WAR GAFALALLU oumyasmeen Da sunan Allah mai rahama mai jin kai duk kan yabo da godiya sun tabbata ga ubangiji ayau Allah ya ƙara haɗa mu a wannan sabon littafin nawa Allah ya bani ikon gamawa lafiya.. GARGADI!!! Ban yadda wani ko wata suyi min amfani da wannan labari ta kuwanne siga idan kunne yaji jiki ya tsira Wannan labarin kirkirarre ne banyi da nufin tuzarta wani ko wata ba duk wanda ya ga yayi dai-dai da rayuwar sa ya dauka arashi ne... بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Allah ya tsare Allah ya kare ban da ɗaukan na mara hakuri amma ban hana ku ɗaukan na wanda yayi wasa rare da kayansa ba ,ku kiyaye bana son Ku dauko min magana daman makota sun sakamin ido idan ban daku ai saidai mu yini ba mu ci ba Sumy tace ''....Momcy kar ki damu yau aljihunki zai cika da ya'yan banki , wata uwar buɗa ta saki tana cewa na gode ta gidana shi yasa ka nake ƙara son ku bakwa son damuwata dafa ta naja tayi tace '' momcy inhar kina doran duniya bamu da damuwa..., wallahi kuwa kudai Allah yayi muku abarka amin ya Allah suka faɗa suna ƙoƙarin fita ko wacce akwai me jiranta a waje tashi nayi dana gama sauraron duk zancen su na fita zama nayi a kan kujera kee mufeeda wai har yau ba me dan danshi da yake zuwa gurin ki ajiyar zuciya na sauke nayi shiru garbati da yake zaune yana nan naɗa tabar wiwi yace ''uwar gafalallu sai kin bada kuɗi an mata roƙon Allah duk wannan kyawun nata ba wani me dan mai ko da yake zowa gurin ta..., a hassale mufeeda tace "...da hallacan yiwa mutane shiru ina neman tsari da wannan rayuwar suma da suka saka kan su a ciki Allah ya shirye su.., Asabe reza tace ...tab lallai yarinyar nan baki da hankali tashi nayi na shiga daki na koma na kwanta abuna idan dai rayuwar gidan mu ce hmm sai dai addu'a zama tayi a dokin kofa tana fito da wiwi da sauri suka taso rufe kayar ta tayi tace '' ku dakata bana son rashin hankali kowa ya bi layi ga ta nan da yawa kuma wallahi.., wai ke me isaka kin fiye yawa da yawa ne.. Gaddafi ya faɗa yana cije baki hadi da zaro huƙa Asabe reza tace '' gaddafi wallahi zakai ka gama baza ku durani da ka ba wallahi ƙarshe mutan unguwar nan su fara nuna ni da baki ana ga asabe reza ta ƙare mata.., cikin cije baki gaddafi yace '' amma dai..., kai yi min shiru ko yanzu billahillazi nayi ƙasa ƙasa dakai tsohon tsumi ya tashi ta faɗa tana zare ido haɗi da nannade hannun rigarta a'a asabe reza duk bata kai haka ba mai kuɗi ya baki, ki bashi fakat wanda bashi da shi ya raka ki da na jiyamu ( ido) kar ma ku kawo ni nasan yadda zanyi da ku yan hau yanzu ina zuwa bakin titi karfe biyun dare wallahi rubibinta za ayi tas zata ƙare haladune ya shigo ya caka huƙa a ƙasa yace '' ...shege naki dan iska naki duk irin laifin da kayi kazo gidan uwar marayu tana da masauki har me tsinuwar iyaye kina mara ba dashi ana gudin dan iska amma ke shi kike so kaga uwar da take kara saka ya'yan ta akan hanya dodar.., dukkan su, suka haɗa baki gurin faɗar doɗar wata iriyar dariya tayi tace '' haladu na gode da wannan kirarin..., kuttumar ubancen lallai yau za a yi ta da mai da yaji ....ni za ta tozar ta tashi tayi tana cewa jalila lafiya yau she kika dawo ban sani ba baki baki balance dauke kai jalila tayi tana cewa momcy yau akwai tashin hankali a gidan nan dan ubanki ni tashin hankali damata yayi bani dai labari me ya faru kike tada jijiyoyin wuya nuna mata wayar'ta tayi tana cewa momcy yan zunan aka turo min picture din naja da honourable suna can hotel wata dariya ta sheƙe da ita har da bugun cinya tace '' wallahi tarairayar customer tafi ki shi ya saka kika ga ya dawo gunta kema sai ki dage idan abin yayi miki ciwo a dinga gyara headquarter sosai ta inda ba ta yadda za a yi yaje gurin wata ko matar sa bata isa ba..amma munafikin da ya turo mik wannan rashin mutuncin shi ya kamata kije kici ubansa.., yanzu dai a takaice kin goyi bayan ta zama asabe reza tayi tana gyara zanin'ta tace '' naja zancen kike so kai ta nawa za'a baka..?, miƙa mata riɗa ɗaya yayi (dari) juya ta ta fara sannan ta soke a ƙafa wani almajiri ya shigo yana cewa sallamu'alaikum wai mufeeda tazo naɗe ledar wiwi tayi ta kulle tana cewa masha Allah inji wa inji malam rufa'i je ka kace bata nan haka kurum mutum yawa maye nace ya barmin ya'ta yaƙi kullum ya zo hannu na bugun cinya , ya wani taje gemunsa yayi tsaibebe a tsaye wallahi baza ta saɓu ba ya'ta kallar gaban mota ce ni bance lallai sai tayi aure ba ya barmin kayata da sauri mufeeda ta fito tana ni wallahi momcy ki dena abin da kike da sauri ta jayo ta aguje ta fita bin ta tayi ganin taje soro ta dawo ƙarasawa tayi tana dariya kallon ta yayi yace "Mufeeda..., Na'am ina wuni yau saukar rana zama yayi akan dan kututturen bishiya yace ''eh wallahi kin ganni nan barka da rana.., yauwa ta faɗa tana wasa da mayafinta Tufafi yace '' ...a maman tamu , kaje can ka nemi uwar ka ni ba uwar ka bace da sauri ta juyo shi kuma ya tashi durƙusawa yayi har ƙasa yace ''barka da rana ...., barka da ubanka ka fitar min daga sabgar ya'ta wallahi ,me nasama ya ci balle ya bawa na ƙasa haba momcy me yasa ka kike haka kowa kina kyale sa amma ni rufe min baki ko na zubar miki da haƙora kece ƙarama amma ki na nema ki gagare ni wallahi bazai yiwu ba hawaye ne suka fara sintiri a fuskarta wannan tozarci da me yayi kama kallon rufa'i tayi tace ''kai hakuri katafi gida mayi magana ta waya..., tashi yayi daga durƙusan da yake ya gyaɗa mata kai kawai ba tare da yayi magana ba juyowa kan momcy tayi tace ''yanzu abin da kikai ya dace kenan..., zo ki wuce ko saina ballaki wucewa tayi ba yadda ta iya tana shiga ta samu guri ta zauna ta ci gaba da kukan ta jalila ce ta fito tace ''mufeeda me ya faru kike kuka...?, momcy ce ta kori rufa'i kallon maman tasu tayi da take ta siyar da wiwi ba abin da ya dame ta juyowa tayi tana ƙasa da murya tace ''kice mai idan har zai dinga zuwa ya tawo da leda idan kuwa ba haka ba wallahi hulakanci yanzu ya fara gani.., ni dai gaskiya bazan iya faɗa mai haka ba tsaki ta ja ta shiga daki itama tashi tayi ta mara mata baya kwanciya tayi tana kallon rufin kwanon dakin nasu tana da burin yin karatu amma halin babu ya hanata yi juyawa tayi ta kalli jalila tace '' aunty jalila dan Allah bani kuɗi na ci abinci yunwa nake ji..., yau baba be bayar da kuɗi bane ajiyar zuciya ta sauke tace ''tun safe da ya futa be dawo ba..., tab aikuwa yau balallai aci abinci a gidan nan ni kuma gaskiya bani da kuɗin da zan baki tun da kin ƙi sakin jiki ayi harkar arziki insha Allahu wannan mutuncin nawa har gidan mijina dariya jalila tayi tana saka waka a wayar ta tana bi jin wata uwar sallama da sauri ta fito tasan me amsar kuɗin huta ne kallon momcy tayi tace '' momcy ya dace ba fa ko baki ji sallamar sa ba..., mufeeda na ji wallahi duk wata karya da zan mai ta ƙare momcy yaufa da uban gidan sa yace zai zo kar ya saka a rufe mu kuma fa haka ne saka mayafin ki ki fita duk wata karrairaya da kika iya da wacce kika ga yan uwanki suna yi kiyi musu ko za a dace Mufeeda tace ''gaskiya ni bazan iya ba haba momcy ki dena abin da kike .., Gaddafi kuna jin abin da take faɗa ko wake amfanuwa da wutar gidan nan idan ba ita ba , bata da aiki sai kayana ya yamutsai bazan iya saka shi a haka ba to wallahi zan ci uwar baban ki idan baki je ba ni kuma zan ci kuttumar uban ki asabe ashe daman rashin mutuncin ki har ya kai haka da sauri ta juyo jin muryar lami mahaifiyar mijinta rufe baki tayi domin idan dai tujara ce sai dai ta take mata baya lami yar tijara ce har yanzu da tsofanta shan taba sigari take dariya mazan gidan suka saka har da masu tafi Allah ya dawo da lami yar gumama kai mufeeda ta girgiza wannan rayuwa da me tayi kama ke dan uwar ki kin tsaya kina kallo na ga kayan nan kin tsaya kina kallo na da idanuwanki yawa na mujiya tafiya ta fara tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki ke barshi kawata jalila ko bakya gidan ne jalila ce ta fito tana miƙa tace '' baba lami saukar yaushe...?, Baba lami tace...wallahi yanzu na sauka kai munsha Niger duk wani kaya da na tafi da shi tas ya ƙare kai masha Allah haka ake so ni wallahi ban taɓa zaton zaki dawo da wuri haka ba baba lami yar gumama tace '' na siyar da kaya zaman me zanyi yar albarka ga kayana nan zoki tayani ɗauka .., karasa fitowa tayi da yake da a dokin kofa data tsaya ɗaukan mata kaya tayi takai mata dakin ta jiki a sanyaye mufeeda ta fita gaban tane ya waɗi ganin yau a mota suka zo daga ganin motar an saka makudan kudade kafin a siye ta gaban tane ya waɗi ganin har wani ya hau yana nema ya tsinke wutar su da sauri ta ƙarasa ta soma.., girgiza tsanin tana cewa wallahi idan baka sauko ba wallahi Allah sai na karya ka ɗan uwar ka ba magana nake maka ba kai wanne irin matsiyaci......ne cire glass dinsa yayi da sauri ta ja baya gaban ta ya yanke ya waɗi ƙarasa cire wayar yayi ya fara saukowa a hankali cikin nutsuwa da izza lokaci ɗaya tsanar yarinyar ta durar mai a zuciya yarinya ƙarama amma tana wannan tujarar tun da suka haɗa ido da shi gaban ta ya yanke ya waɗi tamkar an kafa mata turke a gurin ta kasa barin wajen zagi ba halinta bane tana cikin wannan hali Anai ya zo wucewa cikin muryar rukakkun yan daba yace '' mufeeda...yane.., da sauri ta ɗago tare da sakin ajiyar zuciya idan har Anai yana kusa tofa ba wanda ya isa ya taba ta shi ya saka ma take tare dashi ko su kansu yan uwanta idan har tace zata haɗasi dashi basa iya yi mata wani abu da zai cutar da ita kallon inda yake tsaye tayi ya murtuƙe fuska yawa hadari ya gangamo ba wani annuri a fuskarsa dukan mace ba dabi'arsa bace amma yau da yarinyar nan sai dai a ɗauke ta har shi zata zagar mai Uwa tasan irin so da kaunar da yake wa mahaifiyar sa duk abin da ya zama sularta ce cije lips dinsa yayi ya fara tafiya da sauri yaran nasa suka karaso ɗaya daga cikin su yana cewa oga wallahi Sai hakuri ba mutunci ne da su ba wai a haka ma gwara ita da sauran kaf gidan ta fisu kirki mahaifinsu shi ne fa tsohon dan daban nan idirisa kyalli zuciyar ta ce tayi mata wani uban baki ko ace babu halin yayyunta to wallahi abin kunyar da iyayensu sukai ba zai taɓa barin su , su zauna lafiya ba kallon ANAI tayi ta zauna akan inda rufa'i ya tashi tace '' kwana dubu ina ka shiga..., gyara hular kaurayen sa yayi yace '' wallahi naje umarane yau ɗin nan aka sallamoni.., me ka ɗauka shiru yayi ɗagowa tayi ta kallesa idanuwanta tab da hawaye tana kaunar rufa'i amma ba yadda zata yi mahaifansa idan har suna numfashi a doran duniyan nan ba zasu bari ya aure ta ba ANAI kuma ɗan daba ne ta baso ta zaɓowa ya'yanta uba na gari cikin rawar murya da take bayyana rauninta tace '' dan girman Allah ANAI Ka nutsu kaga ɗaukan hakkin wani babbar illace gidan yari ya zamar maka tamkar ibada yau kana can gobe ka fito.., harki damu insha Allahu na kusan ajiye komai muyi aure Anai bazan iya auren ka ba inhar kana wannan abun wannan shi ne gaskiya to ba matsala duk sanda na shiryu mayi auren nima ba yanzu nake nufi ba sai yau she kenan...?, ba rana ya fada yana gyara zaman hukarsa a jikin sa tashi tayi tana cewa....okay kar ka sake ka ƙarayi min magana ta faɗa tana shige wa cikin gidan su yauwa ya kikai da su sun hakura cewar momcy dafa kejin kaji tayi tana cewa momcy yaufa da Uban gidan su suka zo wallahi ya yanke amma wannan anyi ƙwallon shege muna talakawa yaushe zamu iya biyan kuɗin wuta muji ma da na abinci wallahi kuwa baba ai wannan shugaban gidan wutar da aka saka bashi da kirki wallahi dakan sa yake yawon karɓar kuɗin wuta dan gidan Alhaji mansur Gwarzo ne... UWAR GAFALALLU OUMYASMEEN Wannan littafin na kudine ku hanzarta payment din Ku free page ba yawa 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay ku turo da she da ta wannan hanyar 09061890481 EPISODE 2 Wannan dai babban dan kasuwar shifa baba lami ta faɗa tana gyara goron da ta siyo Baba lami yar gumama tace ''..kwanaki na taɓa zuwa gidan su karɓar sadaka ubansa mutumin kirki ne dana san shi ne yazo da wallahi sai na fita ya bani sadaka wallahi duk irin wannan abin ne yake zubar