ta, a madadin ta fuskancin halin da yarta take ciki a'a kawai sai ta fara fada da ciwa a kashe ta mana, ita ina ruwanta an san uwa da tausayi amma Maryam ta kasa fahimtar ita ce matsalar Yaranta. Jin haka yasa Hajiya mata faɗa da ta je ta ga yarta amma taki kamar bata san Hajiya na magana ba, wannan takaicin yasa jinin Hajiya yayi mugun hawa. Da ciwo dan da ka haifa ya nuna ya fi karfinka. Bakiɗaya Hajiya tana ganin kamar abin da ya faru laifinta ne, shi yasa rayuwar Yaranta ya zama haka. Yana zaune likitan yana mishi bayani, shiru yayi yana jin shi. "Yallabai Hajiya tana bukatar hutu da nutsuwa, idan aka cigaba da haka wata rana jininta yana iya tab'a zuciya ko kwakwalwarta, don Allah a kula da ita." Jinjina kai yayi yana jin likitan, mikewa yayi yana fada a ranshi. "dole ya saka a sallame Sa'adiyya!" Bangaren Saadiya ya nufa bayan ya bar office din likitan ya samu Hajiya Kaltuma a wurin an hanata shiga, murmushi yayi mata sannan aka bude mishi kofar wata yar sanda mace. Shiga yayi ya ga saadiya tayi shiru, kamar tana nazarin wani abu. "Baby!" Da sauri ta d'ago kai tana kallonshi a tsorace. "Muje gida ko?" Idanunta ne ya cika da kwalla bakinta yana rawa yake girgiza mishi kai. "Babu abinda zan miki muje babu abinda zan miki!" "Don Allah ka bar ni zan tafi ba zan tsaya ba!" "Tow zuwa an jima zan saka a sallame ki!" Ya mike tare da barin dakin tana rokonshi, juyawa yayi ya kalleta. "Shiii! Kada kowa ya fahimci haka idan ba haka ba, zaki ta zama a nan baki warke ba!" Zubewa tayi akan gwiwarta tana kuka tare da faɗin. "wallahi ba zan faɗa kome ba!" Murmushi yayi yana barin dakin. Gida ya koma ya sauya kaya bayan sallah isha ya isa gidan Abba, yadda ya ga Kaltuma tana drama take, Hindu kuwa kuka take tana faɗin a bata yarta. "Kai ma Aliyu sai kace dole ka sake mata yarta ka huta." "Ko na sake ta ba zan huta ba, domin kuwa nasan rayuwar Sa'adiyya yana cikin hatsari!" "Me ka ce?" Abba ya tambaye shi. Gyara zama yayi yana faɗin. "Abba mafi alkhairi a bar min Saadiya a tare da ni, domin kuwa yau ta gaya min wai akwai masu bin ta zasu kashe ta, naso tayi min bayani amma taki gaya min, ta ce min ita a yanzu tafi sha'awar Mutuwa da rayuwa, haka yasa nake ganin kada a dawo da ita nan, a barta a can ni zan ji da kome. Ban san me yasa aka koma kanta ba, idan ma ni ake hari ba gani ba, a kashe ni mana sai a koma kan matata na rasa Ummu Hadiyya yanxu itama wacce nake farin cikin ina tare da ita ana shirin raba ni da ita!" Yayi kasa da kansa yana share kwalla, alamar yana kuka. "Tow Hindu Kun dai ji ko? Ba zai barta ta yi nisa da shi ba, tunda yana kula da ita don Allah ku bar mishi kome Allah ya bata lafiya!" Kuka Shuwa ta sake tana faɗin. "A'a ya sake min ita don Allah ya sake min ita!" Yadda take kuka da ihu, yasa shi kallon Kaltuma da take ta ciwon bakinta,alamar ranta yayi bala'in b'aci. Murmushi yayi ya ce musu. "Don Allah ku yarda da ni,ku bar min ita a wurina in sha Allah babu abin da zai faru da ita, zan bata kariya kamar yadda zan bawa kaina!" Daga haka yayi shiru yana rufe fuskarshi da tafin hannunshi. Yana kallon yadda Kaltuma take kallon shuwa. *** *Ummu* Ihun Ummi ya tashe mu daga barcin da nake na bude idanuna. "Ni zaki kunyata ki dauko min abin kunya Safina? Mijinki a hotel ya ce ya ganki ni wallahi baki isa ki kunsa min abin kunya ko na bakinciki ba" kafin ta fashe da wani irin kuka, ina kwance a wurin cikin damuwa da tashin hankali, wanda ya hadu min guda biyu, domin ina kwance nan jin wani abu nayi kamar ya wulga a cikina. Sake jin wulgawar haka yasa na rike zanin gadon, ina zare idanu. Da sauri na mike ina raruman wayata, jikina yana rawa na shiga niman number Sagir bugu daya yayi ya ɗauka. "Kazo ka duba ni don Allah!" Na fada kamar zan mutu don bakinciki. "Ok!" Kashe kiran nayi na zubawa kofar dakin idanu duk da dare ne, amma yadda ake hayaniya a gidan ya d'aga min hankali, karshe Mama shigowa tayi da Safina tana kuka. "Wallahi Mama tsautsayi ne, na rantse miki da Allah tsautsayi ne ba abin da Adam yake tunani nake aikatawa ba, Mama don Allah ki fahimce ni!" Duk da tarin maganar da yake bakin Mama amma sai ta zabi tayi shiru ta raka lamarin da Addu'a sama da tayi magana, yana daga cikin dabi'ar mutanen da can. Basu bin dan kowa da baki, a yadda mijin Safina yake magana cewa ta jima tana cin amanarshi ba wannan ba ne farko, sannan yana da hujjar da ya dogara dashi duk da bai kamata tana yin wani abu ba, amma ya ga abubuwa dayawa na masha'a da take aikatawa......(Ku min uzuri yau na tashi da ciwon kai ne sai yanzu na samu kaina na karasa muku na gode! 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH *Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,* *Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 62 Sai Mama ta rasa me zata ce, musamman yadda take rantsuwa, Uwarta tana can tana ihun ta lalata mata suna, ni ina nan ina jin takaici da alamu cikin jikina bai fita ba, sallamar Sagir ya sani fita zuwa dakinsu Zakiya ya shigo, kallonshi nayi ban san lokacin da kuka ya kwace min na zauna ina kuka nace mishi. "Cikin jikina yana raye fa?" Na fada cikin wani irin kuka. Ina juya kaina har ga Allah ban son wani abu ya kara hada ni da Tafida ko shi yasa yake bibiyata? "Kamar ya ba anyi miki wankin ciki ba?" "Ina zan sani bayan nima haka suka gaya min!" Murmushi yayi ya ce mishi. "Ikon Allah kenan! Ubangiji ya raba lafiya." Ya fada yana kallona, "Ni bana son cikin, bana son abin da zai kara hada ni da Tafida ne, don Allah ka gane mana.!" "Na gane kai amma kada laifin Ubansa ya shafe shi, kada laifin Tafida ya shafi abin da baku da ikon dakatar da shi. Don Allah ki kwantar da hankalinki idan don Tafida ne mai sauki ne." Wani irin kuka na sake ina jin ciwon abin da ya faru a raina, na d'ago kai ina son nayi magana nayi ido biyu da Mama. Ita kanta madadin tayi faɗa sai naga tana murmushi ban san na bakinciki ne ko na kwantar min da hankali ne ta zauna tana kallon Sagir. "Ka je kawai zata fara zuwa awo!" "Tow shi kenan Mama! Allah ya baki lafiya Ummu!" Jan majina nayi ina gyad'a mishi kai, yana fita ta kalle ni yadda nake kukan sai ta rasa yadda zata yi ko zata ce min ma, "Duk abin da kika ga ya faru tow haka Allah ya nufa, bawa bai tab'a wucewa ƙaddaransa. Kowani mutum da arzikinsa, ƙaddaransa, girmansa da mutuwarsa. ake haifarsa duk abin zai faru da wanda ya faru da wanda aba a fatan faruwarsa ki dauki haka a matsayin ƙaddara! Nasan da zafi sosai sannan da ciwo kina tunanin kin huta amma Allah bai nufa ba. Ummu Hadiyya Allah yana sane dake bai manta da ke ba, Ummu Hadiyya ba zan ce ki rike cikin har haihuwa ba, amma Ummu Hadiyya, ina ga ki haife shi kamar wani ikon Allah ne! Domin ba kowa Allah yake bawa wannan damar ba, sai wanda Allah ya so. Tun kafin a haife ki aka san haka zai faru idan kika rike Allah dai ki ga kome da sauki ya zo miki, duk rashin hankalin Tafida a zamanku na farko ya kiyaye wani abu da ke ce silar haka. Yana da damar sake ki amma tsoron mahaifinsa da gudun b'acin ran mahaifinsa yasa shi zama dake duk da baya sonki, anan Aliyu ya nuna cewa ko babu ran mahaifinsa idan ya ce ya zauna dake zai iya koda kuwa baya sonki, Ummu Hadiyya ban ce ki koma gidan Aliyu ba domin nima na gaji da damuwa amma kuma waye zaki samu gaba? Waye zai rike mishi Yaranshi?" D'ago kai nayi da sauri. "Eh mana, Yaranshi ne fa wata rana zai bukace su, kin ga dole ki bashi Yaranshi. Dole zai koma gare su, yau badon na samu mijin da yake sona har nake kwaso wasu yaran kina tsammanin idan wani ne zai kyale ni ne? Ummu kina ganin idan kika zubda cikin kika rabu da Aliyu zaki huta? Ko tunanin Yaranki ma ya ishe ki, amma ba zance ki huta ba, idan har Aliyu da gaske yake ba zai huta ba zai ta bibiyar rayuwarki zai zame miki kamar inuwar gajimare ne, sannan ya hanaki sakat duk inda kika shiga ya hana ki zama. Da ciwo kan amma idan aka yi hakuri zai kome ya wuce." Yadda Mama take rarrsshina muka manta da Safina a dakin ina nan ina kuka. Idan nace ban yi bakincikin abin da ya faru ba nayi karya wallahi nayi karya nayi karya,haka kawai naji wani irin tsanar Tafida wanda ya lullube min zuciyata da idanuna. Bakiɗaya bana fatan ganinshi ko jinsa, bana fatan mu hadu domin zan iya aikata mugun abu. "Ya isa haka!" Amma don Allah ki ce kada ya kusanci inda nake xan haifi cikin amma don Allah kada ya dame ni, kada ya ce zai zo na yafe idan ba haka ba zan aikata kome don Allah ki ce mishi kada yazo!" Murmushi tayi tana faɗin. "ban yi wannan lalacewar ba, ki gaya mishi da bakinki!" Kukan da na saka mata yasa ta ce min. "Ya isa haka!" Yadda nake mata kukan yana bata dariya, haka yasa ya shiga rarrsshina har nayi shiru, tashi tayi ya samu Safina tana waya, ganin Mama yasa ta kashe tana jan hancinta. "idan kina irin wannan abin zai saka kowa ya zarge ki, ki gane babu wanda zai yarda ya ga kina waya a boye bai xargi wani abu ba, ko don Mahaifiyarki zaki rufawa kanki asiri. A wannan zamanin kayi na kwarai ya aka kare balle kayi sakarci, ki rufawa kanku asiri Allah ya baki Yara mata kada ki shafa musu fentin da ba zai gogu ba har tsofarsu. Gara a maka shaidar fada da a maka shaidar abu uku sata, zina, karya masifar tafi muni ne, idan aka kama ka da wannan biyun farko don Allah ki tuna da rayuwar Yaranki!" Kifa kanta tayi akan cinyarta, tana kuka maganar Mama ya kashe mata jiki wallahi bata yi niyyar aikata wani abu ba, amma Allah ya kawo mu zamanin da zina ta zama ado da kwalliya, a da acan boye shi kake gudun kada wani ya sani sunanka ya lalace, amma a yanzu a fili ake yinta. Har ga Allah mijinta yana da rufin asiri, sannan yana da damar shi ba laifi, sai dai tun daga ranar da suka ga Mijin Ummu hankalinsu duk ya tashi, burinsu shine auren Ummu ya mutu ta samu wanda bai kai Tafida ba, zai fi musu kwanciyar hankali da ace suna ganin Ummu tayi musu nisa har matsayin Matar gwamna. Haka yasa duk inda suka zauna sai sun yi maganar Ummu ko a zage ta ko ayi gulmarta sai Allah yasa Tafida ba me yawan barin fita ba ne balle har su hadu ayi mata wani abu. Sai gashi rigimarsu ta farko kamar su zuba ruwa a kasa su sha, domin sai da suka yi ta posting a status Ummu Kulsum da bata da hakuri ita ke ce musu Rai dai kwai mutuwa akwai tsofa, ga uwa Uba kwanciyar kabari. Wannan yasa suka yi ta ƙoƙarin cin mutuncinta da ta gayawa Mama ta ce tayi banza da su, don ko labarin abinda ya faru Mama tayi bala'in kai zuciya nesa don kusan suka hadu da Umma sai ta gaya mata magana, haka Mama zata yi Murmushi ta ce mata. "me kayan bunnu baya bada gudummawar gobara, da dukiya dai ba a musu mugunta sannan ranar da babu damar dawowa!" Wannan yasa ta gaji da abin da take yi ta tsiro da zancen Ummu tana aiki a hotel nan ma Mama idanun ta zuba mata, domin har ga Allah ita ba me son tashin hankalin mijinsu ba ce,idan Ummi Hajiya Balkisu ta ji tana fadar haka girgiza kai take ta ce mata. "Kina nufin Allah bai isa ya hukunta ki bane? Shi kaddaran wani ba abun dariya ba ne Hajiya Karima, tausayi kike ba ni, domin irinki basu iya amsa kaddaransu ba!" Kusan abin da ya faru kenan domin ana cikin wannan halin aka fasa ihun ta fadi a sume, haka suka nufi asibiti da ita jikin sauran Yaranta yayi sanyi, wacce take adawa da ita, tow itace a kanta. Yadda ta tsaya akanta har zuwa aka maida ta dakin da zata zama, Mama ce a kanta. Ni kan na rasa yadda zan yi kawai damuwa yayi min yawa, haka na zubawa ikon Allah ido. ** Tafida Ganin yadda Hajiya Kaltuma take kara tinzura Saadiyyah yasa shi dauke Saadiya daga Asibitin zuwa gidan ya kuma hana kowa zuwa,domin kuwa Hajiya itama gida aka dawo ........🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 63 Tafida karfi da yaji yasaka Kaltuma hauka, domin sau uku tana son ganin Saadiya amma ya hana, na karshen da suka zo aka ce musu yayi tafiya, lumshe idanu tayi tana faɗin. "Yaron nan yana wasa ni, dole na tab'a shi yaji yadda nake ji, dole na saka shi ya ji yadda nake ji!" Tafida bai yi tafiya ba, yana nan a gari Sa'adiyyar ce baya tunanin zai bata ita, sannan kamar yasan shirinta. Kawai ya saka aka shiryawa Abba da Hajiya da Umar tafiyar Umara, ya ce tayi jinya a can, sannan ya saka wani irin jami'an tsaron farin kaya, a unguwarsu Ummu yadda ko waye idan ba a yarda da shi ba, a bude mishi wuta. Domin yayi imani da Allah ko da wasa aka tab'a Ummu zai haukace, duk da ya boye damuwar Ummu, sai ya bayyana na Saadiya, haka kawai yake jin kamar akwai wani abu mai karfi da yasa Kaltuma take bibiyar Sa'adiyya, haka yasa shi saka idanun. Har tsawon kwanaki goma kafin ya bada damar, Hajiya Shuwa ta ganta ita ɗaya. A lokacin da aka barta ta shiga yana parlour yana bawa Saadiya abinci wacce take nutse ba zaka ce wani abu ya same ta ba, kuka ta saka tana kallon shuwa. "Mamy me yasa kuka juya min baya? Me yasa baku nime ba? Don Allah ki gaya mishi abin da yake son sani zai kyale ni!" Borin kunya ta fara, ya ce mata. "Nasan kina tsoro ne amma ina zuwa!" Wayar shi ya dauka ya saka a kunne, yayi magana can aka shigo da Mahmoud. Watsa shi aka yi a tsakar parlourn. "Mahmoud!" Saadiya ta kira sunanshi a razane. A matukar gajiye ya kalli Tafida ya ce mishi. "Hajiya Hindu bata san kome ba, Saadiya ma bata san meke faruwa ba, abinda na sani shine ni da ita muna!" Girgixa mishi kai take tana kuka. "Ina jinka! Ni da ita muna ha'intarka, bayan nan babu wani abu da ta sani na cutar da kai, Hajiya Kaltuma ce take kome, duk abin da ya faru!" "Ka je kayi nisa da inda nake, na kyale ka ne don girma da amintarmu,bayan nan kada ka sake ka kuma waiwayata. Ba tsoronka yasa na kyale ba, ba kuma don ka isa ba babu abinda zai saka na kyale ka kawai nayi haka ne domin Ummu ta rufa maka asiri amma ka tonawa kanka, Allah yana gani ban tab'a cutar da kai ba, ban ha'ince ka ba. Amma ka lalata min yardan da yake tsakanina da Matata. Ni bana tsoron kome ama na sani Allah zai saka min Allah zai saka min, matukar muna raye! Allah zai bi min hakkina, kema Saadiya akwai abin da nayi miki na cancanci haka? Idan har da gaske ma hango nadama a idanunki, tow ba makawa ki je na yafe miki nima ina fatan Allah ya yafe min. Sannan Hajiya Hindu nayi haka ne akan idanunki domin ya rage miki zogin da yake damunki, na sani da ciwo sosai ba zan manta da rike min hannu da kika yi ba lokacin da na rasa me rike min zaku iya tafiya!" Ya mikawa Sa'adiyya takardanta, "na sani zaki ji haushi amma iya adalcin da zan miki kenan, domin na fahimci damuwarki yana tare da Mahmoud, ni kawai kin shiga rayuwata ne ta hanyar cusa miki ni, babu soyayya da kike min, na gode da Allah ya bani damar gano matsalata. Kuje na gode sosai kowa yayi na gari don kansa." Daga haka yayi waya aka zo aka fitar da su, Mahmoud kan asibiti aka wuce da shi, Hajiya Hindu da Saadiya gida aka wuce da su, ta kofar baya suka shiga. Suna shiga parlour Sa'adiyya ta ce mata. "Mamy me yasa Hajiya Kaltuma take takura min? Me yasa ta saka ni lallai sai na auri Tafida?" "Saboda ni na haife ki!" Ta fada daga bakin kofar tana murmushi, shigowa parlourn tayi ta zauna tare da daura daya akan ɗaya. "Ban gane ba?" "Ni ce nan na haife ki, ba ita ba!" "Idan kece kika haife ni me yasa kike saka ni aikata mugun abu? Ban yarda da ba!" "Ita ce mahaifiyarki, ni ta kashe min nawa Yarinyar!" Inji Hindu tana da jin kamar zata yi kuka, kafin ta sake murmushin mugunta ta ce mata. "Daga yanzu zuwa lokacin da kike shirya mugun abu, Tafida yana kallonki, idan har kika sake wani abu ya faru tow ba makawa zaki ga hauka!" Dariya ta saka tana nuna kanta ta ce. "Bai isa ba!" "Ya isa domin yasan duk abin da kike aikatawa idanunshi yana kanki da mu bakiɗaya kuskure kaɗan zaki yi ya fito miki a mutum!" Dariya ta saka tana nuna musu kanta tana faɗin. "Wallahi ko Ubansa bai isa ba" "Allah ya baki sa'a! Ke bita na gaji da saka ni magana da Uwarki take, nima zan huta sai dai ina son na tuna miki abin da kika yiwa Ayyah in sha Allah sai Allah ya saka mata, ko saka idanunki da kyau abin da ka shuka shi zaka girba!" "Ki min shiru, wallahi xan baki mamaki kika sake wani ya ji wannan labarin kiyi kuka da abin zai faru, sannan Sa'adiyya bata da inda ya wuce nan wurinki waye zai yarda ina da alaka da ke indai ba sharri ba." Ta fita tana murmushin nasara. Saura Tafida, ** Kwanan Mahmoud uku a asibiti Iyayenshi suka sani, hankalinsu ya bala'in tashi ganin yadda ya koma amma ya ce musu. "Da sauki fa, ai da ko zama bana yi!" "Me ya faru da kai?" "Hmm! Hatsari nayi amma da sauki dake na fito daga Chad ." "Amma sai ka gaya mana tsawon kwanakin nan da baka nan hankalinmu ya tashi ga Rayyan da baya nan na rasa inda ya tafi!" Inji Ammyn da take zama a gefensa. Murmushi yayi yana faɗin. "na gode sosai Ammyn zai dawo!" "Allah yasa!" Washi gari aka sallame shi, ya dawo gidan Mama Saubai'atu bata nan, ya kalli Ammy ya ce mata. "Ina Saubai'a ta tafi?" "Tun ranar da kayi tafiya ta bar gidan nan ban san inda ta je ba gaskiya don ko sallama bata min ba!" "Shi kenan bari na koma can na duba abu!" "Tow!" Ya fita a hankali, dakinshi ya shiga ya kunna wayar shi. Sakwaani suka yi ta shiga kafin ya kira number ta, a can wani ya ɗauka. "Hello ina me wayar?" "Yawwa kace mata ta dawo min da kudaddena da ta kwasa ko na biyota har gida na wulakantatta ita karamar karuwa ce da take sata ashe bata isa international karuwa ba!" "Kai Malam kasan da waye kake magana?" "Da mijinta ai naga alamar haka, kai jakin ina ne da baka san matarka tana bin maza ba? Kai ka gaya mata nan da kwana uku ta dawo min da kudina ko nazo har gadon barcinka da Yarana su bi kanta daya bayan daya, kai kasan waye Ni? Wallahi kwana uku ku dawo min domin sai na baka mamaki!" Ihu Mahmoud ya fara mishi yana faɗin. "Kayi kaɗan ka tab'a min matata wallahi karya kake! Matata ba karuwa ba ce." Yayi mishi ya cigaba da musu ihu, yana musu zagin wulakanci. Tare da musu alƙawarin kashe su idan wani ya kuskura ya zo gabanshi, yadda ya haukace kamar zai mutu, domin yana jin bala'in kishin Matarshi. Dariya Mutumin yayi ya ce mishi. "Nayi maka alƙawarin duk ranar da na kama ka, sai na dasa maka ciwon da ba xaka iya maganinsa ba, ku dawo min da kudina, idan ka sake muka hadu babu kudina hatta uwarka matukar tana raye sai na fanshi kudina akanta baka san waye kake tab'awa ba, zan yi hakuri akan kome, zan share akan zagina da kayi amma kada ka tab'a min kudina domin shi kamar fitar numfashina yake. Dukiyata bana wasa da su." Mahmoud a tunaninsa sharri aka yiwa matarsa aka yi yasa shi, aunawa Mutumin da kana jin muryanshi kasan irin marasa mutuncin nan... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76 (Kuyi hakuri nasan page din yana kaɗan, amma zuwa Friday kome zai zawo dai-dai yanzu ina wani uzuri ne in sha Allah Friday zan gyara bana son na ɗauki hutun jaki da kaya ne nake muku kaɗan)64 Dariyar da Mutumin yayi ya kara fusata Mahmoud sosai wanda ya janyo yayiwa Mutumin alwashin matukar suka haɗu sai ya kashe shi. "Ni duk wannan bai dame ni ba, kudina kawai na sani kuma ya dawo min da shi xan kyale ta xan maka afuwa idan kuma kuka sake muka hadu haka ba zai mana kyau ba domin zan ɗauki duk matakin da yayi min. Sannan zan rama cin mutuncin da ka yi min akanka da kuma duk wanda ya shafe ka." Ihu Mahmoud da yake mishi yasa Mutumin kashe wayarshi. Kamar mahaukacin kare haka yayi ta ihu da faɗa shi ɗaya kafin ya iya calming kanshi kamar ba shi ba, sannan yayi wanka ya shige dakinsa ya kwanta. Sai yau yake matuƙar jin haushin cikin da Khairat ta dauka, da yanzu yana tare da ita yana moran arzikin da Allah ya mata, sai dai har yau bai cire ranshi da Ummu ba, Saadiya kuwa yana hauka ne zai aure ta bayan yasan da auren Tafida ta iya bashi kanta, kut ai karen hauka bai cije shi ba da har zai iya zama da ita, Ummu da ko wadancan abin da ya haɗa su zamanta da Tafida babu jin dadi bata yarda dashi ba, amma ita saadiya da jin dadin da kome ta bashi hadin kai, gaskiya ba zai iya wannan gangancin ba, gara dai Ummu ita ce daidai da lissafinsa, don yasan matukar Ya aureta, zai samu yara na gari masu tarbiyya da sanin ya ka mata, duk abinda zai fito daga Ummu to me daraja ne, shi yasa da yaga ba zata rabu da Tafida, idan taki ya lalata mata rayuwa amma shima ta tsira, "Mace ta gari kenan!" Ya furta yana murmushi lokacin da ya tuna da Saubai bata nan take ya ji hankalinshi yayi azabar tashi. Don gani yake ba zata tab'a cin amanarshi ba. *** *Ummu* Ina ga tunda aka gayawa Tafida, cikin nan bawan Allah nan bai barni ba, kai ni mamaki ma nake da cikin bai zube ba, yake kuma duk abin da aka yi, kallona Tinah tayi da tazo jiya, "Malama lafiya?" Na fada ina hararanta." "Kau kawai yadda kika yi kiba ne abin ya dame ni." "Tow sannu aiki yana gabanki!" Na fada ina cikin dan wake. "Allah da gaske kin yi kiba!" Ta ajiye min duk abubuwan da tazo shi. "wanann karon za ayi shi ne Egpty, ga shi nan ki fita ki nunawa duniya baiwarki." Shiru nayi na wani lokaci kafin na cire hannuna a cikin dan waken na ce mata. "Wani lokaci bamu cancanci kyautar da muke samu ba, imma ya zame mana alkhairi imma ya zame mana sharri. Tinah nasan waye Tafida shi ya ce miki ina bukatar haka?" "Ko daya ni na ga dacewar haka!" Gyara zama nayi, na ce mata. "Zan je amma ki gaya mishi kada ya sake ya shiga rayuwata. Irin waɗannan abubuwan da yake faruwa ya dakatar da shi. Bana son haka" Ajiyar zuciya ta sauke tana kallona, yadda na hade rai ina kokarin mikewa. "Babu hannun Tafida, idan ba zaki ba ba laifi amma ki daina jingina da na miki da Tafida saboda bana tare da abin da ya miki" ban kara magana ba, har Mama ta shigo, tinah ta gaya mata abinda yake faruwa. Tayi murna sosai kafin ta ce mata. "Zata je ko Ummu!" Ta fada tana murmushi, nima murmushi nayi ina kallon yadda take farin ciki. "Eh Mama!" A ranar Kulsum ta zo, ta wuni domin kuwa tunda yazo Uban mijinta ya hanata fita, sai yau kuma itama ta rantse ba zata koma gidan ba sai ana jibi zata koma gidanta. Da la'asar aka zo daukar Tinah, ina tsaye a gefenta da hijab yellow ta ce min. "Sai mun haɗu a lagos!" "Allah ya kai mu!" Na fada ina kallon har ta isa wurin motar security ya bude mata. "Ina saka idanunki akwai kome sannan zasu turo miki duk abinda kike bukata!" Murmushi nayi mata sannan na cigaba da d'aga mata hannu. Zan iya cewa wasu nasarar basu samuwa sai da kalubale, haka yasa na samu Mama a gefena, domin ta taka rawa sosai a rayuwata. Ina shiga dakin Mama na zauna, Mufidah ta zo ta hau cinyata. Hayaniyar da na fara ji yasa na leka, ta window Mama, Baba Bulama ne ya saka Safina a gaba yana zane ta, dakyar Mama ta shiga tsakiyar yana huci ya ce mata. "Ni zaki kunyata? Har kasuwa Abdulhadi ya same ni da cewa nayi hakuri kada na ga ya sake, ba laifin shi bane yayi kokarin zama dake amma abin ya ci tura duk abinda ya faru na tambaye. Na tambaye ki kin ce Baba na Tambaye mahaifiyarki ta ce babu, ashe abin da kike aikatawa kenan mai nayi miki na cancanci wannan kyautar? Hatta bukata na ce idan kuna da shi ku gaya min, hassada da yake damun mahaifiyarku shine kuka dauka? Nan ko wata biyu ba ayi ba take gaya min Tafida ya sake Ummu don taci amanarshi, lallai na kori Ummu tunda tana da gidan Ubanta bayan karya ce, sharri ce na kwabeta Karima kin ga sakayyar Allah tun a duniya kenan ba a je lahira na, wallahi kuka sake Allah ya kama ku da abin da kuke aikatawa kun shiga uku. Ba zan miki baki ba amma Allah zai saka min" ya fada yana me barin wurin, Mama sai hakuri take bashi amma ranshi ya b'aci, Ummi kan babu ruwanta. Don ta ga Ishara akan abin da ya faru da. Ajiyar zuciya na sauke ina jin ba dad'i, zama nayi ba kalli Mufid da shima ya shigo, dake suna samun kulawa yadda ya dace tafiya suke. Shigowa Mama tayi ta ga nayi zuru -zuru. " Kina buƙatar wani abu ne?" Ta tambaye ni, murmushi nayi na ce mata. "Kawai ban ji dadin yadda kome, yake tafiya haka ba, gani nake kamar wata rana za a samu matsala." "In sha Allah babu matsala!" Ta fada tana zama. "Allah yana sonki da rahama ne yasa kome yake bayyana, sannan ban nufi kowa da sharri ba taya ni wasu zasu nufe ni bayan na yarda da akwai Allah, shine wannan rayuwar kamar aika ce, idan aka yi dace aka samu a tafi lafiya idan aka rasa kome ya cab'e. Bana fatan ki saka wasu a gabanki, ki cire kome ki rungume kaddaranki Allah baya barci kuma baya gyangyadi, kafin yau nasan ai kin san me yake tafiya, bayan yau kuma kome ya tafi yadda ake bukata, nayi imani da Allah babu abinda ba zai wuce ba sai ikon Allah kuma muna nan muna gani idan muna raye mai rai baya fidda tsammani da nasara ko faduwa. Ki rike Allah ki kuma rike mutuncinki." Gyada kai nayi kawai ina jinta. Janyo kular dan waken tayi ta fara ci tana faɗin. "Kai Alhaji Muhammad zo muci!" Rarrafawa yayi wurinta, ya zauna ta fara ci yana mata wasa. "kin koshi?" Gyada mata kai nayi, wayata ta fara kara. Ganin number Tafida yasa ban dauka ba, d'ago kai tayi ta kalle ni. "me yasa ba zaki dauka ba." "Bani da matsala da shi ne!" "Haka ne!" Ta fada tana cigaba da cin dan waken, ganin ya kara kira ban dauka ba sai ta dauki Yaron suka fita, a fusace na dauka. "Wai kai meye matsalarka da ni ne?" "Baki gane ba ne har yanzu? Tow dama na gaya miki Hajiya tana son magana dake ne, idan don ni ne ba zan kira ki ba!" Shiru nayi "kina jina? Zata kira ki duk da Fanna ce Please ki saurare ta, Hajiya bata da lafiya." Duk da hankalina ya tashi amma na danne kafin na ce mishi. "Tow me zan yi?" "Ummu mahaifiyata ce, kada ki fadi abin da zan ji ba dad'i kin ji." Kashe wayar nayi, ya turo min sakon. *Don Allah kada ki kullace ta har yau tana sonki sosai* shiru nayi ina nazarin maganarshi. Duk halin da nake ciki na rasa waye zan daurawa laifi, Hajiya son Tafida yasa ta kasa boye shi a ranta, su kuma yan uwansa kyashin da hassadar Allah ya d'aga shi cikinsu yasa suke jin haushinsa. Su Matan gani suke kamar tunda ya ajiye yarinyar da bata musu ba, zata mallake shi sai yadda tayi da shi. Sannan babban tashin hankalinsu yadda ta haifa mishi yara har biyu har da namiji, ina laifin tayi ta haihuwar Yara mata, yadda basu kwashe duk wani abu da ya tara ba, amma ta haɗa da namiji. Wannan shine a zuciyar Maryam ita matukar tana raye Tafida ba zai ajiye iyalinsa ba da tana da halin kashe yaran ma da tayi domin ta haka ne duk abinda tafida ya tara zai zama su. Maryam da Abubakar lissafinsu ɗaya. Don haka ita Maryam yakinta ta samu Tafida yadda zata yiwa mijinta da Iyayensa rashin mutunci, idan ta gama da shi ta kwace Yaranta. Sai dai kuma inda labarin ya sha bambam tunda Tafida ya sake Ummu basu kara gane kanshi ba, domin ya sauya musu sosai dama kuma tunda Ummu ta dawo bayan rigimar farko ta gane tafiya ya fada soyayyar Ummu yadda ba zai iya sauraron kowa ba, tasan yana mugun son Ummu ta kuma yi imanin da haka, sai dai inda matsalar take, Ummu Hadiyya ita ce rayuwar dan uwansu..... Hajiya ta kira ni, mun yi waya da ita sai dai bana jin abin da take fada, sai da Fanna ta amsa ya ce min. "Aunty Baby don Allah ki zo! Duk da muna da nisa kizo Hajiya tana son ganinki!" "Shi kenan In sha Allah zan zo!" Tayi shiru sannan ta ce min. "Aunty Baby!" "Na'am!" "Don Allah ki zo ki ga Hajiya muna asibitin jidda." Ajiyar zuciya na sauke na ce mata. "Fanna ba haka bane, yadda xan zo ne yana matuƙar wuya, sannan kuma ban san da wani yare zan gaya Mamana zan zo wuri gaskiya ba zan iya." "Shi kenan!" Ta fada a raunane, kashe wayar tayi, nima na bi wayar ina kallonshi kamar ina ganinsu a cikin wayar, "Waye ba lafiya?" Mama ta tambaye ni, "Hajiya ce kakarsu Mufid!" "Allah ya bata lafiya!" "Amin Ya Allah!" Daga nan ta cigaba da harkan gabanta, tana faɗin. "Wani abu suke bukata?" "A'a cewa suka yi wai Hajiya tana son magana da ni, kuma da na mata magana ban san me take fada ba, alamar tana cikin ciwo sosai!" Murmushi tayi tana faɗin. "Kina son ganin ta ne?" Nan kan shiru nayi mata domin ban san yadda zata fassara abin ba, kawai sai na zabi nayi shiru da nayi magana. "Ba zan rabaki da dangin mijinki ba, sai dai har ga Allah yan uwansa suna da matukar hatsari domin sun maciji hatsari, Ummu ban hana ki komawa Tafida ba, sai dai kisan aure da zargi." Wannan kalaman da Mama tayi amfani da shi yasa na kasa motsi, "har abada ba zaku tab'a nutsuwa da juna ba, domin ya riga da ya zarge ki, koda kuwa a ce kun haifi Maiduguri ne." Sai na rasa bakin magana na sunkuyar da kaina ina jin hawaye na zuba min. "Ki taimakawa kanki kada kiyi kuka domin zuwa nan gaba zaki hnago abin da nake nufi, tun daga farko nayi kuskure yanzu kuwa." Shiru tayi bata kara magana ba, haka yasa na fahimci Mama sosai, murmushi tayi ta ce min. "Bana jin dadin mutuwar aurenki, amma akan zargi gara ki nime wani mijin, domin har tsufa da jikoki Aliyu zai na tuna abokinsa ya ganki tsirara sai yaji abin ya dame shi. Sannan zai najin ba iya lamarin ya tsaya ba an biye mishi wani abu! Mutane masu kishi irin na Tafida, suna da matuƙar wuyar sha'ani, domin koda sun yi nadama gani suke kamar zaka aikata wani abu.".yadda Mama take bayanin nan sai nake ganin kamar da na gaya mata cewa Tafida sun kwana daki guda da saadiya tabbas da yau sai ta ce abin da ya shiga yake girba, ko ni yau sai naji kamar Tafida ya boye min wani abu don ko da ban fada ba Tafida yadda suke ta malakewa juna shi da Saadiya duk me hankalin yasa akwai magana a kasa, haka yasa naji hankalina ya tashi. ** Mahmoud Yau kwana shida kenan, a yau Saubai'a ta dawo, da la'asar a matuƙar gajiye. Duk yadda ya so dauke kai domin a tsakanin kwanakin nan babu inda bai je nimanta ba, amma maganar daya ce ba a san inda take ba, a wurin aikinsu suka ce an bata excuse ne domin ta tafi wani aiki. Shigowa dakin yayi ya same tana zaune gaban Mirror tana gyara kanta. "Daga ina kike?" "Na tafi aiki mana ba gashi na dawo ba." "Karya kike, ina kika je waye kika sacewa kudi ya kira Ni?" "Wani irin magana ce haka? Zargina kake? Nace zargina kake? Ka gaya min me nayi da zafi kake zargina bayan kuwa kai ne ka fara sanina y'a mace shine zaka min mummunar zato" "ba haka ba ne baby, yadda Mutumin ya kira ne, yasa." Wayarshi ce tayi ƙara, da sauri ya dauka yana nuna mata. "Me yasa ba zaka dai na kira na ba? Matata gata nan aiki ta je kuma ni na yarda da Matata dari bisa dari!" "Ka ce mata ta ajiye min kudina a waje damuwta kudina idan ka sake na zo akan kudina wallahi ba zan kyale ku ba na rantse da Allah!" Ihu da rashin mutuncin da Mahmoud yake kamar zai shiga wayar ya daki mutumin, haka duk bai mishi ba yayiwa Mutumin barazana. Tare da cewa matukar suka haɗu sai ya mishi abin da ba zai tab'a mantawa ba. Ita kam sauba'a tsoro ne ya kamata, ta san waye Oga Hakim, kazungurmin dan fashi da makami, kusan kansu a hade da ogansu na banki, domin bibiyar masu ajiya a bankin suke suna bin su gida suna musu fashi da makami, tasan Oga Hakim ba zai kyale ta ba, gara ta kai mishi kudinsa, ta shi tayi ta nufi waje ta kiran James tayi ta gaya masa ya bawa Oga Hakim. Muryanta yana rawa ta ce mishi. "Oga Hakim kayi hakuri ga shi nan zan dawo maka da abin da na dauka don Allah kayi hakuri!" Dariya yayi ya ce mata. "Nayi kokarin koyawa kaina hakuri amma Mijinki ya zage ni ta sanadinki, kina tsammanin zan yafe mishi ne? Idan kina tsammanin haka tow ki daina domin ni baya yafiya, kudi kuma ki ajiye shi zan zo daukar abina, amma kiyi barci da ido daya domin bana bada notings sai dai a ganni kawai." Hakuri take bashi tana kara gaya mishi ba zata kara ba, dariya ya saka ya kashe wayar bayan ya mata gargadin kada ta kara kiransu. Wani irin tsoro ne ya kamata domin ya gaya mata duk inda zata ta sani ana bibiyar sawunta don haka ba ta isa gudu ba..... