[12/31/2019, 11:20 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *IཽNཽDཽOཽ Aཽ BཽIཽRཽNཽIཽ* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *Rasheedat Usman* *(Ummu Nasmah)* *(MAKAMAR KAINUWA)*👸🏻 📱 *08147537180* *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* (Baya hana gamji) Toho *1 / 1 / 2020* Tsarabar sabuwar shekara domin ku masoyana. *Deducated to* *Aunty Fauza yar Amana* Uwa mabada mama k'aunar ki dabanne gare ni, domin ke d'in shugaba ce, dake Adalci ga duk na k'asa dake, Allah ya barmu tare Aunty nah. *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ Alhamdulillahi Ala kulli Halin dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah madaukakin Sarki, salati da d'aukaka da Aminci su tabbata ga cikamakin Annabawa Annabin k'arshe muhammad S'A'W da iyalan gidan sa da sahabban sa har izuwa Ranar Sakamako. Ina godiya ga Allah daya sake dawo dani lfy, domin sake nishad'antar daku, ina rok'on Allah da yasa yanda na fara lfy ya bani ikon gamawa lfy, Allah ya bamu ikon Amfana da Abunda ke ciki. Ameen 🙏🏻 *P* 1️⃣ ➡️ 2️⃣ Yara biyu na hango suna cin Uban gudu, yayin da wacce ke gaban take gudun ceton Rai, sosai take gudun Saboda kar wacce ke bin bayan nata ta kamo ta, wani gida naga yarinyar ta fad'a, binta cikin gidan itama yarinyar dake biye da itan tayi, da Gudu ta fad'a wani madaidaicin d'aki, cikin haki. d'akin da yarinyar ta shiga, itama wacce ta biyo tan take k'ok'arin shiga. Cikin Sauri wata matashiyar mata ta tare ta tare da cewa. " Lafiya *INDO* kuke wannan Uban gudu, sannan kuma zaki bita har d'aki, aiko mutuwa ma tana kunyar Idon Uwar d'a, meye *Zainabun* ta Miki? kika biyo ta har gidan ubanta ba ko kunya. Huci wacce aka kira da *INDO* take Cikin masifa da bala'i take cewa. " Sai mutuwa taji kunyar Idon ki, ni kuma *INDO banji taki ba, wlh yau Babu mai hanani cin Uban Zainabu cikin gidan nan, gobe koda kud'i aka Had'a ki baxaki k'ara nema na da tsokana ba, cemin fah tayi *INDO BALA'I* a gidan uban waye aka yanka min suna da *INDO BALA'I* Kinga *Goggo Hali* ki kauce ki bani hanya, kar nayi gefe dake kiga rashin kunya ta, dan wallahi, na ture ki na shige cikin d'akin nan baxai bani tsoro ba, ehe sai dai duk abunda zai faru ya faru, ta k'arasa maganar tana murgud'a baki. Gam sukaji An rufe k'ofar d'akin tare da dannawa k'ofar sakata, daga rufen zainabu tace " Baxan fiton ba, kuma na fad'a *INDO BALA'I* ko k'arya nayi ke ba masifaffiyar bace. Matsawa wacce ta kira da *Goggo Hali* tayi tare da cewa to Kinga ma ta rufe d'akin sai dai idan ni zaki Kama ki daka, tunda ke baki da mutunci, kowa ya miki shaidar tsiya a cikin garin nan. Cewa *INDO* tayi " Idan anga dama Amin shaidar Abunda yafi Rashin mutunci ma, kuma wlh yau sai kinga yanda ake tsiya a cikin gidan nan, badai y'ar ki ta rufe d'aki ba, d'aga murya *INDO tayi, tace zainabu kina jina ai idan ba tsoro ba ki fito, mana shegiya y'ar matsorata, kuma wallahi Yau saina huce haushi na akan *UWARKI*. Juyawa *INDO tayi, karaf kuwa sai idon ta yayi toxali da Randar k'asar Goggo Hali, Wacce take cike fal da Ruwa, Da Gudu tayi madafin Goggo