mana da mutunci gaskiya baki kyauta ba da sauri bana ta dauki roba ta wullo mata kaucewa tayi baba lami yar gumama tace ''kaji yar butar uwar nan sabe ce bata kyauta ba koni.., shiga daki tayi tana cewa aunty jalila wallahi duk abin da akai mana a unguwar nan su baba suna da sa hannu wannan wanne irin son kuɗi ne har ki dinga tafiya bara bayan Allah ya wore miki lafiyar da zaki nema... banza tayi mata taci gaba da shirinta daga ko ina na jikinta take yi tana zuba turare tare da murya ko ina kai ta girgiza sallamar naja taji da sauri ta saka zani ta fito tana cewa yau wallahi me rabamu sai Allah ki rasa wacce zaki ci amana sai ni dariya naja tayi tana daga ledojin da ta shigo dashi tace '' yarinya kwantar da hankalin ki ba wani abu mukai ba kawai sau ɗaya yayi ashe ma ba wani jarumi bane..dan haka na barmi ki shi kawai dandana shi nayi kullum baki da zance sai honourable ashe muna maza ne ba namiji bane..., kut ni kike faɗawa haka tab lallai yau me rabani dake sai Allah momcy kina ji ko jalila bana son neman fitina dame zanji da wannan masifar ta yaran nan kina ga an kama sunusi dan kuɗin da suke tarawa a guri na saboda bacin rana nawa yake dole naje nayi belinsa su kan su yayensu sun barmin su komai ni kenan raina ɗaya ku ga kunan kuna mata ban wuta ba jalila fitinar ki ta isheni Nuna kanta ta shiga yi tana cewa momcy yau ni kika juyawa baya dan ta shigo da abin duniya duk irin abin da nake kawo miki a'a jalila yanzu ba wannan maganar ake ba ku duka haifar ku nayi to ba wanda zan ware nace bana so i dan fadar gaskiya ta tashi zan faɗa muku ato naja ce tayi dariya tare da juya duwawu tace '' momcy manta da ita ga wannan yace na kawo miki.., da sauri ta saka hannu zata amsa jalila ta warce buge hannunta tayi ta amsa tana cewa wallahi ki, kiyayeni jalila ni sa'ar wasan ki ce batare da tace komai ba ta shiga daki dariya naja tayi tana cire mayafinta akan igiya ta rataye ta shiga bayi Sumy ce ta shigo ba ko sallama da alama a buge take zama tayi a kasa yawa yar bori ta miƙe ƙafafuwan ta jakarta ta jefar kanta na mata wani irin juyawa da kyar ta kawo kanta gida wayar tace tayi ringing bude jakarta tayi ta dauko ba tare da ta daga ba ta kara a kunne tace '' hello ka-na-ji-na ta fada a rarrabe ajiye wayar tayi Gaddafi ne yace ''tab yau kinsha wacc tafi ƙarfin kanki..., wara hannu wanta tayi ta yi a lamar uku da yatsun hannunta dakyar ta iya cewa kwalba uku nasha nayi tatul naja ce ta fito tace '' badai kamru uwar laifi kika sha ba...?, ita na sha wani abu ne tab tsoho ya haifi wacce tafi ƙarfin sa dan Allah lokacin ku momcy tsoho yasha giya...?, tab ai besha ba iya kacin sa taba daga baya ma tun kafin muyi aure ya dena to yau gashi ya haifi wacce ta fi karfinsa wai dan Allah momcy a haka kika yadda kika aure tsoho dariya tayi tana gyara zaman rigarta tace '' ke nima gagara nayi mahaifina ya bashi ni na san kuma ɗan dabane mene abin gudu a dan daba wallahi ina sane na aure shi...kuma ina son kayana wani ihu su Gaddafi suka saki suna mata kirarin da suka saba yi mata cau cau cau uwar gafalallu dan iska naki ban da dan banza dan kirki me tsinuwar iyaye shi ne babban shedani na hannun daman ki an buga dake an barki maƙiyan ki fadawanki dubu jiran dubu bilahillazi ba me taddo ki cau cau ki yi taki kinyi ta wasu bata kare miki ba Sai ma gaba da kikai ke ce uwar da zamu ɗauko magana ki shige mana gaba a fito damu ya isa haka yanzu haka sumy salon ki saka a dinga zagina a unguwar nan shi ne kika tawo a haka haba sumayya so kuke baƙin mutane ya durarmin dakyar ta iya tashi tana haɗa hanya komai da ta shigo dashi anan ta bar shi tana zuwa daki ta kwanta a ƙasa matsawa mufeeda tayi ta fito tana cewa wallahi momcy idan har ba zaki gyara halinki ba mu tare da dana sani kai ka kai turƙashi mufeeda ashe bayan tafiya ta niger rashin kunyar ki ta kara gaba to yanzu ni ko mahaifiyar ki , kike faɗawa haka..., baba lami ta faɗa tana kama haɓa baba gaskiya ce dole a faɗa wallahi bana jin dadin rayuwar nan da muke Please mu canza mu koma irin ko wanne gida mana jin sallamar mahaifinta ta ɗago amsawa tayi ai kafin kace me kowa ya tashi ya fita ƙarasa shigowa yayi cikin sanyin murya kamar ko da yaushe tace baba sannu da dawowa yauwa yar kirki Allah yayi miki albarka sauran kuma Allah ya kwashe musu wallahi idirisa ka dena raba kan ya'yan ka girgiza kai yayi a ko wacce rana yakan yi dana sani mara adadi na zaɓowa ya'yansa uwa bata gari ba shima rashin dacen uwa bata gari ba shi ya jefa shi halin da ya shiga a baya kallon mahaifiyar sa yayi yace ''baba kin dawo lafiya.., kallon ledar hannunsa take yi tana sakace hakoranta tace ''lafiya qalou me ka shigo da shi ne..., tabbas hausawa sunce me hali baya fasa halinsa ƙasa yayi da kansa yace '' taliya ce na samo dakyar bayan nayi faskare a gonar Alhaji mansur gwarzo shi ya saka kuka ga ban dawo da wuri ba ga manja nan ku dafa kowa yaci..., baba wazai ci wannan abar saidai ban ƙi ba kai da mufeeda kwaci jalila ta faɗa tana gyara zaman riga a jikinta duk tabi ta dameta... banza yayi mata yana yi mata fatan shiriya ko sau daya be Allah wadai da halin ya'yansa ba ko yayi mu su baki addu'a ce yana tafi ko yana zaune yi musu yake ungo lami baya yaran nan su dafa mana Wani kallon hadarin kaji tayi masa sannan ta ɗauke kanta mikawa mufeeda yayi ta amsa tana godiya ƙara cewa yayi Allah yayi miki albarka ya kai ki inda zaki huta a zuciya ya amsa da amin murhunsu ta nufa tana kokarin saka icce da sauri asabe ta kwace tace ''wallahi baku isa ba tab ni zaku dura da ka..., Momcy girki zanyi fa dawanau zaki dafa dan ubanki shi da ya baki ai sai ya kawo miki iccen da zaki kona mufeeda ajiye jike ki waje akwai ledoji ki zo ki dafa mana wallahi bani da kuɗin icce kai ta gyaɗa mai ta fita ta jima kafin ta dawo ajiye wa tayi ta soma haɗa huta kuttumar uba nan kusa da kajina kike wannan aiki salon ki babbaka min su shiru tayi jikinta duk yayi sanyi bayadda ta iya da mahaifiyar ta amma sam halinta ba me kyau bane matsa gefe tayi da kyar taliyar ta dawo saboda rashin makamashi Bayan ta gama ta soya manja tace '' momcy a zobo muku..., girgiza kai tayi tana cewa Allah ya sawwaƙe ni dacin fara damai ko magi babu yawa a gidan jero (prison) Baba lami na zobo miki aa barshi kina jin abin da asabe ta faɗa ita da take da sauran kwarinta balle ni a'a kuci kayar ku daga haka ba wanda ta ƙara yiwa tayi zobo musu tayi wadali ishi suka ci har da ragowa tashi sumy tayi tana zuba wata uwar miƙa da hamma zuwa yanzu ta dawo dai-dai amma ba sosai ba tashi tayi ta shiga toilet wanka tayi a lokacin ana kiraye kirayen la'asar aunty sumy baki ji ana kiran salla ba zaki koma makka naji ana kira ta faɗa tana zabga mata uwar harara shiga daki tayi ci gaba da alwalarta tayi bayan ta idar ta tashi ta shiga daki shinfiɗa daduma tayi ta ɗauki hijabin da ya rage musu ta saka ta tada sallah TUDUN YOLA cikin sauri yake toki babban burinsa ya isa gida so yake ya ga gaskiya saboda gudun da yake zabgawa ai kuwa ya isa a yan mintoci ƙalilan tun daga nan babbar ma'aikatar wutar lantarki horn yayi me gadi ya buɗe mai parking yayi ya fito cikin sauri stairs case bibbiyu yake haɗawa na barandar inda zata sada shi da main parlour Cikin sauri yake komai Hajiya ya tarar tana zagaye yawa me ɗawafi tana ganinsa tace '' doctor ya zo yanzu haka yana ciki asharaf anya kuwa ba ƙasar waje zamu ƙara fita ba ko zasu gano abin da ke damun inteesar..., ƙasa yayi da idanuwansa duk irin dauriya tasa nema yake ya zubar da kwalla a hankali ya buɗa baƙin sa yace '' Hajiya kawai mu haƙura mu barwa Allah sau biyar ana fita da ita ba canji kullum abin kara gaba yake wancan satin likita ce min yayi a ƙara taka tsantsan da ita saboda lakarta tana gab da ƙarasa zubewa..., yanzun nan nake ce mata na fito da ita ta sha iska kai ta gyaɗa min shine na dorata a kan wheelchair na fito da ita wallahi bansan yadda akai ta zabe ba wai photo ka zata gani runtsai idanuwansa yayi yana roƙon Allah ya bashi ikon cinye jarabawar nan yana cikin mahuyacin hali ya rasa matar sa sakamakon haɗari inteesar ce ka dai ta rage masa sai yayyunsa biyun da kanin sa junaid duk wanda ya kalli haɗarin sai ya shiga roɗani motar lotsaiwa tayi jini sai mulala yake ba wanda yayi zaton za a samu mutum ɗaya ya tsira a cikin motar sai gashi inteesar ta tsira lokacin da motar take murginowa nusaiba ta cillota banda kujewa da tayi ba abin da ya sameta sai daga baya an kaita asibiti aka ga lakarta ta sami matsala haɗa gawar ta aka kai ta gidan gaskiya ba irin kuɗin da inteesar bata lashe ba amma ji kake shiru ba wani ci gaba maganar ta ma ba fita take sosai ba... Fitowar likita ita ta katsai mai tunanin sa da sauri ya karasa gurin doctor Imam yace '' doctor me yake damunta..?, calm down ansh komai ya zo da sauki yanzu haka ma tana bacci nayi mata allura kamar yadda na faɗa maka zan kara maimaita maka inteesar tana buƙatar me kulawa da ita har tayi bacci Ummina take faɗi dole idan muna so tunaninta ya dawo normal irin nada UWAR GAFALALLU OUMYASMEEN 3-5 sai an nemo wacce zata zame mata copy din mahaifiyar ta cemin tayi zan nemo mata umminta nace mata eh yarinyar abar tausayi ce kamar ta ta haɗu da wannan lalurar gumine ya wanke mai fuska handkerchief ya zaro a aljihunsa ya goge zufar dake tsassafomasa yace '' insha Allahu zan yi maganin matsalar..., wani kallo Hajiya tayi mai ta maida hankalin ta gun doctor tace '' dr na gode sosai..., bakomai Hajiya ki huta lafiya sai anjima to mu jima da yawa fita yayi shiga dakin sukai tana kwance kalbar da Hajiya tayi mata ta kara yi mata kyau an mata ado da beat pink da blue colour adon rigar ta zama yayi a bakin dan gadon ta yana shafa fuskarta Allah ya baki lafiya takwarata a hankali ya motsa lalɓansa yace '' amin..., wacce shawara ka yanke akan batun doctor ba ƙaramin saka shi rudani maganar Hajiya tayi ba sarai yasan halinta kamar yunwar cikin sa gashi doctor ya ƙara saka ta a hanya daman kullum maganar ta nusaiba ta tafi baza ta dawo ba kayi kokarin fitar da ita a ranka tsakanin ka da ita addu'a ganin kamar baya sauraronta tace ...kai da kai fa nake Hajiya wallahi ban san abin yi ba ban gane ba lafiyar ka ƙalau kuwa asharaf ta gumi yayi yana fargabar a bin da Hajiya zata ce ba zai iya zama da ko wacce mace ba tun da nusaiba ta tafi ta barmai duniyar zai ci gaba da zama har shima randa kwanansa zai ƙare yana fatan Allah ya haɗa su a aljanna wallahi asharaf buɗe kunnen ka da kyau ka jini idan har baka nemi mafita ba to wallahi ni da kaina zan ne mi wacce naga ta dace na aura baka shima mahaifinka ya zuba maka ido yanzu Junaid yau sauran wata biyar a yi bikinsa amma kai ko a jikin ka rayuwar ka kake ba abin da ya dame ka ina ji ina gani ba zan rasa inteesar ba bayan kana da maganin matsalar ta na rasa yar uwata na zo na ƙara rasa nusaiba ita nake gani nake jin sanyi a raina ita kaɗai ce ajiyar da nake gani kamar yar uwata hamdiya to itama Ubangiji ya dauke ta shiru yayi ya kasa kwakkwaran motsi har ta gama ya tashi yace '' zan shiga daga ciki bazan koma gun aiki ba ....., okay haka kurum tace masa ganin kamar ranta a ɓace yake ya ɗurƙusa yace '' Hajiya kiyi hakuri insha Allahu komai zai zo ƙarshe.., murmushi tayi ta dafa kansa tace '' da yardar Allah , Allah zai zaɓa a maka matar da zaka ji daɗin zama da ita zata kula da maraicin inteesar nasan abin da kake hange kenan shi ya saka ka kasa aure insha Allahu zaka sami farin ciki Allah ba zai taɓar da kai ba..., tasho yayi yana murmushi fakar idonsa tayi ta goge kwalla hakika suna cikin jarabawa Sai dai Allah ya basu ikon cinye ta fita yayi kai tsaye shashinsa ya shiga ciro wayar sa yayi ya ajie sannan ya kwanta a kan kujera yana kallon P.O.P ya lura duniyar tunani UNGUWAR YAN BITA,KOFAR NASARA tun daga nesa kake hango yan ca'ca damƙam sai bugata suke asabe ce ta fito tana gyara daurin zanin ta da taba a faranti irin na silver din nan da goro har da letar ta ajiye wa tayi tana cewa yauwa jagwa gashi nan ta dubu biyar ce cib wallahi naga ba haka ba billahillazi sai