Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 1 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Cikin nutsuwa nake kara sa wanke plates din da aka gama cin abincin, aiki nake yi amma fuskata ba alamar fara’a a daure take kamar ko yaushe. Sai da na gama gyara kitchen din tsaf na bar wankin tukwanen sauran ma’aikatan dake kasa dani su wanke, hannuna na goge da towel din da nake zuwa da shi sbd goge hannu in na gama taba ruwa, a nutse na mayar da towel din cikin jakata na rataya jakar a kafada ta. Cikin nutsuwa nabi ta kofar kitchen din na fito harabar restaurant din don bana son na bi ta ciki ko dan yadda Ogana ya takura min. Har na fita daga restaurant din kai na yana kasa Ina tafiya Ina dan yamutsa fuska sbd yadda garin yake yau ana rana sosai. Adaidaita na tsayar na shiga bayan na fada masa Inda zai kai ni, waya ta dake ringing na dauko a cikin jakata, ganin sunan wanda yake Kira yasa ni tsaki Ina mayar da wayar cikin jakar. A kofar layin mu ya sauke ni don adaidaita bata shiga ciki sai dai babur, kudin sa na basa na huta ma shiga layin kai na a kasa ina kara hade rai sosai sbd samarin unguwar da basu da aiki sai gulma, dai-dai kofar Gidan mu samarin da suke zaune suka hada baki gurin cewa “Ina wuni Ya Aasma” Fuska ba yabo ba fallasa nace “lafia qalau” Ina tura kofar gidan mu wacce ake lallabawa don saura kadan ta fadi. Sai da suka tabbatar na wuce sannan daya daga cikin su yace “Wallahi Ya Aasma tana mugun kashe ni, kai nifa sonta nake shiyasa nake yawan zama anan in na dai dai ci lokacin dawowar ta daga aiki ya kusa” Kallon sa Auwalu yai yace “eh lallai Khalifa baka da hankali ynxu Ya Aasma din kake so” Lumshe ido wanda aka Kira da khalifa yai yana dafe dai dai zuciyar sa yace “hmm baza ku gane ba kawai amma nayi nisa a kogon kaunar ta, ta hadu ne fah ta ko ina Wallahi” Auwal ne ya taba sani da bai ce komai ba sai kallon kasa da yake yi kawai. Dagowa yai yana sauke ajiyar zuciya yace “ina jin sa Auwal, Ai baxan ce masa komai ba don nasan duk irin son da zai ce yana mata ba kamar yadda ni nake kaunar taba” Cacar baki suka fara tsakanin sa da Khalifa da kyar Auwalu ya raba su kuwa ya mike ya tafi hanyar sa daban ba tare da sunyi wa juna magana ba. Lokacin dana shiga dan matsakaicin tsakar gidan namu Umma tana zaune akan tabarma tana jin radio iska sai kada bishiyar fruit din dake tsakar gidan namu wanda yasa gidan sanyi mai dadi. Zama nai akan tabarmar ina fadin “Barka da yamma Umma” Murmushi Umma tai tana rage volume din radion ta tace “lafia qalau Aasmaa ya aikin” Dan yamutsa fuska nai nace “Alhamdulillah Umma, duk na gaji yau wallahi gashi gobe da wuri zan fita an bada order din abincin biki” Murmushi Umma tai tana dafa kafada ta tace “Allah ya bada sa’a toh” “Ameen” na fada Ina mikewa na shiga dakin mu. Gidan mu dan karami ne sosai mai dauke da daki falle biyu sai toilet a tsakar gidan da wani guri daga can karshen gidan inda aka kewaye mana shi da langa langa anan muke ajiye kayan kitchen dinmu. Daki daya muka dauka nida Umma wanda yake da dan girma, raba sa mukai da labule daga ciki katifar muce da yar karamar wardrobe din kayan mu sai wasu tarkacen dai a gefe, daga inda muka mayar palo kuwa ledar daki ce kawai sai wani karamin table a gefe wanda Umma take ajiye kayan kukar da take siyar wa akai. Cikin dakin na shiga na cire kayana Ina dan tsaki sbd zafi, zani na daura na zira hijab, kwandon wanka na na dauka na fito. Sai da na jawo ruwa daga rijiya sannan na shiga toilet, na dau lokaci Ina wanka sannan na yi alwala na fito Ina sauke ajiyar zuciya don sai Ynxu iska take shiga jikina. Daki na shiga na zira rigar bacci ta mai tsantsi na sa hula, wayata na dauka daga jaka ta na fito zuwa tsakar gidan. Ban nemi abinci ba sai hira da muke da Umma a hankali Ina bata labarin irin girkin dana yi yau da kuma yadda nake yin abincin. Sallar magriba da aka Kira ne yasa mu tashi muka shiga daki, ni da yake Ina da alwala sallah nai, bayan na idar ban tashi ba zama nai ina jan carbi a nutse, sai da nayi sallar isha’i nayi shafa’i da wutr sannan na tashi Ina ninke sallayar. Daki na shiga na dauko bargo da pillow na shinfida a palon na kwanta Ina gane a wayata don ynxu Umma lokacin jin radion tane nasan baxa ma ta tsaya saurara taba shiyasa nayi kwanciya ta a palon. Da Sallama Umar ya shigo hannun sa rike da bakar leda. Ina daga kwancen na amsa masa sallamar. Zama yai daga gefena yace “Ya Aasma barka da dare” Murmushi na masa har dimple dina suna lotsawa, a nutse nace “lafia qalau Umar ya kasuwa?” Murmushi yai shima yana gyara zama yace “Alhamdulillah yau kasuwa tai kyau ai har kayan abinci na siyo mana don naga namu sun kusa karewa” Mike wa nai Ina janyo ledar na bude fuskata dauke da fara’a kamar yasan tunanin dana wuni Ina yi kenan, don jiya na duba naga shinkafar mu saura baifi kofi uku ba sai masara da gero. Dagowa nai na kalle sa nace “Masha Allah, Allah yayi ma albarka kamar kasan abin da nake ta tunani wallahi tun da safe abin da yasa ma ban maka magana ba sbd gobe in Allah ya kaimu zamuyi abincin biki kuma nasan za’a sallame mu akai”. Gyada kai yai yana murmushi yace “ai bata baci ba Ya Aasma sai mu karo wasu kayan da kudin yadda zamu dan dade bamu siya ba koh” Daga kai nai nace “hakan zamu yi Insha Allah kuwa”. Mikewa yai yana dafe cikin sa yace “yunwa nake ji sosai bara naje na dibi abinci nasan nawa ne ya rage kawai”. Umma dake daki tana sauraren su hawayen daya zubo mata ta goge tana kara godewa Allah daya bata yara masu tausayi da Jin kai, da badan yaran ta ba ai da bata san yadda rayuwar ta zata kasance ba lokacin da mijin ta ya rasu. Lumshe ido tai tana binsu da addu’a. Ni kuwa Ina game bansan lokacin da bacci ya dauke ni ba sai da Umma ta tashe ni na mike na shiga daki da kyar don baccin nawa ya fara nauyi. ******** Mami ce ta mike ta nufi dining area don ganin me Abdallah yake yi tun dazu wajen 2 hours kenan ko tashi bai yi ba. A zaune yake idonsa akan handout dinsa yana karatu, sosai ya bada dukkan attention dinsa gurin karatun don gobe suna da test. Dafa sa Mami tai tace “Abdallah karatun ya Isa haka don Allah ka tashi kaje ka huta mana”. Dago sexy eyes dinsa yai da suka dan yi ja alamun gajiya a tattare dasu, daga kai kawai yai ya mike yana hada kan takardun sa. Kallon Mamin yai da kyar ya bude bakin sa murya kasa kasa yace “good nyt”. “Allah ya tashe mu lafia” ta fada tana binsa da kallo don ynxu miskilan cinsa ya daina bata mamaki sai dai tsoro mutum kamar aljani sam baya magana. Dakin sa dake gefen part din Mami ya bude da key din hannun sa ya shiga yana lumshe idonsa, dakin ya gaji da haduwa da tsadaddun furnitures komai ash ne da ratsin white. Akan resting chair din dake dakin ya zauna yana lumshe idonsa, mika kawai yake yana tsaki akai akai sai da ya gaji da tsakin sannan ya mike ya shiga toilet yayi wanka. Gajeran wando yasa kawai ya kwanta akan lallausan bed dinsa yana jan bargo ya lulluba idonsa a rufe. Tunanin test din da zai yi yake ga kuma lawyer dinsa yace ya samu lokaci a goben yazo yayi signing paper din estate din da zai siya Abuja. Karamin tsaki yaja yana matse kafafun sa, shi duk wannan ba damuwar sa bace sha’awar dake damunsa kadai ta ishe sa, juyi kawai yake akan bed din yana matse kafa da kyar ya samu bacci ya dauke sa…….. Ya kuka ji salon labarin labari neh mai dauke da tsantsar soyyaya mai tsaya wa a rai🥰🥀 Domin magana da marubuciyar kai tsaye 09066728387 Mrs A.M🥰 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 2 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Washe gari Ina idar da sallar Asuba ban koma bacci ba sai fito wa da nai tsakar gidan mu na share simintin dake kasan duk da wasu guraren sun farfashe haka na share da kyau na dibi ruwa a rijiya na wanke simintin, toilet na wanke da toka da omo sannan na shiga daki shima na gyaro shi. Ba alamar gajiya a tattare da ni ko bacci don na saba da wannan aikacen tun da akai wa Maryam aure ni nake yin komai sai dai wani lokacin in na makara ko Ina sauri na bar wa Umar yayi. Ruwa na jawo a rijiya na ciki katon durom din mu dake ajiye daga gefen kitchen, sai da na tabbatar na gama cika ko Ina har randar dake daki d wacce take tsakar gidan sannan na jawo dan karamin gas dinmu na kunna. Tea na dafa wanda na sa masa Kayan kamshi na juye a cikin flask din mu, flour da Umar ya siyo jiya na kwaba nayi fanke, kafin 7 na gama komai na ajiye a daki. Wanka na shiga nai a nutse bayan na fito shirya wa nai cikin Riga da zani sun min das a jikina kamar a jikina aka dinkasu, duk kuwa da yadda nake tabbatar da kar ayimin dinki matsattse a banxa don ko ya yake in nasa sai yabi structure dina. Umma dake zaune a kan sallaya kallo na tai tana murmushi ita kan ta tasan duk namijin daya auri yar tata ya moree. Murmushi nai cikin kunya na zaune a gefenta ina janyo flask din tea, tea na hada mana na bata cup din ta ina zuba mana fanken a plate. Muna cikin ci Umar ya shigo shima da alama yayi wanka, zama yai yana gaishe mu shima ya hada tea dinsa. Da muka gama tattare kayan yai ya wanke su ya kife, dama haka muke in har muka gama cin abincin safe ko dare shi yake wanke wa sai dai in baya gidan. Mikewa nai na zira Hijab dina light brown wanda ya min kyau sosai, jakata na rataya a kafa da Ina Murmushi na kalli Umma nace “na tafi Umma kar na makara”. Murmushi tai tace “Allah yayi muku albarka ya bada sa’a”. Fuskata dauke da Murmushi nace “Ameen” Kallon Umar nai nace “na tafi Allah ya bada sa’a”. Murmushi yai yace “Ameen Ya Aasma, ko zan baki kudin mota?”. Irin kallon dana masa yasa shi dariya yana daga hannun sa yace “wasa nake miki wallahi”. Tabe baki na nai Ina nufar kofar zan fita don ni maganar da zan fada masa ma ta min wahala gwanda nayi shiru. Muryar Umma ce da take ce min “kinga Aasmaa na manta ban fada miki ba kuwa, jiya Maryam ta kira ni tace don Allah wai me yasa baki son zuwa gidan ta”. Juyuwo nai gaba daya Ina kallon Umma bakina yana motsi magana nake son yi amma sbd miskilancin daya zamar min jiki yasa in har zanyi magana sai na dan yi shiru na some seconds. Ajiyar zuciya na sauke ina gyara hijab dina nace “Umma ita dai Maryam ta cika rigima Wallahi, Ynxu kawai god’ai god’ai dani sai naje gidan kanwa ta”. Tsaki Umma tai tana kawar da kanta fuskar ta a hade tace “toh meye a ciki dan kinje gidan nata? Ina ba kwana zaki je kiyi ba ziyara ceh fah Aasmaa” Dan turo baki gaba nai nace “Umma kawai ki bata hakuri Gaskia ai ni tasan baxan ma saurare ta ba shiyasa ta biyo ta gurin ki” Kafe ni da ido tai tana nazari nah, gyada kai tayi tace “ynxu dai baxa ki je ba kenan?” Gefe na juyar da kai na badan naso ba sai dan ganin kamar ran Umma ya baci nace “zan je” Murmushi Umma ta saki tace “ko ke fah, Ynxu yaushe zaki je na buga mata waya na fada mata”. Shiru nai kafin nace in “na tashi daga aiki sai na leka kawai Umma”. Da sauri tace “ban yadda ba gaskia, nasan irin zuwan da kike nufi ko 30 minutes baxa kiyi ba zaki fito ki bari sai ranar da baxa ki aiki ba koh kinga ai sai ku dade ma kuna hira”. Daga mata Kai kawai nayi nace “Allah ya kaimu” Sallama na sake musu na fito duk rai na a jagule, ni Sam bana son zuwa gidan Maryam don wani iri nake ji in naje, tana kanwata kawai sai na dinga zuwa mata Gida ai abin ma kamar ba tsari, Ko Yaya itama ban cika zuwa gidan taba don ni Ynxu ma na manta yaushe rabon naje gidan nata. Ajiyar zuciya na sauke kawai Ina Jin wani abu daga kasan zuciya ta yana tasomin mai daci. Ina wannan tunanin na tari adaidaita na tafi gurin restaurant dinmu. Tun da na shigo ciki na hade rai na ganin motor wanda bana son tarayyar mu da shi, ban san meye matsalar sa dani ba da yake son lallai sai ya jefa rayuwa ta a cikin hatsari. Kai na a kasa naji yace “Assalamu alaikum Queen” Sbd nasan muhimmancin Sallama shiyasa na amsa shi Ina kara hade rai na. Murmushi ya saki yana nade hannun sa ya zuba min ido fuskar sa dauke da Murmushi daya ke bayyana farin cikin sa na ganin na da yayi. Ganin yadda ya babbake hanyar yasa ni kara daure fuskata nace “Malam matsa min koh” Langwabe kai yayi cikin kasa kasa da murya yace “Haba Queen ynxu kin daina fadin sunana me yasa uhm?”. Dago ido nai nayi masa wani kallo da manyan idona, lumshe idonsa yai yana dafe dai dai zuciyar sa a nutse yace “ina kaunar ki” Tsaki nai Ina girgiza kai na kawai cikin kausasa murya wai ni nan irin zan sa ta zama katuwa sai dai a bisa rashin sani kara mata dadi nai. “Me yasa ka tsane ni neh Kabir, a hakan kake ikirarin kana so na bayan ni dai kiyayya nake gani kawai kana nuna min”. Rude wa yai jin cewa wai tsanar ta yake, shi daya ke haukar son ta, tun ranar daya soma dora idanu akan ta zuciyar sa ta mace a cikin kaunar ta amma wai yau shi take cewa baya son ta. Tausasa murya yai yace “Queen taya zaki ceh bana son ki don Allah magana ko dadin ji babu haka” Hade rai na sake yi sosai nace “tabbas baka sona don naga alama nema kake ka janyo min zagi a gurin mutane, sannan amintar da aka kulla tun yarinta kake so ka rushe ta” Gyara tsayuwar sa yai yana kallon ta dama yasan wannan ne damuwar tata. A nutse shima yace “maganar mutane duk ba damuwa bace Queen, ni dai Ina son ki kuma fata na shine ki amince dani wallahi bada shiririta nazo ba auren ki nake son yi”. Ajiyar zuciya ya sauke yana dan dafa motar dake gefen sa yace “ita kuma Hajjo bata da damuwa nasani, sbd kullum maganar ta shine tana so taga kinyi aure kema”. Murmushin takaici nai Ina girgiza kai na namiji kenan, wai ni yau mijin Hajjo yake bi yana fada min cewa so na yake da aure mijin aminiya ta wacce muka tashi tare har ynxu bani da aminiyar data fi ta duk da Ina dan jan baya da Ita tunda Kabir yazo min da wannan maganar. Kallon rainin wayo na masa cikin takaici nace “daya ke yawan ce maka tana son taga nayi aure ta taba ce ma ka aure ni” Da sauri ya tari numfashi na da cewa “don Allah kar ki haramta min abin da yake halal neh, Wallahi ko lokacin dana fara ganin ku ke ceh wacce zuciya ta take matukar kauna, kwarjinin da kika min ne yasa na koma gurin Hajjo ba wai don ita din nake so ba sai dai Ina ganin kamar ke din matar Manya ceh?”. Tabe baki nai Ina gyara tsayuwata na kalle sa cikin ido nace “tabbas bakai karya ba ni matar manya ceh ka yi min yaro da yawa don nasan baxa ka bani shekaru 10 ba ni kuma na fison na auri Wanda ya girme min sosai ta haka neh kawai zan samu nutsuwar yi masa biyayya yadda ya ka mata”. Juyawa nai na shiga cikin restaurant din kai na yana sara min don wannan maganar da nayi dashi har ta haddasa min ciwon kai, ban taba tsaya wa nayi magana dashi sosai ba don bana son tsautsayi ma yasa wani idon sanin ya ganmu tare yaje ya fada wa Hajjo don baxan ki dadin hakan ba, shiyasa yau na tsaya na fada masa abin da yake rai na in yaga dama ya kyale ni yaje can ya kulla da matar sa. Tsaki naja a fili rai na duk a bace wai ni yake so mutumin dana san in ya girme ni Toh da shekaru uku neh. Haka na shiga kitchen muka fara aiki gadan gadan don karfe 3 za’a kai abincin. Kabir kuwa yana tsaye har sai da yaga shigar ta cikin restaurant din sannan ya lumshe idonsa, Allah ya sani yana matukar kaunar Aasmaa kuma baya jin zai iya rabuwa da ita. Nannauyan numfashi ya sauke yana dafe kan sa shi Ynxu yadda zai shawo kan Hajjo yake ne ma, wata kila in ya shawo kanta ya samu Queen dinsa ta saurare sa. ****** Cikin takun sa na cikakken namiji ya shigo palon, sanye yake da gajeran wando black wanda ya kama sa daga kasa sai riga white mai gajeran hannu wacce ta kama sa ta fito da damtsen hannun sa, kafarsa sanye da black boot. Yayi kyau har ya gaji shigar ta matukar haska farar fatar sa sai kamshi yake. Yusrah ce zaune a palon tana kallo sai twins da suke game a iPad dinsu, bin ko Ina da kallo yai so yake ya bude baki ya tambaye su ina Mami amma bakin ya masa nauyi kawai sai ya nufi hanyar dakin nata. Ajiyar zuciya Yusrah ta sauke da karfi bayan wucewar sa, tun da ya shigo gabanta yake faduwa don har sai data matse remote din dake hannun ta da karfi sbd yadda zuciyar ta take bugawa. Allah ya dasa mata son Yayan nasu har bata san yadda zata yi ba gashi ita dai ba zata iya fadawa Mummy ba don tasan kashe ta ne kawai baxa ta yi ba. Yadda Mummy din suke zaman kishi da Mami tasan abu ne mai wuya su amince wa auren su da yayan nasu, bama wannan ba in har sun amince shi zai yadda kuwa? Wannan tunanin ne yasa taji wani hawaye mai zafi ya zubo mata da sauri ta mike ya fita daga palon, garden dinsu taje ta zauna ta hada kai da gwiwa tana kuka mai tsuma zuciya.. ** Kallon sa Mami take tana Murmushi, yaron nata kullum girma yake sake yi yana zama cikakken saurayi, a yadda yake dinnan ba wanda zai yi tunanin shekarun sa 24 sbd girman jikin sa tsaf sai kace ya kai 30. Yar dariya ta saki tace “toh Abdallah na zama sirikar kane, kana zaune amma kayi shiru tun dazu kan ka a kasa” Idonsa dake lumshe ya bude yana bude baki da kyar yace ……. Comments nd share please🥹 Mrs A.M🥰 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 3 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Idonsa dake lumshe ya bude yana bude baki da kyar yace “Mami na dawo daga school neh” Cire tagumin da tai tayi tana kallon sa yadda yake maganar da kyar kamar wanda yake ciwon baki, ita da take mahaifiyar sa har yau baya iya zama da ita yayi hira sosai, dama in kaji maganar sa toh yana tare da Musbahu neh aminin sa ko kuma Iya kakar sa wacce ta haifi Baban sa itama don dole take sa shi magana ba wai don yana so ba. Gyada kai tayi tace “ina ta zuba ido tun safe ai kazo kayi breakfast sai ce min akai ka fita”. A hankali yace “uhmm test mukai neh kuma Ina son na sake karatu a school”. Murmushi tai tace “Allah ya taimaka toh ya bada sa’a”. A kan lips dinsa taga ya amsa ba tare da sautin muryar sa ta fito ba. Ita dai kallon sa kawai take miskilancin sa yana damun ta. Mikewa yai tsam ya dawo kusa da ita, kwanciya yai ya dora kan sa akan cinyar ta idonsa rufe . Itama bata sake masa magana ba sai hannu data sa tana sosa masa gashin kan sa. Sun fi 10 minutes ba Wanda yayi magana har ta cire rai da maganar tasa taji yace “Na siya estate a Abuja Mami, Ina son zuwa ko weekend ne na duba”. Shiru yai yana mar mar da bakin sa kafin yace “uhmm in yana bukatar gyara sai ayi mutane sun fara neman sa koh” Fara’ar tace ta dadu sosai cikin murna tace “Masha Allah, Allah ya kara dauka ka yasa kafi haka”. A hankali yace “Ameen Mami” Bude kofar dakin akai wata matashitar budurwa ta shigo hannun ta rike wayar ta tana dannawa, birki taja ganin Yayan nasu kwance ya daura Kansa akan cinyar Mami. Juyawa tai zata fita taji yace “kee”. Sai da Kayan cikinta suka juya sbd tashin hankali, ita wallahi sam bata san yana cikin gidan ba da abinda zai sata fito wa sai ya fita. Kamar zatayi kuka ta juyo tana takowa a hankali, tsugunna wa tai kanta a kasa tana jiran mai zai ce mata. Mikewa yai daga cinyar Mami din ya tsaya yana zura hannayen sa a aljuhun wandon sa, sexy eyes dinsa ya zuba mata yana karantar ta. Tsaki yai yana girgiza kai wayar sa ya ciro daga aljihun sa yayi danne dannen sa. Kofar dakin ya nufa sai da ya bude zai fita yace “ki duba wayar ki” daga haka ya fice. Nannuyan ajiyar zuciya ta saki tana mike wa, kallon Mami tai a tare suka fashe da dariya, miskilancin Abdallah yawa gare sa. Cikin dariya Faty tace “wai Mami da ya bude baki yayi min magana gwanda ya turo min message tab lallai besty tana da aiki a gaban ta wallahi”. Wayar ta bude tana zama a gefen Mami, message ya turo matan kuwa kamar haka “Kar ki kara jawo min wannan yarinyar kuzo dakina, in ba haka sai na karya ku”. Baki ta rufe da sauri tana zaro ido, kallon Mami tai tace “Mami wai ni da besty zai karya sbd jiya data zo tace sun dade basu hadu ba muje dakin sa su gaisa fah kuma Wallahi a bakin kofa kuma tsaya muka yi knocking”. Tabe baki Mami tai tana mikewa tace “ke kika so ni dama ai na fada muku bana son ku dinga yawan zuwa dakin sa, amma bakya ji”. Turo baki tai a shagwabe tace “amma Mami itace fa wacce zai aura meye a ciki don taje ganin sa”. Hararar ta tayi tana wucewa toilet tace “in aka yi auren ai sai tayi ta shiga dakin nasa amma ynxu ba” Bin bayan Mami da kallo tai tana Gyada kai, ajiyar zuciya ta sauke tana cewa lallai besty ta hadu da aiki wallahi. Shi kuwa Abdallah daya fito garden ya nufa kasancewar gurin yana matukar burge sa yasa yake yawan zuwa gurin yana zama. Sheshekar kuka yake ji a hankali wanda yana hankalin sa ya shiga ciki sosai don ganin wace take kuka haka. Bayan ta kawai ya kalla ya gane ita ce, dazu daya shigo ya dan kalle ta hakan yasa ya shaida Kayan ta, kafe ta da ido yai yana kallon ta kawai, yarinyar tana da hankali sosai shiyasa suke dan shiri don wani lokacin har murmushin saman lips dinsa tana gani. Shi dai kuma haka kurin jinin sa ya hada dana yarinyar ko hantarar ta baya shi don tausayi ma take basa yadda take shiru shiru dinnan ko yaushe zaka ganta cikin nutsuwa. Gyaran murya yai da dan karfi wanda ya janyo hankalin Yusrah ta juyo gare sa. Saurin mikewa tai tana goge hawayen idon ta, sai da ta gama goge wa tsaf sannan ta sunkuyar da kai cikin rawar jiki tace “ina wuni Ya Abdallah” Daga kai yai kawai yana tsare ta da ido, cikin taushin muryar sa yace “ke mene kike kuka?” Da sauri ta dago ta kalle sa zuciyar ta na tsalle sabon son sa yana mamaye zuciyar ta, cikin inda inda tace “umm physics test ne na fadi shine nake kuka”. Karamin tsaki yai kawai yana kallon ciyayin da suke koraye shar mamaye da garden din, murya a dakile yace “dauko na koya miki”. Zaro ido tai tana bude baki da mamaki tace “Ya Abdallah zaka koya min da…..” kallon daya mata ne yasa ta rufe Baki da sauri ta fyalle a guje zuwa part dinsu don dauko book din nata Mummy dake zaune taga Yusrah ta shigo a guje ta shige dakin ta. Ganin ta fito hannun ta rike da books tace “keh lafia Ina zaki”. Tsayawa tai tana sosa gashin girar ta, cikin murya kasa kasa tace “Ya Abdallah ne yace nazo ya koya min physics” Tsaki Mummy tai tace “ban hana ki wai shige ma wancan yaron ba, bana son tarayyar ki da shi Ina sake maimaita miki ki shiga hankalin ki wallahi”. Kan ta a kasa idonta na kawo ruwan hawaye tace “Mummy karatu fah zai koya min kawai” Tsaki Mummyn tai tana juyar da kan ta, ita dai tasan koma meye in ma wani abu Yusran taje sakawa a ranta Toh wallahi baxai sabu ba. Ganin Mummyn ta juyar da kanta yasa yusrah fitaa a guje tana sakin Murmushi yau Abin kaunar ta zai koya mata karatu.. ****** Aiki muka sha sosai, duk na hada gumi ga shi nice shugabar su a kitchen din. Kafin azahar mun gama komai an ajiye a gefe, tsaftace kitchen din da yar barandar dake bayan kitchen wacce muke wanke wanke a gurin. Sallah muka yi sannan muka dawo kitchen, tuwon shinkafa da miyar taushe na daura sai sakwara da miyar agushi. Har na gama na zuba a inda muke zubawa ake ajiye wa in kazo siya a ma a microwave ba’a zo daukar abincin ba. Fita nai na wanke fuskata na gyara hijab dina duk na hada gumi. Ina zaune Ogan mu yazo yasa aka fara fita da abincin ana sawa a mota. Sai da aka gama sakawa wadan da zasu je suyi rabo suka shiga motar, Ina daga zaune Ina kallon su so nake kawai 5 tayi na tafi tunda na gama abinda zanyi da wuri nake son tafiya Gida yau. Ogan namu ne yazo ya tsaya a kai na yana bina da wani kallo irin kallon dana tsana kenan. Murmushi yai yace “Aasmaa yau ma baxa ki taimaka kije ayi rabon da ke bah”. Hade rai nai Ina juya Kai na gefe nace “bana son zuwa kaga ni aiki na a kitchen yake bare acee” Murmushi yai yace “da kin taimaka dai kin je kin sa ido tunda kinga kece babbar su koh” Mikewa nai Ina rike jakata a hannu na da kyau nace “maybe next time Ynxu kam bana ra’ayi Gaskia” Wuce wa nai gate don nama fasa jiran 5 din tayi. Bin bayan ta da kallo yai yana lasar baki, shafa gemun sa yai yana fadin Allah ya kai damo ga harawa Comments nd share please🥹 09066728387 Mrs A.M🥰 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 4 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Sallama nayi daga bakin kofa na shiga cikin gidan, Umma bata tsakar gida nasan wata kila tana daki ko toilet. Dakin na shiga sai dai bata ciki haka yasa nayi sauri na chanja kaya, fito wa nai na dora mana abincin dare. Ina zaune Ina Candy crush Umman ta fito daga toilet. Dago Kai nai na kalle ta Ina murmushi nace “Ina wuni Umma”. Murmushi tai tana zama a gefen tabarmar tace “lafia qalau, ai Ina Jin sallamar ki nace yau da wuri kika dawo kenan”. Dariya nai Ina gyara zama na don na dan jingina da bango nace “Umma mun gama duk abinda zamuyi shine kawai naga me zan tsaya ai gwara na taho koh”. Daga Kai tayi tace “tabbas kuwa, tunda kin gama dama mai zaki jira neh”. Muna hira jefi jefi har na gama mana dan waken da nayi, namu na zubo mana Wanda zamu ci nida Umma ynxu ragowar kuma na zuba a flask. Sallamar Yaya da naji yasa na dago da dan sauri Ina bude manyan idona. Yaya ce kuwa sai babbar yar ta Basma wacce har ta zama budurwa ma don shekarar ta 15, sai autan ta wanda take goyen sa Walid. Murmushi kwance a fuskata nace “wa nake gani kamar mutuniyar”. A guje Basma ta taho ta rungume ni, nima rungume tan nai tsam cike da kaunar ta, Ina son yarinyar sosai kamar yacce take sona don ni na yaye ta. Tabe baki yaya tai tace “toh sai me don an rungume wata mu an bar mu a shanye”. Dariya nai Ina Kama baki nace “Yaya abin kuma hadda haka”. Zama tai akan tabarmar da Umma take zaune tai tana cewa “oho dai kuma Ina kallo dan wake ne dole a zubo min naci”. Murmushi nai ina juyo ragowar dan waken, tare muka hadu duka muka ci walid na kan cinya ta Ina basa yana ci. Da muka gama ci Basma ce ta dauki plates din taje ta wanko su, daukar Walid dake kan cinyata tai ganin ya fara bacci ta shiga daki da shi. Kallon Yaya nai nace “ai da nasan zaki zo dana fadawa Maryam itama tazo ai”. Dariya tai tace “na fada mata sai ce min tai ita baxa ta zo ba don tasan in har tazo baxa ki yadda kije gidan ta ba”. Kallon Umma nai dake sauraren mu nace “Umma kina ji dai koh”. Itama Umman dariya tai tace “ai da gaskiyar ta Aasmaa ayi mutum shi sam baya son zuwa gidan yan uwan sa”. Shiru kawai nayi don nasan duk yadda zan yiwa Umma baya ni baxa ta fahimce ni ba. Hira muka sha sosai sai bayan isha’i sannan ta tafi ita da Walid, Basma kuma hutu zata mana. ******* Kara hade ran sa yai tam yana yatsina fuska, baya son takura amma ya lura yarinyar nan bata da hankali sam. Musbahu da yake kallon sa dariya ya kara kyalkyalewa da ita hadda faduwa kasa. Tsaki Abdallah yai yana kifa wayar akan hannun kujerar don ma kar ya ga yadda take haske Fuska a hade ya kalli Musbahu da yake ta zanga dariya, Kara tamke fuskar nan yai sosai har sai da ta fara ja-ja. Kokarin sai ta kansa Musbahu yai amma duk da haka murmushi ne kwance a fuskar sa, cikin tsokana yace haba angon Meena, ka daga wayar mana tana ta kira amma ka wani share ta. Irin kallon da yake wa Musbahu kadai zaka gani kasan cewa lallai ransa a bace yake sosai, girgiza Kai kawai yayi yana dan saussauta fuskar sa a nutse yace “ni sa’an kane Musbahu”. Dariya Musbahu yai yace “kwarai kuwa har na ma baka wata 5 sai dai kuma in a harkar kudi ne kasan ance Yaro da kudi abokin tafiyar manya” Kuyi min uzuri yau plz da kyar na samu nayi wannan Comments nd share plz Mrs A.M🥰 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 5 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tsaki Abdallah yai yana mikewa kawai ya shiga dakin sa tare da banko kofar. Dariya sosai Musbahu yake yi hadda kwanciya, yasan ya gama kule abokin nasa shiyasa ya mike kawai ya dauki wayar sa ya fita. WAYE ABDALLAH Asalin su yan Mambila neh, Iya kakarsu ce wacce ta haifi babansu, su biyu ne a wajen Iya da Ahmad sai Bilkisu. Allah yayi ma mahaifin su rasuwa tun bayan haihuwar Bilki, iya bata sake aure ba ta zauna tana kula da yaran ta, kuma Alhamdulillah basu sha wuya ba kasancewar mijinta ya rasu ya bar musu dukiyar shanu da gonaki. Lokacin da Ahmad ya gama diploma dinsa a jalingo sai ya ke fitar da albarkacin gonar su gari gari, ganin yafi kasuwan cin ya dan fi karbuwa a kano sai ya kasance in yaje can bayan ya siyar da Kayan gonar sai ya sari atampopi ya dawo dasu jalingo din ya siyar, a haka har ya koma harkar dillanci. Shima daya lura da irin albarkar da kasa take da shi sai kawai ya koma Mambila sukai shawara da Iya aka raba musu gadon su, Gonar sa daya kawai ya bari amma ya siyar da komai ya taho da kudin kano. A lokacin barayi sun yi kokarin sace masa kudin sa don har sun ritsa shi Allah ya kawo Sani gurin wanda yake dan taba rashin ji a zamanin. Sun san ko waye shi sai suna tsere, tun daga nan abota ta kullu tsakanin Ahmad da Sani har dai Ahmad ya fada masa abinda yake son yi na siyar filaye da gidaje. Da yake harkar Baban Sani kenan sai abin bai zowa Ahmad da wuya ba, Baban sani kuwa ya tsaya Akan gaskiyar sa ya koya wa Ahmad yadda zai gudanar da kasuwan cin sbd shima yaji dadin yadda sanadiyyar Ahmad din Sani ya shiryu. Ai kuwa Allah ya sawa abin albarka cikin lokaci kankani kudi sun fara zamar masa, har ya gina gidan sa. Da shawara Baban Sani din ya bude shaguna a kwari ya bayan da haya. A kuma lokacin Allah ya hada sa da Mami wato Maimuna, da farko ya ji tsoro don Baban Maimuna babban likita ne a AKTH. Zuwan sa na farko gidan su Maimuna din hankalin sa ya kwanta don Baban nata karbar mutunci yayi musu shida Sani daya raka sa, ya tambaye shi game da asalin sa bai boye masa komai ba ya fada masa. Shima kuma cikin dattako ya fada ma Ahmad yaje garin su ya fada wa iyayen sa suzo ayi maganar aure don tun kan ya basa izinin zuwa zancen sai da yayi bincike a kansa. Da murnar da yaje ya fadawa Iya itama taji dadi sosai, ba bata lokaci manya suka sa shiga maganar har suka yi aure. Zama suke mai kyau da tsafta don ba karamin son junan su suke ba, zuwan su Mambila na farko tare ya taho da Bilkisu wacce Iya tace da bata yadda ba sam bazai tafi da Bilkin ba, yadda ita bata zauna da Kanwar miji ba itama Maimuna din bata zauna da su ba gudun matsala. Da kyar dai Maimuna ta samu ta shawo kan Iyan bayan ta nuna mana ba wani matsala wallahi, ba dai a san ran iya ba suka dawo da biki din, don itama da ya so dauketa ta murzawa idonta toka tace ita da barin Mambila sai dai in ziyara zata kai musu amma In sha Allah kabarin ta a Mambila yake. Zaman Maimuna da Bilki abun sai sam barka, don cikin lokaci kan kani suka yi wata iriyar shakuwa. Bilki tana zuwa B.U.K don yin degree dinta, kuma tana da kokari sosai, bata da fara’a sosai kuma mace ce ita mai son komai ace ita ce a gaba kuma ta iya. Zaman su da Maimuna ba matsala don ita Maimunan ta iya zama da mutane shiyasa ta San yadda zata zauna da Bilkin ba tare da sun dinga samun matsala ba. Arzikin Ahmad sai dai ace Alhamdulillah don kuwa kudi kullum zuwa suke, haka kuma kullum cikin sadaka yake, duk ranar juma’a haka mutane suke taruwa a kofar gidan sa yana muku sadakar kudi inda Maimuna kuma take fitar da jallof din shinkafa d wake a hade a cikin takeaway ake sawa ana rabawa, wannan dabi’a tasu ta janyo musu soyayyar al’umma sosai. Shekarar su biyu da aure Maimuna ta samu ciki, fadar irin murnar da suka shiga bata baki ne, sai dai kuma tunda cikin ya shiga wata tara suka rasa gane kan Ahmad, yawan walwalar sa ta ragu kullum cikin tunani yake. Wannan abin ya daga hankalin Maimuna da Bilki, sunyi juyin duniya ya fada musu abinda yake damunsa yace bkm kawai yaka yake jin jiki sa wani iri wannan abin ya rage musu walwala sosai. A wani dare wanda yana daya daga cikin dararen da Maimuna baxa ta taba manta wa dashi ba. Tsakiyar dare ne cikin bacci taji kamar ana mata waiwayi a ciki, a hankali ga bude idonta. Sai da gabanta ya fadi ganin Ahmad zaune yana shafa cikin cike da kulawa da tsantsar soyyaya. Da sauri tayi kokarin mikewa sai dai yadda cikin ya mata nauyi sai ta kasa, shi ne ya taimaka mata ta mike zaune tana dan bude kafafun ta yadda zata ji dadin zaman. Kallo fuskar sa tai cikin damuwa tace lafia kuwa Yaya har ynxu baka yi bacci ba gashi wajen 3. Murmushi kwance a fuskar ta yana shafa cikin ta yace kawai bana jin baccin ne, yau ji na nake cikin wani irin farin ciki Maimoon(sunan da yake kiran ta in har yana cikin farin ciki) Itama samun kanta tai da Murmushi cike da Jin dadin yadda yace mana yana cikin farin ciki. Hira sukai sosai kamar ba dare bane in da yake ce mata in mace ta haifa ta sa mata Maimuna in kuma Namiji ne Abdullahi sunan Baban sa, sai turo baki take tana ce masa da kansa zai sawa dan sa suna In Sha Allah. Kallon ta yai ganin 4 tayi ya umarce ta da tayi alwala suyi sallah, shi y jasu suka yi yayi musu addua sosai, suna hawa gado ya janyo ta jikin sa duk da yadda yake jin tsinkewar zuciya amma haka ya daure suka raya sunna. Bayan sun samu nutsuwa wanka sukai a tare suka zo, kwanta da ita yai yana shafa kanta a nutse yana karanta mata Suratul Baqara har sai da yaga tayi bacci sannan shima ya kwanta yana mai sauke ajiyar zuciya. Zuba mata ido yai hawaye masu zafi suna zubo masa, a jikin sa yake jin mutuwa zai yi shiyasa yake matukar tausayin Maimoon din da kuma dan da zasu Haifa, sai kuma Iyar sa wacce bata da koya sai shi da Bilki. Lumshe idonsa yai yana maimaita kalmar shahada a hankali har bacci ya dauke sa. A hankali ta shiga bude idon ta tana dan yamutsa fuska ganin haske daya shigo ta jikin window, da sauri ta mike duk da nauyin da jikin ta yai, tasan waye mijin ta baya son ya makara sallar asuba, kuma tunda taga bai tashe ta ba alamun cewa shima ya makara kenan. Zagayawa tai ta bangaren sa ta shiga tashin sa sai dai shiru, tsoro ne ya fara shigar ta a hankali ganin yadda ya sandare ya kara wani irin haske sosai akan wanda yake da shi fuskar sa dauke da Murmushi. Da mugun gudun da batayi tunanin zata iya ba ta kirawo Bilki, itama ta rude sosai da kyar dai Bilki din ga fita ta kirawo gate man. Shine ya lullube fuskar Ahmad yana share hawaye ya fada musu Ahmad ya cika(Allah kasa mu cika da Imani Ameen). Wannan maganar tasa ta tayar wa da Maimuna hankali don labour ne yazo gadan gadan, da taimakon Bilki aka fitar da ita zuwa mota amma ta kasa cewa komai sai ajiyar zuciya take saukewa. Baza ta iya haihuwa ba dole CS aka mata aka ciro mata baby boy dinta. Lokacin data farko tayi arba da son din nata rungume sa tayi tsam tana wani irin kuka mai tsuma zuciya, kamanin sa gaba daya na Ahmad ne don duka kyaun Ahmad ya dauka har ma ya dara sa. Da aka sallame su ma gidan ta ta koma acan Iya ta zage take kula da ita da jaririn daya ci suna Abdallah. Sai da tayi arba’in sannan iya ta koma Mambila, taso tafiya da Bilki amma suka hade kai ita da Maimuna suna kuka akan su fa anan gidan zasu zauna tare dole Iya ta kyale su, sai dai daga bangaren Maimunan an turo mata kakar ta suna zama tare. Shekarar Abdallah biyu Sani ya fito da muradin sa na auren Maimuna, tashin farko ta ki amincewa a cewar ta wannan kamar cin amana ne ga marigayi. Da kyar dai aka samu ta amince aka yi auren ta tare gidan Alh Sani. Matar sa ta farko itace Hafsa suna kiran ta da Mummy tun farkon basa shiri da Mummy don tana mata hassada na yadda mijin ta ya fi nata mijin arziki. Ba karamin hauka tayi ba da Alh Sani wanda suke Kira da Alhaji y fada mata zai auri Mami, har yaji tayi sai da ta tabbatar da an daura auren ba yadda zatayi sannan ta dawo lokacin tana da yarinyar ta Waleeda wacce ta girmi Abdallah da shekara daya. A ynxu Mami (Maimuna) yaran ta uku da Alhaji sani Fatima wacce suke kira Faty mai shekaru 22, sai twins sultan da Sultana masu 13 years. Mummy kuma tana da Yara uku itama, Waleeda wacce ynxu tayi aure hadda yaron ta sai Yusrah mai 18 years sai auta Aryan mai 10 years shi sunan masa ma ya bata don kowa Auta yake ce masa. Zaman su ba yabo ba fallasa ita dai Mami bata shiga harkar Mummy sai ta kama taja mutuncin ta sosai, hakan da Mummy ta gani ne yasa itama ta share Mamin. Abdallah Matashin saurayi mai shekaru 24 a duniya, dogo ne sosai mai faffadan kirji wanda ya wadatu da kwantacciyar gashi mai laushi bakikirin. Yana da jiki dai dai mitsali wanda ya taimaka gurin dai-dai ta tsayin nasa, fari ne sosai amma mai ja yana da fuska mai kyau wacce take dauke da manyan sexy eyes masu zaiba zaiba, sai dogon hancin sa wanda y dace sosai d fuskar tasa, yana da karamin baki masu siraran lips jajaye kamar wanda yake sa musu jambaki. Yana da suma irin ta Fulani mai kyau da sajen da ya kara kawata fuskar sa, yadda yake kashe wa sumar da sajen nasa kudi ne yasa kullum kaga gashin zaka ga yana kyalli da daukar ido. Miskili ne na karshe don zaku iya zama da shi tun safe har dare ba tare daya ce miki ko kalma daya ba, son girma ne dashi kamar gembo shiyasa bai cika zama a cikin kannen sa ba a hausar sa kar su raina shi. Yana da kirki kuma yana da kyauta sosai sai dai mutuncin nasa ba kowa ne ya san da shi ba ko dan yadda yake mara son magana sai mutane da dama suke masa kallon mai girman kai. A Ynxu yana level 4 a university inda yake karantar Computer Science. Tun da ya gama secondary school Alhaji Sani ya saka shi a harkar kasuwancin babansa, don an dade da raba gadon yana juya masa ne kawai, kuma da y lura yaron yana da hazaka da kuma fahimt gashi duk abinda ya taba sai Allah yasa masa albarka sai kawai ya tattara dukiyar sa gaba daya ya damka masa tare da basa shawarwarin yadda zai gudanar da kasuwancin nasa. Da taimakon Alhaji Sani da kuma Uncle Usman lawyer din babansa ya shiga kara