[22/09 à 11:11] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman. _____________________ 21/09/24 1-2 #Damagaram Ƙarfe uku na dare agogon ɗakin ya nuna,a sa'ilin da mutane ke kwance suna hutawa a daidai wannan lokacin ne Hajara ta hana idonta bacci saboda yawunta da suke tsinkewa tsabar yadda suke kwaɗayin ɗanɗanon jini. Idonta ta fara rikiɗarwa tun farko kafin ta tura ƙofar ɗakin wacce ta yi sa'a ba a kulle ba,ɗakin cike yake da duhu amma bai hana idon Hajara hango Safeenat ba wacce ke kwance ta tallabe ƙaton cikinta tana sharara bacci. Yawun Hajara suka ɗiga ga ƙasa lokacin da ta yi tozali da ɗan jinjirin da ke kwance a marar uwarsa,ta ɗaga ƙafa da niyyar isa gare ta kawai sai ga wani haske da ba ta san daga ina ya fito ba ya luluɓe Safeenat.Da wani mugun sauri ta yi baya tana zarar idonta da suke jawur kamar wuta kafin kuma ta fice daga ɗakin gaba ɗaya,ba wai don ta haƙura ba sai don ƙara yin wani sabon shirin. “Hajara lafiya kika zo kika tsaya tsakiyar falo?” muryar mijinta Dayyabu ta daki kunnenta,da mugun sauri ta lumshe idonta gudun kar asirinta ya tonu,ba tare da ta amsa masa tambayar ba ta yi gaba ta koma ɗakinta ta ja ƙofa ta rufe.Sai a lokacin ta ja wani numfashi haɗi da buɗe idon, ƙarƙashin gadonta ta je jawo wata tukunyar laka.Banda baƙin hayaƙi babu komai a ciki,wani yare ta yi sai ga shi ta rikiɗe ta koma tsakaka haka ta fito ta fara bin bango ba ta zame ko ina ba sai ɗakin Safeenat a karo na biyu.Har yanzu hasken bai ida gushe wa ba,wannan dalili yasa ta sauka kan dressing mirror ta fiddo harshenta tare da fara zuba yawunta cikin man shafawa da Safeenat ta bar shi a buɗe . Bayan ta gama ne ta ƙara bin bango ta fito mijinta ta gani ya buɗe ƙofar ɗakinta ya shiga ya kuma fito da alamu rashin ganin ta ne yasa haka. Da sauri ta koma ta je ta ɗauki siffarta ta bil'adama,gefen gado ta zauna tana jin har yanzu kwaɗayinta bai kau ba.Haka wannan dare ya kasance daren rashin sa'a gare ta,sam ba ta yi wani baccin kirki ba. Washegari Tun safe Safeenat ta yi wanka ta shafa mai da turare sannan ta shirya cikin doguwar riga kasancewar cikinta ya tsufa ba ta da wata sutura mai yi mata in ba doguwar rigar ba. Cikin sanyin jikin da ya zama tabi'arta ta fito,a falo ta tarar da ahalin gidan kan table suna cin abinci. “Daddy ina kwana?” ta gaishe da mahaifinta,ya amsa cikin sakin fuska yana cewa “ lafiya lau Feenat ya ƙarfin jikinki?” “Alhamdullah!” ta amsa tare da maida dubanta gefen Hajara ta ce “ina kwana Gwaggo?” Hajara ta haɗe rai ta ce “ da ban kwana ba za ki gan ni ? Tsabar munafurci ba ki tashi fito wa ba sai da baiwarki ta gama girki kin fito ki kwashi banza to ban girka da ke ba” Feenat ta sunne kai tana jin wani irin zafi na tasowa daga ƙasan zuciyarta,babban takaicinta kuma da ta ji Daddy yayi shiru bai ce komai ba.Yaran Hajara Munir da Munira suka shiga yi mata dariya,ba ta kula su ba ta wuce kitchen ɗin ta nema wa kanta abin da za ta ci.Ƙasan tile ta zauna dirshen ta soma tunanin bayan ta gama cin abincin,hawaye suka zubo mata ba ta shirya ba da sauri kuma ta dafe ƙaton cikinta da ke faman juyawa tana jin muguwar ƙaunarsa don a yanzu shine kawai zai rage mata raɗaɗin rashin masoyinta Bashir. “A yi dai mu gani in tusa ta hura wuta! Yo wannan kukan shi zai maido miki mijin? Ai dama duk abin da aka yi shi da cin amana ba zai je ko ina ba.Yanzu da kika yi sanadin hana Bashir auren Murjanatu ina ce ya mutu ya bar ki,kuma ita Murjanatun na can Saudi Arabia cikin gata tana auren farin ciki” Goggo Hajara ta faɗa lokacin da ta tarar da Feenat a kitchen tana kuka.Ta yi kutufo da ƙafafunta ta ce “ ja ki ban wuri na wuce ko kuma na sabanta ki muguwa mai halin uwarta” da mugun sauri ta janye ƙafafunta wani sabon kukan na ƙwace mata. Cikin masifar nan Goggo Hajara ta ci gaba da balbale ta da masifa,“ ki tashi ki fitar min daga kitchen zan ɗora girki ,ki koma can ɗaki ki ci gaba da munafurcinki” Daga bakin ƙofa Daddy ya ce “Hajara ki zo ina son ganin ki ɗakina” Idonta kamar za su faɗo ƙasa tsabar yadda take hararen Feenat,haka ta wuce ta je ɗakin Daddy a tsaye ta tarar da shi ya ba ƙofa baya. “Daddyn yara ga ni ” ta faɗa cike da ladabi. “ Haja ki kiyaye ni,bari gani na ƙyale ki ɗazu kin ci mutumcin ƴata,na yi shiru ne kawai don in nunawa Feenat ba ta kyauta da ta bar ki ke ɗaya ki ka yi aikin gida ba .Amma ba zan lamunci ki tozarta min ƴa ba,nan gidana ne don haka tana da ƴanci sake wa yadda take so.Mine ne na yi mata gori? Maimakon ki rarrashe ta akan halin da take ciki shi ne za ki tsiro mata da wata sabuwar masifar? Ta rasa mijinta wannan kaɗai abun tausayi ne,sannan ga tsohon ciki.Na san tun bayan da Feenat ta auri Bashir ki ka tsane ta,kin manta cewa matar mutum kabarinsa tun can farko Allah bai nufa Murjanatun ce zai aura ba” Cike da munafurci Goggo Hajara ta soma kuka har da jan majina kamar wata yarinya,da mugun sauri Daddy ya juyo tare da jawo ta jikinsa yana cewa “mine ne kuma na kuka? Ke fa uwa ce bai kamata sai an faɗa miki abin da ya dace ba,ɗa na kowa ne ba ka san mai taimakon ka ba” “Amma Daddyn yara ka fi kowa sanin yadda na riƙe Safeenat da zuciya ɗaya amma rana tsaka ta ruguza alaƙar nan don kawai ta ga banda burin da ya wuce Murjanatu ta yi aure” “To ai yanzu komai ya wuce,ba ga shi ta yi auren ba? Jiya ma mijinta ya min magana kan yana so ta dawo gida ta haihu ” Jin ƴarta za ta dawo sai ta manta da zancen kuka ta washe baki ta ce “au ! Madallah! Yaushe za ta zo?” Daddy ya murmusa ya ce “a'a ƴarki ta ce kar a sanar da ke za ta yi miki bazata kawai ki zamana cikin shiri” da wannan Daddy ya fice ya bar gidan zuwan can Company wurin aikinsa. Goggo Hajara kuwa kitchen ta koma sai ta tarar da Feenat ta ɗora girkin rana sai gumi take saboda zafin wutar gas,ta taɓe baki kafin ta fito. Ita kuwa Feenat baiwar Allah sam ba ta ƙaunar tashin hankali wannan ya saka ta ɗora girkin duk don a zauna lafiya.Kafin ta gama jikinta ya soma ƙaiƙayi, soshe-soshe ta fara yi ganin abun na ta yin gaba yasa ta kashe gas ɗin ta fito.Ɗakinta ta je,direct toilet ta shiga ta soma yin wanka sai dai ba ta canza zane ba sai ma wani ja da fatarta ta yi.Dakyar ta daure ta je ta ida girkin ta zuba a kuloli ta jera kan table,da ta koma ɗaki sai ta ɗauki hoton hannunta inda alamun jan ya fi yawa ta tura wa ƙawarta Sakeenatu tana tambayarta ko mene ne wannan kasancewarta likita .Babu jimawa ta kira ta bayan sun gaisa ne take cewa “ sai dai ki zo asibiti a duba ki ta waya ba a ganewa,kuma ni ba aikina ba sai dai na haɗa ki da likitan fata” Feenat ta ja ajiyar zuciya ta ce “ KEENAT kin san Daddy ba zai bari na fita ba,kuma dama bai dace mace mai takaba ta fita ba” Cike da tausaya wa KEENAT ta ce “ na sani amma ai lafiya ta fi komai ,ƙila kuma kin ci wani abu ne da ya haifar miki da hakan” “Ban ci komai ba fa,ya aikin ana ta fama ko?” “Wallahi kuwa,in sha Allah in na sauka zan biyo nan gida na duba ki” sosai suka yi hira kafin su yi sallama. Daga inda take zaune ta fara kallon hotunan Bashir inda yake sanye da Kakin soja,nan ta lalace wurin kallonsu har sai da Munira ta shigo kiranta .Ta miƙe dakyar ta fita,a falo ta tarar da Goggo Hajara tun da ta fito ta lura idonta na kan cikinta.Ta sunne kai tana mai karanta ‘ Hasbunallahu wani'imal wakil ’ a can ƙasan zuciyarta,cikin nata ne ya soma yin motsi kamar zai fito mata ta cibiya.Tsabar yadda take jin ciwon juyinsa yasa ta kai hannu ta dafe ƙasan mararta tana mai fitar da nishin wahala,ido rufe ta ci gaba da sauraren azabar da ke ratsa duk sassan jikinta. Goggo Hajara ta yi wani makirin murmushi tana mai cewa “ Safeenat lafiya kuwa?” Sai a lokacin ta ware idonta da suka yi wani mugun ja,bakinta sam ba zai buɗu ba ballantana ta iya yin magana.Bayanta da ƙugunta suka ƙage lokaci guda wanda ya haifar mata duƙawa ba ta shirya ba,tuni idonta sun fara ganin dishi-dishi duk da wannan ne cikin farko tuni ta fahimci haihuwar ce ta zo bilhaƙi. Goggo Hajara ta ce “ Haihuwa ce kam,Munira fita waje bari na ɗauko leda ” “Mama in kira mai taxi ku wuce asibiti ko?” Munira ta faɗa tana kallon Safeenat wacce tuni ta fara wani gurnani mai haɗe da nishi. “Uwar mai taxi za ki kira ,fice na ce” Goggo Hajara ta faɗa tana mai shiga ɗakin Safeenat ta ɗauko robar da aka tanadi duk wasu kayan haihuwa. Da kanta ta shimfiɗa leda ta ɗora wasu zannuwa akai kafin ta ce “ Safeenat ki cire rigar nan mai haihuwa ina ruwanta da wata sutura” tsabar azabar da take ji yasa ba ta yi yunƙurin hana Goggo cire mata kayan ba. Yawun Goggo Hajara har wani dalala suke suna tsinkewa lokacin da ta ga kan ɗa ya sawo kai.Jikinta har rawa yake wurin taimakawa yaron ya fito ,babu wani jinkiri ko ɓata lokaci ta fara juya ido tare da soma kai wa kurwar jinjirin hari sai dai ba ta ida cin galaba ba nishin Safeenat haɗi da kukan wata babyn ya dawo da ita hayyacinta. Ƙirjin Goggo Hajara ne ya kusan ɓallewa zuciyarta ta faɗo tsabar firgici,jaririyar da faɗo cibinta a yanke yake sannan kuma babu marakiya saɓanin shi namijin da har yanzu take masa reto. Sai a lokacin ne ma ta samu zarrar yanke mahaifar,ba tare da kuma ta san dalilin kawar mata da mugun nufinta ba ta soma kimtsa Safeenat wacce babu laifi ta dawo hayyacinta. Goggo Hajara ta wanke kayan da kuma gyara ɗakin ta saka turaren wuta,ita ce kuma ta zaɓo wa Safeenat riga da zane.Har da haɗo mata tea mai zafi ta sha,gefe ta koma bayan ta gama komai tana tunanin zuci ‘ mi ya shiga kaina ni Hajara? Kamar ni kamar ba ni ce ba’ kukan jariran ne ya katse mata tunani ,ta ce “ ki ɗora su ga abincinsu” sai kuma miƙe ta soma nuna mata yadda za ta yi.Namijin kawai ya sha ita kuwa macen baya ga kuka babu abin da take,Goggo Hajara na ɗaukar ta sai kuma ta yi shiru kamar ba ita ce ke kukan ba.Muƙut ta haɗiye wasu yawu hango wani baƙin kallo daga cikin ƙwayar jaririyar da ko minti talatin ba a yi ba da haihuwarta...... [22/09 à 19:14] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 22/09/24 3 Sannu a hankali Gwaggo Hajara ta soma jin wani sanyi na ratsa ɓargo da tsokarta,kamar wacce aka yi wa doli kuma ta ƙi kawar da dubanta daga cikin idon Babyn.Idonta suka soma kafewa saboda wata irin shaƙa da ta ji an yi wa wuyanta,babu shiri ta buɗe bakinta na maita kurwar jaririn da ta soma cin galaba kansa ta fara fitowa daga can cikin hanjinta tana fitowa ta bakinta .Wani koren hayaƙi ne ya soma shiga cikin jaririn wanda daga bakin Gwaggo Hajarar yake fitowa,wata irin atishewa ya soma yi kafin ya tsala kuka. Da mugun sauri ta yi baya ta zauna kan kujera,idonta na kan babyn wacce tuni ta soma bacci. “Gwaggo ya ƙi yin shiru ko cikinsa ke ciwo?” Safeenat ta faɗa kamar za ta yi kuka tana ririga yaron,ran Gwaggo Hajara ne yayi mugun ɓaci sai yanzu tunaninta ya dawo a tunzure ta ce “ uban mi zan yi masa to? Lokacin da na yi haihuwata uban wa ya kama min wurin rainon ? Ki riƙe abin ki” ta faɗa tare da ajiye mata babyn kusa da ita,jikin Safeenat sai yayi sanyi dakyar ta samu yayi shiru bacci ya ɗauke shi.Ta shimfiɗe shi kusa da Baby girl ɗin kafin ta je ɗakinta don ɗauko wayarta,tana dawowa sai ta hangi maciji kan jaririyar duk ya naɗe jikinta da shi ba ta san lokacin da ta saki wata ƙara ba wacce ta yi daidai da ɓacewar macijin.Safeenat ta zo da mugun sauri ta ɗauki yaranta ta mayar da su ɗakinta,sai da aka ɗauki lokaci kafin nutsuwarta ta dawo ta soma kiran mutane tana shaida musu zancen haihuwar.Hatta Daddy sai da ta kira shi ta sanar da shi,babu jimawa kuwa sai ga ƙanwarsa Habiba ta zo gidan sosai Safeenat ta ji daɗin ganinta musamman da ta ga har da ƙullin kayanta ta zo da alamu za ta jima. Ruwan zafi ta je ta ɗora cikin ƙatuwar tukunya kafin ta dawo,“ Safeenat ya zama doli ki kula da yaran nan musamman namijin don na ga shi ne mai rauni” Habiba ta faɗa tana shafar twins ɗin. “In sha Allah Gwaggo Habibah zan yi,da alamu ma ya fi kuka dakyar na samu yayi baccin nan” cewar Feenat. “Hum! Baccin wahala ne,ah to ai doli ma yayi Allah dai ya kyauta” “Amen!" Feenat ɗin ta amsa ba tare da ta san dalilin Gwaggo Habibah na faɗar haka ba.Bayan ruwan sun tafasa ta juye su ta yi wa yaran wankan,namijin ana saka shi a ruwa ya farka tare da canyara kuka amma ita hajiya babba har aka gama wankan tana bacci tamkar wacce ba ta rai.Gwaggo Habibah kuwa sai murmushi take tana jin wani farin ciki ƙasan ranta,dama ita Allah bai taɓa bata haihuwa ba . Safeenat ma sai da ta yi wanka da ruwan zafin ta gasa kanta da kyau ta fito ɗaure da towel,sai kuma yanzu ne Gwaggo Habibah ta lura da yadda fatar Safeenat ta yi ja.Da wani mugun sauri ta tashi ta cabke hannunta da ke ƙoƙarin ɗaukar kwalbar mai,“ jira na duba na gani” ta faɗa tana mai duba man ba tare da ta ce komai ba sai kuma ta fita direct ɗakin Gwaggo Hajara ta wuce ko sallama ba ta yi mata ba kuwa ta yi tsaye kai gare ta tana mai cewa “ an gaishe da uwar mugaye ta duniya,wato baƙar zuciyarki na nan daram babu canji .To asirinki ya tonu na ga bala'in da kika zuba cikin man shafawar Safeenatu,sai dai ki sani sai dai ki ci kanki amma Twins sun fi ƙarfinki ” Da wani mugun sauri Gwaggo Hajara ta tashi zaune,dama tun bayan da ta shigo ɗaki take jin duk jikinta babu daɗi dalilin kwancin da ta yi kenan sai kuma yanzu da ƙanwar mijinta ke feso mata kalaman rashin mutumci.Wani makirin murmushi ta yi kafin ta ce “ da alamu dai kin manta wace ce ni ko Habibah? Amma za ki gani” “Babu abin da zan gani sai alkhairi...” “Eh lalle wuyanki ya isa yanka” Gwaggo ta faɗa tana juya ido,Habibah ta tuntsire da dariya ta ce “au kin zata guntun tsafinki zai iya yin tasiri a kaina? To ki canza shawara tun wuri bai ƙure miki ba don yanzu daidai nake da ke” Ganin alamun tabbas ba Habibar da ce ke tsaye a gabanta ba yasa Gwaggo Hajara haƙura da surkullen,idonta masu cike da mugunta ta tsura mata ta ce “ mi ya kawo ki ɗakina?” “Ina so ki fita sabgar Safeenat da ƴaƴanta,in kuma ba haka ba....” sai kuma ta yi shiru tana cije baki haɗi da jinjina kai. “Ki tona min asiri? A tunaninki akwai wanda zai yarda? Hahaha! Yaro man kaza,Habibah kar ki manta hatta gyatumarki a tafin hannuna take....” ta yi saurin katse ta da “sai dai shi wanda kike tutiyar da shi mugun tsafinki bai yi tasiri kansa ba ,na san kin san haka” Ran Gwaggo Hajara ne ya ƙara yin baƙi,duk duniyar nan Habibah ce kawai ta zame mata ciwon ido duk yadda take son gudanar da lammuranta to muddin tana ga wuri sai ta roga su. Ƙarar buga ƙofa ce ta maido ta daga guntun tunanin da take,ta bi bayan Habibar da mugun kallo tana jin baƙin cikin da ba ta da MAITAR IDO (MRS SADAUKI,duk mai son complete book ɗin nan zai iya tuntuɓa ta kai tsaye ta lambar da na rubuta a can sama) da tabbas ta jefa wa Habibah ƙwayar cutar da za ta zama ajalinta. SAKEENATU Tana tashi daga aiki ta fito don samun adaidaitar da za ta kai ta can gidansu Safeenat kwatsam sai ga kiran wayar mijinta Abbas . “Mamuh ta ce yau ba ki bar mata abin da za ta ci ba ina son sanin dalili?” shi ne abin da ya fara cewa ko sallama babu,ran Sakeenatu ya ɓace amma ta haɗiye shi ta ce “ na samu ƴar aiki fa kuma kafin na fito na shaida mata kan ta girka mata abin da za ta ci” “Ƴar aiki za ta kula da uwata? Keenat mi ya shiga kan ki ne? Yanzu dai na baki minti goma ki tabbatar kin yi mata girkin abin da take so” yana gama faɗa ya yanke kiran. Tamkar za ta fashe haka take ji,mai ɗan sawu ma dakyar ta faɗa masa inda zai kaita.Tana shiga gidan ta tarar da Mamuh zaune kan kujera ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana wani yamutsa fuska,gaban Sakeenatu ya faɗi kamar kullum muddin dai za su haɗa inuwa ɗaya da surukarta ta. “Barka da yamma Mamuh” ta faɗa murya na rawa,Mamuhn ta ce “ in kin gama yawon tanbaɗar sai ki shiga kitchen ki girka min wake da shinkafa” Idonta tab ƙwalla ta shiga kitchen ɗin ta ɗora tukunya ko kayan ba ta cire ba haka ta tsaya sai da ta tabbatar ta gama sannan ta zuba a plate ta kai wa Mamuh. Da zafi da komai ta saka hannunta tana ci mai na bin hannunta sai wani lumshe ido take alamun yana yi mata daɗi, Sakeenatu wacce ta tsaya don ganin ko yau ma Mamuh za ta yi irin yanayin nan sai kuwa ta ga ta yi.Idon Mamuh sai wani haske-haske suke fitar wa kamar kullum muddin dai wake da shinkafa ta girka mata. A tsorace ta nufi ɗakinta ,kayan jikinta ta rage sannan ta shiga toilet.Shower ta sakar wa kanta,kamar abun almara haka ta soma jin yanayin jikinta na canzawa tana jin feeling wanda kuma abu ne mai wuyar faruwa da ita muddin dai ba Abbas ke a wurin ba. Abu kamar wasa amma sai yin gaba-gaba yake,kafin Sakeenatu ta farga tuni ta hankalinta ya soma gushewa ta dumulmiya duniyar son kasancewa da mijinta.Tamkar a mafarki ta soma jin kamar ana wasa da sassan jikinta,sai dai idonta sun yi nauyin da ba za ta iya buɗe su ba ballantana har ta ga shin zahiri ne ko kuwa? Sama da minti goma tana cikin wannan yanayi kafin ta dawo hayyacinta,a doli ta tsarkake jikinta ta fito tana mamakin al'amarin.Bayan ta shirya tsab cikin riga da zane sai ta fito falo,Mamuh ta gani sai sharar bacci take kamar matatta .Dining ta je ta zauna ta buɗe kulolin da ƴar aikinta ta yi girki,shinkafa ce da miyar kaji haka ta zuba ta soma ci tana mamakin yadda aka yi Mamuh ta zaɓi cin wake da shinkafa akan lafiyayen abincin nan .Bayan ta gama ta ɗauki waya ta kira Safeenat ta shaida mata za ta zo yanzu ,sai kuma ta koma ɗaki ta saka hijabinta ta ɗauko jaka ta fito.Tana fita ba ta wani wuya ba ta samu ɗan sawu ya kaita,da sallama ta shiga gidan har ta wuce can ɗakin da Safeenatu take wanda ya cika da mutane kusan dangin Bashir ne. A mutumce take gaishe da kowa amma yanayin jikinta na bata ana kallonta,tana juyawa suka haɗa ido da Habibah wacce ta kasa ɗauke idonta kan Sakeenatu har sai da ta ji ta tsargu.Ta zauna kusan Safeenat tana mai cewa “waccan wace ce sai kallona take?” “Ƙanwar Daddy ce fa ba ki gane ta ba?” Feenat ta faɗa tana mai miƙa mata boy bayan ta shafi kansa sai kuma ta ajiye shi aka miƙa mata girl ɗin.Wani irin shock ne ya ratsa Sakeenatu har sai da ta zabura,yayin da gabanta yayi mummunar faɗuwa ganin Babyn ta buɗe idonta tana kallon ta alhalin lokacin da aka miƙo mata ita tana bacci.Sakeenatu ba ta ida shiga tashin hankali ba sai da ta ga tamkar Babyn na yi mata murmushi...... [23/09 à 04:23] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 23/09/24 4-5 Wani irin abu ne marar misaltawa ke ratsa Sakeenatu tun daga kan babban yatsan ƙafarta har zuwa kwanyarta da ta soma toshe wa .Lamarin da take ji a al'aurarta kuwa kusan girme wa hankalinta ya yi,tamkar wacce ake fitar wa da wani dafi haka take jin ana yi mata motsi gami kuma da samun sassauci a doli ta lumshe ido ba ta shirya ba.Ita kuwa Gwaggo Habibah da ke can gefe sai murmushi take tare da yin zancen zuci don duk tana ankare da abin da ke faruwa.‘ Tabbas a duk inda ke da mugunta da cutar wa Allah sai ya kawo mai ceto mai magani,na zo kenan a gidan nan mutuwa kawai za ta fitar da ni zan saka ido sosai akan jaririyar nan zan raine ta da hannuna ta yadda zan taimaka mata wurin fahimtar baiwar da Allah ya yi mata da yadda za ta sarrafa ta’ sai kuma ta miƙe tana yin wani murmushin nasara.Babyn ta ɗauke daga cinyar Sakeenatu wacce gumi ya jiƙa ta har goshinta na ɗiga,babu kuma wanda hankalinsa ke wurin hatta ita Safeenat sai hira take da dangin mijinta waɗanda suke cewa shi namijin a saka masa suna Bashir a yi madadi. Sakeenatu ta ware idonta jikinta na ɗan rawa kamar wacce ta farka daga mummunan mafarki.Idonsu ya sarƙe cikin na juna,Gwaggo Habibah ta ce “ sannu! Bari na nemo miki ruwa masu sanyi” sai kuma ta shimfiɗe babyn wacce tuni ta koma baccinta. Kitchen ta nufa don samo ruwa masu sanyi,sai suka yi kiciɓis da Gwaggo Hajara ƴar kallon-kallon suka yi kowacce na hararen ƴar uwarta. “In tusa za ta iya hura wuta a yi mu gani mana,sai shegen kinibibi da nuna isa kan an san ɓoyayyar duniya nan kuma ba asss ” Gwaggo Hajara ta faɗa don kuwa a goshin Habibah ta fahimci sun karya wata muguntar tsafi. Ita kuwa Habibar murmushi ta yi don ta fahimci mi take nufi wato in ta isa ta yi wa kanta maganin damuwarta.“ Nan gishirinki zai ƙare a dafuwar ƙaho,yadda bacci ya bar ido haka za ki gaji ki bar Habibah saboda kabewar kan kabari nake baƙin cikin masu taushe” “Aikin banza sai aukin cika baki ,a hakan kuma na yi sanadin hana ki baccin kullum cikin kukan kin ƙi haihu ba” “Haihuwa ai ta Allah ce,kuma alhamdullah yanzu na samu irina wacce tsoron samun ta yasa kika jefo min mugun nufinki ” Habibah ta faɗa tana wani murmushi,Gwaggo Hajara ta kasa cewa komai yayin da ita kuma ta ci gaba da cewa “ ko ba ki gane abin da nake nufi ba? To Safeenatu ta haifi wata Habibar sak irina ce ko na ce ma ta fi ni don ita murucin kan dutse ce ba ta fito ba sai da ta shirya” muƙut! Gwaggo Hajara ta haɗiye wasu yawun tsoro don kuwa ta fi kowa sanin babyn Safeenatu ba normal jaririya ce ba tun da ta ga zahiri. Ta ja wani irin numfashi jin saukar ruwan sanyi kan fuskarta,dakyar ta ware ido tana kallon Habibah wacce tuni ta juya ta yi tafiyarta tamkar ba ita ce ta gama zuba mata ruwan a fuska ba.Cike da baƙin ciki ta koma ɗakinta,a yadda take jin jininta ya hau in ba jini ta sha ba ƙila zuciyarta sai ta buga.Tukunyar tsafinta ta ɗauko ta yi ƴan surkullenta kafin ta ɗauki mayafi ta fita waje,yara ta gani suna wasa daga inda take a tsaye ta soma kiran kurwar wani yaro cike da ƙwarewa wurin maita tsafi.Yaron ya dafe gefen wuyansa inda ya ji kamar an tsikare shi da allura amma bai bar wasar ba haka yake ci gaba da gudun yana son kamo wani,idonsa ne suka soma rufe wa kafin bugun zuciyarsa ya tsaya cak kawai sai ya faɗi ga ƙasa.Ita kuwa Gwaggo Hajara da wani mugun sauri ta rufe ƙofa,tuni yara sun fara ihu suna faman kiran sunansa. Ɗakinta ta koma ta ci gaba da tsotse jinin yaron ko jira ba ta yi ba,don ta san sarai in ta jinkirta ajiye kurwarsa Habibah za ta iya fahimtar haka.Tsawon lokaci ta ɗauka cikin siffar mugunta kafin ta dawo normal,zuciyarta ta ji fayau babu ƙunci.Tana nan zaune sai ga Munira wacce rabon ta da gidan tun lokacin da aka ce ta fita.Kusa da mahaifiyarta ta zauna ta soma bata labarin yadda yaron maƙwabciyarsu ya faɗi suna tsaka da wasa,“ je ki nemo min Munir ya dawo gida ” shi ne kawai abin da ta ce tana jin wani daɗi a ranta ba don komai ba sai don ta yi mugunta. Habibah na shiga ta miƙa wa Sakeenatu gorar ruwa mai sanyi haka ta shanye su tasss tana sauke ajiyar zuciya.