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7665 Da gasken gaske ta tsorata da lamarin, yasa ko barcin kirki bata yi ba tayi ta kiran Ogansu na wurin Aiki tana bashi hakuri, shima ya ce babu ruwanshi ya ga yadda take da hankali ne ya hada ta da Hakim bai san haka take ba, babu ruwanshi ta je can yasan halin Hakim idan yayi mishi magana yanzu sai ya ce ya hada baki ne da ita ta mishi sata, kuma dama ya kira shi ya mishi bala'i da masifa kenan ta kira itama, har gari ya waye Saubai'a bata nutsu ba, ta shirya ta nufi bank, koda ta isa ta rasa yadda zata yi domin kuwa tana son zuwa wurin MD amma tsoron kada ta samu wani tashin hankalin yasa ta zama har wurin karfe daya na rana sannan ta nufi office din, MD din tana zuwa ta shiga a tsorace, Oga Hakim da ta gani bata san lokacin da ta zube a kasa ba, tana me faɗin. "Ka rufa min asiri nayi laifi ka!" "Ni laifinki bai bata min rai ba kamar yadda Mijinki yayi ta soka min zagi yana cin zarafina. Ke kin san waye ni me yasa kika tab'a min kayana? Kin san akan wannan kudin zan iya kashe kowa me yasa kika tab'a tab'a min kayana?" "Kayi hakuri Oga Hakim wallahi son zuciya ce!" "Na yarda son zuciya ce amma ni ban san da haka ba, je ki zan duba abin da ya dace!" Haka ta mike kamar tayi kuka, amma bai kulata ba. "Hakim Yarinyar nan tayi danasani!" "Ni ba ita bace matsalar Mijinta zan koyawa hankali daga kaina ya daina zagin kowa yadda ya so!" "Gaskiya ban ji dadin abin da yayi ba, amma yarinyar ta yi kuskure tace zata dawo da kome!" "Bana yafe cin mutuncin da hakkina da ace na wani ne bai zai dame ni ba, duk inda aka shiga aka fita sai na hukuntasu itama dalilin tab'a min kayana." MD zai kara magana ya d'aga mishi hannu. "Ya isa haka! Idan dai ba so kake na zargi wani abu ba!" "A'a Hakim wallahi ba haka ba ne!" Daga haka yayi shiru. Shima ya juya tare da barin office din. ** Maryam Yayi ƙoƙarin kyautatawa Maryam amma gani take kamar baya son bata kudade, in fact su gani suke tunda ya zama gwamna ya kamata ace yana musu wadaka da kudi, haka yasa ta nime Abubakar ta kai mishi kukan abinda yake faruwa. Murmushi yayi yana faɗin. "Kina tsammanin ke daya kike cike da haushin haka? Nima nan ina jin zafin haka, balle ke don haka ki daina b'ata rai akan abin da baki da yadda zaki yi!" Zata bude bakinta wayarta tayi kara rukayya ce. "Ruky ina kike?" "Ba ita ba ce, yar uwanki tana hannun HQ na yan sanda idan kina son sanin me tayi muna jiranki!" "Innalillahi wainnalihir rajou! Tana ina yanzu?" "Na gaya miki tana Headquarter na Police!" Mikewa tayi tana faɗin. "Gamu nan zuwa!" Kallon Abubakar tayi tana faɗin. "Rukayya ce tana hannun yan sanda dai? Eh baka ji bane;" ai kusan a tare suka fita da shi, kamar yadda ya gaya mata tana Headquarter haka suka same ta, tayi wani laushi. Fashewa da matsanancin kuka tayi, tana faɗin. "Na gaya musu ni yayar gwamna ce suka ce min karya nake, wallahi na gaya musu amma suka ki!" Kallon Abubakar Maryam tayi ta ce mishi. "Ka kira dan iska!" Ko minti ɗaya bai yi ba, ya dauka suka gaisa da juna kafin ya gaya mishi halin da suke ciki, kashe wayar yayi can sai ga Commissioner of police, yana zuwa ya mikawa Abubakar hannu suka shige cikin office dinsa. Magana yayi aka kawo file dinta. "Alhaji Abubakar kayi hakuri, babu wanda ya yarda cewa yar uwar Yallabai ce idan ba haka ba ai ba me riketa. Sannan maganar gaskiya laifi tai na sata, ana ta nimanta amma bata yarda ta bayyana kanta ba, sai shekaranjiya aka same ta, gata na nan mun tambaye ta ina ta kai abin da ta ɗauka amma taki magana balle har a san yadda za ayi." Kallon takaici Maryam tayi mata tana faɗin. "Ke dai kin yi asara, me kika dauka kuma? Bayan kayan auren da kika diba bai miki ba, me kika kara diba?" "Wallahi ban debi kome ba." Marinta Abubakar yayi yana faɗin. "Don Ubanki zaki fada ko sai mun barki nan?" "Yana bayan gidanmu, na hak'a rami na saka!" Takaici ya rufesu bakiɗaya. "A gaskiya ba don mai girma Gwamna ne ya kira ba, da sai mun kaita kotu domin ta bawa hukuma wahala, amma ta kiyaye gaba!" Haka ya umarci yan sanda suka tafi har bayan gidanta aka hak'a ramin sai ga kuɗin da sun tashi kan miliyan goma, da sarka da yan kunnen gwal. A ina ta samo su, shine Tambayar da Abubakar ya mata. "Biki naje shine na kwana a can wallahi ba zan kara ba!" "Rukayya satarki ta fara yawa , da kika yiwa Ummu cewa muka yi karya ce. Ashe lokaci na zuwa da zaki dauko wanda ya ci Uban wanda kika yi" shiru tayi tana kuka, ita Maryam takaici ya hanata magana, haka suka amshi belinta sannan suka fito. "Ina zamu kaita?" "Nasiru ya ce ko na fito kada na koma gidansa, ya sake ni ga shaidar sakin nan!" Zare idanu suka yi, "Akan me?" "Saboda yan sanda sun kama shi kafin suka sake shi aka kama ni, bana tunanin ma zai yarda na kusanci Yarana." "Amma dai kin yi asara, wallahi kin b'ata wayonki!" Daga haka suka wuce gidan Tafida, sun samu ya dawo, yana ɓangaren Asiyah, wacce ya kawo mata wata babbar mace kullum da yamma tana zuwa koya mata karatu. Wucewa bangaren Hajiya suka yi Abubakar ya wuce abinsa domin yana jin babu dad'i akan samun Tafida, yayi alƙawarin sai ya saka Tafida ya rasa kome, su dawo kamar yadda suke da. Ya zama matsiyaci irinsu, sunan da ake kiranshi yayi vanishing a manta da an tab'a wani mai sunanshi ma. Murmushi yayi yana kara tuna yadda kome zai tafi idan yayi nasara. Sai da yaci abincin da ya samu sun girka da matar, yadda ya gansu ba laifi tana samun nutsuwa duk da ko wancan satin, sai da yayi ƙoƙarin ganin likitan ƙwaƙwalwa, akan shaye-shayen da take don sau biyu yana samunta a zube a banɗaki haka yasa ya kira Falmata ta hada shi da wani likitan yazo ya dubata, sannan suka sake zuwa asibitin aka mata gwaji. Kallonta yayi yarinyar bakiɗaya rayuwarta a nakashe yake, kama daga tarbiyyarta zuwa lafiyarta ta samu na kasu sosai, domin a binciken da aka yi akanta akwai wani kari da ya fito mata, saboda shaye-shayen da tayi ta yi a baya, ya haifar mata da tsirowan wannan karin a kanta, shi yasa ta fadi har sau biyu sakamakon girmanshi sannan jini baya samun damar wucewa. Mikewa matar da take koya mata abubuwa tayi tana faɗin. "Hajiya zan tafi!" "Allah Mama zaku tafi!" Ta fada tana kallonta. "Eh xan tafi kin san ana zuwa karatu da yamma!" "Shi kenan!" Ta mike tare da nufar dakinta, ta dauko kudi ta samu Tafida yana mata tambayoyi tana amsawa. Kafin ta raka mata, "ke ina Tafida!" Abin da tsohuwar yar kwaya kallon Maryam tayi, kafin ta ce mata. "Sandar kiwon da kika bani ya b'ata!" "Ke!" Ta bangaje ta, jiri ne ya kwashi Asiyah ta tafi zata fadi, Matar da take koya mata karatu ta riketa. "Yau sau biyu kika kokarin fadi baki da lafiya ne!" Kallon Maryam tayi tana faɗin. "Bani da lokacinki Maryam! Muje Mama!" Ta fada tana share jinin da ya zubo a hancinta. "Jini ne fa a hancinki!" Ta fada a rude!, "ki cewa Matori ya kai ki gida!" Ta juya a hankali, Maryam zata kara kai mata hannu, Security da take tsaron lafiyarta ta rike hannun Maryam. "Madam ki kiyayye kanki!" Ta fada tana shiga tsakaninsu. "Idan naki fa!" "Helin kyaleta!" Inji Asiyah tana rike kanta da yake mata bala'in ciwo. Ɗaya security din ce ta zo ta rike Asiyah har parlournta, kallonsu Tafida yayi yana jiran karin bayani. "Hajiya Maryam ce ta" "Jeki helin!" Ta fada tana kwantar da kanta a kafadarshi. "Ya Aliyu! Kayi kokarin ka dawo da Aunty Baby! Kana sonta, kana buƙatarta, don Allah ka dawo da ita." Ta fada tana gyara kwantar da kanta. "Ummu ba zata dawo ba, domin tayi fushi sosai." "Zata dawo!" Janyo kanta yayi zuwa cinyanshi yana wasa da gashinta. A hankali tayi yunkurin mikewa, ya d'aga ta. Tissue paper ya dauko ya saka mata a hancinta. "Ina ji a jikina kamar zan tafi ne, gashi ban gyara alakata da Allah ba, idan na mutu a wannan yanayin Allah ba zai yafe min ba ko?" Wani abu yaji ya tsaya mishi a rai, murmushi yayi yana faɗin. "Zamu je ganin Hajiya ina ganin kema zaki ga likita!" Shafa fuskarshi take a hankali, tana mishi wani abu, a yau sai yake jin shi cikakken d'a namiji, domin kome na shi ya taso mishi kamar da lokacin Ummu. Sai dai yadda yake jin kyamarta yasa shi maza ya rike hannunta. "Kyamata kake ji ko?" Ta fada tana jin hawaye na zuba mata. "Ban ga laifinka ba." Hade bakinshi yayi da nata, duk da yadda yake jin zuciyarshi. Asalin kyamarta yake ji, kamar zai yi amai. Janye jikinshi yayi yana sauke numfashi. Ita kuwa tayi lumo a kujeran. _Tunda ka gano gaskiya akanta me yasa lallai sai ka zauna da ita? Ka sake ta kada ka kara aikata irin kuskuren da kayi a baya, zargi yana lalata aure abin da yasa Ummu ba zata dawo gare ka ba kenan, don kome gaskiyarta wata rana sai ka zarge ta_ kalaman Deen kenan da yake yawo kanshi. Lumshe idanunshi yayi kafin ya cire kyamar ya rungume ta. Saboda yadda take kuka sosai. Ba karamin tab'a mishi rai yake ba, yana buƙatar mace kuma macen ma Ummu Hadiyya, amma taki ta fahimci yadda yake bibiyarta. A hankali kome ya warware tare da haifar da wani irin nishadi a yanayin da bai tab'a kawowa zai tsinci kanshi a ciki ba, yanayin ya tafi da lissafinsa yayinda ya warware wasu lissafin, barci me nauyi ne ya dauke su. Bude, duk da babu Ummu a rayuwarshi yanzu sai dai ya yarda kusantar barna da yayi a baya,.Allah ya hukuntashi da Sa'adiyya da Asiya, sai dai the worst part shine Asiyah tana bukatar kulawar at any cost, kiran sallah Magariba yasa shi bude idanun tana kwance a jikinshi, hancinta yana bleeding, amma a haka take barci ko ya ta sauke numfashi sai jinin ya zubo. "Asiee!" Ya fada a hankali, bude idanunta tayi tana kallonshi. "Na zata Ummu zaka kira?" Ta fada tana share hancinta da bayan hannunta. "Kana bukatar Ummu." "Baki ga kina zubda jini ba ne?" Dariya tayi tana faɗin. "Ba wani abu bane fa, abin da nayi ne na ke girba kana tsammanin Allah zai bar wanda ya zalunci wani ne? Kasan me? Kai na musamman ne, i'm sorry to say amma kai a cikin maza na musamman ne. Kasan me? Idan aka wayi gari bana raye ka rike Ummu da daraja, idan har ƙaddara zata kara hadaku, ka sota sama da yadda kake sonta yanzu. Ka tsaya mata yadda ba zata yi kuka ba. Ummu Hadiyya mutuniyar kirki ce, tana kuma da kirki. Nasan cewa wani abu ne me muhimmanci ya faru a tsakaninku ka zama Adali a cikin lamarinta, Yan uwanka kuwa ba san me zance ba amma tabbas ka san yadda zaka yi da su, domin ko ka dawo da Ummu." D'ago kanta yayi yana faɗin. "Ina son Ummu! Amma na cutar da Ummu sosai, a yanxu na hakura da Ummu ba wai don bana sonta ba, kawai don ina jin kunyar sake niman Ummu nake. Da ina da uzuri tabbas da Ummu bata bar rayuwata ba, na san nayi laifi amma Ummu ta tafi kenan sai dai na bada labarin na tab'a auren Ummu...... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7666 Girgiza kai tayi tana faɗin. "A'a haka ba zai yiwu ba. Lokacin sallah ya gota mana." Kasa magana yayi ya rungumi kanta, da yake kirjinshi, yana faɗin. "Na gode sosai!" Ya fada yana mikewa da ita, suka wuce dakinta ban dakin suka nufa suka yi wanka, sannan suka fito ya saka kayanshi da kanshi ya jasu sallah, bayan sun idar da sallah ta kawo littafanta, yana jin ana buga Kofar entry dinta amma ya dauke hankalinta da karatun Alqur'ani, yadda take tana tuntube, kuma ta nace. "Aliyu!!" Maryam ta shiga kwala mishi kira, Allah ya gani Maryam tana cikin ƙaddaranshi ta addabe shi ta hana shi sakat.. d'ago kai tayi tana kallonshi. "Kina jin tsoro ne?" Gyada kai tayi domin har yau bata manta dukar da Saadiya ta mata ba, Allah ya gani Asiyah tausayi take bashi, idan ya cire abin da tayiwa Ummu, amma yarinyar tana da sanyi sosai. Sauke ajiyar zuciya yayi ya shafa fuskarta. "Ki jira ni yanzu zan zo!" Ya mike ya fita, ya samu ana shan dagga da Maryam. "Ku kyaleta!" Ya fada yana me ratsa tsakanin jami'an tsaron. Ya kura mata idanu babu wasa a fuskarshi. "Me kike bukata?" Yadda ya tsare gida yasa bakiɗaya ta gigice, ta rasa me zata ce mishi. "Amma mun dawo ya !" "Ni nace ki dawo min da ita ne? Maryam!" Ya gyara tsayuwarshi ya cigaba da cewa. "Ki saka kai ko bar min part ko nayi miki ba dad'i, ina danne zuciyata a kanku kada ku fusata ni!" Ya juya zai shiga ta ce mishi. "Amma ya kamata ka san abin da ya faru!" "Bana bukatar sai na ji, idan kika kara damuna sai na baki mamaki!" Ya wuce ciki, parlourn ya same ta, tana ta fama da karatun. Kallonshi tayi kamar zata yi kuka ta ce mishi. "Ya Aliyu! Na kasa ganewa ba." Shiru yayi ya kara maimaita mata, har sau uku sannan suka cigaba a tare. "Me zaki ci?" "Zan ci abincin dazun!" "A'a ki saka kaya da face mask, zamu tafi cin abinci ne." Ware idanu tayi tana faɗin. "Ki shirya bayan Isha zamu tafi!" "Ok !" Ta fada tana me nufar dakinta, fita yayi zuwa part dinsa ya shirya sai da yayi alola kafin ya wuce wurinta, sallah suka yi, sannan suka shirya, yana gaba tana biye dashi. Har wurin motar da ya samu an ajiye mishi. Sai da ta shiga, ta zauna sannan ya shiga ya zauna. A hankali yake jan motar. "Don Allah ka kai ni gidansu Aunty Baby!" "A'a ba zaki ba!" "Kai kace zaka min duk abin da na roke ka? Yanzu na roke ka don Allah!" Shiru yayi mata, sannan ya cigaba da tukinsa, yana kallon hanya kafin suka isa gidan cin da babu kowa an sallami kowa, a tare suka shiga manajan gidan ya karɓe su da wasu staff din gidan, aka kai su wurin cin abincin. Aka fara hidima dasu, ana ta kawo musu abinci. Kallon yadda take daukar hoton abincin a waya ba. Shi a wannan yanayin Ummu ce kawai take yawo a kanshi, domin har yau baya jin akwai macen da zai mata irin son da yakewa Ummu, Ummu wata aba ce na da bazai ina mantawa da ita ba. "Bar ɗaukar hoton nan ki ci abincin!" "Tow!" Ajiye wayar tayi tana me fara cin abincin, a hankali ta fara cin abincin, yana kallonta, har ta ci sosai kafin ta d'ago kai tana murmushi. "Ka ga yadda nake cin abincin ko? Kayi hakuri." "Ai saboda ki ci na saya miki!" "Kai fa!" "Na koshi!" Cire Hannunta tayi tana faɗin. "nima na koshi!" Ta fada tana goge yatsunta. "Ok ki huta sai mu koma!" Haka ta jingina da kujeran tana ta wasa da wayarta, lokaci zuwa lokaci tana d'ago kai tana kallonshi, shi kuwa hankalinsa yana kan wayarshi da yake turawa Deen sako. Shima turo mishi yayi yana mishi dariya. "Mu gani kana hira da budurwa ce!" Ta leka, hoton Deen ta gani akan profile dinsa. Sosa Kai tayi tana faɗin. "Sorry!" Murmushi yayi ya ce mata. "Muje!" Bata yarda ta kalle shi ba, saboda abin da tayi sai kunya ya ishe ta. Har inda motar su take suka rako su. Manajen sai godiya yake yana har suka bar gidan abincin. A hankali yake tuki yana kallon yadda take sauke numfashi, kanta ta kai jikin window tana shaƙar iska. "Zauna da kyau!" Gyada zaman tayi tana faɗin. "Wani lokacin muna son Abu amma haka muke sadaukar dashi, ba don mun so ba!" "Kiyi shiru!" Yana kallon hanya, unguwar Ummu ta nufa. Kallonshi tayi tana faɗin. "Ina zamu!" Bai bata amsa ba, har kofar gidan. "Ki shiga!" "Zata karbe ni kuwa?" Hararanta tayi yana faɗin. "Yadda kika sani zuwa sai kin wuce mun je!" Tura baki tayi tana faɗin. "Don ka samu xan gyarawa soyayyarku hanya!" Ta fada tana fita daga motar, dafe goshinsa yayi yana kallon yadda take nufar gidan. Allah yasa kada zuwanta ya haifar da wani abu mara kyau, domin yasan yanzu sai Ummu ta fishi daukar zafi. *Ummu* Ina kwance hira Uwani suke da Mama, ina jin su amma ban tanka musu ba kasancewar kwana garin ana zafi. Muna tsakar gida muna shan iska. "Assalamualaikum!" "Waalaikumunsalam!" Muka amsa mata, domin duhun da yake wurin, sai haske farin wuta. "Ina wuninku!" "Lafiya!" Na gano Asiyah ce, haka yasa nayi mamakin zuwanta. "Maman Mufidah tana nan kuwa?" "Me kike bukata wani asirin kika kawo ki min!" Na fada ina haska mata touching wayata, kare fuskarta tayi tana faɗin. "Don Allah ki saurare ni!" "Malama bar mana gida bana son ganinki, kafin a sake min wani asirin." "Aunty Baby kiyi hakuri ki saurare ta!" Inji Kulsum, "akan me zan saurare ta? Gaya min me ye laifina da zata min asiri?" "Amma tace ki saurare ta mana!" "Mama matar Tafida ce!" "Na sani wani abu ne?" Yadda tayi maganar sai naji na kasa mata musu. Zama tayi a kujeran tsuguno. "Babu wanda baya kuskuren, kullum akan kuskure muke kuma muna masu kaskantar da kai da rokon Allah ya yafe mana, Aunty Baby ke mace kuwa? Taya zaki zubar da kayan yakin da kika fara? Waye ya zai gyara miku sauran aikin da kika fara? Na sani da ciwo amma kuma kada ki juya mishi baya yana bukatar ki a rayuwarsa, yayi kuskure kuma Allah ya yafe mana, kiyi hakuri Aunty Baby. Tafida yayi kuskure, amma mu mu fishi laifi domin bamu gane irin gwagwarmayar da muka yi ba burin mu kawai mushi cikin gidanki!" Duk sai naji raina ya ƙara b'aci. "Kice har ya gaya miki abin da ya faru? Tow maza ki fita min kafin nayi miki rashin mutunci!" Yadda na fusata yasa Mama rike hannuna. "Baki da hankali ne? Ko an gaya miki." Sallamar Aliyu yasa Mama shiru. Har kasa ya durkusa ya gaishe ta yana kallon inda nake ganin na mike zan tafi cikin daki ya ce min. "Ya jikinki? Kina Ansar magani kuwa?" A fusace nayi cikin daki, "Ke Ummu!" Mama ta daka min tsawa. Dawowa nayi na tsaya musu a kai kerere! "Zauna baki ji yana gaishe ki ba ne?" "Meye matsalata da shi? Yayi harkan gabanshi nima nayi nawa!" "Allah ya shirya ki!" Sannan Mama ta amsa mishi suka gaisa kafin ta bashi labarin gobe xan tafi maganar gasar abincin da za ayi. Murmushi yayi yana faɗin. "Allah ya bada sa'a yasa a dace." "Amin Ya Allah!" Kanshi a sunkuye yana kallon kasa. "Mama ina su Mufid?" Aasiya ta tambaye ta, kunnena yana waje ban san lokacin da nayi tsalle na fito na kwashi Yarana, duk da basu ganin fuskata, amma na watsa musu harara. Na wuce dakin da Yarana. "Tow Mama zamu wuce!" "A gaida gida!" "Gida zai ji" daga haka suka fita. "Baka ce mata kome ba, ka koma ka ce ka mai da ita don Allah!" Bai kulata ba har suka isa motar, tana rokon ya koma cikin gidan ya ce ya maida Ummu amma yaki kulata. Wato ni Tafida zai wulakanta ya dauki min Matarshi zuwa gidanmu? Don gani yar iska, bakin cikin da na kwana da shi Allah kaɗai ya sani sai na rama wulakancin da ya min don wallahi ba zan yafe ba, wannan ai cin fuska ce. Kwafa nayi na juya ina me jin karan takaici, sako ne ya shigo min ina dubawa na ga shine. Kamar na ruga mishi zagi amma wannan ba tarbiyyar Mama ba ce, duba sakon nayi naji kamar na saka hannu a kai na fasa ihu. Lallai ma Tafida ya rena min hankali. *Kiyi hakuri! Wallahi ban san zuwanta zai b'ata miki rai ba da bamu zo ba, yarinyar tayi nadama!* Bakincikin wannan sakon yasa ni tura mishi da cewa. _Kaje Allah zai saka min tunda cin mutuncin bai isa ba sai ka kawo min matarka gidanmu na gode!_ sai kuma ja rushe da kuka, domin wallahi raina yayi bala'in b'aci, kuka nake ƙasa ƙasa, sai gaza fahimtar kishi ne ko takaici ne, domin Tafida ya bala'in b'ata min rai, haka yayi ta turo min sakon ban hakuri amma naki kula shi karshe kashe wayar nayi, ranar nayi barci cikin wahala. Washi gari ina tashi na nufi inda kayana yake na dauki towel naje nayi wanka da alola, ina fitowa sallah na gabatar na zauna a wurin har gari yayi haske. Sannan Mudan yazo ya wuce da ni Airport. Abun mamaki a airport din na same shi. Tare da Asiyah da alamu suma tafiya zasu yi, babu abinda ya dame ni da su. Abuja muka nufa tare. "Aunty Baby!" Banza nayi musu na cigaba da abin da nake. "Kin ga ki kyaleta bata son magana!" Ina lura da ita ta wani kanta a kafadarshi, dauke kai nayi ina jan tsaki kasa ƙasa, a wurina yau ta zame min ranar b'acin rai, domin dai abin da suke yi yana bala'in sosa min rai. Tashi nayi zan wuce ban daki , kallonta yayi ya ce mata. "Gyara zaman ki zata wuce!" Ba musu ta gyara na wuce abina, koda na shiga ban dakin sai naji ina ma da na zauna anan ɗin wallahi har mu sauka. Can dai na hakura na dawo, sai dai nayi ba zan kara saka idanun akansu. Domin kada Tafida ya dauka kishinsa nake ji, koda na dawo na zauna ba yabo ba fallasa ta min magana na amsa sama-sama, sannan na zauna har muka dauka tana yi tana saka ni cikin maganarta, bana biye mata sai dai na share su, muna sauka na samu tinah tana jirana, yadda na tsare ta da idanu sai da ya bata dariya "Iyawo Aliyu irin wannan muzuran!" Share ta nayi kawai na wuce gaba tana bina a baya, d'aga musu hannu tayi, domin su da sauran lokacin tafiyarsu ko ni zan je na huta ne saboda ba zan iya zaman airport ba. Muna isa na lura da yadda take dariya na gano chat suke da Tafida hade rai nayi ina hararanta. "Ka ga kada ka hada ni fada da Iyawo!" Haka tayi ta min tsaya ina share ta, kafin na sake nake bata labarin abin da ya faru. "Ummu kin ce baki son Tafida meye na kishi akanshi?" Kamar xan yi kuka na gaya mata abin da suka min jiya. Share zancen tayi kawai tana mika min bowl shake da fruit, ina ci ina kallonta. "Ummu!" Mika min wasu takardu tayi, tana faɗin. "Duba min wanene yafi miki kyau!" Amsa nayi ina dubawa. "Wannan tafi kyau!" "Ok makarantar girki ce ake son a gina a Maiduguri, amma ba a samu malamar ba shine nace ko zan miki magana ne sannan zai hada da shagon sayar da abincin bakiɗaya." Ajiyar zuciya na sauke ina jin wani irin abu a raina na ce mata. "Anya ba wani bane ya biya kike min hanya haka?" Dariya tayi tana faɗin. "No ina son ki tsaya da kafarki ne, yadda babu wanda zai ce kina jiran tsammani! Ummu Hadiyya ko don hidimar da da kika min zan biya wannan kyautatawar!" Sai naji na kasa magana bakiɗaya, muna nan har lokacin tafiyarmu yayi. Karfe goma na dare. *** Maiduguri Ance dare mahutan bawa, amma ga wasu mutanen wannan ne lokacin aikinsu. Domin cikin kwarewa da sanin kan aiki yau suka dirka gidansu Mahmoud..... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7667 Kafin yau! Jiya kenan Yayar Mahmoud da Yaranta mata biyu, mai suna Hamdiyya sun zo daga lagos, kasancewar sun jima basu zo ba mijinta dan Damaturu ne, ita kan ta Banbanta da Iyayenta domin halinta daya da Rayyan. Hamdiyya tana da matukar kirki da sanyin hali, amma bata daukar reni haka yasa tun fil azal suke faɗa da Mahmoud, har tana nuna mishi abin yake ba kyau ya daina kafin lokacin ya kure mishi akwai wani zuwan da tayi da yar aikin Yaranta, Mahmoud ya kama latsa Yarinyar Allah ya taimaka ta kama su, Amma sai aka juye laifin akanta na zuwa da yarinyar wai ba mamaki yar iska ce tazo zata lalata musu tarbiyyar D'ansu. Su akansu, sun san Mahmoud bai da mutunci amma haka suka rufe abin musamman Ammyn da take cewa bata haifi dan iska, tayi masu aiki dayawa amma Mahmoud ya yi sanadin barinsu gidan wasu yayi musu fyade wasu kuma bai musi ba, Allah kaɗai yasan irin bakincikin da ya cusawa iyayen Yara, wannan kenan.. Dirkowa Tango, daya daga cikinsu Oga Hakim, ya bude gidan, bayan ya sumar da me kula da gidan, sannan ya rufe suka shiga babu sand'a ko tafiya a hankali, basu yi magana ba amma daga takunshi zaka fahimci kosasun mutane kamar wasu shanu, raba kansu suka yi wasu suka yi bangaren Ammyn suka taso ta. Bayan sun ɓalle kofar gidan, wasu suka wuce bangaren Mahmoud, suka shiga shi kan Matar Mahmoud bata rufe ba domin Oga Hakim ya gaya mata matukar ta rufe sai ya rabata da rayuwarta haka yasa bata rufe ba, ta bar kofar a bude. Koda suka shiga cikin gidan, sun same ta zaune domin bata yi barci ba, sai Mahmoud da yake ta sharar bacci, amma ta daure hannunshi da kafarshi, sai bakinsa da ta saka salitep ta rufe gam, kunna wutar dakin suka yi. Oga Hakim ya ja kujeran mirror ya zauna yana murmushi. "Ina kudina?" Bude drower din ta tayi ta ciro wata jaka, ta ajiye a gabanshi sannan ta zube akan gwiwarta. "Oga Hakim ga shi nan!" Murmushi yayi ya ce mata. "Akan kudina ba laifi ba ne, zan iya karba tunda babu abin da nake ganin mutuncinsa sama da kudi, kuskuren da kika yi auren dan iska da bai san darajar na gaba da shi ba. Wanda bai dauki Amanar abota da zuciya daya ba. Da ace ya mai da hankali ya rike amanar abotarsu tun na yarinta, da wani magana ake ba wannan ba. Amma yau zan nuna mishi yadda ake rashin mutunci ganin idanunsa." Ya kalli Yaranshi ya ce musu. "Ku yi waje da shi!" "Tow!" Duk sauran fuskarsu a rufe yake, shi ɗaya ne fuskarsa a bude wacce kana gani kasan zai yi rashin mutunci, domin kuwa fuskar tasha fetching kamar kwarya zani, daya daga cikin yaranshi ne ya wake Mahmoud da mari, sai da ya farka domin ya zaci da katako aka mare shi. A lokacin aka shigo da su Ammyn, parlour aka zube su a tsakar parlourn.. "don Allah ku dauki kome ku kyale mu?" Dariya Oga Hakim yayi ya ce musu. "babu abin da zan dauka a gidan nan, sai dai zan yi abin da na ga zan iya. Kwanaki d'anki yayiwa Yarinyar da tazo aiki nan ciki kuka kore ta?" Murmushi yayi ya kalli Yaranshi kafin ya ce musu . "Ya ma sunan Uwar Yarinyar?" "Yahanasu me mana aikin abinci!" "Thank you Rainbow!" Ya kalli agogon hannun shi ya cigaba da cewa. "Kuka ce sharri ta mishi! Bayan ga video abin da ya faru. Shi d'a ita kuma baiwa ce saboda ta zo niman abincin da zata ci ko? Haka ne kafin yau wacce yarinya ce ma yayiwa Fyade ta mutu wurin haihuwa?" "Atika Oga! Kanwar Bobo!" Wanda aka nuna da sunan Bobo ya gyara zaman bindigarsa. "Hajiya kin tuna da kakarsu tazo kika kore ta?" Wani irin kuka Ammyn ta fashe da shi tana girgiza kai, "Taya ka samu videon abin da yayiwa Matar Tafida?" "Hmm mutumin nan dabba ne yafi a kira shi da dabba acikin dabbobin ma mara amfani kai ko alade yafi dacewa da a kiran da ita." "Sana'armu fashi da makami, sai dai muna kyautata alakarmu da mutanen da basu da shi kuma suke da karamin karfi, na san wacece matarka tun kafin ka aureta, saboda na biyo bayanka na saka ta kare kanta yadda zata shiga jikinka! Bayan aurenku muka daura akan inda ka fara. Baka tuna fuskar ta ba ko?" Shiru yana yana motsi kafin Bobo ya kwad'a mishi mari sai da ya fadi. "Na so na maka adalci na kyale ka, amma na fahimci dole na dasa maka abun da ka dasawa mutane dayawa." Ya juya ga Hamdiyya da take kuka rungume da Yaranta. "Matar mataimakin controller na custom ko? Mijinki mutumin kirki ne, sau uku yana min Alfarma na shigo da motocina arewa, Mun san halacci, Jazu kaita wancan bangaren da Yaranta, ka rufe su domin muna cin haramtacciyar abinci ne ba ma haɗawa da halataccen abinci, Uban Yaran mutimin kirki ne,.mun yi gwagwarmayar a wani lokaci, amma bai tab'a lakatar wata mace ba. Idan muka tab'a ta Allah ba zai bar mu mutsira ba kamar kullum!" Ya fada yana mikewa. "Ni dan kasuwa ne da nake shigowa da motoci, sana'ata kenan sai kuma bayan fage ina bashi da makami waye ya sani? Waye ya damu da ni? Amma na damu da mutanen da suke buƙatar taimakona, Hajiya sai hakuri akan idanunki Mijinki da d'anki suke tabargaza baki tab'a hanawa ba, haka yasa karamin danki ya bar gida, zaku yi mamakin yadda aka yi nasan kome a'a nima na turo mutumina yayi min aiki, ai ba ku kadai bane masu lissafi, Baka gane fuskar ta ba ko? Ka tuna Wafiyya?" Wani irin rikice yayi yana kallon Saubai'a yana ja da baya. "Ka san me kayi ai? Bayan haka ka saka makarantar ta kore ta bayan ka lalata mata rayuwa kai da mahaifinka kuka lalata mata sauran damar da take da shi ka tuna ta? Wannan kanwarta ce Saubai'a a'a Affiyah fansa ba zata yiwu ba saboda kana tare da Safiyyudeen da Aliyu Tafida ba zasu bari a cutar da kai ba zasu baka kariya a matsayinka na amininsu! " Juyawa yayi yana kallon Baban Mahmoud. "Kai da kanka ka lalata d'anka bayan kasan haka kayi ya ƙoƙarin boye laifinka bayan kasan cewa abu daya muke yi! Bari ka ga yadda ake gudanar da hisabi a duniya domin kayi naka muma zamu yi na mu." Janyo Ammyn suka yi. Ihu Mahmoud yake suka kwashe da dariya, "Jazu kai kace Uban kake bukata je kayi kodumo da shi!" Su rai goma sha biyar nan haka suka yi layi akan Ammyn, Mahmoud yayi bakinciki kamar zai mutu yayi ihu yayi kukan ya buga kanshi yayi kome. Yana kallon Matar shi Saubai'a tana murmushi, hawaye na zuba mata. "Kaji yadda ake ji, Yar uwata ta rasu ta bar duniya da bakin cikin abin da ka aikata mata,mun rasa kowa na mu bayan rasuwar Mahaifiyarmu, dama Mahaifinmu ya jima da rasuwa, domin ta rufa mana asiri Mamanmu tayi ta sana'a, ka kunsa mata bakin ciki biyu ga ciki ga kora, ita kanta ta fada fyade ka mata, haka bai maka ba kayi bibiyar rayuwarta har sai da ta mutu hankalinka ya kwanta, ka godewa Allah da ban kashe ba domin Abokan da ka ci amanarsu sune suke kare ka, yanzu babu kowannensu a tare da kai. Ai Tafida ya gaya maka ba zai maka kome ba ka zata tsoronka yake ji kada ka kara fitar da hoton matarshi a'a yasan Allah baya bariin hakkin aure ka tab'a ya bada damar an.tab'a naka. Nayi Imani da Allah fansa ya shigo da ni rayuwarka amma ko da wani abu ya shiga tsakaninmu ka yarda kai ne sanadi." Ga Ammyn da Babanshi cikin mawuyacin hali domin Jazu gay ne, sau tari idan suka je fashi tow shi abin da yake yiwa maza da mata kome, yadda suka tozarta Ammyn yasa ya daina gani sosai, alamar zai suma. "Ku tale min Dan iska!" Oga Hakim ya fada yana mikewa, yana zuwa ya saka kafarshi da katon takalmin shi me kama da dutse ya daki gaban Mahmoud sai uku anan ya zube sumamme. "Zaki zauna ne ko zaki zo muje!" Hawaye ta share, ta ce mishi. "Zan bika!" Ta fada tana shiga dakinta, ta dauko akwatinta ko inda suke bata kalla ta bi bayansu. "Ina zaki daga nan?" "Zan je na dauki Little Wafiyya na tafi da ita inda zamu zauna babu wanda zai dame mu!" "Na ce Taj ya baku takardun shaida barin kasar ya baki?" "Ya bani!" Ta fada tana kallonshi. "Nan babu tsaro sana'ata na kasada ne da wasa da rai, idan na samu lokaci zan na zuba duba ki da Wafiyya!" "Na gode sosai!" Mika mata jakar kudin yayi yana faɗin. "Na ki ne dama, kada ki sake yarda ayi amfani da ke don cin amanar wanda ya yarda dake, na san ba don kina buƙatar fansa ba, ba zaki yarda nayi ruin dinki ba. Ki kula da yarinyar nan sosai kada ki yarda ta nime wani abu ta rasa, idanuna yana kanki." Daga haka kowa ya kama gabashin, Hamdiyya suka bude ta kafin suka tafi abinsu. Bayan tafiyarsu, ta fita zuwa bangaren da ta samu iyayenta cikin wani irin mugun hali, ihun niman taimako da a gaji tayi ta yi, babu wanda ya fito a cikin daren kamar zare sai da asuba ne, aka ta kawo musu ɗauki. Tare da nufar asibitin da su, Hamdiyya bata taɓa tsintar kanta a cikin tashin hankali da bala'in irin na daren jiya zuwa yau ba, Yaranta ma kuka suke su a kaisu wurin Babansu kawai ba zasu zauna ba. Karfin imani yasaka ta iya zama asibitin domin gani take zasu iya biyo su asibitin, ta girgiza iya girgiza, mijinta kuwa ta kira shi ya kai sau dari, ce mishi take yazo. Karfe shida na yammacin ranar Alhaji Abbas ya rasu domin kuwa abin ya tab'a shi sakamakon abin da aka mishi dayawan mutane da suka san halinsa basu fadi maganar alkhairi akanshi ba, sai bayan sallah jana'sarshi Mahmoud ya farka, labarin ya karad'e ko ina na garin Maiduguri, har a jarida an fashi sun shiga gidan tsohon Kwamishina. A lokacin da Hajiya Kaltuma ta ji labarin, tafi kowa murna domin Mahmoud shine mutum ba farko da zai fara bada shaidarta. Haka yasa ya ta nufi asibitin bata samu ganinshi ba, har washi gari. Deen da ya samu labarin ya kira Tafida ya gaya masa, hankalinsu duk a tashe duk da abinda Mahmoud yayi basu manta da abotarsu ba domin kuwa sun yi kokarin sakawa a kare shi kada a sake farmakarsu. A ranar da suka cika kwana uku Deen ya iso, yana asibitin karshe da bai yarda da Asibitin ba, domin ya ga wani da bai yarda da shi ba. Wato Jazu haka yasa aka mai dasu asibitin da yake cikin fadar gwamnatin kasar, wanann lokacin likitoci suka tsaya akan shi sosai. *** *Ummu* Kasancewar na kwana biyu ban shiga kitchen ba, haka bai saka na manta da yadda ake rike ludayin miya ba, nayi matukar kokarin ganin nayi kome yadda ya dace, sai dai ma yasan tsayuwar da nake yana haifar min da ciwon kafa da gajiya, haka yasa kafin wani lokaci na gaji, idan na koma masauki gajiya nake a daddafe nake sallah na kwanta. A hankali kwanakin suka ta tafiya, har muka samu sati uku kafin muka gama, cikin ikon Allah da yadda na tsammaci lamarin domin yawan gajiyar da nake yasa nake ta zuwa ta biyu ko ta uku, a kullum sai nayi baya. A ranar na karshe ne muka yi aikin kamar babu gobe haka yasa ni jin kamar ba jikina ba, ina gamawa na tafi ban dakin da yake wurin nayi ta amai. Na gaji sosai, a hankali naji kamar jiri na daukata zama nayi na rufe idanuna, a hankali naji an dauke ni sama. Idan idanuna bai min karya ba Tafida nake gani. A hankali na lumshe idanu na gyara kwanciyata a kafadarshi. Hawaye na zuba min. Tun farin abin yake bibiyarsu, sai dai wani abu da ya lura Ummu tayi rauni Ummun da ya sani ba ita ba ce, yana hango gazawa da rauni a tare da ita, haka yasa koda ya samu Asiyah ta ga likita, ya bar Jidda, domin ya shiga Makka yayi Umara, anan suka hadu da Abba, yake gaya mishi abin da Ummu take a can. "Abba na ga gazawa a tare da ita, sannan rauni da gajiya na tattare da ita. Abba na shirya na zauna da Ummu Abba ka saka baki a karo na biyu Ummu ta dawo min!" "Ummu ko ta dawo taya zata yi handling matsalar danginka? Yaran da basu ji maganata ba, maganar waye zasu ji? Ummu ba kai take gudu ba danginka take gudu. Domin kuwa danginka sun fi kome tashin hankali ka kyaleta, ta huta bana son Kai Yarinyar nan tana fuskantar kalubale. Is too much ta cigaba da ganin bakinka sanadin yan uwanka!" "Abba nayi maka alkawarin zan gyara!" "Gyaranka zai lalata zumuncinku, idan har na fahimci Mahaifiyarta tsoro kada son da kake mata ya lalata zumuncinku ne!" "Abba ya zan yi?" "Ka kyale ta amma ka tsaya a gefenta, yadda zata ji ashe tana raye, matukar kayi haka tow zata iya tunawa da kai na musamman ne idan bata yi nazarin haka ba ka kyaleta tayi rayiwarta, wannan shine kaddaranku!" "A'a Abba kaddaranmu a hade take, ba zan iya rabuwa da ita ba, domin ita din rayuwata ce, ana iya sauyawa tuwo suna Ummu a rayuwata ƙaddara ta ce ita, don Allah kada ka ce min rabuwarmu ƙaddaran mu ce!" Murmushi yayi yana kallon Tafida da yake kallon dakin Ka'aba. "Yarona ka girma!" "Abba bashi nake son ji ba, ina son jin kace min go a head!" "Ni kuma?" "Eh Abba!" "Shi kenan Tafida idan kana ganin zaka sake dawo da ita duniyarka ina farin ciki, kuma na yarda ni na haife ka, idan kuma kayi fail ba zan ce kome ba zan kira shi da Fated!" "No need ka kira shi da ƙaddara! Ummu tana sona zata dawo gare ni na sani!" Dariya irin ta Manya yayi sannan ya wuce da zance zuwa ga faɗin. "Me ya samu Mahmoud da iyayensa?" "Yan fashi suka shiga gidan suka musu ta'addancin." "Wani mataki ka dauka a matsayin Abokinka?" Abba ya tambaye shi. "Abba babu abin da zan yi domin kuwa kamar fansa ce ba zalinci ba ne!" Shiru Abba yayi kafin ya ce mishi. "Yanzu waye a tare da shi?" "Deen!" "Wannan yaron dan halak ne, Allah ya mishi albarka domin duk ya fiku karfin imani!" Murmushi Tafida yayi ya ce mishi. "Abba ina kishin Deen fa!" "Sai kayi!" Dariya suka yi baki dayansu. "Abba har yanzu baka ce kome akan Hajiya Kaltuma ba." Murmushi Abba yayi ya kalli Tafida da kyau kafin ya juya yana kallon dakin Ka'aba, ya ce mishi. "kana tsammanin lamarin zai tafi da sauki ne? " "Kamar ya Abba?" Murmushi yayi kafin ya ce mishi. "Kaltuma ita ta mai da kai Gwamna.........(What?) Jira jira jira..... Jama'a anya kun hango wani kwarya - ƙwaryar gurmi kuwa......🏃🏻‍♀️ Muje bingo ....... 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +2348130269641 Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7668 "Ban fahimce ka ba Abba!" Shiru yayi kafin ya sauke ajiyar zuciya yana me hura iskar bakinshi ya ce a hankali. "nasan abin da Kaltuma take aikatawa tun daga kashe mazajenta har zuwa mahaifiyarta, amma kana da hujja? Idan baka da hujja ka kyaleta ka barta kawai!" "Abba me kake faɗa ne?" Murmushi Abba yayi kafin ya ce mishi. " A shekaru irin naka ba zaka iya hango abin da nake nufi ba, amma da zaka fahimci yadda rayuwa take tabbas zaka iya boye mai laifi domin wata kusurwan!" "Kenan Kaltuma ba zata fuskanci kome ba!" Lumshe idanun Abba yayi ya bude yana Murmushi. Tashi Tafida yayi hannunshi a cikin aljuhun wandonsa ya ce mishi. "Gobe xan wuce!" "Ubangiji ya tsare maka hanya ya kare ka da mugun ji da mugun gani!" "Amin Abba, amma me yasa ka ke kare Kaltuma?" "Na zata mun bar wannan maganar, akwai wani gidana a Dubai da na saya shekarun baya, yana wurin Deen zai tura baka, ko ya turo maka Dubai ka ɗauke matarka da Yaranka, ba laifi bane don kayi haka amma ka sani any single mistake zai iya janyo more regret har karshen rayuwarka." Kasa magana yayi yana kallon Abba, kafin ya bar haramin. "Ya Allah ka ga Aliyu ya Allah ka taya shi yaki da azzalumai na ci danna waje!" Ya fada yana zubda hawaye. Domin ya kai matakin da bai isa ya bari a cutar da iyalinsa ba, yasan idan ba haka yayi ba zai iya rasa Aliyu yasan wacece Kaltuma sau biyu yana tsallake rijiya da baya akan tuggun da ta haɗa mishi har yau yana taka tsantsan akan abinda zata bashi ya ci ko ya sha, yasan darajar rayuwa amma bai kawo zata iya saka Yaranshi a cikin lissafinta ba, yasan me take bukata yasan meye harinta. Na farko abin da ya faru akwai wani had'akar kamfanin hako zinari da Alhaji Bashir Ishaq suka saya a Zamfara wanda ake fitar da zinari zuwa kasashen waje, wannan kamfanin shi bai da wani kaso me yawa a cikinsa kashi ashirin da biyar ne na shi, saba'in da biyar na Alhaji Bashir Ishaq ne, wanda Alhaji Muhammad Jadda ya saka sannun Babban Yaron Alhaji Bashir din wato Ishaq Bashir Ishaq, wanda ya dauke yaron zuwa canada saboda yadda Kaltuma ta saka a kashe yaron da kanwarshi. Barista Sallau Jibia wanda yake zaune a Lagos shine lauyansu, sannan ya san kome domin da shawarar shi aka dauke Yaran zuwa can. Don har Kano ta saka aka bi yaran a kashe, Allah ya tsiratar d su, Kaltuma ba matsuyaciya ba ce tana da rufin asiri amma yadda kasan mayunwacci idan ta ji zancen kuɗi ko wata sabga na kudi, haka yasa, take farautar rayuwar Aliyu domin kashi ashirin da biyar na wancan kamfanin hako ma'adanan na Tafida ne, domin sun yi alƙawarin barwa Yaransu ne, tun a lokacin Haihuwar Tafida Allah ya budewa Alhaji Muhammad Jadda wani irin kofar samu da duk abinda ya tab'a sai yayi albarka, haka yasa yake gayawa Alhaji Bashir Ishaq, shi kuma ya ce su sayawa Yaransu wani abu da zasu amfana tunda sune silar samun damar haka, ance kowani Yaro da arzikinsa Amma zai iya cewa Tafida shi ake kira goshi daga haihuwarsa har zuwa yanzu bai tab'a fuskantar Babu ba, haka yasa yake matuƙar son Yaron, kuma ya lura rufin asiri da albarka a jininshi take, domin tun yana ƙaraminsa idan yayi baki suna mishi alkhairi, tow wannan kudin ya karba ya ajiye mishi yana tarawa idan ya sayi wani abu da shi sai yayi albarka, haka yasa shi gane cewa A Yaranshi Aliyu na daban ne kuma me albarka ne shi. Abin ya faru a Saudi kenan. Nayi barci kamar ba ni ba, koda na bude idanuna a gajiye kallonshi nake yana zaune akan abin sallah. Hannunshi dauke da hisnul Muslim. A hankali na fara kokarin tashi ya ce min.."Please ki kwanta za a zo duba ki!" Ya fada yana daukar wayar dakin ya danna number "ta farka!" Naji ya fada, ko minti goma ba ayi ba sai likita da nurse a gefenta, suka gama duba ni kafin suka bar dakin, likitan ya ce mishi.."akwai gajiya da damuwa a tattare da ita tana hutawa." "In sha Allah!" Ya fada yana me kallona, kafin ya shiga ban daki ya haɗa min ruwan dumi, ya fito . "Tashi ruwan na ciki, kiyi wanka zaki ji daɗin jikinki." A hankali na sauke kafana kasa, na nufi ban dakin na shiga ruwan nayi wanka, sannan na fito daga ban dakin, ya ajiye min doguwar riga da abin sallah, ina sakawa na gabatar da sallah, ina idarwa Tinah tana shigowa ta same ina addu'a, shafawa nayi ta ajiye min abincin. Sannan ta mika min newyork magazine! D'ago kai nayi ina kallonta, "me ya faru?" "Wai cewa aka yi a tarin girkin ba tab'a samun mai juna biyu da mijinta ya tsaya mata shi ya amshi kyautar da aka baki, sannan da aka tambaye shi me yasa yayi replace ɗinki ya ce kina buƙatar hutu saboda yanayin yadda kike aiki sannan kun yi da shi zai amshi kyautar." Kamar wawuya haka na sake baki ina kallonta, shigowa dakin yayi ya kafe shi da idanuna da ya cika da kwalla. "Me yasa?" Kasa magana yayi cikin fashewa da kuka nace . "Me yasa?" Na daka mishi tsawa, da yasa shi matsowa kusa da ni! D'aga mishi hannu nayi tare da cewa. "Ya isa kayi tafiyarka bana son ganin ko Inuwarka!" Hannuna ya kamo yana me sakawa a kirjinshi, wanda nake jin bugunsa kamar zai fito waje, wato zuciyarshi. "Ki saurari sakon nan don Allah!" Hawaye ne ya zubo min cikin shashekar kuka na rintsa idanuna nace mishi. "Kafin yau ni ka ajiye a inda kake, da kayi tunanin yadda zan fahimci Yaren zuciyarka, ba zaka tab'a juna min baya ba, amma sai ka juya tare da yanke min hukuncin nima mutum ce ka tab'a tunawa zuciya ce a kirjina! Kuskurena soyayyarka ka tafi ina son hutu daga kome har da kai, idan ka dame ni zan yi fatar na mutu." Hadiye yawu yayi yana kallon yadda nake kuka, tare da juyar da kai ina dan bubuga gefen zuciyata inda nake jin zafinta da kuna! "Please je ka!" Inji Tinah, fita yayi na kifa kaina a tsakanin cinyoyina duk da cikin da naji ya fara turo min. "Ki ci abinci!" Ta ce min tana ajiye min abincin. "Kin san da zuwan shi ne?" "Eh tun daga farawa yake tambayata shin kina da lafiya kuwa? Ya ga kamar kin yi rauni, ban tab'a sanin cewa kin yi raunin sai da kika yi ta zuwa na biyu na fahimci raunin da kika yi, Ummu kina son Tafida soyayyar shi kike bukata kuma ya baki amma me yasa kike rejecting dinsa?" Hawaye ne ya zubo min, "Tafida bai san meye so ba, sai ya rasa wanda yake so a lokacin da yake tsakanin sonshi a nan zai fahimci ainihin kalmar so, yanzu yana wannan yanayin ne saboda abu biyu zuwa uku, na farko kanshi da bukatarshi na biyu saboda iyayenshi da gidansa na uku saboda kada Yaransa su taso babu uwa tare da su " sake baki tayi tana faɗin. "Ummu waye ya gaya miki haka?" "Nasan da haka ne, tun kafin mu samu matsala!" Ya fada ina shan tea me dumi tare da share kwalla da yake zuba. Yana jikin kofar a jingine, sai ya rasa me mishi daɗi domin bai zata sonka shi na farko Ummu zata fahimta, gashi nan kome ya jagule shi, kamar ya saka hannu a kai yayi ta ihu, damuwa ta sako mishi kai daga ko wacce kusrwa ji yake kamar bashi ba, yana ji yana gani ya dasa kiyayar shi a idanun Ummu yana hango yadda take kin hada idanun da shi, bakiɗaya jin shi yake kamar fanko kamar bai da wani amfani, barin kofar yayi ya nufi waje. Yadda nake kuka sai na kasa gane kukan abin da nayi mishi ne ko na farin cikin abin da yayi min ne, bana ce na ji zafin abin da yayi min ba, domin ban tab'a kawowa zai zo inda nake ba, "Me yasa?" Na tambayi kaina ina wani irin kuka wanda na rantse da Allah kukan abin da nayi mishi ne, ina jin zafin shi amma bana nufin nayi mishi abin da zai kara nisanta shi da ni ba, ban san me yasa naji zafin tsawar da mishi ba, haka yasa nayi kuka sosai. Tsawon kwanaki uku, ina kwance duk wannan kwanakin ina samun kulawar da ya dace, sai dai har yanzu zuciyata bata huta da ciwon da nake ji ba, jin muryan Tinah nayi tana magana ƙasa - ƙasa, daga yadda na ji tana kallona yasa ni gano da Tafida take. "Ok bari mu shirya tunda jidda ne!" Bude idanun nayi ina kallonta. "Ina zamu?" "Surprise zamu miki!" Naji tace Jidda amma fir taki magana, haka yasa nima naki yarda na shirya ina kallonta. "Ki shirya muje duk inda zamu ai ba zan bari wani abu ya same ki ba,sannan tsakaninki da Allah koda Tafida yayi miki wani bai dace kina nuna mishi har yau abin na ranki, na zata Ummu da na sani ce me maganin kowa da ruwan sanyi ashe zuciyarta yayi rauni idan kika cigaba da fushin da Tafida zai ta nisa daga gare ki, kina son shi kina gudun tashin hankali ne, eh ba laifi ba ne." Tun daga nan na tashi na shirya na shiga ban daki nayi wanka na samu ta haɗa mana kayanmu, daga nan na shirya muka nufi airport, mun bar kasar Amurka da tarin kyauta me tarin yawa wanda na samu daga gare su saboda na zo na ɗaya, duk da haka farincikin da nake ji ba wani can ba ne, lokacin da muka bar kasar ina jikin window ina kallon kasar wanda ko a mafarki ban ta tsammanin zuwa ba. Bayan wasu awowi muka sauka a jidda, naji na gaji, haka muka isa masaukin shi kuma ya wuce asibitin, sai da muka huta har washi gari sannan muka tafi asibitin, lokacin da muka isa asibitin, anan na gane Allah da girma yaƙe, dakin Hajiya muka fara sauka inda Hajiya ta kara ya mutsewa, sai gashi ina kuka fita yayi daga dakin yana me jan Tinah suka bar ni da Hajiya da ta mika min hannunta, da dan sauri na matsa kusa da ita. "Ummu!" "Na'am!" Na amsa ina kuka domin na rasa me yasa nake jin tsinkewar zuciya, rike hannun juna muka yi. "Ki ce su kai ni Makka nayi umaran bankwana!" Cikin wani irin tashin hankali na rike hannunta gam. "Hajiya ki daina fadar haka, Hajiya kece kwarin gwiwa Tafida, idan kina fadar haka ina muke son ya cusa ranshi?" Yau na gane ashe hauka nake, shigowa dakin yayi yana faɗin. "Hajiya kin ci abinci kuwa? Ina Fanna?" "Na ci ai." Kallona tayi tana son na mishi magana. "Daadi ko zamu shiga Makka Umara ne?" Kallona yayi bakinshi ya kasa furta kome, "Are You pity for me?" Dauke kai nayi na juya mishi baya, ina jin wani irin kuka na zuwa min. "Idan kika ganin zaki iya tafiya a mota Hajiya ai ba matsala!" Murmushi tayi mishi, tana me mika mishi hannunta, ya daura hannun a saman nata. Kallonshi tayi ta ce. "kayi min alƙawarin ba zaka sake barin tayi kuka ba idan ba na farin ciki ba!" Ta daura hannunshi akan nawa, kallon hannunmu nake hawaye na zuba na rasa gane soyayya ce ko tausayi ce. "Bari nayi muku booking!" Ya fada yana me zare hannun shi a saman nawa. "Ummu!" "Na'am Hajiya!" Yadda ya juya zai fita sai ya kasa fita. "Koda ba isa Makka ba Allah ya amshi rayuwata ayi min sallah a harami don Allah! Kada a maida gawata gida a binne ni a Makka wannan shine alfarman farkon da xan nima a wurinki, na biyu don Allah ki saka idanun akan Aliyu duk cikin Yarana shine ya rasa soyayya da jin kai na uwa amma ko daidai da rana daya ban fasa kai goshina kasa ina mishi addu'a ba, nasara da sa'a ban san iya adadin da na roka mishi ba, na kara roka mishi Allah ya bashi mace tagari Allah bai kunya tani ba, ya amsa min. Ummu ga amanar Tafida don Allah na baki amanarshi ban ce ki koma rayuwar shi iya haka kika min kin cika min burina, Ummu na gode sosai da zuwan da kika yi." Ban tab'a shiga wani irin yanayi kamar yau ba, fita yayi can sai gashi ya dawo ya ce mata. "Hajiya driven yazo bari na gyara kujeran!" Ya dauko ya gyara daga ni har shi jikinmu a mace, ya gama sannan ya nufe ta, ya dauke ta cak ya daura ta akan kujeran marasa lafiya. Yana me kallona, "muje ko!" Kayan dakin na kalla. "Kada ki damu zata dawo ai kwana sati daya zata yi a Saudiya sauran a zata yi a Madinah daga can jirgi zaku bi ku dawo nan sai ki wuce gida, kiyi hakuri na miki kutse." Ban iya bashi amsa ba haka nayi ta bin bayansu jikina wani sanyi yake kamar an lullube ni da danyen nama, sai da ya kai mu dakin Asiyah wacce suke ta hira da Tinah da Fanna. "Habibi! Kayi min addu'a Allah ya bani lafiya." Ta fada tana murmushi, idanunata yana kaina ta ce. "Hajiya Allah ya baki lafiya, yau ban zo miki hira ba da nazo har rawan larabawa zan miki!" Zuwa yayi ya make kafadarta yana me rungume. "Zan dawo ki jira ni kin ji!" Sunkuyar da kai nayi ina jin wani abu yana tokare min kirji idan wannan shine kishi tabbas zan jima da wahala. "Allah ya baki lafiya, yasa zakkar jiki ne ki kula da kanki kin ji ina son ki kula da mijinki dakyau!" "Hajiya gawa kike bawa sallawu?" Gabana ne ya fadi jan kumatunta, "waye yasan gawan fari yar nan? Ai kawai Allah yasa mu cika da imani, idan kika ji labarin mutuwata kizo min jana'iza kin ji!" "Hajiya ina hanata kina farawa me yasa suke son haukata ni ne? Ita bata da hiran sai nan da shekara daya zata mutu kema kina kara tayata!" Dariya suka saka Hajiya ta ce mata. "Kin ji ko? Yanzu zai fara faɗan nashi!" Tashi tsaye Asiyah tayi tana mata rawan larabawa tana faɗin. "Hajiya kyale shi dai nayi rawan nan!" Tura keken yayi yana faɗin. "Allah ya ganar dake!" Sai yanzu na kara jin hankalina yayi bala'in tashi, domin bayan waɗannan bayin Allah babu inda Tafida yake walwala, daurewa nake ina kallon yadda ya zabge amma yadda zaka hango juriya da hakuri zai tabbatar maka Aliyu ya sauya sosai, har muka isa wurin motar ya d'aga Hajiya ya saka ta a cikin motar, sannan ya rufe inda ta zauna zan bude yazo ya bude min, na shiga sannan ya rufe min kofar yana me shiga gaban motar, asibiti bar asibitin, titi mutumin ya ɗauka a guje, ta riko hannuna tana murmushin da ya ke karawa fuskarta kyau, Ni sai naga ta kara kyau zuciyata ce ta tsinke kamar zata buga. "Ummu kwanta Babangida ya gaya min cikin ki yana nan!" "A'a Hajiya ke zaki kwanta dai!" "A'a kwanta Ummu ina son koda xan kwanta a kan kafarki ya zama na karshe haka kema nake son ki kwanta, shi wannan rayuwar da kika gani abin da kake so ba shi kake samu ba!" Ta fada tana kokarin kwantar da ni, nace mata. "A'a Hajiya bar ni na zauna ki kwanta ke!" "Hajiya ki kwanta kawai tunda ta ce hakan!" Bata so ba, haka ta kwantar da kanta tana min nasiha, da bani shawarar kada na kara yadda nayi irin kuskuren da tayi, kafin tayi shiru, a hankali muka cigaba da tafiya kafin wani lokaci ta ce min. "kun zo min da ruwa ne?" "Eh gashi!" Ya mika min, na bude mata, na d'ago kenan ina bata ruwan sai na ga kamar ruwan yana dawowa jikina ne ya fara rawa nace mata. "Hajiya ruwan baya. Wucewa ne, Daadi ruwan yana dawowa !" Juyowa yayi yana kallon yadda nake rike ta, murmushi yayi ya fara biya mata kalmar shahada daga nan na fahimci Hajiya nesa tazo kusa, "A'a Hajiya don Allah kada ki min haka A'a Hajiya don Allah Tafida yana buƙatar ki!" Tana karanta kalmar shahada tana murmushi, damke hannuna tayi da karfi da har sai da naji karar ........(Allah ka jikan Iyayenmu bakiɗaya!) 🚫 LITTAFINA NA KUƊI 500₦ 8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay Shaida biya a turo ta wannan numbers din. +2347035133148 Or +234813026964169 Ban tab'a ganin mutuwa a idanuna ba, ban tab'a zama inda wani Allah ya dauki rayuwarshi ba, yau akan idanuna a gefena Allah ya amshi rayuwar Hajiya akan kafadata a Hajiya ta cika, yadda yatsuna suka yi ƙara na kafin a hankali ta sassauta riƙewa, na ji kome na duniyar nan ya tsaya min cak, wani tsoron Allah . "Daadi mu koma asibiti Daadi!" Driven ne ya tambaye shi, ya juya Jidda ko ya? "Muje tace ko ta rasu tana bukatar ayi mata jana'iza a Makka wannan shine wasiyyarta." Ha fada da Larabci, gefen hanya ya saka driven ya sauka, ya fito tare da bude min, yana bude min na fara kwara amai, domin cikina a hautsinewa yayi. "sannu!" Ya ce min, ina ajiyar zuciya ya shiga bayan motar ya gyara mata kwanciyar, sannan ya ce min." Ki daura kanta a cinyarki kada ki takura!" Gyada kai nayi, ya juya zai shiga motar, ban san ya akayi ba, sai ji nayi ya rungume shi. "Ba lokaci Ummu!" "Kayi hakuri!" "Mutuwa yana kan kowa nima kema, dukkanmu lokaci muke jira!" Ya fada yana me nuna min yadda xan zauna, akwai abin kuka ma yaci kaniyarshi domin mutuwar Hajiya bakiɗaya na nemi kuka na rasa kuka ya ƙare sai ciwon da nake ji, kiran Abba yayi da yake Madina ya gaya mishi, sannan ya kira Asiyah. "Ku kwashe kayan Hajiya a kai masauki sannan ki ce Tinah ta nima miki sallama, ku zo Makka Hajiya ta rasu." "Wasa kake ko? Yaushe Hajiyar ta bar nan ko awa daya baku yi ba!" "Na gaya miki kuyi abinda nace ku tawo Hajiya ta rasu ki gayawa Fanna!" Ya kashe wayar, ina kallon juyowa yayi yana kallona kafin ya amsawa Balaraben "Dan koma gefen hanya!" "Zaka dawo da ita gaba ko?" "Eh!" Haka kuwa aka yi na koma gaba ya dawo baya, yana mata addu'a, ni kamar ban tab'a zaman aji ba, bakiɗaya ilimina ya dauke karatuna babu kodaya, haka yasa naji kamar bani ba ce. Tafiyar da muka yi ko digon barci babu a idanuna, bana minti ɗaya ban juya na kalli Hajiya da take bayan motar kwance ba, tare da shi kanshi Tafidan har muka isa garin Makka, duk wani doka da ake cikawa yayi, karfe hudu da wani abu aka yiwa Hajiya jana'iza a babban masallacin harami, tare da dubbanin mutane da suka halarci sallah la'asar, sai a lokacin na samu damar yin kuka, sai nake ganin kamar nice na rasa Hajiya ba Tafida da Yan uwansa ba, Hajiya ta tafida burin Yaranta su hada kai, Hajiya taso Yaranta su had'e kai koda ba zasu kasance a wuri guda ba, Hajiya ta tafi da matukar son zumuncin Yaranta, daga cikin kalaman hajiya da ta fada min ta ce min. "Ummu zumuncin daga mahaifa Allah yake sakata, idan mace ta tsarkake kanta da darajarta Allah zai sanyawa Yaranta su zama masu matukar zumunci, Ummu Hadiyya ban tab'a zina ba, ban tab'a raba kowa da dan uwansa ba, Ummu gaya min hadin kan Yarana yana da nasaba da laifina na tafi na barsu, na dawo na fifita soyayyar Aliyu akan na kowa na manta da cewa dukkansu Yayana ne, Ummu Hadiyya ki taimaka min kada kan Yarana ya rabe, naso kaina na nuna son zuciya don Allah ki taimaka min!" Wani irin tsoron Allah ne ya shige ni, har aka yi sallah Magariba da isha a lokacin su Fanna suka iso, Tafida yana bakin kofar mashigan mata, yana musu bayani, yayi sanyi kamar ba shi ba na hangosu. A hankali nake takawa har na iso inda suke. Da kuka Fanna ta rungume ni, na dan rungumeta ina kallonshi duk sai ya bani tausayi kamar zan yi magana sai nayi shiru. "Fannah saketa!" Inji Asiyah, "Hajiya ta huta, domin ciwo azaba ne;" kallona yayi ya karaso yana kallon yatsun hannuna. "Sorry da zafi ko?" Ya riko hannun yana hura min. "Ka ci wani abu?" When Ummu ta tambaye shi ya ci wani abu? Yadda nake kallonshi murmushi yayi, ya ce min. "Muje akwai clinic a duba hannun!" "Ka ci wani abu?" Na kara tambayarshi, ina kallonshi a sanyayye ya ce min. "Na koshi!" "Muje ki tea ka sha!" Riko tsinsiyar hannuna yayi yana faɗin. "tow!" Muryan shi tayi bala'in sanyi, haka muka wuce masaukin, yayi mana oda a wani parlour muka zauna muna shigowa Abba yana shigowa, gaisuwa muka yi sannan muka zauna shiru. Na rasa yadda zan fadi yanayin da Tafida yake ciki, a wannan yanayin na tabbatar da shi din babban mutum ne, ban san me yasa nake jin kamar bana iya sarrafa kaina ba, domin hatta abinci kusan yadda na saka shi a gaba yasa shi ci ba wai yana jin dadinsa ba. Yadda nake ta kallonshi yasa suka yi ta watsewa, ya rage daga shi sai ni ganin Babu kowa ya d'ago ya kalle ni. "Tsawon rayuwata nayi ba tare da ita ba, nayi ta jin haushinta ina ganin kamar tayi min wani abu, na manta Uwa tana haifar d'a bata ganshi ba bai ganta ba ta mutu." Ya ja hancinsa yana d'ago kai yayi yana kallon sama. "Ummu! Na zata