bunkasa kudin, manyan supermarkets guda biyu ya bude a kano, bisa shawara ale Alhaji ya siya katon fili a Abuja ya gina wani a Garki Area 1. Manyan mutanen daya fara kasuwanci dasu ne suka tallata masa siyan Estate a Abujan tare da fada masa yadda ake samun kudi a harkar. Sai da yayi shawara da Alhaji da Mami da kuma Uncle Usman duk suka basa goyon baya sannan ya siya manyan estate har biyu, daya a Maitama daya a Apo. Dabarar da yayi sai yasa kudi masu dan dama nan da nan kuwa aka Kama haya wasu kuma suka siya, bai tsaya harkar filaye da gidaje ba har gidan Mai ya bude ya kuma siya Manyan shaguna a kwari ya zuba kaya a ciki. Kudi ne na fitar hankali sai dai ba kowa ne yasan haka ba don boye kan sa yake, a school dinsu ma bai san ya akai suka sani ba shi dai kawai ji yai ana ce masa young billionaire. Yan mata da suke son sa yawa gare su, wasu ma iyayen su ne suke takowa takanas har gidan su samu Alhaji ko Mami sai dai ita Mami kai tsaye take ce musu yana da Mata already ai MEENA. Comments nd share 🙏 Mrs A.M 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 6 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Meena yarinyar Bilki ce Kanwar Baban Abdallah kuma aminiyar Mami, ita kadai ce yar Bilki wacce tare sukai aure ita da Mamin. Baban ta mai kudi ne shima don Custom ne kuma babba ne, yar gata ce ta gaban kwatance a wajen uwar ta, bata hada farin cikin Meena dana kowa. Meena farar bafullata na ce wacce take Kama da Abdallah don itama kyakkyawa ce sosai tana da kyaun fuska mai daukar hankali, budurwa ce mai shekaru 22 a duniya wacce take amfani da kyaun ta gurin gara kan samari. Meena budurwa ce mai iyayi da mugun jiji da kai, ta dauko halayen mahaifiyar ta gurin son ganin cewa tafi kowa, sai dai abinda yake damunta duk wannan kyau nata bata da structure mai kyau, tsayi kawai yake da shi amma duk wani abu na cikar mace ita komai nata karami ne don siririya ce sosai, shiyasa Bilki wacce suke cewa Aunty take siyo mata abubuwan ciko tana sawa, wannan ya taimaka gurin kara iyayen Meena don Jin kanta take dai dai da kowa. Tun bayan rasuwar Ahmad Mami da Aunty sukai alkawarin in har Bilkin ta haifi mace zasu hada su aure kuma sai Allah ya amsa musu ta haifi macen, dukan su sun san da zancen auren nasu daga Meena har Abdallah. Meena wannan auren da zata yi da Abdallah yasa kanta yake kara girma zata auri young billionaire, ko ac cikin friends ta dinga hura hanci kenan tana fadin Abdallah nata ne ita kadai. Shi dai Abdallah kawai ya karbi zabin Mamin ne ba wai don yana son Meena din ba ko kuma ta masa kawai ya yadda ne don baya son Mami ran ta ya baci, amma shi sam bata masa ba bata cikin tsarin macen da yake so sannan shi baya son ma farar mace yafi son baka. A yadda su Mami din suke so shine in Abdallah din yayi masters dinsa lokacin Meena din itama ta gama Uni sai ayi musu aure. Meena bata ji don tana taba soyayyar shan minti da samarin ta, duk da maganar auren Abdallah kowa ya sani amma haka take samarin ta sai dai tana boye wa Faty kanwar Abdallah kuma bestyn ta. Yusrah Yusrah yarinyar Mummy ce ta biyu kamar yadda kuka sani, shekarun ta 18 yarinya ce mai kyau fara tana da kyau, kyaun bahaushe farar fatar da take da ita ta taimaka sosai gurin kara fito da kyaun ta kuma duk gidan ita kadai ce fara don su Faty duk chocolate colour ne sai kuma Abdallah da yake fari. Yarinya ce mai hankali da nutsuwa mara son hayaniya, bata dauko bakin halin Mummy ba don ita tana son yan uwanta sai dai ita Faty bata wani cika shiga harkar Yusrah din ba don basa shiri da Mummy. Tun da ta tashi take kaunar Abdallah, son ta ya shiga cikin jinin ta kuma bata san lokacin da hakan ta faru ba, kawai dai ita ta ga tana son sa ne da kaunar sa ta girma a zuciyar ta sai dai tasan samun nasa abu ne mai wuya duk da kuwa nata cire rai ba kullum cikin addu’a take Allah ya bata Abdallah in alkhairi ne shi in kuma ba alkhairi bane Allah ya c cire mata son sa amma kuma kullum kara son sa take haka yasa ta dage da addu’a. Musbahu Aminin Abdallah ne gidan su yana jikin gidan Alhaji sani, makaran tar su daya daga boko har Islamiyya hakan yasa suka shaku sosai, tun Abdallah yana share sa sbd miskilancin sa har ya sake ya dawo yana kula sa duk da yawancin hirar tasu Musbahu ne karfin ta. Aminin kwarai ne Musbahu sun shaku da yan gidan sosai har ba wanda bai san gidan Musbahu ba mutuncin da ke tsakanin Abdallah da Musbahu yasa gidajen biyu suma suke zumunci sosai. *Cigaban Labari* Sai da Musbahu ya leka dakin yaga Abdallah na bacci sannan ya shiga toilet yayi wanka, Kayan sa da suke wardrobe din Abdallah yasa ya kwanta shima a gefen Abdallah yana chatting a wayar sa yau a gidan yake son kwana kuma ya fadawa Ummin sa dama ya saba kwana a gidan shiyasa ma yake da kaya a wardrobe din Abdallah din. Abdallah din ne dai bai cika zuwa gidan su Musbahun ba har sai yayi fushi sannan yake zuwa. ******* A palo nake kwance idona yana lumshe Ina tunanin rayuwar mu, Basma da Umma na bari a daki su kwana a kan katifar ni kuma na dawo palon na kwanta. Idona a lumshe nake tunanin rayuwar mu, mu hudu ne a gurin Umma, Yaya, ni, Umar sai Maryam. Mun tashi cikin rufin asiri don Baban mu kayan masarufi yake siyar wa a kasuwan singa yana da Sharon sa dan karami da yake siyar da Kayan sa. Da akwai soyayya sosai tsakanin mu bama ni da naci sunan Maman sa. Shekarar sa 16 da rasuwa Ynxu don a shekarar da aka yi bikin Yaya ya rasu. A lokacin abubuwa da dama sun zo mana da wuya kuma munsha wuya sosai, tym din Ina Ss 2. Shagon Baba wanda shi ne kawai mallakin mu sai gidan da muke ciki Kawu laminu Kanin baba yaso ya karbe, Umma bata tsaya kunya ko wani abu ba fa fadawa Liman din unguwar mu wanda yake Aminin Baba kuma mahaifin Hajjo. Shine ya karbe shagon daga hannun kawo Laminu ya bayan hawa duk karshen wata ana kawo mana kudin, da kudin muke rayuwa Umma kuma tana da siyar da kosai da safe tayi shinkafa d wake da yamma sai awara da daddare. Aikin baya mata wahala don kusan komai ni nake yi, Maryam tayi yanke yanke Umar kuma yayi wanke wanke shi. Tym din data gama secondary school taso matuka ta shiga university sai dai kuma kudin mota da abubuwan da za’a kashe yasa kawai ta shiga catering school. Tana gama wa kuma Allah ya taimaka ta ta samu aiki a wani hotel, duk da albashin ta bashi da wani yawa amma kuma yana taimaka musu sosai shima. Wannan aikin data fara Kawu ba karamin zagi tasha a kai ba lokacin shekarun ta 22 yace taki aure ta tsaya karuwanci an fake da aiki. Tasha kuka sosai sai dai Umma ta kwantar mata da hankali akan kar t daga hankalin ta ita ta yadda da ita tasan kuma In sha Allah baxa ta bata kunya ba. Maryam na da 19years aka kawo kudin ta, kudin da sai da Aasmaa ta yi kamar zata zane ta sannan ta yadda aka kawo amma kullum cikin kuka take zata yi aure ta bar Yayar ta wacce lokacin take da 24years. Auren Maryam ya sa Aasmaa cikin kadai ci sosai, duk da kasancewar ta miskila amma Maryam din taka rawa gurin rage masa wasu damuwar da take da ita tunda Umar namiji ne kuma shima miskilin ne. A lokacin kuma ta kara shiga wani catering school din, da ta gama ne ta samu aiki a restaurant din da take ynxu da taimakon wata class mate dinsu. A ynxu Aasmaa tana da shekaru 29 a duniya, tun da take kuma saurayi bai taba tsayar da ita wai da maganar so ba, duk wanda zai zo gare ta toh fa Jan zuwaira ke kawo sa, ita kuma bata kasa a gwiwa take korar su wannan yasa Kawu kullum yake cewa ta tsaya zaban mai kudi shiyasa take koran samarin ta. Kabir mijin Hajjo ne kawai yazo da maganar aure da gaske, ita kuwa yadda take ji ai ko maza sun kare a duniya baxa ta auri Kabir ba. Ita fa ko ba Mijin Hajjo bane to yayi mata karami don Hajjon ta taba fada mata shekarar sa 34 shekara 5 kenan kawai ya bata, toh ta aure sa tace ta auri sa’an ta sam baxai yi ba, tafi son babba kamar 45 zuwa 50 haka sune dai dai ita a ganin ta don bata son rai ni gwanda ta auri Wanda ya girme mata sosai…. Aasmaa chocolate color ce wacce take da wani irin daukar ido da sheki, don tana kula da fatar ta sosai tunda basu da arzikin da zata siya mayukan gyaran fata masu tsada sai take siyan kayan gyaran jiki yake yin abinda duk karshen wata kamar so biyu. Tana da manyan ido masu dauke da black eye ball, bata da dogon hanci can sai dai kuma ba gajere bane dai dai yake wanda ya dace da round face dinta sai karamin bakin ta mai kala biyu, lip din kasan light pink ne sai na saman kuma yayi dan duhu kadan. Tana da cikar suma sosai don tun daga cikar gashin girar ta zaka gane haka, kanta yana da tsayi sosai har tsakiyar bayan ta kuma yana da cika sai dai ba wai laushi ne dashi ba yana da dan tauri bata sa masa relaxer. Bata da tsayi sosai kuma baza a kirata da gajeriya ba, tana da dan jiki a cike take sosai tana da wasu irin manyan boobs masu daukar hankali da tsokale idon mai kallon su, sai kasanta daya baje sosai hips dinsa suka fito ras da mazaunan ta da suka kara kawata surar tata, shafaffen cikin ta ya taimaka kwarai gurin barin shape din ta fito wa sosai, shiyasa kullum zata fita cikin Hijab take ko Ina zata kuwa don ita bata ma siyan mayafi sai Hijab. Aasmaa miskila ce kuma mara son rai ni yadda take da shekarun nan yasa bata sakin fuska don kar a rai na ta. Ynxu Yaya nada 34 years sai Aasmaa mai 29, Umar 27 sai Auta Maryam mai shekaru 24(Ashe ma sa’ar Abdallah ceh🤫) Lumshe idonta tai bayan ta gama wannan tunanin tana dan matse kafafun ta, yana daga cikin dalilan da yasa bata son yana yin sanyi da d’anima tana matukar wahala da sha’awar dake damun ta. Kara matse kafar tana jin kamar zatayi hauka, lumshe idonta tai kuma a karo na farko da inhar tana cikin wannan yanayin hawaye mai zafi suka shiga zubo mata…… Tohhh Alhamdulillah munji Asalin Abdallah da Aasmaa ynxu sai mu shiga cikin labarin muji ya zata Kaya…… Comments nd Share please Mrs A.M 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 7 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Kara matse kafar nayi Ina fashewa da wani marayan kuka, kuka nake a hankali Ina jin wani irin mahaukacin feeling ni dai haka nayi ta juye juye, sai gab da asuba na samu wahallalen bacci ya dauke ni. Umma ce ta tashe ni sallah, a nutse na mike kai na a kasa don bana son taga yadda idona yai, duk da ban kalli idona a mirror ba Ina jin yadda yayi luhu luhu nasan ya kumbura. Dan shin da nake ji a pant dina yasa nayi tunanin mafarki nayi, kirjina sai bugawa yake don ynxu in nace zan yi wanka Umma tasan wankan me zan yi, karin abin ma ga Basma kuma da wayon ta tunda ta fara period har saurayi ne ma da ita duk da dai ba’a basa damar zuwa zance ba amma suna waya kuma iyayen sa sun je nema masa aure gurin Baban ta. Toilet na nufa jikina duk a sanyeye, cikin ikon Allah ashe period ne wani ajiyar zuciya na sauke da karfi Ina murmushin da ban san yaushe yazo ba. Fito wa nai rai na fess, dakin mu na shiga ina kara sunkuyar da kai na. Umma dake zaune tana lazumi tace “har kin yi alwalar Aasmaa?” Kai na a kasa Ina bude yar karamar wardrobe din mu, cikin nutsuwa nace “a’a Umma bakon wata nane yazo cikin dare wanka zanyi tukun”. Gyada kai kawai tayi tana cigaba da jan carbin ta. Pad na dauka da pant sai zanin wanka na fita zuwa toilet. A nutse kamar yadda na saba nayi wanka na, sai da na wanke Kayan jiki na Ina fito wa na shanya akan igiyar mu ta shanya sannan na shiga daki. Basma da ta gama shara tana goge ledar tsakar palon da tsumma dagowa tai ta kalle ni fuskar ta dauke da Murmushi tace “Ina kwana Aunty Aasmaa” Nima murmushin na mayar mata nace “lafia qalau Basma ya ke war su Yaya”. Dariya tai tace “tab ai bana kewar su Aunty Aasma Ina ganin ki da Umma”. Murmushi nai cike da kaunar ta nace “toh masha Allah, anjima zaki raka ni gidan Maryam kinji”. Cikin d’oki tayi dan tsalle cike da farin ciki tace “Allah ya kai mu Aunty” A hankali nace “Ameen”. Labulen daya raba daki da palon na daga ma shiga ciki. Umma da har lokacin tana zaune akan sallaya kallona tai tace “yau zaki je gidan Maryam din”. Daga mata kai nayi Ina shafa mai a jikina. “Toh yau baki da aiki neh kar fa kiyi yamma kizo kije gidan nata sharp sharp ki fito” Karamar dariya nai Ina daukar kayana zan fita nasa don bana iya sa kaya a gaban Umma nace “Umma yau aikin nawa mai sauki ne nasan kafin azahar ma na gama In Sha Allah”. Daga Kai tayi tace “Allah ya taimaka toh”. Kaya na sa na Ina fito wa na daura mana breakfast, kunu na dama kamar yadda yawancin lokaci nake yi tun da Umma tafi son kunu sai kosai dana soya mana, tun dare ba gyara waken da sassafe kuma Umar ya kai min markade. Tare muka ci kosan a plate daya muna ci muna hira. Hannu na wanko na zira hijab dina nayi wa su Umma Sallama na fita, bacci nake ji sosai amma baxan iya yi ba tun da nasan dole kafin 8 tayi min a restaurant don daura irin abincin da wasu zasu suyi breakfast da shi. ******* Shi da Musbahu ne zaune a cikin jirgi zasu Abuja, flight din safe su ka yi booking don baya son ya kwana a can. Sabon filin daya siya wanda zai gina babban estate zai je suyi magana da Wanda yake bawa contract din ginin. Babban estate yake son yi sosai don wannan hadda katuwar Plaza zai bude a ciki, duk da sauran biyun ma ko wanne da Plaza a ciki amma wannan babba yake son yi. Kallon sa Mushahu yai yaga yadda yayi shiru yana danna waya. Murmushi Musbahu yai cikin tsokana don yasan abinda zai fada dole sai ran Abdallah din ya baci yace “baka manta ba dai koh, next week birthday party din Meena, kuma kasan yadda suke ta tsare tsare dole kai ma fa ka gayyaci friends dinka”. Tabe baki yai bai ce komai ya Riga yasan tsokanar sa Musbahun yake tun da ai a gabansa ta kira tace masa next week ne party din nata yazo fa don in bashi ba party, a take a tym din yace mata baxai zo ba data nemi masa magiya kawai ya kashe wayar ya kuma yi blocking number ta sai da Mami ta masa magana sannan yayi unblocking. Ganin bai ce komai ba Musbahu ya fashe da dariya yace “young billionaire dole fa sai kaje wannan party din haba kana mijin da zata aura”. Manyan sexy eyes dinsa ya dago ya zubawa Musbahu, tabe baki kawai yayi yace “ban da tym dinka Man”. Shima Musbahun ganin bai kule ba yasa kawai ya janyo wata hirar suka shiga yi akan school dinsu da ya rage musu saura semester daya in suka gama exam. **** Faty da Meena ne zaune a dakin Faty din suna yin list din wadan da zasu gayyata. Kallon Meena Faty tai tace “besty wai ya ake ciki neh, har ynxu Ya Abdallah bai ce zai je ba?” Tabe baki Meena tai tana juya manyan idonta tace “bai fada ba amma zan san yadda zan yi gaskia, na fa gama fada wa friends dina zan gaba tar da su a gurin sa in bai je ba ai class dina zubewa zai yi”. Shiru Faty tai tana kallon Meena ita dai a iya sanin ta ba’a yi macen da zata chanja wa Ya Abdallah tunani ba bayan Mami, ta sani farin sani Meena ba zata iya sa shi zuwa ba amma ba yadda za’a yi ta fada mata don tana fada mata sai sunyi fada. Da sauri kuma Faty tace “ga shawara besty mai zai hana mu samu Mami mu fada mata kinga sai ta lallaba mana shi ya daure yaje koh”. Ihun Murna Meena ta saki Tana rungume Faty din, sakin ta tayi tana dariya tace “gaskiya besty kin hadu, kin san wannan idea din bata zo min ba kwata kwata”. Murmushi kawai Faty tai suka ci gaba da list din, sai da suka gama sannan aka dawo maganar abincin da za’a ci. Cikin rashin damuwa Meena tace “wannan maganar yana hannun Dad, yace ya Riga na ya bawa wani restaurant order din zasu yi abinda ya kamata”. Haka suka tashi ko waccen su ta dauki mayafi suka fita. Gyran jiki ake wa Meena din, tun wancan week din aka fara mata sbd yadda take son ya kasance a wannan ranar ba Wanda yake haska wa irin ta…. ***** Tura dakin Yusrah Walida yayar ta tayi, a kwance ta same ta tayi rigingine tana kallon sama, fuskar ta jike d hawaye. Zama tai a gefenta tana dafa kafadar ta, da sauri Yusrah ta mike tana share hawayen ta amma wasu sababbi suna kara zubowa. Kallon ta kawai Walida take yi sai da taga ta dan nutsu sannan tace “Yusrah me yake damun ki, tun da Mummy ta kira ni tace nazo na tambaye ki abinda ne damun ki hankali na a tashe yake Yusrah wani abun ne yake faruwa?”. Girgiza Kai tayi tana share hawayen ta kawai sai ta fada jikin Walidan tana tana sakin kuka. Kuka take sosai zuciyar ta na mata zafi, ya zata yi da wannan soyayyar da take wa Ya Abdallah irin son sa da take yayi yawa sosai, hankalin ta ne ya kara tashi lokacin da taji Meena da Faty suna maganar cewa ai Ya Abdallah din zai je birthday party dinta, har tana cewa Yusrah gyaran jikin nan ma da take so take in zasu yan ka cake hankalin sa ya tashi sbd yadda zai ji kamshi da taushin jikin ta. Rintse idon ta tayi da karfi tana Kara sakin kuka, tana matukar kaunar Ya Abdallah haka kuma take kishin sa, abinda yasa ma kishin nasa take iya controlling dinsa sbd shi wanda take yi domin sa bai sani ba, Karin abin kuma an riga an zaba masa matar aure. Sai da tayi kuka ta koshi sannan ta d’ago ta kallo Walida, sunkuyar da kai tayi tace “Ya Walida abinda ke damuna ko na fada a banxa ne tun da baza a iya yi min Maganin sa ba”. Zuba mata ido Walidan tayi tana sauke ajiyar zuciya tace “fada min dai Yusrah in kika fada wa wani zaki samu saukin abun in sha Allah”. Kara sunkuyar da kai tayi sosai tace “Ya Abdallah…. naa… kee….. s…….o”. Zaro ido Walida tai gaba tana Juyawa da sauri ta kalli kofa ko Mummy ta biyo ta, ganin ba kowa yasa ta janyo Yusrah jikin ta tace “kin san mai kike fada kuwa?” Kuka Yusrah ta kara saki tana daga kan ta cikin kuka tace “Wallahi Ya Walida Ina matukar kaunar sa, gashi shi ko sani bai yi bama kuma an masa mata nasan baxan taba auren sa ba, kuma in ban aure saba baxan iya aure ba Allah shi kadai nake so da son sa na girma Ya Walida”. Shafa bayan ta Walida take yi gaban ta yana faduwa, wannan abun da kyar ya faru amma sbd ta kwantar wa da Yusrah hankali sai tace “ki ta addua Yusrah in Allah yayi mijin kine shi sai kin aure sa”. Da sauri ta d’ago daga jikin Ya Walidan tace “da gaske in Allah yayi shine miji na sai na aure sa?” Daga mata kai Ya Walida tayi cikin tabbatar wa. Dariya ta saki a lokaci daya hawaye na zubo mata tace “ko da fah Mami da Mummy da shi kan sa basa so fah”. Nan ma daga mata kai tayi. Sai kawai ta fada jikin Ya Walidan tana sakin ajiyar zuciya cikin kwarin gwiwar sake dagewa da addu’a. ******* A nutse nake zuba abubuwan da muka yi a manyan flask. Abubuwa kala 8 muka yi cutlet, croquette potato, cinnamon rolls, kenorkey fried chicken, vegetable white rice, shredded beef sai cowtail soup sai banana smoothie. Ogan sune ya shigo tun da ya shigo yake ta Murmushi, shiyasa ya ke rike Aasmaa da kyau tun da ta fara musu girki restaurant dinsu yake cika don ta iya abubuwa da yawa daga na kwadayin har na gargajiya. Kallon ta yai yana murmushi yace…… Comments nd share please Mrs A.M 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 8 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Kallon ta yai fuskar sa dauke da murmushi yace “ranar Monday za kuyi aikin wani birthday da aka bayar, kuma Ina son kije da kan ki gurin taron kisa ido akan yadda za’a yi rabon komai bana son a samu matsala ko kadan”. Hade rai nayi kamar zan musa sai dai kuma tunanin yadda yake daga min kafa a duk lokacin da na ce baxan je rabon abincin ba yasa kawai na daga nasa Kai. Kara washe baki yai yace “toh ai shikenan, kinga ranar dama zaki dawo daga hutun ki koh”. Kara daga masa kai nayi don bana son wata magana kuma. Shima ganin yadda nake Shan kunu yasa ya fita yana ya mutsa fuska yarinya ba wani shegen kyau ba amma sai girman kan masifa. Ina gama abinda nake gida na koma nayi wanka nida Basma muka tafi gidan Maryam. Mun dade sosai don sai bayan Isha’i muka dawo, naji dadin zuwan kuwa mun dade bamu hadu nida ita ba, mijin tane ya dawo damu a motar sa wanda da kyar na yadda ba shiga motar. Ranar Thursday na samu Hutu, dama duk friday, Saturday nd Sunday din karshen wata nake hutu a restaurant din mu, a ranakun nake samu na shiga kasuwa tunda an yi mana salary na siyo abubuwan da nake bukata na kuma hadu Kayan jiki. A ranakun ukun nan nake warewa nake gyaran jiki na, ko zan fita to sai na sa liqab. Ynxun ma haka ce yau Friday dawowar mu daga kasuwa kenan nida Basma mun siyo kayan gyaran jikin. Muna zaune a tsakar gida ina hada gyran Basma nayi min magiyar don Allah nayi mata itama. Shiru nayi mata kawai sai da na gama hada komai sannan na kalle ta nace je ki rufe gidan kizo nayi miki. Tsalle tai cike da murna tace Yauwa Auntyna. Rufo gidan tayi tazo ta zauna, cire kayan ta tayi ta janyo under skirt kirjin ta na shiga murza mata hadin. Sai da na gama mata sannan na shiga daki na rufo kofar bayan na dauko garwashin da zan sa dukkan a ciki na shiga shafa wa nima. Sai da nayi 20 minutes akan dukkan din sannan na tashi Ina murje jikina a kan ledar dana shinfida. Kwana uku na dauka ina yin wannan gyaran na kara wani kyau sosai, fatata ta kara sulbi da taushi kamshi mai sanyi da dadi kawai jikina yake. Basma data zuba min ido bayan na shigo daki sanye da Kayan bacci tace “Gaskia Aunty Aasmaa kinyi kyau sosai kamar wata Amarya wallahi” Murmushi nai nace “kema ai kinyi kyau din kamar amarya Basma” Turo baki tai tace “aa Aunty Aasmaa kin fini yin kyau gaskia sai kamshi kike ba ruwanki da sa turare”. Dariya nai Ina zama nace “kema ai kina kamshin Basma”. Dan kwalin ta ta janyo ta rufe fuska tace “Aunty in aure na yazo ke zaki yimin gyaran jiki”. Duka Umma ta kai mata tana cewa “ja’ira wato maganar auren ki kike koh” Dariya nai nace “Toh Umma ai da gaskiyar ta, tunda Auntyn ta ta iya gyaran jiki ba amfanin zuwa gurin masu gyaran da kai na zan dirje diyata koh”. Da sauri Basman ta mike ta shige daki tana dariya. Ni da Umma din ma dariyar muka shiga yi mata muna hira. ******* Zuba masa ido Mami tai tace “kana ji koh Abdallah, hakuri zaka yi ka je tun da take hada birthday party din ta baka taba zuwa ba, wannan kuwa kaga duk fa sbd Kai take wannan shirye shiryen”. Ganin yayi shiru yasa ta kalli Musbahu da yake shan zobo tace “ka sa baki kaji Musbahu kayi ta lallaba sa har ya yadda”. Cire cup din daga bakin sa Musbahu yai ya kalli Mami yace “Mami ni Kai na Ina ta fada masa Wallahi amma banxa ma yake min shiyasa kawai na kyale sa”. Dauke idonta daga kam Musbahu tai ta mayar kan Abdallah wanda ya lumshe idonsa yana sauraren su. Shi duk sun kasa fahimtar sa neh, mai zai je yi wai wani party sbd kawai ita yar kauye ce shine zata wani hada party ita bata san irin wannan abubuwan sam basa burge saba a haka kuma ake cewa ita zata aura bayan har ynxu ta kasa nutsuwa ta fahimci waye shi. Kallon sa kawai Mami take yadda take son Abdallah baza taso ta tilasta mata ba, amma kuma Hajia Bilkisu tun dazu take damun ta da waya akan zuwan Abdallah din, a cewar ta Meena sai kuka take tace ita in har Abdallah baxai je party din ba to ta fasa. Ita kuwa ko dan mutuncin Hajia Bilksi ai dole ta sa Abdallah ma yaje. Ajiyar zuciya ta sauke tace “ynxu Abdallah baxa ka iya yimin wannan alfarmar ba, ba fa wai sbd wani zaka je ba ni zaka duba da kuma Auntyn ku”. Bude idonsa yai da suke lumshe yana mikewa tsaye yace “Allah ya kaimu”. Washe baki Mami tai tace “Allah yayi ma albarka son Ya tsare ka a duk inda kake ya jikin mahaifin ki”. A hankali ya amsa da “Ameen” yana wucewa bangaren sa, ciwon mara yake damun sa sosai don haka yana shiga part din nasa dan karamin kitchen dinsa ya dora ruwan zafi a kettle. Yana cikin matsa lemon tsami a cikin cup din daya hada tea Mushabu ya shigo, yana ganin shigo war sa ya hade rai sosai don baya cikin mood din da za’a masa iya shege. Shima Musbahun duk da yadda yake son tsokanr sa amma kuma sai yayi shiru don yadda yga fuskar Abdallah tsab zai iya Kai masa duka. ******* Iya gajiya na gaji sosai da aikin sa muke yi, tun 6 na fito sbd yadda Oga ya dinga kira na akan nayi sauri abubuwan suna da yawa. Ai kuwa muna aikin Ina tsaki don abubuwa wajen 12 ne ake yi ko wanne kuma na mutum 50, sai 2 muka gama gaba daya na hada gumi. Sallah na idar na dawo kitchen din Ina kara gyara abubuwan yadda zasu yi kyau sosai Oga Kona ya shigo. Kallona yai yace “kin shirya dai koh, by 3 nake son ku tafi can tunda zaku fara serving mutane snacks da smoothie kafin a fara party din sosai”. Fuska ba yabo ba fallasa nace “Oga Ina son zuwa gida ne nayi wanka duk na hada gumi”. Zuba min ido yai yana lasar Baki yace “me zai hana kiyi anan, in ma Baki da Kayan ne ai sai nasa a siyo miki koh”. Juyar da Kai gefe nayi nace “shikenan ma kawai”. Da sauri yace “no ba Ina nufin wani abu ba fah, kije amma kiyi sauri kinga 4 za’a fara”. Godiya nayi masa na fita Ina dan sauri. Ina zuwa gida toilet na shiga nayi wanka sharp sharp, doguwar rigar material dina nasa sai dogon hijab light brown, har zan fito naga yadda fuska ta take maiko sai na tsaya na dan shafa powder da kwalli nasa lips balm Ina fito wa Umma dake kallona tace “Inyee Allah yasa dai a samo min siriki acan”. Zaro ido nai nace “Umma gurin party ne fah duk kananun yara neh a gun”. Tabe baki Umma tai tana cewa “Allah ya kiyaye”. Dariya nai Ina ma Basma bye na wuce nasan Umma haushi taji don nace duk yara ne a gun to ai ba karya nayi ba duk yaran ne, babban mutum zai je wani birthday party neh. Ina zuwa na tarar har sun shiga motar ni suke jira, a baya na zauna nima muka wuce……. Comments nd share please Mrs A.M 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Dedicated to Aysha 2rawax❤️❤️ Page 9 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Madaidai cin hall ne wanda aka kawata shi da decoration sosai, daga farkon shigo wa a bangaren dama gurin mu yake. Jera abubuwan mu mukai tunda ba wai zamu yi serving dinsu bane sit by sit, kowa zuwa zai yi ya dibi abinda yake so, mu aikin mu kawai kula da yadda zasu diba da kuma Kai musu ruwa da drinks. Zama nai akan kujeran Ina kallon yadda mutane suke shigowa mata da maza kowa yaci kwalliya, daga yanayin shigar su zaka gane wannan partyn na masu abun ne. Muna zaune aka fara party din, ni dai kallo daya nayi wa birthday girl din na dauke Kai na Ina tabe baki, ta sanya wata farar gown wacce ta mugun matse ta ko Ina nata ya fito gashi daga wuya net ne ana hango saman na shanun ta. Babban cake din dana yi na bawa Salma abokiyar aiki na kuma tare muke girki, duk abokan aiki nama mun fi shiri da ita don ita Ina dan zama muyi hira da ita sbd zamu yi sa’anni, tana da aure har da yara biyu. Salma ce ta tura abin da aka d’ora cake din ta kai sa tsakiyar gurin da aka tana da don rawa.. Dawo wa tai ta zauna tace “Tabdijan Aasmaa abu kamar ba musulmai ba”. Murmushi nai Ina dan muskutawa nace “musulmai ne mana Salma kawai sbd sun fi fifita nasara akan addinin su ne amma abin sam ba tsari”. Tsaki tai tace “Ina fa tsari anan sam yaron ynxu kunya tayi musu karanci Wallahi”. Shiru mukai kowa yana danna wayar sa. Muna zaune mudai muna kallon yadda mutane kowa yake zuwa yana diban abinda yake so. Ni dai nawa lura da yadda al’amuran suke gudana amma fuska ta a hade take. Dafa sa Musbahu yai yace “ka tashi muje mu dibi abinci don Allah ni yunwa nake ji fah”. Kara hade rai yayi, shi Musbahu ya kasa fahimtar sa, ran sa a bace yake sosai na ganin yadda Meena take ti kar rawa a cikin maza, ko wani namiji zai zo ya rikota ita kuma ta wani langwabe kai tana dariya suna hoto. Ba wai kishin ta yake sbd yana son ta ba shi ko kadan baya son ta kawai dole yayi kishi mana tunda ita zai aura, ko bama zancen aure a tsakanin su ai kanwar sa ce. Ganin yaki magana kawai sai ya tashi shi yaje ya zubo abinda yake so, ya kuma zubo tandori chicken da KFC a wani plate din, yafi kowa sanin yadda Abdallah yake kaunar kaza, abinci bai dame sa ba amma da in har kaza ce baya wuce tayi. Ai kuwa yana zama idon Abdallah ya sauka akan plate din kazar, hadiyar yawu yayi yana lumshe idonsa yadda yake jin kamshin kazar nan ya tabbatar ba karamin dadi zata yi ba. Zuba wa Musbahu ido yai yaga wai ko zai ce masa yaci amma yaji shiru bai ce komai ba sai ma cin abin sa da yake yi yana lumshe ido tare da gyada kai. Tsaki yayi ya mike kawai ya nufi gurin da yaga masu abincin suna zaune. Ina zaune ni kadai su Salma duk sun tafi kai Chapman, naji mutum a tsaye a kai na. D’ago ido nai idona ga fada cikin nasa, a tare zuciyoyin mu sukai wani irin bugawa da karfi. Shi ya fara janye idonsa yana wani hade rai, Nima sai na janye nawa idon Ina tabe baki. Shiru yai yana jiran yaga ta dauki plate ta zuba masa yaji shiru sai danne danne take a wayar ta, tsaki yaja da dan karfi wai ko zata d’ago amma yadda take ko motsi batai ba balle yaga alamar taji tsakin da yai. Kara buga tsakin yai da karfi amma yadda tayi shiru haka tai don haka a dan zafafe yace “baza ki zuba min abincin ba?” Sai a lokacin na d’ago manyan idona na sauke a cikin nasa idon da suke a lumshe, tabe baki nai kawai na rausaya kai na Ina maida shi kan wayata. Zaro ido yai yana kallon ta, yau shi Abdallah yake wa wata magana take masa banxa kamar ba magana yake da mutum ba. Tsaki ya buga da karfi yace “ke wata iriyar mara kunya ce ana miki magana kin yi banxa”. D’ago wa nai da sauri na kalle sa, ni wannan yaron yake cewa Mara kunya, yaron da nake masa kallon zai yi sa’a da Maryam in ya girmi Maryam da kadan ne ni yake cewa Mara kunya. Irin kallon da nake masa shima irin sa yake min. Girgiza kai nayi Ina hade rai sosai nace “waye sa’an ka anan gurin da zaka zo kana min rashin kunya, nayi kama da sa’ar wasan ka? Ku yaran nan daga kunga kun fara balaga sai rai na na gaba da ku koh” Kara bude idonsa Abdallah yai yana kallon ta Musbahu da ya taho yana hango su daga gefe hannu ya dora a kai yana zare ido, Addu’a kawai yake Allah ya sa kar Abdallah yayi wani abu da zai hargitsa gurin party din. Tsaki nai Ina cigaba da danna wayata, wannan yaron lallai bashi da kunya kk hmm. Abdallah ji yayi hankalin sa y tashi, yau shi ne ake kira da yaro tashin hankali. Kara zuba mata ido yai yana son karanto shekarun ta amma cute innocent baby face dinta kawai yake gani ta hade rai. Ya bude baki zai yi magana Musbahu yai saurin kara sowa yana kallona Aasmaa yace Aunty don Allah kiyi hakuri. Dan kallon sa nai kawai ba gyada kai na Ina mayar da idona kan waya ta. Jan hannun Abdallah Musbahu yai suka fita daga hall din gaba daya. Kallon Musbahu yake yana Jin kamar ya rufe sa da duka, zai yi magana Musbahu yai saurin cewa don Allah kayi hakuri Abdallah ba girman ka bane ka tsaya kana sa’in sa a cikin gurin can, kuma fa Kai ne mara gaskia kowa yazo da kan sa yake zuba abincin taya zaka je ka tsaya kana zabga mata tsaki. Shi dai kallon Musbahun yake kenan shi laifin sama yake gani koh…… Comments nd share plz Mrs A.M 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 10 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Yana tsaye yana tunanin irin yadda yarinyar ta raina masa hankali har bai san lokacin da Musbahu ya tafi ba. Mota y shiga ya zauna yana huci ya ma rasa ta Ina zai huce wannan takaicin, yana zaune yaga ta fito tana tafiya a hankali kan ta a kasa. Zuba mata ido yai yana kallon ta kafin wani idea ta zo masa yayi wani mugun Murmushi ya fice da motar da sauri. Ni kuwa jin da nayi gaba daya mood dina ya chanja yasa na cewa Salma kai na ciwo yake min zan je gida na huta tun da an kusa tashi a party din. A hankali nake tafiya kai na a kasa na dan yi nisa da hall din Ina so na tafi babban titi yadda zan samu adaidaita da sauri kawai naji an watso min wani abu mai sanyi a fuskata ya gangaro har light brown din Hijab dina. Da sauri na d’ago don ganin wane mara mutuncin ne ya aikata min haka, ido na ne ya fada cikin idon wannan tsageran yaron da yake ce min bani da kunya. Irin kallon da yake min na dage girar sama yana min kallon kyama ya tsaya min a rai, Kara kallon jikina nayi yadda nonon ya zubo min da alama nonon saniya ne da aka dama da fura. Kallon jikina kawai nake kamar zanyi kuka don takaici, in na bude baki da niyyar magana ba abinda zai hana hawaye zubo min don haka kawai na gyada kai na yi gaba da sauri Ina goge fuska ta da hijab din nawa. Bin bayan ta da kallo yai ran sa fess don yasan ya gama bata mata rai. Wani murmushi ya saki ya juya kan motar ya nufi gida hankalin sa kwance. Da kyar na samu adaidaita na shiga, ban da ajiyar zuciya ba abinda nake sauke wa. A bakin layin mu na sauka na basa kudin sa, ko tsayawa kar bar chanji ban yi ba na shige ciki Tun daga kofar gidan nake jin muryar Kawu Laminu yana fada, rintse idona nayi gaba na yana faduwa. Da sallama na shiga ciki, da sauri Kawu y juyo yana bina da mugun kallo yace “an dawo daga yawon barikin kenan ko”. Lumshe ido nayi ina sunkuyar da kai na kasa, tsugunna wa nai nace “Ina wuni kawu”. Tsaki yai yana kankance ido yace “rike gaisuwar ki bana bukata, ni Yaya ya cuci Inna Wallahi daya sa maki sunan ta kowa yasan innar mu mace ce mai kamun kai amma ke kuwa lokacin da ake raba kamun kai kina daki kina baccin asara”. Kara sunkuyar da kai na nayi hawaye yana zubo min, bakin cikin abinda yaron can ya mun da wanda kawu yake min ynxu yasa naji baxan iya daure wa ba. A hankali nake kuka na Ina goge wa da hijab yadda Umma baxa ta fahimta ba sai dai na makaro tini ta fahimci kuka nake. Shiru tai kawai bata musa wa Kawun ba don bata son tashin hankali, tana magana zai harzuka tun da haushin ta yake ji dama tun bayan rasuwar Baban su Aasmaa din daya so ya aure ta tace ita sam ba maganar aure ynxu a gun ta zama za tayi ta kula da yaran ta. Kallon sa Umma tai tana hade rai tace “laminu Ina fada maka tun ba yau ba ka daina jefar min y’a da wannan muguwar kalmar ni nasan wace diya ta kuma na yadda da ita”. Tsaki yai yana duban Umman ran sa na kara baci, nuna ta yai yace “tun da yau ba dama nasan cewa ke kike goyawa yarinyar nan baya take duk abinda yake so, ta Ina ma baxa ki goya mata baya ba tun da duk abinda ya samo ke take kawo wa kuke ci tare, ni dai na fada muku wallahi wata 6 na baku ta fito da Miji in ba haka ba zan bawa Alhaji Inuwa auren ta tunda ai shi kadai ne yace ya ji ya gani duk da muguwar dabi’ar ta”. Juya wa yai cikin fushi ya fita daga gidan ran sa na kara baci, har shi Zainabu(Umma) zata wulakanta ai ya riga ya rantse tun da ta murza wa idon ta kwalli tace baxa ta aure sa ba shi kuma baxai gaji d kuntata masu ba, ya san cikin wata 6 ba Wanda zai zo gurin Aasmaa din tun da dama ba wani farin jini gare ta ba, shi kuma zai yi amfani sa matsayin sa na kanin uban ta ya aura mata Alhaji Inuwa. Dafa ni da Mama tai yasa na mike Ina share hawaye na. A nutse Umma tace ki fawwalawa Allah komai Aasmaa, nasan kin karbi kaddarar ki da hannu biyu ki cigaba da addu’a in sha Allah wata ran sai labari kinji. Daga mata kai nayi kawai na shige daki, Basma na makure a jikin kofa da alama ta ji komai. Sassanyan murmushi na sakar mata Ina shige wa cikin dakin, kaya na cire na shiga wanka. Haka muka wuni dukan mu suku suku yau din, a haka har akai sati muka koma yadda muke Basma kuma ta koma gida sbd hutun su ya kare. ****** Ina jingine a jikin kitchen cabinet Ina candy crush a waya ta Oga Kona ya shigo. Kallona yake yana tande baki kamar tsohon maye, shi dai kullum yana mamakin wannan yarinyar tun da ta fara aiki tare da su shekara 3 kenan bai taba ganin ta ba Hijab ba, yana fatan wata ran ya ganta ba hijab shiyasa yake yawan fado wa kitchens din a mafi yawon lokaci a nasa tunanin ko tana aiki zata cire hijab din amma kullum cikin sa take bata cire wa. Sauke wayar nai daga fuskata na kalle sa nace “Oga wani abu kake soh?” Murmushi yai yace “yess shawarma zaki hada guda biyu ynxu da banana smoothie ki kai table din vip zaki ga mutane biyu kiyi sauri plz sabin customers neh”. Daga masa kai kawai nayi na shiga aikin hada musu abubuwan, cikin 20mins na gama komai na d’ora akan tray madaidai ci ba riko na tafi gurin VIP din. A saman restaurant din yake guri ne da yake a rufe ba wanda zai gan ka kuma ba hayaniya ko kadan. A nutse nake tafiya a hankali Ina Jin yadda zuciya ta take wani irin bugu da karfi. Table din da mutum biyu suke kai na nufa, ba tare da na yadda na kalle su ba na ajiye tray din. Bude idon sa da yake lumshe yai cike da gajiya sbd jin kamar kamshin ta yake ji fah, a nutse ya sauke lumsassun sexy eyes dinsa akan ta kuma akai sa’a ita ma ta d’ago cikin tsautsayi idon su suka sarke dana juna. Ido na zaro da mamakin ganin wannan mara kunyar yaron, sai dai kuma nayi kokarin dai dai ta kai na Ina danne bacin rai na na juya a nutse na sauka zuciya ta na bugawa. Mai da idonsa yai ya lumshe cike da wani irin yanayi da baxai ce gashi ba. Kallon sa Mushabu yai yana murmushi yace uhmm abokina kaga kawar ka koh? Bude idon yai ya zubawa Musbahu yana yamutsa fuska kamar yaga kashi, gajeran tsaki yai kawai ya janyo shawarma ya fara ci a hankali. Lumshe idon sa yai yana sakin wani siririn murmushin daya tsaya iya lips dinsa, in yace tun da yake a rayuwar sa bai taba cin shawarma mai dadin wannan ba bai yi karya ba. Shi da yake fushin Mushabu ya janyo sa restaurant sai gashi ya cinye nasa ya kuma dau na Musbahu da bai ci ba yana danna waya ya cinye. Banana smoothie din ya dauka ya kora yana lumshe idonsa cikin nutsuwa, amma sai yaji shawarmar bata ishe sa ba sam kuma. D’ago war da Musbahu zai yi yaga tray din wayam sai paper din da akai wrapping shawarma kawai. Zaro ido yai yana kallon Abdallah da mamaki yace “Ina kayan suka tafi?” Tabe baki yai kawai yana goge