Hali ta d'auko tab'aryar ta, Randar k'asar INDO* ta nufa da Gudu tare da buga tab'aryar akan Randar, fashewa Randar tayi, take kuwa Ruwan ya zube kasa, bokiti na k'arfe dake ajiye gefen Randar k'asar *INDO* ta raruma tare da shek'awa a d'akin mahaifin Zainabu, tsayawa Goggo Hali tayi tana kallon ikon Allah a gun *INDO* domin kuwa Idon ne kawai tsakanin ta da ita, tasan Idan tayi gangancin zuwa ta tare *INDO* to Babu shakka zata iya sauk'e mata tab'aryar a kanta ba damuwar ta bane, domin kuwa tasan Halin INDO tsaf babu wanda ta gyale kaf fad'in kauyen. Cikin Huci INDO tace. " Kuma na watsa Ruwan a d'akin Malam Hamxa idan ya dawo shima yasan cewa y'ar sa ta tab'o *INDO* yau, Bata jira mai Goggo Hali zata ce ba tayi ficewar ta tana rera wak'a. " Ikon Allah cewar Goggo Hali, yarinya ta Addabi gari, kowa yake Allah wadarai da Halin ki, Yanxu fah ki duba kiga b'arnan da yarinyar tamin, Amma dai wallahi Albasa batayi Halin Ruwa ba dan dai iyayen ki kam, mutanen kirki ne, Su kuma tasu jarabawar kenan, na Samun fitinanniyar yarinya, to Allah dai ya shirye ta. Jin motsin mutum a bayan ta ne yasa Goggo Hali juyawa, zainabu ta gani tsaye tana sauk'e Ajiyar zuciya, ai kuwa nufar ta Goggo Hali tayi, tare da sauk'e mata rankwashi a kanta, tace. " Yanxu ke zainabu ki Rasa wa zaki tsokana sai *INDO*, sai kace wacce baki san Halin ta ba, to maxa shiga d'aki ki d'auko min mayafi na, naje wajen Uwar ta wlh sai sun biyani Randa ta, dan baxan yi Asara ba wlh. D'akin Zainabu ta nufa tana cewa. " Kije ki wlh Goggo a biyaki Randar ki, tunda y'ar su bata da mutunci. Ita kuwa INDO fitar ta daga gidan su zainabu, hanyar gidan su ta nufa, tun daga nesa ta hango motar sa, cikin murna da zuwan sa, garin nasu yasa *INDO* kwasa a guje, cikin zumud'i, ta nufi motar, kasancewar Gudu baya bawa *INDO* wahala, kullum a cikin sa, take sam bata da nutsuwa, k'azanta kuma wajen *INDO* subhanallah ba'a magana, domin kuwa k'azama ce ta ajin farko, duk inda ake neman k'azama, to idan aka Samu indo ayi fatiha a tashi, domin kuwa kaf fad'in K'auyen Babu wanda yakai *INDO* k'azanta. Wannan kenan. A nutse ya fito daga cikin motar, tare da tsayawa jikin motar yana duba yaran da zasu shigar masa da Kaya cikin gidan, tsohuwa mai ran k'arfe *HAJIYA INNAH* da Gudu INDO ta k'araso wajen nasa tare da yin turus da k'afar ta cikin bak'ar kasa mai k'urar dake shinfid'e a wajen, take kuwa k'asar ta bulewa wannan bawan Allah k'afar sa. Da sauri ya daga kansa ya dubi *INDO* cikin takaici kuma cikin tsawa yace. " Wacce irin mahaukaciya ce ke, ki duba kiga yanda Kika bule ni da k'asa, wawiya marar Hankali, Zaki kauce min da gani ko sai na makeki, Useless kawai. Tura bakin ta INDO tayi, tace " Wlh yau Kam baxan bar nan ba sai kace kana Sona, shikenan kullum sai ni kad'ai zanta sonka, kai baxaka soni ba, wlh yau sai kace kana Sona, ko kuma kamin Irin Abunda nake gani y'an India suna yiwa y'an matan su, a tibin *Hajiya Innah*, Bari ma na tuno sunan Abun 🤔 Yawwa na tuno kuss, suke cewa, sai kamin sannan zan tafi, turo masa bakinta tayi, tace gashi kamin, kaji mustapha na. Zaro Idon