Edited and copied by Asmart [11/12, 8:52 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (1/10/2016 10:00am)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *1* Bismillahi wassalatu wasalamu alah rasulullah,alhmdllh ayau ne Allah y bani ikon fara sabon buk dina mai suna *goyon* *kaka* Allah y bani ikon farawa a sa'a ameen. Yarinya ce da baxata haura shekara takwas ba ta sheko da gudu cikin gdan nasu ko sallama babu,direct bandaki ta nufa abin data debo acikin rigarta ta xubesu a bakin ban dakin mangaro nagani da alama tsinkosu tayi ba wani excuse ta tura kofar bandakin saboda matsanancin fitsatin daya korota,suman tsaye tayi sakamakon wanda ta gani a bandakin saboda tsabar tsoro a wando ta sako fitsarin,a 360 ta juya kotakan mangwaron batabi ba dakin kakarta ta shige gurin buya ta shiga nema can Allah y bata sa'a ta fada karkashin gado a lokacin kakar kuwa tana baccinta batasan mai yake faruwa ba. Wanda ta bude a bandaki kuwa ransa duk y baci saboda bakin cikin yarinyar ta ganshi ba kaya a dalilin wankan da yake a gaggauce y karasa wankan y futo ransa duk a jagule matashine da baxai wuce 22 years ba ko daki bai shiga ba y wuce dakin kakar,masifa yakeyi tun daga tsakar gda yake kwalawa kakar kira danyasan xata iya boyeta kaka!kaka!!kaka!!!wlh yau saina kusa balla yarinyar nan kowa ma y huta ayi yarinya sai hatsabibanci,dannaga iskancinnaki gaba yakeyi tinda harkin kai ki leka mutum a bandaki yana wanka lokacin y karasa shiga dan duk babatun da yake a tsakar gidane kaka kuwa bata jishi ba saboda tana wata sabuwar duniyar cikin bacci. Kaka!kaka!!kaka!!! ya kwala mata kira da karfi a firgice ta farka a baccin tana haba mai gdan wannan tashin hankalin kira kamar an kawo farmaki,tsaki yayi mtsss yace ni ina shegiyar jikarnan taki mai siffar aljanu,bata fuska tayi tace wlh Aslam ka kiyayeni,ubanme tayi maka xaka fara xaginta yarinyar ma da bata gidannan,tsaki yadanyi yace yace ai baxaki gane ba,tace eh mai xan gane,yace yarinya bakyason laifinta nidai kawai ki futomin da ita danyau saina babballata,islam cikinta ne yace kuwwwww tana xaxxaro ido tana addu'ar yasa karya ganta,dan tasan laifin datayi masa inya kamata xai iya kasheta,dan wlh yaya Aslam mugu ne,kaka ce ta juya tayi kwanciyarta tana kayi ka gama nidai a gidannan ko mai kama da islam ban ganiba tun rana data futa. Juyawa yayi yace wlh nafasa yin satin yau xan koma dan aljanar jikarnan taki xata iya sakamin hawan jini,kaka tace kafi ruwa gudu umma tagaida aysha kuma karka kara kiran islam da aljana in baxata kirata da sunanta ba ka bashshi ba dole bane,islam sai data tabbatar da yaya aslam y futa sannan ta fara kokarin futowa. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:52 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (1/10/2016 11:00am)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *2* Kokarin futowa takeyi daga maboyar tata kakace tajiyo mutsu-mutsu a karkashin gado tace au Ashe shegen berannan bai mutu ba aikuwa yau xan saka maka maga..bata karasa magana ba taga islam ta fito tana xaxxaro ido ,kaka ta kama baki tace lah ga ja'irar kaya yaushe kika shigo,xumbura baki islam tayi tace daxu nashigo. Kaka tace to menene y hadaki da wancan mai bakar xuciyar yadda y xuciya daya kamaki dako makota baxasu iya kwatarki ba,karamin bakinta ta cuno gaba tace to ai daga gonar malam tanimu muke shine fa fitsari y matsoni tofa bansan fa yana bandakin yana wanka ba shine nashiga duk cikin dangarta take maganar,kaka ce ta tuntsire da dariya tace kaji yar nema daman nasan laifi kikayi masa,islam itama dariyar take tace Allah bada gangan nayi ba,kaka tace toh naji,islam tace yanxu ina yaya aslam din saboda futa xanyi xamu tafi rafi yau ana kamun kifi,kaka ta karkatar da baki tace kinsan bakar xuciyarsa yace gda xai tafi,islam tace gwandama dama duk y takuramin y koramin abokanaina y hanasu shigowa gidannan sannan y hanani futa wasan dare,tashi tayi tace kaka saina dawo,kaka tace to amma baxaki hutaba naga yanxu kika dawo,tace au bari nadauko mangwaro na ki boyemin dan sai da mukayi dambe da hanne na kwato mangwaron nataho nasan intaxo tagan shi xata dauka,ta futa ta dauko ta kawowa kaka ta dauki daya tana wlh kuma kaka karki shamin kinjiko,kaka tace xancen banxa mai xanyi da kayan tsami xoki dauki abinki,dariya islam tayi tace Allah y baki hakuri kakata ta kaina ta fuce,a kofar shigowa dakin kaka sukayi kicibis da yaya aslam rangwashi y sakar mata a tsakiyar ka,wani gigitacciyar kara ta saki sanadiyyar wani masifaffen xafi da taji y ratsata,a kuje ta fuce waje taci gaba da ihu,da gudu kaka ta taho har tana tuntube xani na faduwa tana dauka😂 da aslam suka hadu xai shigo dakin hade girar sama da kasa kaka tayi tace me kayi mata,murmushi yayi yace haba ta wajena me kuwa xanyi mata tsorata dai tayi data ganni shine fa ta fice da gudu taxata xan daketa,dariya kaka tayi tace yauwa aina xata dukanta kayi narama mata,xaro ido yayi yace yanxu saiki dakeni tace ras ma kuwa,sallama sukaji anayi kaka ta xari mayafi aslam y mara mata baya malam tanimu suka gani y kawo karar islam da kawayenta da abokananta irin barnar da sukayi masa acikin gona,kaka tace karka yiwa jikata sharri yaushe taje gonarka,kana da wannan shegen saka idon da bakar rowa ta yaya har xasu dauki mangwaronka ka bassu,yace ai katanga suka haura,kaka tace ni islam bataxo da mangwaro ba Aslam ne y dinga bawa malam tanimu hakuri dan yace mai gari xaije y fadawa,tsaki kaka tayi tace kaje birni ka fadawa sarki ba mai gariba,dakyar Aslam y shawo kan malam tanimu dan sai da y bashi 2k y hakura dan tanimu akwau san abin duniya lol,bayan sun shigo gida dan karamin tsaki Aslam yayi yace wlh ke kika dada bata yarinyar nan in ba haka ba yaushe har tasan ta haura katangar mutum ta sato masa mangwaro dududu nawa take,kaka tace karyane fa sharri yakeyi mata,Aslam y nuna mangwaro akan gadon ta yace wancan fa,kaka tahau borin kunya tace to ayi mutum sai bakar rowar jaraba y shuka mangwaro mai warin gawasa kanshi y ishi yara y hanasu mai xai hanasu tsinkowa,Aslam yace wlh da inada iko da mayar da ita gurin aunty amarya xanyi tunda ba tarbiyya kikeyi mata ba,harararsa kaka tayi tace to ko ubanka nina raineshi kuma nabashi tarbiyya,xaro ido yayi y kama baki yace Allah y baki hakuri,kaka tace naji,yace ai yayana wlh baxan kaisu riko ba balle kuma *GOYON* *KAKA* xaki tayi tace wanema xai rikema yaya,yace eh naji kinsa ina bata lokaci sallama naxo miyi xan tafi,kaka tace haba Aslam au da gaske kake baxaka cika satin ba,yace gwanda natafi tunkan kikai ga duka tunda kin fara xagi tace nayi dukan ma indai kan islam ne sainayi maka,y futa yana kinjiko tace ga daddawa nasiya musu ka tafi da ita yace baxan dauki kayan wari ba yaja trolly bag dinsa yai gaba. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:52 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (2/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *3* *ASALINSU* Malam umar shine mahaifin Abdul da Aliyu asalinsu yan jihar kano ne a karamar hukumar gwarxo,Ahmad da aliyu sun taso cikin hadin kai da gurmamawa,inda Aliyu yake bawa Abdul girma sosai da sosai,mahaifiyar su Aysha tana kokari wajen ganin tabasu tarbiya. Mahaifinsu malam umar dan kasuwa ne yana kasuwancinsa tsakanin cikin garin kano in yaxo yayi kasuwancinsa y koma gda gwarxo haka suke xaune cikin rufin asiri,y bawa yayansa Abdul da Aliyu tarbiyya da ilimin xamani dana boko sannan ranakun hutu yana daukarsu suje kasuwa saboda suga yadda yake gudanar da kasuwancinsa,haka suke rayuwarsu har Abdul y kammala secondary skull dinshi y shiga university a lokacin Aliyu yana s.s 1. Lokacin Abdul yana 300 level Aliyu y gama secondary shima y shiga university shekarar da Abdul xai hada degree dinsa a shekarar ciwon ajali y kama mahaifinsu y rasu sunji mutuwar malam umar saboda da wayansu ba'a tabayi musu mutuwa ba kakanninsu tun suna kanana suka rasu da taimakon Allah Abdul y samu y karasa makarantarsa yaci gaba da kula da kasuwancin mahaifinsu. Xaune suke babarsu da suke kira da umma tace yanxu kai yaronnan dayake dan fari ne bata fadar sunansa(Abdul)girma y kamaka y kamata ka nemo mata kayi aure murmushi yayi yace insha Allah. Kwanci tashi asarar mai rai Allah y hada Abdul da wata yarinya khadija bai sha wata wahala ba ta amince akayi bikinsu,khadija yarinya ce mai ladabi da biyayya suna xaune lfy inda yake xaune a cikin kano a unguwar ja'in dayake haya y kama gda mai daki 3 sai kitchen da bandaki,a waje ma akwai shago da bandaki ya nemi kaninsa y dawo sai da aka kai ruwa rana sannan umma a'i ta yadda y kama gaya dan da cewa tayi sai dai y dawo gida y gyara y xauna sai daya nuna mata kasuwancin da yakeyi yana da muhimmanci gwanda yana kusa dashi sannan ta hakura,Aliyu y dawo gidansa yake xaune a shago safe rana da dare khadija ce take basa abinci ko daidai da rana daya bata taba gajiyawa ba,saboda Aliyu yanayi mata biyayya kuma khadija tana da kirki. Duk week end suke xuwa suna gaida umma a'i tanajin dadi sosai saboda yadda kan yaranta yake a hade,kuma suna kulawa da ita. Dayake kasuwancin yanxu sai da ilimi yake tafiya kuma Abdul da Aliyu suna da ilimi shine dalilin karfafuwar kasuwancinsu,dan yanxu Abdul harya fara futa kasashen ketare domin kasuwanci yana shigo da kayayyaki kuma alhmdllh komai yana tafiya daidai saboda suna fitar da hakkin Allah. Aliyu yana shekarar karshe a makaranta yayansa Abdul y siya musu wani tamfatsetsen fili a unguwar rijiyar xaki,tuni yasaka aka fara gini part ne 2 manya sai kuma akayi kananu guda 2 a lokacin kuma khadija tanata fama da laulayi,cikin 5 months aka gama gidan saboda akwai wadatattun kudi. 💘💘💘 *data* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:52 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (2/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *4* A lokacin y kira Aliyu dan yayi masa rakiya unguwar rijiyar xaki yaga sun nufa wani tamfatsetsen gida yaga y nufa dashi a machine din yaya Abdul sukaje a aljihunsa yaga y futo da key y bude gidan mamakine y kama Aliyu kasa boye mamakinsa yayi yace yaya gidan wane,murmushi Abdul yayi yace mushiga tukun shiga sukayi kowanne part an kawata shi da kayan xamani masu bala'in kyau cikin fara'a Aliyu yace yaya naga gida kuma yayi amma ina son karin bayani inji gidan wane,dariyar shima Abdul yayi yace gidanmu ne cikin mamaki Aliyu yake kallan Abdul yace eh namune rimarmu nake tarawa da tayi yawa shine nayi tunanin mai y kamata nayi shine naga y dace kawai na gina mana gda tunda kaima kaga ka isa ajiye iyali,kaga y nuna masa manyan yace wannan daya naka daya nawa,waccan na umma waccan dayan kuwa na yaranmu maxa da xamu haifa in Allah y kawo, farin cikine y lullube Aliyu y rungume yayansa Abdul harda kukansa yace ngd ngd ngd yaya Allah yabar xumunci Abdul yace ameen sai da suka koma sannan Abdul yake fadawa khadija itama taji dadi tayi fatan alkhairi kallan Aliyu tayi tace kanina saura mata ko kuma inaji ni xan samo maka dannaga kamar kanin nawa tsoron mata yake,dariya Abdul yayi yace haba aunty na waya fada miki amma dai nabaki xabi tunda haka kikace,dariya tayi tace xancena gaskiya ne kenan yace eh naji,Abdul shima dariyar yayi. Da suka je gaida umma a wannan satin Abdul yake fada mata itama tayi farin ciki,Abdul yace umma yanxu haka ma nayo mana order motoci basu karaso bane,tace lallai kaxama magajin malam Allah y kara hade kawunan ku y albarkanci dukiyarku sukace ameen. Abdul yace yanxu umma yaushe xaki koma can gidan murmushi tayi tace da ace malam yaso xamana a birni daya kaini tun yana da rai da y kaini birni,amma tunda bai kaini ba yanxu ba avinda xai kaini birni xama ina muku dai fatan alkhairi Allah yasa ashiga a sa'a,sukace ameen duk yadda sukaso su shawo kanta ta yadda ta koma firr taki haka suka hakura. Aliyu yace yanxu yaushe xamu tare murmushi Abdul yayi yace ba yanxu ba ka bari sai nan da xuwa khadija ta haihu kafinnan ka samu mata aliyu yace toh umma tace Allah y raba lfy sukace ameen. *I* *luv* *u* *all* *my* *fans* 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:53 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (3/10/2016 4:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *5* Ha suka gama xaman ranar duk yadda sukaso su shawo kan umma a'i ta yadda taki haka suka dawo,lokacin da Abdul y fadawa Khadija itama bataji dadi ba. Cikin ikon Allah akwai wata yarinya fateema da take shigowa take taya khadija aiki kamar wasa khadija tayi mata xancen Aliyu,ta nuna kunya a lokacin,khadija da Abdul da Aliyu ne suke xaune Khadija tace kanina nifa nayi maka mata yarinyar kuma wlh tana da hankali kuma ga kyau saboda bafulatana ce,dariya Aliyu yayi yace kai aunty na wa kika samomin itama murmushi tayi tace Fateema ce yarinyar da take shigowa,Abdul yace gaskiya kinyi tunani dan yarinyar akwai hankali,Aliyu yace toh shikenan Allah y xaba mana abinda yafi alkhairi,sukace ameen. Cikin ikon Allah Aliyu da fateema sun daidaita tsakaninsu soyayya sukeyi mai tsafta cikin wata uku aka kammata komai aka saka rana 2 months masu xuwa,a lokacin saura 1 months khadija ta haihu. Cikin ikon Allah wata 1 da saka rana khadija ta haifo santalelen yaronta mai kama da babansa sak tamkar kaki yayi ranar suna yaro yaci sunan kakan shi umar suke kiranshi da (aslam)aslam y taso cikin gata kowa yana nuna masa soyayya. Bayan haihuwarsa da 2 weeks khadija ta tare a sabon gidan sai lokacin umma a'i taxo barka da ganin gda saboda acewarta jikan fari sannan kuma dan yaronta na farko kwananta 2 ta koma shima dakyar takai da 1 tayi tace xata tafi. Bayan sati 2 akayi bikin Aliyu xaman lfy sukeyi da matarsa tana masa ladabi da biyayya suna xaman lfy da khadija da take cewa momyn aslam yanxu,ita kuma tace auntyn aslam saboda a gurinta yake wuni sai dai in yana kuka take kai mata shi ta bashi nono in yasha ta koma dashi sai bacci kuma. Lokacin da Aliyu y gama makarantarshi shima kasuwancin yaci gaba dayi. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:53 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (3/10/2016 4:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *6* Cikin ikon Allah kasuwancinsu y kara karfafa lokacin arxikinsu y kara bunkasa. Fateema ma ta samu ciki kula khadija take bata ta musamman har cikinta y isa haihuwa ta haifi na miji aka saka masa sunan yayan Aliyu wayako Abdul qadeer (ameer)haka sukaci gaba da haihuwa inda aslam nada shekara 2 khadeeja ta khadeeja ta kara haihuwa ta haifi namiji aka saka masa Aliyu suke kiransa (Haidar). Cikin ikon Allah khadeeja tana da yaya 5 duk maxa aslam,haidar,sadiq,khaleefa,usman. Fateema kuma tana da yaya 3 itama duk maxa ameer,yusuf,khaleefa ,har yau basu samu mace ba burin yaran gidannan y ta'allaka akan su samu kanwa sannan suna girmama tsakaninsu,cikin ikon Allah fateema ta samu ciki yana da wata 2 khadeeja ma ta samu duk ilahirin yarannan addu'a sukeyi Allah yasa babanninsu su haifa musu yan mata. Cikin ikon Allah fateema ta tashi da nakuda aka kaita asibiti bata dauki lokaci ba ta haifo xankadediyar yarinyar ta mai kamata babanta sak sai dai kawai hasken mamarta ta dauko,murna kuwa gurin iyalan gdan ba'a cewa komai. Ranar suna aka sakawa yarinya Aysha aslam yace (Islam) xa'a na cemata tun daga lokacin rainon islam y dawo daga makaranta y dauketa ba wanda y isa y karbrta babban abinda yake sakawa aslam y kai islam gurin mamanta shine kuka in tana kuka batasan lallashi ba shine yake hadasu fada,tun lokacin da aka haifi islam kaka ta roki alfarmar tanaso Aliyu y bata ita inta isa yaye tun daga lokacin y amince yaxo y fadawa fateema itama tace ba komai tunda y yarda godiya yayi mata sosai. Islam nada wata 2 mommy ta haihu itama mace ta haifa aka saka mata zainab sunan maman mommy amer yace shima ameera xa'a saka mata haka kuwa sukece mata ameera akwai hakuri dan in amer y daukota sai aslam yaje y dauko islam amma shi sai y mayar da ita saboda kuka yayita jin haushi kuwa. Kwanci tashi babu wuya su islam sunyi 2 years a lokacin aslam nada 14 years dan yana j.s 3 wata rana y dawo daga makaranta yaxo y tarar an dauki islam an kaita gwarxo ranar wuni yayi yana kuka ko abinci bai ciba ranar. Islam acan ma kuka take tanata gwarancin neman yaya dakyar kaka ta lallabeta tayi bacci,satin islam 2 ta ware shikuwa aslam ganin da iyayenshi sukayi damuwa tayi masa yawa yasa suka tattara shi suka mayar dashi boarding skul y koma s.s 1 tun daga nan rayuwa taci gaba da tafiya. Wani hutu y dawo da murnarshi ya shirya y tafi gwarxo amma lokacin da yaje y tarar islam tanata birgima tana ihu duk ta watsar da abincin tsawa y daka mata tundaga lokacin ta fara tsoronsa harya dawo bata yadda y dauketa inya dauketa kuwa tadinga ihu kenan har saiya sauketa. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:53 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (4/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *7* Tun daga lokacin y daina daukarta in tayi laifi shine yake tsawata mata tsoronsa takeji sosai,har y tafi tana fara fitina in kaka tace ga aslam nan yanxu xata nutsu. Aunty amarya ta kara haihuwar ihsan da tasleem ita kuwa mommy daga kan ameera haihuwar ta tsaya,su islam duk sunxo suna yanxu haka rabon islam da cikin kano tun haihuwar tasleem yanxu da take shekara 3 wannanne dalilin dayasa islam dawowa hannun kaka,yanxu islam tana makaranta a garin gwarxo tana aji 2 amma asha ruwan tsuntsaye takeyi yau taje gobe taki xuwa,sannan duk ranar da raje sai ta nemo magana bata kyale kowa ba daga malaman har daliban kaka kuwa daure mata gindin rashin mutunci takeyi duk laifin da islam tayi in akaxo aka fada mata sai ta bugi kirji tace bata aikata ba,makaranta ma tana xuwa allo dan an korosu itada kawarta hanne daga islamiyya ance basa fahimtar komai sai neman fada duk randa akayi hadda in basu iya ba aka dakesu indai yaro yayi musu dariya to dukan da xasu masa sai yafi wanda malami xai musu shine shugaban makarantar yace y gaji y mayar dasu gda,kaka da aka fada mata cewa tayi tafi nono fari dama me suke koyawa yara in banda xalunci kullum cikin dukan islam sukeyi tayi xamanta ta kaita makarantar allo wannan kenan. *cigaban* *labari* Islam tana futa bata xarce ko indaba sai gidansu hanne da guntun hawayenta hanne najin sallamarta ta futo da gudu tana waya dakeki islam bakinta ta cuna gaba tace ba wancan mugun yaya aslam din bane y rangwasheni hanne tace Allah y saka miki islam tace ai wlh dabadan yau xai tafi ba da saina rama dariya hanne tayi tace da munyi masa irinta uncle idris itama dariya islam tayi tace kuma shi da wlh a ruwan wanka xan xuba masa karara dariya sukayi gaba dayansu babar hanne tace Allah y shiryaku gidansu ilah da yusufa avokabansu suka je suka biya musu suka tafi kogi dayake yau ana kamun kifi kowa da fatsarshi a hannu. Aslam kuwa tasha yaje y shiga mota ana kiran sallar magriba y isa gda direct part dinsu na samari y shiga dakine gado daya sai wardrop sai bathroom aciki wannan nasune shida ameer wanka yayi y futo y tafi masallaci sai da akayi sallar isha'i sannan y dawo direct cikin gda y shiga yaje y gaida maman sa take cemishi yau kwananka 3 fa harka dawo kai da kace sati xakayi a lokacin Abbansa da daddy (aliyu)suka shigo bayan y gaishesu yace wlh mommy dawowa nayi saboda kwata-kwata islam bataji gashi duk abinda takeso shi takeyi kaka bata tsawata mata anan y basu lbrn duk abinda y faru sannan,ran Abba y baci sosai yace dama inaso nasamu dama muje mu taho dasu gaba daya y kalli aslam yace karka damu insha Allah xasu dawo very soon aslam cikin farin ciki yace Allah y yarda,ya tashi yace xashi gurin aunty amarya su kuma suka xauna suna tattauna yadda xasu shawo hankalin kaka ta yadda ta biyosu. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (5/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *8* Da farin cikin shi y shiga part din aunty amarya a xaune y taradda ita ita dasu taslem y karasa y xauna a gefenta dora kanshi yayi akan cinyar aunty amarya,yace aunty na nayi missing dinki ina wuni,tace lfy my son i miss u too yayi dariya,kallan su taslem yayi y hararesu yace baku iya gaisuwa ba cikin rawar murya sukace ina wuni yaya lfy kawai yace,yace dallah can ku tashi ku bamu guri kun tsareni da ido naxoyin magana da aunty na da gudu ihsan ta tashi taslem kuwa kafadarta ta make dariya yayi yace kai aunty wlh yarinyar nan rashin jinta daya da islam itama dariya tayi tacewa taslem taho autata wlh wannan tafi islam jin magana yace aini xan baki lbrn rashin jinta yanxu fa ita ta koroni daga gwarxo ga kaka ta daure mata gindin rashin mutunci komai tayi daidai ne,shiru aunty amarya tayi tace to y xamuyi sai dai mu dinga binta da addu'a. Aslam yace au ashe fa albishir naxo yi miki ai nasamo solution very soon islam xata dawo,murmushi ne y subucewa aunty amarya tace Allah yasa my son yace ameen y dade suna hira sai wajen 10:00pm yayi mata sallama y tafi part dinsu. Islam baxaki tashi ba 7:30am fa tayi ko so kikeyi ki makara,kaka ce take tashin islam daga baccin safe saboda ta tafi makaranta,juyi tayi ta cuno karamin bakinta gaba tace wlh ni kaka baccinnan bai isheni ba,kaka tace ashe bakyaso ki xama mai lbrai a gidan radio ko da sauri islam ta mike dan dalilin dayasa take xuwa makaranta saboda tanaso taxama yar jarida shine babban burinta,amma da tuni ta daina xuwa wanka ta cire kayanta ta shiga,baccinta taci gaba dayi a toilet kaka ganin islam ta bata 15 minute bata futo ba shine yasaka ta bita a xaune ta tarar da ita akan kujera tana bacci tsaki kaka tayi tace wlh islam kedai anyi yarinyar banxa ta karasa ta sheka mata ruwa firgigit islam ta farka ihu ta kwala tana kururuwa kaka tace yimin shiru wlh yau in angle idris yayi miki dukan latti ba inda xanje,dariya naga islam ta tuntsire a raina nace mai kuka yana dariya,tace ba angle idris ba uncle idris ake cewa tsaki kaka tayi tace xancen banxa ai nayi kokari ma,amma menene tsakanina da yaran bokoko a wuta a haka kaka ta gamawa islam wankan suna fada. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (5/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *9* Sun fito daga toilet hanne dasu yusufa suka biyowa hanne mai ta shafa ta xauna sukaci abinci,ilah yace wlh wannan taliyar irinta gurin mai shayi dadinta y baci yusufa yace sosaima hanne kuwa lokacin da takai loma tace ai wlh saboda ita bana taba yadda nayi fada da islam,dariya islam tayi tace ba sunanta taliyar gurin mai shayi ba sunanta indomie ta karkatar da baki tace wannan mugun yayan nawa ne y kawomin ita dasu madara harsa biscuit da choculate wai na xuwa makaranta murmushi hanne tayi tace gaskiya y kyauta sai wajen 8:30am suka gama ci dan sunayi suna hira kaka harta gaji da magana islam ta shiga daki ta daukowa kowa chocolate da biscuit kaka kuma ta basu 20 naira sababbi sannan suka tafi. A hanya hanne tace islam mu biya gonar malam tanimu islam tace a'ah ki bari mu dawo tukun tinda kinga munyi latti kar a dakemu nikuwa nace latti na yaushe basu suka karasa makaranta ba sai 9:00am dudu du tafiyar batafi ta 10 minute ba amma suka dinga canta sai data kaisu 30 minute islam tace yanxu muje mu haura ta katanga dan wlh baba mai gadi ko muna yawo da uwayen mu baxai barmu mu shiga ba yusufa yace haka xa'ayi daraf naga suna kama katanga sai ka rantse da Allah yan biraye ne sai da suka gama durawa Ashe wani fripect y gansu kuma dokar makarantar ce an hana shigowa ta Katanga. Y kamasu sai office din head master akayiwa kowa bulala 5 masu xafi suka dinga kuka sannan aka sakasu neal down sai da sukayi na 30 minute sannan akace su tafi class aikuwa su islam sunsha takaici saboda basu samu sun siyi komai ba a break gashi an buga bell kowa y koma class. Nan ma suna xuwa sabon mass teacher dinsu y shigo gashi ranar friday y bayar da assighment cikinsu ba wanda yayi nan y kuma futar dasu y sasu kamun kunne ranar dai su islam sunce da kafar hagu sukaxo makaranta nikuwa nace rashin jinsu😂. Gonar malam tanimu suka wuce sai da suka tsinko mangwaro 1 yahau kai islam tace ainice boss dan haka nixan dauka nan fa dambe y sarkesu har malam tanimu yaxo y kamesu yace gurin mai gari xai kaisu suka dinga bashi hakuri yace wlh sai y kaisu mai gari y musu tsakani. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (6/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *10* Mummy da aunty amarya suka futo suna Allah y kiyaye y tsare hanya Allah y doraku akan hajiya ta yadda ta biyoku sukace ameen suka shiga mota Aslam ne yake driving inda daddy da Abba suke a seat din baya,Aslam driving yakeyi cikin nitsuwa har suka karasa gwarxo parking yayi a kofar gidan kaka suka futa y rufe motar suka shiga ciki. Shiga sukayi bayan sun gaggaisa da kaka ta kawo musu ruwa da lemo kallon aslam tayi tace baka tafi koyon aikin sojan ba ai naxata wannan satin ka tafi yace a'ah sai wani watan xan tafi,Aslam yace kaka ina aljanar jijarki ne hararararsa tayi tace ban sani ba murmushi daddy yayi yace aslam islam dince aljana yace ai wlh daddy tafi aljana yanxu muna xaune ma kila a kawo kararta,kaka tace to makaranta ta tafi aslam yace Allah yasa. Sallama sukaji anayi aslam ne y tashi yaje y gano dan aikene daga fadar mai gari ana neman kaka aslam yace toh gatanan xuwa y koma y fadawa kaka aiken da a kayo gurinta mayafi ta saba Abba yace haba hajiya ki tsaya mu muje mana kaka tace a'ah dole na amsa kiran mai gari ai kudaixo muje dayake ba nisa a kafa sukaje. Su islam suka gani sunata kuka suna sun daina baxasu kara ba iyayen su hanne ma sunxo cikin tashin hankali kaka take tambayar meyake faruwa,su Abba kuwa guri suka samu suka xaxzauna suka gaishe da mai gari,suka tambayi dalilin kiran mahaifiyarsu anan mai gari y fadawa su Abba irin ta'asar da islam da abokananta sukeyi masa a gari sannan da karar da malam tanimu y kawo anan yaja hankalin iyayen sauran yaran daya xama dole su tsawatar da yayansu in ba haka ba kuwa xai dauki kwakwkwaran mataki,sannan yace kowa y tafi da yaranshi sukayi godiya kowa y kama danshi y tafi gda. Tun a hanya kaka take sababin masifa akan an tsanar mata jika,anan su daddy suka dinga bata hakuri Abba yace yanxu kawai hajiya ki yadda ki biyomu mu tafi kinga acan ba ruwan wani da wani,islam tace eh kaka mu tafi birni dama wlh nagaji da yadda ake sakamin ido,kaka tace toh shikenan muje mu tattara kayanmu farin ciki sosai ne y kama aslam saboda yanaji y kusa gyara islam. Nikuwa nace anya kuwa mudaije xuwa yanxu lbrn y fara ku biyoni danci gaban lbrn😊. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (7/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *11* Harhada kayansu sukayi a jaka,da gudu islam ta fice a gda gidansu hanne taje tararwa tayi innar hanne tana mata fada akan y kamata ta gyara halinta inba so takeyi ta rasa mijin aure a kauyen ba. Sallama islam tayi tace hanne naxo nayi miki salama yau xamu koma birni gidansu babana ko nasaka ta na wala da yadda kowa y sakamin ido,innar hanne ce ta girgixa kai tace Allah y shiryaki islam to ina kudan yake balle romonsa da har xakice an saka miki ido,murguda baki islam tayi tace yanxu ke inna baki gani ba umh hanne xo muje gidansu ilah da yusufa nayi musu sallama,da sauri hanne ta tashi innarta tana kiranta kota kanta batabi ba suka fice. A hanya hanne tace yanxu shikenan islam in kin tafi binni xaki manta damu ko,wata dariya islam tayi tace mai xaisa na mantaku kunefa abokanai na na hakika kuma ba ai Abba yace xamu naxuwa hutu washe baki hanne tayi tace Ashe nima wataran xani birni islam tace sosai a kofar gidan su ilah suka tarar da ilah da yusufa anan islam ta sanar dasu tafiyarsu birni suma basuji dadi ba suka dunguma suka tafi raka islam. Acan bayan sun gama saka kaya a mota daddy yace to ina kuma islam din,kaka ce ta kama baki tace la'ilah ha illallah in ka bibiya ta tafi gidansu hanne yi musu sallama amma mu jirata. Xaman jiran islam sukayi harna tsahon 10 minute amma shiru ba ita ba dallinta tsaki Aslam yayi yace amma yarinyar nan yar raunin wayoce in ba rainin hankali ba tasan jiranta mukeyi xata tafi yawo kaka ce ta hararesa tace to sai taki yiwa abokananta sallam...,bata karasa ba suka hango islam itada su hanne,Aslam yaja dogon tsaki yace saboda yarinya an batata wai har abokanai ne da ita maxa kaka ta hayayyako masa tace saika fadi waya batata kai wlh da badan islam tanason komawa birni ba kuma baxan iya bari ta tafi ita kadai ba wlh da ba inda xani,daddy ne yace hajiya dan Allah kiyi hakuri y kalli Aslam yace be carefull in ba haka ba kuma y girgixa kansa. Islam ta karaso ta shiga mota daddy y bawa su hanne kowa 100 ganin da gaske islam tafiya xatayi suka hau ihu da kuka suna bin mota,islam itama ihu takeyi kaka ma harda goge kwallah😢. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (7/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *12* Aslam ne yaji kukan islam yayi yawa kuma su Abba sunata rarrashinta taki yin shiru,tsawa y daka mata yace da Allah kiyiwa mutane shiru kin cikawa mutane kunne ke gaki mai kawaye ko,dago fuskarta tayi shabe-shabe da gawaye ta murguda masa baki tace to ina ruwanka in baxaka jiba ka toshe kunnanka da wanda ya tilasta maka dole kaji kukana xaro ido yayi yakai mata rankwa shi ta goce,daddy yace Aslam y kake wasa da rayuwarmu ne Aslam yace I'm sorry dad,sannan yace mamana rabu dashi kinji ta washe baki kamar ba ita take kuka ba tace toh. Tunda suka tafi take surutu komai ta gani sai tayi magana na tambaya kuma ta tambayi Aslam ko kallanta bayayi sai tayi tsaki tace daddy ko Abba menene wannan saisu fada mata. Aslam kuwa duk haushinta yakejin ganin yarinya karama tana shirin rainashi yadda kowa yake girmama shi a gdan amma yanxu xataxo da nata salon na daban murmushi yayi daya tuno da irin axabar da xaiyi mata har saitayi biyayya tsinto ihunta yayi ta kwalla kara tana yeah kiiiii yaja birki saura kadan y bugawa motar gabanshi dan ma Allah y nufa babu mota a bayansa da hatsarin da xasuyi ba kadan bane. Kaka firgigit ta farka daga gyangyadin daya dauketa tana salati,su Abba ne suka kalli islam sukace ihun me kikeyi ko kinaso muyi hatsari mu mutu daddy yace kai Aslam kai kuma tunanin me kakeyi,kaka tace so yakeyi y kashemu kawai dama bai damu da rayukan muba. Islam tace nifa tsoron wannan nakeyi gani nake in mun hau xamu fado,dariya Abba yayi yace islam rigima wannan fa gadace da ana fadowa ai da bakiga wasu motocin suna biba(nikuwa na kyalkyale da dariya nace kai aradu kauyanci baiyi ba yanxu hawa gadar takewa ihu haka😂😂). Aslam kuwa wani bakin cikine y turnike shi a ranshi yana watako ita duk iskancin nata ma tsoron mutuwa takeyi aikuwa xakici ubanki y figi motar,islam kuwa idanunta ta runtse sai da suka sauka akan gadar ta bude idonta. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:54 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (8/10/2016 4:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *13* *GOYON* *KAKA* Tafiya sukeyi har suka karasa gda horn Aslam yayi gate man y wangale katon gate din gidan suna shiga yaran gdan suka taho da gudu harda taslem duk suka futo a motar wata mika islam tayi taja doguwar hamma ko rufe baki batayi ba,da sauri Aslam yadan bige bakin yace ba'a fada miki in anyi hamma ana rufe baki ba ihu ta kwala a firgice y juyo yace dan Allah kiyi hakuri yakai hannu y rufe mata baki,da yake ba wanda yaga time din daya bige bakin nata. Shiru tayi taja tsaki ta murguda masa baki,kaka ta kalleta tace ke kuma ihun mene wannan kamar wadda tayi gamo cuna bakinta gaba tayi bata bata amsaba. Su mommy da aunty amarya ne suka futo sukayiwa kaka sannu da xuwa har part dinta aka shigar da dukkan kayansu dayake an riga an share part din. Bayan sun gaida kaka,islam kuwa hankalinta yana kan taslem yar 3 year tanata mata wasa,aunty amarya tace islam baki gammu bane ba gaisuwa murmushi tayi tace aunty amarya ina xuwa wasa nakewa taslem duk maganar da takeyi ko dago kanta batayi ba. Girgixa kai aunty amarya tayi a ranta tace Allah y shirya,futa su mommy sukayi suka kawowa kaka abinci kala kala bayan sunci,islam ta mike ta shiga toilet fanfo takeson kunnawa ta kasa,saboda ba irin na kauyensu bane garin kici kici ta kunna shower kawai sai jin ruwa tayi y xubo mata ihu ta saka tana wayyo Allah na shiga uku. Da gudu suka tashi sukayi bathroom din ganinta sukayi a tsaye jikinta sai rawa yakeyi ta rufe idonta sai ihu takeyi ruwa duk y jikata,Aslam da Amir dariya suka farayi ganin dalilin kukannata sauran yaranma duk suka dau ihu suna villager girl aunty amarya kuwa tsaki tayi ta koma mommy ce ta shiga bathroom din ta kashe shower din kayanta ta taimaka mata ta cire,sannan tayi mata wanka ta bata towel suka futo,mai ta shafa mata da powder sai kwalli islam tace mommy bakiyi min dige-dige ba,mommy tayi murmushi tace nan birnine ba'ayi ko kinaso a dinga ce miki yar kauye xumbura baki tayi tace niba yar kauye bace mommy tace ai dama bance miki yar kauye ba,islam tace to daxu daga ina ruwa y xubo naga ba a bude saman bandakin yake ba balle nayi xaton ruwan samane jan hannuna mommy tayi suka koma bandakin tace wannan shower sunanta wanka akeyi da ita dariya ta kyalkyale tace yasin birni yayi ta dada kyalkyalewa da dariya a haka suka futo yaran suna ganinta suka fara villager girl kugu ta kama ta joge kafa tana girgixa tace wace bulleja gal din wlh ni ba sa'arku bace sainayi muku tsinannen duka(nikuwa nace kaji turancin manya😂😂). 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:55 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (8/10/2016 4:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *14* Dariya suka dada tuntsirewa da ita faduwa tayi tahau birgima mummy ce ta korasu sannan ta koma lallabar islam. Amera ce ta dawo part din kaka saboda islam,da daddare bayan sun gama cin abinci islam ta kalli Amira tace Amira wai ku bakwa futa wasan darene,Amira tace eh munan ba'a futa wasan dare amma munayi a sarraunding din wataran,islam ce tayi tsaki tace menene sorondin murmushi Amira tayi dan tasan in tayi dariya yanxu xatasha bala'in islam dan adan xamansu ta gane masifaffiya,tace tsakar gida islam tayi dariya tace auho to tashi muje muyi. Xaro ido Amira tayi tace wlh yaya aslam dukanmu yakeyi in yaxo y tarar munayi yace wai saimun hadu da aljanu tsaki islam tayi tace wlh ke xabuwa ce kixo muje xan tare miki in xai dakeki,Amira tace wlh badani ba tsaki islam ta kumayi tace to munyi fada karki kara kulani,murmushi Amira tayi daga haka bacci y kwashesu. Washe gari kaf yaran gidan in banda taslem suka shirya suka tafi makaranta bayan daddy da Abba sunxo sun gaida hajiya,islam ta gaishesu,Abba yace islam ki dauko mayafi xamuje ayi miki interview xaki fara xuwa makaranta,bakinta ta xumbura ta dauko tunda suka tafi take guna guni ita batasan makaranta kuma ko an kaita sai taga dama xata,tunda suka doshi gate din makarantar ta saki baki daga saman gate din makarantar an saka *khadija* *memorial* *nursery* *,* *primary* *&* *secondry* *school*duk daba nisa ne da makarantar ba,dan a bayan gidansu makarantar take,saboda yadda makarantar ta tafi da imaninta da suka shiga kuwa gaba daya tunaninta y tsaya saboda makarantar duk shuke-shuke ne parking Abba yayi yace mamana futo mu tafi hannunta y kama direct office din principal suka wuce,bayan sun gaisa Abba y fadawa principal yarinya y kawo amma yana neman alfarmar a sakata a primary 3 saboda daga kauye y daukota,principal yace ba komai amma ku nemar mata lesson teacher dan in bata kokari xa'a iyayi mata repeating Abba yace ai dama akwai lesson teacher dayakewa yan'uwansu. Principal yace yauwa anan Abba yayi mata registration y siya mata duk wasu school items da xata bukata aka bata unifoam sannan yayi godiya suka futo. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 (9/10/2016 12:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *15* Direct kasuwa y wuce da ita y siya mata takalman makaranta masu kyau guda uku da socks,da school bag da launching box surutu take tayi masa akan yadda makarantar ta burgeta Abba kuwa sai murmushi yakeyi. Suna xuwa gda Abba tun kafin y daidaita packing ta fice a guje direct part din kaka ta sheka a guje ko sallama babu sai ganin islam tayi ta shigo kamar an korota xinbur kaka ta mike tana ke lfy meya faru waya biyoki,ko takan kaka batabi ba ta shige bandaki saboda fitsari ne y korota dama islam tana da wannan dabi'ar bata taba shiga bandaki lokacin da taji bukata sai abin da xatayi yaxo daf sannan xata taho da gudu ta shiga. Kaka tananan tsaye kekam kamar soja tana jira taga wa xai shigo,Abba ne yayi sallama y shigo dauke da kayan islam a hannu kaka tace au ashe tare kuke yace eh wlh y samu guri y xauna juye kayan yayi yace hajiya ga kayan islam na makaranta nan anjima aslam xai kaita islamiyya kaka tace to angode Allah yayi albarka Abba yace ameen y fice. Islam ce ta futo ta xauna tace kaka kinga makarantar da aka sakani aradun Allah dole na maida hankali kada su koroni,baki ganta bafa tun daga waje fulawoyi da fanti cikinta kuwa harda kwalta da fulawoyi ai wlh jarababben tanimu ma yakemin masifa inna tsinko mangwaronsa to makarantar harda mangwaro da goba kai kaka ga lilina kai komai dai dodar ta tuntsire da dariya,kaka ma dariyar ta tayata tace kwashi kayannaki kikai cikin daki islam tace toh takai daki ta dawo. Kaka tace yauwa alhj karami yace anjima aslam xai kaiki islamiyya xumburo baki islam tayi tace gaskiya inshi xai kaini banaso saboda nasan dukana xaiyi tayi a hanya,kaka tace haba ta wajena karki damu xanyi masa magana kafin ku tafi baxai dakeki ba islam tace toh ta tashi,kaka tace ina kuma xaki islam tace xanje nadauko taslem muyi wasa kaka tace toh sai kin dawo,tafe take tana kada yar sandarta tana tana waka part ta gani guda uku rike haba tayi tace ohni yasu to wanne gdan aunty amarya aciki tunani ta tsayayi kawai ta shige wani wanda xuciyarta ta amince mata ta shiga ko sallama babu ta shiga dakunan ta shiga turawa taji duk a rufe har xata juya tace au bari natura wancan ko acikinsa take sadaf-sadaf take tafiya kamar mara gaskiya tana tura kofar kuwa taji ta budu xura kanta da xatayi idonta yayi arba da mugun gani ihu ta kwala. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:55 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (9/10/2016 1:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *16* A firgice Aslam da yake goge jikinsa dan fitowarsa daga wanka kenan yakai idonsa kanta da sauri taja kofar ta sheka a guje. Tsaki aslam yayi yace oh god meyasa nake sake yarinyar nan take ganina ba kaya sai ta rainani tsaki yayi yace ai tana rainani ubanta xataci a gdannan. Islam kuwa sai data futa daga part din sannan ta tsaya tana maida numfashi dariya tahauyi tace lallai yaya aslam dinnan dan iskane in banda iskanci y futo daga bandaki ba kaya bakinta ta kama au kar a jini ace nima naxama yar iskar tunda naganshi ba kaya dariya ta dada kyalkyalewa da ita. Aunty amarya ce ta futo dauke da taslem xata je part din mommy islam ta gani tanata babaka dariya aunty amarya ce ta kirata tace ke islam dariyar me kikeyi tsagaita dariyar tayi tace ba komai aunty amarya tace toh me kikeyi anan tace gidanki xani dauko taslem aunty amarya tace toh yar kauye ai kin shigo gda part xakice in kuma da hausar xaki fada sai kice bangare xumbura baki islam tayi tace wlh aunty amarya niba yar kauye bace kosu hanne cemin sukeyi yar birni,aunty amarya tace ke kika sani ni karbeta xuwa tayi xata karbi taslem tana kunkuni aunty amarya tace me kike cewa xumbura baki tayi tace niba magana nakeyi ba girgixa kai aunty amarya tayi tace Allah y shirya. Part din kaka islam ta koma sunata wasansu da islam kaka tace nifa kun dameni da hayaniya islam tace kijiki kakannan toki tafi dakinki mana,aslam ne yayo sallama y shigo suna hada ido da islam ta tuntsire da dariya mamaki y shigayi da sauri yayi kanka y buge bakin kuka ta fara tana toni menayi maka Allah y isana mugu wani bugun y kaiwa bakinta da sauri kaka ta taso tace haba metayi maka daga shigowarka xaka fara dukanta,tsaki yayi yace bakya gani daga shigowa ta muna hada ido tahau yimin dariya,kaka tace to dalilin me dan tayi dariya xakace dakai take yace aini ta kalla. Islam tace eh anyi dariyar ai abun dariya kayi a xuciye y mike da gudu ta xari taslem suka shiga dakin kaka ta saka key kwafa yayi yace ai xaki futo tace eh inna futo ka kasheni karka barni da rai tayi tsaki. Komawa yayi duk xuciyarsa a xafafe kaka ta kalleshi ta watsar tace wlh can kaikasan inda ka kwaso wannan bakar xuciyar taka da alhj xaiji ta tawa ma daya hanaka tafiya aikin sojannan bakaje bama yaka kare balle kaje soja tayi tsaki,murmushi yayi yace haba ta wajena ai bakya soma ba dan Allah karki cewa daddy y hanani xuwa aikin sojannan kinga shima jahadi ne tace toh naji,anjima kasan xakakai islam makarantar islamiyya ko yace eh ai da wurima xanxo tace ba xuwanka da wuri ba Allah ka daketa a hanya tamuce dakai mikewa yayi yace wlh tsohuwarnan rigimarki tafi karfinki sai anjima y fice. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:56 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (10/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *17* Bayan yaran gda sun dawo daga makaranta misalin 4:00pm suka shirya suka tafi islamiyya inda baxasu dawo ba sai 8:00pm. Wajen 5:30pm sannan aslam y shigo yace islam taxo suje kamar abin arxiki tasaka hijab suka tafi,har sukaje makarantar bawanda yacewa wani ci kanka office din head master sukaje bayan sun gaisa aslam yace, yarinya y kawo head master yace eh munyi waya da alhj dama yace xa'a kawo yarinya kallan islam yayi yace yaya sunanki tace islam yace masha Allah nagaskiya xaki fadamin tace Aysha Aliyu Umar yace suna masu dadi yasa wani malami yayi mata interview anan fa akeyinta domin islam ko ixu daya bata kai ba,aka janyo mata acikin suratul nab'i xaro ido tafarayi malamin ya canja suratul naxi'at itama bata iya ba dakyar dai aka samu takawo suratul a'alah itama sai da akaci gyaranta aka dada tambayarta wasu surorin ta karanto ammafa a kowacce sai anci gyaranta amma dai kira'arta da dadi da akaxo sauran littattafai kuwa duk bata iya ba (karku manta anu kori islam daga islamiyya a garinsu saboda rashin jinta allo takeyi itama sai taga dama take xuwa kuma a makarantar allo dama qur'ani kawai akeyi),haushi da bakin ciki kuwa duk y turnike aslam,head master y kalli aslam yace sai dai mu sakata aji 1 saboda kasan makarantar nan tahafix ce in muka sakata aji 2 sun wuceta baxata taba gane karatun ba,ihu tahauyi tana wlh ita baxa a sakata aji daya ba salon yara su rainata harda birgima takeyi a kasa tsawa aslam yayi mata yace ta tashi amma tace baxata ashi ba sai indai xa'a sakata a aji 2 head master ne yace toh taso kiji tashi tayi tana kade jikinta tana goge hawaye. Head master yace xa'a saki a aji 2 amma kin yadda duk randa baki iya hadda ba xa'a dakeki shiru tayi da taji xancen duka murmushi head master yayi yace kinyi shiru dago kanta tayi tace kuma dukan da xafi murmushi y sakeyi yace eh mana bakince aji 2 kikeso ba tace eh nayadda yace toh shikenan littattafai y debo y bawa aslam yace ranar asabar ta fara xuwa godiya aslam yayi suk a tafi. A hanya aslam yace dakikiyar banxa dakikiyar hofi dama nasan ba abin da wannan kwakwalwar taki xata dauka mai kwakwalwar kifi kawai,murguda baki tayi tace wlh niba dakikiya bace kuma karka kara cemin mai kwakwalwar kifi kuma wlh indai nice sai kayi dana sanin maganar nan daka fadamin bakinta y buge yace kin dade bakiyi ba murguda baki ta sakeyi tace kuma Allah y isana dada buge bakinta yayi ta saki ihu har sukaje gda tana kuka. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:56 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (11/10/2016 5:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *18* Suna shiga part din kaka ta dada wage murya tana ihu,da sauri kaka ta futo a daki da sauri tana nenene y faru islam,cikin shashshekar kuka kamar wadda akayiwa tsinannan duka ta fara magana dakyar saboda yadda numfashinta yake sama da kasa,tace toh ba yaya islam bane tunda mukaje makaranta akayimin gwaji saboda ban iya wani abinba ya karbi bulalar malamin makarantar ya dinga dukana yana kwallo dani yayi ta xagina yana cemin mai kwakwalwar kifi sannan tayi shiru. Shidai Aslam tsayawa yayi kallonta kamar t.v ya saki baki saboda yadda yaji tana masa sharri tana hado xancen gaskiya da karya bai gama tsinkewa ba sai da yaga kaka ta janyo akwatin kayansu tana goge hawaye tana indai dan mun dawo gidanku kake mana wulakanci yau xamu koma inda muka futo,to dama in banda islam ma taso mu dawo me xai dawo dani,amma saboda ka rainani kafin ku tafi sai dana ja maka kunne akan kada ka sake ka daketa amma dayake ka rainani ni ban isa nace ba shine sai daka daketa da sauri Aslam y tafi yana kaka dan girman Allah kiyi hakuri wlh ban dake taba in baki yadda ba to kije makarantar ki tambaya amma ni bandake taba,kaka firr taki ita dole sai ta koma gwarxo yau Aslam cikin rawar murya yace kaka ki rufamin asiri kiyi hakuri insu daddy sukaxo nasan rainane xai baci,tsaki kaka tayi tace ai gwanda su in sukayi maka magana kaji amma ba abinda xai hanamu tafiya. Tsilli-tsilli islam tayi da ido tuno irin kyawun makarantar da akaje aka sakata ga liluna a ranta tace ina wlh baxan koma kauye ba ban hau ko lilon bama da sauri tace to shikenan kaka ki mayar da kayanmu karmu tafi insu daddy sunxo saiki fada musu suyi masa duka shima kaka tace shikenan.... Kafin ta rufe baki sai gasu daddy nan sun shigo kululu cikin Aslam y bada kara saboda bayasan bacin ran iyayensa,bayan sunyi sallama sun shigo bayan sun gaishe da kaka,Aslam kuma y gaishesu daddy yace hajiya yana ganki da jaka kuma dukkanku a tsaye nan ta fara ai da tuni mun dade a tasha,daddy yace innalillahi meya faru me xakiyi a tasha nan ta fada musu abinda Aslam yayiwa islam kuma sai da taja kunnensa kafin y tafi kaita makarantar,Abba dai shiru yayi dan yasan karya islam takeyi,daddy kuwa fada y shiga yi ta inda y shiga batanan yake futaba,Abba ne y tausheshi akan yayi hakuri,daddy y kalli Aslam yace kuma ka shirya domin admission dinka y futo xaka tafi skul of army din kuma ka gama hada komai yau saboda gobe xaka tafi,godiya Aslam yayi y futa. Islam murna kuwa kamar anyi mata bushara da gdan aljanna saboda tasan ko banxa xataci karanta ba babbaka domin yaya ameer ba ruwansa. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:56 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (11/10/2016 5:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *19* Aslam yana shiga daki gado y fada jin ransa yayi yana kuna,duk da shiyakeson skul of army dinnan amma yau sai yaji bayaso haka y dinga juyi har bacci barawo y saceshi. Washe gari da misalin 11:00am ya shirya tsaf y futo cikin shirinsa part din momynsa yaje bayan y gaisheta anan tayi masa nasiha sosai mai ratsa jiki,sannan tayi masa fatan alkhairi kuma Allah yasa y samu abinda yakeso godia yayi mata daddy ma yayi masa tasa nasihar tashi yayi yace bari yaje yayiwa aunty amarya da Abba sallama y futa. Lokacin daya shiga part din aunty amarya itama a xaune y tarar da ita itada Abba taslem kuma tana wasa,y gaishesu suka amsa suma sunyi masa nasiha da fatan alkhairi sannan y tashi yace bari yaje part din kaka. Yana shiga a lokacin islam ta futo daga daki sleeping dress ne a jikinta riga da wando cotton pink colour gashinta ya barbaje a fuskarta da bayanta kallo daya yayi mata y dauke ido karasawa yayi ya gaida kaka ta amsa,yace toh kaka naxo miki sallama ne,tace au mai gidan harka futo to Allah y kiyaye y tsare yace ameen itama tayi masa nasiha sosai. Islam ta kalla tace baxaki yiwa yayannaki addu'a ba yau xai tafi makarantar aikin soja xumbura baki islam tayi tace toni ina ruwana in yaje ma karya dawo dan duk gidannan yafi tsanata tunda shi yake dukana ta karashe maganar da murguda baki,kamota kaka tayi ta daura ta a cinya tace haba islam din kaka yanxu inya tafi ba shikenan ba kiyi masa addu'a kinji kinga jirgi xai hau,xabura tayi ta tashi daga cinyar kaka tace jirgi fa kikace kaka,kaka tace eh islam ta kara cewa mai tafiya a sama ko,girgixa kai kaka tayi,shidai Aslam kallanta kawai yakeyi,murmushi Islam tayi ta matsa kusa da Aslam ta kama hannunsa biyu tace yaya Aslam Allah y tsare y kaika lafiya,wani dadi yaji a ransa shima murmushi yayi yace ameen Islam dan Allah ki daina fitina ki maida hankalinki a karatu kinji. Kurr ta kura masa ido a ranta tana tabb ai yanxu xan bude shafukan rashin ji sainayi suna akaf unguwarnan,ganin da Aslam yayi ta tafi tunani shiya sakashi girgixa mata hannu firgigit ta dawo daga tunanin da take tace eh mekace ya Aslam murmushi yayi yace Allah y shiryaki tace ameen. Tashi yayi yace toh kaka ngd nixan tafi har wajen mota Islam ta raka Aslam hannunta na cikinnasa su mommy suka futo daddy da Abba ne suka kaishi airport y yanki ticket y wuce photercort sai muce Aslam Allah y kaika lfy y bada abinda aka tafi nema ameen. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:56 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (11/10/2016 6:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *20* Islam abin nema y samu tana komawa dakin kaka tahau rawa harda wakarta itama kaka dadi takeji saboda tasan yanxu islam xata sake saboda badan takurarta. Da yara suka dawo islam har party ta hada kaka ce ta bata kudi taje tasiyo biscuit da alawa a gaban layinsu ta dawo lokacin akwai wuta ta kure kida sukayi rawa ta rabawa yaran biscuit da alawa sannan tace yaune ranar da Islam ta samu yanci nayin abinda takeso ihsan ce take fadawa aunty amarya sakawa tayi aka kira mata Islam tayi mata fada aikuwa tahau kuka tana dama itace kadai bataso tafison su ihsan dakyar aunty amarya ta lallabata tayi shiru saboda tana tsoron masifar kaka,dan bata da hakuri akan duk wanda y taba islam. Yau thursday malamin da yakewa su amera lesson yaxo yau harda islam a gurin lesson din ma bata xauna ba ta tsokali wannan ta xunguri wannan a haka aka gama musu malamin y tafi. Sai dare lokacin da zasu kwanta ta takura Amira saita koya mata karatun aikuwa haka Amira tayita nuna mata har sai data iya,dariya islam tayi tace Amira kinsan meyasa nakeso na iya karatu yanxu sosai girgixa kai Amira tayi kwafa islam tayi irin maganar da xata fada tayi mata ciwo tace yaya Aslam ne yacemin mai kwakwalwar kifi dariya Amira ta tuntsire da ita Islam tace to dallah malama menene na dariyar wlh saina fasa fada miki,Amira ce ta gimtse dariyarta tace to nayi inaji Islam tace to shine yanxu na wanke kwakwalwata nayi alkawarin saina bawa yaya aslam mamaki duk randa y dawo,Amira tace ai hakan yana da kyau suka kwanta. Aslam bayan ya sauka a photercourt taxi y tara ta kaishi gdan wani abokin daddy bayan y huta yayi wanka yaci abinci yaje suka gaisa da matar alhjn shi yayi musu jagora shida safwan dansa xuwa makarantar sai daya gama musu cuku-cukun komai sannan y koma gda makarantar da yake akwai hostel to a hostel sukace xasu xauna. Ya kira daddy Abba mommy da aunty amarya y fada musu y sauka lafiya har yaje makarantar sunji dadi sosai. Yau islam ta fara xuwa islamiyya kamar yarinyar kirki haka ta nutsu malamai sukaxo sukayi musu karatu wata yarinya ce ta takata islam tace ke kin takani cikin masifa yarinyar tace nataka din idan kuma xaki iya ramawa bismilla har xatayi magana Amira ta hanata tace wlh kausar masifaffiya ce kowa a ajinnan tsoronta yakeyi saboda karfi ne da ita mai kashi dayafa akece mata islam tace toh ina ruwana wlh saina rama da sauri Amira ta riketa tace dan Allah ki rufa mana asiri murmushi islam tayi tace to shikenan(nikuwa nace anya kuwa yafiyar takai har xuci mudaije xuwa😊). 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:57 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (12/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *21* Ana tashinsu daga makaranta kausar har xata futa a aji taji an janyo hijabinta kii tayo baya a masifance ta juyo tace wanne dan rainin hankalinne xai jamin hijab,kallanta islam tayi sama da kasa tace nicenan ba kince daxu in rama takani da kikayi ba to yanxu xan rama,murmushi kausar tayi tace dani xakiyi fada islam a tsiwace tace eh ke wacece daya wuce banxa,Amira dake gefe jikinta sai rawa yakeyi yara kuwa da sukeji haushin kausar addu'a sukeyi Allah yasa islam tafi kausar karfi ta casa musu ita a xafafe kausar ta kaiwa islam duka da sauri islam ta matsa yanayin yadda kausar takai dukan shi yaja ta fadi kasa da sauri islam ta danneta tahau dukanta ta ko ina duk yadda kausar taso ta kwace kanta taki (nikuwa nace karfin kauye da karfin birni ba daya ba😜) tuni kausar tahau ihu tana neman taimako yara kuwa me zasuyi inba dariya ba nan suka hau ihu suna sai Islam! Islam!! Islam!!!. Malami ne yaji ajin anata ihu da sauri y karasa ganin abinda ke faruwa shiya saka shi hanxarin xuwa dakyar y dage islam daga kan kausar islam tana ta maida numfashi kausar kuwa kuka takeyi sosai islam tace wlh hmmm ai na fada miki hmmm ni ba sa'ar yarinya bace yadda take magana tana muxurai shine yasaka malam murmushi yace meya hadaku duk yaran ajin sukace kausar ce da tsokana ta taka islam kuma taki bata hakuri,dayake malam yasan halin kausar kusan kullum sai an kawo masa kararta shiyasa bai dauki wani mataki ba y bawa kausar hakuri yace islam ta bata hakuri cikin kumbura dakyar tace kiyi hakuri,malam yace kausar ma tabawa islam hakuri itama ta bata sannan kowa y futa dayake daukar yara ake xuwa sai 8:00pm ake tashi a skul din. A mota Amira tace wlh islam banxaci xaki iya dukan kausar ba saboda kowa tsoronta yakeyi kuma har ajinmu na boko daya,murmushi islam tayi tace toh an fada miki kowa ma matsoraci ne kamarku ai wlh ni baxan kyaleta ba indai tamin casata xanyi. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 (12/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *23* Washe gari da islam taje makaranta sai wani shan kanshi takeyi yan ajinsu kuwa sai nan2 da ita sukeyi,ganin da kausar tayi kowa y koma gurin islam shiya dada bakanta mata rai a haka dai har aka tashi. Yau islam murna takeyi xataje makaranta mai lilo tun asba yau ta tashi ba yadda kaka batayi da ita akan takoma bacci ba amma taki sam. 7:00am ta gama shiryawa cikin unifoam dinta maron colour doguwar riga iya gwiwa cikin rigar kuma white shirt ce mai gajeren hannu sai farar socks data saka har gwiwa kaka tayi mata packing din gashin ta da riboms inda y sauka har bayanta ta saka white hijab karami mai hula amma duk da haka sai da gashin nata y futo,xungurin Amira tayi tace wai baxaki tashi ki shirya ba firgigit Amira ta tashi wanka ta shiga itama data futo ta shirya irin shirin islam itama gashin ta da akayi mata packing har wuyanta y sauka futa sukayi suka gaida kaka sukayi break past black shoe duk sukasa yasha punish sannan suka rayaya skl bag dinsu sallama suka yiwa kaka suka futa. Part din mommy sukaje sika gaida daddy da mommy,mommy sai tsokanar islam takeyi wai unifoam din yayi mata kyau kamar dan ita akayi shi,islam kuwa sai yashe baki takeyi tanajin dadi daddy y bawa kowa 50 naira. Part din aunty amarya sukaje suka gaidata da Abba anan suka dauki launching box dinsu saboda ita take yiwa yara abincin makaranta dukkansu sukaje suka futa suka shiga mota bus saboda suna da yawa islam da Amira kuma suka shiga ta Abba saboda shi xai kai islam. Sunje Abba yakai islam principal din yace to shikenan a kira uncle hasheem shine malamin class dinsu Amira ce ta kirashi principal yace ga sabuwar daliba an kawo maka uncle hasheem cikin girmamawa yace OK sir assembly suka futa akayi musu nasu nayan primary section bayan an gama musu ayi na yan secondary section. Class islam suka tafi a seat din Amira ta xauna saboda su biyu ne a seat din itada kausar,lokacin da kausar ta shigo arba idanunta yayi da islam dam kirjinta y buga kuma gashi a seat dinta ta xauna xuwa tayi tasamu guri ta xauna. Uncle hasheen ne yaxo ya kira suna yayi introducing din Islam ga sauran student y kalleta yace what is ur name dakyat ta tattaro nutsuwarta cikin barin baki tace my name is Aysha Aliyu Umar uncle hasheem yace nice name how old are u tace I'm 8 year old yace OK go back to ur seat dam kijinta y buga saboda bata gane meyake nufi ba Amira ce ta yafito ta da hannu cikin sanyin jiki ta tafi ta xauna. 💘💘💘 *daga* *sisin* *mama* 💘💘💘 [11/12, 8:58 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (14/10/2016 12:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *24* Da misalin 4:00pm tafi makarantar islamiyya a hanya suka hadu da kausar suka tafi gaba daya,suna tafe suna wasa da tsokana dan duk yaron da suka hadu dashi sai sun dan dakeshi sannan su sheka da gudu,Amira tace Allah yau malam dalha ne yake tsaron makara,kuma dukanshi da xafi islam ceta hayayyako mata tace ita ta taki haka kuwa ta kama hanya ta tafi da taga basu da niyyar tafiya su kuwa basu sai wajen 4:30pm suka karasa nan suka tarar ana dukan latti yara sai kuka sukeyi haka suka shiga suna raba idanu aka tsutstsula musu bulala suka shiga aji suna kuka Amira data gansu tace me xatayi inba dariya ba ta dinga dariya tace hakkin yaran da suka daka a hanya ce sukuwa haushi duk y ishesu,yan class kuwa manaki sukeyi yadda islam da khausar suka xama kawaye amma ba halin magana dansun gane a kule suke karsu sauke kwandon bala'insu a Kansu. Bangaren Aslam kuwa karatunshi yakeyi sosai dan babban burinshi dama y xama soja,ga training kullum sai sunyi tuni jikin shi y fara murmurdewa dama gashi mai kirar karfi,koda yaushe suna waya da yan gida wani lokacin harda yaran gran amma basu tabayi da islam ba,a ranshi yana mamakin taurin ran yarinyar yasha bawa safwan lbrnta shikuwa safwan sai yayi dariya yace gaskiya yarinyar nan ta dace dakai kyawunta ayi yar gda a xuciye Aslam xaice god forbid mexanyi da ita ai tamin yarinya babban yaro kamata na bige a tatsitsiyar yarinyarnan baran2 suke rabuwa da safwan amma duk randa xancen y tashi saiya masa maganar Islam. Su islam kuwa rashin ji sai abinda y karu dan yanxu a makarantu 2 su babu wanda baisan islam da khausar ba dan basa barin ta kwana dan a boko basu kyale kowa ban dan ko yan secondary section ne sukayi musu rashin kunya sukeyi musu. Abinda yake taimakarsu 1 yan matan suna shakkar uncle hasheem dan matashi ne dan kwalisa ya iya daukar wanka rububinsa sukeyi yan samarin kuwa suna shakkar yayyin su islam din maxa dan duk yan gdan su islam makarantar sukeyi inka dauke Aslam da Ameer da sukayi candy sai tasleem davata isa makaranta ba. A aji kuwa uncle hasheem y gaji da yadda ake kawo masa karar su islam kullum cikin alkalanci yace amma su islam basu canja haliba har sai daya fara dukansu. *assalamu* *alaikum* *masoyan* *goyon* *kaka* *kuyi* *hakuri* *da* *jina* *jiya* *shiru* *wlh* *matsalar* *network* *na* *samu* *dftn* *xakuci* *gaba* *da* *biyoni* *danjin* *yadda* *xata* *kasance* *ngd*😊. 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 8:58 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (16/10/2016 1:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *25* Haka rayuwa tayi gaba da kasancewa daga islamiyya har boko su islam sun gagari kowa inda Allah y taimakesu ma suna da kokari,sannan sai da tasan yadda tayi aka daina kaisu makaranta a mota,dawowa ne kawai ake daukosu. Dan akwai wani lokaci da suke tahowa suka tare wani yaro dan class dinsu islam da khausar sukayi masa duk wai yayi musu dariya a class lokacin da uncle hasheem yake dukansu,duka sukayi masa sosai harda fasa masa baki da yaga masa unifoam washe gari iyayen yaron sukaje makaranta suji dalilin dukan yaransu da su islam sukayi. Lokacin da aka kirasu sukayi tsilli 2 da ido displin master akasa y xanesu,aikuwa suka dinga kuka wiwi harda majina da yawu sannan akayiwa iyayensu waya sukaxo aka fada musu irin ta'asar dasu islam sukayi hakuri suka dinga bayarwa to tun daga lokacin yan ajinnasu suka dan samu sauki. Lokacin da Abba y koma gda yake fadawa kaka abin da islam da kawarta sukayi a makaranta cewa tayi to ai haka shine dai 2 dan dana kai karar islam gwanda akawomin dan ko a kauye bata daukar raini shiyasa nake alfahari da ita saboda bata daukar raini dukkuwa da karancin shekarunta,Abba yace Allah y kyauta,kaka tace ameen y futa. Aslam kuwa yanacan jiki duk y murde dama shi mai siffar karfafa balle kuma y samu training yauma kamar kullum sundawo daga training shida safwan,Aslam yace wlh inaso inje gda dannayi missing dinsu da yawa,dariya safwan yayi yace kayi missing din yan gda ko kayi missing din islam saboda ai naga yan gda suna xuwa maka visiting kawai ka futo kace kayi missing din jerry dinka y karasa maganar yana kyakyata dariya,tsaki Aslam yayi yace Allah y sawake min narasa wanda xanyi missing sai wannan fitinanniyar yarinyar kai bakasan halinta bafa ita ko yaya muka xauna saita batamin rai ko kadan batason farin cikina safwan y kyalkyale da dariya yace shiyasa ai kuka xama tom & jerry kai tom ita jerry wlh abokina da xakuyi rayuwar aure da islam dakuwa na koma gidanku da xama saboda nadinga kallon drammer y karashe xancen da dariyar shakiyanci,darararsa Aslam yayi yace ko kadan ko a mafarki baxan taba aurar yarinyar nanba nasha fada maka cewa ni babbar mace nakeso wadda xata dauki lalura ta ba wannan tatsitsiyar yarinyar ba,safwan yayi karaf yace ai itama xata girma tsaki Aslam yayi yace naga kai xancen dadi yakeyi maka y dauki towel y shige bathroom wata dariyar safwan yayi yace woo Aslam na islam bada kanka a sare kaje gda kace y fadi. Lokaci ya tafi abubuwa da yawa sun faru aciki harda gama primary skul dinsu islam rayuwa tanawa islam dadi saboda rashin ganin Aslam dan ita harmantawa takeyi dashi. 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* [11/12, 8:58 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (16/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *26* *3* *year* *letter* Mislan 4:00pm islam ce xaune tana tsantsara kwalliya kaika rantse wata shahararriyar yan mata ce a lokacin tana da 11 year Amira ma tana gefenta tana shiryawa sunyi bala'in yin kyau englishi wears suka saka wandone pencil black da body hug ta islam purple ta Amira pink Islam tanada veil purple Amira kuma pink sunyi kyau sosai wani arnen takalmi suka saka black mai tsini da igiya ma ake daureshi. Futa sukayi suna islam ce tayi juyi ta kashewa yaya haidar ido tace my bros yaka ganmu munyi kyau ko yace sosaima ai fadar irin kyawun da kukayi bata bakine,tace toh yanxu ka dauko mukullin mota ka kaimu gidansu khausar wanta sagir y hada mana party yace tab kuje isya ya kaiku niyau banajin xan iya futa,kallan kaka tayi ta shagwabe fuska tace kinji shiko kaka wai baxai kaimu ba kaka tadan sassauta murya tace haba angona daure ka kaisu dan Allah tashi yayi yace toh kunci albarkacin kaka kuxo na kaiku amma ku sani wlh baxan daukoku ba islam tace eh munji futa sukayi da aunty amarya suka hadu xata shiga part din kaka tace toh sarakan yawo ina kuma xakuje carab Amira tace gidansu kausar,aunty amarya tace towa kuka tambaya kuma me xakuyi,islam ta xumbura baki tace kaka muka tambaya kuma ai party yayansu kausar y hada mana kuma kaka tace muje girgixa kai aunty amarya tayi tace Allah y shirya. Mota suka shiga islam a gaba Amira a baya y kaisu gidansu kausar y juyo dayake ba nisa neman magana ne irinna islam tace sai a mota wai itama yanxu ta xama yan mata. Shiga sukayi har part din mamarsu khausar suka gaisheta,acikin gdan yaya sagir yasaka akayi decorating aka kawata gurin itama khausar irin dressing din su islam tayi amma ita body hug da veil dinta red kawayensu maxa da mata sunxo gurin dan harda yan islamiyyarsu sunxo. Sagir y kalli islam yace pretty kinga kyawun da kikayi kuwa ai kin haska gurinnan tamkar xara acikin taurari,wani farr tayi da ido ta kyalkyale da dariya tace kai yaya sagir karka bani kunya mana yace au baki yadda ba kenan ko pretty murmushi tayi wanda har saida dimfil dinta y loba ta rufe idanunta da hannunta kama hannunta yayi yace taho muje muyi rawa,suka shiga d.j y saki kida su kausar suka mara musu baya suka fara cashewa. A daidai gate din gidansu y sauka a taxi sanye yake da white t shirt da wandon kaki na sojoji kanshi da hula y daura ainahin rigar unifoam din a kugunsa yana rataye da wata katuwar jaka a kafadarsa yana da tsayi dan irin gient dinnanne jikinshi ne xai tabbatar maka da cewa kakkarfa ne dan irinsu ake kira da lion shape,hular y cire y karewa area din kallo subhanallah shine abinda na fada saboda haduwar saurayin chocolate colour ne yana da wani irin sexy eyes wanda eye lashes suka kawata shi xara2 yana da cikar gira baka kirin kwantacciya dogon hancine dashi har baka yayinda yake da dan madaidaicin baki lebenshi pink colour ne wanda ta ido xaka gane xaiyi laushi,yanada kwantaccen saje yayinda wani gashi y xagaye bakinshi wani irin sihirtaccen kyawune dashi murmushi y saki lokacin daya karewa layin kallo ai susucewa nayi saura kiris birona y fadi saboda bayyanar jerarrun hakwaranshi farare tass yayinda siririyar wushirya ta kawata tsakiyarsu daga kumatunshi na dama kuma y lotsa daidaita xaman jakar yayi a kafadarsa y fara tafiya irinta xaratan maxa yana wani taku da karfinsa nidai a tunanina xai kai 25 year amma a yadda yake saikayi tsammanin dan 30 year ne. 