bakin sa da tissue. Ashar Mushabun ya danna masa cike da takaici, yunwa suke ji gaba dayan su tun safe ko breakfast basu yi ba Abdallah din yaja shi suka shiga zagye supermarket dinsa don lura da komai yana tafiya dai dai, sai da kyar Mushabun ya roke sa suka zo nan din su dan ci wani abu kafin su karasa gida su ci abinci kuma sai yaga wayam. Ya bude baki zai yi magana Abdallah yai saurin tarar numfashin sa da cewa plz gaya musu su karo wani. Tsaki kawai Musbabun yai kafin yaje ya fada aka wo guda uku, suna zaune aka kawo da sauri Abdallah din ya dauki daya ya fara ci sai dai gutsira daya yai ya cire yana yamutsa fuksa. Kallon Oga Kona yai daya zo don yana farin cikin yadda sabbin customers din suka ce a karo musu shawarma din sai Murmushi yake yai. A dakile yace “wannan ba irin wancan bane”. Dan sosa kai Oga Kona yai yace “uhmm eh ai da yake ita wacce ta kawo muku na dazun ita ce tayi kuma ynxu lokacin tashin ta yayi ta tafi gida sai gobe”. Kara hade rai yai sosai yana kicin kicin da fuska yace “ka kira ta Kace ta dawo ynxu Ina bukatar shawarma din”. Zaro ido Oga Kona yai yace “ita Aasmaa din zan cewa ta dawo ynxu”. Tsaki Abdallah din yai yana zira hannu a aljihun sa ya fito da bandir din 500 sabbabi ya ajiye akan table din. Da sauri Musbabu yace “kana da hankali kuwa Abdallah, akan shawarmar 1500 zaka bada 50k”. Juyar da kan sa yai gefe yana tsotsar harshen sa, abinci sam bai dame sa ba yafi cin abubuwan kwadayi kuma kowa ya san sa yasan soyayyar sa da shawarma da Kaza baya iya fushi da su a rayuwar sa. Da rawar jiki Oga Kona ya danna wa Aasmaa kira, sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka. Kasa da murya yai yace “kina Ina Aasmaa kin tashi bayan baki fada min ba, kiyi maza maza ki dawo customers na bukatar shawarmar ki alkhairi ne yake kiran ki”. Yamutsa fuska nai nace “Oga gaskia nayi nisa bana jin zan iya dawo wa ai Salma na nan kasa tayi musu mana itama ai ta iya”. Kara marairaice murya yai yace “ai Salma din ta musu amma suka ce batai musu ba, kinga Aasmaa ki dawo plz in kika musu 15k zan Baki wallahi kuma ba’a salary din ki be”. Tabe baki nai ai in har ni zan yi wa wannan mara kunyar yaron shawarma ya dade shi Oga Kona din bai bani 15k ba, wata tsanar yaron ce kawai ta shige ni tun wulakancin daya min wancan satin kuma na kasa manta wa kullum na tuno abin sai idona ya ciko da kwallar takaici. Jin batai magana ba yasa cikin sarewa Oga Kona ya kalli Abdallah daya tsare sa da ido yace “sir taki yadda kuyi hakuri ko zuwa gobe kawai”. Hannu ya mika masa alamar ya basa wayar. Ba musu ya basa ya sa wayar a speaker Cikin husky voice dinsa yace keeee baki da kunya koooohhh…….. Jama’a ku jawa wannan yaron kunne da naga alama ya rai na mu da yawa🤨 Comments nd share please Mrs A.M🥰 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 11 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Zaro ido nai da mamaki nace “wane yaron ne kuma haka da bai iya magana da manya ba…” Bude manyan idonsa yai yana wani munafikin murmushi yace “uhmm yaro manya keee waye tsa’anki wai…” Tsaki na naja da karfi nace “naga alama kan ka na hayakin balaga bani da tym din ka karami” na kashe wayar Ina kara jan tsaki. Shiru yai fuskar sa na soma ja sbd bacin rai, shi wannan yarinyar zata dinga cewa tashar balaga, bama wannan ne yafi damun sa ba illa kalmar yaro da take dangan tasa da ita. D’ago idonsa da suka rine zuwa ja sbd bacin rai yai ya zubawa Musbabu su wanda yayi tagumi yana kallon ikon Allah. Ganin kallon sa ma kawai Mushabu yake bashi da niyyar rarrashin sa akan wannan cin mutuncin da aka gama masa yasa shi kawai mike wa a fusa ce ya sauka. Da sauri Oga kona ya bi sa da gudu yana cewa kudin sa gashi ya bar su fah. Musbahu ne yace masa ya rike kawai, tun da Abdallah ya fitar dasu daga aljihun sa baxai karba ba, Allah yayi rabon sane. Godia Kona ya dinga yi yana juya kudin a hannun sa, lallai dole gobe da wurwuri yasa Aasmaa yi musu shawarma biyar kyauta ya bawa mai delivery ya kai musu tun da ya karfi number din Musbahu. Ni kuwa Ina adaidaita sai zabga tsaki nake, tsabar rai nin wayo wai ni wannan karamin yaron zai dinga cewa kee yana kira na mara kunya, girgiza kai nai cike da takaici ni dai ban san me nayi wa wannan yaron ba gaba daya ya rai na ni. ******* Dafe kan sa yai da ke barazaranar fashe wa sbd tashin hankalin da yake ciki, shi kadai yasan yadda zuciyar sa take mugun bagawa a duk lokacin da ya tuno kalaman Aasmaa a gare sa. Dafa sa Ibrahim aminin sa yai yace “ka kwantar da hankalin ka don Allah Kabir, nutsuwa zaka yi mu samo mafita akan wannan lamarin”. Ajiyar zuciya mai karfi ya sauke yana zubawa Ibrahim idanun sa da suka chanja launi. A nutse Ibrahim yace “ni dai abinda zan ce shine anjima ka dauke ni muje ni da kai gurin ta in duhu yayi sbd munafukai, in har muka je bamu shawo kan ta ba zan baka shawarar da nake gani ita kadai ta rage mana”. Ba dan ya aminta da cewa da akwai shawarar da zata bulle masa ya amince da zuwan nasu gurin Aasmaa ko ba komai yayi missing din ganin wannan kamillaliyar fuskar tata. ****** Muna zaune a daki ni da Umma da Umar muna hira waya ta ta shiga ringing, kallo daya nayi mata na dauke idona akan ta ganin sunan Kabir. Tun Ina blocking din number dinsa har na gaji na dai na, sbd in nayi blocking da safe zuwa rana yayi yawa ya sake kira na da wata number din, dole na hakura da blocking din number din sa kawai nake kin daga wayar. Kallona Umma tai tace ba kiran ki ake ba Aasmaa. Ba tare da na kalli Umma ba nace kiran bashi da amfani ne Umma. Daga kai tayi kawai tana mayar da hankalin ta gurin Umar da yake fada mata yadda cinikin da yai a satin nan da ya gaba ta. Sallamar wani almajiri ne yaja hankalin mu, Umar ne ya mike ya fita tsakar gidan don jin abinda ya kawo Almajirin. Bai dade ba ya dawo fuskar sa washe da murmushi yace “Ya Aasmaa gurin ki aka zo kina da baki a waje.” Kau da kai na gefe nai ina tabe baki don tun da naga yadda Kabir yake kira na dama jikina ya bani zuwa zai yi ko kuma yazo din. Umma data zuba min ido tace “baki ji abinda aka ce bane bako kike da shi ki tashi ki fita”. Na bude baki zan yi magana ta hade rai dole na mike kamar zanyi kuka na shiga daki. Hijab dina na zura ban sa turare ba amma kamshi yake mai dadi sbd yadda nake turara su da kabbasa. A bangon gidan mu na same su a tsaye suna hira, suna ganin zuwa na suka juyo suna kallona fuskar su dauke da murmushi. Fuska a hade na musu sallama daga nan naja bakina nayi shiru sai Ibrahim ne yake ta zuba kan yadda Kabir din ya susuce a Kai na. Ganin naki cewa komai Ibrahim ya marairaice murya yace “kiyi magana kinji don Allah gimbiyar mata”. Kallon sa nai Ina tabe baki nace “uhm…” Daga haka na juya na shige cikin gida abu na… Dukan su bina da kallo sukai kafin kabir ya kalli Ibrahim kamar zai yi kuka yace “kaga abin da nake fada ma koh..” Dafa sa Ibrahim din yai yana sauke ajiyar zuciya yace “shawara daya ce ynxu kuma ita kadai ce mafita kawai ka samu Hajjo ka fada mata, in Allah ya taimake ka ta fahimce ka kaga shikenan sai ta sa baki nasan in tasa baki da kyar Aasmaa din ta ki amince wa tun da ita na girma take kuma tana bukatar namiji a kusa da ita”. Girgiza kai Kabir yai yace “anya kuwa zan yi haka Ibrahim duk da fa cewa nasan Hajjo bata da hayaniya amma wallahi ina tsoron tunkarar ta da wannan maganar, dama da ace ita Aasmaa din ta amince da abun yazo min da sauki”. Murmushi Ibrahim yai yace “abokina wannan ita kadai ce mafita daga ita kuma gaskiya bani da wata dabarar”. Haka suka wuce kowa yai shiru har ya sauke Ibarhim a gidan sa ya wuce gidan sa zuciyar sa na bugawa. ***** A hankali rayuwar take tafiya wata ran farin ciki wata ran aka sin haka. A gajiya nake matuka amma na tsaya hada wa wannan dan rainin hankalin Shawarma, kullum sai yazo yaci safe da yamma, in bai zo ba ma za’a bawa mai delivery ya kai masa. Ynxu haka ma guda 12 yace yana so, duk da gajiyar da nayi amma haka Oga Kona ya lallaba ni nake nasa Ina yi Ina tsaki, baya cin ta kowa sai tawa da farko zame wa nai a tunani na ai baxai gane ba amma ana Kai masa yace a dawo dashi. Dole ni na yi masa, tun Ina korafi don har Umma na bawa labarin wulakancin da yake min tace nayi hakuri har na ma dai na mata korafin. Sai dai ban taba kai masa da kai na ba, tun lokacin da yazo na farko bamu sake haduwa ba, duk hanyar da na san zata sa mu hadu na toshe ta, Ina jin Oga ya leko yace na hada masa shawarma bana fita har sai Salma tace min ya fita. Na gama sa masa a leda amma ban san wanda zan bawa ya Kai ba tun da ba kowa a kitchen duk suna cikin restaurant din suna goge goge da kimtsa gurin. Zama na nayi Ina game, Oga ya leko. Da alama sauri yake sbd yadda yake ta duba tym yace “Abdallah yana waje a parking space ki Kai masa plz sauri nake yi kuma yana jira neh”. Kafin ma nayi magana ya juya da dan sauri ya fice. Na dade a tsaye Ina tunani kafin nayi tsaki na rataya jaka ta na dauki ledar na fito. Ina a tsaye Ina dube dube ido na ya sauka akan fuskar sa dake kwalli sbd hasken rana. Zuba mata ido yai yana kallon ta a ran sa kuwa gulmar ta yake yadda kullum take sa Hijab ita ko zafi bata ji. Tabe baki yai yana kallon ta fuska a hade yana sauraren karasowar ta. Nima hade fuska ta nai ina yamutsa fuska don yadda ya tsaya dinnan nasan jira yake kawai na kawo masa. Girgiza kai nayi Ina dan murmushi kadan, don wannan yaran bai san ko wace ni ba. Ganin yaki taho wa kuma lokaci na kawai yake ci yasa na buga tsaki na yi bakin gate, gate man na bawa nace ya Kai masa ni kuma na wuce. Ajiyar zuciya ya sauke mai karfi yana lumshe idon sa, bai san me yake damun sa ba, tun ranar da ya fara ganin ta duk lokacin daya lumshe idon sa ita yake gani tana watso masa harara da wadannan manyan idanun nata. Gaba daya ta hana sa sukuni ko motsi yayi sai ta fado masa a rai, kullum yana zuwa ne kuma don ko zai gan ta tayi masa wannan kallon rai nin amma baya samun ganin ta sai yau. Murmushi ne ya subuce masa yana shige wa motar sa yayi mata key ya tafi……. ******* Lokacin da na Isa gida Umma bata nan kuma dama ban yi tsammanin samun taba tun da tace zata je gidan kanwar ta. Girki na daura don shinkafa sa wake nake sha’awar ci, salad na yanka na wanke na ajiye a gefe. Kafin 6 na gama komai na juye a flask, a gurguje nayi wanka na zira doguwar riga mai hannun vest don garin yau ana zafi sosai. Ina zaune a kan kujera a tsakar gida Umar ya shigo, kallon sa nai fuska ta dauke da murmushi nace “Sannu da zuwa mutanen kasuwa”. Dariya yai yana zama a kan dakalin dake kofar dakin sa bayan ya dan kade kurar yace “Sannu Aunty Aasmaa mutanen restaurant”. A tare muka yi dariya, hira muke yi a nutse cike da shakuwa da akwai shakuwa mai karfi tsakanina da Umar ko dan sbd dade wa ta a gida ne kuma shi kawai nake gani bayan Umma a cikin gidan. Sallamar Umma ce ta samu mike wa da sauri fuskar mi dauke d murmushi sai dai kuma ganin tana tafiya a hankali kuma hannun ta an daure sa ga kanta da bandage yasa mu nufar ta da sauri. Dukan mu rikice wa mukai gurin tambayar ta abinda ke damun ta, ba bude baki zan sake magana ta makale a wuya na ganin sa ya shigo hannun sa rike da jakar Umma da kuma wata leda ta asibiti. Shima tokare wa yai ya zuba mata ido yana kallon ta cikin son gasgata ita ce dai ko ba ita bace a tsaye haka yana kallon ta ba Hijab. Tun daga sama yake kallon ta yadda rigar ta lafe a jikin ta duka surar ta ta bayyana a fili, wani yawu ha hadiye yana Jin yadda wuyan sa ya bushe lokaci daya. Da kyar ya maze yana hade rai ya Kawar da kan sa kamar bai ga komai ba, idonsa ne ya sauka akan Umar sai kuma ya mai da duban sa jikin Aasmaa wani irin mugun hade rai yayi yana jin yadda ran sa yake baci, Ynxu haka take zaune ita da wani gardi yana kallon ta a haka duk da yaga kamanni amma toh meye zata zauna gaban wannan sangamemen saurayin kusan tsirara…….. Comments nd share please Mrs A.M🥰 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 12 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Cikin seconds 30 hankalin na ya dawo jikina da sauri na matsa daga kusa da Umma na shige daki a guje don dauko hijab dina, zuciya ta tana bugawa da sauri da sauri. Rai na gaba daya a jagule ga tunanin halin dana ga Umma a ciki ga kuma tunanin wannan yaron da na gani yazo gidan mu tare da Umma. Da sauri na zira Hijab din nawa na fito a zaune na samu Umma akan tabarma ta mike kafafun ta, shi kuma yana daga tsaye a gefe yana kallon ta. Hada ido mukai na ban ka masa harara na wuce gurin Umma Ina zama. Hannun ta da ba’a daure ba na kama cikin rawar murya nace “Umma lafiya kuwa me ya samu hannun ki?” Murmushi tai tace “Alhamdulillah nazo tsallaka titi ne wata mota ta buge ni kuma wanda ke ciki ya gudu, shine da Allah ya kawo babana yaron kirki ya kai ni asibiti aka gyara hannun karaya ceh”. Zaro ido mukai nida Umar a tare muka ce “karaya kuma Umma?” Murmushi tai tace “naji sauki ai, an riga an d’ora hannun kuma an bani magunguna abin ma yazo da sauki ai”. Sannu na shiga jera mata sannan na shiga daki da sauri na debo mata ruwan randa the wanda yayi sanyi. Kawo mata nai ta karba tasha tana kallon Abdallah da yake danna wayar sa kamar bai san da mutane da gurin ba. Murmushi Umma tai tace “babana zo ka zauna mana a zubo maka abinci”. Da kyar ya bude baki yace “I’m ok zan tafi”. Da sauri tace “A’a zo ka zauna kaci abinci.” Kallona tai tace “tashi ki zubo masa abinci Aasmaa..” Dan dai kawai Umma ce shiyasa na mike ba tare da nace komai ba na shiga daki, abincin na zubo masa a plate na sa spoon sannan na debi ruwan randa a wani cup din silver nawa ne ma da shi nake shan ruwa sbd yana da murfi, ban san me yasa na zuba masa ruwan a ciki ba bayan bana barin kowa ya taba mun, tabe baki nai a rai na nace sbd shi naga bako ne ai. Sai da na gama jera komai a kan wani tray sannan na fito Ina hade rai, kallon Umar nai da yake ma Abdallah magana da alama hira yake jan sa da ita. Kara hade fuska nai cikin bada umarni nace “Umar je ka dauki tray a palo ka kawo masa”. A nutse ya mike yace “toh Ya Aasmaa”. Abdallah bai san lokacin daya d’ago Kansa ba ya kalle ta ya kuma kalli Umar, ko shakka baya yi ya girme sa amma yake cewa waccan yarinyar Yaya, tabe baki yai irin I don’t care dinnan ya mai da kan sa kan wayar sa. Abincin da Umar ya ajiye masa ya kalla yana dan sakin murmushi kadan Wanda ta tsaya masa iya saman lips, yana son shinkafa da wake sosai cikin abincin hausawa shine fav dinsa. Da farko bai yi niyyar cin abincin ba amma ganin shinkafar yasa shi yin bismillah yana ci a nutse, duk da ba Nama ko kaza ko kifi ko egg amma abincin ya masa dadi sosai. Sai da ya duba yaga ya cinye tass sannan kuma ya dan ji kunya, d’ago wa yayi ganin hankalin kowa ba’a kan sa yake ba gashi kuma shi abincin ba wai ya ishe sa ba ya kalli Aasmaa dake zaune a kusa da Umma yace “keh!” Gaba dayan mu juyo wa mukai muka zuba masa ido. Shima idon sa a cikin nawa yace “ban koshi ba, karo min..” Wani mugun hade fuska nai Ina banka masa harara kamar wacce idon zasu fado nace “kai waye sa’an ka anan gurin wai me yasa Kai baka da kunya neh eh”. Bude sexy eyes dinsa yai yana zaro su yace “ni kike cewa mara kunya, lallai ma yarinyar nan kin mugun rai na ni…” Da sauri na kalli Umar da ya sunkuyar da kan sa kasa tana kokarin hana kan sa dariya, cikin tsawa nace “Umar wanka wa wannan yaron mari plz, naga alama sai an sai ta masa hankali Sam bashi da kunya”. Umma ce da tunda muka fara magana take bin mu da kallo tana murmushi tace “meye haka Aasmaa da girman ki kike wannan abun, bakon mune fa shi”. Idona daya soma ci kowa da hawaye nace “Umma kina kallo fa amma yadda yake min magana kamar wani mijina ko ubana keh fa yake ce min”. Wani shegen murmushi ya saki yana shafa gemun sa yace “uhmm waya sani ko Mijin naki neh?” Ban san lokacin dana fashe da kukan da nake rikewa ba na mike da sauri nace “Allah ya kiyaye na auri sa’an kannen baya na Wallahi”. Daki na shige da sauri Ina rufe fuskata Ina kukan takaici, Ina jiya dariyar Umma da Umar suna magana kasa kasa. Ban san lokacin daya tafi ba tun da na shige daki ban sake fito wa ba har sai da Umman suka shigo ciki…. ********* Cikin fada fada Ya Waleeda tace “don Allah Yusrah ki sawa ran ki hakuri da dangana mana haba don Allah, kina jin doctor tace jinin ki ya hau sosai gashi zuciyar ki ta kusa tabuwa so kike ki mutu ne a banxa a kan soyayyar wanda bai ma san kina yi ba”. Shiru kawai Yusrah tai tana share hawayen ta, gaba daya duniyar ta mata zafi ne sosai ta yadda yake Jin ita gwanda ma mutuwar ta, tana ji tana gani aka kai kudin auren Abdallah da Meena kuma aka sa biki shekara daya lokacin Abdallah ya gama school dinsa. Ajiyar zuciya ta sauke mai karfi wacce har sai da ta bawa Yaya Waleeda tsoro. Dafa ta tayi cikin lallashi tace “don Allah kanwa ta ki sawa ranki salama kinji, ki dage da addu’a kawai kinga har Abba na samu na fada masa amma cemin yayi shi baxai taba iya rokar Abdallah ya aure ki ba baya son yaga kamar sbd duk abinda ya masa ne yasa shi cewa ya auri yar sa duk da shima yaron sa ne kuma yasan in ya fada masa ya aure ki din baxai musa ba”. Kuka sosai Yusrah ta kara fashe wa da shi, only hope dinta dama Abban nasu ne ynxu kuma shima ga abinda yace. Cikin rawar Murya tace “don Allah Yaya Waleeda ki taimaka min wallahi ina son sa sosai, in ya kubuce min mutuwa kawai nasan zanyi, zo ki taba kirjina Kiji yadda yake min zafi”. Kallon ta kawai Waleedan take ita ma hawaye ba zubo mata, wannan kaddara ce babba a gare su, kafin ta sami Abban nasu da maganar sai da ta fara zuwa gun Mummy ta mata bayanin duk abinda ke damun Yusrah din. Cikin rashin mafita Mummyn tace ita ynxu bata san yadda zata warware wa Yusrah damuwar ta ba tun da dai kowa yasan irin cin kashin data yiwa Mami farkon zuwan ta gidan kuma dai tana gani ynxu ai ko kowa ya amince da auren Mami baxa ta taba amin cewa ba, ganin ba mafita a gurin Mummyn ne yasa taje gurin Abba amma shima dai haka ta dawo jiki a sanyaye. Tari ta shiga yi sosai har hakan yasa jikin ta ya soma rawa tayi gaba zata fado daga kan gadon asibitin. Cikin zafin nama ya tallafo ta gaba daya ta shige jikin sa tana lumshe ido Jin kamshin turaren data san cewa a jikin masoyin ta kadai take jin sa. Idonsa a kan fuskar ta data kara haske hancin ta ya sake tsayi yake kalla. Gyara mata kwanciyar yai yana zama a kan kujerar dake gaban gadon, da sauri Yusrah ta yunkura zata tashi ganin da gaske Abdallah din ne ba wai gizo bane kamar yadda ta saba yi. Hade rai yai sosai yace “koma ki kwanta bana son musu”. Jiki a sanyaye ta koma ta kwanta din, sai dai kuma gaba daya jin ta take cikin wani irin nishadi, ynxu har ta kai matsayin da Ya Abdallah din zai zo duba ta. Wani murmushi ta saki sai dai maganar da yayi mata tasa a take murmushin ya bace. Ganin irin kallon da take masa yasa shi kara cewa zaki aure ni Yusrah? Da sauri ta juya ta kalli Ya Waleeda wacce ita ma idon ta tuni sun soma zubar da kwalla. Ganin kamar bata fahimci abinda yake nufi ba yasa shi riko hannun ta a nutse yace zaki aure ni Yusrah ki zama matata? Kuka kawai ta fashe masa da shi tana kankame hannun sa……… Mrs A.M 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs A.M Free book neh 🥰 Page 13 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Cikin muryar kuka tace “Yaya zaka aure ni da gaske Yaya, Mami zata yadda…” Zame hannun sa yai daga cikin nata fuskar sa dauke da murmushi yace “uhmm ke dai wannan ba hurumin ki bane, in har kin amince so nake nan da wata biyu ayi mana aure Kanwataa..” Da sauri tasa hannu ta rufe fuskar ta tana jin wani madaukakakin farin ciki a zuciyar ta. Murmushi yai ynxu har hakoran sa suka bayyana, mikewa yai yana zura hannu a aljihun sa yace “so nake kuna gama WAEC ayi mana aure yadda baxa ki sakè kwanciya a asibiti ba kar zuciyar ki ta buga”. A ynxu kuwa ya yadda cewa Yayan nasu ba wasa yake ba don haka ta mike tana rufe rabin fuskar ta, cikin rawar murya tace Yaya amma Meena fah.. Hade rai yayi yace “kika ce kina so na bayan kuma bakya kishi na, ynxu tambayar kishiyar ki kike”. Duk da maganar ta mata zafi amma haka tayi murmushi cikin sanyin ta dama already ai tasan cewa Meena zai aura ynxu ne dai kawai daya ce mata zai aure ta sai kuma taji tana kishin Meena din sosai. Ya fahimci halin data shiga don haka yace “Yusrah ban miki alkawarin cewa baxan sake aure ba ko da na auri Meena din kuwa, amma abinda nake so ki sa a ranki shine duk wacce zan aura baxan taba wulakanta kiba in sha Allah sbd ke din kina da kima da daraja a idona”. Hawayen daya zubo mata tasa hannu ta goge, ba abinda take fada a ran ta sai Alhamdulillah. Sai da ya tabbatar ta ci abinci kuma doctor ya sake duba ta sannan ya tafi. Haka kurin bayan ya gama sauraran maganar Yusrah din da Waleeda yaji ba abinda zai yiwa Alhaji ya biya sa duk hidimar daya masa a rayuwa amma zai iya auran yar sa ko dan sbd ya ceci rayuwar ta. Shi dama ba wai son Meena yake ba, don mahaifiyar sa kawai zai aure ta amma ko kadan baya son ta, yarinyar bata da kunya kuma yasan yadda take bin maza yasha ganin ta a gaban motar maza ko sun rungume juna ko suna kiss, da farko Mami yake sanar wa yana fada mata shi dai gaskia a fasa auren baya son ta bata da tarbiyya amma Mami din take nuna masa bacin ran ta shiyasa kawai ya kyale su. Yana isa gida bai tsaya ko Ina ba sai gurin Alhaji ya fada masa dukkan kudirin sa na son auren Yusrah kuma cikin lokaci kan kani. Fuskar Alhaji Washe da fara’a yace “Alhamdulillah Ya Rabbi, amma wani hanzari ba gudu ba Abdallah kana tunanin Mamin ku zata amince”. Murmushi yayi yana shafa gemun sa yace “in sha Allah Abba”. Gyada Kai Alhaji yayi yace “toh shikenan kaje tukun ku fara magana da ita, duk abinda tace sai ka fada min nidai Ina Jin kunyar na tunkare ta da maganar kar ta yi tunanin ko IKO da fin karfi nake son mata”. Mike wa Abdallah yai ya nufi part din Mamin, so yake ayi komai a gama kawai asa ranar auren. A dakin ta ya same ta don haka ya samu guri ya zauna bai tsaya kwana kwana ba ya fada mata abinda ya kawo sa da kuma maganar da sukai da Alhaji. D’ora wa yai da cewa “don Allah Mami Kar ki hanani auren Yusrah don tana matsayin yarinyar Mummy, kinga kin bani umarnin auren Meena duk da bana so amma haka na hakura don na faranta miki plz Mami kar ki ce a’a” Shiru tai Tana goge gumin daya ke zubo mata, ya zata yi da Bilkisu shine damuwar ta, ita ai ba butulu bace da zata ki amincewa da auren Yusrah, duk da mahaifiyar yarinyar ta kasance kishiyar ta kuma wacce bata ji dadin ta ba da farkon auren amma ita yarinyar tana da hankali sosai tunda kusan ma tarbiyyar Mamin ce kwana ne kawai bata yi a part din Mamin. Ganin yadda tayi shiru yasa shi fadin “Mami….” Murmushi tayi tace “tashi kaje zuwa da safe zan samu Baban namu muyi magana”. Ba dan ransa yaso ba ya tashi ya fice yana addu’ar Allah yasa Mami ta amince. ******** Washe gari da wuri na tashi na tafi restaurant don Ina son a bani hutu ko na sati biyu ne yadda zan kula da Umma sosai. Oga Kona ba dan ran sa yana so ba ya amince sai dai kawai sbd tace mahaifiyar tace ta karye kuma tun da Aasmaa din ta fara aiki a restaurant dinsu bata fashi, ko bata da lafiya tana zuwa da wuri tayi aikin daya samu sai ta koma gida. A kwanakin da baxa ta zo ba yasan sai sun jigata, tunda yawancin manyan mutane suna zuwa ne don abincin Aasmaa din, wasu kuma son ta suke da fasikanci in taki amincewa sai suyi ta zaryar zuwa restaurant din suna cin abinci don kawai su ganta. Ai bama su ba shi kansa zai yi missing abincin ta, kullum kafin ya tafi gida sai ya cika cikin sa shiyasa in yaje gida baya cin abinci, tun matar sa na Jin haushi har itama ta ware tun da wani lokacin da kanta take kiran sa ta ce tana son Aasmaa ta mata abu kaza zata ci in zai dawo ya taho mata da shi. ****** A cikin sati daya aka sa bikin Abdallah da Yusrah wata 1 da sati 3. Irin murnar da Yusrah ta dinga yi bata baki ne, kullum bata da aiki sai turawa Yayan nata text na godia kala kala da kuma nuna masa irin yadda yake da matsayi a zuciyar ta. Sai da kuwa ynxu wasan buya take yi da Mami da Abdallah din kansa, kunyar su take ji sosai shiyasa kullum tana daki a zaune sai dai su Sultan da Sultana da suka saba da zuwan Yusrah din ne suke zuwa part din Mummyn ynxu tunda ita ta bar zuwa part din su. Sai murna suke yi Yayan su zai auri yayar tasu. Mummy ita kam duk kunya ce ta Kama ta don haka ranar da aka sa bikin ta je part din Mami tayi mata godiya sosai ta kuma bata hakuri akan dukkan abubuwan data mata a da. Murmushi kawai Mamin ta keyi tana ce mata bkm ynxu ai komai ya riga ya wuce an zama daya. Ita Mami duk bata cikin nutsuwar ta don irin bala’in da Bilkisu tazo tayi mata a cikin gidan, ba irin cin mutuncin da bata mata ba har ita kanta Meena din dake kuka tace dama can ai Mamin ba son ta take ba kawai munafurci ne. A gaban Abdallah ta fadi haka tun da yaga zuwan Auntyn tasa dama ya shigo palon don yasan cewa baxa ayi mai dadi ba, ai kuwa dai Meena ta daku a hannun sa don zage karfin sa yayi ga dinga kwallo da ita cikin zafin zuciya yana cewa dama shi can ba son ta yake ba don bata cikin matan da yake so in banda darajar Mami ma mai zai yi da ballagaza irin ta mai rabawa gayu a titi. Da kyar Mami ta kwaci Meena a hannun Abdallah tana masa fada akan me yasa zai mata irin wannan dukan, shiru kawai yayi yana numfashi yana jifan Meena da Hajiya Bilkisu din da wani mugun kallo. Haka suka koma gidan su bayan a take a gurin tayi wa Mami transfer din kudin zancen da aka kai wa Meena a cewar ta yar ta tafi karfin Abdallah ynxu kuma. Shi ya dinga rarrashin Mamin tasu ganin tana kuka sosai, bata taba zaton Hajiya Bilkisu zata mata irin wannan cin fuskar ba, bama ita Bilkisu din ba yar ta Meena wacce zata aura wa dan ce take kiran ta Munafuka, ashe gaskiyar Maman tane data ce ita sam tarbiyyar Meena din bata mata ba dama sbd kawai taga sun dage ne shiyasa bata taba maganar ba. ******** Wanki nake a nutse na kayan baccin mu ni da Umma, cikin sati dayan nan da bana fita ko Ina har wani fresh na sake yi. Ba abinda nake sai kula da Umma sbd hannun ta, Ynxu ma tana daki bacci ne ya dauke ta shine ba fito na yi wankin. Hankali na baya kan wankin da nake yi tunanin yadda zanyi da Alhaji Inuwa nake yi, kwana biyun nan ya matsa min sosai kullum sai yazo shi da gaske yake aure ne ya kawo sa. Alhaji Inuwa babban mutum ne don Autar sace ma sa’a ta ita ma kuma tuni tayi aure ta haifa, Ina zai kai ni ai ya mun tsufa baxai iya biyamin bukatu naba. Ajiyar zuciya na sauke Ina dauraye Kayan duk rai na ba dadi. Sallama naji ta namiji kuma kamar muryar wannan mara kunyar yaron, da sauri na juyo don ganin waye kuwa…… Plz kuyi hakuri da jina da kukayi shiru bani da lafiya ne amma ynxu Alhamdulillah naji sauke🥰 Ngd sosai My fans da yadda kuka nuna kulawar ku a gare ni Allah ya bar mu tare har a Aljanna 😘😘 Mrs A.M 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by Mrs Elhajj Assalamu alaikum My fans fatan kuna cikin koshin lafiya, kowa yasan ni da *MRS AM* toh an samu sabani da akwai yar uwata writer da take amfani da *MRS AM* itama mutane suna rasa gane wace ita wace ni. Ni Marubuciyar *NOOR* *TASWIRAR KADDARA* *ELHAJJ* *ASMAA……* Zan chanja suna na daga *Mrs A.M zuwa MRS ELHAJJ* Domin magana da ni kai tsaye 09066728387 Free book neh 🥰 Page 14 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tsaye yake yana sanye da three quarter light brown sai riga mai dogon hannu wacce ta matse sa black colour, yayi kyau sosai har ya gaji ga wani aski da aka masa wanda ya matukar haskaka fuskar tasa. Da sauri na Kawar da kai na Ina tabe baki, wanki na na cigaba da yi cikin kwanciyar hankali duk kuwa da cewa kirjina banda bugawa ba abinda yake yi. Abdallah bayan ta yabi da kallo idon sa na sauka akan mazaunan ta yadda suka baje akan kujerar sai da yaji tsigar jikin sa ta tashi. Da sauri ya juyar da kan sa yana bin gidan kallo, tabe baki yai ya kalli Apple Watch dinsa dake hannun sa na dama. Tsaki ya saki yana taka wo a hankali, yau Umma zata sake ganin likita shiyasa ya zo dan ya Kai ta hospital din a duba hannun. A bayan ta ya tsaya yace “keee!” Da sauri na juyo Ina kallon sa yadda ya zuba min manyan sexy eyes dinsa sai da gabana ya fadi, yatsina fuska nai Ina motsi da baki a nutse nace “wa kake cewa haka…” Kawar da kan sa yai yace “Ina Umma…” Juyar da kai na nima nai ina boye Bra dita da nake wanke wa a cikin ruwan nace “me zaka mata…” Ba tare da ya kalle ta ba yace “ina ruwan ki….” Ynxu kam mikewa nai ina dan jan rigata yadda baza ta dinga lafe mun ba na nufi daki ina cewa “in ka koyi girmama na gaba da kai sai ka min magana mara kunya kawai….” Shi dai Abdallah bin mazaunan ta yai da kallo kawai yadda suke juyawa yasa shi lumshe ido yana Jin kaikayi a wuyan sa. Ajiyar zuciya ya sauke kawai shima ya nufi kofar daya ga ta shiga ya daga labulen ya leka. Daga Murya yayi yace Ummaaa…. Da sauri na d’ago Ina kallon sa yadda y ke ziro jikin sa yana Kara fadin Umman, mike wa nai da sauri Ina cewa kana da hankali kuwa zaka fado mana daki kai tsaye haka… Ko kallon ta bai yi ba ya sake bude baki zai sake kiran Umman ta daga labulen dake tsakanin palon ta fito jikin ta sanye da Hijab. Murmushi ta sakar masa tace “babana kai ne da ranar nan”. Shima Murmushin yayi yana sosai sunkuyar da kan sa yace “Ina wuni”. Da fara’a sosai tace “lafiya qalau babana ya mutanen gidan”. Dan sosa girar sa yayi da key din hannun sa yace “duk Alhamdulillah”. Gyada Kai tayi tace “Maa sha Allah”. A nutse yace “dama zamu koma yau ne a sake duba hannun”. Murmushi tayi tace “Allah yayi maka albarka ni na manta ma, bara na dan kintsa ko”. Kallon Aasmaa tai wacce take zaune ta zira hijab ta hade girar sama da ta kasa tana danna waya. Murmushi Umma tayi tana kallo ta tace “ki shirya ko Aasmaa sai muje tare”. Daga Kai kawai nayi na mike na shige ciki. Shima koma wa yai tsakar gidan ya tsaya yana danna wayar sa. Ni da Umman muka fito a tare Ina rufe dakin da key, kallon Umma nayi nace Umma “amma fa su Yaya da Maryam sun ce zasu zo yau gashi kuma zamu fita”. “Toh ai sai a bawa Sani mai shigo key din ko, in sun zo sai su karba”. Daga kai nayi kawai Ina riko mata jakar ta. Fita yai muka mara masa baya, shi da Umma sukai gaba ni kuma na tsaya na kulle gidan sannan na mika wa Sani key din. Tafiya nake a nutse ina dan gyara zaman hijab dina har na fito daga layin, idona ne ya sauka akan wata lafiyayyar mota baka sai daukar ido take tana kwalli kamar wacce aka shafawa mai. Fito wa yai daga motar yana kallo na a dake yace ke naje jira fa. Tabe baki nai kamar ban ji mai yace ba na nufi motar, hannu nasa na bude baya zan zauna Umma tace “toh shi driver din ki ne da zaki zauna a baya shi yana tuka ki”. Kamar zanyi kuka nace “Umma kawai sai na zauna a gefen sa salon ya sake rai na ni. Tsaki Umma tai tace “matsa na sauka ni Aasmaa na koma gaba, yaron nan bashi ne ya kade ni ba amma dubi yadda yake tsaye akan lafiya ta har kudin asibitun shi ya biya amma kike son wulakanta sa Aasmaa”. Da sauri na sauka Ina cewa “yi hakuri Umma bara na shiga gaban”. Motar shiru ba Wanda yake magana har muka isa asibitin, tun daga wajen zaka fahimci na kudi ne. Ni dai nawa ido har muka shiga aka duba muka fito, a hanyar mu ta koma wa ne wayar sa ta shiga ringing. Kasancewar wayar tana tsakiyar mu yasa na dan juya a nutse na kalli wayar, haka kurin gaba na ya fadi ganin anyi saving da Wife da emoji na heart a gaba. Shima juyo wa yai ya dauki wayar idon sa a cikin nata yana kallon ta, yadda ta bisa da ido sai abin ya dan basa mamaki amma ya waske yana sa wayar a speaker. Cikin shagwaba Yusrah tace “Assalamu alaikum Yayana”. Murmushi ya saki wanda hakan ya baiyana jerarrun hakoran sa yace “Waalaikumussalam Wifey”. Lumshe ido Yusrah tai tana jin wani nishadi da farin ciki, gaba daya Yayan nata sauya mata yake yi haka kurin lokacin daya zo part din Mummy yace wai ta fito suyi zance, haka ta fito sai sussunkuyar da kai take cikin kunya a lokacin ne ya bata wayar sa yace tayi saving numbern ta da sunan da take so ya ringa kiran ta, har tasa baby sai taga kamar tayi rashin kunya kawai tasa wifey da heart a gaba ta gudu daki. Tun lokacin ne ya dai na kiran ta da Yusrah sai dai Wifey wanda wannan sunan ba karamin farin ciki yake sata ba. Teemah ita ma data zubar da Kayan yakin ta tun da Meena tayi wa Mami rashin kunya ta dawo ta jone da Yusrahn ce ta zunguri Yusrah din cikin mamakin wai yayan nasu ke kiran Yusrah da wifey. Cikin rawar murya tace “uhmm dama dama su Teemah ne da Ya Waleeda suka ce wai zaka zo dinner din sbd asan yadda za’a tsara, da sauri ta ce ni dai nace ba ruwana baka so amma sun ce dole na tambaye ka”. Dan lumshe ido yai yana kallon Aasmaa wacce ta mugun hade rai tana kallon titi, murmushi ya saki yana gyaran murya yace “uhmm ke kina so nazo neh”. Waro ido Yusrah tayi tana rufe wa Teemah baki wacce take kokarin sakin Ihu, cikin inda inda tace “me zai hana Yayanaa” Gyada kai yayi yace “an gama Wifey amma part din abinci kar kusa da akwai wadan da zan sa suyi ohk..” Siririyar dariya tayi tace “Jazakallah bil Jannah Yayana, Allah ya tsare mun kai aduk inda kake i love u……” Girgiza kai yayi jin ta katse wayar yasan kunya taji shiyasa. Yana tsayawa a kofar layin namu na sauka da sauri Ina banko kofar nayi cikin layin, haka kurin nake jin haushin wayar da ya gama yi da dukkan alamu aure zai yi wannan yaron wai shi za’a bawa mata to yayi mata uban me, tsaki na saki da karfi Ina gyada kai. Daga Umma har Abdallah din da kallo suka bi ta, ita dai Umma tunani take Allah yasa ba abinda take hange bane don in har shine akwai kura. A tare suka fito da Umman, har suka isa gidan. Dan tsayawa yai yana bin gidan da kallo sbd mutanen ciki, juyawa yayi da niyyar tafiya Umma tace “shigo mana babana”. Ba yadda ya iya dole ya shigo kan sa a kasa zama akan kujerar da Maryam ta basa. Gaisar da Yaya yayi sbd daga ganin ta ma ai yasan babba ce shi kuma Maryam ta gaishe sa. Kallon su Yaya Umma tayi tace “shine Baban nawa da nake fada muku”. Godiya suka shiga masa shi dai kan sa a kasa bai ce komai ba sai dan Murmushi daya ke kokarin yi. Umma ce ta nuna Yaya tace “wannan itace Yayar su, yaran ta biyar sai Aasmaa sai Umar ai kasan sa shi sai auta Maryam ita kuma diyar ta daya Iyman gata nan sai kuma wanda ke hanya”. “Ita Aasmaa din har ynxu Allah bai kawo ba muna ta addu’a dai Allah ya kawo na gari.” Su Yaya da Maryam suka amsa da Ameen banda ni dana hade rai Ina juyar da kai na gefe. Shi kuwa shiru yai yana tunanin shiyasa ashe take wani hade rai ita a dole babba, Ashe Yayar Umar ce shi da yace masa shekarun sa 27 kenan ita sai 29 ko 30, dan tabe bakin sa yayi kuma irin Ina ruwan sa din nan, yarinyar da in ta tsaya a gabansa yake ganin ta yar cukul. Waleed yaron Yaya ne ya boyo abu a hannun sa yana mul mul da baki ya nufi Abdallah yana bangara dariya. Da sauri Basma data lura da Bra ce kuma ta tabbata ta Aunty Aasmaa ce tun da Kayan ta ne daya wanke bata shanya ba, don har zata shanya da suka zo sai kawai ya bari zuwa dare sbd mutane. Da sauri Basma ta nufo sa tana cewa Waleed zo nan kaji, ai kuwa yaron daya lura abun hannun sa take son kwacewa kawai yayi wulli da shi bai sauka ko Ina ba sai a fuskar Abdallah………… Mrs Elhajj😘😘 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Na Chanja Mrs Elhajj din😂😂😂 na fison DijahAM sunan da nake amfani dashi a wattpad… Page 15 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Dan yamutsa fuska yayi jin wani abu mai dan danshi danshi ya sauka akan fuskar sa, hannun sa ya mika ya ciro yana shakar sansayyan kamshin da abin yake. Dan ware idon sa yayi yana sake bin red bra din da aka mata adon flower da kallo, bai san lokacin daya ware idon sa gaba daya ba ganin size 42. Da sauri kuma ya dago ya kalli Basma da ta tsaya tana kallon sa ita ma sai sosa keya take. Yaya ce tace “ke Basma karbi mana kije ki ajiye mata abin ta”. Juya wa tai ta kalli Aasmaa wacce ta sunkuyar da kan ta idon ta taf da kwalla tace “kema dai ban da abinki Aasmaa ai da kin shanya ynxu sai kin sake wanke wa don nasan Waleed duk ya zuba miki miyar hannun sa a jiki”. Dagowa nai idona cike taf da kwalla nace “ynxu Yaya dole sai kin fada a bainar nasi cewa tawa ce salon a rai na ni bayan duk ga yara a gurin”. Da sauri Abdallah ya dago ya zuba mata ido yana kallon ta, ynxu ita ce take sa wannan babbar bra din dama haka take da cika ko dai ciko ne. D’ago wa nayi na kalle sa ganin yana kallona yasa na hade rai nace “lafiya Malam”. Kasa kasa yayi da idon sa kafin ya tabe baki yana mike wa fuskar sa a dan hade. Umma yayi wa sallama ya ciro kudi a aljihun sa ba dai san nawa bane ya bawa Waleed ya fita. Yaba halayen sa su Yaya suka shiga yi wanda hakan ya bata mun rai na mike kawai na shige ciki. Sai da naji sun dauko wata hirar sannan na fito muka shiga yi…. ****** A hankali yake kara kallon tym ganin 9pm, tsaki yayi shaf ya manta da maganin da doctor ya ce ya siyo na Umma wanda zata dinga shafawa a hannun. Mushabu ne ya kalle sa yace “wai lafiya kuwa kake ta tsaki tun dazu”. Tabe baki yayi yace “pharmacy zan je zan siyo wani magani”. Kallon sa Mushabu yai yace “wane magani ne haka zaka siya”. Juyar da kan sa yayi titi yace “Matar dana kai asibiti wacce ta karye, dazu mun koma toh ban siyo ba kuma nasan suma basu san da shi ba da wannan Mara kunyar zata siyo…” Da mamaki Mushabu yace wace “kuma mara kunya….” Shiru Abdallah yai yana bude motar kawai y fita don baya son maganar wannan mai manyan abubuwan kuma. Maganin ya siyo a pharmacy din har zai wuce yaga inda ake siyar da gasassun kaji, tsayawa yayi ta siya guda 8 ko wanne biyu biyu a leda daya, biyu nasa biyu na Mami biyu na Mummy biyu kuma zai kai wa Umma haka yake duk abinda zai siya wa Mami sai ya siya wa Mummy. Ajiye ledojin yayi a baya ya shiga yaja motar suka nufi gidan su Aasmaa. Tun da suka shigo layin Mushabu yake bin layin da kallo, a ran sa yana kara ganin mutuncin Abdallah, kwata kwata shi baya kyamar masu karamin karfi ynxu da wani ne yake da dukiyar Abdallah Allah ne kadai yasan abinda zai yi. Abdallah kuwa ban da bugawa ba abinda kirjin sa yake yi, wata yake gani kamar wannan mara kunyar a tsaye tana murmushi har ana ganin fararen hakoran ta kuma kamar tayi kwalliya don yana iya ganin yadda bakin ta yake kyalli sbd wutar nepa da ta haska layin. Shi ba ma wannan ne damuwar sa ba yadda yaga kamar mayafi ne a jikin ta kuma ta yafa sa a kafada ana hango wuyan ta yafi komai daga masa hankali. Gaba daya ran sa yaji yana mugun baci har wani yaji yaji yake ji a idon sa. Har suka karaso kusa dasu ya tabbatar da cewa ita ce, kallon wanda suke tare yayi yaga babban mutum sosai don har yar furfura ce a gemun sa, yana da kiba sosai ga katon ciki. Tabe baki yayi yana kallon ta kawai ya shige cikin gidan Musbahu ya mara masa baya. Sallama sukai Umar ya fito ya musu iso zuwa cikin palon tun da Umma na ciki. Shiga sukai suka gaisa ya bawa Umma ledar maganin da kuma ledar kazar, godiya sosai Umma ta masa shi dai ce komai ba sai Murmushi kawai da yake yi. Hankalin sa gaba daya yana waje ganin har 10mins da shigo war su amma bata dawo ba, mike wa yai kawai yana kallon Musbahu yace “bara naje na dawo”. Bai ma jira amsar sa ba ya fice da sauri. Har lokacin suna tsaye suna magana wacce bai san mai ake cewa ba don ita tana magana a hankali ne shi kuma Alh Inuwa sai kasa kasa yake da murya a dole yana tsara ta ta amince ta aure sa. Daga bayan ta ya tsaya yace kije “Umma tana kiran ki”. Da sauri na juyo na kalle sa har ga Allah sai da gaba na ya fadi ganin yadda ya mugun hade rai amma nima sai na hade rai Ina kau da kai nace “gani nan zuwa”. Ganin alamar zata iya cigaba da magana a harzuke yace “tace kiyi sauri ne fah plz haba Umma fa nace miki…..” Kallon Alh Inuwa tayi tace kayi hakuri Alh ko a waya sai mu karasa maganar kaga Umma na kira na. Murmushin yake Alh Inuwa yayi yace bakomai sarauniya ta ki kula da kanki kinji. Gyada kai nayi Ina sakar masa Murmushi, fata na shine ya fahimta ya rabu da ni don nidai Allah ya sani bana son auren sa sbd zan cutu sosai a wani fannin. A gaba ya sani muka shiga cikin gidan shi dai Abdallah bai san me ya hau kan sa ba kawai yaga dai ya zubawa bayan ta ido yana ganin yadda suke juyawa a cikin mayafin suna rawa. Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da suka shiga cikin palon. Zama nayi ina mayafina nace “gani Umma”. Cikin rashin fahimta Umma tace “ban gane ba”. Kallon sa nayi yadda yake tsaye a bakin kofa nace “ce min yayi wai kin ce nazo ynxu ynxu”. Kallon sa Umma tayi jiran karin bayani don haka yace “gani nayi ta dade kuma dare yayi”. A zafafe nace “wai kai Ina ruwan ka dani neh, haka kurin Ina zance zaka zo ka wani ce dare yayi nazo Umma na kira na bana son hauka fah”. Yamutsa fuska yy yace “ki dai na ihu mana”. Fararen idona na zaro nace “ni ce mahaukaciya ma kenan koh, wai meye damuwar ka dani ne ynxu da na dawo gida mai zaka min”. Dan hade fuska yayi yace “toh meye zaki wani fita gurin wancan mai katon cikin da mayafi kina wani masa murmushi wai ke son sa ma kike yi neh”. Tsaki kawai nayi Ina kallon Umma data zuba mana ido tana murmushi nace “Umma don Allah ki jawa wancan yaron kunne ba ruwan sa dani, Ina ruwan sa da saurayi na kuma ko ba mayafi naje meye damuwar sa”. Da sauri yace “kee yarinya ba dai kin dauka son ki nake ba koh”. Watsa masa wani mugun kallo nayi nace “kaso wa din ni Aasma ai abun kunya ne na nayi tunanin sa’ar autar mu yana so na wallahi”. Tabe baki yayi yace “better don ni ba wai son ki nake ba kawai dai sbd Umma ne, ni bana ma son gajerar mace….” Mikewa nai Ina buga tsaki nace “banxa kawai….” Zaro ido yai y kalli Umma yace “wai ni take zagi Umma” A fusace na juyo zanyi magana Umma ta zunguri kafa ta dole nayi shiru na shige cikin dakin ina kwafa.. Musbahu da yayi tagumi yana binsu da kwallo murmushi kawai yake, a ran sa kuwa mamaki yake dama akwai wacce zata iya sa Abdallah magana haka ta fada ya fada, bama wannan ba wai Abdallah son ta yake ne don ga kishin ta nan karara a idonsa dama tun da suka hango su dazu ya lura da yadda gaba data fuskar sa ta sauya, haka kuma da suka shigo ya kasa nutsuwa sai da yaje ya taso keyar ta, murmushi yai yana addu’ar Allah yasa aminin nasa soyayy ya fada sai dai kuma yana hango kura duba da yadda ga lura ita din tana da zafi gashi daga yanayin maganar ta ya nuna cewa ta girme musu kenan… Sallama sukai wa Umma da Umar suka fito. A mota Musbahu ya saki Murmushi yana kallon Abdallah yace “gaskiya amma wannan Aasmaa din ta hadu ga sunan ta na yan gayu gata kuma da kyaun fuska dana jiki”. Hade rai sosai Abdallah yayi yana tsaki yace “ina ruwana to ni”. Langwabe fuska Musbahu yayi yace “da zaka amince ni ai da kamun jagora inje gareta don ni dai ta gama birge ni a rayuwar nan komai yaj……” Bai kara sa ba sbd wani wannan birki daya ji Abdallah yayi a tsakiyar titi. Kallon sa Abdallah yayi da idon sa da sukai mugun ja yace “don uban ka saukar min a mota”. Zaro ido Musbahu yayi yace “na sauka akan titi Abdallah, me nayi ma”. A fusace yace “sbd kai dan iska ne zaka zo kana ce min wani wai wannan yarinyar tana da kyaun jiki, Musbahu yaushe ka zama dan iska ido ya zuba mata kenan kana kallon halittar ta”. Cikin son sake tado kishin Abdallah din da yake danne wa Musbahu ya Lumshe ido yace “wallahi tayi ne Abdallah kaga yadda take magana kawai nifa zuba wa lips dinta ido nai do….” A mugun haukace Abdallah ya fito daga motar ya zagaya inda Musbahu yake ya bude ya fisgo sa waje da karfi ya rufe motar ya koma side dinsa ya bude yaja a guje zuciyar sa na wani irin dokawa ….. Musbahu kuwa mai zai yi in ba dariya ba, shi ko hauka yake sai ya tunkari Aasma da maganar soyyaya, shi fa Wallahi tsoro ta ma yake ji don haka kurin take masa mugun kwarjini irin su ai sai su Abdallah din…. ******* Shigowa tayi dakin Mijin nata bayan bayan ta gama yiwa yaran ta addu’a ta sunyi bacci. Tana sanye da doguwar rigar bacci wacce ta kai mata har kusa da kafar ta mai siririn hannu sai kamshi take mai nutsuwa. Ta matsu taji wani magana ne wannan mijin nata yake son fada mata wanda yace magana ce mai muhimmanci, irin yadda yayi serious dinnan yasa ta kagara data ji ko meye. A zaune ta same sa a bakin gadon yayi tagumi da alama ita yace jira. Yar dariya tayi tace “Abba irin wannan tagumi haka kamar Wanda aka aiko wa da wani mummunan sako”. Yake yayi yana janyo hannun ta ya zaunar da ita a kan kujera shi kuma ya zauna a kasa. Taso kwarai ta hana sa zaman a kasa amma ya hana ta yace yafi son ya zauna a kasa din dai. A hankali yace “Hajjo kin San Ina son ki, kuma baki gaza a ko Ina ba kina iya bakin kokarin ki don faran ta min bani da abinda zan ce miki sai dai Allah yayi miki albarka kawai.” Ajiyar zuciya ya sauke yace “nasan abinda zan fada miki dole zai bata miki rai kuma zai hautsina tunanin ki amma ba yadda na iya ya zama dole na fada miki Hajjo, Aure nake son kara wa”. Wani irin bugawa kirjin ta yayi da karfi har sai da ta d’ora hannun ta akan kirjin, tun da ya fara magana dama gaban ta yake faduwa don tasan za’a zo wannan gabar. Bata ce komai ba ya riko hannun ta yace “wacce nake so taki amincewa da ni Hajjo, Ina kaunar ta sosai amma ita nuna wa take data aure ni gwanda ta dawwana a zaune ba aure, ki taimaka min Hajjo ke kadai ce zata iya shawo kanta domin ta amince Wallahi zanyi adalci a tsakanin ku don duk Ina son ku……” Cikin rawar murya tace “wace haka Abba da baza ta amince da auren ka ba sai na sa baki kuma”. Lumshe idon sa yai cike da shaukin sunan ta ma kawai da zai fada yace “Aasmaa taaa….” DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 16 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Wani irin mugun duka da zuciyar ta tayi sai da taji kamar zata faso kirjin ta. A zabure ta mike tace “ban gane ba Abba kana nufin aminiya ta wai Aasmaa dai tawa…” Gyada kai yayi yana riko hannun ta yace “don Allah Hajjo ki fahimta Wallahi tun farko dama Ina son ta, kawai a lokacin na dauka ba son ta nake ba ke nake so shiyasa ban ma wai waye ta ba sai bayan munyi aure”. “Duk yadda zan yi da ita don ta gane wallahi taki bani hadin kai don Allah ki taimaka min ki roke ta nasan zata yadda tun da dama sbd ke taki amincewa”. Jiri ne taji yana diban ta so take ta gaya masa bakar magana wacce har ta mutu baxai taba manta wa ba amma kuma taji gwanda tayi shiru da dukkan alamu ba iya gaskiyar ya fada mata ba yana boye mata wani abun ita kuma tafi son taji komai. Ajiyar zuciya ta sauke tana koma wa ta zaune ta zuba masa ido, mijin ta wanda take cika baki akan ba wata mace a gabansa bayan ita ashe yana can yana bibiyar aminiyar ta akan ta amince ta karbi soyayyar sa ta aure sa, aminiyar da ta gama sanin sirrin ta ko jiya jiya sai da ta kira ta tana mata complain cewa Abba yace ta bude gaskiya me ya kamata ta sha don ta hade ita kuma bayan ta gama mata fada akan ta rike sirrin ta sai ta fada mata abubuwan da zata hada don taji ta matse din tun da ita ta fita sanin abubuwan gyaran jiki. Murmushin yake ta saki tana kallon sa wai ita ce yau Abba ya zauna a gabanta kamar mai neman gafara akan kawai ta amince ta shawo masa kan Aasmaa. Hannun sa ta rike tace “ynxu dan wannan ne yake damun ka Abba shiyasa naga kwana biyu duk baka cikin walwala, ita Aasmaa din in ban da abin ta ai ba komai bane”. Ajiyar zuciya ya sauke da karfi wacce har sai da ta sake zuba masa idanun ta, kara matse hannun ta dake cikin nasa yayi yace “Wallahi na fada mata haka nace mata nasan baki da matsala tun da ai kun san juna kin san baxa ta mallake miki ni ba amma taki yadda”. Dan gajeran tsaki Hajjo tayi tace “gaskiya amma ta wahalar min da kai Allah ne kadai yasan tsawon lokacin daka dauka gurin shawo kan ta, wata kula ma da tuni ta haihu”. Da sauri yace “tuni ma wallahi ai da tana da yara uku haka ma, kin San kusan shekara 6 fa kenan ba in da ban je ba gurin aikin ta kusan kullum sai naje da safe amma Wallahi ko kallo bata ishe ni ba, haka in naje gidan su ma kwata kwata bata fito wa tama yi blocking dina a wayar ta”. Wani irin kuna Hajjo take ji a cikin zuciyar ta wani irin cin amana ne haka ace shekara 6 Mijin ta yana yawon neman soyayyar aminiyar ta lokacin shekarun su 2 da aure da haihuwar ta daya, amma ita ta kasa fada mata wannan maganar haka kullum bata da aiki sai na zama ta bude wa Aasmaa sirrin ta ita tana neman shawara ashe ma Mijin ta yana can yana fada mata kalaman soyayya. Mike wa tayi daga zaunen da take fuska ba yabo ba fallasa tace “zan yi shawara zuwa da safe in sha Allah, in ta kama ma gobe sai naje gidan nasu muyi magana”. Bin ta yayi da kallo har ta fita daga dakin yana so yace mata don Allah kar ta yi shawara da Ummu yayar ta amma kuma yana tsoron tunanin da zata yi. Ajiyar zuciya ya sauke yana addu’a a ransa Allah yasa ba zata Kira Ummu ba don yasan matukar ta Kira Ummu lamari ya baci ya dade da sanin cewa Ummu bata son Aasmaa, da akwai lokacin daya gaba dawo wa daga aiki ya tarar da Ummun tana zuga Hajjo kan ta rabu da Aasmaa in ba haka ba sai ta aure mata miji, a lokacin Hajjo gwasale Ummun tayi ta nuna mata cewa tasan Aasmaa ko maza sun kare baza ta taba auren Mijin taba sannan kuma ta yadda da Abban ma tasan baxai auri Aasmaa ba. Ynxu ya tabbata in har Hajjo ta fara kiran Ummu to fah lamari ya lalace.. Hajjo kuwa tana zuwa dakin ta kuka ta dinga yi sosai na bakin cikin wannan ranar data ke gani, kamar wacce aka zabura ta dauki waya ta kira Ya Ummu, fada mata komai tayi cikin kuka in da ya Ummun tace mata ta kwantar da hankalin ta gobe da sassafe ta nufi gida ita ma zata je can su hadu. ******** Idar da sallar Azahar nayi Ina zaune ina jan carbi a tsakar gida cikin nutsuwa umma tana kwance a gefe na akan tabarma don garin yayi luf luf alamun hadari sai iska mai dadi dake kada wa. Da sassarfa Ummu da Hajjo suka shigo kai tsaye ko sallama babu, Kara Ummu tasa tayi ball da robar dana ajiye sbd ko ruwan sama zai sauko ya taru a ciki. A razane na mike tsaye gaba na yana faduwa sbd mugun kallon dana ga Hajjo na min. Cikin rawar baki nace “Hajjo lafiya kuwa”. Kafin tayi magana Ummu ta riga ta da cewa “ai dole kice lafiya tsohuwar guzuma, wato kina nan kin nade a gida ana miki kallon saliha ashe mazajen mutane kike farauta, sbd abin kunya ma ki rasa mijin wa zaki dinga bibiya sai Mijin aminiyar ki”. Hajjo dake kallon Aasmaa cike da tsana tana bin jikin ta da kallo tace “Allah y isa tsakanina da ke Aasmaa, ba dauki amanar duniya na baki duk sirrina ba wanda baki sani ba ashe kina nan kina mallake min miji a waje ban sani ba”. Cikin rawar baki nace “Hajjo Ina kika ji wannan maganar don Allah Kar kiyi min mummunar fahimta ki tsaya ki saurare ni kiji”. Cikin karaji tace “in saurare ki akan me Asma’u ai Wallahi kin bani mamaki, tsawon shekara 6 Abba(sunan da yaran su suke kiran Kabeer da shi shiyasa itama take ce masa haka)yana neman ki wai har kofar gida da gurin aiki yake zuwa don kawai ki amshi tayin soyayyar sa amma ki kasa fada min, wannan wani irin yaudara neh Asma’u Ashe bakin ciki kike min sbd nayi aure shiyasa kika shiga kika fita kika farauto zuciyar Mijina, Mijina fa Asma’u”. Umma da bata fahimci abinda yake faruwa ba ta mike a hankali tana kallon su tace “lafiya kuwa Ummu meye yake faruwa neh”. Da sauri Ummu ta daga mata hannu tace “don Allah Umma kar kisa baki bana so na fadi wata magana ne sbd kar kice nayi rashin kunya amma ai ba a banza Aasmaa tayi kokarin kwace wa aminiyar ta miji ba, kowa yasan ai da yadda kuke da Mama amma haka Liman yaso ya aure ki da kyar da addu’a ya dawo hayyacin sa ya bar maganar auren….” Ynxu kuwa ji nayi rai na ya fara baci haka yasa na isa gaban su Ina duban su nace “Ummu bana son na zage ki ko ba komai Umma tayi min tarbiyyar girmama na gaba da ni, amma Wallahi kinji na rantse matukar kika ce zaki zagar min mahaifiya sai na sai ta miki baki”. Tafa hannu Ummu ta shiga yi tana dariya tace “eh lallai abin na yi neh, wato sbd baki da kunya shine zaki zo ki tsaya a gabana kina cewa zaki sai ta min baki bayan kin aika ta cin amana”. Tsaki Hajjo tayi tana kankance ido tace “Ya Ummu ban da abinki ai karuwa bata san wani abu wai shi kunya ba”. A tsorace na juyo Ina kallon Hajjo cikin rawar murya nace “Hajjo ni kike cewa karuwa?” Cikin idona Hajjo ta kalle ni tace “kwarai kuwa in ba karuwa ba wace zata dinga janyo attention din mazan mutane, ai duk mutumin da aka ce yayi aiki a hotel kawai a kalle sa ne a juya don an san kawai an gama farfarke sune, ai shiyasa kullum kike zama da hijab kamar saliha Allah ne kadai yasan abinda ke kasan Hijab din”. Umma data yi shiru ce ta kalli Aasmaa da tayi sakato tana kallon Hajjo hawaye na zubo mata tace “Zo nan kin ji Aasmaa”. Da kyar na iya daga kafata na nufi Umma Ina zuwa kawai na rungume ta Ina fashe wa da kuka. Lumshe ido tayi tana shafa bayana cike da kulawa. Ummu da Hajjo kuwa bakaken maganganu suka cigaba da gasa min son ran su sai da suka ga ba wanda yace musu komai sannan suka juya bayan Hajjo tace na bar mata miji in ba haka ba Wallahi sai ta halaka ni…. Sai da nayi kuka na mai isa na Umma bata hana ni ba sannan na d’ago na kalle ta nace “Umma ynxu kowa kallon karuwa yake min sbd nayi aiki a hotel, Umma girki fa kawai nake yi a kitchen Wallahi Allah Umma”. Murmushi Umma tayi tana shafa kai na tace “ba wanda yake Miki wannan kallon sai mara tunani Aasmaa, Kar ki damu d abinda mutane zasu yi tunani matukar kin san ke dai baki sabawa Mahaliccin ki ba toh ki rabu da maganar mutane don su ba’a iya musu kin ji.” A sanyaye na daga kai Ina share hawayen daya zubo min. Dan hade rai Umma tayi tace “mene tsakanin ki da Kabeer Mijin Hajjo?” A nutse na fada mata yadda ya dinga damuna a cewar shi sona yake, sosai Umma ta min fada kan rashin fada mata ba dan yi ba duk tsawon lokacin sannan kuma ta ce ko da ace son Kabir din ma nake bata amince na cigaba da kula saba, nima dama ba son sa nake ba ai ko son sa nake sbd darajar Hajjo ma zan hakura da shi. Duka yinin ranar haka muka shi sa suku ku, da daddare Liman ya shigo ya bamu hakuri ni da Umma yace kanwar Hajjon ce data ji abubuwan da suka zo suka mana ta fada masa, suma kuma ya musu fada sannan ya kara da cemin in har na amince da Kabir din na fada masa zai kira sa ya turo magabatan sa. Girgiza masa Kai nayi da sauri nace ni dai sam bana son sa, ba dan Liman yaso ba ya mana sallama ya tafi yaso lallai ace Aasmaa din tana son Kabir shi kuma ya aura mata shi yaga yadda zasu yi da haukan su daga ita har Maman tasu da suka daga hankalin su. ******* A hankali rana ku suke tafiya har na koma aiki na, kuma tun daga ranar da su wannan Mara kunyar yazo da daddare bamu sake haduwa ba, sai biyu yana zuwa yana mai da Umma asibiti amma bana nan shiyasa bama haduwa ma. A gajiya nake matuka akan aikin da nake yi yau, aiki ne na abincin gargajiya za’a kai gidan deputy governor da ake taro, sinasir ne da masa sai miyar taushe data ji naman talo talo, ga kunu aya da muka yi mun zuba a cikin jarkoki abin sai sam barka. Mun gaji matuka sai dai kuma mun samu alkhairi don da muka kai abincin gidan 100k matar deputy governor din ta bamu. Shiyasa abokan aiki na sai murna suke suna kasafa yadda zamu raba kudin tun da mu uku muka je ni da Salma sai Abubukar dayai driving din mu. Nidai murmushi na musu kawai har muka koma restaurant din suka bawa Oga Kona kudin, 30k ya bamu kowa shi kuma ya dauki 10k, wannan na daya daga cikin halayen Oga Kona daya sa muke ganin girman sa bashi da mugun ta akan kudi in har aka baku zai baku abin ku ba tare daya zaftare muku ba. Cikin farin ciki na isa gida Ina fadawa Umma kudin da muka samu, 10k na dauka na bawa Umar ya ajiye min a bank dinsa haka nake yi in har na samu kudi ko aka mana albashi Ina cire wani kaso ba basa ya ajiye min sbd aure na in ya tashi. Kallona Umma tayi tace “Babana dai shiru kwana biyu baya zuwa ya dade bai zo ba gashi ban kar bi number din sa ba balle mu kira muji ko lafiya”. Turo baki nayi a shagwabe nace “Umma don Allah kar ki wani damu ai gwanda ma da baya zuwa kwata kwata yaron bashi da kunya ni murna nake ma da baya zuwa wallah”. Baki sake Umma take kallona tace “wai lafiyar ki kuwa Aasmaa mai yaron nan ya miki da kika tsane sa haka neh wai…” Yar dariya nayi Ina mike wa nace “Umma bashi da kunya wallahi shiyasa ni kawai bana son sa…” ******* Ihu take sosai tana watsi da kayan da suke jere akan tafkeken mirror din ta, tun da taga katin dinner din Abdallah da Yusrah hankalin ta ya tashi take kuka, abin da ya sake daga mata hankali ma hoton su da Teema ta dauka zuna zaune akan kujera da alama a palon Mami ne, Abdallah ya zuba mata idon nan nasa yana murmushi ita kuma ta sunkuyar da kai tana rufe fuska da mayafi. Wannan hoton ya dugunzuma hankalin Meena har taji zata iya hauka akan Abdallah…. Da sauri Hajiya Bilkisu ta riko ta tana cewa “ki kula don Allah Meena mana kar Kiji ciwo”. Cikin kuka tace “wallahi Mum Ina son sa Ina matukar kaunar sa, ynxu Mum aure zai yi Ina ji Ina gani ba yadda zan yi, Mum aure fa za’a daura masa ni shikenan baxai aure ni ba kenan Mum”. Shafa kan ta take cikin damuwa tace “ki kwantar da hankalin ki bara Iya tazo ai ta kusa zuwa bikin zan same ta na mata magana nasan zata yadda kuma zata tursasa Abdallah din ya aure ki tun da dukkan ku ai jikokin ta neh”. Da sauri Meena ta d’ago ta kalli Hajiya Bilkin tace “da gaske Mum iya zata iya sawa ya aure ni” Daga mata kai tayi alamun tabbatar wa haka yasa ta koma ta kara lafewa a jikin Mum din tata tana jin tsanar Yusrah na kara kama ta, dama tun farko ba son ta take ba Ynxu kuma ai tana da hujjar kara tsanar ta tun da zata aure mata masoyin ta……. DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 17 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tagumin da tayi ta cire tana goge hawayen daya zubo mata, ta rasa meye mafita akan wannan lamarin, tun ranar da suka je gidan su Aasmaa suka ci mata mutunci Kabeer ya dai na kula ta gaba daya. A daran ranar taga tashin hankali ganin idon ta, ashe Liman ya kira sa y fada masa duk abinda suka aika ta. Sosai ya nuna mata bacin ran sa kuma ya rantse mata neman soyyayar Aasmaa ynxu ma ya fara in har taga ya daina bibiyar ta to an daura mata aure da wani a masallaci, kuma ya taba tabbacin ana daura mata auren zai baxa ma neman Matar aure cikin wata biyu zai sake aure wallahi. Hankalin ta gaba daya a tashe yake ta rasa me yake mata dadi a duniyar, data kira Ummu ma ce mata tayi ta yi dabaru ta janyo hankalin sa gare ta, to taya zata janyo hankalin nasa bayan ya kaurace mata baya mata magana da sassafe yake fita baxai shigo ba sai 12 na dare, baya cin abincin ta gaba daya kullum haka yake shigowa karshen magana ma ko ruwan gidan baya sha, da ruwan sa yake shigowa. Bukatar ta kuwa in taje tana shafa sa zai biya mata bukata amma gaba daya ba alamun samun nasara, babban tashin hankalin ta ma jiya da tasha magungunan da Ummu ta kawo mata taje tace tana bukatar da yana sassakar ta amma kiran sunan Aasmaa yake, wannan abun ba karamin bakanta mata rai yayi ba da kara mata tsanar Aasmaa din. Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon agogo karfe 1:30 amma bai shigo ba. Alamun bude kofa da akai ne yasa ta dagowa ta zuba masa ido, a nutse ya shigo sai dai ko kallon ta bai yi ba ya shige dakin sa. Da sauri ta mike ta bi bayan sa ta kuwa taki sa’a bai kulle kofar da key ba. Durkusawa tayi tana fashe wa da kuka tace “don girman Allah Ya Kabeer ka yafe min, wallahi sharrin shaidan ne amma hakan baxai sake faruwa ba”. Ko kallon ta bai yi ba sai kayan sa da ya cire ya daura towel zai shiga wanka, da tasan halin da zuciyar sa take ciki ba taba ce masa haka ba, kullum sai yayi wa Aasmaa message na ban hakuri bata taba masa reply ba sai yau tace duk abinda aka mata ai shine ya ka mata don haka ita bata ga lefin Hajjo ba tasan kishi ne amma ba wanda ya jawo mata sai shi, ta kuma kara da ce masa ko zata mutu bata yi aure ba baxa ta taba auren sa ba. Wannan maganar tata ba karamin daga masa hankali yayi ba, shi kam yasan kaddarar sa ce kaunar Aasmaa amma yana mata wani irin so ne mara misaltuwa. Ganin ya mata banxa zai shige toilet ta rungume kafafun sa tana basa hakuri. A kufule ya fisge kafar tasa ya na nuna ta cikin rawar murya yace “da kin san irin son da nake mata da baki je kin zage ta ba har ki Kira ta da karuwa, a lokacin dana fara ganin ku ita nake so ba ke ba, amma sbd ta min kwarjini Ina ganin cewa tafi karfina yasa na koma gare ki Hajjo, bayan auren ki hankali na ya kasa kwanciya da ke sbd ke da gangar jikina kike rayuwa zuciya ta tana gare ta, shiyasa na fara neman soyayyar ta don ta amince min na aure ta amma taki sbd ke, duk amintar sai gashi kina kiran ta da Karuwa”. Zama yai a bakin gadon hawaye na zubo masa, cikin kuka yace “da kin san irin son da nake mata da kin amince min kin taya ni neman soyayyar ta, sbd Ina mata son da zan iya mutuwa sbd ita Hajjo….” Baki sake Hajjo take kallon sa ganin yadda yake kuka yana ambatan son da yake wa aminiyar ta, itama ji tayi hawaye na taruwa a idon ta cikin sanyin jiki tace “don Allah ka dai na kuka Abba”. Girgiza kai yayi yace “kuka ai ynxu na fara tun da har ta budi baki tace baxa ta taba aure na ba ko zata dawwama ba aure, abu daya na sani wallahi in har ta auri wani ba ni ba toh ki shirya bayan wata biyu kema zaki tarbi taki kishiyar….” Daga haka ya mike ya shige toilet yana goge hawayen sa. Mike wa tayi cikin sanyin jiki ta fita daga dakin zuwa nata zuciyar ta tana bugawa, ynxu in Aasmaa tayi aure kenan Mijin ta zai auro mata wata kishiyar ce dai sai ya mata kenan… Zama tayi a kasa yana fashe wa da kukan bakin ciki…… ******** Kallon Yusrah yake wacce take ta sunkuyar da kan ta kasa cike da kunyar irin kallon da yake mata. Kankance ido yayi yace “wifey wani turare kike amfani da shi ne uhmm…” Lumshe idon ta tayi cikin shaukin soyayyar sa tace “bkm Yayana..” Ware mata ido yayi yana kallon ta, shi kadai yasa irin abinda kamshin nan yake masa, daure wa kawai yake yana magana amma gaba daya ya shiga wani yanayi ne, yana son kamshi sosai balle wannan kamshin da yake ji yana shiga dukkan wata kofofin jikin sa. Ita dai Yusrah rufe fuskar ta kawai taka tana murmushi, gyaran jikin da ake mata ne ya kama jikin ta sosai, Mami ce da kan ta take mata tun da ta iya, da kyar ta yadda Mamin ta fara mata sbd kunya amma ita Mamin ko a jikin sa dage wa take tana gyara Yusrah, a cewar ta ai ko ba Abdallah bane zai aure ta ita mai gyara Yusrahn ce tun da yar ta ceh. Tun da aka fara gyaran basu taba hadu wa da Abdallah ba 3 weeks kenan, boye ta ake sai yau da ya rage saura kwana 6 daurin aure kuma ta tare a gidan sa shine ya kira ta akan yana bukatar katin dinner guda biyar, shima Mummy bata san ta fito ba satar hanya tayi ta kitchen ta fito. Mika masa katin tayi tace “gashi Yayana, wasu friends dinka zaka bawa koh, Teemah ta bawa Yaya Musbabu bai isa bane kenan koh”. Lumshe idon sa yayi yace “no ya isa wata zan kai wa”. Da sauri ta d’ago ta kalle sa haka kurin taji gaban ta yana faduwa, cikin rawar murya tace “yaya wata zaka kai wa cards din har 5 friend din ka ceh”. Zuba ma idon ta kallo yayi yana hango kishin sa dake kwance a ciki, murmushi ya saki yace “uhm zan basu ne ita da maman ta sai sisters dinta”. Turo baki tayi tana juyar da kai gefe duk ran ta a jagule. Murmushi ya Kara saki yace “wifey haushi na kike ji neh…” Turo baki tayi a shagwabe tace “Yaya ba kai bane wai zaka bawa wata cards din bikin mu har 5”. Shiru yayi don bai san kuma mai zai ce ba, ajiyar zuciya ya sauke yace “bara na tafi ki koma ciki kar sanyi ya dake ki”. Bin sa da kallo tayi kwalla na tarar mata, tasan baya son ta ita kadai ce take son sa amma tsoron ta shine kar yaje ya samu wacce yake so tasan sai ya fifitata akan ta. Hawayen daya zubo mata ta goge ta shige ciki. A nutse yake driving din sa yana tunanin sabuwar rayuwar sa zai fara in aka kai masa mace gidan sa, yasan ba wai son ta yake ba amma yana ganin girman ta sosai a idon sa, shi kan sa a ynxu ya shaida cewa tana son sa soyyaya ta gaske na kuwa. Duk abinda yace yana so nan da tan take yi wanda kuwa ya nuna baya so barin sa take duk irin son da take ma abin kuwa. Sai da ya tsaya ya siya tsire da yawa sannan ya nufi unguwar su mara kunyar sa yana murmushi. Da sallama a bakin sa ya shigo kan sa a kasa yana haska wa da wayar sa tun da ba wuta sai hasken farin wata. Umma da Umar da sauke zaune ne suka amsa masa fuskar su Washe da murmushi. Shima murmushin yayi yana zama akan kujerar da ke tsakar gidan. Cikin girmama wa yace “Umma Ina wuni”. Murmushi tayi tace “lafiya qalau babana kwana da yawa Ina ta cigiyar ka gashi ban da number ka balle Umar ya kira ka”. Shi fa Wallahi haka kurin yake jin kunyar mata ya rasa dalili kawai kunyar ta yake ji, dan sosa girar sa yayi yace “na shiga hidima ne yau saura kwana 6 bikina”. Ina zaune a daki ban san lokacin da na mike da sauri ba ina dafe kirjina da yayi wani mugun bugawa. DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 18 Dedicated to Abubakar Musa Sulaiman Ina godia sosai Allah ya bar zumunci ya baka mata ta gari mu sha biki💃 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Mike wa nayi daga zaunan da nake Ina dafe kirjina jin yadda yake bugawa da karfi, lumshe ido nayi Ina jingina da bango don ban san wani abu ke damu na haka ba da nake jin zafi a kirjina. Daga waje kuwa Umma ce ta kalli Abdallah cikin murna tace “Maa sha Allah babana, ashe ango ne a zaune a gabana ban sani ba”. Sunkuyar da kai yayi yana sosa kan sa don kunya yaji kawai yana ji. Umar ne ya mika masa hannu yace “congratulations bro zan so daurin auren kuwa in sha Allah”. Mika masa yar karamar jakar daya sa cards din yayi yace “gashi na daurin aure ne sai na dinner”. Umma ce tayi murmushi tace “dinner din dai sai dai su Yaya dasu Aasmaa amma ni tsohuwa kawai sai naje wani dinner”. Marairaice mata yayi yace “plz Umma ai dinner din har da manya ba ta yara bace kadai”. Girgiza kai tayi tace “Aa babana kaga ban gama warke wa bama da saura su Yaya zasu je in sha Allah”. Ba don ran sa yaso ba ya bar maganar suka shiga wata hirar yana bata amsa a nutse, kasan zuciyar sa so yake ta fito amma bai ganta ba kuma yana jin nauyin ya budi baki ya tambayi inda take. Ledar tsiren ya mikawa Umma yace a hanya ya gani shine ya siyo mata, sosai ta masa godia cike da farin ciki tana ajiye ledar a gefe. Sai goma ya mike zai tafi Umma ta kira Aasmaa akan ta fito su gaisa da Abdallah ta masa murnar auren da zai yi. Hijab na saka na fito ina turo baki, tun da na fito yake kallon ta zuciyar sa na bugawa duk da ba haske a gidan amma yana iya hango baby face dinta d take a hade kamar wacce aka ai kowa sakon mutuwa. A hankali na kalli Umma nace “Umma gani”. Dan hade rai Umma tayi tace “baki ji shigowa babana bane baki leko kun gaisa ba gashi ashe aure zai yi kinga katin bikin ya kawo nace ni dai baxan iya zuwa ba sai dai ku”. Waro ido nayi irin ban san abinda ya faru ba nace “Umma ynxu wannan yaron za’a ma aure”. Tafa hannu na shiga yi na d’ago Ina kallon sa cike da mamaki nace “ynxu wata yarinyar ce ta yadda zata aure ka don Allah, dan yaro da kai har wani iya rike aure zaka yi”. Tsawa Umma ta daka min tace “meye haka Aasmaa taya mutum zai zo ya kawo mana katin sa kawai ki fara maganar shirme, ynxu baban nawa ne baxai iya rike aure ba”. Turo baki nayi Ina langwabe kai a shagwabe nace “Umma to gani nayi fa don Allah yayi yarinta da yawa kawai sai a masa aure duka duka nawa yake ma”. Abdallah daya zuba mata ido ran sa yana baci sbd yadda take kiran sa da yaro yace ma Umma bara na dan wanke hannu nah Umma kafin na wuce. Daga masa kai Umma tayi tana watsawa Aasmaa harara. A nutse yake tafiya sai da ya maso kusa da ita ya tabbatar hankalin Umma da Umar basa kansu kawai yasa hannu ya fisgo ta jikin sa, dan matsawa yayi baya kadan don yadda ta taho din saura kadan kirjin su ya hade. A fusace na bude baki zanyi magana sai dai ban kai ga cewa komai ba na tsinkayi muryar sa a dai dai kunne na yana fadin “ki kula da kira na yaro bar ganin ki kin fini shekaru in na damke ki a hannu na sai na farka ki tsab don daga ganin kugun kima na miki yawa….” A razane na daka tsalle nayi baya da sauri Ina fadin “A’uzubillahi” Umar ne ya mike ya taho guri na da dan sauri yace “lafiya Ya Aasmaa”. Ban basa amsa ba sai kallon Abdallah kawai da nake Wanda ya gama wanko hannun sa yazo ya wuce kamar bai san abinda ya aika ta ba. Sallama yayi ma Umma ya wuce Umar ya mara basa baya don masa rakiya. Umma fada ta kama min bayan sun tafi akan na dai na wannan tsanar da nake nuna ma babanta, ni dai ban yi magana ba sai idona dana lumshe kawai duk lokacin dana tuna kalaman sa sai tsigar jikina ta tashi kafin na ankara kawai sai ji nayi na jika pant. Nidai haka na kwanta gaba daya sukuku a rai na kuwa ban da Allah ya isa ba abinda nake ja masa, wannan maganar da yayi min ta taso min da mugun feeling din da nake danne wa, a wahalce bacci ya dauke ni cike da mafarkai. Karfe biyar na farka a lokacin da aka yi kiran farko, lumshe ido na nayi kawai hawayen takaici yana zubo min Ina kara jawa wannan yaron Allah ya isa. Da sauri na bude idon kuma sbd mafarkin sa da nayi ni da shi muna duniyar ma’aurata muna tsotse wa juna man Kai yasa na tashi da sauri Ina share hawaye na. A rai na kuwa Allah ya kiyaye kawai nake har na shiga toilet, a gurguje nayi wanka don kar Umma ga farka taji ina wanka da sanyin safiyar nan, kayan jikina na mayar tun da ba yadda zanyi na chanja kaya Umma sai ta fahimta. A toilet din na wanke pant dina na fito na shanya akan igiyar dake bayan dakin mu na koma ciki da sauri. Sai da nayi sallah sannan na tashi Umma ita ma tayi sallah… Bani da aiki yau don haka kwanciya ta nayi na koma bacci. ****** Ranar Daurin Aure💃 Shirye shirye ake ta ko wani bangare da safiyar yau juma’a data kama daurin aure, jiya sukai mother’s eve/kamu bai je ba shi dai su kadai sukai kayan su sai yau da za’a yi dinner karfe 7 gobe asabar suyi yini a kai amarya kuma da daddare. Yana kwance a daki har 12 tayi ana ta shirye shiryen tafiya masallaci tun da sai 2 daurin auren amma shi ya kasa tashi haka kurin yake jin jikin sa yayi masa weak sosai. Musbahu ne ya dala masa duka a cinya yace “baka da kirki wallahi Abdallah ynxu har 12 amma baka yi wanka ba.” Bude idon sa yai da suka masa ja yace “bana jin dadi sosai ne”. Dariya Musbahu yai yana zama a gefen sa yace “ko dai tunanin sabuwar rayuwar da zaka shiga kake, kai ni ban ma yadda da kai ba tunanin Aunty Aasmaa kake koh”. Wani mugun kallo ya jefe wa Musbahun wanda yasa Musbahu mike wa yana kyalkyala dariya. Da kyar ya tashi ya shiga toilet yayi wanka, shiryawa yayi cikin wata farar dakakkiyar shadda maikon da take ne zai fada ma cewa ba karamar shadda bace, yayi kyau sosai sai dai bai sa babbar rigar ba ya rike ta a hannu ne kawai. Shi da Musbahu da sauran friends dinsu ne suka tafi masallacin Umar bin kattap anan za’a daura auren… A cikin gida kuwa fada ne ya kaure tsakanin Meena da Teemah, sbd Teemah din tana wakar bikin su Abdallah da Ali jita yayi musu shine Meena ta mike daga zaunen da take ta sha gaban Teemah tana ce mata da take wakar bikin Abdallah din an fada mata zata damu ne, kuma ta rubuta ta ajiye auren Abdallah ne dole tayi sa ko ba dade ko ba jima. Ita ma Teemah din dama tana Jin haushin Meena sbd lokacin da tayi wa Mami rashin kunya bata zage ta ba tun da Mami ta ha mata kunne don haka tayi dariya cike da tura wa mutun haushi tace a Ina din zaki auri Yayan nawa, ai auren Yaya na sai mace kamila mai daraja ba wacce take raba wa gayu ba. Wannan maganar ta bata wa Meena rai sosai ai kuwa ta shako wuyan Teemah suka kacame da fada, da kyar aka raba su Teemah ta fita zuwa part din Mummy ita kuwa Meena zama tayi a gaban iya tana kuka. Hjy Bilkisu da tayi tagumi tana kallon yadda tilon yar ta take kuka ce tace “don Allah iya ki sa baki Abdallah ya auri Amina, mu ynxu mun amince ma zata je a ta biyun wallahi kuma In sha Allah zasu zauna lafiya”. Iya mace mai daraja da sanin ciwon kai da take zaune cikin shiga ta alfarma tana jan carbi a nutse ba birkicewa irin ta tsoffi ce ta kalli Bilkisu tace “ynxu ke Bilki baki ji kunya ba, duk irin zagi da dibar albarkar da kuka gama wa Uwar yaron nan amma ynxu kice dan ta ya auri yar ki, ba kun ce baxa ku aure sa ba Ina har cewa kika yi dama ke ai rufa masa asiri kikai ynxu kuwa yar ki tafi karfin sa kinga sai kuje ki bawa wadanda basu fi karfin nata ba”. Ihun kuka Meena ta saki tana riko hannun Iya tace “don Allah iya ki tausaya min ki taimake ni ki fada wa Ya Abdallah ya aure ni Wallahi Ina son sa, kishi ne ya rufe min ido a lokacin amma baxan sake ba na yadda zan zauna da Yusrah din Allah ki taimaka iya”. Hade rai iya tayi ta kalli Hajiya Bilkisu data sunkuyar da kai kawai tace “dauke min yar ki daga gabana Bilki tun kafin rai na yayi mugun baci, kin san halina bana daukar rai ni koh don haka ki gode ma Allah ma da ban miki fada ba a cikin jama’a akan abinda kika aikata, ba wai kyale ki nayi ba kawai na miki shiru ne sbd taro ana gama wa kuwa In sha Allah har gida zan zo na same ki mara kunyar banxa da wofi wannan ba tarbiyya ta bace sam”. Daga Meena Hajiya Bilkin tayi tana bawa Iya hakuri suka fita don fa tafi kowa sanin wace mahaifiyar ta bata daukar raini, ita ma data zo bikin tayi mamaki da taji mahaifiyar tata bata maganar abinda sukai ba har ta fara murna cewar maganar bata je kunnen ta ba ashe shiru tayi mata kawai. Ajiyar zuciya ta sauke tana addu’a Allah ya sassauta zuciyar iya ta huce kafin a gama bikin. A dakin Yusrah kuwa suna zaune yan mata da kawayen ta suna tsokanar ta, ita dai tana zaune a gefen gadon cikin wata farar shadda anko Abdallah ya musu ita da shi tayi kyau sosai don dinkin da aka ma shaddar ha haskata sosai, fuskar ta yayi kyau da make-up din da Teema tayi mata tayi kyau sosai kamar ka sace. Zuciyar ta kawai bugawa take tana addu’ar Allah ya tabbatar da alkhairi don ji take kamar za’a ce an fasa auren shiyasa duk ta rasa nutsuwar ta. Karar shigowar message a wayar ta ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, da sauri ta kunna wayar ganin sunan My King❤️💍👑 daya fito, da sauri ta bude message din ta karanta sakon kamar haka “Allah ya bamu zaman lafiya Wife Alhamdulillah” Lumshe ido tayi kawai sai ta janyo mayafinta ta kara yafa wa sosai ta dauki sallayar da take ajiye a gefen ta ta shinfida ta tayar da sallah, raka’a biyu tayi ta dade tana addu’a a sujjada kafin ta d’ago tana kuka. Sai da ta sallame sannan ta juya gurin Ya Walida data shigo ynxu kawai ta sai ta mike da sauri ta fada jikin ta ta saki kuka, cikin kuka tace “an daura Ya Waleeda shikenan na zama Matar Yaya Abdallah..” Guda