sa, mustapha Yayi tare da saurin kawar da kansa gefe, jin bugun warin bakin INDO ya bigi hancin sa, wani Irin hucin wari yaji mai tayar da zuciya, cikin k'yank'yamin ta yake cewa. " Allah ya sauwak'a naso k'azama irin ki, k'azamar k'auye, waima tukunna uban waye zai miki kiss, da wad'annan yellown hak'waren naki, b'ace min da gani kafin na targad'a ki, mahaukaciya kawai, marar lissafi, Amma dai wlh Allah ya isa tsakanina dake, ki rasa waye zakice kina so saini, to wlh Allah ya isa kin cuceni. Murgud'a masa Baki tayi tace. " Niba mahaukaciya bace wlh, kuma sai kamin kuss d'in nan, rarumo rigarsa tayi, ta duk'unk'une a ciki. kasancewar babbar riga yasa, sai buga k'afa take, tana ihu tana cewa. " *Wayyo Allah na shiga uku wayyo jama'a kuzo ku tayani rok'ar ya mustapha ya min kuss wayyo Allah Jama'a kuxo ni kad'ai nake sonsa shi baya Sona.* Rasa Yaya mustapha zaiyi da INDO yayi, gashi kuma yana hango wasu dattawa biyu suna, tahowa, ta inda suke, "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Allahumma ajirni fil musibati, nidai wannan yarinyar ta zamo min masifa wlh, Duk Randa zanzo k'auyen nan, da tsinkewar zuciya nake Zuwa, tunda nasan zan had'u da Bala'i. da k'arfi mustapha yasa Hanun sa cikin kyamar INDO ya b'anb'aro ta da kyar, tare da hankad'a ta, gefe. fad'uwa tayi tare da bige kanta jikin bango, wani Irin zafi taji a kanta, Amma duk da haka Bakin *INDO* bai mutu ba, cikin Rashin Kunya, ta taso kamar wacce zata Doki Mustapha, tace. " Ka ture Allah ya Isa wlh, mungun Azzalumi, kuma wlh Bashi ka d'auka, sai na Rama wlh. Tana gama fad'in haka ta juya ba tare da ta k'ara Kallon mustapha ba. Tsuka mustapha yaja, tare da tab'e bakin sa, yace. " Wawiya kawai marar Hankali da nutsuwa, ai ko d'aura min ke Akayi a kaina, saina sinke ki da k'arfin tsiya, nayi wurgi dake gefe, *K'AZAMAR K'AUYE* kawai. Yara biyu ya hango, Kira ya k'wala musu, bayan sunxo ne, ya umurce su, da su kwashi kayan sukai masa gidan *Hajiya Innah.* Tsayawa yayi har suka gama shigar da kayan sannan yasawa motar sa security, yayi gidan, *Hajiya Innah*. Sauk'ar Ruwa a jikin sa mustapha yaji' wani Irin shid'ewa Yayi, a gigice ya bud'e Idon sa, karaf suka had'a Ido da *INDO* tsaye da bokitin Ruwa a Hanun ta wanda ta juyewa Mustapha a jikin sa, takaici da haushin ta, shine ya hanasa magana, saima wani mungun kallon daya tsaya yana aika Mata. Juyawa INDO tayi a guje tana dariyar k'eta tace. " Na Rama tureni da kayi, daman ai na fad'a maka Bashi kaci, kuma na Rama Yanxu Babu bashi tsakanin mu, masoyina mustapha, *INA SONKA ARADU* tana gudun ne take wannan zancen. Kad'a kansa mustapha yayi, cikin Jin haushin *INDO* da mamakin ta, yake cewa. " Anya kuwa wannan yarinyar bata da Aljanu, don ba k'alau take ba, Kam, wai *masoyina mustapha* ko a gidan uban waye na zama masoyin nata, sai Allah, shigewa Yayi cikin gidan, tare da Sallama. Tana Zaune gefe tana b'arar gyad'a ga kuma tarin kayan da mustapha yasa aka shigo masa dashi, a gefen ta, d'aga kanta tayi tare da cewa " Lale maraba' da mutanen Binni, sai Kuma tayi shuru tare da tsurawa jik'ak'k'un kayan jikin