duk yadda na yi mata zata yi fushi ne, na zata idan nayi ta nuna mata bana buƙatarta zata yi fushi ne, sai na ga ashe zata iya karban haka. Nayi ta b'ata mata rai, don ta ji haushi sai na ga duk abin da nayi mata, sai naga kamar farin ciki take." Numfashi yake saukewa me nauyi yana kallona. "Bayan na hadu da ke ce na fahimci girma da soyayyar Uwa, ba a tarin dukiya ba ne, ba a tarin daukaka ba ne soyayyar Uwa daban take bata da na biyunta, kamar yadda ba zan iya kwatantta zafin haihuwa da zafin mutuwa ba, haka ba zan iya kwatantta yadda soyayyar Uwa yake ba, Hajiya tayi me wuyar saura mu, mu mu rakata da addu'a. Ummu kin san me?" Girgiza mishi kai nayi, ya rike hannuna yana faɗin. "Ina son nayi kuka kamar yadda naga Abba yayi da muka iso da gawarta, sai dai I try all my best na kasa ko zubar da hawaye, Ummu ina son nayi kuka ko zan huta da abinda da nake ji sauki abin da nake ji, ban sani ba ko zuciyata ba irin naku bane, bana jin tsoro ko faduwar gaba, bana jin kome anya da zuciya a kirjina?" Ya ƙarshe maganar da tambayata, sai naji kamar bani da amfani a rayuwata idan na barshi shi daya don kanshi, "Kana da Allah kana da Abba, suna tare da kai ga As..." "Ummu ina da Allah ina da Abba ga Asiyah!" Abin da zan fada kenan ya ƙarshe min, tabbas yana da Asiyah, sai da yadda ya dauki goran ruwa ya sha, yasa ni karan jin tausayinsa sama da koda yaushe. "Ina da Asiyah, amma ki sani zan koyawa kaina zama cikin kaɗaici kafin lokacin ya zo, domin itama kokuwa take da rayuwa zata rayu ko zata mutu ! Ba mu sani ba, domin kaso me yawan gaske na kwal-kwalwarta ya lalace cutar kansa ya lalata mata su, tana nimawa kanta farin ciki ne domin bata son ta kasance cikin kad'aici, ba soyayya a cikin al'amarinmu amma kuma yarinyar bata da kowa a tare da ita sai ni, sannan nayi kokarin janye ta daga mahaifiyarta yadda zata samu nutsuwa. Ummu Mama tayi kokari ganin ta gina miki tarbiyyar da ya da ce, amma ki sani kafin na samu mace irin Mama sai an tona, from beginning Asiyah bata samu soyayyar Uwa ba, a yadda naji a bakin Saadiyyah Mahaifiyarta kwaso cikinta tayi a wurin yawon bin malamai da bokaye, bayan nan ta rasa tarbiyya da rashin kare kai, Ummu na gaya miki ne saboda na gaji da nauyin al'umma." Taysayin Tafida ya gama raunana min zuciya, ban san ina kuka ba, sai da ya rike hannuna yana faɗin. "Ni bance ki tara min jama'a ba, ni dama can haka Allah ya halicce ni, a lokacin da zan samu soyayyar gaskiya a lokacin nake rasa wanda zai so ni, na farko na rasa ki yanzu na rasa Hajiya. Bani da kowa a gefena. Na san Allah yana sane da ni kuma yana sane da rayuwata." Rungume shi nayi ina kuka, ban san yadda aka yi ba, na tsinci kaina da faɗin. "Ina tare da kai, ba zan nisance ba, ina tare da kai Tafida ba zan kuma nisa da kai ba." Murmushi yayi ya kwantar da kanshi a kirjina ina shafa bayanshi. "Ummu ina jin kadaici babu kowa a tare da ni!" "Na sani!" Na fada cikin kuka. "Ummu kin ji dad'i, kina kuka ni kuma bani da ikon yin kukan, Ummu ina son nayi kuka ya zanyi ina son naji yadda ake jin maraici, ina son nima a kalle ni a ce min maraya! Ummu ina son ganin Hajiyata, Ummu ina kewar Hajiyata!" Ya zan gaya mishi ne ya bar gaya min haka yana sani kuka? Ya zan gaya mishi maganarshi yana saka ni kuka, taya zan fahimtar da shi nima zuciyata tana tabuwa!" Taya xan gyara abinda yake tsakaninmu. "Ya isa haka!" Na fada ina cigaba da kukan. "shiiii! Nayi shiru na daina maganar. Ummu ki kira Deen kirjina zafi yaƙe min, ciwo kirjina yake min, Ummu " yadda ya birkice min a wannan yanayin yasa ni kiran Abba da ƙarfi, haka ya fito ya same ni rungume da Tafida ya rikice min kamar yaro karami irin yaron da aka yaye shin nan, ba kuka yake ba sai wani irin rikici da yake ji, kiran likitan masaukin aka yi, shi yazo aka kaishi daki, aka mishi allura. Damuwa ce tayi mishi yawa, haka yasa yake min wannan rikicin. "Maman Mufidah ko zaki tafi ki kwanta ne?" Inji Asiyah, kallo daya nayi mata fuskata babu wanda yasa ta juya a hankali ta kama hanyar waje, na kwanta a gefenshi ina kallonshi. Ina kallonshi tare da tuno zamanmu da shi da duk abinda ya faru. Zuwa yau da ya rasa Hajiya s rayuwarsa sai nake jin kamar an wanke min zuciyata bana jin fushi a kanshi bana jin zan cigaba da hukuntashi da laifin da ya dace na yafe mishi, na san yau da Hajiya tana nan ba zan dawo rayuwar Tafida ba, akwai asiyah ga Abba amma bana jin sun wadatar, shafa kanshi nayi a hankali barci yayi gaba dani. Asiyah Tun da suka bar parlourn nan, hankalinta yaƙe tashe domin idan ta ga Ummu sai ta dinga jin kamar ta ji haushinta amma idan ta tuna, cewa idan kana son ganin haukar Tafida ka tab'a Ummu yanxu zai haukace maka sai taji wani mugun tsoro, tunda suka dawo dakin take juyi, yawan tunani yasa kanta ya fara ciwo, wanda ya haifar mata da habbo,ban daki ta shiga ta sake ruwan sanyi akanta har wani lokaci kafin ta fito ta kwanta, sai dai ta kasa barci ta mike tare da nufar waje, a dan koridon din da zai kai la parlourn ta makale, tana jin abinda suke fada bata san lokacin da tayi ta kuka. Tana rike da hannunta wannan ita ce ƙaddaransu bakiɗaya. Yanzu idan Ummu bata dawo rayuwarsa ba, haka zata tafi ta bar Tafida alone wani irin kuka take mara sauti, sai take jin kamar wani abu suka yi haka ya faru su ne? Tayi kokarin rike kukanta har lokacin da Ummu ta kira Abba kafin su iso ta riga kowa zuwa, durkusawa tayi a gabanshi, tana kuka hannunshi cikin nata tana faɗin. "A'a Yaya ka farka Yaya dube ni don Allah. Ka nutsu." Ta fada tana kuka, lokacin da Abba ya fito ma tana durkushe har aka kai shi dakin. Ganin babu wanda ya ce ko Ummu zata bashi wuri don tafi kusanci da shi, sai dai yadda Ummu ta kalleta sai take jin kamar kallon nan ne na mai wuri yazo, cikin sanyin jiki ta bar dakin. Tasan za ayi haka sai dai wani irin girman Ummu take gani da kwarjinin haka yasa kome tayi take bala'in shakkar ta ko tsoronta. Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 7670 Ummu Da asuba na riga shi tashi, yana kwance da alamu barcin yayi mishi nauyi ko nace hala sun saka mishi alluran barci ne, ban iya tafiya masallaci ba domin gani nake kada na tafi wani abu ya same shi, sai naga kamar zan dawo naji labarin ya rasu shima. Bakiɗaya bani da nutsuwa. Haka yasa na zauna a dakin har nayi sallah asuba, karfe shida da wani abu ya bude idanunshi, tashi zaune yayi yana kallon inda nake. Tashi nayi na je inda yake, a hankali ya rungume ni ya daura kanshi akan cikina. Sai a lokacin naji ya sake wani irin shashekar kuka, bubuga bayanshi nake yana sai a lokacin yayi kukan da dakyar yayi shiru, janye jikina nayi na shiga ban daki na hada ruwan dumi na zo na saka shi yayi wanka da alola yana fitowa ya gabatar da sallah, sannan na fito amsar abin karya, a bakin kofar na ga Asiyah da alamu bata yi barci ba. "shiga yana ciki!" Kamar zata kifa ta shige dakin, samunshi tayi yana zaune, har lokacin hawaye bai daina fita a idanunshi ba. Zuwa tayi gabanshi ta zauna tana me rike hannunshi. "Kana son Hajiya sosai ko?" Ta tambaye shi itama idanunta cike da kwalla. "Kayi hakuri kada kayi kukan dayawa, ka manta ina da sauran lokaci ne har zuwa shekara daya! Kada kayi kuka don Allah ka yi hakuri." Rike hannunta yayi yana kallonta. "Kin sha maganinki?" Gyada kai tayi tana faɗin. "Eh na sha!" Hannunta ta kai tana share mishi kwallar da yake zuba mishi. "Kayi hakuri kaji!" Ta fada tana kukan itama. Murmushi yayi yana me kallon kofar da nake tsaye. "Shigo Ummu!" "Tow!" Na ce a hankali, ina me shiga dakin na ajiye mishi tire din, dauka tayi ta mika mishi kofin tayi tana. "Da zafi ma!" Mika mishi tayi tana cigaba da cewa. "Ko zaka surka ne?" Murmushi yayi yana kallona ya ce mata. "A'a!" Aliyu Muhammad Jadda, da na sani a baya bashi bane wannan a gabana. A hankali na juya zan fita ya ce min. "Jirgin yamma zamu bi, ki shirya kafin na gama!" "Tow!" Na fada ina me fita, kallonshi tayi ta ga har lokacin idanunshi yana kan kofar, "sha Ya Aliyu!" Kurba yayi yana kallon yadda take ta mishi surutu yana jinta har ya gama, sannan ya mike ya shirya tana ta mishi magana. Tunda na fito nake kallon wayata domin na kasa cin kome, har muka shirya sannan muka bar masaukin, zan iya cewa tunda na kifa kaina a kan cinyata. Sai dai lokaci zuwa lokaci Abba yana tambayata lafiya nace mishi ba kome, wurin karfe biyar muka iso airport na jidda, dakyar na sauko saboda jirin da nake ji. Kallona yayi yana tambayata, "yunwa nake ji!" Na fada a sanyaye. "Yunwa?" Suka kara tambayata, ya karaso inda nake yana riko hannuna. Ya tallafe ni har cikin airport din, abinci aka fara nimomin amma na kasa ci, ruwan zafi aka kara kawo min na sha sosai, sannan naji zufa na karyo min. Sallah suka tafi aka bar ni da Tinah. "Yarinyar nan tana da sanyi Sosai!" Da idanuna bita da shi, "Matar Tafida nake nufi!" Murmushi nayi da zan kira shi murmushin dole. "Eh!" Murmushi itama tayi tana faɗin. "Amma naji tana da matsalar ƙwaƙwalwa ko?" "Eh yace Cancer ne!" "OMG!" Gyada mata kai nayi, ita kanta sai jikinta yayi sanyi domin kuwa bana son ta ji haushi Asiya idan tayi wani abu, koda suka dawo na gaji don har na fara barci. "Maman Mufidah idan tana barci tafi kyau inji Asiyah tana gaya mishi. " "Nima nasan da haka!" "Amma me yasa bata cika magana ba!" "Nature dinta ce bata da yawan magana kamar ke!" Ya fada yana kallonta, yar dariya tayi tana faɗin. "Hmm! Haka dai ka ce." Ta fada tana zuwa inda nake kwance. "Ma.." "me zaki yi? Ba kyau tashin mutum idan yana barci!" "Ayya ban sani ba ne!" Ta fada kamar tayi kuka domin yadda Tinah ta mata magana. Koda Lokacin tafiyarmu yayi, shi ya tashe ni na tashi ina faɗin. "Banyi sallah ba fa!" "Ki shiga idan mun isa gida kinyi ai ke sai da Uzuri!" Ya fada yana dauke kai, yadda yake magana da kome na shi na san yana yi ne na dole,, domin ya kwantar mana da hankali, amma nashi hankalin ba a kwance yake ba, wannan abin ya ƙara saka ni cikin zulumi, wanda ya kai da ko motsin kirki bana iyawa ba tare da na kalle shi ba, tun da muka bar jidda, naji hankalina ya dawo jikina ya zamu kwashe da Mama kut, bata san nazo nan ba, wannan shi ne asalin satar fita. Hankalina yayi bala'in tashi, jirginmu sai da ya sauka a abuja, sannan muka yi bankwana da Tinah, kayan da muka saya tun zuwan mu can ta ce min zata aiko min idan sun iso, kafin mu wuce Maiduguri nayi sallah da ake bina, sannan muka jira jirgin can muka wuce, wato nice ban fahimci waye Aliyu ba domin tun anan Abuja yan majalisun wakilai na jahar Borno da na dattawa suka zo mishi gaisuwa, a lokacin yake gabatar musu da ni. "Ga Madam nan!" Sai na tsaya kallonshi, shi akewa Ta'aziya tare da ni, yana fada musu. "Ai akan cinyar Madam ta rasu, she love Madam sama da yadda take sona, ni da ta haifa." Sai suce ayya, sannu. Haka ta fita ya gama gabatar da ni a ga mutanenshi koda yake ya nuna musu Abba. Sannan muka bar Abuja, kallona Asiyah tayi tana faɗin. "Don Allah me yasa Ya Aliyu yake sonki? Bayan kin ki dawowa gare shi." Murmushi nayi domin na lura Asiyah wawuya ce sosai. "Ban tab'a cutar da kowa saboda da shi ba, na aure shi ne tun yana Tafidan shi ba yanzu da ya zama me kumbar sosa da wasu suke rubibinsa ba, ni na san waye shi kafin yau, don haka idan yayi min wani abu kyautatawa ce domin bayan ni babu wacece zata ce miki tasan waye Aliyu." Gyada kai tayi tana faɗin. "Hmm!" Ta cigaba da kallon waje, bata kara min magana ba, nima kuma ban bi ta kanta ba, domin kuwa yadda zan taradda Mama yafi kome d'aga min hankali. Koda muka iso garin ya hadu da hadari dama tun a jirgin ake fada yanayin zai iya sauyawa saboda yanayin damina da muke ciki. Muna sauka ruwa na tsinkewa, zama muka cigaba da yi a cikin jirgin har wurin karfe uku kafin ruwan ya tsaya muka fito, tawagar mai girma Gwamna suka iso karbanshi, ana ta mishi gaisuwa, koda muka bar airport abin da ya ce ya kara gigita min lissafi na. "Kiyi hakuri ki cewa Mama tayi hakuri, ban sani ba ko zan zamu kara haduwa" kallonshi nake yana tsaye har na shiga motar a jikin window ya tsaya ya ce min. "Thank you for everything!" Ni dai ban ce mishi kome ba, har muka bar airport din, shima gidanshi suka nufa. Sai da aka fara ajiye Abba a gidan yayi ta bashi hakuri da ban baki, ya gyada kai, koda suka isa kofar gidan ya samu tarin Jama'a da alamu anan zaman makoki kenan, har cikin gidan suka shiga Deen ya hango a barandar gidan yana zaune da Umar. Nufarsu yayi suka mike hannu Umar ya mika mishi suka gaisa kafin suka rungumi juna. Daga nan suka zauna yayi ya gaiswa da bakin wurin, har da Deen. Shi dai bai ce kome ba, wani almajiri yayi sallama ya shigo ya durkusa ya ce musu.."Ni muna tare da ita ne a wancan unguwar yau nake jin labarin rasuwarta to Allah ya mata rahama." Daga nan yayi ta addu'a, addu'a yake yana karawa har sai da yayi kamar ba zai daina ba, Deen ya ciro dubu goma ya bashi sadaka, a wurin a hankali suka hada mishi kudi sosai. Sannan ya tafi sai yanzu mutuwar ta shiga jikin Tafida, domin sai da ya kebe yayi wanka yayi Sallah azahar da La'asar. Domin su a masallaci zasu yi, haka ya sa shi yi a gida. Yana zaune, Asiya ta shigo da sallama abinci ta kawo mishi. "Har kin yi girki?" "A'a kawo min Fanna tayi daga cikin gidan!" "Je ki ci na koshi Deen zai kawo min abin da zan ci!" "Tow!" Ta fada tana barin parlourn, jallabiyar da yayi sallah ya sauya sannan ya fito ya nufi cikin gidan bangaren Hajiya, a parlourn kawayen Maryam da Rukayya ne ana ta cin abincin ana hira. Yadda yayi sallama yasa kowa ya shiga hankalinshi. Yadda yake musu wani irin kallo kafin ya juya zai fita, Fanna ta ce mishi. "Kowa za a kawo maka abinci ne?" "A'a!" Ya fada yana barin parlourn, mai zai yi da abincin? Barandar da Deen yake ya nufa ya zauna suka kara gaisawa. "Su Ammah sun zo, an jima zasu zo gaishe ka!" "Kace tayi min kunu." "Eh nasan zasu zo da abinci bari na ce ayi maka kunun!" Shiru yayi yana me kiran Matarshi ta gayawa Ammah tayiwa Tafida kunu, bayan ya gama wayar ya kalli Tafida. Shigowar Umar da Abubakar yasa shi zuba musu idanu. Domin ya lura da yanayin Umar da ya sanya. "Aliyu ko zaka zo zamu yi magana!" "Tow!" Ya ce yana mikewa, parlourn shi ya nufa da su, suna shiga parlourn Umar ya kalli Abubakar cikin fushi yana faɗin. "Ka maimaita abinda ka fada?" "Hmm!" Dariya yayi yana faɗin. "Ka zata tsoron Tafida nake ne da ba zan fadi abin da na fada ba? Karya nayi ne? Waye zai san shi da naci ba? Mutuwar Hajiya ba mutuwar Allah da Annabi ba ne shi ya kashe ta domin mulkinsa!" A firgice Tafida ya kalli Babban Yayansu da ya furta wannan kalaman da suka fi kome muni. Tsuma jikin Tafida yake jininshi yana wani irin tafasa, ranshi yana wani irin zafi, kallon Abubakar yayi ya ce mishi. "Ban san me kake nufi ba, ban kuma gane me kake faɗa ba ko zaka iya maimaita abin da ka faɗa!" Mamaki ya kara rufe Abubakar ɗin ya ce mishi. "Kana nufin baka fahimci abin da nake nufi ba? " "Eh ban fahimta ba!" "Jinin mahaifiyarmu ka bada domin mulkinka!" "Tow meye ribana?" "Waye ya sani!" "Ka je na barka da Allah!" Wannan shine abin da ya iya furta mishi, wato yan uwan Tafida mugaye ne, bayan Fitar su Deen ya kira ya gaya mishi kome, yana dafe kanshi. "A gayawa Abba mana!" "A'a kada ka gaya mishi kyale shi na barsu da Allah!" Ya furta yana murmushin baƙin ciki, da damuwa. Ummu. Tunda na dawo Mama ta rasa gane kaina, asalima bata tambaye ni abin da ya faru ba, amma tabbas naga yanayin sanyi da tausayi a idanunta, domin tunda na shigo gidan na samu wuri na zauna nayi kuka har sai da kaina ya fara sarawa, sannan na shiga nayi wanka da alola nazo nayi sallah. Ina zaune ta shigo tana kallon yadda nake ta addu'a, a hankali ta ce min. "Kiyi addu'a Allah ya zab'a miki abin da yafi alkhairi idan gidan Tafida ne Allah ya tabbatar idan ba gidanshi ba ne, Allah ya baki wani mijin da ya fi shi." Kasa cewa Amin nayi, taya zan gaya mata Tafida Mahaifiyarshi ta bar min amanarshi, taya xan gaya mata yanzu Tafida Amanarshi Hajiya ta bani.? Mama zata fahimci yadda ake ji kuwa? Ba ta gane yadda ake ji ba, abinci ma sama sama na ci, da Tunanin Tafida na kwana, washi gari ban tashi da wuri ba, tun bayan Sallah asuba na cigaba da barci, wurin karfe tara na farka ashe har ta bada abinci a kai gidan. Wurin karfe daya wayata ta samu charger. "Key bangarenki yana nan a hannunki?" Girgiza kai nayi na ce mata. "Yana wurinsa!" "Ki rashi zan yi magana da shi ne!" Wayar na dauka na kira shi sannan na mika mata. "Waalaikumunsalam Malam Deen, ina Tafida yake ya hakuri kuma? Hajiya lokaci yayi!" "Alhamdulillahi, yana kwance ne baya jin dadi!" "Tow ko za a samu key din shashin Ummu gamu nan dawowa." "Tow Mama za a samu!" Ya fada cikin farin ciki. Mika min wayar tayi sai godiya yake. "Gobe za a kawo miki kayanki, tunda akwai wasu a can, Yaran kuma ki bar su anan, Tafida bai da Hajiya kece hajiyar yan uwansa kuwa ba zan kyale kowani dan iska ya kara tab'a min ke ba....71 Ba dai yanayin da na shiga yasa Mama zata mai da ni ba? Ba dai damuwar da nake ciki yasa take ganin kamar don Tafida na shiga ba, idan don haka ne tabbas Mama ta sake kulle ni kamar baya, Babana na kira na ce ya bawa Mama hakuri ko na mata laifi ne. Tambayata yayi na gaya mishi, ya ce min. "Baki mata laifi ba, ina ga halin da ya shiga ne take tausaya mishi. Ki bita duk abin da ta ce." Ya fada min sai naji bakiɗaya jikina yayi sanyi na kasa magana ma, haka muka yi sallama yana ta min addu'a. Tashi nayi na saka doguwar riga, sai yafi da na yafa ina son magana amma ina tsoron yadda zata dauki lamarin. Tare dasu Uwani muka nufi har da Yaran, lokacin da muka isa Deen yana bakin kofar gidan har parlourna ya bude mana, wanda aka share aka goge, tunda muka zo naga ana ta lekenmu, "Bari xan mishi magana!" Inji Deen, Yana fita sai ga Rukayya tare da Saadiyyah. "Burinku ya cika an kashe Hajiya!" Inji Rukayya, zata kara wani maganar, kamar wanda aka koro shi sai gashi nan ya fado parlourn. "Idan baku bar min gidana ba, sai na saka an rufe ku na har abada!" Ya fada da karfi, da sauri suka fita. Zuwa yayi ya durkusa gaban Mama kanshi a sunkuye, "Umnu zata iya ruwa a duniyar da nake kuwa? Ki tafi da ita kada wani abu ya same ta." "A matsayinka na gwamna ana bawa matanka security da duk wani abin da ya dace na tsaro,ina ga suma sun isa babu me iya cutar da ita. Idan kuma suka sake wani abu ya kara faruwa ni zan shigar su kara. Yanzu rashi aka muku me zai saka muyi fushi har mu harzuka? Ummu ce dai zan dauka mata lauya domin bana jin zan kara yarda wani ya cutar da ita." Tashi yayi ya suka fita da Deen, bangaren Hajiya ya nufa Deen ya rike shi. "Gobe za ayi addu'ar Uku, daga gobe zasu bar gidanka kayi hakuri." Da wannan ya dakatar da shi, amma zuciyarshi ba dad'i, bayan Magariba su Mama suka tafi, kulawa da Tafida ya dawo hannuna a daren, duk da a halin da yake ciki tambayata yake na duba Asiyah kuwa, gaskiya naji babu dadi ya ni da nazo akan jinyarshi zai hada ni da wata Matarshi. Sai dai kuma wani abu da na kasa fahimta shine tsakanin Tafida da Asiyah waye yake jinya? Domin a lokacin da na fito duba ta, na same ta a bakin kofar tana tsugune, "me kike yi a cikin sanyin nan!" Mikewa tayi ta ce min. "Aunty Baby, dama nazo duba Ya Aliyu ne!" "Ki shiga yana cikin!" Na juya ina bata hanya, kamar zata tashi sama ta bi inda na nuna mata, tana shiga yana jingine da allon gadon. "Ya Aliyu!" Ta kira sunanshi, bude mata hannu yayi, a hankali na juya na koma parlourn. Ina jin kamar na bar gidan, amma babu damar haka. Kukanta da dariyarta a lokaci guda take yin shi, kafin can na ga ya fito da ita a hannunshi. Sunkuyar da kai nayi ina jin hawaye na zuba min, idan Wannan shine kishi tabbas bai min adalci ba, me yasa ban yi kishin Sa'adiyya ba? Ɓangarenta ya wuce da ita, ya kwantar da ita sannan ya dawo ya same ni har lokacin ina parlourn hawaye na zuba min. "Ummu!" Ya kira sunana yana zama a gabana. D'ago kai nayi ina kallonshi, hawaye na zuba min. "Nasan da zafi kuma da ciwo, amma ina son ki aro hakuri da juriya, Asiyah yarinya ce da take buƙatar kulawarmu, duk abinda yake da wa'adi wata rana zai wuce. Na rasa Hajiya." Rufe bakinshi nayi da hannuna. "Kayi hakuri ba zan kara ba. Na fahimce ka sosai." Na fada ina danne kukana, hannunshi bakiɗaya yana cikin nawa, kafin ya daura kanshi a cinyata, nayi ƙoƙarin danne kukana amma ban iya ba haka nayi sosai. Can na matsa mishi muka koma daki, a dakin ma yana kwance a cinyata. Haka muka kwana domin ina jingina da allon gadon, cikin dare naji yana nishi, bude idanuna nayi na zuba mishi, k'amkame ni yake yana faɗin. "Ban kashe Hajiya ba, bana son mulkin ma bana bukatar Ummu wai ni ne na kashe Hajiya!" Addu'a nake tofa mishi ina shafa kanshi har ya yi shiru, tashi yayi yana kallona yana d'aga hannunshi. "Ummu da gaske ni na kashe Hajiya?" Girgiza mishi kai nayi ina shafa bayanshi, ajiyar zuciya yake saukewa yana kara k'amkame ni. Lallabashi nayi muka shiga ban daki yayi alola. Kusan rabin daren mun shi ne a tare, washi gari kuwa naki barinshi ya fita da Deen muka yi magana na gaya mishi yadda ya kwana. "Tafida yana buƙatar addu'a sosai ina ga har sauka za ayi mishi!" Ya fada yana barin parlourn. *Malam Zailani* Shiru yayi yana kallon Deen, "Yanzu ka fahimci abin da na gaya maka wani lokaci da ya wuce? Tafida da kai da Ummu kuna tare da shi ne dad'i ko wuya, ba zaku iya fushi da shi ko ku rabu da shi ba, Allah ya gani ina son alakarku! Ka je ayi sadaka a rabawa kowa da kowa Allah ya kare mu da mugun ji da mugun gani, duk wanda yake da wani abu don ya cutar da shi Allah ya mai da mishi." "Amin Ya Allah!" Ya furta, sannan ya bar gidan. Tare da katon jarka zam-zam. ** Karfe goma ya farka, ina parlourn da Asiyah. Motsin da naji yasa na tashi itama tashi tayi tana zare idanu. "Ko zaki je ki kula da shi ne?" Na tambaye ta, yake tayi tana faɗin. "A'a jeki kawai!" Ta zauna tana kallon kofar, sai da na shiga na samu yana zaune. Ban daki na shiga na hada mishi ruwan wanka, sannan na fito na ce mishi "bari na turo Asiyah ta taimaka maka!" "No need Ummu!" Ya fada yana janyo ni na zauna a gefenshi. Yadda yake sauke ajiyar zuciya zai kara tabbatar maka yana kukan zuci ne,haka nayi ta shafa hannunshi har ya yi shiru sannan na raka shi ya shiga ban dakin. Fitowa nayi na ga idanunta kuru akan kofar dakin. "Tashi ki je ki cire mishi kayan sawanshi." "Tow!" Ta fada da sauri tana nufar hanyar dakin, "kin karya kin sha magani!" "A'a ina jiran ya bani ne maganin yana wurinshi!" Sai wani abu ya fado min ko shine dalilin zuwanta jiya, kitchen na dawo na ga kayan tea ne kawai na hada mana sannan na wuce na kai dakin lokacin ya fito tana share mishi ruwan kanshi, sai murmushi yake mata wanda kana gani kaga na dole ne. "Aunty Baby!" "Na'am!" "Sannu da kokari!" Fita nayi na basu wuri na bi ta daya kofar na koma bangarena, a can na gyara gidan na shiga kitchen, number na duba a wayar Tafida na kira shi muka yi waya babu kayan abinci. "A'a akwai a wurinsu Maryam." "Ka kawo min nawa kawai don ba zan amsa a wurinsu ba!" Domin idan na kai kaina wurinsu nice na zo fitina. Haka na gaya mishi na kwanta jiranshi domin nayi wanka. Wurin karfe sha daya ya kawo abincin dake an saka addu'ar sai karfe hudu na yamma, a gidanmu kuwa abincin sadaka har da masa da panke Mama tayi, a gidansu ma Hajiya Salamatu sun yi abincin sadaka tunda a gidan Tafida za ayi addu'ar, haka na daura abincin nima don ya ce ayi abincin. Kafin karfe uku n gama na kai mishi na shi, na samu Deen yana parlourn har a shi, Asiyah tana kwance a saman kujera rike da kanta. "Daadi jikin ya motsa mata ne?" "Eh dazun tayi ta zubar da jini!" "Sannu Asie!" Murmushi tayi sai lokacin na ga hancinta yayi ja alamar jini ya bushe idanunta sun wani haske sosai, "sannu ya jikin naki?" Tashi zaune tayi tana tallafe fuskarta. "Da sauki kin ga na tashi ai." Mika mata wayarta yayi yana faɗin. "Mamanki?" Fuskarta ce ta sauya daga yadda take ta kalle shi. "Dauka!" Dauka tayi tana faɗin. "Hello Mamyn!" "Asiyah kuma sai ki daina daukar kirana ya kike Ashe Maman shi ta rasu gamu muma zamu zo gobe in sha Allah!" "Eh tow Allah ya kawo ku!" "Amin Ya Allah!" Sannan ta kashe wayar ta mika mishi. "Zata zo gobe!" "Hmm!" Ni sai ma shiga duhu daga Tafida har Asiyah kamar suna boye wani abu, bayan na ajiye abincin Tafida ya ce min. "Zamu tafi wurin addu'a a gidan Abba idan zaku tow maza ku shirya!" "Tow!" Nace mishi, na shiga na shirya su Uwani suka kwashi kayan abincin muka tafi da shi, tunda muka fita take jingine da kanta. "Bakya jin dadi ko?" "Eh Aunty Baby!" "Waye ya gaya miki sunan nan ne?" "Ya Aliyu yace shi kuma yana kiranki yar ka..." "Asie surutu ko?" Dariya tai tana faɗin. "Kana son kada na fada ne!" Haka muka isa gidan, gidan ya cika sosai kamar me, muna shiga aka shiga gaishe gaishe. Idanun Sa'adiyya yana kanmu. Ta lalace kamar ba ita ba, dauke kai nayi muka wuce dakin Abba. Bayan mun gaisa ya ce mana. "Ku tafi dakin Maman Sharif!" "Tow!" Muka ce sannan muka fita, dakin Hajiya Kaltuma na nufa tana ganina ta mike har jikinta yana . "Ummu!" "Na'am Hajiya!" Na gaishe ta da ta'aziya na mata, bayan mun zauna na wuce dakin Hajiya Salamatu, anan muka zauna har aka gama addu'a aka fara watsewa, sannan na wuce dakin Inna Hajja Ganaah tana ganina ta fara gaishe ni. Sai da suka sake samu kuka. Bamu bar gidan ba sai dare, a yadda na fahimci Asiyah bata da lafiya sosai, boyewa take lokacin da muka iso gidan, na bude motar zan fita ta ce min. "Yau Hajiya kwananta uku ko?" Juyawa nayi na kalleta zuciyata tana wani irin tsinkewa. "Eh Asie!" "Allah ya mata rahama!" Tace a hankali, sannan ta sauka a motar ina kallonta tana share hancinta, dake Tafida yana tare da Deen, bin bayanta nayi har parlournta. Kwanciya tayi tana nishi, jini na fitowa daga hancin. "Ko zamu je asibitin ne?" "Ko munje basu cire min ciwon ba, ko mun je ba zasu hanani tafiya ba, don Allah kada ki tsane ni kin ji. Ya Aliyu ya gaya min cewa yana tausayina , amma so da kaunar da yake zuciyarshi naki ne ke daya akanki ya san so da ciwo!" A ranar na fara jin juyayyen kalmar so da ciwo! A madadin ciwon so ba shi da magani! So da Ciwo! Na furta ina kallonta. "Kin san ma'anar haka?" Rike hannunta nayi nace mata. "Bar ma'anar nasan So da ciwo! Domin bakiɗayanmu muka raye ne akan so da ciwo! Ina sonshi amma ina cutawa, yana sona amma bai gaza fuskartar damuwa da ciwon rai ba. Kina son shi amma ciwon sonshi ta kassaraki, bayan kina ganin kamar damar ki ce na ki samu soyayyarshi. Amma ciwo ya shiga tsakanin." Murmushi tayi tana girgixa kai ta ce min. "Ban yi miki musu ba, amma na samu abin da nake bukata na kuma samu kulawar da nake nima, Aliyu ya damu da ni ya kula da ni, ko yau na tafi na samu mutum daya a gefena. Kin san ma'anar so da ciwo? Duk soyayyar da za a baka matukar makusantanka basu baka damar shaƙar iskan yanci ba, har abada ba zaka tab'a samun soyayyar nan ba, daga farko rayuwata an samar da ita ne ta wani lalataccen matsaya, na rayu lalace gatar da nake da shi na rasa shi, domin na lalata kome, da hannuna na kassara lafiyata, saboda soyayyar da ake min babu Cutarwa a cikin shi a baya fa, amma a yanzu ina son a soni, a kula dani, a ririta ni na zama matacciyar tsiron da bai da banbanci da babu shi!.idan soyayyar da Hajiya tayiwa Tafida shine zunubin da yake bin shi, lallai na yarda so da ciwo, idan soyayyar da Tafida yake miki shine zunubinki lallai so da ciwo, idan soyayyar da Mahaifiyata tayi min! Shine zunubina lallai so da Ciwo, ciwon da bashi madadinsa sai mutuwa.... *So da Ciwo*72 "Kin more kin ji dadinki, Allah ya baki mahaifiyar da ta san kukanki tasan damuwarki, haka yasa na kara fahimtar baki san yadda rashin nagartaccen asali yake ba, zunubi zunubi ce imma ka aikata laifin, imma wani naka ya aikata ni dai na san na aikata kuma na yarda ni mai laifi ce,na cutar dake kuma na zalince kaina da hannuna, sai dai ina jin kunyar na d'ago kai da sunan ki yafe min, don nasan ba yafe min zaki yi ba." Wannan maganar ta daure min kai ta sani jin wani irin abu ya tsaya min a rai, tausayi da kaunar Yarinyar ya dirsu a zuciyata, ban sani ba ko don ban iya tashin hankali yasa nake jin kamar na yafe mata ko don duniyar bakiɗayanta ba kome ne a cikin ta ba, yasa naji ba zan iya kallonta a cikin wannan yanayin ba, tayi ta fama da ciwo yasa na mike da sauri. "Zaki tafi amma kada ki ce mishi bani da lafiya!" Ta fada tana murmushi, nima gyada mata kai nayi, na fita. Sai da na shiga bangarena na fashe da kuka, me yasa? Me yasa? Me yasa kome yazo min a hakan? Nayi kuka nayi kukan da har ya shigo ya samu ina kukan, zama yayi a kusa dani yana kallona. "Kin shiga bangaren Asiya ne?" Gyada