yan matan suka saki cike da farin ciki…. ***** A wajen daurin auren kuwa sai bayan an daura sannan Umar ya samu damar hango Abdallah a cikin mutane ana musu hoto. Kara sawa gurin sa yayi ya mika masa hannu sukai musabaha, 10k din da Umma ta basa ya bawa Abdallah din ya mika masa yace “gashi inji Umma tace gudummawar tace”. Dan zaro ido Abdallah yayi yace “gaskiya baxan karba ba ka mayar mata da shi Ngd Allah”. Hade rai Umar yayi yace “in baka karba bafa zata ce ka rai na ne”. Ba don ran sa yaso ba ya karba yace “Kace Ngd sosai Allah ya saka da alkhairi, ai anjima zaku zo koh”. Daga kai Umar yayi yace “in sha Allah hadda su Yaya ma duk Umma tace suzo muje”. Murmushi Abdallah yayi yace “ita zata zo”. Kallon sa Umar yayi yana boye murmushin sa yace “wace fah”. Dan hade rai Abdallah yayi yana sosa girar sa yace “wannan mara kunyar mana”. Dariya ce ta kwace wa Umar ba shiri cikin dariya yace “ai ba yadda ta iya Umma tace dole taje”. Wani murmushi ya saki yace “Yauwa kar ka bari ta fito ba hijab kaji kaga gurin hadda maza ita kuwa yadda take bata son rai ni ka tuna mata kaji”. Cikin dariya Umar daga kai yana masa sallama a ransa kuwa addu’a yake Allah yasa su daidaita kan su don fa shi bai ga wanda ya dace da Yayar sa ba sai Abdallah yaron data rai na da alama shi baxai yadda ya zama Mijin tace ba. ******* A gajiye na dawo sbd aikin abincin bikin da muka yi, ban yi mamakin ganin su Yaya da Maryam ba tun da Umma tace musu suzo don Allah aje wa wannan mara kunyar bikin, ni kam ba dan naso ba zan je sai dai kawai sbd yadda Umma ta nuna tayi fushi dole na amsa zanje. Mu hudu zamu ni da Yaya sai Maryam sai Umar sai Basma. Karfe 7 muka shirya gaba dayan mu kowa yayi kyau nima cikin lace red color na shirya doguwar riga ce wacce ta kama ni ba sosai ba amma ta fito da dukkan diri da structure dina, light makeup nayi nasa red jambaki wanda ya min kyau sosai, Hijab na dauka coffee iya gwiwa nasa na fito tun da ni kadai ake jira duk suna tsakar gida. Da mamaki gaba daya suke kallona ganin nasa hijab Yaya ce tace “ba dai da wannan zaki je gurin Dinner din ba Aasmaa”. Cikin rashin damuwa nace “eh mana Yaya ai ba abinda yayi ko yayi datti ne”. Dariya Umar yayi yace “wallahi Ya Aasmaa kamar Abdallah ya san za’a yi hka yace kar ba bari ki fito ba hijab ni dariya ma nayi tun da nasan da Hijab din zaki”. Tsaii nayi Ina kallon sa fuskata a hade, a dakile nace “shi ne yace na kar ka yadda naje ba Hijab”. Daga kai yayi yana dariya kawai na koma ciki na cire hijab din, farin mayafi na dauka amma babba na yafa bayan na gyara daurin dankwali na. Fito wa nayi duka suka bini da kallo ba wanda yace komai dai muka yi wa Umma sallama muka fito. Adaidaita biyu mukai zuwa wajen kafin mu isa har 8 tayi. A tare muka shiga gaba daya idona dai yana kasa Ina tafiya a hankali don gurin ba dai girma ba kuma yadda muka shigo sai aka bimu da ido ana kallon mu. Umar ne yayi mana jagora har zuwa wani table da ba kowa tun da yana daga baya baya ne, gaba dayan mu muka zauna a kai. Abdallah da yake zaune cikin wani dark blue voile ya hade yayi kyau sosai har ya gaji abinka da farar fata ta hadu da abinda ya haskaka ta ya kara fito da hasken fatar sa, gefen sa Yusrah ce wacce ta yi kyau sosai itama tasa light blue gown. Tun da suka shigo idon sa ya sauka akan ta dama kuma tun dazun idon sa na kallon kofa yana jiran shigowar su ai kuwa yayi nadamar kallon nata, yadda ta yafa mayafi ba karamin kona masa rai yayi ba, sai da yaga ta zauna sannan ya sauke ajiyar zuciya yana lumshe ido. Muna zaune muna hira a tsakanin mu ni dai kallo daya nayi wa bangaren da amarya da angon suke ban sake gigin kallon wajen ba don ni kai na ban fahimci dalilin daya sa rai na yake baci ba. Muna zaune mu dai kawai naji sallama daga bayana, dan juya wa nayi idona ya sauka akan wani mutum kallo daya zaka masa kaga kamala a tattare da shi. Murmushi ya sakar min y sake yin sallama, su Yaya ne suka amsa ni dai a saman lips dina na amsa masa. Kujerar dake gefena wacce ba kowa a kai ya kalli Umar yace “zan iya zama kani na”. Dan waro ido Umar yayi yana kallon Aasma data hade rai sosai yace “eh ka zauna”. Murmushi yayi y zauna yana kallona. Fuskar sa dauke da Murmushi yace “barka da hutawa Queen”. Ko kallon sa ban ba sai idona dana mayar kan wayata Ina game. Ya bude baki zai sake magana kawai muka ji daga bayan sa ance “tashi na mayar da ke gida…” Da sauri na juya ganin waye wanna yake bani umarni. Da tsananin mamaki nake kallon sa sai kuma na juya na kalli bangaren da amarya da ango suke, Lumshe ido na nayi na sake bude wa don tabbatar da cewa eh tabbas baya gurin amaryar sace kawai a gurin itama kuma hankalin ta yana kan mu. Muryar sa data ke dauke da bacin ran d yake ji a zuciyar sa ta sake fito wa a kausashe yace tashi na mayar da ke gida tunda amanar ki Umma ta bani…… DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 19 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Muryar sa da take dauke da bacin dan da yake ji a zuciyar sa ta fito a kausashe yace “tashi na mayar da ke gida tunda amanar ki Umma ta bani”. Gaba dayan mu zuba masa ido mukai har ni kuwa, a yadda nake kallon sa so nake na gurza masa rashin mutunci ko dan na goge rainin da yaron nan ya min a kwanyar sa sai dai kuma sabanin hakan ne ya biyo baya don wani irin kwarjini naji yayi min wanda yasa baki na yin nauyi. Ganin yadda muka zuba masa ido ne yasa shi juyawa gurin Umar fuska a hade yace “amma Umar ya muka yi da kai don Allah, ba nace kar ka bari ta fito ba Hijab ba ni da nasan irin shigar da zata yi tazo baxan ma fara tunanin bata card din ba Allah”. Umar da yayi tsifi tsifi don shi kan sa yanayin daya ga Abdallah din ya basa tsoro don haka cikin sauri yace “hijab fa tasa da zamu tafi kawai don na ce mata ai kuwa kace kar tasa mayafi dama shine ta koma ciki ta sa gyale”. Lumshe idonsa yai yana kokarin controlling fushin sa ya bude idon ya zuba wa Aasmaa din wacce ynxu take danna waya hankali kwance. Samun kan sa kawai yayi da magana cikin sanyin da bai san yana da shi ba yace “so kike ki kashe ni ko *Husna*” Wani irin bugawa kirji na yayi har sai da na rufe ido da karfi, salon yadda yayi maganar da sanyi da kuma yadda ya fadi Husna sunan da ba wanda ya taba kirana da shi ya dake ni sosai. Duk kokari na ganin ban kalle sa ba kasa wa nayi sai da na juyo idona ya shiga cikin nasa, da idanun sa ya shiga hora ni don wani kallo yake min wanda yasa na masa janye nawa idon duk kuwa da yadda naso yin hakan amma yaki bani damar janyewar. Kamar wacce aka mintsina kuma ba tuno da auren sa fa ake yi sai ba tabe baki Ina maka masa wata muguwar harara. Dauke idon sa yai daga kan ta ya mai da shi kan mutumin da yake zaune yana kallon su kawai fuskar sa cike da mamaki, sarai ya gane sa Kanin Mummy ne wanda matar sa ta rasu wajen shekaru 5 kenan a gurin haihuwa ta rasu ta bar yaron. Hade rai yayi sosai shi fa ba damuwar sa bace don wai Kanin Mummy ne ko ma waye kawai ya tashi ya daina shakar kamshin Husna ai amanar ta Umma ta basa tun da auren sa suka zo ai. Kara tamke fuska yayi yace “zaka iya tashi daga kan kujerar Alhaji”. Da mamaki Sadam yake kallon Abdallah din ganin kamar bai gane sa ba yace “Abdallah baka gane ni bane Sadam ne fah”. Kankance ido yayi cike da tijara yace Sadam na gane ka mana ka tashi plz kana bata min lokaci. Kafin Sadam yayi magana Musbahu yazo da sauri ya janyo sa, tun dazu yake hango yadda Abdallah din yake magana duk da baya kusa dai amma yasan cewa ai maganar gizo bata wuce koki kawai kishin da har lokacin bai san yana yi bane ya motsa. Bai sake sa ba sai da ya kai sa tsakiyar filin inda Yusrah yake tsaye yan uwa sun zagaye ta suna mata liki, wannan ne dalilin daya sa bata kara neman inda Abdallah din yake ba a tunanin ta ya shiga gurin friends dinsa ne. Mu dai ganin 9 muka tashi muka fito Sadam yana bayan mu, nace min yayi har sai da na basa number na sannan ya kuma yace zai sauke mu gida. Anan kuwa sai da Yaya ta kusa mangare ni sannan na yadda na shiga motar ya ja muka tafi. Da sauri Abdallah daya fito sbd ganin su sun fita kuma Sadam na bayansu yayi baya ganin ta shiga motar Sadam yaja. Da sauri Musbahu ya riko sa yana fadin ka bi a hankali don Allah Abdallah da ka fadi mana. Cire hular kan sa yayi yana fifita jin wani gumi yana keto masa, ganin zafin karuwa yake kawai ya sabe babbar rigar ya rataya a kafada ya shiga zirga zirga a gurin. Shi dai Musbahu ido kawai ya zuba masa cike da tausayi, ynxu abin Abdallah din ya dai na basa dariya ya dawo basa tausayi zai iya cewa tun da yake tare da Abdallah bai taba ganin abinda yake daga masa hankali kamar lamarin Aunty Aasmaa din ba. Ganin Abdallah ya nufi mota yasa shi saurin zuwa gare sa yana rike murfin motar. Da sauri yace “Ina zaka Abdallah?” Daga idonsa da sauka yi jajir yayi yace “gida zan je kai na ke ciwo”. Bai bawa Musbahu damar magana ba ya ja motar a guje ya fice. Shiru Musbahu yayi duk ran sa ba dadi yadda Abdallah din yake yasan ba karamin kaunar Aasmaa din bane ya Kama sa amma bai sani ba, Kai shi fa yadda yasan Abdallah ko ya gane yana son nata baxai yadda ya fada mata ba abin gaba daya a cukurkude yake Abdallah da Aasmaa wacce t girme sa. Gyada Kai Musbahu yai kawai ya shige cikin hall din ko za’a nemi Abdallah zai fada musu cewa ya tai gida kan sa yana ciwo. ******** A hankali rayuwa take tafiya yau fari gobe baki, wata uku kenan da haduwar mu da Sadam a cikin watannin nan duk ranar Saturday sai yazo Umma sai murna take amma su Yaya da Umar basa yin Sadam din wanda ban san dalili ba. Baxan ce bana son Sadam ba kuma baxan ce Ina kin sa ba, yana da faran faran da mutane da kyauta matsalar sa kawai iko tun kafin na shiga gidan sa ya fara dora min doka wai dole in zan fita sai na kira na tambaye sa, a take a lokacin na nuna masa baxan yadda ba don ba a karkashin ikon sa nake ba ya bari In na shiga gidan nasa sai yayi min wannan ikon. Na biyu kuma yadda yake abu kamar yana zargina, ba dama ya kira ni yaji line busy ya dinga fada kenan wai da wa nake waya ko da kuwa da safe ne ko rana, kusan kullum in yazo yana yawan cewa na basa wayata ya buda sai dai kawai na kalle sa na gyada Kai. Wannan halayan nasa yasa ba fara jan jiki da shi don a yadda nake ganin wannan in muka yi auren zan samu matsala dashi, gashi na taba masa maganar ina son in nayi aure ko Mijina baxai yadda ba cigaba da aikin restaurant ba toh zan dinga snacks da abincin biki a gida, a lokacin na nuna min cewa shi dai gaskiya baya bukatar Matar sa ta dinga sana’ar komai wai in mace na samun kudi bata girmama mijin ta sosai. Wannan halayen nasa na fada wa Umma duk abinda yake fadawa ta kwantar min da hankali tace na cigaba da addu’a Allah ya zaba abinda yafi alkhairi. Ba wai Alhaji Inuwa ko Kabeer sun dai na kira na bane kiran Alh Inuwa dai Ina dagawa time to time na Kabir ne gaba daya ban daga wa amma kamar maye kullum da message dinsa nake farkawa na good morning da kuma wanda yake min da daddare. Ni kai na nasan Kabeer yana sona kuma Ina tausayin sa wallahi har rai na da ace ba Hajjo bace matar sa da zan iya auren sa don na shaida soyyaya yake min ta gaskiya amma kuma baxan iya auren nan ba ai ana barin halak ko dan kunya, tausayin sa da nake ji ne yasa nima in na bushi iska nake masa text akan yayi hakuri ya mai da hankalin sa kan matar sa don ni dai baxan iya auren sa ba, a kullum reply dinsa shine bkm yana jira in naga ya rabu da ni to aure aka daura min da wani. ****** HAJJO Wata ukun nan sun zo mata cikin rashin walwala gaba daya lamarin gidan ta ya tabarbare ita da kan ta Ynxu ta fara tunanin zata je ta roki Aasmaa data auri Mijin ta ko zata samu nutsuwar zuciya. Kabeer ya chanja mata gaba daya taba da labarin cewa aure yake nema tun da kanwar sa ta hannun daman tace kuma ta fada mata yarinyar bata da kunya wallahi amma haka kullum dare sai yaje zance gurin ta kuma shi ne yake kai ta unguwa. Ranar data samu labarin nan ba karamin tashi hankalin ta yayi ba da tayi confronting din sa sai ce masa yayi eh zance yake kuma budurwar sace ya raba kafa ne don in Aasmaa bata amince ba ya auri yarinyar. Hankalin Hajjo ya tashi sosai ta dinga basa hakuri akan ya bar yarinyar wallahi ta amince ya auri Aasmaa din zasu zauna lafiya amma ko uhm bai ce mata ba ya fice daga gidan. Shi da kan sa yasan dama dole Hajjon Zata ji haka tun da tana son sa kuma tana kishin sa da ace ma shi tayi wa tiijarar zai dinga lallaba tane amma Aasmaa taje tayi wa diban albarka hadda kiran ta da karuwa wanna kalmar tafi komai bata masa rai. Kuma shi tun farko dama yana da ra’ayin zama da mace biyu ko dan karfin sha’awar da yake da ita, yarinyar ma da yake zuwa gurin ta ba wai son ta yake ba sosai kawai sbd sunan Aasman sace da ita Asma’u kuma itama tana yawan sa Hijab shiyasa yaji ta kwanta masa. Ya sauko ynxun tun da yana cin abincin ta in ta girka kuma suna kwana a daki daya amma kullum a darare Hajjo take tana dana sanin amincewa da maganar Ummu wai a haka don Aasmaa din bata fada masa kalar zagin da ta dinga tura mata ba a group dinsu na school ta shiga ta fada musu Aasmaa din tana nemar mata miji har yana mata barazanar rabuwa da ita akan Aasmaa din haka suka hadu da Hajjon da wasu mates dinsu suka dinga zagin Aasmaa suna ce mata karuwa shiyasa taki aure sbd tsaya karbe wa maza Jen mutane kudi, in ku da kuke karanta wa kun tanka musu Aasmaa ta tanka, banxa ta musu kuma bata fita daga group din ba har suka gaji suka gama ganin wacce suke na din ta bawa banza ajiyar su.. DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 20 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Yusrah da Abdallah amarci suke ci sosai hankali kwance, yadda Yusrah tayi tunanin zata samu Abdallah ba haka ta same sa ba don ta dauka bai iya wani soyayya ba amma kuma sai gashi yadda yake tattalin ta wani lokacin har hawaye take yi in ta shiga daki. Duk da ba wai hira yake mata sosai ba don miskilancin sa yana nan amma ita in tana masa yana bata attention dinsa ya saurare ta, kuma a ynxu tana ganin murmushin sa sosai har ma da dariya wani lokacin bama in yana tsokanar ta a ozar room. Tana iya bakin kokarin ta taga yana samun gamsuwa da ita a ozar room tun da ta fahimci shi mutum ne mai yawan bukata kullum ne dai sai anja zuwaira ba fashi. Cikin wata ukun nan daga shi har ita sunyi wani fresh sun kara kiba abinsu kana kallon su dai kaga sabbin auren da suke zaune cikin nutsuwa. Abdallah kuwa shi kadai yasan irin azabtuwar da yake yi don kawai ya yakice tunanin ta a ran sa ya man ta da ita amma kamar wacce take masa asiri kullum tunanin ta yake duk abinda yake ita ce a makale a ran sa yana bakin kokarin sa na ganin wannan sabuwar halayyar tasa bata shafi zaman sa da Yusrah ba. Yana girmama Yusrah sosai sbd yadda yake kula da dukkan lamarin sa, a ynxu kuwa in yace baya son Yusrah ma ai yayi karya ta riga ta gama samun wani guri a zuciyar sa ta zauna, yana alfahari da ita sosai kuma yana godiya ga Allah daya sa ya ta zama matar sa. ****** Yau hutun karshen wata nake ina zaune Ina kwaba mana flour zanyi mana wainar fulawa Kash ya shigo ko sallama bai yi ba. Da sauri na daga na kalle sa gaba na yana faduwa, ganin mugun kallon da yake min yasa ni saurin sunkuyar da kai kasa cikin rawar baki nace “Kawu Ina wuni”. Yatsina Fuska yayi yace “rike gaisuwar ki bana bukata”. Kallon Umma yai wacce tun da y shigo kallo daya ta masa ta dauke Kai tana tabe baki, zuwan sa tasan mu ba alkhairi bane a rayuwar su duk lokacin daya zo to fa da wani tashin hankalin yake zuwa, yadda ta karye ya sani ba wai bai sani ba tun da dan da yazo ya duba ta amma shi ko Kira bai yi ba kuma matar sa taba zo ba, bata damu ba dama ita Umar ne ma yayi ta kunkuni shima kuma a take a gurin ta taka masa burki maganar ta wuce. Hade fuska kawu yayi yace “zuwa nayi na fada muku ku fara shirin auren da wannan tsohuwar guzumar, yau an zo an kawo kudin auren Binta(Autar sa ce shekarun ta goma sha bakwai)kuma basa son auren ya dau lokaci wata daya da sati biyu nasa don haka na riga na gama magana auren ta da Asma’u zan hada dama su biyu ne kadai mata da suka rage min na aurar don haka tare zan hada ayi bikin nasu na huta da kawo min tsegumin cewa anan ganin wacce banxar tana yawo”. Mai da duban sa kan Aasmaa yayi wacce ta rike ludayin hannun ta gam ta rintse ido, a dake yace “na baki sati daya ki kawo min wanda kike son aura in sati ya wuce na rantse da girman Allah kudin Alh Inuwa zan karba da shi za’a yi auren kuma kinji dai yadda na rantse miki ko, to ko kina so ko bakya so sai kin aure sa in har ni ne nan madaurin auren ki”. Daga haka ya juya ya fice daga gidan yana baxa babbar rigar sa don ma kar su kawo masa raini, a iya sanin sa Aasmaa din bata da saurayi sai ko Alh Inuwa don haka ya shirya tsaf don ya kona musu rai daga ita har uwar tata ya aura mata Alh Inuwa. Daga ni har Umma din shiru mukai cike da tashin hankali, ni dai na hanga ban gano mafita ba Sadam baxan iya auren sa ba ko dan halayen sa shi kuwa Kabeer dama baya lissafi sai kuwa Alh Inuwa din shi Alh Inuwa bashi da makusa kawai dai shekarun sa ne uwar gidan sa Kawar Umma ce a da kafin Alh Inuwa ya fara neman aure na ta daina shiga harkar Umma, yana da yara da suka girme ni ma don a shekarar data wuce na ya aurar da jikokin sa mata har biyu, Ynxu in na aure sa a maganar shinfida anya baxan cuci kai na ba. Ita kuwa Umma tunanin yadda zata bullo wa lamarin take, Kawu ta san sa mutum ne mai mafisar tsiya baya jin maganar kowa ta taba hada sa da Liman akan yadda yaso yayi wa Aasmaa din auren karfa karfa da yadda ya takura mata. Rashin kunya da yayi wa Liman yasa bata kara sa Liman a lamarin su ba ko dan ya tsira da mutuncin sa. Kallo na tayi yadda na sunkuyar da kai kasa Ina kwaba flour din ba karamin tausayi ta bata ba, don haka ta mike ta isa gare ta. Sosai Umma tayi mun nasiha akan na dage da addu’a komai yayi farko zai yi karshe. Tun da Kawu yazo mana da wannan maganar na rasa nutsuwa ta, na rame sosai a cikin kwana 6 na kara baki don bani da nutsuwar kula da jikina, wanka kawai nake na shirya na fita aiki, a gurin aikin ne kadai nake dan samun nutsuwa. Su Umma ma dasu Yaya duka hankalin su a tashe yake ba Wanda yake son aure na da Alhaji Inuwa amma ya zamu yi, da Umma taje gurin Kanin ta da maganar cewa yayi muyi ta addu’a kawai don shi kan sa yasha zuwa gurin Kawu din yana wulakanta sa. Da Umma tasa masa kuka ne yace mata zai je gurin Kawun ya basa hakuri amma da yaje ma karshe da bacin rai ya dawo sbd munanan maganganun da Kawun ya fada masa har ce masa yayi wai ko sune suke amfani da Aasmaa din shiyasa basa son tayi aure, wannan maganar ta kara daga mana hankali matuka. Ynxu haka ma tunanin cewa gobe ne ranar da Kawu ya bani ta karshe yasa hankali na tashi sosai, Ina zaune a bayan kitchen ni kadai da waya a hannu na tunani nake na Kira Sadam na fada masa cewa na amince zan aure sa ko kuwa.. DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 21 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tako wa yake a hankali don ya wanke hannun sa da zobo ya bata, gware suka yi da wani da alama shigowa restaurant din yayi ya shiga zobon kuma ya fara sha a ciki shine ya fito da shi a hannu ya zuba masa yana danna waya bai kula ba. Tsaki ya kara ja a hankali, tun da yayi aure bai kara zuwa restaurant din ba sai yau da tunanin ta ya addabe sa shi ne ya ce dai bara yazo ko bai ganta ba yaci shawarmar ta. Bayan inda aka nuna masa cewa da akwai ruwa ya nufa a nutse, yana zira kan sa a lungun idon sa ya sauka akan ta tana zaune akan farar kujera hannun ta rike da waya tana kuka. Gabansa yaji ya buga da karfi dan kara daga kafa yayi har ya isa kusa da ita bata san ya zo ba sbd yadda tayi nisa a tunani. Kamar a mafarki naji muryar sa muryar mutumin da shi kadai ne yake kira na da wannan sunan yace “Husnaa” D’ago wa nayi da sauri na kalle sa yana tsaye ya zuba hannayen sa cikin aljihun wandon sa yana kallona, da sauri nasa hannu na goge hawayen amma Ina wasu ne suke zubo wa da zafin su, kyale su nayi kawai su zuba tun da ko na goge sai sun kara zubowar. Lumshe idon sa yayi har cikin ran sa yake jin zafin hawayen nata, a hankali ya janyo kujerar dake gefenta ya zauna ya fito da wayar sa yana dannawa. Mun dauki tsawon lokaci a haka ba wanda ya sake wa kowa magana, ganin dai baza ta daina kukan ba yasa shi mayar da wayar aljihun sa ya zuba mata sexy eyes dinsa. Cikin husky voice yace “Husnaaa…” Yadda yaja sunan dole na d’ago na saka idona a cikin nasa, kalar duban da yake min ne yasa naji wani rauni wanda nake ta kokarin boyewa yana taso wa kawai nasa hannu na rufe fuska na fashe kuka. Cikin kuka nace “ kawai sbd anga mahaifina baya raye sai a daura min tsana, auren nan da ban yi lokaci nane bai yi ba ni ma ai ba’a san rai na nake zaune har wannan lokacin ban yi aure ba”. Kallon ta yake yana sauke ajiyar zuciya, ya dauka wani babban abu ne ya faru shiyasa yaji ya kasa nutsuwa har sai da ya zauna a gurin. A nutse yace “waye ya takura miki Husnaa”. Cikin sheshekar kuka nace “Kawu ne yace ya bani sati daya na fitar da miji don aure zai yi min nan da sati 5 gashi kuma ni bana kula kowa yace in ban fito da miji ba zai aura min Alh Inuwa don Allah taya za’a aura min tsohon nan wallahi ya tsufa ba abinda zai iya min kawai zaman hakuri zan yi in kuma na kasa hakura fa”. Dan ware ido Abdallah yai yana kallon ta yana sakin wani shegen murmushin da shi kadai yasan abinda yake nufi. Cikin kuka na ceh “kawai sbd ban yi aure ba shikenan sai a dinga min kallon mara kamun kai karuwa, ynxu ya zan yi da rayuwa ta dama su biyu ne sai Sadam”. Wani irin bugawa kirjin Abdallah yayi jin ta ambaci Sadam, bai san lokacin da yace “dama kuma tare da Sadam ne”. Daga masa kai nayi hawaye yana zubo min nace “baxan iya auren sa ba amma sbd tsauraran ra’ayin sa, sai kuwa Kabeer dama shi bana sa shi a lissafi Mijin aminiya tace a da don ynxu mun rabu tun da taji Mijin nata yana so na”. Gyara zama Abdallah yayi yace “ynxu dai shi Kawun yace nan da 5 weeks zai miki aure in baki fito da shi tsohon can in baki fito da miji ba right”. Daga kai nayi Ina lumshe ido wasu hawayen suna zubo min, nace “eh haka yace ya bani 1week na fito da miji in ba haka ba zai karbi kudin Alh Inuwa gashi gobe ne cikar sati dayan ban san yadda zan yi ba, kawai Ina tunanin zan fada wa Sadam y turo din kawai tun da kaga gwanda na aure sa da na auri Alh Inuwa ko?”. Hankali kwance Abdallah yace “Ina da shawara da kuma yadda za’a yi” Da sauri na d’ago na kalle sa Ina goge hawayena nace “plz fada min meye mafita duk kai na ya toshe Allah”. Gyara zaman sa yayi yana kallon ta cikin ido yace “ki aure ni kawai.” Da sauri na shiga jefa masa wani banxan kallon daya sa murmushi subuce masa bai shirya ba. Juyar da kai yayi yana kokarin hana kan sa murmushi yace “kin ga dukkan su baki son auren su, kuma ni ba wai zan aure ki bane don Ina son ki ko nayi zaman aure da ke ba”. Girgiza kai yayi yace 0sam kawai zan aure ki ne don kada Kawun ki yayi miki auren da bakya so, kin ga in muka yi auren bayan kamar shekara sai na sake ki ki koma gida a lokacin Kawun ki bai isa ya miki auren dole ba sbd ke bazawara ce kina da damar da zaki zabin Mijin auren ki”. Shiru nayi Ina kallon sa Ina tunani, duk abinda ya fada haka ne amma kuma in naje yaki saki na fa, kuma kawai sai mutane suga an aura min wannan yaron gashi fa bai dade da aure ba. Ajiyar zuciya na sauke nace “kawai to sai na aure ka meye ma zai tabbatar min da cewa zaka sake ni nan da shekara daya”. Baya yayi yana tabe baki yace “kin san bana son ki kuma ke ma ai bakya sona to akan meye zamu zauna tare muna cutar juna”. Gyada kai nayi nace “toh Matar ka fa kaga baka dade da aure ba kuma ace ka sake wani nan da 5 weeks”. Sai da gabansa ya fadi data ambaci matar sa, shi Wallahi ya ma manta da yana da wata Matar a gida burin sa kawai ta amince masa shikenan. Shafa gemun sa yayi yace “zan fahimtar da ita kuma zata fahimta in sha Allah, ai ko gurin Abban da zanje ce masa zanyi kawun ki ne yace in ban fito ba zai aurar dake ga wani”. Shiru nayi Ina tunanin mafita duk inda na juya na juya akan shi kawai mafitar take kaga in ya sake ni sai naje nayi aure na daga baya in Allah ya kawo min miji dai dai da ni. Daga kai nayi Ina hade rai nace “na yadda amma fa ba haka yake nufin cewa zaka rai na niba kasan dai na girme ka koh”. Gyada kai kawai yayi yace “kuma kar ki fada wa kowa ni ma baxan fada wa kowa ba ya zama sirri a tsakanin mu, kin ga in har kika fada wa wani zasu san yadda zasu yi su hana mu rabuwa”. Bai kyale ta ba dai da ya tabbatar ta gamsu iya gamsuwa sannan ya karbi numbern wayar ta. Jiran ta yayi har sai da ta gama abinda zata yi sannan ta shiga motar suka tafi gida don a yau suke son ya je gidan Kawu….. Yawan comment yawan typing💃 DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 22 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM A tare muka shiga gidan ina gaba yana bina a baya, dan turus nayi ganin Yaya da Maryam wacce take rike da jaririn ta tana basa madara sai Umma da Umar a zaune da alama magana suke mai muhimmanci. Dukkan su zuba mana ido sukai ganin haka yasa na shigo Ina yake gabana ban da faduwa ba abinda yake yi, tsoro na kar Umma ta dago shirin mu shiyasa duk nake ji na wani iri. Gaisawa muka yi da su na shige daki nace bara na chanja Kaya. Su dai nasu ido don yadda nake ta wani abu kamar mara gaskiya. Abdallah da yake zaune a kusa da Umar ya kalli Umma yace “Umma magana ce mai muhimmanci nazo da ita”. Mai da hankali Umma tayi kan sa tace “Ina jin ka Babana Allah yasa dai lafiya”. Dan sosa girar sa yayi yana sunkuyar da kai haka kurin yaje Jin wani nauyin ta a ran sa. Da mamaki Umma take kallon sa yadda yake yi din ya nuna kunya yake ji a akan abinda zai fada. Da kyar ya jawo dauriya yace “dama mun daidaita kan mu ne da Husnaa..” Zaro ido yaya tayi tace “wace Husna din?” Dan kallon ta yayi ganin mamaki sosai a fuskar ta yasa ta fuske yace “Husna dai ta gidan nan”. Umma da take zaune kamar an dasa ta kasa gane komai jira take yayi mata bayani wace Husna sai ji tayi yace ta gidan nan ita dai tasan Asma’u Husna daya ce a gidan nan kuma a yadda ta san Aasmaa baxa ta taba soyayya da kanin bayan ta ba. Ganin dai dukkan su mamaki ya kama su yasa shi gyara zama yace “Umma ai tun kafin ki samu hatsari dama na san ta a restaurant din su kullum nan nake zuwa cin shawarma toh ita kuma taki kula ni sbd tana ganin nayi mata yaro da ywa”. Dan tabe fuska yayi kalar tausayi yace “kwatsam kuma sai gani a gidan nan, toh daga nan dai na cigaba da takura mata har ta yadda take dan kula ni muyi hira a waya shima sai da aka kafa mun sharuda”. Sosa kai yayi yana mamakin kan sa shifa bai iya karya ba gaskiya amma ji bi yadda ya zauna yana tsara zance kamar ya faru da gaske. Maryam data matsu taji cigaban maganar sa tace “muna ji Yaya Abdallah”. Watsa mata idon sa yayi jin ta Kira sa da yaya shi fa a iya sanin sa Abdallah take ce masa wato don yace yayar ta yake so shine zata fara ce masa wani Yaya ba, lumshe ido yai yana hasaso sai na sun ganta da cikin sa tukunna🏃‍♀️🏃‍♀️ “Cikin haka maganar aure na da Yusrah ya taso, nayi tunanin zata fara university ne kamar yadda muka tsara sai kuma wani dalili yasa aka mana auren, a so na da in auren ya tashi na hada su biyun na aura hakan bai yi ba”. Yusrah kanwa tace “mahaifin ta shine a matsayin mahaifina, mijin Mamina neh kuma aminin baba na”. Dan shiru yayi don tuno da cewa ko fuskar mahaifin nasa bai taba gani ba sai a hota kuma shima baban nasa bai san me aka Haifa masa ba mace ko namiji. D’ago wa yayi yana murmushi don boye abin da yake taso masa yace “mahaifina ya rasu tun kafin nazo duniya, ni kadai ne dan sa sai ynxu da Mami ta haifa min wasu yan uwan”. “Baxan boye muku ba Ina son Yusrah matata kuma ba wai don ta rage ni d komai zan kara aure ba tun da can kafin na aure ta dama Ina son auren Husna”. “A cikin satin nan naga tana cikin damuwa ko waya muke bata bani attention shiyasa na je gurin aikin ta yau take sanar da ni maganar kawu shine nazo in kin amince Umma mune tare ni da Umar yau gurin Kawun gobe in sha Allah manya na zasu zo ayi maganar auren”. Ajiyar zuciya ya sauka yana Jin kumatun sa na dan masa zugi sbd maganar da yayi da yawa. Umma kuwa murmushi kawai take yi tana fadin Alhamdulillah a ran ta, hankalin ta bai kara kwanciya da Abdallahn ba sai da yace yana son Matar sa kuma ba abinda ta rage sa da shi wannan yana nuna ko gaba zai kara wani auren baxai wulakanta mata Aasmaa din ba. Mike wa tayi kawai ta shiga daki, duk bin ta da kallo sukai kowa yana addu’ar Allah yasa ta amince don su fa dama tuni suke fatan wannan abin ya tabbata. Karo muka yi da Umma don Ina labe a jikin kofa ina jin yadda yake tsaro zance Ina addu’ar Allah yasa kar ya kwafsa, da yace wai yana son Matar sa tabe baki kawai nayi Ina kokayar maganar tasa don haka kurin naji rai na ya dan sosu. Kallona Umma take kallon daya sa na ji kunya ta Kama ni nayi saurin matsawa baya. Murmushi tayi tace zauna Aasmaa magana zamu yi. Gyada kai nayi na zauna akan sallayar dake shinfide akan red carpet din palon. Ita ma zama tayi tana kallona tace “yaushe kuka fara soyayya da babana amma ban sani ba kuma da alama a cikin yan uwan ki ba wanda ya sani shima”. Kara sunkuyar da kai nayi gaba na yana faduwa, da kyar na bude baki cikin rawar murya nace “gani nake kamar za’a min dariya ne Umma tun da na gama cika baki baxan yi soyayya da mai karancin shekaru ba”. Murmushin manya Umma tayi tana hasaso wani abu a maganar su amma kuma koma meye tun da dai aure suka so suyi zata yi ta addu’a Allah ya tabbatar da alkhairi ya kuma zaunar da su lafiya har karshen rayuwar su. “Nasan kinji duk abinda babana ya fada ynxu in har kin yadda zaki aure sa zasu je gurin Kawun ki kuma zai sanar da gida gobe azo ayi maganar aure kin yadda”. Hawaye naji yana kokarin zubo min ga yadda gaba na yake faduwa ynxu in na yadda shikenan haka kowa zai dinga kallo na ana min dariya cewa zan auri yaro, tuno maganar mu da shi ne yasa na daga wa Umma kai kawai Ina mike wa na shige daki da sauri. Hannu Umma ta daga tayi addu’a hawaye yana zubo mata, hawaye ne na farin ciki yau Aasmaa ta amince zata auri wani Alhamdulillah Ya Rabbi. Fito wa tayi fuskar ta dauke da murmushi tace “nayi magana da ita Babana kuje tare da Umar din gurin Kawun naku Allah ya tabbatar da alkhairi”. Wani guda Yaya da Maryama suka saki a tare suna cewa Alhamdulillah. Shi kan sa Umar murmushi kawai yake yi yana addu’ar Allah ya tabbatar da alkhairi. Tare suka fita a motar Abdallah Umar na nuna masa hanya har suka isa gidan Kawun. A kofar gida suka tsaya Umar ya aiki yaron Kawun ya ma kawu magana yana tare da bako. Suna tsaye kusan minti 10 sannan kawu ya fito yana fadin “meye kuma zaka wani zo da sanyin magribar nan to in ma kudi kuke bukata bani da shi”. Kunya da takaici ne suka hadu suka rufe Umar, kamar yayi kuka don takaici yake kallon Kawu. Gaisawa sukai da shi yana kallon Abdallah yana mamakin meye hadin wannan balaraben da Umar kuma. Umar ne ya nuna Abdallah yace “kawu dama wannan shine saurayin Yaya Aasmaa yazo ne don ka gansa kamar yadda ka bata lokaci kuma yana so gobe ya turo iyayen sa”. Zaro ido Kawu yayi cikin tashin hankali yace “Kace shine saurayin Asma’u kuma”. Daga kai Umar yayi cikin tabbatar wa. Goge gumi Kawu y shiga yi cikin tashin hankali shifa ya fada ne amma bai taba tunanin Asma’u din tana da saurayi ba, ya riga ya sakankance Alh Inuwa zai aura mata ko dan ya cigaba da karbar kudi a gurin sa. Bude baki yayi zai yi magana Abdallah daya zuba masa ido kawai ya Mika masa bandir din 500 , 50k kenan. Cikin rawar jiki Kawu ya damke kudin yana mici mici da ido yace “kudin zancen ne ka bayar ynxu na dauka dai iyayen ka sun zo ai”. Girgiza kai Abdallah yayi yace “Baka nayi ka sayi goro”. Zaro ido kawu yayi yana manne kudin a hammatar sa yace “duka ni ka bawa dubu hamsin ne fah”. Daga masa Kai kawai Abdallah yayi. Murmushi ne ya kwace wa Kawu yace “Sannu da zuwa Alhaji ai kayi hakuri dazu ban ma tarba mai kyau ba na zata irin samarin nan ne masu lalata yaran mutane ashe da gaske kake auren ne ya kawo ka”. Shiru Kawu yayi yana tunanin yadda zai kara karbar wasu kudin a hannun Abdallah, ai shi yadda Abdallah ya masa kyauta dubu hamsin tashi daya Wallahi Aasmaa ko bata son sa sai ya aura masa ita, duk tsawon kyautar da Alh Inuwa yake masa in aka hada baza su kai 20k ba gashi tashi daya an basa 50k ai gaba ta kai sa. Kallon Abdallah yayi yace “dama ban so fada maka ba amma ganin zaka aure ta y Kama ta na fada maka, da akwai kudin zancen ta dana karba a gurin wani wanda yake son ta, a tunani na bata da wani saurayi sai na karba kuma aka samu matsala kudin na cika na bayar a fara mata gado, kaga ynxu bansan yadda zan yi na mayar masa da kudin ba”. Umar ne yayi saurin kallon Abdallah yaga mai zai yi ji yake kuwa kamar ya daura hannu a ka ya dinga zabga Ihu yana kukan bakin cikin da kawu ya jawo musu. Murmushi Abdallah yayi yace “nawa ne kudin Kawu”. Washe baki Kawu yayi yace “dubu dari ne dannan”. Gyada kai Abdallah kawai yayi ya nufi gurin motar sa bai dade ba ya dawo hannun sa rike da rafar 1k guda biyu. Mika wa Kawun yayi yace gashi ka basa kudin sa ragowar kuma a sha ruwa. Godiya kawu y shiga masa har yana yi kamar zai durkusa kasa. Shi dai Abdallah bai ce komai ba sai jan hannun Umar da yayi suka wuce suka bar Kawu yana ta zabga godiya. Kawu kuwa kudin kawai yake yana tunanin yadda zai shiga gari ya zabo cancareriyar budurwa yayi wuf da ita… A bakin layi ya sauke Umar ya wuce gida gabansu don samun Alhaji gabansa yana faduwa bawai fada wa Alhajin ne yake kayar masa da gaba ba sai Yusrah daya ke tuno wa…. Kuma ganin Alhaji da Mami zasu yadda Ya Yusrah zata ji💔🥹 DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 23 Dedicated to Maman Rumana❤️ Uwa ta gari Allah ya tsare ki a duk inda kike ya raya miki zuri’ar ki Ina alfahari da ke Mama❤️🥹 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Jikin sa a sanyaye ya shiga cikin gidan, bai nufi ko Ina ba sai part din Alhaji. Da Sallama ya shiga palon sai dai yayi dana sanin shigowar don kuwa Alhaji ne zaune tare da Mami tana yanka masa fruit a wani plate mai kyau suna hira. Ganin yadda ya tsaya a bakin kofar ne yasa Alhaji cewa ka shigo mana Abdallah. Murmushin yake yayi ya shigo ciki a hankali, yaso matuka ace bai samu Mamin anan ba don yaso ace sai ya gama da Alhajin ya kuma amince sannan zai tunkari Mamin. Gaishe su yayi ya ja gefe yayi shiru ya zuba wa TV ido yana kallon news bawai don yana fahimta ba. Kallon juna Alhaji da Mami sukai kafin Alhaji ya budi baki yace “son”. Juyo wa Abdallah yayi ya zuba masa idon sa da sukai jawur. Murmushi Alhaji ya masa yace “mene yake damun ka son, ka fada mana damuwar ka kaji kaga gani ga mahaifiyar ka a zaune, tun da ka shigo na lura hankalin ka a tashe yake kuma magana ce a bakin ba”. Ajiyar zuciya Abdallah yayi ya dan saci kallon Mami, kawar da kan sa yayi ganin yadda ta zuba masa ido tana kallon sa. Jikin sa duk sanyaye don sai ynxu yaga wautar abin da yayi amma kuma in ya tuna da cewa Husnaa za’a aura ma wani sai yaji eh tabbas abinda yayi shine dai dai, da za’a aura mata wani ya tabbata haukace wa kawai zai yi. Kara sauke ajiyar zuciya yayi yace “Alhaji abinda ke tafe da ni nasan ba yadda zai muku dadi amma don Allah kuyi hakuri dai”. Murmushin karfin hali Mami tayi tace “muna sauraran ka”. Sunkuyar da kai yayi murya a tausashe yace “dama kafin na auri Yusrah akwai wacce muke soyayya”. Dan dagowa yayi yaga yadda iyayen nasa duk suka zuba masa ido, yana kallon yadda Mami take masa da ido alamun yayi shiru kar ya cigaba shi dai ya kawar da kai kawai. Lumshe ido yayi yace “a da nayi tunanin zan aure su ne su biyu a lokaci daya toh komai sai ya chanja na auri Yusrah din, muna tare da ita na mata alkawarin bayan 2years zan aure ta toh ynxu matsala aka samu mahaifin ta ya rasu Abba, Kawun ta ya bata sati daya ta fito da miji in ba haka ba zai aura mata wani tsoho da yake nacin zuwa gurin sa”. “Yau ne kwana shida dazu naje gurin sa na gaishe sa shine yace ba turo iyayena a gobe cikar sati, in ba haka ba jibi zai karbi kudin tsohon can, kuma auren ya hada dana yar sa ne nan da sati 5 yake so ayi”. Mike wa Mami tayi da sauri tace “wallahi baka isa ba, sbd kana so ka jawo min zagi Abdallah so kake ace sbd kana auran yar kishiya ta shine na zuga ka zaka sake aure yarinya ko rabin shekara bata yi ba to bada yawu na ba baxan taba yadda ba Wallahi ne yarinyar nan ta maka da zaka saka mata da wannan abun Abdallah”. Alhaji ne ya Kira sunan ta a nutse, idonta daya soma tara hawaye yake kalla, bakin cikin ta shine wani irin zagi zata sha ga Hajiya Bilki kusan kullum tana hanyar gidan tana cewa tayi hakuri ta sa Abdallah ya auri Meena wai Meena din duk ta zabga bata da aiki sai kuka ita dai sai dai tace mata tayi hakuri in Abdallah ya sauko zata masa magana ba wai don zata masa maganar ba kuwa don tuni ta gode Allah daya sa Abdallah din bai auri Meena din ba yarinyar Sam bata da tarbiyya. Ko mawa tayi ta zauna tana kara hade rai sosai Murmushi Alhaji yayi yace “Hajiya shin kallon baban Yusrah kike min kawai bakya kallona a matsayin baban Abdallah ko dan sbd bani ne ainahin mahaifin sa ba”. Da sauri Mami ta juyo