sa Ido, cikin mamakin meya jik'a masa Kaya, kasa hakuri *Hajiya Innah* tayi tace. " Muhammadu dake haka take kiran sa dashi, menene ya jik'a maka kayan ka, kodai ka biya Rafi ne kayi wanka? Tambayar *Hajiya Innah* ta k'arshe itace ta bawa mustapha Haushi, *wai ko ka biya Rafi ne kayi wanka* sai kace ta tab'a ganin nayi hanyar rafin nasu, cikin gatse ya mayar mata amsa da cewa. " *A'a ba Rafi Naje ba, tekun Maliya na biya nayi wankan na dawo*. " To Uban y'an bak'ar magana da zafin Zuciya, Idan da Akwai inda yafi tekun Maliya ruwa ma kaje kayi wankan, aikin banxa kawai daga tambaya sai cibi ya zama k'ari. Tabe bakin sa yayi tare da d'aga kafad'ar sa, Alamun wannan damuwar kine, shigewar sa Yayi d'akin daya kasance nashi idan yaxo k'auyen. D'akin fess dashi gwanin ban sha'awa komai a tsare kamar d'akin Mace, kan dressing merron shi kuma kayan shafe shafe ne kalakala masu tsadar gaske na maxa. Wanka ya shige yayi a ban d'akin Hajiya Inna dake tsakar gidan ta. Itako Hajiya Inna sai mita take ita d'aya. " Yaro ace sai shegen Bak'ar Zuciya gare sa, ga rashin hak'urin tsiya, shiyasa nake Allah Allah *Habeebu* ya dawo ya dinga ziyarta ta, sai munfi shiri dashi, fiye da wannan mai Bak'in Ran tsiyar, dan *Habeebu* yaron kirki ne d'an Albarka, na Rasa wani Irin Aiki yake a k'asar wajen Nan, da yak'i dawowa k'asar sa ta haihuwa. Mustapha daya fito daga ban d'aki ne, yana jin duk mitar da take yi ne, yake ce Mata. " Kamata yayi ki bisa k'asar wajen ai, ki dawo shi wannan K'auyen da Zama K'arshen K'auna, hakan ne zai tabbatar da kina sonshi, Nima banda k'addara da biyayyar iyaye mai zai kawo ni wannan, Bak'in k'auyen harma wannan jarababbiyar yarinyar ta Addabe ni. Kuma wlh Hajiya koda wasa naga k'afar yarinyar nan *INDON* cikin gidan nan sai na b'allata. " Kan Uba cewar Hajiya Innah, to a Bak'in k'auyen aka binne cibiyar Uban ka, kuma baka da wajen daya fi wannan K'auyen tunda shine Asalin Ubanka Haruna. da kake maganar cewa *INDO* karta shigo cikin gidan Nan, gidan kane koko akwai kud'in ka cikin ginin gidan, to ko ubanka Haruna bai isa ya hana *AISHATU* shigowa cikin gidan Nan ba, bare kuma kai *Karan kad'a Miya* , sai dai Kuma Kai kabar min gidana, badai *INDO* ba Zan Kuma ga Uban da zai hana ta shigowa. Hararar Hajiya Innah mustapha Yayi, tare da shigewa cikin d'akin nasa ba tare daya k'ara tankawa Hajiya Innah ba. Itama D'akin ta ta shige tana ci gaba da zagin mustapha, wanda shine gaisuwar da sukayi daga isowar sa. 😄 " Gafaran kudai masu gida cewar Goggo Hali, dake tsaye k'ofar d'akin, Mama mahaifiyar *INDO*. Fitowa mama tayi, tare da cewa, "Lale marhaban da Halima, kece yau tafe a gidan nan. " Eh Nice cewar Goggo Hali, na sameki lfy. " Lafiya lau Halima ki zauna mana, mu gaisa, naga kin tsaya bayan ga shimfid'ar taburma. Cewar Umma. Kad'a kanta Goggo Hali tayi tare da cewa. " Ba zama bane ya kawo ni Mairo, Y'arki ce tayi min D'ibar Albarka, yau a cikin gidana tare da Kuma b'arna, shine naxo a biya Ni, dan baxan iya Asara ba wlh, tunda ku y'arku tafi k'arfin ku. Mama taji Zafin maganganun da Goggo Hali ta mata, sai dai Kuma