ka biyani ficikata ba za tayi ciwo ba asabe idan zaki dinga zargina to wallahi zan dena amsar kayan ki ke kenan kullum zuciyar ki da tsatsa kut langa langa ce ba tsatsa ba sau nawa kake min runto shafa gemunsa yayi yace sau uban talle ehyi mee kace yar dariyar shaƙiyanci yayi yana cewa a'a ba magana kika ji nayi sarai ta gane sunan babanta ya kirawo ya ce sau uban talle tashi tayi tace '' na tafi police station..belin sunusi..., to sai kin dawo gyautai ne ya ɗago da sauro yace '' Asabe ina zuwa haka da yammacin nan..kike sauri kamar zaki tashi sama ko wani abin ne ya faru ki dan tsakura min..., wani kallon banza tayi mai tace '' Gyautai inda ka aike ni..., to abin kuma har da faɗar magana cewar gyautai yana har haɗa katin karta gyara matafinta tayi tace '' ajiye ni kayi da zakai min wannan maganar wallahi gyautai ka kiyayeni ke kenan jiya a yau ko ca'car nan ba wani min sa'a kake ba..., girgiza kai yayi yace ''Allah ya baki hakuri amma wallahi zaki zo ki same ni saina karta miki rashin mutunci.., yana gama faɗar haka ya juya ya ci gaba da ca'car sa., wata dariya ta sheƙe da ita tace '' mudai kartawa juna har ni zaka faɗawa tashanci ka manta wacece ni.., ina fa namanta wane besan halin uwantale ba kudai ga kunan duk ba na Allah gwara mu gidan mu gidan malamai ne wata uwar dariya tayi tana buga cinya tare da rausaya irin na tsofaffin yan bariki sannan ta juyawa tayi ta fara tafiya wayar ta ce ta fara ringing a ciki ta soke ta da sauri ta fito da ita ganin sunan D.P.O wata uwar dariya tayi tana cewa shegen kaya yaga har yanzu be ji wani motsina ba shine yanzu ya biyo sawu na to gari yaci wuta aljihu ba ko sisi ɗagawa tayi ta kara a kunne tace '' to uban son kuɗi daman tun da naga ka kama yarona kuɗi kake nema.., D.P.O yace '' ki zo da wuri wallahi dan gobe zan tattara su na kai kotu babban laifi ya aikata kuma har ke ta shafa domin cewa yayi ke ce dilar sai da kayan maye duk wani kayan maye kina siyar wa har hodar ibilis dan haka idan baki zo ba har ke ta shafa ato..., a fusace tace '' kai anya kuwa kanka ɗaya na zama dilar kayan maye na zauna a haka kai kasan wallahi nafi karfin gidan da nake zaune sai dai zama a j.r.a kuma wallahi karya kake kace ya faɗa maka haka , haka kurum sai ka bushi iska ka dinga kama mini yara to wallahi hawainiyar ka ta kiyaye ramata gani nan zuwa dubi biyar zan baka daga ita ko kobo bayan ƙara ba domin wallahi a haka ma da nawa na ƙara kasan an kama ANAI to na batar da kuɗi wallahi kafi a sako shi hukuncin shekara biyar fa aka yanka mai to ko wata bakwai beba suka sako shi yanzu a kudin da suke tarawa sauran dubu uku yar satar nan ba samu suke sunayi ba yanzu kowa taka tsantsan yake da abin sa rayuwa tayi tsada.. yanzu so nake na tafi nijar na nema musu sa'ar rufe ido damfara za su fara wallahi ina dalili bani da komai ya ƙare..., cikin ɗaga murya D.P.O yace '' to wallahi kar ma ki sake ki zo, me kika mai dani ban san me nake ba kome belin kwatan dan ta'adda shi ne za kiyi a 5k yawa belin ƙaramin ɓarawo tab gyara kalaman baƙin ki kema kinsan bazai saɓo ba bindiga a ruwa..., da sauri ta tari numfashin sa tace '' to ka ci gaba da riƙe shi......yawa da chainanci nake maka bayani ka kasa fahimta kana ga jibi ajon dan bashir ya kake so nayi da raina sarai kasan yadda ajo yake ba sai na tsaya ina yi maka dogon bayani ba dole rance zanci nima na fito na watsa yan dubu dubu..., ke wai da ruwa muke magana...kin tsaya kina yi min sokiburutsu kema baki wuce na jefa ki a cell ba hhhhhhh anayi muna jin dadi ni asabe reza zaka jefa a cell tab to wallahi ka iya baƙin ka ni abin kunya baya na bashi sai na tona asirinko ko banza zan samu sassauci a gurin hukuma amma kai fa ba hukuncin da baka sani ba ka take kana karbar haram ta faɗa tana girgiza yawa a gabasa take jin wayar ta tace kitt da sauri ta duba dariya tayi ta soke ta a inda ta fito da ita kamar saukar a rado taji durowar mutum yace '' ke kawo wayar hannun ki.., da sauri ta ɗago tana hura hanci tace '' ban gane ba..., zaki fito da ita ko sai nayi gunduwa gunduwa da naman ki Cikin sauri asabe tace '' a'a sala sala za kai da nama na dan kuka ashe haka ka zama., da sauri wanda yake laɓe ya fito shine wanda idan ya kwata zai cilla mai ya gudu yana shan sholisho yace '' baba ankar mana uwar gafalallu ce..da hallacan zo mu ware.., a'a hafizu da ka barsa na ci kuttumar ubansa wallahi har yanzu nima ina ji da dabanci banda haihuwa da ta gama buɗa kashina ai wallahi da tuni wani zancen ake yi ba wannan ba cewar asabe tana kulle mayafinta a ƙugu wucewa sukai ba tare da sunce mata komai ba kunce mayafinta tayi ta daura a kafaɗa ta ci gaba da tafiya tana yar waƙa bakin titi ta fita batare da ta tsayar da me napep ba ta fara tafiya har ta isa police station tana shaga tace '' dan bala ina DPO yake.., banza yayi mata ya ci gaba da rubutun sa doka kantar da yake rubutu tayi tace '' kai dan bala ba da kai nake ba amma ka ci gaba da rubutun ka bawa banza ajiyata to wallahi zanyi maganin ka har ni zaka kalla ka watsar yawa sa'ar wasan ka...?, daga littafin sa yayi yana dubawa tamkar da dutsai take magana a fusace ta warce littafin tace '' tambayar ka nake ina DPO yake...?, ya tafi koyo sallama ya bata amsa kamar ba shi yayi magana ba kama kugu tayi ta ajiye littafin tace '' to yanzu na fahimci inda ka dosa kuma zanyi maganin ka ..., kofur inusa ne ya shigo yana cewa tab yau manyan ƙasa ne a gidan namu gyatsuna fuska tayi tace '' kai ni ajie wannan wasan a gefe tawa ce ta kawo ni shi wannan cutar kurumta ce ta kama shi na tambaye shi yayi shiru yana yi min kallon hadarin kaji.., kofur inusa yace '' hajjaju me ya faru duk wata hanya ta kurɗa kurɗa kinsan na kware a gurin nan ba inda bana shiga na fito indai da hatumin na sara kina mannamin zaki ji information.., zama tayi a kan benchi tace ''hmmm kufa tsiyata da ku kenan komai kuɗi wallahi ku guje ranar da Ubangiji zai damƙe ku ina ji ye muku wannan rana amma ku bakwaji haram kuka saka a gaba duk inda cin hanci yake kuna nan ku dashi kamar dan jumane da dan jummai.., kinga faɗamin me ya kawo ki na lura yau ba arziki kika zo gurin nan cewar kofur inusa kamar kuwa ka sani dan wallahi kalma kaɗan za ayi min na zubar da haƙoran mutum wallahi har ni za a nunawa rashin mutunci cikin daga murya kofur yace '' asabe reza tamayar ki nayi me ya kawo ki...?, amma kin tsaya kina tayi min wasu zantuttuka ga abin da na tambaye ki amsar da kike bani dabam to bani da lokacin fast fast maza ki faɗamin ina da abin yi..., to sai ka nuna wanda bashi da abin yi ta faɗa tana harararsa ke ki fita idan sa'insa kika zo yi gurin nan dan bala ya faɗa yana haɗe rai domin sam ba shiri suke da ita ba tofa yau nake ganin kudirar Allah yanzu fa tsab zai iya dagani ya fitar dani to wallahi ba ka san wace mace ba za ka haɗu da dana sani mara a dad'i ta faɗa tana wura hanci a'a abin duk be kai haka ba mu nan gurin wajen sasanci ne ba gurin tada tarzoma ba ke asabe me ya kawo ki gwara kiyi kiyi ki bar gurin nan domin na lura yau transformer kika haɗiyo Alkur'an baza ki amayar mana da ita a nan ba yanzu jikin ki sai yayi tsami hukuma gaba take da kowa cewar kofur inusa tamkar me shirin dauko duniya haka ta zura hannu a zaninta tana lalube tsayawa sukai suna kallon kudirar Allah sai can ta fito da kudi washe baki tayi tace '' kofur ina DPO..?, kauda fuska yayi yana gyara zaman hularsa kallon sajan dan bala yake domin shine gaba dashi yanzu yana ba dai-dai ba DPO zai ta magana yawa yayi me wanna hali nasa shi yake gudu UWAR GAFALALLU Episode 6-7 tofa kai ma nayi maka magana kayi shiru me hakan ke nufi wallahi ni karamin aikina ne na shiga har office dinsa to wajen nan baƙona ne bani da wani lokaci wani satin nijar zani naje na nemo sa'ar da yaran nan zasu dinga samin dan na ɓatarwa komai ya tsaya chak dan kuɗin da suke tarawa shima yanzu ba wani bane da yake yanzu ba lokacin siyasa bane, ba dan siyasan da nake gani dan haka raina duk a bace yake kuyiwa kanku kiyamal laili ku fadamin inda yake, bayan kuma shi ya ce na zo ya kama sunusi kallon kallo suka shiga tsakanin su ba me magana sajan dan bala ne yace '' yana ganawa da baki ne ..., ai be rufi bakin saba sai gashi ya fito yana washe baki yawa gonar audiga shi da wata yar duniya sai gyara mayafinta take yana ganin ta yace '' sweet sai mun ƙara haduwa nagode da kawo miin ziyara da kikai..., wani far tayi da idonta tace '' sweet kar ka damu insha'Allah zaka dinga ganina akai akai.., wata dariya DPO yayi yana shafa ƙaton cikin sa yace '' aikuwa sweet nagode sosai..., hannu ya daga mata har ta kulewa ganinsa sannan ya juyi kan asabe yace '' asabe yar tasha ke da nace miki karki zo shi ne kika zo me zan miki belin katotan dan ta'adda zan bayar a dubu biyar yawa belin ƙaramin ɓarawo me satar kaji to ko masu satar waya idan sun kawo min ziyara haka kurum batare da wani abu ba dubu hamsin suke bani shi yasa ka zaki ga bana kama su na barsu suna yadda suka ga dama a garin nan balle belin dan daba makashi mutum nawa ya naƙasta a ƙa'ida ma wallahi gidan gyaran hali za a kai shi ai mai daurin rai da rai amma saboda kin daure mai ai gashi nan yana yawo a gari..., kwantar da murya tayi tace '' DPO ka temaka wallahi dubu biyar ɗin nan ce dani kuma kaga ..., kinga bana son dogon bayani shigo daga ciki tashi tayi ta bi bayan sa zama tayi a kan kujera shima ya zauna a tasa yace '' ci gaba ina jin ki..., yauwa temakawa za kai ka sakar min shi a haka yanzu harkar damfara nake so su fara wallahi gari fa yaci wuta ji kake ɗib ba wani bayani yan siyasa ma yanzu ba lokacin zaɓe bane kasan ita wannan gwamnatin bawan Allah nan baya yawo da yan daba sai ma ya nema musu abin yi dan shiru yayi sannan yace '' to bani amma wallahi dan kece da ace wata ce wallahi bazan karɓa haka ba ko kuɗin da na kashe mai ban mayar ba ga zagina da yadin Ka yi kullum sai ya saka na a siyo mai tabar wiwi da maganin sauro saboda tsabar samun waje har da a siyo mai turaren wuta nace wallahi baka isaba nan dakin uwar'ka bane ko gidan uwar gafalallu ne..., rausayar da kai tayi tana cewa nagode DPO Allah ya barmu tare Allah ya saka wata ran a baka IG wai za aga iya shege ai harka zan fara da yan fashi kinsab fa sun fi kawo kudi me tsoka wallahi wata miliyan ashirin a sati sai na jita a account dina wallahi Kai DPO wai ina zaka kai kuɗi haka hmm nima bani kaɗai nake cinyewa ba ni da abokanan hurɗata muke cinyewa sun fini ma ci wallahi sai da kuɗi suke zama idan ba kuɗi wallahi kashi ya fika mutunci a idon su shi yasa ka nake neman kuɗi hurjajhan domin a samu a faranta musu rai cewar DPO yana amsar kuɗin da ta bashi tashi tayi tana cewa to zo muje ka sako shi mu tafi tare domin wallahi bazan yadda ba na tafi na barsa ka sake saben lale tashi yayi yana cewa ke ko irin kewarnan tawa baki ba haɗe rai tayi tace '' wallahi tun da nayi aure na bar wannan sabgar ko sha'awa bata bani wallahi daidai har a kwanar dan gora na zauna zaman kaina kai duniya haka ma fa tayi mana da kyau wasu su nan sun haukace..., amma kika saka ya'yan ki a wannan hanya kinsan da haka ya faɗa yana kafeta da ido domin har yanzu da kyen jikinta komai yana nan kamar ba ita ta haifi zaratan yan matan nan ba har guda hudu rigis lashe baki yayi ya ci gaba da cewa Please ko sau ɗaya a bani na taɓa sai kuma fa kayi wallahi haka kurum da aurena to biyo ni ki amshe shi wallahi ya bari muka ƙara kama shi hmmm sai ya gammace kiɗa da karatu dan wallahi sai na goge mai duk wata hadda dake kansa ban da rashin mutunci ace duk wani fadan daba kai ne a sauhun gaba kwanaki fa gwamna ya kirawo shi akai sulhu amma shine ya ƙara jan wata tawagar kaga bana son dogon jawabi muje ta faɗa tana gyara zaman mayafin ta a jikinta domin idan ba wuta wuta tayi mai ba sai dare yayi mata anan kuma kyalli baya son ta kai dare duk inda taje magariba tayi mata a gida dan ma dai ba wai tsoransa take ji ba be isa ya saka mata doka tabi ba .... batare da yace mata komai ba ya fita binsa tayi har baƙin cell ya bude sunusi fitowa yayi daman yana baƙin