kai nayi ina kallonshi. "Haka take fama da jinya?" Murmushi yayi yana me jingina kanshi yana kallon sama. Buga kofar aka yi bai yi magana ba, sai Ni ce nace a a shigo!" Rukayya ce da Maryam, sunyi zuru-zuru, a wulakance suke kallona. "Tafida kofar bangaren Hajiya a rufe yake." Tashi yayi ya zuba musu idanu. Murmushi yayi ya ce min. "Ki shiga dakinki, ki duba wurin kayan Yaran nan, na wurga key din bangaren Hajiya kawo min sannan ki gyara kayan da kika ga a wargaje!" Gyada kai nayi ina faɗin. "Tow!" Na tashi, kallonsu yayi da kyau ya ce musu. "Hajiya itace kashin bayan zamanku a nan, ni ban haife ku ba ni kaninku ne, idan kun shiga ku tattara kome na ku, ku koma gidan Abba kada ku yarda gobe na ganku a gidana domin Hajiya na hakura yanxu bata nan bana jin zan iya shaƙar iskar da kuka fesar." "Tafida!" D'aga mata hannu yayi yana faɗin. "Kin manta ne? Ko kin manta kuna tsaye akan kalamanku na, kashe Hajiya nayi saboda mulki?" "A'a wallahi bani ba ne Yaya Abubakar ne!" "Wallahi sai kun bar min gidana!" Yadda ya kafe haka har na kawo key ya amsa ya cilla musu, ya kuma ce musu. "Awa daya ku bar min gidana ko na dauki doka a hannu!" Jin haka yasa Maryam ta juya yana kallona. "Zaki gani!" "Ba zan ga kome ba, domin kullum ina da mai Addu'ar Allah ya kare ni, kiyi kokarin fahimtar kema Uwa ce, idan kika cigaba da bina da sharri zaki shiga uku!" Daga haka na juya ina kallonshi. Haka suka fita bakiɗaya ma sun fita a rayuwarmu,domin a ranar suka bar gidan. Suna isa gidan Abba suka gaya mishi Tafida ya kore su, shima ya ce musu. "Idan har Tafida zai iya koranku saboda masifar da take bibiyarku tabbas gidana babu masaukinku, ku tafi na yafewa Abubakar ku, in sha Allah sai Allah ya saka mishi sai kun gani a ƙwaryan cin tuwonku!" Haka suka juya suna ji suna gani suka bar gidan. Tsohon gidan Hajiya da take Unguwar Abubakar suka koma akwai kome a gidan, abinci ne babu kawai. *** Mahmoud kuwa bakiɗaya ya rasa lafiyarshi, domin kuwa yana raye ne amma bai da banbanci da mamaci, Ammyn kan Lagos, domin abin ya so tab'a mata ƙwaƙwalwa, shi yasa ta tafi da ita. Jinya Ammyn take mai ciwo da tashin hankali domin kuwa a cikin yan fashin nan bakiɗaya babu wanda bai kwanta da ita ba sai Hakim, sannan babban tashin hankalin shine cututtukan da suka mata dabaibayi, domin bayan ciwon infection me mugun ciwo, ga cutar zamani da suka daura mata. Haka ya tab'a garkuwar jikinta. Ammyn bata da lafiya sosai,yadda Hamdiyya take kuka domin gani take kamar Mahaifiyarsu ita ta amshi zunubin mahaifinsu da Mahmoud, sune da laifi ita ce da amsar hukuncin, wannan tashin hankalin kawai aka bata da shi amma bata iya ko barci. Haka tayi ta jinya. Mahmoud da aka sallame shi, barin garin yayi domin idan ya cigaba da zama zai iya mutuwa, don koda yaushe gani yake Hakim Ummu bata gama sake shi ba, akwai abin da zai kara samunshi. ** Ummu Bayan wata uku Wanda yayi daidai da shekaran daya da hawan Tafida mulki. Duk da kuwa yana fuskartar kalubale, amma da sauki duk da yan adawa ne, sai dai lokaci zuwa lokaci ana sake rumors akan shi ɗan shan jini ne. Yau da ya cika shekara daya a mulki wanda yayi dai-dai da cikan Yarana shekara daya suma, Asiyah ce da ta matsa aka dauko su tun jiya da Yaran sabirah, da suka dawo bayan rasuwar Hajiya. Suna wurinta domin tana bala'in son Yara, akwai wani abu da na kara fahimta Asiyah yar gayu ce idan ka cire shiririta, akwai wasu tarurrukan da yaje tare da ita, kasancewarta girman yola ce kuma yar gayu ce, yasa idan tana magana da turanci wanda yabi jikinta da harshenta sai ka ɗauka yanga take, a yadda ni da tafidan muka sakata a rayuwarmu sai yarinyar kome ya zo mata da sauki, kamar ba kishiya ba, domin ko zuwan mahaifiyarta tayi ta zugata tana zaginta, amma taki yarda da abinda Mahaifiyarta ta kawo mata kayan asiri kallon kayan tayi tana faɗin. "Ni da bani da wani burin da ya wuce na koma ga Allah ina mai takawa da tsoronshi zan.sake komawa baya? Mamana nasan cewa mahaifina boka ne, amma kuma bana jin zan kara yarda na sauka akan hanyar da Aliyu da Ummu suka daura ni, ki tafi da abinki bana bukata don Allah koda zaki ji labarin Mutuwata ki min addu'a, ki ce Mahaifina ya tuba ya daina abinda yake yi." "Ni zaki gayawa kin daina ? Bayan ta wannan hanyar aka samo miki tafka, lallai Asiyah ni zaki kunyata? Tow na barki da su Tafida!" Ta saka kai ta bar gidan, babu nadama a tare da Asiyah ta kawo kayan ta jibge a gabana. "Kin gansu duk kayan mallaka ce, ni da nake jin na kusan komawa ga Allah me zanyi da wannan? Kai ina a konasu!" Ta kuma fitar da shi waje ta bawa security mata da suke gidan, aka tafi aka kona su. Zuwa tayi tana kallon cikina. "Allah yasa Little me ce a cikin nan naki!" Ta fada tana murmushi. "Koda yake na ji, ance suna yana effecting ko? Kawai a saka mata suna Amatullah!" "Saboda kawai ranki ya miki dadi a saka Amatullah!" "Eh mana y'ata ce idan namiji ne a saka sunan Abbanmu na biu!" Tun lokacin rasuwarsa da yazo bayan addu'ar Uku Ya kawo mana abubuwa yarinyar nan bana sani sai dai ya ce min takira shi, haka Mama take gaya min Asiyah tafi Sa'adiyya domin tana kiranta. Kai hatta yan uwana sai da ta saba da su, karewa idan muka dauka cewa take . "Nifa idan na mutu ban yarda wani ya tab'a gawata ba daga Mama sai Aliyu kema ban yarda da ke ba, kada ki min bita da kulli dukar kabarin kishiya." Murmushi nake mata, Asiyah mutum ce kawai na kasunta bai hanata farin ciki ba, duk da a wanann satin ta dawo daga Abuja ganin likita, sam taki yarda ta nuna min sakamakon har shi mijin, kuma da ya tuntubi Likitanta cewa yayi a barta kada a dame ta. Bayan la'asar cikina ya fito sosai, na fito a hankali na ga anata gyara gidan ana kawata shi. "wai me ake yi ne?" "Ana shirin birthday dinsu twins ne. Tana tsaye sai bayani take tana nuna inda bai mata ba. "Allah gani gare ka." Na furta yana tsaye kamar wata model sanye take da wani palazzo sai riga da ya wuce cinyarta amma an kame shi daga cikinta, dama gata kamar kara. Ta saka hular da ya dace da kayan takalmin kafarta baki ne, Dora tana mata bayani. "Madam idan kin gama bayani a dauko miki madaranki!" Juyawa tayi tana faɗin. "Me ya kawo me ciki nan? Ni bana son ana show a bata mana dress code dinmu da wani abu nan kamar tulu!" "Kinyiwa kanki mtseew!" Na ja tsaki ina barin wurin, kafin karfe shida biyar an gama, ni ban san lokacin da aka shirya taron ba, ashe tun tana Abuja tayi kome nata, shima Tafidan da yake ya zama irinta har da bata kuɗi don barna. Ana tsaka da hidimar Fanna ta shigo da jaka, wai ashe har Tinah aka gayyata. Sake baki nayi ina kallon munafunci irin na mutanen da nake tare da su, tinah bata shigo min ba ta tare a wurin Asiyah kasa hakuri nayi domin naji haushi ina shiga na samu har da su Mama da Hajiya Salamatu da Inna da Hajja Ganaah, sake baki nayi ina faɗin. "Yau naga ikon Allah, sai ku zo ku tare anan!" "Ke Malama Bama gayyar mai ciki oya je ki sauya kaya, za a zo a miki kwalliya ko Tinah!" "Hey Aunty Baby!" Juyawa nayi na bar parlourn suka saka dariya. Ina komawa na zauna a parlourn, naki tashi da kanshi ya zo ya zauna a wurina. "Duk wanda kika ganshi a wurin, tausayinta yake ji, domin duk ta gaya musu bata da lafiya! Kuma zata iya mutuwa kowani lokaci. Ummu kada ki ji haushi kuce zata rabaki da kowa ne a'a' ba haka ba ne, kin san a yanzu haka tana raye ne da magani da kuma ikon Allah, shine dalilin da yasa taki gaya min. Ummu kin ga takardanta da aka turo min dakyar." Ya nuna min har da stamp da aka mata na lamar kowani lokaci zata iya tafiya ya barmu!" Sai na rasa meke min dadi. Da taimakon shi na sauya kayan jikina amma naki makeup, sannan na fito muka hadu a wurin, an kashe kudi itama ta kashe kudi, don ma Tafida yana zuba mata kudi duk wata aka bashi albashinsa, haka kawai idan ya samu allowens zai bamu kudi masu bala'in yawa. Sannan a wata ukun nan da muka yi na kara fahimtar waye shi da kuma me yasa ka a gaba, al'ummar jahar Borno suna alfahari da shi, anci an gyatse sannan ta fitar da wani takardan da ta ajiye tace musu. "Wadannan takardun nawa guda uku ne, daya na same kyauta ce a lokacin wani raka oga da nayi Abuja, ta sanadinsa na samu, shi yasa zan barwa marayun da nake rike dasu. Koda bana raye na su ne. Wannan shi yake bani duk wata za a kai gidan marayu a taimakawa Yaran da suke gidan Marayun nan. Wannan na uku tsawon rayuwata na tara kudi, amma wannan na barshi ne wa Yarana Mufid da Mufidah. " tashi tayi tana kallon mutanen wurin, akwai dadi da farinciki ka samu wanda zai rike hannunka, musamman Miji kamar Tafida. Sannan ka samu kishiya Irin Ummu Hadiyya da gaske kafin ka samu zai bada wahala, amma for me is okay domin nayi dace." a hankali take magana tana faɗin. "A cikin wata uku da muka yi bayani rasuwar Hajiyarmu, a Write story about my life da mijina da kishiyata! Amma wannan ba karshen bane wannan shine mafarin! Ummu tayi kokari amma Mahaifiyar Ummu itace jarumar, sai dai behind the corner akwai Deen da wasu bayan Deen, nayi fatan da zan rayu na tsawon shekaru sama da hamsin zan bada labarin mijina da yadda na aure shi, by connection, nayi rayuwa a past dina, amma a present dina bana tunanin xan yi dogon rayuwar da nayi a baya!" Yadda take magana tana dariya yana saka mutane nishadi, amma ga ni da Tafida tsinkar mana zuciya take, d'ago kai tayi tana faɗin. "A duniya bana tunanin za a sa samu wanda yayi choosing good path kamarshi, ba koyi sadauakrwa da juriya, idan ka ji mutum ya ce hakurinsa ya kare dama can ba hakuri yayi ba, i learn this words ta wurin mother in law na, Hajiya A'isha Aliyu, Maman Ya Aliyu, Hajiya ta ce min, Ummu tana da mutunci sosai, Ummu tayi mata abinda Yaranta basu mata ba, a lokacin da tarasa kowa Ummu ta mata adalci ta kula da ita kamar na. Tace kiyi hakuri da Ummu bata da yawan magana amma zata kula dake kamar nata, Ummu ta koyawa Tafida yadda zai kula da kowaye a tare da shi, shi Yasa yau muke moran shi wannan aikin Ummu Hadiyya ce, ta amma ba dukkan ba ne aikinta Mamanta ita ce abin jinjinawa, ina mika godiyata ga Mamanmu." Kasa da kai Mama tayi tana share kwallan da yake zuba mata .. (Allah da gaske ni gaskiya labarin nan kuka yake saka ni 😭)73 Asiyah tayi magana masu nauyi, dariya tayi tana faɗin. "Ya Aliyu ka rike Matarka, domin itace sirrinka, dangi irina da sauran lady's like me muna kyasa namiji readymade ne saboda bamu san yadda Matarka tayi kokarin gina gidanta ba, we are always looking for what we want not what she build! Hmm, ba zaku gane yadda mace take kokarin gina mijinta da gidanta ba, kawai mu wurga musu rayuwa mu shiga." Murmushi tayi ta d'aga kofin hannunta. "Ina maka fatan Alkhairi bakiɗaya rayuwarku. Ina sonka daga baya amma nasan bai zama dole ka biya ni son da nake maka ba, amma kuma ina jin kamar na samu yanci. Na gode sosai da zuwa taya mu murnar zagayowar ranar haihuwar yan biyu da cikan Ya Aliyu a shekara daya na zama gwamna!" Sannan ta koma ta zauna aka cigaba da cin abincin, kowa yana yabawa da halinta. Kallonshi nayi da yayi shiru yana kallona. "Yan mata!" "Na'am!" Na amsa ina kallonta, tana hira da su Mama. "Allah ya bata lafiya mai daurewa!" "Amin Ya Allah!" Ya fada yana rike hannuna muka karasa har inda suke muna gaida Mutane. "Tafida kai da Asiyah kun kwace min Yaran ko?" "A'a Asiyah ce wallahi!" "A'a' kaji tsoron Allah Daadi kai ne kace na dauko su kana missing dinsu ko Aunty Baby!" "Ba ruwan Ummu cikin wannan maganar ke kika dauko su!" "Ni ban dauko su ba, a tambayi Matori gashi can!" Aka yi ta dariya ana hira cikin nishadi, kafin aka watse. Shi da ita suna rungume da yaran ni kuma na ja cikina nayi bangarena, wanka nayi na kwanta. Shigowa dakin yayi yana kallon yadda na kwanta. "Ina suke sun kwanta ne?" "Eh sun kwanta nace bari na zo nayi miki sai da safe!" Murmushi nayi ya sumbaci cikina." Yana shafa cikin ya kashe min hasken dakin ina kallonshi ya fita, na lumshe idanuna, barci yayi gaba da ni. Washegari. Tinah tazo muka wuni da ita, sai dai kuma naji dadin yadda ta bawa Asie kyauta da abubuwan karuwa ya min dad'i. "Aunty Baby ya dai?" "Me nace?" Na tambaye ta cike da kosawa yarinyar nan bata ji ina sake mata zata fara saka ni magana. "Wai tambayarki nake kawai ya kike jin gullin babyna!" Tsaki nayi bance mata kome ba, domin bana son Magana ita kuma kamar dama niman hanyar surutu take yi, don haka ta cigaba da tsokanata, ina mata murmushi Tinah dariya take, kwanan Tinah uku ta koma da tsaraba me yawan gaske, sannan muka cigaba da kula da Asie wacce kullum sai ta saka mu a damuwa domin kullum gaya mana tafiya zata yi, don Allah kada wani dalilin mara tushe ya lalata zamanmu. Bana ce Asie tafi ni kaunar zamana ba, amma tabbas ina son zaman gidan mijina duk da kuwa nasan waye shi, kuma nasan halinsa -- A wata uku da rasuwar Hajiya su Maryam suka gane wani bangaren da Hajiya ta ta rufe musu, domin dai abincin da zasu ci sai da ya gagare, da gatansu a garin Maiduguri amma abincin da zasu ci ya gagare su, sannan wani babban tashin hankalin shima Abubakar ɗin garin son zuciya sun tabka wani rashin mutunci inda suka kwashi kudin da zasu yi rubda ciki akai, kawai sai gashi an kama su kuma aka sallame shi, Deen ne ya tsaya akan case din domin Tafida da Abba sun ce babu ruwansu, Umar da ya rike Allah cikin lamarinsa sai gashi yana.ta samun nutsuwa da nasara akan aikinsa, yayinda tafida ya kara mishi wani hanya ya tafi Japan akan kasuwancin karo, Tafida ya zuba musu idanun ya kuma rungumi abin da yake nashi. Yau muna zaune a parlourn, Asie ta shigo tana kallona. "Don Allah dubi yadda kika koma? Kamar wata mage tashi akan cinyar Yayana na kwantar da kaina." "Asie kyaleta don Allah cikin yana juya mata ne!" Zama tayi kusa da shi, tana tambayar shi. "Haihuwa ce? Na shirya kaya mu tafi asibitin? Yaushe ne EDD dinki?" "Barta haka ta huta mana!" Shiru tayi sai kuma ta mike tayi gaba kamae zata fita sai ta dawo ta ce mishi.."Ta fada nakuda ne?" Daga shi har ita suka kara cusa min takaici na ce mata. "Zaki saka kiraren kafafunki, ki bar min parlourn ko sai kora ki da pillow!" Na fada ina kallonta. "Allah ya baki hakuri!" Ta zauna kamar zata yi kuka, "ina ma da ni ce." Ta fada tana hararata. "Sai kin fi kowa raki." Tura baki tayi tana hararan Tafida. "Ina kai ne ka k'i min ciki ina da nima ina ta tutturawa." Bashi ba har ni sai da muka fashe da dariya, domin wallahi Asie mahaukaciya. "Tow kai me yasa ba zaka mata ciki ba, gashi nan tana tafiya bata tutturawa." "Bana son shiga wannan maganar" ya kafe ta da idanu. "Tow me na kallona!" "Ashe kin gane ina kallonki!" "Tow me kake son nace!" "Addu'a nake miki Allah ya baki haihuwar!" "Amin amma kasan ba zan iya haihuwa ba ai, na fada ne kawai don raha!" "Na sani nima bance ki fadi kome ba, Allah ya baki lafiya sai Ummu ta kara miki da new Baby." Murmushi tayi tana faɗin. "Da zan yi nisan kwana!" "Tashi ki tafi ki cigaba da bawa su Mufida labarin yadda zaki mutu kafin lokacin yayi!" "Aunty Baby ki ce ya daina korata." "Tow kema ki daina maganar nan mana!" "Ya Aliyu ka ce ta daina bin bayanka!" Dariya abin ya bani kamar wata yarinya kowa ya mata magana idan bai mata ba zata kawo karanshi. Haka muka cigaba da hiran kiranshi aka yi a waya ya dauka, fuskarshi ce ta sauya ya kallemu. "Duk wanda ya sake suka shigo min gidana, sai ya rasa aikinsa na rufe shi." Daga can aka ce Yes Sir! Kallonshi nayi, kamar zan yi magana sai na fasa ko jiya mun yi maganar da Fanna tace sai kiranta Maryam take tana cewa ta dibo mata abinci, basu da abinda zasu a cikin wata uku kawai sun sayar da kayansu da gadon da Hajiya ta bar musu. Shiru Asiyah tayi ganin yadda ya fusata, tsoro ya sata dawowa gefena, kaina a cinyarsa. Sai tab'a ni take ina ji naki kulata. "Hakkinsu ne ka basu abinda kake da shi!" "Inji waye?" "In Allah da Manzonsa!" Na fada a zafaffe, zuba min idanun yayi yana mamakin yadda na fusata. "Ba zan bada ba!" "Zaka bada fa, don ni tun jiya na hada musu kayan abinci, a samu Kwamishinan jin kai da walwala ya basu ka tambayi Deen na gaya mishi saura a tura musu ne!" "Me yasa? Tow banyi niyya ba!" "Ai ban basu da niyyarka ba, na basu da niyyar Allah ta bawa Asiyah lafiya ne. Sai kuma da niyyar na sauka lafiya!" Sake baki yayi yana kallona, abin mamaki ya bashi yadda na tsaya ina ta fada sai abin ya bashi haushi ya bar mana parlourn yana mita, kallona tayi tana me dawowa gabana ta ce min.." Yayi fushi fa!" Dariya nayi na ce mata. "Zai huce ma!" Tayi shiru kafin ta sake matsowa ta ce min. "Me yasa kika yi haka kin san ranshi zai b'aci!" "Saboda wasiyyar Hajiya ce!" Gyada kai tayi tana faɗin. "Gaskiya ne abin a duba ne!" Wani lokacin kamar me wayo dai tayi abin sai ya dame ta, ashe fitan shi kiran Deen yayi cikin masifa da tijara yayi ta bala'i akan me zai munafunce shi! Dariya Deen yayi ya ce mishi. "Ka godewa Allah da ka samu irin Ummu wife material, idan ka fahimci kanka ba zaka na ihu akan abinda Ummu tayi ba, katse wayar!" Ya kashe yana shiru. A bangarensu Maryam an kawo kayan abincin, amma Rukayya ta kwashe rabi tayi gidan Dillaliya da shi, domin dai ta saba da kashe kudi da na sata da nata, kuma kafin tafida ya cire subsidy din da yake basu, ba karamin wasa da kudi take ba, haka yasa ta saba da kashe kudi, kuma ko kafin Zaman shi gwamna Tafida ya bauta musu. Bayan sun bar gidan Tafidan suka dawo nan tsakaninsu da Abubakar abin karya wane! Idan aka basu ba ankara basu sai kuma gobe, a da can abincin yana nan jibge sai yadda ya musu, a lokacin su dafa su bawa Hajiya ma tashin hankali ne, musamman ita Maryam kome Fanna take yi, kowa yasan yadda ciwon sugar yake da baya son kome, amma haka zata shiga kitchen ta dafa abinda ranta yake so ta zuba wa Hajiya, idan Tafida yazi ya gani zai magana Hajiya rike shi take tana girgiza kai ta ce mishi. "Uwa tana haifar yara goma ta kula da su, amma a cikin goman nan Allah yana iya cire daya da ba zata ba ya kyautata mata sauran taran tana kulawa dasu saboda dayan nan da ta tallafeta." Sai ya rasa yadda zai yi, yasa zuwa ya samu anyi abincin da ya dace a zuba ganye haka zata ki zubawa, idan Fanna tayi magana ta fara masifa tace tafita son Uwarta ne? Haka zata yi ta masifa tana zagin Fanna. Ita kan bata magana sai dai tayi shiru. Yau gashi an wayi gari abincin da zasu ci ya fi karfinsu, kamar su yi sata gara ma Rukayya tana fita yawonta, taci abinci. Ita kuma Maryam bata fita sai kunci da yake damunta. Ranar da ta samu Abubakar a gida ya rufe idanun yayi mata rashin mutuncin akan bai sakata kashe aurenta ba, shi ba Tafida ba ne da zai na musu barin kudi, shima yanzu nima yake. Ya kuma gaya mata har wurin Abba ya je ya saka baki a dawo da shi aikinsa yayi mishi koran kare, amma zai sami Hanyar da zai koma bakin aikinsa, sai yayiwa Tafida sanadin da ba zai kara sha'awar siyasa ba. Dake mugunta da hassada ya ginu a ransu, haka suke ta kullawa. Amma Allah baya basu nasara, ba don kome ba, Tafida ya samu albarkan Uwarshi, shi ne bai samu gatan da suka samu, amma shi ya dace da rabuwa da uwa lafiya, Hajiya har ta mutu tana jin zafin rashin zuwan Abubakar ya duba ta ko lokacin da suka bar kasar ita take kiranshi ta tambaye shi ya suke, wai shi ya kullaci Hajiya akan me zata zauna a wurin Tafida saboda don ya zama gwamna, wannan bai isa ba haka tana jinyar nan basu tab'a kiranta ba, ita din dai zata bisu har gara Umar kullum zai kira, su gaisa shi yasa tana rasuwa kamar wnada aka gaya mishi ya kira Tafida yana tambayar shi. Ina Hajiya yana jin kamar wani abu ya same ta, ya gaya mishi ai ta rasu, kuka riris yayi. Sauran duk sun ji mutuwar amma bai wani dame su ba, domin suna ganin kamar don basu da abin duniya Hajiya ta tare a jikin Tafida idan ta tafi sai tafida ya bita da abin duniyar, yadda Maryam take fada kenan, ta fifita Aliyu sai su bita da abin duniyar ita ba don Allah ya ce yiwa iyaye addu'a ba, wallahi da ba zata yiwa Hajiya ba domin kiri-kiri ta banzatar da rayuwarsu ta rungume Sabira da Tafida. Abin yana masifar bata mata rai ai suma Yaranta ne sai dai bata san darajar da Allah yiwa wanda zai rungume uwa a lokacin da take gab da komawa ga Mahaliccinta ba, bata san falalar da Allah yayiwa wanda ya kyautatawa wanda ya rabu da uwarsa lafiya ba, ko nace basu sani ba basu sani ba suna da yawo da bulayi amma tabbas asara da tab'ewa ta tabbata akan wanda ya wofatar da mahaifiyarshi, boni ya tabbata ga wanda yayi wasa da iyayenshi, zai kasance mara daraja da albarka da sun san yadda tafida ta rabu da hajiya lafiya da sun ta kwad'a kansu da kasa suna kuka. Amma ina idanunsu ya rufe da kishi da hassada gani suke kamar zasu kashe kome basu domin ganin bayan Tafida. -- Lokacin da ta dawo domin Fanna ta kirata ta gaya mata an kawo kayan abincin, tasan halin Rukayya duk da hankalinta ya tashe yake amma tasan idan ta kara jinkiri Rukayya zata iya salwatar da abincin haka yasa akan lokaci ta isa sai dai ta makara domin kuwa Rukayya ta kwashe kashi saba'in cikin dari na abincin ta sayar, sannan ita kanta bata san inda ta kai kudin ba, domin ta dawo gida da kudi. Bata san cewa Dillaliyar da ta kaiwa abincin ta saka danta yana sane ya biyota ya kwashe kudin, sai nima take tana fadin. "Wallahi kudin nan ta bani har dubu dari da goma amma kamar tsafi ya zube!" Kuma ai dama a kudin aka bata ba, rufa ido ne aka mata sannan takardun kudin da aka bata yaron ya biyota ya sace bata sani ba, wannan abin ya ƙara fusata Maryam ta fita cikin fushi ta dauko katako ta shiga dukan Rukayya kamar zata kashe ta, abu goma da ashirin ya same ta domin Ubansu Naziha ya kirata yana ta fada da zaginta yau kwana uku kenan an nemi Naziha an rasa wannan tashin hankalin da me yayi.kama haka suke ta yawon niman inda take babu labarinta, dab zata dawo ne aka kira su wai ga naziha an kaita asibiti, daga hotel din da aka kaita, abin babu dadin ji, domin kuwa yarinya karama ta hadu da iftula'in rayuwa, na farko an bata kwayar da fitar da ita hayacinta, haka bai isa ba sai da suka dauki hotonta tsirara suka bari a wayarta tare da barazanar idan wani abu ya faru sai sun fitar da videon, duk da mata ne dukkansu amma asibitin sun tabbatar da an tab'a jikinta, domin gabanta kamar an saka reza an yanyankata don kuwa ta hadu da yan iskan mata ne, suka mata rashin mutunci, kuma ba kome ba ne ja janyo haka sai yadda Uban ya watsar da su,babu abincin babu kulawa tunda uwar gidan gifan dake itama sakarya ce. Shima Uban ai matar da ya aura yar iska ce domin sanadinta Yarinyar da babu ruwanta ta hadu da yan iskan kawayenta, suka ja ta zuwa hotel din da cewa zasu bata kuɗi kawai abu zasu yi da ita, wannan tashin hankalin Maryam ta gani ya kara fusatatta, yasa ta rufe Rukayya da duka kamar jaka. Ai kuwa ihun Rukayya ya janyo makota aka zo aka kwace ta a hannun Maryam taci bugu, ta shige daki ta rufe kanta, tana faɗin.."tabbas Ummu ce, wallahi ba zan yarda ba, yadda aka lalata min Yarinyata sai lalata miki naki yar wallahi baki isa na Ummu kece kika yiwa Naziha asiri!" Haka take ta fada tana kuka domin tayi imanin cewa Ummu ce zata mata haka, kaf duniya bata da abokiyar gaba kamar Ummu. Don haka sai ta dauki mataki akan Ummu domin Ummu ce zata mata haka. Rukayya fa sai da Abubakar ya kira Umar aka kaita asibiti domin ta mata jahilin dukar da ko motsi bata yi, sai da ta sha ruwa na tsawon kwana uku, a lokacin labarin ya isa kunnen Tafida ko ta kansu bai bi ba. A can asibitin da Naziha take, har yau bata farka ba, domin kwayar tayi mata karfi......74 Hankalin Maryam yayi bala'in tashi, idan ta tuna Naziha. Haka tayita zirga-zirga akan Naziha sai da ta kwashe kwana goma kafin ta farka, duk da kakarta ce akanta itama ganin bata farka ba, Yaranta mata suka zugata ta bar asibitin da cewa ba zata yi jinyar yar kwaya ba, tana addu'a bayan ta idar da Allah Naziha ta farka. Kallon Mamanta tayi tana lumshe idanu tana son ta tuna abinda ya faru. A hankali ta tashi zaune, sai lokacin Maryam ta lura. "Naziha?" Kallon Mamanta tayi, tana lumshe idanu tana budewa. "Ya jikinki naki? Bari na kira likita." Haka ta fita can sai ga su tare da likita da nurse, aka duba ta, ya mata tambayoyi ta amsa mishi. Sannan ya kalli Maryam ya ce mata. "Alhamdulillahi, ki bata abinci ta don ta dawo hayacinta!" "Tow na gode sosai!" Godiya tayi ta mishi kamar ta kwanta a kasa, bayan ya fita ta dauki kwano tana faɗin. "Naziha muje kiyi wanka da alola!" Sauka tayi a gadon suka shiga ban daki, ta haɗa mata ruwa. "Ko na miki ne?" "A'a xan iya!" Ta fada tana tsaye tana kallon ruwan. Bata san yadda zata ce ba amma tausayin Naziha ya cika ranta, haka ta fito ta kira Baban Nazihan ta gaya mishi, ta farka ta buga kofar tace mata."bari na nimo miki abinci!" "Hm!" Ta ce mata, sannan ta fita a ban dakin kuwa kuka yarinyar ta fashe mai karfi, yunwa, duka, azaba suka kaita wannan abin. An hanata makaranta balle tana samun sauki don tasan idan ta je gidan Uncle Tafida Aunty Ummu ba zata hanata abin da zata ci ba, shima Uncle ba zai kore ta ba. Amma Kakarsu ta hana su don kada wani ya ji tausayinsu ya taimaka musu. Amma dake an shirya wannan lamarin kai tsaye aunty Dayyiba ta aike ta hotel wurin kawayenta. A hotel din. Tayi kuka sosai, kanta a sunkuye tana kallon ruwan hawaye na zuba mata. Aunty Dayyiba ce da kawayenta. Ja da baya tayi tare da durkusawa jikinta yana bala'in rawa. Dariyar da suka hadu suna yi yasa ta ji kanta ya fara juyawa kafin su kai hannun jikinta, ta zube a bandakin ta suma. Lokacin da Maryam ta dawo ta ji shiru buga kofar tayi amma shiru kara bugawa tayi, amma babu amsa kawai tana buɗe kofar ta hangota kwance. Hankalinta a tashe ta saka mata kaya, ta fito da ita ta fita, sannan ta kira likita. Suma sun y mamakin amma kasancewar kwayar bata gama barinta ba, shi ne dalilin sumanta. A hankali suka gama kome sannan suka fita, ita kan ta ga Jarabawa. Halin da take ciki babu bukatar tayi kuka, tasan Naziha yarinyar kirki ce, bata da wannan yanayin da zata lalace har haka ba. Sai dai idan asirin da Ummu tayi mata ne, matsuyaciya ita ce zata mata asirin. Zata rama ba zata tab'a barin abin ya tafi a haka ba, sai dai duk abinda zai faru ya faru. *** Ummu Tunda Fanna ta gaya min halin da Naziha take ciki domin Maryam tana gaya mata kome, sai dai ta boye min cewa ni Maryam take zargi da nayiwa Naziha asiri, bana son ina samun matsala da Tafida akan yan uwansa ne haka yasa na share zancen amma na kira Mama na gaya mata, kamar yadda na zata matar nan balbale ni tayi da fada tana faɗin. "Ban yarda ki je ba, domin zata iya miki wani abu babu wanda zai bu bayanki!" "Amma ai jinya ce ta wuce kome, kuma ko ba kome ai abin da ya faru ya riga da ya wuce don Allah ki yi hakuri!" Yadda ta yanko min wani katon ashar yasa na rufawa kaina asiri nima dai da saka kaina Uku goro a miya. A hankali na kashe wayar, sannan na kira Fanna. "Ki kai musu abinci asibitin!" "Kin san an sallami Rukayya! " "Me ya same ta itama?" "Wai Maryam ya buge ta da katako!" "Allah kadiran a lamanya sha'u! Tow tana ina ita;" "tana gidansu!" "Yanzu sai ki kaiwa su Maryam! Don kin ga ban ji labarin ba sai jiya da kike gaya min, na zata Tafida ya gaya miki!" "Ba zai gaya min ba domin zai ce na cika shiga abinda bai dame su ba!" Shigowar Asiyah yasa muka yi shiru, kamar wacce Tafida ya sakata zaman yar lekan asirinmu duk abinda ya tambaye ta sai ta faɗa, wani lokaci kamar na mangareta. "Gulmar wa kuke?" "Bamu kira sunanki ba;" inji Fanna, "tow ai kun huta!" Ta fada tana zama a gefena, muka cigaba da wani hiran, Fanna ta barmu ta wuce ta dauki abincin ta fita. "Ina zata?" "Gidan Abba!" Daga haka nayi shiru domin ta fini kwakwa. Bayan Magariba muna cin abincin da shi, sai kallonshi nake har ya tsargu. "Ummu ci abinci mana!" "Na koshi ne!" "Tow me kike so?" "Asibiti zamu je duba Naziha." A harzuke ya d'ago kai yana kallona. "Fatan Hajiya ce, ni kuma ba zan gushe ba sai na iya yina!" Na fada ina cin abincin. "Au dama shine kika saka Fanna ta kai abincin?" D'ago kai nayi na harari Asiyah. "Kiyi hakuri tambayana yayi!" "Sam baki da wayo!" "Kiyi hakuri!" Haka na cigaba da cin abincin. "Babu inda zan je idan zaku Bismillah." "Hmm zaka je wallahi!" Na fada ina kallon cikin idanunshi. "Ummu!" "Meye matsalarka da yan uwanka? Me yasa ta kowani fuska ba zaka fahimci yadda kake kara nisanta ni da kwanciyar hankali ba? Kai kasan kuskuren da kake aikatawa kuwa? Idan baku yafiya da afwa gaya min taya duniyar zata zauna lafiya ce maka aka yi wayonka ne ya baka damar zama cikin amincin Allah? Idan kana son nisan kwana da kyakkyawan karshe ka rike zumuncin kada ka ga don ina tare da kai ina matsa maka wata rana ba zama dole na tuna maka girma da daraja na zumunci