ba laifin ta bane *d'an kuka ne mai jawa uwarsa jifa* da Indo mutum ce mai jin magana da tuni ta daina jawo musu zagi a gari, amma kunnen k'ashi gare ta, sai dai kullum tana mata Addu'a tare da fatan shiriya, ta kintsu ta dawo y'a ta gari wacce kowa zaiyi Alfahari da ita, kuma tasan Allah maji rok'on bawan sa ne, yana jinta yana ganin ta kuma zai Amshi Addu'ar ta. Bata tsaya tambayan Goggo Hali me Indo tayi mata ba gudun kar taji abunda zai b'ata mata rai, yasa ta cewa goggo hali. " Kiyi Hkr Halima, *d'an yaune ka haifesa baka haifi halin sa ba* Nawa ne kud'in b'arnan da INDO tayi Miki. " Randata ta fasa min, sabuwa gal Ranar da naje, garin Sauro na sayo ta, Naira D'ari Uku da hamsin 350. Kunce bakin zanin ta mama tayi, ta Ciro gudan d'ari biyar ta mik'awa Goggo Hali, tace. " Gashi Idan kin sanja sai ki Aiko min da d'ari da hamsin. Karb'a Goggo Hali tayi Babu ko kunya ta fice tare da cewa zan Aiko miki sanjin ki anjuma. Shuru mama tayi tana tunanin Halin, *INDO* ita tsoron ta ma kar wani ya mata mungun Baki ya kamata, domin kuwa ita kanta Da ta haifi INDO hakuri take da ita, bare Kuma Al'ummar gari. Tana cikin tunanin ne INDO ta shigo gidan da Gudu tana dariya, tare da zama kusa da Mama tace. " Mama ina Abinci na, yunwa nake ji wlh, d'azun nan naci Abinci Amma wlh Yanxu ji nake kamar na kwana biyu banci Abinci ba. Kallon ta Mama tayi, tare da cewa. " Za kuma yau ki kwana baki ci Abinci ba, domin kuwa kud'in cefenen da Malam ya bani d'ari biyar, na d'auka na biya, Halima kud'in Randar ta, da kika fasa, kinga yau sai mu wuni da *Azumin Dole* d'ari da hamsin ta saura, kuma k'annen ki, zan sayawa garin rogo da suger su Sha. " Kutumar Uban nan, Goggo Halin ne taxo tace na mata b'arna, ita bata gaya Miki Abunda Zainabu tamin ba. To wlh Mama sai Goggo Hali ta gwammace Bata karb'i kud'in nan ba, dan wlh sai nayiwa Zainabu mungun dukan da sai sun kashe DUBU a kantin Hassan mai magani. Gwanb'are bakin ta Mama tayi tare da cewa. " Ke dai INDO bakya nemawa Rayuwar ki Albarka wlh, yanxu ma sake komawa zakiyi gidan nasu, ki jawo min wani maganar ne, to wlh ko a hanya kika had'u da Zainabu, karki kuskura kisa hanu a jikin ta, Idan Kuma kika sa Hanu jikin ta, to kuwa ranki zai b'aci a wajena shashashar banxa marar kunya. Tashi INDO tayi tana tura baki tare da maganganu k'asa k'asa, wanda bakin ta ne kawai ke motsi, Sanda taxo daf da k'ofar barin cikin gidan nasu tace. " Wallahi Mama Babu mai hanani cin Uban Zainabu yau, sai dai Idan bamu had'u ba, gara ma kiyi hakuri kawai. Tashi Mama tayi tana dawo ki samu waje ki zauna INDO yau wuni zakiyi cikin gidan nan tunda Allah ya yoki mai kunnen k'ashi. INDO bata tsaya sauraron Mama ba ta fice a d'ari tana dariya. Gidan su k'awar ta Hansai, tayi shigar ta Zauren gidan su hansai ta jiyo muryar Baffah mahaifin Hansai, tsayawa INDO tayi tare da dafe k'irji tace " Alhamdulillah Allah yaso ban shiga ba, Ashe wannan masifaffun tsohon yana nan. Kasancewar Baffah mahaifin Hansai ya hanata kula Indo acewar sa zata Lalata masa tarbiyar yarinya. Juyawa INDO tayi tare da zagawa, ta katangar Ban d'akin