“Ki dinga kula da kan ki mana,ko barin kai a buɗe ai yana sa maƙiya su yi galaba kanka” “To in sha Allah ” Sakeenatu ta faɗa tana mai ɗan satar kallon jaririyar ƙawarta,ido ɗaya babyn ta buɗe ita ma tana kallonta babu shiri Sakeenatu ta miƙe tsaye tana cewa “ Feenat zan tafi sai kuma gobe in sha Allah zan zo da safe tun da babu aiki” “Na gode sosai Keenat wai ina Ma'idah?” “Tana wurin Mama tun wancan satin na kai ta kin san Komandan ta zo” Safeenat ta waro ido ta ce “ ki ce dai a takure kuke yanzu,kai tsohuwar nan an yi ƴar masifa mine ne na zuwa hutu ke ba ƴar makaranta ba” Sakeenatu ta tuntsire da dariya ta ce “ kar a yi babu ita mana,duk gani take wasu kuɗi ne da shi ba ta san rabin hidimar gidan ni ke yi ba a haka kuma za ta dinga tsiro da abubuwa tana saka sharaɗin abin da take so” Safeenatu ta ce “ ah lalle ta ci sunan Komandan ɗin” nan dai suka yi sallama Sakeenatu ta fito.Kafin ta isa gida sai da ta saya wa Mamuh kifi don ta san tana son shi,da sallama ta shiga amma ta ƙi amsa mata sai ma tambaya da ta jefo mata “ daga gidan uban wa kike? Wato kin matsu na koma ƙauye shi ne kika je gidan malamai da bokaye a yi min asiri na tafi ban shirya ba” Jikin Sakeenatu banda rawa babu abin da yake yi,kanta ƙasa ta soma rantse-rantse tare da sanar da ita inda ta je. “Ita ƙawar taki ce ta baki magani kika yi wanka da shi ta yadda zan ji tsoron ki? Sakeena lalacewar taki har takai ki dinga faɗawa ƙawarki ƙarya da gaskiya akan ta baki magani? In maganin za ki nema mi yasa ba ki ce a baki na haihuwa ba sai na korar maƙiyiyarki” “Wallahi Mamuh babu wani magani da aka bani,na faɗa miki barka kawai na je” Keenat ta faɗa cikin muryar kuka. Mamuh ta tsure ta da ido,sam babu tabon duk muguntar da ta ajiye a jikin Sakeenatun komai ya rushe ta koma normal.Sannan a baccinta aka nuna mata ta yi wanka da ruwan magani duk mugun nufinta ya fita daga jikinta,jin shiru yasa Sakeenatu ta ɗago ido da zumar kallon Mamuh mugun ganin da ta yi ne yasa zuciyarta kusan faso allon ƙirjinta ta faɗo. Idon Mamuh sak irin na maciji yanayin fuskarta ma ya canza duk ta yi baƙi,“ in kin gama gulmar sai ki wuce ki ɗora min wake da shinkafa” Mamuh ta faɗa tare da yin gaba,Sakeenatu ta ce “ akwai sauran na ɗazu bari na zubo miki ” Ba tare da ta juyo ba ta ce “ ban so wani nake so ki dafa min” Jakarta ta ajiye ta shiga kitchen ta ɗora girkin,wannan karon ko waken ba ta wanke ba kamar yadda tsarin dafa shi ya zo mata daga Mamuh ɗin ,dama ita shinkafar ba irin wacce ake wankewa ce ba.Cikin plate ta zuba bayan ta tsalala mai dayawa,sai ta fito ta nufi ɗakin Mamuh da sallama ta shiga duk da ta san ba za ta amsa ba. Cike da ladabi ta duƙa har ƙasa ta miƙawa Mamuh plate ɗin wake da shinkafar amma ta ƙi karɓa sai ido da tsura mata.Tuni gaban Sakeenatu ya fara dukan uku-uku,“ ba zan ci ba!” “Amma ke kika ce na girka miki ” ta faɗa murya na rawa. “Tun zuwana gidan nan na faɗa miki sai an dirje wake an waken shi da hannu sannan ake girka min mi yasa yanzu ba ki yi ba?” “ Na zata kina jin yunwa ne sosai shi yasa na yi haka don na yi sauri” “To sai ki je ki sake dafa wani” Mamuh ta faɗa tana mai miƙe wa tsaye,cikin dakiyar zuciya Sakeenatu ta ajiye plate ɗin ta ce “ ki yi haƙuri Mamuh akwai aikin da nake son yi yanzu,ki ci wannan ɗin gobe in Allah ya kai mu sai na yi miki irin wanda kike so ɗin” Sam ko kaɗan Mamuh ba ta yi mamakin furucinta ba ,don dama da tsafi ne ta ci galaba har Sakeenatun ke mugun tsoronta yanzu kuma komai ya karye.Ita kuma tana gama faɗar haka ta fice,da ta fito har sai da ta ja ajiyar zuciya tana mamakin yadda yau ta cire tsoron Mamuh. Tana shiga wanka sai ta ga period ɗinta ya zo,wanda kuma ba komai ya haifar da haka ba sai gwagwarmayar fitar da sihirin jikinta.Cikin ƙananan kaya ta shirya sannan ta haye bed tare da kiran Abbas,cike da nishaɗi suka yi hirar soyayya nan ne kuma ya shaida mata gobe zai zo sannan a karɓo Ma'idah don ita yake son fara cin karo.Har ƙasan ranta ta ji daɗin furucinsa , wannan yasa suna gamawa ta kira can gidansu ta ce a kawo mata Ma'idar. Washegari Kuwa tun safe Sakeenatu ta soma gyaran gida ita da ƴar aikinta wacce ba za ta wuce shekara ashirin ba mai suna Fa'iza.Mamuh dai na ta kallonsu ba ta ce komai ba don fushi take da Sakeenatu,da kanta ta yi girki Fa'iza na kama mata. “Shi kuma waken nawa sai yaushe za a girka?” Mamuh ta leƙo kitchen ɗin tana mai faɗar haka. Sakeenatu ta ce “ yanzu zan yi” ba ta ƙara cewa komai ba ta tafi. “Fa'iza wanke min waken nan da kyau sai ki girka wa Komandan ban son ta kawo min cikas ina cikin farin ciki” Ƴar dariya Fa'iza ta yi kafin ta soma wanke waken kamar mai wankin kaya,ita ce ta girka shi kuma.Sakeenatu ta zuba a plate da kanta ta kai wa Mamuh jikinta har rawa yake ta soma ci tana lumshe idonta waɗanda tuni suka soma yin hasken nan.Ita dai Sakeenatu Allah na gani tsoron yanayin nan take ,da sauri ta wuce ɗakinta ta yi wanka ta shirya cikin wani rantsatsen less tana tsaka da fesa turare Ma'idah ta shigo da gudunta ta na kiran Ammyna.Ita ma sosai ta yi kewar yarinyar sai ta rungume abarta tana cewa “ ke da wa ne?” “Anty” ta bata amsa. A ɗan firgice Nafisa ta shigo tana cewa “ anty Sakeena wace ce waccan a kitchen? Zo ki ga abin da take” “Ƴar aikina ce lafiya?” “Zo dai ki gani” cewar Nafisar tana mai yin gaba Sakeenatu na take mata baya har suka shiga kitchen ɗin. Fa'iza suka tarar duk ta cire suturar jikinta tana fitar da wani nishi idonta a rufe suna tsiyayar da hawaye....... [25/09 à 08:09] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 24/09/24 6-7 Tamkar wacce ke wata mu'amala da namiji haka Fa'iza ke yi ,hankalin Sakeenatu in yayi dubu to ya watse.Ta kalli ƙanwarta ta ce “ Nafisa ko iskokai ne? Dubi abin da take yi” Nafisa ta ce “ anty Sakeena tun da nake ban taɓa ganin mai kalar iskokan nan ba,hatta masu aljanin soyayya ai sai in suna bacci ne suke zuwar musu dubi ita wannan fa tamkar idonta biyu fa” “Yanzu dai don Allah ki taimaka mata tun da ke Malama ce kin ga Ma'idah har ta soma kuka” cewar Sakeenatu tana mai jan ƴarta zuwa waje.Nafisa ta cika kofi da ruwa ta tofa ayatul ƙursiyu da amanar rasulu sannan ta shiga watsa ma Fa'iza ruwan,a sannu a hankali ta soma barin abin da take daga ƙarshe ta buɗe idonta waɗanda suka kaɗa suka yi ja.Nafisa ta shiga yi mata sannu kafin ta taimaka mata ta mayar da kayan jikinta,“ dama kina da aljanu?” Sakeenatu ta tambaya wacce ta dawo. Fa'iza ta girgiza kai,“ to tashi ki yi wanka sai ki zo ki zuba abinci ki ci” Da “ toh” ta amsa kafin ta fita zuwa Toilet ɗin tsakar gida kamar yadda Sakeenatu ta shaida mata da ita za ta dinga amfani. Wanka ta soma sai da ta saɓa jikinta har sau biyu sannan ta fito,wasu kayan Sakeenatu ta bata ta saka abincin ma da ta zuba gidansu ta wuce da shi. Su kuwa a falo suka zauna suna hira Nafisa na bai wa Ma'idah abinci a baki,Abbas yayi sallama da gudu ta nufe shi tana “ Daddyyy” ya caɓe ta tare da cira ta sama yana yi mata wasa haɗi da kai mata sumba. Cike da farin ciki ya ƙarasa ya zauna,Nafisa ta gaishe shi yayin da suke aikawa juna wani kallon so shi da Sakeenatu mai cike da kewa. “ Mu je ka fara yin wanka ko?” “A bani abinci tukuna don Allah ” ya faɗa yana wani murmushi,Ma'idah ta ce “ Daddy ni ma ina ci” sai aka zuba musu ya dinga bata a baki ita kuma sai surutu take yi masa.Suna tsaka da nishaɗinsu sai ga Mamuh ta fito,fuskar nan kicin-kicin,“ ita kuma wannan farar tinkiyar?” ta yi tambayar tana zunɗen Ma'idah wacce ta tsorata da ganin Mamuhn. “Ina wuni Mamuh? Fatan na same ku lafiya?” Abbas ya faɗa cike da ladabi. “Ka bani amsa ta” “Ma'idah ce fa ƴar wurin Keenat” ya bata amsa a sanyayye. “Shegiya za ka ce wacce ba a san taƙamaimai wane ne ubanta ba,kai da ka iya kwashe-kwashe ka rasa wacce za ka auro sai wadda ta gama yawon duniya ta tsiyayar da duk ƙwayaƙwayin haihuwarta a titi.To ban yarda ban lamunce wannan tinkiyar ta zauna a gidan nan ba” Mamuh ke faɗa cikin masifa ita kuwa Ma'idah tuni ta soma kuka musamman irin abin ban tsoron da take hangowa a fuskar Mamuh. Abbas ya sunne kai ya ce “ a dai yi haƙuri Mamuh dukkan bawa bai wuce jarabawa,Ma'idah ita yarinya ce ba ta san komai ba” “Wallahi sai ta bar gidan nan” Mamuh ta faɗa cikin ƙaraji, Sakeenatu kuwa banda kuka babu abin da take yi . Hannun Ma'idah ta kama da niyyar jawo ta,ita kuwa baiwar Allah cike da tsoro ta ɗauki cokali mai yatsu ta caka ma Mamuh ita a ido da zumar ceton kanta ga dodo. Wani uban ihu Mamuh ta yi tana cewa “wayyo idona! Ƴar daba ta kashe ni” jikin Abbas na rawa ya je ya kamo Mamuh wacce tuni idon ya soma fitar da jini,hankali tashe ya soma goge jinin wani na zubowa a doli ya kama ta zuwa asibiti. Bayan tafiyarsu ne Nafisa ta soma tofa ma Ma'idah addu'o'i saboda yadda take wani irin kuka tana firgita,cikin kuka Sakeenatu ta ce “ Nafisa ki ɗauke ta ku wuce gida don Allah” “Ke kuma a nan za ki zauna? ” “To ina zan je Nafisa? Haƙuri zan yi dama aure ya gaji haka sanin kan ki ne a can gidan ba wani jituwa muke ba ni da Mama ta ɗauki ƙiyayyar ɗan farin ta ɗora min” “To amma dai ki kula da kan ki,in kin ga abin ya yi yawa kawai ki tawo gida” Kuɗi ta basu sannan suka bar gidan,ita kuma ta ɗauki waya ta kira Abbas don jin asibitin da suke shi da Mamuh yana shaida mata ita ma ta fita ta je.Tuni Mamuhn ma ta yi bacci an naɗe idon nata da bandeji ga kuma ƙarin ruwa an saka mata. Jikinta a sanyayye ta ce “ ka yi haƙuri” Abbas ya kamo hannunta ya ce “ dama haka Allah ya tsara,ina Ma'idah?” “Nafisa ta koma da ita can gida” “Don me? Zan rarrashi Mamuh na san za ta amince ta zauna da mu” Ta sakar masa murmushi ta ce “ na gode sosai da kawaicinka gare ni” wani kallo yake aika mata yana mirza tafin hannunta,da ido ɗayan mai lafiya Mamuh ke kallonsu tana jin wani irin haushi da takaici. “Mine ne haka? A asibiti fa muke ka bari har mu koma gida” Sakeenatu ta faɗa tana janye jikinta daga nasa ganin abin zai wuce gona da iri. “Mu je gidan to tun da kin ga Mamuh ta samu bacci ,sai mu dawo daga baya” Abbas ya faɗa yana langwaɓar da kai saboda ba ƙaramar kewar ta yayi ba. “To ai na farka” cewar Mamuh tana mai tashi zaune haɗi da hararen Sakeenatu,da ɗan sauri ya miƙe yana tabayarta jiki.“ Ka kira likita ya cire min ƙarin ruwan nan sai mu wuce gidan tun da uwarka ba za ta barin ka cikin salama ba” cewar Mamuh a zafafe,Abbas ya fita don kiran likita. “Duk tsiyarki dai ba za ki iya canza ma tuwo suna ba,Abbasi ɗana ne ba naki ba don haka ni ke da iko da shi ba ke ba.Kuma wannan shegiyar taki sai ta san ni ta caka da cokali sai na shayar da ke mamaki” Da wani mugun sauri Sakeenatu ta je gaban Mamuh ta tsuguna ta ce “ don girman Allah Mamuh ki yi haƙuri , Ma'idah yarinya ce ba ta da wayo ko me za ki yi to ki yi min amma kar ki taɓa ƴata” ta ƙarashe maganar hawaye na zubo mata saboda zuwa yanzu ta yarda Mamuh muguwa ce. Kafin ta kai ga bata amsa Abbas ya shigo shi da likita,ya ce “ sai kin yi kwana uku sannan za mu sallamar ki” “To ka sanar da uwarmu wacce ta matsa mu je gida” Mamuh ta faɗa a zuciye tana hararen Sakeenatu. Likitan yayi murmushi ya ce “ yanzu yadda za a yi sai ka nemo wacce za ta zauna da Mama,amma gaskiya ba za mu sallame ta ba yau” sai yayi wa Mamuh allurar bacci,duk yadda masifa ke cin ta haka ta haƙura saboda ƙarfin allurar. Shi kuwa Abbas Gwaggonsa ya kira wacce ke nan Damagaram ita ke bi ma Mamuh,babu jimawa kuwa ta zo .Ya ja matarsa zuwa gida,cike da zallar soyayya suka gamsar da junansu. SAFEENATU Tun bayan da kowa ya watse aka bar su ita da Gwaggo Habibah sai ta nutsu sosai kafin ta ce “ Gwoggo ni kam ɗazu wani abin ban mamaki ya faru,maciji na gani ya naɗe Baby girl ɗin nan ina yin ihu ya ɓace kamar aljani ” Gwaggo Habibah ta yi murmushi ta ce “ kar ki wani ji tsoro,sannan ina so ki kwantar da hankalinki duk wani abu da za ki gani ki yi shiru da bakinki.Duk kusan ƴan biyu suna da wannan baiwar,to ke macen ce ke da shi don haka ki shirya ganin abubuwa iri-iri wasu na tsoro wasu kuma na almara” Safeenat ta ja wani numfashi kafin ta ce “ to Allah cire min tsoron” ba ta ida rufe bakinta ba hasken ɗakin ya ɗauke duhu ya turnuƙe shi kai ka ce dare ya tsala.Duk tsit suka yi babu wanda ya ce wani abu,sai kukan jaririyar da ya soma tashi sannu a hankali tsawon minti biyu kafin ta yi shiru.Hasken ɗakin na dawowa Safeenatu da Gwoggo Habibah suka yi ƴar rige-rigen ɗaukar babyn duk suka yi tsaye suna kallon yadda goshinta ke fitar da wani haske yana ƙyalli a gaban idonsu ya ɗauke sai ga shatun haƙoran maciji ya bayyana raɗau .Safeenat ta kai hannu ta shafi wurin sai kuma ya ɓace,ta ja ajiyar zuciya tana mai ɗaukar jaririyar ta soma shayar da ita. Daddy ya yi sallama ya shigo,duk suka gaishe shi kafin a basa babys ɗin ya gani.Sosai yayi musu addu'a sannan ya fita,haka suka ci gaba da yin hirarsu har dare ya tsala.Duk sun yi shirin bacci za su kwanta amma ita Baby kamar ɗiyar aljanu ta ƙi baccin sai ma wani kuka-kuka da take yi. “Safeenat ki bata abincinta mana” Gwaggo Habibah ta faɗa tana shirin tashi ta kunna wuta. “Ina ta ƙoƙarin bata ta ƙi karɓa” cewar Safeenar. Kusa da ita ta zauna tana shirin ɗaukar babyn sai ta lura da yadda hannunta na hagu ke fitar da wani zane mai hasken wuta kamar ta murhu.Wani irin murmushi ne ya suɓuce wa Gwaggo Habibah ba tare da ta shirya ba cike da murna ta jawo hannun jaririyar ta riƙe sannu a hankali har zanen ya fito raɗam letter M ta fito sai a lokacin kuma jaririyar ta yi shiru sai ajiyar zuciya da take saukewa. A ɗan ruɗe Safeenatu ta ce “Gwaggo mine ne kuma wannan?” Sam Gwoggo Habibah ba ta bata amsa ba sai safar hannu da ta je ta binciko cikin kayansu ta saka wa hannun mai zane.“Daga yau kar ki ƙara barin hannunta a buɗe ki dinga saka mata safar hannu ” “Gwaggo ina tambayar ki mine ne ba ki bani amsa ba” “Alama ce ta prophétie/prophecy,da yawan ƴan baiwa tana soma aiki ne in sun kai shekara sha takwas amma ke yarinyarki tun farkon dirowar ta duniya tata baiwar ta fara aiki.Ta ceci ɗan uwan tawaicinta sannan kuma ta ceci ƙawarki Sakeenatu ” Ba don ta fahimci zancen da kyau ba ta ce” mi ya samu Keenat ɗin?” “An yi mata ajiya cikin ruhinta ta yadda esprit zai samu damar yin yanda ya so da gangar jikinta har ya cutar da ita” “Ya aka yi kika sani to?” “Safeenatu yi bacci in lokacin fahimtarki yayi babu buƙatar ki yi tambaya” Da wannan duk suka yi bacci, Safeenatu na tsaka da yin mafarki akan goben ƴarta Gwaggo Habibah ta tashe ta daga bacci.“Ruwan wankan ki na can toilet ta tsakar gida,ki je yi wankan sabulu kafin na zo na gasa miki jikinki da towel” Ta yi miƙa ta tashi a gajiye saboda kwana dare ta yi tana shayarwa,sai da ta ɗauki wani zane da hijabi sannan ta fita ta bar Gwaggo Habibah za ta yi wa Twins wanka. Sakeenatu na fitowa suka yi kiciɓis da Gwoggo Hajara ta gaishe ta sannan ta wuce toilet.Ita kuwa tsabar mugunta yasa ta koma ɗakinta ta yo shirin mugunta yau ma siffar tsakaka ta ɗauka ta yi tsinke can toilet inda Safeenatu ke wanka tun tuni.Da ga can saman katanga Gwaggo Hajara ke ƙarewa surar Safeenat kallo,cikin salon mugunta ta mayar da harshenta dogo sannan ta zuro shi tun daga can sama har ƙasa yana taɓa tile. Safeenatu ta yi wani ihu wanda bai sauka ko ina ba sai cikin kunnen ƴarta jaririya,kwacaaaa Gwaggo Hajara ta faɗo cikin ƙatuwar robar tafasasshin ruwan zafi....... Ga masu son fara yin payment su yi min magana ta lambata na basu detail na sabon account number da za a tura kuɗin ba waccan na Ecobank ba.DM +22795045822 [25/09 à 09:17] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 25/09/24 8 Da wani mugun sauri Safeenatu ta yi tsalle ta koma jikin ƙofa tana kyarma ,idonta ƙur cikin robar wacce tsakakar ke ta ƙoƙarin fitowa daga ruwan .Ganin ta soma yin girma sosai yasa Safeenatu ta buɗe sakatar toilet ɗin zane a hannu ta fito Allah yayi sa'a babu kowa a tsakar gidan,dakyar ta yi ɗaurin ƙirji kafin ta nufi can ciki da gudu. “Ke lafiyar ki?” Gwaggo Habibah ta yi tambayar . Feenat ta dafe gefen zuciyarta da yake mugun bugawa ta ce “ tsaka...ka ce ta faɗa cikin ruwan da nake wanka” “Shi ne kike wannan haƙin? Kai Allah ya shirya min ke ban san lokacin da za ki girma ba” “Gwaggo ba normal tsakaka da kika sani ba ce, wannan ƙatuwa ce inda kin ga yadda halshenta ke da tsayi ya fi pampo fa” Shiru Gwaggo Habibah ta yi tana kallon Baby girl don kuwa a gaban idonta da tana yi mata wanka wani mugun haske ya fita goshinta tamkar an jefa kibiya. “Allah ni dai ba zan sake shiga toilet ɗin waje ba ƙila ma aljani ne” muryar Safeenatu ta katse mata ɗan guntun tunaninta. “Bari na je na gani ” cewar Gwoggo Habibah kafin ta miƙe ta fita zuwa Toilet ɗin tsakar gida,tun kafin ta ƙarasa ciki take jin nishin wahala . Ido huɗu suka yi da Gwaggo Hajara wacce zuwa yanzu tuni ta galabaita ta yi wani tsamo-tsamo cikin ruwan zafin ta kasa fita . Gwaggo Habibah ta yi wani murmushi tana kallon yadda ruwan suka yi baƙi tsabar yadda muguntar da ta shiryo ma Safeenatu ba ƙarama ba ce. “Ƙarshen alawa ƙasa! Yanzu wa gari ya waya? Shi dama ramen mugunta an ce ka gina gajere in kuma ka gina dogo kai za ka faɗa .Ai wallahi ba zan taimaka miki ba sai dai ki dawwama a ruwan zafin nan,in kuma kin ga na taɓa robar nan to wallahi cikin masai ne zan zubar da ku ke da ruwan” Gwaggo Habibah ta faɗa tana wani murmushin jin daɗi. Kamar daga sama tsakaka ta soma magana wacce ta kasance Gwaggo Hajara ,“ ki taimaka min Habibah na yi miki alƙawarin daga yau na zubar da makaman yaƙi” “Kar ma ki zubar ki yi ta riƙon su har sai Mahadi ya bayyana,ba dai maita ita ce jarinki ba? Ki ci gaba da yi wata rana mutuwarki za ki ci” tana gama faɗar haka ta fito daga toilet ɗin,sai kuma ta tuna duk wanda ya mutu a ruwa yayi shahada da sauri ta koma ba tare da ta ce komai ba ta ɗauko robar ta fito da ita tsakar gida tare da juye ruwan ga ƙasa. Tamkar acid haka turɓayar ta soma yin bori tana fitar da kumfa tsabar bala'in da ke tattare da ruwan,a kunyace Gwoggo Hajara tsakaka ta soma jan ciki ta nufi hanyar ɗaki. Ita kuwa Gwaggo Habibah ji ta yi kamar ta sa ƙafa ta laɓe shegiya kowa ya huta.Tana komawa ciki ta cewa Safeenatu “Ki shiga toilet to kafin na juye ruwan yi miki wankan” sai kuma ta fita ta ciko ƙaton bokiti da ruwan zafi,da ɗan ƙaramin towel ta soma yi wa Safeenatu wankan jego ita kuma tana ihu kamar wata ƙaramar yarinya. Macijin jiya ne ya sake bayyana a jikin macen yana wani naɗe jikinta,ita kuma ta buɗe ido taram tana kallonsa kamar mai wayo.Tsawon lokaci ya ɗauka tare da ita yana yi mata wasa kafin ɓace jin motsin su Safeenatu za su fito.Gefen gado ta zauna ta soma shayar da yaran kafin ta kimtsa cikin riga da zane,sai da Gwaggo Habibah ta gama wanka ita ma ta fito ta shirya sannan ta je ta kawo masu abinci suka ci daga nan suka wuce asibiti bayan sun karɓi kuɗi wurin Daddy.Lafiyarta da ta babys aka duba kafin su dawo gida,tuni kuma ƴan Barka suka fara zuwa in waɗannan sun fita wasu sai su shigo. SAKEENATU Tana rungume jikin Abbas ta ce “ Yau tana ɗaya daga cikin ranakun ovulation ɗina,yau na gama period ” cikin tsokana ya ce “ period ɗin ɗaya rana ” ta ja hancinsa ta ce “ eh na dai ji,inda ina jimawa kafin ta ɗauke ai da yanzu ba ka kasance da ni ba don jiya ne na gan ta” Ya gyara mata kwanciya kan ƙirjin nasa yana mai cewa “ Keent don Allah ki dinga bin Mamuh a hankali kin san ta tsufa,ban so kina yin abin da zai ɓata ranta ki guji ɓata mata don farincikina.Ina yi miki wani mugun so ne wanda na san ke ko rabin shi ba ki yi min” “To in sha Allah na yi ma alƙawari zan kiyaye,ai Ma'idar ma an tafi da ita” “A'a za ta dawo,sanin kan ki ne yadda nake mugun sonta ba zan iya yin nesa da ita ba” Wani daɗi ne ya luluɓe zuciyar Sakeenatu,ita ce shaida kan son da yake yi wa ƴarta duk da ta fito ba ta hanyar aure ba.Za ta iya cewa halarcin bai nuna mata ƙyama ba ne ya ɗunguza ta ga aurensa,soyayyarsa ma ba ta jima da samun gurbi a zuciyarta ba. “Ina son ki Keenat!” furucinsa ya katse mata tunani,ta yi murmushi mai ɗan sauti ta ce “ na gode” “Ke ba za ki faɗa kina sona ba? Keenat sai yaushe zan ji furicin so daga bakinki?” Ta laƙace masa hanci ta ce “ sai ranar da na haifo ma kyakkyawan Prince mai kama da kai” sai kuma ta miƙe ta je ta shiga toilet,shower ta sakarwa kanta tana tunanin saurayinta mahaifin Ma'idah.Ruwan hawayenta haɗi da na pampo suka haɗu wuri ɗaya suna zuba.Daga bayanta ta ji an rungume ta,da sauri ta juyo suna fuskantar juna kallo guda yayi mata ya hango damuwa a shimfiɗe a ƙwayar idonta.Zuciyarsa kuma ta basa ta yi kuka,bai tsaya tambayar ta ba ya ɗora bakinsa kan nata a wannan rana a kuma daidai lokacin nan Abbas ya shayar da ita zumar ƙauna mai haɗe da yayafin kalaman soyayya masu nuni da sadaukarwa.Ba tare da ta shirya ba ta ce “ I love You Abbas!” numfashinsa ne ya kusan tsaya wa tsabar murna da farin ciki,kamar wani ƙaramin yaro ya soma yi mata kuka saboda kawai ta ce tana sonsa. Shi yayi musu wanka ya shirya su,a ranar a gida ya ja su sallah har ta isha'i .Bayan sun salamce sun yi dogayen addu'o'i ya dube ta da kyau ya ce “ Keenat fatan bayan tafiyata duk salloli kin yi su kan lokaci kuma kin tsare su?” Da sauri ta sunne kai ba tare da ta basa amsa ba,yatsun ƙafarta ya soma ja mata tare da soma yi mata nasihar da ya saba game da mai wasa da sallah a ƙarshe yake cewa “ in kuma na ga kin ƙi yi zan kawo miki ƙanwa ustaziya” a shagwaɓe ta faɗa jikinsa ta ce “ to ai ina yi ko” “Kina yi ko za ki dinga yi?” “Duka biyun! Ba za ka koma asibiti ba?” “Tare za mu koma tashi ki shirya” da “ to” ta amsa kafin ta canza kaya suka fito,sai da ya tsaya ya saya musu fruits sannan suka isa asibitin.Da sallama suka shiga ɗakin Gwaggo Rahamu ce ta amsa yayin da Mamuh ta juya musu baya tana jin wani irin baƙin ciki ya turnuƙe ta saboda a yadda ta gansu cikin farin ciki suna nishaɗi ta san sun keɓe da junansu.Abbas ya ƙarasa yana mai cewa “ Mamuh ya jikin naki?” “Ka damu da ni ne ka sa ƙafa ka yi tafiyar ka? Wato Abbasi matarka ta fi ni ko?” ta faɗa cike da masifa tana juyowa. “Ki yi haƙuri Mamuh Allah dai ya baki lafiya ” ya faɗa kansa ƙasa. Tsabar fitina ta Mamuh sai cewa ta yi “ ina wakena?” Abbas ya ɗago da sauri yana kallon ta yana mai cewa “ wane irin wake kuma Mamuh yanzu da daren nan? Ga ayaba nan da lemu da apple na sayo ” “Na yi da kai na ce ka sayo? Ita waccar abar ai ta san wake nake ci mi yasa ba ta dafo ba?” “Yi haƙuri Mamuh gobe sai a daf....” bai rufe baki ba Mamuh ta saka kuka yana cewa “ shinenan tun da mata ta fi uwa” Da mugun sauri Sakeenatu ta ce “ bari na koma gida sai na dafo mata” Abbas ya ce “ to ki yi sauri” ta yi tunanin shi zai kai ta amma sai kuɗin ɗan sawu ya bata,tana zaune tana hawaye har suka iso gida ta biya shi kuɗin kafin ta wuce ciki. A gaggauce ta soma aikin tana mita “ an yi tsohuwa kamar mayya kullum wake yanzu nan in ban wanke shi ba sai ta sani mtsww ” ta ja tsuki tana dirje waken amma jin ita ma an ja mata tsuki yasa ta zabura tana dube-dube sai dai babu kowa.Watsar da tunanin ta yi ta ci gaba da aikinta wani tsukin ta kuma ji sannan ana magana ƙus-ƙus,gabanta ya faɗi jin tamkar ana tafiya cikin falo.Tana shirin fitowa aka ɗauke wuta,lalubo ta soma yi cikin duhu ko Allah yasa ta ɗauko wayarta ta kuwa yi sa'a ta samu jakarta hannunta har rawa yake ta zuge zip ta ciro wayar sai ta ga saura ƙiris batirin ya mutu alhalin a cike ta bar ta.Tana ƙoƙarin ganin ta kunna fitilar ta ji tamkar saukar huci kusa da ita,ta wani juyo da sauri ta inda take jin abin tare da haska hasken screen babu kowa sai ƙafafuwan ƙofato da ta yi arba da su babu kuma gangar jiki....... My book is only 500 via 6042551755 Hassana ibrahim Keystone bank,DM +22795045822 [26/09 à 08:25] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 26/09/24 9 Babu shiri Sakeenatu ta saki wayar ta arta a guje,sai dai ta nemi ƙofar fita ta rasa saboda mugun duhun da ya mamaye gidan baki ɗaya.Cikin ƙanƙanan lokaci duk ta firgice,dakyar ta iya samu ta fito tsakar gida da lalabe zuciyarta sai ƙara tsananta gudu Waige-waige ta fara sai ta ga ashe kaf unguwar ne babu wuta,ba ta gama daidaita numfashinta ba wata baƙar mage baƙa ƙirin ta soma yin kuka miyau!miyau! Kukanta duk ya cika gidan. Ta ɗaga kai dakyar ta dubi inda sautin kukan ke fitowa,ido huɗu suka yi da magen wacce hasken idonta yake kamar na lantarki sai canza kaza suke.A hankali ta sauko daga katangar ta soma nufo inda Sakeenatu ke tsaye da gajiyayun ƙafafunta,Allah ya gani ba ta wani ba wai karatun addini muhimmanci ba dukkan lokacinta da hazaƙarta ta zuba su ne a harakar boko wannan ya sa ba ta iya wasu addu'o'i ba .A halin yanzu da take tsaye ta yarda kuma ta aminta rayuwarta na cikin haɗari,tabbas ta san wannan magen ba normal ba ce muguwa ce cutar da ita za ta yi. Ta na dab da ta kawo kusa da ita ta samu bakinta na furta “ la haula wala ƙuwata illa billah!!!” ƙiiii magen ta wani ci burki tana mai canza salon kuka zuwa na jarirai amma sam Sakeenatu ba ta yi gigin yin shiru da bakinta ba sai ma ƙaimi da ta fara wurin maimaita addu'ar.A gaban idonta magen ta soma mayar da idonta kamar na mutane kafin ta ruga a guje ta yi tsalle ɗaya ta haye katanga,daidai nan kuma aka maido wuta yaran unguwa suka hau ihun murna.Sakeenatu ta ja ajiyar zuciya tana mai yin hamdala ga Ubangiji,bakinta bai gushe ba yana ta furta lahaula wala ƙuwata illa billah a haka ta koma can ciki.Gas ɗin ta kashe saboda muguwar gajiya da ta saukar mata wacce ba ta san dalili ba,wayarta ta ɗauka Allah yayi sa'a babu abin da ya same ta abun mamaki kuma yanzu cajin wayar a cike yake saɓnin ɗazu da aka nuna mata ta kusa mutuwa. Lambar Nafisa ta kira,tana ɗauka babu wani tsaya wa gaisuwa ta ce “ Nafi ki turo min karatun nan da kike saurare don Allah duk dare” “Anty Sakeena lafiyar ki kuwa?” “Ki turo min karatun dai don Allah ina son saurare ” “Ok to bari na hauda data yanzu zan turo miki” “Yawwa ina jira” ta faɗa tare da kashe kiran,ita ma datar ta kunna babu jimawa kuwa karatun ya shigo suratul Baƙara ce ta turo mata sai Yasin .Tamkar abun tsiya network ɗin ya ɗauke ɗif ko ɗaya babu wanda ya buɗe,juyin duniya ta yi amma sun ƙi buɗewa har wayar ta kashe ta kunna amma network ɗin ya ƙi yi.Cike da damuwa ta sake kiran wayar ƙanwarta,tana ɗauka sai ta rasa abin da za ta ce mata kawai ta fashe da kuka.Daga can ɓangaren Nafisa ta ce “ subahanallah! Anty Sakeena don Allah mike faruwa? Mike damun ki?” Cikin muryar kuka take cewa “ Nafisa tsoro nake ji! A tsorace nake ji nake kamar ba ni ɗaya ba ce cikin gidan nan tamkar ina ....inaaa” ta kasa ida maganar saboda motsin da ta gani ana yi can cikin labule wanda ta tabbata kuma ba ɓera ne ba saboda girman halittar.Ihu ta fasa ganin ƙatuwar gafiya ta faɗo timmm da ƙasa,yayin da kuma wata ta biyu ita ma ta sake fitowa a guje ya kama waccan wacce ta faɗo a gaban idonta suka soma faɗa suna cizon junansu.Babu shiri Sakeenatu ta haye ɗaram kan bed ta na kuka,Nafisa na jin haka ta ziri hijabi ta fito ko Mamarsu ba ta sanar ma ba ta fito ta samu ɗan sahu.Allah yayi sa'a ba wani nisa ne sosai a tsakaninsu ba,da gudu ta shigo gidan tana ambaton sunan Allah daidai nan gafiyoyin suka yi ɓatan dabo hatta. Nafisa ta je ta rungume ƴar uwarta wacce da ace tana da cutar asuma da tuni numfashinta ya fita,“ yi shiru don Allah ya isa yi min bayanin mike faruwa? Ina shi Abbas ɗin?” “Yana asibiti wurin Mamuh,na dawo na dafa mata wake da shinkafa ne shi ne ake ta firgita ni” nan ta kwashe duk abin da ya faru ta shaida wa ƙanwarta. Nafisa ta ja dogon numfashi bayan ta saurare ta,sannan ta ce “ wannan duk sharrin miyagu ne shi yasa a kullum ake son bawa ya keɓe wani lokaci don nemawa kansa kariyar ruhi da gangar jiki ba wai gyaran duniyarka ba kawai.Ni wallahi na fara zargin Mamuh ɗin nan,kina dai ganin yadda Ma'idah ta caka mata cokali da dukkan alamu ta hango abin da idanunmu basu gani.In ba masifa ba cikin daren nan za ki dafa mata wake kamar mayya,ke ƙila ma ita ce.Tashi mu je ki yi alwala ai zama bai gan ki ba tun da kin ji kin gani aure a inda ba a ƙaunar ki” Da taimakon Nafisa ta yo alwala dama ita Nafisar kusan kowanne lokaci tana da alwala mace ce mai riƙo da addini ba ta da sake,hasali ma malamar makaranta ce a wata islamiyya. Karatun Alkur'ani ta soma koya wa Sakeenatu kamar wata ƴar yarinya haka take biyawa inda ta yi kuskure kuma ta gyara mata. “ Ki kasance kullum cikin tsarki bima'ana alwala saboda tana da muhimmanci sosai wurin bada kariya,ko sheɗanu suna shakkar mutum mai zama da alwala a koyaushe,ke ko period kike to ki yi abarki sannan ki riƙe azkhar na safe da maraice” “Amma ai kin san ban iya su ba ko?” “Ki koya mana anty Sakeena ,shi ilimi ai bai da ƙa'ida shekaru ko tsoho ɗan shekara ɗari zai iya shiga makaranta ballantana ke da ko talatin ba ki kai ba” “ Ni rubutun larabcin ne ke bani wuya ” “Zan nemo miki littafi mai fassarar Hausa ,sai na dinga koya miki yanzu bari na tura miki app ɗin Alkur'ani sai ki dinga saurare ” Ta karɓi wayarta ta tura mata tare da saita mata komai ta kunna sautin ya soma tashi,ta ce “ to ni zan tafi gida ko Mama ban sanar ma ba” “ Don Allah Nafisa kar ki tafi ki bar ni ki jira har Abbas ya dawo,bari na kira Mamar na shaida mata” haka suka yi kuwa,tun suna jiran Abbas har ƙarfe sha biyun dare bai zo ba a tare suka fito suka rufe gida da ko ina sannan suka je suka kwanta. A can asibiti kuwa bayan fitar Sakeenatu,Gwaggo Rahamu ta yi wani kishingiɗa ga kujera kamar mai bacci nan kuwa ruhinta ne ta soma fitar wa daga gangar jikinta.Sawun Sakeenatu ta bi,hasali ma ta rige ta zuwa gidan duk abin da take yi akan idonta hanyar farko da ta soma bi shi ne tafiya ta shiga tunanin mai kula da nepa na unguwar ya ɗauke wuta ba tare da shi kansa ya san dalili ba a cikin wannan duhun ne ta yi ta yi wa Sakeenatu mugunta.Da ta koro ta da addu'a shine ta biya wurin wasu miyagun ƙawayenta ta basu address suka je a siffar gafiya,su ma ba su bar gidan ba sai zuwan Nafisa. Abbas na daga can gefe Mamuh na yi masa hira tana murmushi saboda duk abin da ke faruwa ita tana gani saɓanin shi Abbas ɗin.Bayyanar esprits biyun yasa yanayin shaƙar iskan ɗakin ta sauya saboda tsabar muguntar su, wannan karon hatta Abbas sai da ya ji wani iri.Har yanzu Gwoggo Rahamu ba ta farka daga baccin ƙaryar da take ba,cikin hirarsu ta ƴan duniyar ɓoye suke bata labarin yadda suka firgita Sakeenatu tana ta yin kuka. “Na gode sosai ƙawayena,kar ku manta in kun gama yawon Maitar dare ku biyo ta nan mu sake komawa mu uku mu haɗa ƙarfi mu shayar da ita mamaki” baƙin ruhin Gwaggo Rahamu ya faɗa ,suka yi dariyar mugunta tare da ɗaukar mata alƙawari kafin su bar wurin.Cikin ƙwarewa ta dawo da ruhinta a gangar jikinta,ta dubi Abbas tana mai cewa “ bacci ya ɗauke ni duk yau ban rintsa ba,ina sauran waken ni ma na ci yunwa nake ji” Shi Abbas sam ya manta da wani zancen wake saboda yadda Mamuh ke masa hira,sai yanzu ya tuna Sakeenatu ta je gida dafawa.Da ya duba agogon hannunsa ransa ne yayi mugun ɓaci,“ uwar tamu ai ba ta dafo ba tana can tana gantalin da ta saba,ah to dama su likitoci ba su da kamun kai tsakaninsu da abokan aikinsu suke neman juna in aka ce miki tana can asibiti wani ƙato ya taushe kar ki yi gardama” Mamuh ta faɗa ,yayin da Gwaggo ta karɓe “ i sosai ita ma wannan shegiyarta ta ai shugabansu ne ya ɗirka mata cikin ya bar yaronmu da wahala,wai Abbasi wai ya ƙaƙaba maka aurenta?” Kasa cewa komai yayi,haushi goma da gomiya tara ya rasa da wane zai ji abin ka kuma da zuciyar namiji sai ya ji zargi ya ɗarsu a ransa.Da ya nuna zai je gida Mamuh ta hana shi tafiya ta hanyar amfani da tsafinta,haka suka dinga kwaso sharri iri-iri suna yaɓa ma Sakeenatu sosai kuma suke samun gurbi a zuciyarsa.Can waje ya koma ya kwanta kan wani banci yana ta tunanin rayuwa baya yadda neman aurensa ya kasance yadda sam Sakeenatu ba ta samu shaidar ƙwarai ba ga mutanen unguwa amma ya rumtse ido ya ce sai ita . Ƙarfe biyu da rabi na dare ƙawayen Gwaggo Rahamu suka biyo mata,kafin su yi tsinke gidan Sakeenatu.Sai da suka shiga kitchen suka cinye kaf abincin da ta dafa sannan suka dawo falo suka fara shawarar abin da za su yi mata,suna dariyar mugunta suka tura ƙofar falon sai dai da zarar sun yi niyyar ɗora ƙafarsu a tile ɗin bedroom sai su ji tamkar cikin garwashin wuta ne suke ɗora su.Gwaggo Rahamu ta ƙanƙance ido tana kallon gefen Nafisa inda kusan kanta ta ɗora wayarta ne sautin karatun Alqur'ani na tashi a hankali wanda ba ma a jinsa sosai,kamar ta san suna nan kuwa sai ta kai hannu ta ƙara volume a tare suka saki wani ihu wanda sai da gidan ya girgiza a firgice Sakeenatu ta farka tana zarar ido My book is only 500 via 6042551755 Hassana ibrahim Keystone bank DM +22795045822 [28/09 à 08:36] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 28/09/24 10 A wahalce Gwaggo Hajara ke bin bango don isa ɗakinta,fatar nan tata ta tsakaka duk ta yi wani taushi ta fara fitar da wani fanko.A yadda bango ke zuzar fatar cikinta ji take kamar ta yi ta ƙurma ihu sai dai ba dama sata lahira! Tana isa ɗakinta ta ɗauki siffa ta mutum nan ne fa ta yi tozali da yadda duk jikinta ya kumbura yayi ja kamar wacce aka soya,mai ta ɗauko ta shafe jikinta da shi tana matsar ƙwalla tare da jin tsanar Safeenatu na sake feso mata daga can ƙasan zuciyarta. A fili ta furta “ sai na wulaƙanta rayuwarki,sai na saka kin tozarta a duniya,sai na shayar da ke gubar azaba wacce sai kin gwammaci mutuwa akan rayuwarki. Ke kan ki Habibah ba zan bar ki ba zan ɗora miki karatu da alamu har yanzu ba ki ji jiki ba shi yasa kike taimaka wa wata wurin ruguje plan ɗina” shiru ta yi jin an turo ƙofa.Daddy ne ya shigo da sallama a bakinsa,ba ta amsa ba sai ma saurin jawo hijabi da ta yi ta saka duk ta luluɓe jikinta. “Ni kam Hajara lafiya kike? Kin ga yadda fuskarki ta yi suntum sai huci take kamar ƙullun wainar da ya ji yis?” Daddy ya faɗa yana ƙare mata kallo.Wani ƙululun baƙin ciki ne ya ƙara turnuƙe Hajara ta ce “ uwar waina ce....” ba ta ida kai aya ba ta ji yatsun Daddy biyar kan kuncinta,shaye da mamaki take kallonsa nan ta hango wani baƙin tauraro tsakiyar goshinsa wanda ko shakka babu aikin Habiba ne ta tura masa shi. Ba ta gama dawowa daga duniyar mamakin da ta je ba Daddy ya soma magana cikin masifa,“ wato abun naki ya fara zama iskanci,daga tambaya shine za ki zagin uwata saboda kin san yau za ta zo.To tsaya ki ji Hajara duk wata tijararki ki tattara ta ki ajiye wuri guda muddin Hajiya ta koma da baƙin cikinki gida to wallahi akan aurenki.Ki tashi ki ɗora girki tsabar lalaci muna da mai jego a gida amma kin zo kin shige ɗaki kin haye gado tare da saka hijabi kamar matar liman kowacce za ta yi aikin ƙwarai” yana gama faɗa ya nufi ƙofa,sai kuma ya juyo ya ce “ Murjanatu na kan hanya sai ki fara shirin tarben ta” kawai ya fice. Gwaggo Habibah da ke zaune kan kujera a falo ta saki wani irin murmushin nasara,tun da uwarta ta haife ta yau ce ranar farko da ta juya taurarinta na baiwa ta yi aiki da su.Tun bayan da ta yi wa Twins wanka ta shirya su sannan ta bai wa uwarsu abin da za ta ci kawai ta fito falo ta zauna,Daddy na fitowa ta soma yi masa transfer ɗin tauraron ta hanyar kallonsa tsakiyar ido da farko har ya tambaye ta lafiya sai kuma yayi shiru jin sabon abu a tattare da shi. Duk abin da yake faɗa wa Gwaggo Hajara sarai ta ji alamun aikinta yayi kyau,ta saki murmushin nasara tana mai cewa ‘ mijinki zai zame miki kumurci,da haka zan raunata muguwar zuciyarki’ “Habibah karɓi wannan ko kuna da buƙatar wani abu sai a ɗauka ciki” Daddy ya faɗa yana mai katse mata tunanin zuci.Ta karɓa tana mai cewa “ Yaya Ɗayyabu na ce bayan biki sai Safeenatu ta koma can gida wurin Hajiya ko?” “Saboda me? Ba a nan za ki zauna ba?” “Eh to ni ma da haka na ce ɗin amma sai na ga kamar anty Hajara ba ta son zamana tun da na zo idonta kamar za su faɗo tsabar yadda take jifana da mugun kallo” Ran daɗi ya ɓace, yanayin fuskarsa ya canza tuni tauraron goshinsa ya ƙara yin baƙi ba tare da ya ce komai ba ya ƙara komawa ɗakin Gwaggo Hajara ita kuwa Habibah har da wata dariyar mugunta ta yi tare da tashi tana taka rawar murna. Daddy na shiga ɗaki ya yi wa Hajara wankin babban bargo,ko ina ana jin muryarsa yadda yake yi mata masifa in ta je yin magana kuma sai ya gwaɓe bakin.Da wannan baƙin cikin ya fita ya bar ta,sai da ta sha kuka wiwi sannan ta fito ta ɗora girki babu jimawa kuwa sai ga Hajiya ta zo .A ladabce Gwoggo Hajara ta gaishe ta wanda sosai ita hajiyar ta yi mamaki don rabon da ta yi mata irin wannan ladabin tun ranar da Ɗayyabu ya kawo mata ita a matsayin matar da zai aura.Cikin sakin fuska ta amsa tare da cewa “ to barkarmu Safeena an sauka Allah raya kan sunnah,kin samu mai taya ki aiki da kuma miji” Hajiya ta faɗa tana murmushi a doli ita ma ta yi murmushin yaƙen a can ƙasar zuciyarta tana cewa ‘ an haifo mana masifa dai aljanar jaririya muguwa wacce ta yi gadon jaraba ’ “Zan shiga daga ciki” hajiyar ta faɗa tare da nufar ɗakin Safeenatu,cike da murna ta zauna tana kallon jariran Gwaggo Habibah ta ɗauki namijin ta bai wa Hajiya ta karɓa tana mai kai masa sumba haɗi da yi masa addu'a sannan ta miƙa shi.Ana ɗora mata macen jikin Hajiya ya ɗau kyarma kamar mazari,murya na ɗan rawa ta ce “ wane suna za a saka musu?” “Basheer da Baseerat ” Habibah ta bata amsa tana murmushi tana kallon mahaifiyarta wacce kambun muguntar Gwaggo Hajara duk ya dabaibaye ta yanzu kuma ya fara barazanar tarwatsewa. Hajiya ta ce “ karɓar ta” tana mai miƙo Baseerat don ruhinta ya soma yin rauni, Habibah ta ce “ Hajiya don Allah ki riƙe t...” ba ta kai ƙarshe ba Hajiya ta miƙe ta je ta shimfiɗe Baseerat a shimfiɗa,sai aka yi rashin sa'a safar da aka saka ma hannunta na hagu ta fita wani mugun haske ya fito ya shiga ƙirjin Hajiya saura ƙiris ta faɗi saboda yadda fitilun idonta suka rufe jiri kuma ya ɗebe ta. Safeenatu dai na daga gefe tana kallon abubuwan ban al'ajabi , Gwaggo Habibah ce ta kamo Hajiya ta taimaka mata ta zauna.Kamar mai cutar huka haka numfashinta ke fita,ruwan sanyi ta nema da sauri aka bata ta shanye ƙatuwar gora. “Habibah bani pilow bacci nake ji” cewar Hajiya ,da sauri ta ɗauko ta miƙa mata ita kuma ta kwanta babu jimawa bacci mai nauyi ya ɗauke ta . Safeenatu ta ce “ Gwaggo Habibah ni fa na fara jin tsoron lamarin Baseerat kina dai ganin abin da ya faru, wannan ai ba zan fita da ita unguwa ba gudun ta jawo min masifa ace mayya ce ma” Da mugun sauri Habibah ta katse ta “ kar na sake jin kin faɗi haka,saboda ƴarki ba mayya ce ba ƴar baiwa ce” “To amma ai wasu ba za su ganin haka ba ko? Tun yanzu tana jaririya tana haka ina ga ta girma?” Gwaggo Habibah ta yi murmushi ta ce “ Safeenatu bari dai na soma ɗan guntsira miki labaran duniyar ɓoye, kowane mutum da kike gani a duniyar nan yana da matriculation na sama.Ko kuma lambar sirri ta samaniya,da wannan ne in aka sayar da ruhin mutum daga lokacin matriculation ɗinsa ta saminiya sai ta canza.Duk wani ɗan Adam kasance yana da taurari iri-iri waɗanda suke taimakawa wurin gudanar da al'ammuran duniyarsa.Ya zama doli kowa ya kare taurarinsa ya basu tsaro,muddin ka yi sakaci da su kuma to wannan mutumin zai iya zama cikkaken maƙasudi wurin tallafawa masu sayar da taurari su ƙwace masa su.” Safeenatu ta katse ta da cewa “ ta ya za a ƙwacewa mutum taurarinsa alhalin mallakinsa ne?” Gwaggo Habibah ta bata amsa da “ ba ki taɓa jin labarin wata ma'aikaciyar saloon ba mai gyaran gashi? Ki nemi littafin Mrs Sadauki na MAITAR IDO a nan duk za ki samu cikakken labarin.Ki sani cewa matsafa don su kama ruhinka ma abu ne mai sauƙi,abin da suke buƙata shi ne kawai keɓaɓen abu na gaskiya ta atomatik da ke fitowa daga mutumin da ake son cutarwar,kamar gashinsa,sunansa,date ɗin ranar haihuwarsa,zufar jikinsa wato tufafin da ya saka ba a wanke ba,ko kuma jinin jikinsa.Daga lokacin da matsafi ya riƙe ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan zai iya buɗe katinka na samaniya kuma ya karɓe ƙarfin ikonka wato power daga nan sai yayi abin da yake so” A sanyayye Safeenatu ta ce “ duk Baseerat za ta iya yin wannan? Gaskiya ni dai ban so in kin san hanyar da za a toshe wannan baiwar tata ni dai ki taimaka min don ina ji a jikina muddin aka bar ta da ita a gaba za ta zame mana masifa” Gwaggo Habibah ta yi mata wani irin kallo irin na ba ki da hankali kafin ta je ta ɗauki safar hannun ta saka ma jaririyar wacce ta buɗe ido sai kalle-kalle take kamar mai wayo,kafin kuma ta kafe idonta ga madubi Gwaggo Habibah ta yi kasaƙe tana kallon Baseerat a sannu a hankali ta ga idon yarinyar na sauya kala har suka zama farare tasss babu ɗigon baƙi,wani abu kuma ya soma fita daga bakinta yana bin direction ɗin madubi.Habibah ta ja wani dogon numfashi don kuwa ta fahimci Baseerat za ta yi tafiya ne ko kuma yawon buɗa ido wanda dayawan mutane na yinsa ba tare da sun san mine ne ba.Sai ka ji tamkar jikinka ya zama gawa kana son tashi daga bacci amma ka kasa tamkar an danne ka da dutse,har kwatanta buɗe ido ake amma baka iyawa saboda ruhinka da yayi balaguro ya bar gangar jikinka a kwance. #SAKEENATU Gefen da Nafisa ke ta sharar bacci ta duba kafin ta ɗaga kanta sama tana kallon yadda rufin ɗakinta ke wani lomaƙawa tsabar yadda ake tafiya a guje.Kukan jaki da na kare ga kuma na mage duk a lokaci guda,gefe guda kuma wata siririyar murya take ji tana kiran sunanta.Idonta ya ciko da hawaye,fitsari take ji amma tsoro ya hana ta tashi.Nafisa ta soma tayar wa,ita kuwa dakyar ta buɗe ido ta ce “ mine ne ?” “Fitsari nake ji” ta bata amsa kamar wata ƙaramar yarinya,cikin magagin bacci Nafisa ta ce “ ki je ki yi mana” sai ta koma baccinta.A hankali Sakeenatu ta zuro ƙafafunta ƙasa a tsorace ta shiga toilet ko Bismillah ba ta yi ba ballantana karanto addu'a,a tsorace ta je ta haye WC ɗin ta soma fitsari sai kuma jikin ya soma kyarma ganin ruwa na ta ɓulɓulowa ta ƙasan tile suna cika toilet ɗin ko kafin ta ƙyafta ido sun kawo mata a wuya ta yunƙura za ta tashi amma sai ta ji tamkar an saka super glue an manna ta a jikin WC ɗin ta ƙurma wani uban ihu wanda dama su mugayen shine suke jira ai kuwa suka tsaga rufin ɗakin ji kake ƙiiiiii kamar suna yaga zane.Idon Sakeenatu duk a waje take kallon yadda bindi mage,na kare da kuma idon wata baƙar mujiya a daidai wurin da suka tsaka.Cike da mugunta suka diro toilet ɗin wanda yayi daidai da tsinkewar numfashin Sakeenatu..... My book is only 500 via 6042551755 Hassana Ibrahim Keystone bank DM +22795045822 💛💛💛GHT B-CLEAR,FEMALE CARE AND GANODERMA💛💛💛 💛💛*BACK TO VIRGIN KIT* *(SABON BUDURCI)* 💛💛Assalam alaikum Mata albishirin ku🧏‍♀️🧏‍♀️ga abin da kuka Dade Kuna mafarkin samu ya samu💃🥰 💛💛Abin nema ya samu ,Kowacce mace aduniya tana mafarkin sake kasancewa virgin 💛💛Ina manyan Mata da suka hayayyafa😁 💛💛ina zawarawa masu shirin aure😍 💛💛Ina budurwa da iftila'i ya fadawa a yayin tsallaka rame 😢 💛💛Ina Mai jego da keso ta dinke ta game tsaf ciki da waje❤️ 💛💛Duk ku marmatso kusa ga GHT back to virgin set na kawo muku ,magunguna ne namu na gargajiya bana bature ba 💛💛Kuma Sha akeyi ,insha Allahu muddin kikayi amfani da wannan Kayan Zaki dawo da martabar ki ta farko 💛💛Sai kin gwada za ki tabbatar da hakan. Sisters no 08142506271 mmn Khadeejah sai najiku [29/09 à 14:24] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 29/09/24 11 💛💛💛GHT B-CLEAR,FEMALE CARE AND GANODERMA💛💛💛 💛💛*BACK TO VIRGIN KIT* *(SABON BUDURCI)* 💛💛Assalam alaikum Mata albishirin ku🧏‍♀️🧏‍♀️ga abin da kuka Dade Kuna mafarkin samu ya samu💃🥰 💛💛Abin nema ya samu ,Kowacce mace aduniya tana mafarkin sake kasancewa virgin 💛💛Ina manyan Mata da suka hayayyafa😁 💛💛ina zawarawa masu shirin aure😍 💛💛Ina budurwa da iftila'i ya fadawa a yayin tsallaka rame 😢 💛💛Ina Mai jego da keso ta dinke ta game tsaf ciki da waje❤️💛💛Duk ku marmatso kusa ga GHT back to virgin set na kawo muku ,magunguna ne namu na gargajiya bana bature ba💛💛Kuma Sha akeyi ,insha Allahu muddin kikayi amfani da wannan Kayan Zaki dawo da martabar ki ta farko 💛💛Sai kin gwada za ki tabbatar da hakan. Sisters no 08142506271 mmn Khadeejah sai najiku Duk da Sakeenatu ta suma hakan bai sa mugayen nan sun ƙyale ta ba,haka suka ajiye mata cutar a jikinta kafin su bar ta nan yashe a toilet.Cike da murna suka koma asibiti suka dinga bai wa Mamuh labarin abin da ya faru,cike da mugunta ta ce “ gobe da safe da hannunta za ta dafo wake ta kawo min ,daga nan kuma zan datse alaƙar farin cikinsu ita da Abbas zan maye mata gurbinsa ” duk suka sa dariya suna ƙara tsara mata wani salon muguntar. Washegari Kiran sallar asuba ya tashe da Nafisa,ta sauka daga bed ta shiga toilet nan ta ci karo da Sakeenatu a yashe babu numfashi.Hankalinta a tashe ta cika bokiti da ruwa ta zuba mata,ta ja ajiyar zuciya kafin kuma ta soma kuka cikin firgici.Nafisa ta kamo ta tare da fiddo ta haɗi da tambayar ta,duk a tsorace take wannan yasa ta kasa yi wa ƙanwarta bayani.Ganin haka yasa ita kuma ta je ta yo alwala ta yi sallah,bayan haka ne ta matsa wa Sakeenatu ta je ita ma ta yi sallar.Ko wanka ba su yi ba ta ce “ Nafisa tashi mu je gida wallahi tsoro nake ji” haka suka runguɗa suka je can gidan Mama wacce ke ta ƙoƙarin hura wuta domin ta ɗora ɗumame,tana ganinsu ta san ba ƙalau ba.Kamar wata ƴar yarinya haka ta je ta rungume mahaifiyarta tana wani sabon kukan,“ Subahanallahi! Nafisa mike faruwa?” “Wallahi Mama ban sani ba ni ma na yi ta tambayar ta amma ta ƙi faɗa min,alamu dai sun nuna tsorata ta ake yi a can gidan nata” Nafisa ta bata amsa. Mama ta ce “ to Allah ya sawwaƙa,ku wuce ciki bari na kira malam na shaida masa ” Can cikin mitsitsin ɗakinsu suka shiga,Ma'idah na kwance sai bacci take ba ta farka ba.Sakeenatu ta ɗauki abarta ta rungume ƙam kamar an ce za a raba su,mugun mafarkin da ta yi kan Ma'idar ya dawo mata a kai.Ta lumshe ido ruwan hawaye na kwaranya a kumatunta,ta yi tunanin kakarta ta yanke saƙa,ba ta taɓa tunanin za ta sake yin ƙunci a rayuwa bayan wanda ta yi a baya ba tun lokacin da Abbas ya shigo rayuwarta komai ya dawo mata normal ashe da sauran kallo a sama.Tsohuwar shuɗaɗiyar rayuwarta ce kwanyarta ta soma yi mata tariya,cikakken sunanta shi ne Sakeenatu Abubakar,ƴar gwagwarmayar rayuwa mai zuciya cike da burin zama wata aba a duniya.Karatun boko shi ne abokin da ta riƙa sannan kuma tubali don gina rayuwa mai inganci,sai dai ƴan magana na cewa rashin sanin ya fi dare duhu.Sakeenatu ba ta taɓa sanin cewa ba sanadin boko ne za ta zubar da mutuncinta ba,zuwanta jami'a shi ya ƙara buɗe mata ido sosai ta waye ta zama ƴar gayu,ƙwazonta a wurin karatu shi yasa ta ciri tuta a wurin malaman makaranta kusan duk maganarta suke suna yabon baiwar da Allah yayi mata banda malam Agali wanda tun ranar da ya ɗora idonsa kanta yake jin mugun sha'awarta saboda ta haɗu ta kowanne fanni.A wata rana Laraba ce wacce ta kasance ranar farko da ya fara ɗana mata tarko da kuɗi,“ki hau taxi” ya faɗa cikin taushin murya a gaban ɗalibai ba tare da ya ɓoye ba kuma ya sakar mata murmushin nan nasa wanda yake haukata ƴan matan makaranta da na wajensu .Ba za ta cewa tana sonsa ba,amma ita ma tana cikin waɗanda yake burge su saboda yadda yake da kyau kamar Balarabe ga baƙar sumar kansa ko wata macen ya fi sannan ɗan gayu ne kullum cikin shiri mai kyau yake.Ƴan matan ajin suka hau yin shewa suna taɓi tare da cewa yau dai an samu wacce ta sace zuciyar Dr Agali,da ido ta bisa kawai lokacin da yake fita daga ajin yayin da ɗalibai duk suka dawo kusa da ita kowacce na tofa albarkacin bakinta.Sakeenatu ta ji wani irin girman kai ya zo mata tare da alfaharin ita ce ta ciri tuta,cours ɗin da aka yi musu na gaba sam ba ta fahimci komai ba saboda tunanin malam Dr Agali.Ba ta buɗe ƴar enveloppe ɗin kuɗin ba sai da ta je gida, kuɗi ne ƴan jika-jika sabbi da su har guda goma.Ta kai su kusan hancinta ta shaƙi ƙamshin turarensa,tuni jikinta ya mutu murus ta na shirin saka kuɗin a jaka ne ta lura ɗaya daga cikin takardun kuɗin an rubuta lamba a jiki.Kamar wacce ake tsikara ta ɗauki wayarta ta loda lambar sannan cike da waswasi ta tura masa saƙo babu jimawa ya kira ta,kamar wani mutumin ƙwarai har da yi mata sallama ta amsa tare da ce masa “ fatan ka je gida lafiya?” Cikin muryar nan tasa ta buzaye waɗanda ba su ida iya Hausa ba ya amsa mata da “ a'a ina wata asibiti an kira ni in tiyata” Ta saki murmushi mai sauti ta ce “ ina son ganin ranar da za a ce Sakeenatu na yin tiyata” “Lokacin zai zo ke dai ki ci gaba da dagewa wurin yin karatu,na ji malamai sai yabon ki suke ashe ba a cours ɗina ne ba kawai kika ƙware” nan ma murmushi mai sautin ta yi kafin ta ce “ burina shine zama babbar likita wacce duk duniya za ta yi alfahari da ita,ana dinga nuno ni a TV” “Kina iya barin Nijar Keenat?” Dr Agali ya tambaye ta,kai tsaye ta basa amsa da “ eh sosai sai in gwamnati bai ɗauki nauyin karatun nawa ba” “To ki fara shiri in sha Allah ni nan zan sa burinki ya cika” “Keee Sakeenatu keee!” Mama ta faɗa tana mai kamata dundu wanda shi ya katse mata tunanin shuɗaɗiyar rayuwarta,da sauri ta dawo hayyacinta tana mai kallon Mama wacce ta janye Ma'idah da sauri tana mai ci gaba da cewa “ kawai ki kama yarinya ki riƙe gam tana kuka da ranta amma kin ƙi sakin ta” Sam ita ba ta san riƙon da ta yi wa Ma'idar ya cutar da ita ba,cike da takaici da zugin da zuciyarta take yi ta tashi ta fita ta cika bokiti da ruwan ta shiga banɗaki.Wanka take son yi amma tunanin Dr Agali sai ƙara kawowa kwanyarta farmaki yake,abin da ya faɗo mata a rai a yanzu kuma shi ne ranar da ya kira ta ya shaida mata Visa ɗinta ta fito ta zo ta karɓa bai jin daɗin jikinsa.Ba tare da wani tunani ba ta je gidan nasa kamar yadda yayi mata kwatance,duk a tunaninta yana da mata amma sai da suka shiga ciki ne ta ga shi ya bata ruwa sannan ya kawo mata lemu wanda ya zubar da shi a jikinta da gayya har tufafinta suka ɓace.Ta wani rumtse ido don takaicin ganin video yadda Dr Agali ya ɓalle maɓallan rigarta ya cire ta ya bar ta daga ita sai bra ya je wanke mata ita duk ta yi tunanin ƙauna ce ta kawo haka sai bayan ya dawo ne ya soma yi mata wasu zafafan romance.