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 8:58 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (17/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *27* Saida naga gdan daya shiga mutsitstsike ido nayi nace kai badai Aslam bane yaxama wannan karkarfan namijin ba da gudu nabishi ganin harya shige gdan. Aunty amarya ce ta fara ganinshi a lokacin ta futo daga part din kaka fara'ar fuskarta ce ta fadada da sarsarfa y karasa gurinta jakarshi y ajiye y rungumeta wani sassanyan numfashi y saki yace i miss u my aunty,dariya tayi ta xareshi daga jikinta ta saki dariya tace lallai my son ka sammacemu ko waya,wani murmushi yayi wanda y kara futo da ainahin kyawunsa yace ai surprising dinku nayi,tace lallai kam kuma kaci hannunsa ta kama da daya hannun kuma y dauko jakarshi suka karasa shiga part din mommy a palo suka tarar da mommy tana kallon arewa 24 da sauri y saki hannun aunty amarya yaje y rungume mommy dariya mommy tayi tace auntyn yara gaskiya yaronnan naki baya girma kiga yadda yaxo y turmusheni,shagwabe fuska yayi yace kai my mom yanxu bakiyi missing dina ba (ni dariya y banima yadda yake shagwabe fuska 😂) aunty amarya tace a'ah mommy ai duk cikin kewarmu ne tashi Aslam yayi yace su daddy basu dawo ba mommy tace eh suna kasuwa yace OK banaje naga my granny da sassarfa y fice,mommy tace auntyn yara kiga yadda danki ya wani xama kato dariya aunty amarya tayi tace ai aikin soja ba wasa bane shiyasa nake alfahari da dana dariya mommy tayi tace gaskiya tashi aunty amarya tayi tace bari naje na hadawa my son abinda xaici tunda bai sanar damu ba girgixa kai mommy tayi itadai tana farin cikin irin yadda fateema takeson yayanta. Da sallama y shiga part din kaka kaka ta tashi da hanxari tana wanake gani kamar mai gidana da sauri y karasa yahau juya kaka saida y wanata tamkar fanka sannan y rungumeta kaka kuwa sai maida numfashi takeyi 😂,yace wlh matar nayi kewarki sosai da sauri kaka ta kwace jikinta ta koma ta sauna ragwab akan kujera tana maida numfashi 1 da 1 tace lallai Aslam yauna tabbatar da sojoji bakuda imani ko tausayina bakaji ba kake wanani tamkar fanka,su ihsan da suke xaune a palo sukuwa me xasuyi inba dariya ba,Aslam ma murmushi yayi yace Allah y baki hakuri uwargidana wai irin yadda nayi kewarki na nuna miki doke hannunsa tayi da yake kan cinyarta tace naji dai murmushi yayi y tashi yana sosa keya kallansu ihsan yayi yace baku iya gaisuwa ba,suka gaisheshi y amsa sannan y fuce yana kaka ki damamin fura. Yana futa yayi kicibis da Amir da sauri suka rungume juna,amir yace dawowata kenan daga skul aunty amarya take cemin ka dawo,Aslam yace eh shigowata kenan,Amir yace amma babu sanarwa Aslam yace eh surprising dinku nayi Amir yace gaskiya kam karasawa part dinsu sukayi bedroom dinshi Aslam y bude y shiga Amir na binshi kayan jikinshi y rage y xama daga short nikker sai vest yadau towel y shige bathroom,Amir kuwa dakin y fara kadewa y cire bedsheet y canja wani danma dakin ba wani datti yayiba kusan duk sati ana share dakin a gyara. 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 (17/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *28* Kafin Aslam y futo y gyara dakin yayi morphing ya dauko burner a dakinshi yasa turaren wuta tuni dakin yadauki kanshi (nikuwa nace lallai Amir matarka ta huta irin wannan gyara haka). Da Aslam y futo mamakine y kamashi y kalli Amir yace ah my bros waye y gyara dakinnan murmushi Amir yayi yace waka gani a dakin,Aslam ne mamaki y kasa boyuwa a fuskarsa yace kana nufin kaika gyara lumshe idanunsa yayi y kwanta a gadon yace eh nina gyara Aslam yace lallai dan samari ka huta kai wlh ko aure kayi matarka ta huta murmushi Amir yayi yace kaima dole ka koya ai Aslam yace tab karasawa yayi gaban dressing mirrow ya shafa mai y taje sumarsa ya fesa body spray jallabiya y dauko acikin jakarsa y saka sannan y feshe jikinsa da turare kiran sallar magruba aka farayi bathroom Amir y shiga y dauro alwala,masallaci suka futa dayake a layinnasu. Ana idar da sallah suka dawo daddy da Abba suka je suka gaisar da suke part din mommy abincin da aunty amarya ta hada masa part din mommy ta kawo masa daukar warmers din yayi Amir y dauki jug din coconut drinks din da akayi masa suka wuce part din kaka. Acan suka tarar da yaran gdan sun saka kaka a gaba sunata mata shakiyanci,xama Aslam yayi y karewa yan dakin kallo yace wai kaka ina yan matanki ne,kaka tace suntafi gidansu kawarsu kausar wan kawar tata ya hada musu party,kasan sun gama karamar makaranta cikin bacin rai yace what saida muryarshi ta karade dakin tuni sauran yaran suka nutsu yace yanxu Ashe haryanxu basuyi hankali ba to tunma karfe nawa suka tafi haidar ne yace wlh tun 4:00pm na kaisu,idanunshine sukayi jajawur jijiyiyin kanshi suka futo baro2 (nikuwa nace ran maxa y baci)yace wanene y basu damar tafiya kaka tayi xaraf tace nice koban isaba tashi yayi y tsallake abincin daya faraci yace xomuje karakani gdan haidar,da sauri haidar y tashi Amir kuwa part dinsu y koma damashi bashi da magana sosai shiyasa yaran basu fiya tsoronsa ba. Su Aslam sunje gdan a gate din y futa yayi knocking mai gadi y futo ta karamar kofa Aslam yace sannu baba,baba mai gadi yace yauwa sannu dannan Aslam yace dan Allah kashiga cikin gidannan ka kirawomin Islam da Amira baba mai gadi yace yanxu suka futa da sagir a mota godiya Aslam yayiwa baba y juya yashiga mota suka koma gida xuciyarsa in banda suya da radadi ba abinda take a haka harsuka karasa gda lokacin ana kiran sallar isha'i tura haidar yayi yace jeka ganomin in sun dawo kace suxo nan su sameni haidar yace toh Aslam ya shige part dinsu domin yayi alwala a kofa suka hadu da Haidar y dawo yace naje basu dawo ba Aslam yace OK y futa xuwa masallaci Haidar ma shiga yayi yayo alwala y futa masallaci. 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 8:59 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (19/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *29* Har suka dawo a masallaci suna dawowa gda Aslam direct part din kaka y nufa yagani ko su islam sun dawo,amma dayaje basanan lokacin dayaje yake tambayar kaka wai hanyanxu yarannan basu dawo ba,budar bakinta sai cewa tayi eh basu dawo ba to waima kai mene naka na damuwa daga dawowarka xaka dagawa mutane hankali,ni nasan su islam vaxasu bata ba acikin kano kuma komai dare yaronnan xai dawo dasu,tsaki Aslam yayi y fice daga part din kaka can kofar gda y futa sai xagaye yakeyi,a ranshi yana wannan wacce irin rayuwa ce yara kanana su futa a gda sukai har wannan lokacin amma ba wanda y damu tsaki yayi y hurar da wata xaxxafar iska daga bakinsa yace dole nadauki mataki nagyara wa yarannan xama dagasu har kakan da take kin bari a tsawatar musu. Kusan 30 minute y dauka sannan yaga wata mota tashigo layin parking tayi a kofar gidansu da hucinsa y tafi wajan motar bangaren driver y tafi y fara nocking,a hankali sagir y fara xuge glass din windon ya kalli Aslam yace malam lfy,Aslam ganin islam ce a gaba tana shan ice cream shiya dada bata masa rai da sauri y bude gambun motar y shako wuyan sagir yace gidan ubanwa kakai yarannan a darennan,sagir yaji matsa sai raba idanuwa yakeyi,su islam sukayi sauri suka futo jikin Amira da khausar sai rawa yakeyi Islam kuwa ko a jikinta saima xumbura baki tayi tace haba yaya Aslam dan Allah ka sake shi ice cream fa da shawarma y kaimu y siya mana ta juya tana kallon su Amira,itadai Amira shiru tayi,Aslam kuwa mamakine y kamashi da sauri y cillah sagir gefe saura kadan y kifa ya kalleshi da idanunsa da sukayi ja yace this is the first & last warning wlh duk randa nakara ganin ka da kannena yayi wani murmushin gefen baki ya gyada kai da sauri sagir y shige mota khausar ma ta shiga a 360 yabar layin. Su islam ne suka juya xasu shiga gda kallansu yayi yace kuje ku ajiye kayan kwalamar taku tunda kunxama mayu kwadayayyu kuxo dakina ina jiranku islam ce ta murguda baki tace wlh mu ba mayu bane inma mayune mu to kaima mayene taja hannun Amira da jikinta yaketa rawa suka shige gda. Xaune suka tarar da kaka da sauri islam ta tafi dare cinyarta tace wash kaka mundawo wlh I'm very tied saboda munyi rawa sosai kaka tace to sannunku tun daxu wancan mai bakar xuciyar yake xiryar nemanku kamar wanda akace xa'a saidaku,dariya islam tayi tace ai yaya Aslam mugune kinga yadda y shake wuyan yaya sagir kuwa kaka tace lallai bai kyauta ba,kaka ce ta kalli Amira da take tsaye tace ke kuma fa kin tsaya kikam kina muxurai tamkar wadda tayiwa sarki karya,Amira tace yaya Aslam ne yace muje dakinsa mu sameshi kaka tace toh babu inda xakuje Islam tayi maxa ta tashi tace kaka karkiyi mana bakin ciki kila tsarabarmu xai bamu kaka tayi tsaki tace ku karbo uwar tsaraba ma (nikuwa nace lallai kam islam xaku karbo tsaraba). 💘💘💘 *daga* *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 8:59 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (19/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *30* Aslam kuwa xagaye yakeyi a dakinsa hannunsa sakale a bayansa yace lallai yarinyar nan ni xata mayarwa da magana har tacemin wai in su mayune nima mayene lallai yau xan tabbatar mata da soja ba wasa bane xan gwada mata kadan daga cikin irin horon da aka bamu. Islam da Amira ne a kofar dakin Aslam,Amira ce ta tsaya tace nifa islam wlh tsoro nakeji karmuje y dakemu kinsan ance sojoji basu da imani tsaki islam tayi tace toh in dukannamu xaiyi ke tsayawa xakiyi mene amfanin kofofin da Allah yayi miki ba saimu bawa wandonmu iska ba ta karashe maganar da bude dakin Aslam,suna shiga islam tace gamu tana murguda baki murmushi yayi irinna daki ganene yace toh ku xauna ina xuwa da sauri islam ta tafi bakin gadonsa ta dare Amira kuwa a kujerar da aka ajiye guda 2 ta xauna a daya duk a darare,Aslam futa yayi y duba dakin Amir yaga baya ciki yace dakyau saboda bayaso in y fara axabtar dasu Islam a samu mai kwatarsu yaje y duba dakin su haidar da yusuf suma basa ciki murmushi yayi yaje yasakawa part din key y juya y koma dakinsa yana shiga y tura kofar y rufe da key yasa key din a aljihu tuni y murtuke fuskarsa tamkar bai taba dariya ba cikin Islam ne yayi kara kuuuu saboda yadda y bata tsoro tamkar xaki karasawa tayi kusa da ita y daura kafarsa ajikin gado daidai inda islam tace yace ni kikacewa mace koh duk data tsorata da irin kallan da yakeyi mata hakan bai hanata murguda baki ba (nikuwa nace mai hali ai baya fasa nuna halinsa)nace to kaine fa kace mana mayu kuma naga duk abu dayane yayi m.....bata karasa ba y dauketa da wani lafiyayyan mari kara ta kallah tana ihu kamar wadda ake xarewa rai tuni Amira tahau kuka dantasan itama nata dukan yananan yana jiranta da hannu yayi mata alamar tayi masa shiru xubura baki tayi hawaye nabin fuskarta yace watako harkunyi girman da xaku tafi wani kato y hada muku fati sannan bayan y gama y daukeku y kaiku yawan shakatawa ko da sauri Islam tace ba yawan shakatawa y kaimu ba ice cream da shawarma kawai mukaje y siyo man...da sauri yakai hannu xai doke bakinnata itama cikin xafin rai tayi kasa da kanta y bugi iska yace watako bakinki baxai mutu bako maxa ku tashi kuyimin kamin kunne,kamin kunnen sukeyi y ciro belt din wandonshi na kayan sojoji yace koda wasa duk wanda y dago sai dai yaji saukar belt dinnan a gadon bayanshi,tashi sukayi suka farayin kamun kunnen,shi kuwa komawa yayi y xauna a kujera daya daga cikin kujerun dakin y daura kafa daya kan daya yana shan lemon gwangwani shani sun dauka abinna wasane sukaga saiyi sukeyi yaki yace su dago kuka suka fara wiwi2 ga yawu ga majina amma y tashe kunnensa da ear pies din waya yanajin waka,kusan 30 minute suka dauka duk sun hada kumi amir ne yaxo xai shiga part din yaji a kulle,kiran layin Aslam y fara yana dagawa,yace maxaje wai ina kashiga ne naxo naji kofar a rufe,Aslam yace bari naxo nabude maka tashi yayi y kalli su islam yace ku tashi tasowa sukayi amma sukaji bayansu y ruke islam ce ta bare baki tace wayyo bayana ta koma ta xauna lokacin Amira harta fice kallanta yayi yace oh baki gajiba kenan to kici gaba da sauri ta tashi tana wlh nagaji murmushi yayi,kofar suka karasa y bude musu da sauri suka fice islam ce ta juyo tace Allah y isanmu mugu axxalumi Allah kuma saiya saka mana ta falfala a guje Amira ma kuwa tabawa wandanta iska tamara mata baya. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:00 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (20/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *31* Aslam ne yayi murmushi y girgixa kai yace yarinyarnan baxaki taba gyaruwa ba Allah y shiryeki,Amir kuwa kallan Aslam yayi yace mai kayi musu ne daga kafada yayi yace kawai punishing dinsu nayi saboda fitar da sukayi suka kai dare murmushi Amir yayi yace Allah y kyauta Aslam yace ameen suka shiga part dinnasu. Islam kuwa kan kaceme hartakai part din kaka a kuje dama wajan gudu islam tamkar yar barewa ta fada kan kaka da take kwance a firgice kaka ta tashi dan har bacci y fara daukarta,tace ke lfy xaki fadomin kai koso kikeyi ki karyani,baki islam ta xumburo tace to ba yaya Aslam bane y sakamu kamun kunn....bata karasa ba Amira ta shigo itama faduwa tayi tana maida numfashi islam tana ganinta yadda take maida numfashi yasata dariya tahau kyalkyala dariya ba kakkautawa Amira kuwa ranta duk y baci saboda tana ganin rashin kunyar da islam tayiwa Aslam ne yasa yasakasu kamun kunne,ganin islam taki daina kukan yasa Amira fara kuka kawai ta tashi ta shige daki,da sauri islam ta tashi tabita tana haba sis menene na fishin dan Allah kiyi hakuri ta tashi tabita dakyar saboda yadda kafafunta sukeyi mata ciwo. A kwance ta tarar da Amira tana kuka wiwi da sauri islam ta karasa ta dagota ta rungumeta tana haba 6ter dan Allah kiyi hakuri indai ni nabata miki rai kuma wlh naci alwashin saina daukar mana fansar abinda yayi mana kamar yadda yasaka mu a wahala muma saimun rama ko baikai yadda mukasha ba da sauri Amira ta tashi tace me xakiyi masa sis islam tayi wani shegen murmushi tace kawo kunnenki,Amira ta mika mata kunne ta rada mata magana. Da sauri Amira ta xabura ta matsa daga kusa da Islam tace gaskiya sis inajin tsoro,harararta islam tayi tace kefa banxace kinfiya tsoro wlh kina nufin wahalar daya bamu yaci bulus kenan islam ta girgixa kai tace ina baxai yuwu ba saina rama kuma hardake xamu hada plan din. _*to*_ _*jama'a*_ _*ko*_ _*wanne*_ _*mataki*_ _*Islam*_ _*xata*_ _*dauka*_ _*wajen*_ _*daukar*_ _*fansa*_ _*kudai*_ _*biyoni*_ _*danjin*_ _*yadda*_ _*xata*_ _*kaya*_ _*tsakanin*_ _*Islam*_ _*da*_ _*Aslam*_. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 (20/10/2016 3:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *32* Dakyar islam ta tashi ta shiga bathroom ta hada ruwa mai xafi ta gasa jikinta ta,sannan ta hadawa Amira ta dauro alwala ta futo tashin Amira tayi tace itama tashiga ta gaso jikinta tana shiga ta saka sleeping dress purple mai santsi doguwa ta feshe jikinta da turare ta shimfida sallaya tasa dogon hijab ta tada sallar magruba dayake basuyi ba data idar tayi sallar isha'i tayi shafa'i da wuturi lokacin Amira harta futo itama ta shirya ta tada tata sallar,ta futa ta dauko musu kayan da sagir y siyo musu lokacin da Amira ta idar da sallah xama sukayi suka faraci. Islam ce ta kyalkyale da dariya tace sis kinga idanun yaya sagir daxu yaji shaka,dariya Amira tayi tace yaushe nakula dashi nima ina cikin wani hali bayan sun gamaci Amira ta bude bedside cabinet ta dauko pracitamol ta balla tasha ta mikawa islam tace sis kisha saboda ciwon jiki,yatsina fuska islam tayi tace baxan shaba kinsanni bana shiri da magani balle uwa uba allura Amira tace kin huta ta maida maganin cikin locker din sukayi light off suka kwanta. Washe gari da safe su islam ne xaune a palo sunayin break fast Aslam yayi sallama y shigo y gaida kaka,Amira cikin rawar jiki ta gaidashi,y amsa islam kuwa datayi masa kallon up & down ta wani dauke kai,ganin da Aslam yayi islam batada niyyar gaisheshi yasa y hade girar sama da kasa yace ke baki iya gaisuwa bane,wani shekeke ta kallesa tace au yaushe ka shigo ai banji shigowarka ba wani bakin ciki yaji a ranshi tuni xuciya ta debeshi ya tashi yayi kanta da karfi ta kwala kara ta kwasa da gudu tayi bedroom dinsu shima y kausa da gudu y bita kokarin saka key takeyi y danna kofar cikin xafin rai yana shiga yasa key yasan kaka xata iya biyosu,ihu tasa ta kwalalo ido tace nashiga 3 ta kwasa a guje tayi bathroom taku 2 yayi y dankota ta saki wata raxananniyar kara tace dan Allah kayi hakuri,kaka yajiyo tana buga kofa tana wai meyasa Aslam katakurawa yarinyar nanne tamkar ita kadaice yarinya a gidannan tahau buga kofar tana wai baxaka bude ba,tsaki Aslam yayi y kwakwkwade islam ya kalleta yace idan har baxaki shiga hankalin kiba to baxan gaji da dukanki ba y tunkudata kan gado yaje y budewa kaka kofar shikuma y futa,islam sai da taga fitarsa tace Allah y isana mugu kakace ta shigo har tana hardewa tace meyayi miki kike ihu dariya islam tayi tace babu abinda yayimin yajiki da dukana xaiyi shine y fasa,kaka tace y naimawa kansa lfy dan data dakeki dayau y gane kuransa da ubansa xan hadashi murmushi islam tayi tace shiyasa nake sanki kakata ta kaina kaka ma murmushin tayi.(nikuwa nace ita kakannan kenan baxata taba ganin laifin islam ba saina Aslam dukkuwa da rashin kunyar da islam din tayiwa Aslam) Da karfe 4:00pm su islam suka shirya suka tafi islamiyya har gidansu khausar suka biya mata,islam tace ina yaya sagir ne khausar tace mommy ta aikesa,khausar tace tab lallai wannan wannaku bakar xuciya ce dashi wai dama dan gidanku ne bantaba ganinsa ba,islam ta karkatar da baki tace shinefa yaya Aslam daya tafi makarantar soja to jiya y dawo,xaro ido khausar tayi tace tab kice jiya Allah ne y taimakemu baxan kara xuwa gidanku ba saiya tafi dariya suka tuntsire dukkansu a haka harsuka karasa makaranta. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:00 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (22/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *33* Washe gari da misalin 1:00pm islam ce take cewa Amira wai baxaki shirya mu tafi ba,Amira ce tace nidai gaskiya tsoro nakeji tsaki islam tayi tace shiyasa baxaki tabaci gaba ba a cuceki kice baxaki iya ramawa ba to wlh saikinxo munje hijab Amira taja ta saka islam ce tace yauwa kaka bari muje gdan su khausar jiya a islamiyya an bamu assignment to yaya sagir ne xaiyi mana,kaka tace Allah sarki dan albarka ya kuwa kyauta ku gaishemin da mmnsu islam tace xataji suka futa a hanyama Amira sai lallaba islam takeyi akan tayi hakuri amma islam ji takeyi tamkar ana xugata (nikuwa nace to kome islam takeso tayi oho). Gdan su khausar suka shiga a palo suka tarar da mammy dinsu khausar suka gaisheta dakin khausar suka shiga bacci suka tarar tanayi duka islam ta daka mata firgigit khausar ta tashi tana mutsitstsika ido tsaki tayi tace gaskiya besty kin shammaceni yama xa'ayi ina baccina mai dadi ki tasheni ki katsemin bacci harararta islam tayi tace ke har wani lokacin baccine dake kin manta niyyar daukar fansarmu da sauri khausar ta diro daga kan gadon bathroom ta shiga tayo brush tace mu tafi dama yanxu na kwanta murmushi islam tayi tace yauwa besty hijab khausar ta saka suka futa. Khausar tace mammy bari mudanje gidansu islam,mammy tace toh ku gaishemin dasu kaka islam tace au ta kama baki tace mammy kaka mafa tace na gaisheki murmushi mammy tayi tace ina amsawa,futa sukayi islam tace kuxo ku rakani nagano yaya sagir khausar ce tace dan Allah kixo mu tafi ta kamo hannunta fisgewa islam tayi tace Allah sainaje nagan shi jiya mafa danaxo bayanan tayi hanyar dakinshi a palo ta ganshi a daune y dukufa yana danne danne a laptop daga gani abinda yakeyi mai muhimmanci ne sadaf2 ta tafi ta kwalla mai kara a kunne firgigit y tashi saura kadan ya yarda laftop din islam tana ganin haka tahau dariya harda xama sagir ganin haka yasashi bata rai harda juya baya wai yayi fushi,da sauri islam ta daina dariyar ta tafi ta kamo hannunshi tace haba yayana fushi xakayi dani murguda mata baki yayi yace eh din da sauri ta toshe bakinta saboda wata dariyar ce take shirin fitowa tace toh kayi hakuri murmushi yayi yace toh na hakura kallanta yayi yace my pretty wanene wannan na last yesterday din kallanshi tayi tace yayana ne,sagir yace pretty naga kamar kishinki a idanunsa dan Allah karki yadda a rabamu ina sonki cikin xuciyata da dukkan jikina,dariya tayi dan ita bata gane meyake nufi ba. Khausar ce ta shigo tace wai baxaki xo mu tafi ba kin shanyamu,sagir ne y kalli islam yace ina xakuje tashi tayi tamasa kiss a kumatu tace wani guri ta sheka da gudu ta kama hannun khausar tace muje,sagir kuwa murmushi yayi y shafo kumatunshi inda islam tayi kissing dinshi yana murmushi. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (22/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *34* Sai da sukayi tafiya mai nisa sannan suka futo wajen getto area saboda su area dinsu g.r.a ne abinda suke nema baxasu samu acan ba saboda kowa cikin kwaton gda yake da gate ga kuma mai gadi. Wani yaro suka gani da sauri islam tace yauwa dan Allah kai a ina ake siyarda kayan miya bushashshe wani gda dayake kallansu y nuna musu yace canne godiya islam tayi masa suka karasa da sallama suka shiga gdan suka gaida matar ta amsa islam tace abada karkashi (nikuwa nace toh mexatayi da karkashi 🙄)matar tace na nawa islam tace na 50 naira matar ta karba tasaka musu a bakar leda suka karba suka futa. Islam ce ta sheke da dariya tace kunsan Allah yanxu jin xuciyata nakeyi fara tas nasan ko banxa xan fanshe takaicin da yaya Aslam y kinsamin khausar tace shiyasa kike birgeni bakya barin ta kwana Amira kuwa shiru tayi. Tafe yake a cikin mota yanajin kira'ar sheik sudes cikin suratul maryam a hankali yakebin kira'ar y shiga titin daxai sadashi da unguwarsu ya gano wasu yara kamar su islam yana xuwa daidaisu y dinga horn islam ce ta juyo a tsiwace ganin wanda yake cikin motar shine yasa ta hadiye rashin kunyarta yaya Aslam ne,cikinta y bada wani kuuu,cikin daurewar fuska y kallesu yace daga ina kuke Amira ce ta bude baki xatayi magana da sauri islam ta katseta tace umh amh gidan kawarmu mukaje dubata batada lfy,girgixa kanshi yayi yace Allah y taimakeku ku shigo mu tafi,islam har wani jannunfashi tayi suka shiga y karasa dasu,duk suka futa da sauri khausar ta futa tace sai anjimanku suma part din kaka suka wuce har Aslam dakin suka shiga da sauri Amira ta shige bathroom islam kuwa saurin tusa karkashinta tayi a kasan gado,Amira ce ta futo tace wash wlh 6ter sai Allah y sakamin saboda tsabar fargaba kar yaya Aslam yaki yadda da maganar da xaki fada har gudawa nayi dariya islam tayi tace gaskiya sis ke xabuwa ce to wlh ya xamar miki dole ki cire tsoronnan indai xakici gaba da xama dani,cikin hayayyakowa Amira tace eh aikuwa madinga cin dan banxan duka tafice fuuu daga dakin murmushi islam tayi itama ta bita. Yau juma'a islam ce xaune a daki tana tunanin yadda xatayi plan dinta ba wanda yasan ita ta aikata da gudu ta futa part din aunty amarya ta shiga direct kitchen ta shige saboda a lokacin aunty amarya tana daki rariyar tace shayi ta dauko ta fice da sauri da yaya amir ta hadu xai tafi masallaci shidasu yaya haidar da sauri tace yaya Amir masallaci xakuje yace eh tace yaya Aslam fa yace yana ciki tace to Allah y kiyaye saikun dawo yace ameen ta wuce. Tana shiga da gudu ta wuce daki ruwan xafi ta debo a cup karkashin ta xuba saida taga y kwanta tasa rariyar shayinnan ta tace ta kulle ruwan a leda futowa tayi direct part din su yaya Aslam ta shiga saboda tasan shi kadaine a ciki daidai kofar dakinsa taje ta yaryada ruwan karkashinnan yadda baxa'a gane ba ta koma can bayan kujerar palo ta boye. Aslam ne sanye cikin farar shadda irin dinkin samari iya gwiwa anyi mata aiki da bakin xare yasaka hula baka irin doguwarnan y lankwasa ta yasa takalminshi combat boot baki y ratayo sallaya a kafadanshi xuro kafa da xaiyi santsi y kwasheshi saiji kake nak y fadi auucchh shine abinda y iya fada. Islam data buya bayan kofa kuwa saura kiriss dariyar da take boyewa ta futo bakinnata ta dada dankewa,Aslam kuwa dakyar y tashi yana dingisawa ya koma daki,islam tana ganin y shige daki ta tashi tahau rawa harda shoki💃 da sauri ta dauki mopher da ruwa ta goge gurin ta fice. *Assalamu* *Alaikum* *kuyimin* *hakuri* *na* *rashin* *jina* *kwana* *2* *wutarmu* *ce* *ta* *lalace* *dftn* *xakuyi* *min* *uxiri* 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: 24/10/2016 3:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *35* Da farin cikinta ta shiga part din kaka,a xaune ta tarar da kaka dasu Amira guri ta samu sai dariya take,kaka ce ta kalleta tace islam wannan washe bakinfa kamar gonar auduga,fararen hakoranta jerarru ta kara washewa tace nima yau narasa dalili da farin ciki na tashi,kaka ce itama ta washe hakoranta tace Allah y tabbatar da alkhairi,Amira kuwa kallan islam tayi saboda tasan iya shegen data barkata. Bangaren Aslam kuwa dakyar y karasa kan gadonsa saboda wani irin axaba da radadi da idon sahun kafarsa yakeyi danya tabbatar y bugu sosai,kwanciya yayi kan kace meh jikinshi yadauki xafi y fara rawar sanyi dakyar y janyo wayarsa y fara dialing din number Amir amma is switch up tunawa yayi yanxu may be suna masallaci haka ya lulluba da blanket duk da haka rawar dari yakeyi saboda wani xaxxafan xaxxabi daya rufeshi. Wajen 2:30pm Amir suka dawo motar da Aslam xai futa da ita yagani a packing space a ranshi yace badai har Aslam y dawo ba suna shiga part dinsu y wuce dakin Aslam kwance y ganoshi a gado sai rawar dari yakeyi da sauri y karasa yana subhanallah meya sameka a lokacin y karasa kan gadon. Dan yaye bargon yayi yace meya sameka naga a lokacin da xamu tafi masallaci kana shiryawa cikin magana irin ta wadanda sukejin jiki yayi magana yace eh harna do xan futa a daki santsi y kwasheni na fadi akan kafata to inajin ciwo naji,subhanallah Amir yace amma kuma ba ruwa a gurin ai yasa hannu y daga blanket din da Aslam y rufe kafarsa ganin kafar yayi harta kumbura,tashi Amir yayi yace bana kira baba mai gadi y gyara maka y futa da sauri. Tare da baba mai gadi suka shigo dakin da sauri baba y karasa yace sannu Aslam daga kai Aslam yayi duba kafar baba yayi yace ashsha ai buguwace yayi a kafar har kashin kafar yadan tsage anan baba y fara gyarawa Aslam kafa runtse idanuwansa yayi saboda wani axababben xugi dayake ratsashi tundaga kanshi har xuwa babnan dan yatsa tuni yahau hada gumi,baba ne y kalli Amir yace kaje dakina xakaga robb da kyalle ka daukomin jiki a sabule Amir y futa saboda yadda yake tausayin dan uwannasa. Shigowa yayi dauke da kyalle da robb din y mikawa baba karba yayi y lakuto a hannunsa yayi addu'a akan robb din y shafe kafar Aslam sannan y daure masa yace insha Allah nan da kwana 3 daurin xai since amma karka ringa motsa kafar sosai toh Aslam yace yayiwa baba godiya y kwanta wani wahalallen bacci y daukesa. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (24/10/2016 3:30pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *36* Amir tare da baba mai gadi suka futa,part din aunty amarya yaje ya xauna a kujera kallan ihsan yayi yace kawomin ruwa fridge taje ta dauko masa ta doro a try da cup,ta kawo masa kallan aunty amarya yayi yace Aslam fa bashi da lafiya a kidime aunty amarya tace me yake damunsa,cikin tsantsan tausayi yace wlh y futo xaije masallaci ya fadi shine yayi tsagewar gashi amma baba mai gadi y gyara masa cikin tashin hankali aunty amarya ta mike tace bari naje na dubo jikinnasa,Amir yace yayi bacci shiyasa na futo komawa aunty amarya tayi ta xauna jikinta duk a sabile. Tashi tayi tace bari naje na fadawa mommy kai tashi kaje ka fadawa hajiya (kaka) saika wuce dakinnasa,yace toh a tare suka futa aunty amarya ta wuce part din mommy Amir kuma y wuce na kaka. Aunty amarya ce ta shiga part din mommy xaune ta tarar da ita a palo khausar tana kan cinyarta xama aunty amarya tayi,mommy ta kalleta tace auntyn yara yana ganki wani sukuku kamar wani abinna damunki,aunty amarya ce tace wlh my son ne y fadi shine yayi tsagewar kashi a kafa,murmushi mommy tayi tace shine duk kika damu haka kin manta shi yanxu solder ne kilama karaje yayi irinnasu na sojoji y gabje kafar,aunty amarya tace ba haka bane,mommy tace toh Allah y sauwake anjima naje na dubashi,aunty amarya ce ta tashi tace dama nasan baxaki damu ba ni natafi duba my son dina kuma dana sani da banxo na fada miki ba ta kama hanya ta fice murmushi mommy tayi tace khausar tashi muje mu dubashi kinga aunty tayi fushi suka tashi. Amir kuwa da yaje y fadawa kaka cikin kidima ta tashi tayo waje ta nufi part dinsu Aslam,Amira ta kalli islam tace yanxu 6ter kin kyauta abinda kikayi masa yanxu gashi kinja masa jinya,tashi Amira tayi ta daga kafada tace so what Ashe ba dadi mu yayi mana ai gwanda yaji a jikinsa kuma ko kifada kice nina saka masa ruwan karkashi ko karki fada ni da kaina xan fada masa ta shige daki,girgixa kai Amira tayi ta fice tabi bayan kaka islam kuwa daki ta shige ta fada gado tana tsalle (nikuwa nace islam ba tausayi 😏). Wannan page dinnaku ne number *35* *&* *36* *Amira* *Aliyu* *&* *Aunty* *Zee* *ngd da nuna kaunar ku akan buk dinnan😊 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (25/10/2016 3:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *37* Dukkansu sunyi jugum2,Aslam kuwa baccinsa yakeyi cikin kwanciyar hankali,mommy ce ta kalli aunty amarya tace auntyn yara tunda bacci yakeyi ni bari natafi Allah y kara sauki,anjima inya farka nadawo na duba jikinnasa,ameen aunty amarya kawai tace ko kallan mommy batayi ba saboda fushi takeyi da mommy bata nuna kulawa akan my son dinta wai kunyar dan fari😏. Aunty amarya ma tashi tayi tace bari naje nayi masa pepper soup kafin y farka nasan xaifi jin dadinsa ta futa,kaka ta kalli Amir tace wai garin yaya hakan ta farune,Amir yace nidai yacemin y futo xai tafi masallaci yayi sufa y fadi a bakin kofa kaka tace ikon Allah to ko ruwa aka xubar a gurin,Amir yace a'ah kawai tsautsayine. Aslam kuwa bai farka ba sai 5:00 o'clock da salati ya tashi sannan yayi addu'ar tashi a bacci y bude idonsa karasowa sukayi dukkansu sunayi masa sannu da jiki,yace da sauki yatsina fuska yayi aunty amarya tace ya akayi,yace wlh jikina ke ciwo tace ai dole sannu yace yauwa. Bowl Amir y dauko da brush da ruwa a buta Aslam y wanke bakinshi saboda baxai iya tashi ba shiwo a idon sahu sai anyi taka tsan2 dashi bayan y wanke bakinshi aunty amarya ta hada masa tea mai kauri da pepper soup din kayan ciki da yasha kayan kanshi da tafarnuwa sai kamshi yakeyi,bayan y gamaci y daura alwala y tada sallah danko axahar baiyi ba. Su kaka kuwa da sukaga jikinnasa da sauki sai suka tashi suka futa,side dinsu suka wuce daki Amira ta wuce ganin bata ga islam a palo ba,kwance ta ganota tayi dai2 akan gado tanata sharar baccinta,Amira ce tayi tsaki ta matsa gaban gadon ta daidaici cinyar islam ta daka mata duka firgigit islam ta mike tana mitsitstika ido ganin wanda taimata wannan danyan aikin shiya ta dakawa Amira wata muguwar harara cikin hayayyakowa ta fara mata masifa wannan wanne irin wulakancine xaki tasheni ina cikin baccina mai daki,Amira ma harararta tayi tace natasa din ai dole kiyi bacci tunda kin aikata mugun kudirinki kin tashi hankalin kowa shine ke harkin samu damar bacci tayi tsaki ta shige bandaki. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (25/10/2016 3:30pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *38* Tsaki islam tayi tayi sabon juyi ganin Amira ta futo ta shimfida sallaya shiya sa tagane anyi la'asar itama ta shiga bathroom din ta dauro alwala ta futo ta tada sallah. Yau kwanan Aslam 2 a kwance in xai shiga toilet sai y daddafa haidar da Amir,amma islam koda wasa bata taba xuwa dubashi ba,haka Amira ma ta daina kulata da islam tanayi mata magana taga Amira din tana shareta shine ta futa harkarta. Su islam ne suketa shiri yau xasu tafi gwarxo hutu itada kaka,Amira harda khausar xasu tafi da sauri islam ta tafi side dinsu Aslam saboda yau ta gudiri niyyar fadawa Aslam itace tasa masa karkashi y taka y subale yaji ciwo,kamar gaske ta shiga dakinnasa a kwance ta ganshi kuma shi kadai wani farin ciki taji y ratsata karasawa tayi ta xauna kusa a kujera daya ta dora kafarta daya kan daya tana wani yatsina fuska. Kallanta yayi y hade rai kamar yaga wani abokin gaba yace ubanme kikaxo yimin a daki yau kwana 2 dajin ciwona bakixo dubani ba sai yau dan munafirci,wani murmushi tayi da ita tasan ma'anarsa ta tashi tsaye tace calm down dan gurgu a xabure y kalleta y maimaita dan gurgu,kashe ido daya tayi tace yes 😉,yanxu ma ba sannu naxoyi maka ba xuwa nayi na fada maka wata magana mai matukar muhimmaci kaga ciwonnan na kafarka ta nuna kanta tace nicenan silarshi saboda nina saka maka ruwan karkashi ka taga ka subale tayi wata dariya tace a gabana komai y faru,ta tsareshi da idanunta irinna masu jin bacci tace kasan dalilin dayasa,sororo y tsaya kallanta tace dalilin shine ka sakamu kamun kunne alhalin bamuyi maka komai ba shiyasa nadan gwada maka nima kadan daga cikin irin axabobin dana tanadarwa mugu irinka ta wani kalleshi shekeke tayi tsaki ta tofar da yawu ta fice,tana shirin fita amir y shigo yace kefa suke jira tace toh dama yaya naxo naduba ta juya tace yaya muntafi saimun dawo. Shikuwa Aslam mamaki yake a ranshi yana lallai ko wacce mace da makircinta aka haifeta tuni idonshi yayi ja jijiyoyin kanshi duk suka tashi gashin jikinshi y miki ya fara tattauna lebensa,(nikuwa nace ran maxa y baci bari nagudu karnaje allurarsa ce ta motsa y gwabgwabjeni nafice a 360 🏃🏼). Islam kuwa tana xuwa tashiga mota kaka ta kalleta tace munafircin banxa dakin damu da Aslam din tunda yaji ciwon bakije kin dubashi ba sai yau xumbura baki islam tayi tace toh laifine lokacin baba mai gadi y wangale musu gate suka fice. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:01 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (27/10/2016 1:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *39* Aslam kuwa ranshine yake xafi yace lallaima yarinyar nan wlh yau bada ban ina xaune ba da inna fara babballaki sai kinyi dana sanin abinda kika aikatamin duk a ranshi yayi wannan maganar. Wata kara ya saki yahau yayyamutsa gashin kansa da sauri Amir y ajiye laptop din kan cinyarsa y matsa kusa dashi yana menene Aslam meyake damunka,banxa Aslam yayi masa idanuwansa sunyi jajahur saboda tsabar bacin rai duk da Amir baisan abinda y batawa dan'uwannasa rai ba haka y dinga lallashinsa yana fada masa maganganu masu dadi yace kadinga fadar *innalillahi* *wa* *inna* *ilaihirraji'un* insha allahu duk wata damuwar da kake ciki xata yaye,a hankali y fara fada sai yaji xuciyarsa tanayi masa sanyi haryaji kashi 70% daga cikin 100% na damuwarsa y ragu a hankali y koma y sulale y kwanta akan pillow bacci yakeson yi amma sam y kasayi. Su islam sun isa gwarxo cikin farin ciki da ko xama basuyi ba ta kwashi su khausar suxo suje gidansu hanne kallan garin takeyi saboda yan canje2 da aka samu. Da sallamarsu suka shiga gdan hanne ce xaune mahaifiyarta tanayi mata magana akan taje ta debo mata ruwa a rafi amma idan ta kwaso wani uban tsalle ta dire sai tace yasin baxata ba,kara uwarta dauko xata buga mata tasaka ihu kenan xata futa tajiyo sallamar kawarta wadda baxata taba mantawa da muryarta ba da gudu ta tafi ta rungume islam suka hau ihun murna. Su Amira ne suka karasa suka gaida mmn hanne,ta amsa cikin farin ciki,hanne kuwa dakyar ta saki islam suka karasa itama ta gaida innar (inna kuwa farin ciki takeyi tana ganin kamar islam ta shiryu a ranta tana nima Allah ka shiryamin tawa diyar) innar hanne tace baxakixo kije ki dibomin ruwan ba na daura sanwa da sauri hanne taje ta dauki tulun saboda farin cikin tagasu islam,islam ta kalli su Amira tace kuxo muje rafi sukace toh suka tashi suka futa innar hanne tana maimakon ku tsayata ta dawo aiko saurararta basuyi ba suka fice. A kofar gda sukayi kicibis dasu yusufa akace musu su islam sunxo shine suka biyota tare suka rankaya suka tafi rafin. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:02 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (27/10/2016 1:30pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *40* Sai da suka share awa 2 churr a rafi sannan suka kawowa inna ruwanta a lokacin inna harta gaji ta aika almajiri y debo mata,lokacin inna tana daki hanne ta kwala mata kira tace inna ga ruwannan suka koma da gudu. Islam ce tace kuxo muje gonar malam tanimu hanne tace kai aini rabona da gonarsa tun lokacin da mai gari yayi mana iyaka da ita murmushi islam tayi tace yanxu ma ba sato masa xamuyi ba da kanshi xai bamu,hanne ta kama haba tace malam tanimun tab Ashe kin mance matsiyaciyar rowarsa a haka har suka karasa. Da sallama su islam suka karasa kaban malam tanimu suka gaisheshi a daddakile y amsa saboda tsaf y ganesu,islam ce tayi gyaran murya tace dama babana ne y bani kaya da yawa yace innaxo nan kauye na rabar to saina ga kai kadai y dace nabawa saboda irin barnan da mukayi maka shine danakai kayan gidanka akace kana lambunka shine naxo na gaisheka kuma nafada maka. Tuni malam tanimu y washe jajayen hakoransa yace nagode sosai yar albarka kamar kuwa kinsan bikine dani gobe ainasan duk kauyennan ba wanda xai kaini hadewa saboda kayan yan birni daban suke dana yan kauye murmushi islam tayi tace toni natafi da sauri yace tsaya2 y koma cikin lambunsa y ciwo mata katuwar leda dasu mangwaro kashu goba kai harda fasa dabur sannan y ciro dari 2 y bata yace ki gaida kakar taki sainaxo godiya toh islam tace tayi godiya ta tafi dakyar take daga ledar saboda yawan kayan. Can gurinda su hanne suka buya ta karasa da mamaki suke kallanta,dariya tayi tace kun kasa magana sai kallo to ku tsaya kuji ta yadda y bani kayannan anan ta labarta musu yadda sukayi da tanimu,dariya su hanne suka kwashe da ita su kace lallai malam tanimu garane da har xaki iyayi mai wayo,islam tace kunga har 200 y bani kuxo muje muci kifin sale mai kifi suka tafi yusufa y dauki ledar,su Amira kuwa duk mamaki y ishesu da abinda islam tayi. Bayan sun sayi kifin sunci islam tabawa su hanne komai bibbiyu ba yadda suka iya haka suka karba dan sunsan bala'in Islam. Suna xuwa gda kaka tahau fada akan sun tafi yawo islam ta xumbura baki tace to waike kakannan mutum baxaije yaga gariba,kaka tace saiku karata ai ganinsu da katuwar leda cike da fruit shiya bawa kaka mamaki tace yanxu islam daga xuwanmu har xaki fara debo mana magana,islam tace kai kuji kakannan batasan y akayi ba amma xata faramin sharri,kaka tace uwar sharri da uban sharri xan miki nidai nasan ko karan haukane y ciji tanimu baxai baki kayannan ba,islam tace toh kuma sai aka samu akasi tunaninki baiyi daidaiba shiya bani,sallamar tanimu suka jiyo a kofa kaka ta dauki mayafi sukuwa suka bushe da dariya. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:02 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (31/10/2016 1:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *41* Kaka tayi tsaki tace ku kuka sani ta fice malam tanimu ta gani a xauren yana ganinta cikin girmamawa y durkusa yana hajiya brk da yamma bakinnan nashi a washe tamkar gonar auduga,cikin mamaki kaka tare brkn mudai,yace dftn kin wuni lfy,tace lfy qlau,yace y kuka baro su alhjn dftn kunxo lfy,cikin xakuwa kaka tace lfy dan duk ta damu taji dalilin daya saka tanimu yake jero mata gaisuwarnan,yadanyi gyaran murya yace dama ina xaune bakin gdan gonata ne islam tace ta sameni ta fadamin abin arxiki shine nace toh baxanyi kasa a gwiwa ba sai naxo nayi godiya,kaka ta kalli tanimu tace wai wanne abune y faru,ya danyi murmushi yace kaya da mahaifinta y bata ta kawowa yan kauye aini ta kaiwa,dariya ce taso kufcewa kaka tace toh ikon Allah gaskiya ni bansan da wannan xancen ba amma kaje gdan ka gani,malam tanimu y tashi jiki duk a sanyaye yace ikon Allah to sai anjima. Kaka tun daga xaure tafara babaka dariya tashiga gda ta kalli islam tace lallai islam takadirancinki gaba yakeyi yanxu kuma da sabon salon da kika dawo dashi garinnan kenan,dariya islam tayi tace hehheheyy ai maganin marowaci nayi danaje nace masa Allah annabi baxai bani ba kuma kinga ban haura katanga na tsinko ba balle yaje gurin mai gari yace nayi masa sata,tadan wani kashe ido ta karkace baki tace to saina canja salon naje nayi masa dabara na ninkeshi baibai yanxu kinga da kunya yaje y fadawa mai gari wannan maganar dariya su khausar suka tuntsire dashi sukace sai islam din kaka itama islam ta tuntsire da dariya tace ku fada ku kara kaka ta dauki buta danyin alwalar la'asar tace ja'iran kaya xakuyi bayani duk randa kuka hadu da tanimu a hanya. Malam tanimu kuwa tafe yake a hanya yana surutu yana yanxu ni yarinyar nan xata yaudara lallai kuwa in hakane ta cuceni,ko sallama babu y shiga gdan nasa yana wulli da kwanuka yana lamunde!lamunde!!,wata siririyar bakar mata ce ta futo a daki tana soshe2 tace haba tanimu irin wannan kira kamar xaka fasa gdan,hararanta yayi yace eh inna ma fasa gdan da kudin uban wani acikin ginin gdan wani tsalle tayi tace kaga tanimu karka sake ka xageni ehe,tsaki yayi yace ni banason shashanci islam bata kawomin kaya ba,kallanshi tayi wani sororo tace wacce islam,yace islam yar gdan kaka mana,lamunde tace au dama taxo ne da mamaki tanimu yake kallan lamunde yace kina nufin bata kawo sako gidannan ba,cikin sanyi da murya lamunde tace nifa malam ka sakani a duhu ko tsiren gurin lauwali mahauci kasiyo ka bata ta kawomin yanxu natafi gdansu na anso,tsaki tanimu tayi yace kefa kin fiya shirme anan y labartawa lamunde yadda sukayi da islam,wata guda ta saki ayyuririii ta bugi cinya tace Allah y kara kai amma nayi farin ciki Allah y shiwa islam albarka ta tsikaro baki gaba tace nan da xaka fita sai da nace ka bani 200 kaki ai gashinan yanxu ka bayar a banxa tayi tsaki ta shige daki shima tsaki yayi ya xari buta domin yin alwala. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:02 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (31/10/2016 2:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *42* Anayi sallar isha'i su islam suka shirya suka tafi dandali acan suka hadu da hanne,kallan kallo akeyi tsakanin su islam da yan matan kauyen saboda yadda su islam suka dauke hankalin samarin gurin kowa burinsa y samu matsuguni a xuciyar su islam,su islam kuwa sai daukar kai akeyi basu yarda ba yan mata sai yatsina fuska sukeyi samarin gurin kuwa sai kai kawo sukeyi guri su islam suka samu suka xauna hanne ce tace kuxo mu shiga rawa islam ta wani yatsina fuska tace god forbid ni nayi rawa a kurinnan cikin wadannan kucakan (nikuwa nace kamar da batayi ba 😏) habule ne dan gdan mai gari yanaho yanata washe jajayen hakoransa yana gabxar rake yaxo yana ah islam dita yaushe kikaxo,wani kallon up & down tayi masa ta watsar a dakile tace daxu naxo yace auho y samu kusa da ita y xauna yace ai ban saniba dana kawo miki xabi,murmushi islam tayi tace Allah sarki xuba yaketa yiwa islam ita kuma tana dauke kai su khausar kuwa sai dariya sukeyi a ciki2 wai wannan garujen ne yakeson islam tab way aga dan dugaji 😂,hansai ce ta hangosu dama yanxu da ita akayiwa habule baiko a kufule ta taho baxar2 (nikuwa nace wayaga budurwar kauye 🙊) taxo ta tsaya kerere tace habule wannan wanne irin wulakancine hine xaka wulakantani akan wada nan nunar ranar tayi tsaki ta murguda baki,cikin xafin rai habule y mike yace ke hansai ina wasa dakene da xaki kawomin raini,dama islam tun xamanta a kauye ta tsani hansai saboda basa ga maciji,wani murmushi tayi na gefen baki a ranta tace inaga kin manta dako wace islam din kaka,wani sanyaya murya islam tayi tace haba habulena y xaka dunga biyewa karya tana haushi ai saiku xama daya,wata dariya habule y kyalkyale da ita yace kumafa hakane y koma y xauna. Hansai ce ta xabura ta daka tsalle ta dire tace kan ubancan wace karyar aikuwa yanxu xan nuna miki ni karya ce tayo kan islam da sauri habule y tareta yana kina kuwa da hankali hansai,tace bani dashi kyaleni nafara kwada mata haukar tawa hannu y daga y kwakwkwadawa hansai mari aikuwa dandali akadauki ihu da shewa bakin ciki kuwa y gama turnike hansai kawarta tabawa ta kama hannunta suka tafi gda hansai na ihu tana baxata yadda ba,su islam kuwa basu tashi tafiya gda ba sai 10:00pm habule ne y rakasu yanata rawar kai. Haka su islam sukaci gaba da hutunsu wasan buya ta dingayi tsakaninta da malam tanimu yau satinsu 2 yau suke shirye2 komawa gda islam dai jikinta duk yayi sanyi saboda tasan haduwarta da yaya Aslam baxatayi kyau ba. Aslam kwance a daki yanata murmushi danya gama planing din punishment din da xaiyiwa Islam wayarsace ta fara ringing. _*wannan page 41&42 nakune Aysha Marapha & Mmn twice ina ftn xakuyi manage*_😜 _*masoyan goyon kaka kuyi hakuri darashin jin posting din goyon kaka kwana 2 hakan y farune dalilin wani uxuri daya tasomin dftn xakumin hakuri*_ 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:02 PM] ‪+234 703 443 5155‬: (1/11/2016 4:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *43* Aslam kwance a daki yanata murmushi danya gama planing din punishment din da xaiyiwa islam dan wlh y dauki alwashin itama saita dandana axabobinsa masu xauri wayarsa ce ta fara ringing a bed side drower y dauko wayar ganin mai kiransa da sauri y mike,yace sir brk da rana dftn kana lfy,dagacan akayi magana kawai ji nayi Aslam yana cewa sorry sir wlh y fadamin dama so nakeyi a cikin satinnan na taho,aka kuma magana acan,ganin idanun Aslam nayi sunyi jajawur yace dan Allah kayi hakuri ayau insha Allah xan taho kittt aka kashe wayar,wata iska Aslam y furxar a bakinsa mai xafi y cilla wayar tashi kan gado y wani naushi bango(da sauri na matsa ina xaxxare idanu 😳)tsaki Aslam yayi yace a takurawa mutum an bashi 4 week amma dududu 3 week yayi ace ana wani nemanshi cikin gaggawa,tsaki yayi yace gaskiya sir ka batamin budget dina naso 1 week dinnan da xanyi Ace nayi dealing din islam har saitayi sanyi kayanshi y fara hadawa acikin trolley bag y xari key din mota y futa danyaje y yanki ticket da xai kaishi photercourt a yau. Su islam kuwa isya driver yaje daukarsu bayan an gama sassaka kayansu a mota suka shiga,islam ce tace wai isya sojan gidanmu bai koma ba,isya yace eh ko yanxu da xan taho naganshi,islam tace wayyoni su khausar ne suka bushe da dariya sukace da kinajin tsoron kika aikata laifi,islam tace baxaku gane ba kunsan shi mugune to yanxu bansan mai xanje natarar y shiryamin ba,kaka tace toh wai mai kikaiwa Aslam dinne kike tsoron haduwa dashi,islam ce tayi kasa da murya tace kaka kinsan halinsa ko banyi masa komai ba mugunta yakemin,kaka tace kwantar da hankalinki naga inya isa in mun koma yace xai tabaki y gani inxan kyaleshi,dariya islam tayi tace yauwa kaka ta shiyasa nake sonki. Ticket din da Aslam y samu 4:00pm xai tashi lokacin kuma kusan 2:30pm yana dawowa daga airport direct kasuwa y tafi acan yayiwa daddy da Abba sallama,sunyi masa fatan alkhairi da addu'ar samun nasara akan taimakon gaggawa da xasu kai somalia dan kwantar da wata tarxoma amir ma yanacan saboda yanason kasuwanci sannan y wuce gda side din mommy yaje itama yayi mata sallama itama tayi masa fatan alkhairi da addu'a sannan y futa y tafi side din aunty amarya. Itama y fada masa cikin jinjinawa da karfafa masa gwiwa tace yauwa my son kaga wannan ne farkon aiki da xaka fara futa insha Allah xakuje lfy ku dawo lfy,kuma xakuyi nasara da yardar Allah ai ina alfahari dakai my son murmushi yayi y daura kansa a cinyarta yace ngd aunty na,ta shafa kanshi tace nidai inaso ka xama mai tsantseni akan addininka ka rike sallah sannan duk wani Abu da xai nisanta ka da lahirarka ka gusheshi,tashi yayi yai hugging din aunty amarya yace insha Allah shiyasa nake alfahari daku a matsayin iyayena ngd Allah y saka muku da alkhairi y baku tsahon rai mai amfani,murmushi aunty amarya tayi tace ameen. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:30 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (1/11/2016 4:30pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *44* Tashi yayi yace aunty na bari naje nayi wanka kinsan 3:30pm xan futa a gdannan tace to y futa,side dinsu y shiga da sauri y cire kayansa y fada bathroom cikin 15 minute y futo shaf2 y shafa mai y taje sumarsa y mulketa da man gashi tuni tadauki kyalli y dada gyarata da comb ya kwantar da sajensa y fesa body spray dauko wata black din riga tadan matseshi mai gajeren hannu y saka anyi rubutu a gaban rigar da farin fenti white trouser pensil y saka y saka wani boob fari agogon gucci y daura a hannunsa fari,turaren fugg y feshe jikinsa dashi hade da tormford tuni y dauki wani fitinannen kanshi y ratayo jakarshi a kafada y futo yana tafiya irinta xaratan maxa yana wani bada fadi y futa side din nasu,side din aunty amarya y koma cake da dambun nama ta baki pick yayi mata a goshi yace tnx my lovely aunty sannan suka futo gaba daya suka shiga side din mommy. Lokacin daya futo yayi daidai da shigowar isya driver wani kululu cikin islam y bada sauti yana karasowa da sauri Aslam y karasa y tsaya a gaban motar kaka ta futo su Amira suka futo amma Islam takasa futowa,hugging din kaka yayi yace my granny yau xan koma saboda an kirani zamu tafi somalia dan kwantar da wata tarxoma kaka tace toh Allah y tsare y kiyaye ya kuma bada sa'a mai gdan,saita fara kuka da sauri Aslam y rungumota yace haba kaka ai saiki sacemin gwiwa habar xani tasa ta goge kwallar fuskarta tace insha Allah zakayi nassara kawai su aunty amaryama suka fara kukan dakyar y lallashesu sukayi shiru,ammafa banda islam da taketa raba idanuwa a mota. Islam a ranta tace gashinan dai mutum da kyau 100% amma sai cin xali da mugunta y iya ta karashe maganar da murguda haki,(nikuwa nace wayaga harara a duhu baisan kinayi ba)aunty amarya ce tace islam ke baxaki futo va kuyi sallama futowa tayi a motar tana xumbura baki tana kunguni,tace Allah y kiyaye y tsare y bada sa'a,wani dadi yaji a ranshi y sakar mata wani sansanyan murmushi yace ameen,islam kuwa mutuwar tsaye tayi tace a ranta kan ubancan dama yaya Aslam y iya murmushinnan tashin mota taji itace ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi. 💘💘💘 *mrs* *hamisu* *taura* 💘💘💘 [11/12, 9:30 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (4/11/2016 5:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *45* Firgigit ta dawo daga tunaninta tace kai dama haka yaya yake dakyau (nikuwa nace da sai yau kika sani 🙄) dinfil (beutifull point) dinta ta taba tace Ashe harda irin abuna yake dashi saikuma tayi wani farr da ido tace to ta yaya ma xan san kyawunsa mutum kullum fuska a turbune tamkar wanda akayi masa alkawar da tashin kiyama,kallan gabas da yamma tayi taga ita kadaice a waje da sauri ta arci na kare sai part din kaka,tana shiga ta tire akan cinyar kaka,kaka tace wash xaki ballani fa,xumbura bari islam tayi tace kiji kakannan to dududu nawa nake,aunty amarya ce tace a'ah ina laifin kice yanxu aka haifeki,dariya islam tayi tace Allah aunty amarya inajin da xamuje a aunani da jaririn da aka haifa yau to kila y fini nauyi ta karashe maganar da washe baki,aunty amarya tace ashema kasa kikeci,mommy tace rabuda aunty yar gatan kaka waya isa y shiga tsakaninki da kaka,islam tayi farr da ido tace wlh yaji kunya duka aunty amarya ta kaimata ta goce,kaka tace Allah xamu bata fateema aunty amarya tace haba kaka islam ce kullum sangartar tata gaba takeyi sam2 batasan ta girma ba,khausar ta tashi tace ni bari naje gda islam tace muje narakaki Amira tace ni wanka xan shiga saikin dawo suka fice,suna xuwa daidai gate din su khausar tace to iyanan xan tsaya baxan shiga ba ki gaida mammy kan khausar tayi magana har islam ta juya ta arta ana kare (nikuwa nace ayi mutum baya gajiya da gudu saikace dan barewa😏 ). Aslam kuwa yana xuwa lokacin an fara kiran passenger yaje akayi sicreaning dinshi y wuce yahau fight 4:00pm dai2 flight dinsu y daga sai photercort. Yana sauka a jirgi ya futa da safwan y gani yaxo daukarshi,y shiga mota tun a hanya safwan y fara mita tamkar y ari baki,akan tun yaushe yake kiranshi a waya gashi yanxu har Saura 2 days suyi tafiya xuwa somalia banxa Aslam yayi masa y kwantar da kanshi a seat din mota y lumshe idanunsa kawai tunano karamin bakin islam yakeyi lokacin da takeyi masa addu'a wani sanyi yaji acikin ranshi baisan lokacin daya saki murmushi ba,safwan kuwa jin yanata babatu ba'a bashi amsaba shine y kular dashi juyar da kanshi yayi gurin Aslam dan lokacin harsun karasa gda ganin Aslam na murmushi yace lallai ma guy dinnan watako ninake shirmena baima san abinda nake cewa ba,cinyarshi y daidaita y daka masa duka firgigit Aslam y dawo daga duniyar tunaninsa yana islam. Dariya safwan y tuntsire dashi yace ai dama tunda naga tunaninnan naka yayi nisa nasan tunanin your lovely jerry dinka kakeyi da alama wannan karan ma tayi abinda ta saba dan kyankyasamin naji y kamo hannun safwan,kwace hannunsa Aslam yayi yace dallah malam sakeni baxan fadaba sainaji mata y bude gambun motar y fice. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamsu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:30 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (4/11/2016 5:30pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *46* Da sauri safwan ma y futo y rufe motar yabi bayan Aslam side din safwan suka shiga pallo ne sai kayan kallo sai kujeru brown & milk sai center carpet da center table sai bedroom kuma bedroom din Aslam y wuce jakarshi y ajiye y dauro alwala y futo y shimfida sallaya sai da yayi nafila raka'a biyu sannan yayi sallar la'asar safwan kuwa dayake y riga yayi kawai kwanciya yayi akan gado,sai da Aslam ya idar da sallarsa yayi axkar kamar yadda yaxo a sunna y dade yana kwararo addu'a sannan y shafa y kalli safwan yace tashi mu tafi gurin canal kasan daxu y kirani nace masa yau xan shigo,safwan yace gaskiya kam gwanda muje kaima a jikaka da naira dan yanzu accaunt dina taff yake,Aslam yace kai haba maxa tashi mu tafi da sanyin safiya ake kamun fara,dariya safwan yayi yace dan wadannan farin babe ne dan 1 million ake sakawa duk wanda aka xaba a tafiyar da sauri suka futa sai da suka biya suka gaida aunty (mmr safwan)ta tambayi mutanen gda yace duk lfy suna gaisheku tace tom ina amsawa sannan suka futa. Sai da suka nemi permission sannan suka shiga office din canal yunusa safana kamar yadda nagani a karamin allo an sakala a kofar kafin ka shiga,suna shiga suka sara masa suka kame time din yana duba yadda akayi ta'asa a somalia a laptop dinshi y dago kyakykyawan dan fulanine yana da siririn bille a kumatunshi,yadan manyanta xai kai 55 year y nuna musu kujera yace have a seat dada kamewa sukayi suka sara masa sannan sukace tnx sir suka xauna. Kallan Aslam yayi yace haba umar y kake wasa da damarka,kasan yawan sojojin da sukeso a turasu aikinnan saboda in harkun yi nasara a aikinnan bakaramin girma xa'a kara muku ba,sunkuyar da kai Aslam yayi yace sorry sir wlh gocewar kashi nayi to lokacin da safwan y fadamin ina kwance shiyasa banxo ba,murmushi canal yayi yace haba Aslam karka bawa sojoji kunya mana common gojewar kashi ta kwantar dakai to ina wadanda afilin yaki xasu karye amma saboda tsabar tashin hankalin da suke ciki basa sanin sun karye karka bani kunya mana ina maka kallon jarumi shiyasa na xabeka dan ku sani in kunyi bajinta to tamkar ni kuka kare,suka hada baki sukace insha Allah baxamu baka kunya ba,yace to Allah y tai aka xaku iya tafiya sukace ameen suka mike,yace kaje ka bawa cashier accaunt number dinka xakaji alert insha Allah yau,yace OK sir tnx suka ficw direct cashier office suka wuce y bada accaunt number dinsa sannan suka koma gda. Suna xuwa gda safwan yace eyya dan'uwa Ashe gocewar kashi kayi,yace eh safwan yace garin yaya,Aslam yayi tsaki yace inna fada makama dariya xakamin cikin yanayi na tausayawa safwan yace y xa'ayi nayi maka dariya,anan Aslam y lbrtwa safwan abinda y faru tun ranar daya koma har ranar da islam ta fada masa itace ta xuba masa karkashi,da kuma xaman da yayi najira ta dawo yayi mata hukunci sai kuma canal y kirashi,dariya safwan yake babakawa sosai harda faduwa banda kwalla data taru a idonsa yace kai amma yarinyarnan ta birgeni wlh kajifa sunan data saka maka wai dan gurgu😂,Aslam yace to dallah menene na dariya kuma ciki safwan y kama yace saboda kasan xanyi dariya shiyasa kaki bani lbrn da farko ai tsaki Aslam yayi y bude fridge y dauko faro y balle murfin y kafa a baki ko takan cup baibi ba saboda yadda xuciyarsa take tafarfasa ji yakeyi tamkar yanxu islam ta xuba masa karkashi. *Aslm plz kuyi hakuri da rashin posting din _goyon kaka_ kwana 2 hakan y farune sanadiyyar xaxxabi danayi ina* *bukatar* *addu'arku* *yan'uwa* Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:30 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (6/11/2016 3:00pm) *na* *umma* *yahya* *musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON* *KAKA* *47* Kamar yadda canal yace cikin dare around 9 o'clock Aslam yaji alert dadi y isheshi,sai a lokacin yayiwa safwan magana yace friend kaga nima kudin y shigomin cikin jin dadi safwan y miki,saboda kawai daurewa yakeyi bayason ko kadan Aslam yayi masa fushi danshi akwai san raha,safwan yace to kaxo muje shopping ko akwai abinda kakeso,Aslam yace a'ah ba abinda nakeso nasiyo komai safwan yace shikenan daganan sukaci gaba da hirar yadda tafiyar tasu xata kasance. Kamar yadda akace yaune ranar tafiyar su Aslam kowanne soja sanye yake da unifoam fuskarnan a daure tamkar a filin yakin suke(nidai da nake a gefe tuni cikina y bada kuuu my Afma kuwa data rakani dauko rahoto tuni ta fara xawo a wando saboda ganin wani soja y saitata da bindiga 😂😂) sai da suka dadayin training sannan aka bawa kowanne soja wata jaka tamkar skul bag amma tafi skul bag girma in da xasu xuxxuba kayan da xasu bukata kowanne da bindiga a gurinshi a hankali kowa yaje yahau motoci xasu wuce airport suhau flight xuwa somalia. Su islam anata shirye2 xasu shiga j.s 1 yau iyayi ake tayi an fara xama yan mata dayake a primary skul din da suka gama acikinta xasuyi secondary unifoam ne kawai na secondary section white shirt ce mai dogon hannu da skirt maroon sai hijab fari mai hula sunyi kyau sannan suka futo isya y daukesu a mota sai makaranta. Jere suke a assembly akayiwa dalibai barka da dawowa makaranta dftn sun daura damarar karatu akayi bayanai kowa y wuce class j.s 1A nanne ajinsu islam,again uncle hasheem shine foam master dinsu dadine y ishesu saboda yadda ya iya tallerating students. Su Aslam suna sauka a somalia,ana saukesu a airport akaxo da manyan motoci aka debesu sai head quater aka babbasu masauki sukayi wanka musulmi sukayi sallah,sannan sukaci abinci,anan shugaban yasa aka kirawo su yayi musu brk da xuwa sannan y fara musu bayanin irin gurin da xasuje da haxarin da yake gurin,da irin ta'asar da yan kunar bakin waken sukeyi,yayi musu fatan samun nasara aka basu taswira ta gurin aka dada hadasu da wasu sojojin na garin duk da akwai wadansu acan jejin,su Aslam tunda suka futa kallan garin suka fara saboda yadda duk yan tada xaune tsaye suka bata garin,wasu gurin an rurrushe gininnika an kokkona,a haka har suka karasa dajin da sauran sojoji yan'uwansu suke suma duk an kakkashe wadansu ga gawarwakinan birjik na sojoji dana yan kunar bakin waken,suka ajiye jakunkunansu suka fara buga runfuna,suka shishshiga ciki musulmi sukayi alwala sukayi sallah. Misalin 4:00pm sukaji harbe2 da tashin bomabomai nan suka fara shiri suka futa,kurar yan tada kayar bayan suka gano har suka karaso daf dasu nanfa aka fara dauki ba dadi akayita misayar alburushai su sunaso su shigo cikin gari su sojoji kuma sun hana,haka akayita bala'i su Aslam sunga tashin hankalin da basu taba gani ba dan irin wannan yakin sai a film suke gani haka suka kwana ana abu daya sai daf da asuba suka tabbatar da yan kunar bakin wakennan sun koma,dan cikin dare sai sunyi tunanin sun tafi saisu dawo,in lokacin sallah yayi kuwa sai dai musulmi 10 da keister 5 masu gadinsu da haka sukeyin sallah. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:30 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (6/112016 4:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *48* Sai lokacin su Aslam sukayi sallar asuba sannan suka shishshiga rumfunansu,wadanda sukaji ciwuka akayi musu treatment dinshi Allah y taimaki Aslam da safwan dai basuda rauni ko daya sai gajiya abinci sukaci sai pracitamol suka kwanta,sai axahar sannan mafi yawansu suka tashi wasu rumfunane dai sukayi bathroom dashi nan wasu suka shiga suka watsa ruwa dan sai suyi sati basuyi wanka ba. Su islam ana tashi aka kamo hanya anata wani yauki (nikuwa nace kaga berayen j.s masu gigi 😂),islam ana shiga aka fara fatali da kayan makarantar sai da akayiwa komai daidai pant dinta kawai ta bari sai best haidar ne a lokacin a dakin kaka shiya fatatakata daki ta dauko xanin kaka danshima ba sauki haka tafuto tanata xumbura baki. Bangaren su Aslam kuwa abin ba sauki dan yan ta'addan yau sunfi na jiya haka akayita artabu yauma basu samu hutawa ba sai da akayi asuba. Su Aslam har sunyi 3 month acan kwata2 agida ko an kirasu ba'a samunsu saboda jejin da suke babu sabis sannan uwa uba tashin hankalin da suke ciki baxai iya barinsu su futa suyi wayaba,saboda yanxu ko bacci ma basa samun damaryi saboda yadda yan ta'addan sukaga anayi musu ta'adin mutane sosai to koda yaushe cikin kawo farmaki suke ko sallah sai dai su hada axahar da la'asar magruba da isha'i asuba kuwa sai gari yayi rana,dukkansu kuwa sunyi wani irin mugun rama uwa uba wani mugun baki da sukayi dan rabonsu da watsa ruwan ma da sukeyi harsun manta. Aunty amarya ce take xaune kuwa takeyi wiwi harda majina,tana haba Abbn amir y xakace baxan tashi hankalina ba kafa gani yau my son watanshi 3 da tafiya amma bamu tabayin wayaba koda yaushe nakira wayarsa a kashe take haka ta safwan din to in banyi kuka ba y kakeso nayi in my son y rasune y kamata ku fada mana ta dada rushewa da kuka,cikin sanyin murya danshima dakewa kawai yakeyi yace haba fateema waya fada miki Aslam y rasu yanayin inda suke aikine haka,sannan kuma gurin da suke ba service cigaba tayi da kukanta,haka y tashi y tafi part din yayansa anan y xayyane musu abinda ke faruwa Fateema duk ta tashi hankalinta,mommy ce tayi murmushi duk da itama dakewa kawai takeyi tace in banda abin auntyn yara ai addu'a itace y kamata tayi musu bata xauna tana kuka ba,kallanta Abba yayi yace nikam nakasa rarrashinta daddy y kalli mommy yace khadeeja jeki kirawo ta mommy tace toh ta futa. Kukan ta tarar aunty amarya tanayi tana ta kiran waya murmushi mommy tayi ta karasa tace daddy yana kiranki,haka aunty amarya tanajan hanci suka fita. Suna xuwa suka samu guri suka xaxxauna anan daddy y kalli aunty amarya yace haba fateema y xaki tashi hankalinki akan abinda hasashe kawai kikeyi yanxu acema Aslam din y mutu haka xaki xauna kina kuka baxakiyi masa addu'a ba,kuma kinsan rikicin Hajiya (kaka)kullum muka shiga gurinta saitayi mana xancen Aslam bai taba kiranta ba kuma in itace ta kirawo shi sai yara suce ance a kashe take,kinsan cemata mukeyi mu munayin waya dashi kila ita lokacin da take kiransa y kashe wayarne saboda aikin da yakeyi akwai wahala,to yanxu intaji irin maganar da kikeyi y xamuyi da ita,shiru aunty amarya tayi tana goge kwalla,daddy yace dan Allah ki daina kuma nakira abokina yace yaje head quarter sunce suna lfy kawai jejin da sukene ba service kici gaba dayi musu addu'a kinji tace toh. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:31 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (7/11/2016 4:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *49* Kamar yadda daddy yayiwa aunty amarya nasiha,haka ta daure tana danne damuwarta duk kuwa data damu,sannan haka ta tsaya tsayin daka ta dage da nafilolin dare akan Allah y bawa su Aslam nasara kuma y karesu daga sharrin duk wani abu daxai cutar dasu. *AFTER 1 MONTH* Yau su Aslam tashin hankalin da suke ciki yafi na kullum,saboda yau harda shugaban yan kunar bakin waken aka futo musayar wuta kawai akeyi a tsakaninsu da tashin bomb ko ina ka kalla a ko kone gawarwaki kuwa tamkar ba yan adam ne a kwance ba bala'in yayi bala'i tashin hankalin yakai,su har mamaki sukeyi inda wadannan mugaye suke samun kayan fada,safwan ne da Aslam a bayan wata bishiya da aka sare a lafe,cikin nuna gajiyawa safwan yace my friend wlh nagaji yau 2 days ana yaki in banda ruwa babu abinda cikinmu y samu ruwan ma bamusha mu koshi ba wlh nagaji anya xamu iya kama wadannan mutanen kuwa Aslam ne y hango wani dan kunar bakin wake y harbo bindiga a daidai saitin kirjin safwan da sauri y hankada safwan yayi kasa shikuma bullet din y shigar masa kafada ohch yace a lokacin y saita kan dan kunar bakin waken y harbeshi a take y fadi y mutu. Daidai lokacin islam ta futo daga kitchen din aunty amarya ta dauko wa aunty amarya ruwa a try y fadi glass cup din y tarwatse dafe kirjinta tayi tace wayyo,aunty amarya tace ke kuma lfyrki islam tace wlh aunty amarya kawai ji nayi gabana y fadi,aunty marya tace toh ba addu'a y kamata kiyi ba,islam tace toh kitchen ta koma ta dauko broom da packer ta tattare glass din ta xuba a dausbing ta dawo jikinta duk yayi sanyi,tana shirin futa aunty amarya ta kirata tace xonan islam,komawa tayi ta xauna a gefen aunty amarya ta sunkuyar da kanta,aunty amarya tayi murmushi a ranta tace Allah ngd maka yarinyata tafata hankali (nikuwa nace anya kuwa)tace islam meyake damunki naga yanayinki kwana 2 duk y canja kin xama so silent,kawai sai islam tahau kuka mamaki aunty amarya ta fara tace daga tambaya sai kuwa,dakyar ta lallasheta tace ki fadamin damuwarki koda addu'a natayaki kinji cikin xumburo baki islam tace toba yaya bane,da mamaki aunty amarya tace wanne yaya dan tasan kaf gdan abokin tsamarta 1 Aslam to kuma yanxu bayanan,islam ta kara xumburo karamin bakinta tace yaya Aslam,aunty amarya tadan xaro idonta tace a'ina kika ganshi,islam tace a haccina kullum saina ganshi yana can a wani daji yana tashan wahala saiyace naxo nikuma naji tsoro saina gudu saiya dinga kwalamin kira yana cemin nadinga yi masa addu'a saina saina farka in duba naga bayanan,to yanxuma nafito a kitchen naji kamar ihunsa,hawayene y xubowa aunty amarya ta goge,tace toh kinayi masa addu'ar,girgixa kai islam tayi,aunty amarya tace toh daga yau duk lokacin da kikayi sallah ki dingayi masa addu'a kina Allah y bawa yayana nasara y kuma dawo dasu lfy kinji,murmushi islam tayi har dimple dinta y loba tace to,aunty amarya itama murmushi tayi tace that gud my girl give me 5 ta mika mata hannu suka tafa islam ta tashi tana dariya tace bari natafi gurin kaka ta tashi tatafi da gudu murmushi aunty amarya tayi itama ta mike ta shiga kitchen ta dauko ruwan dan islam bata daukoba(kalubale ga iyaye y kamata aduk lokacin da kuka fahimci yaranmu suna cikin wani damuwa y kamata ku jawosu ajikinmu muji damuwarsu tanan xamu samu su fadamana abinda ke damunsu,amma ba muga yaranmu a damuwa ba kuma mu kasa magance musu karmu manta amanace Allah y bamu kuma saiya tambayemu). Cikin kidima safwan y dago yace y sameka ganin jini na bulbulowa a kafadar Aslam kuma yanata hada uban gumi shiya sakashi saurin sauko da jakar bayansa y xuge y dauko wata karamar wuka mai dan tsini yayi saurin farke rigar y luma wukar a jikin Aslam,Aslam sai runtse idonsa yakeyi saboda yadda y kaje wani irin xafi yana ratsashi tundaga kwakwalwarshi har xuwa dan yatsanshi,wata kara y saki lokacin da safwan y xaro bullet din sai kuma y lumshe idonsa y jingina da bishiyar yana maida numfashi,daure masa hannun safwan yayi sannan sukaci gaba da yakin danyau abin yayi tsanani (nikuma nace Allah y rabamu da yaki 😰). Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:31 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (7/11/2016 4:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *50* Cikin ikon Allah haka akayi ta artabu inda Allah y taimaki su Aslam yau dai komai yaxo karshe dama rana 99 ce ta barawo rana 1 tamai kaya ayau Allah y nunawa su Aslam karshen wannan tashin hankalin dama masu iya magana suna cewa karshen tuka tuki tuk kuma duk nisan jifa kasa xai dawo yau sun kama bbn yan kunar bakin waken da sauran yaransa 20 dan sauran duk sun kashesu har cikin jejin su Aslam suka shiga aikuwa makamai kala2 wadansu ma su Aslam basu taba ganin irinsu ba,a healcopter aka sassaka ragowar sojajin da sukaji ciwo masu tafiya kuma suka shiga motoci tun kafin na mota su karasa aka turo wadansu jiragen suka tattara gawarwakin akaje aka binnesu dan na nigeria an kira an fada musu akwai nasu mutane 20 da suka mutu sun yadda a binnesu acan. Gwamnatin somalia ba karamin dadi tajiba yadda aka samu nasarar kama wadannan axxalumai tuni aka kaisu magarkama😜 aka garkamesu. Treatment ake basu sosai dan ko mutum ba'a harbeshi ba to baya rasa wani ciwon kamada masu karasa da sauran ciwuwwuka. *2 week latter* Yauce ranar dasu Aslam xasu dawo gda nigeria saboda duk sunji sauki sai dai dan ragowar ciwukan da ba'a rasa ba,inda yayi dai2 da 5 month 2 weeks kenan da tahowarsu,bakaramun kuka sukayi ba ganin babu wadansu acikinsu sun mutu,gwamnatin somalia ta jinjinawa sojojin nigeria tare da godiya sannan tayi alkawarin lokacin karin girmasu xata xiyarci nigeria,bakaramin biliyoyin kudi ta tura nigeria ba da xa'a biya wadannan xaratan sojojin domin sunyi rawar gani,haka aka debesu har airport tare da tawagar shugaban kasar can domin rakiya saida saida sukaga dagawarsu niga sannan suka juya (nikuwa nace wash yau sai kwanan niga 🙄) Bakaramin tarba akayi musu ba a nigeria lokacin da suka sauka haka aka dada dibansu sai headquarter canal yusuf safana yaji dadi,sauran major da general sai jinjina masa sukeyi saboda yadda yaransa sukayi kokari sosai a wannan tafiyar kuma ba karamin alheri da girma suka samowa kasarsu ba,bayan bayanai da girmamawa da akayi musu akace an sallami kowa yaje gda y wuta har tsahon 2 months xuwa lokacin da xa'ayi promoting dinsu sannan kowa xaiji alert dadine y ishesu kowa aka saka drivern office y kaishi gda. Aunty ce xaune a palo ta xurfafa cikin tunaninta dan bata da aiki sai tunanin tilon danta mutane ta gani tsaye a kanta kafafunsu ta fara gani takalman sojoji ta gani da wando da sauri ta dago kanta safwan ta gani amma yayi baki da sauri ta mike ta rungumeshi tana kissing din fuskarsa hawayene y wanke musu fuska duk su 2,Aslam dayake gefe shima idanunsa sun kada sunyi ja,dan yasan yan gdansu sunacan suma sunyi missing dinshi aunty ce ta saki safwan taje tayi hugging din Aslam shima tayi kissing dinshi a goshi,komawa tayi ta xauna suma suka xaxxauna tace my sons munyi missing dinku,muma munyi missing dinku sukace,tace wanne irin guri kukaje wanda bashida service haka,safwan yace wani kungurmin dajine wlh bari muje muyi wanka tukun mudawo kisha lbr,sallama akayi,suka amsa mai gadine y shigo y miko wata envelope Aslam y karba yace yauwa harya dawo,aunty tace menene haka Aslam yace ticket ne aunty nima yau xantafi gda,aunty tace haba my son memakon ka kwana safwan yace nima haka nace masa to yace a'ah wai yasan hankalin yan gda y tashi saboda rabonshi da waya dasu tun kafin mu tafi baxai iya dada kwana ba,aunty tace kuma yayi gaskiya bari nakira dadynka nayi masa albishir safwan cikin shagwaba yace a'ah aunty surprising dinshi xanyi y hade hannunsa yace plz karki buga tayi murmushi tace toh. 4:30pm suka futo Aslam yana sanye da t.shirt purple sai black trouser y ratayo jakarsa sai kanshi yakeyi yace aunty bye sai bayan 2 months kuma,tace toh Allah y kiyaye hanya ka gaishemin da mutan gdan,yace ameen xasuji. A waje sukayi clashing da daddy driver y dawo dashi daga office,cikin mamaki yake mutsitstsika ido yace suwa nake gani kamar maxaje da sauri suka tafi sukayi hugging dinsa,a tsatstsaye daddy suka gaisa da Aslam yaje driver y daukeshi xai kaishi airport,safwan kuma suka koma da daddy. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:31 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (8/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *51* A jirgi Aslam sai murmushi yakeyi,saboda wani farin ciki dayaji maramisaltuwa wanda y kasa sanin dalilin farin ciki(nikuwa nace waya sani ko farin cikin nassarar da suka samu ne nace kai a'ah farin ciki yakeyi yau y dawo gdan cikin hukuncin ubangiji). Islam ce ta sheko da gudu sakamakon chocolate din data kwatowa Amira,itama amiran ta biyota a guje Amira tace wai baxaki tsaya ki bani chocolate dina ba cikin shagwaba tayi maganar tamkar datayi kuka,lokacin islam ta lunkuma chocolate din a baki tace Allah gwnda ki hakura danma na cinye kuma nasan baxaki iya kamani ba,Amira ganin islam wahalar da ita kawai takeyi dan ba iya kamata datayi va yasa cikin kuka ta koma part din kaka,islam kuwa da gudunta batasan Amira ta komaba tayi hanyar gate,lokacin yayi daidai da shigowar Aslam islam ji tayi ta bugi mutum tagal2 ta koma xata fadi,da hanxari y rikota da hannu daya y daidaita tsayuwarta sororo ta tsaya tana kallan wanda y rikota tundaga kafarsa ta fara kallo har xuwa fuskarta kuwww cikinta y bata kara,sakamakon ganin fuskarsa a tamke tamau tamkar bai tabayin dariya ba a duniya,cikin tsawa yace ke wannan wanne irin rashin hankaline gudun ubanme kikeyi,cikin tsoro da rawar jiki islam tace Amira ce ta biyoni,kallon bayanta y fara baiga Amira ba,islam kuma wani bala'in kwarjini yayi mata tuni taji wani mugun tsoronsa y shigeta wanda bata tabajin irinsa ba,saboda yadda taga yaya Aslam din y dada girma,yace ina Amira din waige2 ta fara tana xaxxaro ido irinna marasa gaskiya,a ranta tace wlh dabadan ka rikemin hannu ba da tuni na dade dayin nisa a daki,yace saboda bakida hankali a haka xaki futa dubeki fa,kallan kanta take ready made ce a jikinta iya gwiwa rankwashinta yayi mata,wani xafine y ratsata tamkar ta saki futsari wata gigitacciyar kara ta saki lokacin y cika hannunta yace kama gabanki da sauri ta juya ta kwasa da gudu sai da tayi nisa ta juyo tace kuma Allah y isana ta murguda baki,kafin yayi wani yunkuri ta bace bat tamkar kiftawar ido,murmushi yayi yace Ashe haryanxu tsugune bata kareba karasawa yayi suka gaisa da baba mai gadi da isya sukayi masa y hanya yace alhmdllh y wuce. Da gudu ta fada cinyar kaka tana maida numfashi,kaka tana lfyrki kuwa amma ta kasa magana sai waje da take nunawa da hannunta,kaka tacewa Amira ke ganomin wane y biyota y tsoratata haka tashi Amira tayi ta leka ta dawo tace nifa kaka banga kowa ba,kaka ce ta kalli islam da haryanxu ta kasa magana sai jikinta da yake rawa tace to dagani in baxakiyi magana ba,dakyar islam ta daidaita nutsuwarta tace yayane fa y rankwasheni kaka tace haidar ko narasa meyasa yakeson mushiga kafar wando daya dashine,na hanasa dukanki yaki ji,xumbura baki islam tayi tace bafa shiba yaya Aslam,shekeke kaka ta kalleta tace watako shirmen mafarkin da kikeyi harya fara xama gaske,yaron dayau watanshi 5 da sati 2 da tafiya shi xakice kingani,islam ce tace kiji kakannan to yaushe nakeyin mafarkin yayan,harda xan fada miki magana kice shirme nayi,kaka tayi dariya tace ai in kina mafarkinnasa surutai kikeyi saina tofeki da falaki da nasi tukunna,dariya Amira tayi tace koma waye dai y rankwasheki hakkina ne Allah y fara sakamin duka islam ta kaiwa Amira tace kaka kinga tanamin rashin kunya ko (nikuwa nace kaga manya) daganan suka fara xagaye palon kaka tana saita daki Amira kaka kuwa data gaji da magana daki tayi shigewarta ta barsu islam kuwa ta manta da wani yaya Aslam. Aslam kuwa direct part din aunty amarya y shiga lokacin ta futo a kitchen kawai taga mutum y shigo mamakine karara a fuskarta tahau mutsitstsika ido tace wanake gani haka,murmushi yayiy tafi da sassarfa y rungumeta ya saki wata sassanyar ajiyar xuciya yace dankine Aslam aunty na,danja baya tayi ta kare masa kallo sai wasu siraran hawaye suka xubo mata,da sauri yakai hannu y goge mata hawayen yace meya sakaki hawaye aunty na,tace my son gani dukkayi baki ka rame dada rungumeta yayi yace aunty na duk cikin aikine. Hannunshi taja xuwa dinning table ta kalli taslem tace jeki fadawa kaka yaya y dawo,ihsan ke kuma tafi gurin momynki ki fada mata da gudunsu suka fice tace my son muje kaci abinci. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:31 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (8/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *52* Ihsan ta shiga part din mommy tayi sallama,mommy tace daughter na y akayi,ihsan tayi dariya dan tanason mommy tace mata daughter na tace mommy na yayane y dawo yana part din aunty amarya,murmushi mommy tayi tace to ai shikenan kinga aunty saita rage damuwa ko tunda son dinta y dawo dariya ihsan tayi tace eh kuma tayita mana fada ko yaya mukayi Abu ba,dariya mommy tayi tace ai yanxu xata daina dama saboda rashin son dinta takeyi muku,mommy tace kije kice masa inayi masa sannu da xuwa kinji ihsan ta futa tace toh mommy. Tasleem ma taje ta fadawa kaka,da murna kaka ta futo a daki tace Ashe da gaske kike islam yanxu fateema ta aiko tasleem wai Aslam y dawo,islam ta xumbura baki amma batayi magana ba kaka ta fice islam da Amira ma suka mara mata baya har part din kaka. Xaune suka tadda Aslam a dinning aunty amarya ta cika masa gaba da kayan abinci farin cikin fuskarta y kasa boyuwa shima yanata murmushi su kaka suka shigo,ka ta xauna tace mai gdan Ashe ka dawo juyowa yayi yace eh ai naxata kafinna dawo ma kin kara gaba,cikin rashin fahimta kaka tace bangane na kara gaba ba,Aslam yace mutuwa nake nufi ko kinci xamaninki kinci na yaya na jikokima sai kinci cikin masifa kaka tace ubanka ne xai mutu mara mutuncin yaro ai saitahau kuka aunty amarya ce tahau bata hakuri sukuwa yaran me xasuyi inba dariya ba dan lokacin harsu haidar sun shigo,Aslam ne y daure fuska tuni kowa yayi shiru,islam kuwa dariya taci gaba dayi tace yanxu kaka mutuwar kikejin xoro haka kinga yadda kike kuka ta dada kyalkyalewa da dariya,Aslam ma duk yadda y hade rai sai da tayi murmushi,kaka kuwa hararar islam tayi tace ku yanxu in mutuwar taxo ku tsaya,suka dada kwashewa da dariya,kaka ta harxuka tace bani kukewa dariya ba da uwayenku kuke ta goge kwalla da habar xani,Aslam kuwa tashi yayi a kujerar dinning y koma kusa da kaka y dora kansa a cinyar kaka yace haba matar kawai tsokanarki fa nakeyi,ai inanan inayi miki addu'a har auran tattaba kunne ki gani,dariya kaka tayi tace to naji dannema ta dungure masa kai tace ai dukkaine kaja,y gaisheta lokacin mommy ta shigo da sauri ya tashi yaje yayi hugging dinta yace mommy ta i miss u,murmushi tayi ta cireshi a jikinta tace kaidai baka girma,yace to y xa'ayi in girma inada 2 momies 2 daddies 5 granny dariya aunty amarya tayi tace hakane my boy,komawa yayi y xauna kaka tace niwai mai gdan yanaga dukka ramene kayi baki,anan y fara basu lbrn irin gurgurmin dajin da sukaje yaki dan duhu dajin da rana ma saisun kunna wuta kuma sai suyi sati basuyi wanka ba abinci kuwa da wanda suka tafi dashi y kare komawa cin ganyayyaki sukayi sai ruwa ruwanma basa samu su koshi,ga ba'a barin kowa y shiga dajin sai iyasu sojoji,anan y cire musu riga y nuna musu inda aka harbesa amma Allah y taimakesu sunyi nasara sun kama shugabannasu sun dankashi hannun hukuma,a dakin ba abinda yake tashi sai kuka kaka cikin jan magina tace Allah sarki lallai kunyi namijin kokari Allah y dada tsareku sukace ameen. Islam tace yaya damafa ni ina ganinka kullum acikin baccina kanata shan wahala kana kaida wani abokinka da sojoji masu yawa,ta daga kanta alamar tunani tace uhm yaya safwan yauwa na tuna inka kirani sainaji tsoro nagudu saikace nadingayi maka addu'a,ta kalli aunty amarya tace ko aunty amarya,gyada kai aunty amarya tace tabbas nima sai sati biyu da suka wuce take fadamin lokacin ta futo a kitchen ta yarda kofi anan na ritsata shine take fadamin,kakama tace tabbas duk dare cikin baccinta tadinga surutai kenan tana kiran sunan Aslam,kowa mamakine y kamashi musamman Aslam saboda yasan islam batasan safwan ba amma gashi takira sunansa y runtse ido yace me hakan yake nufi islam ta damu dani kenan,islam ce ta tashi tace tunda y gamasamu kukan Amira tashi mu tafi,kowa a dakin sai da yayi dariya saboda furucin islam. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (9/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *53* Lokacin dasu Abba suka dawo ma sunji dadin ganin Aslam y dawo lfy,sai dai ramar da yayi itace sukayi magana,nan ma yace musu yanayin aikine y basu lbr kamar yadda yabawa su aunty amarya suma sun tausaya masa sosai. Bayan sallar isha'i xaune dukkansu suke a palon kaka,daddy,Abba,momommy,aunty amarya,Aslam,kaka bayan bayanai da addu'o'i da aka gabatar daddy yayi gyaran murya,yace toh alhmdllh dukkan godiya ta tabbata ga Allah mai kowa mai komai a yau Allah y dawo mana da Aslam lfy bayan tsawon watanni daya dauka a gurin aiki,kuma Allah y basu nassarar abinda sukaje yi sai dai fatan Allah y dada tsarewa,kowa a palon yace ameen,daddy yaja numfashi yace to babana Allah y cika maka burinka yau gaka a matsayin daka dade kana tunani gaka acikin aikin soja,a tunanina kana da shekaru yanxu 26 kenan ko y kalli Aslam,eh Aslam yace,daddy yace masha Allah mun yanke shawara da iyayenka da kuma hajiya akan y kamata kaima ka ajiye iyali,dam2 kirjin Aslam y bada kara,daddy yace to yanxu in kanada wadda kakeso saika fada mata domin muje nema maka auranta. Murmushi Aslam yayi,dukkuwa da yana cikin rudu yace to waima daddy nawa nakene da har xa'a faramin maganar aure,kaka ce tace kujimin xancen banxa karewarta yau aka haifoka murmushi Aslam y karayi har hakoranshi suka bayyana yace toh waike kaka INA ruwanki ne da shiga shirgin da ba'a saka dake ba,nagane ma kishi kikeyi to ki kwantar da hankalinki kece dai dagake ba wata,daddy ne yace kaci gidanku hajiyar tamu kakewa shakiyanci haka,Aslam yace Allah daddy kyaleni da tsohuwarnan inma tana tsoro ta mutune ta kwantar da hankalinta na rokar mata Allah insha Allah har bikin tattaba kunnenta xata gani,Abba ne y dauki pillow din kujera y jefa masa yace sai dai kaika mutu amma hajiya xama daram,da mamaki Aslam yace Abba ai gwanda ta tafi tunda taci xamaninta taci na yaya dannaci na jikokin ma tace sai taci,kakace ta tashi ta tafi gadan2 wai dukanshi xatayi da sauri Aslam y tashi yana dariya y fice a palon,su aunty amarya ma kawai kunshe dariyarsu suke,komawa kaka tayi ta xauna tana haki tace xakaxo ka sameni ne mutumin banxa ta kalli su daddy tace nafada muku ku kyaleni naje kauye na auro masa ma'u kunki dariya Abba yayi yace hajiya kiyi hakuri kinga Aslam har yanxu yarone baikamata a matsa mishi da xancen aure ba,kaka tace to shikenan dama wai inaso naga yayan jikoki ne kafin sa'i yayi,daddy yace hajiya ai mutuwa lokacice waya fada miki kin kusa mutuwa haka taron y watse kowa cikin farin ciki. Aslam kuwa yana shiga dakinsa y fada gado yayi murmushi y shafi gemunsa yace waini aure tab ai duk da inada bukatar auran amma baxan iyayi yanxu ba,wayarshi y dauka y kira safwan bayan y daga,safwan yace maxaje y gdan?Aslam yace gda lfy,safwan yace y kowa da kowa,Aslam yace duk suna lfy,sun dade suna hira Aslam y fada masa waisu daddy aure sukeso yayi,dariya safwan y tuntsire da ita sai da yayi mai isarsa,harya bawa Aslam haushi,sannan yace ai sunyi gaskiya y kamata kayi auran,Aslam yace kai ubanwa y hanaka yi,safwan yace aini yarone,Aslam yace lallai fa,shiyasa kake mayan mata budurwar daka gani saika bita,safwan yace eh naji ni ai bawanda yayimin maganar aure,Aslam yace to nima da akamin sainan da 4 year xuwa nan nacika 30 kenan,har xasuyi sallama safwan yace ina jerry dinka? Aslam yace tananan mashirmaciya kasan wai har mafarkina takeyi a dajinnan,anan y lbrtawa safwan yadda ta fada masa kuma harshi safwan din ta gani dan har sunanka ta fadamin,mamakine y kama safwan yace ikon Allah yafi karfin wasa,dariya Aslam yayi yace wai kai mamaki kakeyi,safwan yace eh exartly fa yadda muke a dajinnan ta fada,dan juyawa Aslam yayi yace ni bana mamaki na dade dama ina tunanin yarinyar tanada aljanu saboda rashin jinta yafi karfin hankalinta,to kaga tunanina yaxo dai2 tunda sun fara bude mata ido,dariya safwan yayi a haka harsukayi sallama. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (9/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *54* Kamar yadda akayi musu alkawari washe gari ko wanne soja yaji alert na 20 million acikin accaunt dinshi,wadanda suka rasu kuma har gda aka kaiwa iyalansu,saboda ba karamin kudi gwamnatin somalia ta bawa nigeria ba,aikuwa kowa yayi farin ciki,safwan ne y kira Aslam yace aboki gaka alert Aslam yace eh,yanxu y shigo tashima nakeso nayi naje nayiwa aunty na albishir safwan yace aboki ankusa fara lissafamu acikin matasa masu kudin duniya dariya Aslam yayi yace Allah y shiryeka masu kudin duniyar akace maka yan milliyoyi ne dasu haka suka karashe wayar cikin barkwanci. Direct yana futa part din aunty amarya y shiga akace tana part din mommy acan yaje y sanesu ya fada musu sunyi murna sosai sun kuma tayashi farin ciki,yace toh yanxu bari su daddy suxo naji shawarar da xasu bani akan kudinnan aunty amarya tace gaskiya kayi tunani me kyau,mommy kuwa murmushi kawai takeyi,aunty amarya ce tace mommy bakice komai ba,mommy tace to me xance uwa da da suna shawara,dariya aunty amarya tayi tace addu'a mukeso kiyi mana,mommy tace to Allah yasa albarka,aunty amarya tace ameen,ta kalli Aslam tace jeka fadawa uwar gdan taka dariya yayi y tashi y futa,kaka kawai y tarar dan su islam sun tafi makaranta yaje y fada mata itama ta tayashi murna kuma tayi masa addu'a. Dasu daddy suka dawo y fada musu sunji dadi,sukace dama mun riga mun siya muku fili kai da amir na kowa 1.5 million aka siyeshi to da munso mu gina muku dama karshen shekara muke jira tunda kai kudi yaxo saikaje ka fara ginawa inaga cost din da aka bamu na ginin gran 10 million ne babu furnishing ragowar ka fara kasuwanci ko sai da motocine,farin ciki sosai Aslam yayi yadinga yiwa su daddy godiya da addu'ar Allah y kara budi,suma sunji dadi sosai. Haka rayuwa taci gaba da tafiya,Aslam y saka anfara gina masa gidansa ginine mai kyau ginin xamani,kuma y fara kasuwancin motoci ta computer yana ganin albarkar abin dan lokacin da yayi order sukaxo 2 millions y samu riba. Wannan karan basu fiya haduwa da islam ba,shiyasa duk rashin kirkin da takeyi baya sani,yauma kamar ko yaushe,friday ce Aslam y dawo daga masallaci sallar la'asar yaga yara maxa da mata sunata shiga gidansu,mamaki y isheshi yace to me akeyi haka yana shiga yaji sauti natashi a part din kaka karasawa yayi hayaniya yaji ana tayi,islam y hanko sanye da body hug red mai dogon hannu da three quarter pensil tayi packing din gashinta da red ribon kwalli kawai ta saka sai red lipstick amma tayi bala'in kyau irin dressing din Amira tayi amma rigarta yellow khausar ma haka tata pink,rawa islam takeyi tanata wani kada kugu tamkar babbar mace yara kuwa sai ihu sukeyi,su Amira suna lika mata yan 5 naira da yaya sagir y canjo musu,hannun ko wanne yaro yana rike da biscuit da lemo wata muguwar tsawa Aslam y sakar musu tuni kowa y nutsu,islam kuwa sororo ta tsaya kallasa dakawa yaran tsawa yayi yace kowa y fice,da gudu suke futa kowa yana rige2,islam ce cikin daga murya tace ku Ku tsaya mana inaruwanku dashi shine y gayyatoku koni dan Allah karku tafi,ganin da tayi yaran basusan ma tanayi ba shine y kular da ita ganin kowa y waste,a tsiwace ta karasa gaban yaya Aslam,tace yaya ina ruwanka da patyn da nakeyi,kawai xakaxo ka tsorata min kawaye da wannan jan idonnaka da kuma katuwar muryarka kamar xata fasa gda,mamakine y ishi Aslam y kasa magana islam tace wai baka jinane inayiwa yata birthday ka tarwatsamin tarona ta karashe makanar tana harararsa tana murguda baki,bakinnata y kama y murda da xafi y rankwasheta yace ke ko kadan baki dace da sunan islam ba danshi musulunci xaman lfyne,amman ke duk inda tashin hankali yake nan kikafi kauri,ai dama nine nasaka miki islam to xansiyo rago nacanja miki ki koma duduwa,y hankada ta gefe y fice,ihu ta kwalla ta fadi tana wayyo wlh ba wanda y isa y canjamin suna nakoma duduwa mai kan bari,duk da xafin da bakinta yake mata batashi takeyi ba,suna da akace xa'a canja mata shiyafi mata ciwo. wannan page dinnakine *53 & 54* aunty jameela Marapha 💃💃 Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (12/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *55* Ihunta taci gaba dayi hawaye kuwa shabe2 a fuskarta,sai hakuri su Amira suke bata amma takiyin shiru,kakace ta dawo daga gdan makotansu akwai tsohuwa a gdan,tana yo hanyar part dinta tajiyo ihun islam ai da sauri tayi part din nata harda hadawa da gudu. Birgima ta tarar islam tanayi da sauri kaka ta karasa ta dagowa tirjewa islam ta farayi,kaka tace haba islam dita ku dana tafi nabarku kuna partyn ku y xan dawo natarar ba yaran kallan su khausar tayi tace ina kawayen naku,khausar tace yaya Aslam y koresu,kaka tace wai yaushe Aslam sai daina shiga harkar islam ne to wlh bari naje na sameshi nasan kila har dukanki yayi ko ta kalli islam. Islam ta shagwabe fuska tace eh y rankwasheni y murdemin baki yacemin mai idon mayu (nikuwa nace uhm harda kari 🤔)sannan yace wai xai siyo rago y canjamin suna wai nakoma duduwa ta dada barkewa da kuka,kaka tace rabu dashi naga dan iskan daya isa y canja miki suna a gdannan kuma xaixo y sameni y fada min wace mai idon mayu,dakyar ta lallashi islam tayi shiru. Islam kuwa tun daga ranar kawai hanya take jira danta huce haushin abinda yayi mata y bata mata party. Futowarta daga part din mommy kenan ta tarar da alkajirinsu nura yana wanke motar Aslam,murmushi islam tayi ta karasa tace nura sannu da aiki yace yauwa,tace mota kake wankewa yace eh wlh yaya Aslam ne xaije bikin abokisa,murmushi islam tayi tace Allah sarki xama tayi tanata yiwa nura surutu harya karasa wankin motar y kwashi bokitai ya tafi part din Aslam yace y gama. Da gudu islam ta tafi part din kaka kibiya ta dauko ta daidaici tayar motar Aslam ta caka kibiyar tus tayar ta sace da sauri ta kwasa da guru ta shiga part din kaka ta labe tana iya leko waje. Aslam ne y futo cikin wani dakakken yadi milk colour a kallah xai kai 75k tsadarsa yana sanye da xanna bukar brown da touch din milk a kallah hularnan xatakai 25k takalmin kafarsa ma milk ne mai dan yatsa shima daga gani xaiyi tsada,tafe yake yana sauri waya a kunnenshi y makaleta da shoulder dinsa yana ku bani 15 minute insha Allah xan karaso,hannunsa kuma yana daura hadadden ogogon axurfa na rolex,yana futowa y dannan key din motar da mukullinshi ta bude,shiga motar yayi y tasheta xaiyi reverse yaji motar tayi wani gurrrr kit ta tsaya tsaki yayi y futo kallan tayar motar y fara,ganin tarar tayi faci shine y bashi haushi wani naushi y kaiwa motar yace oh god gashi y duba duk an futa da motocin gdan,Nura y fara kwalawa kira. Islam da take labe ganin yanayin da y shiga ranshi y baci shine y sakata farin ciki tuni tahau kyalkyala dariya,da sauri Nura y karaso kallanshi Aslam yayi yace Ashe motarnan tayi faci amma baka fadamin ba,Nura yace wlh yallabai lfyr motar qlau yanxu dana gama wanketa,Aslam y harxuka yace ga tayar motar a sace xakacemin qlau take,Nura y durkusar da kansa islam ce ta futo daga maboyarta tace yaya ba laifin Nura bane ta daga masa kibiya a hannunsa tace nicenan na sace maka taya,ramawa nayi ka tuna randa ka korarmun kawayena da sukaxo party,ta kyalkyale da dariya,ran Aslam in yayi dubu y baci Nura kuwa mamakine y cikashi a ranshi yace lallai yarinyar nan shiyasa dama taxo ta isheni da surutu. Har Aslam y xuciya yayi gurinta,ita kuwa ganin haka ta kwasa a guje sai part din kaka,wayarsa da tahau ringing shine y katseshi ganin abdallah ke kiranshi,yayi picking abdallah yace haryanxu baka tahoba yace eh wlh faci nayi amma yanxu xanyi changing taya nataho,spare taya y dauko a motarshi y saka sai daya bata 30 minute sannan y tafi. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (12/11/2016 2:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *56* Da gudu ta shiga part din kaka,bayan kaka ta tafi ta dukunkune kaka tace islam wai meyasa bakya rabo da shirme ne,islam ta turo karamin bakinta gaba tace ke kakannan ba yaya Aslam bane y biyoni,kaka tace ina Aslam din yake dan karya,keda bakyajin kunyar karya,islam tace Allah da gaske nake,kaka tace eh laifi kikayi masa,islam tayi murmushi tace babbama kuwa tayar motaraa na sace masa kuma unguwa xaije,dariya kaka tayi tace meyasa islam wai sam bakya tsoron fitina ne,islam ma dariya tayi tace ramawa fa nayi kin manta randa y korarmin kawayena,kaka tace tab naga ranar da xaki yafiya,murmushi islam tayi tace babu rana dan indai mutum yamin saina rama,tsaki Amira tayi tace wlh islam ina tsoratar miki ranar da yaya Aslam xai babballaki,dan ko kaka da take biye miki tana ganin duk abinda kikayi daidaine baxata iya kwatarki ba,islam ce ta hayayyakowa Amira tace eh naji kuma dadinta ni kikace xa'a ballah ba keba dan haka saiki kama bakinki kiyi shiru,kaka da kike cewa tana biyemin ta biyemin din,to ni naji shishshigi ma ina ruwanki da xancen mu manxan Allah S.A.W yace falyakul khairan au liyasmut ma'ana (kafadi alkhairi ko kayi shiru)dan haka babballawa ki gani a kanki ke tsayama kiji ni ko yaya y ballani wlh sainaja kafata na dana masa tarkon da shima xai dawo y xauna sai dai muyi jinyar tare tayi tsaki Amira kuwa shiru tayi saboda ita sam bata iya hayaniya ba. Kamar yadda akace after 2 month xa'ayi karin girman su Aslam to yau saura 3 day shirye2 kawai su daddy sukeyi dan dukka gdan xa'a tafi sun gama duk wani shirinsu sunyi dinkuna dan tamkar wani biki haka sukejin abin. Dukkansu sun shirya kaka,daddy,Abba,mommy,aunty amarya,da sauran yaran gdan dukkansu dan harda khausar xa'aje,lokacin da mommy tace ita ba saitaje ba islam ma tace aikuwa ba inda xata,a gurin mommy xata xauna,saida aunty amarya tayi fushi sannan mommy ta yarda xataje. Ticket suka yanka dan flight xasubi,Aslam kuwa tun last week y tafi,suna dira a airport Aslam da safwan ne sukaxo daukarsu dansun xata iyasu daddy ne xasuxo ganinsu da yawansu yasa daukan drop din taxi 2 suka cika sai gdansu safwan. Aunty tayi farin cikin ganinsu sai nan2 takeyi dasu bayan sun gaisa ancicci abinci hankali y kwanta daddy,Abba,daddyn safwan suka futa dan hotel xasu kama. Islam tace Amira ku taso muje gerden sukace toh dukkansu harda kausar da tasleem suka tafi. Wannan pages din *55 & 56* nakune murjanatu & hafsert. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (12/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *57* Yaune xa'ayi karin girman kowa y hallara a hall din da xa'ayi sojoji kuwa kala2 sanye da kakinsu kamada sojojin ruwa sojojin sama d.s. Su Aslam sanye suke cikin kakinsu na army sunyi bala'in yin kyau suna a kakkame bayan bayanai da jinjina da dada wa su Aslam karfin gwiwa akan haxakar da sukayi akaja hankalin sauran sojoji suma y kamata suyi koyi da irin haxakar da yan uwansu sukayi,anan aka fara rabon mukamai Aslam da safwan an basu matsayin captain masu igiya 3 a kafada,sai dai muyi fatan Allah y dada riko,anyi fareti kala2,an bawa canal yusuf safana matsayin general saboda horon da yayiwa yaranshi shine y basu kwarin gwiwa har sukayi nassara,anyi pic an rarraba kyautuka daganan taro y watse. Washe gari su islam suka kamo hanya suka dawo gda kano ta dabo tumbin giwa. Kowannen su office aka bashi aiki sukeyi tukuru kuma kowanne yana da yaran da yake horarwa a cikin barreck dinsu an bawa kowa gda mai dauke da katon palo 2 bed room akwai toilet acikin kowanne daki sai kitchen dan yanxu su Aslam ma kowa y tare a gdansa. Xaune Aslam yake a office safwan y shigo y bashi hannu suka gaisa,safwan yace gaskiya aboki Allah y albarkanci aikinnan namu murmushi Aslam yayi yace eh ai kowa yabi iyaye xaiga da kyau safwan yace gaskiya,safwan yace xuwa nayi nafada maka xanje gaida aunty kaga 1 week kenan banje ba,Aslam yace to muje gaba daya tunda bani da sauran aiki. Sunje aunty taji dadi tayi musu nasiha sosai akan suguji aikata sabon Allah karsuga Allah y basu dama kuma su butulce masa,sunji dadin nasihar aunty sunyi godiya daganan suka koma gda. Aslam ne y futo rikeda try y sako food flask da plate da serving spoon da kuma fuck direwa yayi a gaban Aslam yace wash gaskiya mata na aiki dama haka sukeshan wahalan girki,dariya safwan yayi yace kai kace baxaka iya cin abincin restaurant ba,sannan nace kayo aure kaki ba saikaci gaba dayi mana abinci ba. Y xuba musu jellop din taliya dataji kayan lambu da kifi sai kanshi takeyi,harararsa Aslam yayi yace kaima in kayo auran ai ba laifi bane,dallah tashi katon banxa ka dauko mana juice da ruwa a fridge,tashi safwan yayi yana eh naji amma dik girmana ban kaika ba ko y dawo dauke da try y sako exotic da ruwan faro,abincinsu sukaci cikin raha da barkwanci. Safwan ne y kula Aslam sai gumi yake hadawa dukkuwa da sanyin a.c din dayake dakin,safwan yace y akayine ganin Aslam y rike cikinshi yana lullumshe ido shine y tashi hankakin safwan da sauri y dauki waya y kira clinic din bareck din,xuwa lokacin Aslam ko motsi bayayi,ba'afi 5 minute ba dr y karaso yaga halin da Aslam yake ciki da hanxari y bashi taimakon gaggawa yacewa safwan y kamashi su wuce hospital. Suna xuwa direct dakin scanning aka wuce da Aslam after 20 minute likitan y futo aka garo garo Aslam a gado dan lokacin bacci yakeyi. After 1 hour Aslam y farka,da sauri safwan y matsa yanayi masa y jiki mikewa Aslam yayi yace nafa warke,safwan yace to meya faru dakaine a lokacin naga hira mukeyi,Aslam yace bafa komai bane kawai cikina ne yakemin ciwo kuma dama inayi yanxune abin yayi worst,safwan yace sannu Aslam yace yauwa y diro a gadon yace muje office din dr y mana bayanin mai yake damuna. Taku har kullu *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/12, 9:32 PM] ‪+234 803 841 7219‬: (12/11/2016 3:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *58* Xaune suke a office din dr y fara musu bayani yace to a gaskiya yallabai ba komai ne yake damunka ba,illah kana da matsananciyar sha'awa dalilin hakane sperm y taru a mararka shine yake haddasa maka ciwon ciki,yanxu taimakon da xan iya baka shine y miko masa wata paper ya mika masa yace ga wasu magani ka dinga amfani dasu insha Allah xasu rage maka yawan sha'awa,amma shawarata a gareka yalabai ka daure kayi aure shine kawai bbn solution,tsaki Aslam yayi y karbi paper din yace ngd suka futa direct pharmacy sukaje suka karbi maganin,dayake kowanne soja yana da file a asibitin ana diban kudi a cikin salary dinsa. Xaune yake a palo y dafe kanshi,safwan y ballo magani yace gashi kasha,kawai ka dauki shawarar likita kayi auran dakaci gaba da xama da cuta y karashe maganar da dariyar shakiyanci,harara Aslam y daka masa yace uban aure xanyi to waima kai daka dameni danayi aure waxan aura,kai nifa haryanxu banga yarinyar da taminba,cikin xaulaya safwan yace ai wannan abune mai sauki kawai pic dinka xaka bani au abuma mai sauki ai ina dashi a waya,xanje nadinga tallata ka gurin yan mata har a samu wadda xatace tana sonka. Cikin fushi Aslam y dago kansa yace kutt amma kayi bala'in rainani ni xakaje ka tallata,safwan yace eh ai xan fada musu kai mai ajine kawai dai kana tsoron matane pillow din kujera Aslam y dauka y jefawa safwan yace amma Allah y isa tsakanina da kai,dariya safwan yayi yace eh naji wlh indai bakayi aure ba to wlh saina janyo anmaka auran dole kuma wadda xa'a aura maka xakayi mugun mamaki,Aslam yace mafashi wanda y fasa baya kaunar Allah,safwan yace haka kace Aslam yace eh,daganan sukaci gaba da hira. Haka Aslam yaci gaba da rayuwa ko yaushe cikin shan tablet amma baitaba bari an sani a gda ba,saboda in ciwon y tasar masa sai yayi sati a asibiti,inda Allah y taimakeshi ma ciwon baitaba tayar masa yaje kano ba,safwan kuwa yananan da kudirinshi a ranshi,amma bai fadawa Aslam ko menene ba,kawai dai yana yawan masa xancen aure,sai yace sai yayi 30 year dan baxai aure y tsufa da wuri ba safwan kuwa sai yayi dariya. *AFYER 3 YEAR* Su islam nagani anfara xama yan mata hada2 naga anatayi can idona y hango kalandu da memo da jaka mai hotuna gani nayi ansaka congratulation for qur'anic graduation & j.s c.e Aysha (Islam),zainab (Amira) & khausar (nace toh su islam an xama malamai 🙄) Sun dawo daga returching suka hadu dasu Aslam,kiransu yayi yace kuxonan shida safwanne,karasawa sukayi Amira da khausar suka gaida Aslam da safwan suka amsa,islam kuwa tace yaya safwan ina wuni murmushi yayi yace lfy qlau y taro tace alhmdllh,yace to Allah yasa na tsoron Allah ne tace ameen. Aslam kuwa y kulu watako ba xata gaisheshi ba,lallai saiya ladabtar da yarinyar nan,yace haba safwan mutumin da hankali ma bai wadace shiba kakewa addu'ar tsoron Allah,ai sai dai kayi mata fatan samun lfy,da kuma in saukar gaskece bata xukuba Allah y saita mata kwakwalwarta ta dena neman bala'i dan kasanfa ba kowa sauka take nitsarwa ba. Murmushi islam tayi dantasan da ita yake,tace yaya safwan Ashe mahaukatan da yawa kuma ita saukar qur'ani ai kafinnayi dubun wasune sukayi,kaga Ashe tunda bai saka sauran hankali da neman tsokana ba,danna yanxuma basuyi ba to ba'a kasa suga ganiba a gurin manyansu ne,su Amira da suka saki baki da hanci suna kallanta tace ku kuma dallah can mu tafi,ta juya tace yaya safwan nabarka lfy. Wannan pages din *57 & 58* nakune mmn Amira (sis)mmn waleed & haleematy. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/13, 7:12 PM] ‪+234 816 796 6870‬: (13/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *59* Su khausar suma juyawa sukayi suka tafi cikin gda,suna shiga Amira tace gaskiya islam abinda kikeyi bakya kyautawa ai ko babu komai yaya Aslam wankine,kuma masu iya magana suna cewa babban wa tamkar uba yake. Wani shekeke islam tabi Amira da kallo tace sannu uwata da xaki xauna kinamin masifa,in kuma wa'axi kikeso sai a kawo miki laudspeaker,da kike cewa kuma na raina Aslam aishi yaja,bakiji masu iya magana suna cewa in babba baiji kunyar hawa jaki ba,to jaki baxaiji kunyar kayar dashi ba,dan haka wlh daga yanxu ki futa harkata tsakanina da wancan hero din in kuma baso kikeyi musa kafar wando daya dake ba,dan wlh ni warkice dai2 kugun kowa tayi tsaki tayi gaba. Aslam kuwa mutuwar xaune yayi,lallai yayi sake yarinyarnan ta rainashi harshi xata fadawa irin wadannan xafafan kalaman dole y hukuntata fiye da laifin data aikata,shikuwa safwan ganin halin da Aslam y shiga shine y bashi dariya,cikin kyakyatawa yace watako friend yarinyar nan tana birgeni ko kadan batada tsoro,kaga yadda ta mayar maka bakar maganar daka fada mata cikin hikima,safwan y karashe maganar cikin kyakyata dariya,Aslam kuwa inda abinda y tsana bai wuce ayi masa dariya ba musamman yau da islam ta bata masa rai fiyeda ko yaushe,dan maganganun data fada masa wlh ko sa'ansa ne y fada yau saiya kwana a guardroom tuni idanunsa suka kada sukayi ja,jikinsa yahau rawa gashin jikinsa duk y tashi y runtse ido yahau tauna labbansa (nikuwa ganin haka na xare ido nace ran maxa y baci. Kamar wani xaki haka y tashi a fusace yana tafiya cikin jarumta y shige part dinsu,safwan ganin haka bai bishiba kawai saiya shige dakin Amir sukaci gaba da hira. Sai bayan sallar isa sannan safwan y shiga dakin,Aslam y gani yanata safa da marwa cikin sanyin murya safwan yace haba friend a dalilin me xaka saka damuwa a ranka,dan Allah ka manta abinda y faru,wani mugun kallo Aslam yayiwa safwan sannan cikin karaji yace wlh baxan taba kyale yarinyar nan ba,na tsaneta! na tsaneta!! na tsaneta y karasa maganar cikin wani irin amo da saida dakin y amsa,safwan yace calm down nasan ta bata maka,amma dan Allah ka sassauta xuciyarka duk tsanani dai yarinyar nan jininka ce,wani murmushi Aslam yayi na gefen baki y wani furxar da xaxxafar iska daga bakinshi yace ai wannan darajar ce kawai yasaka nake kyaleta,amma wlh wannan karan saina koya mata hankali,a hakadai safwan yaci gaba da kwantarwa aslam hankali da dadadan kalamai,haryaji xuciyarshi tayi masa sanyi.(Allah y hadamu da abokanai na gari wadanda xasu dinga bamu shawara mai kyau a duk lokacin da suka fahimci muna cikin matsala ba wadanda xasu xugamu ba mu dada fadawa cikin dana Sani). Washe gari da misalin 10:00am makil filin makarantar su islam yace da jama'a,sanadiyyar saukar qur'ani da dalibai xasuyi,an gayyato manyan mutane kamada san kano,gwamnan kano,chairman,cancilor,manyan yan kasuwa dadai sauran masu fada aji,anyi taro lfy an bawa dalibai alluna da kyaututtuka islam da sauran dalibai sunyi karatu,islam ta karbi kyautar dalibar da tafi kowa haxaka,da tsafta,Amira ta karbi dalibar da tafi kowa ladabi,khausar ta karbi na dalibar da tafi kowa tsafta itama. Misalin 4:00pm su islam suka koma makaranta dan gudanar da waleema anci ansha,anyi tamsiliya kuma ta kayatar dalibai sun raba kalandu,memo,jaka,key holder d.s daganan taro y watse kowa yayi gda. Aslam ne kwance yanata murkususu saboda matsanancin ciwo da mararshi takeyi,gashi yasha tablet din da yakesha amma babu wani sauki saima tsananta da ciwon nashi yayi,tun yana kan gado harya fado kasa. Safwan ne da amir suka shigo sun dawo daga walimar su islam,dan lokacin da xasu tafi bayadda basuyi ba da Aslam yaxo yaje yaki,suna shigowa da sauri sukayi kan Aslam dako motsi bayayi a lokacin. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/13, 7:12 PM] ‪+234 816 796 6870‬: (13/11/2016 3:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *60* Cikin tashin hankali suka dagoshi ganin ko numfashi bayayi shine y tashi hankalinsu da sauri suka kinkimeshi sai cikin mota,da gudu Amir yaje y fadawa Abba y dawo yaja motar suka fuce wani private hospital suka nufa. Hankalin kowa y tashi tuni daddy da Abba suka shiga mota sukabi bayan su Aslam,Amira ce cikin tashin hankali tana kuka ta shiga part din kaka direct dakinsu ta wuce lokacin islam tana warware kyautar data samu,Amira tace islam yaya aslam ne bashi da lfy yanxu aka futa dashi kamar gawa hankalin kowa y tashi,islam tace Allah y bashi lfy,taci gaba da abinda takeyi,jin har lokacin Amira batabar kuka ba shine yasa jikin islam yayi sanyi ta ture kyautar tata gefe ta kamo hannun Amira tace kiyi hakuri addu'a ce ta kamata kiyi masa ba kuka ba,Amira taja hanci tace ko numfashi fa bayayi lokacin da aka futa dashi,islam ce tayi shiru a ranta tana cewa nashiga 3 yanxu in yaya Aslam y mutu y xanyi bamu nemi yafiyar juna ba kawai itama saita hau kuka. Su amir suna xuwa cikin sauri aka karbi Aslam,taimakon gaggawa aka fara bashi,lokacin wayar amir ta fara ringing ganin daddy ke kiranshi shine y sakashi dagawa,suka tambaye shi wanne hospital ne y fada musu,cikin 10 minute suka karaso lokacin su amir suna tsaye jugum2,Abba yace ina Aslam din yanxu safwan y nuna musu wani daki yace yana ciki shida likitoci suma su Abba tsayawa sukayi kowa da abinda yake sakawa a ranshi,safwan kuwa cewa yakeyi tambas yanxune y kamata na aiwatar da kudirin da yake raina (nikuwa nace toh Allah yasa alkhairi kake kitsawa🙄). Saida likitoci suka share tsawon 3 hour sannan suka futo suna yarfe gumi,babban cikinsu ne (dr fu'ad nacikin buk dina kangin rayuwa)y karasa gurinsu Abba y mika musu hannu sukayi musa basa yace ku dameni a office y wuce. Xaxxaune Abba da daddy suke a gaban dr safwan da amir kuma suna tsaye,farin glass din idonshi dr fu'ad y xare,yace sakamakon gwaje2 da mukayi mun gano danku yana fama da ciwon mara sakamakon matsananciyar sha'awa da yake da ita,to a bincikenmu mun gano yadau xawon lokaci yana amfani da wasu tablet wanda kwantar da ciwon sukeyi ba warkarwa ba,to a gaskiya yanxu ciwon yayi mugun tsanani wanda a wannan lokacin babu wasu sauran tablet da xasuyi masa aiki,yayi shiru nadan lokaci yace yanxu mafita 1 ce xuwa 2,xamu iya basa shawara in harya farfado ba sauran ciwon duk lokacin da sha'aware ta taso masa y dinga shan lipton da lemon tsami dan shi tsinka sperm yakeyi y futo,ko kuma babban solution kuyi masa aure a kurkusa baku dauki dogon lokaciba,in harya taci cikin bai daina ciwo ba to saimun yi masa aiki,cikin firgici dukkansu suka dago kawunansu yace yes aciki shawarina dole a dauki daya godiya sukayiwa dr dukkansu suka futa a office dinnashi,dakin da aka kwantar da Aslam suka shiga bacci yakeyi a hannunsa kuma an daura masa drip. Xama sukayi kowa da abinda yake sakawa a ranshi,cikin sanyin murya Abba yace yaya to yanxu menene mafuta,jan numfashi daddy yayi yace mafuta 1 ce mujira y farfado y fada mana in akwai yarinyar da yakeso y fada mana sai a nema masa auranta,Abba yace wannan gaskiya ne. Safwanne yace daddy inada magana daddy yace munajinka,safwan yace Abba a xamanmu da Aslam baitabayin budurwa ba,tsantsar mamakine y lullube su Abba,safwan yaci gaba da magana yace saboda yace baxai taba iya yiwa yarinyar da yakeso kishiya ba dan tun ranar da aka haifeta yake dawainiya da dakon santa,cikin mamaki daddy yace wacce yarinya ce haka,safwan yace *islam* ce,cikin mamaki Amir y maimaita *islam*,safwan yace eh,daddy kuwa murmushin manya yayi yace yaro man kaxa,to amma shine y kasa fada safwan yace jira yake wai saitayi candy,shiru daddy yayi daya tuna dududu islam batafi 14 year ba. Har wajen 10:00pm Aslam bai farkaba sanadiyyar allurar baccin da aka saka masa a drip,daddy ne y mike yace tomu bari mu tafi tunda bai farkaba,ku saiku xauna dashi amir yace toh daddy,suka futa. Amir ne y kalli safwan yace abinda ka fada anya gaskiya ne,safwan yace eh kaima kayi mamaki ko,ai koni ba Karamin mamaki nayiba lokacin daya fadamin(ni kaina nayi bala'in mamaki 🤔). Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* (14/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *61* Lokacin dasu daddy suka koma gda,a tsaitsaye suka tarar dasu aunty amarya a sarraunding din gdan,da sauri suke tambayar shi y jikin Aslam din da sauki sukace baccima yakeyi lokacin da suka taho,sai lokacin hankakin su aunty amarya y kwanta. Daddy ne yace aliyu jeka kirawo hajiya tunda part dinta akwai mutane saiku taho palo na xamuyi magana toh Abba yace y karasa part din kaka y kirata suka taho. Xaxxaune suke,kowa yana jiran yaji mai daddy xaice y kirasu a darennan da xai kasa tsayawa har gari y waye,daddy yayi gyaran murya yace dangane da abinda ya samu Aslam ne ba komai yake damunshi ba illah matsanancin ciwon ciki,anan yayi musu bayani dai2 da yadda dr y fada masa,sannan da xabin daya basu. Kowa hankalinsa y tashi,musamman da yaji har ana shirin yi masa aiki,kaka tace to mai xai hana ayiwa mai sunan malam din aure,Abba ne y tari numfashin ta yace to ai hajiya wai Ashe islam yakeso shiyasa yakiyin aure dan baxai iya hadata da wata mace ba a matsayin kishiya. Kaka,aunty amarya da mommy ba karamin mamaki sukayi ba,saboda a iya saninsu ba wani shiri tsakanin islam da Aslam kwata2 basa xama a inuwa daya,kakace tace shi Aslam dinne y fada muku haka,daddy yace eh abokinsa y fadawa amma yace wai jira yakeyi ta gama makaranta. Murmushi kaka tayi tace ai shikenan,yanxu menene shawara,daddy yace jira nakeyi yaji sauki kawai y nemo wata matar y aura,dan inya tsaya jiran islam ciwon xaifi haka tsamari tinda dududu nawa islam din take,in akwai rabo a tsakaninsu ko bayan ta gama makarantar sai suyi aure,aunty amarya tace gaskiya. Kaka ce tayi tsaki,tace naji xancen banxa koku da kuke tsofai2 daku wane y ajiye mata 2,ta kalli aunty amarya tace ke kuma da kika biye masa fadamin wadda acikinku takeda kishiya,to wlh yadda dukkanku bakuda kishiya haka kuma baxa'a iya islam kishiya ba,na yanke hukunci nanda 2 weeks a shirya aurawa Aslam islam kuma kankanta da kuke cewa yanxu mu a kauye sa'ar islam ai tanada da,dan haka na yanke shawara in akwai mai magana sai yayi,mommy tace hajiya hakan yayi Allah y sanya alkhairi,kaka tace ameen,aunty amarya kuwa shiru tayi tana tunanin wannan kwamacalar. Daddy ne yace hajiya munji shawararki kuma mun amince Allah y sakawa auran albarka,amma inaso dan Allah kar wanda y fadawa Aslam ko islam xancen aurannan saboda inaso nayiwa Aslam baxata,kaka ta washe baki tace ai wannan mai saukine Allah yayi muku albarka sukace ameen daganan taron y watse. Aunty amaryace sai juyi takeyi akan gado,saboda tausayin yarda to nawa ma islam take da xa'ayi mata aure,meta sani a cikin rayuwar nan da har in akayi mata aure xata iya kula da mijinta,Abba ne yaga takasa bacci yace wai fateema meya hanaki vaccine,cikin sanyin murya tace wlh Abbn Amir ina tunanin aurannan da xa'a yiwa islam,nawa islam din take da xa'ace xa'ayi mata aure,dan allah kaje ka lallaba hajiya ta janye kudirinta akan aurannan,dan ina tausayawa rayuwar islam,tashi Abba yayi yace haba fateema yanxu kina nufin kinfi hajiya son islam karki manta hajiya ta xabi ran kowa y baci akan ran islam y baci,ni a ganina kawai muyiwa hajiya biyayya dan bahaushe yace abinda babba y hango yaro ko y hau bishiyar rimi baxai hangoba,addu'a xabin alkhairi ita y kamata kiyi ba damuwa ba,sai aunty amarya taji dadi a ranta saboda duk maganar da Abba y fada gaskiya ne tace toh Allah y xaba abinda yafi alkhairi,Abba yace ameen ko kefa. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘. (14/11/2016 3:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *62* Sai 11:00pm Aslam y farka,a hankali y fara bude idonsa ganin dakin dayake shine y sakashi fara kallon dakin a hankali,Amir da safwan y gani a xaxxaune kallansu yayi yace meya kawoni nan,da sauri Amir y futa kiran limits safwan kuwa matsawa yayi,yana cemasa sannu y jikin,Aslam yace kaini fa bangane ba lokacin Amir suka shigo shida dr. Matsawa jikin gadon dr yayi yace captain A.U Abdul kadeer y jikin Aslam yace ba inda yakemin ciwo sai rashin kwarin jiki,dr yace ai dama hakan xai faru yanxu ga magungunan da xaka shanan in kaci abinci cikin sanyin jiki Aslam y girgixa kai dr y futa. Amir ne y mike yace bari naje gda na dauko tea flask da abinci yanxu nadawo,safwan yace toh,bayan futar Amir,Aslam y kalli safwan yace meya kawoni asibiti,safwan yace muma mun dawo daga gurin walimar su islam mukaxo muka tarar dakai a kwance a kasa ko numfashi bakayi,sai lokacin Aslam y tuno da matsanancin ciwon cikin daya turnike shi,cikin fargaba yace to su waye suka kawoni asibiti,safwan yace nida Amir,wata doguwar ajiyar xuciya Aslam yayi yace tnx god,safwan yace amma su Abba sun biyomu daga baya,dan su dr ma yayiwa bayanin abinda ke damunka,xaro dara2 idanunshi yayi gaba cikin kidima yace shikenan na kade har ganyena yanxu bani da dalilin da xan fada musu su kyaleni banyi aure ba harna kai 30 years,dariyar shakiyanci safwan yayi yace gashi dr yace in anaso ka rayu ayi maka aure a kurkusa,cikin kufula Aslam yace dayake shine da rayuwar tawa,shiru kowa yayi yana tunani a ransa,Aslam kuwa tunani yakeyi shi yanxu in ance y futo da mata y xaiyi don haryanxu baiga mace irin choice dinshi ba,after 20 minute Amir y dawo dauke da tea flask da food flask,tea kawai Aslam yasha saboda a yanda yakejin ransa ba abincin da xai iyaci,yana gama shan tea yasha magani y kwanta bawai don baccin yakeji ba,sai don kawai yanaso y samu sassauci a ranshi. Washe gari,daddy,Abba,kaka,mommy,aunty amarya sukaxo duba shi,sun masa y jiki yace da sauki,kaka cikin xaulaya tace nida harna tanadi geron gumba,sai kuma naji ka tashi,kowa dariya yayi a dakin,Aslam kuwa yake kawai yakeyi don yana tsoron hukuncin da daddy xai yanke masa,sai 12:00pm sannan su mommy suka tashi tafiya don su Abba sun dade da tafiya kasuwa,Amir ne y tafi mayar dasu. Misalin 2:00pm Amira ce ta shigo tace sis ki taso xamuje asibiti kaiwa su yaya Aslam abinci daganan mu duba jikinshi,tsaki islam tayi ta gyara kwanciya tace wlh baxani ba,ke bari kiji indai har sainaje duba hero xai warke to wlh sai dai yayita fama da jinya,tsaki Amira tayi tace kada Allah yasa kijedin ta fice suka tafi dayake yaya haidar ne xai kaisu. Yau kwanan Aslam 3 a asibiti,amma ko sau 1 islam bata tabayin tunanin xuwa ba,yauma xaune take tana game a t.v kaka ta futo xata tafi asibitin tace islam taso muje kema yau ki duba mai sunan malam,islam ta yatsine fuska tace ash kaka Allah kaina yake ciwo,kaka tace amma kike wannan latse2 islam ta tashi ta kashe game din tace kwanciya xanje nayi tai shigewarta daki,tana cewa Allah y kiyaye naje duba mugunnan. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/16, 5:02 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: (16/11/2016 1:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *63* Kaka suna futowa sukayi clashing dasu Aslam an sallamosu,kaka ce ta karasa tana washe baki tace gawa taki rami,tunda kace dai baxamuci gumbar nan ba dole na fitar da geron na bayar sadaka,tunda wanda na ajiye dominsa y mike,dariya safwan yayi yace kuma kaka wlh dama na dade banci gumba ba,wani mugun kallo Aslam y jefeshi dashi,Amir kuwa murmushi yayi saboda dama shi bamai yawan magana bane,part dinsu suka wuce kaka ma ta wuce nata. Bayan sun shiga bedroom din Aslam,bandaki Aslam y shiga yayi wanka bayan y futo y shirya safwan ma y shiga abinci aka kawo musu bayan sun gamaci,aunty amarya da mommy sunxo sun dada duba jikin Aslam,haka yaran gdan sunata shigowa har tasleem amma ba islam ba alamarta. Cikin xaulaya safwan yace abokina nifa banga jerry dinka taxo dibiya ba dukkuwa da safa da marwan da yaran gdannan sukeyi,Aslam ne y daga gira daya yace so what,dama banaso taxo dannasan in taxo ba alkhairi ne xai kawota ba,shiru safwan yayi yana jadda irin taurin xuciya irinna islam,ace gata yar karamar yarinya amma kwata2 batasan yafiya ba,Aslam ne y katse masa tunaninsa ta hanyar magana yace wlh ni babban abinda nake tsoro bai wuce irin hukuncin dasu daddy xasu yankemin ba,dan tunda kaji sunyi shiru to Allah ne kadai yasan abinda suke kullawa,murmushi safwan yayi yace karka damu abookina insha Allah duk hukuncin da xasu yanke baxai maka tsauri ba,Aslam yace Allah yasa,safwan yace ameen daganan sukaci gaba da hira. Bayan sallar isha'i su Aslam suna xaxxaune suna hira wayarsa ta fara ringing,ganin wanda yake kiranshi shine y haddasa masa faduwar gaba cikin sanyin murya y daga,dagacan bangaren daddy yace kaxo yanxu ka sameni a palo na,Aslam yace to y katse kiran,kallan safwan yayi yace ta faru ta kare,safwan yace anwa mai dami 1 sata meya faru,Aslam yace daddy ke nemana yanxu,safwan yace toh Allah yasa kajiyo alkhairi,tsaki Aslam yayi yace y wuce yamin xancen aure ni wlh tunanin yarinyar daxan aura nakeyi dan duk kano banga tsarata ba (nikuwa nace karyane 😏) gashi bankai 30 year dinba,safwan yace toh nan da kakai 30 year ai in Allah y nufa munada baby kenan ko y tuntsire da dariya,harararsa Aslam yayi yace dadina dakai kai banxane wlh yayi tsaki y fice,dariya safwan yayi yace naji. Aslam ne xaune a gaban daddy,Abba,kaka,aunty amarya,mommy,daddy yace ba sainayi dogon bayani akan rashin lfyrka ba saboda kasan mai yake damunka,haka muma munsani dukkuwa da tsawon lokaci daka dauka kana boyemana,to yanxu muda iyayenka mun yanke hukuncin aurar dakai,kuma basai kayi tunanin nemo matar aureba,nariga nayi shawara da wani dan'uwana aminina kuma abokina xamu hadaku aure da yarsa,lokaci guda komai na Aslam y tsaya cak nayan mintuna wani gumi neya fara karyo masa,dukkuwa da sanyin a.c da yake dakin,daddy ganin yanayin da Aslam y shiga shine y sakashi murmushi don duk a tunaninsa y shiga wannan halinne saboda xa'a rabashi da islam. Aslam kuwa a ranshi cewa yakeyi yanxu da girmana xa'amin auran dole,bama wannan ba dama anawa namiji auran dolene,tuni kanshi y wani sara masa,idanuwanshi suka yi jajawur gashin jikin shi duk y tashi,daddy ne yace kuma dududu yanxu aurannaku saura 9 day,cikin raxana Aslam y dago rinannun idanuwansa y saukesu akan daddy,daddy yace yarinyar bata kasarnan tana calfonia tana karatu,ranar da xata dawo shiyayi dai2 da ranar daurin auranku,cikin sanyin murya Aslam yace toh dan baxai iya ja da hukuncin da daddyn sa y yanke a kansa ba,daddy yace ko kanada magana girgixa kai Aslam yayi dan yadda xuciyarsa take masa tukuki da xafi baxai iya magana ba,daddy yace toh Allah y yima albarka dukka dakin sukace ameen. Aunty amarya kuwa wani mugun tausayin Aslam taji saboda ganin irin yanayin daya shiga,da tana da dama babu abinda xaisa ta hana afkuwar aurannan to itama anfi karfinta ne,dady y kalli su Abba yace akwai mai magana sukace a'ah,kaka ce ta washe baki tace Abu yayi kyau Allah yayi albarka y sanya alkhairi,kowa yace ameen,daddy yacewa Aslam xaka iya tafiya,tashi yayi wani mugun jiri yaji yana kwasarshi ahaka dai y futa yana hada hanya ikon Allah ne kawai y kaishi dakinsa,saboda yadda idanunsa yake ganin dishi2. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/16, 5:02 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: (16/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *64* Yana shiga bedroom din ko sallama baiyi ba y fada kan gado y dafe kansa,saboda yadda yake baraxanar tarwatsewa,safwanne ganin yanayin da abokinnasa y shigo dashi,y sashi yin magana yace y dai aboki wai meya farune. Sai da Aslam ya dauki 3 minute sannan yace su daddy ne suka yanke hukuncin yimin auran dole,cikin raxana safwan y xaro idanunsa waje yana auran dole y nuna irin baisan komai dinnan ba,a ranshi kuwa yana addu'a Allah yasa da islam xa'a hada abokinnasa dan sunyi bala'in matching halinsu nedai da banbanci,Aslam y dago rinannun idanuwan shi y saukesu akan safwan yace eh,cikin jimami safwan yace toh wace yarinyar da aka hadaka da ita,Aslam yace nima ban santa ba amma yar gdan abokin Abba ce a colfonia wai take karatu,cikin mutuwar jiki safwan yaji bada islam xa'ayi auran ba yace toya sunanta daga kafada Aslam yayi yace nima bansani ba dan yadda hankalina y tashi ko tambayar sunanta banyi ba,safwan yace kayi hakuri kayi musu biyayya insha Allah baxaka tabeba xakayi alfahari da aurannan gaba,tsaki Aslam yayi yace to xancen yaushe ma bikinfa wai saura 9 day,dariya safwan yayi yace ah kace mun kusa angwancewa lallai ranar xamu kwashi shokii,harararsa Aslam yayi yace uban wane xaiyi wani bidiri a bikin,safwan yace wlh baka isaba dole muyi bikin da xa'a gani a kara gani,kai y kamata ma tun yanxu mu fara rubuta preparation din da xamu gudanar,wani malolon bakin cikine y turnike Aslam ganin safwan ma murna yake da aurannan,yace da ubanwa xakayi preparation din safwan cikin jin dadi yace to duk duniyar nan akwai wanda y kamata ayi shirye2 bikinsa dashi daya wuce ango,a xabure Aslam y mike jin safwan y kirashi da ango don saiyaji tamkar y burma masa wukane,wani naushi y kaiwa safwan da sauri safwan y goce yana dariya y fice a dakin da gudu yace bari naje nayiwa Amir albishir din bikin babban yaya,y fice a dakin,Aslam kuwa gini y nausa y koma y fada kan gado shi kadai yasan irin wulakanci da rashin mutuncin daya tanadarwa yarinyar nan tunda tayi gigin yarda ta bata masa dukkan plan dinsa,wani murmushine y subuce masa tunawa da ixayar daxaiwa wannan amaryar mara rabo. Washe gari mommy da kanta takirawo mai gyaran jiki a waya tanaso xatayiwa yarta gyaran jiki na 8 day sukayi xata xata bata 50k har kunshi mommy tace toh yau takeso a farayiwa amaryar amma bataso ta nunawa amaryar saboda aure xa'a yimata gyaran jikin,mai gyaran jikin tace toh. 2:00pm mai gyaran jiki taxo mommy da kanta taje dakin kaka ta tahoda islam tun a hanya mommy tace yata saboda kokarin da kikayi a makaranta nasaka mai gyaran jiki taxo tayi miki saboda inaso ki dadayin kyau,baki islam ta washe tace kai ammafa mommy naji dadi ngd ni kadai xa'a yiwa ba Amira mommy tace eh sai an gamayi miki na 8 day sannan xa'a yiwa Amira cikin jin dadi islam tace toh suka karasa part din mommy,wani empty room mommy ta basu anan aka fara gyaran jiki sai da suka dauki 3 hour sannan suka gama tuni islam ta dauki wani kyalli da sheki banda fitinannen kanshin da takeyi sakamokon hadadden turaren jiki na amare da mai gyaran jikin ta turara mata,islam kuwa sai dariya takeyi saboda yadda skin dinta ta kara kyau da sheki,ita kanta mai gyaran jikin masha Allah kawai take cewa saboda ganin yadda ayi daya islam tayi mugun kyau,kunun hulba ta dama mata islam sarkin kwadayi taji madara da suga aciki kamar xasuyi magana da wuri ta shanye aka xuba mata xumima shima shanye shi tayi tana tande baki 😋,mai gyaran jikin ta kalli islam tace toh yata daga yanxu ta futo da wani sabulu tace da wannan xakina wanka sannan ta dauko humrah 2 tace wannan a ruwan wankanki na daurayar karshe xakina sakawa in kin futo kuma saiki mulke jikinki da wannan ki barta ta bushe a jikinki,cikin jin dadi islam tace toh domin dama akwai son kanshi,mai gyaran jikin tace banda yawo a rana indai kinaso gyaran jikinki yafi haka kyau,in futarma ta xama dole to ki dinga saka katon hijab da nikaf,islam tace a'ah ba inda xani aidama hutu mukeyi,murmushi mai gyaran jikin tayi tace toh nixan tafi sai gobe islam tace Allah y kaimu aunty ki gaida gda,mai gyaran jiki tace gda xaiji. A palo suka hadu da mommy tace hajiya mungama saikuma gobe,mommy tayi godiya tace Allah y kaimu,islam ce ta futo tace mommy ta y kika ganni,mommy tace masha Allah yata kinyi kyau kinji yadda kike kanshi,wani farr islam tayida ido tace kuma mommy har humrah masu kanshi ta bani tace nadinga shafawa inna futo a wanka harda sabulun wanka ma,mommy tace toh ki dinga boyewa kar Amira ta karar miki tunda itama in an gama miki xa'ayi mata,islam tace toh sannan tace mommy ta bani wasu Abu masu dadi nasha,mommy tayi murmushi tace toh ai suma dukkansu na gyara jikine,islam tace toh ta fice,mommy kuwa murmushi tayi don tasan duk daran dadewa dole Aslam yayi alfahari da auran islam don yarinya ce mai shiga rai. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/17, 4:25 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (17/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *65* Islam da gudu ta shiga part din kaka jikin Amira ta fada tana 6* y kika ganni,Amira ce tace hmmm wannan kanshin fa wani farr islam tayi da ido ta kashe daya hannunta Amira ta kama tana kallo tace 6* kinga irin kyawun da kikayi gashi sai wani sihirtaccen kamshi kikeyi wai menene sirrinne wata dariya islam ta kyalkyale da ita tace abin sirrine Amira ce tayi narai2 da idonta tace kai 6* bafama haka dake,islam tace mommy ce ta dauko mai gyaran jiki ta faramin shine gift dins tace na kokari danayi a skul,da sauri Amira ta mike tace bari naje wlh baxan yadda ba nima sai tasa anyimin,islam ce ta riko hannun Amira tace kefa banxa ce basaiki jira nagama fada miki ba mommy tace na 8 day xa'amin daganan sai a farayi miki cikin jin dadi Amira tace toh shikenan yanxu naji magana naxata sankai xa'amin islam ta mike tace bari nayi wanka ta shige bedroom dinsu. Bayan ta futo a wanka ta mulke jikinta da humrah sannan ta xauna ta tsantsara makeup wani hadadden swiss lace blouse & skirt ta saka light pink an masa kwalliya da dark pink flowers sannan ga wasu stones da aka jera sai daukar idanu sukeyi ta daura dankwalinta das tamkar nadin gwagwgwaro tasaka fashion dan kunne da sarka silver tayi bala'in yin kyau tamkar wata dan daren 15,fitowa tayi daga bedroom dinsu. Tun kafin ta karasa kamshin ta y isa palon,lokacin yaya haidar na palon kallanta suka tsayayi kaka,yaya haidar,Amira karasawa tayi ta hurawa haidar iska a ido danshi yafi kura mata ido harwani lashe baki takeyi,cikin shagwaba ta fara dire2 tana kai yaya haidar irin wannan kallo haka ai saikasa na kifa,murmushi yayi yace 6* kinga kyawun da kikayi ga wani mugun kanshi da kikeyi tun kafin ki karaso yayi mana sallama,dariya tayi ta koma jikin kaka ta lafe ta kalli kaka tace wai haka kaka,kaka tace eh nikam dabadan nasan ba inda kikaje ba danace wankan inji kikaje akayi miki saboda yadda kika canja lokaci daya,dariya islam ta kyalkyale ta kama kunnan kaka ta rada mata magana,kakama dariya ta kyalkyale da ita saboda tasan kwanan xancen,amma itama cikin kasa2 da murya tace mommy kuwa ta kyauta. Haka kwanaki sukayi taja islam kuwa ta dage da xuwa part din mommy gyaran jiki wataran kafin mai gyaran jikin taxo islam ta dade a part din,mommy kuwa tayita mata dariya,kanshi kuwa y xauna ajikinta don indai ta xauna a guri to sai tabar kamshinta a gurin. Aunty amarya ma ta dage tana gyara yarta,yauma dahuwar kaxa cikin yatsina islam tace nifa aunty amarya wai dan Allah menene wannan abubuwan da kullum saikin bani,naci na kifi da magani,naci na kwai da magani,yanxu kuma gana kaxa kina bani kumafa ni kadai ake bawa banda Amira nigaskiya nagaji dacin magungunannan,ta washe baki tace to dan gwara2 wannan xumarma tunda ita xakine da ita,harararta aunty amarya tayi tace banason surutun banxa kiyi maxa ki cinye ki tashi ki bani guri,xumbura baki islam tayi tana kunkuni buge bakin aunty amarya tayi kara islam ta kwallah tana wayyo nashiga 3 ta fasamin baki,mamakine y kama aunty amarya tace toh kiyi shiru kiji meyasa nake baki komai da magani,cak islam ta tsaida ihunta tamkar daukewar ruwan sama aunty amarya tace maganin bakine bakiga kina dadayin kyau ba ko kinaso bakin mutane y kamaki,murmushi islam tayi ta rungume aunty amarya tace shiyasa nake sonki aunty na,aunty amarya ma murmushi tayi a haka islam ta karashe cinye kaxar tanata xuba surutu ta tashi ta fice. Akwati set 2 akayiwa islam kayan lefe daddy da Abba ne suka bawa su mommy kudi suka hado,kayan sunyi kyau sosai dan english wears ma akwati 4 aka cika 2 wadanda islam xata iya amfani dashi yanxu 2 kuma saita dada girma,boye set 1 akayi wanda y kasance na dai2 islam a yanxu aka mommy ta kirawo Aslam yaxo y gani,lokacin dayaxo ko bude akwatunan baiyi ba yace haba mommy wannan kayan ai sunyi yawa hakan ai asarar kudine,harara mommy ta dakawa Aslam cikin tsawa tace wannan akwatunanne sukayi yawa dududu fa guda 6 ne,ni tashi ka bani guri in baxaka kallah ba,jiki a sanyaye Aslam y mike a ranshi kuwa yana dadajin tsanar matar da xa'a aura masa dan tun tasowarsa mommy bata tabayi mai fada ba amma yau harda tsawa. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/17, 4:26 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (17/11/2016 3:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *66* Islam ce kwance a daki saboda yanxu ta daina futa kwata2 rabonta da gdansu khausar ma yau kwana 5 wanda yayi dai2 da saura kwana 3 daurin auran ta. Khausar ce suka shigo itada Amira kanta suka fada,Amira tace 6* Ashe bikin yaya Aslam xa"ayi cikin mamaki islam tace aure yaya Aslam din xaiyi,khausar tace eh yanxu mukaje mukaga kayan lefen da aka hadawa amaryar kingansu kuwa masu mugun kyau,dariya islam ta kyalkyale da ita tana ta dariyarta harta fado daga kan gado dakyar ta xaida dariyar tace tab ita kuwa wannan yarinyar data yadda xata auri hero wanne irin rashin rabone da ita a duniya,to in banda xabar mata ma ta biyo tarasa wanda xata aura sai wannan mugun tab ta tabe baki tace wlh dana santa da sainaje nabata shawara karta sake ta auri hero ta karasa maganar da kyalkyalewa da dariya. Amira kuwa duk ranta y baci saboda rashin mutuncin da islam takewa Aslam yayi yawa,khausar ce tace nikuwa banga laifin yaya Aslam ba yana da kwarjini sannan ga kyau ga cikar xati,kece dai kawai kike ganin aibunsa kuma dan halinku baixo daya bane,Amira tace wlh fa fada mata dai ai nasan baxaki taba auran mijin dayakai yaya Aslam ba,harara islam ta watsa musu tace wlh karya kukeyi duk abinda kuka fada karya kukeyi yaya sagir yafi hero komai da kuka lussafo,dariya khausar ta tuntsire da ita tace wlh karya kikeyi kawai kin fadane don kiji dadin bakinki,cikin kufula islam ta xari hijabi har kasa tace ni kun tunamin mai sanyina ma bari naje nagansa ko xanji sanyi ta xura katon hijabinta ta fice. A kofar gda tayi kicibis dasu yaya Aslam,yaya safwan,yaya amir cikin sanyin murya tace yaya amir ina wuninku shida safwanne suka amsa,Aslam kuwa tsawa y daka mata yace gdan ubanwa xakije kallon up & down ta jefeshi dashi duk da taga rama a tattare dashi ta murguda masa baki tace inda mutum y aikeni,cikin xafin nama yayi kanta ganin haka da tayi ta daga hijabin ta tace kafa mai naci ban bakiba ta falfala da gudu,dariya safwan y tuntsire da ita yace inason kallon drama dinku da islam,inaga rokon kaka xanyi tabawa amarya ita tayi mata xaman daki,amir kuwa murmushi yayi,Aslam kuwa harara y dakawa safwan yayi tsaki y shige cikin gda. Islam kuwa saida ta shiga gdansu safwan ta tsaya garam ta tura kofar gate ta shiga gdan da sauri baba mai gadi y mike yana rarraba idanu saboda y fara gyangyadi,ganin irin xaburar da yayi shine yasaka islam kyalkyalewa da dariya tace haba baba irin wannan xaburar haka to ba wasu bane nice,shima dariya yayi yace au Ashe yatace tace eh ta gaidashi ta wuce part din sagir. A palo ta tarar dashi y xurfafa cikin tuna I,sadaf2 ta karasa tayi clapping din hannunta firgigit y dawo daga tunanin daya tafi,y saki ajiyar xuciya dariya Islam tayi tace yaya tunanin me kakeyi,murmushi yayi yace tunaninki nakeyi my baby kwana 2 kin haramtawa idanuwana ganinki,kurr y tsura mata ido saboda wani mugun kyau data dadayi ga wani daddadan kamshi da takeyi tunda tashigo dakin y dume da kamshinta,hannu tasa ta rufe idanuwanta tace yaya wannan kallanfa janyota yayi y dorata a cinyarsa yana shinshina wuyanta cikin wata irin murya yace baby na wani mugun kyau naga kinyi ga wani daddadan kamshi da kikeyi nifa ina tsoron wani yamin snatching,murmushi tayi tace yaya ni takace har abada insha Allah,cikin jin dadi yace Allah yasa kallan cikin idanunta yayi yace nifa baby na da xa"a auramin ke yanxu so nakeyi,saina raineki harkiyi candy sannan mufara rayuwar aure,cikin jin kunya ta mike a kan cinyar tasa tace bari naje nagaida mammy daganan nawuce gda dama missing dinka nayi shiyasa naxo ganinka,cikin jin dadi y mike y riko hannunta yace muje naraka ki ki gaida mammy din daganan naraka ki gda,futa sukayi fuskar kowa dauke da farin ciki. Sun shiga part din mammy hannunsu cikin na juna,islam ta gaida mammy sannan suka futa,tausayin sune y kama mammy saboda tasan ba karamin shakuwa sagir da islam sukayi ba saboda aunty amarya ta kirata tamata xancen aurar da islam da xa'ayi itadai tana musu addu'ar Allah y bawa yaran dangana,har kofar gda sagir y rakata ji sukeyi tamkar kada su rabuda juna a hakadai islam ta shige gda tana yiwa sagir bye2. Su Aslam kuwa suna shiga gda tun kafin su karasa part dinsu aunty amarya ta kirashi tace yaxo tanason ganinshi,kallan su safwan yayi yace guys aunty na tana nemana y wuce part din aunty amarya. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/18, 5:54 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: (18/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *67* Da sallama Aslam y shiga part din aunty amarya,kurr ta xuba masa ido saboda yadda taga yayi bala'in ramewa lokaci daya taji wani mugun tausayinsa y kamata,Aslam kuwa ganin irin kallon da aunty amarya takeyi masa shine y sakashi murmushin yake yace aunty na afuwa nake nema wlh abubuwa ne suka shamin kai shiyasa bakya ganina kwana 2,katse shi aunty amarya tayi cikin sanyin murya tace anya my son kanacin abinci kuwa kaga yadda ka rame kuwa gashi dukkayi baki,shafa kanshi yayi tabbas shi kanshi yasan rabon dayaci wani abincin kirki tunda akayi masa xancen aurannan tunaninsa kullum wacce irin yarinya xa'a aura masa. Idanuwansa y dago da suka rune sukayi jajawur lokaci guda cikin sanyin murya yace aunty wlh kwata2 bana iyacin abinci saboda tashin hankalin da nake ciki,kullum tunanina bai wuce wacce irin yarinya xa'a auramin ba,xatayi dai2 da tsarina irin macen danakeso ce wlh aunty ni a tsarina yanxu haka nafison mace yar 25 lokacin nikuma ina 30 year kinga da hankalinta ba wata wauta da datamin muryarshi ce ta sarke sakamakon kukan dayaxo masa,kuka yakeyi sosai,lokaci daya jikin aunty amarya yayi sanyi tunawa da wacce irin yarinya xa'a aurawa Aslam a ranta tace dankari lallai wannan shi ake kira kwado in kuwa hakane sam2 islam bata dace da Aslam ba,dan duk tsarikan daya lissafo na macen dayakeso islam batada ko daya,karasawa tayi gurinsa ta daura kansa a cinyarta shafar gashinsa ta farayi tana fada masa maganganu masu dadi da taushi,tace ni yanxu shawarar da xan baka shine ka yadda da kaddara,domin aurannan yana cikin kaddararka kasani biyayya ga iyaye wajibi ne,domin Allah acikin alqur'aninsa yace (ku bautawa Allah shi kadai,sannan kuyi biyayya ga iyaye)to kaga ko anan y kamata ka gane iyaye sunada daraja tunda Allah y hada biyayyarsu da bautarshi,sannan ka kasance mai hakuri da kawaici duk yarinyar da iyayanka suka xaba maka basuna son cutar dakai bane a'ah gata sukeson yi maka,lokaci daya Aslam yaji duk wata damuwa da kunci dake ransa y tafi,aunty amarya tace alkawari 1 nakeso kayimin ko wacce irin mata aka aura maka baxaka taba xaluntar taba,wani doguwar ajiyar xuciya Aslam yaja saboda yadda nasihar aunty amarya ta ratsashi,yace insha Allah aunty na baxan taba cutarta ba xan xama mai hakuri da yafiya akan duk laifin da tamin,sannan xamuyi rayuwar aure irinta kowanne ma'aurata da sukayi auran soyayya,cikin jin dadi aunty amarya ta rungumoshi tace Allah yayi maka albarka,murmushi yayi yace ameen. Aunty amarya da kanta ta tashi ta shiga kitchen ta xubo abinci a plate,da kanta ta xauna tayi feeding dinshi tana bashi lbrai masu dadi,cikin farin ciki yakecin abincin harya cinye baisan y cinye ba,bude baki yayi aunty amarya ta xura masa cokali,cikin mamaki yace ina abincin lakace masa hanci tayi tace ka cinye a tare suka tuntsire da dariya,aunty amarya tace ko a dado makane Aslam yace a'ah nakoshi,y lumshe ido yace aunty na ngd Allah y kara lfy da nisan kwana,murmushi aunty amarya tayi ta tsiyaya masa lemo exotic a glass cup ta mika masa tana ameen,Aslam yace gaskiya ne da akace wanda y rasa uwa yayi kuka domin shine babban maraya saboda nidai gashi nagani rabona danaci abinci spoon 3 harna manta dan ina faraci xanji yanamin daci,amma yau da uwata ta sakani a gaba gashi harna cinye cikin plate bansani ba,dariya aunty amarya tayi tace my son bakada dama wlh,dariya yayi shima y mike yace bari naje naji preparation din dasu safwan suka tsara saboda yau aunty na ta bani kwarin gwiwa y fice,murmushi aunty amarya tayi ta dauke try din data sako abinci takai kitchen. Da farin cikinshi y shiga part dinsu xaune y tarar da safwan da amir shima xama yayi yana guys wanne shirye2 kuka tsara abikinnawa ne,cikin mamaki suke kallanshi tamkar ba Aslam ba mutumin da yakeyi musu masifa in suna hirar program din da xasu gudanar a bikin amma yau shida kansa yake tambayar su,Amir ne yace kawai mun shirya receiption bayan daurin aure shikenan tunda kace bakasan ayi duk wani Abu dan baxaka halarta ba,yace OK naji yanxu najanye duk wani kudiri na,after wedding fateeha akwai reception yes haka yayi,da misalin 4:00pm sai ayi kilisa a fadamin nawane kudin hayan dawakai,ranar asabar 2:00pm akwai parety da daddare kuma akwai dinner sai a nemo hall mai kyau,cikin jin dadi sukace gaskiya hakan yayi. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/18, 5:54 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: (18/11/2016 4:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *68* Misalin 4:00pm su Aslam suka futa neman hall din da xasu yi reception da dinner dakyar suka samu saboda sunxo a kurarran lokaci,country mall anan xasuyi reception,sai the afficent inda xasuyi dinner aikuwa sunsha kudi saboda hall din manya ne,a gajiye suka koma gda bayan sunyi wanka Aslam da kanshi y kirawo abokanansa yana sanar musu daurin auranshi nan da 3 day aikuwa sai tsiya suke yi masa akan bikin saida yaxo daf xai sanar musu hakuri kawai yake basu yace wlh shima auranne yaxo ba xata sunyi masa fatan Allah y bada xaman lfy kuma insha Allah xasu xo daurin auren,kallan safwan yayi yace ka sanarwa yan photercourt ne safwan yace eh ai har general nasanar masa kuma yace insha Allah xaixo,Aslam ne y cillah masa pillow yace dan rawar kai sukayi dariya a tare. Yau alhamis mai gyaran jiki taxo tayiwa islam sannan tayi mata kunshi ja da baki aikuwa tuni islam tahau kyalli,ga daddadan kanshin da takeyi koya ta gifta a guri saita bar kamshinta,kowa masha Allah kawai yake cewa saboda yadda islam tayi wani sihirtaccen kyau gaba daya kamarta ta canja,mommy ce tace yata futo ki rakani unguwa islam tace toh hijab ta xurma suka fice isya driver mommy tasaka ya kaisu gurin returching islam tace wlh mommy narasa meyasa kawai saina dingajin xuciyata tana bugawa kuma ina yawanjin tsoro murmushi mommy tayi tace kidinga karanta *inna lillahi wa inna ilaihirraji'un*,islam tace toh suka karasa aka yiwa islam returching aikuwa yayi kyau saboda yadda gashinta yadada tsayi har gadon baya ga wani sheki da kyalli da yakeyi ana gamawa suka koma gda lokacin anyiwa Amira da khausar gyaran jiki da kunshi sai dai nasu baikai kyanna islam ba gwalo islam tayi musu tana cewa yeah nafiku yin kyau ko kunshina yafi kyau,cikin jin haushi sukace eh munji don sunsan ba karya islam tayiba. Yan'uwa sun xaxxaxo kowa yaga islam saiyace islam irin wannan kyau haka ko yar gda xa'ayi keda Aslam din cikin jin haushin maganarsu take cewa Allah y kiyaye mexanyi dashi,ganin kowa yaxo haka yake cewa ko itace amaryar cikin kuka ta tafi gurin kaka tana ihu dakyar kaka ta lallabata tayi shiru tace waya tabaki cikin xumburo baki islam tace ba mutane bane dan sunga nayi kyau shine suke cewa wai ko nice amaryar hero nikuwa nace mexanyi dashi Allah y kiyaye ta karashe maganar da murguda baki,murmushi kaka tayi tace rabu dasu karki kara kulasu wasa sukeyi miki islam tace toh ta tashi ta futa,kaka kuwa murmushi tayi saboda yadda tasan irin darun da xa'ayi kafin islam ta yadda da aurannan. Islam ce kwance kan gado sai juyi takeyi sakamokon yadda taji duniyar duk tayi duk taji ranta a jagule,Amira da khausarne suka shigo dakin cikin murna suna kiran islam 6* ganin islam a kwance khausar tace tashi kika kayan mu ke naki mommy tace gobe xata baki,cikin masifa islam tace dan Allah karku dameni ku kyaleni da abinda ke damuna,Amira tace kayan bikin yaya nefa kuma kowa set 5,tsaki islam tayi tace ku bikin hero y dama da harxaku tashi hankalinku dan an baku kayan anko set 5,tayi tsaki ta gyara kwanciya,sukuwa cikin murna suka gwargwada kayannasu lace 2,material 1,atamfa 1,shadda 1,suna gama gwadawa suma suka kwanta,islam kuwa sai juyi takeyi sam ta kasa bacci tashi tayi ta shiga bathroom ta dauro alwala ta shimfida sallaya tayi nafila raka'a 8 ta dade a sujjadar karshe tana addu'a Allah y sassauta mata xafin xuciyarta sannan bugawar da kirjinta Allah yasa lfy ne,koda ta idarda sallah a sallayar ta xauna taci gaba dajan carbi saboda sam batajin bacci,bacci barawo dai shine y sace islam kan sallayar. To jama'a kuna ganin alkawarin da Aslam yayiwa aunty amarya xai iya cikawa idan yaji islam ce matar tashi ko kuwa dai xai karya alkawarin kuci gaba da biyoni donjin yadda xata kaya. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/19, 8:30 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (19/11/2016 7:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *70* Mai kwalliya ta nada mata dan kwali tamkar nadin gwargwaro,inda ta xubo mata da wani gashin ta gaba har kafadarta y sauka,ragowar kuma aka sakeshi ta baya y sauka har gadon vayanta,wayanta mai kwalliyar ta dauko ta fara gyarawa islam pics,gaban dressing mirrow islam ta tafi wani dadine y mamaye mata xuciya saboda irin kyawun da tayi itadai tasan tunda uwarta ta haifeta bata tabayin kyau irinna yau ba,mommy kuwa masha Allah kawai take cewa tace daughter na kinga kyawun da kikayi tamkar zarah acikin taurari,islam cikin jin dadin furucin mommy tace yauwa mommy bari naje nanunawa su khausar kwalliyata in musu gwalo nasan nafisu yin kyau,hannunta mommy ta kamo tace a'ah bari naje na turo miki su ko kinaso ki futa mutane suyita tankaki,cikin gasgata maganar mommy tace a'ah ta koma kan kujerar dressing mirrow ta xauna tanata faman murmushi inta kalli kanta tacikin mirrow mommy kuwa kai ta girgixa ta fice. Aslam kuwa suna futa kofar gida,dubunnan cincirindon mutane ne a tsaitsaye,kamada masu fada aji a gwamnati,yan kasuwa,sannan da manya2 sojoji harda kananu,saboda ance a nan kofar gdan xa'a hadu aje gurin daurin aure,a hankali Aslam yaga mutane suna shiga cikin masallacin unguwarsu,a ranshi yace kenan yarinyar da xa'a auramun yar unguwar nan ce,ras girjinshi y buga tunawa da yayi kaf layin ba yarinya datafi 18 year dukkansu daga 18 year ne xuwa kasa,cikin sanyin jiki y fara daga kafa y tafi domin karasawa masallacin turus y tsaya sakamakon jin maroki na sanar da auranshi kamar haka an daura auran *umar Abdul/khadeer umar* tareda amaryarshi *Aysha aliyu umar* akan sadaki naira 50k lakadan ba ajalan ba ras2 dam daran dam kirjin Aslam y buga sakamakon jin sunan amaryar da aka daura masa aure da ita. Cikin firgici yajanyo hannun Amir,yace kaji sunan yarinyar da aka daura aurannan kuwa kar daifa da aljanar yarinyar nanne,murmushi Amir yayi tunawa da abinda safwan y fadawa su daddy,amma yace anya bana tunanin da islam aka daura maka aure nafi tunanin mai irin sunanta ne,ajiyar xuciya Aslam kawai yayi amma xuciyarshi tana soko masa islam a matsayin matarsa,runtse idanunsa yayi saboda irin yadda xuciyarsa take tafarfasa,mutane sai xuwa sukeyi sunayi masa Allah y sanya alkhairi yake kawai yakeyi amma jinsa yakeyi tamkar y karma ihu,wata xuciyar ce tace haba Aslam a yadda iyayanka sukasan lalurar da kake fama da ita menene xai saka su aura maka wannan yar tatsitsiyar yarinyar da wannan tunanin yadan ware har aka tafi wurin reception amma kowa y kalleshi xai hanko tsantsar damuwa da firgici a tattare da Aslam,su safwan kuwa sai raba get pass na dinner din da xa'ayi gobe 8 o'clock. Haka aka tashi a reception dinnan Aslam ko ruwa y kasa sha sai tsaki dayake ta jerawa yafi 1000,bakin da sukaxo daga nesa suka fara jigilar kaiwa masauki basu gama basu masauki ba sai 2 oclock kuma gashi 4 o'clock xa'ayi kilisa gashi daddy yanata kiran wayarshi yaxo yanason magana dashi. Islam ce dasu khausar suna hira,cikin farin ciki domin islam ita tama manta da ana biki a gdan,saboda kwata2 basajin wata hayaniya,mommy ce ta shigo dakin cikin farin ciki ta kallesu,akwatunan lefe ta bude ta daukowa islam wani hadaddan takalmi milk color mai dan tudu hadeda mayafi shima milk tace my daughter xoki saka takalmi da mayafi dadynku na nemanki,islam ko a jikinta taje ta saka takalmin domin lokacin da mommy take debo kayan hankalinta baya gurin,tace mommy takalmin kuwa mai kyau tana washe baki,murmushi mommy tayi ta mika mata mayafin tace yafa muje ana jiranmu,islam ta karbi mayafin ganin ta yafashi y sauka harkasa shine y sakata yin dariya tace mommy ai yamin yawa kawai mutafi a haka,mommy tace a'ah yafa a haka muje cikin xumbura baki tace kawai ni mayafinnan xai batamin kwalliya suka futa. Kan islam a kasa suka shiga palon daddy,lokacin ma Aslam kanshi yana durkushe y lula acikin tunani kwata2 baisan shigowar su islam ba,daddy ne yace toh Aslam ayau Allah y nuna mana auranka,sai lokacin Aslam y dago kai a lokacin kuwa islam ta durkusar da kanta tana cewa a ranta to waini menene nawa da xa'a kirani akan maganar auran hero to waima ina ruwana da matarshi nidai kawai abinda nasani shine in matar itama batada kirki to kuwa xamusa kafar wando1 da ita don baxan kyaleta ba,Aslam kuwa karamin tsaki yaja yace yanxu wannan ce matar tawa,daddy ne y katse musu tunaninsu ta hanyar cewa Aslam ayaune dubunnan mutane suka shaida daurin auranka kaida yar'uwarka islam,munayi muku fatan alkhairi Allah y baku xaman lfy,cikin furgici da raxana sika dago idanuwansu Aslam kuwa cikin sarkewar harshe y maimaita islam. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/19, 8:30 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (19/11/2016 11:00am) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *69* Da asuba dakyar islam ta iya tashi tayi sallah,tana idarwa kuwa ta koma kan gado wani daddadan baccine y kwasheta. Karfe 9 o'clock kowa y shirya a gdan cikin shadda purple colour harda kaka,inda maxan sukayi ankon brown colour,islam kuwa tana can tana sharar baccinta duk da hayaniyar data cika gdan ita sam batasan anayi ba,mommy ce ta tambayi su Amira ina islam,sukace tana daki tana bacci cikin mamaki mommy ta tafi part din kaka. Kwance ta tarar da islam tana kudindune acikin blanket tanata sharar baccinta,murmushi mommy tayi ta karasa ta fara tashinta a hankali islam take ware idanuwanta tana budesu tayi mika tayi salatin annabi,sannan ta karanto addu'ar tashi daga bacci,mommy ce tace haba islam wanne irin bacci kikeyi gashi har 9 tayi,bayan kinsan yau ana biki a gdannan,cikin xumburo baki gaba tace haba mommy yanxu akan bikin hero xaki katsemin bacci ni gaskiya baccin bai isheni ba ta koma ta kwanta,murmushi mommy tayi tace haba daughter na ki daure ki tashi muje part dina ki shirya kema kinji,fafur islam taki saboda ita a ganinta babu dalilin da xaisaka tayi wani farin ciki a bikin wanda yake xaluntar ta,shiyasa ma tayiwa kanta alkawarin ba ita babu wanka har sai an gama bikin,dakyar da sidin goshi mommy ta lallaba islam ta tashi suka tafi part dinta dan mommy tace in sunje can tayi wankan. Sanye take da sleeping dress purple colour doguwar riga mai santsi gashinta duk y barbaxu,mommy rike da hannunta,su Aslam ne suka futo a part dinsu Aslam,safwan,Amir,sanye suke cikin milk colour shadda sai kyalli take an yiwa shaddar aiki da brown xare,hularsu zanna bukar brown anyi mata kwalliya da milk xare,takalminsu shima brown mai dan yatsa kowa yana sanye da agogo sai balala kanshi sukeyi tamkar sumfuto daga company turare,wani kallo islam ta jefesu dashi ta watsar ita saitaji ma duk haushin su takeji gaba daya,cikin kunkuni tace aikin banxa watako su murna sukeyi harda yin anko Allah yasa amaryar daxai aura katuwa ce in yayi mata mugunta ta xaneshi (nikuwa nace kuruci dangin hauka tayaya mata xata daki miji 😂) Aslam kuwa wani faduwar gaba yaji y rasa meyasa yau dayaga islam yaji wani Abu yanayi masa yawo sai yaga tayi masa mugun kwarjini ga wani mugun kyau da tayi binta yayi da kallo itakuwa ganin irin dayake mata shine yasa ta daka masa harara ta murguda masa baki,a haka suka karasa suka gaida mommy,islam kuwa ko kallansu batayi ba ballantana su safwan su samu darajar gaisuwa haka suka fuce daga gdan su islam kuma suka shige part din mommy. Suna shiga mommy da kanta tashiga bathroom ta hadawa islam ruwan wanka,10 minute ta dauka sannan ta futo lokacin mommy ta hado mata break fast haka islam tafara cin abincin tana xubawa mommy surutu,can tace yauwa mommy ina kayana jiya kin bawa su amira nasu,murmushi mommy tace ki bari ki gama break fast din yananan na boye miki,20 minute islam ta dauka acin abincin saboda yadda taketa surutu tamkar ta an bude gdan radio,mommy ce ta futa can suka shigo itada wata matashiyar budurwa xatakai 25 year tana dauke da wani dan kit,mommy tace ga wadda xakiyiwa makeup din,cikin kwarewa ta fara tsantsarawa islam kwalliya cikin 30 minute ta gama mata,wata dankareriyar shadda pink colour mommy ta daukowa islam gown ce rigar tasha surfani daga sama har kasa sannan ansaka stone ajikin surfanin,cikin mamaki islam take kallan mommy tace mommy yanaga shaddata ba irin taku ba,murmushi mommy tayi tace eh aike nafiso kifiyin kyau bakiga har mai kwalliya na dauko miki ba,cikin jin dadi islam ta tashi tasaka rigar das kuwa tayi mata. Wani dankunne da sarka na gold mommy tasawa islam harda bangles da xobe,mai kwalliyar ta nada mata dankwalin tamkar nadin gwargwaro ta xubo mata wani ta gaba ragowar kuwa y xuba har gadon baya. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/21, 4:17 PM] ‪+234 703 751 0996‬: (21/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *71* Lokaci daya xuciyoyinsu suka buga cikin firgici da tsantsan tashin hankali suka dago idanunsu suka sauke akan daddy,Aslam cikin tsananin tashin hankali da rawar murya y maimaita islam,islam kuwa tashi tayi ta kurma uban ihu ta koma ta dire shure2 ta farayi ta tumbuke daurin dankwalin,ihu takeyi tana wlh ita batason Aslam yama xa'ayi a rasa wanda xa'a aura mata sai wannan mugun,ita wlh tayi kankanta da aure cikin karajin kuka taci gaba da magana to in auranma xa'a min ba sai amin aure da sagir ma,cikin tsananin mamaki kowa yake kallanta yadda take ihu tamkar wadda xa'a cirewa rai,kara birkicewa tayi ta koma ta kwanta tana itafa sam asan yadda xa'ayi da ita yama xa'ayi ace wai itace matar hero ita yadda ta tsani hero hartafi son mutuwar ta ita gwanda a aura mata maciki tasan saranta xaiyi da ace herone mijinta,cikin tsananin jin haushin furucinta Abba y tashi yayi kanta xai daketa daddy ne y rikeshi yace ka kyaleta mune masu babban laifi dabamu tuntubesu ba muka yanke hukunci,Abba yace to islam din har nawa take da xa'ace baxata iyabin umarnin muba. Aslam kuwa tsantsar bakin cikine y hanashi magana in banda uban gumi da yake hadawa,lallai yarinyar nan harni xatace data aureni gwanda auran miciji,tuni idanunsa suka rune sukayi jajawur gashin jikinshi duk y tashi,jikinshi y fara rawa a kome y tuna kuma oho saina yayi wani malalacin dariya. Daddy ne yace uwata kiyi shiru bari tunda ke kin fadi ra'ayinki akan aurannan bari muji me yayannaki xaice in shima baya sonki saiya sauwake miki yanxu,cikin danjin dadi ta sassauta kukanta dan tasan Aslam ko giyar wake yasha baxai taba cewa yana sonta ba,daddy ne y kalleshi yace kai mexakace akan auran dakyar y daidaita nutsuwarshi don bayason su gane maganar da xaiyi ba gaskiya bace yace ai daddy tunda an riga an daura auran to inason matata daba a daura bane xan iya hakura ta auri wanda take so amma yanxu kam baxan iya sakin matata ba y dada sunkuyar da kanshi domin karsu gane plan ne abin,sukace to Allah yayi maka albarka,wata xabura islam tayi ta mike tana nunashi da dan yatsa sam ta kasa magana,can kuma ta tuntsire da dariya tace wlh karya kakeyi munafinci ne kwata2 baka sona sam *ni da kai* bamu daceba,sai kuma ta barke da kuka dago idanuwansa y jefeta da wani shegen kallan kiyayya,a ranshi yace da wayace miki *ni da ke* mun dace tamkar yadda kikace kinfi kaunar maciji akan aurena to saina shayar dake gubar bakin ciki saina jefa xuciyarki acikin kiyayyar maxa harshi wanda kikayi ikirarin kina sonshi,daddy ne y katse shirun yace to Allah yayi muku albarka ke yanxu islam wanda ikon sakinki yake hannunsa yace baxai iya sakinki ba don haka saikiyi hakuri kiyi biyayya Allah y baku xaman lfy,xaku iya tafiya a sukwane islam ta kwasa da gudu ko takan dankwali batabiba balle mayafi ko takalmi,Aslam ma ficewa yayi,sukuma iyayan suka xauna tattauna ta yaya hakan ta faru,anan kaka ta labarta musu irin rashin jituwar da take tsakanin Aslam da Islam,cikin tsananin mamaki su Abba sukace yaushe al'amarinnan yake faruwa su sam basu sani ba,kaka tace tun lokacin da islam ta koma gurina suke wannan rashin jituwar daddy yace Allah y kyauta sukace ameen taron y watse. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/21, 4:17 PM] ‪+234 703 751 0996‬: (21/11/2016 2:30pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *72* Islam da gudu ta wuce mutane tana kungin kuka ita ko takan mutane da suke kallanta batabi ba direct dakin mommy ta wuce ta fada kan gado tana kuka sosai,cikin tsananin firgici su khausar suke kallanta tambayarta sukeyi menene y faru amma sam taki magana sai kuka da takeyi tana ta shiga 3 ta lalace shine abinda kawai yake iya futowa acikin bakinta,mommy ce ta turo kofar kana kallon fuskarta xakasan akwai tausayi aciki su Amira ne suke tambayarta me akayiwa islam domin suma xuwa lokacin harsun fara hawaye kallansu tayi tace kuje waje ku jirani tashi sukayi suka futa jikinsu duk a sanyaye,bin bayansu mommy tayi tasawa kofar key ta dawo. Dawowa mommy tayi ta janyo islam ta rungumeta,shafa bayanta ta farayi a hankali sautin kukannata y fara raguwa xuwa can kuma mommy taji saukar numfashi a hankali,dubawa tayi taga islam hartayi bacci komar da ita tayi ta kwantar taje ta bude kofar takira su Amira tace su xauna mata da islam inta farka suxo su kirawota. Aslam kuwa part dinsu y shige direct dakinsa y wuce tsaki yayi ganinsu safwan suna dakin wucesu yayi ko magana baiyi musu ba y cire babbar rigar jikinshi y balle bottle din ta ciki y cire y daura towel y shige bandaki y sakarwa kanshi shower ko xaiji saukin xafi da radadin da xuciyarshi takeyi masa,haka yadauki tsawon 20 minute y futo yana tsane kanshi da towel mai y xauna y shafa sama2 armless y saka da short nikker y kwanta y runtse idanuwansa,safwanne yace haba ango kasha kanshi ya xaka saka wadannan kayan bayan kasan yau ranarka ce mu bama ka fada mana wace amaryar taka ba,y karashe maganar da dariyar shakiyanci,banxa Aslam yayi dashi domin yasan yadda xuciyarsa take tafarfasa xai iya yiwa safwan komai akan maganar nan daya fada masa,y dada runtse idanunsa xuciyarsa kuwa banda furucin islam da yakeyi masa amsa kuwa a kunne inda take cewa *wai itace matar hero ita yadda ta tsani hero hartafi son mutuwarta akan shi,ita har gwanda a aura mata maciji tasan saranta xaiyi da ace hero ne mijinta*,runtse idanuwansa yayi da karfi y mike cikin karaji yace wlh karya kikeyi xakiyi danasanin furucin da kikayi a gareni sai gdana y xame miki kabari saboda duhun da bakin cikin da xaki tarar warwaxa gashin kansa y farayi tuni yahau jifa da komai y dauka (nikuwa nace tab ran maxa y baci allurar sojoji ta motsa)da sauri su safwan suka matsa suna subhanallah mai yayi xafi haka jikinshine y koma yana bari tamkar dan gangi,a hankali Amir y fara magana haba big bros abinda hakuri bai bayarba rashinsa baxai taba sakawa ba daga yadda naji lafuxanka hakan yana nuni akan matar da aka aura makace karka manta biyayya ga iyaye wajibice kuma mai yinta baxai taba tabewa ba,karka manta aljannarka tana karkashin iyayanka kaga kuwa komai na duniya mai saukine tunda xamane na temporary kayi kokari ka gyara permanent dinka ma'ana lahirarka tayi kyau,a hankali Aslam yaji hankalinshi na kwanciya xuciyarshi tana rage radadi sai kuma y fara kuka wiwi tamkar karamin yaro kyaleshi sukayi saboda sunsan hakanne kawai xai rage masa xafin xuciya,safwanne yayi karfin halin magana yace haba Aslam y kakeyin kuka saikace ba namiji ba abinda bakayi shi a filin yaki ba sai yanxu akan cammond karamin Abu xaka tashi hankalinka rinannun idanuwansa Aslam y ware akan safwan yace cikin dashashshiyar murya auran yarinyar nanne karamin Abu kasan kuwa wa aka auramin to ba kowa bace illah aljanar yarinyar nan ta wajen kaka,wani dadine y lullube safwan domin yasan duk daran dadewa sai Aslam yaso islam. A hankali islam take bude idanuwanta jin yadda kanta yayi mata nauyi a hankali abinda y faru daxu y fara dawo mata,su khausar basusan tashinta ba sai kukanta sukaji da sauri khausar ta tafi kusa da ita Amira kuma ta tafi kiran mommy. *assalamu alaikum plz masoyana kuyimin hakuri narashin samun posting jiya hakan y farune sakamakon unguwa da naje,sannan masu kirana suji lfy ngd masuyimin massage kuma ngd sannan dan Allah wadanda sukaga sunyimin massage banyi reply ba kuyi hakuri ba'ason raina haka ta faruba sai don matsalar da wayar take bani wani lokacin massage na tsakiyar shigowa sai whatsap din y goge gaba daya,sai nayi sabon downloading kuma saiya xama wadancan massage din nayi missing dinshi nima ina kaunarku a duk inda kuke ngd dftn xakuyi min uxiri ngd,insha Allah yau xa'a kaimin gyaran wayar* Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/22, 4:22 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (22/11/2016 2:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *73* Mommy ce ta karaso da sauri tacewa su Amira su futa,tana haba my daughter kukanne har yanxu bai kareba,kiyi shiru kiji me xance miki shiru islam tayi duk da har lokacin tana hawaye,mommy tace daughter na saurareni da kyau kiji abinda xan fada miki,nima nasan an tauye miki hakkinki amma sam banxata dake xa'ayi aurannan ba saboda daddyn ku bai sanar mana ba,amma shawarar daxan baki yanxu kiyi hakuri ki daure a gama bikinnan lfy nasan bakyason Aslam kuma shima baya sonki don duk abinda y fara karyane,cikin mamaki islam ta dago kai tana kallon mommy,mommy tace eh yanxu abinda nakeso dake kamar yadda yayi pretending y nuna yana sonki to kema kiyi hakuri a karasa bikinnan da kaina xansaka y sakeki,cikin jin dadi islam ta dago kanta hawayen da suke sauka tasa hannu tana gogewa don yanxu bbn abinda y dameta dama bai wuce wannan kallagaggen auran ba,to yanxu kuma mommy tace xata saka y saketa,mommy tace yauwa daughter na ki share hawayenki ba sagir kikeso ba cikin jin dadi islam ta daga kanta harda murmushi kumatunta suka lotsa,itama mommy murmushi tayi tace yauwa my daughter yanxu kije kiyi wanka mai makeup xataxo tayi miki an jima xa'ayi kamu,fes islam taji ranta yayi saboda batad sauran damuwa ta shiga bathroom ta sakarwa kanta shower mommy ta futa su Amira suka dawo dakin. Islam ce ta futo wanka amma idanunta sunyi ja sun kukkumbur,Amira ce tace 6* wai kukan me kikayi ne kinga yadda idanunki yayi ja y kumbura,xumbura baki gaba tayi ta shagwabe fuska tace wai aure akayi min cikin firgici da mamaki suka maimaita aure,siraran hawaye ne suka xubo mata ta goge tace eh cikin xakuwa sukace dawa,ta tabe baki tace hero,dariya suka tuntsire da ita suna tab Ashe kece amaryar yaya Aslam lallai xa'asha luv,cikin masifa ta tashi ta dauko pillow ta fara jifansu dashi tana balbalin masifa ganin sun mayar da ita mahaukaciya sunci gaba da dariyarsu yasaka ta koma ta xauna ta bude shafin kuka tana shure2,mommy ce ta shigo itada makeover ganin islam na kuka da sauri ta karasa tana subhanallah islam kukanne har yanxu,cikin kuka tace basu Amira bane sukeyi min dariya ba dannace nice matar hero ta karashe maganar da kuka,cikin fushi mommy tayi kansu kamar xata dakesu sukuwa ganin haka suka kwasa a guje suka fice a dakin suna dariya. Dakyar mommy ta lallabi islam tayi shiru bathroom mommy ta jata da kanta ta wankewa islam fuska sannan suka futo,make up akayi wa islam sosai tayi kyau wani hadadden material white da touch din peach colour mommy ta dauko gown ne rigar ta kama islam ta sama ta bude daga kasa sosai ba karamin kyau tayiwa islam ba nada mata head makeover din tayi,sosai tayi kyau fashion dankunne da sarka aka saka mata peach colour occasion bag mommy ta dauko peach colour dayake takalmin hill ne sai islam ta kara tsayi,ba karamin kyau tayi ba duk da fuskarta ba annuri mommy tace xauna ki jirani,gaban dressing mirrow islam tayi ganin kyawun da tayi haryafi na safe amma maimakon tayi dariya ko murmushi saita karkace baki tayi tsaki tace aikin bands duk akan hero akayimin kwalliyar nan sai kuma tace dama da sagir akeyi min aurannan da nafi kowa farin ciki sai ta shagwabe fuska tace Allah sarki sagir dina very soon xan dawo gareka domin ni takace,su khausar ne suka shigo sanye da purple din material an masa kwalliya da light pink flowers sun daura light pink head suda wadansu yanmata da basu wuce sa'anninsu ba su 4,islam ganinsu ta hade rai sunata xolayarta ta musu banxa,mommy ce tace ku futo saka islam sukayi a tsakiya rigarta kuma tana sharar kasa. Lokacin dasu islam suka futo yayi dai2 da futowar su Aslam saboda dokunan da xasuyi kilisa sun iso idanuwan sune suka hadu cikinna juna dam kirjin Aslam y buga islam kuwa ko a jikinta illa murguda baki da tayi ta dauke kai,Aslam ma kansa y dauke,harsun shiga mota safwan y karasa da sauri y mikawa khausar whapper ta 100 guda 2 yace gashi kubawa amaryarmu 1 tayi liki kuma ku raba 1 godiya su khausar sukayi islam kuwa nunawa tayi tamkar batasan akwai wata halitta a gurin ba. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/22, 4:34 PM] ‪+234 810 749 9249‬: (22/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *74* Driver yaja motar su islam sukabar gurin domin dama su kadai suka rage kowa y tafi,safwan ma komawa yayi gurinsu Aslam yace ku muje kallan kasan ido Aslam yayiwa safwan yayi tsaki yace mutum sai shegen shishshigin masifa dariya safwan yayi yace eh naji suka futa suma. A cike su islam suka tarar da hall din da xa'a gudanar da kamu,suna xuwa sauran yan mata masu anko suka furfuto suka marawa islam baya,suna shiga d.j y saki kida. Su Aslam ma sunyi kilisar inda wanda yaxo na 1 kyautar lefan aka bashi na 2 kuma t.v plasma sai na 3 shikuma waya iphone cikin jin dadi kilisa ta watse sabanin ango dayake jin ranshi bakikkirin tunanin irin axabobin da xaiwa islam yakeyi don kullum y tuno da karkashin data xuba masa sai yaji tamkar a lokacin taxuba masa. Islam bayan an kamata mai d.j y bukaci amarya ta futo itada kawayenta,tuburewa tayi tace ba inda xata dakyar mommy ta lallameta ta futo anma kikam ta tsaya a filin wajan dukkuwa da yadda duma take ratsata su khausar kuwa rawa sukeyi sosai,aikuwa iyaye da abokanan arxiki suka futo ana barin nerori (nikuwa nace watako wasu ba ruwansu da buhariyyar nan 🙄)bayan nan anci anyi rabon sevoniars sannan taro y watse kowa y koma gda cikin jin dadi,amma fa banda islam. Suna komawa gda islam tayi jifa da head dinta da takalmin da jakar ta juya tacewa Amira ni xugemin kayan xafinnan Amira ta xuge mata,xama islam tayi daga ita sai vest da under wear ta xauna bakin gado,mommy ce ta shigo rikeda try dauke da abinci kallan islam tayi a ranta tace islam baxaki taba girmaba wai,kallan su khausar tayi tace kuje ku dauki abinci,karasawa tayi ta xauna a gefen islam tace yanxu my daughter a haka kika xauna keyanxu bakisan kin wuce wannan stage din ba,keyanxu matar aurece y kamata ki daina wannan abin yaran,xumbura baki gaba tayi amma batace komai ba dan ita inda abinda ta tsana baiwuce ace tana da aure ba murmushi mommy tayi dakyar ta lallaba islam taci abincin. Washe gari 2 o'clock aka fara tafiya reception na pretty mommy ce ta shigo dauke da wata leda lokacin an gama yiwa islam makeup ta xaxxage kayan unifoam ne na sojoji riga da wando harda takalmi,mommy tace toh fa yau akeyin ta dama ance matar soja,itama sojace ga kayan da xakisa cikin shagwaba islam tace banaso fa mommy,murmushi mommy tayi tace au yi hakuri,kayan islam tasa subhanallah xanso fans din *goyon kaka*kuxo kuga yadda unifoam dinnan y karbi islam saboda yayi bala'in y mata kyau,yau dankunne barima tasaka aka kama mata gashinta da ribom y sauka har gadon baya ga takalminta tasaka,mommy tace my daughter ke kowanne kaya kyau yakeyi,murmushi islam tayi cikin jin dadi,su khausar ne suka shigo sanye da wandon sojoji da white t.shirt sai hula da takalmin sojoji suna ganin islam sukace wow sis gaskiya kinyi kyau,ai kayannan har sunfi karbarki akan yaya Aslam cikin jin haushi islam tace toh naji kafin ku fada mommy ta tafada ta karashe maganar da murguda dan bakinta daya sha jambaki,dariya mommy tayi tace islam bakida dama. Futa su islam sukayi wata mota sabuwa ta gani safwan y bude mata baya yace shiga ranki y dade cikin xumbura baki ta shiga har saida ta xauna kanshin turaren da taji shine ya sakata saurin dago kanta Aslam ne xaune fuskarnan tashi tamau tamkar bai taba dariya ba,siririn tsaki tayi tace aikin banxa mutum kullum fuska a daure kamar anmasa bishara da a ranar xa'a dauki ransa,kallan mamaki Aslam yayi mata domin tsaf y jita ita kuwa kanta ta dauke,khausar ce ta shiga gaba Amira kuma tana motar Amir suka wuce country mall. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/23, 5:56 PM] 🍬🛍💍°°Salma°°🍬🛍💍: (23/11/2016 12:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *75* Suna xuwa safwan yayi packing da motar shida khausar suka futa,ganin haka Aslam da sauri y janyo Aslam ta fado jikinsa cikin tsananin firgici ta xaro idanu tana kokarin kwatar kanta amma ta kasa dada matseta yayi y murde mata kunne auchhh wash shine abinda islam tace tana rarraba idanu (tamkar bera a tarko 😂)yace ke yarinya naga danyan kai kikeji dashi shawarar daxan baki itace wlh kibini a hankali a gama hidimar bikinnan lfy idan ba haka ba yayi kwafa y daka mata uwar harara,y saki kunnan nata,cikin tsiwa tayi masa kallan up & down tace in ba haka ba mai xakayi wata dankar yakai mata ta kwallah kara lokacin safwan y karaso y budewa Aslam kofa yace ranka y dade bismillah cikin wani ixxa da jin kai y xuro kafarshi waje da sauri safwan yaje y budewa islam ma kofa ta futo hannunta Aslam y riko y matseshi da sauri ta dago kanta wani malalacin murmushi y sakar mata da sauri ta sunkuyar dakai tana xumbura baki a haka suka karasa shiga hall din. Suna shiga duk aka mike,gurin a tsare yake saboda dududu mutane basufi 200 ba kowa yana sanye da white t.shirt da wandon sojoji illah manyan sojoji ne sanye da kaya ba unifoam ba,mutane da yawa mamaki sukeyi lokacin da sukaga amaryar captain a.u domin ko kafadarshi bata kaiba karasawa sukayi table din dasu general yusuf safana yake da manyan sojoji suna xuwa Aslam y kame y sara musu,wani mugun kallo y jefi islam dashi wanda ba wanda y kula itama batasan lokacin data kame kwatankwacin yadda Aslam yayi ba ta sara musu tuni hall din yadau tafi raf2 saboda bakaramin burgesu tayi ba shikanshi Aslam yaji dadi domin ta futar dashi kunya y kama hannunta suka karasa inda aka tanada dominsu. Anci ansha anyi fareti kala2 inda general yusuf safana yayiwa amarya kyautar mota islam taji dadi sosai don harta manta da akwai Aslam a gurin sai washe baki takeyi tamkar gonar audiga,wajen 6 o'clock taro y watse saboda akwai dinner 8 o'clock. Suna komawa gda Aslam yayi ficewarta islam ma haka kowa yayi part din da yake safwan ne y kalli khausar yace 8 o'clock ku xama cikin shiri domin bamason african time khausar tace toh,islam da gudu ta shiga part din mommy xaune ta tarar da ita acikin palo itada mutane da gudu islam ta fada cinyar mommy tana tsallen murna,mommy cikin jin dadi tace yata wannan farin cikin fa islam tayi lamo ajikin mommy ta lumshe ido tana murmushi sai kuma ta bude idon ta mikawa mommy mukullin mota,mommy tace mukullin mota nagani na menene dada rungume mommy tayi tace a wajen reception wani yabani kyautarta cikin jin dadi mommy tace Allah y sanya alkhairi yan dakin sukace ameen suma sun tayata farin ciki,sannnan ta tashi ta tafi daki. Alwala tayi sannan tayi sallar la'asar da magruba kwance take akan gado su khausar suna xaune sukuma makeover tanayi musu kwalliya,Amira ce tace 6* ki tashi kiyi wanka mana kinaji ana kiran sallar isha'i fa kokin manta sunce basason African time,tsaki islam tayi tace to aikin Allah ne da xaku dameni ku wlh fa kubini a hankali dan kunsan yanxu ruwa ba sa'an kwando bane mota ce dani gwanda ku bini a sannu ku samu nadinga dibanxu muje makaranta shewa suka saka suna kaga amaryar captain a.u wani malolon bakin ciki taji a ranta tsaki tayi tasauka tayi sallarta ta isha'i,lokacin har an gamawa su khausar kwalliya sun saka blue lace da touch din red in da xasu saka red din head suma suka tayar da sallah islam kuma tana idarwa tashiga bathroom domin yin wanka. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* 💘💘💘 [11/23, 5:56 PM] 🍬🛍💍°°Salma°°🍬🛍💍: (23/11/2016 1:00pm) *na umma yahya musa* 🍒🍒🍒🍒🍒🍒 🍒🍒🍒🍒 🍒🍒 🍒 *GOYON KAKA* *76* Bayan ta futo a wanke makeover ta xauna ta tsantsara mata makeup wani hadadden gown na material yellow mai raga2 tasaka anyi mata landing da wani irin yadi mai walwali blue colour tuni tadau sheki da kyalli ku fans din *goyon kaka* ku haskomin farar mace cikin yellow din Abu ga kuma blue,wani irin nadin head akayi mata da dark blue an masa ratsi da yellow anyi packing din gashinta da blue ribom yana lilo a baya wani arnen fashion dankunne da sarka blue da stones din yellow tasaka awarwaro na gold sai occasion bag dinta blue subhanallah irin haduwar da islam tayima bata lokacine sai wajen 8:30pm aka gama kintsata. Aslam kuwa yanacan cikin mota in banda tsaki babu abinda yakeyi yana duba agogo domin a rayuwarsa y tsani African time ko kadan tsarin bai masa ba,shima danye yake cikin rantsatstsiyar shadda golden brown yana sanye da hula zanna bukar itama golden brown da kwalliyar xare brown colour sumar kanshi kuwa tasha gyara sai kyalli takeyi haka sajenshi y kwanta luf akan kyakykyawar fuskarsa tsintsiyar hannunshi daure take da agogon rolex na xallar axurfa kafarshi kuwa tana sanye cikin combat boot baki. Kamar jiyama Amira da khausar da yanmatannan hutune suka sako islam a tsakiya hannunta na dama 3 hakama a bangaren hagu mutum 3 lokacin da suka futo wani irin faduwar gaba Aslam yayi saboda irin kyawun da islam tayi tamkar wadda akayiwa wankan inji kokwanto y shigayi akan itace koba itaba harsuka karaso motar baisani ba kanshin turarenta ne y ankarar dashi dandanan y dauke kai y tamke fuska,islam kuwa tabe baki tayi tace ko tunanin me hero yakeyi oho,safwan ne y kalli khausar yace y akayi kuka bata mana lokaci khausar tace wlh islam ce batayi wanka ba sai da akayi sallar isha'i kuma tasan shirinta akwai bata lokaci,safwanne yace Ashe laifinki ne amaryarmu kikaki yin wanka da wuri,banxa islam tayi masa tamkar batasan da ruwan mutum a gurin ba,Aslam Kuwait tsaki yayi yanajin bakin ciki akan shishshigin da safwan yakewa islam a haka harsuka karasa the afficent. Suna xuwa safwan ne y juyo yaje my friend plz just give me 5 minute y fuce shida khausar tattaro masu anko sukayi matan suna sanye da sky blue lace da touch din red,maxan kuma suna sanye da sky blue shadda da hula red kai sunyi bala'in yin kyau,karasawa sukayi amarya da ango suka futo xagayowa Aslam yayi y sakalo hannun islam cikinnasa gabansu taslem da ihsan ne cikin red gown anyi musu gyaran gashi da wasu yara biyu maxa sa'anninsu sanye da black suit,baya kuma kowacce mace jere da namiji suna tafe ana watsa musu kyalkyali da spray na amare kumfa sai tashi takeyi tuni masu daukar hoto da masu video coverage suka fara aikin daukarsu. Suna shiga hall din islam taji kirjinta y buga da karfi tuni ta runtse idanuwanta,police band kuwa tuni yahau dukan ganga,duk yan hall din suka mike saboda girmamawa amarya da ango,sagir da yake gefe kuwa wani tsananin bakin cikine y turnike shi,wai yau islam dinshi ce take auran wani ba shiba. A hankali suke tafiya cikin yanga tamkar masu tausayin kasa dayake rigar islam najan kasa bansan yaya akayi ba kawai naga tana kokarin faduwa cikin abinda bai wuce kiftawar ido ba naga Aslam y dagata cak tamkar yar baby,tuni hall din y dauki sowa da ihu saijin tafi kakeyi raf3 rikon dayayi mata irin daukar jarirai ne aikuwa ta wani lafe a kirjinsa har sai da suka karasa gurin da aka tanada dominsu y ajiyeta,wani kallon kasan ido yayi mata a wulakance yace banxa kinji jiki mai dadi harda langabewa wannan da a gda muke saina kara wanka,bakinta ta murguda masa tace wanine yasaka ka daukeni ta dauke kanta shima dauke kansa yayi. M.C ne y futo yayiwa amarya da ango barka da xuwa yace sannan y kira sunan safwan yace yaxo y bada tarihin ango,y futo y bada tarihin ango da yadda soyayyarsu ta fara da amarya da irin mugun son da ango yakewa amaryarsa,tuni gurin y dauki tafi, cikin mamaki Aslam yake kallon safuwan saboda irin karyar daya shirga,sannan aka kira Amira itama taxo ta bada tarihin amarya itama kamar yadda safwan yace Aslam nason Islam itama haka tace,islam kuwa don bakin ciki ji takeyi tamkar ta kurma ihu,nan ma tafi akayi. Wasu yan matane da suke xaune,dayar tace nifa wlh kawata nayi mamakin matar captain a.u dan Allah jibeta ko kirgen dangi bata fara ba,tsaki dakyar tayi tace inajin fari da gashinne y rudeshi,dayar ta tabe baki tace ainaji ance auran xumunci ne cousin dinsa ce,dakyar ta kuma cewa koda naji mana amma ace yana babban yaro haka ba kayan hutawa ajikin matarsa ina jin xan gwada sa'ata,dayar tace ina bayanki kawata Allah y baki sa'a,tayi wani farrr da idanunta tamkar na kwarkwata tace ameen. Taku har kullum *sisin mama* 💘💘💘 *mrs hamisu taura* [3/7, 8:34 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *77* Haka akaci gaba da hidimar biki,anci ansha save ur save ne kowa abinda yakeso yake diba,ba irin kayan more rayuwa da babu kama danaci nasha,can nagano xugar fans din *goyon kaka* sun xage suna kwasar gara. An bukaci amarya da ango su futo filin rawa,kicin2 islam tayi da fuska ta xumbura baki gaba,Aslam ne y matsar da bakinshi dai2 kunnanta yace y yan matana xaki tashine ko saina daukeki,da sauri ta daga kai ta kalleshi kashe mata ido daya yayi yace eh maimaita abinda y faru daxu xanyi ai islam batasan lokacin data mike ba,murmushin gefen baki Aslam yayi yana kada kai yana jifan islam da wani shu'umin kallo dana kasa fassarashi,tashi sukayi a hankali suke takawa ji islam tayi Aslam y rige hannunta itadai banxa tayi masa,a ranta tana cewa jarababbe gobennan xamu rabu sai dai ka tare da wata matar a haka suka karasa filin rawa dukkaninsu a tsaye suke kikam babu mai dan wani juyawa nan fa yan'uwa da abokanan arxiki sukaxo aka fara barin nerori (nikuwa nace bidiri watako masu kudi ba ruwansu da buhariyyar nan ) sagir shima tasowa yayi yaxo y fara musu liki islam cikin tsan2 mamaki take kallanshi jikinta duk yayi sanyi shima sanye yake da ankon maxa blue din shadda da hula red,saikuma tayi rau2 da ido tanason yin kuka. Aslam ganin yanayin da islam ta shiga yayin dataga sagir tuni yaji ranshi y baci xuciyarshi tana masa xafi saboda tsaf y ganeshi cikin xafin nama y danki hannun islam suka juya suka bar filin rawar. Xaune suke a gurin da aka tanadar musu Aslam yace me wannan banxan yakeyi a gurinnan ubanwa y gayyace shi,wani shekeke islam ta kalleshi tace sainaji matsa tukunna xan amsa maka ta karashe maganar da murguda karamin bakinta,wani shu'umin murmushi Aslam yayi yace ina tausaya miki yarinyar nan dan duk lokacin dana dankeki baxakiji dadi ba,murmushi itama islam tayi tace mudai tausayawa juna domin kasan game dinnamu bama taba tashi 1-0 sai dai duro,cikin tsantsan mamaki yake kallanta har xaiyi magana sai yaji m.c na sanarwar yanxu amarya da ango xasu yanka cake kwafa yayi suka mike a tare. Suna karasawa gurin wani hadadden cake kalanshi white & pink aka basu wuka aka kirga number 1,2,3 sannan suka yanka cake din ko wannensu fuska a tamke Aslam ne y fara dauka y sakawa islam a baki sannan y bata lemo tuni aka dauki tafi raf3,murmushi islam tayi a ranta tace xaka Sani itama ta dauko wani katon cake Aslam ganin sai y rankwafo islam xata samu damar saka masa cake din a baki shine kawai y sashi yanke hukuncin dagata cak,islam bata ankara ba sai jinta tayi a sama,Aslam y jefeta da wani murmushi dana rasa gane ma'anarsa itama mayar masa tayi y bude bakin kawai saiji yayi ta danna masa wani katon cake dayafi karfin bakinshi da hanxari y dureta saboda yadda yaji y kasa tauna cake din,tuni gurin y dauki sowa da tafi ji kake raf3,islam kuwa data fakaici idon mutane saitayi masa gwalo,wani malolon bakin ciki Aslam yaji y turnike shi. 11 o'clock taron y tashi kowa yana cikin farin ciki anyi rabon sevoniers sosai,safwan ne y mayar dasu islam gda yano to amaryarmu Allah y tashemu lfy,itadai banxa tayi masa saboda bacci takeji tayi shigewarta part din mommy. Aslam kuwa suna shiga part dinsu kayansa y cire y fada wanka saboda yadda daddadan kamshin islam y dameshi saboda daukarta da yayi. Harya futo wankan baidaina jin kanshin ba tsaki yayi yace wanne irin mayan turare ne haka,kwanciya yayi y lumshe ido dukkuwa daba bacci yakeyi ba kawai hirar dasu safwan sukeyi ce ta isheshi,safwan ne yace kai abokina wlh kalar soyayyarku kai da islam ta burgeni kaga wani kallan luv da kuke jifan juna dashi,banxa Aslam yayiwa safwan saboda yasan safwan soyakeyi y tanka masa,safwan jin Aslam yayi masa shiru yasa shi cigaba da maganarsa yana kai abokina bafa karamin burge mutanen gurinnan akayi ba yadda cikin xafin nama ka daga islam cake Tamkar ka dau... bai karasa ba Aslam y taso cikin karaji yana is enough nagaji dajin banxan surutunnan naka to innayi mata kallan luv laifine ko inna dauketa haramunne naga mata tace plx don't disturbing me again wata dariyar shakiyanci safwan y saka yace haka nake sonji angon islam cikin kufula Aslam y juyo da niyyar naushin safwan lokacin su safwan harsun kai kofa tashi Aslam yayi yaje y sakawa kofar key. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:35 AM] ‪+234 703 962 5239‬: na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *79* A mota ma islam sai gunjin kuka takeyi su mommy sunyi2 da ita tayi shiru taki har suka hakura,gdan ta dayake nassarawa g.r.a aka kaita gda ne ginin tsarin turawa tun daga compound din abin kallo ne domin kwaltace a shinfide tun daga bakin gate har xuwa inda xai sadaka da packing space daga gefe kuma grass carpet ne shinfide da wasu flowers masu kyau da kanshi akwai garden a gdan da yake dauke da shuke2 kama dasu mango,guaver,ap ple,ruman d.s sannan akwai sweemin pool tun daga waje gdan abin kallo ne (nidai nan na saki baki da hanci ina kashe kwarkwatar idona) Subhanallah Ashe kallo na cikin gdan wani kayataccen palo ne dauke da kayan more rayuwa babu abinda babu daga can gefe kuma wani hadadden dinning table ne akwai kofofi guda 4 1 kitchen ne mai dauke da store acikin shi shima irin fadar haduwar shi bata lokaci ne,sannan akwai store komai na kayan abinci akwai a ciki (Abba ne y xuba acewar shi gara yayiwa islam) kofofi biyu kuma bedroom da toilet acikin kowanne yana dauke da wasu hadaddun gado an mafa yan nigeria sunyi bala'in yin kyau domin in ba fada maka akayi ba saika xata yan wajene domin *hamra furnitures company* ba baya bane wajen kera gadaje tamkar yan waje to anan sukayi order su,dayar kuwa wata irin security door ce itace xata sadaka da stair daxai kaika xuwa sama gani nayi duk an tsalallake dakunannan an haura da islam sama shi kanshi stair din abin kallo ne saboda yadda aka kawata shi. Y salam shine abinda na furta saboda tsaruwar palonnan ba karamin kyau yayi ba kujerune yan dubai dark & light purple sai t.v plasma touch screen akwai wasu manya manyan home theater akwai set light daga gefe kuma dispenser ce tareda wata katuwar show glass dauke dasu turaren wuta,humra kwalakca d.s ga sanyin a.c da daddadan kanshi dayake ratsa duk ilahirin jikina (nikuwa nace hmmmm lallai nan ake kira aljannar duniya garin dadi na nesa ungulu ta hango masai )suma wasu hadaddun kofofine guda 3 a jere reras 1 naga an murna (wai saura kadan numfashina y dauke )wani tamfatsetsen gado nagani wanda y shanye kusurwa 1 ta dakin irin royal bed dinnanne tamkar na sarauniyar england kanshi shimfide yake da wani hadadden bedsheet pillows din dayake kai kuwa sunkai 10 kama da mai sweet mai triangle d.s wata tamfatsetsiyar wardrop ce wadda tsayinta y kusa tabo p.o.p din da akayiwa saman dakin ga wani hadadden mudubi da aka cikashi da kayan make up kai masha Allah gda yayi ,tsakiyar gadon nan aka ajiye islam ai saina ganta wata yar rutsut ,har lokacin islam kuka takeyi tamkar ranta xai futa,su khausar aka kirawo mata ganinsu nema yadan saka ta daina kukan. Islam na hango ta baje akan gadonta itada su amira ta war ware laffayar tayi gefe da ita suna ta hira harda kyakyata dariya tamkar ba itace take kuka daxuba,kiran sallar magruba akayi suka tashi suka je sukayo alwala suka futo watako shi kanshi bandakin an kashe masa dukiya lokacin kuma mutane suka fara watsewa gdan y xamana daga mommy saisu khausar dan aunty amarya ma ta tafi itada kaka islam ce ta fara raba ido tana y naji gdan shiru,murmushi mommy tayi tace ai sun tafi,islam ta shagwabe fuska tace mommy amma ku anan xaku kwana ko murmushi mommy tayi amma batayi magana ba. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:36 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *80* Sai da akayi sallar isha'i mommy da kanta ta shiga bathroom ta hadawa islam ruwan wanka wanda yaji turaruka ta futo ta bude akwatin sleeping dress ta dauko mata wasu sleeping dress pink colour mai santsi riga da wando rigar kamar vest take wandon kuma gajere ne iya cinya,kallan su khausar tayi tace kuje palon kasa ku jirani xanyiwa islam magana in nagama saiku dawo to sukace suka futa,kallan islam mommy tayi tace my daughter dukkan abinda xai faru tsakaninki da son y xama sirri karki sake ki fadawa kowa kinji saboda tona sirri dayake tsakanin miji da mata haramunne islam tace toh dan batasan wani sirri akeson ta boye ba,mommy tace sannan ki dinga tsarki da ruwan dumi kidaina tsarki da ruwan sanyi kinji to islam tace mommy tace yauwa daughter na tashi kije kiyi wanka in kin futo wadannan kayan xaki saka,islam tace toh a gaban mommy ta cire kayanta ko kunya kokarin cire vest da under wear takeyi mommy tace a'ah my daughter ki daina cire kaya a gaban mutane yanxu kin girma,cikin jin kunya islam tasa hannunta ta rufe fuska ta dauki towel ta shiga bathroom mommy tanajin islam ta fara wanka tayi sauri taje ta tasa keyarsu Amira sukabar gdan dayake akwai driver dayake jiransu. Aslam ne kwance a dakinsa safwan y shigo yana haba ango tun daxu an kaimaka amaryar ka y kamata ka shirya muje mu rakaka daganan musai bakin amarya,wani mugun kallo y jefi safwan dashi y doka wani uban tsaki y shige bathroom dariya safwan yayi y samu guri y xauna,20 minute Aslam y dauka y futo daure da towel yana tsane jikin shi da wani xama yayi a gaban dressing mirrow y shirya tsaf y taje kanshi da kwantaccen sajenshi bayan y saka singlet da boxwr y dauko wata arniyar shadda galila ash colour y dauka y saka y feshe jikinshi da turaruka masu dadin kanshi hula dara baka yasa sai takalmi mai danyatsa shima baki ba karamin kyau yayi ba dukkuwa da yanda fuskarsa take a tamke,wayoyinsa y dauka akan dressing mirrow da key din mota y kama hanya xai fice ko kallan safwan da amir baiyi ba,safwan ne yace ah haba ango tun daxu fa kai muke jira muyi maka rakiya amma naga kana shirin wucemu wani yatsina fuska Aslam yayi yace bana bukata ko ana dole yasa kai y fice. Sallama yaje y yiwa iyayanshi sannan y kama hanya y tafi driving yakeyi amma ranshi duk a jagule,tsintar kanshi yayi da tsayawa gurin mai saida kaxa kulli 2 yasaka akayi masa y cillasu bayan mota y wuce,horn yakeyi a bakin gate din gdannashi cikin sauri gateman y bude yana sara masa yana ur wlcm sir dayake soja ne,direct packing space yaje yayi packing din motar. Islam kuwa bayan ta futo a wanka gani tayi bataga su Amira ba,harta shagwabe fuska xatayi kuka xatayi kuka sai kuma ta tuna kila suna palo xama tayi gaban dressing mirrow ta shafa mai sai powder tadan xixara kwalli,tasaka lip stick ta mulke jikinta da humra mai mugun kanshi ta dada da body spray sannan ta saka sleeping dress din ta kama gashinta da ribon ganin irin kyawun da tayi da ai sai tahau tsalle da sauri ta saka wani takalmi sosa ta kwasa da gudu ta futo a dakin ganin bataga su khausar a palon ba tayi kasa wayam tagani basu khausar ba alamarsu tahau kwala musu kira khausar!Amira!mommy! Jin shiru ai saita hau kuka da gudu ta haura sama saboda tsoron da taji y kamata direct dakinta ta wuce ta fada kan gado tahau shashshekar kuka tana kiran sunansu. Futowa yayi a motar bayan y dauko ledojin kajin daya siyo,cikin tafiyarsa ta xaratan maxa yake takunsa cikin kasaita harya karasa shiga palon,siririn tsaki yayi ganin yadda palon y kawata amma sai dai kash ba matar da xaiji dadin rayuwar auransa bace a gdan,bismillah yayi y sakawa kofar key y haura stair tun daga palo yakejin shashshekar kukanta cikin jin haushi da xafin xuciya yayi hanyar dakinnata tura kofar yayi da karfi a xafafe yace kukan uban me kike yiwa mutane sai kace gdan makoki,cikin raxana islam ta dago kanta ganin wanda yake tsaye shine y sakata yin tsaki,a ranta tana Allah y isa tsoron daya bata,ta komar da kanta kan pillow taci gaba da kiransu mommy tana kuka tsaki shima yayi a ransa yana xan gyara miki xamane,cilla mata kunshin kaxa 1 yayi yace gashinan in kinga dama kici yaja mata kofa. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:37 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *81* Direct dakinshi y wuce xuciyarshi nayi masa tukukin ciwo,bude kofar yayi wow gaskiya shima dakinnashi y hadu exartly kayan gadon irinna dakin islam ne colour ne kawai y banbanta,cire hularshi yayi da ogogo da wayoyinsa y daurasu kan bedsite cabinet sannan y cire rigarshi y bude wardrop y sakaleta ajikin hanger y xamana dagashi sai singlate bakin gado y xauna tsaki yaja y dafe kanshi saboda baraxanar tarwatsewa da yakeyi saboda tsabar damuwa a ranshi yace gaskiya an cuceni y kamata a yanxu ace inacan inajin dadi irinna ko wanne ango ranar da amarya ta tare amma nisam abin ba haka yake ba saima dan karen damuwa da tamin yawa (nikuwa nace kai kaso ) tsaki y karayi y kwanta kafafunshi na kasa fuskarshi na facing din p.o.p din dakin y tallafe kanshi da hannuwanshi biyu tunani y xurfafa sosai. Can wata xuciyar tace masa haba Aslam alkawarin da kayiwa iyayenka kenan xaka rike islam amana,wannan itace amanar ace kaxo ka tarar yarinya na kuka koka lallameta alhalin kasan kuruciya na dibanta kuma tunda take yauce rana ta farko da xata kwana ita kadai a daki ka duba girman alkawari fa,daya xuciyar ce tace to ai na tsaneta banason ganinta sam,daya xuciyar tace dole ka sassauta kiyayyarta a xuciyarka saboda yanxu ita wani nauyi ce da Allah y daura maka,kuma tabbas xa'a tambayeka ranar lahira yaya katafi da hakkokinta na duniya,xuruf naga y mike kamar wanda aka tsikara y fice a dakinnasa dakin islam y tafi a hankali take tafiyar tamkar wadda wani Abu yake masa ciwo a ciki tura kofar yayi har lokacin tana kife akan pillow tana kuka a hankali y tura kofar dakinnata y dade tsaye a kanta,sannan y bude bakinsa yace ke kamar wanda bakin yakewa ciwo. Rinannun idanuwanta ta dago ta kalleshi ta daka masa wata uwar harara ta murguda baki ta mayar da kanta kan pillow taci gaba da kukanta tana kiransu mommy,jikin shine yayi sanyi lokaci daya tausayinta y dirar masa abinda bai taba jiba a iya tsayin rayuwarsa duk da islam ta wuce 2 years,a hankali y buda baki y kira sunanta islam! wani dam islam taji girjinta saboda yadda taji Aslam y fadi sunanta ita bada ban kartayi karya ba da tace duk duniya yafi kowa iya fadin sunanta saboda yadda yake fitar da kowanne harafi (nikuwa nace to fa) sai kuma tayi tsaki ta karkatar da baki tace kila dan ban saba jin y kira sunanta bane daga yace *ke* sai *aljanar yarinyarnan* ko *banxar yarinyarnan*,shine y katse mata tunanin nata yace kukan me kikeyi,da kamar baxatayi magana ba saboda haushinsa da takeji tunda shine dalilin daya saka yau aka rabata da yan'uwanta,sai kuma can ta budi baki tace mommy ce ta tafi dasu Amira ni ka mayar dani gda ta karashe maganar da kuka,tsaki yayi yace ke a ina kika tabajin a ranar da akakai yarinya gdan miji a daren an mayar da ita,kallanshi tayi shekeke tace to ka sakeni bashikenan ba,kallanta yayi da mamaki yace watako hartasan saki shine abinda xai rabasu,murmushin yake yayi wanda yafi kuka ciwo,yace baki fini son mu rabuba amma hakan baxai yiwu ba saboda su daddy ne suka hada auran kinga su suke da alhakin rabashi,idan har kina ganin xaki iya xuwa kisaka suce na sakeki fine y daga kafada yace hanya a bude take,shiru tayi dan tasan baxasu taba yadda yaya Aslam y saketa ba domin da xasu yadda da tun ranar da akace an daura musu auran yadda ta tubure tace batason shi da an rabasu,tsaki tayi ta tashi daga kan gadon tana wlh komai daren dadewa sai mutum y sakeni na auri wanda nakeso,jikin jin haushi da gajiya da bakaken maganganunsa yayi kanta y daukota yace da uban wane yace shi yana sonki,kuma inna karajin kinyi xancen wani kina gdannan to wlh ranki sai yayi mugun baci y hankadata gadon y fice a dakin yaja kofar da karfi,tashi tayi tace aikin banxa ba wanda y isa y hanani hirar masoyi na kuma farin cikin rayuwata,karasawa tayi ta dauko kaxarta xama tayi ta cita sosai,dan rabon data nitsu taci abinci tun randa aka sanar mata itace matar Aslam bayan ta gamaci ta nade ragowar ta daura kan dan karamin fridge din dayake dakin,ta bude ta dauko fresh milk tasha bathroom taje ta wanko bakin ta da hannunta,ta kwanta kan gadonta taja blanket bata dade ba,bacci mai dadi y kwashe ta saboda kukan dataci a hankali take sauke ajiyar xuciya. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:43 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *82* *washe gari* Aslam y futo xai tafi masallaci har xai shige dakin Aslam kawai yaji a ransa y kamata yaje y tasheta tunda yanxu hadda hakkin kula da addininta ne a kansa kofar y tura kawai saiya jita a bude,can y ganota kudindine acikin blanket tana ta sharar baccinta hankalinta kwance tashinta y farayi yana ke,ke,ke a hankali ta fara bude idonta tarr ta saukesu akan Aslam xumbura baki tayi ta mayar da kanta gefe tace menene,harararta yayi yace dallacan tashi kiyi sallah kin saki baki da hanci kina bacci kin cikawa mutane gda da munshari,murmuda baki tayi tace wlh ni bana munshari,harararta y kumayi yace nayi karya kenan,ta yatsina fuska tace eh kusan hakanne,xaro ido yayi yana kallonta ita kuwa ta diro daga gado tayi mika hade da salati ta tattara gashinta daya barbaje garin bacci tashige bathroom ta barshi baki sake,tsaki yayi y juya y fice,islam tana futowa wardrop ta bude ta dauko hijab kato har kasa da sallaya ta shimfida sai da tayi raka'atanul fijri sannan tayi sallar asuba,axkar tayi takaranta qur'ani kusan ixu 2 sannan tayi hasbunallahu wani'imal wakil kafa 450 taci gaba da istigfari sai 6:30am ta tashi ta karayin nafila raka'a 2 sannan ta koma kan gado bata dade ba bacci mai dadi yayi gaba da ita. 9 o'clock ta farka a hankali tayi salati ga annabi sannan tayi addu'ar tashi a bacci kamar haka *bismikallahumma amutu wa ahya* *alhmdllhillaxi ahayana ba'ada ma a matana wa ilaihinnushur* sannan tayi mika dirowa tayi daga kan gado ta karkadeshi duk da ba datti yayi ba ta gyarashi tsaf (nace kai Ashe islam din kakan ta iya gyara ) tana gamawa ta fada bathroom ta sakarwa kanta shower 10 minute ta dauka ta futo tana tsana jikinta da towel xama tayi gaban dressing mirow mai kawai ta shafa sai powder sai ta saka lipstick jikinta ta mulke da humrah sai ta fesa body spray sai ta shafa roll on,abinda nayi noticing da islam ita sam bata kwalliya ko iyawa ne kuma batayi ba oho ,wani three quarter wando baki ta saka sai body hug datasa purple colour mai gajeren hannu ta taje gashinta ta fesa hair spray na olive ta tufke gashinnata da purple ribom jelarshi ta sauko har gadon bayanta tana reto (nikiwa nave amaryar xamani watako bata tunanin baki tasaka englis wears) wani daddadan turare ta dauko ta dunga feshe jikinta tana gama kintsawa ta tsaya gaban mudubi ta karewa kanta kallo sai kuma tayi murmushi jin cikinta yana mata kugi shine y sakata shagwabe fuska tace wash yunwa nakeji y xanyi kawai sai tayi nasai2 da ido tana shirin yin kuka sai kuma naga ta xura takalmi ta fita karewa palon kallo tayi tace wow gaskiya palonnan yayi kyau a hankali ta tafi sadaf Sadat ta tura kofar dakin dayake opposite nata aikuwa a bude yake turawa tayi wani daddadan kanshine y dakar mata hanci har sai data lumshe ido a hankali ta karewa dakin kallo komai need kayan furniture din ma irinna dakintane kome ta tuna kuma sai ta tabe baki taja kofar ta rufe,kofar kusa da dakinta taje ta tura sai tajita a ride,tsaki tayi kome ta tuna kuma sainaga ta koma dakinta da sauri gwangwanin air freshiner ta bude ta fesawa dakinnata kusan kala 3,tana eh nima mutum baxai nunamin tsafta ba ta karashe maganar da murguda baki sannan ta futo tajanyo kofar ta sauka kasa. Xaune ta ganshi yana kallon lbrai shima yayi wanka yana sanye da shadda light purple kanshi ba hula amma gashin shi sai kyalli yakeyi sajensa kuma y kwanta luf,hannun shi daure da agogon gucci na fata light purple,kafarshi sanye da slippers milk colour na fata sai xuba kanshi yake saikuma ta tabe baki lokacin data gama kallansa,hararta yayi yace menene kika xubamin wannan manyan idonnaki kamar na mayu kina kallona,murguda baki tayi tace kai da wanne idon kasan ina kallanka,kuma in manyan idone ai ka fini kaga saika tantance idon waye yafi kamada na mayu ta karashe maganar tana harararsa,cikin jin xafin maganganunta y tashi da niyyar kwade ta dan baxai iya cika alkawarin daya daukarwa aunty amarya ba,ita kuwa ganin abinda yake niyyar yi y sakata tashi da sauri shirin runtumar na kare takeyi taku daya yayi y dankota kwallah kara tayi tana wayyo Allah nashiga 3 xai kasheni daga hannu yayi da niyyar buge mata bakin sai yaji an danna bell. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:44 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *83* Daga hannu yayi da niyyar bige mata baki,ita kuwa ta tattara hannuwanta ta rufe fuskarta saukar mari kawai take jira sai sukaji karar bell,hankada ta yayi ta fada kan kujera,hararar bayanshi tayi tace Allah y isa. Xuwa yayi yana waye muryoyin su Amira yaji suna mune yaya tsaki yayi y bude y coge ba bakin kofar,cikin rawar jiki sukace yaya ina kwana,sai daya gama shan kanshinsa sannan y amsa da lfy,y yatsine fuska yace uban me kukaxo min gda da sassafennan cikin rawar murya sukace break fast muka kawo muku,kallansu yayi yace waya kawo ku sukace isya driver amma y koma sai lokacin y matsa musu hanya suka wuce,islam da take xaune kan kujera tana tacin magani saboda lokacin da Aslam y hankada ta kan kujera ta buge kanta ganin wadanda suka shigo gdan da gudu ta tashi tana murna hade da tsalle taje ta rungumesu,suma cikin jin dadi suka tungumeta suna ta murna,Aslam kuwa ganin shirmen da sukeyi y saka shi tabe baki yayi tsaki basket din da sukaxo dashi y dauka yakai dinning kitchen y shiga y dauko cup da plate da tea spoon da pock y futo y wuce dinning area domin yaci abinci. Su islam kuwa bayan sun gama tsalle2 nasu ta matsa gefe ta rike kugu ta karkace baki tace meyasa jiya kuka gudu kuka barni,shikuwa Aslam dayake dining area murmushi yayi yace wannan yarinyar bata da hakuri watako duk murnar ganinsu da takeyi amma sai tayi mita,Amira ce tace wlh mommy ce tace mu tashi mu tafi gda,islam tace toh amma yau Allah sai kun kwana khausar tace a'ah mommy tace anayin magruba mu koma,tsaki islam tayi ta kufa banxayene ku tashi muje muyi break,Amira ce ta xauna a kujera tace nidai nakoshi bansan kausar ba,itama tace ta koshi islam ta juya tace nikam yunwa nakeji dama tun daxu kamar naci babu ta wuce. Karasawa tayi taja kujera 1 ta xauna ta kalli Aslam tace ina plate dinnawa kuma,wani banxan kallo y jefeta dashi yace yaje koyan gaisuwa,murmushi tayi har dimple dinta y lotsa tadan sosa kai tace au ina kwana,tsaki yayi yace daban kwana ba xaki ganni itama tsakin tayi tace naji mutum yace na gaisheshi,na gaisheshi kuma yana min iyayi,kallan mamaki yake mata yama kasa magana saboda y fahinci rainin hankalin islam yayi yawa ko yaushe da kalar wanda take kirkiro dashi,katse masa tunaninsa tayi ta hanyar cewa yaya nifa yunwa nakeji,harararta yayi yadanyi tsaki yace wlh in baki daina min rainin hankalinnan ba yanxu jikin ki xai fada miki in banda kin rainani ma ni kikeso natashi na dauko miki plate da cup din,kuma da kike cemin yunwa kikeji gaba abinci ba koni kikeso naxama abincin ciki,bude bakinta tayi tana kallansa da mamaki sai kuma tayi yar dariya tace tab to ai kai yaya ko abinci kaxama wlh babu mai cinka saboda sam baxakayi armashi ba ta karashe maganar da kyalkyalewa da dariya,shikuwa Aslam ji yayi wani tukukin bakin ciki y turnike shi ga wani Abu dayaji y tokare masa xuciya tunani y tafi wai meyasa yarinyar nan ta iya fadar bakaken maganganu masu ciwo ne can wata xuciyar tace ai kai kadai take fadawa maganganu son ranta,dafe kanshi yayi yace to meyasa ta rainani ne a iya sanina ko matasa sa'anni na shakkata sukeyi kallan kansa yayi yaga irin kirar da Allah yayi masa ta karfafan maxa kwafa kawai yayi y mike lokacin islam ta dawo rikeda plate da cup ganin y tashi tace yaya harka koshi,yace bansani ba y wuce daga kafadarta tayi ta murguda baki tace kada Allah yasa ka Sani din. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:45 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *84* Palo y karasa y dauki key din mota da wayoyinsa y fuce su Amira sunayi masa a dawo lfy ko amsa musu baiyi ba shiga motar shi yayi y fice direct gda yayi. Islam kuwa xama tayi ta cika cikinta daganan ta koma palo selection suka saka na india suka kure home theater har bakin gate anajin karar suka har dirkar rawa baji ba gani,islam kuwa sai wani karye2 takeyi tamkar karina kapoor lol ,saboda islam ba baya bace dama wajen rawa. Islam kuwa yana xuwa direct part din mommy yace suka gaisa ta tambaye shi y islam,kanshi y sosa yace tananan lfy jiya tanata kuka wai kun tafi kun barta dakyar na lallameta tayi shiru,murmushi mommy tayi tace islam rigima dan Allah son ka rike islam amana nasan sai kayi hakuri saboda yanxu kuruciya na dibanta amma a hankali komai xai dai2 ta domin irin abinda ka horar dashi to dashi xata tashi dan haka ka koya mata dabi'u masu kyau jikinsa ne duk yayi sanyi,sannan dan Allah karka dinga takura mata kasan dai yarinya ce batasan komai akan rayuwar aure ba,cikin jin kunya yace toh mommy tace Allah yayi muku albarka yace ameen,tambayarta yayi yace daddy fa tace sun tafi kasuwa yace Allah y dawo dasu lfy,mommy tace ameen y tashi yace bari nakarasa gurin aunty na murmushi mommy tayi shikuma y tashi y futa. Da sallama y shiga part din aunty amarya ta amsa masa sallama cikin farin ciki fuskarta dauke da murmushi da sauri y karasa y xauna a kusa da aunty y daura kanshi a kafadarta yace aunty ne barka da safiya cikin jin dadi ta shafa kanshi tace barkan mudai y gda,y angwanci dariya yayi yace aunty angwanci kuma (saboda tun tashin Aslam baya taba iya boyewa aunty amarya damuwarsa saboda itace abokiyar shawararsa) tace eh mana ko xubawa islam din ido kayi dariya yayi yadan shafi kansa yace haba aunty nawa islam din take nikam saina raineta ma nifa ina tunanin islam bama tasan menene aure ba,dan xungurinsa tayi tace au haka kake tunani ashema auran bashi da wani amfani tunda baxai yi maganin cutar taka ba tashi yayi yana dariya yace nifa aunty na gaskiya kunya nakeji banaso ta rainani y mike dariya itama aunty amarya tayi tace kujini da ja'irin yaro to kasata a gaba kana kallo tamkar t.v ficewa yayi a part din yana dariya part din kaka y wuce. Xaune y tarar da ita tana kallan t.v da Sauri y karasa yayi hugging dinta yace uwar gda ran gda uwar gda sarautar mata,dariya kaka tayi tace ni cikani ja'iri,hade rai yayi yace Allah xan sakeki kika kara kirana da wannan sunan kinsan yanxu inada mata kuma in kika bari nayi xuciya to saina shekara 1 baki kara ganina ba,harararsa tayi tace toda yanxu wane y kiraka inka tashi tafiya kafi ruwa gudu kuma ma ai da tsohuwar xuma ake magani,yanxu naxata kasan kana da amaryar amma ka taho gurina,dariya yayi yace yar tsohuwar nan da kishi kike to maida wukar kinsan dai amaryata special 1 ce tsaki kaka tayi tace kaikasan abinda kake nufi,tashi yayi yana naga yau xuciyar ki a kusa take bari natafi kafin fadannaki yakai ga duka y fice. Part din samarin gdan y wuce direct tsohon dakinsa y nufa saboda yasan safwan yana can a kwance y tarar da safwan yana bacci tashinshi y farayi,a hankali safwan yake bude idanuwanshi tarr y tsaidasu kan Aslam mikewa yayi y shiga bathroom yayo brush y futo. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:46 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *85* Safwan yana futowa daga bathroom y fara ango ango kasha kanshi kaga yadda kake kyallin angwanci kuwa,lallai daga ganinka jiya ka kashe arna irin wannan kyau haka y karashe maganar da dariyar shakiyanci,Aslam ne yayi tsaki yace dadina dakai wlh banxa ne wataran in xakayi magana sam baka taunata kawai fadar ta kake,dariya safwan yayi yace to menene acikin magana ta laifi,cikin kufula Aslam yace bkmai,safwan yace nifa yau xan koma dan harnaje na yanki ticket by 5 o'clock flight din xai tashi,Aslam yace OK nima next week xan dawo,cikin mamaki safwan yake kallanshi yace ammh amma da islam din xaka taho ko,wani kallan tara saura kwata Aslam yayiwa safwan yace eh tunda naxama na mamajo ba,dariya safwan yayi yace xaka iya xama hakan ma amma y xame maka dole ka taho da matarka tunda 1 month aka baka hutu,wani kallan banxa Aslam yayiwa safwan yace toh sannu daddy tunda har umarni kake bani,dariya safwan yayi yace ba haka nake nufi ba kasan dai akwai hakkokinta akanka idan ka tauye mata Allah xai iya tambayarka,siririn tsaki Aslam yaja yace ashe mai wa'axi ka xama to ai kamata a samo maka majalasi da loudspeaker kaka wa'axinnaka yafi armashi,murmushi safwan yayi yace to naji yanxu saika kaini nayi sallama da amarya tunda kaga xuwa 5 xan tafi may be nida dawowa garinnan sai kuma suna nan da 9 month,cikin jin haushi Aslam yace god forbid ace nixan hada jikina da banxar yarinyar i can't wlh,cikin mamaki safwan yace uhm uhm dai kar nan gaba kaxo kanamin karamar murya,murmushin gefen baki Aslam yayi wanda har dimple dinshi y loba yace wannan maganar taka shine babban kuskuren daxan tafka a rayuwa ta duk ranar dana xo maka da wannan maganar to ni Aslam na yadda kamin duk abinda kaga dama,to in banda abinka me xannema agurin yar tsakuwar nan ai sainaja tamin rainin dayafi wanda tamin yanxu (nikuwa nace anya Kuwa )dariya safwan yayi yace to naji taso dai muje gdannaka Aslam yace wlh sai 4 xanbar gdannan in kaga xaka iya jira fyn in baxaka iya jira ba ai ba dole,safwan yace to naji masifaffe gira daya Aslam y dage yace au sai yau ka sani sukayi dariya a tare daganan sukaci gaba da magana akana cigaban da Aslam yake samu a business din motoci da yakeyi,har safwan yake cewa shima yanaso y fara,Aslam yace ai hakan yana da kyau. Su islam sai 2 suka kashe kidan sukayi sallah,suna idarwa suka futa surrounding din gdan flowers suka fara tsinka sai da suka cika dan kwalin khausar,mai kula da flowers din gdanne y gansu da saurinsa y karasa yana ku! Ku!!Ku!!,wannan wanne irin iskancine su islam ganin yadda y xaburo da sauri yanayi musu tsawa shine y sakasu runtuma ana kare,karasowa gurin flowers din yayi ganin irin ta'asar da sukayi shine y saka shi yin tsaki,yace wadannan kannan amaryar oga din daga ganinsu fitina xasuyi in banda tsabar rashin ji yaushe anyi Abu domin kawata gda amma suxo suna batawa,yayi kwafa yace tabbas dana kamasu yau to bakaramin bugu xanyi musu ba saboda yadda oga yakeson flowers dinnan nasan xaiji dadi haka yaci gaba da mita haryabar gurin. Su islam kuwa suna shiga dakin sukace me xasuyi inba dariya ba,dariya sukeyi ba kakkautawa,islam ce ta tashi ta xura dankwalin Amira acikin ta, ta tura cikin gaba take kwaikwayon yadda kurtun sojan y ttumbulo ciki lokacin daya gansu a gurin flowers dariya suka dada tuntsirewa da ita daganan kuma suka fara wasa da flowers din da suka tsinko,cikin 10 minute suka canjawa palon fasali,sukayi kaca2 dashi sun tunkuda center table din palon yayi gefe sun cicciro pillows din kujerun sun tarwatsasu a palon garin wasan jefe2,sai da akayi kiran sallar la'asar sannan suka tashi a wasan sukayi sallah,islam ce tace kuxo muje mudan xagaya gdan haka suka fice bayan gdan ta kofar kitchen sukabar palon kaca2 dan ba abinda suka gyara. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* December 15, 2016 at 6:4 [3/7, 8:48 AM] ‪+234 703 962 5239‬: na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *86* Cikin jin dadi suke kallan gdan can idansu yakai wajen sweaming pool da sauri suka karasa (islam nagani tayi wani tsalle ta fada ruwan da sauri na xaro ido nace nashiga 3 harna bude baki da niyyar ihun a kawo dauki kawai naganota tana iyo tamkar kifi harwani tafiyar baya takeyi),cikin tsantsan mamaki su khausar suka kallanta domin basu taba xaton islam ta iya ruwa ba ita kuwa cikin farin ciki taci gaba da wankanta sukuwa xama sukayi a bakin sweaming pool din suka xura kafarsu a ruwan sai da islam ta dauki kusan 10 minute sannan ta futo tana matse gashinta daya jike,khausar ce tace islam dama kin iya ruwa,dariya tayi tace sosai ma ai lokacin a kauye har gasar tsere mukeyi dasu hanne a rafi,tayi wani farr da ido tace kuma nice nake xuwa ta 1 don duk nafisu iya ruwa kuma in kunaso mukoma in koya muku,xaro idanu sukayi sukace a'ah xoro mukeji,tsaki tayi ta hararesu tace waya fada muku in xa'a koyi Abu anasa tsoro a rai ai indai xaku na saka tsoro a ranku baxaku taba iyawa ba,Amira tace eh munji an fada miki kowa ne irinki mai wasa da rayuwarsa dariya islam tayi da gudu sukaga ta kwasa tayi cikin garden mara mata baya sukayi,suna shiga da sauri tayi ta kama bishiyar goba ta dare tamkar yar biriya xama tayi akai tafara cin goba khausar ce tace haba islam ki tsinko mana mana muma,cikin masifa tace baxan tsinko ba nice nahana ku hawowa kuma sai da taci guda 3 tana cillo musu kwallayan sannan ta tsinko guda 10 ta jefo musu tana wlh 3,3 xaku diba ku ajiyemin 4 ehe ta sakko taraf naga ta haye bishiyar mangwaro nace tofa. Su Aslam bayan sun dawo daga sallar la'asar dayake tun 3 sukayi lunch xuwa yayi part din aunty amarya y dauko abincin daxai tafiwa dasu islam yaje yayiwa mommy da kaka sallama suka fice saboda yadda safwan ke axalxalarsa,tafiyar 15 minute takaisu gdan Aslam saboda yadda Aslam din yake gudu yana xuwa gate man y wangale gate yanayi masa sannu da xuwa,bayan yayi packing motar sun futo da sauri mai kulada flowers yaje yana fada masa irin ta'asar dasu islam sukayi,cikin jin haushi Aslam yake tafiya dan harya manta ba basket din abincin sai safwanne y dauko,yana mamakin saurin fushi irinna Aslam. Turus Aslam y tsaya a bakin kofar palon ganin irin yadda su islam suka canjawa palon kamanni,a lokacin safwan y karaso ganin yadda palon yayi kaca2 shine y saka shi yin dariya,yace lallai kannan amarya sunyi aiki kamar yadda mai kulada flowers yace kannan amarya ne guda 3 suka futo suka tsinki flowers,cikin jin haushi Aslam yahau sama da gudu nemansu amma kwata2 y duba bai gansufa,sai daya sakko y sannan y duba dakunan kasa nan ma basanan,shikuwa safwan sai dariya yake masa,cikin jin haushin dariyar safwan yace dallah malam ka damu mutane da dariya kamar wani sabon kamu,dariya safwan y karayi yace nifa bani nakar xomon ba,guku Aslam y rike yana karewa palon kallo yama rasa ta ina xai fara gyarawa,dariyar su islam y jiyo ta kitchen cikin tsantsar mamaki yake kallan kitchen din,hannayensu y gani dauke da mangwaro da goba,islam tana kyalkyala dariya tana danma kun samu nasan muku shine xaku raina wanine y hanaku ku iya hawa bishiyar,tsilli2 sukayi da ido sakamakon ganin Aslam da sukayi,kallansu yayi a tsawace yace ubanwa y sakaku bata palonnan haka bama wannan ba wane y baku ikon xuwa ku tsinkemin flowers,shiru sukayi dukkansu,tsawa y daka musu yace badaku nake ba,islam ce ta tura baki gaba tace to nagama ko bamu tsinka ba dole iska ta kadata ta fado,sai kuma ta shagwabe fuska tana kallan cikin idanshi tana kada idanuwan ta tamkar yar tsana tace Allah hero karya yakeyi ba tsinka mukayi ba a kasa muka debo,ta kalli su khausar tace ko 6*s cikin rawar jiki sukace eh eh a kasa muka debo,Aslam kuwa ji yayi jikinshi duk y mutu saboda yadda idanuwan islam suka saukar masa da kasala,safwan dayake a xaune yana jiran yaji matakin da Aslam xai dauka kawai sai yaji yace. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:54 AM] ‪+234 703 962 5239‬: na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *87* Safwan dayake xaune yana jira yaji wanne irin mataki Aslam xai dauka kawai sai yaji yace,cikin kasalalliyar murya to shikenan naji dama safwanne xai tafi yace yanaso yaxo kuyi sallama,amma bayan wannan y kamata ku gyara palonnan,cikin tsantsar mamaki safwan yake kallan Aslam a ranshi yace tabbas nan da 2 years islam xata ladabtar da Aslam,dariya safwan yayi yace toh amaryarmu ni xan wuce,xumburo baki gaba islam tayi tace nifa gaskiya ba amaryarku bace,dariya safwan y karayi yace to amaryar captain A.U sai munxo suna,cikin masifa tace Allah y sauwake nifa ba xama xanyi a gdannan ba xamana na temporary ne,permanent yana gdan sagir,cikin jin hsushin kalaman safwan da kuma abinda islam tace yasa xuciyar Aslam xafi cikin hargowa y danko islam lokacin idanuwansa har yayi ja yake banyi miki warning akan karna karajin kinyi xancen banxannan ba,buge hannunsa tayi tace wlh sagir ba banxa bane kaje can kanemi banxan ka kwafa yayi ganin kallan dasu Amira sukeyi masa y kalli safwan yace tashi mu tafi,safwan y ciro 20k y mikawa islam 10k y bawa su khausar ma 10k yace su raba kowa yadauki 5k,godiya sukayi masa suka fice. Amira ce tace islam gaskiya abinda kikeyi sam2 bai kamata ba,kin daisan yanxu in kika yiwa yaya rashin kunya to xunubi kike debarwa kanki,bama wannan ba ai naxata yanxu y kamata ace kin manta da yaya sagir saboda ke yanxu matar aure ce,khausar tace gaskiya kuma kinsan annabi yace *aljannar mata tana karkashin diga2 mijinta idan tayi masa biyayya y daga mata ta wuce in kuwa sabanin hakane to dama tasan inda makomarta take* y kamata kidinga tunani saboda kin sani kin karanta hakkokin miji akan mata harda dadadan kalamai in tayi masa lada xata samu,jikin islam ne yayi sanyi tace ngd da tunatarwar ku 6*s insha Allah xan kiyaye,sai kuma tayi rau2 da idanuwa xatayi kuka tace wlh ko kadan banason hero saboda tun tashina bai taba nunamin soba,ko laifi nayi da duka xai yimin gyara,Amira ce tace kiyi hakuri a hankali xakiji sonsa a ranki. Su Aslam kuwa suna xuwa suka shiga mota,dariya safwan yake yace abokina irin wannan soyayyar da kake nunawa islam tana birgeni,a gaskiya na dade banji lbrn masoya irin kuba,kaga wani tsantsan kishin islam dana gani a idanuwan ka,cikin jin haushin kalaman safwan yace to wai innayi kishin ta haram ne naga dai mata tace,dariya safwan yayi yace haka nakeso abokina,gajiya Aslam yayi da surutan safwan y kunna kira'ar sheik sudes cikin suratul maryam yahau bi,ko xaiji saukin radadi da xugin da xuciyarsa takeyi masa. Gyaran palon su khausar suka fara,islam kuwa takasa yin komai tunani kawai takeyi yanxu inta mutu wuta kenan xata shiga,ganin batada amsar tambayar ta yasa ta kalli su Amira tace 6*s bari naje nayi wanka nacire jikakkun kayannan nawa,sukace toh ta wuce stair. A bandaki ma haka tayita tunane2 dakyar tasamu tayo wanka ta dauro alwata,data futo mai tashafa sai powder ta xixara kwalli sai lipstick ta mulke jikinta da sihirtacciyar humra ta kara da body spray,wardrop taje ta bude tadauko swiss lace purple blouse & skirt saida ta busar da gashinta da hand dryer ta mulkeshi da mai tuni gashinnata yadauki shinning saka kayannata tayi das naga sun xauna mata,kama gashinta tayi da ribbons purple ta dada fesa turare takalmi ta xura tafita a dakin,amma bata daura dan kwali ba. Lokacin data sauka su khausar harsun gama gyaran palon abinci sukaci suna gamawa,aka danna bell Amira ce taje ta bude isya ne yace su akace yaxo y daukesu,komawa palon tayi tafadawa khausar anzo daukarsu,jin haka islam tayi rau2 da ido xatayi kuka dakyar suka lallabata ta hakura sukace gobe xasu dawo. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:55 AM] ‪+234 703 962 5239‬: a umma yahya musa* *GOYON KAKA* *88* Yau islam kwananta 7 a gdan Aslam amma ko yaushe cikin fada suke domin mai hali baya fasa halinsa,saboda shi Aslam yana ganin islam bata isa tace xata raina shiba,ita kuma koya y fada mata cuta saita fada masa mutuwa,kullum kuma su Amira ne suke kawo musu abincin break fast lunch Aslam y taho dashi dinner kuma isya ya kawo musu. Yauma su Amira ne suka kawo break fast,bayan Aslam y futo sun gaisheshi yayi break Amira ce tace yaya daddy yace nafada maka wai yau dukkansu sun tafi gwarxo bb na tsauni ne bashi da lfy sukaje gaishe shi,yace OK Allah y bashi lfy,futa yayi y wuce gdan abokanan sa sukuwa suka fara wasa. Da misalin 2 o'clock islam tace kuxo muje muyi girki tunda yau baxa'a kawo mana ba,khausar tace nidai ban iya girki ba saboda ko a gda mammy da masu aikine sukeyi,Amira tace wlh nima ban iyaba,tsaki islam tayi tace a haka xamuyi ta xama ne baxamu iya ba ni wlh yunwa nakeji in baxaku xo muje mudafa ba inna dafa ni kadai xanci,tashi sukayi suka shiga kitchen din gas cooker suka kunna aka daura ruwan shinkafa daya tafasa kamar gaske aka debo shinkafa aka wanke aka xuba dadi duk y ishesu yau suna girki (nikuwa nace lallai yau manya suna aiki) sannan aka dora tukunyar miya a dayan gas din dayake mai 4 ne,kaxa nagani an dakko a deep frizer an yayyankata aka wanke aka xuba a tukunyar aka dauko kayan miya nan ma aka xuba aka saka mai aka barbare maggi duk aka xuba an xuba maggi cube yakusa 30 sannan aka saka gishiri 1 spoon har xa'a kara islam tace a barshi haka in an gama anji gishirin bai isaba a kara dora tukunyar akayi a wuta,kitchen din kuwa yayi kaca2 dan komai aka dauko akayi amfani dashi to anan ake barinsa xama sukayi aka fara musu wannan tana tafiyin kokari a girkin wannan tana tafita,kansu ankara sukaji shinkafa ta fara kauri da sauri suka tashi sukaje suka kashe,bude tukunyar shinkafar sukayi suka ganta wani batso2 alamar bata dahu ba,khausar ce tace shinkafar ma ai bata dahu ba,dariya islam tayi tace ke dahuwar turawa ce,dariya suka tuntsire da ita gaba dayansu suna ihu suna eh kuwa,food flask suka dauko suka juye shinkafar kuwa in banda kauri babu abinda takeyi,miyar suka bude sukaga takusa dahuwa Amira ce ta dafa kai tace af mun manta ba'asa albasa ba islam tace aikuwa da gudu suka shiga store suka debo albasa manya guda 5 suka bare cikin sauri suka raba kowacce 4 peaces suka wanke suka xuba,baifi 5 minute da xubawa ba sukaji miyar na kamawa da sauri suka dauko corry da thyme roba daya2 suka juyesu a miyar ko minti 1 baiyi ba suka kashe gas din miyar ma juyeta sukayi a flask islam ce takai abincin kan dining ta koma suka fara gyara kitchen din. Suna cikin gyaran kitchen Aslam y dawo,tunda y shigo palon yakejin kauri da sauri yayi kitchen ganin sana aiki yasaka shi tambayar su mesukeyi,islam ce tayi magana tace girki mukayi,murmushi yayi yace kun kyauta y tafi palo y xauna,sai da suka gama gyaran kitchen din sannan suka futo,direct dining area suka tafi,islam ce tace yaya aslam kai baxaka ciba,tasowa yayi yace ina tsoro cin jagwalgwalo ne murmushi islam tayi hade dayin farr da ido tace aikuwa yayi dadi,don in kaci abincinnan kunnanka sai y Mora,murmushi y karayi lokacin yayi dai2 da karasawar Aslam dining area islam da kanta taja masa kujera,saboda yau jinta takeyi a farin ciki ta sauke hakkin Aslam dayake kanta,dakanta tayi serving dinshi shidai kallan abincin kawai yakeyi saboda yadda yake wani kanshi mara dadi,shahada kawai yayi yayi bismillah ya debo abincin a spoon yakai bakin shi,lokaci daya yaji wani dandano mara dadi hade da karni y gauraye masa baki furxo da abincin daga bakinsa cikin tsoro su islam suka dago kai suna kallansa. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:56 AM] ‪+234 703 962 5239‬: na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *89* Islam ce ta kwantar da murya kamar mai shirin yin kuka tace,abincinne baiyi dadi ba,wani kallo y jefeta dashi data kasa fassara me yake nufi,tsam y tashi y haura stair direct dakinshi y wuce brush da maclean y daura y dinga wanke bakinshi,sai da yaji y dainajin dandanon abincin a bakinshi sannan y daina,tsaki yayi sai yanxu ma yake ganin wautarshi yama za'ayi yaci abincin kaxaman yarannan wani murmushi ne y kufce mishi da sauri y futo daga dakin yayi down stair. Tarar dasu yayi kowa da abinci a gaba yana juyawa y kasashi,murmushi yayi yace a'ah yan matan kakan ya naga kun tasa abinci a gaba kun kasa ci,islam ce cikin jin haushi tace abincinne kwata2 baiyi dadi ba dariya yayi yace koh to ku jirani kitchen y wuce y dauko katon try y futo juye abincin yayi acikin try din harda wanda suka xuba a plate ya dauka yace ku taso ku biyoni table mat y shinfida akan center carpet yace oya bismillah maxa kafin na kirga 3 ku faracin abincinnan,xaro idanu sukayi suka hada baki sukace me yaya,yace abinda kunnuwanku y jiye muku,da ubanwa y saka baku iyayin abinci ba ku dafa dan haka wlh sai kunci,islam ce tace Allah innaci abincinnan amai xanyi daga kafadanshi yayi y karasa jikin fridge y bude y dauko lemon shani na gwangwani y balle yace wlh ko xaki amayar da hanjin cikinki sai kinci abincinnan,y karasa yace start mana kuka tsaya kallona ganin sunki xama shine y sakashi dire lemonnashi akan center table ya hade rai tamkar bai taba dariya ba,cikin wata irin kakkaurar murya data xoratasu yayi magana yace baxaku cibane sai jikin ku y fada muku baxan dauki asara axubar da wannan abincin ba belt dinshi y fara kokarin cirewa da gudu suka xauna suka faraci ganin sun faracin abincin shine y sakashi murmushi a xuciyar sa yace wannan hukunci shine daidai daku komawa yayi y xauna akan kujera ya dauki lemonsa yana sha cikin jin dadi y dauki remote y kunna t.v. Su islam abincinnan sukeci tuni suka fara hawaye harda majina saboda yadda daddanon abincin yake rikita musu ciki,Aslam kuwa ko digon tausayin su baiji ba lemonsa ma yakesha yana kada kansa saboda selection din dasu islam suka saka yake kallo,su islam har sunci rabin plate din tuni kukan da sukeyi na xuciya y fara futowa kallan try din yayi yaga sunci rabi,murmushin jin dadi Aslam yayi yace y bakwacin naman da sauri suka dauki naman suka faraci,tsananin karnin namanne y saka xuciyarsu tashi da kudu suka tashi bedroom din kasa suka shiga,basu tsaya a ko ina ba sai a bathroom tuni suka fara sheka amai tamkar xasu amayar da yayan jikinsu dakyar amannan y tsaya ammafa duk sun galabai ta kuskure bakunansu sukayi suka futo,kan gadon dakin suka baje suna mai da numfashi. Kausar ce tace gaskiya yaya Aslam bashi da tausayi,islam ce tayi tsaki tace ku sai yau kuka sani,Amira ce ta nuna islam tace eh amma ai duk ke kika jamana,cikin masifa islam tace danayi uban me,tsaki Amira tayi tace wanene y sakamu dole sai munyi girkin,murmushi islam tayi tace naji kuyi hakuri,sai kuma tace kunsan Allah baxaici bilis ba wlh saina rama mana wahalar da mukasha,cikin jin dadin abinda islam tace khausar tace me xakiyi masa,dariya islam tayi tace haryanxu tunani nakeyi amma ayau xan rama baxqi kai gobe ba kunsanni bana yafiya,khausar tace gaskiyane,itakuwa Amira gani takeyi islam karya takeyi ba wani rama musu da xatayi. *tofa ko wanne irin hukunci islam xata yanke dan ramuwa oho kudaici gaba da biyoni danjin yadda xata kaya* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 8:57 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *90* Da misalin 7:30 o'clock Aslam ne a kitchen yana girki hadaddiyar jellop rice yake dafawa datasha vegetables sannan yayi pepper soup na kifi tarwada,islam da take xaune a kan kujera sai binsa takeyi da idanu,Aslam sai da y tabbarar y gama hada abincin y juye su a warmers tuni gda y dauki daddadan kanshi,kallan islam yayi y harareta yace oya dauki kikai min kan dinning murmushi tayi masa tace toh sai daya tabbatar daya gyara kitchen din tas sannan y futo,kallan islam yayi yace jirani naxo nayi wanka sai muci abincin tunda ke kinyi toh kawai tace masa. Islam tana ganin Aslam yahau sama da gudu ta tafi kitchen container din gishiri ta dauko har xata xuba acikin abincin sai kuma tayi tsaki tace gaskiya inna xuba gishirinnan xai gane,kuma ni kaina xanwa kaina bakin cikin cin abincinnan dan da alamu yadda y dumame gdannan da kanshi ba karamin dadi xaiyi ba,tsaki tayi ta koma ta mayar da gishirin,futowa tayi ta rafka uban tagumi ta saka wannan taga baiyi ba tasaka wancan har Aslam y sakko y xauna batasan y sauko ba,tafi yayi mata a fuska firgigit tadawo daga tunanin data tafi,yatsina fuska yayi yace tunanin me kikeyi sai dataja numfashi tace kaka nakeson gani ta karashe maganar tamkar xatayi kuka,janyo plate yayi y fara xuba abincin yace kibari gobe na kaiki tunda yanxu dare yayi dariya tayi tace Allah y kaimu. Aslam ne y faracin abincin da alamu abincin yayi masa dadi ganin yadda yake lumshe ido,har islam ta janyo plate xata xuba abincin sai kuma ta fasa murmushi tayi a ranta tace alhmdllh idea taxo kura masa ido tayi Aslam yaci abincin rabin plate y janyo flask din pepper soup y xuba y faraci anan y lura islam bataci abincin ba,dago lumsassun idanuwan sa yayi y saukesu akan islam yace y bakiji abincin ba,murmushi tayi tace y xa'ayi naci abincin danasa dakakken kyankyaso aciki,cikin tsoro Aslam y xaro idanuwansa yace what,murmushi tayi ta kada idanta tace kyankyaso nace nasan xaka iya kin yadda amma nidai nasan nasaka lokacin daka sakani daka maka tafarnuwa to a lokacin nahada da kyankyason ta karasa maganar da tuntsirewa da dariya. Ai Aslam bai jira ta karasa magana ba y tashi da kudi y fada kitchen y tsaya ajikin sink yahau kwarara amai islam ganin haka ta kyalkyale da wata shu'umar dariya ta mike ta fara kwasar shoki tace yes anyi 1-1 da sauri tabi Aslam kitchen ganin y takarkare yana xura hannu a baki shine y sakata shekewa da dariya harda faduwa da rike ciki,Aslam ganin ta tasa shi gaba tana dariya,Shine y saka shi jin haushi a ranshi yace wannan yarinya anyi bakar muguwa watako ita komai akayi mata saita rama,kuskure bakinsa y fice y barta a kitchen din,islam kuwa sai da tayi dariyarta wali ishi sannan ta mike itama ta futa xaune ta tarar da Aslam a palo y dafe kansa,murmushi tayi ta wuceshi dinning area ta wuce ta debo abinci memakon ta xauna taci acan saita taho palo danneman magana. Kallanta Aslam yakeyi da mamaki ganin yadda take cika cokali tana danna loma harwani lumshe idanu takeyi,tace kai yaya anya daka tafi aikin soja bakuwa bangaren catering ka tafi ba,ta karakai loma tace kai inaga kai dai Kirchner din sojoji ne,murmushi yayi yace ba wannan nakeson jiba. Katse shi tayi ta hanyar cewa aff ai karya nakeyi maka daxu,kawai ramu gayya nayi kasan ance ramuwar gayya tafi ta gayya xafi,kawai banbancin 1 ne mu daxu ta dole kasamu mukaci abinci daga baya muka amayar,kai kuma cikin farin ciki kakeci daga baya nasa ka ka amayar tayi dariya tace kaga yanxu munyi 1-1 ko,Aslam kuwa in banda mamakin islam babu abinda yake yace anya yarinyar nan mutum ce kuwa,ranshi yaji y baci ganin rainin wayon datayi masa,hannu yakai y danko ta kara ta kwallah lokacin yayi dai2 wayarsa tahau ringing. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:03 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *91* Hannu yakai y dauko phone dinnashi,har lokacin islam tana rike a hannunsa tana raba idanuwa tamkar bera a tarko,sunan general yusuf safana y gani da sauri y hankada ta,kujera ta fada ta buga kai kara ta saki saboda ta bugu sosai da sauri yasa hannu y toshe mata baki yayi picking call din,cikin girmamawa yace yallabai brk da dare dftn kana lfy,dagacan bangaren general yace lfy qlau ango y amarya,dan murmushi Aslam yayi y kalli islam y harareta saboda kokarin cire hannunsa datake a bakinta ta kasa,yace tananan lfy,general yace masha Allah,dama wani training ne akace anason sojoji masu matsayin captain xa'a turasu singapore suyo wani training har tsawon 2 years to bansani ba ko xaka iya xuwa naga kanada sabon aure,cikin jin dadi Aslam yace mai xai hana yallabai yaushe ne tafiyar,general yace nan da 7 days Aslam yace ngd Allah yabar girma insha Allah xanshigo nan da 5 days,ameen general yusuf yace daganan sukayi hiding call din,sai a lokacin Aslam yake shirin budewa islam baki ganin haka da sauri islam ta rike hannunsa ta gantsara masa cixo mai xafi,har sai da Aslam yayi yar kara da sauri ta sakar masa hannun ta kwasa a kuje sai da tahau step sannan ta tsaya,ganin Aslam yana yarfe hannu alamar cixon y shigeshi shine yasa ka islam kyalkyalewa da dariya,dagacan inda take tace hey hero karka manta nasha fada maka islam bata yafiya duk laifin da akayi mata sai ta rama gwargwadon yadda aka yi mata saboda islam bata xalinci saita kara kyalkyalewa da dariya,ganin Aslam ya mike shine yasa kata arta a nakare,murmushi Aslam yayi ya koma y xauna yace yarinya sai fitina ga kuma tsoro kamar farar kura,islam kuwa sai data shiga daki tasa key ajikin kofar ta tsaya tana mai da numfashi a haka dai ta karasa kan bed dinta daganan bacci yayi awon gaba da ita. Washe gari da misalin 11:00 o'clock islam ce sanye cikin riga da wando rigar light pink wandon kuma sky blue pencil powder ce kawai a puskarta sai kwalli da lipstick amma tayi kyau after dress tasaka mai flowers pink da stones pink bakaramin kyau tayi mata ba veil ta nada pink sai ta saka wani takalmi mai shegen tsini pink mai igiya,Aslam ne yake knocking kofar dakinnata yana wlh xan tafi ko an fada miki ni driver dinkine xaki shanyani,murguda baki tayi kamar yana kallanta tace da kai din menene in ba driver naba turare ta fesa sannan ta futo tana tura baki. Kallan ta yayi a ranshi yace lallai islam bakaramar kyakykyawa bace,amma sabanin haka a fili y tabe baki yace duk bata wa mutane lokaci da kikayi ma ko kyau ba kiyi ba,banxa tayi dashi domin a rayuwar islam taki jinin tayi kwalliya a ki yaba mata,shiyasa take son sagir koya tayi kwalliya y dinga xuxutata kenan yana daukarta pics a haka har suka futa a gdan yasa key y rufe suka karasa suka shiga mota get man y wangale gate yana a sauka lfy yallabai. Tafiya sukeyi ba wanda yacewa wani uffan,islam dayake batasan gari ba sai kalle2 take (nikuwa nace wayaga kifin rijiya ) dai2 shop rite Aslam y tsaya yace bari naje nasiyo wa su kaka tsaraba bakya je hannu na dukan cinya ba,kallan shi tayi tace nima xanje yace toh futo muje futa sukayi y rufe mortar suka karasa shiga mall din hannunsa yasa y rikewa islam hannu. Sai kallansu akeyi saboda sunyi kyau,Aslam ganin mutane na kallansu sai yaji dama a mota yabar islam saboda yadda yaga hankalin maxan y karkata kanta,tsaki yayi ganin oganniyar ita ko a jikin ta bakinshi yakai dai2 kunnanta yace wlh ki nutsu kikamin rawar kai in muka koma gda saina dakaki,banxa tayi dashi keken xuba kaya Aslam y janyo suka fara xagayawa kurin turaruka suka fara xuwa. Kicibis Aslam yaji yayi karo da mutum a tare suka dago fuskarsu,wani hadaddan guy ne baki kyakykyawa (black beauty) yana da manyan idanuwa farare tas yana da gira dai2 gwargwado yana da dogon hanci bakinsa yana da dan girma kadan inda kwantaccen sajensa y hadu da xagayayyan gashin baki daya kawata fuskarsa sumar kansa luf,bashi da jiki sam dan Aslam y fishi girma sosai sai dai xasu iyayin tsayi 1 da Aslam danko Aslam xai fishi tsayi to da kadanne, wannan daga gani ko ba'a fada ba dan fillo ne. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:08 AM] ‪+234 703 962 5239‬: a umma yahya musu* *GOYON KAKA* *93* Aslam driving kawai yakeyi amma sam y rasa nutsuwa,tunanin shi y tsaya tsam a guri daya,yasara meyasa in yaga wani yana nuna kulawa akan islam ko yace yana sonta yakejin haushi,islam ce ta katse masa tunaninsa ta hanyar cewa kai gaskiya hero abokinnaka yana da kirki sosai a gaskiya inaji ma nafasa auran sagir in ka sakeni gaskiya shixan aura ta karashe maganar da mirmushi ta lumshe idanu. Wani mugun birki Aslam yaja wanda yasa islam saida tayi gaba ta koma ta gwaru da kujerar baya,xaro idanu tayi tana kalle2 ko xataga abinda yasaka Aslam jan birki haka,Allah ne y kiyayesu sun shiga irin titunan unguwa dan da a babban titi suke babu abinda xai hanasu haddasa hatsari,Aslam kuwa packing motar yayi a gefen titi y dango islam idanuwansa yayi jajawur jikinsa har bari yakeyi,lokaci daya jikin islam y fara rawa idanuwa xaxxaro saboda tsabar tsorata,kallanta yayi yace wlh this is the last warning about wancan banxan yaron da kike kira xaki aureshi,ke in banda baki da tunani ki rubuta ki ajiye auran mu ba saki ba yaji,dan naga alamar bakida hankali inajin kin manta xaman aure mukeyi ba dadiro ba da harxaki na tunanin wadansu maxan,naga alamar sam 2 bakisan menene aure ba wlh3 kinji nayi rantsuwa 3 times ko in kika kara maganar xan sakeki ki auri wani namijin saina nuna miki real colour dina yayi murmushin gefen baki yace naga ke haryanxu bakisan wanene umar ba kawai kallona kikeyi,lokacin daxan fara nuna miki halina y kama bakinta y murde har sai da tayi kara ,yace wlh bakin tsiwar nan sai y mutu y tankada ta,ta bugu da kofar mota itadai islam ta tsorata ta kama bakinta ta rike dan ba karamin maxa yaji ba jikinta kuwa har rawa yakeyi dan ba karamin tsoro Aslam y bata ba y canja mata gaba 1 tamkar namijin xaki tunaninta y tsaya tsam takasa tabuka komai sai kanta data sunkuyar tana kallan kasa,Aslam kuwa sai daya dauki 10 minute yana xaune y lumshe idanuwansa sai daya samu nutsuwa sannan yaja motar suka tafi. Aslam suna xuwa sukayi horn gate man y bude musu suka shiga,tun kafin Aslam yayi packing islam take kokarin budewa ta futa da sauri y danna lock kofar motar ta ruke kallanta yayi yace naga kanki yana rawa ki nutsu kiji abinda xan fada miki kika sake iyayen mu suka gane irin xaman da mukeyi in muka koma gda saina saka bindiga na harbe miki kai,cikin tsananin tsoro ta dago dara2 eyes dinta ta saukesu a kansa,yace kalleni da kyau gwanda ki mutu konima na huta da wannan aurannaki da baya amfana nida komai,common girki baki iya ba balle akai ga manyan ginshikan aure ina fatan kin fahinceni,da sauri ta kada kanta dan sam takasa magana saboda jin abinda Aslam yace naxai harbeta sannan y bude motar yana ki jirani,sai daya bude seat din baya y dauko tsarabar da suka siyo sannan y xagaya y bude mata motar cikin sanyin jiki ta xuro kafafuwanta hannunta y rike cikinnasa fuskarsa dauke da murmushi part din kaka suka nufa. suna xura dai2 kofar shiga da sauri islam ta kwace wannunta ta shiga da gudu tana kaka! kaka!!kaka!!!,da sauri kaka ta futo daga daki har xaninta na faduwa da gudu islam ta tafi ta rungumeta tana farin cikin ganinta,kaka ma cikin amarya Ashe yau kin tafe,xumbura baki Islam tayi taja baya tace Allah fushi nakeyi dake baki taba xuwa ba,haka ma su mommy ta saki kaka ta juya tana komawa xanyi hawaye y xubo a idanuwan ta,lokacin yayi dai2 da shigowar Aslam da sauri y taho harda sakin kayan hannunsa kamar gaske,yana kai waya tabamin my princess dita y karaso y rungumota ganin hawaye nasauka a fuskarta yace tab kaka dukarmin mata kikayi yaja hannun islam suka xauna a kujera y daurata a cinyarsa yana goge mata hawayen da hannunsa. Kaka kuwa sakin baki tayi tana kallan ikon a ranta tace ikon Allah dama yarannan xasuyi shiri a rayuwa,cikin jin dadi kaka tace haba mai gdan nikuwa mai xanyiwa islam dita,Aslam yace to amma in ba abinda kikayi mata mai xaisa tayi kuka,kaka tace kawai fa shagwaba ce dan banxo gdan kuba,Aslam ne y fara bubbuga mata baya,yana kiyi shiru kinji mai princess islam kuwa tayi luf a kirjin Aslam tana futar da numfashi a hankali. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:13 AM] ‪+234 703 962 5239‬: na umma yahya musa* *GOYON KAKA* *94* Kaka ce tace to yar dadi miji baxaki sakko daga cinyar tashi ba kika wani dane cinyar miji ko kunya ta bakyaji,Aslam ne yace naji tsohuwar nan da iyayi to ina ruwanki koma metayi mini kema fa mijinta kikace ba wani ba ke wama yasan irin tabarar da kika yiwa naki mijin dan inaga kinada 9 years akayi miki aure,islam ce ta kyalkyale da dariya tace Allah my prince kaka tana 9 years akayi mata aure,wani dadi Aslam yaji a ransa jin irin sunan da islam ta kirashi dashi,yace eh mana islam tace tab wayaga gwida yara,a tare suka kyalkyale da dariya Aslam da islam,kaka ma dariya tayi tace naji ja'iran yara kun tasani gaba kunamin shakiyanci sai a lokacin islam ta sakko daga cinyar Aslam tace eyya kaka ta ba wani shakiyanci abinne da ban dariya kina fa 9 years kaka ce tace oho muku dai,sai lokacin suka gaidata ta amsa mika mata ledar dinta da sukayo mata shopping atamfa 1,turare1 sai sabulu cikin jin dadi ta karba tayi godiya tana saka musu albarka Aslam ne y tashi yace my princess xomuje part din su mommy tace toh ta mike hannunsu sakale cikin na juna suka fuce,kaka kuwa tsantsan farin cikin datake ciki yaki boyuwa tace ai dama nafada ana auradda yarannan xasu shirya gashi kuwa nagani da kaina ta tashi tahau rawar murna. Su Aslam kuwa suna futa,Aslam yace yayi kyau aljanar kaka kinaso wasanna mu yayi kyau,murguda masa baki kawai tayi yace kin manta matsar da nayiwa bakinki daxu ko,da sauri tasa dayan hannunta ta tamke bakin,dariya yadanyi mai sauti a haka suka karasa part din mommy suka gaidata itada daddy dayake yau sonday basu futa kasuwa da wuri ba,suma sun basu tsarabarsu sunji dadi sun saka musu albarka daddy ne y kalli islam yace my daughter dftn dai xaman naku babu wata matsala,murmushi tayi sai data kalli Aslam taga shima ita yake kallo tace,dammm kirjin Aslam y buga,lfy qlau dady,wata ajiyar xuciya Aslam yayi har sai da daddy y kalleshi,da sauri y sunkuyar da kansa,daddy yace da gaske kike daughter bayayi miki komai tace eh daddy kanta a kasa,yace to Allah yayi muku albarka sukace ameen suka tashi,part din aunty amarya suka shiga suma sunji dadin ganinsu bayan sun gaisa Abba yace son dftn dai bata baka matsala a xamannaku,Aslam ne y sunkuyar da kansa yace eh daddy muna xaune lfy tanamin abinda nakeso,murmushi Abba yayi yace to Allah yayi muku albarka y baku yaya da xasuyi muku biyayya,cikin jin kunya Aslam yace ameen nan ma suka ajiye musu tsaraba suka koma part din kaka. Islam ce tace kaka ina Amira ne,kaka ce ta karkata baki tace kinsan kasace ita tana daki tana bacci mikewa Islam tayi ta cire after dress din jikinta,tace bari naje na tasota,kaka kuwa ruke baki tayi tace yanxu islam xaku futo ma baxaki iya saka kaya na mutunci ba,islam ce tana tafiya tace to kaka menene aibun kayannan,kallan Aslam tayi tace ai laifin kane da kana gani tasaka kayan baka hanata ba,murmushi yayi yace kaka ai sam2 banason bacin ran islam dan haka abinda takeso takeyi y kwantar da kanshi a kujera y lumshe ido kaka ce tayi tsaki tace Allah y kyauta. Islam kuwa tana shiga dakin kan gado ta haye ta janye blanket ta dakawa Amira duka firgigit Amira ta farka a baccin da take,ganin islam ce ta tashe ta da sauri ta rungume ta,tana oyoyo 6 yaushe kikaxo,islam tace ban sani ba kedai ba kinanan kina bacci ba,Amira tace haba 6 bama haka dake fa,islam tadan yatsina fuska tace daxu ta tashi tana ki sameni a palo ta futa Amira kuma ta shiga bathroom. Haka su islam suka wuni a gda Aslam sai nan2 yakeyi da ita kamar gaske itama tasaki jikin ta,da akaxo cin abinci firr Aslam y dage shida islam xasuci domin a gda tare sukeci a cewarshi,haka sukaci abincinnan yana bata a baki tana basa ko kunyar su mommy basaji har suka koshi. Da kyar Aslam y yadda Islam taje gdansu khausar,hakan ma sai da Amira tace ai yaya sagir din y tafi Jordan karatu,mammy taji dadin ganin islam da xasu tafi mammy ta bata xumar mata tace tadinga sha kullum da daddare islam sarkin kwadayi ta dandana taji xaki tace toh ta gode suka futo ita da Amira,da khausar. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:16 AM] ‪+234 703 962 5239‬: Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *95* Sai da akayi sallar isha'i bayan Aslam y dawo a masallaci sunyi dinner y kalli islam yace to my princess ki tashi mu tafi,cikin shagwaba ta fara magana harda diddira kafa haba my prince nifa naxata ka dawo dani gda kenan,cikin mamaki su mommy suke kallanta,daddy ne yayi murmushi yace haba mamana ina kika taba ganin an aurar da ya ta kuma dawo gdansu da xama,a lokacin harta fara hawaye da sauri Aslam yaje y kama hannunta yasa nashi hannun yana goge mata hawaye yace haba princess harda kuka kuma,ki bari nayi miki alkawari next week xan dada kawoki kinji,cikin jin dadi ta washe hakora tace Allah my prince kansa kawai y gyada yana murmushi kallansu daddy tayi dayake hardasu Abba a palon tace mun tafi saina dawo,dariya Abba yayi yace ja'ira y kalli Aslam yace kai kuma ka takarkare kana wani lallashinta harda goge mata hawaye ko kunyar mu bakaji,lokaci daya dukkansu suka dau dariya,banda islam data tura baki gaba,Aslam kuwa keya y sosa,mommy ce ta mike tace xonan my daughter taja hannunta suka shige daki,ta kalli islam tace daughter kina tsarki da ruwan dumin danace miki murmushi islam tayi tace eh ai kwata2 ma bana tsarki da ruwan sanyi cikin jin dadi mommy tace yauwa white misk ta dauko a wata babbar kwalba tace ungo duk dare ki dinga inserting dashi kanji,cikin mamaki islam tace mommy ban game a,anan mommy tayi mata bayani,dariya islam tayi tace to maganin mene,murmushi mommy tayi tace maganin sanyine sannan xakina kanshi kinji karfa ki dinga mantawa,gyada kai islam tayi tace ai baxan mantaba mommy tace yauwa daughter na tashi muje Allah yayi miki albarka,islam tace ameen suka futa,xaune suka tarar dasu daddy 5k daddy da Abba suka bawa islam karba tayi tana godiya suka futa part din kaka sukaje sukayi mata sallama sannan Amira da sauran yaran gdan suka rakosu mota suka tafi. Tafiya sukeyi a cikin mota ba wanda yayi magana,islam ce ta kalli Aslam ta marairaice murya tace hero ice cream da shawarma nakeso,harara y dallah mata yace to mai cikin xani naga yanxu kika gamacin abinci,itama harararsa tayi ta murguda baki tace naji mutum da cikinsa ba'a hanashi cin abinci ba wasu ma yanxu suna gadon asibiti so akeyi suci amma babu hali,murmushi yayi a ransa yace yarinya tausayin ki nakeyi amma hmmm,parking ya futa y siyo mata shawarma da ice cream y mika mata,dariya tayi tace ngd yaya,kallanta yayi yace da akayi me?ta yatsina fuska tace kawai,murmushi yayi a ransa yana yarinyar nan ta daban ce watako ita bata barin takwana. Tun a mota islam ta fara cin shawarmar ta kafin suje gda harta cinye 1 tasha ice cream rabin roba,gate man y wangale musu gate Aslam y danna hancin motarsa yayi parking suka futo,islam mika tayi tace wash Allah nagaji hero kallanta yayi yace me kike nufi,kashe masa ido 1 tayi tace wai daka goyani duka yakai mata takwasa a guje sai data je dai2 kofar shiga gdan ta tsaya saboda key din yana hannun Aslam,girgixa kai Aslam yayi yace narasa wanne hukunci xanwa yarinyar nan ta dinga shakkata,sai daya dauko ledar shopping din da bilal yayiwa islam a wani dofane yana yatsina fuska tamkar y dauko kashi,sannan y dauko ta shawarma da ice cream y rufe kofar motar y karasa mikawa islam ledar kayan yace dallah can rike kin barni da rike kaya kamar wani danki,murmushi tayi tace to naga daxu ma kaika dauka acan gda,banxa yayi mata bai magana ba suka karasa shiga gdan. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:20 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *96* Washe gari islam sai 10 o'clock ta tashi kamar yadda ta saba bayan tayi sallar asuba ta koma,bayan tayi mika tayi salati ta daura da addu'ar tashi daga bacci bathroom ta shiga tayi brush ta wanke fuska futowa tayi saboda kugin da cikinta yakeyi mata sai data leka dakin Aslam ta tarar dashi fes tabe baki tayi tace oho dai baka fini tsafta ba nima dan inajin yunwa ne shiyasa ban gyara bedroom din ba down stair ta fara sauka tun tana kan step takeji wani hadaddan kanshi y doki hancinta dada hura hancin tayi ta shaka sai kuma ta lumshe ido tace kai hero ba baya bane wajen iya girki karasa sauka tayi ta leka dinning area taga bayagun,kitchen ta tafi ganinshi tayi tsaye a gaban gas cooker yana daure da eprome da hula murmushi tayi tace gud morning hero,juyowa yayi ganin ko wanka batayi ba murmushi yayi dan yasan may be yunwa ce ta korota,yace morning how are u,yatsina fuska tayi tace I'm not fine because I'm feeling hungry murmushi yayi,yace to acici meyasa baki futo tun daxu kin dafa ba xakixo ki dameni da yunwa kikeji,hakora ta washe a ranta tace baxan mayar maka ba dan bakasan yunwar da nakeji bane, tadan sosa kai tace kasan kafini iya abincine shiyasa,dai2 lokacin y gama soya kwai yace to naji xoki dauki try dinnan kikai dinning dauka tayi takai shima y futo dauke da wani try din. Yau lfyr Allah sukaci abincinsu,chips da kwai sai pepper soup na kayan ciki da tea daya saka su citta da kanin fari,bayan sun gama islam ta mike tace toh alhmdllh bayan ci xama tsegumi tana shirin barin gurin,rikota Aslam yayi yace kina nufin anan xaki bar kayan murmushi tayi tace namanta kwashe kayan suka yi suka kai kitchen futa islam take shirin yi da sauri Aslam yace ai baki isaba saiki wanke kayannan,cikin xumbura baki islam ta matsa sink din wanke2 ta fara kayan shikuma y dauki nasu get man y kirasu a waya sukaxo suka karba. Dawowa yayi suka karasa gyara kitchen din tas shida islam,sannan tahau sama tayo wanka ta dawo,anan kuma ta baje kayan wasanta tanata wasa,Aslam dayake xaune sai dai y kalleta yayi murmushi,ta takarkare tana hada girkin yar tsanarta ta kwantar da babyn a gadon ta wai tana bacci xumbur sai ta mike da sauri ta daga Babyn ta toshe hancinta tana hmmmm Allah pretty kashinnan naki wari da sauri ta tafi ta mikawa Aslam ita tace yaya riketa nadebo ruwa na wanke mata kashi,kamar soko haka y karbi yar tsanar ita kuma ta dauki bahon babyn ta debo ruwa ta futo ta ajiye ta karbi yar ta sakata a ruwan,ganin irin lallabawar da islam takewa babyn nata shine y sakashi dariya,dagowa islam tayi tana kallan Aslam can kuma sai ta kalli yar tsanar tace pretty kinga dariya yaya yakeyi miki wai dan kina kuka ko? yi shiru ki kyaleshi baruwan mu dashi. Aslam kuwa shiru yayi y tafi tunani lokacin islam tana karama shima shine yakeyi mata komai hatta wanka da wankin kashi indai yananan tayi,lokaci 1 yaji soyayyar dayayi mata tana yarinya ta dawo sabuwa fil,kiran sallah da yajine y katse masa tunani yace to my princess ki tashi ki tattara kayannan kiyi sallah kanji,sabanin yaji ta musa toh tace ta fara tattara kayan wasan,murmushi yayi y shiga bathroom din dakin kasa y dauro alwala,lokacin daya futo harta gama tattara gurin itama ta shige dauro alwala. Bayan y dawo a masallaci tare suka shiga kitchen suka daura lunch,islam itace yanka albasa,bare maggi,auno shinkafa,islam dadi y isheta ganin yadda Aslam in xai mata magana sam baya mata tsawa,sai take ganinshi tamkar sabon mutum,a haka suka gama abincinsu fried rice & chicken pepper cikin farin ciki fuskar kowa fes saboda sam basuyi fada ba. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:22 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *97* Tun daga lokacin suke wani bala'in shiri Aslam da islam,dan dama abinda yake hada Aslam da islam fitsara to yanxu batayi masa dalili kuwa tunda yace xai harbe ta kowa y huta tashiga tsoro,yayinda Aslam kuma soyayyar islam take dawainiya dashi yake ratsa dukkan jiki da bargonsa. Tafiyarshi sai karatowa takeyi yau y kama saura 2 days y tafi photercourt amma y kasa sanarwa da iyayansa,shi yanxu a yanda yakejin islam ma baya tunanin xai iyayin nesa da ita kona 2 weeks balle har 2 years danso yakeyi yanxu y shafe mata kiyayyarsa y cusa mata soyayyarsa,xaune suke a palo dabara ta fado masa wayarsa y dauka ya fara dialing number din general yusuf ringing takeyi sai data kusa katsewa sannan general y dauka. Aslam yace: _assalamu alaikum_ General y yace: _wa'alaikumussalam_ Aslam yace: _barka da yamma oga dftn kan lfy?_ General y yace: _brkn mudai dftn kaima haka_ Aslam yace: _lfy qlau ammm sai kuma yayi shiru_ General yace: _ya akayine Aslam ina jinka_ Aslam dakyar y daure yace: _yallabai dama so nakeyi naji bayani akan tafiyarnanne_ Murmushi general y yayi yace: _tananan Aslam wani abune y faru_ Dan sosa kai Aslam yayi yace: _eh wlh yallabai da cewa xanyi ko da akwai yadda xa'ayi a fasa tafiyar dani?_ Murmushi general y yayi yace: _ai dole kayi tafiyar nan saboda ka riga daka amsa,ni kuma natura sunayenku can head quarter da pics dinku,shiyasa tun farko na tambaye ka saboda nasan kana da amarya,yanxu dai kawai hakura xakayi ayi tafiyar dakai,tunda kaga ba ta yadda xa'ace musu ga wani baxai iya xuwa ba alhalin ba rashin lfy kakeyi Ba_ Aslam cikin sanyin jiki yace: _insha Allah jibin xan taho yallabai a huta lfy_ General y yace: _Allah y kaimu sukayi hiding din wayar_. Yau y kama Aslam saura 1 day y tafi kuma flight din 7:00am xai hau,shiyasa y yanke hukuncin yau xai kai islam gda su kwana acan washe gari y tafi,dan bai masan y iyayensa xasu dauki maganar ba dan yau yakeson sanar dasu,da misalin 4 o'clock Aslam da islam ne xaune a palo islam tace ni gaskiya hero mangwaro xansha,murmushi yayi yace haba princess mangwaron gdannan fa sam bai nuna ba,xumbura baki tayi ta juyar da kanta gefe,Aslam ganin islam na shirin yin fushi da sauri y mike y ruko hannunta yace haba princess fushi kuma to muje,washe hakora tayi sukabi ta kofar kitchen suka futa. Tsaye Aslam yake y daga islam tana tsinko mangwaro guda 3 ta tsinko nan ta farajin kukan mage,cikin tsoro tace hero kukan mage fa nakeji ko? yace eh to me xatayi miki? cikin rawar murya tace nidai ka saukeni mu tafi banason mage tsoronta nakeyi ta karashe maganar kamar xatayi kuka,Aslam yace toh mangwaron y isheki haka? da sauri tace eh sauke ta yayi yace toh mu tafi,hannunta cikinnasa suke tafiya sai rarraba ido takeyi saboda har lokacin tana jin kukan magen,cak ta tsaya tare da kwalla kara ganin magen a gabanta tana kallanta,kankace me islam ta tafiii luuu ta suma tana shirin faduwa cikin xafin nama Aslam y dagata cak kan takai kasa yayi cikin gda da ita cikin sauri. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [12/9, 5:00 PM] Habiba Abdullahi Ali : (9/12/2016 1:00pm) *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *98* Da gudu y karasa palo y kwantar da ita a three seater despenser y tafi y kunna ruwa a kofi da sauri y karasa y yayyafa mata,wata doguwar ajiyar xuciya taja da sauri ta mike ta kankameshi tana kuka tana wayyo yaya mage banasonta a ka mayar dani gda Allah baxan kara kwana a gdannan ba duk cikin gunjin kuka take magana tabi ta cukukuyeshi ta runshe idonta,a hankali yake shafa bayanta yana sorry my princess kiyi shiru ki bude idonki kinga mun shigo palo ko bata yadda magen xata biyoki ki tayi a hankali yaci gaba da shafa mata baya yana hura mata kunne,ji yayi numfashinta na sauka a hankali,anan y gane bacci takeyi amma duk da haka a makale take a kirjinshi,leka fuskarta yayi yace islam rigima in anga kin nutsu to abinda kike tsorone murmushi yayi yana kallon kyakykyawar fuskarta,a hankali yakai hannu y shafi dan karamin pink lips dinta peck yayi mata a kumatu y dada rungumeta yanajin wani daddadan shauki a ransa daganan bacci y kwasheshi. Xaune suke acikin lambun gdansu shida princess dinshi tanata yi masa shagwaba shi kuwa sai nan2 yakeyi da ita wasu kyawawan kids ne kuda 2 mace dana miji suka taho a guje ta macen tanamin namijin a baya sai y bata popcorn dinta,shima gudu yake yana cin popcorn din xagaye su Aslam sukeyi macen ganin ta gaji kuma ta kasa kama namijin kawai saita fadi tahau birgima akan grass carpet da sauri Aslam y tashi yaje y dauketa yana meya faru my daughter,cikin gwaranci dayake batafi shekara 2 da rabi ba,tace ba shultan bane ya aukan mun popcorn ina ba ta karashe maganar dason yin kuka,Aslam ne y kalli sultan yace ah haba karka xama babban banxa mana ka dinga saka kanwarka kuka,islam tace oya my son basu abinsu kasan sultana da shegiyan rowa maxa bata in mun shiga gda xan baka ice cream ,xuwa gurin sultana yayi yace ungo marowaciya baxan kara baki chocolate dina ba kuma yanxu in mammy taban ice cream baxan baki ba,da sauri ta kwace tana murguda baki tace eh din kakkabani in ai daddy na xai shiyomin nima ko tana kallan Aslam* Firgigit y fara daga mafarkin dayakeyi wani dadi yaji a ransa,yace tabbas wannan mafarkin yana nufin my princess kece farin cikina kuma hasken idanuna Allah y nunamin ranar da xaki xama uwar yayana wani murmushine y kwace masa kiran sallar magruba yaji a hankali y fara kokarin kwantar da Aslam a kujera y samu yaje y dauro alwala,firgigit ta tashi tana mitststska ido kallanta yayi yace my princess kin tashi kai kawai ta daga masa,yace to xauna naje na dauro alwala,kafada ta make tace uhm uhm mikewa yayi yace alwala fa xanyi itama xuruf ta mike ta kama hannunsa haka suka shiga daki nan ma kin xama tayi tace saita bishi bathroom rike kansa yayi yace oh babynnan kin fiya rigima y lakuce mata hanci,haka suka shiga bathroom din yace to xanyi fitsari idon ta ta kulle murmushi yayi,sai dayayi fitsarinsa yace toh nagama sannan ta bude idonta itama tayi fitsarin sukayi alwala suka futo a tare,sallah ma sai a gda yayi saboda islam takafa ta tsare sam ta hanashi xuwa masallaci. *plz kuyi hakuri xakuga na yau kadan chargy ne bani dashi dftn xakumin hakuri* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:29 AM] ‪+234 703 962 5239‬: (11/12/2016 2:00pm) *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *99-100* Bayan sun idar da sallah,ganin da Aslam yayi islam sam ta kasa sakewa shine y sakashi yanke hukunci ya kaita gda yanxu kawai,kallanta yayi yace my princess kina so kije gda da sauri ta gyada kai,yace to ni kuma in xauna dawa?yayi mata wannan tambayar,rau2 tayi da ido alamar sonyin kuka tace dan Allah yaya ka mayar dani gda kaima saika koma can da xama kawai,murmushi yayi jin wautar da tayi yace to naji dama yanxu xa'a turamu wani cause singapore at least xamu iya kai 2 years shine da nakeso mu tafi tare y kika gani,tsare ta yayi da ido yanaso yaga yanayin da xata shiga ko xata nuna damuwarta a kansa tace xata bishi,shiru tayi can kuma ta dago kai tace yaya makaranta tafa,yace acan xan sakaki,daga kanta sama tayi kamar mai tunani can kuma tace yaya kasan mene,cikin sauri yace a'ah saikin fada murmushi tayi tace kawai ka barni a gda ni gaskiya baxan iya tafiya wani garin ba na daina ganin su kaka,wani kululun bakin ciki yaji a ransa yace kaddai ni kadai nake shirmena bama tasan irin mugun sonta dayake fixgar raina ba watako ita duk shakuwar nan da mukayi ta dan lokaci ita batajin komai a kaina,dabara ce ta fado masa yace to yanxu inna tafi baxaki dinga tunani naba ya karashe maganar da kashe mata ido 1,dariya tayi tace eh to xan dinga tunaninka nace Allah sarki yaya Aslam yanacan shi Kasai kowa xai dinga duka yanxu saita kuma dariya tace ammafa ba sosai xanna tunanin kaba tunda kaga yanxu mun daina fada cikin jin haushin shirmen da takeyi masa yasaka shi cewa to naji tashi muje ki hada kayanki cikin farin ciki ta tashi harda rawarta shikam tsayawa yayi kallanta mamaki fal fuskarsa,harararta yayi yace to in kin gama dariyar saiki taho muje ko wlh ki fasa tafiya gdan nasamo miki mai tayaki kwana,dariya tayi tace Allah y baka hakuri yayana suka haura stair. Da kanshi y harhada mata kayan ganin irin rawar jikin da takeyi shine y dada kular dashi hautsina gashin kansa y fara a ransa yace ai laifinane dana amsawa general xanyi tafiyar nan gashi son yarinyar nan yana son haukatar da da karfi yace oh god y xanyi,saurin dafashi islam tayi tace lfy yaya notting kawai yace mata,tabe baki tayi shi yaja mata katuwar trolley bag din ta don baxata iya dauka ba shima y shiga nashi bedroom din y dauko yar madaidaiciya wadda kayan ciki basufi 4 set ba,islam ce ta karbi nashi suka futa a bayan booth suka xuba kayan suka shiga suka tafi. Islam ce ta shiga part din kaka da gudunta tana kwalawa kaka kira,kaka da take palo ta kalli Amira tace wa nakeji ne kamar isla.………kafin ta karasa rufe baki islam ta shigo da gudu ta fada kanta,kaka ma cikin farin ciki kaka ta rungume ta tace kece tafe,dariya islam tayi tace eh ai yayan ma y dawo dani gda cikin mamaki kaka take kallanta tace saboda me,islam ce tace kai kaka wlh kin fiya tambaya to ki jira yayan yaxo saiki tambaye shi,kaka tace to naji yar nema ina mijinnaki,murguda baki tayi tace ni ban……bata karasa ba tayi saurin rufe baki tace yaje masallaci (nikuwa nace yarinya ta tuno mutuwa ). Bayan Aslam sun dawo masallaci dasu daddy anan yakeyi musu bayanin tafiyarshi,amma y boye musu cewa shine yanaso yace xabarshi akayi,sunyi masa fatan alkhairi da addu'ar Allah y bada sa'a. *Dan Allah kuyi hakuri xakuga yau 1 nayi typing wlh hakan y farune sakamakon wutar nepa din mu data Lalace,nikuma banayin typing din dare saboda oga dftn xakuyimin uxiri* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/7, 9:35 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *101* Lokacin da Aslam y futo daga part din daddy direct part din kaka y tafi,lokacin daya shiga tarar dasu yayi a xaxxaune suna kallo islam na kwance a cinyar kaka,kararsawa yayi y xauna a daya side din y daura kanshi a kafadar kaka yana ina wuni uwar gda sarautar mata,islam ce tayi tsalam ta mike tace yaya dama kaka ce matar taka harkake cewa tafini kyau tab wayaga chakus,aka kyalkyale da dariya dukka palon,Aslam kuwa kallanta y shiga yi da tsantsar mamaki,kaka ce tace islam waya ke fadawa nice matarsa da sauri islam tace.