su Hansai da nufin ta dirk'a ta ban d'akin yanda zata samu shigewa d'akin Innar su Hansai ba tare da Baffah ya ganta ba. Kama katangar INDO tayi, kasancewar katangar guntuwa ce, ta dira cikin ban d'akin. Lami kishiyar mahaifiyar Hansai dake tsugunne Kan shadda tana bayan gari, taji dirowar mutum cikin ban d'akin, cikin tsoro ta fara bin k'afar INDO da kallo, ba tare da ta d'aga kai ta kalli fiskar taba, ihu Lami tasa cikin tsoro, tana cewa. " Na shiga Uku ni Lami, dan Allah kuyi hkr wlh mantawa nayi, na shigo ba tare da nayi addu'a ba, kuyi hkr dan Allah *ku kuke ganin mu, ba muke ganin kuba ba* wayyo Allah ku kawo min agaji yau Kuma Nayi gamo. Yayin da fitsari ke bin k'afofin Lami. Dariya INDO ta shek'e dashi har hawaye na fita cikin idanun ta, ganin yanda Lami ta gigice ta fice hayyacin ta har tana fitsari a jikin ta, yayin da Idon ta, ke rufe gam tak'i bude su. D'alewa saman katangar INDO tayi ta zauna tana cin dariyar ta, tare da nuna Lami da yatsa. Nan zan dakata sai naji yanda kuka karb'i book d'in kafin naci gaba da typing. *Yawan sharhi yawan typing.* *Share* *And* *Comment* *Alk'alamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/2, 8:05 PM] MAKAMAR KAINUWA🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽* *A͓̽* *B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *N̸͟͞A̸͟͞* *R̸͟͞A̸͟͞S̸͟͞H̸͟͞E̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞* *U̸͟͞S̸͟͞M̸͟͞A̸͟͞N̸͟͞* *(U̸͟͞m̸͟͞m̸͟͞u̸͟͞ N̸͟͞a̸͟͞s̸͟͞m̸͟͞a̸͟͞h̸͟͞)* *( ოႩlႩႪႩR kႩiႶႮwႩ)*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *(Baya hana gamji)* *Toho* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza yar Amana* Uwa mabada mama k'aunar ki dabanne gare Ni, domin ke d'in shugaba ce dake Adalci ga duk na k'asa dake, Allah ya barmu tare Aunty nah. *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P* 3️⃣ ➡️ 4️⃣ Ilu d'an Lami ne da Baffah sai Innar Hansai sukayo ban d'akin da gudu jin ihun Lami, turus suka tsaya sakamakon ganin *INDO* zaune saman katanga sai washe yellown Hak'waren ta take, tana cin dariya, Salallami Innar Hansai ta d'auka cikin Al'ajabin meya kawo INDO ban d'akin su. " Ke INDO meya kawo ki nan, yau kuma tsiyar taki cikin gida na kika kawo sa, cewar Baffah. Jin an Kira INDO ne yasa Lami saurin bud'e idon ta, fes kuwa ta sauk'e su kan INDO dake ta famar dariya ta maida su mahaukata, Cikin Haushin INDO Lami tace. " Amma dai Allah ya isa tsakanina da ke INDO, tsabar rashin mutunci duk k'ofar gidan nan bai isheki sai kin diro ta ban d'aki, baki sani ba koda mutum koko Babu, ki shigo ki sami mutum a Halin da bai dace ki samesa ba. Dariya INDO ta sake shek'ewa dashi, cikin dariyar take cewa. " Kamar dai yanda naxo na same ki kina *Kashi* kai Amma Lami Anyi matsoraciya, duba fah kiga yanda kika jik'e zanin ki da fitsari, sai kuwa ta k'ara shek'ewa da dariyar, *Aradun Allah Lami kashin ki wari gare sa, ni kin gama ma cika min ciki da warin kashin ki*. Ilu ne zuciyar sa taxo kusa, cikin haushi da hasala yayi kan INDO da gudu, da niyar ya mata dukan da sai anxo an kwashe ta. Ganin ilu yana nufa ta yasa INDO dirawa daga