“ Ni fa dama ba zan yi miki komai ba, wannan ɗin ma ban san ya aka yi ya faru ba ki yi haƙuri ba zan sake ba sai bayan aure” Dr Agali ya faɗa lokacin da ta sakar masa kuka. “Anty Sakeena don Allah ki aje tunanin nan gefe ki yi wanka ki fito ga malam nan ya zo” Nafisa ta faɗa daga bakin ƙofa.Sai a lokacin Sakeenatu ta fara wankan ,bayan ta fito ta je ta gaishe da malam wanda ya kasance ƙanen Mama ne.Cikin garwashin wuta ya zuba ƴaƴan habbatu sauda hayaƙi ya turniƙe ɗakin,idon Sakeenatu duk suka fito waje ta soma tari kamar ranta zai fita shi kuwa karatu ya soma nan lamarin ya ƙara yin gaba don tuni ta soma yin kuka .Tsawon lokaci kafin ya bar ta haka nan,magani ya bada wanda za ta dinga shafawa da hayaƙe jikinta da kuma gidan.Bayan tafiyarsa ne ta samu ta ci abinci,wunin ranar dai Mama haka ta ƙare shi wurin yi mata nasiha dab da magrib Nafisa ta yi mata rakiya zuwa gidanta.A tare suka yi gyaran gidan da girki kafin ta yi wanka ta shafa man da malam ya bata ta kuma yi turare. A can asibiti kuwa tun safe da Abbas ya bar su bai koma ba,kuɗi kawai ya bar musu hakan bai yi wa Mamuh daɗi ba.Ana yin sallar magrib ba tare da likita ya sallame ta ba Gwaggo Rahamu ta haɗa tarkacensu suka fito a ɓoye.A bakin hanya suka samu adaidaita wacce za ta kawo su gida ,suna tafe suna hira “ ai tun da kika ga bai dawo ba to tabbas babu makawa da ya koma gida karuwanci ta yi masa kin san halin namiji kan mace sakarai yake zama” Gwaggo Rahamu ta faɗa . Mamuh ta tsuke bakin nan nata ta kasa cewa komai saboda baƙin cikin da ke addabar baƙin ruhinta,gani take yi ma tamkar adaidaitar ba ta gudu. Suna isa gida tun a bakin ƙofa suka canza kalar idonsu daga na mutum zuwa na mugunta,sai aka yi rashin sa'a Nafisa na tsakiyar falo tana hayaƙa hantiti da tazargade .A tare suka shigo,a tare kuma suka saki ihun azaba suna masu faɗuwa ƙasa suna yin wani irin huci a gaban idon Nafisa suka rikiɗe suka zama jibga-jibgan macizai kowa yace shi ba ma matsoraci ne ba to bai ga abin tsoron ba .Da wani mugun sauri Nafisa ta mangal ɗin hannunta mai cike da garwashi,da azama ta nufi hanyar ɗakin Sakeenatu sai dai kafin ta isa Gwaggo Rahamu ta yi wani uban tsalle ta naɗe handle ɗin ƙofar da bindinta tana mai buɗe ƙaton bakin,Nafisa na shirin komawa baya ta ji ana bin ƙafafunta wanda kuma tunaninta da ruhinta tuni sun shaida macijiya Mamuh ce...... My book is only 500 via 6042551755 Hassana ibrahim Keystone bank DM +22795045822 ASSALAMU ALAIKUM Mata masu abun dadi *Zuzeam empire* takawo muku babbar gara basa Duka akan 5500 ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki Garabasa gara basa 🗣️🗣️🗣️😁🎁💃🏽💃🏽 Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 5500 na 1. Kaza rabi 2. Ciccibi 3. Gumba 2 4. Gari 1 5. Tsimi 2 sunada kyauta abubuwa kamar haka 1.Matsin ba a Fira da wando sa mai gida kukan dadi 1k 2. Matsin maganin infection 300 3. Dripping pills 1pcs 300 4. Matsin dare daya wanka goma 400 Total total gift 2k 😁 Kiyi kokari ki kasance aciki Garabasa kan garabasa Da 5500 dinki ki mallaki kayan da ko 10k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah *08144015291* Maman yasmeen takuce 😍 Wa.me/+2348144015291 For more information say hi 👋 Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam empire tashirya tsaff dominku💃💃💃 muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu *DAHUWAR KAZA* Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato *Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya* Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt *Akwai kyauta 🎁 mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya* *INA MASU JEGO DA AMARE* Karku bari wannan dama ta wuceku *08144015291* Zuzeam empire ASSALAMU ALAIKUM Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 08144015291. 1000 kacal 👌🏽 Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd Maganin karin kiba Maganin nono da hips Rage tunbi da kiba Infection set Sabon budurci set Niima set Basir set Matsi mallaka Amarya set Uwar gıda set Mai jego set Dadai sauransu [30/09 à 18:07] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 30/09/24 12 ASSALAMU ALAIKUM Mata masu abun dadi *Zuzeam empire* takawo muku babbar gara basa Duka akan 5500 ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki Garabasa gara basa 🗣️🗣️🗣️😁🎁💃🏽💃🏽 Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 5500 na 1. Kaza rabi 2. Ciccibi 3. Gumba 2 4. Gari 1 5. Tsimi 2 sunada kyauta abubuwa kamar haka 1.Matsin ba a Fira da wando sa mai gida kukan dadi 1k 2. Matsin maganin infection 300 3. Dripping pills 1pcs 300 4. Matsin dare daya wanka goma 400 Total total gift 2k 😁 Kiyi kokari ki kasance aciki Garabasa kan garabasa Da 5500 dinki ki mallaki kayan da ko 10k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah *08144015291* Maman yasmeen takuce 😍 Wa.me/+2348144015291 For more information say hi 👋 Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam empire tashirya tsaff dominku💃💃💃 muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu *DAHUWAR KAZA* Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato *Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya* Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt *Akwai kyauta 🎁 mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya* *INA MASU JEGO DA AMARE* Karku bari wannan dama ta wuceku *08144015291* Zuzeam empire ASSALAMU ALAIKUM Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 08144015291. 1000 kacal 👌🏽 Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd Maganin karin kiba Maganin nono da hips Rage tunbi da kiba Infection set Sabon budurci set Niima set Basir set Matsi mallaka Amarya set Uwar gıda set Mai jego set Dadai sauransu Ido ta lumshe jikinta na ci gaba da kyarma,tuni Mamuh macijiya kuma ta ɓullo kanta tsakanin ƙirjin Nafisa ta fiddo halshe ta lashi fuskarta,yawunta masu mugun ɗohi suka daki hancin Nafisa.Ba tare da ta buɗe ido ba ta buɗe bakinta murya na rawa can ƙasan maƙoshi kamar mai yin raɗa ta soma karanto wasu ayoyin Alkur'ani da ke cikin suratul Yusuf daga aya ta 79 har zuwa 82 .Jikin Mamuh macijiya ne ya soma yin sanyi tsabar yadda ayayoyin ke dagargaza ruhinta musamman da ya zamana Nafisa ta soma ɗan ɗaga murya.Sululuuuu Mamuh macijiya ta faɗo daga jikin Nafisa ,a mugun tsiyace Gwaggo Rahamu ta bi ta ƙarƙashin ƙofa ta shiga ɗakin Mamuh don kuwa ƴan magana na cewa in ka ga gemun ɗan uwanka ya kama da wuta to kai ka shafa wa naka ruwa. Nafisa na jin saukar macijin ta buɗe idonta a hankali tare da sauke su ƙasa inda Mamuh ke kwance har yanzu cikin siffar maciji sai wani irin numfashi take fatar cikinta na lotsawa kana gani ka san ta wahala. Nafisa ba bakinta bai gushe da ci gaba da yin duk addu'ar da ta zo bakinta ba,a yadda take tsayen suka ƙure juna ita da Mamuh wacce duk wanda ya san ta to tabbas in ya ga macijin zai shaida wannan idon na Mamuh ne.Nafisa ta saki wani murmushin nasara lokacin da ta ga hawaye sun fara fita daga idon macijiyar,ta sani sarai har da kunya da gajiya suka hana Mamuh ƙoƙarin guduwa don babu abin da Mayu suka fi tsana kamar asirinsu ya tonu wannan yasa Nafisa ta nufi ɗakin Sakeenatu.Tana shiga daidai ita kuma ta fito daga Toilet ta yi wanka ƙugunta ɗaure da towel,“wani wankan kika sake yi?” Nafisar ta tambaye ta ba tare da ta nuna mata alamar wata damuwar ba. “Eh wallahi,maganin nan da na yi hayaƙi da shi sam babu daɗi shi yasa na yi wanka” Sakeenatu ta bata amsa tana mai kallon Nafisa,“Me? Wannan kallon fa?” “Fuskarki ce nake ganin kamar tana min wani iri” “Wani iri kamar ya fa?” Nafisar ta tambaya tana mai shafar fuskarta a daidai wurin da Mamuh ta lasa. “Babu komai! Bari na shirya na san yanzu Abbas zai shigo” “Ni zan yi sallah” cewar Nafisa tare da shiga Toilet,har ta gama alwala tana tunanin abin da ya faru da ta zo ta yi sallah sosai ta yi addu'ar neman tsari. Sakeenatu ma ta yi sallah tare da fara bitar karatun jiya da aka koya mata,in ta yi kuskure sai Nafisa ta gyara mata suna nan zaune har aka kira isha'i suka miƙe suka gabatar sai bayan sun ida ne suka fita falo. Nafisa ta dubi daidai wurin da ta bar Mamuh a ɗazu,tuni capet ɗin yayi alamun datti. “Anty Sakeena ni kam ina mai aikinki?” “Wa Fa'iza ? Wallahi kin ga shaf na manta da zancen ta.Ga shi kuma ba waya ce da ita ba ballantana na kira ta amma gobe in ba ta zo ba zan je gidan nasu na gani tun da babu nisa nan baya ne gidan Fulanin nan” “Oh! Can take ashe,tun da babu nisa bari na je na dubo” Kafin Sakeenatu ta bata amsa Abbas yayi sallama tare da shigowa,duk fushinsa ne ya ɓata nan take ganin uban adon da matarsa ta yi. “Ina wuni Ya Abbas ?” Nafisa ta gaishe shi tana mai yin murmushi don tana mugun sha'awar soyayyar antynta da mijinta,ba ƙaramin so yake yi mata. “ Lafiya lau Nafi ya gida?” ya amsa. “Alhamdullah” ta faɗa tana mai fita,ita kuwa Sakeenatu kamar wata yarinya haka ta wani rugo da gudu ta faɗa a jikinsa tana kuka.Abbas ya lumshe ido ya na mai cewa “ mene ne kuma na yin kuka uhum?” ba ta basa amsa ba ta dai lafe a jikinsa,tsawon lokaci suna a haka kafin ta hauƙura ta ja shi zuwa cikin bedrom ɗinsu.Da taimakonta yayi wanka ya shirya cikin ƙananan kaya sannan suka fito suka ci abinci,cikin hira ne take faɗa masa ba ta da lafiya har sai da ta je gida. Ya ja dogon numfashi kafin ya ce “ni kina Keenat ban san abin da ke damuna ba yau gani nan dai” “Allah kawo mana sauƙi” “Amen!” FA'IZA Tun da lamarin nan ya faru da ita duk jikinta ya zama wani iri,tun da take ba taɓa jin makamancin abin da ta ji ba a ranar nan.Tana da saurayi don har manya sun shiga zancen amma duk tsawon lokacin da suka ɗauka ita tun can ba ta taɓa jin sha'awarsa ba don a tunaninta ma ba ta da lafiya ne tun da ta ji ana faɗar akwai matan da basu jin feeling.Sai ga shi babban al'amari ya faru da ita mai kamar mafarki kamar zahiri an yi wasa da sassan jikinta,a ranar da ta isa gida kasa cin abinci ta yi.A washegari kuma ta tashi da zazzaɓi dalilin da yasa ba ta je aiki ba,yanzu ma tana kwance kan tabarma ta shafe jikinta da wani maganin zazzaɓi sai ga sallamar Nafisa.Duk da gidansu bai da ƙwan lantarki zamani amma suna kunna uban sanjo wannan yasa ta gane Nafisa duk da ƙarancin haskensa.Ta tashi da sauri tana mai cewa “sannu da zuwa” Ita kuwa Nafisa gaisa wa take da Mamar Fa'iza wacce ba ma sosai take jin Hausa ba,ta zauna kan tabarmar tana mai cewa “fatan dai lafiya? Anty na ta jira shiru ba ki zo aiki ba” “Zazzaɓi ne ya rufe ni amma da sauƙi gobe zan je in sha Allah ” Fa'iza ta bata amsa. “Allah ƙara lafiya,ni zan koma” cewar Nafisa tare da miƙewa,har ƙofa Fa'iza ta rako ta sai a lokacin kuma ta yi mata tambayar “ni kam Fa'iza abin da ya faru da ke gidan anty Sakeenatu dama kina yin haka?” “A'a wallahi ban taɓa yi ba” “To ki dage da addu'a kin ji ko,saboda yanzu duniyar sai a hankali” “To na gode” da wannan suka rabu maimakon Nafisa ta koma gidan Sakeenatu sai ta yi tsinke gidansu tun da dai ga mijinta nan ya zo. #GIDANSU SAFEENATU Wuni guda currr jaririya Baseerat ta ɗauka tana bacci wanda gangar jikinta ta koma kamar gawa ko motsi ba ta yi. Idon Safeenatu taf da hawaye ta ce “ Gwaggo Habibah jaririyar nan fa ba ta motsi,ina ga ta mutu ne” “Da ranta Safeena,don Allah ki fitar lamarin yarinyar nan tun da dai ba ki da ƙarfin zuciya.Tun farko na faɗa miki Baseerat ba normal ba ce,kenan sai ki shirya ganin abubuwan ban mamaki.Wannan kwancin da kika gani ruhinta yayi tafiyar dogon zango ne amma da ranta,ƙila sai goshin magarib su maido ta” Hawayen da take ƙoƙarin mayar wa ne suka yi nasarar sauko wa akan kumatunta,ta girgiza kafin ta ce “ ni kam ba zan iya rainon ta ba,don muddin na ce zan zauna da ita zuciyata na iya bugawa.Su wane ne za su maido ta? Yarinya kamar ɗiyar jinnu ace tun safe tana bacci ko nono ba ta sha ba alhalin ɗan uwanta ya sha fiye da goma.Haba kuma ace ba zan yi magana ba?” Safeenatu ta faɗa zuciyarta na yi mata ciwo kafin ta miƙe ta fita, frigine ta buɗe ta ɗauko ruwa masu mugun sanyi ta juyo a roba sannan ta koma ɗakinta.Babu wani tunani ta ɗauki Baseerat ta tsoma cikin ruwan ƙanƙarar nan ,ko daƙiƙa biyu ba yi ba ta buɗe idonta farare tasss babu ɗigo baƙi kafin su rine su koma ja kamar nunnanen tumatur.Safeenatu ta yi baya da sauri cike da tsoro,tana jin wani azababen sanyi na game duk illahirin jikinta tamkar wacce aka jefa a frigini.Haƙoranta ne suka fara dantsewa suna fitar da wani ƙasƙas,sai a wannan lokacin Gwaggo Habibah ta miƙe ta cire Babyn tare da lumshe ido tana mai bata haƙuri “ku yi haƙuri uwa-uwza ce ta yi kuskure ba za ta sake ba” tana maganar ne tana jimƙe da hannun hagun Baseerat wanda ke fitar da haske,Gwaggo Habibah ba ta buɗe idonta ba sai da ta ji Sakeenatu na sauke numfashin wahala ta yi mata wani kallo ta ce “yanzu kin fahimci abin da nake son yi miki nuni?” kai ta gyaɗa,Baseerat ta soma yin kuka. “Zo ki bata ta sha” Safeenatu ta maƙe kafaɗata ta ce “wallahi tsoronta nake” “Sun tafi yanzu ita kaɗai ce ,zo ki bata yunwa take ji” tana ji tana gani haka ta shayar da jaririyar. Ana kiran sallar magrib Murjanatu ta dira a gidan da ɗirkeken cikinta,cike da murna suka rungume juna ita da Gwaggo Hajara.“Na yi kewarki sosai Mama ” cewar Murjanatu tana matsar ƙwalla,shiru Gwaggo Hajara ta yi jin ƙaton cikin ƴarta na tokare ta yayin da kuma yawunta suka soma tsinkewa tsabar maita...... My book is only 500 via 6042551755 Hassana ibrahim Keystone bank DM +22795045822 💛💛💛GHT B-CLEAR,FEMALE CARE AND GANODERMA💛💛💛 💛💛*BACK TO VIRGIN KIT* *(SABON BUDURCI)* 💛💛Assalam alaikum Mata albishirin ku🧏‍♀️🧏‍♀️ga abin da kuka Dade Kuna mafarkin samu ya samu💃🥰 💛💛Abin nema ya samu ,Kowacce mace aduniya tana mafarkin sake kasancewa virgin 💛💛Ina manyan Mata da suka hayayyafa😁 💛💛ina zawarawa masu shirin aure😍 💛💛Ina budurwa da iftila'i ya fadawa a yayin tsallaka rame 😢 💛💛Ina Mai jego da keso ta dinke ta game tsaf ciki da waje❤️ 💛💛Duk ku marmatso kusa ga GHT back to virgin set na kawo muku ,magunguna ne namu na gargajiya bana bature ba 💛💛Kuma Sha akeyi ,insha Allahu muddin kikayi amfani da wannan Kayan Zaki dawo da martabar ki ta farko 💛💛Sai kin gwada za ki tabbatar da hakan. Sisters no 08142506271 mmn Khadeejah sai najiku [01/10 à 07:39] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 01/10/24 *Last free page 13-14* Wani irin mugun ƙishi ne ya wanzu a maƙoshin Gwaggo Hajara saboda Maitar shan jini ta motsa.Dakyar ta iya sakin Murjanatu ta koma gefe tana kallon ta,sai kuma ta kasa haƙuri sai da ta shafi ƙaton cikin da mugun sauri Murjanatu ta kai hannunta ita ma kan cikin saboda mugun juyawa da yayi. “Washhh! ” ta furta a wahalce kafin kuma ta dafe ƙugu jin kamar ta soma naƙuda ne,“ sannu Murjanatu ki zauna mana” Gwaggo Hajara ta faɗa tana haɗiyar yawu don tsaf take kallon jaririn wanda sai juyi yake a ciki. Kan gwiwanta ta zube tana mai ci gaba da yin gumurzu,tuni ita Hajara ta san da yau in ba wani iko na Allah ba sai ƴarta ta haihu.Da sauri ta shiga cikin ɗaki ta fito kafin ta ce “tashi mu je asibiti” a wahalce ta ɗago ta dubi mahaifiyarta ta ce “ wallahi Mama ban iya tashi” “To haka za ki zauna? Sai nake ganin kamar haihuwar ce” Ba ta rufe bakinta ba Murjanatu ta fasa wani uban ihu wanda ya jawo hankalin Gwaggo Habibah da saurinta kuwa ta fito tana tambayar lafiya sai kuma ta yi tozali da Murjanatu a cikin mawuyacin hali.Da taimakonta suka samu suka Murjanatu ta miƙe tsaye,Munir ne ya je ya nemo musu mai ɗan sahu.Kayan robar Safeenatu aka yi aro aka kai ta asibiti,sai uban ihu take tana kururuwa tana faɗin za ta mutu. Daga nan waje kuma inda mutane ke zauna wa,ran Gwoggo Habibah ya ɓace sosai tun tana ɓoyen abin har ta kasa ta ce “ yanzu ke hatta ƴarki ba ki bari ba? Wannan mugun hali naki bai yi ba.Wato babu babban makunyaci a duniya irin maye,tun da har jininsa bai bari ba” Gwaggo Hajara ta ƙanƙance idonta da suka kaɗa suka yi ja kafin ta ce “ ina ruwanki da ni ? Ke kika haifa min Murjanatun? Ƙanwar uwa ko ta uba?” Gwaggo Habibah ta miƙe ta ce “ kina fa da gaskiya,amma ki yi haƙuri farar zuciyata ta taimakon jama'a tasa na zo na tsoma hannnuna inda ba a gayyace ni ba.Tabbas Murjanatu ƴarki ce in kina so ki haɗa har da ita duk ki cinye” tana gama faɗa ta yi tafiyarta ta bar Hajara a zaune babu jimawa kuwa Murjanatu ta haifo ɗanta namiji. Ɗakin hutu aka kai ta,murya na ɗan rawa Gwaggo Hajara ta ce “ yo ina jaririn?” “Nurse na duba shi ne don tabbatar da lafiyarsa” ta bata amsa. Tsawon lokaci kafin a kawo shi jikinta har rawa yake ta karɓe shi,nurse ta ce “ a basa abincinsa ya sha da alamu yunwa yake ji” “Toh! Toh” cewar Hajara tana wani kafe yaron da idon mugunta,ya soma kuka Murjanatu ta tashi zaune babu kunya ta ce “ Mama kawo shi” ba don ta so ba ta miƙa mata shi ta koma gefe cike da ƙwarewa ta damƙe kurwar yaron .Da ta fita wankin kayan da suka ɓace ta samu wuri ta haƙa rame ta binne ,duk da zuciyarta babu daɗi amma ji take ya zama doli ta cinye jikanta na farko ko yawunta sun koma. Daren nan dai ba su yi bacci ba jariri nata yin kuka hatta likitocin sai da suka shigo suka duba shi,sai asubahi ya rumtsa wuraren ƙarfe tara na safe aka basu takardar sallama bayan sun biya.Hajara ce ta je ta taro ɗan sahu,bayan ta saka kayansu Murjanatu ta shiga sannan ita ma ta shige tana kallon wurin da ta binne kurwar jariri can ƙasan zuciyarta ta furta ‘ zuwa dare zan zo na tone’ haka suka isa gida. Ta kuwa ci sa'a Daddy bai fita ba,Murjanatu ta gaishe shi ya amsa tare da yi mata barka kafin ya maida dubansa ga Hajara wacce sai raba ido take kana gani ka san ba ta da gaskiya. “ Hakan da kika yi daidai ne? Don dai ba ni ne na haifi Murjanatu ba shine kika koro Habibah daga asibiti? ” “Ka yi haƙuri ba koro ta na yi ba,na dai ce ta dawo gida tun da ba za a barin mai jego ita ɗaya ba a gida” “Mi yasa ba ki kira ni kin shaida min zancen haihuwar ba? Ban cancanta ba ne ko me?” “Ka yi haƙuri Daddyn yara,yanzu dai ka kira shi mijin nata ka shaida masa zancen haihuwar ” Bai amsa mata ba ya fice,sai a lokacin Habibah ta fito idonta kan jaririn wanda ke baccin wahala.Cike da tausayinsa ta ƙarasa ta ce “ barka Murjanatu Allah raya shi kan sunnah” “Amen na gode” ta amsa tare da miƙa mata jaririn,Habibah ta karɓe shi tana mai zaunawa kan kujera ta shafi sumar gashinsa tana kallonsa da kyau ta tabbata kurwarsa na gidan yari ba a cinye ba sai dai ba ta san a ina aka binne ta ba.Haka ta gaji da binciken ta miƙa shi ga uwarsa ta miƙe suna ƴar kallon-kallon ita da Hajara wacce idon nan nata suke wiƙi-wiƙi na maras gaskiya. A sanyayye Habibah ta koma ɗakin Safeenatu,“ ya dai Gwaggo Habibah lafiya na gan ki duk kin yi wani iri?” Feenat ta tambaya. “ Babu komai Safeena,bacci Baseerat take?” “Eh ba ta jima da rufe idon ba” “Mu gan ta” Habibah ta faɗa tare da yin zama, Safeenatu ta ɗora mata jaririyar kan cinya.Hannunta mai safa ta kamo ta cire sannan ta soma shafa shi , [01/10 à 08:45] MRS SADAUKI 💫: *ZAWARCI* LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️ *Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo (MRS SADAUKI💫✍️) *Lambar waya:* +22795045822 *FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️* Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation. *Sadaukar wa:* Rahama Sabo Usman _____________________ 01/10/24 *Last free page 13-14* Wani irin mugun ƙishi ne ya wanzu a maƙoshin Gwaggo Hajara saboda Maitar shan jini ta motsa.Dakyar ta iya sakin Murjanatu ta koma gefe tana kallon ta,sai kuma ta kasa haƙuri sai da ta shafi ƙaton cikin da mugun sauri Murjanatu ta kai hannunta ita ma kan cikin saboda mugun juyawa da yayi. “Washhh! ” ta furta a wahalce kafin kuma ta dafe ƙugu jin kamar ta soma naƙuda ne,“ sannu Murjanatu ki zauna mana” Gwaggo Hajara ta faɗa tana haɗiyar yawu don tsaf take kallon jaririn wanda sai juyi yake a ciki. Kan gwiwanta ta zube tana mai ci gaba da yin gumurzu,tuni ita Hajara ta san da yau in ba wani iko na Allah ba sai ƴarta ta haihu.Da sauri ta shiga cikin ɗaki ta fito kafin ta ce “tashi mu je asibiti” a wahalce ta ɗago ta dubi mahaifiyarta ta ce “ wallahi Mama ban iya tashi” “To haka za ki zauna? Sai nake ganin kamar haihuwar ce” Ba ta rufe bakinta ba Murjanatu ta fasa wani uban ihu wanda ya jawo hankalin Gwaggo Habibah da saurinta kuwa ta fito tana tambayar lafiya sai kuma ta yi tozali da Murjanatu a cikin mawuyacin hali.Da taimakonta suka samu suka Murjanatu ta miƙe tsaye,Munir ne ya je ya nemo musu mai ɗan sahu.Kayan robar Safeenatu aka yi aro aka kai ta asibiti,sai uban ihu take tana kururuwa tana faɗin za ta mutu. Daga nan waje kuma inda mutane ke zauna wa,ran Gwoggo Habibah ya ɓace sosai tun tana ɓoyen abin har ta kasa ta ce “ yanzu ke hatta ƴarki ba ki bari ba? Wannan mugun hali naki bai yi ba.Wato babu babban makunyaci a duniya irin maye,tun da har jininsa bai bari ba” Gwaggo Hajara ta ƙanƙance idonta da suka kaɗa suka yi ja kafin ta ce “ ina ruwanki da ni ? Ke kika haifa min Murjanatun? Ƙanwar uwa ko ta uba?” Gwaggo Habibah ta miƙe ta ce “ kina fa da gaskiya,amma ki yi haƙuri farar zuciyata ta taimakon jama'a tasa na zo na tsoma hannnuna inda ba a gayyace ni ba.Tabbas Murjanatu ƴarki ce in kina so ki haɗa har da ita duk ki cinye” tana gama faɗa ta yi tafiyarta ta bar Hajara a zaune babu jimawa kuwa Murjanatu ta haifo ɗanta namiji. Ɗakin hutu aka kai ta,murya na ɗan rawa Gwaggo Hajara ta ce “ yo ina jaririn?” “Nurse na duba shi ne don tabbatar da lafiyarsa” ta bata amsa. Tsawon lokaci kafin a kawo shi jikinta har rawa yake ta karɓe shi,nurse ta ce “ a basa abincinsa ya sha da alamu yunwa yake ji” “Toh! Toh” cewar Hajara tana wani kafe yaron da idon mugunta,ya soma kuka Murjanatu ta tashi zaune babu kunya ta ce “ Mama kawo shi” ba don ta so ba ta miƙa mata shi ta koma gefe cike da ƙwarewa ta damƙe kurwar yaron .Da ta fita wankin kayan da suka ɓace ta samu wuri ta haƙa rame ta binne ,duk da zuciyarta babu daɗi amma ji take ya zama doli ta cinye jikanta na farko ko yawunta sun koma. Daren nan dai ba su yi bacci ba jariri nata yin kuka hatta likitocin sai da suka shigo suka duba shi,sai asubahi ya rumtsa wuraren ƙarfe tara na safe aka basu takardar sallama bayan sun biya.Hajara ce ta je ta taro ɗan sahu,bayan ta saka kayansu Murjanatu ta shiga sannan ita ma ta shige tana kallon wurin da ta binne kurwar jariri can ƙasan zuciyarta ta furta ‘ zuwa dare zan zo na tone’ haka suka isa gida. Ta kuwa ci sa'a Daddy bai fita ba,Murjanatu ta gaishe shi ya amsa tare da yi mata barka kafin ya maida dubansa ga Hajara wacce sai raba ido take kana gani ka san ba ta da gaskiya. “ Hakan da kika yi daidai ne? Don dai ba ni ne na haifi Murjanatu ba shine kika koro Habibah daga asibiti? ” “Ka yi haƙuri ba koro ta na yi ba,na dai ce ta dawo gida tun da ba za a barin mai jego ita ɗaya ba a gida” “Mi yasa ba ki kira ni kin shaida min zancen haihuwar ba? Ban cancanta ba ne ko me?” “Ka yi haƙuri Daddyn yara,yanzu dai ka kira shi mijin nata ka shaida masa zancen haihuwar ” Bai amsa mata ba ya fice,sai a lokacin Habibah ta fito idonta kan jaririn wanda ke baccin wahala.Cike da tausayinsa ta ƙarasa ta ce “ barka Murjanatu Allah raya shi kan sunnah” “Amen na gode” ta amsa tare da miƙa mata jaririn,Habibah ta karɓe shi tana mai zaunawa kan kujera ta shafi sumar gashinsa tana kallonsa da kyau ta tabbata kurwarsa na gidan yari ba a cinye ba sai dai ba ta san a ina aka binne ta ba.Haka ta gaji da binciken ta miƙa shi ga uwarsa ta miƙe suna ƴar kallon-kallon ita da Hajara wacce idon nan nata suke wiƙi-wiƙi na maras gaskiya. A sanyayye Habibah ta koma ɗakin Safeenatu,“ ya dai Gwaggo Habibah lafiya na gan ki duk kin yi wani iri?” Feenat ta tambaya. “ Babu komai Safeena,bacci Baseerat take?” “Eh ba ta jima da rufe idon ba” “Mu gan ta” Habibah ta faɗa tare da yin zama, Safeenatu ta ɗora mata jaririyar kan cinya.Hannunta mai safa ta kamo ta cire sannan ta soma shafa shi ,zuciya cike da rauni ta soma yin magana “ ki tausaya ki ceto jaririn da bai san komai ba,ki sani shi ma tamkar