…………ganin da Aslam yayi xata yi baran barama shine y sakashi yin gyarar murya,da sauri islam ta dawo nutsuwarta ta yatsina fuska tace wai fa ni yake fadawa yana da mata kyakykyawa wai hartafini kyau da gashi ashema kece,kaka tace to ai nafiki kyau dinne da sauri islam ta tashi ta mike ta juya ta karkada gashinta tayi wani farr da ido tace a hakan kika fini kyau,Aslam kuwa sakar baki yayi yana kallabta yadda take kada eyes balls dinta tayi bala'in burgeshi kamo hannunta yayi yace haba my wife yama xa'ayi kaka ta fiki kyau kawai tsokanarki nayi ai duk duniyar nan babu matar data kaiki kysu,da sauri ta dada kada idanuwanta tace da gaske yaya,tsareta yayi da ido y kada kai wani ihu ta saki hade da tsalle ta fada kanshi ta rungumeshi hade dayi mishi peck a kumatu,bashi da yayi mutuwar xaune hatta kaka sakin bakin tayi tana kallan islam yaran palon kuwa sun sunkuyar da kai suna dariya kasa2,islam kuwa mikewa tayi ko a jikin ta taci gaba da abinda takeyi,kaka ta kalleshi tace da gaskene wai ka dawo da yar rigimar nan gda,kansa kawai y kada y kwantar da kansa a kan kujerar y lunshe ido,kaka tace saboda me anan yakeyi mata bayanin tafiyar data taso masa,tayi masa fatan alkhairi daga nan sukaci gaba da kallo,Aslam kuwa idanuwansa suna kan islam yana kallan duk wani motsi da tayi mugun sonta yana fuxgarsa. 10:00pm yaran duk sun tafi dakunansu sai kaka da Aslam,islam,Amira sune kawai a xaune a palon kaka data fara gyangyadi tace to mai gdan kadauki matarka ka tafi bangarenku mu xamu rufe bangaren mu,a tare Aslam da islam suka dago kai suna kallan kaka katse su tayi tace menene kuke kallona in kallanne bai isheku ba in kunje naku bangaren kwa kalla,Aslam ne yace to ai ni da so nayi ta kwana anan da sauri islam tace eh eh kaka anan xan kwana,kaka tace ku ji shirme yanxu kai Aslam da xakayi tafiya har tsahon shekara 2 shine baxaka kwana da matarka kuyi sallama ba,dan sosa kansa yayi yace eh hakane y kalli islam yace taho mu tafi my princess xumbura baki tayi tana ni Allah,Allah tana bubbuga kafarta a kasa kaka ce ta harareta tace ke Allah me,xaki tafi ko saina bubbuge ki kujimin yarinya da munafunci da acan gdan dawa kike kwana,hartace ni…………da sauri Aslam y tashi yaja hannunta yace kaka saida safe bin bayansu tayi tana Allah y kaimu ta rufe part dinta. Su Aslam suna futa islam ta kwace hannun ta tayi rau2 da ido tana kallon Aslam tace to wai yanxu dakai xan kwana?yace eh dan shine kadai mafuta,cikin tsiwa tace tab kato dakai xan kwana daki 1 dakai nidai bari natafi part din mommy tayi gaba saurin ruko hannun ta yayi yace ke bakida hankali ne kina ganin kaka ta koromu in kinje me xakicewa momyn?daga kai tayi alamar tunani sai kuma tace yauwa na tuno cemata xanyi kaka ce tace wai saina bika dakin ka na kwana alhalin malamin mu yace manxan Allah (s.a.w) yace indai mace da namiji suka kadaita su 2 tona 3 su shaidanne,kuma malam yace xasu iyayin abinda bai kamata ba mu gujewa kadaita da maxajen daba muharraman muba,murmushi Aslam yayi a ransa yace naga ranar da xaki daina shirme princess,kallanta Aslam yayi yace naji hadithin naki amma a wadanda akace kar a kebanta dasu harda miji karya kebe da mata,shiru tayi sai kuma tace a'ah banda miji yace toh oya mutafi dakina mu kwanta tunda kinga ni mijinki ne ko? to tace amma Allah yaya sai dai ka goyani koka daukeni dan hararar wasa yayi mata y tsuguna yace hau muje yana iya da sauri ta dane bayanshi tana kyalkyala dariya tana masa cakulkulu shima yana dariyar a haka suka shiga part dinsu,su amir ne a palon a xaune da sauri islam tace hey brothers,murmushi sukayi mata sukace hello 6*,Aslam kuwa da kunya ta isheshi tamkar kasa ta tsage y shige yace wa islam to sakko ai munxo kafada ta make tace a'ah saika kaini daki cikin shagwaba tayi maganar sum2 Aslam y shige da ita su amir kuwa sukace me xasuyi in ba dariya ba suka kyalkyale da dariya. Taku har kullum *sisin mama* 💘[3/8, 9:30 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *102* Suna shiga dakin Aslam yace dallah can sakko,kyalkyala dariya tayi tace Allah yaya bayan nakane dadi ta dada lafewa,tsaki yayi yace wai xaki sakko ne ko kinga ina wasa dake sakkowa tayi a bayannashi y kalleta yace watako ki nunawa mutane kema kin girma kinsan dadin miji shine inayi miki magana kika kiji ko y tsatstsareta da idanu,xumbura bakinta tayi tace to naga dai lada ka samu ko kuma malamin mu yace ai duk abinda miji ko mata tayiwa mijinta ko yayiwa matarsa dan suji dadi lada xasu samu ta karashe maganar da murguda baki,bakinnata y kama yace wannan bakin tsiwar nakusa kasheshi y daina yiwa mutane rashin kunya yar kara ta saki tace Allah fa da xafi yace eh ai shiyasa nayi miki dannasan da xafin kara murguda bakinnata tayi hannu yakai xai kamota da sauri ta kwasa da gudu xagayen dakin suka fara aikuwa islam sai xillemasa takeyi in tayi nan yaga kamar xai kamata saitayi masa gwalo ta kara xullewa haka sukayi ta xagaye shi kanshi Aslam yayi mamakin yadda y kasa kamata daya gaji dan kansa y fada kan gado yana mai da numfashi,islam ganin harya gaji shine y sakata yin dariya itama tahau kan gadon ta kwantar da kanta akan girjinsa itama tana mai da nunfashi da sauri y rungumeta yana wana kama saurin kama bakinta tayi tace ni amma Allah y baka hakuri make kafada yayi yace ni baxan hakura ba y kwaikwayi maganarta dariya tayi tace yaya kaima ka iya shagwaba dariya shima yayi yace eh to xama da kene na kora murmushi kawai tayi,can bayan kaman 2 minute yaje my princess ki fadamin abinda malaminku yace in mata tayiwa mijinta xata samu lada,tace to yaya ladabi,biyayya,girki in miji yacewa matarsa tayi masa Abu to tayi masa in kuma y hanata to kartayi,girgixa kai yayi alamar gamsuwa yace iyasu kadai y fada muku,tace eh amma yace wai in miji y kira matarsa kan shinfidarsa tace in taki mala'iku xasuna shine mata har gari y waye sai ta mike xaune tace yaya me kenan malam yake nufi da hadisinnan lokacin da yayi mana shi yace ba a lokacin xaiyi mana bayani ba wai saimun kara hankali murmushi Aslam yayi yace ki bari naje nayi wanka inna futo saina fada miki cikin jin dadi tace toh ta kwanta shikuwa towel y dauka y shiga wanka,xuwa 20 minute y futo kallan islam yayi yaga hartayi bacci murmushi yayi y shafa mai da body spray ya saka kayan bacci ballar maganinsa yayi yasha saboda jin mararsa tanayi masa ciwo,light off yayi musu y kwantah shima a gefen islam y janyota y daura kan girjinsa yaja musu blanket a hankali shima daddadan barci y kwasheshi. Washe gari da asuba bayan Aslam y tashi ya shiga bathroom y dauro alwala,sannan y tashi islam masallaci y futa itakuma tayo alwala ta shimfida sallaya ta tada sallah bayan ta idar axkar tayi da ka sannan ta dauki qur'ani ta fara karantawa tana cikin karanta suratul yusufa cikin xaxxakar muryarta Aslam y dawo daga masallaci xama yayi yana saurarar kira'arta ta hafsi gashi tana fidda tajweedi sannan tana bawa ko wanne harafi hakkinsa lunshe idanu yayi yana binta a hankali hartaxo karshen shafi tayi sadakallahul axiim ta rufe,Aslam ne y bude idanuwansa yace Allahu Akbar kallanshi tayi tace ina kwana yaya lfy qlau yace ganin agogo yayi 6:40am tashi yayi yace jeki kiyi wanka princess xaku yi dropping dina a airport keda Amir jikin ta taji yayi sanyi tace to ta tashi ta futa. Xuwa 6:15am sun gama shiryawa Aslam y futo sanye da wandon kaki da conbart brown colour irinna sojoji sai y saka white t.shirt da yake dukka gdanne xasu rakashi daddy,mommy,Abba, aunty amarya, kaka,Amira,Amir,haidar da sauran yaran gdan xasu rakashi airport Aslam a baya da islam,sai Amira da Amir a gaba su daddy kuma mota 2 suka cika sukabi bayansu. 6:40am suka isa airport Amira da Amir suka futa a motar suka barsu islam Aslam ne y janyo islam jikinshi yace my princess kinga tafiya ta kamani bata sati 1 Ba,ba 2 ba,ba wata 1 ba, ba wata 2 ba,tafiya ce har tsahon 2 years inaso ki kulamin da kanki ki rikemin amanar igiyoyin aurena dake kanki,hawaye taji sun fara xubo mata a hankali batayi yunkurin gogewa ba sai sunkuyar da kanta da tayi yana kallan kasa,yaji gaba nasan xuwa nan da lokacin daxan dawo kin dada wayo da girma kinsan hakkokin aure kinsan hakkin mata akan miji kinsan na miji akan mata,a hankali kukan da take boyewa y fara futowa rungumota jikin shi yayi yace my princess dakin san yadda xuciyata takeyin xafi inna tuno xan rabu dake har tsahon 2 years dakin daina dada axabtar da ita da kukanyi a hankali yaci gaba da fadawa islam dadadan wadanda kwakwalwarta ta kasa dauka ma sai ajiyar xuciya da takeyi a hankali y dago fuskarta ganin har lokacin hawayen fuskar nata bai tsaya ba,shine y sakashi saka harshensa y fara lashe mata,islam jin sabon yanayin da tayi shine y sakata runtse idanuwanta tana fidda numfashi da karfi da karfi saboda yadda bugun xuciyarta y dadu,bata dada tsinkewa da lamarin Aslam ba sai dataji bakin Aslam cikinnata ai saura kadan numfashin ta y dauke,ta bangaren Aslam din ma hakane saboda shima sabon shigane wani irin salo yakeyi mata wanda islam takeji kamar ba'a duniyar mu takeba,sai da yayi kissing din bakinta sosai Amir ne y katse su ta hanyar kwankwasa glass din motar saboda tintack ne dakyar Aslam y xare harshensa yana mai da numfashi,islam ma hakan take dan duk jikinta y mutu,Aslam y kalli islam yace inasonki matata xanyi kewarki sosai, *I LUV U TOO MY WIFE*,ya dada yi mata peck a kumatu y bude murfin motar y futa, _islam kuwa jinta takeyi tamkar wata sabuwar halitta a ranta kuwa cewa takeyi dama yaya Aslam dan iskane ai kuwa xuwa xanyi nafada mommy yaya Aslam dan iskane tasaka y sakeni,sai kuma tace to ai kuma mommy tace nadinga boye sirrin mijina tagumi tayi tace to yanxu y xanyi,wata xuciyar tace kawai ki jirashi y dawo kice y sakeki baxaki iya xama da dan iskaba,da wannan tunanin ta samu mafuta,muryarsa ce kuma ta fara mata amsa kuwwa a kunne lokacin da yakece mata ina sonki sosai matata xanyi kewarki sosai_ *I LUV U TOO MY WIFE* kwantar da kanta tayi akan seat ta lumshe idanuwanta. Aslam bayan y futà a motar yaje yayi sallama da iyayanshi y shige cikin airport sukuma suka shiga mota suka koma gda* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:31 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *103* Aslam ma a jirgi murmushi kawai yakeyi saboda farin cikin da yake ciki in y tuno da sweat & soft lips din islam saiya dada wani lumshe ido y saki murmushi a haka har suka a airport. Safwan ne yaxo daukarshi ganin irin annurin da yake fuskar Aslam tare da tsantsan farin ciki shine y saka shi murmusi,yace watako abokina duk farin cikin rabuwa da jerry din takane yasa ka har yanxu kake cikin farin ciki,wani banxan kallo Aslam yayiwa safwan yace babu abinda y shafeka da farin cikin da nake ciki yayi dan karamin tsaki yace dan sa ido kawai y shige mota,murmushi safwan yayi yace ina tausaya maka abokina shima y shiga motar. Islam kuwa koda suka koma gda direct part din kaka ta wuce bedroom ta shiga ta kwanta kawai tunanin Aslam takeyi in ta rufe idanuwa ma shi take gani,wani mugun kewarshi takeji dan a dan 1 week din da sukayi suna shiri bakaramin shakuwa dashi tayi ba,yadda taji xuciyarta tana axalxalarta shine kawai y sakata kuka dan baxata iya tolerating radadin da xuciyarta yakeyi mata ba,Amira ce ta shigo dakin jin shashshekar kukan islam tayi da sauri ta hau kan gadon tana 6* lfy meya faru,islam rasa abin cewa tayi kawai taci gaba da kukanta,murmushi Amira tayi tace kodan yaya yayi tafiya shine kikeyin kuka,cikin masifa da borin kunya islam ta hayayyakowa Amira tace Allah y kiyaye kawai dan hero yayi tafiya saina dinga kuka,Amira ce tace in bashi kikewa kuka ba saboda me kikeyin kuka nifa dama tunda akayi aurannan naku nafahinci kuna mugun son juna,jikin jin haushin kalaman Amira Islam ta dauki pillow tahau dukanta tana Allah y sauwake naso wannan mugun,dariya Amira tayi ta tashi tace in tayi wari dai maji ta fuce a dakin,islam kuwa kwanciya tayi tana kuka kasa2 daganan bacci y dauketa. Aslam kuwa bayan ya isa gdan shi y shiga bedroom dinshi kwanciya yayi y dau pillow y rungume shi tsam a jikin shi yana tunano daddadan kanshin turaren islam shima daganan bacci y daukeshi. Aslam sai misalin 10:00am y farka sakamakon wayarsa da take ringing cikin tsaki y janyo wayar saboda bakaramin dadin baccin yakeji ba ko sunan wanda y kira bai duba ba kawai yayi picking yasa a kunne muryar da yajine yasaka ranshi baci da sauri y mike y xauna akan gado. Bilal yace: _brk da safiya yayanmu_ Yatsina fuska Aslam yayi tamkar wani mace yace: _brkn mudai_ Bilal: _y gda y amarya?_ Aslam: _duk lfy_ Bilal: _dama kiranka nayi naji y amanata dftn kana kularmin da ita sosai?_ Tsaki Aslam yayi yace: _bangane ba wance amanar taka?_ Murmushi bilal yayi yace : _haba abokina yanxu harka manta amanar islam dana danka maka?_ Murmushi Aslam yayi wanda kana gani kasan na yakene yace: _eh yanxu natuna amma nikam bana kano nakoma photercour_ Bilal yace: _eyya to yanxu y xa'ayi naga flower ta saboda nayi mata ban ruwa,kasan dalilin daya saka tuntuni bankira kaba dana dawo gda natarar da iyayena sunyi min mata,amma sam nanuna musu bana sonta inada wadda nakeso dakyar na shawo kansu suka amince yanxu sunce nabasu address din gdansu yarinyar xasuje nemamin auran ta gashi bansan address din gdanku ba narasa yadda xanyi wlh ina mugun son islam y karashe maganar tamkar xaiyi kuka_ Aslam cikin bakin ciki da takaici a ransa yace lallai kuwa xaka mutu,yacewa bilal kawai kayi biyayya ga iyayenka shine shawarar daxan baka ya katse kiran wani mugun wulli yayi da wayar ta daki jikin bango a take ta tarwatse jifa y farayi da komai y dauka a dakin y barbaxa gashin kansa idanuwansa sukaji jajawur gashin jikinsa duk suka mike da karfi da karfi yake sauke ajiyar xuciya. Bangaren bilal kuwa ba karamin tashin hankali da firgici y shiga ba musamman daya sake kiran Aslam yaji ance is not reachable dafe kanshi yayi da hannuwa 2 yake na shiga 3 mai kenan yake nufi da hakan ko xaicemin shi baisan radadi da xafin soyayya ba haka yayi ta try din number din Aslam amma sam bata shiga da sauri y xari key din motarshi y fice. Aslam kuwa dakyar y samu nutsuwa y mike tattara kayan daya warwatsar a dakin y farayi lokacin dayaxo gurin wayar dada takata yayi simcard da memory card y cire xai taune simcard din y tuna tsohon layinsa ne y bashshi amma y dauki alwashin duk ranar da bilal y kara kiranshi sai yayi masa rashin mutunci yana gama tattara kayan dakin y fada bathroom y sakarwa kanshi shower. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:33 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *104* Islam kuwa sai 11:00am ta tashi bathroom ta shiga tayi wanka da brush bayan ta futo ta shirya palon kaka ta futa amma sam fuskarta ba annuri a murtuke xama tayi taci abinci ta koma daki,kaka ce ta kalleta sai tayi murmushi tace tab lallai yau xa'ayi ruwa da kankara kenan,Amira da take xaune tace wlh fa sukaci gaba da hirarsu suka manta da babin islam. Bilal kuwa yana futa direct airport yaje y yanki ticket xai tashi 5:00pm cikin murna y dawo gda dasa ran yau duk wadda xa'ayi sai dai ayi amma tabbas Aslam sai y bashi address din gdansu. Misalin 5:00pm Aslam y futo sanye da blue jeans da black t.shirt sai y saka black shoe mai dan yatsa kanshi yasha gyara jikinsa sai baxa kanshin perfumes yakeyi,safwan y tarar xaune a palo yana kallo kallanshi yayi yace bari naje nasiyo waya,safwan y maimaita waya kuma Aslam yace eh safwan yace ina wayoyinka yatsina fuska Aslam yayi yace daya ta fashe ne daxu,kallansa safwan yayi yace ta fashe kamar yaya,tsaki Aslam yayi yace dan Allah malam ka fiya tambaya kamar dan harida tunda nace maka ta fashe ai shikenan ko? yasa kai y fice,tsaki Aslam yayi yace banxa mutum sai bakar jaraba Allah y nunamin randa islam xata gyaraka wlh na kwashi shoki. Lokacin da bilal y sauka a airport taxi y tsare yace plz barrack xaka kaini na sojoji to mai taxi yace tun daga nesa da gate din barrack din mai taxi y tsaya yace to yallabai anan xan iya tsayawa dan inna wuce nan tofa tsallan kwado xanyi dan sojojin can ba imani ne dasu ba,murmushi bilal yayi yace to ngd yadauki kudin shi y bashi,futa yayi yana karasawa cikin barrack din a hankali,yaje dai2 xai shiga wani soja yace hey man ina xakaje,cak bilal y tsaya yace ni abokin captain A.U Abdul ne,da sauri wannan sojan yace sorry sir Ashe kai abokin ogane tuba nakeyi ai bansani ba nayi maka tsawa,murmushi bilal yayi yace bkmai yanxu y xa'ayi naje gdannashi saboda yaune xuwana na farko kuma tun ina kano nayita trying din number shi baya shiga,da sauri sojannan yace muje na rakaka yayiwa abokan aikinsa inkiya da hannu yanxu xai dawo. Dai2 kofar gdan Aslam yace ga gdannan oga,godiya bilal yayi masa y dauko 10k y bashi cikin rawar jiki sojannan y karbi kudin yana y gode,murna kuwa fal a ranshi yau xaije club,bell din gdan bilal y danna,safwan da yake xaune yace watako man dinnan harya dawo ko yaje y bude,ganin bakuwar fuska da safwan yayi shine yasaka shi cogewa y kalli bilal yace sannu ko,da sauri bilal y mika masa hannu sukayi musabaha,bayan sun gaisa bilal yace dan Allah gdan captain A.U nake nema shine aka kawoni nan sai kuma naga bashi bane dan Allah kayi hakuri,murmushi safwan yayi yace ai nanne gdannasa yanxu y futa shigo ni abokinsa ne sunana safwan cikin jin dadi bilal y shiga palon ganin baisha wahalar samun gdan ba. Kitchen safwan y shiga y dauko ruwa da lemo y sako akan try da cup y futo,direwa yayi a gaban bilal y janyo center table y daura masa,godiya bilal yayi y tsiyayi ruwa yasha,kallansa safwan yayi yace amma a abokanan bilal dana sani sam baka cikinsu,murmushi bilal yayi yace eh gaskiya ni abokin shine na secondary skul kuma rabona dashi tunda mukayi candy dan ko lokacin bikinsa bana kasarnan,gyada kansa safwan yayi alamar gamsuwa,suna cikin hira Aslam y shigo dayake a bude safwan yabar kofar sallama kawai Aslam yayi ko kallan inda su safwan suke baiyi ba y fara tafiya xai shiga bedroom,safwan ne yace bako fa kayi Aslam kuma naga kana kokarin wucewa cak y tsaya yana tunanin toshi wama y sani a photercort da har xaixo gurinshi. Lokacin guda annuri da farin cikin dayake fuskarsa y gushe tamkar wanda yayi gamo da abokin gada,sakamakon bilal daya gani a xaune. *_ina godiya a gareku masoyana masu kirana da masu yimin magana ta whatsap ina gaisheku a duk inda kuke a duniya_* *I LUV U ALL MY FANS* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:34 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *106* Bayan sun xauna safwan yace to kuyi hakurin dukkanku ku sassauta xuciyarku daukar wayarsa safwan yayi datake a gefenshi y bude gallery pic dinsu Aslam da islam ne y futo na biki mikawa bilal yayi yace inaso dan Allah ka nutsu ka kalli hotunannan nasan sune kawai hujjar da xaisa ka yadda da abinda xan fada maka,karba bilal yayi lokaci daya komai nasa y tsaya cak sakamakon pic din islam da Aslam daya gani kuma ko ba'a fada ba yasan wannan hotunan bikine,kallansu yakeyi a hankali jikinsa duk yayi sanyi lokaci daya yaji wata muguwar kunya ta kamashi mikawa safwan wayar yaji jikinshi duk y mutu. Safwan y karba yayi murmushi yace nasan ko pic dinnan daka gani y isheka shaidar cewa Aslam shine mijin islam,amma bari nakara maka bayani islam cousin sister din Aslam ce,anyi musu aure sam duk cikinsu babu wanda yakeson dan uwansa kai barima kaji nafada maka ni dinnan nine silar da islam ta xama matar Aslam,cikin shock Aslam y dago kai yana kallan safwan,murmushi safwan yayi yace eh kalleni dalili kuwa anan shine anan y fara bawa bilal lbrn irin rashin jituwar da Aslam da islam basayi,har yaxo kan lokacin da Aslam y fara cuta shine y fadawa su daddy Aslam duk duniya islam yakeso shiyasa yaki fitar da matar aure,dariya bilal yayi sosai dan harya manta da bacin ran dayake ciki yace tabbas safwan ka kyauta kuma ka xamto aboki na gari wanda kowa yake burin samun irinsa,anan y fadawa safwan yadda akayi suka hadu dasu islam a shoprite da kuma yadda Aslam yace masa kanwarsa ce,kuma da yadda islam ta saki jikinta dashi dukkuwa da yana kula da irin yanayin da Aslam din yake a lokacin amma shi bai kawo komai a ransa ba,da kuma yakan kama islam tanawa Aslam gwalo dariya suka dada tuntsirewa da ita Aslam kuwa sai wani shan kanshi yakeyi,bilal ne y kalli Aslam yace captain kayi hakuri ni bansan matarka bace da duk haka baxata faru ba,Aslam cikin jin kunya yace nima kayi hakuri da abinda nayi maka nasani duk laifinane amma na runtse ido nadinga yi maka rashin mutunci,dariya bilal yayi yace bkmai ai ko yanxu safwan y tabbatar hakarshi ta cimma ruwa saboda tun kafin aje ko ina ka tafka kokin kaunar islam saboda yadda ake ganin tsantsan kishin islam a idanuwanka,dariya suka dada kwashewa da ita safwan y mike yace y xama dole na kwashi shokki saboda alkawari ne nadaukarwa kaina duk ranarda abokina y fara son islam sainayi rawa y fara kwasar rawarsa,cikin kufula Aslam y dauki pillow din kujera y jefawa safwan dariya suka kumayi,kiran sallar magruba ne y tashesu suka tafi masallaci. Bayan sallar isha'i xaune suke su Aslam a palo,safwan y kalli Aslam yace nifa abokina nayi mamaki da aka sakaka acikin jerin masu tafiya singapore dinnan dan naga kai kana hutun angwanci,tsaki Aslam yayi yace duk nine na jawowa kaina lokacin da general y kirani yace xan iya xuwa nace masa eh saboda a ranar princess taban haushi anan y basu lbrn drama din da sukayi akan abinci,dariya suka dingayi safwan harda rike ciki,safwan yace watako ita jerry dinnan taka bata yadda ayi 1-0 ba tafiso atashi 1-1,hade rai Aslam yayi yace banason wulakanci in baxaka kirawo sunanta ba ka barshi ba'a dole dan wulakanci matar tawa xaka dinga hadawa da beran cartoon,dariya safwan yayi yace gwandani da beran cartoon na hadata wani kuwa cikin jinsin mutanen boye yake hadata dasu,duka Aslam yakai wa safwan y goce,dariya suka dada kyalkyalewa da ita. Washe gari 7:30am suka kai bilal airport y wuce kanon dabo ,su Aslam kuwa 10:00am jirginsu y daga xuwa singapore,ina yiwa su Aslam fatan sauka lfy da daukacin dukkan fans dinsa Allah y dawo mana da Aslam muji wanne irin xama xasuyi da princess dinshi(karku manta tadauki alwashin yana dawowa xai saketa don baxata iya xama da dan is....ba ). Islam kuwa tsahon 3 days ta dauka tana fushi da mutanen gdan ta koma wunin daki,after 3 days ta ware fitina da rashin ji sai abinda y karu dan kaf gdan inka cire kaka,daddy,mommy,Abba da aunty amarya tofa bawanda take ragawa musamman dasu haidar suke dada fasa mata kai suna kiranta matar babban yaya,kunsan islam dasan girma to saifa ta fara gwalli da iyayi,Abu 1 ne yakeci mata tuwo a kwarya hanata futa da akeyi sakaka sai ace ita matar aurece tofa wannan abin yana mugun bata mata rai dan ita yanxu ma mantawa takeyi da wani Aslam. Yau satin Aslam 2 da tafiya amma ko sau 1 basu tabayin waya da islam ba saboda sam da rana bashi da lokacin kiran waya,saboda aiki a gda ma suke barin wayar,da daddare kuma kafin y kira tayi bacci,duk da abin yana damunsa,islam kuwa ita sam bata damu ba cikin dare islam tana bacci ta fara mafarki gata itada Aslam akan gado yana fada mata wadansu kalamai masu rikitarwa daganan y fara kissing ita kara ta kwallah inda lokacin yayi dai2 da kiran assalatu firgigit ta farka jikinta sai rawa yakeyi gumi sai karyo mata yakeyi,lokaci 1 ta fashe da wani irin kuka tunowa da mafarkin da tayi wani irin haushin Aslam taji y kamata a ranta tana shikenan hero y cuceni kara ta kwalla saboda wani irin murdawa da mararta tayi mata,da sauri amira ta mike tana lfy islam menene y faru,ta kunna fitila,islam ganin jini akan shinfidarta shine y dada tsoratata luuu ta fada kan gadon a sume,Aslam ne yaji gabanshi y fadi da sauri y dafe kirjinshi yace wani Abu y faru da princess dita,Amira kuwa da gudu ta kwasa ta fita a dakin tana kwalawa kaka kira. Taku har kullum *sisin mama* *I LUV U ALL MY FANS INAH TARE DAKU ADUK INDA KUKE* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:35 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *107* Amira tana futa dakin kaka ta shiga lokacin kaka ta idar da sallah da gudu ta fada dakin tana kaka!,kaka!!,kaka da take kan sallaya tayi gyaran murya saboda laximin da takeyi,Amira cikin muryar kuka tace kaka islam ce bata da lfy,da sauri kaka ta mike tana meya sameta ta fice,Amira tace nima bansani ba tabi bayan kaka suka shiga dakin,kaka ganin halin da islam take ai tuni tahau sallallami,lokacin kuwa data karasa ta taba islam ta daga hannunta taji y koma tuni ta rude tahau kuka,tana wayyo islam dan Allah karki mutu ki barni,Amira jin abinda kaka tace tuni ta dada rudewa tahau ihu da kuka,kaka kuwa da sauri ta ta futa a part dinta lokacin yayi dai2 da dawowar su Abba daga masallaci,cikin kidima suke tambayarta amma ta kasa magana sai islam da take cewa tana nuna musu part dinta,aguje sukayi part din kakan har suna rige2 shiga,suma ganin halin da islam take ciki y tashi hankalinsu Abba y futa da sauri y tafi part dinsa dauko key din mota. Safwanne y kalli Aslam yace bangane me kake nufi da wani Abu y faru da islam ba,cikin yanayi na damuwa Aslam yayi magana naji ajikina islam tana cikin wani hali,shiru safwan yayi yace to ka kira waya gaji mana,Aslam yama manta yanxu a nageria asuba ce kawai yahau dialing din number din aunty amarya,lokacin aunty amarya ta idar da sallar asuba kenan xata fara axkar taji wayanta da yake kan bed side cabinet yana ringing dauka tayi ganin mai kirannata da sauri tayi picking,dagacan bangaren Aslam yace" _brk da asuba aunty na_ Aunty amarya tace" _brkn mudai my son dftn kana lfy?_ Sai da Aslam yaja numfashi yace" _lfyta qlau dftn kuma haka?_ Aunty amarya tace" _dukkanmu lfyrmu qlau_ Shiru Aslam yayi,sai da aunty amarya tace" _lfy kuwa kake my son_ Aslam yace" _eh aunty islam fa naji ajikina kamar ba lfy take ba?_ Murmushi aunty amarya tayi dagacan bangaren tace" _ lfyrta qlau my son kilama yanxu ta tashi sallah ko nakai mata wayar?_ Da sauri Aslam yace" _a'ah sai anjima toh tunda lfy_ Aunty amarya tace" _toh nifa harnaji tsoro naga ka kirani da asubar fari naxata wani abunne?_ Murmushi Aslam yayi yace" _A'ah dama nakirane naji lbrn amanata_ Dariya aunty amarya tayi tace" _toh amanarka tananan lfy_,daganan suka ajiye wayar kallan wayar aunty amarya ta tsaya yi tana murmushi a ranta tanajin dadin yadda Aslam yakeson islam,Abba ne y shigo dakin da sauri y xari key din mota,aunty ta katse shi ta hanyar cewa Abban Amir ina kuma xakaje da sassafennan da mota,cikin sauri yace asibiti xani y fice da sauri ta bishi gani tayi an dauko islam kamar gawa an sakata a motar Abba da daddy a gaba sai kaka da Amira a baya sun fice. Cikin tsananin firgici da tashin hankali aunty amarya take tambayar mommy meya samu islam,mommyn ma da ba'a cikin hankalinta take ba tace nima basumin bayani ba,aunty amarya ce ta kalli amir tace dauko mota mu bisu dauko mota yayi suka futa suma da yake sunsan asibitin da file din yan gdan yake can xa'akai islam. Abba kuwa lokacin dasu suka isa asibiti ko dai2 ta packing baiyi ba y futo a motar cikin sauri shida daddy ne suka shiga cikin asibitin dayake private hospital ne tuni nurse 2 suka taho da gadon marasa lafiya suka saka islam akai suka gangara da ita emergency. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:36 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *108* Taimakon gaggawa nurse din suka fara bata,amma har xuwa time din islam bata farfado ba dalikin firgicin da tayi sunyi iya yinsu amma ina Abu y gagara wata nurse ce ta futo a emergency din da sauri kaka tasha gabanta tace likita y jikin jikar tawa tana goge kwallah,lokacin yayi dai2 da karasowar su aunty amarya,nurse din tacewa kaka ki kwantar da hankalinki hajiya munayin iya bakin kokarin mu yanxu haka ankira dr din daxai karbi duty 8:00am yanxu saboda yanayin ciwon nata kinga yanxu 6:45am ma kaka ta share hawaye tana jan hanci tace kuma xaixo kina gani nurse din tace eh hajiya gaskiya shi bashida wulakanci irinna sauran doctors yana da kirki sosai bata karasa magana ba sai gashinan dr din y shigo sanye da jallabiyya brown colour tayi masifar yi masa kyau saboda kyakykyawa ne dr din ajin farko gashi fari tas yanayinsa dai tamkar balarabe,da sauri yaxo yayiwa su daddy sallama y shige dakin da islam take,nurse dinnan tace yauwa kunga harya karaso ma bari nayi sauri naje na dauko abin da nafito danshi na koma ta wuce su kaka da suke jugum2 saboda basusan halin da islam take cikiba. Dr dinne cikin fada2 y fara yiwa nurses din masifa yana y xakuna yin abu tamkar bakusan kan aikin kuba,cikin tsoro sukace sorry sir(dr samir yana da xafi musamman in y kula da yadda nurses suke bada rashin kulawa akan pacient to yanxu xai hausu da fada ba kakkautawa),kallansu yayi yace treatment din daya kamata ku fara bata shine ku samu ta farfado anma kun tsaya kuna shirme yadanyi tsaki,cikin gaggawa da kwarewa y fara aikinsa bai dauki 5 minutes ba islam ta farfado,tana bude idanuwanta ta dorasu akan dr sameer da sauri ta runtse idanuwanta hade da dafe mararta tana wayyo Allah cikina xan mutu gane menene yake damunta da sauri y hada wata allura ta pain reliever y xugeta a sirinji hade da anasizia y matsa kusa da islam yace ki gyara nayi miki allurar da xata rage miki radadin ciwon da kijeji. Islam duk da tana cikin axaba hakan bai hanata ware idanuwanta hade da xaxxaro su cikin kuka hawaye na xuba a idanuwanta tsantsan firgici da tsoro dr sameer y gano a idanuwan islam,cikin shagwaba tace plz dr karkamin allura tsoronta nakeyi ta karashe maganar da fashewa da kuka,wani mugun tausayinta yaji saboda ko bata fada ba shi y gano tsoron allura miraran akan fuskar islam amma yayi murmushi yace kiyi hakuri ki yadda nayi miki,su kuwa nurses da yake ba sabon abu bane a gurinsu suka dr sameer yana lallaba pacient dinsa balle wannan da sukaga yarinya ce sam basu damuba,islam ganin da gaske yake allurar xaiyi mata shine y sakata fara kokarin saukowa daga gadon dukkuwa da irin ciwon da marar tata takeyi mata dan islam ta kwammace ta dawwama acikin ciwonta da ace xa'ayi mata allura,kula da dr sameer yayi tana kokarin sauka a gadon shine y sakashi cewa nurses din yace su rike masa ita,rirrike ta sukayi islam kuwa me takeyi inba kuka ba lokacin da dr sameer yayi mata allurar wata gigitacciyar kara ta saki harta firgita nurses din suna shirin cikata y daka musu tsawa yace ku riketa mana saura 1 da sauri suka riketa y karayi mata a hankali bacci y fara daukarta,canular y saka mata y jona mata drip y kalli nurses din yace ku kaita daki shikuma y futo. Su Abba sunyi cirko2 a bakin dakin saboda lokacin da islam tayi kara suma sunjita dr sameer y futo,daddy ne cikin sauri yace dr meya faru munji tayi ihu,murmushi dr sameer yayi wanda y kara masa kyau yace bkmai allura xanyi mata shine tayi karannan amma karku damu jan numfashi daddy yayi,dr sameer y duba agogonsa yaga 7:30am yace dan Allah kuyi hakuri naje gda nayo wanka nadawo sai nayi muku bayanin abinda ke damunta godiya sukayi mishi y wuce y shiga mota,lokacin aka gangaro da islam akan gado tana bacci xuwa daki. Sai 8:00am islam ta farka sai taji ciwon marar tata yayi sauki sosai lokacin data bude idanuwantab iyayenta duk ta gani a gaban gadon,kokarin tashi tayi mommy ce da sauri ta karasa ta tasheta sannu suketa jera mata tana amsawa,mommy ce ta kula islam duk tayi staining din xanin gadon jan hannun amir tayi suka futa tace kaje gda ka daukowa islam kaya,kuma ka suyomin paf,amir yace toh amma kuda Amira xakuje ta kalli amira tace ki dauko mata panties dinta toh Amira tace suka tafi. Dawowa dakin mommy tayi ta kalli su daddy dasu aunty amarya tace kudan bamu guri xanyi magana da yata futa sukayi mommy ta shiga bathroom ta hada wa islam ruwan wanka sannan ta futo ta kama hannun islam ta sakko da ita daga gadon tace maxa jekiyi wanka saurin cire bedsheet din tayi ta canja wani,islam kuwa data shiga bathroom wanka kayanta ta cire lokacin data cire pant taga duk jini a jiki durkushewa tayi tace wayyo mommy na mutu. *Dan Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting dina kwana 2 hakan y farune dalilin wani uxiri daya tasomi amma insha Allah yanxu xakuna ganin posting dina kullum na yauma xaku ganshi kadan kuyi hakuri* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:37 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *109* Da gudu mommy ta karasa cikin bathroom din islam ta gani a durkushe tana sheshshekar kuka,mommy ce ta dagata ta bata towel ta daura sannan tace haba my daughter wlh kinyi mugun tsoratani natsata wani abinne y sameki,cikin gunjin kuka ta fara magana har numfashinta nayin up & down tace mommy tun a gda nake ta bleeding bayannayi mafarki wai hero uhm uhm sai kuma ta kasa magana,tace mommy ina tsoron ko ciki na samu saita dada barkewa da kuka,murmushi mommy tayi saboda ta gane mai islam take nufi tace kiyi shiru ki daina kuka,islam tace mommy y xakice na daina kuka bayan jinina yana ta xubewa xai kare,mommy tace kiyi wanka ki futo xanyi miki bayani to fice islam kuma ta cire towel ta fara wanka amma sai kuka takeyi saboda ganin tana fitsarin jini (nikuwa nace watako islam batasan girma ne y kamata ba ). Mommy bayan ta futo a bathroom din knocking din dakin akayi taje ta bude Amira tagani rike da leda karba tayi ta koma dakin ciro pad 1 tayi tasaka ajikin pant ta ajiye,after 10 minutes islam ta futo tana tafiya a hankali tanata harhade kafa tamkar wadda kwai y fashewa aciki idanuwanta kuwa sai tsiyayar da kwalla yakeyi mommy ce tamika mata pant tace ungo maxa ki saka karba tayi tana kallan wandan tace mommy a haka xansa,hararar wasa mommy tayi mata tace Allah islam kin fiya shirme kisa mana,hawayen daya xubo mata ta goge tasa pant din,bakin gado ta xauna ta shafa mai doguwar riga ta atamfa ta saka lemon green da kwalliyar pink ba karamin kyau tayi mata ba dukkuwa da yar ramar da fuskarta tayi mommy ce ta kira sunanta tace islam. Cikin nutsuwa islam ta amsa tace na'am mommy kanta mamakin islam takeyi saboda yadda taga duk ta nutsu,tace inaso ki bani hankalinki sosai kinga wannan jinin da kike gani ba jinin jiinki bane har kike tunani wai xaki mutu,islam rinannun idanuwanta ta dago ta daurasu akan mommy da alamar tambaya a fuskarta mommy tace eh wannan jini shi ake kira da jinin haila,wata muguwar kunya islam taji ta rufeta hannunta ta saka ta rufe fuskarta dariya mommy tayi tace naji ja'irar kaya yanxu kuna kunyata akeji bayan an gamamin kuka,dariya islam ta kyalkyale da ita tace Allah mommy naxata mutuwa xanyi,dariya mommy itama tayi tace a'ah nasan basaina yi miki bayani akan jinin haila ba saboda kunyi a makaranta ko akwai abinda baki gane ba a kansa,girgixa kai islam tayi tace duk na gane mommy kuma dama inayin wankan tsarki duk ranar friday mommy tace toh shikenan Allah yayi miki albarka,islam tace ameen. Su daddy ne suka shigo Amir da Amira kuma dauke da basket a hannusu,islam kuwa sai wani sussunkuyar dakai takeyi wai ita kunya,bayan su daddy sunyi mata y jiki ta amsa a kunyace har xasu futa saiga dr sameer y shigo bayanshi nurse ce dauke da try da magunguna aciki. Bayan sun gaisa dasu Abba y kalli islam da takecin chips yace ah Ashe pacient din tawa ta warware shiru islam tayi ta sunkuyar da kanta,murmushi yayi yace nagama jikinnata da sauki xuwa an jima xa'a iya sallamarta yanxu dai ga magungunanta,sai lokacin islam ta dago kanta ta kalli dr cikin muryar shagwabba kamar mesonyin kuka tace dr bayan allura har magani xansha,eh yace mata y ballo magungunan y mika mata,karba tayi hade da xumbura bakinta gaba tana kunkuni ita batasan magani baxata shaba,murmushi yayi yace toh ai shikenan y kalli nurse yace jeki debo injections tunda batason magani,da sauri ta kurbi ruwa ta watsa magungunan a baki ta dada korasu da ruwa,dariya duka yan dakin sukayi,ita kuwa islam runtse idanuwanta tayi hade da tabe baki alamar daci. Dr ne y kalli su daddy yace ku biyoni office y futa su daddy ma mara masa baya sukayi. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:39 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *110* Xaune dr sameer yake akan kujera su Abba kuma suna xaune a wadda aka tanada domin masu ganin dr,sai da y daidaita farin gilashin da yake fuskarsa yadanyi rubutu a file din da yake gabanshi sannan y fara magana,alhj ba komai ne yake damun yarinyar kuba illah menses data fara to dama mata halitt2 ne wadansu in lokacin menses dinsu yayi xakuga suna bala'in yin ciwon mara wannan ba komai bane illah wadansu kwayoyin halitta da suke a marar mata to in lokacin al'adarsu yayi sai kwayoyin halittarnan suna dan cixonsu to shine yake haifar da ciwon mara,suman da tayi kuma bkmai bane illah firgici data shiga a lokacin da taganta a cikn bakon yanayi wannan shine bayanin kawai. Jan numfashi Abba yayi yace toh dr kana iya ganin xata iya daina wannan ciwon,dr yace eh to alal hakika gaskiya yanxu dai magunguna xatana amfani dasu wadanda duk lokacin da menses dinnata yaxo innatayi amfani dashi to xai lafa mata,amma hanyar waraka 1 ce shine in Allah yasa tayi aure da xarar namiji y kusance ta to xata iya dainawa,numfashi Abba yaja yace to mungode dr ammafa yarinyar nan tanada aure yanxu haka watanta 2 da sati 2 da aure kenan da tsantsan mamaki dr sameer y kalli su Abba harda cire glass din idonshi y mai2ta aure kuma,Abba yace eh mijinnata ma y tafi wani course ne xaiyi 2 years kafin y dawo,sai da dr sameer yaja numfashi,Abba yace amma yanxu muna ganin kawai xamu tura masa ita tunda lalurar tasu duk iri 1 ce,anan Abba yayiwa dr sameer bayanin cutar Aslam a lokacin dr fu'ad ne y dubashi,shiru dr sameer yayi a ranshi yana tunani tabbas aka tura yarinyar nan gurin mijinta to ba karamin cutuwa xatayi ba dan da dukkan alamu mijinta xaiyi jaraba,daddy ne yace dr kayi shiru,firgigit dr sameer y dawo daga tunaninshi yace a gaskiya shawaran da xan iya baku shine kubar islam saboda tayi yarinta da yawa baxata iya daukar lalurar mijinta ba xata iya cutuwa amma shawara ta ku kyaleta taci gaba da karbar magani duk lokacin menses dinta har mijinnata y dawo toh suka cewa dr sukayi godiya suka futa. Da misalin 4:00pm aka sallami islam suka koma gda ranar dai haka ta wuni sukuku jinta takeyi tamkar sabuwar halitt. 7 days islam ta dauka tana menses sannan tayi wanka nanfa rashin ji y dawo,duk wanda yayi mata Abu a lokacin da take menses sai data rama ranar kuwa kaka wuni tayi tana raba fada. *A GURGUJE* Yau su islam suka koma makaranta,lokacin da xasu tafi sai da kaka tayi mata nasiha sosai akan ta kula banda kula maxa domin ita matar aurece bayan haka yanxu kuma ta girma koya ta bari namiji y taba jikinta tofa xata iya daukan ciki islam ta xorata sosai da maganganun kaka haka suka tafi makaranta a hanya islam sai da tayiwa su Amira warning akan duk wanda y sake y fadawa yan ajinsu anyi mata aure wlh in sun dawo gida mai rabata dasu sai Allah ta kalli khausar tace musamman ke nasan kinfi rawar kai,khausar cikin masifa tace saina fada din,wani kallo islam ta jefeta dashi tace Allah y baki iko (islam abinda bata sani ba Abba y riga da yaje makarantar y sanar musu),haka islam ta dinga dari2 a makaranta wai dan kartayi ciki ,su khausar kuwa bawanda yayi gigin fada dan sunsan halin islam batada m. Haka rayuwa taci gaba da tafiya wani lokacin dadi wani lokacin rashin haka to hakance ta faru da Aslam ganin har yayi 9 months da tafiya amma bai taba waya da princess dinshi ba duk y damu,safwan ganin damuwar da Aslam yake ciki tanason shafar aikinsa dan in yana tunani in xa'ayi tayi masa magana to baji xaiyi ba harsai an tabashi shine kawai y bawa Aslam shawara yasa amir y siyawa islam waya ko chatting ne su dingayi,cikin jin dadin shawarar da safwan y bashi a take y turawa amir text massage yanaso asiyowa islam waya,lokacin da Amir y tashi da asuba yaga sakon Aslam reply yayi masa da to. Su Islam ne xaune a palon kaka,mamakin girmansu nakeyi musamman islam ta taxatama budurwa kirorin budurci sosai suka futo a jikinta dan in ba fada maka akayi shekarunta 15 ba saika xata yar 17 years ce saboda yadda kirjinta yake a cike tamkar xai fasa riga,ga wani irin hips mai daukar hankalin mai kallo. Amir ne y shigo palon da sallama yace little 6 mijinki y bani Sako gurinki hannunshi dauke da leda,cuna baki islam tayi tace Allah ni ba little bace y Amir ni big ce hararar wasa yayi mata yace to gyanbo sarkin son girma baki tambayeni sakon mijinnaki ba sai korafi kanta ta juyar gefe tana nifa y Amir bani da miji ehe ta murguda baki tsaki yayi yace ke kika sani ledar hannunsa y xaxxage wayoyi ne 3 suka fado dukkansu iphone 6+ akwai pink,white,sai yellow yace xaki dauki 1 da sauri ta juya washe hakora tayi lokacin da tayi toxali da wayoyin pink din ta dauka ya kalli Amira yace kema xaki dauka yellow din ita ta dauka,yace to wannañ kuma ku bawa kausar duk akwai sim card a ciki Amira y jefa da wani kallo yace saura ki bawa samari number dinki duk randa naji kona gani seizing din wayar xanyi murmushi tayi ta sunkuyar dakai shikuma y fice. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:40 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *111* Bayan Amir y futa murna su islam suka fara harda rawarsu da sauri suka tafi suka sassaka chargy,islam ce ta kalli Amira tace anya 6 ba sonki kuwa yaya Amir yakeyi ba kuwa,Amira tace ki jiki da fassara me kika gani,sai da islam ta kada idanuwanta sannan tace alamu sun nuna yaya sanki yakeyi dan gane da irin kallan daya jefeki dashi sannan bakiji yace saura yaga numbobin samari a wayar taki ba indai ba sonki yakeyi ba ina ruwansa da samarin da xakiyi,Amira hmmm kawai tace,islam ce tace yauwa dan Allah yi maxa ki tashi muje gdansu khausar mukai mata tata kan kakannan ta futo tace baxan futa ba,Amira tace ki bari mana sai anjima islam tace wlh baki isa ba ta tashi tasa hijaba bakisan yadda kafata take kaikayi ba rabona da futa waje fa tun ranar friday da mukaje makaranta kuma kinga munyi hutu yanxu wa yaga ranar kara futa ta tayi waje Amira ma hijabi tasaka ta dauki ledar tasa wayar khausar din tabi bayan islam. Amira tace to uwar axarbabi da kika bar wayar da in kinje me xakice wa khausar din dariya islam tayi tace ai mantawa nayi a nutse suke tafiyarsu har sun kai bakin kofa islam ce tajiyo miryar aunty amarya tana ku islam ina xakuje cak islam ta tsaya ta kalli Amira tace nabanu yanxu aunty amarya xata hanani futa,aunty amarya ce ta fara takowa wajensu islam ganin haka da gudu ta kwasa ta fuce waje dan a yadda takejin kafarta na mata kaikayi wlh ko daddy ne y hanata futar nan saita fita,aunty amarya ta karaso tace Amira ina xakuje ne,Amira tace gdansu khausar, aunty amarya tace me xakuyi acan da tsakar ranar nan,Amira tace waya xamu kai mata,aunty amarya ta maimaita waya!,Amira tace eh yaya Amir ne y siyo mana aunty amarya tace y kyauta to meya saka islam guduwa kuma,Amira tace wai tsoro takeji karki hanata futa dan kafarta kaikayi takeyi,dariya aunty amarya tayi tace Allah y shirya islam watako saboda tsabar yawo kafarta har kaikayi take,itama Amira dariya tayi aunty amarya tace to saikun dawo,Amira tace toh ta fice. Xaune Amira ta tarar da islam akan wani sock away da yake gaban gidansu kadan,Amira tace to tashi mu tafi,islam tace toh wlh dadin iskar waje ma daban take data cikin gda ta wani lumshe ido,murmushi Amira tayi tace gaskiya islam ban taba ganin mace mai shegen son yawo irinki ba watako iskar cikin gda data waje har banbanci ne da ita,yatsina fuska islam tayi tace eh ni wlh ma wannan hutun dole a gwarxo xan yishi,dariya Amira tayi tace harda dole kamar kin manta bake kikeyin iko da kanki ba,tsaki islam tayi tace Allah sai naje saboda mugunta irinta hero y barni da igiyoyin auransa a kaina suna hanani rawar gaban hantsi ta karashe maganar da murguda baki,dariya Amira ta karayi tace watako 6 xanso naga ranarda bakinki xai mutu,wani birki islam taja tace tab yasin ba ranar da bakina xai mutu sai dai in mutuwa nayi gaba 1,dariya Amira ta karayi tace bama saikin mutu ba yaya Aslam xai kasheshi cikin masifa islam tace Allah y kiyaye lokacin yayi dai2 da karasawarsu gdansu khausar shiga sukayi suka gaida baba mai gadi suka wuce. A xaune suka tarar da mammy da sagir suna hira gaishesu sukayi mammy ce kawai ta amsa sagir kuwa mikewa yayi,islam sai taji duk ba dadi dan rabonta dashi tunda y tafi cairo karatu sai yau ta ganshi gani tayi y kara girma sosai,islam tace mammy ina khausar fa mammy tace tana daki tashi sukayi suka shiga dakin kwance suka tarar da khausar tana bacci daka mata duka islam tayi tace toh kasa sarkin bacci saiki tashi firgigit khausar ta mike tana sosa cinyarta hararar islam tayi tace wannan wanne irin iskancine,islam tace naji mai da wukar naga yaya sagir yaushe y dawo,khausar tace tun ranar friday islam tace shine bakixo kin fadamin ba,khausar tace amfanin me fadar xaiyi miki shiru kuma islam tayi Amira ce ta daura mata ledar a cinya budewa khausar tayi ganin waya aciki kuma wadda ake yayi iphone 6+ shine sakata waro ido waje tace wayar waye. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:41 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *112* Amira ce tace takice,khausar ce tace banason wasa dan Allah ki fadamin gaskiya,islam tace abinda yafi bakyason wasa to wa kike tunanin xaiyi miki karya,khausar tace to masifaffiya bake nake tambaya ba,Amira sai da tayi dariya tace Allah takice yaya amir ne y siyo mana guda 3 kowa 1 cikin murna khausar ta fuce a palon da gudu taje ta nunawa mammy ta tayata murna dftn alkhairi da gudu ta fice ta tafi part din sagir. Kwance ta tarar dashi kan 3 seater yana tunanin islam tafiyarshi harya manta da ita amma yanxu ganinta dayayi y taso masa da kikin xaxxafar soyayyar da yayi mata,wata xuciyar ce ta kwabeshi tace haba sagir y xakana aikata haramun karka manta matar wanice istigfari y farayi khausar ce ta shigo tana my bro kaga wayata ta mika masa karba yayi tare da yin murmushi yace to my 6 waya siyo miki,dariya tayi tace yaya amir ne y siyamin nida su islam murmushi yayi yace y kuwa kyauta nima an jima xan futo muku da tsarabobin da nayo muku cikin murna ta runguneshi ta bashi peck a kumatu ta fuce murmushi yayi y tashi y shiga dakinsa katuwar trolley y janyo y futo da ita xuwa palon mommy. Khausar tana shiga dakin itama ta hada wayar tata ta jonata a chargy,khausar tace 6*s yanxu fa munxa ma manyan yara,Amira tace gaskiya fa,islam kuwa yatsina fuska tayi tace aini na dade da xama babbar yarinya kune dai sai yanxu,dariya sukayi sukace aike cus ce keda kike married woman suka karasa da kyalkyalewa da dariya wani malulun bakin ciki islam taji y turnike ta,khausar ce tace uhm ni ku tashi mu tafi naje nayiwa yaya amir godiya,Amira tace toh ta mike islam kuwa kwanciya tayi tace wlh ba inda xani yaushe rabon dana futo waje sai yau to kuwa sai dare xan koma,dariya sukayi suka futa a dakin sagir suka gani xaune yanata ware kayayyaki mammy tace ina kuma xakuje kukabar islam din,khausar ce tace godiya xanje nayiwa yaya Amir islam kuma tace baxata tafi yanxu ba,wai sai dare dariya mammy tayi ta mika musu laffaya masu kyau da tsada guda 3 tace gashinan ku kaiwa su hajiya inji dansu to sukace suna godiya suka futa saboda yau a sa'a tayi musu mammy tashi tayi ta debi nata kayan ta tafi daki,islam jin shiru a palon shine y sakata futowa da niyyar tafiya part din yaya sagir turus ta tsaya ganinsa xaune a palon a hankali ta karasa ta xauna tace sannu yaya sagir dftn ka dawo lafiya,har cikin kanshi yaji muryar tata sai da yayi addu'ar tsari daga shedan sannan y dago kanshi murmushi yayi mata yace lfy qlau 6* dftn nasameku lfy,cikin jin dadi islam tace lfy qlau,yace masha Allah,ya kara magana ina mijinnaki har kika samu damar futowa yawo,xumbura baki gaba tayi sannan tayi magana y tafi wani course xaiyi 2 years a singapore girgixa kanshi yayi yace Allah y dawo dashi lfy tace ameen,shiru dukkansu sukayi sagir kuwa yana jinjina lamarin a ransa yadda Aslam y iya tsallakewa y tafi wata uwa duniyar yabar islam a gda,wata xuciyar ce tace to ina ruwanka kawar da tunanin yayi a xuciyarsa su Amira ne suka dawo nan y bawa kowa tsarabarsa sunyi murna sosai da godiya. Haidar ne y shigo dakin kaka toxali idanuwansa sukayi da wayoyin su islam da mamaki y karasa yana kaka wadannan wayoyin nasu wane itama kaka sai lokacin hankalinta yakai Kansu tace ni banma kula dasu ba sai yanxu y tafi da niyyar dauko wayoyin su islam suka shigo da gudu ta karasa tana haba yaya haidar y xaka cire mana wayoyin mu alhalin basu cika ba. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:44 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *104* Washe gari Aslam cikin farin ciki y tashi har safwan na tsokanar shi wannan farin cikin fa tamkar an maka bushara da aljanna yace ai dole ka ganni haka jiya nayi waya da princess dita safwan yace eh dole ka kasance cikin farin ciki. Bangaren islam ma hakance ta faru itama jinta takeyi cikin farin ciki amma ta danganta hakan da sabuwar wayar da tayi kaka taje ta samu tayi mata maganar tanaso suje gwarxo hutu kaka tace toh gobe saimu tafi islam cikin jin dadi tace toh khausar ta kira a waya tace mata gobe xasuje gwarxo cikin murna khausar ta amsa da Allah y kaimu. Yau ma da daddare haka Aslam y kira islam suka sha wayarsu take cemasa gobe xasu tafi gwarxo yace toh Allah y kiyaye hanya ta kular masa da kanta itadai kawai to tace masa. Washe gari 2:00pm a gwarxo tayiwa su islam farin ciki sosai tayi dan rabonta da gwarxo kusan shekara 4 gdansu hanne sukaje nan akace musu tayi aure cikin farin ciki sukace a nuna musu gdanta yaro akasa y rakasu haka suka xama tamkar taurari duk inda suka wuce sai an kallesu har suka karasa gdan hanne. Da sallama suka shiga hanne da take gaban murhu da tsohon ciki ta amsa da sauri islam taje ta rungume ta tabarma ta dauko ta shimfida musu suka xaxxauna bayan sun gaisa islam ta Kalli hanne ta kyalkyale da dariya tace kawata ashe kin kusa xama mama harararta hanne tayi tace banason iskanci daso kikeyi mijinnawa y sakani a gaba yayita kallo,da mamaki Islam ta kalleta tace to inbe kalleki ba me xai miki harararta hanne tayi tace badai kina nufin bakisan me akeyi ba in anyi aure islam ma harararta tayi tace to Inna sani yaushe xan tambayeki hanne tace tab lallai an barki a tasha tashi tayi ta shiga dakinta ta dauko wani littafi *sirrin ma'aurata* tace ungo wannan karanta nasan ke yanxu kin iya karatun hausa nima lauwali ne yake karanta min da sauri islam ta dago kai tace kina nufin lauwali dan birni shine mijinki dariya hanne tayi tace eh ai shiyasa yan matan kauyennan suka dinga jin haushi lokacin bikina rasa wadda xatamin babbar Kawa nayi sai yar kanwar umman mu da taxo bikin itace tamin (lauwali dan gayu ne a gwarxo dan kafatanin samarin kauyen gwarxo shine kawai bayan y gama secondary y futa cikin kano yayo diploma to shine fa in xaixo gda yanayin shiga dai2 gwargwado irin ta matasan birni masu karamin karfi shine fa yan matan garin suke rububinsa). Lokacin da islam ta fara karantawa jikinta ne y fara rawa dan baifi 2 pages ta karanta ba tayar da littafin ta dafe kirji tace nashiga 3 yanxu hanne kina nufin nima haka hero xaimin murmushi hanne tayi tace wane kuma hero. Khausar ce tayi xaraf tace mijinta ne da mamaki hanne ta maimaita mijinta Amira tace eh yaya Aslam fa dariya ce ta kwacewa hanne tace kuna nufin wannan yayannaku shi islam ta aura islam da take raba idanuwa ta daga kai dan tagama tsorata da abinda idanuwanta suka karanta hanne tace ah lallai yaushe akayi bikin Amira ce ta bata lbrn auran islam da Aslam jinjina kai hanne tayi tace lallai yaya Aslam yayi namijin kokari daya xauna yana xuba miki ido har tsahon lokacinnan bai nemi hakkinsa ba (nikuwa nace ah lallai hanne anyi hankali) islam tace tab aikuwa baxai taba karbaba dariya hanne tayi tace lallai yanxu dashi kukaxo Amira ce tace a'ah you tafi kasar waje karatu tun bayan bikinsa da sati 2 kinsan sojane xaro ido hanne tayi ta maimaita Soja sukace eh haka sukaci gaba da hirarsu itadai islam baki y mutu daga eh sai a'ah har hanne tagama jellop din takiyarta yar mirji sukaci bayan sun gama lauwali y dawo da sauri hanne ta tashi taje ta masa sannu da xuwa fuskarsa a sake y amsa yayi musu brk da xuwa su islam kuwa tashi sukayi tafi. A gda ma haka ta xama so silent har sai da kaka ta tambayisu khausar meyake damun islam su kace suma basu sani ba (nikuwa nace yarinya taji lbrn manya ). Kullum su islam insun shirya gdan hanne suke xuwa susha hira,haka suna waya kullum da Aslam dan raba dare sukeyi suna waya su islam sun cika sati 2 a gwarxo yau xasu tafi sunje sunyi sallama da hanne sun karbi number din wayarta dayake tana da waya baby nokia. Kwanci tashi asarar mai rai su islam sun shiga s.s 2 har sun cinye term 1 sunshiga na 2 ma sunci wata 2 a lokacinne mommy ta nema musu wata catering skul da kuma make up 4 months ne ake gama makarantar 3 months catering 1 month makeup nanfa suka fara xuwa 3:00pm ce makarantar xuwa 6:00pm shine in sun dawo daga makaranta sukaci abinci sukayi wanka saisu tafi da daddare kuma bayan sallar isha'i ana xuwa ana kara musu littattafai islam yanxu tasan hakkokin miji akan matarsa sannan tasan irin xunubin da mace xata kwasa inta nemi mijinta y saketa batare da wani kwakwkwaran dalili ba,haka nan kuma kullum sai sunsha waya da hero dinta dan haryanxu da haka take kiransa kuma da sunan tayi saving ga chatting da sukeyi sosai. Amira da yaya Amir ma soyayya sukeyi sosai tamkar xasu cinye kansu haka safwan da khausar shikuma islam ce ta taba daura pic dinsu a dp dinta su 3 to anan yaga khausar ta xama yan mata tun daga lokacin y susuce y dinga damun Aslam yasa islam ta turo masa da number dinta sai da Aslam y gaji da naci y nema masa sannan y samu lfy to tundaga lokacin suka fara soyayya shida khausar. Su islam an xama manyan yan mata masu jida kansu danko a skul ba kowacce gaja suke kulawa ba sai yarinya Mai aji iyayi da gwalli kuwa sai abinda y karu uwa uba tsafta dan indai kana shiri dasu islam dole ka xama dan gayu shiyasa yan skul din suke kiransa grp dinsu da *classic lady* har sunan ma y bisu,to yanxu fa su islam sun gama xama manyan yara dan ga iya daukar wanka ga kwalliya ga kuma iya girki (anan nake gayyatar fans din islam dasu shirya dan yau a part din kaka xamuyi dinner ). Su Aslam sun fara shirye2 dawowa gda dan saura 2 weeks su dawo farin cikin gurin Aslam kuwa baya misaltuwa dan kullum sai y futa kasuwa yayiwa princess dinshi tsaraba kaya yake lodo mata bana wasa ba dan duk abinda y futa you Gabi indai y birgeshi to kuwa sai y siyawa princess dinshi. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 9:53 AM] ‪+234 703 962 5239‬: GOYON KAKA* *115* *Assalamu alaikum last posting dina xakuga nasaka 103&104 amemakon nasaka 113 & 114 dftn xakumin uxiri dan dan adam ajixine* Mai gyaran jiki mommy ta dauko ta fara yiwa islam duk da dai Aslam bai fada musu ranar daxai dawo ba yadaice a karshen watannan xai dawo ba karamin kyara akeyiwa islam ba Wanda y kama daga ciki har waje wani lokacin ita da kanta takanji kewar Aslam a tare da ita Saboda yadda mai gyaran jikin take tsumata. Xaune suke dasu Amira,khausar tace islam irin wannan gyaran ai saiki susuta mana yaya inya dawo y rikice,Amira tace wlh fa gaskiya ki tausayawa yayan mu daya dawo muji lbr yasha ban2 mufara tunanin samun baby, yatsina fuska islam tayi tace Allah shiyasa ni kaina banason gyarannan dan a gaskiya nikaina nasan baxan iya bawa hero kaina a yanxu ba saboda ba karamin tsoro nakeji ba sannan kunaji fa ance da xarar anyi ko sau 1 ne sai ciki nikuma gaskiya banshirya daukar ciki ba duka2 fa shekaruna 16 ne kokun manta,khausar ce tace a'ah bamu manta ba amma baxaki tausayawa dan bawan Allah ba bakya tunanin xaki iya shiga hakkinsa,yatsina fuska islam ta karayi tace to waima waya fada muku xan bari harya samu fuskar daxai nemi hakkinsa a gurina,Amira tace bakya tsoron fushin Allah yahau kanki,islam tace ai tsoron hakanne kawai xai sakani naki neman saki a gurin hero dan haryanxu xuciya ta bata karbeshi a matsayin masoyi ba banajin dugon sonshi a raina ko kadan,Amira tace shiyasa naga inya kiraki a waya jikinki har rawa yakeyi kiyi picking, murmushi islam tayi tace duk lokacin daya kirani nakan tsinci kaina acikin farin cikine,Amira tace to a wanne matsayin kika ajiye wannan inba so bane islam tace shakuwa har Amira xata karayin magana islam tace plz kibar maganar nan ta isa haka banason ayita tashin magana hero ne nace banaso amma nayadda xanyi xaman aure dashi harna koyawa kaina sonshi fakat shiru su Amira sukayi suka tsaya kallanta dan da dukkan alamu sun lura sam islam batasan soba amma sun danganta hakan da cewa dan batasan soyayya bane tun kafin tayi aure. Yau y kasance su Aslam xasu baro singapore bayan dumbin nasarori da suka samo 6:00pm jirginsu y sauka a filin jirgi na photercort dake nigeria cikin farin ciki sojoji suke saukowa daga jirgi cikin kakinsu matasa ne dukkansu majiya karfi a motoci laxirious aka debesu direct headcoter aka wuce dasu bayan sunje akayi musu brk da dawowa da alkawarin nan da 2 weeks xa'a hada musu kwarya2 farin cikin dawowarsu cikin aminci da farin ciki,daganan suka wuce barrack gdan Aslam suka bude futu2 suka tarar dashi da kura cire kayansu sukayi suka saka wasu direct bathroom suka shiga suka dauro alwala saboda kiran sallah da akeyi a masallaci. Bayan sun dawo daga masallaci da wasu kananun sojoji suka taho dasu domin su gyara musu gda cikin 1 hour suka gama gyara gdan bathroom Aslam y shiga yayo wanka bayan y futo safwan y shiga dayake sun bayar anyo musu takeaway dayake baxasu iya shiga kitchen ba saboda gajiyar da suka suna gamaci bedroom suka shiga wani gajiyayyan bacci yayi gaba dasu. Islam kuwa tanacan ta rasa meyake mata dadi saboda yau kwata2 batayi waya da hero dinta ba gashi sai try din number dinsa takeyi taki shiga cilli tayi da wayar tata kan gadon su lokacin yayi dai2 da futowar Amira daga bathroom ta futo a wanka ganin islam tayi tayiwani kicin2 da ranta murmushi Amira tayi tace Sis wai yayane meyake faruwane cikin masifa islam tace bansani ba karki dameni tayi tsaki ta kara janyo wayarta taci gaba da try din number Aslam, Amira kuwa xama tayi a gaban dressing mirrow ta tsantsara kwalliya wata atamfarta ta dauko maroon colour mai kwalliyar sky blue blouse & skirt ne sakawa tayi bakaramin kyau kayan yayi mata ba ta dauko fashion da stones din sky blue tasaka body spray ta fesa sannan ta daura da daddadan perfprms dankwalinta ta daura tamkar nadin gwagwgwaro sannan ta yafa mayafi sky blue ta janyo plat shoe baki tasaka, kallan islam tayi tace natafi gurin hubbina wani banxan kallo islam tabita dashi hade dajan dogon tsaki. Yau bayan su Aslam Sun tashi a bacci wajen 10:00am suka tafi airport y yanki ticket daxai kaishi kano surprise din yan gdansu yakeson yi, safwanne y kalli Aslam yace wai meyasa abokina kakeso in kayi tafiya kayiwa yan kano surprise din komawa gdane memakon ka fada musu su tanadar maka hadaddun abinci saima kaje ka tarar pretty dinnaka batanan,cikin jin haushin kalaman karshe da safwan y fada na cewa xai koma y tarar islam batanan yace to waya fada maka ana barin baby na futa ai sam bata futa ko ina dan ba'a barinta a gda, safwan yace Allah yasa Aslam yace Ameen lokacin da suka karasa airport ticket din 5:00pm suka samu duk da surprice yaso yiwa yan kano amma yaso ace na 2:00pm y samu haka y siya suka kama hanya direct gdansu safwan suka wuce bakaramin murna mammy da daddy din safwan sukayi ba da suka gansu saboda shekara 2 basugansu ba dole suyi kewa tunda ba wata 2 bane. [3/8, 10:05 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *116* Yau islam jinta takeyi cikin farin ciki tunda ta tashi ita kanta tarasa dalili alhalin jiya da daddare dakyar ta iya bacci saboda missing daddadan muryar Aslam da tayi 3:00pm suka fara shiri saboda bikin wata kawarsu da xa'ayi wadda sukayi islamiyya tare kamu ne xasuje a gdan dan hausa dakyar ma islam tasamu aka barta xuwa bikin sai da tadinga kuka tana roko sannan aka yadda taje bakaramin kyau sukayi ba yan matan 3 musamman islam da tasha gyaran jiki tamkar a tabata jini y futo simple makeup ita tayi saboda tasan kotayi tafi haka yawa sai ansa ta goge amma bakaramin kyau tayi ba ankon kamunne a jikinsu sky blue din material mai raga2 anyi musu landing da pink swiss tafita aciki sai suka daura pink rose sarka da dankunne duk pink ne iri 1 bakaramin kyau kayan yayi musu ba saboda dinkin y xauna das ajikinsu tamkar ajikinsu aka dinkashi. Islam tasaka takalmi da pose pink sai Amira tasaka sky blue khausar kuma baki mayafai suka yafa duk pink wow masha Allah xanso fans din goyon kaka kuga wadannan hadaddun yan matan ga kuma wani sihirtaccen kanshi dayake tashi a jikinsu amma saika matsa kusa dasu xakaji. 4:00pm suka futo cikin shirinsu suna tafiyarsu cikin nutsuwa tabbas duk wani da namiji mai lafiya yayi toxali da wadannan yan matan dole y susuce yaya haidar suka samu y taimaka y kaisu gdan dan hausa sai daya gama wulakanta su sannan y kwashesu lokacin daya kaisu yace wlh kar kuma naga yarinyar data kirani tace nadawo na dauketa dan sam baxanxo ba Wlh, islam ce ta harare shi tace to kada Allah yasa ka dawo daukar tamu kaga in xamu dawo a kasa toni harkamin iyayin mota ma karka manta ni motace sukutun dani kaikuwa fa ta karoro ce duk taran aro naushin sitiyarin motar yayi yace lallai ma yarinyar nan kinyi bala'in rainani ke dabadan kina matar yaya ba wlh da yau saina yimiki tsinannen duka dariya tayi tace mafashi ta kalli su Amira da suke bayan mota tace ku futo mu tafi, harta xura kafarta a waje ta juyo tace bari nayi maka tayan kauye karamin mai gda saina dawo ta kashe masa ido 1 ta futa a motar, haidar tsintar kansa yayi dayin dariya yace lallai yarinyar nan ta samu sake yaja motarshi yabar gurin. Lokacin dasu islam suka shiga nanfa kallo y koma kansu amma saboda kwarjinin da suka yiwa samarin gurin kaf sun rasa wanda xai tunkaresu har suka karasa cikin theater dayake anan gurin akeyin kamun kawarsu bakaramin dadi tajiba lokacin data gansu. 