tace “Subhanallahi haba Alhaji taya zaka yi wannan maganar don Allah”. Murmushi yayi yace “in har kina kallona a matsayin mahaifin Abdallah me yasa zaki ce bada yawun ki ba, Haba Maimuna ban san ki da haka ba, yaron nan kin ji abinda ya fada dama can suna tare da yarinyar nan kuma ynxu ga abinda Kawun ta yace so kike yana kallo ya rasa masoyiyar sa, yana da inda zai sa ta ba wai bashi da shi ba zai iya dauke mata dukkan bukatun ta kiyi hakuri don Allah ki bisu da addu’a kawai kin ji”. Gyada kai tayi ta mike ya fice daga palon ta wuce bangaren ta. Kallon Abdallah Alhaji yayi yace ka kwantar da hankalin ka kaji gobe in sha Allah ni da Alhaji Muhammad(baban Musbahu) zamu je muyi maganar auren kuma in sha Allah baxa a daga ranar auren ba kaji. Gyada kai Abdallah yayi kunya ta gama lullube sa har bai san yadda zai daga ido ya kalli Alhajin ba. Tunanin Yusrah daya fado masa ne yasa shi Jin wata faduwar gaba, dagowa yayi a hankali ya kalli Alhaji yace “Abba don Allah ka fada wa Yusrah kaji”. Murmushi Alhaji yayi anzo inda yake so tun da aka fara maganar yake tunanin ta ko ya zata ji in maganar ta isa gare ta, kuma daga dukkan alamu ko wace Abdallah din yake son aura ba karamin kauna yake mata ba don kana iya gani a idon sa yadda yake maganar cike da shaukin da shi kan sa bai san yanayi ba, tsoro yake ji kar Abdallah da Matar da zai aura su wulakanta Yusrah din tunda ai yafi kowa sanin cewa Abdallah baya son Yusrah ya aure ta ne kawai sbd ya taimake ta. Gyara zama Alhaji yayi yace “Abdallah shawara zan baka shine a yau in ka isa gida ka zaunar da Matar ka ka fada mata zancen auren da zaka yi, matukar ka bari gari ya waye muka je muka kai kudin gaisuwa to labari zai basu ne kuma tabbas wasu zasu iya kiran ta su fada mata, kasan mata kafin kai ka zaunar da ita za’a iya hure mata kunne shiyasa nake baka shawara ka zaunar da ita ka fada mata da bakin ka ace daga kai ta fara ji”. Kan sa a kasa yace “baxan iya ba Abba tsoro da kunyar ta nake ji nace mata zan kara aure bana son na bata mata rai Abba”. Wani sassanyar murmushi Alhaji ya yi yana sauke ajiyar zuciya, lallaba Abdallah yayi da yan dabaru da yadda zai tunkari Yusrah din sannan yace masa kar ya shiga gurin Mami ya wuce gidan sa kawai zai fada masa lokacin daya kamata ya je gurin ta amma a ynxu dai yayi wa gidan kaura. Fita yai daga gidan sai da ya tsaya gidan su Musbahu ya fada masa auren da zai kara kuma Aasmaa ce amma ya boye masa yarjeje niyar da sukai, sosai Musbahu yayi mamakin yadda Aasmaa ta yadda har suke soyayya gashi zasu yi aure, daga baya kuma suka gangaro kan Yusrah, shima kwarin gwiwa ya basa sukai Sallama ya wuce gida. ******* Ni kuwa yinin ranar su Yaya saka ni a gaba sukai suna min tsiya sai murna suke yi, in na kalli yadda suke murna sai naji kamar na yaudare su tun da basu san yadda auren zai kasance ba. Umma kuwa sai nan nan take da ni tana lissafa kudin shanun ta da zata siyar da filin ta don a samu ayi wa Aasmaa din Kayan daki, ita kadai ce ta rage mata don haka take son komai tayi sa yadda zai burge Aasmaa din. Murmushi kawai Yaya take yi tace “Umma ai Kayan kitchen ki cire su a lissafi don mun gama siyan Kayan kitchen komai an siya, suna ajiye a gida na fa a store a kudin albashin ta take ciro wa tana kawo min, kuma ni ma in naga wani abu ya burge ni siya mata nake, zannuwan gado ma duk mun gama da wadannan ai dama, ynxu kawai Kayan furnitures zamu mayar da hankali koh Umma tun da bikin cikin lokaci kankani ne”. Murmushi Umma tayi tace “Allah yayi miki albarka dai ya zaunar da ku lafiya a gidajen ku, ya kara muku zaman lafiya da mazajen ku”. A tare suka amsa da “Ameen”. A hankali Umma tace “Allah ya jikan mahaifin ku da yana raye sai ya fi kowa murna Aasmaa din sa zata yi aure”. Duka muka amsa da Ameen nan hira ta balle aka cigaba da lissafin abubuwan da ya rage a siya, ni dai Ina zaune a gefe Ina kallon su. Muna zaune ya kira Umar yace masa gobe manyan sa zasu zo amma please yana so ayi komai a gaban Kawun su na gurin Umma ko kuma Liman tun da Umar din ya fada masa yadda suke da shi, kuma ya fada masa dalilin sa na son a yi komai a gaban Liman ko Kawun su don a damkawa Liman kudin zancen kar a bar su a gurin kawu. Godiya sosai Umar ya masa don shima dama yana ta tunanin haka. Da suka gama wayar Umma ya fada wa abinda Abdallahn yace, murmushi kawai tayi tace ya leka yace ma Liman din don Allah ya shigo zasu yi magana. Liman daya ji dalilin kiran hadda hawayen sa don murna, kuma yayi mata alkawrin in sha Allah dashi za’a tun da sai sun fara biyo wa ta gidan sun dauki Umar sai Liman din ya bisu. Ni dai nawa ido don tun ynxu jikina ya fara sanyi ji nake kamar nayi babban kuskure dana amince da auren nan yaushe ma nasan wannan yaron duk rashin kunyar daya ke min na manta har na amince da auren sa….. ******* Shafa kirjin sa Yusrah tayi tace “Yayana ka fada min don Allah wata magana ce kake so muyi duk na kagu naji ta Allah…” Kallon fuskar ta tayi yana d’ago kanta daga kirjin sa, hannayen ta ya riko gam yana kallon cikin idon ta yace “kafin na fada miki ki yafe mun Wifey nasan dole ran ki ya baci” Ita dai Yusrah da ido kawai ta ke binsa ya tabbatar duk maganar da yake son fada mata mai muhimmanci ce sosai tun da ya dawo ya lura baya cikin walwalar sa komai cikin sanyin jiki yake yin sa shiyasa taji duk hankalin ta a tashe. Kara damke hannun ta yayi yace “Yusra aure zan kara nan da sati biyar” DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Dedicated to Mufeeda tah💗 Uwar Amani kuma aminiyar Maman Amani❤️💗 Page 25 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Da sauri tayi A’uziyya tayi Murmushi tace mun gode sosai Yayana Allah ya cigaba da baka ikon yin adalici a tsakanin mu. Cikin jin dadin addu’ar ta yace Ameen Ya Rabbi Matata. ****** Shirye shirye biki kawai ake yi a dukkan bangaren, ta bangaren Abdallah dama ba abinda zai yi in ba lefe da kuma kayan furnitures ba, suma already ya riga ya gama da su lefe kanwar Mami ya kai wa ya hada masa komai don baxai ma iya gigin fara zuwa gun Mami ba. Da kyar ma ya lallaba ta ta fara masa magana amma da dogon fushi ta dauka sosai har sai da ya hada da Mama(Kakarsa) sannan ta sauko. A gida kuwa yana bakin kokarin sa ganin yana kyautata wa Yusrah kuma baya sa tana feeling jealous, kullum cikin nuna mata yadda take muhimmanci yake yi wanda haka yake kara kwantar wa da hankali. Yusrah.. A bangaren Yusrah kuwa tana iya bakin kokarin ta ganin tana boye kishin ta kar hakan ya dinga bayyana, ta dage da addu’a sosai kuma ta toshe kunnen ta daga jin maganganun mutane. Yau ma zaune take a dakin Abdallah tana kwashe kayan ta daga wardrobe din Abdallah, hira suke yi da shi wanda yake taya ta kwashe kayan tun da yau saura 1week bikin. Dagowa tayi ta kalle sa fuskar ta dauke da Murmushi tace “Yayana wai ni baka fada mun kayan a zan sa a dinner ba”. Kira mata ido yayi yana dan hararar ta cikin wasa kafin yace “ba dinner din da zanyi sai kace wani saurayi”. Juya manyan idon ta tayi tace “ai saurayin ne Yayana wa zai kalle ka ma yace kana da mata a gida”. Tabe baki yayi cikin son ya faranta mata yace “ba wani dinner da zanyi ko auren fari ma nayi ne kawai don na faranta miki amma ynxu baxan yi ba gaskiya ai na girma kuma”. Dariya kawai Yusrah tayi tana zuge akwatin data gama hada kayan, in tace kalamansa basu faranta mata ba tayi karya, tana alfahari da mijin nata tun da akai maganar auren nan bai taba chanja mata ba ita wani lokacin ma manta wa take yi cewa wai aure zai yi sai dai in ta fito taga part din dake gefen ta. Kiran ta yayi ganin zata fita daga dakin yace mata gobe dangin amaryar zasu zo suyi gyara. Sai da gabanta yayi mummunan faduwa amma kawai ta gyada masa Kai ta wuce tana Allah ya kawo su lafiya. ***** Ajiyar zuciya na sauke lokacin da Maryam ta zuge akwatin karshen, yau aka kawo lefe maza ne suka karba kuma Liman ne ya amsa. Tun da aka kawo ban kalla ba Ina daki sai ynxu da Umma ta sani dole na zauna na kalla, akwatina guda 16 ne saiti 4 wanda aka zubo kaya masu kyau na gani na fada, kusan rabin su a dinke suke da English wears masu kyau da tsari. Ni dai kallon su Yaya kawai nake yadda suke zuzuta lefen da sarkunan gold din da aka zubo masu kyau. Tun da bikin nan ya matso jikina a sanyaye yake gaba daya komai cikin sanyin jiki nake, ranar da aka kawo kudin zance ban Kara fita ba Umma ta hanani da kan ta take yi min gyaran jiki kullum sai biyu ake min. Nayi wani mugun fresh jikina ya Kara laushi sosai, ga maganin sanyin da na sha masu kyau wanda Umma ta hada min da kan ta, Ynxu kuwa tsumi kawai take bani da hadin kaza. Ni dai ba bakin magana amma wannan gyaran da ake min nasan kawai suna bata kudin su ne kuma ana wahalar da ni tun da kullum cikin matse matsen kafa nake. Washe gari su Yaya suke je suka kara gyara gidan suka tafi kuma da lefen gaba daya, kayan kitchen ne kawai dama suka je da shi sai frames da wasu abubuwan dai da na siya. Da suka dawo nan suka shiga santin gidan suna bawa Umma labari, gida ne mai hawa biyu a kasa babban palo ne mai dauke da dinning area sai kitchen babba da akwai daki a kusa da stairs mai dauke da toilet, hawa na farko shima kana hawa zaka ga palo bai Kai na kasa girma ba dan madaidai ci ne sai kofofi guda biyu suna kallon juna suna dakunan ne sai hawa na biyun shi kuma kana hawa kujeru ne guda biyu da table a tsakanin su sai dakuna biyu suma suna kallon juna, kuma duka dakunan ba wanda bai sa Turkish beds ba masu mugun kyau bama dakunan dake hawan karshen. Ni dai kallon su kawai nake Ina ganin abun kamar a mafarki, shirye shirye ake sosai biki ya kankama. Ranar Wednesday Yaya da Maryam suka dauke ni muka je salon din baby beauty aka min gyaran Kai sosai ta kuma tsantsara min Lalle ja da baki. Kallon hannun kawai nake ganin komai nake kamar a mafarki wai yau ni Aasmaa ce dauke da Lalle kuma na aure na wai amma ba wani farin ciki da nake ji kamar yadda nayi tsammanin in na tashi aure. Sai bayan isha’i muka koma gida wanda ya cika sosai da yan uwa na nesa dana kusa, mu dama a dakin Umar muka ajiye kayan mu don shi tun ana saura kwana uku ya koma gidan Liman sbd mata. Washe gari Thursday kamu aka yi a wani fili dake bayan gidan mu, ni farko ma cewa nayi bana son kamun sai da Umma tayi min fada sosai sannan na yi shiru. Gaba daya jikina a sanyaye yake, Ina tunanin gobe a irin wanna lokacin Ina da aure igiyoyin aure a Kai na duk sai naji hankali na ya tashi gashi dama Umma tace goben za’a kai ni baxa a tsaya sai Saturday ba. Haka aka yi kamu aka tashi sai san barka mutane an yi min kara sosai yan restaurant din mu duk sun zo matan hadda gudunmawar su suka hada aka bani. ******* Rana bata karya sai dai uwar diya taji kunya yau Juma’a aka daura auren Abdallah Ahmad da Asma’u Muhammad akan sadaki dubu hamsin. Ina zaune a dakin Umar sanye da shaida fara wacce aka mata aiki brown a jiki tayi mun kyau sosai ta kwanta a jikina, Kai na farin mayafi ne na yafa a kai na hawaye ne kawai yake zubo min daga idona. Tun da Liman ya dankamun sadakina na fashe da kuka, kukan dana rasa na meye farin ciki ne ko bakin ciki. Umma ma dake palon ta hada Kai suka yi da Yaya suna kukan farin ciki, Allah ya amsa Aasmaa tayi aure cikin mutunci wannan abin farin cikin in basu godewa Allah ba mai zai suyi. Salma ta gurin aikin mu ce ke aikin lallashina tana bani baki nidai gyada kai kawai nake ba wai don Ina fahimtar abinda take fada ba, ni kadai nasan abinda nake ji a rai na game da wannan auren shekara daya da muka yi. Bana salla wanka Yaya ta sani na sake yi ta taya ni shirya wa cikin wata red atampa riga da zani sai farar lafaya mai adon ja kadan da na nada. Lafayer tayi mun kyau sosai bama yadda ta kwanta a jikina kana kallon nadin kasan wacce ta nada ta iya dama. A gaban Umma Yaya ta zaunar da ni Umma ta shiga yi min nasiha mai ratsa jiki, kuka kawai nake yi Ina rike hannun Umma lokacin da Aunty Murja kanwar Umma ta dago ni zamu fita. Kuka nake sosai har aka sani a motar, tun da nayi wayo ban taba kwana a wani gidan ba in ba namu ba, yadda na tashi Ina da kwalafacin uwa shiyasa bana zuwa ko Ina ko Yaya In ta haihu duk yadda zata yi da ni naje na kwanar mata ko ana gobe suna ne bana zuwa dole haka take kyale ni sai Ynxu gani an baro ni da gidan mu za’a sadani da gidan da zan rayu na tsawon shekara. Har muka iso gidan kuka nake yi sai dai a hankali nake kukan Yaya dake gefena tana kara min nasiha mai ratsa jiki. Riko ni suka yi muka nufi bangaren matar sa kamar yadda yake a al’ada. Yusrah tana zaune gefenta Teema ce sai Walida, su kadai tace su zo bata son mutane kuma Mummy da Abba ma sun goya bayan ta, su ma din tace suzo ne don tarbar amaryar amma amaryar na zuwa su tafi su bar ta, daga baya ne ma Abba yace a tura mata manya guda uku dai kar dangin amaryar suga kamar an rai na su yara ne suka tarbe su. Tun da suka shigo da amaryar ta damke hannun Walida jikin ta yana rawa rawa amma fuskar ta kokari take tayi Murmushi, addu’a kawai take yi a zuciyar ta ita kadai tasan abinda take ji a zuciyar ta(I’m sorry Yusrah🥹) Jarumta ta aro ta mike tana Murmushi ta nufo su Aunty Murja cikin fara’a ta tsugunna har kasa ta gaishe su tana riko hannun Aasmaa din fuskar ta dauke da Murmushi. Kusan a tare kirjin mu yayi wani irin bugawa muka dago muna kallon juna, ni dai ta cikin lafayar Ina hango fuskar ta tar da hasken fitulu suka haska, tana da kyau sosai don kuwa ta fini kyaun fuska da hasken fata ga kuruciya sosai kana hango wa. Ita kuwa Yusrah bata ganin fuskar ta amma laushin hannun Aasmaa din da kuma kamshin da take ji yana tashi daga jikin ta shi yaso tayar mata da kishin ta. Zaunar da ita tayi a gefen kujera ita ma ta zauna a gefenta, nasiha aka musu sosai da addu’oin zaman lafiya sannan Yaya Murja ta kara riko ni muka fito. Ajiyar zuciya na sauke lokacin da Yaya ta zaunar da ni a kan gadona bayan nayi addu’a, Lumshe ido nayi wasu hawaye suka sake zubo min, wai yau ni ce aka kawo gidan miji amma bana farin ciki don auren ba irin ko wani aure bane auren yarjeje niya ne. A rai na nace dama Sadam na aura nasan ko banxa sai na fi jin sassauci, da sauri nayi istigfari tuno wa da nayi da auren wani a Kai na. Ina ji Ina gani su Yaya suka tafi amma kafin su tafi sai da suka Kara gyara min gidan suka kunna Turaren wuta. Ina zaune shiru a gefen gadon har na gaji na koma tsakiyar gadon na kwantar da kai na a cinyoyina. ****** Da sallama ya shiga dakin Yusrah, dagowa tayi tana kallon sa wani mugun haushin sa yana turnike ta. Yana sanye da jallabiya fara kal sai kamshi yake hannun sa rike da leda babba ya shigo, ajiye ledar yayi a gefen kujerar dake dakin ya nufo ta yana sakar mata Murmushi. Riko hannun ta yayi ta tayar da ita yace “barka da wannan lokacin Uwargidan Abdallah”. Lumshe ido tayi wasu hawaye nasu dumi suka zubo mata, shikenan ynxu ta daina amsa sunan Uwargida kuma amarya kamar yadda yake kiran ta a da. Rungume ta kawai yayi yana shafa bayan ta yace “na sani Kanwata nayi miki laifi, Yayanki kuma mijin ki mai laifi ne tabbas ke din Haruna ce Matata, Allah yayi miki albarka ya saka maki da mafificin Aljanna, ba ko wace mace bace zata iya dauriyar da kika yi wata 6 da aure ace mijin ki ya sake aure kuma ki hakura ki danne Ina alfahari da ke Matata”. Kuka ta fashe da shi wanda take rike wa tun tuni, kuka take sosai tana dan dukan kirjin sa a hankali. Sai da ya tabbatar ta amayar da abin da ke damun ta sannan ya ja ta suka shiga toilet tayi alwala, kwantar da ita tayi ya kunna mata karatu a Mp din ta ya ajiye a kan bed side drower, addu’a yayi mata ya shafa mata ya mike zai fita. Riko hannun sa da tayi ne yasa shi juyo wa, Murmushi ta sakar masa cikin dauriya tace “Yayana ka kwantar da hankalin ka in sha Allah bacci zan yi ynxu ma baxan damu Kai na ba nasan kana so na bani da wata matsalar kawai dai dan kishi ne kadan yke mintsina na a nan”. Ta karashe tana nuna sai tun zuciyar ta tana turo baki gaba a shagwabe. Bai san lokacin da ya saki dariya ba ya dawo da bata deep kiss a baki, sai da ya tabbatar da hankalin ta ya kwanta kaso 100 na damuwar ta 70 ya kau sannan yayi mata Sallama ya fita. Bayan sa take bi da kallo kishi yana nukurkusar ta ganin zata sawa kan ta hawan jini yasa ta Lumshe ido taba bin karatun Qur’anin hawaye ba zuba daga idon ta. Abdallah kuwa kan sa a kasa ya shiga part din Aasmaa yana tunanin Yusrah, wani kima da daraja ta Kara a idon sa sosai tabbas ba dan yana jin Aasmaa a duk wani bugawar zuciyar sa bazai taba auren taba. A hankali yake take matattakalar benen yana bin ko Ina da kallo har ya hau hawan karshen, dakin hagun sa ya bude ba kowa a ciki fitilar ma a kashe take, rifo kofar yayi ya bude dayan dakin. Dago kai na nayi daga kwancen da nake idona ya shiga cikin nasa……. Comments nd share don Allah. DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 26 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Dago kai na nayi daga kwancen da nake ido na ya fada cikin nasa. Hade rai nayi sosai na gyara kwanciya ta na zuba masa ido ina son sanin dalilin da yasa ya shigo min daki a irin wannan lokacin tun da ai auren mu ba wai irin normal aure bane. Shi ma a nasa bangaren hade rai yayi sosai yana bin ta da kallo ta kasan idon sa, tayi masa mugun kyau sosai bama yadda fatar ta take glowing, idonta daya dan kumbura sbd kuka y zuba wa ido. A nutse ya shigo dakin har gefen gadon da take ya tsaya yana kallon ta, cikin sanyin murya yace “Assalamu alaikum”. A saman lips dina na amsa da “Waalaikumussalam”. Dauke idon sa yayi daga kan ta yace “Barka da shigowa gidan Abdallah Amaryar Abdallah, fatan zaki jure sauye sauyen da zaki tarar”. Tabe baki nayi Ina dan Marsala baya kadan a nutse nace “ko ma meye zan daure nan da shekara daya ne ai in sha Allah kamar yau ne”. Girar sa daya ya dage yana mata wani kallo kafin ya gyada kai ya saki wani Murmushi ya juya kawai ya fice. Ajiyar zuciya na sauke lokacin da naji rufe kofar sa, mike wa nayi na cire lifayar na bude kofar a hankali na fita, ba inda ban shiga ba don in ga ko yana nan sai sa na tabbatar baya nan sannan na rufe kofar palon Ina jinjina dukiyar da aka Barka a part din, yau ni Aasma wacce na taso naga gidan mu da daki falle biyu nice mamallakiyar 5 bedrooms. Dakin na koma na cire kaya na, Kayan baccin da Yaya tasa mun a wata akwati na ciro na zira doguwar rigar na bi lafiyar gado duk jikina ciwo yake mun. Ban farka ba sai karfe 8, da sauri na mike na shiga toilet nayi wanka. Shirya wa nayi cikin Riga da zani na wani lace pink wanda ya min kyau sosai ya zauna a jikina das, rigar ta matse ni daga sama har boobs dina sun dan fito, sai da na shafa powder yar kadan na zira kwalli sannan nabi jikina da turare Ina lumshe ido. Gyara gadon nayi na kashe AC Ina tabe baki a rai na kuwa gulmar sa nake Ina cewa kamar baxa a mutu ba AC har biyu a daki daya. Waya ta na dauka na fito kasa dan kara gyarawa nayi duk ba datti sai abinda ba’a rasa ba na kunna turaren wuta. Ledar daya shigo da ita jiya na bude na saka gasassun kajin a fridge na ajiye yogurt din a fridge shima. Karar door bell dana ji ne yasa ni fito wa daga kitchen Ina tunanin ko waye da sassafen nan tun da 9 a lokacin kuma rai na bai kawo min cewa mai gidan bane. Bude kofar nayi Ina dan matsa wa baya, Yusrah ce ta shigo cikin jallabiya dark purple wacce tayi mata kyau sosai tayi kwalliya abin ta sai kamshi take bayan ta kuma mai aikin tace dauke da wani babban basket. Murmushi muka sakar wa juna a tare bayan bugawar da zuciyar mu tayi. Matsa wa nayi suka shigo ciki, karbar basket din tayi tayi ma mai aikin nata umarnin tafiya bayan ta gaishe ni. Zama tayi akan kujera tana dan bin palon da kallo a takaice komai irin nata ne banbancin color nata golden ne na Aasmaa kuma dark ash ne. Dagowa tayi ta kalle ni tace “Aunty Ina kwana ya kwanan bakun ta”. Murmushi na sakar mata nace “lafiya qalau”. Duk sai muka yi shiru kuma, Yusrah ce tayi magana tace “breakfast dama nayi muku nace amarya baza ta shiga kitchen ba ai gaskiya”. Yar siriryar dariya nayi nace “mun gode kuwa Allah ya Kara arziki da lafiya”. Cikin Jin dadi Yusrah tace “Ameen Aunty”, da farko da Teema tace mata ai amaryar ta girmi Yayan nasu na ta dauka zata ganta zabgegiya sai ta ganta kuma yar caras kuma mai kirki sabanin da ta dauka amaryar zata kasance Mara mutunci ne. Fito wa yake daga kitchen hannun sa rike da jarkar ruwa da alama sha yayi yana sanye da three quarter black sai riga mai gajeran itama black wacce ta matse sa sosai ta fito da kirar sa ta cikakken da namiji. Duk zuba masa ido muka yi ni kallo nake masa na mamakin yaushe ya shigo tun da daka kitchen din nake amma ban gansa ba. Yayin da ita kuma Yusrah take kallon sa kishin sa yana damun ta amma ta daure tana addu’a a zuciyar ta. Shi kuwa Abdallah fitowar sa daga kitchen din da yayi arba da Aasmaa sai da numfashin sa ya kusa dauke wa, ta gefen ido yake kare mata kallo yadda dukkan su baza su fahimci cewa kallon ta yke ba, tayi masa kyau sosai bana kirjin da suka dan dago ta kasa shi kadai yasan abin da yake ji. Nutsuwar sa ya sai ta ya nufo inda Yusrah take direct yana sakar mata wani Murmushin daya kusa sa Aasmaa zunduma ihu. A kan kujerar da Yusrah take zaune ya zauna tun da 3 seater ce yana murmushi yace “Wifey kece da sassafen nan”. Murmushi Yusrah ta sakar nasa ta zamo daga kan kujerar ta durkusa a kasa tace “Yayana Ina kwana”. Wani sassanyan Murmushi ya kara saki wanda y fito tun daga zuciyar sa ya sa hannu biyu ya dago ta yace “lafiya qalau Kanwata, me kike yi da sassafe haka uhum”. Dan turo baki tayi a shagwaba tace “girki nayi muku Yayana kar Aunty ta shiga kitchen yau”. Dan satar kallon ta yayi yaga tana danne danne a waya a kaci sa’a ta dago kai suka hada ido ta sakar masa wata muguwar hararar da bata san dalilin ta ba. Murmushi yayi ya dauke kan sa ya mayar kan Yusrah cikin kasa kasa da murya yadda ita kadai Zata ji abinda zai ce yace “kin yi kyau sosai Wifey wannan jam bakin me yasa kika saka shi baki bari na shigo na tsotse sa ba uhm..” Dan zaro ido tayi tasa hannu biyu ta rufe fuskar ta alamar kunya tana dariya.. Murmushi kawai yake yana kallon fuskar Yusrah a daren jiya ya yadda ya amince yana ma Aasmaa wani irin so mai wuyar fade ko dan yadda yake Jin sa sakayau da yadda yayi bacci cikin farin ciki da nitsuwa wanda rabon da yayi irin sa tun ranar da ya fara ganin sanya ta a idon sa. A gefe daya kuma ya tabbatar da cewa Yusrah ita ce mahadin farin cikin sa duk farin cikin da yake ciki in bata a ciki Jin sa yake wani iri, yau da safe da tunanin zaman da zasu yi da amaryar sa ya tashi wanda hakan yaso haifar masa da ciwon kai, amma kuma daga magana da Yusrah Jin sa yke sakayau, yana ganin girman Yusrah da kimar ta wanda baki baxai iya faduwa ba, kunyar ta yake ji sosai ko da asuba daya je tayar da ita yana ganin ta bude ido ya juya ya fice don yana jin tsoron ran ta y baci in ta wartsake daga baccin zuciyar ta ta raya mata cewa ya kwana da amaryar sa. Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Aasma yace “Husna dan bani hankalin ki anan”. Dago ido na da suka chanja kala nayi na kalle sa dasu, tun da ya fara yi wa matar sa magana kasa kasa naji zuciya ta tana min zafin da ban san ko meye dalili ba, amma haka kurin naji Ina jin haushin sa. Murmushi ya saki ganin irin kallon da take masa ya dauke Kai ya shiga musu nasiha cikin tattausan lafazi. Sosai y musu nasiha kuma ya roke su da su hada kan su domin hadin kansu shine farin cikin sa da kwanciyar hankalin sa. Sai da ya gama yayi addu’a sosai sannan ya juya ya kalli Yusrah yace “Wifey kwana nawa nawa zaku dinga yi kuyi shawara k. Murmurshi tayi ta kalli Aasmaa tace “Aunty kwana nawa zamu dinga yi ni da nace ko biyu biyu koh?” Daga Kai nayi Ina mayar mata da martanin Murmushin nace “yayi hakan ma” a rai na kuwa tabe baki nayi Ina cewa nayi masa ne a kwana biyun ai ni da badan ma ya ce kar mu nuna wa kowa sanadin auren mu da kwanan nawa zan bata kyauta har na bar gidan. Sallama Yusrah tayi mana ta juya ta fice, Ina ganin fitar ta na mike nima zan haye sama tun da ban ga mai zan zauna nayi masa ba. A nutse yace “dawo muyi magana” Kallon sa nake kamar kar na dawo sai dai yadda ya zuba min idanun sa ya hana ni masa musu kawai na gyada kai na na koma na zaune a inda na tashi Ina warware dankwali na na yafa. Tabe baki yayi yace “daga baya kenan”. A zafafe na dago na kalle sa nace “ban gane daga baya kenan ba”. Dago sexy eyes dinsa yayi ya zuba mata cikin kasa kasa da ido yace “ba dai wadannan balloons din kike boye wa ba ai tuni na gama kalle su tsaf”. Zaro ido nayi cikin bala’i na mike nace “Abdallah ka fita ido na na rufe Allah kar ka manta cewa auren yarjejeniya mukai kuma ko ba haka ba sbd tsabar rai ni ka kalli ido na a matsayina na yayarka ka jefe ni da wannan iskancin”. Kasa kasa da ido yayi yace” Husna Kar ki kara kiran aure na auren yarjejeniya, yadda na aure ki dinnan Kar ki manta fa Ina da hakki a kan ki kuma ko Ynxu na nema dole ne fa ki bani..” DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 27 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Wani mugun kallo na watsa masa nace “me kake nufi”. Murmushi yayi yace “ina tuna miki ne wai wannan maganar bana don kowa ya ji ta amma ban san me yasa kike son maganar ba, Ynxu in wani yaji fa maganar ta watsu kema kin san ai ba son ki nake ba kamar yadda kema bakya sona ni da nake da zukekiyar mata kamar wifey ai na rufe kofar wata kuma a zuciya ta”. Lumshe ido na nayi Ina hana hawaye zubo min daga ido na don ba karamin zafin maganar sa naji ba na cewa baya so na da kuma ambatar matar sa da yayi, ban san me yasa nake jin zafi ba amma tabbas kuka ma naji Ina son yi sbd tashin hankali. Koma wa nayi na zauna Ina Lumshe ido na. Yana kula da yanayin ta sai Murmushi yake saki Jin sa yake cikin wani madaukakin farin ciki. Gyaran murya yayi cikin tsare gida kar ta kawo masa musu ma ya soma da cewa “ba wani abu bane yasa na ce ki tsaya sai abubuwa guda uku, na farko dai dole ne duk ranar da ya kasance girkin ki ne ke zaki dafa min abinci da kuma gyara min bangare na, ban ce ki kwana a can ba ko Kar ki kwana in kina bukata zaki iya zuwa in bakya so kiyi zaman ki a part din ki”. Wani kallo na masa cikin hade rai nace “ban gane ba”. Kankance ido yayi yace “zan miki bayani a gaba”. “Na biyu kuma bana son kowa ya fahimci abinda yasa muka yi aure, duk lokacin daya kasance da akwai wani na uku a tare damu zamu dinga pretending kamar masoya ne mu”. “Sannan na karshe muji tsoron Allah dukkan mu, Kar ki manta cewa ni mijin ki ne Ina da hakki akan ki kuma kema kina da hakki a Kai ba, baxan takura miki ba don ni ba sbd wani dalili na aure ki ba sai don yarjejeniya kawai Ina son ki sani cewa daga yau ni ne a saman ki Husna ki bar ganin wai kin girme ni aure na kike yi kuma an daura a bainar jama’a kiji tsoron Allah a duk abinda za kiyi”. Zuba mata ido yayi yaga ta hade rai sosai tana girgiza kafafu. Murmushi ya saki yace “kina da abin fada ne” Yatsina fuska nayi nace “babu mai gida”. Mikewa yayi yana tabe baki don yasan gatse ta masa yace “bara naje gurin wifey nayi missing dinta yau daya da ban kwana a jikin ta ba”. Wani mugun kallo na bisa da shi kamar na janyo sa na shako wuyan sa don haushi, kwafa nayi na wuce sama ko breakfast din da yake kan table din palon ban kalla ba. Daki na na shige na shiga jera Kaya na a wardrobe, a nutse nake aikin duk na gaji amma don wani bacci nake ji sai dai Ina son na gama jera kayan tukun. Bani na gama ba sai 12 na rana, akwatinan na shiga sauko da su na ajiye a dakin dake hawa na farko, Ina tabe baki ganin dukiyar da aka narka. A palon saman na zauna na jona kayan kallo, sunna TV na sa na zauna akan kujera na shiga neman layin Umma amma har ta katse bata dauka ba. Ajiye wayar nayi a gefe na zuba wa Tv ido ina kallo ba wai don Ina fahimta ba. Waya ta da ta shiga ringing na janyo ganin Yaya yasa nayi Murmushi na daga da Sallama. Daga bangaren Yayan tace “yi sauri ki zo ki bude mana kofa tun dazu muke tsaya muna ta bugawa amma shiru ko bakya nan ne”. Da sauri na mike da wayar a kunne na na shiga sauko wa nace “ina sama ban ji ba wallahi”. Bude musu kofar nayi suka shigo ciki, cikin murna na rungume Basma wacce ta rungume ni itama cike da farin ciki. Zama mukai akan kujera Ina kallo suna shigo da manyan fararan bokiti guda 8 na Kayan gara. Kallon Yaya nayi nace “wai kayan garar ne wannan”. Daga min Kai tayi tace “daga gidan sirikan ki muke, sai da muka ajiye musu nasu sannan muka taho miki da naki nan”. Murmushi nayi nace “Allah ya saka da alkhairi kuwa”. Hira muka shiga yi na dauko musu breakfast din da Yusrah ta kawo suka ci. Aunty Murja ce sai Yayar Umma sai kuma matar kawu sai Yaya da Maryam da Basma. Aunty Murja ce ta mike ta kalli matar Kawu tace “to mu tafi Furera tun da mun zo mun ga yarinyar kuma Alhamdulillah guri yayi kyau Allah ya bada zaman lafiya”. Hade rai furera tayi tace “ke kuwa Murja daga zuwan mu sai mu tafi ko huta wa bamu yi ba”. Tabe baki Aunty Murja tayi tace “me zamu zauna yi Toh Furera Ina ce mu manya ne ai abin kunya ne ma sirikin mu ya shigo ya ganmu gotai gotai da mu a zaune”. Yayar Umma ce ta mike ita ma tace “da gaskiyar Murja fa Furera ki tashi mu tafi kawai ai ga su Maryama nan zasu dan taya ta zama ko”. Ba dan Furera ta so ba ta mike suka fita tana bata rai. Dariya muka sa dukkan mu bayan fitar su, Yaya ce taja tsaki tace “Allah y shirye ta Wallahi daga ita har mijin nata duk ba halin kyau” Ni dai ban yi magana ba sai Murmushi kawai da nayi, taya ni suka yi muka gyaro gidan gaba daya aka Kara sa turaren wuta, wajen 2 sai ga mai aikin Yusrah ta kawo mana abinci. Godiya nai mata na bata basket din safen da basma ta wanke ta juya dasu. Yaya ce tayi Murmushi tana cin white rice din tace “Allah dai ya baku zaman lafiya Aasmaa amma da dukkan alamu kishiyar ki bata da damuwa”. Murmushi nayi nima nace “gaskiya bata da matsala Yaya da safen ma fa da kan ta ta kawo min breakfast din da alama tana da hankali”. Sai bayan La’asar su Yaya suka tashi tafiya kafin nan sai da Yaya ta matsa na sake wanka ta fito min da wata doguwar riga fitted gown wacce ta kama ni sosai duk motsin da nayi sai jikina ya motsa. Tire kaga tsiya nayi wanda ya matukar daukar kan nawa sosai nayi kyau har na gaji sai kamshi nake, mayafi na yafa muka sha hotuna dukkan mu akan Maryam zata nuna wa Umma sannan muka sauko. Robobin dana zubawa Yusrah dukkan kayan garar na bawa Basma a cikin wata babbar leda tun da sun ce zasu leka gurin ta in suka fita. Kamar zanyi kuka haka nayi musu sallama na koma sama ba tare dana rufe kofar ba, tunanin Umma ne yake damuna da kuma kewar Umar gaba daya sai nake ji na wani iri. Waya ta na janyo na kunna data wacce ban cika kunna wa ba don chatting ba wai ya dame ni ba. Ina zaune Ina kallon reels a instagram wanda sai ynxu da nake zaman kadaici sannan nake jin dadin sa naji kamar an bude kofar palo an shigo. Shiru nayi don jin ko waye ni sai ynxu ma na tuna cewa ban rufe kofar ba. Jin kamar muryar Yusrah tana kiran Aunty ne yasa na mike na zira flat shoe dina red color mai gashi a jiki Wanda na ware don yawon cikin gida na shiga sakkowa a nutse. Tun da na soma sauko wa suka zuba min ido dukkan su ukun, ni dai fuska ta dauke da Murmushi har na Kara so cikin palon. Zama nayi akan kujerar dake fuskantar wacce suke zaune a Kai nace “Sannun ku”. Murmushi Walida tayi tace “lafiya qalau Amarya Ina wuni”. Murmushi nima na mayar mata nace “lafiya qalau ya gida”. A hankali tace “Alhamdulillah” Mai da kallo na nayi gurin Yusrah wacce take kallona tana Murmushi a ran ta kuwa addu’a kawai take amma maganar gaskiya ta rude da ganin surar Aasmaa, ba wai ita ma bata da structure mai kyau bane kawai dai na Aasmaan kirar ta mai jan hankali ne sosai. Murmushi na sakar mata nace “Sannu Aunty”. Dan zaro ido tayi da mamaki tace “lalala Aunty ni kike cewa Aunty kuma”. Yadda tayi din sai ya bani dariya don haka nayi Murmushi nace “eh mana ai gaba kike da ni a gidan nan dole na baki girman ko”. Girgiza Kai tayi tana Murmushi tace “A’a gaskiya Aunty bana son Auntyn nan kawai ki ce min Yusrah”. Bata bani damar magana ba ta nuna Walida tace “wannan yaya tace” sai ta nuna Teema tace “wannan kuma yayata ce ita ma dakin su daya da Yayana”. Murmushi nayi nace “Sannun ku da zuwa” Kallon Teema din nayi naga sai wani yatsine yatsine take Murmushi na sakar mata nace “sannu kanwarmu”. Kallona tayi tana tabe baki tace “yauwa amarya”. Mikewa nayi na shiga kitchen don kawo musu abin sha. Teema ce ta kalli Yusrah tace “tabdijan ynxu wannan ce kishiyar ki kalli fa yadda ta matse jiki kamar wata karuwa sai wani Murmushi take”. Hade rai Walida tayi tace “Teema ban miki magana ba wai wallahi kika kara wata maganar sai na fada wa Abba”. Ba don ta so ba tayi shiru a ran ta kuwa mamaki take wai wannan ce ta girmi Abdallah. Babban tray dana dora drinks da cups na ajiye sai wani tray din dana dora kayan gara. Yusrah ce tayi saurin cewa “Aunty da kin bar su Allah kin kai min da yawa fa”. Murmushi nayi nace “ai wancan a part din ki ne nima anan sai na samu ladan”. Suna zaune ya shigo yana amsa waya, kamar zanyi kuka haka nake ji sbd yadda nake ta samun sabani sai lokacin da nake zaune cikin shigar da bana so sannan yake zuwa. Kashe wayar yayi suka gaisa dasu Walida sannan ya kalli inda nake na zuba wa TV ido kamar wani abu nake kalla bayan ba abinda nake kalla din. Murmushi yayi yasan dalilin ta na juyawa shi kuwa ai haka yake so yayi ta zuwa a lokacin da bata so din Juyowa nayi jin ido a kai na ai kuwa idona ya shiga cikin nasa, kallon da yake min yasa na fahimci abinda yake nufi kawai sai na samu kai na da rage kaifin kallon da nake masa cikin tattausan harshe nace “barka da zuwa”. Lumshe idon sa yayi yace “yauwa Husnaa”. Walida data lura da yanayin da kanwar ta ta fara shiga ce ta mike tana Murmushi tace “bara mu wuce amarya”. Mike wa nayi nima nace “Ngd sosai kuwa Allah ya mai da ku gida lafiya”. Raka su nayi har bakin kofa suka fita sannan na rufe kofar. Nazo daidai tsakiyar palon Ina kokarin juya akalar lafiyar tawa zuwa sama kawai naji yasa hannu ya fisgo ni jikin saa…. MEENAA DijahAM 09066728387 Salamu alaikum💃💃💃💃 Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵 Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜. Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃 Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥 Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉. Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥 Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din +234 809 699 9490 Bissalam❤️❤️ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 28 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM MEENAA Hankalin ta ba karamin tashi yayi ba ita da Hajiya Bilki lokacin da suka ji maganar Abdallah zai Kara aure. Kuka ta shiga yiwa Hajiya Bilki ta daga mata hankali ita kuma ta shiga zarya gidan Mami akan kar ta yadda ayi auren ta tilastawa Abdallah ya auri Meena kawai tun da ita yar uwar sace kuma tana son sa. Ita ce tayi bincike mai zurfi akan Aasmaa din taje ta fadawa Mami cewa tsohuwa Abdallah zai aura don ta fi shekaru 30 ta girme sa. Da Mami taga abin nasu ba hankali ne taja wa Hajiya Bilki babban warning akan Abdallah cewa bata isa tasa ta yiwa dan ta dole akan ya auri yar ba, tun da ya nuna baya son ta su rabu da shi mana suyi nata addu’a ta samu wanda ya fisa, wannan abin ya bakan tawa Hajiya Bilki rai sosai ta kuma yi alkawarin in sha Allah Meena ta rabu da Abdallah har abada. A bangaren Meena din ne dai ita wannan sam bai dame ta ba don haka tama ci damarar neman yakin Abdallah don tayi rantsuwa ko da bala’i sai ta aure sa…… ****** Wani mugun kallo na masa Ina kokarin raba jikina da nasa, kara janyo waist dina yayi dole kirjin mu suka hadu. A masifance na kalle sa nace “wani irin Iskanci ne wannan Abdallah ko ka manta wace ni ceh..” Lumshe idon sa yayi yana tura kan sa cikin wuya na yana shakar kamshin dake tashi a jikin ta. Da sauri na rintse idona jikina yana fara rawa, ni kadai nasan kalar tashin hankalin da nake ji, tun da su Umma suka fara bani kayan da’a dauriya kawai nake yi amma gaba daya a rikice nake gashi kuma wannan yaron yana neman dagula min lissafi. Dago kan sa yayi ya zuba ma fuskar ta ido ganin yadda ta rintse ido jikinta na rawa, murmushi yayi cikin wata kasallaliyar murya yace “Husnaa sha’awa kike ji”. Da sauri na bude fuska ta ba tare dana shirya ba, wani mugun kallo na jefa masa kafin na tattaro duka karfina na hankada sa. Daki na shige na rufe kofar Ina sauke ajiyar zuciya gaba daya hankali na a tashe yake, sai mammatsa kafa nake sbd azaba wata kwalla ce ta zubo min nasa hannu na goge ina ja masa Allah ya isa. Shi kuwa Abdallah lumshe idonsa yayi yana sauke ajiyar zuciya, gaba daya ma ba’a nutsuwar sa yake ba don haka a daddafe ya fita ya shige part din sa don naso da ya leka Yusrah. Cikin kwanakin da suka wuce nayi su cikin kewar gida matuka da taka tsan-tsan, in har bana daki to da hijab na ke yawo kuma har yau ban far girki ba Yusrah ce take kawo min. Oga kuwa tun ranar daya min iskanci ban kara ganin sa ba, in na ajiye breakfast da lunch din da aka kawo min zan samu ya ci ya bar plate din akan dining, ni hakan ma yafi min sbd dama don shi take guduwa falon sama in ta sauko kasa to an yi knocking ne ko kuma zata dibi abinci. A lissafi ta yau take cika kwana bakwai kuma yau zai koma gurin matar sa rai na fess ko ba komai zan dan sake a part din. Zaune nake a falon sama da misalin 10 na safe, chatting nake da Salma ina fada mata nan da sati daya in sha Allah zan koma aiki. Ban ji tsayuwar sa ba sai kamshin turaren sa dana ji ne yasa ni juyawa a hankali na kalle sa, yana tsaye cikin shigar kananun kayan da suka masa kyau sosai suka kuma fito da kuruciyar sa. Dauke kai na nayi kamar nan gan sa ba na juya Ina jira ya gaishe ni tun da ai nice gaba da shi. Shi ma hade rai yayi sosai don so yake ya fara nuna mata waye gaba da ita, a dake yace “baki iya gaisuwa ba”. Juyo nayi na zuba masa lumsassun idona da suke rufe wa kamar mai jin bacci, harara ba sakar masa Ina hade rai nace “wace zata gaishe ka?”