kofa wata uwar miƙa yayi yace '' hajiya asabe reza...sai yan zu kika ga damar zuwa.., kaga nususi idan baka godemin ba ai baka tsinemin ba dududu kuɗin da kuke tarawa nawa yake ....? yanzu ma sai da na saka jagwa ya ɗan har hadomin sannan na samu damar tawowa wallahi rashin hakurinka yayi yawa yasin to ai shikkenan hakan ma na gode a gidan mu wane yazo sai ke da bakya gajiya damu au ashe ka gane gaskiya wuce mu tafi cewar asabe tana dafa kafaɗar sa kai kuma zamu haɗu a way ne wallahi sunusi ya faɗa yana mai da idanuwansa ciki dariya DPO yayi yace '' wa kake faɗawa haka lallai yaron nan wallahi idan bakai wasa ba sai na mayar da kai inda ka fito wallahi.., wani kallo sunusi yayi mai yana nuna mai ya tsunsa biyu tankaɗa ƙeyar'sa tayi tana cewa maza maza mu tafi shige mu tafi shigewa yayi yana faɗi yaci uban malin malin da takalmi combos da hula irin ta kaurayen nan kai bani wayata tunda bata tsoho bace kofur inusa ya miƙo mai warta yayi yana cewa wallahi da kudina a ciki naga babu sai na dawo anyi ta wallahi domin bazan yadda ba haka kurum ku cinye min kudina da sauri asabe tace '' kai wanne kuɗi kake magana...?, to uwar son kuɗi katina ne na saka na dari biyu sunusi ya faɗa yana bincika wayar sa to bana son neman magana shige mu tafi bana son bar baɗa haka kurum ka ƙara ballo min ruwa har nawa kuka tara da zan ƙara zuwa belin ka wallahi sai dai akai ka gidan yari idan na samu na fito daga kai cewar asabe tana tankaɗa keyar sa sukai waje ci gaba tayi da magana tana cewa yauwa nifa a kafa na tawo dan haka idan zaka iya to sai ka tawo mu daɓa dan wallahi bani da kuɗin mota ƙaramar wayarsa ya fito da ita yana lallatsawa dakyar take dannuwa sunƙuyawa yayi yana neman tsinke yace '' Bara na kirawo honourable ya turo min da kuɗi domin wallahi ba zan iya tafiya a ƙafa ba yawa wani doki ai sai maƙiya ma su yi dariya ana nunani da baki ana cewa ga sunusi ta ƙare mai idan ke zaki iya tafiya to ga hanya nan mu haɗu a gida kawai...idan ma ban same shi ba zan kirawo bazzawara ta turomin kuɗi..., asabe dundu tayi mai tace '' a'a kirawo shi idan naji zai bayar sai ka bani kudina ni zan tafi a ƙafa..tafiyar nawa take.., kai ka kai ni kika daka me nayi miki wannan wanne irin cin zaline sunusi ya faɗa yana ɗagowa ganin bata kula shi ba ya ci gaba da kiran amma ba a ɗauka ba duk wanda ya kira ba a picking kamar haɗin baki suka juyo a tare suka kalli juna wata dariya asabe tayi har da buga cinya tace '' me kake jira naga jikin ka yayi la'asar kaga tun kafin dare yayi mana a nan gurin kazo mu tafi.., Ba tare da yace mata komai ba ya fara tafiya binsa tayi har suka isa gida ba me ce wa dan uwansa kala al'adar gidan ce bayan sallar magariba wa'yannan masu ca'car zasu kasa gurmi ai ta kiɗa mahauta nata sudda baru dan haka kafin isha tayi har sun hallara, wani maroƙine ya taso yana cewa cau cau cau sarkin daba ko wa yaƙi bin umarninka yanzu lahira za tayi baƙo huƙa ya ƙarba a hannun wani yana wulwulawa sosai maroƙin nan ke wasa shi kuɗi yan gurin suka fara zuba mai ana liƙi shiga gida tayi ta bar su da sauri tace '' innalillahi me zan gani jalila daman ban gama kashe wutar nan ba shi ne kuka ƙara wurata har ta kai ku da gwada yar ƙashi .., Cikin haƙi jalila tace '' wallahi momcy idan ban karya yarinyar nan ba wallahi Allah ba zata fahimci ni da ita da babbanci takwalas ne ya turo da kuɗi yace gashi nan mayi kunshin bikin ajo shine wai dubu daya zata bamu ta riƙe dubu shidda.., taɓarya ta dauko a kusa da bayi tace '' ku cika juna ki na sauke muku allon kafaɗa wannan wanne irin iskanci ne ku bani kuɗin kowa ya rasa da man ke jalila baki kawo min balance ba maza maza ke sumy zo ki ciro min kuɗin nan wallahi kun rasa saboda da tsabar mammaƙo wanda kika je gurin sa ko kobo bani da tabbacin ya baki..., rabuwa sukai har rigar naja ta yage bako kunya ta bata rufe jikin ta ba duk kirjinta a buɗe maza ku miƙo min tun kafin na ci mutuncin ku asabe ta faɗa tana kafe su da idanuwanta miko ATM din tayi amsa tayi tana cewa mene pin din Kau da kai naja tayi ita bawai faɗar ne ba za tayi ba yanzu momcy zata samu damar ɗaukar mata kuɗi tana yi mata bincike tace '' kawo naje na curo har yanzu sumy bata cikin hayyacinta..., miƙa mata tayi ta amsa shiga daki tayi ta canza kaya ta fita neman guri jalila tayi ta zauna akan tabarmar da mufeeda ta shinfiɗa Lami yar gumama tace '' sai yanzu kika dawo.., wallahi baba sai yanzu dakyar ya bani shi kinsan fa yanzu komai ya tsaya asabe ta faɗa tana zama ɗaukan kayan da ke gaban baba tayi tana cewa kai wannan riga tayi kyau Ajiye ninƙin da take tayi tace '' nima wallahi naga kyawunta yan zun nan challi ta kawo min su gobe insha Allahu yarinyar nan zata dauka mi tafi kasuwa.., ni wallahi Allah bana son zuwa gurin yan gumamar nan yan iska ne wallahi mufeeda ta faɗa tana turo baki wani kallo baba lami tayi mata sannan tace '' dan kan uwar ki sai kin je su wa'yannan manyan mata ne ke ce ƙarama duk da dai kina nema ki kere'su ga kirga dangi nan duk ya cika miki kirji yawa za su faso kirjin ki su fito amma ba fuss tsuliyar me duki..., turo baki tayi tana kunƙini ta tashi jin an kira sallar magariba tashi tayi ta dauro alwala bayan ta idar ta kalle su tace '' baba an kira sallar magariba fa.., ba wanda ya tanka ta balle baba da ta cika tayi fam ninke kayanta ta ci gaba dayi tana rera wakarta da tashi tayi ta shiga daki ta tada salla zama tayi har aka kira sallar isha'i lokacin kuma har gidan su ya fara dinkewa da jama'a na kallon gurmi bata fita ba ta kwanta a ɗaya tana jan carbi domin hana zuciyar ta tunanin komai ke miko min mayafina kinga naja shiru yawa an aiki bawa garin su kar dai yau ba a nan zata kwana ba tashi nayi zuciyata na ƙuna na miko mata mayafin ta sannan na koma na zauna fita tayi tana sababi TUDUN YOLA ƘARFE 8:45 baka jin karar komai sai ta chokali da AC kowa ya mai da hankali kan abincin da suke ci ido Hajiya ta karawa Ashraf tace '' Ash kamar akwai abin da ke damunka tun dazu sai juya chocali kake ka kasa ci idan har ba zaka hana kanka tunani ba wallahi zakai mutuwar tsaye ka takurawa zuciyar ka sai tunani kake mara makama da abin yi to wallahi ka rufawa kanka asiri ni wallahi abin ka har tsoro yake bani ai wannan rashin tawakkali ne yanzu ina iyayena ba hakura nayi ba na ci gaba da rayuwa bawai tana yi min dadi ba a'a kawai dai na ɗauki hakuri amma kai ke nan ai ta abu ɗaya.., ƙasa yayi da kansa kallon sa mahaifinsa yayi yana cewa haba Ashraf yan zu kai takure kanka da kayi shine jin dadin ka kome Ubangiji yana jaraba mune yaga iya kacin imanin mu mutane nawa suke naman damar da Allah ya baka mutane nawa suke cikin wani mawuyacin hali amma sun saka hakuri da dangana Ubangiji fa yana jarabtar bayin sa na kware ne Ashraf sunkuyar da kai yayi yace '' insha Allah zan ɗauki nasihar ku bawai na kasa cire nusaiba a raina bane yanzu wannan lalurar da inteesar take ciki ita take ƙara jefa ni cikin rudani..., damuwar ka ba zata saka ta samu lafiya ba sai ma ayi biyu da kwance uwa kwance kaga ba amfani ke na ko Hajiya ta fada tana goge bakinta da tissue Kai ya jinjina sannan ya ci gaba da cin abincin sa dan ƙadan ya ci daman shi dabi'arsa ce baya cin abinci da yawa tashi yayi yana cewa Hajiya Alhaji sai da safe insha Allahu nan da wani satin zan kaiwa junaid ziyara Cyprus daga nan zan biya nayi umara to masha Allah Allah Ya kai mu lokacin Alhaji ya faɗa cikin kulawa Hajiya tace '' insha Allahu lokacin da matar ka zaka tafi.., ajiyar zuciya ya sauke ya juya ya fara tafiya hajiya ta kasa fahimtar sa shi ba wai zama da macen ne bazai iya ba a'a gani yake ba matar da zata iya kula da inteesar gwara su zauna su biyu har ta girma yayi mata aure ba zai juri ganin ana wulakanta mai yarinya ba musamman ma , matan yanzu da kansu kaɗai suka sani babban burin su idan sun shigo ba wanda zai raɓi mijin su sai su kaɗai da yan uwansu wata ma kuwa duk wani naka saita rabaka dashi sun matana da ita rayuwa shiga da fice ce wanda beba ma akai mai balle kinyi wata da addabawa uwar miji ta manta da wannan karatun cewa itama uwar miji ce wata rana yana wannan tunani har ya kasara shashinsa chak ya tsaya ganin kamar tana yi mai murmushi ta wara hannu wanta biyu da sauri zai kamota sai ta ɓace runtsai ido yayi jijiyoyin kansa sun fito rada rada tabbas shi da kansa yasan ba lafiya yake ba anya kuwa be zama dis order ba ta ko ina ya kasa haɗa son da yake wa nusaiba ta ko ina tayiwa mata fintinkau adai zamanin nan ba lallai a samu kamar ta ba 🤔 dakyar ya ja ƙafafuwansa ya dauko mukulli ya buɗe shiga yayi tsayawa yayi yana kallon ko ina na gurin kamar yau fa aka kawo masa ita a matsayin mata duniyar tunani ya lula wai waye adon tafiya wallahi nusaiba ji nake kamar na janyo ranar nan ta dawo yau Ashraf ya faɗa yana kafeta da idanuwansa kau da kai nusaiba tayi tana wasa da hijabinta tace '' da yau da ranar juma'a duk ɗaya ce a gurin Allah, Allah dai ya kai mu da rai da lafiya..., Anya kuwa ban fiki son mu kasance tare ba rufe fuskarta tayi da tafukan hannayen ta tace '' bansan da wanne baki zan kwatanta maka irin adadin son da nake maka ba.., ni wallahi sweet anya kuwa wannan kunyar take zata bari ki nunamin son da kike min jin gina tayi a jikin kujera tace '' kaidai Allah ya nuna mana lokacin lafiya.., sarkin wayo maganar ce bakya so ko har abada bazan gaji da sauraron daddaɗar muryar ka ba ina rokar Ubangiji idan zaka mutu mu mutu tare bazan iya rayuwa idan bakai son ka shine jini na jikina kaga kuwa mutum zai iya rayuwa ba idan babu jini lumshe idanuwa yayi sai kuma ya buɗe su yawa me jin bacci yace '' nima bazan iya rayuwa babu ke ba Allah ya raya mu tare ya kashe mu tare.., amin ya Allah tashi yayi yace '' zan shiga daga ciki lokacin da Hajiya ta diba mana ya cika tsoro take kar nayi aika aika.., murmushi tayi batare da tace mai komai ba wallahi maganganun sa kunya suke bata ashe shima ba kanwar lasa bane a satin nan fa lamarinsa har mamaki yake bata kamar ba yayan da tasani bane me muzurai da tsare gida amma a yanzu kam ita sheda ce ko kallon da yake mata na zallar so ne magana fanake miki kinyi shiru ko na zo na raka ki dakin ki Ashraf ya faɗa yana ƙara kafeta da idanuwansa rufe baki tayi tana zaro Ido UWAR GAFALALLU EPISODE 8-9 PERFECTLY PEN'S rufe bakin ta tayi tana zaro Ido tace Please yaya ka rufan asiri ka tafi kar Hajiya ta biyo sahun mu wallahi Allah jiya faɗa tayo min sosai tace sai ta hana ni fita idan an kai ni gidan mayi kome za mu yi dariya yayi ya nuna mata hanya yace '' Hajiya kenan ta gama isarta ƙarshe dai dole ta kawo miki bissalam Allah ya tashe mu lafiya.., nusaiba tace '' amin ya Allah tana fara tafiya sai da yaga tayi nisa sannan ya juya ya tafi part dinsa yana shiga junaid ya shigo da yake dakin su yana kallon na juna kallon a gogon parlour ASHRAF yayi yace ''9:30 kai kuwa ina kaje haka kasan fa Alhaji baya son yawa Junaid a dinga kiyaye wa kar kuma ya saka maka dokar fita.., kallon a gogon dake manne a bango Junaid yayi yace '' wallahi naje gidan su Abubakar ban san lokaci ya ja haka ba amma insha Allahu zan dinga kiyaye wa hakan ba zata sake faruwa ba ..., Kai ASHRAF ya jinjina yace '' Allah ya saka yana shiga dakinsa shirin bacci yayi sannan ya kwanta.., Washegari cikin sauri take haɗa musu breakfast Hajiya ce ta fito tace '' a'a nusaiba har kin tashi kin fara aiki...?, Eh wallahi Hajiya bana so na ɓatawa yaya lokaci ransa ya ɓaci yayta jira shi ya saka na ɗora da wuri cewar nusaiba kanta tsaye domin ta manta da halin hajiya na zolaya yanzu zata tusata a gaba dafa table din kitchen Hajiya tayi tace '' kaga me miji wato kar ki ɓara mai rai daman haka ake so matar kware ta dinga yi.., murmushi tayi batar da tace komai ba fita Hajiya tayi bayan ta gama ta kwashi komai ta kai dining jin sallamar su ta ɗago amsa wa tayi tana gaishe da Alhaji har ƙasa Cikin kulawa ya amsa jawa kowa kujera tayi sannan ta zauna zuwa kowa tayi junaid na tsokanarta Alhaji na tare mata shi kuwa ASHRAF kamar baya gurin cin abincin sa yake cikin kwanciyar hankali bayan