ba! Na koshi!" Rike hannuna yayi yana tab'a shi a hankali, kuka Asiyah ta saka tana faɗin. "Me yasa kike fada har haka!" Murmushi yayi yana faɗin. "Shi kenan ku shirya muje!" Nayi mamakin saukowar shi,.amma nasan daren yau sai dai na hakura da barci da asuba zan yi domin duk lokacin da muka yi irin haka sai ya fanshe a shimfidarmu. Bayan mun gama aka shirya har da Fanna muka.nufu asibitin, tunda muka shiga muka samu yarinyar tana zaune a tsakiyar gadon. "Nazy!" Ya kira sunanta, tana ganinshi ta cire karin ruwan hannunta ta nufe shi tana faɗin. "Uncle don Allah kada ka tafi ka barni zasu zo wallahi sun ce zasu zo, don Allah ka tafi da ni!" Ta juya kaina tana faɗin. "Aunty Baby ki tafi dani don Allah ki tafi da ni, wallahi zasu zo " yadda ta rikice mana sai jikin kowa yayi sanyi. "Zaki zo ki zauna a wurin Dodonkin ko sai na zabga miki mari!" Uwar ta fada fusace, duk da ranta tayi farinciki da zuwansu amma kuma maganar gaskiya taji takaicin zuwa dasu Ummu da yayi domin tasan tazo ne ta ga yadda Naziha take ciki, "Ya mai jikin?" "Da sauki!" Ta bawa Asiyah amsa fuska a sake, ina bude baki nayi magana ta wani dauke kai, taki amsawa, yadda tayi min haka shima yayi mata domin bai tambaye ta ba, gaban yarinyar ya je ya durkusa yana tambayarta me ya faru, kuka ta fashe da shi ta ce.."Uncle yunwa ga duka, bana zuwa school Baba ya hana ni fita, shine Aunty Dayyiba ta aike ni wurin kawayenta a hotel, tunda naje.suka kwace wayar hannuna suka bani wani abu daga nan ban kuma sanin inda kaina yake ba, na rantse iya gaskiyar kenan!" Ta fada tana kuka, d'ago kai tayi tana faɗin. "Uncle wallahi suna zuwa na gansu sun zo!" Shiru yayi yana faɗin. "Ba zasu kara zuwa ba, za a saka miki security a bakin kofar kin ji!" "Uncle ba zan koma gidan Babana ba ko? Aunty Dayyiba!" "Ba zaki koma ba!" Ya fada yana shafa kanta, a hankali ya mike yana faɗin. "muje Ummu! Baby zan ga likitan sai mu ga yadda za'a yi kinji!" Mika mishi hannu tayi ta ce mishi."promise!" Juyawa yayi yana kallon Uwarta. "I promise!" Ya haɗa hannunta, ya tuna lokacin tana yarinyar idan ya je gidansu zai tafi sai ta tambaye shi zaka je ka dawo ne promise zaka dawo! Fita yayi ya samu duk likitocin asibitin ga su nan, "Matori ka turo wasu su kula da yarinyar, Ummu ku jira gani nan zuwa." Sannan ya nufi likitocin ya ce.."ina bukatar bayanan Yarinyar nan da awa daya, a turawa Kwamishinan lafiya, zai kawo min sannan a kula da masu shiga cikin dakinta tana razane har yanzu." "In sha Allah za ayi haka." Juyowa yayi ya saka mu a gaba muka dawo gida. Tun a hanya na kalli Mufidah bakiɗaya sai naji jikina yayi bala'in sanyi. Yarinya kamar Naziha ace wani ya wasu sun mata haka abin da tashin hankali, haka muka isa gidan , ban san meye shirinsa ba, amma da sassafe sai ga Deen, yana zuwa suka shiga tattaunawa, anan ya karya sannan ya fita shi kuma ya tafi office. Yaran na wurin Fanna, shiru ban ga Asiyah ba na tafi wurin. Na buga kofar Amma shiru kuma naji ya zo wurinta amma kamar bai shiga na ne, ko ya shiga oh. Ina shiga naji kar'ar ruwa, na ta zuba leka dakin nayi naga ruwa har cikin dakinta. "Asiyah!! Asiyah!!! Asiyah!!!" Na kara buga kofar ban dakin. Daga karshe na bude kofar ban dakin, a kwance na ganta a kasa da sauri na isa gare ta ina kiran sunanta amma shiru, waje na fito na wuce dakina na dauko wayata, kiranshi nayi. "Don Allah duk abinda kake ka dawo yanzu nan Asiyah!" Na kashe wayar, na fito na koma dakinta, kayan ta na ciro na saka mata, doguwar riga zan iya cewa ban tab'a kula da wani abu na musamman a rayuwata kamar asiyah ba, ana kishiya kishiya amma Asiyah kishiya ce da naso ta da dukkan rayuwata da zuciyata, jingina ta nayi, na cincibota zuwa waje, ban san da na fashe da kuka ba, ina janyo ta tsakar dakinta. Ina me rungume ta, ina jin karar saren dinsa, na kara rungume ta. Haka ya shigo yana ganin mu ya sa jikinshi yayi mugun sanyi, yana isowa ya ce. "Sako hijabta mu tafi!" Ya dauke ta, hijab dinta na dauka muka fita, wato Aliyu ba iya shi kaɗai yazo ba har da likitoci suka zo, haka yasa muka nufi asibitin, tunda muka isa cire babban rigarshi yayi aka bashi kayan aikin ya shiga dakin Emergency, zama nayi jin kamar zasu fito ace ta rasu, Deen yake bani hakuri har tsawon awa uku kafin suka fito. Aka wuce da ita ICU. Zama yayi a kusa dani, na daura kaina a kafadarshi. Ya rike hannuna yana faɗin. "Idan sun kaita dakin ki shiga ku yi bankwana domin bai zama dole ta kara bude ido ba, Asiyah tana mana bakwana, ashe abubuwan da take yi tafiyar ta ce take mana bankwana,ko kafin na fita tana fada min kanta na ciwo, na bata magani ta shiga wanka. Har zata shiga ta juyo ta rungume tana faɗin. Ina sonka Ya Aliyu ka so ni mana, don Allah ko akan gawata ka furta min kana sona nima, idan kayi min haka Allah zai amintar da ruhina! Ina sonka ina sonka ina sonka!" Yayi shiru, ya rike hannuna ya cigaba da cewa. "Rabona da tarayya da ita tun kafin mu tafi Saudiya, amma yau ta bukaci haka na juya mata baya. Bata yi fushi ba sai ce min tayi iya haka ma ya min wallahi na gode sosai, ni dai ina sonka!" Shi yake bani labarin ni ce nake kuka ina faɗin. "Me yasa baka bata abin da take so ba, me yasa baka mata yadda take so ba, wallahi da ace wani abu ake bukata domin Asiyah ta tashi na rantse zan bada xan bata tana son rayuwa tana son rayuwa da mu, Ya Allah ga baiwarka Ubangiji ka tashi kafadarta...75 Na fada cikin shashekar kuka, wani irin tausayin Asiyah na kara cika min zuciya," me yasa? Me yasa sai wanda muke fatar mu rayu da sune suke tafiya su bar mu?" "Kada ki tuhumi Allah da abin da ya tsara mai kyau ko mara kyau!" Kifa kaina nayi akan kafadarshi, ina shashekar kuka domin na rasa yadda xan yi idan har Asiyah ta tafi tow daga ni har Tafida zamu zama abin tausayi, shima zuwa yanzu na fahimci son da yake mata, ba na wasa ba ne, duk da yana boyewa amma nasha ganinsa yana zama yayi zurfin tunani idan na tambaye shi akan me yake zaune har bai yi barci ba, murmushi yake ya ce myanzuin. "Kwanta kawai, Asiya nake tunanin inda xan kaita ta samu lafiya, ina son ganin ta samu lafiya itama!" Ashe ba lafiyar bace, abokin tafiyarta ce. Har aka fito da ita suka wuce ICU, na kasa binsu dan adam ba a bakin kome yaƙe ba. Musamman idan Allah ya jarabci lafiyarshi. Tunda na isa bakin kofar daga bakin kofar nake hangota domin dakin ba a cika shiga ba, nima abin da yasa aka bar ni na shiga don matsayin Tafida ne, zuwa yayi ya rike hannuna ya shigar da ni dakin, gaban gadon naje na tsaya, hawaye na zuba min. Tsayawa nayi ina kallon Asiyah, Allah mai kyauta da ƙari. Wata Nurse ce ta zo ta ce mana. "Yallabai ko zaka fita da Madam!" Juyawa yayi ya kalleta, ta sunkuyar da kai. "Muje Ummu!" Ya kara riko hannuna muka fita, a ranar nayi kuka kamar kaina zai fashe, karshe ciwon kai ne ya kama ni babu ji babu gani, haka ya wuce da ni gidan Mama, a can na wuni, da dare suka dauko ni a lokacin yake gaya min Asiyah Mahaifiyarta tazo kuma dama Mama sun tafi dubata. Sai dai an hana kowa shiga, koda muka dawo gida ranar raba dare nayi ina fadawa Allah matsalar Asiyah, shima a bangaren shi haka ce lallai Asiyah ta tab'a rayuwarmu ta shiga rayuwarmu tayi mana kane-kane ta shiga yadda babu wanda zai iya cire ta. Wurin karfe uku na kwanta shima barci da jiri ya dame ni na kwanta. Barci me nauyi ne ya dauke ni. Hajiya na gani zaune akan wani kujera ga korayen ciyayi sun lullube inda take, hannunta daya riƙe da casbi, sanye take da fararen kaya, fuskarta tayi fayau sai dai murmushi, "Hajiya kina huta ne?" Murmushi tayi ta mika min hannu. Na mika mata na zauna a gefenta. "Ummu Hadiyya!" "Na'am Hajiyata!" "Na gode sosai! Kada ki daina kada ki fasa! Allah zai kare ki da Yaranki, ki yi hakuri na tafi ban karasa abin da ni ce musabbabinsa. Ki kula da Tafida kin ji shine abin da zan kara rokonki akai." Tashi tayi tana faɗin. "Allah ya albarkaci rayuwarku!" Zan bude baki nayi magana, shiga sallah asuba ya farka da ni, bude idanun nayi ina faɗin. "Hajiya !" Tashi zaune nayi ina tuno murmushin da na gani a kan fuskarta, kamar zan yi kuka na tashi zaune ina me nufar ban daki, tsarki nayi tare da sake sabon alola, na fito na tadda sallah, ina idarwa na wuce gado na kwanta, zazzabi ne ya rufe ni. Na kwanta ban farka ba sai karfe sha daya na safe, kallon Tafida nayi gabana ya fadi. Tashi zaune nayi ina zare idanu. "Lafiya? Ya jikinta?" Zuciyata tana kara tsinkewa ganin yadda na ke wurga idanuna akan fuskarshi ina jiran naji me zai ce min ya saka shi dariya.."Alhamdulillahi jikin da sauki." "Saukin gaske ko sauƙin hausawa?" Jan hancina yayi yana faɗin. "Saukin gaske mana, Allah da sauki sosai jikinta!" Daura kaina nayi a tafin hannunshi ina murmushi.."Alhamdulillahi!" Na furta, "kaina yana ciwo ne na kwanta shi yasa ban farka da wuri ba, amma yanzu Alhamdulillahi." Na fara kokarin sauka."Ummu ina zaki?" "Abincin asibiti!" Girgiza kai yayi yana faɗin. "Ki huta na saka a kawo me girki namiji zai na abinci, dazun Sagir yazo kina barci. Domin naga barcinki ba na lafiya ba, shine ya duba ki yace jininki yana hawa ne, damuwa tayi miki yawa Ummu, kina cire wasu abubuwan don Allah. Rashin maganarki bai da amfani kina gaya min damuwarki ko zamu ba magance matsalarmu, daukar matsalar ke daya akwai damuwa." Murmushi nayi ina faɗin. "kawai laluran Asiyah ce kawai ya dame ni amma ba wani abu!" Duk yadda yaso nayi magana naki tow me zance mishi. Haka nayi wanka ya kawo min abinci na ci, na shirya a parlour na same shi, yana zaune yana aiki. "Matori zai ajiye ki a asibitin!" "Tow kai fa?" Na tambaye shi, murmushi yayi ya ce min. "Na je dazun ne!" Gyada kai nayi ina faɗin. "Tow! Wurin su Maryam ka leka su kuwa?" "Bani da lokacin zuwa idan na samu lokacin zan duba basu." "Tafida Hajiya tana bukatar kuyi zumunci Daadi, kuyi zumunci kafin lokaci ya kure wallahi nayi mafarkin Hajiya kayi zumunci Tafida." Murmushi yayi yana shafa fuskata, "zan yi Ummu." Haka ya fada min, sannan na raka shi ya fita, nima na leka su Fanna. Sannan na wuce asibitin, ban san me yasa yace ba zai je ba, sai da naje na fahimci dalilin kin zuwa da ni, domin Mahaifiyar Asiyah bata da kyau, yadda take fade-fade da cewa an gaya mata ya fara shan jinin domin mulkinsa, a gaban kowa ta kunyata Tafida ta ci Mutuncin bawan Allah da babu ruwan shi, na tausayawa Asiyah domin bata samu uwa ba, uwar da take gabanta ba uwa bace monster ce take raye a matsayin Uwarta, yadda take fadar da hadin bakina za a sadaukar da Yarta yasa na bar asibitin , muka wuce babban asibitin Maiduguri, duba Naziha. Sai dai lokacin da naje ana ta fama da ita tana ihu, tare da saka hannunta dukka biyu tana sosa gabanta tana ihu da a cire mata kaikayi yasa naji wani tashin hankali da firgici. Danneta aka yi suka mata allura. Na sunkuyar da kai kasa ina jin wani irin tausayin Yarinyar. "Munafuka kin zo ganin halin da muke ciki ne? Kin zo ganin yadda kika mata asiri ne?" "Allah sarki tausayi kike bani, wallahi kina ba ni tausayi domin." Kai hannu tayi zata tab'a ni, Dora ta sha gabanta. "Maam muje!" Abin ya bata mamaki domin bata tab'a zaton zan iya samun kariya ba, zuwa wurin Naziha nayi na shafa kanta. "Allah ya baki lafiya!" Sannan na kalleta. "Kiyi hankali da rayuwa ba mata dole!" Na fada ina murmushin baƙin ciki, domin rayuwarsu Maryam abar tausayi ce. Bata gane hakan ba kuma ba zata gane ba. ** An samu kusan sati guda ana.fama da jikin Asiyah, wanda zamu ce kawai sai godiyar Ubangiji, domin tunda ta faɗin nan bata kuma bude idanu ba, asalima kawai mun cire rai ne da ita, wannan abin ya ƙara kashe mana jiki, ga mahaifiyarta da ta sako Tafida a gaba sai da aka hanata shiga karshe aka dawo da ita asibitin gidan gwamnati, aka hana kowa zuwa inda take domin kuwa tana bukatar kulawa. Rukayya ma naje na gaishe ta, da sauki iskancinta domin ta daku, kuma zuwa yanzu babu wani abinda take da shi, Abba ya kore su, Abubakar da suke takama da shi ya hanata zuwa gidanshi. Umar bai mata alkawari ba domin tunda ya samu nasarar wani aikin da ya samu ta hannun Tafida bawan Allah nan ya fece Abuja. Yanzu idan ka cire Alfah, Sharifai sai Umar sune suke jikin Tafida ba don kome ba sai don sun yarda haka Allah ya nufa ya kuma ware daya a cikinsu ya azurtashi. Sun kuma kara godewa Allah akan Ni'imar da yayi musu. Ciwon Asiyah sai da ta kai da dole aka fitar da ita, duk da bai so Mahaifiyarta ta shiga lamarin ba, haka Abba ya dakatar da shi ya barta aka tafi ita, domin yadda take nunawa kamar Tafida zai kashe mata yarta, don haka yasa shi ya barta suka tafi tare da Deen, Har abada Tafida ba zai tab'a mantawa da Halaccin Deen ba, domin shi yayi musu kome aka kaita babban asibitin ƙwaƙwalwa na kasar America, Tafida da wulakanci har da matarsa suka tafi, ya ce suyi honeymoon, suka sha soyayya lafiya. Satinsu biyu Deen ya dawo yayi shar da su. Gwanin ban sha'awa, Ni ce nayi musu abinci Matori ya kai musu, Naziha ta ji sauki amma kuma Ubanta yace ba gidanshi ba, don dole Maryam ta daukata suka dawo gidan, dan sauran abincin lokacin da yiwa Rukayya duka ta boye, shi suka yi ta ci har aka sallame Naziha, a hankali wasu abubuwan suka yi ta faruwa, musamman Abubakar da gobara ta kona mishi kome na gidansa. Sai da Abba ya bashi daya bangaren da muka zauna, Tafida yayi banza da shi, sannu Allah sannu Annabi Tafida ya taimaka mishi da wani karamin aiki sai da ya roki. Alfarma aka dauke shi, a matsayin karamin ma'aikaci, shima koyarwa ce a wani kauye can. Aka bashi asist headmaster, Wai kada ace yana Gwamna guda, amma Allah yana gani ba karamin wahala nake ciki da Tafida akan yan uwansa ba, domin zuciya ce da shi kamar kuturu, haka nake fama da shi, akansu amma su ganin suke kamar na mallake shi na cusa mishi kiyayyarsu, Bayan wata biyu na shiga watar haihuwa na, a lokacin Asiyah tana da wata biyu da tafiya, aka fara shirin bikin Alfah da Jalilah, ba zama don ma cikin ya hana ni sake , haka nayi ta faman kai gwauro da mari, har aka gama bikin, kwana biyu da da bikin da sauka lafiya. Inda na samu da namiji, yaron kato da shi kamar Tafida, duk wanda ya ganshi har Mamaki ake yi idan aka ji ni ce na haife shi, gashi fari tas har yafi su Mufidah, lokacin da na cika sati daya aka yi suna Yaro yaci sunan Safiyyudeen an yi shagali takwara kuwa yayi bajinta, domin katon rago ya kawo da bankara shi aka yi ta ci akan abincin, a bakin Jalilah nake ji wai ashe Maryam ta je tayi ta ihu da hauka, wai na cika gida da Yara maza, Tafida yana gidan suka yi ta gayawa Juna magana sai da Abba ya kore shi. Bayan mun yada wanka muka tafi biu bikin Hafsa kanwar Raliya, an sha biki sosai sannan muka dawo satin mu bakwai ya shirya mana tafiya ganin Asiyah, Hmm Asiyah lokacin da muka je sai dai mu mata fatan Allah ya bata lafiya, domin kuwa har yau bata gane kome, bata gane wanda yake kanta, haka yasa nayi ta kuka domin yadda aka kawo ta haka take babu wani cigaba. Sai uban kashe kudi da ake yi wanda babu wani cigaba, mahaifiyarta kuwa tayi kyau tayi shar da ita sai yawo take zuwa, tana baza capacity iya capacity. Kallo daya Tafida yayi mata yaji gara a dawo da Asiyah gida, domin babu amfanin kashe kudi ita tana moran kudin, ita wacce ake yi domin ta tana kwance bata sani ba, don haka yayi ta shige da fice bata sani ba, sai da wata rana ta dawo ya mika mata ticker dinta, ta fara masifa da ihu da tarawa kanta mutane yayi tafiyarshi ya barta. Haka muka tattaro Asiyah muka dawo Maiduguri da ita, Hajiya Turai bata san Tafida ba, sai da ya haukace mata dakyar aka shiga tsakaninsu, ganin da gaske zai iya maketa yasa ta shafawa kanta ruwan sanyi, shi abin da ya bashi haushi ita ba zama take a jikin Asiyah take ba, sannan tana yawo sauran wasu magungunan da aka rubuta taki saka hannu ta a kai, sai dai tayi ta kashe kudi, domin duk bayan wata kudi yana tura mata kudin magani da na bukatunsu amma matar nan kanta kawai ta sani, a yadda ya fusata ya gaya mata maganar da sai da ta gigice tare da gaya mata ciwon Asiyah da halin da take ciki ita ce sanadin haka da ta rike tarbiyyar asiyah da haka bai faru da ita ba, sannan Asiyah tasan waye ubanta don haka kada ya kara ganinta domin shi ya tsayawa Asiyah bata bukatarta, ta je can tayi rayuwarta. Wannan abin ya tashi hankalinta domin bata tab'a zaton gaba daga gare shi ba, taso tayi ta moran arzikin Tafida....76 A yadda Tafida ya hau dokin naki akan Asiyah da yan uwansa yasa nima nake taka-tsantsan da shi, domin yanzu yana da nutsuwa an jima kadan zai birkice mana, haka yasa na zuba mishi idanu, bana yarda na shiga sabgarshi, tun sau daya da na tab'a mishi magana akan yadda yake abubuwan a cikin gidan nan, sam na kasa gane kanshi ya rufe idanun ya gaya min magana har da cewa don ciwon bani bace nake yin shi yasa nake cewa haka, kuma maganar gaskiya, tunda muka dawo bawan Allah nan ya tare a ɓangaren Asiyah, duk da akwai nurse da take dubuta sannan Yarana sun dawo gabana domin Fanna tana zama a jikin Asiyah, shi ma idan ya dawo yazo muka ga juna bana kara ganinshi sai gobe idan zao tafi aiki. Duk da yanzu muna da mai girki da kome, amma haka bai wadatar ba, nima mutum ce amma ya manta da hakkina, bai da lokacinmu a yadda ya hayayyako min, yasa na ja da baya na ce mishi. "Indai akan lokacinka da muka rasa ne ba kome na barwa Asiyah kai har lokacin da zata tashi da kafarta, Allah ya huci zuciyarka." Na juya na barshi yana fada, nima da na fishi rashin mutunci na dauke shi na watsar, sai zama hakan ya gundure shi na dawo da sana'ata na abincin, kwana biyar da Rigimar na ga zai tafi aiki bai shigo ba kuma dama haka ya dauki fushi, sai ka fita na same shi zai shiga mota nace mishi. "Zan fita an jima na tura maka sako tun kwana uku da suka wuce baka duba ba!" Dake ance taburman kunya a nad'e shi da hauka sai gashi ya tattaro naman goshinsa zai fara min jidali na dakatar da shi. "Malam ni ba tashin hankali na bukata ba, kasan halina kuma kasan abinda xan iya yi da wanda ba zan yi ka sake ka min tijara wallahi idan na tsallake bakin wancan get din ko duniya zata hadu ba zan dawo ba." A rude ya kalle ni, cikin ko in kula kamar bani nayi maganar ba ina kallon farcena nace mishi. "Zan fara koyar da girki shi ne abinda na zo na gaya maka!" Na juya abina, ina xan iya rashin mutunci irin na tafida, kuma na dauke wuta bakiɗaya, na ki yarda na kula lamarinsa. Ban san ya suka kaya ba, sai ga Mahaifiyar Asiyah a gidan a lokacin Fanna ta dawo ta cigaba da kula da Yaran dake babu kunya a idanunshi, shima ya dibo kafa wai yazo. Ai kuwa na rufe idanun naki kula shi, na kuma mishi iyaka da ni haka yasa shi kasa zama, wato a yanzu nake da amfani a da bani amfani, ai kuwa nima na nuna mishi bani da lafiya, jinya sosai na nuna mishi ina yi da zai dame ni nace mishi bani da lafiya, da nake da lafiya na nuna mishi hakkinmu cewa yayi bani da tausayi, shiru yayi ya zuba min idanun. Na kwanta na cigaba da barcina. Haka zaman ya kasance na doya da manja, sannan ya kasa hakuri nacin da yake min yasa na sallama mishi kaina a zauna lafiya, kwanakin Maman Asiya biyar da zuwa cikin ikon Allah sai ga asiyah ta farka cikin dare muna barci ta buga kofar bangaren shi, haka muka taso muka je har bangaren, sai dai ya yadda na fahimce ta bata so na zo ba, waya yayi aka kira Likitoci a daren suka zo aka yi ta dubata,sannan aka mata alluran barci ta koma, saboda bata magana sai bin kowa da idanun. Kusan a bangaren Tafida ya kwana domin uwar ta rike shi da tattaunawa wai tana da yakinin ciwon Asiyah ba ta asibiti ba ne, asiri ce kuma ance an gidan aka binne. Share ta yayi ya bar bangaren ina kwance yazo ya kwanta ya juya min baya, abin da bai cika yi ba, share shi nayi na cigaba da barcina kawai kamar daga sama ya fara min magana yana gaya min abin da ta ce, dariya nayi na ce mishi. "Ai sai su tono inda aka binne." Na cigaba da barcina, shi dai anan ya kwana da damuwa, washi gari na shiga bangaren dubata amma matar nan tayi kicin-kicin ta hana ni, na kwaso yan matan kafana na dawo ban kara zuwa ba sai da na ga ya dawo zai shiga na bishi muka shiga tare, sai na lura haka bai mata ba, a lokacin na samu Asiyah a zaune ta jingina da allon gadon. Murmushi nayi mata na ce mata. "Asie!" Murmushi tayi tana lumshe idanunta. "Ya jikin naki?" Gyada kai tayi na riko hannunta. Murmushi ne ya daddu akan fuskarta. Shima Tafida kamar ya cinye ta, ganin haka yasa na bar dakin, domin wani irin farin cikin yake ciki, ina fitowa na ji uwar tana faɗin. "Eh Alhamdulillahi Iya ta farka sai godiyar Allah, da fatan zaki zo ki ga gidan dai!" Na fita ban kulata ba. Sai can ya dawo ya ce min."ko zaki mata wani abu ne tace tana son cin abincinki!" Ban wani ki zancen shi ba na shiga kitchen a tare da shi muka.yi aikin lokacin sallah ya fitar da shi, bayan fitar Tafida a bangaren Asiyah Uwarta ta shiga tare da kawo ruwan rubutu ta wanke mata hannu har da shafe mata jiki, tana kallon uwar dake muryanta ya dashe can ƙasa ƙasa ta ce mata. "Da Ummu tana da mugun nufi da yau ban kawo haka ba!" Ita bata yarda ba, amma tunaninta kawai asiri akawa yarta. Koda muka kai abincin nan matar nan kiri-kiri ta so nunawa Tafida bata son abincina, shi kuma ya ce ai Asiyah ce tace tana so, duk yadda taso hanawa bai samu ba, haka ya bawa Asiyah taci ta sha magani. Tun daga ranar sai ta tsiro da wani abu kafin nayi abinci na kawo ta gama, ta bata dole ta ci, a hankali lafiya na samuwa, Mahaifiyar Asiyah na kara neman hanyar raba zaman lafiyarmu. Kwana biyu sai ga baki daga Yola sun zo yayun Asiyah mata ne, Amrah da Safna. Sai wata dattijuwa, me kama da yan bori . Kana ganinsu kaga marasa mutunci, tunda Fanna ta gaya min yadda suka mata, da ta kai abinci sannan suka dawo min da shi, na saka Fannah ta mikawa su Matori. Allah ya sani tunda ta fara wannan abin na rufawa kaina asiri na mike da addu'a, ba dare ba rana. Haka yasa bakiɗaya na tattara shirginsu na watsa a gefe, a idan yamma yayi lokacin dawowar Tafida za a bunka wani hayaki, wanda kowa ya shaka sai ya ji wani irin abu, Tafida da yake bai da kirki ranar da ya shafa sai da ya rufe idanunshi yayi ta fada shi baya son irin wannan hayakin bai da dad'i. Ina ruwana ni kan su suka ji wurin. Sai aka bar shi sai bayan ya dawo ake sakawa. Sun zata Tafida haka kawai yake zaune, basu san cewa a shirye yake ba. Ai kuwa aiki suke kamar ba kama hannun yaro, satin matar nan daya da zuwa da safe muna barci naji hayaniyar mutane ana ta salati, tashi nayi na d'aga labulen parlourna, hango dattijuwar nan nayi dauke da wani bakin abu kamar leda, ta fito tana nunawa. Tafida da ya fito daga ɓangaren shi ya tsaya yana kallon abun. Kallon windowna yayi ya ga ina tsaye nima, ba zan iya karantar abin da yake kan fuskarshi ba amma tabbas akwai wani abun da na kasa ganowa b'acin rai ne ko takaici. Oho Ni dai kitchen na shiga na yi abin karyawa na ci tunda sun mishi magana cewa yana raba mana kwanakin mu don ana shiga hakkin Yarta, wato da sune abin da yayi min hala mutuwa zasu yi, a bangaren Asiyah kuwa bata jin dadin abin da suke yi. Domin tayi ta fada kenan tana kuka ita bata son tashin hankali su bar mata aurenta kada suyi abin da zai janyo ta rasa mijinta da aurenta. ** Kallonshi Deen yayi a tsannake, kafin ya cigaba da cewa. "Ka gaya musu gaskiya domin Ummu itama ba jin dadinka take ba, asirin da suke fada tayiwa yarsu basu san cewa yarsu ce ta yiwa kanta ba ko me suke bukata? Ni wallahi shi yasa bana son Tara iyali,kai kanka kasan cewa babu adalci a cikin gidanka." "Yes i know Deen amma ya zan yi? Wallahi kamar nayi hauka, itama Ummu ta zuba min idanu." "Ba dole ba, tunda ita Asiya ce y'a ita kuma baiwarku!" "A'a Safiyyudeen!" "Da gaske mana, yaushe Ummu zata huta a gidanka?" "Na sani tsorona daya kada su min sanadin b'allewar sauran aurena, domin zasu cuce ni ne!" Tsaki Deen yayi zai bar office din. "Ina zaka muna magana!" "Idan Ubanka zan tafi !" Ya fada a hasale, "Allah ya baka hakuri!" Dawowa yayi ya zauna yana kallon Tafida, "ka zauna da iyayenta da kai kanka, da itama kuyi maganar gaskiya, idan da hali ka sako Ummu a cikin lamarin nasan ta ba mai yawan magana ba ce,." Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce mishi. "A'a Ummu ba sai ta shiga ba. A haka ma suna cewa ta gama da ni!" Shiru Deen yayi kafin ya ce mishi. "Kayi duk yadda kake so!" Sannan ya bar office din, kanshi ya kulle kamar yayi ta ihu, haka ya taso office din ya dawo gida. A hankali ya wuce bangaren Asiyah ya same su, tana parlour a wheelchair. "Barka da dawowa." Ya fada tana sauke ajiyar zuciya. "Asie ya jikin naki?" " Da sauki!" Ta fada a hankali, "Kin ci abinci?" "Eh!" "Me kike so?" "Zan tafi wurin Aunty Baby ne kwana biyu ta ki kawo min Junior na ganshi!" Shafa kanta yayi ya koma bayan keken ya turata suka fita akan idanun Yan uwanta babu yadda suka iya, asalima sun tare a gidan kamar gidan Ubansu. Shi ma Tafida a bangaren shi ai yaso haka domin kashe musu kudi yake kamar hauka, don saka Asiyah suke ta kira shi tana son abu haka za a kawo mata, idan kudi ne haka zai tura mata account dinta kafin kwana biyu sun kwashe tas. Wannan abin yana damunta, ko tayi magana basu kulata haka yasa yayi shiru tana kallon, asirin da aka tono kuwa wai nice na binne kada Asiyah ta haihu da Tafida basu san ni tsabar tsoron haihuwar har FP nayiwa kaina ba, ina zan iya jarabar Tafida. A wurina ta zauna sai dare muka mai da ta ɓangarenta, bayan tayi ta bani hakuri da irin zaman da muke, da zata tafi ta rike hannuna. "Aunty Baby kiyi hakuri don Allah kiyi hakuri." "Ba kome wallahi." Na turata har parlournta, anan na ga Yayarta tana min wani irin kallo. "Ke dai bakya jin magana, uban me kika fita yi a wajenta? Bayan kowa yasan yadda ta miki asirin hana haihuwa!" Murmushi nayi mata sannan nace mata. "Asie Allah ya baki lafiya, sai da safe." Ina fita suka rufeta da fada, ba ruwana su suka sani yar Uwarsu ce. Bangarena na wuce na je na gyara yarana muka kwanta. Can wurin sha daya Tafida yazo. Na fara barci ya tashe ni. " Wai me ke faruwa ne a gidan nan?" "Ban gane ba?" Na mai da mishi tambayarshi. "Kin bawa Asiyah wani abu ta ci ne?" "Babu abinda na bata ban gane ba, wani abu ta ce an bata anan?" "No kawai dai yanayin ne sai a hankali, tana can cikinta yana ciwo!" "Tow ba dai nan ba!" Na gyara kwanciyata, ni ban san wani irin yanayi muke ciki ba, haka ya gama zaman shi ya fita a daren suka kaita asibiti, wurin asuba aka dawo da ita. Aka ce food poisoning ne, shi kenan aka saka ni a gaba na bata guba ta ci, waye ya mutu waye ya dawo duk ka zuba musu idanun bayan na kai ƙarar su wurin Allah, domin abin ya min ciwo shima Tafida bai nuna min ya ji haushi ba.76 A yadda Tafida ya hau dokin naki akan Asiyah da yan uwansa yasa nima nake taka-tsantsan da shi, domin yanzu yana da nutsuwa an jima kadan zai birkice mana, haka yasa na zuba mishi idanu, bana yarda na shiga sabgarshi, tun sau daya da na tab'a mishi magana akan yadda yake abubuwan a cikin gidan nan, sam na kasa gane kanshi ya rufe idanun ya gaya min magana har da cewa don ciwon bani bace nake yin shi yasa nake cewa haka, kuma maganar gaskiya, tunda muka dawo bawan Allah nan ya tare a ɓangaren Asiyah, duk da akwai nurse da take dubuta sannan Yarana sun dawo gabana domin Fanna tana zama a jikin Asiyah, shi ma idan ya dawo yazo muka ga juna bana kara ganinshi sai gobe idan zao tafi aiki. Duk da yanzu muna da mai girki da kome, amma haka bai wadatar ba, nima mutum ce amma ya manta da hakkina, bai da lokacinmu a yadda ya hayayyako min, yasa na ja da baya na ce mishi. "Indai akan lokacinka da muka rasa ne ba kome na barwa Asiyah kai har lokacin da zata tashi da kafarta, Allah ya huci zuciyarka." Na juya na barshi yana fada, nima da na fishi rashin mutunci na dauke shi na watsar, sai zama hakan ya gundure shi na dawo da sana'ata na abincin, kwana biyar da Rigimar na ga zai tafi aiki bai shigo ba kuma dama haka ya dauki fushi, sai ka fita na same shi zai shiga mota nace mishi. "Zan fita an jima na tura maka sako tun kwana uku da suka wuce baka duba ba!" Dake ance taburman kunya a nad'e shi da hauka sai gashi ya tattaro naman goshinsa zai fara min jidali na dakatar da shi. "Malam ni ba tashin hankali na bukata ba, kasan halina kuma kasan abinda xan iya yi da wanda ba zan yi ka sake ka min tijara wallahi idan na tsallake bakin wancan get din ko duniya zata hadu ba zan dawo ba." A rude ya kalle ni, cikin ko in kula kamar bani nayi maganar ba ina kallon farcena nace mishi. "Zan fara koyar da girki shi ne abinda na zo na gaya maka!" Na juya abina, ina xan iya rashin mutunci irin na tafida, kuma na dauke wuta bakiɗaya, na ki yarda na kula lamarinsa. Ban san ya suka kaya ba, sai