. Gira daya ya daga min yace “Amaryata mana”. Tabe baki nayi nace “kasan dai ni ba sa’ar wasan ka bace ko?” Zame takalmin sa yayi ya shiga takowa kan carpet din a nutse, zuba mata ido yayi fuskar sa a hade ya ciro key a aljihun sa ya ajiye akan kujerar da take zaune. Zuba mata sexy eyes din sa yayi cikin hade gira yace “kije ki gyara min part dina, shi ne a tsakiyar naku kuma ki ajiye key din a gurin ki duk ranar girkin ki kije ki dinga gyara mun kuma a gurin ki zan dinga cin abinci”. Wani kallo na masa Ina so nayi magana amma yadda ya hade tan nan sai naji baxan iya fada masa maganar da zata kara harzuka sa ba don haka kawai na sauke ido na na mayar kan TV. Tabe baki yayi ya juya ya fice yana tunanin dole fa sai ya koya wa Husna hankali don ya gama karantar sa ita gaba daya auren su baya kan ta shi kuwa ai ko yanka sa ake yi baxai iya sakin ta ba. Sai da naji rufewar kofar palo sannan na turo baki gaba Ina kunkuni, a rai na nake cewa bawai don ya isa ya sani aiki bane zan dinga gyara masa part din kawai dai sbd kar matar sa ta shiga girki taga part din a hargitse ta mun kallon kazama. Mike wa nayi na dauki Hijab dina da yake gefena na zira na sa takalmi na dauki wayata da key din na fito, rufe kofar part dina nayi da key na nufi part din sa da yake tsakiyar namu. Key na sa na bude kofar na shiga baki na da sallama, palo ne babba wanda zai kai nawa na kasa girma sai wata kofa daga gefe da alama guest toilet ne, daga karshen palon kuma corridor ne don haka na nufi corridor din kawai, ban yi wata tafiya mai tsayi ba na bulli cikin wani katon palon da zai yi biyun na farko, ware ido nayi Ina bin palon da kallo cike da mamaki, kujeru sai ti biyu ne a palon sai daga karshe dining ne wanke gefen sa kuma kichen ne dan dai dai irin na cikin palon nan. Ajiyar zuciya na sauke ina tunanin yadda zan gyaro wannan katon palon, kofofi biyu na gani gefe na nufe su na farko bedroom ne kato da toilet na biyun kuwa girman sa za’a iya yin palo da daki da kitchen da alama shine master bedroom hadda kujeru shima anan. Zage wa nayi na shiga gyara part din ban samu Kai na ba sai wajen 1 don ba inda ban gyara ba kuma ban wanke ba, koma wa part dina nayi na dauko turaren wuta nazo na saka, sai da na jira duk suka gama kone wa har a toilets na saka sannan na rufe part din a gajiya ba koma nawa. Ga yunwa Ina ji kuma nasan dai dole yau zan shiha kitchen ai tama yi min kokari sosai. Wanka ma fara yi na zira simple doguwar rigar atampa na sauko kasa don yunwa nake ji sosai duk na gaji gashi dama da safe ni ma na gyara part dina ba inda ban gyara ba, gashi Yaya tace sai nayi sati biyu zata sa wacce take kawo mata mai aiki ta samo mun don aikin gidan da wuya sosai. Noodles kawai na dafa a kitchen din ma naci sbd wahala ko wanke wanke ban yi ba na fada dakin kasa na kwanta akan gado Ina sauke ajiyar zuciya. YUSRAH Yau ta tashi da farin ciki sosai sbd zata karbi girki ba karamin missing din Yayan nata tayi ba don ya riga ya saba mata da kullum sai ya neme ta shiyasa yau da zata karbi girki sai rawar jiki take yi. Tsawon sati dayan ta yi su ne cikin Ibada kullum karfe uku na dare take farkawa baxa ta koma bacci ba sai tayi asuba ta mika lamuran ta ga Allah shiyasa take jin ta cikin kwanciyar hankali. A gefe guda kuma gyara kan ta take sosai, Mami da kan ta ta aiko mata da babbar jarka ta tsumin baure da tabaje, wuni take tana shansu ai kuwa tana gani aikin su gashi yau tun safe bata ci abinci ba hadin kankana tayi kwallo biyu ta wuni tana shan kayan ta, da kwakwa da dabino a gefe(kun san kuwa yau dole Aasmaa ta toshe kunne don za’a haukata Oga ne😜) Kafin 4 ta gama girkin ta tsaf, jira tayi har 5 tukun ta mike ta nufi part din Abdallah don gyara masa, a gyare ta same sa sosai bata san lokacin da Murmushi ya kwace mata ba ga kamshi mai dadi da part din yake. Ko Ina ta shiga ta duba taga komai neat sannan ta koma ta shirya. A daren ranar kuwa ta gurzu a hannun Yayan nata don sai da ta dawo tana rokon sa ya taimaka ya rabu da ita, ganin da gaske ta ji gata ne yasa shi kyale ta ba wai don ya gaji ba. Ita kam Yusrah bin da take da ido kawai tana mamakin yadda yake ta rawar kafa kamar ba daga gurin amarya yake ba….. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Dedicated to Abubakar Musa Sulaiman😂😂 Page 29 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Wanka na fito ina tunanin wai yau ni ce wacce nayi sati biyu da aure, ajiyar zuciya na sauke ina sauri sauri na shirya don na tafi restaurant. Gama shirya wa nayi cikin Riga da zani na dora Hijab babba har kasa, so nake nayi sauri na je kar naji magriba don yau zan karbi girki Ina so na dawo na masa abinci, tun da na fahimci baya wasa da cikin sa yasa nima bana masa wasa da abinci breakfast da dinner kullum suna kan dinning table na shirya plates da su serving spoons, bana sanin lokacin da yake zuwa yake ci sai dai in na sauko naga anci. Gyara masa part ma har na dan fara sabawa kuma Ina bakin kokari na ganin ko Ina fess yake don gudun kazanta. Gashi yau Yaya zata kawo min mai aiki shiyasa nake so duk inda 5 tayi ace Ina gida In sha Allah. Turare na fesa kadan na fito Ina tunanin ya kama ta dai na kira mai gidan na fada masa zan fita tun da ai ba zaman kai na nake ba. Sauko wa nayi Ina tunani gashi bani da number din sa balle na kira sa kuma bana son na makara don karfe 8 har tayi. Ina sauko wa shi kuma yana shigo wa, zuba mata ido yayi yana kallon ta tun daga sama har kasa da mamaki a fuskar sa, ba wai ganin ta da hijab bane ya basa mamaki don in wannan ne ya riga ya saba ganin ta da jaka da alama kuma fita zata yi shine ya basa mamaki. Kenan da bai zo ba fita zata yi kawai bata tambaye saba yayi wannan maganar a zuciyar sa. Ni kuma tun da ya shigo gabanta yake faduwa irin kallon da ya min kawai yasa naji jikina yana rawa rawa, mamaki nake yi ni yadda in har na kasance a gaban wannan yaron nake jin wani abu kamar tsoro tsoro. Cikin rawar baki nace “barka da Safiya”. Sai da ya dauki wasu seconds kafin yace “barka ashe fita zaki yi?” Da sauri na kalle sa Ina jin bugawar zuciya ta tana karu wa, dakiya na aro Ina tuna wa Kai na cewa wannan ba kowa bane fa a gaba na sai kanin baya na kuma ba wai Mijina bane kawai ya aure ni ne don ya taimaka min nan da shekara zai rabu da ni. Wannan tunanin ne ya bani kwarin gwiwar ce masa “eh dama Ynxu nake tunanin yadda zan fada ma tun da bani da number din ka, restaurant zan koma yau”. Folding hannun sa yayi ya jingina da jikin bango yace “da izinin wa”. Kallon sa nake yi da mamakin sa Wanda ya kasa boyuwa a fuska ta, da mamaki nace “to izinin wa zan nema da”. Ware manyan idon sa yayi yana kallon ta da tsananin mamakin wannan yarinyar, ynxu shi zata kalla tace masa da izinin wa. Gyada Kai yayi yace “izinin mijin ki, kuma a iya sani na ni kadai ne mijin naki koh?” Hade rai nayi na kawar da Kai gefe cikin haushi nace “plz ka dai na cewa wani Mijina don Allah, in muna tare mu biyu”. Manyan idon sa da suke masa yaji sbd haushin ta yace “ynxu ni kike cewa na dai na kiran Kai na mijin ki to sbd me?” Tabe baki nayi nace “ynxu kawai don Allah kana sa’ar autar mu kawai sai na ce Mijina ne Kai, ni Kai na fa kunya nake ji in na tuna cewa Ina matsa yin matar ka da fa gida daya muke har tsarkin pupu zan iya ma”. Ran sa in yayi dubu ya gama baci a duniya baya kaunar a dinga masa kallon karamin yaro amma shi wannan yarinyar take duba haka, gyada kai yayi yace “in kin isa da kan ki don Allah ki fita”. Daga haka ya juya ya fita yana banko mata kofa, Wallahi yayi alwashin yau dai sai ya koya wa yarinyar nan hankali ta yadda ko sunan sa taji sai gaban ta ya fadi lallai dole su raba rai ni ma wallahi, da wannan tunanin a ran sa ya fita ko kara leka part Yusrah bai yi ba don baya don ta gan sa cikin wannan yanayin. Gaba daya ni ma sai naji rai na ya baci, hade rai nayi sosai na koma sama ba don naso ba na ajiye jakar da Hijab dina, yadda naga tan sa a bacen nan sai naji Ina shakkar fitar dole ba don naso ba na koma na kwanta kawai ina ajiyar zuciya har bacci ya dauke ni. Ban tashi ba sai karfe 12, toilet ba shiga nayi brush na fito Ina kunkuni ni kadai duk rai na a bace, kasa na sauko na shiga kitchen na dora abinci gwanda nayi komai ynxu na huta. Tuwon shinkafa nayi da miyar alayyahu da taji kifi sai pepper soup da nayi, nasa daban na sa masa a flask ragowar nasa a normal flask sbd Yaya, kunun aya naji Ina sha’awar sha kawai na shiga hada wa, da wuta don haka a blender na markada aya ta kafin karfe hudu na gama komai nasa kunun Ayar a fridge. Dakin kasa na shiga nayi alwala nayi sallah ina kan dadduma naji door bell, mike wa nayi bayan na cire hijab din na fito ba bude. Yaya ce bayan ta kuma wata yarinya ce da baxa ta wuce shekara 13 ba tana rike da ledar data saka kayan ta. Matsa musu nayi cikin farin ciki nace sannu da zuwa Yaya. Shigowa sukai ita ma tana Murmushi a ran ta kara godewa Allah take wai yau Aasmaa ce a gidan Mijin ta abinda suka dade suna fata gashi ynxu lokaci yayi har an yi sati biyu. Gaishe ni yarinyar mai suna Binta tayi tana zaune daga gefen carpet. Fuska ta dauke da Murmushi na amsa mata don na yana da hankalin yarinyar da alama tana da tarbiyya. Zuwan Yaya ya dauke mun damuwa ta da haushin da na wuni da shi, falon sama muka je muka sha hirar mu Binta tana kasa tana kallo na kunna mata Arewa 24. Gab da Magriba na ce na dauki abubuwan da zan bukata na gyara part din sa na dauki key na fito tare da Binta wacce na bata basket din dana zuba flask din abinci a ciki tun da Yaya tana naga gwanda na Kai masa can. A bakin kofa nace ma Binta ta tsaya ni kuma na shiga ciki, sai da na ajiye abubuwan dake hannu na sannan na fito na karbi basket din nace ta koma. Gyara part din na shiga yi duk da na wani datti amma haka na gyare shi tsaf, bedroom din sa na shiga don dama haka nake shi nake bari na karshe a gyara. Kan gadon na nufa don na gyara na cire shinfidar, Ina jan bargon bra da pant sai boxer suka fado, da sauri nayi baya cikin wani irin bugawar kirji. Gadon nabi da kallo hankali na yana tashi ni ba yarinya bace duk da Ynxu nayi aure kuma ba abinda ya shiga tsakanina da Mijin amma ai daga kallo daya na gadon nasan ansha gumurzo a Kai. Kai na naji yana juyawa Ina sake bin boxer din da kallo, da sauri na rintse idona dai dai lokacin naji an bude kofar da sauri. Juyawa nayi don ganin wane ya bude kofar ya shigo……. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 31 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Kiran Sallah ne ya farkar da Abdallah daga baccin da yake yi, a nutse ya kalli Aasmaa shafa kan ta yayi yaji jikin ta yayi zafi sosai. Sunkuya wa yayi ya manna mata peck a goshin ta sannan ya mike ya shige toilet, wanka ya sake yi yayi alwala. Jallabiya ya zira ya nufo gadon don ya tashe ta suyi sallah, shafa kan ta ya shiga yi cike da zallar kaunar ta da yake ji tana kara ninkuwa a zuciyar sa ya shiga hura mata iskar bakin sa a hankali a kan fuskar ta. Ganin bata motsa ba yasa shi dan bubbuga hannun ta, still bata motsa ba sai wani numfashi da take yi kamar mai asthma. Cikin tashin hankali ya shiga toilet ya debo ruwa ac cup yazo ya shafa mata a fuska amma bata tashi ba, rasa in da zai saka kan sa yaji dadi yayi kawai ya juya a guje ya dauko jallabiyar sa ya saka mata, ko hijab bai iya tsayawa ya samata ba ya dauke ta cak ya fisgi key din motar sa dake ajiye akan mirrow ya fito a guje. A bayan mota a ya sata ya shiga gurin driver yaja a guje already dama gate man ya riga ya bude masa kofar don tun da ga yadda yaga mai gidan nasa ya fito yasan ba lafiya. Asibitin da su Mami suke zuwa ya kai ta kasancewar na kudi ne ko yaushe da akwai doctor, ya kuma ci sa’a Doctor Hafsa na nan family doctor din su. Ita ta duba Aasmaa sosai tayi mamakin barnar da Abdallahn yayi tun da tana da labarin auren da ya sake yi, ana ganin sa shiru shiru ashe ya iya ta’asa har haka. Dinki aka ma Yaya Aasmaa ta sha kuka abinta tana jawa Abdallah Allah ya isa a ran ta, ana gama mata dinkin doctor Hafsa ta mata allurar bacci. Fito wa tayi daga dakin da aka kwantar da Aasmaa din lokacin har 6:30 tayi, ganin yadda Abdallah yke zagaye ya rungume hannun sa a bayan sa ya kusa sata dariya ta dai daure tace ya same ta a office. Kallon Doctor Hafsa Abdallah yake yi kamar baya gane bayanin ta. Da mamaki yace “ynxu doctor daga sharar fage har na yaga ta sai da aka mata dinki”. Bata fuska Doctor Hafsa tayi tace “dinki ciki da waje na don haka plz Abdallah ka daga mata kafa ko nan da sati biyu ne kafin ka Kara”. Kankance ido yayi yana kallon Doctor da iya gaskiyar sa yace “gaskiya baxan iya ba”. Tagumi Doctor Hafsa tayi tace “kokari zaka yi ko dan ta warke sosai don taji rauni gaskiya”. Gyada Kai kawai yayi ba wai don ya amince ba shi ai ba don anyi mata dinki ba bai ki ba ma ya mata dadin baki suna komawa gida a sake. Duban ta ya sake yi yace “ynxu yaushe za’a sallame mu”. “Eh zuwa anjima in sha Allah in ta farka zaku iya tafiya sai dai zaka dawo da ita nan da sati don na duba dinkin, amma in naga Ina da tym zan iya zuwa har gida ma na duba kawai”. Godiya ya sake mata ya mike ya dauki takardar magungunan da ta rubuta ya fita. Sai da ya fara zuwa masallaci yayi sallah sannan ya shiga mota ya koma gida, wanka yayi y shirya cikin manyan kaya farare kal don yau jin sa yke a angon sa sai fara’a yake yi. Part din Yusrah ya shiga tana zaune akan kujera a kasa tayi wanka ya zira simple doguwar riga batai kwalliya ba sai dai tayi kyau sosai ta kara haske. Ba karamin burgesa tayi ba har bai san lokacin daya isa kusa da ita ba ya zauna a kasa yana shafa fuskar ya da ta Kara laushi da kumatu masu kyau. Cikin bacci ta bude idon ta, ganin sa a zaune a kasa ya sa ta kokarin mikewa don ya gaishe sa. Bai bar ta ta mike ba shi ya tashi ya dauke ta ya shiga hawa sama da ita, a dakin ta ya sauke ta yaja hannun ta har kan gado ya kwantar da ita. Mikewa yayi yana yarfe hannun sa cike da zolaya yace “gaskiya Wifey kin kara nauyi saura kadan na karya hannu”. Harara ta sakar masa tana turo baki a shagwabe, dariya yayi cikin nishadi ya sunkuyo ya manna mata kiss a lips. Bai fita ba sai da yaga ta koma bacci sannan ya fita yana murmushi, ya amince Yusrah mahadin farin cikin sace duk irin nishadin da yake ciki a yau da yayi arba da ita sai yaji farin cikin sa ya Kara nunkuwa, ya tabbatar duk wani kwanciyar hankali da nutsuwa da yke samu ynxu bisa jajircewar Yusrah ce, da ace lokacin daya zo mata da maganar zai Kara aure ta tashi hankalin ta da ba wannan zancen ake ba. Murmushi ya saki yace “I love u Wifey Allah ya miki albarka” ******** A hankali na shiga bude idona, ganin kamar asibiti yasa ni saurin kokarin mike wa. Doctor Hafsa data shigo Ynxu don ta duba ko ta tashi, ta taho da dan sauri ta kama ta cikin nutsuwa tace Sannu kin ji sister ki bi a hankali da akwai dinki a jikin ki. Kallon ta nayi kamar ban gane mai take nufi ba, rigar jikina na kalla ganin Jallabiya ce yasa ni saurin rintse idona abinda yaron nan ya min yana dawowa a Kai na. Kuka na fashe da shi kawai cike da takaici da bakin ciki, ni kadai nasan abinda nake ji akan wannan wulakancin da yayi min har ciwo yaji min ashe. Ganin yadda take kuka yasa Doctor Hafsa fara rarrashin ta tana mata fada kuma a nutse akan yadda tayi gardama bayan mijin tane sbd yadda taga abin tasan tazo da gardama, cigaba da fada mata yadda zata kula da kan ta tayi har ta warke. Suna cikin maganar ya turo kofar ya shigo hannun sa rike da yar karamar jakar daya sako mata hijab. Ganin yadda take kuka yasa shi karasowa ciki da sauri, hannun sa yasa ya riko duka kafadun ta cikin kulawa yace “ina ke miki ciwo *NOORIE*” Bakin ciki ne ya cika mun zuciya jin sunan daya kira ni da shi ni Wallahi tsanar sa ma nake ji a rai na sbd irin wulakancin da yamin bayan yasan auren da muka yi. Ban dai ce komai ba sbd Doctor da take gurin, sallamar mu tayi shi da kan sa ya zira min hijab sai wani rawar jiki yake yana ta jero min Sannu. Da kyar nake taka wa Ina hawaye sai goge hawayen nake amma wasu ke zubo wa, a mota ma ko uhm ban ce masa ba sai magana yake mun yana bani hakuri da lallashi ko kallon sa ban yi ba bare yasa ran zan basa amsa. Muna zuwa gida na bude kofar na fito da kyar cike da dauriya na shiga takawa, Ina jin tahowar sa a bayana ban tsaya ba kuma ban juya ba har na isa kofar part dina. Bude kofar nayi na shiga a dan tsanake nabi ko Ina da kallo ko mai fess sai kamshi palon yake da alama Binta ta gyara ko Ina. Sama na shiga hawa da kyar Ina hawaye har na isa daki na, Ina zuwa na shiga toilet na rufe kofar, ruwan dumi na tara a bathtub mai yawa na shiga ciki Ina gasa jikina ina kuka, sai da naji dan dama dama sannan na nayi wanka nayi alwala na fito daure da towel. Duk da na gan sa zaune akan kujerar dake dakin ban nuna na san yana gun ba na tsaya bakin mirrow na dibi abubuwan da nake da bukata na bude wardrobe ma na dauki kayan da zan sa na shige toilet. Ajiyar zuciya Abdallah yayi cikin shakkar ta, shi Wallahi bai taba jin yana tsoron mace ba sai ynxu da yake jin tsoron Husna yana kama sa, so yake yaje yayi mata magana amma ya kasa sbd yana tsoron abin da zai fito daga bakin ta……. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 33 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM A hankali rayuwa take tafiya yau har nayi wata biyu da aure kuma wata daya kenan da sati biyu da abin nan ya faru. A cikin kwanakin nan nayi matukar mamaki yadda Abdallah ya cika alkawarin sa, ko hannu na bai kara rike wa ba ko da a kuskure ya dan taba ni cikin azama zai matsa gefe yace min nayi hakuri, duk ranar daba ranar girki na ba zai shigo da Asuba ya duba ni kuma zai shigo da daddare ya min sai da safe, in kuwa ranar girki nane baxan iya kirga sau nawa yake shigo wa ba in har yana gida. Tsakani na da shi sai dai gaisuwa da kuma girki da bana fashin masa breakfast da dinner In weekend ne dai nake masa lunch, a kan dining nake ajiye masa da daga baya kuma kawai in har na gama sai na kai masa part din sa, bana fashin gyara masa part dai duk ranar girki na. In nace ban yi kewar sa ba nayi karya don duk da uwar azabar da na sha a hannun sa amma in na tuna da abubuwan da yamun kafin naji azabar sai tsigar jikina ta tashi, ni ynxu ba wai mai azabar nake so ba kawai dai ayi romance dai amma ban san yadda zan tunkare sa da wannan maganar ba don abin da kunya ai. Gashi tun Ina nuku nuku da naji abin dai ni zai wahalar sai na fara shigar daukar hankali duk lokacin da nasan zai shigo sai na ki sa hijab in kuwa dare ne haka zan sa rigar bacci mai shara shara amma baya kallona in yaga irin shiga ta ma baya dade wa yake fita dà sauri, wannan abun ba karamin daga min hankali yake ba. A bangaren Abdallah kuwa ba karamin tashin hankali yake ciki ba na rashin Aasmaa, duk ranar girkin ta a wahale yake kwana kuma ya riga yayi wa kan sa alkawarin baxan taba ta ba har sai da amincewar ta, shaukin sa daya yana da Yusrah wacce sai ynxu yake kara ganin kimar ta sosai. Da akwai lokacin da yana bacci yana mafarki Aasmaa sai kiran sunan ta yake yi ashe Yusrahn wacce ta tashi tana sallah tana Jin sa, sai da ya farka take ce masa in har yana kewar Aasmaa din ne ta yafe masa kwanan ta yaje gurin ta daga haka ta mike ta dauki carbin ta ta bar dakin. Wannan abun ba karamin kunyar Yusrah ya kara masa ba, Washe gari da safe haka yayi ta boye boyen ido baya so su hada ido ita kuwa tayi ta tsokanar sa tana kwaikwayon yadda yake yi daga karshe kawai sai ya biye mata shikenan maganar ya wuce. Kullum cikin tura wa Aasmaa yake da sakon soyyaya baya gajiya da tura mata bata taba masa reply ba amma bai damu ba so yake ta amince da soyayyar sa ta kuma yadda cewa ba wai jikinta yake so ba. Amma Allah ya sani ya jigatu matukar gaske da rashin ta, ko hannun ta yake rikewa yasan da ya rage har yar rama yayi sbd kewar ta shi dana sanin dandana zumar tata ma yake tun da ai da bai san yadda take ba yncu kuwa azabtuwa kawai yake yi akan ta. ***** Ina zaune a palo sanye da riga da skirt na lace Wanda ya kama ni sosai ya min kyau, rigar daga sama ta kama ni sosai har balloons din ana hango su, na saka siririyar sarki mai heart da dankunnen ta sai kamshi nake yi. Zama nayi Ina jiran dawowar su don ya fita kai Yusrah asibiti da zasu fita yazo ya fada min bata Jin dadi zai kai ta shine nake jira in sun dawo naje na mata sannu. Binta tana kitchen tana yanka min carrots don yau danderu nake sha’awar ci Ina so nasa carrots kuma a ciki. Bude kofar da aka yi ne yasa ni kallon mai shigowar. Shine ya shigo yana sanye da riga da wando farare kar wanda suka masa kyau matuka, lumshe ido na nayi wani wutar kaunar sa tana kara ruruwa a zuciya ta. Ji nake kamar na tashi na fada jikin sa kawai ko na huta da azabar da nake ji. Kamar wacce aka tsikara kuma na bude idona na zuba masa sai Murmushi yake yi, mike wa nayi tsaye cikin wani salo na kasa kasa da murya nace “barka da rana”. Murmushi yayi yace “barka kadai Noorie”. Juya ido nayi wanda ni kai na ban San lokacin da nayi sa ba sbd jin dadin sunan sa yake kira na dashi, kallon sa nayi kasa kasa nace “ya mai jikin?”. Murmushi ya saki sosai ynxu yace “tana lafiya qalau ai abin murna ne ma Alhamdulillah Ya Rabb”. Kallon sa nayi cikin rashin fahimta. Murmushi yayi yace “kun kusa zama iyaye in sha Allah nan da 6 months”. Ware ido nayi cikin murna nace “ciki ne da ita?”. Dariya yayi yana daga min Kai. Nima sai nayi karamar dariya nace “Allah ya raya ya kuma sauke ta lafiya”. Murmushi ya Kara saki yace “Ameen Ya Rabbi bara na je gurin nata dama cewa nayi bara nazo na fada miki mun dawo”. Gyada kai nayi nace “nima in sha Allah anjima zan shiga” Murmushi kawai ya saki yana bin ta da kallo ta kasan ido, shi kadai yasan abinda yake ji ya fara tunanin karya alkawarin sa gaskiya don ya gama fahimtar Husna kashe sa take son yi kawai. Ni kuwa ganin irin kallon da yake min yasa ni juyawa na nufi kitchen Ina wata tafiya dana tabbatar zata tayar masa da hankali, ta kuwa tayar din don baya yayi sbd wani jiri daya ji ya kwashe sa. Lumshe ido yayi yana sauke wata wawuyar ajiyar zuciya, sai da ya dan nutsu sannan ya fita daga part din. Dandarun ma tsaya nayi na dibar ma Yusrah sai lemon kankana dana mata na zuba mata a jug, sama na koma nayi wanka don duk kamshin spices nake yi na zira abaya maroon color wacce tayi min kyau sosai, bata da ado ko kadan sai jela da take da ita wacce ake daure wa, mayafin abayar na yafa ma dan fesa turare sama sama tun da gurin mai karamin ciki zami zai iya yuwa bata son kamshi sosai. A basket na zira flask da jug din na dauka na nufi part din ta gaba na yana dan faduwa sbd tun haduwar mu da ita lokacin da Ina gyara part din mai gidan bamu sake haduwa ba. Door bell na danna ban dade a tsaye ba mai aikin ta tazo ta bude min. Sa kai na nayi a ciki a hankali Ina cire takalma na daga bakin kofa, a takaice na karewa Kayan palon kallo komai irin nawa ne banbancin color kawai da kuma wasu frames din. Zama zanyi akan kujerar mai aikin tace min na hau sama suna palon sama, kamar dai kar na hau sai kuma na mike Ina tunanin ai tunda tace na hau maybe sun fada mata ne. Hawa na shiga yi tun da kafata ba takalmi ba lallai suji takowa ta ba, sai da gabana ya fadi sbd yadda na gansu, suna zaune akan kujera daya ita ta kwantar da kan ta ne akan hannun kujerar hannun ta rike da goro tana ci shi kuma ya daura kafafun ta akan cinyar sa yana matsa mata a hankali. A tare suka jiyo suka kalle ni da mugun sauri Yusrah ta janye kafafun ta daga kan cinyar Abdallah, saurin da tayi sai da Abdallah ya riko ta yace yi a hankali Wifey plz kar kiji ciwo. Murmushi kawai tayi tana kallon Aasman da take takowa a hankali, Murmushi nima nake sakar mata duk kuwa da irin zafin da kirji na yake min. Zama nayi akan kujerar dake kallon wacce suke nace “kuyi hakuri plz yarinyar data bude min ce tace na hawo so nayi tunanin ku kuka bata izinin haka”. Murmushi Yusrah tayi tace “bkm Aunty Ina wuni kwana da yawa”. Nima murmurshi na mata nace “lafiya qalau Yusrah ya jiki jiki Allah ya raba lafiya”. Sunkuyar da Kai tayi cike da kunya sai shine ya kalle ni yana murmushi yace “Ameen Noorie”. Dan satar kallon sa Yusrah tayi Jin sunan daya Kira Aasmaa da shi sai dai gudun shedan ya raya mata abu mara kyau tayi saurin addua a ran ta tana tuna wa kan wa matar sa ya fada wa haka fah ba wata ba. Basket din na dan tura mata nace “ga shi kanwata danderu ne nayi sai na zubo miki da lemon kankana”. Murmushi tayi tace “Ngd sosai Aunt Allah ya saka da alkhairi”. Murmurshi nima nayi nace “Ameen ya Rabbi, duk abin da kike so dai plz ki fada min kin ji kinga muna kusa sai da dafa miki in sha Allah”. Da sauri Yusrah ta girgiza Kai tace “haba Aunty bkm wallahi wannan ma na gode”. Zungurin ta Abdallah yai cikin zolaye yace “kee kanwata waya fada miki ana kin abincin Noorie da kika ganin ta haka babbar chef ceh”. Zaro manyan idon ta yusrah tayi tana tabe baki tace “Amma Yayana baka taba dan kafco min a leda ka kawo min ba”. A tare muka sa dariya gaba dayan mu Ina jin wata nutsuwa wacce tun da na shigo ban ji irin ta ba. Kallona Abdallahn yayi yana Langwabe Kai yace “ynxu Noorie shi wannan kayan dadin Wifey kawai kika kawo wa ni ban da ni kenan”. Kallona Yusrah tayi cikin dariya tace “Aunty Kice nawa ne ki kadai plz muga yadda Yaya zai yi da bakin cin nama”. Dariya nayi nace “na kanwata ne kadai gaskiya”. Turo baki yayi kamar yaro ya juyar da kai gefe yace “dama ai bakya sona baxa ki bani ba”. Wani irin faduwa gaba na yayi ban san lokacin da na ce masa “ni nace bana son ka”. Kallon da ya min yasa ni gane baranbatamar da nayi sai na waske Ina Murmushi kawai. Nayi wajen 30mins muna hira wanda karfin hirar Yusrah ce da Abdallahn ni sai dai nayi Murmushi kawai ko na ce eh ko a’a . Mike wa nayi nace “bara na tafi Yusrah me kike so amma zuwa anjima sai nasa a kawo miki”. Shiru tayi alamun tunani kafin ta dago ta kalle ni tace “wainar fulawa Aunty”. Yar dariya nayi nace “yncu kike so ko kuwa zuwa anjima”. Murmushi tayi tace “ko yaushe ne Aunty”. Mike wa Abdallah yayi yace “wifey bara na dan taka mata”. Daga masa Kai tayi tana kwantawa akan kujera. A tare muka sauko mun jeru muna tafiya a hankali, sai da muka isa har kofar part dina sannan ya tsaya ya kalle ni yace “Ngd sosai Noorie”. Tsayawa nayi na juyo na kalle sa Ina sarke hannu na nace “akan me kake min godiya”. Murmushi yayi yace “yadda kika nuna kulawa akan wifey ban yi tunanin haka ba”. Tsare sa nayi da ido cikin wani kallo nace “me yasa baka yi tunanin zan iya kula da ita ba?” Langwabe kai yayi yace “sbd ni bakya nuna kin damu da ni Noorie, don Allah kiyi hakuri ki yafe min wallahi kin hora ni da yawa baki ga yadda na rame ba wai ki tausaya wa Kanin ki”. Wata katuwar harara na sakar masa nace “kar ka kara cewa kai kanina ne Abdallah lokacin da ka min fata fata ai baka tuna cewa na girme ka ba”. Kasa kasa da murya yace “ki bani wata damar Allah a hankali zan yi”. Da sauri na kalle sa cikin mamaki nace “me zaka yi din….” DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 34 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Da sauri na kalle sa cikin mamaki nace “me zaka yi din”. Kasa kasa da murya yayi yace “na sake shiga gurin Allah a nutse zan yi kin ji Noorie nah”. Girgiza kai nayi da sauri na bude kofar Ina cewa “baka da kunya Allahu ya shirya ka”. Murmushi yayi yana dafe saitin zuciyar sa a hankali yace “ina matukar kaunar ki fiye da yadda nake son Kai na Heartbeat..” Ni kuwa Ina shiga ciki rufe kofar nayi da sauri Murmushi yana subuce min, a rai na Ina tunanin na fi sa son mu kasance tare amma kuma ban san yadda zan fada masa ba….. HAJJO Yau wata daya kenan da aka kawo mata amarya gaba daya ta rikice ne komai tana yin sa cikin rashin nutsu wa har ynxu ta kasa yadda cewa Kabeer ne ya Kara aure. Ba wai yana rashin adalci a tsakanin su ba yana iya bakin kokarin sa amma kawai ita gani take yi duk ranar da ya kasance girkin amaryar rawar jiki yake yi. Gashi amaryar ta zo ne da wani kissa na jan yaran ta a jiki, kullum suna gurin ta sbd in suka je sai abinda suke so take dafa musu gashi har homework ynxu ita take musu. Ta dake su akan su dai na zuwa gurin amaryar amma sun ki ji kullum suna dawowa daga makaranta Kaya kawai suke chanja wa zasu tafi gurin amaryar in kaga basa gurin ta to tayi baki ne Ko kuma baban su yana nan. Ita Ynxu babbar damuwar ta shine yadda zata yi kokari su shirya da Aasmaa don tana so taje ya bata hakuri, tayi ta kokarin kiran ta amma bata shiga wanke take tunanin ko blocking din ta tayi. Bata bata lokaci ba taje har gidan Umma ta bata hakuri akan abinda suka zo suka musu ita da Ummu, Murmushi kawai Umma tayi mata tace mata ya wuce In sha Allah ita dama bata rike ta ba. A gurin Umman ta karbi address din gidan Aasmaa ta tambayi Kabeer bai hana ta ba kuwa ya amince don shi kan sa ynxu zai so Aasmaa ta hakura ta cigaba da kula Hajjon ko dan yadda HAJJO ta zama ynxu duk ba nutsuwa ko yaushe a birkice take. Washe gari kuwa karfe goma tayi wanka ta shirya Kabeer ya sauke ta a kofar gate din gidan ya tafi bayan ya bata kudin motar dawowa yana fatan komai yayi dai dai tsakanin ta da Aasmaan. Tun da Hajjo ta shiga gidan take bin gidan da kallo da tsananin mamakin wai anan Aasmar tayi aure, part din Yusrah ya shiga mai aikin Yusrah ce tace mata ba nan ne part din Aasmaa din ba, tare suka fito da Hajjon ta kai ta har bakin part din Aasmaa sannan ya tafi. Binta ce ta bude kofar tana kallon Hajjon tana mata Murmushi, shigowa ciki Hajjo tayi ta zauna akan kujera. Ruwa da lemo Binta ta kawo wa Hajjo akan tray sannan tace “bara na Kira ta tana sama”. Murmushi kawai Hajjo tayi tana gyada kai tana bin palon da kallo cike da mamakin wai nan duka na Aasmaa ne. Ina kwance a daki ina chatting da Maryam Binta tayi knocking, mike wa nayi na bude mata kofar nace wani abunne Binta Daga kai tayi tace “Aunty bakuwa kika yi tana kasa”. Da mamaki nace “bakuwa kuma?” Gyada Kai tayi, juya wa nayi cikin dakin nace “kice mata ina zuwa” Ban yi wanka ba don haka na shiga toilet a gurguje nayi wanka na fito na shirya cikin Riga da zani, ban wani yi kwalliya ba powder kawai na shafa sai lip-balm mai danko. Waya ta na dauka na fito, tun kan na karaso nake kallon Hajjo da mamaki sosai, tana sanye da Hijab kuma fuskar ta ba kwalliya shine abin da ya bani mamaki. A sani na da Hajjo bata sa Hijab sai zata yi sallah kuma kullum fuskar ta bata rabuwa da kwalliya mai sauki har ta haihu kuwa, so tari muna shan fada da ita in zamu fita taga nasa Hijab dole nayi mamaki yau ita ce sanye da Hijab. Hajjoo kuwa kallon Aasmaa take cike da sha’awa ganin yadda tayi bul bul tayi kyau sosai sai kamshi take yi. Murmushi nayi Ina dafa kujerar da take gefen tata nace “wa nake gani kamar Hajjo”. Dariya tayi cikin kunya tace 0nice Aminiyar”. Dan kallon ta nayi jin sunan data kira ni da shi, sai nayi Murmushi kawai na zagayo na zauna, Binta na kira ta kawo mata kayan gara su dubulan a cikin wasu bowl masu kyau data dora akn tray. Sai bayan Binta ta shige dakin ta sannan na kalle ta nace “sannu Hajjo ya gida da yarana”. Tabe baki tayi tace “yaron ki suna nan lafiya qalau, gida kuwa sam ba dadi ko baki da labarin Abba ya kara aure ne”. Murmushi nayi nace “to ke ynxu Hajjo don Kabeer ya kara aure sai ki wani daga hankalin ki, kalle ki fa don Allah kamar ba Hajjon dana sani ba”. Girgiza kai tayi idon ta na ciko wa da kwalla tace “baxa ki gane bane wallahi Aasmaa amma ni kadai nasan abinda nake ji a zuciya ta gaba daya Kabeer hankalin sa baya kai na ynxu kar kiso kiga yadda yake rawar kafa duk ranar girkin ta”. Murmushi nayi nace “Allah ya kiyaye”. Kallona tayi galala tace “abinda zaki ce kenan Aasmaa” Kallon ta nayi nace “to me zan ce Hajjo”. Gyada Kai tayi tace “ni duk ba ma wannan ne ya kawo ni ba zuwa nayi na baki hakuri akan abinda na miki don Allah kiyi hakuri ki yafe min Aasmaa mu koma kama da don Allah” Murmushi nayi nace “Hajjo kenan maganar na yafe miki ni tuni na Riga na yafe miki, amma batun mu koma kamar da baxai taba yiwu wa ba Hajjo don kin riga kin nuna min matsa yi na, na karashe fuskata dauke da Murmushi”. Idol ta ne ya ciko da kwalla tace “don Allah ki yafe min Aminiyata wallahi ynxu na gane ba karamin hauka nayi ba da na miki abinda na miki, gaba daya Ynxu bana cikin nutsuwa ta amma na rasa wanda zan je gare sa ya bani shawara da kwarai ke kadai ce dama wacce take bani shawara kuma nayi amfani da ita naga dai dai ki yafe min”. Girgiza kai nayi ina dan Murmushi nace “bkm wallahi Hajjo ai maganar ya wuce kawai batun mu koma kamar da ne har abada”. Mike wa nayi nace “ina zuwa don Allah”. So nake na aika Binta ta tambayo Yusrah me take so nayi mata na kwadayi ban taba jin haushin rashin numbern ta da bani da shi ba sai ynxu. A dakin Binta na same ta nace taje ta tambayo Aunty me take zo nayi mata, na kuma bata waya ta nace tace ta samin numbern ta bani da ita. Dawowa nayi gurin Hajjo na zauna tana min hira ina amsawa ba wai na saki jiki da ita bane don ni daga kan ta dan Adam ya kara bani tsoro a iya tunani na yau in Kabeer yace wa Hajjo yana son aure na zata iya danne kishi ta amince duk da kuwa zaman kishi yafi karfin wasa amma tayi biris taje har gidan mu ta zage ita da yayar ta, taya kuwa take tunanin zan amince na mu koma kamar da. Binta ce ta shigo ta bani wayar tace “ta samun wai tama yi saving tace kuma don Allah in zata samu wainar fulawa irin ta jiya”. Gyada mata kai nayi nace “je ki yanka albasa babba guda daya ki kuma jajjaga attaruhu guda uku, in kin gama ki min magana”. “Toh” tace ta mike ta shige kitchen. Wayar na kunna na shiga call log naga tayi saving da kanwata, Murmushi nayi ina girgiza Kai yarinyar tana burgeni kuma Ina ganin darajar ta, a ynxu Nima ina addu’a Allah ya bani ikon koyi da ita a wasu halayen nata, na kara ganin darajar ta da kimar ga a jiya da Abdallah yake yaba girki na a gabanta amma ko alamun sauyin fuska ban gani a tattare da ita ba sai ma biye masa da tayi wanda nayi imani da nice sai rai na ya sosu don kuwa ni ina da kishi matuka wanda nake Addu’a Allah ya sassauta min. Wainar flour din na mata wadda nayi da manja, guda biyun da na fara yi na sa yaji na bawa Binta ta kai mata don kowa yasan wainar flour tafi dadi daga kasko sai kitchen. Ina soya ta hudu suka shigo ita da Binta hannun ta rike da plate din tana dangwalar yaji. Kallon Hajjo tayi ta gaishe ta ta nufi kitchen inda take jiyo kamshin wainar tana lumshe ido. Ina tsaye naga ta shigo juyo wa nayi na kalle ta tana sanye da riga wacce ta sauko mata har gurin gwiwa sai wando palazzo ta yafa mayafi dan daidai tayi kyau sosai ta kara wani haske. Dariya nayi nace “kika biyo ta kuma kanwata”. Lumshe ido tayi tana hayewa kan table din dake tsakiyar kitchen tace “Aunty ina kwana, ai ina ci naji baxan iya jira ba Allah ni kamshin ma kawai nake son shaka”. Murmushi nayi nace “lafiya qalau kawo plate din to na sa miki wannan”. Miko min tayi na sa mata na cigaba da suyar tana min santin dole Yayanta ya rikice da girkina itama gaskiya a dinga hada kwano da ita, Murmushi kawai nayi ina cigaba da suyar. Ina soya kaskon karshen muka ji shigowar sa, yana tsaye a bakin kitchen ya zuba hannayen sa duka a cikin aljihu yana kallon mu fuskar sa dauke da Murmushi a ran sa addu’a yake Allah ya dawwamar da wannan zaman lafiyar har abada a cikin gidan sa……. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 35 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Yusrah ce tayi Murmushi tace “Yayana me kazo yi nan kuma”. Hararar ta yayi da wasa yace “tambaya ta kike ma mai nazo yi koh, na shiga part dinki aka ce bakya nan kina nan ashe dadi kike ci son ran ki anan”. Fari tayi da ido tace “Auntyna tana so na shine take min wainar flour”. Dan hade rai yayi yace “ni bata so na kenan koh”. Da sauri ta waro ido tana rufe baki ta kalle ni tace “Aunty ba ruwana wannan maganar ke zaki bada amsar ta”. Satar kallon sa nayi naga yadda ya zuba min ido yana murmushi kawai nima sai na saki Murmushi ina kallon sa, shaf mun manta yusrah tana gurin kallon juna kawai muke muna Murmushi. Yusrah kallon su take tana jin wani irin zafi a zuciyar ta, tabbas kishi gaskiya ne duk irin yadda take kokarin rike kishin ta ashe don basu cika haduwa su uku bane a guri daya, daga kallon da suke wa juna zaka fahimci tabbas ba karamin soyayya suke wa junan su ba. Hawayen daya zubo mata tayi saurin goge wa tana karanta addu’a a zuciyar ta har lokacin kuma kallon juna suke yi cike da kaunar da bakunan su baxai fadu ba. A nutse ta sauko tayi dan tafi tana Murmushin yake, cikin tsokana tace “kaga masoya irin wannan kallo haka gaskiya bara na baku waje” ta fada tana yar dariya kawai ta sa kai ta fice daga kitchen din. Ajiyar zuciya na sauke duk sai naji ba dadi kallon sa nayi Ina dan langwabe kai nace “kaga ni koh, ka tsattsare ni da ido bayan tana zaune baxa taji dadi ba, bana son na zama sillar motsawar kishin ta don Allah”. Ajiyar zuciya ya sauke yace “baxan taba yin abinda zai sosa zuciyar kanwata Ina sane ba sbd tana da matukar daraja da kima a idona bara na bi bayan ta sa min wainar flour din na tafar mata da shi”. Saka masa nayi na zuba yaji a gefe na basa ya tafi duk rai na ba dadi muna zaman mu cikin farin ciki, dan Murmushi nayi sbd ni ma rai na ya dan sosu da yadda ya fadi matsayin ta a gabana lallai kishi bala’i neh. Koma wa nayi gurin Hajjo muka cigaba da hira ban bata fuskar da zata min maganar Yusrah ko Abdallah ba ita ma ganin ba fuska sai tayi shiru bata ce ba. A dakin ta ya same ta ta fito daga toilet tana goge fuskar ta da towel idon ta yayi ja alamun kuka tayi. Kallo daya ta masa ta dauke kai kamar bata gan sa ta zauna a gefen gado tana shafa aboniki a kafafun ta da suke dan mata zafi. Durkusa wa yayi a gabanta ya karbi man zafin yana shafa mata, bai ce mata komai ba sai da yaga ya shiga toilet ya wanko hannun sa sannan ya kawo wainar ya Mika mata. Murmushi tayi tace “na koshi”. Zama yayi a gefen ta yace “plz kanwata kar ki ce fushi zaki yi da yayanki uhm”. Zaro ido tayi tace “akan me zanyi fushi da kai Yaya me kayi min”. Girgiza kai kawai yayi yana kallon ta, cikin sigar lallashi ya shiga fada mata maganganu dake nuni da yadda yake daraja ta da ganin kimar ta ya karasa da fada mata matsayin sa a zuciyar ta da wadannanan kalamun nasa ta sake har tana murmushi. Sai azahar Hajjo ta tafi bayan taci abinci. Ina sallah na shiga kitchen ni da Binta muka shiga aiki, tuwon semo nayi da miyar alayyahu sai Zogale da na hada na kuma yi kunun aya, dukkan abin da na dafa sai da na zuba wa Yusrah na ba wa Binta ta kai mata. Karfe 6 na shiga part dinsa yau special gyara nayi masa don yau fa karshen hakuri na ya kare gaskiya ko romance ne sai anyi. Kayan abincin na dauka na kai na jera a part din sa a gurguje na dawo nayi wanka na shirya cikin Riga da wando na Pakistan, nayi kyau sosai Kai na da yake tsefe na taje na shafa masa mai sai kamshi yake. Sai da nayi wa jikina barin turare sannan na dauki wayata na fito na nufi part din sa gabana yana dan faduwa. Yana zaune akan dining da alama serving kansa zai yi. Murmushi na sakar masa na dan durkusa nace “Barka da yamma an dawo lafiya”. Ware ido yayi da mamaki ganin wai yau shi Husna take durkusawa ta gaishe sa, kasa gasgatawa yayi sai da yace “wai ni kika durkusawa da gaske?” Wani kallo na masa Ina mike wa na shiga serving din sa abincin. Ya zage ciki kuwa yaci sosai kwadan zogalen ne dai yace na bar sa in ya dawo daga sallar isha’i sai muci tare. Kunun ayar dai sai da ya kusa shanye sa sannan ya ajiye ya nufi palo. Kwashe plates din daya bata nayi na shiga kitchen na wanke komai sannan na dawo na zauna a palon nima ina kallon TV duk a matse nake ji nake kamar na tashi na koma kusa da shi amma Ina daure wa. Zaman kurame muke yi kowa da abinda yake saka wa a ran sa, sallar isha ne ya tashe ni na koma part dina. Kankana na dauko a fridge na yayyanka ta na zuba madara da zuma sai dabino da na bare, sai da na cika cikina dam da shi sannan na mike na nufi sama yau nayi alkawarin a part din sa zan kwana in sha Allah. Wanka nayi na musamman na shafa mai, jikina nabi da humra masu kamshi sosai sannan na dauki rigar bacci ta iya cinya ce mai siraran hannu, kunya ce ta kamani dana tuno wai duk wannan abin da nake yi sbd Wanda ya ke sa’an autar mu ne sai nayi saurin kawar da tunanin na zira rigar ban sa bra ba don dama bani iya kwanciya da ita. Powder na sa da kwalli nasa lipstick fari na kara bin jikina da turare. Hijab na sa na dauki swt na sa a baki na ban dauki waya ta ba tun da dama a cike take sai na ajiye ta kawai na dauki karamar na fito bayan na rufe dakina da key na boye a dayan dakin. Sai da safe nayi wa Binta na dauki flask din dana dafa masa tea na nufi part din sa. Yana zaune yana kallon ball na shigo baki na dauke da Sallama, a hankali ya amsa yana bina da wani kallo cike da mamakin ta. Zama nayi a gefen kujerar da yke zaune nace “sannu da hutawa”. Lumshe idonsa yayi yace “yauwa Noorie”. Nima lumshe nawa idon nayi nace “na zubo ma tea din ne”. Da sauri ya tashi ya kashe TV yace “no bacci nake ji sai da safe” ya shige daki ya bar kofa a bude, zagaye ya shiga yi a dakin yana addua Allah yasa ta shigo sai leke yake yaga ta taho amma tana xaune. Ni kuwa shiru nayi Ina tunanin na bisa dakin ne ko kar na bisa amma azahar da nake ji a kasa na na tabbatar yau in ba an sosa min ba baxan iya bacci ba. Ajiyar zuciya na sauke gabana yana faduwa ina tsoron azabar dana ci wancan lokacin haka dai na daure na nufi dakin gabana yana faduwa. DijahAM 09066728387 I You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 36 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Yana ganin tahowar ta yayi tsalle ya tafi gado a sukwane ko jallabiyar jikin sa bai cire ba ya kwanta yaja bargo ya rufe jikin sa shi ala dole bacci yake yi. A sanyaye na shigo dakin ina tuno abinda ya faru da ni wancan karan, rufe kofar nayi na lumshe idona. Na dan jima a tsayen kafin na sauke wata boyayyiyar ajiyar zuciya na shiga tako wa zuwa gurin gadon. Sai da na hau sannan na cire Hijab dina na ajiye akan bed side drower. Da sauri Abdallah ya mike yana rintse ido da karfi don wallahi yadda yaga surar ta ba abinda zai hana shi danne ta. Cikin rawar baki yace plz Noorie ki fita don Allah kar na saba alkawarin dana daukar miki baxan iya jurar ganin ki a haka ba don Allah ki taimaka min ki fita. Duk sai naji ba dadi ganin cewa hakkin sa ne amma yake nisanta kansa da karba kawai don ya nuna min cewa da gaske yana sona ba wai jikina yake so ba. Mike wa nima nayi cikin nutsuwa na shiga tako wa har na iso gare sa, ban yi wata wata ba kawai na fada jikan sa. Wata wawuyar ajiyar zuciya ya sauke yana rungume ni tsam a jikan sa ji yake kamar ya fashe da kuka ko zata tausaya masa ta fahimci irin son da take masa. Cikin rawar murya yace “Allah ne shaida ta NOORUL HAYAT ina matukar kaunar ki wallahi ba sha’awar ki nake ji ba tun ranar dana fara ganin ki nake matukar son ki ina boye wa ne kawai sbd a da ban san yadda zan nuna ina son ki ba duba da cewa….” Hannu nasa na rufe bakin sa n dago ina kallon idon sa, lumshe masa ido nayi nace “ba sai ka fada min ba iya abinda nake ganin a idon ka ma kawai ya ishe ni hujja”. Manne bakin mu yayi yana bata wani kalar kiss mai zautar da mutun, ban san lokacin dana shiga mayar masa da martani ba cike da wani salo da ya kusa zautar da shi. Soyayya muke gwadawa juna a aikace gaba daya bama hayyacin mu baki baxai iya buduwa ya fadi abinda muke ji akan juna ba amma aikin mu ya nuna. Kalar soyayyar da yake gwada min ta tsaya min a rai sosai ta kuma Kara min wata zazzafar kaunar sa da kishin sa a rai na. Lokacin da yake karanto addu’a sai da na kusa ture sa amma na daure na bar sa ko dan ya samu cikakkiyar nutsuwa, ba karamar wahala nasha a hannun sa ba wai a haka ma don yana sassauta min ce a cewar sa amma ni kuwa na ji jiki. Da kansa ya gasa ni yau ban hana sa ba sai kukan shagwaba nake yi yana biye min yana jera mun sannu, rungume da juna bacci ya dauke mu. Shi ne ya tashe mu sallar asuba, sai da na gasa jikina sannan na kuskure baki na mouthwash tun da bani da brush a dakin duk kuwa da ina gani wasu sababbi a cikin drower ban dauka ba. Salla nayi kafin ya dawo na gyara gado amma yana dawo wa ya dauke ni cak muka koma kan gadon yana kara laluba ta. Ynxu kuwa kuka na masa sosai sannan ya rabu da ni sai hakuri yake bani ni. Wanka muka yi ya kwanta bacci ni kam ban koma ba duk da yadda nake jin jiki haka a daddafe na gyara masa part din sama sama na koma part dina. Breakfast na mana na koma sama nayi wanka na shirya na sauko na dauki breakfast din na Kai masa part din sa. Yinin ranar tare muka yi sa duk inda nasa kafa ta yana biye da ni ko fita bai yi ba duk kuwa da yadda Musbahu ke danna masa kira. Kwana biyun na nayi na girki na mun yi sane cike da bawa juna wata soyayya mai zafi, a kwanakin nan da nayi da shi na fara karantar sa na jinjinawa Yusrah yadda bata tayar da hankalin ta ba da ya auro ni. Ni yau da zan fita daga girki wani irin kishin sa nake ji bana in na tuno duk abinda yake min shi zai yiwa Yusrah da kyar na samu bacci ma ya dauke ni bayan nayi sallah don dana kwanta tuno sa kawai nake yi Ina hasaso haka yake kashe Yusrah ma da wannan kalar soyayyar. Soyayya muke gudanar wa mai kyau da tsafta, ya siya min mota iri daya ce da wacce ya siya wa Yusrah color ce kawai ta banbantasu, ya chanja min waya mai tsada komai dai sai dai nace Alhamdulillah. Na kara cika na yi kyau sosai kowa y ganin yasan Ina cikin kwanciyar hankali, duk ranar weekend ya yamma muke fita ni da shi yana koya min mota, Yusrah yace ta bari ta haihu sbd cikin ta da ynxu ya shiga wata biyar. Shirye shiryen azumi ake wanda muke fatan gobe ne za’a dauki azumin, ban taba fita ba tsawon wata biyar dinnan sai yau da yace mu shirya anjima zai zo ya dauke mu zamu je gidan su. Tun da ya fada min haka ban zauna ba na fito da naman da yake freezer na shiga aikin dambun nama, ban taba haduwa da Sirika nawa ba duk da nasan baxan taba kamo matsayin Yusrah ba tun da ita yar su ce amma zan so nima ace na samu fada dai, sau daya kannan sa suka taba zuwa Sultan da Sultana sai Auta kanin Yusrah. Kafin 2 na gama lafiyyar fried rice da potato salad sai kunun aya da na yi ga dambun nawa, sai kayan snacks. Duk na dibar wa Yusrah na bawa Binta ta kai ma don tun da cikin ta ya shiga wata biyar ba abinda bata ci kuma cikin yazo mata da ci sosai. Wanka nayi na shirya cikin lifaya yellow mai tsada da taushi a lefena take duk da ban san kudin ta ba amma nasan zata yi tsada. Ina cikin fesa turare ya shigo yasha manyan kaya sai kamshi yake. Murmushi na sakar cikin wani salo na shiga tafiya Ina zuwa daidai shi na fada jikinsa a hankali yadda nasan cewa balloons din zasu taba sa yaji su sosoi. Ya kuwa ji sun don Lumshe ido yayi ya riko waist dina sosai, sunkuyo da fuskar sa yayi dai dai fuskata yana shinshinar kamshin dake tashi a jikina. Dariya nayi na raba jikina da nasa nace “ba ruwana Hub kar ka bata min kwalliya ta”. Lumshe idon sa yayi yace “Noorie ko kiss ne plz ki bani mana”. Dariya nayi nace “sannun ka Hub da ban san ka bane dai”. Shima dariya yayi, a tare muka sauko flasks din na dauki wasu na basa wasu ma sannan Binta ta rike wasu muka fito tare. Baya na bude na shiga don yau girkin Yusrah ne kuma shine fitar da zamu fara yi mu uku a tare. Ina zaune na hango su sun taho yana rike da ita tasha kwalliya cikin doguwar riga ta kara kiba wacce ta mata kyau, sai Murmushi take da alama wata maganar yake fada mata da ta mata dadi sosai. Lumshe ido nayi kishin sa yana taso min ina addu’a don na danne sa. Bude mata yayi ta shigo muka gaisa tana min godiyar abincin da Binta ta Kai mata. Hira muke yi jefi jefi gabana yana faduwa ina Jin tsoron tarbar da zan samu daga sirikata.. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 37 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tun da muka shiga cikin gidan gaba na yake faduwa a hankali, addu’a kawai nake yi. Yusrah cikin farin ciki ta fito don tayi kewar gida sosai duk da dai bayan sake auren Yayan nata tazo har sai biyu amma ynxu kusan wata biyu kenan. Cikin sanyin jiki na fito su Sultana da suke zaune a compound din gidan suna ganin mu suka taso a guje suka zo suka rungumw ni, Nima rungume su nayi Ina tambayar su ya school. Su ne suka dauko kayan abincin da nayi suna min hira har muka isa part din Mami. Da Sallama na shiga idona ya sauka cikin nata tana zaune cikin shiga ta alfarka sai Murmushi take mana. Da sauri na sunkuyar da Kai na kasa har muka karasa cikin palon, cikin girmamawa muka gaishe ta ta amsa mana kuwa ba tare data nuna banbanci ba. Kallon Yusrah Mami tayi tace “sannu Yusrah Allah ya raba lafiya”. Sunkuyar da Kai tayi sai mune muka amsa da Ameen. Kallona tayi tace “sannu Aasma ya gida”. Kara sunkuyar da kai na nayi nace “lafiya qalau Mami”. Murmushi tayi tace “Allah yayi muku albarka Toh”. Gaba dayan mu muka amsa wannan karon, mun dan jima tana mana nasiha sannan tace na mike nabi Yusrah mu gaisa da Mummy. Tare da Yusrah muka je part din Mummy nan ma ta karbe mu cikin fara’a sosai, na dan zauna kusan 30mins sannan nayi mata Sallama na koma part din Mami. A nan na tarar da Teema a zaune tana cin mat pie din da nayi. Gaisawa mukai yau dai bata min rashin kunya ba ko kunkuni ba yabo ba fallasa muka gaisa. Godiya sosai Mami tayi min da abincin dana kawo masu, ni dai Murmushi kawai nake. Tun ina shiru tana ja na da hira akan girki har na ware nake fada mata ai abinda na karanta kenan, da yake itama Mamin tana da baiwar girki sai gamu muna hirar abubuwa da yawa har na ware. Sai wajen la’asar Yusrah ta shigo muka cigaba da hirar da ita sai gashi shima. Mun dade muna hira har aka Kira sallah yace mu shirya ana idar da sallah a masallaci zamu tafi. Bayan mun shirya tafiya Mami ta bamu leda mai dan girma nida Yusrah kowa daya daya. Kallon Yusrah tayi tace mu tafi gurin Abba tare yncu Abdallah din shima zai zo. Bayan fitar su ta kalle sa tayi masa nasiha sosai akan adalci sannan tace “kayi kokari kana iya boye soyayyar da kake yiwa Aasma a gaban Yusrah don Allah Abdallah, ina lura da kai a zaman ku gaba daya sai kallon ta kake kana Murmushi amma zan iya irga sau nawa ka kalli Yusrah shima sai in tayi magana ne”. Cikin sanyin jiki yace “In sha Allah Mami zan cigaba da kiyaye wa ki taya ni da addu’a”. Addu’ar ta masa sosai sanna ya fita lokacin har mun fito daga gurin Abban shima ya mana nasiha. Shima shiga yayi gurin nasa bai dade ba ya dawo muka tafi, tun da muka shigo unguwar mu nake kallon sa ban tabbatar da unguwar mu bane dai da yayi parking a bakin layin mu. Kallon sa nayi ta mirror nace “Hub da gaske gidan mu ka kawo ni”. Lumshe ido yayi yace “ku zo muje mu gaishe da Umma zamu biya ne muyi siyayyar azumi”. Sosai Umma taji dadin zuwan mu don ta rasa inda zata samu, bamu dade sosai ba muka fito ta bamu Kuka da daddawa nida Yusrah da yawa har da hawaye na da zamu fita. Daga nan supermarket din sa muka je kowa ya dauki abinda yake so don ya fada mana dama tun ranar farko ta ramadan har karshe duk mai girki ita zata yi abincin shan ruwa zamu hadu a part din sa a ci. Duk abinda nasan zan bukata sai da na dauka da wasu abubuwan na gida sannan muka fito. Cikin amincin Allah an rasa azumi lafiya na dage sosai da ibada bama duk ranar da ya kasance bani da girki. Tun da ko abincin da Binta zata ci Yusrah ce take aiko mata da shi haka ni ma in ranar girki nane ni nake bawa mai aikin Yusrah abinci. A haka azumi yau har anyi kwana sha biyar, komai yana zuwa min da sauki tun da tun da daddare nake dama tsara abinda zan dafa don haka bama kwanciya sai mun rage aikin na feraya ayi, jajjage ko yanke yanke. YUSRAH… Wannan azumin da ake na hada abinci ake aiki baya mata dadi sam da farko itama hakan ya mata ko dan ganin hutun tane itama zata samu kwana biyu ta huta amma kuma sai ta fara fuskantar kalu bale tun da tana da ciki bata da taste wani lokacin sai da dan saki gishiri ko ta bawa mai aikin ta dandane tace mata komai yayi ita ji take kamar bai ji ba sai ta kara. Don haka in zun zo cin abinci ita zata ci komai lafiya a gurin ta, amma shi Abdallah abu kadan yake ci in tace bai ci sauran ba yace gishiri yayi yawa ne. Duk ranar girkin Aasmaa kuwa zage wa yake ya cika cikin sa duk abinda tayi sai ya ci, wannan abin yana matukar bata mata rai danne wa kawai take yi. Iya kokari tana yi bama kuma tun lokacin da yake yawan mata korafi tana cika gishiri take kiyaye wa, sai ta zuba dan daidai koda ita Zata ji a bakin ta bai yi ba nan ma sai yace yau abincin magi bai ji ba kanwata, abinda yke kara bata mata rai a gaban Aasmaa yake fada mata irin haka ai da ko fadan zai yi sai ya bari sai sun kebe su biyu. Duk wannan karamar matsala ce akan yadda yake wani kallon Aasmaa in suna tare sai yayi ta mata kallon kasa kasa yana murmushi, wannan abin ba karamin kona mata rai yke ba tana tunanin ko gani yake ita bata da kishi ne don kawai tana kawaici tana kawar da kai. Wadannan abubuwan su suka sa taji zaman shan ruwan duka ya fita a kan ta bata son sa. Yau ma girkin ta ne tayi iya kokarin ta na ganin tayi komai dai dai, mai aikin tace ta taya ta suka jera abincin a part din Abdallah. Koma wa tayi tai wanka lokacin har an sha ruwa tana da tabbacin kuma Abdallah ya dawo ita yake jira tayi serving dinsa shiyasa take ta sauri. A gurguje ta shirya ta nufo part din sai kamshi take yi, tana nufo palon cikin tayi birki ganin yadda Abdallah ya daura Aasmaa akan cinyar sa yana bata wani kiss. Daure wa tayi ta hana hawayen dake don zubo mata sauko wa tayi Sallama. Da sauri na dago duk sai naji kunya ta kamani da sauri na sauka akan cinyar sa Ina gyara riga ta data ya mutse, sai da na ce masa ya rabu da ni kar ta shigo amma ya kafe akan kiss kawai zai min dan kadan.. Shima duk kunyar ce ta Kama sa sai ya shiga sosa kai duk ya diririce. Serving din su tayi ita kuma ta sawa kan ta kunnu don bakin ta duk ba taste. Kiran ta da Abdallah yayi ne yasa ta dago ido cike da gajiya wa ta kalle sa. Plate din sa na komai ya tura mata yace “kin dandana kuwa Wifey kin ji yau yafi na ko yaushe gishiri”. Kallon sa take da idon ta da suka kada suka yi ja kawai ta mike ta dire cup din hannun ta tace “Allah ya baku hakuri ban san yayi gishiri ba daga haka ta bar palon”. Baki sake Abdallah yake kallon ta cike da mamakin ta shi bai ga abinda zata tsaya tana yi wa fushi anan ba. Kallon sa nayi nima a ko yaushe ni Ina mata uzuri don naga yadda wasu masu cikin suke girki sai ana ci da hakuri don ba kowa bace take da taste. Cikin sanyin murya nace da baka mata magana na don Allah ai sai ka duba halin da take ciki.. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 38 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Shima kallona yayi yace “me nace mata Toh?” Girgiza kai nayi nace “ba wacce zata ji dadi kullum in tayi abu miji y kushe kuma a gaban kishiyar ta sai ka duba ka gani ai da ba haka take ba yanayi ne yasa ta haka mace mai juna biyu sai ana mata hakuri Hub”. Shiru yayi bai yi magana ba shi har ga Allah ya dauka an zama daya ne in ya fada cewa abinci yayi gishiri ba wani Abu bane. Haka muka gama nice na tattare ragowar na ajiye a gefe, wanda muka bata kuma na wanke mata sannan nayi masa sai d safe ma bar masa part din. Shiru Abdallah har karshe goma Yusrah bata shigo ba sai yaji hankalin sa ya fara tashi don yasan bata wuce 9:30 tun da da wuri suke bacci. Mike wa yayi ya nufi part dinta. Da Sallama ya tura kofar dakin ta ya shiga tana zaune akan kujera tana jan carbi idon ta a rufe, a saman lips din ta ta amsa masa kawai ba tare da ta bude ido ba. Tako wa yayi a hankali har ya iso in da take, cikin sanyin murya yace “Wifey ki tashi mu tafi bacci nake ji”. Banza ta masa kamar bada ita yake ba don wallahi a yadda take jin zuciyar ta zata iya zagin sa in har tayi magana, ita zai zo yana wani Kira da Wifey uban Wifey din karewar soyayya. Kujerar da take zaune ya zauna shima ya dora hannun akan cinyar ta. Da sauri ta tashi ta ture hannun ta zuba masa idanun ta suka yi jajir sbd kuka. Da sauri ya mike shima yace “wifey kuka kika yi haka.” Wata muguwar harara ta sakar masa murya a kausashe tace “fitar min daga daki don Allah tun kafin na fada ma maganar da zan zo Ina dana sani daga baya”. Zaro ido yayi yace “Wifey me nayi miki”. Kallon sa take hawaye yana zubo mata, cikin kuka tace “tambaya ta kake mai kayi min Yaya, ka manta ko kuma ture wa kayi sbd rashin adalci”. Nuna kansa yayi cikin mamaki yace “nine mara adalci Yusrah”. Cikin ido ta kalle sa tace “eh kai ne Mara adalcin Yaya, tun da aka fara azumin nan bana cikin nutsu wa duk ranar girki na fargaba nake yi kar nayi abinda zai sa ka kushe girki na amma duk kokari na sai ka kushe a gaban KISHIYA ta”. Kuka ta kara fashe wa da shi tace “duk ranar girkina haka zaka tsakuri abinci kadan kaci amma ranar girkin ta farin cikin da kake baya boyuwa a fuskar ka, haka zaka zauna komai sai kaci kana santi amma ni kuwa ko sau daya da azumin nan ka taba sha ko cin wani abu nawa ka yaba min Yaya?” Kallon ta yake jikin sa a sanyaye duk abinda ta fada gaskiya ne to me kuma zai ce. Murmushin takaici tayi tace “bayan wannan haka Ina zaune a gurin zaka dinga kallon ta kana mata Murmushi cike da soyayya ni kana min irin kallon da kake mata ne Yaya ko a tunanin ka bani da zuciya a kirjina da zan ji zafi”. Numfashi ta sauke tana share hawayen ta da mayafin data daura tace “kar ka manta wata na shida da aure ka kara aure Yaya, ba irin maganganun da ban ji ba na toshe kunne na, Ina iya kokari na don naga na boye kishi na duk kuwa da cewa ba wai bani da shi bane kawai son da nake ma ne yake sa ni danne kishin don a zauna lafiya”. Kallon sa ta kara yi ganin yayi shiru ya zuba mata ido ta girgiza kai tace “Ina boye kishi nane don nasan ban kai matsayin da zan yi kishi da matar son ka na tun da ni ba sona kake ba dama taimakona kayi”. Cikin tashin hankali yace “don Allah Yusrah ki dai na wannan maganar kamar ya taimakon ki nayi Wallahi Ina son ki”. Girgiza masa kai tayi cikin kuka tace “baka so na Yaya duka alamu sun nuna haka kuma ni din matar cushe ce wacce ka taimaka ka aura sbd yadda na mace a son ka har na kwanta a gadon asibiti sbd kai, ynxu da ka auri matar so Ina ganin soyayya kala kala Yaya duk iya hakuri na ka kure ni”. Nufo ta yayi hankalin sa a tashe don tun da yake da Yusrah bai taba ganin ta cikin bacin rai irin haka ba, baxai ce basa samun sabani ba amma ko yaushe ko shi ne ya mata laifi tana basa hakuri don kawai ya hakura komai ya wuce. Cikin tsawa tace “kar ka sake kazo kusa dani Yaya Wallahi in ka sake ka taba ni zan baka mamaki kwarai da gaske”. Tsayawa yayi cak cike da dunbin mamakin ta yace “Yusrah ni ne fah Yayanki”. Girgiza Kai tayi tace “Hub din Noorie ne ba Yayana ba, a da kafin ka auro ta kana nuna min soyayyar data ke mantar da ni cewa auren taimako kaii ashe ban sani ba a lokavin sbd baka da muradin ran ka neh, duk abinda kuke yi Yaya kawar da kai nake sbd Ina fada wa zuciya ta kai din Mijin mu ne ba nawa ba ni kadai”. Murmushin takaici ta sake saki tace “yau din ranar girki nane Yaya ban haka ka yiwa matar ka kiss ba amma da ka daure duk irin yadda ka zaku daka ji bakin ta da ka bari in ka shiga part din ta sai kuyi in abinda yafi kiss ne amma sbd baka dauke ni da daraja ba kamar yadda ka dauke ta sai gashi ka daura ta akan cinyar ka kana mata kiss, ni duk ranar girkin ta ko zama a kujera daya da kai bana yi kuma kai ma baka yi sbd ita matar so ce baka so ran ta ya baci amma ni ai bola ce ko wacce Shara aka zuba min dauka zan yi”. A sanyaye tace “fitar min daga daki bana son ganin ka wallahi Allah ABDALLAH”. Wani irin bugawa kirjin Abdallah yayi ciki da tashin hankalin da zai ce ya dade rabon da ya shiga irin sa yau shi Abdallah Yusrah take cewa ya fita bata son ganin sa shi Abdallah ne yafi Yusrah ya ambaci sunansa gatsal sunan da tun da suka yi aure bai kara ji ta fada ba sbd Yayana take ce masa. Haka ya fita daga dakin jiri yana kwasar sa. Ita kuwa Yusrah ba karamin kuka ta sha ba sbd tuno wa take da irin kallon da Abdallah yake yawan jifan Aasmaa da shi da kuma yanayin data same su dazu. Kasa bacci tayi don haka tayo alwala kawai ta fara sallah. Gidan dai yau gaba daya ba’a yin kwanan dadi ba don ni kai na duk juyin da zan yi yanayin da Yusrah take ciki kawai nake hango wa. Mata da yawa suna cewa KISHIYA baxa ta taba kaunar kishiyar taba amma ni zan bugi kirji na karyata su, Ina ganin darajar Yusrah sosai kuma Ina son ta har rai na sbd yadda take girmama ni. Nice amarya amma Aunty sama Aunty kasa ne kamar ba uwar gida bace ita wanda ina da yakinin a zamanin nan da wuya a samu irin haka. Haka dai Washe gari ma na tashi jiki na a sanyaye da yake ni ce da girki da wuri na shiga kitchen kamar yadda na saba don nayi abinci. Ko da aka sha ruwa Ina zaune a part din sa Ina gyara kayan abincin ya dawo daga masallaci sai wara ido yake. Kallo daya na masa na karanto tarin damuwar da yake damun sa. Murmushi na masa nace “sannu da shan ruwa”. Daga mun kai kawai yayi yace “Yusrah bata zo ba”. A nutse nace “eh bata zo ba” Gyada Kai yayi ya juya ya fita ya nufi part din Yusrah cika da zumudin ganin ta don dazu daya zo tana daki kuma duk bugawar da tayi masa kin bude masa kofa tayi. Ya kuwa ci sa’a tana zaune a kan kujera tana shan tea idon ta yana kan TV tana kallon Sunna Tv. Ajiyar zuciya ya sauke da ganin ta da yayi cikin sanyin jiki ya kara so ya zauna a gefen ta. Ko kallon sa bata yi ba duk kuwa da cewa tana jin yadda ya zuba mata ido DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 39 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Tsoron mata magana yaji da kyar ya jawo jarumta yace “barka da shan ruwa Wifey”. Akan lips din ta tace “barkan mu dai”. Shiru yayi yana kallon ta a sanyaye yace “ki zo muje muci abinci ke kawai muke jira”. Juyo wa tayi ta kalle sa fuskar ta dauke da Murmushi tace “ai kaga abinci nake ci Yaya bana jin Yunwa na baka space ne kuyi kallon love din ku kaga ba sai kana satar kallon taba bana gurin ynxu”. Dafe kan sa yayi yace “don Allah kiyi hakuri Kanwata nasan nayi kuskure hakan baxai kara faruwa ba in sha Allah”. Murmushi tayi tace “Yaya ai ni zan baka hakuri ni da kullum nake cika ma gishiri a abinci kuyi hakuri don Allah ni ynxu girkin nawa ma na bar wa Aunty kawai har na haihu sai na kar na in sha Allah kaga baxa ka dinga cin abincin da zaka dinga complain ba in sha Allah”. Hannu yasa ya rufe baki cikin tashin hankalin yace “Innanillahi wa inna ilaihir raji’un”. Murmushi ta kara sakar masa tace “Yaya nayi laifi ne”. Hankalin sa a tashe yace “ynxu Yusrah ni kike cewa zaki bawa Noorie kwanan ki sbd na dai na complain”. Girgiza kai tayi tace “Yaya kawai na taimake ka ne fah kaga bakin ka zai dai na ma ciwo”. Daga haka ta dauki cup din ta ta wuce sama. Bin ta da kallo yayi hankalin sa a mugun tashe sai ynxu yake hango girman laifukan da yke aikata wa Yusrah din. Rintse idon sa yayi dake mugun sara masa da kyar ya tashi ya koma part din sa. Abincin da yake ci kullum cikin farin ciki yau kunu kawai yasha rabin cup ya hau kan kujera ya zauna yayi tagumi. Kallon sa nayi duk sai naji ba dadi a tunani na ko dan sbd abinda muka yi mata jiya ne take fushi. Sai da na haka kwashe kayan abincin sannan na dawo kusa da shi ma shiga tambayar sa mai yake damun sa, bai min magana ba. Nima dana fahimci baya son fada min sai kawai na shiga masa tausa a jiki. Gaba daya ynxu zaman shan ruwan ba dadi duk ranar girkin ta baxa ta ki yin abinci ba kuma tana gyara masa part din sa amma sai taga baya nan. Duk iya hakurin da zai bata tayi biris don a ynxu so take ta nuna masa tana da daraja ba komai bane in yayi zata dinga dauke ido akai don taga shirun ta shi ne yake sa wa ake kwarar ta ake tunanin ai kamar bata gani ne. Abdallah kuwa gaba daya baya ma cikin nutsuwar sa, kullum haka zai sha kunu kadai sai in yaji yunwa ya tsakuri wani abu, a ynxu yake Kara tabbatar wa cewa Yusrah ita ce cikon farin cikin sa duk irin farin cikin da yake ciki in Yusrah bata tare da shi sai yaji tabbas da akwai babban gibi. Ni kai na yncu zaman gidan duk gashi nan dai ne amma nasan hankalin Mijina a tashe yake bai fasa sauke hakkin sa dake kai na ba amma kallo daya zaka masa kasan cewa cikin farin cikin sa ya bata a tattare da shi. ***** Yau ake gobe sallah Yusrah na zaune a dakin ta tana turara Kayan ya Abdallah ya shigo. Kallo daya ta masa jikin ta yayi sanyi gaba daya kamar ba Abdallahn data sani ba ya rame kadan yayi zuru zuru. Mike wa tayi ta ajiye mayafin abayar ta, nufo sa tayi taga yadda yayi tagumi yana kallon ta. A hankali ta cire masa tagumin tace “Yaya mene?” Cikin sauri ya riko hannayen ta sosai yace “don girman Allah ki yafe min Wifey Wallahi baxan sake ba rashin sani ne yasa nayi amma in sha Allaj hakan baxai Kara faru wa ba”. Turo baki gaba tayi tace “ai ni tuni dama na yafe maka”. Mike wa yayi ya sungume ta ya shiga zage ye dakin da ita yana fadin I love U Yar Aljanna tah. Dariya Yusrah take sosai tace “Yaya sauke ni don Allah kar mu fadi”. Sauke ta yayi ya zaunar da ita akan cinyar sa yace “kar ki Kara fadar cewa taimakon ki nayi Yusrah, Allah ne shai da ta ina matukar kaunar ki wallahi, fadar irin son da nake miki bata baki ne ni kadai nasan irin tashin hankalin dana shiga akan horon nan da kika min ki yafe min don Allah kuskure ne nayi miki baxan sake ba in sha Allah.” Bata basa amsa ba sai hade bakin su da tayi. Ranar a dakin suka kwana dama kuma ranar girkin ta ne. Washe gari sallah da wuri ta tashi suka yi tuwo da masa da sinasir tare da wata Tsohuwa da Mummy ta kawo mata sbd harkar abinci tun da tayi wa Mummy complain ynxu bata taste. Komai sai da aka dibar wa Aasmaa aka mai mata. Ni ma yau na tashi cikin farin ciki kamar yadda ko wanne musulmi yake tsintar kan sa a irin wannan ranar. Ni ma nayi abincin sallah na zuba wa Mami da Umma a flask na kuma zuba wa Yusrah ma na bayar aka aika mata. Wanka nayi na shirya cikin shadda fara kal doguwar riga data ji aikin light blue zare har kasa sai na saka light blue din Hijab dogo wanda ya kara kawata kwalliyar tawa. Na gama fesa turare ya shigo yana saba babbar rigar sa, fara’ar da na gani akan fuskar sa ce ta shaida min sun shirya kenan hankalin sa ya kwanta, Murmushi na sakar masa nima cike da tsokana nace “ynxu ka dawo Yayanmu da muka sani”. Murmushi ya saki shima yace a da ai rabin zuciya tace kawai a gefena a ynxu kuma na samo ragowar rabin kinga an tashi zuciya daya kenan ai dole ki ganni fess. Dariya nayi nace Maa sha Allah. Hannu na Mika masa muka yi musabaha nace “barka da sallah Hub”. Murmushi ya saki yace “barka da sallah Nisful Hayat”. A tare muka fito sai fara’a muke yi, a zaune a motar na samu Yusrah tana zaune ita ma da Hijab din ta tayi kyau sosai. Tana hango mu ta fito tace “Barka da Sallah Aunty”. Hararar wasa na mata nace “sai ynxu kika tuna kika da Auntyn”. Rufe fuska tayi tana dariya tace “afuwan Auntyna kiyi hakuri don Allah”. Murmushi na sakar mata kawai kafin mu tafi sai da muka yi hotuna sosai, ni na fara karbar wayar sa nace bara na musu shida Yusrah, sannan Yusrah ta karbi wayar ta mana mu biyu ni da shi sai muka yi mu uku sannan ya mana ni da Yusrah. Mun yi kyau sosai tun a gurin ya turawa kowa hoton wayar sa. Haka muka je idi muka dawo cikin farin ciki, a part din sa muka zauna muka ci abincin Sallah gaba dayan mu a tray daya sannan kuma muka sake shirya wa muka fita. Gidan mu muka fara zuwa muka yi wa Umma Barka da sallah sanna muka tafi gidan su anan muka wuni sai dare muka dawo. Yawo muka sha da sallar nan don da mota ta nake je gidan mu na wuni, a rana daya kuma naje gidan Yaya da gidan Maryam. Tun bayan sallah na dai na lafiya kenan kullum bani da lafiya da yau ciwon Mara gobe ciwon kai. Abinci kuwa na dai na ci ma gaba daya kullum kunu ne abinci na, ko girki zan yi sai na sa face mask in ba haka ba amai zan ta kelaya. Ranar dana kwana da zazzabi Washe gari ya dauke ni muka tafi asibiti aka dibi jinina. Doctor Husna ce ta mana albishir din cikin da nake dauke da shi na wata biyu. Sosai ya dinga murna don tun a asibitin ya Kira Yusrah ya fada mata. Kullum cikin tattali na suke shida Yusrah sbd cikin yazo min da laulauyi sosai bana sati sai an kara min ruwa a haka Yusrah ta haihu lafiya ta samu baby boy ne Kama da Abdallah. DijahAM 09066728387 You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj 🥀🥀🥀🥀🥀 Aasmaa 🥀🥀🥀🥀🥀 Written by DijahAM Free book neh 🥰 Page 40 🔚🔚🔚🔚🔚 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Yusrah taso tafiya gida amma Abdallah ya kekashe ido yace ba inda matar sa da dan sa zasu tafi dole haka ta hakura. Ranar suna yaro yaci sunan baban Abdallah Ahmad muna ce masa Aryan. Nayi mata kayan barka masu kyau na kai mata har Umma dasu Yaya kowa sai da ya kawo mata atampa. Haka har suka yi arba’in kusan kullum Aryan yana guri na sai yayi kuka ne kawai nake bayar wa a Kai ma Yusrah ta basa nono. Kwanci tashi har cikina ya shiga watan haihuwa lokacin watan Aryan 4 yayi kiba sosai ya fara zama ga wayo a cikin sa. Ranar Juma’a Allah ya sauke ni lafiya na haihu lafiya wanda da har za’a min aiki sbd yadda na jigata sai kuma gashi na haifo baby girl dita katuwa Tubarkallah mai Kama da Baban ta sak. Lokacin dana farka yana zaune a gefena sbd haihuwar dare ne bai fada wa kowa ba bayan Yusrah da tasan mun taho. Kallon sa nake naga yadda ya zuba wa babyn ido yana kallon cike da so. Murmushi na sakar masa nace “Hub”. Da sauri ya tashi ta taho kusa dani fuskar sa dauke da Murmushi, yarinyar ya ajiye a kan gadon ta sannan ya dago ni ya gyara min za mana. Dauko min ita yayi ya dora akan cinya ta yace “kinga Babyn mu Husnaa ta” We . Lumshe ido nayi hawaye yana zubo min na riko hannun sa a sanyaye nace “don Allah Hub ka yafe min dukkan abinda na maka”. Murmushi yayi yace “ni ba abinda kika min Yar Aljanna”. Sunan daya Kira ni da shi ne yasa ni lumshe ido nace “I love u Abdallah”. Da sauri ya zagayo ta gabana ya zauna akan gadon yace “me kika ce Noorie”. Murmushi nayi Ina sunkuyar da kai nace “I love U Babyna”. Wata kyakyawar runguma ya min nida Babyn cikin tsantsar farin ciki yace “ina kaunar ki Nima sosai Noorie ta” Washe gari aka sallame mu muka koma gida anan na cigaba da je go na Aunty Murja ce tazo ta zauna da ni, tana kula da ni da babyn data ci sunan Mami muna ce mata Iyman. Sai da ta min kwana arba’in sannan ta tafi ta bar mu cike da kewar ta. Zaman lafiya muke yi a gidan Abdallah don yana kokarin yin adalci a tsakanin mu wannan yake yayyafawa kishin mu ruwan sanyi. Kamar yadda rainon Aryan ya dawo hannu na haka na Iyman ya koma hannun Yusrah. MEENA A ynxu rayuwa ta mata zafi sosai don kuwa baban ta da ya gaji da yawan samarin da take yi Kai tsaye ya bawa abokin sa auren ta don dama ya taba masa maganar ya nuna kin amince wa. Ba kalar borin da Aunty Bilki bata yi ba daga karshe dole ya hakura don kuwa baban MEENA yace ko ta yadda ko kar ya yadda aure ba tashi amma ta sani in har ta cigaba da daga masa hankali zai bata red card dole ta hakura tayi shiru. Tana ji tana gani aka yi auren MEENA da abokin baban ta. Ita ma Meenan da farko ta tayar da hankalin ta sosai daga baya dole ta hakura tabi Mijin ta duk kuwa da cewa Abdallah na nan makale a ran ta. Bayan auren MEENA na dade wa Baban ta ya Kara aure, ba kalar haukan da Hajiya Bilki bata yi ba karshen dauke matar sa yayi suka bar kasar bai dawo ba sai bayan wata hudu lokacin matar ciki ne ma da ita. Da farko har yaji sai da Hajiya Bilki tayi ta tafi mamabila amma Iya da kan ta ta dawo da ita dakin ta dole ta hakura ta zauna. Bayan wasu shekaru….. A ynxu yaran Abdallah 10 cif, Yusrah nada hudu uku maza mace daya sai Aasmaa dake da hudu 3 maza 3 mata. Daga haihuwar Iyman tayi twins duka maza, sai ta kara haifo namiji sai autan su suma twins ne mata. Kan yaran a hade yake baka iya banbance wace mamar su don sun hada ne gaba daya sun runguma. A ynxu Yusrah da Aasmaa ko wannan su ya mallaki supermarket manya guda biyu biyu bayan shagunan da Abdallah ya mallaka musu a kasuwar kwari. Sauri nake na karasa shiri na don ma yaran basa part dina gaba dayan su suna part din Yusrah wai yau acan zasu kwana. Kara mulke jikina da lafiyyar humra nayi sannan na zira hijab na dau karamar waya na nufi part din Hub dina. Ban same sa a palo na daki na shige kawai, yana zaune kuwa yana danne danne a system din sa. Murmushi nayi na nufe sa Ina Murmushi, shima ture system din yayi ya janyo ni kan cinyar sa. Cikin tsokana yace “kin kara nauyi Noorul Qalb” Turo baki nayi a shagwabe nace “naji din” Murmushi yayi yana zare hijab din yace “meye sirrin Noorie kullum kara kyau kike yi”. Shafa gemun sa nayi nace “kai ne sirrin Mijina, tun daga ranar daka shigo cikin rayuwa ta nake ganin haske Kai Alkhairi nane Mijina, Allah ya saka maka da gidan Aljanna ya baka ikon cigaba da yin adalci a rayuwar ka”. Murmushi kwance a fuskar sa yace “Ameen Noorie gaskiya aure zan kara ma don yadda kuke sani kwanciyar hankali imagine na karo muku wata”. Wata harara na sakar masa ina Murmushi nace “lallai ni da kanwata da kuwa mun murkushe ka daga Kai har amaryar tak”. Dariya yayi shima ya mike dani a hannun sa yace “ni ma kun ishe ni a duniya dai in sha Allah, Allah ya muku albarka”. A zuciya ta na amsa da Ameen don bakin tuni ya hade da nasa yana bani zazzfan sako ni kuwa Ina anshewa…. ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH Allah na gode ma daka bani ikon gama wannan littafi lafiya abinda na rubuta dai dai Allah ka bamu ladan sa Wanda nayi na kuskure Allah ya yafe mana. Ngd sosai My Fans da irin kaunar da kuka nuna min a wannan littafin Allah ya bar mu tare. Fatan zaku nuna min soyayya a sabon book din da zan yi in sha Allah na kudi🥹🥰❤️ Mrs AM AKA DijahAM 09066728387