ya gama ya saka tissue ya goge bakinsa ta tashi zai bar gurin yana cewa Zan tafi gun aiki kallon sa alhaji yayi yana cewa gaskiya bana son zuwan ka wajen wutar nan ga kasuwanci nan idan ma baka san zama a ƙasar nan ga shaguna na Dubai kaje kayi kasuwancin sai da gold ana samu sosai ƙasa yayi da kansa baya so ya tashi a jingina da ƙarfin mahaifin sa yafi so ya nemi nasa yasan zafin nema dariya Hajiya tayi tana cewa ASH ba magana naga kayi shiru sosa ƙeyarsa yayi yana cewa sai na dawo na tafi Alhaji ne yace '' Allah ya kiyaye hanya ya bada nasara da sa'a tun da kafi son nan sai mu bika da addu'a..., wallahi kuwa Hajiya ta faɗa tana kallon nusaiba ta ci gaba da cewa nucy ba rakiya...?, kai ta gyaɗa mata a hankali tace '' Hajiya ba sai na raka shi ba.., kwaji da shi zama ku dawo dai-dai ne ta faɗa tana tashi daga gurin shiga bedroom dinta tayi bayan kowa ya gama ta kwashe kayan ta kai su kitchen akwana a tashi ba wuya yau ta kama juma'a za ayi daurin aure sosai manyan ƙasar nan suka halarci daurin auren NUSAIBA ABDUL HADE da ASHRAF MANSUR GWARZO amma ban da dangin mahaifin nusaiba kalilan ne suka zo domin ba son auren suke ba akan wani ban zan dalilinsu mara makama da abin yi gani suke Hajiya ta nuna musu kuɗi taya yaya yarinya ta taso a gunta kumu ta aurer da ita ba tare da ta Da musu da ita ba dan tana taƙama da kuɗi... bayan an gama daurin aure da yamma akai lecture daga nan a ka wuce da ita dakin ta ba abin da Hajiya da Alhaji suka rage ta dashi komai sun mata haka kowa ya watsai ya bar ta ita kaɗai bata da tarin ƙawaye bayan isha na shigo gidan.... nima da yake bani da abokanai abokina ɗaya salim shima a waje muka rabu shiga nayi tare da addu'ar Allah ya kade mana fita Allah ya bamu zaman lafiya tura kofar nayi abin da na zata shi ya faru a buɗe take na shiga bakina dauke da sallama bakowa a parlour direct bedroom na nufa nayi sallama ɗagowa tayi ta amsa min sallama ta tsayawa nayi ina kallon ko ina tare da da yiwa Allah godiya da ta cika mana burin mu mun mallaki juna tun da mukai aure ba mu da taɓa samu. Saɓani ba nusaiba tana da haƙuri za kai mata ta dauke kai ni ko da tasan Kai mata din har Allah ya azurta mu da yarinya, ranar da zata tafi ganin dangin ta lokacin inteesar tana da two year hatsari ya faru me kama da almara ajiyar zuciya ya sauke lokacin da ya gama tunaninsa tafiya ya fara har ya shiga palour sa zama yayi akan two seater ya zuba ta gumi kallon agogo yayi karfe 12:00 gaskiya ya dade a zaune a gurin nan haka ya kwashi lokaci.. Wannan kenan baccin tane yayi nisa ta tamkar daga sama taji ana bugu tashi tayi tana kunna yar ƙaramar fitila tana jan tsaki ashe naja bata dawo ba tun daga zuwa ciro kudi tashi tayi jin zata karya musu kofar da suke ƙarawa da ita ta fita tayi ta isa soro ta buɗe kofa ta tsaya a baya tana liƙe bak'ar motar da aka kawo naja a cikin ta har da tinted to munafuka uban me kika tsaya yi sauran kuma kice mata na dawo dan ubanki bani kuɗin da kika ciro da wanda kika samo ni wallahi bansan ke yar marasa bace sai yau wallahi momcy be bani wani kuɗi ba yau muka haɗu dashi ta faɗa tana turɓune fuska uban be baki wani kuɗi ba bani ko ya zu wallahi na caje ki asabe ta faɗa tana zaro ido ba yadda ta iya haka ta miƙa mata kudin murmushi tayi tana kirga su dubu arba'in cis tace '' ina dubu biyar din ta kwalas...?wallahi naja ki kiyaye ni kuɗin nan zu zasu wanke ki daga laifin da ki kaimin, zun buro baki tayi ta miƙa mata amsa tayi tana washe baki Allah ya tsare ya kuma buɗa kofofin hanyar samu... saboda takaici kasa barin gurin nayi ƙafafuwana sun kasa ɗauka ta yan zu rufa'i ko kirana ba yayi saboda taje har gidan su taja mai kunne tashi nayi na bar gurin ganin sun tafi sun barni kulle kofar nayi na koma ciki shiga daki nayi runtsai ido nayi ganin tashin hankalin da na gani jalila sumy suna ta aikata masha'a kamar ba yan uwa ba kamar addinin mu be yi hani da wannan dabi'ar ba kasa shiga nayi na dauro alwala na daman da hijabi a jikina shiga dakin baba lami nayi sai sharar bacci take har da mun shari shim fida daduma nayi na fara nafila bayan na idar bacci ya ɗauke ni can kuwa ɗaki ai ko a jikin su ganin mufeeda ta gansu breast din sumy da shi jalila tayi bacci basa tunanin Ubangiji zai iya ɗaukan ransu a haka a kuma tashe su a haka me za su ce mai jin kiran sallar asuba suka tashi ko wacce taje tayi wanka ta dauro alwala kallon su mufeeda tayi tana cewa kuji tsoron Allah abin da kuke aikatawa ba me kyau bane abu mafi muni tun kafin ta ƙarasa sumy tace '' kiyi mana shiru wallahi kema baki wuce na kwantar da ke ba na kwakuleki tas..., kai ta girgiza ta bar gurin ƙasa sheƙewa sukai da dariya suka tafa har sun tada kabbarar salla suka ji muryar takwalas da sauri suka sallame sallar suka fito yana sanye da jallabiya yaci dauri ture kaga tsiya wata uwar buɗa ya saki yace '' kut gaskiya mutane na kun yi kyau kunyi acan acan dan tafiya lagos da nayi shine kuka tara wannan kayan aiki haka to gaskiya nima ba za a barni a baya ba ina momcy take ...?, dariya sumy tayi tace '' tana bacci kai ma wallahi Lagos ta amshe ka.., kan bura ubancan kayyasa ai anan kano ba komai ake ba sai da naje Lagos sanna na ƙara fahimtar rayuwa wallahi idan har zata bar ku hmmm kudi ta riga da ta zama attajira sufa ba irin biyan nan suke ba musanman ma ki haɗu da direba ko yare ba abin da basa kashewa mace ya faɗa yana buga cinya hadi da fari naja ce tace '' dan Allah ta kwalas ...?, murguɗa baki yayi yana fari da idanuwansa yace '' zauna wasa har lokacin ki yayi ya ƙare ba abin da kika tara can fa ba me damuwa da wani kowa harkar gaban sa yake..., Ikon Allah yanzu kowa sai yayi sabgar gaban sa ba me damuwa da kowa anya kuwa jalila ba nan za mu tafi ba cewar naja gyara daurin kirjin ta tayi tana cewa nima fa abin da nake tunani kenan wallahi gwara mu shiga sahun manyan mata wata uwar shewa suka saki tare da cewa a hayye ras wannan shewa ita ta tasar da momcy ta fito dai-dai shigowar baba cikin daure fuska yace '' kai bana ce maka kar ka ƙara shigo min gida ba ..?, gaskiya ba ruwan ka malam ya kake yawa ne nan ina gidan yake kwango dai amma wannan ba gida bane ka bari sai arziki ya zo ya same ka kana kwanciyar asarar nan da kake kayi gida wallahi ba ruwan ka da kawayena da suke zuwa guna da kuma na ya'yana naga ma gado aka ci aka bar maka shine kake tun ƙawo da shi Asabe ta faɗa tana yatsuna fuska da tabe baki kasa magana yayi sai ma kasa da yayi da kansa ya wuce be ƙara ce mai komai ba bayan kaddarar da Allah ya yi mai to Ubangiji sai ya ƙara jarabar sa da asabe bayan ya shiryu shiga daki yayi yana jan carbi ko zai samu saukin zuciyar sa kunga zo mu shiga daki takwalas sai ka sako da ga farko asabe ta faɗa tana nuna musu dakin ta shiga sukai ya dinga basu labari momcy tace '' bara mu gama bakin ajo ko bayan ka tafi ne sa tawo har waccen yarinyar sai an tafi da ita naji dakai na wallahi..., sai ma karshen watan nan zan tafi sai mu tafi tare hakan ma yafi yi min gwara su sauka a hannun ki ai momcy ina faɗa miki gida na gina kowa ya zo ya shiga ya bani yan kudina a agege kai ka akai kace litkafa taci uwar ta da Kware da gaske ai ina tare da addu'ar iyaye ai kuwa Ubangiji bazai taɓar da ke fa ji sukai an ɗaga labulan dakin zaro ido sukai gaban su ya yanke ya waɗi ɓare baki takwalas yayi yana cewa Kai lafiya ka zo ka tsaya mana a ka da zabgegiyar huƙa yimin shiru ko yanzu naci kuttumar..ubanka ba wajen ka na zo ba ya faɗa yana kallon asabe tashi yar kwalas yayi yana girgiza kugu yace '' ke idan kana ta ƙama da kai dan dabane ni naje inda baka je ba naje inda aka fika dabanci da iskanci Dan haka maza wuce ka bani guri dan iskan ƙarya ai be ƙarasa ba yaji saukar duba a bakin sa ihu ya saka yana cewa na shiga uku momcy ku duba min ya cire min hanci ko momcy da cikin ta ya ɗuri uwa bama tasan me yake cewa ba kai a sabe da sauri ta ɗago jikin ta yana rawa yaci gaba da cewa daman na faɗa miki inhar kere na yawo zabo ma yana yawo rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya tak ta me kaya kin saka an kai ni gidan yari to yau zan aika ki lahira dan uwar....ki ke shegiyar ƙarya ce kuma wallahi sai nayi maganin wa'yannan ya'yan naki ba sune yan zuga ki ba to duk yanzu zan yanke musu hukunci kai kuma dan daud ko to yau zan dawo da kai kalar ka ta ainiyi a zaton ki zan dawwama a gidan yari ko to yau zan ci ubanki ala'ada waje zan nuna miki jiya ba yau bace...... UWAR GAFALALLU EPISODE 10-11 UWAR GAFALALLU EPISODE 10-11 Gumi ne ya shiga wanke momcy tasan bata kyauta ba takurewa guri ɗaya su sumy sukai jikin su har rawa yake takwalas kuwa sai zare ido yake be taɓa ganin tashin hankali irin na yau ba wannan wacce irin rana ce Wannan shi ake kira da ya taka sahun ɓarawo yace '' talge dan girman Allah kai min rai wallahi Allah ban shirya mutuwa ba..., wata dariya ya saki irin ta arnan nan kamar anyi ruwa an ɗauke sai kuma ya murtuƙe fuska yace '' wallahi sai na ci uban ku.., jin hayaniya baba lami da baba suka fito turus sukai baba lami ta dafe kirjinta tace '' innalillahi wa'inna'laihir raji'un idirisa kaga a kwashe kwashen asabe abin da ta kwaso mana insha Allahu sai dai abin ki ya ƙare miki a kai..., kai lafiya ka shigo mana gida wani kallo talge yayi mai sannan yace '' ba gurin ka nazo ba dan hakai ba idan kai wasa wallahi kai ma yanzu nan zan sala sala da naman ka.., kama haɓa baba lami yar gumama tayi tace '' idirisa yi baya ita da tajawa kanta ya yanka ta ya soya ka na ganin huƙar nan sai kyalli take to wallahi maza zo mu bar gurin nan..., Mufeeda ce taji abin yayi yawa ta fito tace '' baba me ke faruwa..., zaro ido tayi ganin talge yana juya huƙarsa ja da baya tayi baba lami tace '' mufeeda kinga abin da uwar ki asabe reza ta jawo mana ko ai gata nan cikin ta ya ɗuri ruwa duk wannan masifar nan tata da daga murya kinji ta tayi muƙus a daki yawa anyi ruwa an ɗauke ko su futsararrun ya'yan nata kin ji su shiru..., ke rufe min baki ko yanzu nayi miki ba dad'i wallahi rufe bakin ta tayi tana zare ido ta ƙara ja baya a hankali har ta rufo kofar ta jikake garam ganin baba lami ta gudu mufeeda ma ta shige daki sai baba da yake kallon kudirar Allah yace '' bawan Allah zo ka faɗa min me tayi maka.., cake huƙa yayi ya bushi sigari ya fesar yace '' wannan shegiyar matar nan da kake gani annamimiya ce ni ta saka a ka kai gidan dan kande dan tana da daurin gindi ta saka a ka daure ni wiwi na ta sara ta hanani kudi na shi ne nazo ta bani ta hanani tare da fadamin mugayen kalamai yau sai naci uwar ta wallahi.., ƙasa yayi da kansa zuciyar sa ba dadi be san yaushe a sabe za tayi hankali ba yace '' kai hakuri yanzu ta dauki kuɗin ka ta baka shikkenan magana ta ƙare.., kai saita baƙin ka ni kake faɗawa haka aini ban san hakuri ba ko baki ji sunan nawa ba talge sai da wuta ya faɗa yana cije baki bawan Allah ina haɗa ka da girman Allah da manzon sa kai hakuri ta fito maka da kuɗin ka jikinsa ne yayi sanyi yace '' billahilla'zi da ace ba ka hadani da Allah ba bazan bar gurin nan ba sai na aikata abin da nayi niya yasin in badan rashin mutunci ya za ayi ta dauki kayana nayi magana ta saka a kulle ni.., kai hakuri bata kyauta ba Allah ya wuci zuciyar ka cikin sauri take fito da kuɗi bama ta san nawa ta miƙo mai ba amsa yayi yana zurawa a aljihu dubu goma yake bin ta da alama ma wannan kuɗin ya fi ƙarfin dubu goma ɗaukan huƙar yayi ya fita da sauri ta fito tana zabga gumi yawa an tsumata a cikin ruwa gyara daurin daukwalinta tayi tana haɗe rai kar ma ya ga fuskar yi mata magana girgiza kai yayi yana mata addu'ar shiriya ya koma daki baba lami yar gumama tana jin alamun kurar ta lafa Cikin sauri ta fito tana cewa amma bansan iskancin ki a sabe ya kai haka ba sai yau wallahi kiri kiri ina so na tafi kasuwa da wuri amma halin ki be bari na tafi ba wallahi tur da wannan dabi'ar take fyece majina tayi ta ci gaba da cewa kwata kwata ke ba san wacce irin mace bace gaki nan ba ƙirar fasali yawa bukka takwalas ne ya fito yace '' yau dai momcy kin birkita yar tsohowa.., Uwar ka ce