ga Mahaifiyar Asiyah a gidan a lokacin Fanna ta dawo ta cigaba da kula da Yaran dake babu kunya a idanunshi, shima ya dibo kafa wai yazo. Ai kuwa na rufe idanun naki kula shi, na kuma mishi iyaka da ni haka yasa shi kasa zama, wato a yanzu nake da amfani a da bani amfani, ai kuwa nima na nuna mishi bani da lafiya, jinya sosai na nuna mishi ina yi da zai dame ni nace mishi bani da lafiya, da nake da lafiya na nuna mishi hakkinmu cewa yayi bani da tausayi, shiru yayi ya zuba min idanun. Na kwanta na cigaba da barcina. Haka zaman ya kasance na doya da manja, sannan ya kasa hakuri nacin da yake min yasa na sallama mishi kaina a zauna lafiya, kwanakin Maman Asiya biyar da zuwa cikin ikon Allah sai ga asiyah ta farka cikin dare muna barci ta buga kofar bangaren shi, haka muka taso muka je har bangaren, sai dai ya yadda na fahimce ta bata so na zo ba, waya yayi aka kira Likitoci a daren suka zo aka yi ta dubata,sannan aka mata alluran barci ta koma, saboda bata magana sai bin kowa da idanun. Kusan a bangaren Tafida ya kwana domin uwar ta rike shi da tattaunawa wai tana da yakinin ciwon Asiyah ba ta asibiti ba ne, asiri ce kuma ance an gidan aka binne. Share ta yayi ya bar bangaren ina kwance yazo ya kwanta ya juya min baya, abin da bai cika yi ba, share shi nayi na cigaba da barcina kawai kamar daga sama ya fara min magana yana gaya min abin da ta ce, dariya nayi na ce mishi. "Ai sai su tono inda aka binne." Na cigaba da barcina, shi dai anan ya kwana da damuwa, washi gari na shiga bangaren dubata amma matar nan tayi kicin-kicin ta hana ni, na kwaso yan matan kafana na dawo ban kara zuwa ba sai da na ga ya dawo zai shiga na bishi muka shiga tare, sai na lura haka bai mata ba, a lokacin na samu Asiyah a zaune ta jingina da allon gadon. Murmushi nayi mata na ce mata. "Asie!" Murmushi tayi tana lumshe idanunta. "Ya jikin naki?" Gyada kai tayi na riko hannunta. Murmushi ne ya daddu akan fuskarta. Shima Tafida kamar ya cinye ta, ganin haka yasa na bar dakin, domin wani irin farin cikin yake ciki, ina fitowa na ji uwar tana faɗin. "Eh Alhamdulillahi Iya ta farka sai godiyar Allah, da fatan zaki zo ki ga gidan dai!" Na fita ban kulata ba. Sai can ya dawo ya ce min."ko zaki mata wani abu ne tace tana son cin abincinki!" Ban wani ki zancen shi ba na shiga kitchen a tare da shi muka.yi aikin lokacin sallah ya fitar da shi, bayan fitar Tafida a bangaren Asiyah Uwarta ta shiga tare da kawo ruwan rubutu ta wanke mata hannu har da shafe mata jiki, tana kallon uwar dake muryanta ya dashe can ƙasa ƙasa ta ce mata. "Da Ummu tana da mugun nufi da yau ban kawo haka ba!" Ita bata yarda ba, amma tunaninta kawai asiri akawa yarta. Koda muka kai abincin nan matar nan kiri-kiri ta so nunawa Tafida bata son abincina, shi kuma ya ce ai Asiyah ce tace tana so, duk yadda taso hanawa bai samu ba, haka ya bawa Asiyah taci ta sha magani. Tun daga ranar sai ta tsiro da wani abu kafin nayi abinci na kawo ta gama, ta bata dole ta ci, a hankali lafiya na samuwa, Mahaifiyar Asiyah na kara neman hanyar raba zaman lafiyarmu. Kwana biyu sai ga baki daga Yola sun zo yayun Asiyah mata ne, Amrah da Safna. Sai wata dattijuwa, me kama da yan bori . Kana ganinsu kaga marasa mutunci, tunda Fanna ta gaya min yadda suka mata, da ta kai abinci sannan suka dawo min da shi, na saka Fannah ta mikawa su Matori. Allah ya sani tunda ta fara wannan abin na rufawa kaina asiri na mike da addu'a, ba dare ba rana. Haka yasa bakiɗaya na tattara shirginsu na watsa a gefe, a idan yamma yayi lokacin dawowar Tafida za a bunka wani hayaki, wanda kowa ya shaka sai ya ji wani irin abu, Tafida da yake bai da kirki ranar da ya shafa sai da ya rufe idanunshi yayi ta fada shi baya son irin wannan hayakin bai da dad'i. Ina ruwana ni kan su suka ji wurin. Sai aka bar shi sai bayan ya dawo ake sakawa. Sun zata Tafida haka kawai yake zaune, basu san cewa a shirye yake ba. Ai kuwa aiki suke kamar ba kama hannun yaro, satin matar nan daya da zuwa da safe muna barci naji hayaniyar mutane ana ta salati, tashi nayi na d'aga labulen parlourna, hango dattijuwar nan nayi dauke da wani bakin abu kamar leda, ta fito tana nunawa. Tafida da ya fito daga ɓangaren shi ya tsaya yana kallon abun. Kallon windowna yayi ya ga ina tsaye nima, ba zan iya karantar abin da yake kan fuskarshi ba amma tabbas akwai wani abun da na kasa ganowa b'acin rai ne ko takaici. Oho Ni dai kitchen na shiga na yi abin karyawa na ci tunda sun mishi magana cewa yana raba mana kwanakin mu don ana shiga hakkin Yarta, wato da sune abin da yayi min hala mutuwa zasu yi, a bangaren Asiyah kuwa bata jin dadin abin da suke yi. Domin tayi ta fada kenan tana kuka ita bata son tashin hankali su bar mata aurenta kada suyi abin da zai janyo ta rasa mijinta da aurenta. ** Kallonshi Deen yayi a tsannake, kafin ya cigaba da cewa. "Ka gaya musu gaskiya domin Ummu itama ba jin dadinka take ba, asirin da suke fada tayiwa yarsu basu san cewa yarsu ce ta yiwa kanta ba ko me suke bukata? Ni wallahi shi yasa bana son Tara iyali,kai kanka kasan cewa babu adalci a cikin gidanka." "Yes i know Deen amma ya zan yi? Wallahi kamar nayi hauka, itama Ummu ta zuba min idanu." "Ba dole ba, tunda ita Asiya ce y'a ita kuma baiwarku!" "A'a Safiyyudeen!" "Da gaske mana, yaushe Ummu zata huta a gidanka?" "Na sani tsorona daya kada su min sanadin b'allewar sauran aurena, domin zasu cuce ni ne!" Tsaki Deen yayi zai bar office din. "Ina zaka muna magana!" "Idan Ubanka zan tafi !" Ya fada a hasale, "Allah ya baka hakuri!" Dawowa yayi ya zauna yana kallon Tafida, "ka zauna da iyayenta da kai kanka, da itama kuyi maganar gaskiya, idan da hali ka sako Ummu a cikin lamarin nasan ta ba mai yawan magana ba ce,." Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce mishi. "A'a Ummu ba sai ta shiga ba. A haka ma suna cewa ta gama da ni!" Shiru Deen yayi kafin ya ce mishi. "Kayi duk yadda kake so!" Sannan ya bar office din, kanshi ya kulle kamar yayi ta ihu, haka ya taso office din ya dawo gida. A hankali ya wuce bangaren Asiyah ya same su, tana parlour a wheelchair. "Barka da dawowa." Ya fada tana sauke ajiyar zuciya. "Asie ya jikin naki?" " Da sauki!" Ta fada a hankali, "Kin ci abinci?" "Eh!" "Me kike so?" "Zan tafi wurin Aunty Baby ne kwana biyu ta ki kawo min Junior na ganshi!" Shafa kanta yayi ya koma bayan keken ya turata suka fita akan idanun Yan uwanta babu yadda suka iya, asalima sun tare a gidan kamar gidan Ubansu. Shi ma Tafida a bangaren shi ai yaso haka domin kashe musu kudi yake kamar hauka, don saka Asiyah suke ta kira shi tana son abu haka za a kawo mata, idan kudi ne haka zai tura mata account dinta kafin kwana biyu sun kwashe tas. Wannan abin yana damunta, ko tayi magana basu kulata haka yasa yayi shiru tana kallon, asirin da aka tono kuwa wai nice na binne kada Asiyah ta haihu da Tafida basu san ni tsabar tsoron haihuwar har FP nayiwa kaina ba, ina zan iya jarabar Tafida. A wurina ta zauna sai dare muka mai da ta ɓangarenta, bayan tayi ta bani hakuri da irin zaman da muke, da zata tafi ta rike hannuna. "Aunty Baby kiyi hakuri don Allah kiyi hakuri." "Ba kome wallahi." Na turata har parlournta, anan na ga Yayarta tana min wani irin kallo. "Ke dai bakya jin magana, uban me kika fita yi a wajenta? Bayan kowa yasan yadda ta miki asirin hana haihuwa!" Murmushi nayi mata sannan nace mata. "Asie Allah ya baki lafiya, sai da safe." Ina fita suka rufeta da fada, ba ruwana su suka sani yar Uwarsu ce. Bangarena na wuce na je na gyara yarana muka kwanta. Can wurin sha daya Tafida yazo. Na fara barci ya tashe ni. " Wai me ke faruwa ne a gidan nan?" "Ban gane ba?" Na mai da mishi tambayarshi. "Kin bawa Asiyah wani abu ta ci ne?" "Babu abinda na bata ban gane ba, wani abu ta ce an bata anan?" "No kawai dai yanayin ne sai a hankali, tana can cikinta yana ciwo!" "Tow ba dai nan ba!" Na gyara kwanciyata, ni ban san wani irin yanayi muke ciki ba, haka ya gama zaman shi ya fita a daren suka kaita asibiti, wurin asuba aka dawo da ita. Aka ce food poisoning ne, shi kenan aka saka ni a gaba na bata guba ta ci, waye ya mutu waye ya dawo duk ka zuba musu idanun bayan na kai ƙarar su wurin Allah, domin abin ya min ciwo shima Tafida bai nuna min ya ji haushi ba.77 Amma kuma idan na bashi abinci ina ganin yadda yake tsince tsince don ma ba Ni ce nake girkawa ba, da wannan abin na barshi da Allah amma da ciwo matuƙa, kai karshe dai lamarin sai da aka kai da Abbanshi ya shiga lamarin domin ya daina shiga harka ne, nima da na ga haka na tattara kowa na watsa a gefe, ko Mama ban gaya mata ba, balle Tina, na hadiye a raina, na cigaba da harkana, abin da suke bukata kenan, ita kan Asiyah tana jin su kamar an rufe mata baki, sai dai tayi ta binsu da ido, amma abinda yake faruwa yana mata ciwo. Ni kuwa zuba musu idanun nayi domin nasan Allah ne zai wanke ni, kuma shi zai bi min hakkina, domin ban yafe musu ba, kullum da haka nake kwana. Abin da ya kai kuwa Abba yazo cikin maganar yadda Tafida ya mai dani ban san ciwon kaina ba, na farko baya cin abincin duk da bani ce nake girkawa ba, amma sai ya kauracewa abincin idan aka kawo aka jera, dalilin da yasa na kara yarda zargina yaƙe ranar na tafi bangarenshi yana girki ya shiga dakinshi kafin ya fito naji kauri a kitchen din, shine na leka kitchen din na kashe gas din, abin mamaki yana fitowa ya fara tambayata da cewa. "Me kika zuba min a cikin abincina? Ummu me kika saka min a cikin abincin yanzu na saka na tashi fa!" Wani abu na ji ya tsaya min a raina, na ce mishi. "Yanzu na kara yarda da zargina kake Tafida tun tuni ban ciyar da kai guba ba, sai yanxu Anya kayiwa kanka adalci? Ba kome!" Na juya na bar bangaren shi ashe wasa farin girki, domin ya zubar da abincin, ya sha tea. Washi gari na shirya yarana na barsu a wurin Fannah. Na nufi gidan Abba da rakiyar jami'an tsaro, koda muka je Abba baya gida a wurin Inna na zauna naki gaya mata kome, ina zaune sai ga shi ya dawo, bayan mun gaisa nayi shiru kafin nace mishi. "Abba nazo niman alfarma ne!" "Na me fa!" Ummu, murmushi nayi me ciwo kafin na ce mishi. "Ina son ka saka Tafida ya sake ni!" Sake goran swan din hannunshi yayi ya kalle ni, "akan me?" Gyara zama nayi, domin yanzu nayi alƙawarin ba zan kara barin a cutar dani da bakina ba. "Abba zama da zargi kasan haramun ne?" Jinjina kai yayi, "tow Tafida ta kai ni madakanta da ba zan iya zama da shi ba, Abba Tafida ba shi ɗaya ba ne, amma namijin da zan tsaya kullum ina kuka akanshi ba, Abba idan na cigaba da kallon Tafida yana zargina raina zai ta b'aci, ina da gata ina da kome akan me zan kashe rayuwata akan Tafida, Allah ya gani ina son aurena amma ba zan iya zama.da Tafida ba kome muka hada da shi na yafe." Na gayawa Abba gaskiya, hakuri yayi ta bani, na sake murmushi na ce mishi. "Abba idan don rigimarmu ce ba zan zo gare ka ba, amma tunda ka ga nazo tow kasan maganar ta wuce iyakarmu tafi karfina, Abba idan Mamana taji abin da Tafida yake min ba zata yarda na koma gidansa ba, gara muyi tsayayya magana." "Na sani amma kiyi hakuri!" Haka yayi ta bani hakuri dakyar na hakura na dawo gidan, ban san yadda suka kaya ba sai ga shi nan ya kwaso babban riga zai min iskanci na dakatar da shi ta hanyar bude mishi idanun nima. "Ce maka aka yi ina tsoron rabuwa da kai ne? Ko an gaya maka akan kawai xan kare? Ba gaji ka je kayi duk abin da zaka yi amma aurenka ka saka a ranka na gama! Auren da tun da nayi shi ban cika shekara daya cikin farin ciki ba." "Haka kika ce?" "Eh na fada sai me? Me xaka yi ko an gaya maka ni wancan Ummu da ka sani ce , bari ka ji da kyau ka sake ka kai maganar nan gaban Uwata zaka fahimci Allah da girma yake na daina jin tsoron saki tun daga ranar da ka sake ni na gane i'm just useless a tare da kai, bukatarka kake biya ni kuma oho!" Jin haka yasa shi kwasar kafarshi ya bar bangarena, ai don bala'i har part dinsa na bishi don ba zan cigaba da kallonshi yana cutar da ni ba, haka muka yi ta rigima ganin bai da gaskiya fita yayi ya bar gidan, na dawo part dina, kada ku dauka ihu da jaraba nake a yadda muryata yake da sanyi a haka nake ta faɗa da masifa. Bai shigo gidan ba sai dare, lokacin munyi barci, washi gari Juma'a, na tashi bana son yin kome ashe ya gayawa me yin abinci za ayi baki, ina kwance ya ta kirana ina ganin kiran naki dauka sai da na ga number Deen na dauka muka gaisa ya ce min. "Gashi nan yana son magana dake!" Kashe wayar nayi, ya sake kira naki dauka. Wajen karfe uku na yamma sai ga Abba, Baba Bulama,da Babana. Suka zo sai Tafida da Deen, anan aka zauna suka bude taro da Addu'a, kafin suka tambaye shi, kame-kame ya fara yana zare idanu. "Ummu ta gaya min kome ban san abin bai wuce ba." "Au dama kasan da rigimarsu?" Baba Bulama ya tambaye shi. "eh na sani Alhaji !" Nan Abba ya gaya musu abinda yake faruwa, take jikinsu yayi sanyi. Kaina a kife a kasa ina kuka. "Ni dai don Allah ya janye igiyar aurenshi na huta da abinda nake gani wallahi zan iya mutuwa don Allah ku roke shi " "A gaskiya ba zan boye muku ba na gaji da maganar auren Ummu da Tafida!" Baba Bulama ya fada kai tsaye, duk suka bishi da idanu. "Alhaji Bulama!" "Da gaske nake gaya muku, Tafida ba yaro bane, duk wani abin da Yarinyar nan zata yi tayi domin ta zauna lafiya a gidan aurenta, Ummu tun tana yarinya ba me fada ba ce bata da abokin faɗa, har mamakin yadda ake kawo min karar kowa amma ban da Ummu. Kai kanka kasan Ummu bata da matsala, zargi ya shigo da batun guba don Allah ya sawwake mata ta huta, yana da damar aure yake bukata yaje yayi, amma ya saka Ummu a gaba gaskiya akwai matsala, idan baka son Ummu ka sauqaqe mata, kayan nama bashi kashe dan kura!" Wannan maganar da Baba yayi ya sani jin tabbas ina da gata, kuma yadda ya tsaya min yasa Ni jin kuka ya zo min, haka aka yi ta bashi hakuri ya ce tow. "yana zaune da ita bata kashe mishi kowa ba sai yanzu zata kashe mishi Matarshi? Har ya kauracewa kome nata, kawai ya sawwake mata, ai tun sakin farko naso kowa ya kama gabanshi amma ganin ita Ummu tana son Mijinta Ni da mahaifiyarta muka dawo da ita me yake da shi da zai na wulakantatta. Kawai ya sake ta ya huta itama ta huta, irin wannan bakin cikin ne za a wayi gari mutum ya mutu?" Sai na kasa cigaba da kuka domin jin dadi da farin ciki, na ce mishi. "Baba wallahi na gaji ne, na gaji ne na gaji ne na gaji kullum na rasa yadda zan yi ita Matarshi bani da matsala da ita, amma shi ya kasa ganewa na gaji!" Ai kamar na kara zuba mishi ruwan zafi haka Baba Bulama ya kara hawa, dakyar Babana ya bashi hakuri ya kuma shiga maganar Abba kan ya kasa magana. Haka aka dawo ana bani hakuri, dakyar dai kome ya wuce aka bamu hakuri suka tafi, ni kuwa naki ko gaida Asiyah na daina,abincin gidan na daina ci nawa nake girkawa. A bangaren Abba kuwa shiganshi wurinsu Asiyah, ya ce Turai ta tattara ta bar gidan Idan ya kara jin labarin tana nan zai saka a sake Asiyah ta je can su zauna, ai dole ma Ummu ta rabu da Tafida an hada makirai a gidan, bayan tafiyarshi aka fara jefa min habaici da zagi da cin mutuncin, abinka da yan Yola ga fulatanci ga shuwa, ni dai ban bi ta kansu, idan ma na damu tow tabbas naji zafi kenan. Kwana biyu a tsakanin suka bar gidan bayan sun yi alƙawarin zaa kawo mata wata me kula da ita, ana murnan an rabu da Bukar ashe za a haifi Habu, yo me kuwa ya kawo haka, ba kome ba ne sai yadda Tafida ya mai da ni hoto, domin bakiɗaya tausayi Asiyah yasa yana min gashin kumma, babu wanda yasan da haka sai ni da shi, ban sani ba amma tabbas na gaji bana son a ga kamar bani da hakuri ne. Ita dai a bangarenta bani da matsala da ita amma a bangarenshi bani da banbanci da da namiji, idan ma mu'amalar aure ce a take zai fara mita ya gaji yayi me,.sai yanxu na kara gano dalilin da yasa matan gwamnonin wasu suka lalace kenan, daga nan ban kara sarewa ba, sai da muka samu wani matsala ya saka Matarshi a gaba suka tafi inda, nayi kuka nayi bakinciki nayi danasanin dawowa ga Tafida, bayan tafiyar shi na fahimci zaman me nake a gidanshi? Haka na danne zuciyata. Nayi kuma hakuri har suka dawo, nayi musu tarba me kyau, sai dai basu wani farin ciki ba, haka na cigaba da dauke kai, har muka samu shekara ɗaya,lokacin Junior yana yawon shi ko ina, na fita hayacina ban san me nake ciki ba, wata rana ina zaune a parlourna, nayiwa Yarana kwalliya ta shigo min. Ina kallonshi kamar wanda aka wurgo shi, ya kalle ni kafin ya ce min. "Ummu!" "Na'am!" "Ko zaki tafi gida ne sai na nime ki!" Bai idda rufe baki ba, na mike zubur, na wuce daki na shirya kayana iya nawa, na juya na fito duk da raina a b'ace yake amma sai naji kamar an yanke min wani azabar da ake gana min, ina fitowa ya kalle ni. "Yaran fa ya zanyi da su?" Ya tambaye ni ban san lokacin da dariya ta kwace min ba. "Bura uba! Ni zan kwasar maka yara? Tow bari kaji ai bada su na zo ba, ka manta ni ne wato? Bye." Na saka kai xan fita ya dibo jiki yana faɗin. "Ummu kizo ki kwashe Yaranki!" "Baka da dangi ne? Ko baka da wanda zai rike maka su ne? Nima gidan Ubana zan tafi malam bani hanya na wuce" na bangaje shi abuna, na bar gidan Matori suka ka ɗauke ni a mota muka wuce biu, tunda na shiga gidanmu. Tunda na shiga parlourn Babana nake kuka nima sai yanzu nake jin kamar an yanta ni da kunci nake ji kamar ma fito daga azaba, nayi sallah nayi addu'a bana barci amma ina Tafida ba mijin aure ba ne.. Bai gayawa kowa halin da ake ciki ba, ya kwashi Yaran ya bawa Asiyah da Fanna, ita kan ba lafiya ce da ita ba, sai Fanna ce take fama da yaran, musamman Junior da yake rikici, A lokacin da ya dawo Asiyah ta mishi magana, "me yasa ka raba su da Uwarsu? Fisabiilillahi Ya Aliyu baka da adalci, Aunty Baby tana kokari tana adalci amma ka rabata da Yaranta, idan har wani abu ake maka wallahi ka tashi tsaye domin rabuwa da Aunty Baby kamar rusaka ake son yi." Daga nan tayi kwanciyarta, ya sani amma bakiɗaya ya daina ganin farin Ummu bakinta yake gani kamar duhu, ya gaji ya rasa me ke damunshi, idan ya fita yana jin sauki kamar ya dawo ya dauke ta su tafi amma idan ya dawo sai yaji gidan ya mishi kunci, kawai ya gaji da ganinta, a watannin bayan mantawa yake da ita, musamman da ya rage shekara daya da wasu watani su gama tenure din nan, bai da nutsuwa baya barci, a lokacin da zai yi barci ya dace yayi sallah sai dai ya tsinci kanshi da barci, sallah lokaci biyar yanzu baya samun yinta, wani bin sai tsakiyar dare yake rama salollin kanshi.....( Wannan labarin rashin sallah akan lokaci na Tafida wallahi naji a bakin malamai uku, Malam Jafar Allah ya mishi rahama, Malam Albani ya fada shima, Malam tijani Yusuf guruntum ya fada dayawa Governor's na arewa basu samun yin Sallah cikakken a rana, duk lokacin da ka rasa sallah babu abinda ba zai faru da kai ba, Allah yana nutsar da duk wanda ya kiyaye sallah, amma an wayi gari sallah tana cikin abin da bamu yinta akan lokaci Allah yasa mu dace)78 Na zata rabuwa da Tafida zai zame min tashin hankali, sai nayi dace Mahaifina bai min magana ba, Mama da ta ji labarin abin da ya faru, ta wanke kafarta ta har gidansu Tafida ta ce maza Abba ya kira mata Tafida ya kawo mata Junior. Ba dauki lokaci ba, sai ga Fanna ta kawo Yaron, amsar Yaron tayi ta bar gidan, tare da fadawa Abba magana daya tak. "Da alamu Tafida bai san kabilar da yake aure ba ko? Allah ya bashi sa'a ya sake Ummu." Abin ya d'agawa Abba hankali, ya kira Tafida muryan shi na rawa ya ce mishi. "yan uwanka, sun kashe mahaifiyarku ko? Ni kuma kana son kashe ni, Tafida wani zunubin nayi maka da kake azabtar da ni akan aurenka? Me yarinyar nan tayi maka ka ce tafi gidans? Laifi ne haihuwar wato? Tafida me nayi maka da zafi?" Yadda Abba yake kuka abin ya tab'a shi rai. "Kayi hakuri Abba!" Iya abinda ya iya fada kenan. Sannan ya ya kashe wayar, tunda abin nan ya faru, bai gayawa ko Deen ba amma ya ce mishi yana cikin tashin hankali, shi kuwa Deen ya cigaba da mishi addu'a. Kuma koda ya tafi wurin Malam Zailani baya kasan iyalanshi sun kai shi jinya Cairo, wannan tashin hankalin ba karamin tab'a su yayi ba. Duk wannan abin da ya ke faruwa, Deen bai sani ba sai da Abba ya gaya mishi. Zuwa Tafida idanun yayi, gashi party dinsu sun matsa lambar sai ya sake fitowa, shi kuwa kamar wanda ake bude mishi kai, ya ce shi ba zai iya ba. Don dole suka tsayar da wani, domin Tafida yaki kuma yaki bada hadin kai. A wannan yanayin ina gidan Babana Mama ta kawo min Junior, nayi farin ciki amma nayi kuka, ta bani hakuri da daurawa kanta laifi, domin ita take kidanta tayi rawanta, ni kaina na fada mata cewa. "Mama nima ina da laifi, tunda ni na kasa hakuri na jira abinda Allah zai yi damu, na shiga damuwa kika mai dani, a yanzu duk abinda zai faru bana fatan na koma gidan Tafida." "Idan rabon bai kare ba, zaki koma Tafida ba sake ki yayi ba, har yau kina nan da aure shi, don haka ki kara hakuri wata rana kamar ba ayi haka ba." Haka yasa na kasa magana nayi shiru, kwananta Daya ta koma Maiduguri. Na cigaba da kula da kaina da Yarona, yarana suna hannun Fanna bani da haufi akanta, ko ina nan ko bana nan. --- Lokacin da Asiyah ta gayawa Mahaifiyarta, Tafida ya rabu da ni, murna tayi ta yi tana faɗin ai dama tasan haka zai faru matuƙar Ummu na gidan Asiyah ba zata yi daraja ba, murmushi Asiyah tayi ta ce mata. "Darajar me ya rage min? Bayan na rabawa karti kaina? Bayan na lalata rayuwata ta hanyar cire mahaifata da ya lalace, ina iya cewa Allah ya bani aron rayuwata ce saboda na gaya miki cewa bani da mahaifar da zan haihu, bani da lafiyar da zan ɗauki ciki. Bani da lafiyar da zan zauna ma kula da namiji idan kun yi baka ne don ku raba tafida da Ummu baku min adalci ba, ina lallabashi ya zauna da ni amma kuka saka ya rabu da Matarshi wallahi Allah ba zai bar mu, ba me yasa Allah ya bani aron rayuwa da mutuwa nayi da duk Ummu bata ga wannan tashin hankalin. " "Dalla yi min shiru, yan uwansa da Hajiya Kaltuma suka saka aka korata bani ba ce, ni dai sanadi na musu, inda na dauki wani shirt shi da na gani a wurinki, ranar da yazo baki abinci ya b'ata, kika gaya mishi akwai kayansa ma a cikin wardrobe, kuka saka rigar a washing machine. Kaltuma da Maryam suka bukaci na basu wani abu daga Tafida na dauka na basu tunda ita Ummu ba harkanta muke shiga ba, shine dalilin da yasa ya juyawa Ummu Baya amma ba mu ne muka mata asirin ba, danginsa ne." Dafe kanta tayi da yake mata wani irin juya. "Kin san inda aka yi asirin?" Ta tambayi Mamanta. "Iyace tayi?" "Ko kan gawata kika zo Allah ya tsayar damu a karkashin alarshinsa ya mana hisabi" daga haka ta kashe wayarta, bata tab'a sanin kiyayyar da akewa Ummu akan Tafida ya kai har haka ba sai yau. Maryam ta manta da nata matsalar tana yaki akan matsalar wani. *** Maryam Wato matsalar wani me dadin gani, Maryam tunda ta faɗi sai ta raba Ummu da Tafida haka bai mata ba, sai da tayi ta shiga da fita, domin tayi imani da Allah ko zata yi yawo tsirara haihuwar Uwarta da Ubanta sai ta raba Tafida da Ummu, sai aka yi dace Kaltuma tazo mata da the same goal zasu buga suna haka Turai ta kawo musu dauki, wannan abin ya ƙara musu kwarin gwiwa yarda da cewa, tabbas hadunsu zai bada abu me muhimmancin, kawai suka yi ta shiga da fita. Sai dai tunda suka yi wannan aikin kamar sun raba kansu da nutsuwa ne, anyi aikin akan idan Tafida ya rabu da Ummu tow ta lalace tayi ta abin kunya, sai gashi Abin kunyar na farko shine Sa'adiya tana yawon banza wani bin tafita sai tai kwana biyu bata dawo ba, Itama Naziha yarinyar ta lalace. Duk abinda suke Rukayya tana kallonshi domin tun da Maryam ta dake ta, wani kusa ya karceta a hannun damarta take ta jinya, duk da maganin da ake amma hannun kamar ya lalace, yanxu tana ta bin Umar a waya akan yazo ya ga halin da take ciki ta je gidan Abba yaki barinta ta ganshi. Ita kan ta tuba, jin haka Umar ya kira Deen ya gaya mishi. Bai so ba amma haka ya zo ya kaita asibiti aka dubata, sannan aka tabbatar da hannun ya lalace, za a yanke shi ne. Garin Bakinciki da kuka tayi ta tonawa Maryam da Kaltuma asiri. Da wani abin da kowa ya ji sai ya zubar da hawaye. Cikin kuka ta ce mishi."Mutuwa Hajiya ba mutuwa ce kawai ba, abincin da aka hanata ci Maryam tayi ta bata saboda Kaltuma ta gaya mata Hajiya tafi son Tafida da mu, ta cigaba da bawa Hajiya abincin da aka hana tana zuba mata sugar a cikin tana bata kayan zak'i!" "Zaki iya faɗar haka a gaban kowa?" Gyada kai tayi tana kuka. "Me zai hana kuwa? Bayan na rasa hannuna me xan yi da ya wuce na tona musu asiri!" "Tow Ummu fa?" Nan ta gaya mishi abin da ta sani akan Ummu ita kan Ya roka mata gafarar Ummu. Domin tasan tayi mata ba daidai ba, Deen gidansu ya kai Rukayya ya ajiye ta, sannan ya wuce wurin Tafida ya saka mishi record. Shiru yayi kafin ya ce mishi. "Yanzu babban tashin hankalin, Abba domin ta iya saka Maryam aikata haka tow babu wanda ba zata saka ba." "Eh Abba ya ce a barta, Maryam kuwa ka kyaleta duniya ta ishe ta, an jima zamu tafi gidan Abba mu gama da case din Kaltumah." Gyada kai yayi. Bai san shirin Tafida ba. ** Maryam kuwa tunda ta fahimci abin da suka yi ya dawo kamar kan Yarta ce hankalinta ya tashi, tayi ta bin Malamai a karya amma ina, fatar da mugun bakin da tayi tayiwa Ummu ya dawo kan Yarta, domin yarinyar tayi wani irin lalacewa, sannan a wannan yanayin Itama Hajiya Kaltuma tana can tana niman sadiya a wani gidan yan iska ta same ta, anyi party wai tasha abu bata biya ba, aka mata shegen duka suka watsar da ita waje..haka ta dauko yarta tana fadar me yasa take son kashe ta ne. Har suka iso gidan, anan ta hadu da Maryam ta gaya mata ita fa ta gaji da abin da yake faruwa. Yarta ta lalace.. "Nima baki ga yadda na dauko Sadiya ba ne?" "Ni bansan wannan ba muje a karya asirin!" "Bayan mun jefe shi ruwa me tafiya ya tafi.da shi ko Aljanu ba zasu iya dawowa da shi ba balle mu mutane!" Ai kuwa Maryam ta fara bala'i da masifa, Hajiya Kaltuma ta rufeta da duka, jin hayaniyar yasa Sadiya tashi daga motar ta fito yana maye, hannunta ɗauke da kwalba. Tana zuwa sai wuyar Hajiya Kaltuma. Jini ya tartsatsu a ko ina, Ihun Maryam da zuwan su Tafida a kusan lokaci guda ne, haka yasa shi aka rufa kan Hajiya Kaltuma aka wuce da ita Asibiti, ita kuwa Saadiya dariya take tana faɗin ku bar ni na kashe ta. Itama Maryam Tafida da kanshi yasa security suka wuce da ita Headquarter na yan sanda, ajiyar zuciya Abba ya sauke, ya ce . "Alhamdulillahi Ubangiji na gode da ka kawo min karshen azzalumai." Cikin gidan suka shiga aka zauna ana tattaunawa. Sannan suka ji kome da Rukayya ta ce. "Allah ya kyauta ina Naziha?" "Bamu san inda take ba!" Haka aka yi ta niman yarinyar, amma bata nan babu ita babu labarinta. *** Naziha. Abin da take yana damunta, haka yasa ta gudu gidan Ubanta amma ya kore ta, bata tsaya nan ba ta tafi gidan wan Babanta suka kore ta, Unguwar su Ummu ta wuce. Ta same Mama ta ce tazo wurin Ummu ne, Mama ta ce mata ta futa ta bata wuri bata san inda ummu take ba. Rike kafar Mama tayi tana faɗin. "Ba tsoron fita nake ba, idan na fita zan cigaba da bin maza da mata ne, ki kai ni wurin Aunty Baby don Allah! Ko sunanta na kira bana jin ihun da ake yi a kaina don Allah Mama." Kallon yarinyar Mama tayi tausayi da soyayya irin ka uwa tasan ba wayonta ya kare mata Yaranta ba, Allah ne kawai ya kare mata yaranta yasa ta ce. "Wani irin abu kike ji?" "Ji nake kamar ana ce min na.tafi nayi ta bin maza babu wani abu, Mama idan na ga mace sai naji kamar don ita aka yi ni." Ta fada tana kuka, kasa magana Mama tayi, kafin ta ce mata. "Zaki iya zuwa Biu?" "Eh!" Nan ta gaya mata har gidansu Ummu, sannan ta kira Ummu ta haɗa su, kuma mama tayi.mata bayani ai ko Ummu ta ce ta je zata biya kudin motar. *** Ummu Tunda Mama ta gaya min Naziha, zata zo naji bakiɗaya jikina yayi sanyi Mama ta kara gaya min halin da yarinyar take ciki, na gayawa Babana, fita yayi can ya dawo ya ce min. "Akwai wani malami a nan baya na gaya mishi ya ce a bari ta zo!" Gyada kai nayi, har bayan isha bata zo ba, sai wurin karfe tara na dare ta iso, kusan yadda yan iska suke kunnen Naziha hujin ya kai biyar, hancinta akwai karfe, gefen bakinta ma haka asalin karamar yarinya ta zama irin wannan abin. Murmushi tayi tana zama, kayan jikinta wasu tsinannun kaya ne. Haka aka bata abinci, ta ci sannan tayi wanka dake dakina ni daya ne, kuma Babana ya gyara min. Ciki ta shiga yayi wanka a ban dakina, na bata kaya ta saka. "Kin yi sallah?" "A'a!" Na ajiye mata hijab, na cigaba da kula da Junior. Bayan ta idar na.bata abinci taci sannan ta kwanta ta fara barci. Bargo na lallubeta da shi, sannan na koma na kwanta. Wurin karfe daya. Kamar a mafarki nayi ta jin nishi, kasa ƙasa da karan wani abu