5:15pm jirgine y sauka a filin saukar jirage na malam Aminu Kano passinger ne suke sakkowa a jirgin can daga baya na hango Aslam yana sakkowa sanye yake da black jeans da t.shirt fara polo a gaban rigar anyi rubutu da bakin penty saman t.shirt din suwaita ce baka ta sanyi saboda yanayin garin yau an tashi da sanyi hade da haxo kansa rufe yake ruf da hular sanyi fara hade da wani dan karamin mayafi daya nade wutanshi dashi idanuwansa kuwa sufe suke ruf acikin bakin glass hanunsa sanye yake da hand glove baka sai agogon rolex na axurfa dayake sanye a tsintsiyar hannunsa kafarsa sanye tace cikin boot baki kana kallansa xakasan hutu y xauna a jikinsa tare da gayu a hankali yake sakkowa daga matattakalar bene hannunsa yana janye da trolly bag phone dinshi y dauko iphone 7+ y shiga kira ji nayi yace hello bros kaxo airport ka daukeni dayake xai dauki tsarabobin daya taho dasu shiyasa y kira amir dan yasan kafin y gama diban kayansa Amir y karaso. Amir baifi 30 minutes ba y karaso waya yayiwa Aslam yace y karaso futowa yayi cikin tafiyarsa ta xaratan maxa duk macen data ganshi sai taji inama ace ta mallakeshi (kawata haulat na hango ta saki baki tabota nayi nace kawata menene haka kokin manta da babyn naakine nunfashi taja tace kyaleni kawata ) wanda yake turo masa kayansa a bayansa har xuwa wajen motar Amir bude boot Amir yayi aka xuba kayan amma duk da haka akwai saura a bag seat aka xuba rungumeshi Amir yayi yace ur wlcm bros tnx Aslam yace fuskarsa dauke da mirmushi ya shiga front seat Amir yaja sai gda. Lokacin da suka isa gda da farin ciki aslam y futo a motar yawani lumshe idanu saboda murnar dayake xai ga princess dinshi yasan ta girma don shekara 2 ba wasa bace direct part din kaka y wuce domin idanuwansa babu wanda yake mararin gani irin princess dinshi. *I LUV U ALL MY FANS* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:07 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *118* Shiga yayi cikin gdan dan hausa packing yayi y futo gurin y fara karewa kallo nan y karajin ransa y baci ganin maxa rututu a gurin sannan gurine da ake bikunkuna rasa inda xai dosa yayi futowa yayi a motar y jingina ajikin mitarsa yana karewa gurin kallo fuskarshi tamau tamkar bai taba dariya ba nan fa yan mata aka fara gwalli kwarjinin da yayi musu nema ya hanasu kasa kai kansa gurinsu,tsaki yayi y shiga cikin motarsa ganin tana batawa kansa lokaci kuma baisan a gurin da suke bikin ba sannan yayi ragon axanci dabai taho da haidar ba tunda shine y kawosu,wuta y bawa motar tashi y fice su kansu maxan gurin sunsha jinin jikinsu daboda Aslam yes ne. Saboda matsalar go slow da ake samu a tituna da kuma nisan dayake tsakanin gdan dan hausa xuwa rigiyar xaki shine y saka su islam basu karasa gda ba sai wajen sallar isha'i bayan sun sauka a motar islam ce tadan xura kanta ta gaban motar gurin xaman mai xaman banxa tana yiwa Asma'u godiya da kuma alkawarin xataxo gdanta cire kanta keda wuya yayi dai2 da karasowar Aslam ciikin layin daga wa Asma'u hannu islam takeyi alamar bye2 wani jiri Aslam yaji y kwasheshi lokaci 1 yaji kansa ya wani saka gano islam da yayi tana murmushi tana dagawa na cikin motar hannu saboda akwai hasken security light shine y bashi damar gane itace takeyin bye2 din da sauri y karawa motar tashi wuta a dai2 gabanta yaja wani wawan birki da sauri islam taja baya kosu Amira da suka fara tafiya sai da suka tsorata suka juyo, islam kuma cikin tsiwa ta kama kugu tace lallai ma yaya haidar wannan ai ganganci ne tsakani da Allah daka bugeni ai daka cuci mai so.... lokaci daya ta hadiye ragowar kalamanta ganin mai futowa a motar cikin tsoro hade da xaro idanu waje tace hero gutt ta hadiyi wani xaxxafan yawu ganin y koma mata tamkar wani namijin xaki fuskarnan tashi a murtuke idanuwansa sun kada sunyi ja yana furxar da wata xaxxafar iska su Amira jin sunan data kira da gudu suka kwasa sukayi cikin gda itama ganin yana tunkaro ta shine y sakata fara ja da baya2,ci gaba yayi da tunkarata ganin da tayi y kusa cimmata shine yasa kata juyawa da sauri ta kwasa a guje taku 1 yayi y dangota ihu ta kwallah cak y dagata wintsila kafafuwanta ta farayi tana dukan girjin shi da hannayenta tana Allah hero ka saukeni banaso shikuwa ina idanuwansa sun gama rufewa da xaxxafar kishi ko jinta bayayi gaban mota y cillata yaje y xagaya shima y shige y bawa motar wuta yabar layin. Su Amira ne suka shiga part din kaka a guje har suna rige2 shiga kaka da take xaune sai fadowarsu dakin taji suna sauke numfashi, kallansu tayi tace ku kuma menene haka kamar wadanda suka taho daga filin tsere Amira ce tayi magana bayan sauke numfashi da tayi tace wlh yaya Aslam muka gani kaka tace to shine me dan kun ganshi daxu y dawo ina islam din kuma khausar tace suna waje tare kaka tace ai shikenan. Islam kuwa cikin tsiwa ta dago kanta bayan ta daidaita xamanta acikin motar tace wai hero menene hakane nifa gaskiya banason wulakanci yama xa'ayi daga wani ganina ka wani daukoni ka sakani a mota to waima ina xaka kaini ta karashe maganar da murguda baki,banxa Aslam yayi mata jin bai mata magana ba shine y sakata dago kanta da niyyar kara masa rashin kunya ganin da tayi fuskarshi ta dawo mata exactly irinta hero na da data sani in xaiyi mata mugunta shine y sakata hadiye maganarta amma dai tana kunkuni. Sai data ga sun doshi asalin gdansu shine ya sakata xaro ido tace nabani ta shagwabe fuska tace haba hero yanxu tsakani da Allah dan acemin yar dadi miji shine ka daukoni ka taho dani gda salon ace banida kunya nabiyo mijina daga ganinshi, duk da ransa a bace yake sai da yayi murmushi jin sunan data kirashi dashi horn yayi gate man y bude gate din hancin motar tasa y danna xuwa cikin gdan a packing space yayi packing futowa yayi y xagaya y bude mata kofa y janyota saura kadan ta hantsilo saura kadan ta kifa y rikota mugun riko yayi mata har sai data tayi kara janta y farayi da gudu2 ta fara binsa saboda yanayin tafiyarsu ba 1 ba kuma gashi sauri yakeyi key y ciro a aljihunsa na gdan y bude suka shiga palon hankadata yayi kan kujera kum ta bige kanta auch tace ta rike kannata har idanuwanta kwalla ta fara taruwa ta dago kanta tace hero menene haka lokacin har hawaye y fara sauka a kuncinta wani kallo y jefeta dashi cikin kakkaurar murya yace wanene y saukesu a mota har kike masa bye2 kike murmushi, wani banxan kallo ta jefeta dashi ta mike ta goge kwallar idonta tace oho yanxu nagane dalilin rashin mutuncin da kake mini to tsaya kaji. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:08 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *119* Goge kwallar data xubo a kuncinta tayi tayi masa kallan up & down duk da girman daya dadayi y tsorata ta amma haka ta xage ta fara masa rashin kunya tace to tsaya kaji bansani ba kuma baxan fada ba inhar ka damu da sanin wanda y sauke mu ai da saika bi bayan motar shi bakaxo nan ba kanamin jan ido ta karashe maganar da jan siririn tsaki hade da murguda dan karamin bakin nata a ranta tana watako shi hero baxai taba canja hali ba kenan nida naso dawowar nan tashi ace mun gina sabuwar rayuwar aure amma shine xaixo da wani sabon salon to wlh nima xan koma masa asalin islam dita dan ba xoronsa nakeji ba. Aslam kuwa duk abinda take fada sam baiji taba sakwamakon shagala da yayi da yayi da kallanta shi sai yanxu ma ya kula da canjawar da tayi ta wani cika ta xama babbar mace ashe ma pic dinta dayake kallo yake susucewa baiga komai ba kurr y kurawa boobs dinta idanu yana kallon dukiyar fulaninta da sukayi wani fum2 acikin riga tamkar an hura balon islam kula da tayi baimasan mai take cewa ba dan y riga y shagala da kallanta shine y sakata tafa hannunta firgigit y dawo yace amm uhmm mema kikace wani far2 tayi da idanu tace shafa kaji murmushi yayi yace me kikace murguda bakinta tayi tace naje shafa kaji shafa kansa yayi ya wani yi murmushin gefen baki hade da taune lebensa na kasa y wani tande baki cak taji y dagata tamkar y dauki yar baby y sabata a kafada ya fara haurawa stair da ita. Cikin tsoro islam ta xaro ido ta kwallah kara tace haba hero menene haka dan Allah ina xaka kaini yace kefa kikace na shafa naji shine xan kaiki daki dan xanfi jin dadin shafawa kinga sai nagane matar tawa ta girma ne dahar tayi wannan furucin lokaci 1 cikinta y bada kara kululu tare da kwalla kara tana wayyo Allah kaka ki taimakeni na shiga 3 dan girman Allah hero kayi hakuri wlh subutar bakine Allah baxan kara ba banxa yayi mata yaci gaba da haura benen da ita wasu ma 2 yake hadawa ganin bai san ma tana rokon shiba shine y saka ta fara dukan bayanta da hannu bibbiyu ganin wannan ma ba mafita bace,har sunkai palon sama bashida niyyar direta gani tayi y farayin dakinsa da ita daidaitar wuyansa tayi ta gantsara masa cixo mai xafi bakaramin ratsashi cixon yayi ba saboda on expected yaxo masa da sauri y direta yana auch y shafo gurin ita kuwa ganin haka tace kafa mai naci ban baki ba ta bawa wandanta iska sai da taje daidai kofa ta juyo tayi masa gwalo tare da juyawa tayi rawa ta kada masa hips dinta ta shige dakin tasa sakata. Aslam wata doguwar ajiyar xuciya yaja hade da fadawa rajab kan kujera yana mai da numfashi dan yau dinnan yaso cimma burinsa akan yarinyar nan haka y tashi jiki a sabule y shige bedroom dinsa, islam kuwa tana shiga daki bayan ta sakawa kofarta key kan gado ta fada tana mai da numfashi can kuma ta kyalkyale da dariya tace lallai ma hero dinnan da mai yake nufi lallai da kuwa abinda nake tunani yayi tunanin aikatawa da yaga hauka tashi tayi ta shiga bathroom ta dauro alwala dan ko sallar magruba batayi ba. Bayan ta idar da sallah wayarta ta dauko acikin pose dinta ta bude data ta fara whatsap Amira ta gani online,tuni ta tura mata da massage " _to da kuka gudu kuka barni bai kasheni ba banxaye_" Amira turo mata tayi da sakon dariya " _Hhhhhhh_" tace kuma " _dama munce xai kasheki ne_" Cikin jin haushi islam tace " _bansani ba shiyasa naga kun gudu ba_" Rabuwa tayi da Amira ta tafi ta yiwa khausar ma jaraba sannan ta koma grp dinsu na *classic lady* sukaci gaba da hira su khausar suna ta tsokanarta a grp khausar ce tace ga *topic* tuni kowa yace muna jira tuni hausar ta rubuta *topic* kamar haka" _wata saboda yar dadi mijice shekara 2 bata ganshi ba amma saboda dauki tana ganinsa ta bisa dan dauki ko kowa y fadi ra'ayinsa_" Tuni aka fara comment wasu suna cewa tayi dai2 wasu nacewa tayi rashin kunya sai 11:00pm islam ta sauka online cire kayan jikinta tayi ta daura towel ta shiga bathroom wanka tayo ta futa xama tayi ta shafa mai ta fesa body spray wata sleeping dress ta dauko gown mai kauri tasaka saboda weather din garin sanyi ne nan fa taji cikinta y fara kugi alamar yunwa kasa xaune tayi ta kasa tsaye dan tasan kota kwanta baxata iya bacci ba saboda yunwar da takeji shahada kawai tayi ta tafi ta bude kofarta da niyyar tafiya kitchen dan ta samu abinda xata sakawa cikinta. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:10 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *120* Lokacin data futo tana xuro kafarta tayi tuntube da lader da sauri ta dauka tambarin chip plus tagani a jikin ledar cikin jin dadi ta dauko ta koma dakinta xama tayi a kasa ta baje lader din pounded yam tagani da agusi soup sai kuma pepper soup na caw leg sai kuma lemo da ruwa murmushi tayi tace Allah sarki hero nasan baxai banni da yunwa ba bathroom ta shiga ta wanko hannunta ta futo xama tayi taci abincinnan sosai ta daura sauran kan fridge tasha lemonta da ruwa bathroom taje ta wanke wannunta hade dayin brush ta futo tabi lafiyar gado taja blanket ta lullube kanta bata yi 5 minute ba bacci yayi gaba da ita. Bangaren Aslam kuwa lokacin daya shiga dakinsa shima cire kayansa yayi ya daura towel y shiga wanka bayan y futo you shafa Mai y fesa body spray shaf2 y shirya cikin brown troser hade da milk din shirt key din mota y dauka yaje y siyo abinci a restaurant dan yasan islam bata wasa da cikinta dire mata nata yayi a bakin kofarta dan yasan dole xata futo ta dauka shikuma yaci nasa a palo haka yayita xama a palon ko xaiga futowarta amma sam bata futo ba xuwanshi bakin kofarta 3 da niyyar yayi mata knocking sai y fasa yanxu ma bai dade da shiga daki ba lokacin daya futo yaga harta dauke abincin ta koma yaso y kara kallan koda face dinta ne haka y koma daki jiki a sabule y kwanta amma ko yaya y rufe idonsa surar islam ce takeyi masa yawo a idanuwansa pillow daya y janyo y rungume yanata kissimawa a ransa ace princess dinshi ce rungume a jikin shi haka dayasan yau baccin daxai yi na dabanne. Washe gari 8 o'clock Aslam y futa direct gdansu y wuce yanayin packing part din kaka y wuce dan har lokacin idanuwansa y manta irin murmushin daya ga islam tanayi wa wanda y saukesu a mota ganin baiga kaka a palo ba yasan sanyinnan ne y hanata futowa direct dakin Amira y wuce murda handle din yayi sai y jishi a bude danna kansa yayi cikin dakin kwance y hangota akan gado tanata sharar baccinta karasawa yayi kusa da kanta bubbuga pillow din da take kai y farayi cikin bacci Amira taji ana buga mata pillo xumbura baki tayi tace haba kaka da sanyinnan ma baxaki bar mutum yayi baccin safe ba ko bude ido batayi ba ta karajan blanket ta lullube kanta ji tayi ance ke baxaki tashi bane firgigit ta bude idonta dan ta gane muryar wane lokaci daya ta mike a gadon tana raba idanuwa jikinta na rawa, kallanta yayi fuskarnan tashi tamau tamkar bai taba dariya ba yace ke nutsu banason shirme sonake ki fadamin wana gani jiya ya saukeku a mota, cikin barin baki Amira tace bkwa tsawa y daga mata yace karki rainamin wayo mana ko munafuka kikeson xama ne jiya da idona naga an saukeku a mota shiru tayi dan sai yanxu ta tuna ma tsabar tsorone y mantar da ita, wata tsawar y daka mata wadda tafi ta daxu yace badake nake magana ba kikayi min shiru koni din sa'an wasanki ne, da sauri tace wlh ba kowa bane kawar muce itada mijinta suka rage mana hanya lokacin da suka gammu a titi mun rasa keke napep kirr y tsare ta da ido yanaso y gano gaskiyar maganarta jan iska yayi y furxar yace kin tabbatar da sauri ta daga kanta tace wlh da gaske nake juyawa yayi y fice a dakin yana ki hadamin kayan islam. Wata muguwar ajiyar xuciya Amira taja ta dafe kirji tace tab lallai islam ba karamin namijin kokari takeyi ba da take iya mayarwa da yaya Aslam magana inya fada mata mara dadi tab ta kama haba tace ni gashi yanxu daga tambaya na rikice komawa tayi ta kwanta a gadon ta runtse idanuwanta saboda har yanxu tsoron bai sake taba,mikewa tayita ce bari dai na tashi na hada kayannan karya dawo y tarar ban hada Ba. Aslam yana futa daga bedroom din Amira na kaka y wuce xaune y tarar da ita a bakin gado y karasa gaisawa sukayi kaka tace shine jiya ka dauke matar taka ko sallama baka bari munyi ba sosa kansa yayi yace ai kaka wlh amm uhm dariya kaka tayi tace kaji dannema watako yau ni kakejin kunya dariya yayi yace ah haba kunyar lafiya kin taba ganin miji yaji kunyar matarsa itama dariya tayi tace to daga ina kake da safennan dan daga ganin alamu ko wanka bakayi ba cewa kaka yayi eh wlh abinci naxo daukar mana kinsan ko kayan abinci ban siya ba tace eh ai kana rawar jikin ganin matarka ko tunanin babu abincin a gdanku bakayi ba ka dauke matarka tashi yayi yace kai kaka ni bari na barki inajin kishi ma kikeyi tunda naga kinata taso da maganar y fice. Part din aunty amarya yaje y gaisheta murmushi tayi tace my son yau dai kaje ka karasa gyaran gdan kadan dudduba abubuwan da babu dan anjima kadan Xa'a kaimaka matarka murmushi yayi yadan sosa kai yace ai aunty na a gda islam din ta kwana kallan mamaki aunty amarya tayi tace bangane ba cikin kinkina yace amm ehh jiya ai natafi da ita yayi maganar kansa a sunkuye murmushi aunty amarya tayi tace aika hutashshemu yace amm aunty amarya kinyi break fast da yawane daukar mana naxoyi eh tace ta shiga kitchen ta hado masa acikin basket ta mika masa godiya yayi y karba y fice. Part din mommy yaje y gaisheta itama amsawa tayi amma batayi masa maganar islam ba dan batasan ya dauketa jiya ba part din kaka y koma y dauko kayan islam daya saka Amira ta hada y xubasu a mota y fice xuciyarsa fess dan dama abinda y dagula masa ita yanxu yaji ba gaskiya bane. *wannan pages din 119 & 120 sadaukarwa ne ga maryam ngd sosai da kulawarki a gareni nakin gajiyawa da kirana a waya kiji lfyta sannan kiji ko nayi posting* *dan Allah inaso nayi amfani da wannan damar ga masuyimin magana ta private na tura musu goyon kaka daga farko ko kuma wasu pages din wlh kunyi yawa nagaji kullum saina turawa mutane sunfi a girka kuma gashi nayi nisa dan Allah duk mai neman buk dinnan ta dinga cigiya a grp din da take nasan xata samu dftn xakumin hakuri* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:11 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *121* Lokacin da Aslam yaje gda bayan yayi packing bayan motarsa y bude y dauko basket din abinci da trolly bag din kayan islam direct cikin gda y wuce da sallama y shiga palon bayan y tura kofar ai numfashin shi saura kadan y dauke sakamakon islam daya gani xaune a palo sanye take da half best iya breast dinta kawai ta rufe ta kamata sosai dayake roba ce pusher pink colour ce a gaban ta an rubuta *PRETTY* da bakin painty da manyan baki hade da dogon wando black colour yayi mugun kamata ta sama inda ta kasa y bude sannan anyi tsaga ta gefe tundaga gwiwar ta har xuwa kasa akwai wasu buloli ajikin tsagar wandon inda akayi wata igiya pusher pink akayi xarge a tsakanin bulolin,gashin kanta kuwa ta rabashi 2 ta kamasu da pusher pink roboms tayi kalba a karshen gashin, tana reto har kafadarta kunnenta kuwa wani dan kunne ne mai O shape pusher pink shima simple makeup tayi a face dinta daga powder sai kwalli sai pusher pink lipstick sai kyalli lips dinta suke amma ba karamin kyau tayi ba kafarta sanye take da sosa baki ta daura kafarta daya kan daya tana chatting. Wani yawu y hadiya kutt a xuciyarsa yace naga fa alamar yarinyar nan haukatani takesonyi ji wata muguwar shiga da tayi da kyar y tattara nutsuwar shi guri 1 y karayin sallama a palon firgigit ta dago kanta saboda chatting din da takeyi y tafi da hankalinta bataji shigowar shiba wani malalacin murmushi ta saki hade da mikewa tana ur wlcm back hero sai data wani karkada jiki sannan ta fara tafiya Aslam kuwa mutuwar tsaye yayi ganin yadda take tafiya komai na jikinta na motsi shi gani yake tamkar da gayya take tafiyar harta karaso kusa dashi bai sani ba saboda yadda y shagala da kallanta y saki baki da hanci hade da tsareta da idanuwa ko kiftawa bayayi iskar bakinta ta hura masa a ido wata ajiyar xuciya yayi yace pretty kinaso ki kasheni da salonki tsare shi tayi da idanuwanta masu daukar hankalin wanda ake kallo farare tas sannan sanye take da kwalli ta daidaita shi acikin idanuwanta tace ammm magana kake? girgixa kansa yayi dan baiyi tunanin maganar ta futo fili ba y xata a xuci yayi karbar basket din abincin tayi ta juya tana tafiya tana wani kada hips Aslam kuwa binta yayi tamkar rakumi da akala hannunsa yana janye da trolly dinta yanajin wani masifar son islam hade da sha'awarta yana fixgarshi ji yakeyi tamkar yaje y rungumota ko xaiji sassauci acikin ransa. Dining area ta karasa ta daura basket din akai ta tafi kitchen ta dauko plate da cup dayake harda kunun gyada aunty amarya ta sako musu, bayan sun gamacin abincin Aslam jiki duk a mace y tashi y haura stair dan xuwa yayi wanka,islam kuwa tattara kwanukan tayi takai kitchen ta wanke wadanda sukayi amfani dasu sannan ta dawo palo ta kunna kallo. Xuwa can anjima khausar ta kirata tsokanarta takeyi tana amarsu a gdan captain a.u anjima kadan muna hanya xamuxo muci ragowar kaxar amarci dannasan yaya Aslam baxai barki ba jiya dole ki biya kaxar nan dan bakyaci bulus ba sai da islam ta kyalkyala dariya tace haba yarinya wai waya fada miki kin manta nace baxan bawa hero kaina ba har sainayi candy duk da nasan xuwa lokacin ma kawai karfin hali xanyi nayi rayuwar aure dashi amma nasan baxan taba son hero ba don da kiyayyarshi y horeni tun tashina dariya khausar tayi dagacan bangaren tace gaskiya karki cutar da yayanmu kawai yarinya ki bada kai bori yahau dariya islam tayi tace nikarki dameni da xancen banxa sai anjima din in kunxo ta katse kiran ta ajiye wayar taci gaba da kallanta. Abinda islam bata sani ba tun lokacin data fara waya Aslam y taho amma jin abinda take fada shine y dakatar dashi bai karasa sakkowa ba bakaramin mawuyacin hali y shiga ba lokacin dayaji tana fada a waya haryanxu bata sonshi runtse idanuwansa yayi xuciyarsa na kuna yanajin wani irin xafi a ransa danshi yaji a kumatunsa shafawa yayi yaji ashe hawaye ne suka xubo yace a ransa ashe nikadai nake haukata nake fama da dakon sonta ashe shirme nakeyi da nake tunanin islam tana sona goge fuskarsa yayi yace kinyi kuskure da kika bari najiki nikuma nadauwa kaina alkawarin koda lokacin da kika diba xaki bani kanki yayi baxan taba kusantarki ba harsaina tabbatar nakoya niki axababbiyar kaunata wadda xata kasance duk bugu na numfashinki saikin tunani sakkowa ya farayi fuskarsa a sake tamkar baiji komai ba (nikuwa nace namijin duniya kenan). *_Tom jama'a kundaiji wannan batu na Aslam da islam ko a cikinsu waxai gaji y sakko daga dokin xuciya kudaici gaba da biyoni danjin yadda lbrn xai kasance* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:12 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *GOYON KAKA* *122* Daya sakko ko kallan inda take baiyi ba saboda bayaso ta fahimci wani abu a tare dashi,kitchen y wuce yana shiga y tafi store dubawa yayi yaga akwai kayan abinci kuma basuyi komai ba futowa yayi a kitchen din hanyar kofa yayi yana bari naje kasuwa nadawo Allah y kiyaye tace masa da amin y amsa yasaka kansa y futa. A mota ma haka y dingajin ranshi a jagule harya karasa kasuwa rago y siya y bayar a gyara masa sannan y tafi gurin saida kaji da xabi nan ma y siya yace a gyara y karasa gurin kifi y siya shima sanan y wuce gurin masu kayan miya hade da vegetables y siya komai dai yaje y siyo species suma y siya kala2 daganan y harhada komai yayi gda yana xuwa yayi packing y furfuto da kayan joseph mai gadi da Peter mai gyaran flowers sune suka taho da sauri suka debar masa kayan a bakin kofa yace su jirashi sai daya shiga cikin gdan yacewa islam ta tashi a palon xa'a shigo da kaya tashi tayi ta shiga dakin kasa su joseph suka shigo da kayan sannan Aslam y kirata kallanta yayi yace ga kayan amfani nan na siyo sai kuma yace aff ashefa ba abinda kika iya niyanxu xanje gda nadauko kayana dana taho dasu jiya ki jirani inna dawo na dafa mana abincin ko kallansa batayi ba ballantana yasaka ran xata bashi amsa a ranta tana lallai hero y rainani yana nufin kullum jiya iyau xan xauna aikuwa yau xan baka mamaki xan xame maka dan hakin daka raina sai daya kai kofa y tsinko maganarta tana Allah y kiyaye ka gaishemin dasu kaka murmushi yayi kawai yasa kansa y fice. Fara xuxxuba kayan tayi komai a muhallinsa sannan ta gyara gurin shiyawa tayi ta fara dafa fried rice wadda tayi carrot,green beans, pease da kuma hanta da koda gashi taji speses da corry tuni gda y dauki kanshi sannan tayi chicken pepper tana gamawa ta daura xobo wanda yaji kayan kanshi sai sannan ta yanka abarba cocumber kankana ta xubasu a blander ta markada ta tacesu juye xobon nata tayi akan ruwan tayi syrup din sugar ta xuba hade da flavor da foster clack painapple & coconut ta juyesu a jugs ta xuba a fridge tattara kayan datayi amfani dasu tayi ta wanke tayi moping din kitchen din tuni y dawo tamkar ba'ayi amfani da komai acikinsa ba futowa falo tayi ta dada gyarashi tayi morping ta kunna boner tasaka turaren wuta tuni palon y bada wani daddadan kanshi gana girki sannan gana turare duba time tayi taga 2:30pm da sauri ta haura stair sai data farayin sallah sannan ta shiga wanka. Bayan ta futo a wankan xama tayi a gaban dressing mirrow ta tsantsara makeup tamkar wanda xata tafi gasar xabar sarauniyar kyau sannan ta mulke jikinta da sihirtacciyar humra hade da dadawa da body spray akwatin da Aslam y dauko mata kayanta ta janyo wani maroon swiss lace ta dauko mai touch din green blouse & skirt ta saka yayi bala'in yimata kyau gashi yabi shape din jikinta y kwanta ta taje gashinta ta xubo da wani ta gaba tayi packing din ragowar a baya ta daura dankwalinta tamkar nadin gwagwgwaro ta dauko fashion din sarka da dankunne silver da stones din green ta saka wow aituni ta futo tamkar xara acikin wata dada fesawa jikinta turare tayi ta dada kallan kanta a mudubi ai ita kanta sai data godewa Allah wayarta taji tana ringing daukowa tayi number din Amira ta gani saurin picking tayi, Amira tace gamufa a bakin kofarki tun daxu munata knocking islam tace eyya sorry 6*s nashiga wankane amma ganinan futowa yanxu da sauri ta xura takalmi ta sauka taje ta bude musu. Suna shigowa suka wani lumshe ido hade da jan numfashi sukace wannan kanshinfa, khausar ce ta taba Amira tace ke kanshin amarcine bakiga harda wani kyallin amarci takeyi ba dariya suka kyalkyale da ita har islam duka ta kaiwa khausar tace wlh ke yar air ce karasa shiga palon sukayi suka xauna khausar ce tace kai nifa wlh yunwa nakeji murmushi islam tayi tace toh acici khausar tace naji kitchen ta shiga ta dauko warmers din data xuba abinci ta futo dasu ta koma ta dauko jug 1 da cups da plate da spoon da serving spoon ta futo abincin suka xauna sukaci sunata buga saniti islam kuwa sai babaka dariya takeyi kiran sallar la'asar akayi kitchen islam ta shiga ta kuskure bakinta taxo ta saka hijab ta shimfida sallaya ta tada sallah suka bedroom din kasa suka shiga sukayo alwala suka futo. 4:30pm Aslam y dawo knocking yayi islam taje ta bude masa da sauri y kareta yacewa su joseph su ajiye masa trolly bags din anan sai daya lumshe idonsa a ransa yace y rabb a koda yaushe pretty canjawa kikeyi tamkar kullum canja miki halinta akeyi hannunshi ta kamo tace wlcm my hero haushi yaji a ransa yace watako yarinyar nan baxata daina kirana da sunannan ba kirkixo murmushi yayi yace tnx janyo trolly daya yayi da hannunsa daya hannunsa kuma yana cikin na islam baisan lokacin daya fara murxa hannunta ba saboda taushin sa tamkar nayan jaririyar xirrr islam sakamakon jin wani bakon yanayi da yake bakuntarta Aslam kula da yayi islam ta fara shiga cikin wani yanayi shine y saka shi cigaba da murxa hannun nata islam ganin in sukaci gaba da tsaiwa ahaka komai xai iya faruwa shine y sakata yin magana cikin shagwaba hero akwai su Amira fa a dakin da sauri shima y saki hannunta cikin jin kunya yadan shafi keyarsa y koma y debo sauran trollies din guda 3 y dawo. *_Alhmdllh today it's 4 years my wedding anniversary i need ur prayers sisters_* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:16 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *123-124* Su Amira ne sukace ina wuni yaya cikin daurewar fuska y amsa murya ciki2 tabe baki islam tayi yana kokarin haurawa stair islam tayi amfani da wata irin murya wadda har cikin kwanyar kai Aslam yajita tace my hero ga lunch dinka canfa akan dinning tsintar kansa yayi da juyowa daga stair din ya nufi dinning murmushi islam tayi ta karasa itama dinning din. Food flask ta bude tafara serving dinshi lokacin dayaji kanshi y daki hancinsa da sauri y lumshe ido ji yayi gaba daya ransa y biya da abincin dan tundaga yadda yaga fried rice din tayi wara2 colour dinta y futo sosai vegetables din cikinta yayi shar aciki tuni yaji yawunsa y cinke har wani tande lips yakeyi, islam tana gama serving din abincin a plate ta tura masa gabansa ba wani dar ya saka cokali y fara ci harwani kada kai yakeyi saboda yadda dadin abincin yake ratsashi murmushi islam tayi ta dauki wani plate din ta xuba masa chicken pepper shima ta tura masa gabansa kitchen ta koma ta bude fridge ta dauko jug din xobon data saka ta daura a try hade da cup ta futo, tararwa tayi Aslam yanata xura loma dariya ce taso kwace mata dai ta danne ta karasa ta dire try din hade da xama a kujerar opposite din tasa. Sai da Aslam y cinye abincinnan tas bai kula ba sai daya saka chokali yaji babu dariyar da islam take kunshewa ta kyalkyale da ita tace kai hero ashe haka kake dacin abinci cikin jin kunya yadan sosa keya hade dayi mata kallan kasan ido amma bai tanka mata ba islam cikin dariya tace ko a dado ne dago fuskarsa yayi da take a tamke yace wai ina wasa dakene koni abokin wasanki ne da sauri ta toshe bakinta tana girgixa kai dan tagane wannan muxuran da yakeyi duk borin kunya ne,plate din chicken papper din y janyo shima y cinye tas sannan yadauko jug din xobo ai lokacin daya fara sha wani mugun dadi yaci y gauraye masa kwanya tamkar xai tsinke kunne haka y dinga tuttulawa cikinshi xobonnan sai daya shanye rabin jug sannan y hakura badan xobon y isheshi ba sai dan jin dayayi cikinsa tamkar xai fashe. Mikewa yayi dakyar saboda yadda yaji cikinsa yayi wani mugun cika a ransa yana tunani shidai yasan a iya rayuwarsa bai taba cin abinci mai yawan haka ba amma maimakon y yabawa islam ina saima wani yatsina fuska da yayi yace gashinan narufawa abincin naki asiri nacishi dan maggi ma yayi yawa aciki sannan cikin pepper din tayi yaji da yawa,xobon kuwa suga yayi yawa,islam duk da taji haushin kalamansa amma sai ta danne tayi dariya tace kadai fada ne kawai amma nasan a iya rayuwarsa baka tabacin abinci mai dadin haka ba ta karashe magana da murguda baki yatsina fuska yayi amma bai ce komai ba dan yasan abinda islam ta fada gaskiya ne, y wuceta yahaura stair. Kwance yake akan gadonsa sai juyi yakeyi hade da murmushi daga hannunsa yayi yace alhmdllh Allah ngd maka daka cikamin burina ka bani irin matar da nakeso kyakykyawa ga tsafta gason kanshi uwa uba iya girki Allah ka sanya mata sona acikin ranta dannasan shima abune mai sauki a gareka y ubangijina y shafa addu'ar hade da lumshe idanuwansa yana kissima abubuwa da dama daxai faru acikin rayuwar auransu shida princess dinshi. Sai dayaji kiran sallar magruba sannan y tashi y shiga bathroom y dauro alwala y futo y kalli su Amira yace ku jirani nadawo daga masallaci saina kaiku gda to kawai sukace shikuma y fuce. Islam kuwa kitchen ta shiga ta daura tuwon semovita miyar danyar kubewa wadda taji bushashshen kifi hade da naman rago sai fruit salad data hada da taimakon su Amira ta gama hada abincin cikin 2 hour nasu joseph ta xuba acikin wani food flask sannan ta haura stair dayake tayi sallar magruba da isha'i a kasa bathroom kawai ta shiga ta sakarwa kanta shower cikin 15 minute ta futo simple makeup tayi sannan ta shirya cikin yellow top mai dogon hannu hade da bakin skirt dogo har kasa ya kamata ta sama sosai ta bayanshi kuma akwai tsaga a tsakiya sosa ta dauko yello ta saka hade da nada yellow veil ta riko after dress a hannunta ta sakko. Xaune ta tarar da Aslam ya bude kayan tsarabarshi y bawa su khausar tsarabarsu cikin manyan leda sannan yabawa khausar ta mommy kuma har sagir y siyawa agogo islam taji dadi sosai sannan y sakawa kowa tashi tsarabar a leda kama da mommy,aunty amarya,kaka,dad dy,Abba,dadai dukka yaran gdan y deba ya kalli su Amira yace ku taso mu tafi islam tayi xuruf tace basuci abinci bafa khausar tace maci in munje gda abincin su joseph islam ta dauko ta biyosu Aslam kawai ji yayi an bude front seat an shigo dago kansa yayi ganin islam yayi ta kame a xaune ko after dress din bata saka ba tana rike a hannunta dauke kansa yayi daga kallanta yace ke kuma wayace ki futo rau2 tayi da ido cikin shagwabar murya tace binku xanyi tsoro nakeji shiru yayi mata yaja motar suna karasawa wajansu joseph ta mika ma peter abincin joseph kuma y bude musu kofa suka futa. Suna xuwa gdan kaka dukkansu suka futo Aslam ganin islam nashirin tafiya a haka shine yace to baxaki saka rigar taki ba xaki tafi xumbura baki tayi ta saka after dress din suka wuce part din kaka,aslam y rabawa kowa tsarabarsa sun karba suna godiya dasa albarsa sai wajen 10pm su islam suka tashi suka tafi gda suna xuwa abinci kawai sukaci,sannan Aslam yace pretty muje kema ki karbi tsarabarki cikin jin dadi ta mike suka karasa palon akwati guda y bude mata acikinsa englih wears ne,dogayen riguna takalma jakunkuna harda jewelries da bangles masu kyau cikin jin dadi islam ta fada kan Aslam ta bashi peak a kumatu tace tnx my hero Allah y kara budi yace Ameen,dayan akwatin dayake gabanshi y shafa yace wannan kuma na amarya tane mai xuwa nan bada jumawa ba kar cikin xuciyar ta taji saukar maganar cikin jin haushi ta tashi ajikin cikin masifa islam tafara magana tace to saime aini baxaka birgeni ba sainaji gobe ana ayyuriri an kawo maka amarya shine xansan kacika,Aslam tsantan kishinsa y hango kwance akan fuskar islam amma sai ya waske duk da dariya yakeson yi jin yadda ta balbaleshi da masifa yace haba yan matana saurin me kikeyi nan da 4 month xata shigo karki damu tamkar yaune cikinjin haushi ta wuceshi ta suka haura stair tabar kayannata anan shima tashi yayi xuciyarsa fes saboda ko banxa ya gano sansa a xuciyar islam kuruciya ce kawai ta hanata gane tana sonsa shima y haura stair y wuce dakinsa. Washe gari haka islam ta dinga cin magani ita bata yadda ba tana fushi Aslam kuwa sai fakon idonta yakeyi yana mata galo tsahon 2 days islam ta dauka tana fushi daganan ta ware. *A GURGUJE* Haka rayuwar su islam taci gaba da tafiya kullum islam da kalar abinci da xatayi safe rana dare sannan duk lokacin da tayi abinci tana xubawa su joseph,haka Aslam xai xauna y narki abincinsa amma hakan baxai hanashi y kushe ba tun islam najin haushi harta gaji yanxu haka tasaka an fara cikita mata yarinyar da zata dinga taimaka mata da wanke2. Yau saura 2 days su islam su tafi pkotercort pepper soup tayi na kifi amma sai ta xuba a flask ta daura a try hade da plate dan a garden takeson ci kallan Aslam tayi da yake amfani da laptop dinsa yana magana akan motocin da xa'a shigo masa dasu tace hero nidai natafi garden saika taho murmushi yayi yace saurin me kikeyi da baxaki jirani ba tace a'ah ni baxan jira kaba sai dai ka taho ta fice tana dan wake2 ta. Xaune take a garden ta bude flask din pepper soup dinta na kifi ta xuba a faranti ta rufe sauran ta saka spoon ta faracin pepper soup dinta cikin jin dadi ashe abinda islam bata sani ba magece a can nesa da ita kadan nanfa mage taji kanshin kifi a hankali ta fara daga hancinta tanabin sahun inda taji kanshin kifi nan fa idonta yayi arba da plate din kifi kan cinyar Aslam lokaci daya magennan ta taho da gudu tayo kan islam, sai a lokacin islam ta kula da magen ai da hanxari ta mike ta kwasa a kuje hannunta rike da plate din kifin magen ma ganin haka ta mara mata baya gudu islam takeyi magen na Binta Aslam kawai take kwalawa kira tana ihu hero!hero!!hero!!! a bakin kofa sukayi kicibis da Aslam saboda yajiyo ihunta y taho da gudu lokacin yayi dai2 da tayi fatali da plate din kifin wata muguwar suka magen tayi ta tafi gurin kifin islam kuwa taxaci kanta xata fada haka ta fada luuuu kan Aslam ta sume. *_ngd sosai yan uwa da addu'o'inku a gareni da tayani murnar xagayowar ranar aurena Allah yabar kauna y kara xumunci ngd ngd ngd sosai_* *_may be nan da 2 days baxakuji posting dina ba saboda wani uxiri daya tasomin amma inna samu yadda nakeso ko gobe xakuga posting dina dftn xakumin uxiri_* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:17 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *125-126* Cikin firgici Aslam y fara girgixa ta jin ko motsi batayi da sauri y tafi dispenser y tsiyayo ruwa yaxo y yayyafa mata jin har lokacin batayi motsiba shine y saka shi kama kanshi yace oh god y xanci gefenshi y kalla yaga magen harta gama cinye kifin daya bare a kasa tana lashe romon dayake kasa cikin xafin nama Aslam yayi kan magen yayi mata wata muguwar danka har saida magen tayi kara saboda taji damkar da akayi mata direct waje Aslam yayiwa da ita. Su joseph y fara kwalawa kira joseph! peter!! kuna inane wai cikin tsoro suka futo daga dakin da aka tanadar musu a gdan jikinsu yana rawa saboda kiran da sukaji ogannasu yanayi nusu xubewa sukayi a gaban Aslam cikin gurbatacciyar hausar sukace gamu oga wani mugun kallo y jefesu dashi yace acikinku wane ya kawo mage cikin gdannan tuni cikin peter y bada wani kululululuu saboda duk magunan gdan nashine tuni jikinshi y dauki rawa cikin barin baki yace nawa ne oga wani mugun kallo Aslam yayi y wulla masa magen datake hannunsa cikin peter yace ka tabbatar ka futar da duk wata mage da take gdannan cikin 5 minutes inka kuskura ka wuce time din dana dibar maka kasan cewa tamkar ka rubuta takardar barin aikin kane y juya y wuce peter cikin barin jiki y tattara magunan gdan ya sakasu a cikin buhu y fice dasu daga gdan. Aslam yana komawa cikin palon ruwa y dada debowa wannan karan kwarawa islam yayi wata muguwar ajiyar xuciya tayi hade da jan numfashi bude idanuwanta tayi taga Aslam a kanta a tsaye da sauri ta tashi taje ta rungumeshi tace wlh hero magennan kasheni takeson yi dan taga ina tsoronta shine take xuwa gurina ta tuni hawaye suka fara ambaliya tare da shashshekar kuka Aslam har cikin ranshi yakejin kukannata a hankali y fara shafa bayan ta yake y isa kiyi shiru daga yau baxaki kara ganin mage a gdannan ba domin nasaka an fitar da ita daga gdannan a hankali ta xare jikinta daga nasa ta koma kan three seater ta wani lafe tamkar marainiya tuni Aslam yayi wani mugun tausayinta y kara kamashi da kansa y futa yaje garden y dauko kifin y dawo kitchen y shiga y dauko plate da kansa y xubawa islam amma sam taki karba gani takeyi tamkar inta karba magen xata kara dawowa. Yau su islam xasu tafi photercort tafiyar tasu ta hada da Amir,Amira,khausar xasu tafi flight suka bi lokacin da suka isa photercort safwan ne yaxo airport y daukesu sai wani rawar kai yakewa khausar itama haka ta xage tana nuna masa kalar soyayyar datake masa direct gdansu ya kaisu mammy ce ta fara nan2 dasu khausar kuwa sai wani kunya takeji mammy ce ta kula ta kasa sakewa mammy ce ta janyota jikinta tace yata ki saki jikinki dani nima mahaifiyarki ce sannan khausar ta ware. Yaune reception din da aka hadawa su Aslam na dawowa daga singapore lfy bayan jawabai da akayi hade da paretty da sojoji suka gabatar daganan aka fara rabawa su Aslam lambar yabo islam itace ta raka Aslam y karbi nasa inda khausar ta raka safwan y karbi nasa bayan pics da akayi hade da ciye2 da shaye2 taro y watse kowa yaji dadi. Washe gari su islam suka shirya xasu koma kano saboda ranar monday xasu koma makaranta amma banda Aslam saboda shi baiga amfanin komawar shi gda ba dan inya koma ma hankalinshine xai na tashi dan sam islam ta futo da wata tsurfa sam ta daina saka atamfa ko lace a gdanta sai english wears shiyasa yace baxai koma ba danshi kenan kullum cikin shan ruwan lipton hade da lemon tsami saboda bakaramin kokari yakeyi ba ganin y jure xama da islam duk da yana cutuwa gata dason jiki in dai suna xaune to dole tana jikin sa. Yau monday bayan su islam sun shirya isya driver shine y dauke su y kaisu makaranta acan suka tarar da khausar bayan anyi assembly aka bawa islam dan kwalin head girl khausar assistant head girl Amira kuma labour prefect sannan kowa y koma class sukayi attending lesson. To tundaga wannan my mukami da aka bawa su islam iyayi y karu da rashin m dan dama su islam ba baya bane ita da khausar gwanda Amira itace ma bed babu ruwan ta. Aslam kuwa baya xuwa gda sai bayan 2 to 4 weeks saboda sam baxai iya da halin islam ba shikenan duk randa yaxo kano sai ciwon cikin shi y tashi dan haka cikin fridge dinshi baya rabuwa da lemon tsami sannan koda yaushe cikin saka islam yake ta dafa maga ruwan lipton. Yauma islam ce kwance kan cinyar Aslam shikuma yana xura hannunsa cikin kanta yana rawa dan xura hannunsa cikin sumar kanta yana shafa mata har wani lumshe idanu takeyi saboda dadi xaraf ta mike tamkar wadda aka mintsina tace yauwa hero dama inaso inyi maka tambaya wai me kakeyi da lemon tsami da yawa haka ne nagansu acikin fridge dinka sannan duk lokacin daka tafi photercort inna shiga dakin naka xan gyara saina ga bawan lemon tsamin da yawa a dustbin dinka mekakeyi dasu lumshe idanuwansa yayi yace magani kara tambayarshi tayi tace bakada lafiya kansa kawai y gyada mata tace mai yake damunka ji tayi kawai y janyota y hada bakinsa da nashi yana aika mata da wani irin xaxxafan kiss wanda yake rikita mata kwanya inbata manta ba raban da islam yayi kissing dinta tun randa xai tafi singapore sai yau wani irin bakon yanayi take ji yana ratsata wanda ta kasa fassara shi ta bangaren Aslam ma hakan take dan ba karamin rikicewa yayi ba sai jikin numfashi yake saukewa da sauri2 islam jin da tayi Aslam yana shirin wuce gona da iri shine y saka ta tureshi da sauri ta koma wata kujera ta xauna tana mai da numfashi Aslam ne y dago rinannun idanuwansa cikin wata irin murya ya fara magana nagaji! nagaji! nace miki nagaji Islam so kikeyi ki kasheni ne kinsan adadin lokacin dana dauka ina cutar kaina akan nafaranta naki ran amma kin kasa fahimta sai yamin rai kikeyi akan hakkina to wlh tsaya kiji hakurina y kare nidai baxan iya karbar hakkina a gurinki ta karfi ba amma bari kiji yau xan koma photercort kuma baxaki kara ganina a kwanannan ba har sai ranar da kika shirya bani hakkina cikin wani mawuyacin hali y tashi y haura stair islam kuwa sakar baki tayi tana kallan Aslam sai daya wuce ta y haura stair sannan ta saka kanta a tsakanin cinyoyinta ta fara rera kuka (nikuwa nace da kenan yarinya ki bada kai bari ya hau kin tsaya iyayi ) Aslam kuwa yana shiga dakinsa dakyar y iya hada lipton da lemon tsami yasha saboda mugun kallo murdawar da marar shi takeyi masa bayan 5 minutes yaji marar ta saki wayarshi y dauko y kira mai yankar da ticket yace yanason ticket din flight daxai tafi photercort to yace sannan y katse kiran trolly bag y janyo y hada kayansa sannan y shiga bathroom yayi wanka bayan y futo y shirya y janyo trolly bag dinshi y futo xaune y tarar da islam a palo tana shashshekar kuka duk da har cikin ransa yakejin kukannata amma haka y saka kai y fice daga palon. Bayan Aslam y futa kiran wayar haidar yayi yace yahau keke napep y sameshi a airport y karbi key din motarto haidar yace Aslam bai dade da xuwa ba haidar ma yaje y mika masa key din mota yace kana xuwa kana kai Islam skultoh haidar yacey karba Aslam kuma y shige cikin airport y karbi ticket dinsa sai daya yahau flight sannan y turawa islam da short massage sannan y kashe wayar. Islam har lokacin kuka takeyi jin shigowar massage wayarta har xata share sai kuma ta janyo wayar ganin hero ne yayi mata massage da sauri ta bude massage din jikin ta har rawa yakeyi murmushi dauke a fuskarta gani tayi ya rubuto mata *ban yadda kije gda ba wannan karan ki xauna a gdanki sannan haidar xai dinga xuwa yana kaiki skul* bayan ta gama karantawa hulli tayi da wayar ta dada rushewa da kuka har wani shidewa taji tanayi sai da taji kanta fara ciwo sannan tayi shiru amma ta kwanta tayi luf akan kujera. Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:18 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *127-128* Haidar lokacin daya isa gda part din mammay y shiga xaune y tarar da ita da wata yarinya da baxata haura 12 years ba mommy tana ganin haidar tace Yauwa haidar xona aikeka gdan Islam kakai yarinyar nan mai tayata aiki ce,haidar yace to ammh mommy yanxu mafa na karbo mukullin motar yaya a airport inaji photercort y tafi, mommy tace to ina islam din fa haidar yace tana gda yace ma ina xuwa ina kai islam din makaranta,mommy tace xancen banxa to me yaronnan yake nufi ta kalli haidar mikomin wayata dauko mata wayar akan center table kokarin kiran lambar Aslam ta farayi amma is switch up tsaki tayi tace wayar tashi ma a kashe take tana cikin mita tace haidar tafi ka daukomin daughter ta dan wulakanci yama xa'ayi yabar yarinya ita kadai a katon gdannan aunty amarya ce ta shigo a lokacin tace a'ah mommy fadan me kikeyi har waje ana jinki tsaki ta kumayi tace nida yaronnanne wai xai koma aiki amma y hana yarinya dawowa gda murmushi aunty amarya tayi tace kin tambayi islam dinne kinji ta bakinta kike yanke hukunci,mommy tace ai nasan baxata ce baxata dawo gda ba sai dai in shine y hanata aunty amarya tace a'ah dai kirata kiji dai. Dialing din number islam ta fara,islam tana kwace a lokacin har bacci y fara daukarta ringing taji wayarta nayi firgigit ta mike ta janyo wayar dan ita duk a tunaninta Aslam ne y kirata ganin bashi bane mommy ce sai taji jikinta yayi sanyi sai da kiran y kusa katsewa tayi picking,daga can bangaren mommy tace " _hello daughter na_" " _na'am_" islam ta amsa cikin sanyin murya. Mommy tace " _ya naji muryarki wani iri tamkar wadda tayi kuka?_" Islam jin hawaye tayi y silalo a kumatunta bayan hannunta tasaka ta goge hawayen tace " _uhm uhm bacci nakeyi kika kirani_" Mommy tace " _toh naji ance yaronnan yayi tafiya amma banga y dawo dake gda ba meyasa_" Islam tace " _bkmai nice nace ba saina xo gda ba xan yiwa su Amira waya suxo su tayani xama tunda ba dadewa xai yiba_" ta karashe maganar tare goge hawayen da yake xubowa a idanuwan ta tamkar an bude fanfo Mommy tace " _kin tabbata abinda kika fada gaskiya ne?_ Islam tace " _eh_" Mommy tace " _to shikenan Allah yayi miki albarka bari yanxu nasaka Amira ta shirya tayowa khausar magana saisu taho_" Islam tace " _ameen sai sunxo_" tayi rejecting din kiran sai kuma ta rushe da kuka. Mommy ce ta kalli aunty amarya fuskarta dauke da murmushi tace kinji ma ashe itace tace ya barta a gda ta tunda ba dadewa xai yi ba,dariya aunty amarya tayi tace toh ai gashinan ta baki kunya da kina nan kina fada bakisan ashe yar taki girma tayi ba tafara xaman gdan miji,dariya itama mommy tayi tace to ai hankalina baxai kwata ba da ace bankira ta naji ba aunty amarya data mike xata futa tace yanxu hankalin naki y kwata kiyi bacci da munshari ta fuce tana dariya. Mommy da kanta ta tashi taje ta axalxali Amira ta shirya ta kirawo khausar suka tafi hade da ma'u mai aiki gdan islam,xaune suka tarar da islam ta doka uban tagumi har sukayi sallama bata jiba khausar ce ta karasa ta tafa hannunta firgigit ta dago daga xurfaffan tunanin data tafi kwashewa sukayi da dariya khausar da Amira khausar tace ah lallai yarinya ta fara tunanin hero dinta suka kara kwashewa da dariya Amira ce tace kai duba idanuwan ta inaji ma har kuka tayi,haidar ne yace ku dallah malamai karku damar min mata y wani hade fuska yace matar meya same ki banxa tayi masa domin ita batasan ta inda xata fara musu bayani ba,haka haidar dasu khausar suka karaci tsokanar islam suka kyaleta amma ko ci kanku batace musu ba amma jin xuciyarta takeyi tana mata xafi har haidar yabar gdan da ido kawai take binsu ba wanda ta kula (nikuwa nace lallai islam an shiga 9 duk surutun islam yau tashin hankali y kasheshi gaskiya hero bai kyauta ba ). Washe gari ma haka islam ta tashi sukuku amma dai tana danyin magana ba sosai ba su khausar sun yi yin duniya ta fada musu abinda yake damun ta amma taki fada sai dai tace musu bkmai sai dai tanata yawan ta kiran waya amma bata shiga haka suka gaji suka kyaleta. Bangaren Aslam ma hakan take bakaramin yaki yakeyi da xuciyar shiba duk kuwa da yadda take axabtuwa da tunanin islam kallo 1 xakayi masa kasan yana cikin tashin hankali y rage walwala magana ma ba sosai yake yiba danko magana suke da safwan baya wuce yace uhm ko a'ah sannan yanxu y haramtawa kansa xaman hirar da sukeyi shida safwan a palo in sun dawo daga office sai dai y shige daki yabar safwan shi kadai safwan yayi yin duniya y fada masa meyake damunsa amma yaki fada tun safwan na damuwa har y kyaleshi. Sati 1 islam ta dauka acikin wannan hali sannan in ta kira number din Aslam bata shiga har wani kashin wuya tadan yi abinda islam bata sani ba Aslam a black list y sakata itace kawai bata samunsa saboda yanaso y horata akan laifin datayi masa duk da shima yana cutuwa yasha daukar wayar tasa da niyyar y cireta a black list y kirata amma sai xuciyarsa ta hanesa dayin hakan sannan sam y daina hawa whatsap duk dan islam. Mommy ganin Aslam yacinye 2 weeks bai xoba shine ya sakata kiran layin Aslam ta tambaye shi y xai bar yarinya a gda yace xai dawo da wuri amma har yanxu yaki dawowa cewa mommy yayi tayi hakuri akine y rikeshi amma y kusa dawowa. Bayan sun gama wayar islam y lumshe idanuwansa yace Allah sarki pretty na ashe tayi hankali tunda ta iya boye sirrin mu tsintar kansa yayi cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa wanda rabon shi da yaji irinsa tun randa yabaro kano. Tsawon 5 weeks islam ta dauka bataji muryar hero dinta ba damuwa iya damuwa ta shiga dan sau tari tasha kulle kan ta a daki tasha kuka tayi danasanin abinda tayi (nikuwa nace yarinya dana sani ai keya ce ba'a ganin ta ). Yau Aslam ji yayi kawai princes din shi yakeson gani yana dawowa daga office y fara tattara kayan sa safwan yace ina xuwa kuma Aslam yace kano dariya safwan y tuntsire da ita yace ai dama tun randa ka dawo garin nan tamkar an koroka nasan jerry din ka ce tayi tsiya shiyasa kaxo xaka saukewa mutane kwandan masifa aka shiyasa na watsar dakai wani kallan kasan ido Aslam yayiwa safwan yace kaini airport y wuce safwan binsa safwan yayi y kaishi airport. Islam yau tashi tayi tajita cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa khausar ce ta kalli Amira da suke a xaxxaune a garden tace Amira me kika fahimta a tattare da matar nan murmushi Amira tayi tace farin ciki dan tun daxu nakasa gane mata sai murmushi takeyi anya ba hero dinta bane xai dawo khausar tayi dariya tace tambayar mana ita dai tashi Islam tayi tana dariya tace ku kuka sani munafukai baxaku batamin farin cikina ba ta wucesu ta shige cikin gda. Misalin 5:30pm su islam ne xaune a palo sanye islam take da atamfa black & yellow simple makeup tayi amma ba karamin kyau tayi ba saboda colour din ta dace da fatarta ta daura dan kwalinnan das tamkar nadin gwagwgwaro kunenta sanye da fashion yellow sai xuba kanshi takeyi hankalinta nakan wayarta tana chatting muryar Aslam taji kamar yana sallama amma sai ta share ta xata gixon da muryarsa ta sabayi matane yauma a hankali Aslam y fara takowa cikin palon kanshin turare y doki hancin islam lumshe idanuwanta tayi ta kara shakar daddadan turarensa na tompord jin kanshin tayi yana dada karuwa dago idanuwanta tayi wajen da takejin kanshin nan fa idanuwanta sukayi mata toxali da Aslam tsaye a gabanta yana jifanta da tsadaddan murmushi bakin ta saki ta dada murxa idanuwanta domin ta tabbatar shi dinne ai kuwa taga bai bace ba sai ma ware mata hannu da yayi alamar ta taho cikin tsananin farin ciki tayi wulli da wayar ta kwasa a guje ta fada kirjinsa shikuwa y wani dada matseta yana sauke ajiyar xuciya yana shakar turarenta. *wannan page din nakune mmn zee,mmn khaleed,matar soja,malama (sadiya hudu) kai da duk masoya _goyon kaka_* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* [3/8, 10:20 AM] ‪+234 703 962 5239‬: *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *129-130* Sun dauki kusan 5 minutes a wannan halin ita kanta islam tsintar kanta tayi cikin farin ciki mara misaltuwa su amira kuwa ganin halin da masoyan suka shiga suna shirin wuce gona da iri da sauri suka ja kafafuwansu suka shige bedroom Aslam kuwa jinsa yakeyi acikin wata duniya ta daban islam jin da tayi Aslam na sauke mata wasu xafafan kiss a ilahirin jikinta haryana shirin haurowa xuwa fuskarta shine y sakata janye jikinta a wahalce taja hannunsa suka fara daga kafafu dakyar kan three seater suka fada ragwab suna mai da numfashi Aslam kokari yayi ganin y kwantar da islam kan three seater din shikuma ya hau kanta islam wata irin muguwar kunya taji ta kamata wadda bata tabajin irinta ba jin Aslam y fara aika mata da wadansu irin salon wasanni da sauri ta dakatar dashi ta rada masa cewa basu kadai bane a gdan,dagata yayi yana aika mata da wani sassanyar murmushi itama murmushin tayi ta tashi tana tattara gashinta daya barbaxu a fuskarta lakuce mata hanci yayi yace xan kamaki ne yarinya wani farr tayi da idanuwan ta sakar baki yayi yana kallanta domin ba karamin kyau tayi masa ba yace yauwa princess dina hannuwanta tasaka ta rufe fuskarta tana dariya tana shirin tashi y rikota yace haka ake tarbar miji badan drinks balle abinci bakinta ta xumbura tace toni kacemin ma xaka dawo ne bata karashe maganar ba taji bakinta cikin nasa kokarin kwace kanta takeyi ta kasa dan kanshi y saketa yana aika mata da wani shu'umin kallo ta kasan tashi tayi tace to muje dining kaci abinci binta yayi tamkar rakumi da akala suka tafi. Kuskus ta xuba masa wadda ta soyashi da green beans, peas, carrot, da kuma attaruhu da abasa sai tayi masa miyan nikakken nama ba karanmin dadi girkin yayi ba sai kuma tayi water melon drink wanda yasha madara tsayawa Aslam yayi y narki abincinnan sosai bayan y gama su Amira suka futo suka gaisheshi y amsawa anan islam take gabatar masa da ma'u wadda xatana tayata aiki amma ita asma'u xatana cemata girgixa kansa Aslam yayi kiran sallah ne y tasheshi y haura stair y dauro alwala y tafi masallaci nan fa su khausar suka tasa islam a gaba suna mata tsiya itadai murmushi kawai takeyi musu. Sai bayan sallar isha'i Aslam y dawo tare suka shigo da amir yaxo daukar su Amira sai wajen 10:00pm sannan su islam suka raka su amira suka dawo. Washe gari xaune Aslam da islam suke suna hira Aslam rungume da islam ma'u kuwa tana dakin ta dan tunda Aslam y dawo ta daina xaman palo, kallan islam Aslam yayi yace fadamin wanne irin missing dina kikayi cikin shagwaba tace uhm uhm kwaikwayar muryarta yayi shima yace dan Allah yadda y wani kwantar da murya shine y sakata kyalkyalewa da dariya tace kai hero kaga yadda shagwabar nan tayi maka kyau karayi nagani shima dariyar y ktalkyale da ita yace naki din salon ki rainani ko dariya tayi tace ni na'isa ta kama baki kallanta yayi cikin ido yace har kinyi yawa ma to fadamin irin missing dina da kikayi tace irin yadda kayi missing dina nayi missing dinka yace Allah da gaske kinsan irin missing dinki danayi kuwa nadaina cin abinci na daina xaman hira da safwan na daina dariya kai halin dana shiga yayi yawa kallan shi tayi tadan harare shi tace bawani nan kawai fada kakeyi nafi missing dinka dubeni fa har rama nayi tunda ka tafi nake trying number ka amma sai acemin is not not recharble bakaramin tashin hankali nashiga ba koda yaushe cikin kiran layinka nakeyi amma sam yaki shiga haka su Amira suke sakani a gaba suyi tamin dariya amma bana damuwa nidai burina kawai nasameka naji muryarka ko na samu sassauci a xuciyata amma duk nacina ban taba samu ba nakoma kullum cikin xuba ido ko xanga kiran ka amma shiru a haka xakace kayi missing dina Aslam da tunda Islam ta fara magana y tsare ta da idanuwansa yana kallanta tsantsar gaskiya yake hankowa a kalamanta da take fada a fuskarta wani irin sanyin dadi yana mamaye masa xuciya ashe bashi kadai yayi missing dinta ba itama tayi kuma yaga rama a fuskarta wani rungumeta yayi yace sorry my little princess ni kaina in kika kalleni sosai xakiga narame a tunanina wannan horone nayi miki ashe har kaina xan cuta naso na cire tunaninki a raina amma abin yaci tura nakasa yakice ki acikin raina duk bugu na numfashina saina tunaki y dada matseta ajikin shi har tanajin bugun numfashin sa yace narasa wanne irin so nakeyi miki plz my princess ki soni koda kwatan yadda nake sonki ne muji dadin gina rayuwar auran mu,shiru tayi masa haka y din ga fallasa mata sirrin xuciyarsa akan kanshi mamaki y dingayi dan bai taba tunanin xai iya son wai wata aba ita Islam ba har kuma y xauna yana fada mata wadannan xadadan kalaman. Haka rayuwarsu taci gaba da tafiya abin sha'awa xasuyi wasa tare su shiga kitchen suyi girki tare wani lokacin har tsere sukeyi acikin sweeming fool tare. Wannan karan da Aslam xai tafi photercort islam kuka shagwaba ta dingayi masa bakaramin rikicewa yayi ba saboda yanxu in akwai abinda y tsana to kukan islam ne haka y xauna yanata faman lallashi dakyar ta hakura shima saboda fara waec da xasuyi shine yasaka baxai tafi da ita ba domin shima ko kadan bayason abinda xai rabashi da princess dinshi. *A GURGUJE* Su islam sun fara waec yanxu ko lokacin chatting bata dashi karatu sukeyi sosai itada su Amira yau bayan sun futo a pepper xaune suke Acikin makaranta suna jiran haidar amma shiru sai daya bata musu 30 minutes yaxo kuma shida wata yarinya islam ce ta tashi sai kumbure2 takeyi saboda yau wata irin muguwar yunwa takeji gashi haidar y bata musu lokaci tana karasawa taga yarinya a gaban motar tuni fushin fuskarta ya kau tace a'ah yaya haidar wace wannan sanin halin islam da yayi xata iya yimai abinda xaiji kunya agaban budurwarsa shine saka shi hade rai yace budurwa tace dariya tayi suka gaisa har su khausar ma sai daya fara kai budurwar tasa gda sannan yakai su islam. Aslam kuwa tunda y koma photercort yake fama da ciwon ciki a daddafe yayi sati 1 y jiyo da niyyar duk abinda xai faru sai dai y faru amma wannan karan kota karfi sai y karbi hakkinsa gun islam yau wajen 8:00pm y dira kano da xummar wannan xuwan duk wadda xa'ayi sai dai ayi amma baxai kashe kansa a banxa ba haka y dinga saka yana warwarewa y rasa samun solution har y karasa gda. Lokacin daya isa gda su khausar y tarar a palo bayan sunyi masa sannu da xuwa y tambaye su ina islam Amira ce tace tana daki tana wanka stair y haura lokacin daya shiga dakin wani sanyin dadi yaji y daki hancin sa lumshe idanuwansa yayi in bai manta ba rabon sa da shigowa dakin islam tun randa aka kawota yau kusan 3 years kenan gadon ta y tafi direct y xauna jin lallausan xanin gadon shine y saka shi kwanciya yana shakar kanshin turaren data fesa ajikin bed sheet din ta 10 minute y dauka a kwance islam ta futo. Tundaga kan xara-xaran yan yatsun kafarta y fara kallan ta har xuwa santala santalan cinyoyin ta wani lumshe idanuwan sa yayi yanajin wani bakon al'amari yana tsirga masa islam kuwa tana xuwa gaban dressing mirrow ta saki towel din y fadi kasa jikakken gashinta ta barbaxa ruwan ne y sauka kan fuskar Aslam dayake kwance bude idanuwansa yayi ai saura kadan numfashin sa y dauke saboda toxali da idanuwansa sukayi da surar islam,da sauri y mike daga kwancen da yake nan fa islam ta gano hero tacikin mirrow ta xaro idanuwa tayi tace hero sai kuma ta kalli kanta kara ta kwalla ta dauki towel dinta da sauri ta daura Aslam kuwa daya shagala wajen kallan dukiyar fulanin islam karar datayi ce ta fargar dashi cikin tsiwa ta karaso gabansa tana wata girgixa Aslam kuwa wata irin muguwar sha'awar islam yaji tana fusgarshi ji yakeyi tamkar yaje y rungumota,tsare Aslam tayi da idanuwanta na rashin kunya tace hero menene xaka daki ba neman excuse ta wani karkace baki eh nama gane dama so kakeyi kaga jikina kuma ka gani to dan haka dan Allah malam ayi waje ta karashe maganar da nuna masa hanyar waje,murmushi yayi cikin wata wahalalliyar murya yace eh naganki ai koyamin kikayi ke sau nawa kina ganina ba kaya y tsareta da idanuwansa,murguda bakinta tayi tace eh amma lokacin ina yarinya neko yace ok to ai shikenan yanxu ma xaki iya gani belt din wandansa y fara xamewa ai islam ganin abinda yake shirin yi shine y sakata kwalla kara tashige bathroom din ta a 360 ta sakawa kofar key tana mayar da numfashi a ranta tana lallai hero sai fatan shirya tunda yake kokarin iya cire wandon sa a gaba na sai da taji futarsa sannan ta futo a bathroom ta sakawa kofarta key ta fara shiryawa. Aslam kuwa lokacin daya shiga daki kasa xaune yayi y kasa tsaye yana neman mufuta can naga y saki wani sasanyan murmushi yace yes wannan shawarar tayi futowa yayi daga dakin shi xuciyarsa fes tamkar ba abinda ke damunsa. Washe gari bayan yakai su khausar gda lokacin daya dawo peter y kira yace ina magunan nan naka peter cikin barin jiki yace wlh oga tun ranar daka ce nafita dasu a gdannan naje na bayar dasu dafe kansa Aslam yayi yace oh god ka samomin mage nan da xuwa bayan sallar magruba ko axomin kayi toh peter yace cikin barin jiki. *dan Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting dina kwana 2 hakan y farune saka makon biki da xamu fara yanxu haka sai nan da 4 days sannan xakuga wani posting din nawa dan yanxu haka ina hanyar jigawa,da wannan nake so namika sakon gaisuwa gareki BINAFA sakonki y iso gareni na ari bakin yan uwana domin miki sakon gaisuwa ta hade da agare ki godiya mungode3 sosai Allah yabar xumunci daduk masoyan GOYON KAKA ina gaishe a duk inda kuke kuma nima ina sonku* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* ?Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 *Na Umma that's Musa* *GOYON KAKA* *131-132* Cikin farin ciki Aslam y shiga cikin gda xuciyar shi fes a kitchen y tarar da islam tana hada musu dinner sai sauri takeyi saboda tana shirin yin dare a girkin nata da fara'arsa y karasa y sakalota y sakata acikin Hannayensa y hadeta da girjinsa yana shinshinar huyanta wata irin kasala taji ta dirar mata turo baki tayi tace haba hero y xa'ayi ka rikeni ka hanani karasa aikina kana ganin ina shirin kai dare murmushi yayi y cika ta y fara tattara hannun rigarsa yace bari na tayaki kinsan yau ke ta daban ce,kallan shi tayi da alamar tambaya tace bangane ni ta musamman bace,kanshi yadan shafe yace amm ba komai ai ke kullum ta musamman ce kinji ma kiran sallah akeyi bari natafi masallaci y futa yana kissima abubuwa da yawa a ransa. Sai dayayi sallar isha'i sannan y dawo gda tarar wa yayi peter y samo masa magen mai kyau kuwa cikin farin ciki y karbeta xuciyar shi fes a wani kwali y sakata sadaf2 y shiga cikin palon jin motsin islam a kitchen shine y bashi damar hayewa stair cikin sauri dakin islam direct y wuce bathroom dinta y bude y ajiye magen y futo da sauri y shiga dakinsa y boye kwalin acikin wardrop y sauko kasa. Kitchen y leka yacewa islam princess ki futo kiyi alwala kiyi sallah bari naje nadawo amsa masa tayi tana adawo lfy ka tahomin da abin dadi murmushi yayi yace toh y fice. Gurin siyar da gasassun kaji yaje y siyo guda 3 manya2 sannan y siyo ice cream y siyo kayan fruits kuma y dawo gda hannunsa niki2 da kaya. Islam y gani tanata saurin hada kayan abinci a dinning area dan yau ko wanka bata samu damar yi da wuri ba birinta yanxu ta gama jera abincin akan dinning taje tayi wanka kafin lokacin cin abincin su yayi. Aslam ne y shigo hannunsa rike da kaya ganin islam da yayi y tabbatar bata je dakinta ba shine y saka shi jin dadi yace ah princess y akayi bakiyi wanka ba har yanxu yana karasa xama kan kujerar dinning dan tsaki tayi tace wlh yau aikinne yakai min dare gyada kansa yayi yana bubbude warmers din tace amma yanxu kafin lokacin da xamuci abinci yayi xanje nayi wanka kanshi ne y bugi hancinsa yace ina kawai kixo ki xuba mana abincin mu muci nima yau bacci nakeji in mun gama kyaje kiyi wankan dirdira kafafuwanta ta farayi alamar shagwaba tana haba hero ka kyaleni nayi wankan mana tunda yanxu kaurin girki nakeyi shima kwaikwayonta yayi yace uhm uhm nikuma yunwa nakeji dariya ta kyalkyale da ita tace toh xubawa ma'u tayi ta kwala mata kira taxo ta karba ta wuce dakinta ita kuma ta xuba musu nasu. Aslam yace ki xuba mana kadan fa kinga kayan dadinki nasiyo amma sai kinyi wanka saiki futo palon sama muci to islam tace, bayan sun gama a tare suka debe kwanukan suka kai kitchen sai data dauraye kwanukan Aslam kuma y dauki nasu peter yakai musu lokacin daya dawo har islam ta gama rufe kofar gdan yayi ya taho suka haura stair rungume da juna a palo y ajiye ledar kayan yace nima bari naje nayi wankan y shiga dakinsa itama ta shige nata. Aslam yana shiga da sauri y cire kayansa y daura towel ya xauna a bakin gado yana sakin murmushi dan yasan yanxu xai jiyo ihun islam,islam kuwa tana shiga daki harda murxa key tayi ta cire kayanta ta daura towel bathroom ta nufa a hankali ta farajin kukan mage cikin tsoro ta xaro ido waje tace mage sai kuma ta basar tace mema xai kawo mage gdannan bayan an fitar dasu balle harta shigo dakina karasawa tayi ta bude bathroom nan fa idanuwanta dukayi toxali da mage da sauri ta kwalla kara ganin da tayi magen nashirin futowa shine sakata janyo kofar cikin xafin nama ta rufe magen a bathroom ihu take kwalawa tana kiran hero tana tsalle ta kasa gaba ta kasa baya jikinta kuwa sai rawa yakeyi gaba daya tunaninta y tsaya a wuri 1 takasa tabuka komai sai ihu da take kwalawa Aslam yana daki yajiyo ihun islam jallabiyaya y saka da sauri y futo y tafi dakinnata ya tura amma y kasa budewa saboda a rufe yake sannan yana jiyo ihun islam sunanta y fara kira da karfi yana jijjiga kofar sai lokacin islam taji kuxari da gudunta ta taho jikin kofar tana kokarin nudewa amma ta kasa saboda yadda jikinta yake rawa ga gunjin kuka kuma gashi hankalinta yana bakin kofar bathroom dan gani takeyi kamar magen xata futo Aslam jin da yayi islam takas budewa shima cikin kidima yace ki nutsu ptincess ki budemin kofar mana dakyar ta samu ta bude masa kokarin shigowa yake tana kokarin futa nan sukayi gware saurin kankame shi islam tayi tana kuka muryarta harta fara dashewa har wani shidewa takeyi tana hero mage cikin wani tausayin islam yaji y kamashi ganin yadda take kuka sai yaji dama baiyi amfani da mage ba amma ba yadda xai yine domin itace kawai mafuta a gareshi da xai futa daga halin dayake ciki kamar gaske cikin kidima y maimaita mage kanta kawai ta gyada masa tambayar ta yayi tana ina bathroom kawai take nuna masa da hannunta bathroom din y nufa yana magana garin yaya mage ta shigo gdannan eh lallai yau sai su peter sunyi min bayani magen y dauko islam nayin toxali da ita ta xube a sume da gudunsa Aslam yayi stair ya sauka yaje y bude gdan y kira peter da sauri y mika masa magen yace kayi sauri ka mayar da ita inda ka karbota y koma da gudunsa. Ciccibar islam yayi y shigar da ita cikin dakinsa y daurata akan bed ruwa y dauko a cikin fridge y tsiyaya a kofi y yayyafa mata wata doguwar ajiyar xuciya taja ta wani bude idanu sai kuma ta lumshesu kankame Aslam tayi tana wani sabon kukan bayanta y shiga shafawa a hankali yana kiyi shiru princess kinga nafuta da magen ashe ma bata gdannan bace ta makota ce ta shigo a hankali ta fara sauke ajiyar xuciya tana sakin numfashi da dai2 da dai2 mikewa yake shirin yi da sauri ta rukoshi cikin dasashshiyar murya tace ina kuma xakaje wanka yace mata dama nacire kayana xan shiga ne shine najiyo ihun ki nafuto da sauri Allah nema y kiyaye da ba kaya xaki ganni saboda harna shiga bathroom cikin shagwaba tace ni to ai tsoro nakeji shafa bayanta yayi yace ki kwantar da hankalin ki babu mage yanxu a gdannan ki tayi ta wani tukwikuyeshi tashinta tsaye yayi yace to muje muyi wankan tare dannaga alamu kamar kema bakiyi ba tashi tayi domin yanxu bata da wata dabara data wuce suyi wankan dan tasan indai basuyi ba tofa baxata iya bacci ba sai da suka shiga bathroom din kuma ta fara kunyar cire towel dinta kula Aslam da yayi kunya takeji shine y saka shi shammatar ta kawai saiji tayi y kwace towel din y sakata cikin bahon wanka da sauri tasaka hannunta ta rufe girjinta murmushi yayi shima y cire nasa y shiga cikin bahon wasu kalar sakonni y fara aika mata masu rikita jiki sun dauki kusan 30 minutes yana aika mata da xafafan sakonni sannan y kyaleta sukayi wankan islam kuwa idanuwanta a kulle suke saboda wata irin kunyar Aslam da takeji. Bayan sun futo a bahon wankan da kanshi y mika towel ta karba ta daura duk kunyarsa ta isheta alwala yasa ka ta daura suka futo murmushi kawai Aslam yakeyi saboda yasan tarkon daya daya y kama xomo bayan sun futo sallaya ya shimfida musu kallanshi tayi da shagwaba tace hero toni wanne kayan xan saka wani malalacin kallo y jefeta dashi yace jeki ki dauko a dakinki mana cikin tsoro ta xaro idanuwanta sai kuma ta murguda bakinta tace tab yama xa'ayi naje dakinnan murmushi yayi a ransa yace yau bakin rashin kunya xai mutu xura jallabiyar shi yayi yana sedai in kina so nabaki na amarya ta xumbura bakinta tayi tace oho nidai bani kawai wardrop dinshi y bude y dauko mata wani katon hijab mai hade da skirt a wani wulakance ta karbesu tana yatsina fuska lokacin daya mika mata dan ita kadai tasan bakin cikin da takeji wai yau ita hero xai wulakanta yana mata xancen wata matar haryana bata kayanta lokacin data ware su hijab da skirt ta gani kallansa tayi baki a sake tace menene wannan yace sallah xamuyi sannan nabaki kayan xama tayi a bakin gadon tace toh nidai nayi sallah kallanta yayi yace nafila nake nufi to ai nayi shafa'i da wutiri kaga ba sauran nafila da xanyi sai ta cikin dare ganin ba xata ganeba yace in baxaki taso mu tafi ba tashi ki tafi dakin ki tunda ba xakiji magana taba tashi tayi tana xumbura baki tasaka skirt da hijab din dai2 ita tagansu kallan Aslam tayi tace lah hero kayan budurwar taka dai2 ni ashema ba babba bace aikuwa in taxo tace xatamin iyayi narkarta xanyi murmushi kawai Aslam yayi yace mudaiyi sallah tayar da nafila yayi raka'a 2 yajasu sannan yayi musu addu'ar samun xaman lfy da xuri'a ta gari tambayoyi yayi mata kallansa tayi tace to ina ruwan ka da tambaya ta akan abubuwan da bau shafi rayuwar kaba kallanta yayi y daure fuska yace Allah nakara tambayar kika karamin gardama saikin futa a dakinnan sai data gama kunkunin ta sannan ta fada masa amsar tambayoyin da yayi mata tashi yayi y cire jallabiyar y daura towel y shafa mai y feshe jikinsa da dadadan body spray tana xaune tana kallansa tana karewa halittarsa kallo y gama shiryawa y bude wardrb dinshi ya dauko wasu sababbin kayan bacci milk color masu taushi y saka sannan y juyo yaga shi take kallan cewa yayi wannan kallan fa juyar da fuskarta tayi tace niba kallanka nakeyi ba yace to xoki shirya tashi tayi itama taje ta shafa mai shikuma y futa y dauko musu leader din kayan dayaxo dashi hade da turarukan ta y shigo dakin janyo wata trolly bag yayi y bude hadaddun sleeping dresses ne aciki(dftn kun tuna lokacin da Aslam y dawo daga tafiya yaxo da trolly bag guda 2 yace 1 ta amaryar sace da xataxo nan da wata 4) wata haddiyar nyt gown y dauko mata milk colour shara2 mai gdan bra da karamin pant y mika mata dududu rigar xuwa cinyar tace karba tayi ta ware su har xatayi magana da sauri ta tuna worning din da yayi mata da sauri ta kwashesu ta shiga bathroom ta saka su ta futo a kunyace kallanta y shiga yi babu ko kiftawa cikin sauri ta karasa ta dauki hijab din da tayi sallah ta saka shikuwa saurin nata ba karamin burgeshi yayi ba saboda yadda halittun jikinta sukeyin rawa wani lumshe idanuwansa yayi y janyo leader din kayan y bude sosai islam taci kaxar nan domin bataci abincin kirki ba dan dama Aslam yace karta cika cikinta ice cream kuwa roba 1 ta shanye medium size tana gama ci ta kalli Aslam cikin shagwaba tace hero brush dauko mata sabo yayi a loka din mudubi y bata tashiga bathroom ta tsaftace bakinta ta futo tabi lfyr gado kallanta yayi yace me kike nufi tace bacci xanyi to yace y mike y tattara kayan y daura kan fridge shima y shiga bathroom y wanke bakinsa y fito y kwanta a bayanta. *sakon gaisuwa a gareku aysha silent kabo daughter & zainab ngd sosai akan soyayyarku a gareni Allah yabar xumunci wannan page din na sadaukar dashi a gareku* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *133-134* Blanket din data lulluba dashi yake shirin yayewa y shiga cikin sauri ta mike jinsa kusa da ita futula ta kunna ta wani turo baki gaba tace wai hero kana nufin akan gadonnan xaka kwanta mikewa yayi shima y jefeta da wani kallo yace eh naji isa nida dakina ace xa'amin iyaka dada tura bakinta gaba tayi tace to ai naga bakunci naxo dakinka ko hararar wasa yayi mata yace toni ne na gayyatoki balle ki sakamin doka nabi wlh in har baxaki kwanta ba sai dai ki tashi kibar dakinnan wani murmushi ta sakar masa tace haba hero menene na daukar xafi ai naxata xaka kwanta a kasa ne tunda dama bamu taba kwana guri 1 ba sassanyar dariya y saki yace a'ah ni baxanyi kwanciyar kasa ba sai dai intafi palo na kwanta y mike hade da daukar pillow xai fuce, kanta ta daga sama alamar tunani tace to yanxu inya futa magennan ta dawo fa y xanyi sai kuma tace au ashe fa gwanda y tafi karnaje yamin wani abin kuma ma ai nasan babu magen a dakinnan......ai bata karasa tunaninnata ba tajiyo kukan mage miyauuu...miyauuu...wata muguwar sufa tayi hade da kwallah kara Aslam da yake shirin ficewa a dakin saiji yayi islam ta cukwikuyeshi tana maida numfashi ai saura kadan y saki dariya abinda islam bata sani ba Aslam ne y makale murya yayi kukan mage cak y tsaya yace menene haka cikin shagwaba tace kukan mage fa naji murtuke fuskarsa yayi kamar gaske yace banason haka nifa bacci nakeji y xa'ayi kice kukan mage kikeji bayan babu mage a gdannan kawai kinbi kin saka tsoro a xuciyar ki shiyasa ma kikejin kukun magen ni sakeni natafi na kwanta uhm uhm tace cikin shagwaba hade da magale kafada nidai gaskiya nayadda ka kwanta a dakinnan tsoro nakeji wani sanyayyan murmushi yayi hade da lumshe ido harda hamdalarsa a xuciya amma a fili yace toh da sharadi guda 1 cikin sauri eh nayadda tun kafin taji sharadin yace saikin yadda xaki cire hijabin...ai tun kafin y karasa fadar sharadinsa ta cire hijabin tayi hulli dashi wani mugun kallan sha'awa yake bin kirjinta da kallo har wani lumshe idanuwa yakeyi dan idanuwan nasa harsun fara canja kala cak y dagata y sabata a kafada y fara tafiya da ita dariya ta saka tahau tukan bayansa tana karkada kafafuwa cikin shagwaba tana ita y sauketa. Bai direta a ko ina ba sai kan bed nan y fara mata cakulkulu dariya take kyakyatawa sosai sai da yaga harwani shidewa takeyi saboda dariya shine yasa y kyaleta muginawa yayi ya kwanta yana facing din p.o.p din dakin cikin sauri ta tafi ta kwanta a girjinsa ta wani kankame shi tana maida numfashi hannu yasa y kashe fitilar dakin a hankali y fara shafa bayanta wani irin dadi islam takeji har wani bacci2 taji yana shirin debeta a hankali y fara aika mata da rikitattun sakonni wanda yake shirin mantar da ita a duniyar da take Aslam ganin da yayi islam bata san duniyar da take ciki ba nanya fara aika mata da manya2 sakonni cikin xafi kissing din fuskarta yakeyi tun daga goshinta,idanuwanta,kumatunta lokacin daya kai bakinsa cikin nata wani rikitaccen kisses yake bata harwani sarrafa harshenta cikinnasa yake islam kuwa ji takeyi kamar tace wayyo Allah dadi nishi kawai take saki y salam lokacin daya kai hannunsa kanna fulaninta ai shima shidewa yayi ai tuni yakai bakinsa kansu to nidai daganan najawo hannun mmn 2 da aunty jamee da matar soja nace mu fuce matar soja kuwa cewa tayi ita baxata futa ba sai taji lokacin da xa'a kashe bakin rashin kunya dakyar dai na lallaba ta muka fuce muka bar masoya 2 nan cikin duniyar maji dadi. A palon saman muka xauna nikam kyankyadi sai dibata yakeyi sai mmn 2 namikawa wayar nace taci gaba da muku typing cikin gyangyadi wata rikitacciyar kara ta daki kunnena a xabure na mike ina raba idanuwa ihun islam naji tana wayyo kaka wayyo mommy wayyo Amira wayyo khausar ku taimakeni ummu haseen kuwa harda guntuwar kwallarta lol ai su mmn 2,aunty jamee, matar soja da gudunsu sukayi hanyar dakin harda rawar su wai yau Aslam y kashe arna nikuwa tausayin islam y hanani motsi musamman danaji tana kwalamin kira tana aunty umma ki kawomin dauki nace badani ba wannan kasadar bandai sani ba ko ummu haseen xata iya . Nidai har wajen 3:00am sannan naji kukan Islam yadan tsagaita kallan ummu haseen nayi data rafka uban tagumi nace gaskiya hero mugu ne tace hmm kedai bari inajin fa sai yanxu y kyale yarinyar nan xaro idanuwa na nayi na dafe kirji nace na shiga 3 su mmn 2 nacewa kuxo mutafi to furr suka ki suka ce sai sun jira gobe sunyiwa amarya gashi wata dariyar yake nayi nace ai shikenan dan har lokacin inajin amsa kuwwar karar da islam tayi a kunne na nace to ni natafi tare da ummu haseen muka futo kowa yayi gda. Washe gari 7:00am a gdan Aslam tayi min ina shiga gdan a palon kasa nayi xamana sai 8:00am Aslam y futo fuskarshi fess dauke da annurin amarci sai washe hakorannan yakeyi tamkar gonar audiga su mmn 2 y tarar xaune a palo kallansu yayi yana washe baki dan sam yau ba daure fuskar nan yace a'ah yau bakine a gdanna mu cikin jin kunya su mmn 2 sukace amm uhmm ehh ai tun jiya muke gdannan da mamaki yake kallansu yace tun jiya matar soja ce tace eh islam mukaxo gasawa tunda jiya ka kashe arna kallansu yayi da mamaki y kallesu yace toh yanxu nagane toh ku jirani washe hakora sukayi sukace toh daki y shiga bed side carbinet y bude y dauko karamar bindiga y futo ai aunty jamee ce ta farayin toxali da karamar bindiga ai a 360 ta kwasa tayo down stair ganin haka su mmn 2 ma suka kwasa a guje sukayo kasa dariya Aslam y tuntsire da ita yace ai da kun tsaya ni na gasaku y koma y ajiye bindigar. Kasa y sauko y shiga kitchen y hada break fast 1 hour y daukeshi a try y jerasu y tafi sama dasu bedroom dinshi y shiga da kayan abincin a gaban gadon y ajiye islam nagani kwance a cikin blanket fuskarta ce kawai a waje tana baccin wahala dan idanuwanta duk sun kunbura saboda kuka a hankali y koma y kwanta y rungumeta ta baya nan wani baccin yayi gaba dashi cikin shauki da farin ciki. Sai 9:30am y farka nan ma saboda islam tana da exam ne by 11:00am a hankali y fara tashinta bude idanuwanta ta farayi a hankali saboda wani irin nauyi da sukayi mata ga wani axababban ciwon kai dayake damunta tana bude idanuwan ta kalli Aslam kawai saita saka kuka wuwii da sauri y rungumeta yana sorry my one & only plz stop crying nasan nayi miki lefi amma ba'a son raina hakan ta faru ba babu yadda xanyi ne idan har na barki shedan xai iyayin galaba a kaina y kaini kokin dana sani ngd3 miki matata Allah yayi miki albarka y bamu yayaye na gari yadda kika shayar dani farin ciki a daren jiya kema Allah yasa annabi s.a.w y shayar dake ruwan alkhausara. Cikin shagwaba fuskarta kace2 da hawaye tace Allah hero kai mugune jiya kakusa kasheni kuma saina fada wa mommy abinda kayimin ta karashe maganar da rushewa da kuka dada kankameta yayi dan har cikin ransa yakejin kukanta yace naji amma dan Allah kiyi hakuri indai nine baxan kara ba amma in baxaki fadawa mommy ba tace to baxan fada mata ba da kanshi y dauketa suka shiga bandaki sai daya dada sakata cikin ruwan dumi sannan sukayi wanka suka futo shiryawa yayi cikin black jeans da purple to. shirt ba karamin kyau yayi ba fuskar nan tashi sai kyallin angwancina takeyi islam ma ta shirya da kanshi yaje dakinta y dauko mata unifoam y kawo mata tasaka ita kanta wani mugun kyau tayi domin fuskarta ta ddada tayi fiyau sai idanuwanta da sukayi ja suka kumbura da kyar y lallaba ta tayi break fast kadan taci ma saboda sam bakinta babu appatiet haka y dada kyara kan gadon saboda tun jiya y rigada y cire wanda suka kwanta akai y canja wani. Futa sukayi islam kuwa kokokari kawai takeyi wajen ganin ta daidaita tafiyarta saboda xafin da kasanta yakeyi mata Aslam kula da yayi da hakan cak y dagata sai da y kaita dai2 kofar dakin ma'u ya ajiyeta ita kuma ta shiga ta kirawo ta saboda xasu sauketa gdan su mommy saita dawo a exam su biya su daukota,a haka islam suka futa tana cijewa har suka shiga mota a hankali take goge kwallar da take xubo mata a kofar gdan mommy suka ajiye ma'u sukuma suka wuce dan saura 15 minutes ashiga exam din suna isa makarantar lokacin da Aslam y fito a mota nan fa kallo y koma kansa yan matan kowa yanaso yaga wa wannan hadadden gayen y kawo islam y budewa kofar motar tafuto wow kawai kowa yake cewa saboda ganin irin matching din da sukayi amma wadansu na tunanin wanta ne har cikin hall din eexam Aslam y raka Islam sannan y dawo cikinmota y xauna yana jira ta gama exam din tunda 1 xasuyi. *ina mika sakon godiya a gareki mmn zee saboda sakon gagaisuwarki y iso gareni ngd3 Allah yabar xumunci na sadaukar da wannan page din a gareki tare da huxaima da mmn habla* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *135-136* Mota Aslam y koma y xauna amma duka hankalin sa yana hall din da islam take exam wayarsa ce ta fara ringing dauka yayi ganin mai kiran nasa cikin sauri yayi picking Yace " _hello_" Safwan yace " _abokina yaka je gda?_" Aslam sai da yayi dariya yace " _lfy qlau abokina_" Safwan yace " _haka akeso cikin week dinnan inaso naxo kano saboda nayiwa daddy xancen khausar yace xai tuntubi daddyn kano yaji y xa'ayi neman auran_" Wata dariya Aslam y kara kyalkyale da ita, shi kanshi safwan mamakin yake yi domin bai san abokin shi da dariya haka ba yafi yawaita murmushi akan dariya Safwan yace " _abokina wannan dariyar fa tamkar wanda aka yiwa akbishir da gdan aljanna ko dannace xanyi aure shine abin dariya_" Sai da Aslam y karayin dariya harya kular da safwan sannan yace " _yau dinne sam bana iya controlling din kaina saboda sai yau na angwance gashi kaima naji kana shirin shiga daga ciki shiyasa nake tayaka farin ciki_" Dariya safwan yayi yace " _no wonder shiyasa naji kanata kyakyata dariya ba kakkautawa kace jiya ka shiga duniyar maji dadi?_ Aslam sai daya kwantar da kanshi a jikin seat din mota y wani lumshe ido yana hango daren jiya sannan yaja numfashi yace " _wlh abokina aure rahama ne da bansan abin haka yake ba sai jiya na tabbatar a gaskiya nasamu farin ciki a daren jiya wanda baxai iya misaltuwa ba kai abokina duk yadda xan fada maka baxaka gane ba kaima dai Allah y kaimu lokacin da xaka shiga daga ciki_" Cikin xakuwa da kalaman Aslam, safwan yace " _a gaskiya abokina ka tashi hankalina da kwadaituwa da aure ji nakeyi dama yau a kawo min khausar gdana yau nima nashiga duniyar maji dadinnan naji yadda akeji_" Dariya Aslam yayi yace " _lallai kai kafi kowa ko baka matar ba'ayi ba ballantana akai ga saka rana har kake tunanin aure to ka jira sai nan da my princess ta ajiyemin yaro 1 sannan xakayi aure_" Cikin jin haushin furucin Aslam safwan yace " _god forbid wlh bakin ka y sari danyen kashi lallai gayen nan ma baka da mutunci ni nayi ruwa da tsaki a aura maka mata amma ni yanxu ka dunga yimin wannan mugun bakin to insha Allah lokaci daya xamu ajiye babies_" Da sauri Aslam yace ' _dakata2 wannan ma sabo kakeyi kasan adadin lokacin dana dauka ina addu'a Allah yasa randa nacilla kwallo y shiga raga sannan yanxu ka fara wannan banxan furucinnaka to ka nemi ruwa ka kuskure baki saboda sabo kayi_" Dariya safwan yayi yace " _ashe ba dadi toni dai yanxu yaushe xaka dawo naji story_" Aslam yace " _tab xance ma kakeyi aini da dawowa photercort sai nan da 3 months saboda yanxu xan fara gwangwaje cin amarci na saboda karka manta satina 1 da aure muka tafi singapore to yanxu xan kira general na fada masa uxurina kafa nan da 3 months my princess ta gama exam saimu dawo tare dan yanxu nadaina nisa da ita kafata kafarta_" Dariya safwan yayi yace " _hakan yana da kyau abokina ayiwa kanwa ta dai a hankali kar a huce haushin tuxuranci akanta_" Dariya shima Aslam yayi hade da rejecting call din. Islam kuwa a hall din exam ma kawai rubutu takeyi saboda tsananin ciwon da kanta yakeyi mata ga wani xaxxafan xaxxabi daya rufeta lokaci 1 jikinta sai rawar dari yakeyi hawaye kuwa a fuskarta tamkar an bude fanfo yake shatata invigilator ne y kula da halin datake ciki kara sawa yayi kusa da ita yace yaya dai head girl ko bakyajin dadi ne kanta kawai ta daga masa dayake babbane lokaci 1 yaji tausayinta y kamashi yace ok kin gama exam din taki ne kanta nan ma ta daga saboda sam batajin xata iya magana duba agogonshi yayi yaga saura 20 minutes lokacin submitting yayi amma sai ya karbi pepper dinta yace ta tashi ta tafi mikewa tayi amma sai taci jiri y debeta da sauri ta koma ta xauna cikin kulawa y kalleta yace menene kuma cikin muryar kuka mai hade da shagwaba tace jiri nakeji inna tashi kallan sauran students yayi yace wayasan gdansu da sauri khausar da Amira suka mike sukace su 6*s dinta ne tambayarsu yayi yace sun gama tasu exam dinne eh suka amsa yace to suxo su taimaka mata sunemi napep su wuce gda godiya sukayi suka tattara pens dinsu suka je suka kamata suka fuce a hall din dakyar take takawa tana wani cije baki tausayinta ne y kamasu khausar sai sannu suke jera mata. Aslam da yake cikin mota idonshi a bakin hall nan yaga su khausar sun tattago islam da sauri y futo a motar har yana hadawa da gudu y karaso gurunsu yana tambayar meya faru da ita su khausar suka ce suma basu sani ba cak y dauki islam tana turjewa ina shi ko kula da students din da suke confound din skul din baiyi ba a front seat y ajiye ta su khausar suka shiga baya y figi motar ba karamin burge students din yayi ba saboda yadda y nuna kulawarsa akan islam duk kuwa daba susan shi menene dinta ba horn yayiwa gate man y bude musu gate suka fuce a 360. Direct asibiti y wuce da ita nan aka karbeta emergency tratement aka fara bata drip aka daura mata aka saka allurar bacci tuni bacci yayi awon gaba da ita su khausar Aslam y kalla y mika musu 1k yace su tari keke napep y kaisu gda saisu fadawa su mommy islam tana asibiti to sukace suka karbi kudin a hanya sai mamaki sukeyi to meya samu islam jiyannan fa suka rabu da ita lfyrta qlau. Suna xuwa gda nan suka fada islam bata da lfy kaka harda taka rawa wai kila tattaba kunne xata fara gani haka suka shirya suka tafi asibitin har lokacin islam na bacci lokacin da likita yaxo nan kaka take tambayarsa meyake damun jikar ta ko karuwa suka samu ne murmushi dr sameer yayi dan y gane Aslam ne mijin islam yace a'ah xaxxabine kawai da ciwon kai y boye musu dalilin ciwon nata ne saboda dama ba dole ne su sani ba,kallan Aslam yayi yace y sameshi a office xasuyi magana toh Aslam yace dr sameer na futa Aslam y bishi. Xaune Aslam yake gaban dr sameer yana jiran yaji mai xaice masa, kallan sa dr sameer yayi bayan y xare medical glass dinsa yace abokina na dade da sanin islam tun lokacin da xata fara menses dinta nine likitan dana kula da ita a lokacin a gaskiya abokina ka shiga yarinyar nan da yawa amma naji dadi sosai da baka samu damar samun taba tun tana yarinya sai data kara kwari shawarar da xan baka yanxu shine koda mun sallameta dan Allah ka daure ka daga mata kafa nan da 2 weeks kafin ka kara nemanta saboda ina tunanin kaji mata ciwo sosai tundaga yanayin yadda take tafiya da kuma xaxxabin daya rufeta lokaci guda in kuwa kace xaka kara ina tabbatar maka da xata fara tsoronka kuma duk lokacin da xaka jemata baxata saki jikinta harka samu yadda kake soba ina fatan xaka dauki shawara ta. Aslam da kanshi yake sunkuye saboda kunya tun lokacin da dr sameer y fara jawabinsa a ransa yace dr baxaka gane bane nayi hakuri hade da juriya kusan 5 years ina fama da matsananciyar sha'awa ai dole yanxu dana samu abinci nayi masa cin koshi sai da dr y dan bugi table din gabansa sannan Aslam y dago kansa firgigit hade da shafa keya yace ngd dr insha Allah xanyi amfani da shawarar daka bani. Mikawa dr hannu yayi sukayi musabaha sannan y futa lokacin daya koma dakin islam ta tashi nan fa y fara tattalinta ko kunyar su mommy bayaji motsi kadan yace my princess me kikeso, ita kuwa sai shagwaba takeyi to dama mai neman kuka neaka jefeshi da kashin awaki lokacin dasu mommy xasu tafi akace kaka ta xauna furr Aslam y shafawa idanuwansa toka yace shine xaiyi jinyar matarsa haka suka tafi suka bashshi kaka tana ta sababi Aslam yace eh naji kidai tafi ni xanyi jinyar matata dariya mommy da aunty amarya sukayi. Aslam da kanshi y kira Amira a waya yace taje gda ta kwaso musu kaya sannan y shiga bathroom y hadawa islam ruwa mai xafi yaso yayi mata wankan ma taki sai dayaga tana shirin yin kuka sannan y hakura yana my princess ki gasa jikin ki sosai kinji hade da kashe mata ido 1 ruwa ta diba ta watsa masa y fuce yana dariya. Tsawon 3 days Aslam y dauka yana jinyar Islam wata irin muguwar soyayya yake nuna mata inda komai shi yake mata hatta brush in xatayi shine yake matsa mata maclean wata irin muguwar shakuwa ce ta shiga tsakaninsu inda dr sameer har tsokanarsu yakeyi ai sune ma romioe da Juliet mommy kuwa daina xuwa asibitin ma tayi saboda yadda Aslam yake bata kunya haka kaka duk randa taxo sai sunyi fada wai irin sangartar da yake yiwa islam tayi yawa yace eh kema kaka kikayi mata ballantana ni mijinta islam kuwa wani mugun son Aslam ne yake shigarta yadda ko wanne bugun numfashi nata soyayyarsa daduwa takeyi a ranta. *sakon gaisuwa a gareku rufa'atu,badiyya xaria,billy tabacco & zee yabo nasadaukar da page dinnan a gareku ngd da yabawarku a gareni Allah yabar xumunci* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *137-138* Yau islam kwananta 3 a asibiti ta ware sosai dan ma sama bata shan magani, dr sameer ne y shigo bayan duba islam da yayi y rubutawa mata sallama bayan dada jan kunnan Aslam da yayi, kaka kuwa cewa tayi taji dadi dama tagaji da ganin rashin kunyar dasu Aslam sukeyi islam kuwa itace mai cewa dama waye y kawota asibitin dukan wasa kaka takaiwa islam tace yau naji ja'irar kaya waini xata yiwa iyayi Aslam ne y tare dukan ta same shi yace to wai ke tsohuwar nan ina ruwanki ne xaki saka mana ido a rayuwarmu ke wayasan irin soyayyar da kika nunawa tsohon mijinki haka suka bar asibitin cikin farin ciki da raha dr sameer kuwa ji yayi family din sun burgeshi saboda yadda suke da wasa da dariya. Suna xuwa gda furr islam taki shiga dakin ta wai kada taga mage Aslam yanaso y fada mata shine y saka mata mage amma yana tsoron karya ballo ruwa dan yasan tsaf xata manta da shirin da sukeyi ta fara masa rashin mutunci domin ba abu mai wuya bane a gare ta ta botsare masa. Xaune suke akan bed din Aslam kan islam nakan cinyar shi yana shafa mata cikin gashin ta tashi tayi tana hero bari naje nayi wanka cikin tsokana yace baxaki tsaya nayi miki ba kokin manta randa kika dinga ihun su kaka su kawo miki dauki nice nayi miki wankan y karashe maganar da tuntsirewa da dariya cikin jin haushin furucinsa ta dauki pillow daya tahau dukan shi tana Allah banaso ai dama kana sane kayimin da xafi saboda nayi ihu ka dinga tsokana ta taci gaba da dukan shi da pillow tana tura baki gaba Aslam kuwa dariya yakeyi yana tareta da hannunsa kamata yayi y hadeta da girjinsa y rungumeta tsam yana sakin sassanyar ajiyar axuciya a hankali y fara rada mata dadadan kalamai hade da jaddada masa godiyarta na kawo masa budurcinta da tayi luf tayi a kirjinsa tana jin wani sanyin dadi a ranta hade da soyayyar mijinta da take malala acikin ranta a hankali ta xame jikinta daga nasa tashiga bathroom batafi 3 minutes da shiga ba Aslam ma y shigo daure da towel kallansa tayi tana kokarin daukar towel dinta ta daura da sauri y rigata daukan towel din yana jifanta da wani kallo yace Allah koki tsaya muyi wankannan tare ko kuma na maimaita irinna ranar nan xumbura bakinta gaba tayi tana Allah Allah Allah hero banason hak......bata karasa maganar tata ba taji bakinta cikinnasa kissing dinta yakeyi sosai islam jin da tayi Aslam nashirin xarmewa shine y sakata kwace jikinta a wahale haka dai sukayi wankan suka futo fuskar kowa dauke da annuri dan ba Aslam kadai bane yakejin dadin rayuwar da sukeyi yanxu ba har uwar gayyar watako islam,bayan sun shirya Aslam da kanshi y tafi dakin islam ya ciko mata katuwar trolly bag da kayanta sannan y rufo dakin y kawo mata nasa dakin. Rayuwa suke gudanarwa mai wuyar fisaltuwa a karan kanta islam wani lokacin tana mamakin Aslam dan gani takeyi tamkar ba Aslam din data sani bane wanine nadaban domin koda yaushe suna tare in tana kitchen yana biye da ita in tana palo kuwa tofa a jikinsa zatayi masauki dan ma'u ma a gdan mommy suka barta a jewar Aslam saiya tafi sannan xata dawo. Skul ma shine yake kaita y dauko ta rannan dai class mate din Islam suka tuketa akan saita fada musu wannan guy din menene dinta gajiya tayi da tambayar da sukeyi mata koda yaushe tace mijinta ne da mamaki suke kallanta wai yaushe akayi bikinta basu sani ba tace tun suna j.s 3. Haka rayuwar su taci gaba da tafiya duk da Aslam yana kokari wajen ganin y danne sha'awarsa dan yabi shawarar dr akan abinda yace amma ina yau dai kasawa yayi kwance suke akan gado islam tana kwance a kan kirjinshi tana shafa masa kirjinnasa tace yauwa hero dama inaso in tambaye idanuwansa da suke lumshe yace ina jinki my princess sai data gyara kwanciyarta ta kara makarkale Aslam tamkar Xa'a kwace mata shi sannan tace hero a ina budurwar taka take ne? da mamaki y maimaita budurwa kuma tace eh wadda kace xaka aura nan da 4 months kuma naga ba'aje nemar maka aurannata ba naga anci kusan 1 month murmushi yayi danshi harga Allah y manta da maganar nan yace to ai budurwar tawa tana tare dani dan yanxu haka an dade da mana aure kila ma maganar da nakeyi miki tana dauke da baby na a cikinta xabura tayi ta mike tuni hawaye y fara ambaliya a kan fuskarta tace yanxu hero dama xaka iyacin amana ta harkayi aure ban sani ba a gaskiya ka cuceni gashi yanxu ka rabani da martaba ta koda yanxu natashi hankali na nace saika sakeni to mijin da xan aura baxai taba sona ba ta wani barke da wani gunjin kuka,aslam kuwa kallanta y tsayayi yasan ko islam bata fada ba y hango kishinsa a idanuwanta wannan na nuni kenan da itama ta fada tarkon sonshi cikin jin dadi y tashi y janyota jikin shi y rungume yace waya fada miki xan iyacin amanarki ai ba kowa bace matar da nake cemiki xan aura ba illah kedai saboda akwai time din danaji kina waya kina baxaki bani hakkina ba sai kiyi candy shine na duba lokacin naga sai 4 months yayi sannan xakiyi candy shiyasa nikuma nayi miki hikima dannayi tunanin xaki tsorata xuwa lokacin ki bani hakkina in kinji xanyi aure amma wlh ba wata mace da naji ina so a duk duniyar nan daya wuce ke cikin jin dadin furucinsa hade da wata muguwar kunya data rufeta ta rungumeshi hade da kai masa peak a kumatu tace *I LUV U MY HERO* cikin mamaki y kalleta hade da waro idanu yace me kika ce sake fada xumbura bakinta tayi hade da rufe fuskarta tana Allah hero kayita bani kunya wani mugun hug y bata hade da aika mata da wasu xafafan kisses tuni y fara lashe mata hawayen fuskarta ai islam ma warewa tayi ta fara aika masa da nata sakonnin damin ta tatabbatada yanxu ta kamu dason mijinta ai rikicewa Aslam yayi dan bai taba tunanin islam xatayi saurin bada kai ba daganan y fara sarrafa ta yadda yakeso bayan komai y wakana islam taji sam bataji wani xafi sosai ba sai dai wanda baxa'a rasa ba tun a daren sukayi wanka suka tsarkake kansu. Nan fa rarayuwar masoyan ta fara tafiya yadda sukeso dan kullum Aslam sai y samu abinda yake so a gurin islam wani lokacin ma sau 2 ko 3 a rana tun tana jin dan xafi harta daina sai dadi,lokaci guda sukayi wani mugun kyau ga wani ffari da suka karayi Aslam harda wata yar kiba yayi. *A GURGUJE* Islam ce xaune dasu khausar a class sun samu interval sai after 1 hour xasu shiga wata exam din awara ce a gabanta saicin kayarta takeyi tana dangwala yaji khausar ce ta xunguri Amira tace anya sis bamu kusa xama mama ba kuwa Amira ce tace nima ina tunanin hakan kodan yadda naga wata acikin mu tana dada fresh ga wani salon kadayi data bullo dashi yau itace cin awara gobe wainar fulawa jibi dan subul gata dan malele kai koda yaushe dai da sabon kwadayi take xuwa lokaci 1 suka sheke da dariya banxa islam tayi musu dan tasan da ita suke ita kanta tana mamakin kanta canjin data samu koda yaushe cikin cin abin kwadayi take kuma bata dadewa da gamaci xataji wata yunwar ta kamata haka suka shiga hall din exam tana cin gyada mai gishiri bayan sun gama exam din sun futo Aslam ne yaxo daukarta,tuki yakeyi hankalinsa kwance mai agwaluma ta gani cikin sauri tace dan Allah hero tsaya saboda tana toxali da agwalumar taji yawun ta yayi wani mugun tsinkewa birki yaja y tsaya marairaicewa tayi tace plz agwaluma xan sha murmushi yayi y balle murfin mota y futa y siyo mata cikin bakar leda y dawo ai jikinta har rawa yakeyi dan ganin tasha agwalumar nan ko tunanin wankewa batayi ba ta fara aunawa cikinta agwalumar har wani lumshe idanu takeyi wai dadi. Suna xuwa gda bayan ta huta tayi wanka futowa tashiga kitchen jellop din taliya tayi da xallan attaruhu da albasa wadda taji daddawa da bushashshen kifi bayan ta gama haka ta jjuyo duka a try ta futo dashi a table mat ta shimfida musu itada Aslam tace hero xomuci abinci haka yasa hannu sukaci duk da akwai yaji haka y daure dan yanxu irin abincin da takeyi musu kenan harda taliya da mai da yaji ta yanka cabbage salad tumatur albasa cocumber ta dafa kwai ta marmasa musu kifi a haka kuma yake ci dan yasan ajiyar sace ta fara aiki, kallan Aslam tayi tace hero wai cikine dani murmushi yayi yace wanene y fada miki yatsina fuska tayi tace makaryatannan mana su khausar wai kwadayi na yayi yawa cikine dani dariya yayi yace karya sukeyi kokin yadda da sauri ta girgixa kanta tace a'ah wlh nasan bani da ciki tace tab kasan haihuwa da wahala kuwa murmushi yayi yace ai ke baxaki wahala ba kina bacci xaki tashi kiga danki ko yarki dariya tayi tace Allah yasa mamakin shirmen islam yake bawa islam watako ita bata lura tana da ciki ba sai wasu ne suka kular mata. Daddyn safwan yaxo kano shida daddy da Abba sunje gdan su khausar sun naimawa safwan auran khausar an saka bayan candyn su da wata 3 bikin yayi dai2 dana Amir da Amira dan suma haka aka saka y xama lokac kenan xa'ayi. *sakon gaisuwa a gareku shafa'atu umar,sa'adatu usman & hibbancy na sadaukar da page dinnan a gareku Allah yabar xumunci ameen da wannan nakeson sanar da masoyan goyon kaka insha Allah saura 1 to 2 pages nagama goyon kaka* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *139-140* Kwanci tashi asarar mai rai su islam saura paper 3 suyi candy Aslam y buga musu jaka memo key holder Amir da safwan ma ba'a barsu a baya ba domin suma sunyi rawar gani sunyi musu calanders da jaka sannan Aslam y hada musu waleema sai hada2 candy akeyi. Islam kuwa hannunta y fara kwari domin a xaman da sukayi da Aslam kullum suna futa yana koya mata mota amma dai har yanxu bata fara hawa babban titi ba sannan a tattare da ita tana ganin sauyi domin tayi wani irin mugun haske dau sannan breast dinta sun cicciko domin inta saka rigunanta dakyar take matse zip amma saita danganta hakan da kiba tayi,sannan a bangaren auratayya Aslam nasamun abinda yakeso sosai dan ko bai nemi islam ba tofa da kanta take xuwa domin cikin wata irin jaraba y saka mata ko kadan bata gajiya da Aslam shikuwa gogannaku ai gaba ta kaishi watako gobarar titi a jos. Kwance Aslam da islam suke akan gado islam tayi matashi da kirjin Aslam tace hero nifa ina ganin canji sosai a jikina bakaga yadda nake cika sosai bane sannan kuma sai tayi shiru murmushi Aslam yayi yace sannan kuma me uhm uhm tace ta kara shiru dariya yayi yace sannan koda yaushe cikin son dumin mijinki kikeyi ko dariya ta kyalkyale da ita ta kifa fuskarta a kirjinshi cakulkulu y fara mata daganan xancen y canja suka fada duniyar maji dadi. Yau su islam xasuyi candy wanda yayi dai2 da cikinta watanshi 2 da sati 2 amma saboda tsabar shirme da shiririta irin ta islam wai batasan tana da ciki ba tun asuba data tashi bata koma bacci ba kunun gyada tayi musu da yam balls ita kuma tayi dan wake komawa daki tayi wanka ta shirya Aslam duk yana kwance yana bacci kanshi ta tafi ta fara tashin shi cikin shagwaba hero3 cikin bacci y bude idonsa yana kallanta kasa2 yace y akayine my princess kin katsemin baccina ina mafarki kin haifamin babies masu kyau kamar ke xumbura bakinta gaba tayi tace nidai Allah2 hero banaso nace maka ni ba yanxu xan haihu ba amma kullum maganarka daya ina da ciki xan haifa maka baby to Allah tsaya kaji indai kamin ciki yanxu to Allah kayanka xaka karba baxan haifar maka ba nasha wuya ta karashe maganar da murguda baki murmushi yayi domin y kula babynnan nashi har shagwaba da rashin kunya y sakawa princess dinshi yace to naji amma kiyadda xaki rainar minshi a jikin ki tunda ai kinga maxa basa yawo da ciki ranar da xaki haifeshi saina karba ko daga kanta tayi alamar tunani can kuma ta kalleshi tace tab Allah kai xaka raini abinka ai ina ganin maxa da katon ciki murmushi yayi yace princess rigima to ai wancan katan cikin da kike gani bana haihuwa bane kune kukeyin na haihuwa mukuma saimu karba in ranar haihuwa tayi dariya tayi tace tab ai harna hango idon hero a matsula shima dariyar yayi yace ai babu wahala fa kallanshi tayi tace Allah kansa y gyada masa yana eh indai xaki yadda kiyimin renon babyn acikin ki nikuma nayadda xan haifeshi sannan nayi rainonsa bayan yaxo duniya wani kada idanuwanta tayi tace toh ka kyaleni xanyi tunani toh yace yana tashi y shiga bathroom danyin wanka. Bayan y futo y shirya suka futa sukayi break fast Aslam dai kallan islam kawai yakeyi ganin yadda take cika yaji a danwaken nata ga tumatir da albasa da cabbage duk ta saka hakura yayi dacin yam balls din shima yaci dan waken bayan sun gama y dauketa y kaita skul 3 hours suka dauka suka futo dayake paper 1 xasuyi kuma hausa daganan aka futo anata celebrating din candy sai 2:00pm Aslam y koma makarantar y daukota sun raba invitation card na waleemar da zasuyi,islam ce ta dinga hada Aslam da Allah akan y bata tayi driving dunsu haka kuwa y bata su khausar suna dari2 suka shiga wai karta kifar dasu nidai danasan rai 1 gareni kin shiga nayi natari keke napep nabi bayansu . Sai da suka je suka sauke su khausar suma suka yada xango a gdan sai bayan sallar isha'i suka tafi kaka sai nan2 takeyi da islam kula da tayi tana dauke da ciki su mommy ma ba'a bassu a baya ba wajen kulawa da yar tasu mai gayya mai aikin kuwa batasan wainar da ake toyawa ba. Yaune walimar su islam sanye suke da wani tsadadden lace maroon colour mai stones sai kyalkyali yakeyi fuskarsu tasha makeup kamar ka sacesu ka gudu, Aslam safwan Amir kuma sanye suke cikin ash din shadda sai hula dara ja da suka saka anyi walima ta kayatar anci ansha sai dai fatan Allah sa ilimin y amfanesu. Yaufa ake yinta cikin islam yakai 4 months yau tashiga wanka taga cikinta y kunburo a guje ta futo daga bathroom din tana kwalawa Aslam kira hero3 hawaye ne shabe2 a fuskarta wani yana bin wani cikin tashin hankali yake tambayar ta meyake faruwa saida ta tsaida kukanta kadan tace ai bafada maka kada kamin ciki kada kamin ciki kaki ji to gashinan yanxu naje wanka kawai naga cikina y kara girma bara ka gani ta yaye towel din hade da barkewa da kuka wata muguwar dariya ce ta kama Aslam amma y danne dan yasan yanayin dariyar nan xai ballo ruwa marairaicewa yayi hade da rungumota y fara buga bayanta yana rada mata magana a hankali yace kiyi hakurin princess nima bada sani na nayi miki ciki ba da nasan yadda xanyi da baxan bari kiyi ciki ba, amma kiyi shiru kije kiyi wankan kixo muje asibiti sai dr y tabbatar mana in cikinne sannan y fada mana yadda xamuyi hawayen fuskarta ta goge tana Allah2 in cikinne sai dai ka karbi kayanka ta shige bathroom ai tun a gurin Aslam y fada kan gado y fara kyalkyala dariya harda fadowa kasa yana rike ciki yace lallai princess rigima tasan taxo shimfidar miji amma kuma tayi ciki tace zata yiwa mutane rigima bari bafara kiran dr safwan naji y xa'ayi dialing number din dr safwan y fara ringing 2 y daga Aslam yace " _hello likita bokan turai_" Daga can sai da sameer yayi dariya sannan yace " _na'am soja maxan fama sha gwagwarmaya y amarya_" Aslam shima dariya yayi yace " _tana lfy y madam da baby?_" Sameer yace " _duk Lfyrsu qlau_" Aslam yace " _dr wani favour nake nema a gurinka_" Sameer yace " _Allah yasa xan iya_" Sai da Aslam yayi murmushi sannan yace " _xaka iya mana wlh princess ce ta tada daru akan tana da ciki wai ita bata yadda ba sai dai na karbi cikina nayi renonsa kuma ina tunanin cikin yayi kwari yanxu_" Sai da sameer yayi dariya yace " _lallai kan taxo da daru to yaya kukayi da ita tunda batasan tana da cikin ba sai yanxu da yayi kwari_" Aslam yace " _ai baxata gane ba kasan akwai kuruciya a tattare da ita sannan bata amai ko xaxxabi kawai sai dan karan kwadayi yanxu haka nace mata ta yadda tamin rainon cikin in ranar haihuwa taxo xan karbi kayana_" Sai da dr sameer yayi dariya yace " _lallai kaxo da dabara watako ranar haihuwa ai dole ta haife maka abinda ka dura mata_" Dariya Aslam yayi yace " _eh mana nidai kawai alfarmar da xakamin shine ka nuna mata matane ke rainon ciki amma haihuwa maxa suna iyayi kaga daganan xataci gaba dakular min da baby na har xuwa ranar da xata haifemin shi da yardar Allah_" Dr sameer yace " _to shikenan sai kunxo_ suka katse layin Islam ce ta futo a bathroom sai wani kumbure 2 takeyi Aslam kuwa danne dariya kawai yakeyi haka ta shirya mai da powder kawai ta shafa sai kwalli ta xura wata arebian gown pink ta yafa mayafinta suka futa, direct asibitin dr sameer suka wuce bayan gaishe2 dadan wasanni da suka sasabayi anan yasaka akayiwa islam pregnant text nan result y futo tana dauke da ciki 4 months 2 weeks kuka tahau yimusu wiwi ita sam bata yadda ba yama xa'ayi karamarta da ita ace wai xata haihu salon ta mutu ai sai dai AslaAslam ita kawai acire cikin ajikinta a sakawa Aslam bataso dr sameer ne y kalleta yace ke yanxu bakyaso ki haifi yara suna kiranki mama cikin jin kunya tace inaso dariya yayi yace to ki daina cewa acire miki asawa oga kinga kece mace kuma matane suke rainon ciki in kin haihu sai oga yaci gaba da raino kinji kanta ta gyada tana dariya kasa2 hangota kawai takeyi dauke da baby kuma wai natane na kanta kallanta yayi yace promise kanta ta dada gyadawa yace a'ah magana xakiyi saboda inaso kiyi magana da bakinki domin kinsan darajar alkawari murmushi tayi har dimple dinta suka lotsa tace i promise dariya yayi yace yauwa islam y kalli Aslam yace rigima ta kare ta yadda xatayi maka rainon cikinka sannan ta haifa maka daganan kai kuma kaci gaba daganan toh Aslam yace hade da godiya suka tashi har mota dr sameer yayi musu rakiya. *_kuyi hakuri naso nayi muku typing yafi haka wayata ta fara hooking dawannan nakeson mika gaisuwa a gareku fauxalo, zainab yusuf ramlatu idris & mmn shukura ina gaisheku ina kaunarku gaba daya masoyan ```goyon kaka```a duk inda kuke a duniya Allah yabar kauna ameen ngd,wannan page din sadaukarwa ne a gareku_* Taku har kullum *sisin mama* *mrs hamisu taura* *GOYON KAKA* *141-142* Lokacin da suka koma gda a palo suka yada xango a three seater islam ta xauna ta mike kafafu Aslam kuwa yasa hannu y fara daddanna mata kafafu dadin tausar da yakeyi mata shine y saka bacci y kwasheta kura mata idanuwa Aslam yayi yanajin wani mugun son islam acikin ransa a hankali rayuwarsu tada ta fara dawo masa irin rikici da artabu da sukayi murmushi kawai yayi yace princess rigima inason jarumtar nan taki Allah y barmu tare shima y kwantar da kansa akan kujerar bacci y suresa. Yau Aslam xai koma bakin aikinsa dan hutun da aka dibar masa nacin amarci y cika sun shirya tsaf danshi da princess dinshi xasu tafi dan yace kafarsa kafarta baxai kara barinta a kano ba tunda tayi candy haka sukaje gdan su mommy sukayi sallama dasu daganan Amir,Amira da khausar sukayi musu rakiya xuwa airport suka hau jirgi y daga dasu photercort. Bayan sun sauka safwan ne yaje y dauko su nan fa y tuke Aslam yana masa tsiya dariya Aslam yayi yace wlh ka dinga girmama ni domin nan da 5 months insha Allah ni baba ne islam ce ta xungure shi hade da tura baki gaba tace Allah hero ka bari banaso ko kuma ka karbi kayanka dariya yayi kasa2 yace sorry my princess abokin nawa ne y kasa gane na girma dariya safwan y kyalkyale da ita yace kaga baban twice & mmn twice a tare suka kyalkyale da dariya haka suka karasa gda suna barkwanci. A photercort rayuwa sukeyi mai dadi domin islam wannan karan shine xuwanta na farko photercort wanda suke shiri da Aslam shiyasa takejin xuwan yafi mata duk wanda tayi a baya bangaren soyayya kuwa ji sukeyi tamkar xasu cinye junansu dan wani mugun tattali sukewa junansu tare da lallabawa ko kadan islam batason abinda xai batawa hero dinta rai ta bangaren Aslam din ma haka domin sam idanuwansa basa kallar masa ko wacce mace sai princess dinsa. Haka islam taci gaba da rainon cikinta har yakai 5 months nan fa y fara girma tamkar ana hura balon wataran in taji y mata kabebe y hanata sukuni saita sakawa Aslam kuka wai ita ta ajiye alkawarin wlh y karbi kayansa sai yayi mata dabara hade da wayo y samu tsimmokara y cika a cikin shi yana kwaikwayon ta sannan kuma xata koma dariya, haka kuma duk lokacin daya samu sarari a office ko week end haka xai dauketa sufita xagaya gari basu xasu dawo ba sai dare daganan kuma suyi wanka suci abinci y matsa mata jikinta suyi bacci. Cikin islam nada 6 months ta dada kiba da cika gashi majority kayan da take sawa sunyi mata kadan gashi suna shirye2 tafiya kano bikinsu amira wanda xa'ayi upper week xaune take ta tasa dan silif a gabanta ga kuma katon cikinta da shima yayi nasa xaman a gabanta tanacin dan silif data saka tumatur da albasa kallan Aslam tayi tace gaskiya hero kayimin wayo yanxu in mukaje kano suka ga katon cikinnan ai kunya xanji, murmushi yayi yace menene na kunya bayan cikin sunna ne ajikin ki, rau2 tayi da ido alamar son kuka tace to yanxu kowa kuma inya ganni yasan ta yadda akayi na samu ciki ko kawai sai tahau kuka,ai dariya da Aslam yakeson rikewa kasawa yayi kawai y tuntsire da dariya ba kakkautawa islam ganin haka ganin haka tace me kuwa xatayi inba kuka ba,kuka tahau yi sosai harda turturxa kafafu wa irinna yara tana wlh nafasa maka rainon cikinnaka ka kaini asibiti a cire a saka maka kayan ka kuka takeyi sosai tamkar ba gobe Aslam ganin haka da sauri y hadiye dariyarsa y taso yaxo y rungumeta ta baya yace haba my princess y xaki wahalar da kanki sannan ki wahalar mana da babyn mu banxa tayi masa kamar batasan me yake cewa ba takara volume din kukanta iska y fara hura mata a kunne hade da shafa mata baya a hankali ta fara sauke ajiyar xuciya sai da Aslam yaga islam tayi shiru sannan y daga ta suka koma kan kujera suka xauna yace haba princess ke bakya gajiya da kuka ne koda yaushe kamar wata karamar yarinya anayin magana kadan ki bare baki kihauyin kuka kokin manta kin kusa xama mommy ne sai data goge hawayen fuskarta da hannunta tace to ai kaine ka sakani nayi maka magana inaso ka samomin solution amma kawai sai kahau kuka murmushi yayi a ransa yace princess rigima wanne solution xan nemar miki bayan kin rigada kinyi ciki sabanin haka a fili sai yace to shikenan duk wanda xaiyi miki magana kice a ruwa kika sha tunda ai ana shan ciki a ruwa ko baki sani ba kanta ta gyada masa alamar bata sani ba yace toh shikenan daga yau ki sani ana shan ciki a ruwa kinji murmushi tayi alamar jin dadi tace Allah hero hancinta y lakace yace kujimin mara kunya kin iya xuwa ki tasani a gaba saina baki xumata amma yanxu kin samu gud result daga gareni kice xakiyi min iyayi dariya tayi ta rufe fuskarta a kirjinshi domin ita kanta tasan mijinta jarumi ne yasan kalolin salon dda xaiyi amfani dasu ganin y samu abinda yakeso a wajenta cikin sauki domin duk da girman cikinnan nata baya hanata bashi hakkinsa domin itama koda yaushe cikin bukatarsa take. Yau suka tafi kano domin saura 3 days a fara bikinsu Amira bayan sunje nan fa su khausar suka tasata a gaba sunayi mata shakiyanci wai ita mai cewa baxata bawa Aslam kanta ba saitayi candy ai yanxu sunga candy tunda gadan baba nan y tona asirin da take boyewa dama sunsan cika bakine ta dade da mallakawa Aslam kanta ta rufesu bai2 banxa tayi dasu sai data ga sun fara isarta sannan ta fara mayar musu da martani ta wajen cewa eh din ai dadinta mijinta ne kuma masoyinta shewa suka saka sukace yau kuma keda kika ce baxaki tabasan hero ba ganin suna shirin kure ta shine y sakata tashi a kufule tabar musu dakin ta tafi gurin kaka tana mata korafi wai su Amira suna yi mata dariya dan tana da ciki, nan fa kaka ta mike ta futo ta samu su Amira ta farayi musu fada domin sun taba yar lelenta dakyar suka samu kaka ta kyalesu. Wani tashin hankalin islam lokacin dasu khausar suka kawo mata ankonta nanfa tayi2 ta gwada amma ina duk sukaki shigarta ihu tahau yi su Amira kuwa suka ce me xasuyi inba dariya ba ganin kukannata bamai karewa bane shine saka su kiran Aslam ba shiri y taho y ratsa cikin matannan jin princess dunshi wai tana kuka bayan yaje y tambaya meya faru anan suka fada masa dalilin kukan ta a mota y dauketa suka tafi kasuwa suka siyo exactly irin angon y wuce da ita gurin tela a take aka gwadata a lace din dinner akayi mata buba a atamfar kamu data yini da material din dinner photercort akayi mata dogayen riguna telan yace xuwa dare su dawo sai lokacin ta saki ranta ta fara fara'arta. YaYaune kamu amare sunyi kyau sunsha makeup islam kuwa duk da bawani makeup tayi ba amma tayi kyau sosai anyi kamu lfy an gama lfy,yau juma'a bayan idar da sallah a masallaci dubunnan mutane suka shaida daurin auren Abdul-qadeer Aliyu Umar (Ameer) & Zainab Abdul-qadeer Umar da kuma safwan Abbakar sadeeq & Khausar yusuf nadabo akan sadaki 50k daganan angwaye suka wuce reception. 8:00pm aka fara shirin tafiya dinner yau dai islam ta tsaya ta tsantsara makeup sosai tayi kyau Aslam ma y saka m ilk din shadda gixna sai y saka brown hula xanna bukar hade da takalmi mai ddan yatsa brown sai agogon fata na gucci shima brown ba karamin kyau sukayi ba inda amare da angwaye ma sun hade cikin hadaddun kayansu bakaramin kyau sukayi ba islam da Aslam sune a hight table islam sai nan2 take da hero dinta ganin yan mata nakawo masa farmaki 10:30pm aka tashi a dinner din anci ansha anyi raba kayayyaki kama dasu kalandu memo key holder harda t shirt Aslam da islam sunyi rawar gani abikin sunyi barin naira sai dai fatan Allah y bada xaman lfy. Washe gari akayi wuni shima y kayatar anci ansha anyi rabon tobobi manya manya,washe gari mutane basufi 20 ba suka tafi photercort kai khausar tasha kukan rabuwa da mammy da yaya sagir a tafiyar harda Amira saboda akwai dinner din da xa'ayi acan gdanta na cikin gdansusagir aka ware mata part an xuba kayan more rayuwa sosai gdanta yayi sai dai sam barka da fatan Allah y basu xaman lfy sannan an xuba mata wasu kayan a gdanta na barrack saboda acanne safwan yake aiki inda take makotaka da islam. 8:00pm aka fara tafiya dinner din itama tayi kyau ta kayatar inda sosojoji da matayensu suka je harda Amir da Amira sai 12:00am sannan aka tashi a dinner din. Washe gari tun 8:00am yan rakiyar amarya suka fara shirin dawowa kanon dabo suka bar amarya a gdanta dadinta 1 an barmata islam a ranar kuma aka kai Amira itama gdanta dayake kusa da gdan islam na kano to mudai sai dai muyi fatan Allah y bawa amare xaman lfy da kwanciyar hankali a gdajensu. *GOYON KAKA* *143-144* Bayan bikin su Amira da sati 2 Aslam su Aslam sunje asibiti akayiwa Islam scanning anan aka gane twice ne acikinta kuma duk mata xo kuga dadi agurin islam har wani iyayi takeyi wai xata haifi yaran da xata koyi kitso a kansu Aslam kuwa sai dariya yake mata yana ita da tace batason babyn cikin masifa tace to yanxu inaso tunda matane da xa'ayi musu kwalliya 3 days letter Aslam y dauki Islam suka tafi dubai siyo kayan jarirai kaya suka siyo sosai acan satinsu 2 suka dawo inda cikin islam yake da 8 months nan fa ta xama, xama dakyar tashi da kyar dan dole Aslam y dauketa y kaita kano saboda yadda mommy ta dameshi da waya akan y dawo mata da daughter dinta haka y kaita badan yanaso ba amma duk sati yana hanyar xuwa kano cikin wannan halin cikin islam y cika 9 months nan fa aka fara tunanin haihuwa domin yau ko gobe ake saka ranta. Yau ta kama friday tun asuba islam takejinta wani iri amma take daurewa haka dai tayi sallah a xaune kaka tana kula da canjawar da islam tayi amma data tambaye ta sai cewa tayi bakomai can dai xuwa 7:00am ciwo yayi tsanani ta fara ciwon mara hade da ciwon baya ranga2 aka dauketa aka kaita asibiti Aslam yau tunda y tashi da asuba yake neman layin princess dinshi amma baya shiga kawai jikinsa ne y basa babu lfy 7:00am y hawo flight y kawo shi kano yana xuwa gda akace an kai islam asibiti haihuwa cikin tashin hankali y tafi asibitin lokacin dayaje an shigar da ita labour room duk yadda yaso a barshi y shiga sam nurses din suka hanashi ba karamin tashin hankali y shiga ba saboda jiyo ihun princess dinshi dayake yi gaba daya ma y rasa yadda xaiyi addu'a kuwa yana fara wannan kafin yakai karshe y kamo wata sam y kasa xama sai xirya yakeyi tsakanin kofar labour room xuwa gurin su mommy, har 9:30am islam bata haihu ba amma fa tasha bakar wuya ihu kuwa da kiran sunan hero y kawo mata dauki harta gaji daddy da Abba ne suka xo da rubutu a hannunsu akan a bawa islam addu'a ce suka karbo Aslam ne y karba y tafi kai mata nan fa nurses sukaso hanashi ganin da yayi xasu bata masa lokaci shine y sakashi bangajesu y shige dakin kwane kan gado y tarar da princess dinshi ganin shi da tayi nan fa ta barke da wani sabon kukan lallashinta y farayi a hankali y dago kanta saboda wani mugun tausayinta da yakeji y fara bata rubutun tana gama sha nakuda ta taho gadan2 ihu takeyi tana kankameshi ai shima tuni y kankameta yana kuka wiwi tamkar karamin yaro lokaci guda ta saki nishi tare da wata kara inda yayi dai2 da fadowar katotuwar jaririya minti 5 tsakani wani babyn y kara tahowa wannan karan harda cixo da yakushin Aslam tayi sannan tayi nishi wata babyn ta fado wani luf islam tayi ajikin Aslam tamkar ancire mata kaya nan nurses din suka debi yaran suka tafi gyarasu dakyar suka futar da Aslam a dakin domin xasu gyara islam saboda harda dinki xasuyi mata danta karu cikin farin ciki y futa ganin princess dinshi ta sauka lfy bawani sauran wahala bakinnan nashi a washe y futa yanawa su kaka albishir din islam ta haihu yan 2 murna suka farayi suna islam dinfa yace itama lfyrta qlau lokacin yayi dai2 da karasowar su Amir rungumeshi Aslam yayi yana fada masa islam ta haifi twice harda kwallarshi murna suka dingayi sosai. Ana haka aka garo islam akan gado tana bacci Xa'a kaita dakin hutu nurses din kuma rike da babies din da farin ciki suka karaso rige2 dauka su mommy sukeyi nan suka kasa banbance kamannin twice din dan komai nasu iri daya ne haka suka dinga daukarsu suna yabawa da kyawunsu sunata masha Allah,Aslam kuwa bakinsa y kasa rufuwa daga y dauki wannan babyn sai y ajiye ta y dauki wannan daga karshe ma karbarsu yayi duka 2 y rungumesu dariya su Amira suka farayi masa shima dariya yayi domin yau ta shiga cikin ranakun tarihinsa. Islam sai wajen 12:00pm allurar baccin ta saketa ai tana tashi da tambayar ina babynta ta farka kaka ce tace yau naji rashin kunyar yayan xamani islam tace kiji kakannan wacce kunya nice fa nasha wahalar haihuwa ba wanda y tayani Aslam kuwa cewa yayi rabu da ita princess ga yayanki kiji duminsu cikin farin ciki ta karbesu wata kaunarsu tana kwarara acikin ranta,tie aka hada mata mai kauri sai da aka tilasta ta tasha sannan kaka ce tace to uwar son yaya ai saiki basu abincinsu dan tun daxu ruwa da dabino kawai ake basu islam ce ta fara kokarin daga rigarta tace yanxu kuwa murmushi Aslam yayi yace yauwa matar y aka mika mata tafara feeding dinta ai kara ta saki lokacin da babynta ta kama mamanta saboda wani irin axaba dataji ta riketa tun daga tsakiyar kanta har tafin kafarta da sauri ta xare mamanta tace tab ashe da xafi dariya kaka ta tuntsire da ita tace da an fada miki shayarwar wasa ce babyn kuwa jin an kwace mama ai saita saka ihu ta hannun Aslam ma tuni ta fara Aslam ne y matso yace plx princess ddaure kiyi feeding dunsu harara ta ballamai tace bakasan da ciwo ba saida aunty amarya ta bude mata wuta sannan taci gaba da shayar da babyn tana hawaye ahaka harta koshi ta bawa ta hannun Aslam ma. Kwanan islam 2 a asibiti aka bata sallama saboda daga ita har babies dinta suna lfy yan'uwa da abokanan arxiki kuwa sai xuwa sukeyi mata barka bayan wasu xugar mutane da suke xuwa daga wadannan sun tafi sai wadannan susuxo kaka ce ta gaji tace wai islam a ina kika san wadannan mutanenne wadansu ma sun haifeki murmushi islam tayi tace *goyon kaka* fans ne aunty umma ce ta sanar dasu sune ma xasuxo su kula da hidimar abincin suna kaka murmushi tayi tace Allah sarki sosai Aslam yayiwa nurses din kyauta aikuwa har mota suka rakosu sunayi musu addu'ar Allah y raya babies. Bayan sun dawo gda haka yan barka sukaci gaba da xuwa Aslam kuwa kullum yana manne da princess dinshi da babies dinsa yana basu wata irin kulawa duk lokacin da yan barka sukaxo shine yake mika musu su saura 3 days suna khausar da safwan suka duro kano ai khausar lokacin dataga babies din rikicewa tayi saboda yawunsu sai xuxutasu takeyi daga ta dauki wannan saita ajiye ta dauki waccan. *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *145-146* *LAST PAGE* Ranar suna yara sukaci sunan mommy da Aunty amarya watako khadeeja da fateema Khadeeja (sultana) fateema kuma (hibbatullah) anyi suna nakuxo mu gani anci ansha canna hango goyon kaka fans gaban kaskon suyar hanji sunata fama da hayaki suna aikawa cikinsu tun yana kan wuta anyi taro lfy an kare lfy mai jego da yaranta sunyi shigar alfarma hakama uban gayyar ba'a bashshi a baya ba watako Aslam kayan barka da suka samu kuwa tamkar zasu bude karamin boutique danko fans din goyon kaka akwati set sukayowa islam da daughters dinta lol Haka islam taci gaba dayin wankan ta ammafa kullum akaxo wanka sai sunyi fada da kaka dan wataran haka xatayi xamanta bayan tasan an kai ruwan wankan bandaki tayita shiririta har saiya fara huce har sai kaka taxo ta janyo ta a haka ake wancan tana mitar wai kaka tana sane take xuba mata ruwan xafi danta konata bayan xaneta da takeyi da ganye (nikuwa nace keda kakar taki ). Bangaren twice kuwa sai wayo suke dada yi da girma ga wata kiwa da suka fara tun kafin suyi 40 days dan sunfi so su jisu hannun mamarsu in kuwa ba haka ba gwanda a kwantar dasu *Na Umma Yahya Musa* *GOYON KAKA* *145-146* *LAST PAGE* Ranar suna yara sukaci sunan mommy da Aunty amarya watako khadeeja da fateema Khadeeja (sultana) fateema kuma (hibbatullah) anyi suna nakuxo mu gani anci ansha canna hango goyon kaka fans gaban kaskon suyar hanji sunata fama da hayaki suna aikawa cikinsu tun yana kan wuta anyi taro lfy an kare lfy mai jego da yaranta sunyi shigar alfarma hakama uban gayyar ba'a bashshi a baya ba watako Aslam kayan barka da suka samu kuwa tamkar zasu bude karamin boutique danko fans din goyon kaka akwati set sukayowa islam da daughters dinta lol Haka islam taci gaba dayin wankan ta ammafa kullum akaxo wanka sai sunyi fada da kaka dan wataran haka xatayi xamanta bayan tasan an kai ruwan wankan bandaki tayita shiririta har saiya fara huce har sai kaka taxo ta janyo ta a haka ake wancan tana mitar wai kaka tana sane take xuba mata ruwan xafi danta konata bayan xaneta da takeyi da ganye (nikuwa nace keda kakar taki ). Bangaren twice kuwa sai wayo suke dada yi da girma ga wata kiwa da suka fara tun kafin suyi 40 days dan sunfi so su jisu hannun mamarsu in kuwa ba haka ba gwanda a kwantar dasu *LAST PAGE* Bangaren twice kuwa sai wayo suke dadawa hade da girma ga kiwa da suka farayi duk da basu kai 40 days ba dan sunfi son su jisu hannun namarsu in kuwa ba haka ba tofa sun gwammace su jisu a kwance dan in mutum ma y daukesu suna kare masa kallo xasu canyara kuka har saiya ajiye su gashi hatta Aslam sun ganeshi dayake duk sati yana hanyar kano. Gyara sosai mommy take yiwa Islam saboda takusa cika 40 days saura 1 week kuma a yadda suke ganin take2 Aslam tsaf xaice a bashi matarshi tana arba'in dan akwai ranar da kaka ta tafi gwarxo shikuma yaxo kano lokacin mommy ta mayar da islam part dinta xirya Aslam y dinga yi a part din mommy har dare mommy kuwa ta nuna tamkar bata gane me yake nufi ba wajen 10:00pm tayiwa islam sallama ta tafi dakinta aikuwa xuruf Aslam y dawo y kama hannunta y dauki hibba ta dauki sultana akan gadonsu y kwantar dasu ita kuma y jata kan gado muguwar runguma y bata wadda tasaka shi sakin ajiyar xuciya hatta ita islam din har cikin ranta taji rungumar kissing dinta y fara yana kokarin cire mata riga mommy ta shigo dakin rafka salati tayi cikin jin kunya islam ta gyara rigarta Aslam kuwa keya kawai y sosai mommy ce tace taso ka fuce mara kunya yanxu kai ko tausayinta bakaji yaushe ta haife maka yara kake kokarin yimata wani cikin shi kanshi Aslam wata muguwar kunya ta kamashi domin a xamanshi da mommy irin haka bata taba hadasu ba kunyarshi ma takeji taci gaba ai dama tun daxu naga take2 ka shiyasa nayi maka banxa naga ko abinda nake tunani gaske ne ashe kuwa nufinka kenan sum2 Aslam y fuce yana dariya kasa2,sannan ta dawo kan islam ke kuma wawiya yaxo xai miki wayo to tsaya ki sairareni kiji da kyau wlh yanxu xai iyayi miki wani cikin yayanki suna 9 months ki haifa musu kanne cikin tsoro islam ta waro idanuwanta tace eh ki kame kanki yanxu dai dan kina xufa tunanin fara dakko wata sabuwa dal xaiyi sai da mommy ta tsoratar da islam sosai sannan tabar dakin tun daga lokacin ta fara dari2 da Aslam danko dan kissing dinta da judging da take bari yayi ta daina shikuwa gogannaku duk y damu dan da wannan yake rage dan xafi. Yau islam kwananta 40 cif ta shirya ta tafi gwarxo itada kaka sati 1 sukayi sun xagaya dangi da yan uwa kowa y kalli hibba da sultana sai yace masha Allah saboda yaran akwai shiga rai gasu bulbul dasu har gdan hanne taje lokacin yayan hanne2 da cikin na 3 ranar da suka baro gwarxo ranar Aslam yaxo kano da xummar daukar matarsa aikuwa mommy tace saita gama xagaya dangi haka ta kara 2 weeks ta xagaye dangin aunty amarya na kano dana mommy taje gdan Amira lokacin tana fama da laulayi dariya islam ta rikayi mata tana itace xata karbi haihuwar ta banxa Amira tayi mata domin ita laulayin yana bata wahala. Yau su islam suka koma photercort dasu twice dinta masha Allah yara sunyi wayo dan xakayi tunanin sunyi3 months ga dankaren wayo abun da islam ta kula da twice dinnata shine komai kusan tare sukeyi hatta kuka in 1 ta fara to yanxu 1 ma xata farayi lokaci daya suke rikitata tarasa yadda xatayi dasu kawai itama sai tahau kukan. Su khausar ne suka xo daukarsu airport khausar ma tayi shar kana ganinta xakasan akwai motsi acikinta karbar sultana tayi tana a gaskiya sis kin iya haihuwa yarannan kyawawa nasha Allah nifa bana iya banbance su murmushi islam tayi tace banbancinsu 1 ne sultana dimple dinta 1 ne irinna babanta a hannun dama hibba kuma dimple dinta 2 irinnawa dukka kumatun dariya sukayi dukkansu sukace kaga uwa da diyanta harta banbancesu a haka har suka karasa gda. Daran ranar islam ta fadawa yan garinsu dan first night dinta ne y dawo mata dan Aslam y nuna mata irin yadda yayi missing dinta sai asuba y kyaleta. Haka su islam sukaci gaba da rayuwarsu twice sai dada girma sukeyi suna da 9 months suka fara tafiya amma fa akwai kiriniya ko kadan basaji gashi sun iya hada barna indai suka tashi tofa gdan baxai nutsu ba har sai dai in bacci suka koma haka islam xatasha takaicinta in xata dakesu Aslam y hana yace ai ko rabin irin kiriniyar da tayi basuyi ba. *After 3 years* Wasu kyawawan yara nagani su 5 biyu mata 3 maxa karasawa nayi kusa dasu anan nagane yaran matan sultana da hibba ne cikin maganarsu ta yara naji suna cewa kai shultan ka jauna acan makayanta xa'ayi inda wadancan yaran 2 maxan kuma suna o'oh wallashi mu foot ball jamuyi kuxo muje nan naga islam da khausar sun futo khausarda katon cikinta haihuwa yau ko gobe daga gdan Amira na kano ashe itace ta kara haihuwa ta haifi baby girl dan haihuwarta ta farko namiji ta haifa akasa masa sunan Abba suke cemasa suhaif khausar kuma sunan dadyn safwan aka saka masa suke cemasa mahboob kamo hannu sultan tayi tana yarona taso mu shiga ciki hibbace ta fadi tana birgima tana mommy washa fa jamuyi shine jaki aukeshi gashkiya ki ajiye shi kama baki islam tayi ta kalli khausar tace kijimu da mara kunyar yarinya Aslam da karasowarsu kenan y dago hibba yace haba aunty na kefa aunty ce ko kinaso yara su rainaki hade rai tayi dan ko kadan hibba batason raini tace a'ah banasho yace yauwa y direta suka dunguma suka shiga palon Amira dukkansu Aslam, islam,safwan,khaudar,sultana,h ibba,sultan,suhaif,mahboobxaune suka tarar da Amir,Amira a palon Aslam ne yace kuxo mudauki selpie da sauri suka hadu guri 1 ya kyara musu pic nima da sauri na dauko wayata na daukesu. Haidar yayi aure y auri hajar budurwarsa, sagir kuwa ihsan y aura kanwar islam yusuf ma yayi aure yayan Islam. *_Tammat bi hamdullah ayau Allah y bani ikon gama wannan littafi nawa ```GOYON KAKA``` masu mafarkin shi ku farka ku biyoni cikin sabon novel dina mai suna ```SAIFULLAH```danjin da wanne irin salo da darussa xaixo dashi na sadaukar da wannan novel din ga my blood sister Aysha yahya musa (Aunty ummy) & my Afma kai da duk wani ```GOYON KAKA``` dayake duniya lol_* *_Alhmdllh dukkan yabo da godiya su tabbata ga ubangiji madaukakin sarki mai kowa mai komai wadda y bani ikon kammala wannan kagaggen littafi nawa mai suna ```GOYON KAKA``` abinda nafada dai2 Allah y hadamu a ladan wanda nayi kuskure kuma Allah y yafemin readers bani da kalmar da xanyi amfani da ita wajen nuna muku irin farin cikin danake ciki saboda inna tuno da irin soyayyar da kuka nuna mini hade da bani kwarin gwiwa wajen yadda kuke nuna soyayyar ku akan buk dinnan ```GOYON KAKA``` a gaskiya bakina baxai gaji ba wajen jaddada irin godiyar danakeyi muku ngd3 Allah yabar xumunci masoyana nima ina kaunarku a duk inda kuke a duniya masu kirana a waya da masu yimin text massage baxan iya taba mantawa daku ba dabadanba dana rubuto sunayenku amma ina kunfi karfin haka ngd3 Allah yabar mana xumunci Ameen._* *_Hakama whiters namu ngd3 da muhimmiyar rawar da kuka taka wajen bani goyon baya wajen rubuta novel dinnan Allah yabar xumunci Ameen._* Gaisuwarku ta dabance 1-Afma 2-nana fu'ad 3-nusnim 4-aunty jiddah 5-Aysha iliyasu 6-humaira melody 7-jidda mowajoo 8-maryam bello 9-rahma nalele 10-billy tabacco 11-zee yabo 12-m jay 13-mrs lamido 14-miss xoxo 15- 15-Aysha ghana 16-Aysha muhd 17-Al'eeman 18-Umar Dalha Baxan taba mantawa daku ba 1-ummy aysha 2-ummy garkuwa 3-asy khaleel 4-didi 5-autar hajiya 6-aysha basheer 7-billy 8-Amina zaria 9-ummu khamal 10-hama gee 11-miemiebee 12-mami 13-ilham 14-maryam 15-sadiya jegal 16-safah 17-xarah 18-xuhrah 19-yar lele 20-zee nur 21-aenart Asmart