tsohuwa bani ba billahilla'zi ku kiyayeni kar nayi muku ba dad'i in banda raini har ni zaka kalla kacewa tsohuwa shege da fuskarka yawa anyi daura yar zunubi sai a lokacin ma asabe ta ƙarewa baba kallo har jagira tayi bakin nan sai maiƙo yake idon ta yawa wata aljana dariyace ta kubbuce mata ai kuwa ta dinga yi tab ku na cikin daki ku fito yan iskan karya asabe dai ta kamu da cutar mental sai dai hakuri... da daddai da daddai suka fito ganin mahaifiyar su na dariya tuƙuru sai suka ɗauka ko duk a cikin rudewa ce ɗagowa tayi ta ƙara kallon baba kamu ashe har bra ta saka tayi sama maman nata yayi ƙasa ya zube yawa slipper yauwa idirisa fito fitowa yayi yace '' baba gani..., kaga daman wata Magana ce me mahimmanci zanyi dan ma dai daya dan uwan naka ba ya nan to baba muna jin ki wata uwar harara ta zabgawa asabe tace '' wallahi ki fita a idona na rufe asabe yan zun nan sai nayi miki ba dadi kin gama haukan kin tashi kome kuma kuma har yanzu da sauran ki.., shiru tayi ta nemi guri ta zauna baba ta ci gaba da cewa to bayan mutuwar uban ku ban ƙara tunanin aure ba sai yanzu cikin yardar Allah zan yi aure mijin nawa a gidan nan zai tare da sauri ya ɗago ji maganar shazali sai saɓa babbar riga yake wane a gurin idirisa kyalli kai kuma awa haba baba me isaka duk harkar da zaku zubar mana da mutunci ita kuke yin ta to yasin ba za ayi auren nan ba ya faɗa yana gyaɗa bulala tashi sumy tayi saboda kan nasa ba dadi tsab zai iya dukan su shi daman haka a ka haife shi yana da cutar taɓin ƙwaƙwalwa naja ma.ganin kamar yau abin ya tashi sai ta matsa daga kusa da shi Baba lami tace '' idirisa yau babu wani labari ne naga gidan kamas..., yan zunnan zan fita na nemo insha Allahu komai ya tsaya wallahi taɓe baki tayi ta kalli mufeeda tace " Daukan min kaya na ki kai min shagon ladidi..., gyara zaman hijabinta tayi ta shiga dakinta ta fito da kaya ta daure su a cikin zani mufeeda tace '' baba ga su...?, ke wacce iri ƙwaƙwalwa kike da ita ce miki nayi ki kai min shagon ladidi ƙawata ko gyaɗa kai tayi ta ɗauki kayan ta ɗora aka yace '' na tafi baba.., to Allah ya kiyaye hanya amin ya Allah ta faɗa tana fita daga gidan cikin nutsuwa take tafiya har ta isa kasuwar rimi wajen yan gumama shagon ladidi ta shiga baƙin ta dauke da sallama fitowa tsuhuwar matar tayi tace '' sannun ki ina lami take naga yau kamar ke kaɗai kika zo..?, tana gida wallahi itama nan da anjima zata tawo na fara yi mata gaba da kayanta ne to zo ki shigo cire takalminta tayi ta shiga ta ajiye kayan tace '' na tafi.., ba zaki tsaya ki huta ba dan murmushi mufeeda tayi tace '' a'a sauri nake yi..., to ungo ta miƙo mata kuɗi kin amsa tayi tace ta gode ta bar gurin ta wajen yan shinkafa ta biyo dai-dai shigar wata mata mota ta yarda jakarta bata lura ba da sauri tabi ta ɗauka bin motar ta shiga yi amma ina tafiya take dakyar ta samu ta tsaya fitowa Hajiya tayi tana kallon ta wata kila irin mabaratan nan ne tace '' lafiya..?, miƙo mata jakarta tayi da sauri ta amsa wato a cikin kaya ta waɗi da tazaro kuɗi ta bawa me saidai agushi jikin tane yayi sanyi da niya tayi ta wan wanka mata mari sannan tayi mata nasiha idan taji zata dauka ta dauka karɓa tayi tana cewa '' Nagode sosai Allah yayi miki albarka..., bakomai wallahi ta juya zata fara tafiya Hajiya ce tace '' ya'ta tsaya mana .., juyowa tayi Hajiya tace '' shigo na rage miki hanya wallahi naji dadin abin da kikai Min a wannan zamani da amana tayi ƙaranci musamman ma yadda mutane basa kauda idon su akan kuɗi amma ke ki tsunta ki dinga bina nagode sosai.., a'a ba komai nagode gidan mu bashi da nisa nan yan bita kai ta jinjina tace '' ya'ta ki yarda dani bazan taɓa cutar da ke ba shigo na kai ki..., shigowa tayi zuciyar ta nayin dar dar ta rufo motar key tayi mata ta fara tafiya sai da suka zo har yan bita sannan ta kalleta tace '' ina ne gidan naku..?, nu na mata wani durkusasshen gida tayi da yan caca suna zaune suna buga ta da sauri ta juyo ta kalle tace '' nan ne..?, eh nan ne dan gaba tayi dai-dai fitowar lami tsayawa tayi dafe kirji tayi tare da zaro ido ganin mufeeda ta fito a motar nan suma wa'yanda ke zaune suna ca'ca suka dakata dayi ganin irin motar da tafito a cikin ta gyautai yace '' wallahi tabi layi itama wannan mota haka..., can kuwa zaro kuɗi tayi a cikin jakar bata san iya adadin su ba ta miƙa mata kin amsa tayi nan yarinyar ta ƙara shiga ranta tace '' to tunda kin ki amsa me kike so nayi miki..?, wallahi ba komai a'a faɗa insha Allahu zan cika miki burin ki dan jim tayi daga haduwa da mata sai tace me za tayi mata haka kurum bata san wace ita ba yanzu da masu lalata yara sun yi yawa a gari tace '' bakomai Nagode.., kati ta ciro tace '' ga shinan idan kikai tunani kya ne me ni.., amsa tayi sai da ta tabbatar ta tafi ta shiga gida tare da yaga katin gutsi gutsi ke dan uban ki nawa ta baki ...?, bata lura da momcy ba sai yanzu da taji tayi mata magana ganin irin kallon da su gyautai suke mata saboda fusgota da tayi ta dawo da ita waje a hankali tace '' momcy mu shiga ko sai na yi miki bayani..., kuma fa haka ne saboda naga munafukai duk an bazo kunnuwa da idanuwa aji information to saidai ku tara a gaba matsiyata a haka dai zaku ƙare a tsuguna ayi da waccan ayi da wannan wallahi haka zaku gaji ku barni asabe da wa kike jagwa ya taso yana ajiye katin karta ɗin sa harara ta galla mai tace '' da wanda ya tsargu...?, lallai matar nan baki da mutunci wallahi wallahi Allah kar ka kuskura ka ƙara ce min bani da mutunci idan kuwa kaki zanyi maganin ka wallahi ni nake da yan daba yan zunan jikin ka yayi tsami su sassaɓa maka halitta wallahi wani ba bazai iya gane ka ba aini naki burgeni ba da kanki zaki tsaya kiyi dan kin saka wasu sun miki me kenan akai lama ce ta nuna na isa ta faɗa tana wuce wa cikin gida ganin mufeeda ta shiga sakar buɗa tayi tana cewa yau Allah ya wanke min takaici na jalila ce tace " momcy me ya faru..., zama tayi tace '' ke kunga bugaggiyar motar da aka kawo mufeeda a cikin ta kai Jama'a.., dan Allah fa momcy kin ganta normal fa zan muku karta ne nifa matar nan temakon ta nayi jakar ta ce ta waɗi shine na dauko mata taji dad'i ta kawo ni gida har ta ban kuɗi nace bazan karɓa ba dan Allah nayi shi ne taban kati duk abin da nake so na kirawo ta kin ganshi nan na yaga shi dakyar asabe take hadiyar yawu domin wani irin bushewa bakin ta yayi mata zuciyar ta na wani irin bugu yawa zata tsaga kirjinta ta fito tace '' shikkenan yarinyar nan ta cuce mu yau ba abin da muka ɗora sai dai kowa yaci kuɗin sa amma da yake ita halinta sai ita shi ne tayi mana haka kuka ta rushe da shi har da fyetar majina gani take kakarta ta yanke saƙa amma yarinyar nan tayi mata baƙin ciki ...... yan aljanna ku hanzarta payment free page ya kusan ya ƙare tafiya yanzu a ka fara baku ga komai ba domin fara payment din Ku zaku biya ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay 500 ku turo da sheda ta wannan number 09061890481 UWAR GAFALALLU EPISODE 12-13 PERFECTLY PEN'S Baba ne ya fito daga daki yana cewa wallahi kin min daidai a ko da yaushe ina godewa Allah da ya azurta ni da samun ya' kamar ki baki biyo halin yan uwan ki ba wallahi kubi duniya a sannu ina jiye muka halin ranar na dama kunto taba tayi a baƙin zanin ta ta fara sha tana busa hayaƙi yana fito mata ta baki ta hanci dariya naja tayi tace '' yau momcy duniyar gajimare take so ta luluƙa.., yar kwalas da tun dazu yana zaune ya zuba ta gumi yace '' ba dole ba kiri kiri ta haife ta amma ta dinga yi mata bakin ciki.., yar kwalas ba iya momcy tayiwa baƙin ciki ba har damu wallahi ka duba fa ka gani yau sai dai kowa yaci kuɗin sa ni yanzu ma zan tashi na tafi gidan Hadiza Dubai ko na samu abin da zanci cewar sumy da dai yafi ye miki amma zama kuɗa ya dinga bin bakin ka babban hatsari ne wallahi nima yanzu zan tashi na tafi nema shifa arziki ba kana zaune yake zuwa ya same ka ba sai ka tashi ka nema wallahi kuwa momcy ta faɗa tana fesar da hayaƙi kai kace ledoji ake wurawa suna fitar da bakin hayaƙin nan idan abin nata ya motsa sai ta sha kara goma wata ran fin haka ma sha take tashi yar kwalas yayi yana cewa momcy dan Allah mayafin nan naki zaki ara min yau zan ci uwar sabada birthday din yar amana za ayi yau ɗin nan kuma kinsan manyan ƙawaye wani irin lu take yi da ido tamkar daga sama yaji saukar bulala a gadon bayan sa kutmesin bura'uban nan wanne shegen ne ya dake ni wallahi bazan yarda ba ya faɗa yana juyowa ganin shazali sai huci yake yawa wani kumurcin muciji taka wa yayi a guje amma taku ɗaya yayi mai ya danko shi ihu yar kwalas ya saka ashe abin asabe reza iskanci ne duk da halin da take ciki tafi kowa gudu har ta shiga bayi dan ubanka ni kakewa tsaki..?, ehyi yaushe nayi maka tsaki zabga mai mari yayi yace '' dan ubanka ni sa'an wasan kane ina magana ba zaka ce to ba.., hawaye ne ya shiga sintiri a fuskar yar kwalas domin yau dai be zo gidan nan a Sa'a daga wannan sai wannan nan fa kowa ya fara tsera yana neman tsira da lafiyar sa yau abin nasa ya motsa haka wata ran har mutanan waje yake rarakawa kai baza kai dariya ba kake kuka ko sai na ɗaga ka sama na buga da ƙasa dariya ya shiga yi ba kakkautawa sakin sa yayi ya fita a guje bularsa ya ci gaba da zab zab gawa duk da bakowa a tsakar gidan fita waje yayi ganin malin malin malin dinsa tana neman ta waɗar da shi ya cire ta su gyautai da suka saka kan su a gabas suna ca'ca kamar saukar aradu da sauri kowa ya shiga danne dan uwansa yana suna neman gurin tsira dariya ya fara ya koma cikin gidan yana cewa zaku fito ko saina balla wa yannan ma tattun kofofin na shigo wallahi jikin mutum sai ya faɗa me tun dazo kuke zagina kuna yi min wani irin kallo ke kuma asabe yau sai na miki rudu rudu da jiki kin dinga tara mana karuwai da yan daudu a gida jikin tane ya fara rawa cikin ta ya murɗa rasai tasan halin shazali tun da ta ce zai yi to wallahu sai yayi ba zato taji mutsari ya shirin kwace mata ƙara buga kofar yayi yana cewa dan uban ki zo ki buɗe min kika bari na shigo wallahi sai na rotsa miki kai yar iska kawai kin zo kin tara mana karuwai a gidan ubana yau dole a raba gado abani nawa kason zare ido ta shiga yi ga gudawa da ta barke mata ba zato ba tsammani a zuciyar ta kuwa sai tsinewa shazali take buga kofar ya shiga yi yana dannowa tana dannowa bugu ɗaya yayi mata sakatar ta zare baba lami ce ta shigo tana cewa tsarman dudu tsarman duduwa tsayawa tayi tace '' kai shazali lafiyar ka kowa naga kana ƙoƙarin cire mana kofar bayi ana zaune kallo a fusa ce a ya juyo yana muzurai nan da nan ta kama kanta tace '' aa ci gaba da abin da kake dan albarka wannan abu yana da kyau bara na fita na siyo abu na yanzun nan zan dawo.., zoo ki nemi guri ki zauna tun da safiyar Allah kike yawo a gari yawa wata yar bijilanti to ba matsala sai na zauna a daki ko banza yayi mata ya ci gaba da tura kofar bayi yana cewa wallahi kika bari na shigo yau sai jikin ki ya faɗa miki ganin ya ba wa kofar bayi mahimmanci ta salallaɓa ta bar gidan jikin ta na rawa kamar mazari... TUDUN YOLA A gajeye ta tayi parking daidai fitowar ASH da file a hannunsa yace '' Hajiya ba dai fita kikai ba ba driver..., fitowa ta ƙara sa yi tace '' wallahi kuwa yau training nayi na shiga kasuwa na danyi siyayya wallahi naji dadin jikina.., haba hajiya me isaka kikai haka bayan kinsan ciwon ki nan da anjima zaki zo kina cewa bayan ki kafar ki na ciwo kar ka damu insha Allahu hakan ma baza ta faru ba wallahi yau na haɗu da wata yarinya yar albarka ba ruwanta jakata ta waɗi ta dauko min ta bani ita bata dubi yawan kuɗin da suke cikin ta ba lokaci ɗaya naji ina son yarinyar kai ya gyaɗa yace '' Allah ya kiyaye gaba ya buɗe motar sa ya shiga domin be ga abin da ya hada shi da zancan yarinyar ba kai Hajiya ta girgiza tace '' Allah ya shirye ka ASH duk maganar da ya shafi mace baka so..., buɗe motar ta tayi ta dauko kayan da tayi siyayya ta shiga main Parlour Hajiya yanzu nake shirin kiran ki sannu da zuwa ajiye kayan hannun ta tayi tace '' yauwa jidda ya kike..?, Alhamdulalilah komai lafiya