Basheer yake mai rauni ne.In kuma har yanzu kuna cikin fushi ne shi yasa kuka hana ta ɗauki mataki ku yi haƙuri,amma dai a duba lamarin” tana gama faɗa Baseerat ta buɗe idonta taram cikin na Habibah,ita kuwa ta shiga kallon abubuwan da suka faru bayan ta bar asibitin a cikin ƙwayar idon jaririyar ta ga komai har inda Hajara ta binne kurwar.Tana gama gani Baseerat ta maida idonta ta rufe, Safeenatu dai na gefe a yanzu ma kallonsu take ba tare da ta ce komai ba. Habibah ta ja ajiyar zuciya ta sakar mata murmushi ita kuwa kai ta ɗauke,tana mai jawo wayarta ta kunna data so take ta yi bincike don gano shin abubuwan da suke faruwa zai iya kasancewa ko kuwa ƴarta ce kawai ke da shi. Tunanin ta watsar ta shiga WhatsApp ta fara duba saƙonnin mutane masu yi mata barka kafin kwatsam ta ganta cikin wani group.A hankali ta soma biyayar abubuwan da ke faruwa sai ta ga amsoshin tambayoyinta kan wani posting. ```“M” CIKIN TAFIN HANNU,MAUME HAND/PAUME DE MAIN Chiromancy wata daɗaɗiyar hanya ce ta hango makomar mutum da kuma fassarar halayyar mutum daga dalilin layukan hannu. Wani lokaci waɗannan layuka na iya samar da lambobi da haruffa. Ɗaya daga cikin waɗannan wasiƙun na iya zama wasiƙar M, ma'anar wacce mystics da dama suka yi nazari a kanta. Kamar yadda mutane da yawa suka yi imani, layukan da ke kan tafin hannunmu suna bayyana halinmu da ƙaddararmu. La lettre M est attribuée à des personnes vraiment spéciales(The letter M is assigned to truly special people). An ba su kyakkyawar fahimta kuma suna wakiltar abokan haɗin gwiwa akan dukkan wasu kasuwanci. Idan mutanen da kake so suna da wasiƙa ta musamman M a cikin tafin hannu ya kamata ka sani cewa ba za ka iya raina masa hankali ba kuma ta wata hanyar ba za ka iya yin ƙarya ko yaudarar wannan mutumin ba. Kasancewar shi mai dubara da hankali da tsantsar lura sosai, mutamin da ke da harafin M a tafin hannu cikin sauƙi zai fahimci cewa ana yi masa ƙarya ne ko yaudara. ``Matan da suke da harafin M a tafin hannunsu suna da zurfin tunani fiye da maza, har ma da waɗanda suke da wannan wasiƙar. Ana yi musu baiwa da ikon sarrafawa da shawo kan duk wani cikas a rayuwa, kuma sun san yadda ake amfani da albarkatu da damar da ake da su. Harafin "M" a kan tafin hannu ma na iya nufin: • Ƙwarewar shugabanci • Iko wato power/pouvoir``` Zuciyar Safeenatu banda bugawa babu abin da take yi har sai da ta ajiye wayar ta je ta ɗauki ruwa masu sanyi ta sha .Ta dawo ta zauna don ƙara duba saƙon sai dai hatta shi kansa group ɗin ya ɓata a wayarta babu shi sam .Kamar mahaukaciya haka ta miƙe ta je ta yi wani gurwanau a gaban net ɗin da aka saka Baseerat,ta zuge zip ɗin ta kalli ƙofar toilet inda motsin ruwa ke ta zuba da alamu Habibah wanka ta shiga ba tare da ita ta san yaushe ta shiga ba . Murya a ɗan kasalance ta ce “ Baseerat ni ce mahaifiyarki,ni na haife ki.Duk wani wanda bai son ganin kin cutu to tabbas sai dai ya biyo bayana,don haka kar ki ga kamar ban son ki a'a wallahi zuciyata raunk ne da ita.Magana nake son yi miki game da abin da na gani cikin wayata,shin kina da masaniya? In dai tabbas ke ƴar baiwa ce kamar yadda saƙon nan ya bayyana to ki buɗe idonki ki kalle ni” ko rufe baki ba ta yi ba kuwa Baseerat ta buɗe idon sai da Safeenatu ta dafe ƙirji saboda tsoro. “Mine ne wai?” daga bayanta Habibah ta tambaya ,zip ɗin net ɗin ta mayar tana mai cewa “ babu komai Gwaggo Habibah,na yarda na aminta da lamarin nan gaske ne ana samun ƴan baiwa to Allah bata ikon yin amfani da ita ta hanyar ƙwarai” ruwan sama ne suka fara sauka a daidai lokacin da Safeenatu ta rufe bakinta. Gwaggo Habibah ta yi wani ɗan ihun murna tare da rungume Safeenatu ta ce “ kin ga ko? Ƴarki ta musamman ce ancestor/ ancêtre suna tare da ita” A wannan daren cike da zullumi da tunani Safeenatu ta yi shi,da ta samu bacci ya ɗauke ta mafarkai ta yi barkatai akan goben Baseerat. Washegari tun da safe kukan jaririn Murjanatu ya cika gidan kamar wanda ake cirewa rai. “Jaririn can ba dai kuka ba” Safeenatu ta faɗa . Habibah ta ja baki ta yi shiru tana tuna jiya irin gumurzun da suka yi ita da Hajara akan kurwar yaron.Dakyar ta yi nasara ta tone ta tare da saka Hajara don doli ta mayar masa abarsa wacce tuni ita kanta kurwar ta yi rauni,kukan da yake yi kuma saboda ciwon jiki ne. ★A kwana a tashi babu wuya wurin Allah yau ne sunan Twins ɗin Safeenatu waɗanda dangin Bashir suka yi bajinta sosai wurin yankan manyan raguna uku biyu na BASHEER ɗaya kuma na BASEERAT .A wannan rana ta farin ciki Safeenatu ta rakuɓe wuri guda tana ta yin kuka,ga shi dai ta sha ƙunshi da kitso ga kuma gizner ta gani ta faɗa amma rashin masoyinta ya dawo mata daram musamman yadda ake ta faɗar an yi masa madadi da kuma addu'o'in da mutane ke yi. Da wannan damar Gwaggo Hajara ta shirya mugunta wacce take kambacin fansar da ta yi niyyar ɗauka akan Habibah da hana ta rawar gaban hantsi.Sai da ta bari duk hankalin mutane ya ɗauku,sannan jarirai duk an fitar da su can tsakar gida saboda zafin da ɗakin ya ɗauka sannan ta nufi ɗakin Safeenatu.Duk da akwai mutane hakan bai hana ta gwada sa'arta ba,“ ungo Safeena Gwaggonki Habibah ta ce ki ci abincin nan kafin ta zo ta yi miki ta ƙarfi tun da dai ke ba ki jin magana kina jego amma kin ƙi cin abinci ” Hajara ta faɗa tare da miƙa mata plate mai cike da nama ya sha jar miya,ta karɓa tana turo baki tare da soma ci don ita duk a tunaninta gaske dai Habibar ta bata.Cike da murna Hajara ta bar ɗakin ta je ta kasa kunne tana jiran sakamako. Da rana mutanen arziki sun cika gida, Safeenatu ta shiga Toilet ta yi wanka da canza kaya daga shadda zuwa less.Kamar wacce aka yi wa wankin ido haka take ganin ƴan biki tsirara tamkar babu kaya jikinsu,zuciyarta ta yi wani mugun bugawa ganin ta soma ganin hanjin cikin mutane yayin da kuma take jin wani abu a bakinta da ba ta san mine ne ba.A daidai nan free page ya ida,duk mai son ci gaba za ta biya kuɗi domin shiga PAID GROUP. *FREE PAGE/ PAGE NA KYAUTA YA IDA* Detail 500 via 6042551755 Hassana ibrahim Keystone bank DM +22795045822 In kin san ba ki shirya saya ba kar ki min magana,ga detail nan kawai ki tura kuɗin ki turo min evidence ta WhatsApp. *NB:* daga lokacin da ya kammala ya zama complete zai koma 1000. 01 octoba 2024 #CHAMSIYA LAOUALI RABO MRS SADAUKI 💫 [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 *Ƙirƙiraren labari ne,bai faru ba a gaske .Ban yarda a juya shi ko a mayar da shi audio doli sai da izinina* 1-2 A nutse nake sauraren mahaifiyata ido a lumshe,tun da ta fara nasihar nake daɗa jin nutsuwa na sake samun gurbi a zuciyata har sai da ta zo da furucinta na ƙarshe wanda yayi tsananin razana ni har ban san lokacin da na furta “mi kika ce Ammy?” na yi tambayar da tunanin ko kunnena ne bai jiye min daidai ba. “A yau an ɗaura aurenka da Maryama ina so ka riƙe amana zuwa gobe in sha Allah zan kawo ta da kaina” ta sake maimaita wa,shiru na yi ina jin wani yanayi marar misaltawa. “Ibraheemu haƙuri za ka yi, wannan ne kawai gatan da za mu yi wa Maryama don nuna soyayyarmu gare ta da kuma jadadda girman alƙawarin da na ɗaukar wa mahaifiyarta kafin ta bar duniya” yanzu ma dai shiru na yi ba don ban ji ba sai don abubuwa da dama da suka dinga gwaro a kwanyata. “Heemu ka na ji na kuwa?” “Na'am Ammy ina ji” na faɗa ina jan ajiyar zuciya,ita ma ajiyar zuciyar ta sauke kafin ta ce “ ina Daddyn ka?” “Ya fita tun jiya bai dawo ba” “Okay sai an jima ” “Ammyyy!” na faɗa da sauri,sai ta tsaya da ƙoƙarin kashewar ta ce “ ya aka yi yarona ina jin ka?” Kamar mai koyon magana na ce “ki bar ta nan wurin ki har zuwa wani lokaci ” “Saboda me?” “Kawai Ammy ” “Sai mun zo” ta faɗa tare da kashe kiran na furzar da huci ina jin duniyar na juya min.Screen ɗin wayar na ƙurawa ido ina kallon hotonmu wanda shine hoton ƙarshe da muka ɗauka tare da ɗan uwa kuma abokina. «Zo mu ɗauki hoto ina jin a jikina kamar ba zan fito daga wannan yaƙin ba»cewar Abakar ya na dariya,wacce ba ta kai ga gushe wa ba na yi amfani da wayata na ɗauke mu selfie.Hoton na shafa yayin da kuma muryarsa ke yi min amo a dodon kunne,da sauri na miƙe na nufi ɗakin motsa jiki na soma training.Na shafe kusan awa biyu kafin na fito na wuce bedroom wanka na yi na shirya cikin t-shirt ta soja da wandon kaki.Key ɗin mota na ɗauka kafin na sauko ƙasa inda ƴan aiki ke ta shawagi,su na gani na suka soma gaishe ni kamar kullum da kai kawai na amsa masu na fita zuwa harabar gidan. Inda motata ke parker na nufa direct, ɗaya daga cikin escort ɗin ne ya rugo ya na tambaya ta inda zan je.“ Ni kaɗai zan tafi babu buƙatar rakiya ko ba ga cikin kayan da nake ba?” “Sorry mai gida yalɓai ne ya bada umarnin duk inda za ka je mu yi ma rakiya” ya faɗa cike da girmamawa. “Yi tafiyar ka” na faɗa tare da shige wa ciki na yi wa motar key,wurin fita ma sai da sojawan da ke tsaron ƙofa suka ɓata min lokaci kafin su bar ni na fita. A hankali nake gudu ina duba yanayin garin da yadda al'amurra ke tafiya,a haka har na isa barikin soja.Daidai ɗakinmu na yi parking,na jima sosai kafin na fito ,key nasa na buɗe ƙofar na shiga a nan take duk wani tsohon tarihi ya dinga dawo min.Dakyar nake cira ƙafa ina takawa izuwa ciki,daidai akwatinsa na je na tsaya tare da buɗa shi na ciro kakinsa mai ɗauke da sunansa Abakar.Na rungume rigar ina jin ƙamshin jikinsa na ratsa hancina,karon farko da na ji idona sun cika da hawaye tun bayan dawowar mu daga yaƙin da ya zame mana shamaki ni da abokina. Sosai nake hawaye ina jin dutsen da ya jima da yin gini a zuciyata na motsawa haɗi da zubar da tururi . “Ibraheem!” ya kira sunana a dake,duk da na san ko wane ne bai sa na juyo ba har lokacin da nake jin takunsa na matso ni. “ Mi yasa ka fito alhalin na ce ka zauna gida? Shi ne kuma ka hana escort su take ma baya,mi yasa ba ka jin magana ta? In fa wani abu ya same ka?” Sai a lokacin na juyo muna facing juna,ban ce masa komai ba sai idona masu cike da baƙin ciki da zafin ɗaukar fansa na ƙura masa. “ Wannan zuciyar da kake ji da ita kar ka manta ni ka gado amma shine don tsageranci za ka ƙure ni da ido ka na kallo kamar sa'an ka.Abakar ya mutu ba shine sojan farko da ya taɓa rasa rayuwa ba a wurin yaƙi amma duk ka bi ka adabi mutane da hauka,shi Abakar ɗin wa ya fi ne da ba za a kashe shi b...” “Daddy???” na faɗa a zuciye kafin kuma na juya na mayar da rigar C cikin akwati na rufe na sungumi akwatin na fito,don yanzu shi ne kawai abin da ya rage min nasa. Bayan mota na saka shi,sam ban damu da tarin sojawan da suke tsaye ba waɗanda na san tare suke da mahaifina.Ko ɗakin ban koma na rufe ba na yi wa motar key,ina tafe ina tunanin ƙiyayyar da Daddy ya ɗorawa Abakar dare ɗaya wacce a can farko ba haka suke ba. Na ja wani huci ina mai danganta abin da don ya fito gari guda ne da mahaifiyata,a haka na isa gida can sama na haura da akwatin na ajiye shi bisa bed ɗina. Gaban mirror na je na yi tsaye na ƙurawa fuskata ido wacce ta ƙara yin ja don ɓacin rai,baƙar sumar kaina mai tarin yawa na hargitsa ina kai wa ƙaton ƙirjina duka ina mai yin wata hargowa kamar kumurcin zaki har manyan damatsana su na masu motsawa. Wayata ce ta ɗau ruri sai da ta yi na uku kafin na ciro ta na ɗauka haɗi da karawa a kunne. “Ka sauko ƙasa ina son yin magana da kai” shi ne abin da ya faɗa kafin ya kashe, toilet na shiga na wanke fuska ta kafin na sauka ɗin.A zaune na tarar da shi ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya,shi ma sanye yake cikin na soja mai ɗauke da adon galolin yabo birjit.Kujera mai facing tasa na zauna ina mai sunne kai saboda sai yanzu ne na ji ban kyauta ba game da abin da na yi masa. “Ibraheem ka ɗago ka kalle ni” yayi furta cike da kulawa,ƙin ɗagowar na yi saboda kallon tsakiyar idon Daddy sai mutum ya shirya,na sha jin sojawa na faɗar su na shakkar kallon nasa wanda ni ma shaida ne ba a ko wane irin yanayi ba ne nake iya kallonsa. “Mine ne damuwar ka? Abakar?” Sai a lokacin na ɗago na dube shi,murya cike da rauni na ce “ Daddy shi ɗin abokina ne tun na ƙurciya ina mugun sonsa,tamkar yadda Wa ke son ƙanensa...” shiru na yi ina jan ajiyar zuciya. Daddy ya ce “ saboda mutuwarsa ce nake ganin rauni a idon ka? Ka gaji ne da aikin sojan na tsige ka?” Wani irin halbawa zuciyata ta yi,da sauri na ce “ haba Daddy ya za ka ce haka? In na bar aikin soja mi zan yi ?” Ya miƙe tsaye ya na cewa “to in ka na son ci gaba da zama a ciki,ka fidda Abakar a ranka ko sunansa kar na sake jin ka ambata” har ya kai bakin ƙofa kuma sai ya juyo muna kallon juna kafin ya ci gaba da cewa “zuwa an jima sabuwar mahaifiyar ka za ta tare ban son jin wata matsala ta fito daga gare ka” ya na gama faɗa ya fice. Tsakanin baƙin cikin sharaɗin da ya gindiya mini da kuma kishin Ammyna da nake yi jin zai kawo wata mace matsayin mata sai na rasa da wanne zan ji.Ɗaki na koma na kunna karatun Alkur'ani ina saurare,a haka bacci ya ɗauke sai wuraren sallar zuhur na farka.Na yi wanka haɗi da alwala na saka jallabiya na wuce masjid da ke nan cikin gidanmu,ni na ja su sallah bayan mu gama na zauna nan na ci gaba da lazumi ban fito ba sai bayan sallar Asar. “Babana yau mi za a girka ma na buɗa baki?” Granny ta tambaye ni,mahaifiyar Daddy ce a nan gidanmu take zaune tun kafin ma a naɗa shi komanda sojoji.Muna gane wa juna ni da ita don ni ɗaya ne kaɗai jikanta,kaf ƴaƴanta kuma tun su na jarirai suke mutuwa Daddy kawai ya tsaya. “Tsohuwa mai ran ƙarfe ina kika shige duk yau ban gan ki ba” na faɗa tare da nufar ta ina ta ƙoƙarin ƙaƙalo murmushi. “Ina ɗakina,ai ba ka neme ni ba tun jiya ƙafar nan ta matsa min da ciwo” ta faɗa ta na nuna min ƙafar wacce ta ɗan kumbura. Kan capet na zauna na soma matsa mata ƙafar,cikin sigar zolaya na ce “ko sai an yanke ƙafar nan dai?” ta dungure min kai ta na mai cewa “ka ji min shashanci in an cire gobe da mi zan tarben amaryar ka?” Fuska na kwaɓe ina mai kallonta,ta sakar min murmushi ta ce “Ammyn ka ta kira ni ai ,t sanar da ni yadda kuka yi da ita.Ka na ji Babana ita wani sa'in rayuwa ita ke tsara mana yadda za mu yi,ba kowanne lokaci ba ne abin da mu muka tsara zai zamana daidai” sai kuma ta canza yanayin fuskarta kafin ta ci gaba da cewa “ka ɗauki misalin Daddynka mana,tun ya na yawo da ragga Maimuna ke sonsa kawai daga samun canjin rayuwa ya wulaƙanta ta ita kuma ta ɗauki abin da zafi mine ne na ɗaukar mataki maimakon ki bar wa Allah komai? ” Na ja numfashi na ce “Granny wai mi ya gama Ammy da Daddy faɗa har suke gaba haka? ” Ta shafi kaina ta ce,“Daddyn ka ya yi butulci,saboda amarya ya mari Ammyn ka da ta so nuna masa kuskuren yin haka ya lakaɗa mata na jaki a ƙarshe kuma ya danƙara mata saki.A ranar da za ta fita ta bugi ƙirji ta ce masa yadda ta fita daga gidansa,haka duk matar da zai auro za ta fita.Wai ka na da ma labarin yau wata amaryar zai kawo?” Granny ta buge da tambayata. Ni kuwa tun da na ji wulaƙanci da tozarcin da ya yi wa Ammyna na soma jin tsohon fushina na sake bijirowa.Na yunƙura zan tashi,Granny ta yi saurin mayar da ni ta na cewa “ina kuma za ka je? Faɗa min abin da za a yi ma na saka ƴan aiki yanzu nan” “Duk abin da kika zaɓa Granny ya yi” na faɗa tare da miƙe wa na haura sama.Ina shiga ɗakina na fahimci tabbas wani ya shigo ciki,to amma mi aka shigo yi? Kafin na kai ga lalubo amsa idona ya sauka kan bed sam babu akwatin da na ajiye. Waya na ɗauko na soma kiran Daddy amma bai ɗauka ba,na fito da sauri ina tambayar Granny “ba ki ga wanda ya shiga ɗakina ba?” “Lafiya mi ya faru?” “Akwatina aka ɗauke” na bata amsa kai tsaye. “Baturen nan ne dai ya ɗauko shi a gabana ya fita da shi” “Joy?” na tambaye ta ta ce “eh shi fa” na dafe kaina,Joy shi ne soja na hannun damar Daddyna.Da wannan takaicin na zauna zaman jiran shi,a nan falo na sha ruwa tare da taimakon Granny har na je na bayar da salloli na dawo babu ko motsin Joy.Mu na nan zaune ni da Granny,aka kawo amaryar Daddy wata ƴar ficiciya da ita ko kunyar aurenta bai ji ba. A gaban Granny aka kawo ta ,tun daga danginta har ita amaryar ƴan iya yi ne Granny ta yi musu Allah sa albarka kafin ta nuna musu sashen Daddy suka wuce da ita. Na dubi Granny cike da jin haushi na ce “yanzu wannan ce ya auro?” “Babu ruwan ka,dama ya ce na ja ma kunne akan haka.Duk gani yake saboda tsamin ranka matansa ke fita daga gidansa,sam ya ƙi yarda aikin Maimuna ne” Na ce “Granny ya za ki ce aikin Ammy ne?” “ A bar zancen to.Mi ka shirya wa goben?” Ban bata amsa ba sai kwanciya da na yi na ɗora kaina kan cinyarta,ta ce “sai son jiki kamar mage,ga ka dai ƙaroto amma da taɓi'a yara in ka karye ƙafar tawa ai shikenan” Na yi ɗan murmushi na ce “granny don Allah yi min addu'a na yi bacci ko zan huta da baƙin cikin nan da nake ji”haka kuwa aka yi ta soma yi min karatu,duk da ta na tsohuwa haka take fitar da harufa yadda ya kamata.Sosai nake jin daɗin karatun sai dai baccin ya ƙi samuwa,a ƙarshe ma ita ce ta soma yin gyangyaɗi a doli na miƙe na yi mata rakiya ɗakinta sannan na wuce nawa.A wannan daren ban rumtsa ba sam, system na ɗauka na soma yin binciken da y shafi aikina har aka kira sallar asubah bayan na dawo daga sallah na ɗora daga inda na tsaya.Wuraren ƙarfe tara na tashi na yi wanka na shirya cikin ƙanana kaya wando jean da rigarsa ,ko agogo ban saka ba na fita. [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 3-4 Tun daga nesa nake ƙare musu kallo,sai kace wani ƙaramin yaro sai ririta amayar yake ya na bata abinci a baki ko kunya bai ji har da wani ɗora ta kan cinyarsa ita kuma uwar iya yi da rashin kunya ta na gyara masa hullar kansa. Na ɗauke kaina,har na ida sauko wa daga kan benen ban kalle su ba ina shirin zama kan kujera na ji Daddy na wata irin dariya mai cike da tsantsar farin ciki ya na cewa “Baby ba fa haka ake ɗora hullar ba,na faɗa miki kan zakin can gefe yake kallo” “Uhum!Umhum! Ni dai haka ta fi min kyau Baby” ta faɗa cikin wata shagwɓar da tasa na yi saurin ɗaga kai na kalle su ,aka kuwa ci sa'a shi ma Daddyn ya ɗago ya na kallon saitin da nake.Da ido na tsure shi da su rai ɓace,da sauri na ga ya sauke ta daga kan cinyarsa ya ɗora ta kan kujera.Ta taɓe baki ta na kallona,ashe kallon tsoro na yi mata a jiya tsohuwar yarinya ce ƙaramin jiki ne kawai da ita ta ci uban bleachin ta yi fayau. “Ibraheem ka fito?” Daddy ya tambaye ni,ban amsa ba na fasa zaman na wuce part ɗin Granny ina jin zuciyata na tururi.A zaune na tarar da ita ta na shafa maganin ciwon ƙafa,na zauna kusa da ita ina mai gaishe ta ciki-ciki. Ta amsa da “lafiya lau ka ci abinci ne?” na girgiza kai ta ci gaba da cewa “da kaina fa na zaɓi abin da za a dafa ganin jiya ba ka ci wani abin kirki ba” ban ce komai ba sai ƙafarta da na soma matsawa. “Babana ban son shirun nan,faɗa min mi aka yi?” “Daddy ne” na faɗa cike da takaici. “Mi yayi kuma?” “Shi da matarsa ne...” na cije leɓen ƙasa kafin na ci gaba da cewa “kamar wani ƙaramin yaro shine zai zo tsakiyar falo da girmansa da darajarsa ya na ba ƙaramar yarinya abinci a baki har da ɗora ta a cinya? Granny in ni ɗansa ne na kawar da kai su kuma ma'aikatan gidan nan fa?” “Don Allah fita batun su,bani makullin ɗakin ka zan sa a ƙara gyara shi kafin Ammyn ka su ƙaraso” Granny ta faɗa . Na ce “wato ke ma kin basa goyon baya ya ci gaba da yin haka?” Granny ta ce “to mi kake so na ce Babana? Duk tsiyarsa dai ai ba zai koma saurayi ba,ban makulli ka ji” “Wai yanzu gaske kawo ta Ammy za ta yi? Allah ni ban shirya wani zama da mata ba” na faɗa ina mai kwanciya kan lalausan capet ɗin. Granny ta ce “yau na ga abin da ya fi ƙarfina wai tsohuwar da ƙirgen dangi! Yanzu Babana kai ne ba ka shirya zama da mata ba? To halan so kake sai ka zama tuzuru sannan?” Na turo baki tare da lalubo key ɗin na miƙa mata na ce “ni dai wallahi inda ma wurin ki ta zauna” Ta na dariya ta miƙe tsaye ta ce “tun da ni aka aura ma ita ba.Tashi mu je ka ci abincin” “A kawo min nan ba zan sake fita na ga kayan takaici ba” “Ka ji wani zancen mutum da matarsa,kai ma ai ka kusa hutawa da zamana gwabranci can a yi wa kaji zabbi hira suke” ban sake cewa komai ba har ta fita,can sai ga ɗaya daga cikin ƴar aiki ta shigo da sallama ta kawo min abincin. Da kaina na zuba na ci sama-sama kafin na sha ruwa na haye katifar Granny,wani bacci ma na soma ji amma ina tunawa da Abakar ya bar duniya sai na ji ya fita idona.Da sauri na fito don tambayar Daddy inda yasa aka kai min akwatina sai kuma na tarar da shi a tsaye ya na kallon tv da ke manne a jikin bango. Zuciyata har wani tsalle take tsabar yadda allurar soja ta motsa,bresking New ne ake ƴan ta'adda sun kai hari a wani ƙaramin ƙauye da ke cikin Zamfara sun kwashe shanu da kuma wasu samarin garin. Daddy na kalla na ce “sai yaushe ne ƙasarmu za ta bar fuskantar ƙalubalen nan? Gagarar mutane ne suka yi ko rashin iya aikin jami'an tsaro ne?” kallona yayi ba tare da ya ce komai ba ya fita,da sauri na nufi matakalar da za ta sada ni da sashena.Bibiyu nake taka ta har na isa,ina shiga ɗakin na tarar da Granny da ƴan aiki su na ta gyaran falon direct bedroom na wuce nan ɗin ma akwai masu gyara shi.Falo na ce su koma na canza kayan jikina zuwa kakin soja,na saka takalmi da belt na ɗora hulla sannan na ɗauki baƙin gilashi na manna.Ƴar madaidaiciyar bindiga ta na ɗauko na soke a ƙugu kafin na fito,Granny ta tare ni ta na cewa “ina kuma za ka je?” “Wani ɗan aiki za mu yi ki sa min albarka ” “Allah tsare ya dawo da kai lafiya” Na amsa da “amen kafin na fito” Ina saukowa ƙasa na ji matar Daddy na waya “iyeee ke tsohon ɗan duniya ne inda kin ga yadda ya susuce jiya a kaina,na san tun da yake aure-aurensa bai taɓa samu mace haɗaɗiya kamar ni ba” Godiya na yi ga Allah da falon babu kowa masu tsaron gidan duk su na waje,da wannan takaicin na fito na ɗauki motata na bata huta. Sai da na hau kan titi sosai sannan na daidaita gudun motar na kira Ammy,har ta tsinke ba ta ɗauka ba sai a kira na biyu. “Ina kwana Ammy kin tashi lafiya?” na faɗa cike da kwantar da murya. “Lafiya lau alhamdullah! Ga mu a mota muna hanya ina ta bacci sai da Maryam ta tashe ni” cewar Ammy,na ɗan jan numfashi na ce “Ammy ni da na so na ce ku ɗan jira kar ku zo yau” “Saboda me?” “Ammy jiya fa Daddy ya kawo wata” na faɗa ina cije leɓena na ƙasa. Ta ce “ina ruwana da matarsa? Ai ni bai gabana ballantana wata can banza” “Zan sake kiran ki in na sauka Allah tsare hanya” na faɗa ,bayan ta yi min addu'o'in da ta saba na kashe.Ina isa can babban Barack na tarar da sojawa birjit duk sun yi uban layi,na san bai wuce umarnin Daddy ne ya na son tura su can inda abin ya faru. Mota na parker sannan na nufi hanyar da za ta sada ni da ofishinsa,duk da ya na mahaifina sannan kuma na kasance soja hakan bai hana masu tsaron ƙofar hana ni shiga ba. “Shi ne ya bada umarnin kar wanda ya shiga” “ Ku bar ni na ce akwai maganar da za mu yi” na faɗa a karo na biyu,amma suka ƙi nan fa muka hau rigimar da ina tunanin ita ta jawo hankalin mutanen ciki har aka buɗe ƙofar. Sergent Yakubu ne ya na ɗaya daga cikin waɗanda Daddy ke hulɗa da su ba a harakar aiki ba kaɗai,“ku bar shi ya shigo” ya faɗa ya na bani hanya don na wuce.Na yi musu kallon banza sannan na shige,a zaune na tarar da Daddy ya zube wasu duwatsu akan teburi alamu dabarun yaƙi yake shirya wa. “Daddy?” na furta ,shiru bai amsa ba na sake cewa “Daddy ina son zuwa don Allah ka sa a tafi da ni ” nan ma ɗin shiru yayi har sai da Sergent Yakubu ya ce “ shugaba za ka ce” “Ka dai barsa ya ɗauka nan a gida muke” Shiru na yi ina kallonsa,ya ɗago ya shi ma ya na kallon nawa kafin ya ce “ a gabana za ka tsaya da baƙin gilashi?” “Ka yi haƙuri yalaɓai ban iya kallon tsakiyar idonka ne shi yasa,amma ina neman alfarma don Allah ka tsara tafiyar nan da ni” “Captain IBRAHEEM Isa ba za ka je ba” ya faɗa tare da miƙe wa tsaye ya mayar da hankalinsa ga Sergent Yakubu ya ce “ daidai nan da nan za mu baza dakarun mu ta yadda za mu zagaye abokan hamayya,ka ga duk yadda aka yi dai mune da nasara in sha Allah saboda kowanne bango mun zagaye su” “In kuma aka yi rashin sa'a kafin su isa su ƴan ta'addan sun bar wurin?” Sergent Yakubu ya tambaya. Daddy ya ce “ har yanzu dai su na wajen kuma ba zata ce za mu yi musu ” “An bi didigi an gano inda suke?” na yi tambayar ni ma ina ƙara matsawa,Daddy ya ɗago a hassale ya ce “ wai mi kake jira ne? Ba na sallame ka ba?” “Don Allah Daddy ka bar ni na je” “Ba za ka je ba fitar min daga ofis ko na sa a zo a fitar da kai ta tsiya ” ya faɗa cikin tsawa ya na nuna min ƙofa. Amma abun ka da soja na dake na ce “ Yalaɓai mine ne amfanina kenan in har wata matsala za ta taso ba tare da na bai wa ƙasata kariya ba?” “ Sai ka ajiye aikin tun da ba ka ga amfaninsa ba,Sergent Yakubu biyo bayana” Daddy ya faɗa tare da kwashe duwatsun kan teburin ya nufi wani ɗaki da ke cikin ofishin.Haka na bi su da kallo har suka shige ina jin lokacin da aka murɗa key ta ciki,na ja ajiyar zuciya tare da zagayawa na zauna kan kujerar da Daddy ke zama .Kamar an mitsike ni na jawo ɗan ƙaramin aljihun table ɗin,wani ƙonanen agogo na gani na ɗauke shi ina dubawa a kallon farko na gane na Abakar ne don ga farkon sunansa nan da na mahaifinsa a jikin ƙarfen kamar yadda duk wani soja da za a bai wa ita ake masa haka.Mayar da ita na yi na soma bincike har na kai ga liste ɗin sunayen waɗanɗa suka mutu,a nan ne na gano ita gawar Abakar sam ba a ganta ba.Jikina har rawa yake wurin maida komai yadda yake kafin na fito,tuni sojawan har sun shiga motoci riƙe da bindigogi. Na je kusa da babban Sojan da ke kula da duk wani yaƙi ko tafiya in ta kama na ce “ a wacce mota zan shiga?” “ Banda sunan ka a jerin sunayen da Shugaba ya bani ikon na tura” ya bani amsa. “Saboda me?” “Ƙila don ba ka daɗe da dawowa daga mission ba” “Amma ya na ga har da waɗanda a tare muka dawo ɗin wasun su na ciki?” Ya dube ni da kyau ya ce “ mahaifin ka za ka tambaya ba ni ba” ya na gama faɗa yayi gaba ya bar ni nan.Ina ji ina gani motocin suka fita suka bar ni,ina cikin wannan takaicin Daddy ya aiko kira na.Ina shiga Sergent Yakubu ya fita ya bar mu,“zan saka wani aiki ne ka cike min takardun nan,sannan ka binciko min bayanai dangane da ƙauyukan nan” ya faɗa tare da miƙo min tulin takardu.Na karɓa har zan fita ya ce “zo ka zauna a nan ka yi” ban musa ba na ja kujera na soma cike takardun ,in jin idonsa a kaina amma na ƙi ɗagowa har sai da na ji muryarsa ya na cewa “Ammyn ka ta kira ni ...” sai kuma yayi shiru ya na kallona,na ce “mi ta ce ma?” “Za ta zo nan gida” Na ci gaba da abin da nake kafin na amsa masa da “eh na sani” “Zuwan nata ne ba na tunanin zai haifar ɗa mai ido,ka san halin ta ba ta ƙaunar zaman lafiya” “Shugaba wannan fa tsakanin ku ne bai kamata ka shigo da ni ciki ba” na faɗa ina mai kwashe takardun,na fita. Motata na shiga ban zarce ko ina ba sai ɗayar Compagnie ɗinmu inda a can wurin kwana yake.