kamar ana kiran waya. Lalubar wayata nayi na haska ina jin kar'ar, naziha ce ya bude kafaffunta sama tana goga wani abu a gabanta ban san lokacin da na yarda wayar hannuna ba.. jikina yana rawa, bata fasa ba wani irin ajiyar zuciya take saukewa lokaci zuwa lokaci alamar ta samu nutsuwa kafin naji tana kuka. "aunty Ummu kiyi hakuri, wallahi idan banyi ba, hauka zan yi." Ki shiga kiyi wanka ." Me zai saka na kyamace ta ina.ta je ana koranta, tasan da kowa ta tsallako gare ni, washi gari da wannan abin na tashi, don tun daren nayi adabo da barci, na tashi akan nawa Yaran ashe idan ka haihu bakai ba barci ba kai ba zagin dan wani ba kai ba lalata tarbiyyar dan wani ban fahimci haka ba, sai akan Naziha ban gane haka ba sai da Naziha ta zo da ciwonta, nasan tana son ta bari ne, tana son ta tuba, tana son ta gyara alakarta da Allah, tana son gobenta yayi kyau ne....79 Idan aka ce maka a duniyar nan abubuwa na faruwa kada ka yi mamaki, amma kuma idan ba kai ba ci kowa ba sai Allah ya kawo maka dauki, wannan shine rayuwar da muke ciki, koda gari ya waye Naziha taki sake jiki da ni. Har muka karya, ina kallonta, wanka na saka tayi muka fita zuwa gidan Malam mai almajirai, tunda muka isa gidan, jikinta ya kama rawa tana son ta gudu. Rike ta nayi wani almajiri yayi murmushi yana faɗin. "Ai ba zata iya guduwa na sake ta." Sake ta nayi ai kuwa ya yinkura zata gudu ta dawo ta zauna sai ga zufa na karyo mata, tun ba ayi kome ba, ko kafin ta fara amai,.zuwa wani lokaci Malam ya zo, ya kalle ta cikin lallashi ya ce mata. "Ya na ga daga zuwa kun zubar da makaminku, kenan zaku tafi ne?" Gyada kai tayi ya ce mata.."da kyau! Me yasa duk haka yake faruwa?" "Mahaifiyarta ce ta tura mu jikin Ummu Hadiyya bayan an bamu jini sannan aka bamu gaban taure muka ci!" Gyada kai yayi yana faɗin. "Hajiya kin ji abin da ya faru! Gaskiya ban san yadda xan warware wannan tashin hankalin ba, domin ke aka nufa suka dawo kanta." "Don Allah ka taimaka Baba Malam, zaka iya." "Eh xan iya amma asirin da aka mata na meye me kuke sakata ta aikata?" "Bin maza da mata!" "Saboda me yasa saboda kawai Uwarta da wasu mutanen sun tsani Ummu!" "Alhamdulillahi kinji!" "Eh a karya yarinya ce, laifin mahaifiyarta bai dace ya shafe ta ba." Shiru yayi yana kallona. Aljanun suka fara magana. "Maryam ta shirya ganin bayanki, keda Yaranki gashi yarta tazo wurin ki sani ba iya ita ɗaya ba ne da bata sonki da Tafida, duk abinda yake faruwa da sanin kishiyarki ita bata da yadda zata yi ne, na rantse da Allah. Ni iya aikomu aka yi sai aka yi rashin dace kina sallah dare mun yi mun yi mu shiga jikinki amma abin ta ci tura kuma a ka'idar idan haka ya faru, muna komawa inda aka turo mu ne, wasu sun shiga jikin ɗaya yarinyar ita kuma wannan mun samu tana cikin tsoro da abinda ya faru da ita, sai muka shiga tunda bamu da inda zamu zauna. An rabo mu da matsuguninmu!" Ban kara razana ba sai da naji suna ta bankad'o magana daga abin da suke aikatawa. Tsoron Allah ya shige ni, na kasa ko kwakwaran motsi. Kawai na auri Tafida ake son na lalace shine Allah ya dawo musu kaidinsu ta kan Naziha da sadiya. Ban kara razana da lamarin nan ba, sai da na ji tana ihu, na kan.saadiya sun dawo kanta suka shiga surutu, da fade-fade anan na fahimci ka ga dai mutum amma kabarshi a inda yake, kafin suka tattara suka bar jikin Naziha, tare da cewa matukar ba aure tayi ba, zasu na waiwayarta domin sun samu yadda suke so a jikinta. Hada magani na Islamic yayi da hayaki, ya kuma bamu shawarar a aurar da ita idan an samu miji, domin aljanun ture suna da matukar biyayya akan abin da aka saka su musamman idan an shayar dasu jini. *** Tafida yana office aka ji ihun Asiyah, Fanna ce ta fito ta nufi bangarenta, Asiyah itama Aljanun basu kyaleta ba, suka yi ta buga kanta da bango har ta suma zuwan Tafida kuwa kamar jira suke tayi wani tsalle ta cakume shi, tana faɗin. "Duk saboda kai, saboda kai saboda kai kawai, saboda kai Ummu ta fi karfinmu Ummu ta fi karfinmu." Nan ta shiga fadar abinda suka aikata, rike kanshi yayi tashin hankalin da yake ji yafi gaban kwantacce, haka ya kwace kanshi ya bugata da kasa, bai damu da ko ta mutu ko tayi rai ba, fita yayi ya kira Deen, ya gaya mishi halin da yake ciki,ko minti goma ba ayi ba, yazo aka kaita asibiti, daga can ya kira Uwarta ta zo ta dauki Ummu. Ajiyar Deen ya sauke, yana faɗin. "An sake Maryam fa, Rukayya an yanke hannunta, ka duba su idan ka samu lokaci." Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon gefen hanya ya ce mishi. "Basu ne matsalata ba, a farko na roki Allah ya bani mulkin alumma, amma ban tab'a tunanin yadda xan roki Allah ya bani ikon rike gidana ba, Allah ya so ni da nabi shawarar ka da na saki Ummu da yanzu ban san me zan yi ba, yanzu shawo kan Ummu ta dawo wallahi ban san ya zan yi ba nasan ni mugu ne mai matukar son kanshi da son zuciya, kuma ko yau na samu dama zan cutar da Ummu amma wallahi ban san yadda zan gaya mata kome ba, ina godiya ga Allah da ban saki Ummu ba." "Hmm" kawai Deen ya fada mishi, Hajiya Kaltuma kuwa kamar zata hauka domin kashe mazajenta da Mahaifiyarta tayi ta cewa gasu nan, ita bata yi hauka ba ita bata zauna a mai lafiya, Maryam kuwa kamar ta zare a garin Maiduguri domin duk inda ake tsammanin Naziha tana nan babu ita, har cigiyarta aka yi tayi babu labarinta. Duk wani Yawon campaign da ake yi Tafida bai je ba. Domin ya matsu ya bar musu mulkin ya huta. Baban Ummu ya kira Abba ya gaya mishi Naziha tana wurinsu, amma maganar ba ta waya.ba ce, idan ya samu lokaci yazo, a satin Abba ya je, da Inna da hajiya Salamatu, aka tattauna akan matsalar Ummu da Tafida, yayinda Mama da suka same ta a nan, ta ce musu. "Rabuwar Ummu da Tafida mai sauki ne, amma yan iska ba zasu iya rabuwa da juna ba, idan kuna ganin karya ne ku barshi da ita su zo na gaya muku, Ummu tana bori ne, yana zuwa zasu shirya." Haka suka yi ta tattaunawa. Karshe aka tsayar da cewa matukar suka bukaci komawa tow kofa a bude yake idan kuma Ummu tace bata bukata babu dole, amma maganar gaskiya kowa yana son Ummu da Tafida. Haka suka watse Alhaji ya bukaci a bashi Naziha ya tafi da ita. Amma tace a'a ba zata bishi ba idan ba Ummu ce zata koma gidan Uncle Tafida ba, domin da haka zata kaucewa fitinar mahaifiyarta. Don zata iya lalata mata kome da ta samu. A lokacin da Maryam ta ji labarin Naziha tana wurin Ummu, ta hauka ce ita sai dai a bata yarta Abba kuwa ya ce ya ji labarin ta je wurin Naziha, Sai ya tsine mata, dama bai tsine mata ba tana cikin masifa domin kuwa bashin da ta tarawa kanta yasa aka yi ta zuwa kotu. *Ummu* Naso Naziha ta koma wurin Mamanta amma Yarinyar taki, don haka na kyale ta, na cigaba da Binta da addu'a. Da fatan Alkhairi. Nima zaman da nake ba jin dadinsa nake ba haka yasa na fara koyar da yadda ake cake, Allah ya kuma dafa min, sai gashi ana yi musamman Christian waɗanda muke dangi na kusa da na nesa, suka shiga zuwa ana musu na birthday da biki da suna, a hankali na zama yar gari ana kawo min ko ina. Alhamdulillahi domin iya wannan ba karamin nasara nayi ba. Kuma naga amfanin sana'ar hannu akwai yar Baffana mai suna Atikah tana gaban Mamawo ga Kanwar Dr Sagir, mai suna Hafizah, tare muka yi aikin sai yaran makota kafin kace kwabo mun bude babban shago a kofar gidan Babana. Ko lokacin da aka yi campaign na su Tafida, naji labarin bai zo ba. Amma akwai mabiya party dinsu, sun yi odar cake da snacks. Naji dad'i sosai, yayinda wasu suka bani wani odar musu girkin abinci aka zuba a takeaway. Bayan an gama suka caske min kudina. Tuni na manta da Tafida na rungume Sana'ata. A yanzu ina niman shekara ɗaya, Baba ya kira shi ya tambaye shi meye nufinsa akan ajiye ni da yayi, ya ce zai zo shi bai sake ni ba, hmm ban san me ya gayawa Baba, na ga Baba ya koma bayan Tafida. Haka ma Mama da Baba Bulama, babu wanda ya koma ce min wani abu sai dai sun bani tabbacin idan nace ba zan koma ba an gama magana, ashe dan waken zagaye suka min, ina zaune a gida aka yi zabin da ya girgiza kowa domin party dinsu ya sha kayi. Bayan zab'en ne party Alhaji Hamza Goza, suka sako Tafida a gaba da cewa yayi rubda ciki akan dukiyar mutane, a wannan yanayin na ji tashin hankali da damuwa, domin sau biyu yana kirana yana cewa na yafe mishi, makiya sun mishi rubdugu, addu'a sadaka, babu wanda ban yi ba, ban san me yasa ba a tsawon shekarar da nayi a gida da haushin Tafida nayi shi, amma ranar da ya kirani naji yadda muryanshi tayi sanyi na fahimci Tafida yana cikin wani hali. Deen da Tinah suka tsaya mishi, wani abun mamaki sai ga Abubakar tare da masu son ganin Bayan Tafida, haka yasa akan abinda ake zarginshi da shi, suka yarda yayi sata, sannan aka kuma kara rub'anya tashin hankalin da yake ganin da sauki. A lokacin Mahmud yazo, ya bada duk abinda ake zargin Tafida da shi. Ya wanke Tafida da shaidarshi ya kuma fitar da wanda yayi satar Abubakar ne tare da Alhaji Hamza Goza. Sai Hajiya Kaltuma da ta sato takardun a wurin Abba. Takardun Tafida ne ya bawa Abba ya ajiye mishi na wasu hukumomin ne na local government, sanin takardan yana da muhimmanci yasa shi bawa Abba ashe Kaltuma ta ɗauke, da wannan takardun tayi ta blackmail din Abba da cewa da iyasu sai ta ga bayan Tafida. Allah ya wanke Tafida, bayan haka gwamnatin da ta samu shugaban kasa har lokacin party dinsu ce, take aka nad'a shi a jakadan Nijeriya a South Africa. *** Wata asabar ina tsaye muna aikin cake, kana ganina kasan ina cikin nutsuwa tunda naji abin da ya samu Tafida na cigaba, sai naji kamar nafi shi murna, ina aikina na ji an ce min. "Mammy!!" Juyawa nayi na kalli yar yarinyar da na tafi na barta bata gama tsayawa da kafarta ba, ita ce s gabana an mata gyaran gashi gwanin ban sha'awa. Sai ga dan uwanta shima ya shigo yana kallona. Durkusawa nayi ja bude musu hannu, hawaye na zuba min. "my apples!" Na fada ina rungume su da kyau ina jin kamar an yanta ni daga azabar da nake ciki. Shigowa tayi yana murmushi. "Finally na zo niman gafara!" Mikewa nayi na bar shagon da Yran a hannuna muka shiga cikin gidanmu. A parlourn Baba na zuba mishi harara. "ka zo min da sakina?" "Ai ke tsakaninmu ba saki ba yaji, ba mugun kallo!" "Ni ba zan zauna da kai ba aure zan yi! Gara ka sake ni!" "Waye ya aike ni, ba fa zan sake ki ba wallahi!" "Na rantse!" Hmm mugu kullum yasan hanyar da zai cuce ni, ban yafe ba dai. Da iya kiss ya dawo da matattun kuzarin da nayi alƙawarin na kashe su, koda kuwa zai mutu akan sona sai gashi yayyafin da yayi ya tado min su, Nasan ina matuƙar son Tafida amma yadda muke samun rashin daidaito a tsakaninmu yasa na ke ganin Gara mu rabu, tun da ya kawo min yara ya tafi can yayi wata uku, sannan ya dawo yayi ta bibiyata yana bawa yan uwa da dangina hakuri kai Tafida mugu ne hatta Naziha sai da ya hada kai da ita, tayi ta min fushi da bori. Ga Mama da Mamawo suma bina suke har Tinah da naji labarin wai ashe sun jima suna dating da Deen, hmm amma kuma tana son shi kuma.zata zauna a bisa ka'idarshi. Mama da kanta ta kawo min me gyaran jiki, tare da rarrsshina na koma kan Yarana, sannan wanann karon dai an saka Tafida a gaba da yarjejeniyar matukar yaga ba zai iya zama.dani ba ya sake ni sun gaji. Yayi ta rantsuwa ba zai kara ba, waye ya mutu waye ya dawo, haka iyaye suka taushe ni na koma gidan Tafida karshe kasan ma muka bari. Unguwar mu ta manyan mutane ne yan boko da attajirai ce. Mun tawo da Fanna da Naziha, wacce Tafida ya mai da ta makaranta, tare da saka idanun akanta. Ana ce bayan wuya sai dad'i. Na ci azaba akan Tafida. #RamlatManga80 Azabar da na sha a hannun Tafida da danginsa ko Makiyana bana fatan ya fuskanci haka, amma kuma yanxu zance Alhamdulillahi, sannan gefe guda daga ni har shi mun fahimci rayuwarmu ba zai tab'a cika ba, sai da dayarmu. Watanni mu goma Rayyan kanin Mahmoud ya kira Tafida ya gaya mishi rasuwar Ammyn, da aurenshi da aka yi da Khairat yarinyar da Mahmoud ya lalata mata rayuwa, Tafida yake gaya min haka, nayi mata Addu'a da fatan rahama. Sai bikin Rayyan din shima Tafida ya kira Deen ya gaya mishi yayi mishi alkhairi, kuma da alamun ayin domin yaron ya kira yayi ta godiya kamar zai yi kuka. An yi haka da kwana biyu, muna kitchen da Naziha. Wayarta yayi kara, Fanna ta kawo mata tana faɗin. "Ke dai wallahi baki da hali, kin ajiye min waya kamar ba naki ba!" Amsa tayi tana faɗin. "Allah ya baki hakuri Nannynmu!" "Zaki sani!" Wayar ta duba, tana faɗin. "Waye?" A hankali tayi karo da wani sako da aka ce mata. _ina ta binki amma kina guduna, na gane kawai bakya bukatar mu'amala da Ni ne, amma nasan ke yar hannu ce_ goge chat din tayi, ta cigaba da aikin da muke. Na yarda babu abinda yafi addu'a, idanuna na kan Naziha, haka yasa kowani motsinta na sani, sannan ina lura da goge sakon da tayi, a hankali na ce mata. "Waye ya turo miki sako?" "Wani Yaro ne, Mammy nayi kamar da yar iska ne? Don Allah Mammy gaya min me yasa maza suke bibiyar sawuna?" Ta fada hawaye na zuba mata, jan kumatunta nayi ina faɗin.."Anya kuwa? Idanunsu ne yaƙe ganin haka" na shiga bata misali da yadda rayuwa take, da ni kaina. Sai jikinta yayi sanyi. Bayan mun gama, muka yi wanka da Mr Man ya dawo ya huta ya ci abinci, a hiran na bashi labarin yadda muka yi da Naziha, shima nasiha yayi min na mata, bayan ya gama ya ce min. "Gobe muna da bako fa, ba zan gaya miki." "Cin amana!" "Eh na yarda!" Muka yi ta hiran kashe tv yayi ya dauke ni, ina zillewa haka ya wuce da ni dakinmu. Sai da ya zane ni da bulalansa kafin ya hakura. Bayan mun fito wanka na ce mishi. "Wai ni ya Asie ne?" Hade rai yayi ya kwanta bai kara min magana. "Wai tambayarka nayi ka share ni." Fisgo ni yayi yana zungure goshina. Tura bakina nayi na ce mishi. "Ka ji tsoron Allah, da Hajiya tana raye ba zata barka ba!" "Eh albarka Hajiya kike daukewa da cin amanarta Hajiya tana son mu cika mata gida da Yara ke kuma Yar renin hankalin kin hana faruwar haka, ki cire roban nan ko ki na gayawa Uwata!" Wato Mama karfi da yaji Tafida ya kwace min iyaye sai ya bar ni da Inna da Abba da Hajiya Salamatu. Daga haka ya mantar da ni Asie da take can tana fama da jinya, ita ba ga Tafida ba ita Baga aure ba. An sake Abubakar saboda Tafida, sai dai da alamu rashin rabuwa lafiya da Hajiya ya janyo yayi ta fama da wasu irin jarabawar rayuwa kome sai an taimaka mishi, hatta Tafida da baya son ganin cigaban shi, ya fi kyautata mishi, addu'ar da Tafida yake sha ba kaɗan ba ne. Washi gari. Tun asuba na tashi nake aiki, ya kai Naziha makaranta tare da niman Yaron, aka nimo iyayen Yaron, hakuri aka yi ta bawa Tafida domin ya ce zai yiwa hukumar tsaro magana a shiga lamarin shi aiki ya kawo shi ba tashin hankali ba. Jin haka iyayen suka saka d'ansu a gaba ya bar makarantar. Sannan ya bar makarantar shima. Wurin karfe daya Naziha ta dawo da farin ciki, kitchen din ta shiga ta ga na gama kome, ai kuwa ta saka hannu ta ɗauka, Fannah ta buge mata hannun. "Mammy ki ce Aunty Fannah ta daina." "Fannah bana son haka!" "Tow Mammynmu!" "Maza ku gaya gyara parlourn Daddy, sai ku zo ku dauki abincinku!" Haka suka gama aka saka turaren wuta, kafin karfe uku mun gama kome wurin biyar sai Tafida da bakonshi. Yana gaba bakon a baya, tsayawa nayi na sake baki kafin na kira sunanshi. "Auta! Ahmad Tijjani!" Tawowa yayi da sauri ya rungume ni, na make kirjinshi ina faɗin. "Kai ne Auta?" "Aunty Baby ni ne amma kada ki manta ni!" Make kanshi nayi ya cewa Tafida. "Yaya ka gani ko? Haka take min su ta cin zalina!" "Mammy me haka!" Tsaki nayi tare da cewa. " da na san girkina wa Tijjani xan uwa da nayi mishi kanzo da garin kuli-kuli?" Aka saka dariya, daga nan aka hau gaisuwa da maraba. "Daga Turkiya kake?" Girgiza kai yayi ya ce min. "yaya bai gaya miki zuwana ba ne?" "Hmm ya kwace min dangina taya zai gaya min, je ka yi wanka sai ka zo kaci abinci kayi sallah ko?" "Eh nayi a office din Yaya Aliyu!" Na nuna mishi dakin da muka ware don baki, na bi Tafida daki. "Me yasa baka gaya min shi zai zo ba? Na ji dadin zuwanshi wallahi kamar nayi ta ihu!" Cak yayi sama da ni yana faɗin. "Ihun nake son kiyi Ummu, ina son nayi ta baki mamaki " "sauke ni tow!" Ajiye ni yayi na wuce na hada mishi ruwan wanka, sannan na saka shi gaba ya shiga. Na cire mishi kayanshi daga shi har Tijjani babu wnada ya gaya min abin da ya kawo shi, haka muka kasance har dare, sannan muka kwanta a wurin kwanciyar ne ya zuba min idanun. "Ummu!" "Na'am!" "Nasan Maryam bata sonki, amma me yasa baki cire Naziha a cikin rayuwarki ba." "Saboda da ita da Mufidah kallo daya nake musu, bana jin akwai dalilin watsa da ita bayan kaf duniya ita ce ta zo gare ni domin mafita! Gaya min wurare nawa ta je aka ki amsarta? Ni uwa ce ina sane da wannan ciwon." Rungume ni yayi yana mai saka kanshi a kafadata. "Idan na ce miki, Mama ta turo Tijjani ne ya ga Naziha zaki yarda?" "Mai zai hana na yarda ai d'a da dukiya baka san waye zaka mora ba, sannan bana tunanin musu mugunta, idan Tijjani Naziha tayi mishi. Alhamdulillahi babban burina ta samu mijin da zai kula da ita ta so ta, idan har Tijjani ya min haka ya kyauta min." Gyada kai yayi, ashe a Maiduguri can Maryam haukarta har gidanmu ta je tayi ta rashin mutunci, Mama ta kuwa gaya mata ai yadda muka mallake Tafida haka zamu mallake mata y'a, sannan mu bata mamaki. Lokacin Tijjani yazo yake tambayar meke faruwa ne, anan Mama ta gaya mishi kome, budar bakinshi ya ce mata. "Mama ni kan ku bani aurenta mana, ina son mace me wayewa kuma da alamu lalacewar ba a ranta yake ba, shi yasa ta koma wurin Aunty Baby." Kallonshi mama tayi ta ce mishi. "Ina fatan ba zaka mata gori wata rana ba? Ina fatan ba zaka juya mata baya don abin da ya same ta ba? Ni dai idan kasan zaka ci mutuncinta, ka bar musu yarsu don Allah kada ka kuma jefa Ummu a cikin tashin hankali." "Mama in dai kece kika haife ni, nayi miki alkawari da sunan Ubangijina, ba zan tab'a tozarta Yarinyar ba, domin kamar Haram Aunty Baby na tozarta!" Da wannan Tijjani ya gayawa Baba Bulama, ya samu Abba ya gaya mishi, kai abu kamar wasa sai ga shi har anyi tambaya da kome, saura aji kome daga Naziha. Don basu son a samu irin matsalarmu da Tafida. ** Naziha Washi gari da sassafe, ta shirya ta tafi makaranta, a can ta kira Mamanta da ta turo mata sakon matukar ta amince da auren dan Uwan Ummu ta sake uwa. Koda ta kirata dakyar ta dauka. "Mama me yasa kike kin Mammy? Mama tasan cewa kune kuka mata kome amma ta zauna dani da haka, ta mai dani kamar babbar Yarta, ban san dalilin zuwan Kaninta ba, idan har aurena zai yi tabbas ya ceto rayuwata daga hallaka, idan ban aure shi ba zina kike so na cigaba da yi? Mama ki tuna akwai Allah kuma abin da kika yi bai tsaya akan iya ni ba, ki saka idanun akan Kannena." Daga haka ta kashe wayar tana kuka, bayan an tashi tana zaune wata yar Nijeriya da suke haduwa Wurin sallah, ta zauna a kusa da ita . "Kamar daga Nijeriya kike ko?" "Eh kema daga can ce?" Gyada kai tayi tana faɗin. "Eh! Sunana Rahmatullah Habib Jimeta, ana kirana Maama!" Isowar wata mota yasa ta mike tana faɗin. "See you baki gaya min sunanki ba." "Naziha Abba Aji!" "Ok sai mun hadu " dawowa gida tayi, tayi a tsarge kamar tayi wani laifi, wanann yanayin ba ita ɗaya ba hatta ni. Sai naji babu dadi na rike hannunta zuwa dakina, kuka take ba kaukkautawa, kukan yasa na kira Sunanshi a waya, can kuwa ya zo muka sakata a gaba da tambayar meke faruwa. Bata cutar da kanta ba, ta gaya mana abin da yake faru, shiru nayi kafin na bude baki zan yi magana ya ce mata. "Ya kin ganshi yayi miki?" Rike hannunsa tayi cikin kuka ta ce mishi. "Uncle, waye zai ki ɗan uwan Mammy, Uncle ko bana son shi yadda yazo don ni na amince amma Mamana!" Ta fada tana kuka. Murmushi yayi ya ce mata. "Yana aiki a kamfanin hada motoci ne a Turkiyya yana amsar albashin Naira miliyan goma a duk wata, zai miki hidima zai yiwa Mamanmu, zai yiwa dangi hidima. Yana da shagon da ya bude na sayar da takalman yan kwallo da kayan yan kwallo, a ƙalla kowani yaron shagonsa yana daukar dubu dari bakwai a wata. Yana da babban shago Maiduguri yana sayar da kayan wuta, yaranshi na nan suna daukar kudi sama da dubu dari huɗu da hamsin gaya min akwai wani matashi irinsa da zaki samu?" Girgiza kai tayi tana shashekar kuka, "Ummu ba zata miki gori ba, Yan uwanta baza su miki gori ba, dukkanmu muna sonki da gaskiya kuma ba zamu yarda ya miki wani abu ba.", rike hannun shi nayi. "Ba zan miki alƙawari ba, amma in sha Allah ba zan tab'a barin wani ya wulakanta ki ba!" "Mammy ya san abin da ya faru da ni?" Rungume ta nayi, ina faɗin. "Bashi yake bukata ba, tun bai ganki ba yace yana sonki, idan kin shiga gidansa, zai yi farin ciki da haka. Kema ba yin kanki ba ne! Haka kaddara take." Haka muka yi ta rarrashinta, kafin muka samu kanta. Tafida ya kira Uban yarinyar ya mishi magana, take ya amince dama kamar ya gaji da yarinyar nan, nawa Naziha take ko ashirin bata rufa ba. A can Maidugurin aka daura aure, ni da Iyalina bakiɗaya muka wuce da ita Turkiyya, inda zata zaune da shi kanshi. Kwananmu biyar a can Mama da su Kulsum suka zo da Ummi Hajiya Balkisu, sai Jalilah sai Rabi'atu kanwar Babanta da Deen da Matarshi, wacce ta gaya min rashin jin dadinta akan Tinah da zai auro, na bata hakuri nace ta kwantar da hankalinta zata iya jure kome, kuma Deen ba irin Tafida ba ne, zata ji dadin tinah, kuma na bata hakuri sosai Deen zai kamanta adalci. Bayan mun bar amarya da ango, mun tattara mun wuce Umara ne har da Mama, sai dai Tafida bai bi mu ba. Ya koma bakin aikinsa. A tafiyar da muka yi kwana goma nayi kacal, na dawo gida domin yadda yayi ta damuna kwana shida a Madina kwana hudu a Makka na barsu. Duk da haka na ji dadin ganinshi. Haka muka cigaba da zamanmu har tsawon wata tara wani azumi ya gaya min Rukayya zata zo, sai da Abba ya gaya min na tattare kayana kada ta min sata, abin tausayi a waya yake gaya min kuma a gabanta. Lokacin da tazo ashe Tafida ne yasa ta zo zasu wuce china da Sharifai ya kawo ta, satinta daya suka tafi za a mata hannun robo, wani lokacin baya gaya min zai yi abu sai yayi idan na tuhume shi ya ce yana da Uwa irin Mama ai ba zai yi shawara da ni ba, kuma haka ne karfi da yaji ya kwace min uwa. Bayan sun dawo daga China watanta biyar, har su Naziha suka da ita da mijin, tayi kyau ga ciki nan, rabo fa. Daga nan muka zo Maiduguri har da Tafida. Kofar gidan Abba an cika ana fadanci, haka ya karbi takardun matasa ya sama musu aikin gwamnati sannan akwai kamfanin da zasu bude da Deen, za a dauki wasu. Har da shagunan Tijjani ma ya kai wasu. Mamanmu kuwa mun tsaya sosai akanta, musamman ni da Tijjani da muke zuba kudi a kanta. Kulsum da Ruman suna bakin ƙoƙarinsu, don ma Tijjani ya basu jari, ni kuma bawa Uwani da Zakiya da za ayi aurenta, Uwani dai Mudan zata aura Zakiya kuwa wani dan Damaturu, an saka sai December, don haka tunda muka koma nake tanadinsu, Maryam da ta ga Naziha ko irin jin dadin nan bata nuna ba, don ma Tijjani bashi da kunya tare tare yake da matarshi kamar kwai. Sonta yake a gaban mu ma tambayarta yake me zata ci me take so, Mama da bata ganin zarau sai ta tsinka, ta taya shi barna kome yi mata take yi. Sau biyu yana kaita wurin Maryam da kuka suke dawowa, amma ana kwana biyu zata koma. A na kudi ne ya fito mata a mutum ya ce mata.."Aunty rigimarku da Aunty Baby daban, ki daina saka min matata kuka, don Allah ya gani ina ganin girmanki na ke ce kika haifi Baby. Bana son na hanata zuwa ne ki ji babu dad'i amma daga yanxu ta haihu ba zata kara zuwa ba." Tunda ya gaya mata haka ta daina damun yarinyar, Ni ce ko mutuwa xan yi ba zata tab'a sona ba. **** A December aka yi bikin su Uwani, a lokacin da muka koma na ga Tafida ya ɗan fara sauyawa, ban damu kaina ba, na fito mishi mutum idan aure ne yayi abin shi ban yarda da sauyi ba. Addu'a na yarda yana tasiri domin bayan nan na tsaya da addu'a, Allah ya zab'a mana mafi alkhairi a rayuwarmu da shi, karshe auren ya watse. Na rungume shi sosai kada kuce ya sauya dukka idan abin ya motsa yana kan yin shi, amma Alhamdulillahi don yana matuƙar gudun abinda zai tab'a alakarmu, bayan shekara daya aka yi bikin Deen, haka Naziha ta sauka lafiya an samu y'ace aka saka mata sunan Mama..tana yada wanka Mijinta ya kawo min ita kwanansu biyar suka koma dakinta. Sai da muka shekara biyar cib, sannan na samu cikin Babana, wanda shima yana tare da ni, don ma yana fama da rashin lafiya ga girma, Mama ma ta ajiye aikinta ita da Baba Bulama da sauran kishiyoyinta. Umma ce Yaran duk matan suna gabanta, ba karamin damuwa take ciki ba, domin irin wahalar da suke sha don ma Baba Bulama yana sassauta musu albarkancinmu, ya daina fita kasuwa ni dasu Bakura da Kawu Gwani, da Ahmad babba da Tijjani mun rike gidan, sosai muka cire kishi muka hade kanmu, a gidan Babana ma Sagir ya tsaya kamar shi babana ya haifa. A gidansu Tafida, girman da bana shi ba ya hau kanshi, kome shine da taimakon Yan uwa irinsu Alfah da Sharifai, Umar. Rukayya ma mijinta ya maida ita bayan ta sami kishiyar da yayi mata. Ita nata da sauki sai dai wani irin abu da yake damunta, ko ta samu kudi lalacewa yake. Haka ta gaya min, nace mata tayi ta sadaka da niyyar ladan a kai ga Hajiya, Allah zai albarkacin rayuwarta, kuma haka tayi ta yi. Hatta sutura sai da yaso fin karfin Rukayya, kafin rahamar Allah ya sauka akanta. Ta fara sana'a sai gashi ana zuwa ana saya. Sai Allah ya jarabceta da Yaronta Khalil da dauke dauke, tayi kuka tayi addu'a, ga niman taimako, sai abin yayi sauki amma tana fama da ciwon abin. Uwani sai da ta shekara biyar ta haihu itama kamar ni tagwaye mata ta haifa, Tinah itama rabo haihuwarta na biyu kenan, Yarana kan sai Godiyar Ubangiji, Rayyan da Matarshi sun tab'a zuwa ma duk da naji Tafida ya gaya min ai yana aiki da shi ne, amma ban yarda yana kowa min wasu mazan gida ba, haka na hada kan Yarana ina kula dasu. Hajiya Hindu take kula da Kaltuma da Sa'adiya, Haka ma Asiyah tana samun kulawa sakamakon alkhairin.da nake mata ni da mijina, daga karshe dai ga mijina ya dawo nawa ni daya. Tarbiyyar Yara ba na mu bane mu daya, ina yi Babansu yana ta ni, haka Addu'a ba dare ba rana. ** A yanzu shekarun mu goma sha daya da aure, kamar bamu ba daga ni har shi kowa hankali ya fara zuwa mana, idan muna hira abin da ya faru sai yi ta dariya. Ga yaranmu Masha Allah, ilimi nutsuwa, sai yan rashin jin da ba za a rasa ba. Da wannan Maryam take yawan gaya min nima sai naji bakin cikin yadda taji, Allah yana kare Yaranta ita dai gata bata ga tsuntsu bata ga tarko, tana yawo kamar mahaukaciya. Deen da gaske yake tsaye a gidanshi, daga Tinah har Sadiqa, suna tsoron abin da zai fusata shi. Kuma Ammah ta maida su Yaranta ko me ta gani bai mata ba zata ajiye su tai musu nasiha dake Tinah ta muslunta, kuma jin familyn Uwarta manyan malamai ne yasa ba a samu matsala ba. Deen bai banbanta su ba, ya nuna musu dukkansu yana sonsu ya ajiye su. Haka yasa yake yiwa Tafida gorin ba zai iya auren mata biyu ba. Duk wani rayuwa mai kyau tushen shi Uwa ta gari ce, Hajiya da Mamana sun kafa mana misali sosai don babu ranar da ba zan yiwa Hajiya Addu'a ba. Mamana ina fatan mi rabu lafiya. Burin kowacce uwa yaranta mata su zauna a dakin aurensu da dad'i ko ba dadi, Mama tayi rawan ganin na zauna a gidana da zuciyar mijina, dadin da take fada gashi nan na hango shi, Mijina da duk sauran da muke tare Alhamdulillahi. *** Yau da yamma makotanmu da na fahimci Yarbawa ne, ana ta biki da hidima, sannan sun gayyaci makota musamman muslmai da muke makota, ana ta hidima nan birthday ake, ba laifi wurin yai kyau. Wasu iyalai naga yan Nijeriya ne, ina zaune abin ka da ka ga dan uwa. Na isa gare su muka gaisa, su biyu ne, dayan tana ta hidimarta sai Mamarsu dayan kuma ta kame, kamar kunya ce ko tsoro ne, sai dai ita Mamarsu yae kano ce. Sai mijinta da yazo daga baya, ina kallon ɗaya yarinyar ta zungure dayan kamar zata yi kuka ita kuwa sai dariya take. Haka aka taso taron na dawo gida ina gayawa Tafida abin da ya faru dariya yayi ya ce . "Prof AbdulGaffar Akindele Rafiq, Yan naija ne Matarshi yar South Turkiya ce wurdawa ce, shi kuma wanda ake abin domin shi Abu Zar! Ban samu zuwa ba ne aiki yayi yawa." "Na ji dadin ganin yan Nijeriya!" "Ai fa ku haka kuke mata." Ya fada yana dariya. Duk yadda ka dauki rayuwa haka take zuwa maka, na dauke shi da sauki ya zo min da sauki. Idan na tuna duk abinda ya faru ribar soyayya ce sai naji Alhamdulillahi Ubangiji ya bamu alkhairi, sharrin da yake cikin dare da rana Allah ya kare mu da shi. Anan na kawo karshen Yar Mace! Alhamdulillahi....... ___________________________________________ Fatan Alkhairi taku har kullum. Ramlat A Manga Mai_Dambu