zama Hajiya tayi tace '' ina su ikram.., suna makaranta nan da anjima za su tawo nan na shiga wajen inteesar na tarar tana bacci ajiyar zuciya ta sauke tace '' maganin da ake bata ke sakata bacci har uku za ta kai tana bacci..., Allah dai ya bata lafiya amin ya Allah baba lantana da sauri ta fito daga kitchen tace '' Hajiya sannu da zuwa.., yauwa sannun ki ya aiki Alhmdllh ta faɗa tana tsugunawa a ƙasa cikin sauri Hajiya tace '' baba dawo nan ki zauna dan Allah ki dinga sakin jikin ki ai an zama ɗaya ni wallahi bana son wannan fadancin ki dena yi min shi.., zama ta gyara tana cewa nan ma ya isa baba lantana Dan Allah Dan kawo min ruwa wallahi kinga duk da ba wata rana bace tayi na fita amma maƙoshina duk a bushe tashi tayi tana cewa sannu Allah ya baki lafiya amin ya Allah ta faɗa tana mai da kallon ta kan tv tace '' wallahi wallahi wata na gani nayi wa ash sha'awar ta.., da sauri aunty jidda ta kalle ta tace '' Hajiya ba ga ni'imatullah ba yarinyat na da kirki wallahi ni wallahi nayi mai sha'awar auren ta ga yadda take nunawa inteesar soyayya..., jidda duk na karya ne wallahi kalli sam yarinyar ba tayi min ba idanuwanta a buɗe yake gwara na sama mai karamar yarinya wacce zata so shi ɗan Allah bata san waye shi ba ta zauna da shi tsakani da Allah amma kinga masu cewa suna son sa wallahi akwai abin da suka gani jidda Gaskiya bana tunanin haka tun da kince haka ga sakina nan itama yar manyan mutane ce idan ya aure ta zai ji daɗin zama da ita jidda abin da nake hangowa sam bashi kike hangowa ba shi ya saka zakiya ta fiki sanin ya kamata ɗaukan wayar ta tayi tana cewa hajiya kenan yanzu gaskiya fa nake faɗa badai wacce zata kula da inteesar ake nema ba a'a ba ita ake nema ba zai yi aure ne domin ra'aya sunan manzon Allah idan Allah ya temake mu ta kula da inteesar tamkar ita ta haife ta amma ni ba dan ita zai yi aure ba Allah ya kyauta Amin ya Allah ruwa baba lantana ta kawo mata amsa tayi ta fara sha sannan ta ajiye tace '' Nagode.., juyawa baba lantana tayi saukowa tayi tace '' baba lantana ga kayan nan kai su kitchen.., ɗauka tayi ta kai su kitchen sannan ta ci gaba da aikin da take Hajiya tace '' wallahi dabi'un yarinyar ya burgeni jaka ta na yar a kan hanya ban sani ba amma yarinyar nan yar mutunci ta ɗauka ta dinga bina har sai da ta kawo min ita naji dadi sosai wallahi..., yanzu Hajiya domin tayi miki wannan aikin shine ta sace zuciyar ki..? abu nawa su ni'imatullah suke miki..?, jidda kenan ke yarinya ce ba zaki taɓa gane ina na dosa ba wasu mutanen suna tare da kai dan wata ni'ima da Allah yayi maka randa ba ni'imar nan kai da banza duk daya dan haka ki kula ki gane ni kwata kwata bata yi min ba yarinyar budaddan ido gare ta kar wata ran muyi dana sanin hada zuri'a da ita ita wannan yar wacce gida ce kafin kiyi wani abu kiyi bincike insha Allahu zan yi sosai sannan sai muje gurin maga batan ta ayi magana Allah isaka yar mutanen kirkice ba kara da kiyashi bace idan har ta gari ce ba ruwana da halin iyayenta rayayye yana fitowa a cikin matacce haka matacce yana fitowa a jikin rayayye be kamata muna yiwa mutane kuɗin goro da wanda ya dace a faɗawa da wanda be dace a faɗawa anya kuwa yarinyar nan ba asiri tayi miki ba ita ni'ima kin ga tayi wani abu da be dace ba dariya hajiya tayi tace '' jidda kenan yau na taɓa ganin ta ita kanta bata san wace ce ni ba..., Allah ya saka haka amma yanzu dan adam abin tsoro ne wallahi irin wannan yabo haka yau ki hadu da ita ki dinga yaban ta Hmmm Allah ya kyauta Amin ya Allah ta faɗa tana tashi daga zaman da tayi tace '' zan leƙa gidan su zainab naga kwana biyu bana ganin ta ko a charting ba magana muke ba..., sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya amin ya Allah ta faɗa tana fita dauko waya tayi tana karanta Alkur'ani mai girma ko zata samu sauki a zuciyar duk lokacin da ta tuno da yar uwarta ta kanshi ga wani hali tana fatan Allah ya kai rahama kabarinta Wannan kenan kora ce ta lafa kowa ya fito daga inda ya ɓoya yar kwalas yace '' wallahi Allah yau naga tashin hankali duk wacce take so tayi magana dani idan ba zata zo gidan mu ba kirani a waya a she haka gidan ku ya koma sansanin huƙuba tun da nazo ake ruɗamin jiki...da duka.., yar kwalas wallahi Allah ban ga laifin ki ba mu ma da da inda zamu da tuni mun tafi wallahi haba wannan wahalar haka kaga hakarkarina yarda yake min ciwo yadda kuka san daddatsa min shi akai cewar asabe ta faɗa cikin tashin hankalin halin da take ciki Mufeeda tace '' momcy ko zaki gurin me gyaran targaɗe...?, kai rufan asiri su daɗa karya ni saya aike ni ta fada tana ƙoƙarin zama shigowa yayi yana saɓa babbar rigar sa kafa me naci ban baki ba asabe cewa take dan girman Allah kuyi min rai ku kai ni daki wallahi bani da kafar guduwa ganin yana ƙoƙarin cin mata ta kama katanga ta shiga gidan hajara gwuicho kut melesi yan sace sace da yaran ki ke min shine ba i she ki ba kika tawo da kan ki , ki daukar min kayana to Allah ya kama ki asabe yau sai naci bura'uban ki wallahi daman nace miki zamu haɗu cikin tashin hankali take kallon hajara gwuicho kiɓane da ita sosai duwawunta yayi kujera two seater ga uban tunbu kallon hannun ta tayi yawa shebur ja da baya tayi tace '' tsaki ji hajara gwuicho kinga wallahi Allah shazali ne ya kore ni tun safe muke abu ɗaya kwata kwata yau bamu da kwanciyar hankali abin yaci tura yau kusan sauke min kafaɗa..., kinga yimin shiru ɓarauniya ke kanki kin sani wallahi nafi ƙarfin ki dan habaicin da kike min ina jiyoki dan haka yau dole na turbuɗa kanki cikin ruwan dafaduka kallon katuwar tukunyar dake kan wuta ruwa sai tafasa yake da yake haraja gwuicho saida abinci take..... sauran fa page biyar na gama free page wannan tafiyar yanzu muka fara ta ko book one bamu gama ba Domin payment zaku turo ta wannan account din ₦500 Opay Amina alhasan Muhammad ku turo da she da ta nan UWAR GAFALALLU daga 25 free page ya tsaya ku hanzarta payment din ko domin jin yadda zata kaya EPISODE 14-15 Dan Allah hajara gwuicho kiyi hakuri karma ta sake ta haƙura daman ke nake nema wallahi yau sai na saita miki zama bake tara karuwai ba shazali ya faɗa yana ƙoƙarin cire malin malin dinsa kallon kallo aka shiga tsakanin asabe da hajara gwuicho hadeyar yawu me kauri hajara gwuicho tayi tace '' Kaga shazali zo ka ɗauke ta ku tafi.. wallahi ba zaku zo gurin sana'ta ba ku daga min hankali.., ke da gurin sana'ar taki kunci kundun uban ku shegiya me kama da tifar yashi yan zunan sai na dilmiya kanki cikin wutar nan wani...ja da baya tayi gashi babu kowa a cikin gidan balle ta samu a ɗauke shi tace '' wallahi asabe kin cuce ni wannan tashin hankali dame yayi kama kiri kiri ina ji ina gani ki hanani kwanciyar hankali a cikin gidana ban da zagin da kike aika min ta katan ga ta faɗa tana goge hawayenta da suke zo bo mata a kurmin idanuwan ta da hallacan rufe min baki nima haka naso ba gurin tsira nake nema ba ta fada tana ƙoƙarin zare hannun ta daga riƙon da jahara gwuicho tayi mata amma ina hakan ya fassaka hajara tace " Wallahi ba inda zaki ki kawo min masifa gidana sannan ki gudu gawara ya jibge mu tare wallahi kamar yadda bazan iya guduwa ba kema dole ki tsaya..ba inda zaki.., gumi ne ya ƙara karyo mata tace '' dan sabbatin Ubangiji ki cika ni..., wallahi Allah ba inda zaki kafin ta ƙarasa shazali ya kara so da gudu suka shiga da cikin daki hajara gwuicho ta zauna akan kafar asabe wani wahalallan ihu ta saki da sauri Hajara ta rufe mata baki tace '' baki da hankali zaki kuka sai kin saka ya shigo mana wallahi zan cillaki waje duk abin da ya ga dama yayi miki..., bata da bakin magana haka tayi shiru tana zare ido hawaye nabin kuncinta wani irin zogi kafar ta ke mata ta tabbata ta karye wannan shegen duwawu na hajara yawa siddin shegu Shazali kuwa sai wuru wuru yake ko zai ga inda suka shiga idonsa faɗawa yayi kan kazar hajara ɗaukan ta yayi, yayi wulli da ita tare da murɗe mata kai yana cewa shegiya tun dazu take ta ihu ai yanzu kyeje can kiyi musu kuka ganin be gan su ba ya fita yana ta masifa da sauri hajara ta fito tana cewa Wallahi bazan yarda ba dole asabe ki ɗauki wannan kaza ki biyani kuɗin ta Asabe da ciwo yaci karfin ta tace '' haba Hajara ina ne ina cin mataccan abu ni da ba arniya ba ki dai bawa ƙaren Haruna yaci..., ke bana son iya shege wallahi dole ki ɗauki wannan kaza duk abin da zaki da ita kiyi da ita amma wallahi dole ki siya ban da ma zuciyar musulunci ba sai na karya miki kashin kafaɗa ba har ni zaki dinga bi da sharri to wallahi tun muna shedar juna ni dake kiyi gaggawar biyana kudin wannan kazar dubu bakwai na siye taci abincin dubu biyu dubu goma sha ɗaya kenan nida bani nayi abin nan ba dan Allah kiyi hakuri ta faɗa tana ƙoƙarin tashi da kyar take jan kafar ta fusgota hajara tayi ta ɗauki kazar da shazali ya murɗe wa wuya tace '' maza biyani sannan kibar gidan nan ...., zama tayi domin abin yayi mata dai-dai tace '' wallahi daman ba son fita nake ba.., au haka kika ce to wallahi yau na lahira sai yafi ki jin dadi asabe kan bala me yashi tab jajar ubancan ke kar kiga ina yi miki lumbu lumbu yan zunan zan choge kafata naci uban ki kowa ya sani fankan fankan bata kilishi kai lallai matar nan kin raina min wayo yau zanyi maganin futsarar ki wallahi mudai yi maganin juna nan fa fada ya kaure a tsakanin su haruna ne ya shigo yana tsalle hadi da rausaya yana cewa ku tasu babba ku tasu ku taso ba me raba ku haka ya dinga mai maita wa ganin faɗan ya ƙara kamari ya canza salon waƙa wanda yafi wani ƙarfi ya cuci Dan uwansa wallahi ba wanda zan kira ya raba ku taya dan akuya zai yi fada da giwa yace zai ci riba baƙaramin wuya suka bawa juna ba ba zato ba tsammani Hajara taji asabe ta gartsa mata cizo abin ka da ta samu tsoka ba ƙaramin shigarta cizon yayi ba ta kwalla kara ta sakita ba shiru tana sakin ta ta fara cewa '' Hajara daman na fada muku faɗa dani babu riba wallahi amma kika toshe kunnuwanki ai gashi nan yanzu kinga uwar bari kin sakeni kaza kuma wallahi ko kobo bazan biya ba kije kine mi wanda ya kashe miki abar ki ya biya ki kiga idan be sace ki ba kin koma samfurin mucija da zani..., Haruna kamo min ita wallahi ba zan yadda ba kaga fa a kirjina ta cije ni shegiya yar iska wallahi sai nayi maganin ki kin dade baki ba Hajara, nace kin dade baki ba kana sakewa ka karaso nan wallahi sai na ɗauki iccen nan na saka maka a fuska shege da fuskar ka yawa kayi sujja a buhun gawayi... kut ashe daman ina kallon ki kamar mutuniyar kirki ke ba ta kirki bace hmmm zan karaso ni kuma tafasasshen ruwan nan zan diba nayi miki wanka da shi.. fakar idanuwansa tayi, tayi wuf ta fita maza maza haruna ka bita kar ka barta ko bayan layin nan tayi bin ta yayi kafin ya cimmata har ta shiga gida dafa gwuiwowinta tayi tana haki tace '' kuna ina dan Allah ku kawo min ruwa wannan bala'i har ina daga wannan sai wannan..., a hankali baba da ba ta dade da dawowa ba ta dan leƙo da kanta dariya ce ta kubbuce mata ganin yadda asabe ta koma yawa wata rubabbiyar gwanda fuskar nan taci bleaching duk tayi ja sai zare ido take.. bayan ki asabe ga shazali nan zan sara miki gadon baya da gudu ta shiga dakin ta dariya lami ta fara yi harda fati tace '' gaskiya kin bani kunya asabe ina daban cin ki yake da sai ki tsaya ku dambatu ku buga yar kashi ke da shi..., takaici ne ya kama ta tace '' yanzu baba dariya kike dan bake yakewa abin da yake min ba haba baba gaskiya haka be kamata ba.., tura dauri gaban goshi tayi tana cewa dole fa shazali ya raina ki duk abinda da yake faɗa gaskiya ne bakya tara karuwai ko dazu ba dan daudu bane ya bar gidan nan? shiru tayi duk ranta ba dadi ta gyara zama tana miƙe kafarta tace '' mufeeda mufeeda.., ta tafi makaranta makaranta kuma ban hanata bin duk hanyar da shegen yaron nan yabi ba kai wannan jaraba har ina anya kuwa ba asiri yayi mata ba tabi ta nane mai ala dole sai shi yasa ubanta ko da yake mahaifinta ke daure mata kinsan ranar nan da naje mahaifiyar cewa tayi ai itama ba ba son wannan alaƙa take ba ke kinga irin mutuncin da taci min kai gaskiya