Ɗakin na buɗe,duk yadda na so kar na yi tunanin Abakar abu ya cuttura.Rabi da rabi na yi aikin,sallah kawai ke tsayar da ni sai dab da magrib na fito na nufi gida.Bayan na yi parking sai da na ɗan zauna na wani lokaci kafin na fito,da sallama na shiga falon idona ya sauka kan Ammy.Da sauri na je gabanta na gaishe ina mai gaishe ta,cike da fara'a ta amsa ta na tambaya ta ya aikin na amsa “Alhamdullah” Granny ta ce “baƙauyar amaryar ka ta zo,sai kuka take da rantse-rantse ita ba za ta haura saman bene ba” Shiru na yi ban ce komai ba,na miƙe na ce “Ammy zan je na yi wanka lokacin magrib ya gabato” “A fito lafiya” ta faɗa ,ni kuma na wuce na fara taka matakala kenan na ji muryar matar Daddy na cewa “Baby ga IBRAHEEM ɗin nan sai yanzu ya shigo,kaiii?” ta wani kira ni kamar ƙaramin yaro ko waigawa ban yi ba na idasa hayewa. Ina tura ƙofar falon wani ƙamshi ya ziyarce ni,na lumshe ido ina shaƙar ƙamshin kafin na wuce bedroom.Allah na gani sam ban lura da ita ba sai da na ji uban ihunta,“na shiga uku na lalace mugun abu soja na a gabana?” ido kawai na zuba mata duk uban ihun nan na zata tsoro ta ji wai ashe murna ce take ta ga soja .Rikitatun idona na zuba cikin nata,da sauri na ga ta je bayan labule ta ɓuya kafin ta fara leƙe ban ce mata komai ba na je gaban mirror na yi tsaye idona na ga sun yi ja sosai. “Je ki waje” na faɗa dakyar don so nake na canza kayan jikina . Da gudu ta fita ta na bangaje ƙofa, cire uniform ɗin na yi kafin na shiga toilet wanka na yi haɗi da alwala sannan na ɗauro towel daidai ƙuguna.Kan bed na tarar da ita ta zuba uban tagumi,muna haɗa ido ta ja blanket ta rufa ta na karkawa har gadon sai da ya dinga rawa ta ce “yi haƙuri....”cikin raunataciyar murya ta na mai fashewa da matsanancin kuka mai cin rai. Na rumtse ido,a duniya in akwai abin da na fi tsana to kuka ne shi yasa ma ban cika son yara ba .Ina shirin fara shafa mai na ji sai ƙara ƙaimi take wurin kukan,zuciya cunkushe na nufi bed na zauna tare da yaye blanket ɗin.Da sauri ta yi baya ta na curewa wuri guda,kamar mai koyon magana na ce “ mine ne?” shiru ta yi bata bani amsa ba,“ ban son kukan nan ki yi shiru” Cike da ƙurciya ta ce “ tsoro nake ji” “Tsoron me?” “Matakalar bene kuma ...kuma ni ban son nan wurin Ammy nake so kar ta tafi ta bar ni ban san kowa ba” ta bani amsa ta na shasheka kamar ranta zai fita. “Ni wane ne?” na jefo mata tambayar ba tare da ni kaina na shirya ba.Ta buɗe fuskarta ta tsure ni da manyan idonta,kafin ta ce “abokin Ya Abakar wanda azzalumai suka kasheee” shaaa kuma sai wasu hawayen tare da ɗaukar wani sanfarin kukan.Ji na yi tamkar ta taƙalo min wata masifa daga can ƙasan zuciyata,raɗaɗin rashin Abakar ɗin ya dawo min sabo dal kamar yanzu ne aka shaida min mutuwarsa.A duniya tun da nake ni ban taɓa rarrashi ba,don banda ƙanwa sannan cikin aikin soja na girma ta yadda zuciyata ba ta san soyayya ba in ka fidda ta iyayena da kuma abokina.Rasa yadda za a yi na rarrashe ta na,kamar wani mai jin tsoro haka na jawo ta jikina tare da ƙoƙarin haɗe dafin da nake ji a cikin maƙogorona don na samu na yi mata magana..... [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 *YA Ubangiji rahama don ƙarfin ikonka ka wanzar da Zaman lafiya a ƙasata Nijar da Nigeria da ma duk sauran ƙasashen da ke fuskantar ƙalubalen rayuwar nan alfamar Manzon Rahama*👏🏻 5-6 “Yi shiru mana,ban son kukan nan Mary . Addu'armu ya fi buƙata a wannan lokacin,ki godewa Allah ɗan uwanki yayi mutuwar mazaje wacce ba kowa ne ke samun irin ta ba.Mutuwa a filin daga,domin kare ƙasarsa” na faɗa tare da ƙara janta jikina ina goge mata hawayen da suke ta faman yi mata zarya. Cikin muryar kuka ta ce “ abokin Yaya ina cikin damuwa na rashin ɗan uwana,amma Ammy ta ce da kai da shi duk ɗaya ne duk kulawar da yake min kai ma za ka iya kuma zan fi jin daɗin zama da kai fiye da in zauna wurin ta”ta yi maganar ta na faman cusa kanta a ƙirjina. Na ce “ eh gaskiya Ammy ta faɗa ,kin manta Abakar ƙanena ? Kin ga ke ma ƙanwata ce.Daga yau ban son ƙara ganinki ki na kuka,duk abin da kike so kuma ki sanar da ni” Ta gyaɗa kai tare da cewa “ Ammy ta ce za ka kai ni ƙaton kanti ka saya min kaya” Na ce “ eh sai in kin huta za mu je” “ Yaushe kenan?” “ Ko zuwa jibi haka” “ Ba gobe ba?” “ Za mu je goben to” na faɗa ina mai janye ta daga jikina tare da ƙoƙarin sauka daga bed ɗin,ta ce “ kenan kai ne mijina?” Dariya tambayar ta bani,na ce “ Mary shekarun ki nawa?” “Sha tara” ta bani amsa,na juyo ina kallon ta ban san mi yasa ba sai nake ji a raina ina son jan ta wasa na ce “ mai ƙarya dai ɗan wuta ne” Ta buɗe baki ta na murmushi,na kafe ta da ido ganin fara'ar nan yasa na ji daɗi . “ Na waɗa ma gaskiya ?”ta yi tambayar cikin Hausar ƙauyensu na Sokoto. Na yi murmushi na ce “ eh faɗa min” “Kai dai shekaruna Sha shida na” “Sha shida ne za ki ce” Ta turo baki ta ce “ ni wa ba zan iya yin Hausar ku ba,yawwa na ce ku nan kowa na da abun hawa na? Gari duk ko ina motoci na birjit awar an taso daga sallar idi ” Ban bata amsa ba na soma shafa mai da turare,ta madubi nake hango yadda take kallona.Na yi gyaran murya na ce “ ki je ki ci abinci” “ Ban jin yunwa” “To koma falo zan shirya” da “toh” ta amsa ta fice. Drower na buɗe na fiddo kayan da zan saka,ina tsaka da saka kayan kamar an ce in juya na hange ta ta na leƙe na.Muna haɗa ido ta tuntsire da dariya kafin ta gusa,na girgiza a zuci ina cewa ‘ yau na ga ikon Allah ’ bayan na gama na fita falon na tarar da ita a zaune ta ƙura wa ƙofar fitowa ido. Na ɗan haɗe rai na ce “ mi yasa kike leƙe na?” Ta sunne kai ƙila ta tsora ta da yanayin nawa,ta ce “ Ammy ta ce kar na ji kunyar ka kai mijina ne duk abin da za ka yi ni zan taya ka har saka kaya da wanka” Na waro ido ina mamakin ya kuma Ammy za ta faɗi haka,na ce “ shi ne sai ki leƙe ni ?” ta ɗago kai ta ce “ to mine ne in na yi hakan kai ai mijina ne” sai ta soma wasa da awarwaron hannunta na duwatsu. “ Na ji tashi mu sauka ƙasa” ta maƙe kafaɗa ta ce “ Allah tsoro naka ji” “Nake ji ake cewa” na gyara mata da sauri kafin na miƙar da ita tsaye ta na turjewa muka fito. “Kwarankwatse ba zan sauka ba” ta faɗa ta na shirin zubewa ƙasa ta riƙe ni gam. Na ce “ to waye ya hauda ke saman?” “Ammy ce da wata tsohuwa” “To na ji ki nutsu babu wuya fa ki kalli yadda zan yi” Ta ce “ Na wa san bene, kai hawar shi ta a ban yi saboda ina ganin jiri ” Cak na ɗauke ta na soma sauka da ita ƙasa,ido ta rumtse gam har muka sauka na aje ta ina mai cewa “ baƙauya” Ammy da Granny suka saka dariya ni kuma na fita zuwa masjid.Ina can aka kira sallah,bayan an gama na shigo ciki muka je muka ci abinci gaba ɗaya Granny ta miƙe ta nufi ɗakinta. Kusa da Ammy na dawo na zauna ji nake kamar kar lokacin ya shuɗe,“ Ammy yanzu tafiya za ki yi?” “Tambayata ce kake?” ta faɗa tare da kallona,na gyaɗa kai. Ta ce “ zuwa gobe in sha Allah zan koma” “Don Allah ki tsaya ko sati ɗaya ne ki yi” na faɗa . Ta ce “ a'a ba zan jure ba Heemu,ɗazu ai ka ga rainin hankali da matar Ubanka ta yi yadda take wani kiran ka da gadara so ta yi na tanka mata don kawai a yi faɗa ” Na ja numfashi na ce “ Ammy mi yasa ba za ki dawo nan da zama ba? Ban son ganin ku a rabe ke da Daddy ” Sai da ta kalli Maryam kafin ta ce “ jeki sama Maryam ” Ta ce “Ammy na dai je ɗakin waccan” “Okay tashi ki tafi” ta miƙe da saurinta ta na gyara hijabinta wanda tun da ta yi sallah ba ta cire ba. Bayan tafiyar ta ne Ammy ta dube ni da kyau ta ce “ faɗa mini matsalar ka” “Babu Ammy ni burina kawai ki dawo nan ɗin” ta girgiza kai ta ce “ na bar Daddynka har abada,tun ka na goye na bar gidansa bai taɓa tunanin dawo da ni ba sai ni ce zan sarkawa? Ya je yayi ta aure-aurensa wata rana sai ya auro aljana” “Ammy na sani Daddy yayi laifi amma hukuncin da kika ɗauka ne yayi tsauri sosai ” na faɗa cikin jimami ina tuno abin da Granny ta ce min game da mafarin rabuwar. Ammy ta yi wani murmushin wanda ka ganinsa ka san na takaici ne kafin ta ce “ tun bayan da na koma gida bai taɓa tako ƙafarsa ba sai da ka shekara goma a ranar da ya zo ya tafi da kai ya saka ka makarantar sojoji,ya nuna min iko ya maido ka gidansa da ace ya na ra'ayina ai a tare zai maido mu” idonta ne na ga sun cika da hawaye,da sauri na miƙe ina cewa “ kuka kuma Ammy? Don Allah a'a” sai na shiga goge mata su. Jiniya ce ta cika gidan alamun Daddy ya dawo,muna nan tare da Ammy amaryasa ta fito cikin murna.Daddy na shigo wa ta yi tsalle ta rungume shi ba tare da ko kunyar escort ɗinsa ba da suka yo masa rakiya. Raina ne na ji ya sosu musamman da na ji Daddy na cewa “ za ku iya tafiya yanzu lokacin iyalina ne” Ammy ta je ta miƙe na mayar da ita. “Muuuah! Muuuah!” kawai kake ji amaryasa na masa kiss wanda ina da tabbacin da gayya take yinsa ,shi kuwa Daddyn kamar wani soko yayi tsaye na yi imanin bai lura da mu ba da tabbas ba zai tsaya ba. “Mi kika girka min Bab...” sauran maganar ce ta laƙe a maƙoshinsa da muka haɗa ido da shi.Da sauri ya janye ta daga jikinsa “ jeki ɗaki ina zuwa” ya faɗa ita kuma ta harare ni kafin ta wuce. Daddy ya wani haɗe rai ya na mai ƙaraso wa inda muke,na taɓe baki tare da barin wurin na fita zuwa masjid. Daddy yayi gyaran murya ya ce “fatan kin sauka lafiya?” Ammy ta ce “ lafiya lau alhamdullah har ina shirin komawa ma” Ya shafi gefen wuyansa ya ce “ to madallah ” Ammy ta ƙure shi da ido ta na kallonsa kafin ta ce “Isah sai yaushe za ka sanin ciwon kan ka? Aure-auren naka har ya kai ka auro karuwa wacce ba ta san mutumcin kanta ba? A gaban ɗan cikin ka kake sumbatar mace? Ayir ɗinka wallahi ka bani mamaki ....” Daddy yayi saurin katse ta da “ don Allah Maimuna ban son tsiyar gumi.Ina ruwan ki da matata ? Wato kishi kike don kin gan kin koma tsohuwar akwala babu mashunshuni haushi ya kama ki kin ga na auri ƴar shilla?” Sam ba su ga zuwan Granny ba sai saukar marin da ta kifa wa Daddy,ya dafe kumci ya na kallonta “ Mama...” da sauri ta katse shi “ rufe mini baki! Wato kai ba ka ƙaunar zaman lafiya daga ta na faɗa maka gaskiya shikenan sai cibi ya zama ƙari?” “Wace gaskiya Mama ? Kawai banda ikon sakewa da matata?” “A gaban ɗanka? In shiriritar kuke so mi zai hana ku yi ta can sashen ku? Kai yanzu ba zubewar girman ka ba ce da matsayinka da ikonka a gan ka kana abin yara? Dubi gemunka farin gashi ne ya fara tsiro wa amma a haka kake rungumar ƙanƙanuwar yarinya a gaban ɗan cikin ka.Maimuna mu je,ke ma da naki laifin ban ma san mi ya tsayar da ke nan ba” Granny ta faɗa tare da jan hannun Ammy suka koma can ɗakinta. Maryam na zaune ta na karatun Alkur'ani,yanayin da ta ga Ammy ne yasa ta yi saurin rufewa ta nutsu sosai. “ Tashi ki koma sashen ku Maryam ki tabbatar kin yi wanka kin yi sallar isha'i kafin ki kwanta” cewar Ammy, Granny ta ce “a'a ki barta a nan har a jima” Ammy ta ce “ to ni zan ɗan kwanta ” dama fashin sallah take hakan yasa Granny ba ta ce komai ba.Karatun suka ci gaba da yi ita da Maryam inda ta yi kuskure sai ta gyara mata,Maryam ta ce “ ya aka yi kika iya karatu Kaka?” “To in ba abin ki ba ta ya ba zan iya ba tun da ba makarantar Boko na yi ba mai zurfi” “ Tun ki na yarinya kenan kika iya?” Ammy ta ce “ Maryam ba a tsare babba da tambayoyi” Granny ta ce “ a'a bar ta mana ita ma in ta tsufa haka jikokinta za su tsare ta da tambayoyi” Maryam ta ce “ ni dai gaskiya ban so na tsufa” Granny ta dinga dariya ta ce “ ai baƙin gashin nan a sannu zai koma fari sol” Maryam ta hau kukan sangarta. Ammy dai na jin su ba sake kula su ba,furicin Daddy sosai yayi mata tsaye a zuciya wai ta ƙi yin aure saboda babu mai sonta.Wasu hawayen takaici suka zubo mata a zuci ta ce ‘ in sha Allahu zan baka mamaki zan cire ka a rai na je na auri wani’ da wannan tunanin dai ta yi bacci. A can ɓangaren Daddy kuwa cike da jin haushi ya nufi ɗakin amarya Zainabu,a yadda ya tarar ta ci uban shiri cikin kananan kaya sai ya nemi fushin ya rasa.Ita ma cike da iya yi ta zo ta rungume shi suka gama shiriritarsu,kafin ta yi masa rakiya zuwa toilet yayi wanka .Sai da ta cika masa tumbinsa sannan ya je masjid ,ganin IBRAHEEM ne yau zai ja su sallar ya ji haushi sosai don ya matsu ya koma ciki wurin amarya . Cike da nutsuwa nake gabatar da sallar har muka kammala,kamar sauran lokuta a tare muke komawa gida ni da Daddy.Da sauri na miƙe na isa gare shi,ina son yi masa magana ne akan Ammy sai dai shi ya tari numfashina ya na mai cewa “ don Allah ka bar jan dogon karatu,wasu ba sa iya jurar tsayuwar nan ka yi ta karatu sai ka ce muna ƙiyamul laili?”yayi maganar ya na ɗaga ƙafa da alamu sauri yake. Na ce “ yaushe soja ya fara tsoron tsayuwa? Duk sojawa ne sun saba dama to ai ni ban ga wata damuwa ba don an ja dogon karatu.Aka yi tsayuwa akan lamarin duniya sai wurin bautar Ubangiji ne za mu samu rauni?” “To in fa mutum na da uzuri ? Irin hakan dai babu daɗi na faɗa ma” “ Daddy na ga alamun kamar ka na sauri ga shi kuma ina son yin magana da kai” na faɗa ina jan numfashi daidai nan muka iso ƙofar da za ta sada mu da babban falon gidan. “Ya ce ba yanzu ba ka bari zuwa gobe” “Amma Daddy...” shiru na yi sakamakon ganin amaryar ta sake fitowa cikin wata shiga ta riga da wando duk sun matse ta rabin mamarta duk a fili .Da sauri na kawar da kai ganin ta rungume mahaifina duk da kuwa ƙoƙarin hanata da ya so yi,“ Haba Zee ya za ki fito haka wuce gani nan zuwa” “ Ni dai... Ni dai Baby na ƙi wayon mu je ƙafarka ƙafata na sh....” sauran maganar ban ji abin da ta ce ba,na fi zaton Daddy ya toshe mata baki ne. “ To na ji na baka minti biyu” ta faɗa kafin kuma na ji ƙarar takalminta alamun ta tafi. “ Ibraheemu mi ka ce?” Daddy ya tambaye ni a ɗan daburce,sai yanzu na juyo na kalle shi da jajayen idona da suka rine tsabar ɓacin rai .A nan tsaye na barsa na wuce part ɗina, matakalar ma ban ganin ta da kyau. Ina shiga ɗakina direct bedroom na wuce na kwanta rairan ina kallon sama,zuciyata sai tuƙuƙi take. ‘ Wai mutumen da in za ka gansa sai ka yi fiye da sati guda ka na shan wuya,mutumen da in shugaban ƙasa zai fita sai ya bayar da izinin zai iya fita babu wata matsala,mutumen kowanne soja jininsa a akaifa yake in ya aiko kiran ka ko kuma in ransa ya ɓace shine waccar abar take cewa ta basa minti biyu?’ na yi wa kaina tambayar a zuci ina jin farashin ƙunci,baƙin ciki da takaicina su na ƙara yin sama. A daidai wannan gaɓar mutum ɗaya ne kacal ke saurin yin nasara kaina wurin sauke fushina,yanzu kuma ba ya tare da ni mutuwa ta yi mana yankan ƙauna.Haka na ci gaba da juyi a bed ina ta ƙoƙarin tunkuɗe lamarin amma abu ya cuttura,sama da awa biyar ina cikin hali guda.Dakyar na miƙe na je na shiga toilet,ko kayan jikina ban cire ba na sakarwa kaina shower.Ina nan daga tsaye na ji kukan Maryam,Ammy kuma na yi mata faɗan doli ta koyi hawa bene sannan ta jaddada mata nan ne ɗakinta kar ta saki ta kwana ɗakin Granny. Ina jin lokacin da ita Maryam ɗin ke cewa “ Ammy shikenan ba zan sake komawa bacci ba tun da kin tashe ni” Ammy ta ce “ ni ma ai don baccin ya sace ni ne amma ai sam da ba zan bari ki kwanta can ba,ki tabbatar kin yi wanka kin yi brush kafin ki kwanta” tsit kuma ban sake jin sautin muryoyinsu ba. Na ja ajiyar zuciya kafin na tuɓe na yi wankan soso da sabulu na fito ɗaure da towel a ƙugu ,ɗan ƙarami kuma ina tsane gashina. Zaune na tarar da ita ta buɗe trolly duk ta zubar da kayan da ke ciki sai wani turo baki gaba take,gaban dressing mirror na tsaya na yi shafe-shafe sannan na zaɓo kayan bacci masu riga mai sauka har ƙasa.Ina ganin lokacin da ta shiga toilet matse da kayan da za ta canza,da wannan ni ma na saka nawa kafin ta fito na je na haye bed bayan na kashe ƙwan lantarki sai na kunna fitilar bacci. Tunani na soma yi kan shuɗaɗiyar rayuwarmu ni da Abakar,«aboki don ba ka da ƙanwa ne da ka ji irin yadda nake ji,Maryam komai ce nawa.Farin cikinta ya fi min komai daɗi a duniya,aikin nan ma domin ita da Umma nake yinsa.Na ci burin yi wa Maryam kayan ɗaki na kece raini a matsayina na waliyinta maɗaurin aurenta» wannan na ɗaya daga cikin zantukan da yayi min game da Maryam. Yadda ta fado jikina ta bi ta kaina yasa ta katse min tunanin,“ ni wallahi sanyi naka ji ba don na yi wa Ammy alƙawarin ba,in na yi wankan nan shegiya nakai ” ta faɗa cikin mita tare da gyara kwanciyarta ta ja bargon da nake ciki ta rufa.Duk da ta rufa ɗin bai hana ta rawa sanyi ba,kamar wanda aka yi wa doli na ɗan matsa kaɗan sai gani kusa da ita sosai.A hankali na ɗan kwanta ta samanta na yi mata rumfa da ƙirjina,hannunta na ji gefen cikina ta sarkayo shi haɗi da riƙe wa gam ta ce “ ina jin sanyi sosai” Bargon na ida ja ya rufe mu har wajen kai,a hankali kuma na matsa fuskata kusan tata ta yadda muna jin numfashin juna.Ƙamshin turarenta ne ya sakar min wata kasala da na kusanci wuyanta,ban san lokacin da na saki wani gauron numfashi ba ina mai sake saka ta ƙirjina.Tuni Maryam ta fara mitsirniya,gefen wuyanta na soma aika ma sumba kafin na yi sa'ar lalubo bakinta na fara kissing.Sam ba ta yi ƙoƙarin hana ni ba da alamu ma ta na jin daɗin haka don sai ƙara riƙe ni take, wannan yanayin da na tsinci kaina sam ba zan iya faɗar yadda yake ba.Bugun zuciyata ne kawai ke ta tsananta ya na bada sauti na musamman,sama da minti talatin kafin na janye daga jikinta na koma gefe ina mayar da numfashi.Blanket ɗin na janye na maido shi iya ƙirji,idona a lumshe ina jin raina yayi ɗan sanyi ba kamar ɗazu ba.Na kai hannu na jawo ta na ɗora kanta kan ƙirjina yayin da kuma hannuna ke kan bayanta.Murya can ƙasan maƙoshi na ce “ kin bar jin sanyin ?” kamar wata munafuka ta ce min “ eh!” “ ok yi bacci” “ uhumm !” shiru duk muka yi ina ta mamakin kaina ,ɗaya ɓangaren kuma na sakawa Ammy da alkhairi da ta haɗa auren nan... [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 7-8 Kiran sallar farin ne ya tashe ni daga dadaɗan baccin da nake.Ina ware ido na yi tozali da fuskar Maryam kwance kan ƙirjina sai baccinta take,moments ɗinmu na jiya ya dawo min na ɗan yi murmushi ina mamakin kaina .Janye ta na yi na nufi toilet na yi wanka,da na fito na shirya caf cikin jallabiya ruwan ƙasa .Sai da na yi nafiloli sannan na wuce masjid ,bayan mun gamo sallah na dawo gida har yanzu ba ta farka ba. Blanket ɗin na yaye ina mai kiran sunanta “ Mary ? Mary tashi ki yi sallah” ta ware idonta kaɗan kafin ta sake lumshe su har da gyara kwanciya ta ci gaba da baccinta.Na dafe goshi na ce “ Ammy kin kawo min aiki” ƙara tashe ta na yi,ta na gunguni ta tashi zaune ni kuma na fita na ɗauki key na je na buɗe mota na ɗauko takardun Daddy ya bani.Ina komawa bedroom na ga ta sake komawa bacci,raina ne na ji ya ɓace cikin ɗaga murya na ce “ keee! Tashi na ce har yanzu ba ki yi sallar ba ne ko me” A firgice ta tashi ta na kuka tare da zuba min manyan idonta,“ ba za ki wuce ba kenan?” na faɗa ina nufo ta da sauri ta ruga ta shige toilet ina jin ƙarar shower na tabbata wanka take.Falo na koma na soma yin aikina,wani iri nake ji na rasa gane mike damuna ma a yanzu. MARYAM Wani irin mugun tsoron Ibraheemu ne ya shige ta,duk yadda take da tsiwa sosai take shakkar idonsa.Ta na shiga wanka ta soma yi kamar yadda Ammy ta sanar da ita kullum kafin sallar asubah ta fara yin wanka ta yi kuma brush.Maclean ɗin da ta gani ta matsa ta wanke bakinta,soso ma da nasa ta yi amfani sannan ta fito ta saka rigar sallah ta gabatar.Bayan ta gama ta soma karatun Alkur'ani inda ta iya kafin ta zo wanda Granny ta yi mata,ganin ta na ta yin gargada yasa ta yi shiru kar ta yi saɓo. Miƙewa ta yi ta gyara shimfiɗar gadon ,ta fesa turare wanda tun jiya Ammy ta nuna mata ma'ajiyarsa.Toilet ma sai da ta je ta wanke ta sannan ta fito ta haye bed sai bacci. IBRAHEEM Ina nan zaune ina aiki kiran Ammy ya shigo wayata, Allah na gani abin da yasa ban je na gaishe su tun da asubah ba don kar ta yi min zancen tafiyarta ne. Kiran na ɗauka ko kafin na ce wani abu ta ce “ ka sauko ƙasa” sai kuma ta kashe. Na ja ajiyar zuciya ina jin wani yanayi kafin na miƙe,sai da na duba bedroom na ga Maryam ta koma bacci sannan na sauka. Ƴan aiki ke ta faman gyaran falo ana ƙara ƙawata shi ,haka na wuce sai gaishe ni suke.Sashen Granny na wuce da sallama a bakina,bayan na gaishe su ne na maida hankalina ga Ammy.Ta sakar min murmushi ta ce “ zan tafi Heemu sai in na dawo wajen suna” Da sauri na sauke idona ƙasa ina cewa “Ammy don Allah ki zauna” “ Mu je ka sauke ni na hau mota” Na ɗago a karo na biyu na kalle ta,sam babu alamun wasa kan fuskarta hakan yasa na dubi Granny na ce “ don Allah Granny ki sa baki mana” Ta ce “Baba tun da ta ce tafiya za ta yi na san babu wanda zai canza mata ra'ayi,haka halin Maimuna yake yadda ka san mutanen farko sai shegiyar kafiya ” Ba don na so ba haka na ɗauki ƙaramin trollynta muka fito,har mota Granny ta yi mata rakiya ta na mai cewa “ wancan tsohon ya ƙi fitowa haka za ki tafi ba ku yi ban kwana ba” Ammy ta ce “ bai komai Mama ai na yi abin da ya kawo ni” addu'a sosai Granny ta yi kafin mu wuce.Gidan Bus na kai ta don Ammy sam ba ta son doguwar tafiya cikin ƙananun motoci,har muka kai ta na yi min nasiha game da zaman aure da kuma jaddada min girman amana .Har ciki na yi mata rakiya,na kunna mata AC seat ɗinta kafin na fito.Ban baro wurin ba har sai da na ga motarsu ta tashi,ina isa gida lokacin ƙarfe takwas na safe ya buga.Sashen Daddy na duba alamun har yanzu su na ciki ba su fito ba,wani takaici ya rufe ni a haka na haye sama. ★A ɓangaren su Daddy kuwa ya na shiga Zeey ta cika bahon wanka ya shiga kamar wani ƙaramin yaro haka ta yi masa wanka.Daddy irin mazan nan ne masu budurwar zuciya sam bai ganin ya girma shi dai burinsa kawai ya ji shi jikin mace ,a kullum bai gajiya haka kuma bai kwanan banza.Yawan buƙatarsa na ɗaya daga cikin abin da yasa ya yi wa Ammy kishiya don an yi rashin sa'a ita ba kalarsa ba ce,auren kuma bai je ko ina ba ya mutu haka yake ta aure-aure har Allah ya kawo shi ga Zee wacce ta kasance bazawara ba ta taɓa haihuwa ba fitinarta yasa mijinta ya sake ta.Yanzu kuma da ta auri Daddy sai ta ga kamar tasu ta zo daidai duk da ta fi zaton ta fi shi juriya, wannan kuma har da don ita da sauran ƙarfinta ba ta yi shekarunsa ba. A wannan daren tamkar sallah haka su Daddy aka ta more aure,sai kace wasu karnai.Sallar asubah ma yau a ɗaki yayi ta,sai wuraren ƙarfe tara suka tashi suka yi wanka Zee ta taimaka masa ya shirya cikin kakinsa na sojoji ta ɗora masa hulla sannan suka fito falo. Jin ta yake kamar ƙwai ya na jin wata muguwar ƙaunarta,ba don komai ba sai don ta iya jure nauyin buƙatarsa. Kan dianing suka zauna,da sauri mai kula da lafiyarsa ya matso ya auna abincin da wata na'ura aka tabbatar normal yake ba komai sannan Zee ta zuba musu suka fara ci ta na masa hirar soyayya. “ In ka tafi zan yi kewar ka sosai Baby ”. “ Zan dawo ai kar ki damu,duk inda zan je ki na maƙale a birnin zuciyata ” Daddy ya faɗa ya na wani murmushi.Zee ta rausayar da kai ta ce “ banda kallon mata Baby don in ka ce za ka yi min kishiya zan kashe kaina” Da sauri ya ce “ haba don Allah bari yi min zancen mutuwa,na yi miki kishiya akan me? Sai in canzawa kika yi kika dinga min rowar kan ki” Ta yi wani fari da ido ta ce “ haba Baby in na yi wa rowa ribar mi zan ci? Ai ni taka ce” cike da murna Daddy ya kamo hannunta ya ce “ Baby kin ci kyautar mota ” Zeey ta yi wani irin ihu tare da rungume shi,daidai nan Granny ta fito a gaban idonta.Ta girgiza kai cike da masifa ta ce “ Allah wadaran naka ya lalace! Yanzu kai Isah mi na faɗa ma?” da sauri Zeey ta janye daga jikinsa ta duƙa har ƙasa ta ce “ ina kwana Mama?” Ba ta amsa ba sai ci gaba ta yi da cewa “ daga yau ku dinga zama can falon ku kuna cin abinci na soke fitowa nan,in kuma wallahi ka ci gaba zan bar ma gidan ka” Hankalin Daddy ya tashi don ya tsani fushin Granny,haƙuri ya soma bata kafin ya je ya kama hannunta ya zo ya zaunar da ita kan kujera.Da kansa ya zuba mata abincin cike da kulawa,ita kuwa Granny hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba. Ta saki murmushi ta ce “ Allah yi ma albarka ” “ Amen Mamana ki daɗe ki yi ƙarko,sai kin yi Hajiya Mama uwar shugaban sojoji kike doli a lalaɓa ki a sannu in ba haka ba a tayar da yaƙin duniya na uku” Daddy ke faɗa har da wani sunkuya wa ya na yi wa Granny kirari.Ranta fari ƙal ta kai hannu ta ɗora kan kafaɗar shi ta ce “tashi ya isa haka nan wuce ka tafi aiki kar ka makara” Sai da Daddy yayi kiran waya ya shaida fitowarsa kafin ya fita,masu take masa baya ne suka yi masa rakiya har motarsa kafin su fice. Zee kuwa kasa zama ta yi kawai ta miƙe ta bar Granny nan ta na cin abinci.Ɗaki ta wuce,akwatin da ta zuba kayan matanta ta buɗe ta zaɓi waɗanda za ta yi aiki da su na daren yau.Murmushi kan fuskarta ta soma jijiƙa su a gorar ruwa ta na girgiza wa,ita kaɗai ta san irin tanadin da ta yi wa Daddy.A fili ta ce “ ba dai lamarin nan kake so ba,yau zan fito ma da asalin maitata sai na gana ma baƙar wuya ” sai kuma ta kece da dariya. IBRAHEEMU Ina shiga ɗaki ko ta kan takardun ban bi ba na wuce bedroom, doguwar jallabiyar na cire na tsaya iya wandon cikin.Hasken ɗakin na kashe na raɓa gefen Maryam,wannan tiririn da zuciyata ke yi na baƙin cikin Daddy na can da wata baƙar amaryasa nake son na kashe. Abin da na lura shine kiss na yaye damuwa,ban taɓa sanin haka ba sai jiya da na yi wa Maryam shi.Bakina na ɗora kan lips ɗinta ,tun ina yi a hankali har na soma zaƙewa saboda abubuwan da nake ji su na ratsa ni.Zuciyata ce ta ƙara ƙarfin gudu jin Maryam na mayar min da martani,ba sai an faɗa min ba ita ma koyo take kamar dai ni tun da jiya ne muka fara sanin al'amarin.Kiss ɗin ne na ji bai isa na haɗa da romance,rigar jikinta na yi nasarar cire wa na soma sarrafa ta.Kuka ta soma yi min wannan yasa na mirgina baya ina mayar da numfashi,ta tashi zaune ta ɗauki rigarta ina kallonta na ga ta mayar da abar ta kafin ta dire daga bed ɗin.Sam ban yin ƙoƙarin hana ta ba sai ma haushin kaina da na ji,ƴar ƙanƙanuwa yarinya ta kwance min tunani abun takaicin kuma ƙanwar abokina.Na ja wani numfashi tare da ɗauko pilow na rungume.Shiru na yi ina tunanin kaina ‘ yaushe na samu wannan canji? Sanina dai sai lokacin damina kawai sha'awa ke damuna,ko kuma in an yi ƙololuwar sanyi’ sai kuma na ja tsuki a fili wani sashen zuciyata na bani amsar da ‘ ƙila don yanzu an yi maka aure ne an gama ka da mace ɗaki guda’ da sauri na miƙe na shiga toilet jin abin na sake yin gaba-gaba. Shower na sakar wa kaina,ina tsaka da wanka na soma jin wayata na ruri.Kiran Ammy ne don waƙarta ta musamman ce,a gaggauce na yi wankan na fito.Ina maida kiran amma ba a ɗauka,gabana ne ya shiga faɗuwa ina shirin aika wani saƙon text ɗinta ya shigo ``` Heemu ƴan ta'adda sun tare motarmu a hanya ba zan iya ɗaukar kira ba don tuni sun sauko mu ƙasa an fara lalubar wasu ma``` Ji na yi kamar an buga min wani ƙaton dutse a kai,da sauri na saka kakina na soja da bindigogi.Jikina har rawa yake,ko kallon inda Maryam take ban yi ba na fita da gudu-gudu.Ina cikin mota na kira Daddy na shaida masa amma yake min zancen banza wai kar na je na jira zai tura sojoji amma ina tuni na soma bibiyar layin Ammy na ƙure gudun mota. Tsawon lokaci ina sharara gudu kafin kira ya shigo da lambar Ammy,na ɗauka da mamakina sai na ji muryarta ce.“Sun yi tafiyarsu sun gudu! Sun bar mu lokaci guda bayan sun yi mana mugun duka Heemu ” na rumtse ido haɗi da jan wani dogon burki ina sauraren yadda Ammy ke rera kuka,dakyar na ce “ gani nan zuwa Ammy don Allah ki bar kuka ki na ɗaga mini hankali” “ Kar ka zo Heemu yanzu ai za mu tashi daga nan...” daidai nan kiran ya katse,a ta na'urar da na jona nake bibiyar Ammy na ga sun fara gusawa daga wurin alamun motar ta tafi.Amma duk da haka bai sa na koma ba,haka na ci gaba da gudun kusan a tare muka shiga gidan Bus ɗin ni da motarsu. Ko jira ban yi ba na nufi motar,ana buɗewa na shiga ciki na riƙo Ammy.Fuskarta ta yi ja sosai ga sawun yatsu nan kwance raɗau,haka na fiddo ta na kai ta motata ina jin haushin kaina.Asibiti na wuce da ita duk ƙoƙarin hana ni da ta yi a cewar ta lafiyarta lau kawai kanta ke ciwo,sai ga shi da muka je asibitin an ce jininta ya hau.Ƙarin ruwa suka saka mata,ina daga gefenta zaune ina saƙar zuci so nake yi na yi mat tambayoyi amma ina jiran har ta dawo hayyacinta. Kamar ta san abin da nake saƙawa a rai sai cewa ta yi “sun tafi da wasu daga cikinmu Heemu” Na dube ta da sauri,idonta na lumshewa take ci gaba da cewa “da dukkanmu za su tafi da mu sai ogansu ya samu kira bayan ya dawo daga wayar ne yake cewa a tafi da iya maza kawai a bar matan” “Da yayi wayar ba ki ji abin da ya ce ba?”na yi tambayar zuciyata na mugun bugawa,Ammy ta ce “ban ji ba,sai dai lokacin da ɗaya daga cikinsu yake tambayar ogan mi yasa ba za a tafi da mu duka ba sai ya ce umarnin Dagaci ne” Dagaci babban ɗan ta'adda ne shine shugaban duk wasu manyan-manyan ƴan daba don ƙungiyarsu guda ce. Shiru na yi ina wani tunani haɗi da zargin da ban son ya zama gaskiya ,sai dai duk yadda nake son tunkuɗe zargin abin ya cuttura sai ma wasu abubuwa da suka faru masu kamanceceniya da suka shiga dawo min. Ganin Ammy ta samu ta yi bacci na miƙe na fita waje na kira lambar Daddy,bugu biyu ya ɗauka kafin ya ce “ina jin ka” sam yanzu babu alamar tashin hankali ba kamar ɗazu da na sanar da shi an kama Ammy kuma gani a hanya zan je ƙwato ta. “Ya ake ciki ka aika sojojin ne?” na jefo masa tambayar ,shiru yayi bai ce komai ba har sai da na sake maimaita tambayar sannan ya ce “ka ga Abraheemu aiki nake ” ƙittt ya katse kiran.Na bi screen ɗin wayar da kallo ina juya maganar Daddyn.Karon farko da na tuna ina da wasu abokai na biyu bayan Abakar ,zama na yi na dinga gwada wayarsu babu wacce ta shiga sai ta mutum ɗaya ya na ɗaga wa ya ce “ya ne Soldier Man ya ƙarin haƙurinmu?” “Alhamdullah! Shamssudeen don Allah ina son ganin ka akwai aikin da nake son ka yi min” Ya ce “yanzu dai ina kan hanya mun je Katsina wani aiki sai gobe za mu koma Kano” Na ɗan nisa na ce “fatan kun yi nasara?” Ya ce “eh mun kama biyu daga cikin yaran Dagaci” Da sauri na ce “yaran Dagaci ka ce?” Ya ce “eh zuwa jibi za a wuce da su Abuja” Wani irin daɗi na ji ta faɗi gasasa kenan.Na ce “to kawai zan bari har ku ƙaraso Abujar ido da ido ma za mu fi fahimtar juna” nan muka yi sallama sai a lokacin kawai na je na yi sallolina,Ammy na farkawa na bata jus ta sha magani kafin mu wuce gidanta..... [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 9-10 Maryam ganin irin halin da Heemu ya fita duk sai hankalinta ya tashi,don ba za ta manta ba irinsa ne Yayanta Abakar ya fita lokacin da ya samu kiran da za a aika su can wurin yaƙi. Tsoro,fargaba da kuma yunwar da take ji duk suka taru suka yi mata mugun bugu.Sallah ma dakyar take tashi ta yi,ga yunwa sai addabar ta take amma ba ta iya sauka ƙasa.Sai dab da magrib ne Granny ta hauro sama,shi ma don ta yi wa Ibraheemu tsiya ne ta ce tun da yayi aure shikenan sai ya ƙumshe a ɗaki . Maryam ta gani a yashe kan capet ,ta nufe ta da sauri ta na tambayar ta lafiya.Lumsasun idonta ta zubawa Granny kafin ta buɗe baki dakyar ta yi mata bayani,Granny ta shiga taɓa hannuwa ta na cewa “ shine sai ki zauna yunwa ta kashe ki a ɗaki? Ko ki na tsoron saukowa ai kya yi magana ƴan aiki su kawo miki.Shi ma dai Baba da nasa laifin ka aje ƴar mutane ka yi tafiyar ka shiru ” sai kuma ta fito ta sauka ƙasa ta sa cikin masu aiki aka haɗa abinci aka kai mata can sama,dakyar Maryam ta haɗa tea ta sha ai kuwa ta soma jin hanjinta na kuka.Babu jimawa fara kakarin amai,da sauri ta miƙe ta shiga toilet ta amaye shi. Ƴar aikin da aka turo ta soma yi mata sannu,Granny ma ta shigo toilet ɗin tare da cewa “ki haɗa mata ruwa masu ɗon ɗumi ta yi wanka” Cike da ladabi ta ce “ to Hajiya ” sai kuma ta nufi bahon wankan ta soma haɗawa ta na zuba kayan ƙamshi da sabulu da ta gama duk suka fita. Maryam ta cire kayanta sannan ta shiga,ta jima sosai ruwan na ratsa ta kafin ta soma cuɗa jikinta.Ta zubar da ruwan sannan ta ƙara tara wasu ta ɗarwaye jikinta sannan ta ɗaura towel ta kuma yi alwala don tuni an soma kiraye-kirayen sallar magrib. Ko da ta fito doguwar riga ta saka ,ta yi sallah ta na nan zaune Granny da ƴar aikin suka shigo. “Ki zuba mata kunnun in ta sha sai ta ci abincin,ya jikin naki Maryama? Ko sai an kira likita?” da sauri ta girgiza kai ta ce “ ai na yi dama kawai dai Yaya Heemu nake son gani” sai hawaye shaaa . Granny ta ja ajiyar zuciya kafin ta ce “ bari na kira Isah na tambaye shi ina kuma ya tura miki miji daga farfaɗowar shi daga jinyar damuwa,kika ce kakin soja ya fita?” Maryam ta gyaɗa kai alamun eh sannan ta karɓi kunnun wanda ake yi da fulawa da madara ta soma sha. “Je ki ɗauko min waya ta tsakar falo na kira na ji” Granny ta faɗa sai dai kuma kafin ma ta tashi jiniya ta cika gidan mai nuni da Daddy ne ya dawo “ bari ma ga shi nan ya dawo bari na sauka na ji” ta faɗa tare da tashi ta sauko ƙasa. Babu jimawa kuwa Daddyn ya shigo maƙarabansa na take masa baya,ya na ganin Granny ya sallame su duk suka fita daga falon. “Barka da shiga dare Mama” ya faɗa da murmushi kan fuskar shi. Ta ce “ yawwa! Ina ne ka tura Babana ya fita hankali tashe?” “Babu inda na aike shi Mama,wani abu aka yi?” “Maryama ta faɗa min ta ga ya fita cikin kakin soja” “Ibraheem ne bai ji ko kaɗan Mama,ko na hana shi abu sai yayi” ya faɗa tare da nufar sashensa don ya matsu yayi tozali da abincin ruhinsa.Granny ta bisa da kallo kawai kafin ta je ɗauko wayarta,lambar Heemu ta kira amma ba ta shiga haka ma ta Ammy a doli ta koma can wurin Maryam. “ Mi ya ce?” Maryam ta jefo mata tambaya, Granny ta ce “ lafiyarsa lau kin san halin Babana komai cikin sauri,abin da bai kai a ɗaga hankali ba shi wurinsa babba ne” Maryam shiru ta yi kawai,ɗan salade ɗin da ta soma ci ta ture kafin ta tashi da gudu ta koma bedroom ta haye gado ta shiga raira kuka. Hankalin Granny duk ya tashi ta rasa yadda za ta shawo kanta kawai sai ta zuba mata ido,har ƙarfe ɗaya na dare Maryam ba ta yi bacci ba ta na ta tsumayen zuwan Heemu amma shiru bai dawo ba.Zuwa wannan lokacin ƙarfin kukan ma ya ƙare sai hawaye kawai,farashin zazzaɓinta kuwa sai ƙara hauhawa yake.Bacci ne ɓarawo ya kwashe ta,yayin da Granny kuma ke kan sallaya ta na ta yin addu'o'in tsari wa jikanta don ita ma hankalin ta ba kwance ba. DADDY Yadda ya tarar da Zee cikin muguwar shigar nan,ya sallama kawai yau ba zai samu jam'in sallah ba.Abun nema ya samu sai wani shagwagwaɓe wa yake kamar wani ƙaramin yaro, Zee na basa abinci a baki bai san ta haɗa masa tarko iri-iri ba sai da suka shiga turaka Zee ta soma zayyano masa irin style ɗin da take so. A matuƙar buƙace yake amma sam ba zai iya yin abin da take so ba,a shagwaɓe ta ce “ Baby ka na fa iyawa kawai tsoro kake ji ” Ya ce “ ki duba shekaruna mana Baby,ki tausaya mini na yi aiki na gaji sosai” Ran Zee yayi matuƙar ɓacewa don ita fa ta fi son style irin na turawa,dakyar ta danne zuciyarta ta basa haɗin kai amma fa sai ta nuna ta yi fushi ta barsa nan bedroom ta shige toilet ta na ta rusa kuka da ta gaji ta shige cikin bahon wanka a nan ta yi baccinta #SOKOTO Tsawon wannan wunin bisa kulawa ta Ammy ta yi shi,har ta shiga baccin dare ban bar gadinta ba.Wuraren biyu na dare na yi alwala sannan na kwanta kan doguwar kujerar da ke nan falo,kwanyata na buƙatar hutu amma sam na kasa bata shi shuɗaɗiyar rayuwarmu nake tuna wa ni da Abakar tun daga ranar da Daddy ya zo ya ɗauke ni. Muna wasa ni da Abakar mun dawo daga makaranta,daidai ƙofar gidanmu Daddy na gani a tsaye ya na murmushi ya ce “na zo tafiya da kai IBRAHEEM zan tafi da kai babban birnin Abuja na mayar da kai SOLDIER MAN ” Abakar na kalla yayin da shi kuma yayi saurin saka hannu ya riƙe ni gam alamun kar na barsa,kai na girgiza wa Daddy na ce “ a'a ni ba zan je na bar ƙanena ba” don haka nake kiransa zan girme masa da shekara biyu haka. Daddy ya ɓata rai kafin ya je ya fizgo ni ya raba mu ni da abokina,ko Ammy ban yi wa sallama ba haka ya saka ni mota ya tafi da ni Abuja .Makarantar yara ya saka ni wacce tun nan ka zama soja sannan yayi tafiyarsa,duk wani horo da ake mini ina daurewa ne saboda yadda zuciyata ta dake su kuwa sosai suke jin daɗin haka ba su yi ƙasa da gwiwa ba suka sanar da Daddy a ranar da ya kawo min ziyara sai dai sun faɗa masa da matsala don ko bacci nake ina yawan kiran sunan Abakar. Kimanin watana biyar kenan da zamana soja na koyi abubuwa da dama daga ciki akwai rashin tsoro,ido na tsura masa babu tsoro ko shakka na ce “ ina son Abakar shi ɗin ƙanena ne amma ka raba mu,muddin ka na son na ci gaba da zama a nan to shi ma ka kawo shi ” “ Kar ka damu yarona in dai wannan ne babu matsala in dai iyayensa sun yarda” “na sani sam Umma ba za ta ƙin yarda ba Please Daddy ” sumba ya mini a goshi ya ce “ farin cikin ka shine nawa Heemu” jin haka yasa na saki raina na soma karɓar aikina yadda ya kamata ashe duk idonsu na kaina ko motsi na yi sai sun sanar wa Daddy. A ranar da na cika shekara ɗaya ,a kuma wannan ranar aka kawo Abakar .Da murna muka rungume junanmu ya ce “ aboki duk ka yi baƙi ka ƙara tsayi” Na sakar masa murmushi na ce “kai ma haka za ka koma” mun yi hira sosai kafin a ja shi izuwa sashen ƴan level ɗinsu.Duk yadda kuwa na so mu kasance tare doli aka raba mu don ba lokaci guda aka ɗauke mu ba,wuraren da muke haɗuwa su ne cin abinci,wanka da kuma training. Abokan karatu waɗanda muke level guda tuni sun fara sabawa da Abakar,ko irin in muna hira in na yi fushi in su na son na sauka daga fushin sai su yi min hirar Abakar .Cikin soja muka ida wasarmu ta yarinta,haka cikin soja muka girma duk inda za mu je a tare muke zuwa Ammy da ummar Abakar sau ɗaya kawai suka taɓa kawo mana ziyara a shekaru biyar ɗin da muka kwashe a ciki. Sai da muka mallaki hankalin kanmu ne sannan aka fara barin mu fita. “Heemu ba ka kwanta ba?” muryar Ammy ta katse mini tunanina.Na ja ajiyar zuciya na ce “ Ammy har kin tashi wai?” Hawayen fuskata ta goge kafin ta ce “ mine ne haka Heemu? Kamar wata mace shine kake hawaye?” na riƙo hannuwanta na ce “ na tuna abokina ne ” “Ka yi masa addu'a ta fi wannan hawayen ” Na ce “ Ammy Abakar ma ya na cikin waɗanda ba a samu gawarsu ba,sai nake ji a jikina tamkar zan iya ganinsa a kowanne lokaci ” “Na dai fi son ka sa a ranka ya rasu,tun da akwai waɗanda boom ta tashi da su ƙila shi ma ya na ciki” Na ja wani gwabron numfashi ina tunawa na ga agogon Abakar a ofishin Daddy. “Ka je ka kwanta don gobe za ka yi sammako” “Zuwa ina?” na yi saurin tambayarta. “Ban son muso za ka koma ” daga haka ba ta ƙara cewa komai ba ta yi gaba. Washegari kuwa tun da safe ta tirsasa mini doli na bar Sokoto zuwa Abuja,sai da na tsaya na sha mai sannan na ɗau hanya.Ko da na iso gida rana ta yi wantsar,ko da na shiga falo babu kowa direct kuma na wuce can sama.Ina tura ƙofar na soma jiyo shashekar ta,Granny ta juyo muka haɗa ido ta saki murmushi ta ce “ alhamdullah ga Babana ɗin nan ya dawo sai ki yi breakfast ɗin ai yanzu” Maryam ta dubo ƙofa da sauri kuma ta tashi ta rugo kamar za ta faɗi ta yi wani tsalle ta riƙe ni gam.Na lumshe ido ina mai sa hannuwana na tallabo ta da kyau,wani siririn kuka ne take rerawa wanda yake samun wuri a zuciyata. ” Yi shiru mana ai gani na dawo” na faɗa ina mai bubuga bayanta,Granny ta tashi ta fice ni kuwa a hankali na soma takawa da Maryam tallabe a ƙirjina har na isa bedroom.Kan gado na kwantar da mu har yanzu kuma ta ƙi sakinazafin jikinta kuma na ratsa ni.Na ja ajiyar zuciya tare da ɗan jaye ta muna kallon juna da idonta da suka yi ja tsabar kuka,“ mine ne?” “Tun jiya ka tafi ba ka dawo ba na ji tsoro sosai kar kai ma....” ban bari ta ida furicin nan ba da na san ba mai daɗi ba ne kawai na ɗora bakina kan nata.Shiru ta yi sai yanayin sheɗarta da ya sauya,sama da minti biyar ina kissing nata kafin na janye na miƙe tsaye kan ƙafafuna.Daga inda take kwance take kallona ta na murmushi,ni kuwa kayan jikina na rage na shiga toilet ina wanka ina tunanin sabon al'amarin nan da ke faruwa da ni.Tun da nake ban taɓa yin budurwa ba amma mugun son kasancewa nake yi da Maryam wacce ba soyayya muka yi ba ballantana na ce zumuɗin bege ne.Towel na jawo na ɗaura sannan na fito,inda take kwance na duba sai na ga har yanzu ta na nan a yadda na bar ta.Na taka zuwa bed ɗin,gefen wuyanta na taɓa na ji shi rau na kalle ta cikin ido da sauri ta lumshe su.Ƙwan lantarkin na kashe na haura gadon ina mai jawo ta jikina,ban wani sha wuya ba na raba ta da doguwar rigar jikinta na barta daga ita sai pant. “ Kullum doguwar riga kamar aljana” na faɗa cikin kunnenta ina mai gyara mata kwanciya kan ƙirjina tare da jawo mana blanket. “Na fi sonta ” ta faɗa a shagwaɓe,“ tun yaushe kike jin zazzaɓin nan?” “Yau ne kawai” ta bani amsa ta na mai ɗan ja da baya ni kuma sam hakan bai yi mini ba sosai na ji daɗin yadda ƙirjinmu ya samu contact. Ban ce komai ba sai rumfa da na yi mata da ƙirjina,na kai hannuna can ƙasan bayanta na tallabo.“ Ban so kar ka yi min” ta faɗa da sauri ta na mai kai hannunta kan haɓata,ta ɗan hasken da ya rage nake kallon fuskarta na ce “ mi a ba ki so?” shiru ta yi ba ta bani amsa ba ni kuma na janye hannun nata na cusa kaina gefen wuyanta,cikin muryar raɗa na ce mata “ wannan zafin da jikinki yayi nake son na rage miki babu abin da zan yi miki ki saki jikin ki” wata irin wawiyar runguma ta yi mini wacce ta kusa sa ƙusoshin kaina kwance har sai da na fitar da wani numfashi ban shirya ba.Sannu a hankali zafin jikin nata ke ratsa ni ya na saukar min da wata kasala,don jan magana Maryam bayana take shafawa kuma ta ce ba ta son na yi mata komai sam na kasa juriya na lalubo bakinta duk da kuwa ƙoƙarin hana wa da take sai da na ci gabala kanta ban barta ba sai da na samu ƴar nutsuwa, toilet na koma na tsabtace jikina sannan na fito. Ina kunna lantarki na hange ta zaune daram ko kayan ba ta mayar ba,na kawar da kai gefe ina mai cewa “in kin jin ƙwarin jikin ki za mu je shopping ” “Na fa warke,garas nake jin kaina dama rashin ka ne” da sauri na juya jin furucinta ta wani sa hannu ta na rufe ƙirji.Na taɓe baki ina zancen zuci ‘ Allah na tuba in ba dai don shi namiji da jaraba ba mi wancan abubuwan za su mini’ ina ganinta ta wutsiyar ido ta ruga ta shiga toilet ko kafin ta fito na shirya na wuce falonmu. Abinci na gani kan table na haɗawa kaina tea na soma sha,zuwa can ta fito cikin wata pink ɗin doguwar riga. “Zo ki zuba mana abinci” na faɗa ina danna wayata ina karanta saƙonni da suka shigo min,plate ta ɗauka ta zuba har za ta zauna na yi saurin jawo ta na ɗora kan cinya sai kuma na tuna na taɓa ganin Daddy ya yi wa amaryasa.Maryam ta faɗo jikina ta na jan gemuna da yake da yawa sosai,“ ina son wanga abun” ta faɗa kamar wata ƴar yarinya. Na ce “ bai da suna ne?” “ Ya nada” ta bani amsa ta na mai ci gaba da wasa da shi ni kuma hakan ba ƙaramin daɗi yake mini ba,kawai sai na zuba mata ido.Ta saka dukkan tafukanta ta na shafar sajena ta ce “ amma wannan ya fi kyau” Na ja hancinta ina mai ci gaba da kallonta kafin na ce “ a bani abinci yunwa nake ji” Ta yi dariya kafin mu soma ci a tare. Littafin kuɗi ne 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 11-12 Assalamu alaikum,ina ma'abotan karatun litattafan Hausa? To kakarku ta yanke saƙa.Mrs Sadauki ta yi muku bajin kolin littatanta duka tun daga na tsafi,soyayya za ta yi muku ragi mai rahusa,kai hatta ma waɗannan da take yi MAITAR IDO da shi kansa SOLDIER MAN za ta yi discount. Ga duk wanda yake ra'ayi ƙofa a buɗe take za ku iya tuntuɓarta kai tsaye ta WhatsApp+22795045822 Allah ya bada ikon biya Ameennnn!!!!! Bayan mun gama cin abinci na ɗauki ATM ɗina,Maryam ta saka hijabi sannan muka sauko ƙasa ina mai rungume da ita. Daddy na gani zaune shi ɗaya yayi uban tagumi kamar ba shi ne mai matsayi da ɗagawar nan ba.Cikin kunne na yi mata raɗa “ za mu je ki gaida mahaifina” sai ta jinjina min kai . Tun kafin mu ida isa na yi gyaran murya,ya kuwa dube mu ni na fara gaishe shi kafin Maryam ta duƙa har ƙasa ta ce “ ina kwana Daddy ” Sai da ya sake haɗe rai kafin ya amsa mata da “ lafiya lau” sai kuma ya kawar da kai gefe.Na sa hannu na ɗago ta ina mai janta jikina na riƙe ta gam,cikin Yaren mu na soja na ce “ ita ɗin ƙanwata ce kamar wancan ɗin dai ina sonta fiye da kalmar so saboda wancan ɗin dai sannan in sha Allah da sannu zan samo shi” Wani irin firgici na gani a fuskar Daddy a lokacin da na kai ƙarshen maganata,na sakar masa murmushi kafin na ja Maryam mu fice ko Granny ba mu je mun gani ba. Da kaina na buɗe mata mota ta shiga sannan na zagaya na hau mazaunin direba,tun kafin na fara tuƙi na kira Ammy na saka wayar a hand free na ce “ Ammy ce in ta ɗauka ki gaishe ta kuma ki yi mata ya jiki” ko bakina ban ida rufe wa ba Ammyn ta ɗauka. Ina kallonta ta turo baki maimakon ta yi abin da na faɗa mata sai ta yi wanda take so,“ shine kika tafi kika bar ni,kuma...kuma ko sallama ba mu yi ba ” Driving na fara aka buɗe min get, Ammy ta yi murmushi mai sauti ta ce “ Maryam Sarkin rigima, lokacin na bar gidan ai na san kin koma bacci.Faɗa mini ai dai bai matsa miki ko?” Sai da ta dube ni kafin ta ce “ da dai sauƙi Ammy amma ...to shi kenan dai..” sai ta yi shiru.Da sauri na ɗauki wayar na kara a kunne ina cewa “ ina kwana Ammy ya ƙarfin jikin?” “Alhamdullah Heemu ! Mi kake yi wa ƴar amanata?” “Kin yarda zan iya yin wani abu da zai cutar da ƙanwarmu?” “Na sani Heemu amma ita gani take kamar takura ce duk da na san ba zai wuce akan tashi sallar asubah ba don Maryama akwai nauyin bacci sai ka yi da gaske” “Ammy ina driving in na sauka zan sake kiran ki” “To yarona Allah ya tsare ku ya kai ku lafiya ya kuma maida