matar nan kwata kwata bata da mutunci wallahi inda yaje bata je shi ba Shiru baba tayi mata tamkar da dutsai take magana Wannan kenan ASH gaskiya Hajiya ke faɗa maka ta kamata ka dawo kamar da ka gina sabuwar rayuwa mahaifina ya mutu na dena farin ciki ne jingina yayi da kujera ya lumshe idanuwansa yace '' har abada farin ciki na ya tafi Yasir.., tab abin naka azeemun ne anya kuwa fatalwar nusaiba ba ita takama ruhinka ba dariya yayi yace '' kome zaka faɗa saidai ka faɗa wallahi ko da yake ba kai kaɗai ba hatta Hajiya kallon da take min kenan.., wallahi dole tayi maka nifa ban taba cin karo da labari irin naka na kabi Ka kwallafa mace ɗaya a ranka file ya ɗago fara dubawa yace '' mubar maganar haka zanyi aiki..., korata kake yi ko to bara na tafi gurin madam ta ɗebe min kewa cewar Yasir da yake danne dariyar da ta taso mai ganin yadda fuskar ASH ta canza ajiye file din yayi yace '' ni ba korarka nake ba kawai dai nace maka zanyi aiki.., okay ai kai daman duk maganar da za a taɓa marigayya ba sonta kake ba idan ka ƙara aure bawai yana nufin ka manta da rayuwar ta bane dafe kansa ASH yayi yace '' ya Allah nifa bana son wannan zancen amma na lura ku kamar dadinsa kuke ji..., sosai ma kuwa wallahi domin bamu da buri da ya wuce mu ganka yau kayi aure har da ya'ya buɗe baki yayi zai magana sai aka turo kofar da sauri dukkan su suka kalli kofar wani irin riga da wando ne a jikinta yawa fata ta saka kimono amma ita da babu duk ɗaya cikin iyayi tayi sallama kau da kai yayi sannan ya amsa sallamar tata zama tayi ba tare da yaba ta izinin zama ba tace '' ya ASH barka da yamma daga school nake nace Bara na kawo maka ziyara ko dan ba aunty nusaiba be kamata mu yar da juna ba..., hankalinsa ya maida kan laptop dinsa yace '' yauwa..., a takaice sam baya kaunar zuwan da ni'imatullah take mai a ce ko da yaushe tana hanyar office dinsa yana raga mata ne dan ita kanwar nusaiba ce step sister dinta ce mahaifinsu ɗaya buɗe jakarta tayi ta fiddo da turare tace '' ga gift nan ka bawa intee.., mun gode ki ajiye shi a nan ya faɗa yana ci gaba da kallon laptop dinsa cije lips din ta tayi ta ajiye turaren ranta duk a jagule kallon ta yasir yayi cikin takaici shifa wallahi bega dalilin da zai yarda yarsa me rawar kai ba ya kaita gaba da secondary batare da tayi aure ba.., duk da abin da ni'ima take yi da halin mahaifiyar ta sam bata so ayi mata faɗa sai abin fa yarta ta ga damar yi gida ne na kishiyoyi kowa na son ya'yan ta ba kwaɓa balle harara ko wacce so take ace dan ta ne a gaba... Ya yasir barka da yamma barka dai ya faɗa yana ƙoƙarin tashi ba tare da ASH ya ɗagowa yace '' ko zaki bi shi ina aiki ne.., murmushin yaƙe tayi tace '' okay ba damuwa sai ma ka sauke ni a hanya.., a'a ba hanyar ki nayi ba da sauri ta kalle sa tace '' ko kana tsoron aunty zee ta gammu.., ai tasan ni daga ita ba ƙari domin ta tattara komai da ake so mace ta gari ta kasance kai ta jin jina ta mai da kallon ta kan ASH tace '' na tafi.., okay Allah ya kiyaye hanya Ba tare da ta amsa ba ta fita duk ranta a bace har gurɗewa take dafa bango tayi ta saita kanta ganin kamar mutane na kallon ta kullum cikin daɗin baki mom take Mata amma ba wani ci gaba yau ma ba irin wankan da ba tayi ba da magunguna ga kwallin da ta saka idonta har yaji yake mata amma ta daure ta cije gashi ba amfani... fita farfajiyar ma'aikatar tayi ta dauko wayar ta da take man a gaji tsaki ta ja ganin sunan jameel ta mai da wayar fita waje tayi ta tsaya a titi tana tarar a daidai ta duk wanda ta tara ko kallon ta ba yayi sai dai yayi gaba abin tamkar haɗin baki gajiya tayi ga uwar rana da take dukan kanta wata jeep ce ta tsaya fara kal da ita sauke glasses din motar tayi ɗauke kai ni'ima tayi kallo saurayin ya ke binta da shi yace '' hy...beb.., ɗagowa tayi ta kalle sa ranta a haɗe ta ƙara kau da fuska yace '' be kamata mace kamar ki tana tsayuwa a kan titi ba idan ba zaki dabu ba ki shigo na rage miki hanya ko ma na kai ki inda zaki.., malam a kwai damuwa zaka iya tafi Nagode haba beb karfa tun kafin ya ƙarasa ta ɗaga masa hannu tace '' dan Allah zaka iya tafiya nace maka bazan hau ba ana dole ne..?, domin payment zaku biya ta wannan account ɗin 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay 500 Mutanen nijar kuma za su biya katin moov na 300fcfah Sannan ku turo da shedar biya ta nan 09061890481 UWAR GAFALALLU OUMYASMEEN EPISODE 16-17 PERFECTLY PEN'S Ba'a dole amma ranar nan tana dukan ki ni daman temaka miki zanyi tunda kin ki shikkenan yana gama faɗin haka yaja motar sa yayi gaba mai da hankalin'ta tayi kan titi sarai ta gane sa me wankin mota ne a bayan makarantar su haka kurum ta daukarwa kanta kara da kiyashi cikin ikon Allah ta samu napep hawa tayi ta fara danna wayar ta kamar daga sama taji danshin huƙa a wuyanta me satar wayar yace '' dan ubanki kawo ta kona farke miki ciki..?, jikinta har rawa yake haka ta miƙa wayar nan sannan yace '' zo ki fita tun kafin na ci uwar ki..., fita tayi ba ƙaramin dana sani tayi ba da bata bi wannan me wankin motar ba tsorata tayi dan haka a kafa ta dinga daɓawa tana tafiya har ta isa gida a jikace ra isa tana shiga ta wullar da jakar ta ta rushe da kuka da sauri mom ta shi go tace '' ke rufe min baki kar maƙiyana suji suyi dariya me ya faru faɗa min..?, yan kwatar waya na haɗu da su suka sace min waya ni wallahi wannan duk be dameni ba mom inda nake wallahi ya ASH be kalla ba balle yasan nazo wai shi wanne irin mutum ne duk kudina da nake ɓatarwa ya tashi abanza kenan kuka ta ci gaba da shi tace '' ai wallahi duk daddy ne ya jawo mana lokacin da ta mutu da yace gani ai ba zai iya yi mai musu ba kuma komai zai zo da sauki amma yanzu ga shinan ya jiƙa mana aiki sai ɓatar da kudade muku ba wani labari..., ai wallahi daddy ki ban san wanne irin mutum bane sai fa dana kwarkwanta mai har gamshashshen bayani nayi mai yadda zai fahimta amma fur yaƙi share hawayenta tayi tace '' ai da ace su waheeda ne da tuni ya yarda kullum a gidan nan sai dai adin ga tauye mu..., bar su ni'ima akwai ranar ƙin dillanci wallahi dan wallahi malam gobe da nisa yace min na gab da mallakar komai na daddy dan haka yanzu na zage dan tsai kwantar da kanta tayi a jikin gado idanuwanta na zubda hawaye kallon ta mom tayi tana. shafa kanta tace '' kiyi hakuri insha Allahu komai ya ku san zuwa karshen dole ya aure ki ko yaƙi ko ya so ai jidda mutuniya ta ce dazu ta bar gidan nan na ƙara jadda da mata manufata..., da sauri ta ɗago tace '' me tace..?, ci gaba tayi da shafa mata kanta tace '' cewa tayi yanzu maganar da suka gama yi da Hajiya kenan amma bata ,bata amsa ba sai cewa tayi Allah ya zaɓa mai wacce tafi zama alkairi a gare shi..., da sauri ni'ima ta tashi tace '' bamu da wata matsala da ta wuce Hajiya wallahi tun farko da ta nuna mai gani yana jin maganar ta ai ba zai ƙi ba.., ke karki damu aure fa kamar anyi shi an gama ne wallahi kar ki sakawa kanki damuwa idan har ina doran ƙasa ko na sati uku ne sai ya aure ki rungumeta tayi tana murna dariya itama mom tayi tana shafa gadon bayanta ta ci gaba da cewa ai idan sun san wata basu san wata ba dole ya kaso kanshi gare ki har shi a wa zai dinga wulakanta min ke cikata tayi ta shiga dakin ta ta kwanta tana kallon ceiling har ta hangota a jikinsa kai ranar wanne irin farin ciki za tayi daga gani fa jarumini ƙara limshe ido tayi tana jinta a wata duniya ta dabam jin sallamar saudat ta miƙe zaune shigowa tayi ta nemi guri ta zauna tace '' besty ina ta kiranki amma shiru bata shiga..., wallahi haɗuwa nayi da yan satar waya ni'ima ta faɗa tana cire dan kunanta da kimono din da take jikinta kawata kice yau kinga tashin hankali.. cewar saudat da take zaune kusa da ita dariya ni'ima tayi tace '' idan aka ce tashin hankali ɗaya kenan toni idan akwai abin da yafi tashin hankali na shiga ke kinga wuƙar da suka sakamin a wuya... wannan ita ake kira da gayawa jini na wuce.., tab ni da nazo muyi hira ashe haka ba zata samu ba wallahi na ra inda zan saka kai na wallahi kuma kin san ba wanda nake mu'amalla dashi kuma daman ke kika nuna min wannan hanyar haɗe rai ni'ima tayi tace '' ban gane ba kafi ni na koya miki daman idan kin ga mutum yayi abu shi ya saka kansa zai yi amma bani na koya miki ba daman can ina sa wannan burin a zuciyar ki samun dama ne baki ba ni wallahi na gaji yanzu ma a makaranta sai da wata ta gama kwakulata tas sannan ta barni nazo gida zan huta ke kuma ki zo tun wuri kisan inda dare yayi miki ki kama wata ko kwa daidai ta.., matsowa kusa da ita tayi tana dafa kafadar ta tace '' dan Allah ki tausaya min yi ɗaya..., maza maza yi ina bani da lokaci da sauri saudat ta kalleta tace '' au ba zaki taya ni ba..?, harara ta galla mata ta kai saudat ta gyaɗa tana cewa haka ma na gode wallahi fasha ta , ta fara lungu da sako.., wa'iya zubilla a haka har ta biyawa kanta buƙata a tare sukai wanka suka fito mahaifiyar ni'ima na zaune a parlour ɓashar bata san me ke faruwa ba koda suka fito ko wacce ta shiraya tamkar wani abu be shiga tsakani ba suka ci gaba da hirar su , suna tafi da shewa sai da aka kirawo sallar isha sannan ta bar gidan dawowa tayi daga rakiyar da tayi wa saudat tace '' mom yau naga kamar baki abinci ba...?, ke ina zanyi iya ni da ba kirkina ba na dan adana ma samu dan abun ɓatarwa a bikin ki zama tayi tace '' ni wallahi yunwa nake ji gaskiya ki nema mana mafita.., wacce mafita zan nema miki yau daddy ki dubu nawa ya baki nafa ci abinci a makaranta ta faɗa tana turo baki gaba to yanzu ma saiki ƙara fito da wani kudin kici abinci wallahi bazan iya ba idan bikin ki ya tashi ba wanda zai temaka min kowa gani yake ina auren me kudi basu san ba abin da nake amfana da shi ba shiru tayi mata bata ƙara cewa komai ba TUDUN YOLA a hankali yake tafiya da ita cikin wheelchair har ya ƙaraso da ita parlour kura mai ido tayi tana kallon ta murmushi ya sakar mata itama mai da mai tayi cikin sarkewar murya tace '' abbey yaushe zaka kai ni gurin ummina..., limshe ido yayi ya buɗe a lokacin ɗaya ba tare da ya ɗauki dogon lokaci yana limshe idon ba yace "insha Allah zan kawo miki ita kinji ki dena damuwa..., maida hankalin'ta tayi kan Hajiya kafa mata ido ba ko kiftawa kallon ta Hajiya tayi tace '' intee na me ke damun ki...?, idanuwanta ne suka cika da hawaye tace ''kullum abbey ce min yake zai kawo min ummina amma yaƙi Hajiya ki sa shi ya kawo min ita shi kaɗai yasan inda take ko..?, karki damu dole ya nemo miki ita ci gaba da kallon ki baki ga cartoon ake ba kallon tv din tayi sai kuma akai sa'a wanda take so ake haskawa na MASHA AND BEAR dariya ta dinga yi tana kauna sukan sataka a cikin farin ciki mara a dad'i Wannan kenan Assalamu alaikum Assalamu alaikum gyara kwanciya tayi bata amsa sallamar ba sai da hajara gwuicho ta gaji dan kanta ta shigo tana wura hanci tace " Sannun ki ishashiya kin samu guri in kwanta kina ji ina sallama amma kikai burus to wallahi sai kin biyani kazata..., Shazali shazali fito ka biya ta kazar ta gaban hajara ne ya yanke ya waɗi ba shiri ta matsa baya jin shiru kamar ma karya asabe take amma don tsaru ba dan tsoro ba sai ta tsaya a bakin kofa da yace ku let tace chus tace '' Allah isaka hunu zaki kirawo daga ƙabari wallahi sai kin biyani..., Shazali ana zagar maka uba hajara gwuicho ce yana kwance ne a daki tun dazu ya dawo dai-dai amma jin ana zagar mai uba ya fito yana muzurai da sauri hajara ta bawa ƙafarta himma tayi gaba dariya ce ta kusan kubbucewa asabe amma sai ta danne gudu tashin hankalin shazali baya son dariya ga shi gidan shiru ba kowa ita ka daice sai mufeeda da take cikin daki tana karatun Alkur'ani Dan haka sai ta saita kanta batare da yayi magana ba ya fita dai-dai shigowar sumy bashi hanya tayi ya fita sannan ta shigo tana cewa wallahi kyenta a haɗa kudi akai kawu shazali asibiti su garkame shi kinga abin da ya fita yana yi yau kina ga ba wanda ya zauna a kofar gidan nan .sumy kenan gidan nan ko gadon ubanane ai na barsa wallahi infa dole ce ke zaune da ni a gidan nan yaufa sai da nayiwa kaina ruwan zafi wallahi