ku gida lafiya” “Amen Ammy ki kula da kan ki kuma ki sha maganin ki” na faɗa tare da kashe kiran. Na ɗan haɗe rai na ce “ wato da na ce ki gaishe ta shine kika ƙi? Sannan kuma mine ne kike shirin faɗa mata?” Ta ɓoye fuskarta tsakanin cinyoyinta ta na dariya ta ce “ laaa babu komai fa ya za a yi na sanar da ita abin da muke yi” Wani haushi na ji ya kama ni,wato ɗan kiss ɗin da nake yi mata ya zama abin faɗa da alamu ma kamar zai kankaro mini raini tsakanina da ita.Wani haushin kaina na soma ji har muka isa ban ƙara ce mata komai ba,ina gama parking na fita ina jiran ta fito amma ta ƙi.Na zagaya na buɗe na ce “ a nan za ki zauna?” Ta turo baki ta na mai cewa “ to ai kai ne ba ka yi saurin buɗe wa ba” “Fito ni na rufe motata” kamar za ta yi kuka ta fito,na rufe sannan na kama hannunta.Muna shiga ciki ta soma zillewa wai na sake ta mutane na kallonmu,wani takaicin ya ƙara rufe ni na ce “ ke nan ba ƙauyen ku ba ne na Sokoto kowa harakar gabansa yake,ki nutsu ki zaɓi abin da kike so in kuma kika cika ni zan mayar da ke gida” sai a yanzu ta nutsu jin zan fasa yi mata sayayyar. Muna shiga ɓangaren kayan mata ta tuntsire da dariya irin sosai ɗin nan har sai da ta jawo hankalin mutane gare mu,kunya da takaici suka luluɓe ni .Da hannu ta yi mini nuni da wani sket irin na ƴan gayu ta ce “ wa kuma ya kawo sket ɗin uwarsa nan terere” hannunta da ke cikin nawa na yi wa wata muguwar matsa a doli ta nutsu. Ta na kumbure-kumbure na soma zaɓar mata kayan muna jefawa cikin kwando,dogayen ruguna kawai ta zaɓarwa kanta kayan bacci da ta ga ina ɗaukar mata ta kira sunana kamar abun ƙwarai “ Ya Heemu ?” na ce “ uhum ” “Su kuma kayan ƴan iskan nan waye zai sa su?” “Wane ƴan iska kuma?” “ To irin na turawa ne fa,ni dai gaskiya ban so” ban kula ta ba har na ɗauki waɗanda na ga sun yi min muka wuce wani ɓangare kuma.Da sauri ta yi gaba ta soma jidar pant da bra,kallonta kawai nake yi kafin na tambayi kaina ‘ ko mi za ta yi da bra ’ kamar kuwa ta shiga tunanin nawa sai cewa ta yi “ to ai za su ƙara girma ba haka za su zauna ba ka ga kuwa ina da buƙatar abun tallabe su” wacce ke riƙe mana kwandon ta ce “ ki na da gaskiya Madam ko ma a haka za ki iya sa abarki ki yi kwalliya” Mugun kallo na watsa mata ina cewa “ mine ne to na kallon ƙirjinta?” Ta yi ƴar dariya ta ce “ haba kai kuwa mi zan kalla a nan Les nake ai wannan ta min ƙanƙa...” ba ta kai ga rufe bakinta ba na wanka mata mari da mugun sauri ta bar wurin dafe da kumci. Na karɓe bra ɗin hannun Maryam na mayar ta sake ɗauko su ta rungume ta na cewa “ Allah ina so” ban ƙara cewa komai ba na yi gaba,ta ce “ kwandon kayan fa?” “Sai ki ɗauki abin ki” na bata amsa,ta biyo bayana ɗauke da ƙaton kwandon yadda take nishi yasa na karɓa. Sai da na saya mata takalmi da jaka sannan muka zo wurin biya,ana ta lissafin kaya bayan ya gama ya ce “ banda kayan kwalliya?” “ Ba ta iya ba”na basa amsa ina miƙa masa ATM ,mai Mall ɗin na tsaye Dattijo ne sosai ya ce “ a'a yarona a saya mata sai ta koya ko ƴata?” Maryam ta ce “ eh Daddy ina so” ta wutsiyar ido na dube ta kafin na ce “in akwai wacce za ku wakilta ta zaɓar mata a kira ta sai su tafi tare” Ya ce “ mace ce mai kula da ɓangaren ku zo na kai ku” a tare muka je,da kanta ta zaɓarwa Maryam kalolin hodar da za su hau da fuskarta sannan sauran abubuwan shafe-shafe. Da muka biya aka kawo mana har mota ,ina tsaka da tuƙi ta ce “ Allah kifi nake so” “Sai ki bari har mu je gida” na bata amsa. “ Babu inda ake kamo shi?” ban bata amsa ba har muka isa gida. Ɗakin Granny muka yi tsinke ta soma baza surutu ni har mamakinta nake,wayata ce ta yi girrr alamun shigowar saƙo na ciro ta daga aljihu na duba ina gani da sauri na miƙe na fito. Can sama na haura ina mai kiran Shamssudeen,ko damar magana ban basa ba na ce “ ka ce mi? Ya tsere? Ta yaya kenan?” “Wallahi kowa mamaki yake yadda ya tsere don wuri mai tsaro muka ajiye shi amma muna tashi yau babu shi” Na dafe kai na ce “ ku duk ku na aikin mi har ya tsere? Dagaci ɗan ta'adda ne mai laifi ban ma san dalilin da yasa ba ku harbe shi ba tun ranar da kuka kama shi ba” na faɗa ina jin allurar sojana na motsawa. Daga can Shamssudeen ya ce “ Ibraheemu kamar dai ba ka san yadda mulkin ƙasar nan yake tafiya ba? Kawai ni na fi tunanin daga cikinmu ne wani ya fitar da shi amma babu wai zancen ya gudu” Cike da masifa na ce “ ai ga irin ta nan shi yasa kullum ƙasarmu ke dawowa baya inda ya kamata a ɗauki mataki kai tsaye wai sai a tsaya sai an bayar da izini” “Ni fa yanzu tsorona guda,kar a jingina laifin a kanmu ” Na furzar da huci na ce “ yanzu ku na ina?” “Muna hanyar Abuja cikin dare muna kawowa in sha Allah ” “ Ya kamata mu yi wani abu ,doli mu yi fito na fito da jadawalin dokar ƙasar ya zama doli a canza su sam ba su yi ba” “Allah dai ya kama mana,duk rashin tsaron da ake cewa babu laifin ya na wurin manya amma sai a dinga ganin laifinmu.Da zarar an kama ɗan ta'adda maimakon ayi yadda kace ɗin a kashe shi sai a tsaya ajiyar shi,ƙarshe sai ka ji an ce ya gudu” “Shamssudeen Allah kawo ku lafiya sai dai kun zo,bari na je can compagnie na ji ya ake ciki” nan muka yi sallama sai da na sake yin wanka sannan na shirya cikin kakin soja ko hulla ban ɗora ba na sauko ƙasa. Da sallama na shiga ɗakin Granny,ita kaɗai ce falon ta na ganina ta kafe ni da ido ko ƙyaftawa ba ta yi kafin ta tashi tsaye ta ce “ Ya Heemu ...” sai kuma ta zo ta rungume ni. Kanta na dafa na ce “ zan je na dawo ne,ba zan jima ba” ta ɗago muna kallon juna ta ce “ ko mu tafi tare ” Na girgiza kai “ a'a wurin aiki zan je,ina Granny?” “ Ta shiga toilet ” ta bani amsa,na ɗan rage tsayi har zan sumbace ta kuma sai na tuna na yi alƙawarin ban sake yi kar ta raina ni. “ Sai na dawo” na faɗa tare da janye ta daga jikina,ba tace komai ba sai ido da ta bi ni da su. Motata na shiga na yi mata key na isa compagnie,ina gama parking na nufi ofishin Daddy yau ma sun so su hana ni amma yadda raina ke a ɓacen nan yasa ba su yi doguwar jayayya ba suka bar ni. Ina shiga duk suka juyo su na kallona,DADDY ne da Joy da alamu wani abu mai muhimmanci suke tattaunawa. “ Wa ya baka izinin shigowa?” Daddy ya tambaye ni,idona ya sauka kan screen ɗin system ɗin gabansa da sauri ya rufe ta na ƙara haɗe rai. Joy na kalla na ce “ ina trollyna da ka shiga ɗakina ka ɗauko?” bai bani amsa ba sai cewa Daddy ma da yayi “ zuwa an jima zan sake dawowa na yi ma bayani” ya na shirin tafiya na damƙo rigarsa,a zafafe ya ture ni ya na cewa “ kar ka sake gigin kai hannu jikina ” na kuwa shaƙe shi ina cewa “ kai ɗin uban wane ne? Ka shiga ɗakina ka ɗauko kayana kuma na kasa magana?” shi ma tawa kwalar ya ci , Daddy sai faman cewa yake “ Heemu ka sake shi!” ni kuma na ƙi na buga wa Joy kai a fuska a nan take jini ya soma yi masa zuba ,ban damu ba na ci gaba da dukansa shi ma ya na ramawa. Daddy ya shiga tsakaninmu ya na mai ɗauke ni da wani gigitacen mari,har sai da na ji kunnena yayi wani dummm.Ya danna wani abu sai ga jami'an da ke basa tsaro sun shigo,da hannu ya masu nuni da ni ya ce “ ku kai mini shi celle ” da mamaki nake kallon Daddy sai na ga ya na bai wa Joy haƙuri da rarrashinsa sai kace shi ne babba gare shi. Muna fitowa waje na ƙwace daga riƙon da suka yi min na ce “ tun da hauka kuke sai ku kai ni can maƙargama” duk su na ƙasa gare ni doli suka bar ni. Wani sashe na nufa inda muke bincike da kuma samun labaran da ƙasa ke ciki dama waɗanda aka gabata.Hotunan waɗan suka ƙone wurin yaƙi na nemo da duk waɗanda ba a ma san inda suke ba,sosai na yi mamaki ganin an canza sunan Abakar daga liste ɗin waɗanda ba a gani ba zuwa na wanda suka ƙone.Sam zuciyata ta ƙi yarda da hakan,don kuwa liste ɗin ta ƙwarai ta na ofishin Daddy kuma ita na soma ganin kafin wannan. “ Tabbas a yau zan soma bincike ” na faɗa ina mai miƙewa na nufi ɓangaren asibitinmu, waɗanda suka ji ciwo a yayin fafatawar na kai wa ziyara.Sosai suka ji daɗin haka kuwa,su na samun kulawa mai kyau dakyar na samu wanda suka yi group guda da Abakar tun da in za a yi yaƙi group-group ake yi duk sai a rarabu to a cikin group ɗin su Abakar tun kafin a tafi na kalle su tsab kuma duk cikinsu wannan ɗin kawai yayi rai. Kusa da kansa na zauna na ce “Ya jikin naka?” “Da sauƙi alhamdullah!” ya bani amsa,cike da jimami na ce “ haka Allah ya rubuta ,ka ƙara haƙuri in sha Allah mune da nasara” Ya ce “ Allah nuna mana ranar da ƙasarmu za ta fita daga cin hanci da rashawa duk da kuwa abu ne mai wahala” A cikin idonsa ina hango wasu abubuwa,ƙunci,tauye haƙi akan gaskiya da kuma fargaba.“Haka ne ai ga shi na rasa abokin...” ban rufe baki ba na ga Joy shi da wasu sojojin a tsaye fuska a murtuƙe. Ankwa suka sa mini kamar wani mai laifi,furgincin idon wanda nake hirar da shi ne na ga ya ƙaru suka tisa ƙeya ta zuwa gaba.Direct ofishin Daddy suka kai ni,sai a lokacin suka cire min ankwa ɗin suka fita suka bar ni da mahaifina. Ya ja ajiyar zuciya ya ce “ Heemu ban san mi kake so da ni ba? Mi ya kai ka ɗakin bincike?” Da mamaki na dube shi na ce “ haramun ne soja ya shiga ya bincika ya ga halin da ƙasarsa ke ciki?” “ A'a ba haramun ba ne abu ne ma mai kyau amma ai ya kamata ka sanar da ni kafin ka tafi” “Yi haƙuri shugaba ban san an canza dokar cewa in soja zai shiga ɗakin bincike sai ya nemi izinin ka ba amma zan kiyaye gaba yalaɓai” na faɗi haka ne don nuna wa Daddy nan kan aiki muke ba wai a gida ba. Ya ja ajiyar zuciya kafin ya jefo min wata tambayar kuma “ to mi ya kai ka ɗakin maras lafiya?” Na yi wani murmushi na ce “ shi ma an saka dokar shiga ne?” bai ce komai ba,sai aljihun table ɗinsa da ya buɗe ya miƙo min wata takarda ya ce “ Abakar na cikin waɗanda suka ƙone ko gawarsu ma ba a iya shaida wa ba,sai dai mun tsinci wannan agogon mai ɗauke da sunansa” Takardar na karɓa,wacce tabbas ba ita ba ce na fara gani ba an canza ta yanzu kuma ya kawo min wata sabuwa tare da miƙo min agogon Abakar.Yi na yi kamar yanzu ne na gansu,na karɓa hannuna na rawa na kai ƙarfen agogon na ɗora daidai saitin zuciya na lumshe ido ina cewa “ Allah karɓi shahadarka abokina haƙiƙa na yi babban rashi” ta wutsiyar ido nake kallon Daddy fuskarsa sharrr babu fargabar nan da na tarar da shi da ita,har da sauke wani numfashi yayi kafin ya ce “ Amen! Allah nuna mini ka aje bindiga lafiya” ban ce komai ba na ajiye takardar kafin kuma na saka ƙarfen agogon cikin aljihu kuma sam Daddy bai yi ƙoƙarin hana ni ba har na yi masa sallama na fito. Da na shiga motata kasa tuƙa wa na yi,tunani birjit ne ya soma ziyartar ƙwalwata,‘ mine ne dalilin Daddy na son mayar da Abakar cikin waɗanda suka mutu? Don na fitar da shi a rai ko me? ’ rasa amsa na yi kawai na daure na soma driving...... Book ɗin kuɗi ne 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 [01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM* ```soldier man``` © Chamsiya Laouali Rabo #MRS SADAUKI💫✍️ *FCWA ☀️* #Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓 Last free page 13-14 Raina duk a jagule na isa gida,benen na soma hawa ina haɗe bibbiyu har na kai sashena.Ina buɗe falon wani sihirtacen ƙamshi ya bugi hancina,ban gama shanye romonsa ba idona yayi tozali da Maryam cikin wasu arnan kaya riga da wando su yin bala'in yi mata kyau. Duk sun matse ta tam ga su sharashara,ta rugo da guɗi ta yi tsalle ta kamo wuyana ta na yin wani murmushi mai tabbatar da tsantsar farin cikinta .Neman ƙuncina na yi na rasa kawai na rungume ta,cikin surutun nan nata ta ce “ albishirin ka na iya hawan bene ni ɗaya,yau Granny ta ce ba za ta mini rakiya ba ni kuma na ji haushi na hau da kaina.Ka ga kuma kayan da ka saya min irin na nasaru sun yi kyau? Na zama kamar ƴar tsanar roba” Murmushi kawai nake ina kallonta,ta turo baki ta ce “ shine ka yi shiru? Ko ba su yi min kyau ba na cire dama ni sun dame ni ” “Kin yi matuƙar kyau preety” na faɗa ina mai takawa da ita maƙale a ƙorjina har na isa ga kunera na zauna.Ta tuntsire da dariya ta ce “ ka ga ƙatuwa da ni amma na yi ɗare-ɗare kan cinyarka,ina da nauyi?” ta tambaye ni tare da ɗora dukkan tafukan hannuwanta kan fuskata ta na shafar sajena yayin da kuma ta tsurawa gemuna ido. “Mary?” ta ɗago muka haɗa ido,a hankali na matsa fuskata na ɗora bakina kan lips ɗinta na mata kiss kafin na janye. Murmushi na ga ta yi kafin ta ce “ bari na haɗa ma ruwan wanka” sai ta sauka daga cinyata,na bi bayanta da kallo har ta shige bedroom.Na dogon numfashi ina jin wani iri,ganin ta jima ba ta fito ba yasa na bi bayanta,sai da na rage kayan jikina kafin na shiga toilet ɗin a tsaye na tarar da ita ta na karanta dettol da duk abin da ke ciki na dangin wanka da kuma gyaran jiki. “ Yaya mine ne wannan?” ta tambaye ni,na ce “ ki karanta mana ai kin yi makaranta” “Ban gane ba ne,rubutun da French ne sai hoton gashi da aka yi,ko mai sa sulɓin gashi ne?” na karɓe na ce “ a'a ki barsa nan tun da ba ki san na mine ne ba” ta turo baki kafin kuma ta ce “ na yi ma wankan?” na girgiza mata,“ don mi? Ni fa matarka ce ” “Ba ki jin tsorona?” “Ina ji mana amma sai in ka murtuƙe fuska” “Fita!” na faɗa cikin bayar da umarni kuma babu alamun wasa a fuskata, sumi-sumi ta wuce ta bar toilet ɗin. Bahon wankan na shiga bayan na cire komai na jikina,na lumshe ido ina zancen zuci ‘ wannan ɗin ce zan nunawa sirrina ƙwaila da ita,sai ilimin faɗar kalmar mijin amma ba ta san mi take nufi ba.Wannan da ace ta san ana wata mu'amala ta aure da tuni ta min ƙorafi ban yi mata ba’ wani haushi ne ma ya rufe ni kawai na soma wankan da sauri-sauri . Ina fitowa na shirya cikin jallabiya fara na fesa turare sannan na fita falo,a zaune na tarar da ita ta saka kwanonin abinci a gaba. “Tun ɗazu nake jiran ka,yunwa nake ji kuma Granny tace kar na sake cin abinci ni ɗaya ba tare da kai ba muddin dai ka na gida” ta faɗa tare da soma buɗe kwanonin,na zauna tare da jawo ta jikina na ce “ki bar abincin nan zo ki ji tukuna” “Ni ban so ka na ɗora ni kan cinya duk sai na takura na ga na sakar ma nauyi” “Kin manta soja ne ni ?” “Haka ne fa an ce wai har mota ku na iya cirawa da hannu shi yasa kuke da ƙaton ƙorji da kuma damatsa” ta yi furicin ta na mai dukan ƙirjina.Na riƙe hannun nata tare da kai yatsanta manuniya bakina na soma sha,ta ƙyalƙyace da dariya ta ce “kar dai ka cije ni don alƙur'an sai na rama” A zuci na ce ‘ai matsalar auren ƙwaila kenan kuma baƙauya sam ba ta san rayuwar romantic ba’ Sai kuma a hankali na fara ƙarewa surar jikinta kallo,na saki wani murmushi da na kalli ƙirjinta yadda ta saka uwar acuci maza. “A bar kalle min abu,can da na ce ma ina son bra ɗin har cewa ka yi a'a ” ta faɗa a shagwaɓe ta na faɗo wa kan ƙirjina,na shafi gadon bayanta na ce “ in dai za ki fita ban yarda ki saka ta ba” “ In fita in je ina ni da ban san kowa a nan ba” “Da zarar hutu ya ida ai za ki koma makaranta ko kin haƙura ne?” “A'a zan je mana ni da nake son zama nurse” “Da wannan tsoron naki?” ta yi dariya kafin ta ce “ yunwa nake ji” Na ce “ faɗa mini ba ki jin daɗin irin wannan yanayin da muke ciki?” “ Ina ji amma in an ƙoshi ai ya fi” ta bani amsa. Na ɗan janye ta daga ƙirjina kafin na ce “ to je ki ci” “Kai ba ka ci” “Eh ” na bata amsa tare da komawa bedroom, system na ɗauko na haye bed na ci gaba da yin bincikena ban fito ba sai kusan sallar magrib.Ban ganta ba falo,na sauka ƙasa su na zaune a babban falo ita da Granny ta na yi mata tausa. Na je na gaishe da Granny kafin na wuce masjid ko da muka gama sallah ban fito ba sai da muka yi isha'i,sosai na yi ta mamakin mi ya tsayar da Daddy da har yanzu bai shigo ba.Da wannan tunani na koma gida,kafin na wuce part ɗina na ce “ Granny ina son Lipton a saka citta da lemun tsami dayawa” ina jin idonta a kaina har na haye step . Granny ta dubi Maryam ta ce “ mi ya haɗa ku ke kuma?” Maryam ta turo baki cike da ƙurciya ta ce “ to Granny kullum kowanne lokaci sai dai a yi ta yin abu guda kamar wasu tantabaru,kawai don na ce masa yunwa nake ji sai yayi fushi?” Granny ta ɗan murmusa kafin ta ce “ Maryama ki yi wa mijin ki biyayya in ba haka ba wuta Allah zai saka ki ,ɗazu duk ba na faɗa miki ki cire kunyarsa ba?” “Granny har fa kayan da kika ce na saka su ne a jikina yanzu haka,hijabi ne kawai na ɗora ko na nuna miki?” “A'a ba sai kin nuna min ba shi mijin naki dai za ki nuna wa in kuma kika tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi miki ƙafa.Wallahi ya auro wata ya bar ki nan sake da baki” Maryam jin zance kishiya ta ce “ a'a wallahi ban so yanzu faɗa mini mi zan yi?” “ Zan baki littatafan Hausa ki karanta don ni ma su suke ɗebe min kaɗaici” Maryam ta yi dariya ta ce “ wai Granny dama tsofi na karatun litattafan dandalin soyayya?” ba ta bata amsa ba sai mai aiki da ta kira ta sanar da ita ta haɗa Lipton dayawa da kuma abubuwan da za a saka. Granny ta je ta ɗauko wa Maryam littafai dayawa ta miƙo mata,ta karɓa ta na duba wa.Ana kawo Lipton ɗin Granny ta ce “tashi ki kai masa,da zarar kin shiga ɗaki ki cire wannan ƙaton hijabin” Da “ to ” ta amsa kafin ta nufi sama,kamar yaro mai koyon tafiya haka take taka step ɗin har ta isa. Ina kwance kan kujera abun duniya ya sha min kai ta shigo da sallama,ban amsa ba kawai na zuba mata ido duk da ta saka hijabi amma bai ɓiye tudun ƙatuwar bra ɗin da ta saka ba. Kan table ta aje tray ɗin kafin ta cire hijabinta wanda ban san dalilinta na yin haka ba,ƙila don ta ƙara cutar da ni wani sashen zuciyata ya faɗa ban ida yarda da haka ba ma sai da ta duƙa don zuba mini Lipton ɗin a kofi .Na maida kaina gefe zuciyata na matsanancin bugawa na ce “ ki saka hijabin ki, sannan ki je ki yi sallolin ki” “ Toh” ta faɗa ba tare da ta bani kofin Lipton ɗin ba ta yi gaba ,wani haushi ya rufe ni na tashi na ɗauka na soma sha sosai na ji daɗinsa lemun tsami ya kama da kyau cittar kuwa sai ƙamshi take.Da na sha Lipton ɗin na soma jin dama kafin kuma madubin idona yayi ta hasko min surar Maryam yayin da zuciyata ke tirza ni akan na je na kawar da damuwata ai da igiyoyin aure na kanta.Na cije leɓena na ƙasa,kafin dakyar na miƙe na shiga bedroom a tsaye na ganta ta cire rigar kayan ta tsaya daga ita sai bra rabin ƙirjinta duk a waje.A yanayin da nake kawai da ace ta na da hankali ta san abin da na fi buƙata,amma ta yi saurin juyawa ta na ɓoye ƙirjinta tare da saka doguwar riga ta sallah ta zumbula uban hijabi kamar matar liman ta ƙabarta sallah. Dakyar na iya saita kaina ta hanyar yin wani wanka,sannan na ɗauki key na fice na bar gidan.Compagnie na nufa inda sojawa ke kwana,ɗakinmu na wuce wanda a yanzu ya zama ni kaɗai ke da shi.Na yi kwance kan ɗan gadona na ƙarfe,a hankali na soma ware idona kan ƙananun rubutun da aka yi a jikin gadon da ke can saman nawa wanda dama can Abakar ke da na sama ni na ƙasa ban ganinsa da kyau wannan ya saka na kunna fitilar wayata na soma karantawa. ```Na san za ka karanta wannan rubutun abokina a lokacin da na yi ma nisa,kake cikin kewata.Ana bibiyar rayuwata ,ina takaicin sanar da kai cewa Daddy na cikin wata ƙungiya ta maras gaskiyan ƙasarmu ,ban san komai akai ba amma don Allah ko bayan raina ka lalubo gaskiyar nan domin ƙasarmu ta zauna lafiya ka ji IB``` Na karanta rubutun nan ya fi cikon casbi,sam hankalina ya kasa ɗaukar wannan lamari wanda na tabbatar Abakar ne ya rubuta shi,domin rubutunsa ne.Sannan shi kaɗai ne ya san in ina cikin damuwa kawai nake hawa gadon nan na yi kwance,hasalima ko a nan zan kwana na fi son na yi shimfiɗa ƙasa saboda in ina bacci ina yawan juyi.Ƙarshen zance kuma shi ne kawai yake kirana da sunan IB. Wani abu ne ya tsargar min na zargi ‘tabbas mutuwar Abakar an shirya ta ne saboda sun gano ya san sirrinsu ’ na miƙe tsaye ina jin a yau ba sai gobe ba sai na yi fito na fito da Daddy ko da zai kashe ni ne.Ina tuƙi ina tunanin yadda Daddy ke ta fafutukar ganin ya kawo zaman lafiya da tsaro a Nijeriya,ni shaida ne akan hakan amma ta ya kuma za a same shi da hannu a cikin ƴan tafa zaune tsaye? Ina cikin gudu ne motata ta samu matsala,an yi sa'a banda nisa da masu gyara.Na fito na yi musu magana aka zo aka fara duba mini,kafin nan sai na yi zaune kan banci ina sauraren hirar abokin ɗan garejin. “Kai amma Komanda Isah ba ƙaramin ƙwaro ba ne,in ba shi ba ina aka taɓa ganin shugaba ya tafi yaƙi shi da ya yaransa ” “Ai in faɗa ma yau an yi ɓarin wuta,yadda ma na ji an ce wai ya samu harbin bindiga a ƙirji amma sun ɓoye abun kawai suka ce ya ɗan ji rauni ne” Ban san lokacin da na ce “Shi Komandan sojojin?” “Eh wallahi! Halan ba ka kallon tv? Yanzu nan aka gama nunawa a labarai” Ban sake cewa komai ba har aka ida min gyaran na biya shi sannan na shiga motata,a tsiyace nake gudu har na isa gida tun yanayin da na tarar da Granny na fahimci abin da na ji ɗin dai gaskiya ne to amma na rasa ta yaya hakan ta faru sunan ina soja kuma ɗansa amma ban san da zancen tafiyar ba. “Zo ka kai ni an ce ya na babbar asibitin nan” Granny ta faɗa ta na hawaye ,ban musa ba na ja hannunta muka shiga mota.Tun da na karyo kwanar asibitin na ga ko ta ina sojawa ne sannan ga ƴan jaridu nan birjit,motata ma dakyar aka bari ta wuce shi ma saboda Granny ne. Sojawa biyu suka yi mana rakiya har ɗakin da Daddy ke kwance an saka masa oxygene yayin da na'urori ke jone a jikinsa.Yanayin sheɗar tasa kawai in mutum ya kalla doli ya firgita don sai tiii!tiii! Ƴar ƙaramar system ɗin ke yi.Daga inda yake kwance yake kallonmu,ko magana bai iya yi ga wurin da aka fasa aka cire alburushin nan an naɗe da bandeji. Granny ta je kusan kansa ta yi zaune ta na shafar sumar kansa tare da soma yi masa addu'a idonta na ɗigar da hawaye,shiru kawai na yi na ƙurawa system ɗin ido yadda ka san addu'ar Granny ita ce magani haka numfashin Daddy ya soma komowa daidai har ya dawo normal.Na lumshe ido ina jinjina girman addu'ar uwa ga ƴaƴanta,wacce Allah da kansa ya ce babu hijabi a tsakaninsa da ita bakin uwa mahaifiya na da matuƙar ƙarfi. “Ibraheemu?” na ji muryar Daddy cikin wani sauti,na matsar da kai ina cewa “na'am Daddy ya jikin naka?” “Da sauƙi alhamdullah! Gobe in Allah ya kai mu ka je ofis ɗina duk wani jadawalin aikin da za a yi ka gabatar da shi a matsayina zan yi wa Sergent Yakubu magana,PIN ɗin system ɗin sunanka za ka saka,don Allah kar ka yi wasa ya kamata a yi komai kan tsari” Na kamo hannunsa ina cewa “in sha Allah Daddy” mun ɗan jima nan kafin mu dawo gida cike da ƙwarin gwiwa akan hanya ina tuƙi ina tunani ‘mutumen da ke da hannu da ta'addanci ta ya zai iya bari a duba system ɗinsa? Ina ganin dai Abakar bai fahimci Daddy ba’ da wannan tunanin na tunkuɗe zargina akan Daddy muka isa gida. Na yi wa Granny rakiya ɗakinta har zan wuce sama ta ce “ka je ka sanar da matar Mahaifin ka halin da ake ciki ita ma ta na da haƙin sanin halin da mijinta yake ciki,kar ka yi min muso in dai na isa da kai” Cike da jin haushi na fita daga nan na wuce sashen Daddy,ko sallama ban yi ba na tura ƙofar kunnuwa ne da idona suka yi min mugun ji da mugun gani.Ƙatuwar tv ɗin da ke manne ga bango ce ke ta wano BF ga sautin duk ya cika ɗakin ,duk tsiyar ka in dai kai lafiyayye ne doli ka ji wani abu.Da sauri na baro ɗakin ina da na sanin shiga,ina haurawa can sama na tarar da Maryam a zaune an ci wani sabon adon na kayan bacci .Lipstick ɗin da ta saka yasa laɓanta suke sheƙi,idona har wani dishi-dishi suke yi na isa gare ta dama na ɗau caji,“kin yi kyau ina son wannan ”na faɗa ina nuna laɓanta da suka sha man leɓe,da na soma sumbatarsu kuwa har wani gajimare nake gani. Ta ƙwace bakinta dakyar ta na numfashi da sauri da sauri ,ta na mai ƙure ni da ido murya na ɗan rawa ta ce “kakkaaa” “Shuuut!” na katse ta tare jawo jikina na yi mata raɗa a kunne ,na ce “duk bayanan da Ammy ta yi miki ba ta sanar da ke haƙin miji ba?” “Ta faɗa mini” ta faɗa cikin rawa murya. Na ce “to yau zan fanshe sadakina wallahi ki nutsu ban son shirmen nan” damatsana ta riƙe ƙwairai tare da fashewa da kuka,wanda sosai yau ya yi min daɗi sai na ji shi cakwai kamar zuma wannan yasa ban kula ta ba na kai ta kan bed. Nan na kawo ƙarshen free page,na kyauta ya ida mai son ci gaba sai ya biya My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank sai ki turo shaidar biya ta WhatsApp +22795045822