katangar, ta kwasa a guji, shima ilu rufawa INDO baya yayi, da Gudu, Babu inda Indo ta nufa sai gidan, *Hajiya Innah* tasan a nan kawai zata tsira daga Hanun Ilu. Hajiya Innah dake Zaune gindin murhu tana ixa wuta ne taga shigowar INDO da gudu a birkice *Hajiya Innah* itama ta tashi tabi bayan indo da gudu. Gudu suke sanda suka shiga cikin d'akin Innah, sannan suka tsaya suna haki, Hajiya Innah ce tace " Ke indo gudun me kike haka, meya faru macijin nan ne, yauma ya k'ara biyo ki. Dariya indo ta shek'e dashi tana nuna Innah da Hanu, tace. " Amma dai Inna ke ba k'aramar matsoraciya bace wlh, daga gani na Ina gudu sai ki biyo baya na. K'ara shek'ewa tayi da dariyar tana nuna Innah yanda taga Innah tayi tsamo a gefe, kamar wanda za'a ce fit ta D'iba da Gudu. Yanxu ke Innah Idan macijin ne, sai na tsaya harki iso ban rufe ƙofa ba, ai wlh kafin ki ƙaraso na juma da rufe ƙofar nan sai dai Kuma kisan tayi. " Amma ke dai INDO akwai ja'irar yarinya, yanxu dan baki da mutunci, sai ki rufe ƙofar ki barni a waje, idan ma kasheni macijin zaiyi ke baki damu ba Koh. " *To me zai dameni Innah, dan kin mutu ai ba Abun damuwa bane, tunda kin mori duniyar, wlh Innah na rufe ƙofar nan baki iso ba shi yafi sauki a wajena.* Haɗa fiska Hajiya Innah tayi kasancewar ta tsani taji ana kira mata mutuwa muraran, tace. " *Bari muga idan na mutu a ina zaki dinga samun taliyar turawa mai harɗe ki dinga ci, tunda gani na ne baƙya ƙaunar ganin ina numfashi*. " Ehhh fah haka ne, kuma Innah, wlh Idan kin mutu Babu inda zan samu taliyar turawan Nan, *to Gaskiya Allah ya Raya min ke Hajiya Innah kodan karna Rasa taliyar turawa,.* Washe Baki Innah tayi tace. " Ameen ƴar Albarka shiyasa nake sonki, faɗan mu baya nisa, saboda kin iya farar Addu'a, yanxu........ Shigowar Ilu yana Banbami ne ya hana Hajiya Innah ƙarasa maganar ta. " *Lafiya mlm ƙaton gardi da kai zaka shigo min cikin gida, ko sallama Babu, kamar wanda ka shigo gidan Ubanka.* Nuna INDO Ilu Yayi, yace. " Ga Wacce na biyo, ki fito INDO wlh idan kika yadda na shigo ɗakin Nan, sai na karya ki. " *To Uban ta, Bismillah shiga ɗakin tunda ɗakin Ubanka ne, cewar Hajiya Innah, har wani cewa kake zaka ƙarya ta, to idan ka fasa ƙarya ta ka raina Uwar da ta haife ka.* Kallon Hajiya Innah ilu yake cikin mamakin ta, yace. " Hajiya kinsan Abunda ta mana kuwa, kike ƙoƙarin shigar mata faɗa. " *Ban sani ba kuma bana son Sani, dake ku mutanen garin nan, manyan ku da yaran ku kun tsani INDO, ko wani laifi ku ɗauko, ku ɗaura Mata, to wlh ta Allah ba taku ba, aniyar ku ta biku, har gadan Baccin ku wlh INDO tafi ƙarfin ku* Hayaniyar da mustapha yaji ne yasa shi fitowa daga ɗakin nasa, yayo wajen Innah, turus ya tsaya yana kallon Innah yanda ta zage, sai zagin Bawan Allah take, ƙarasawa mustapha yayi tare da dafa kafaɗar Ilu yace. " Abokina lafiya me yake faruwa. Juyowa ilu yayi, ya fara bawai, mustapha labarin abunda INDO tayiwa mahaifiyar sa, yace wlh da gaske nake, har banɗaki ta faɗa mata. Shi mustapha baima lura da INDO a wajen ba, sai dai yaji akanta ake Case ɗin tukunna, A zuciyar sa yake cewa, " wannan yarinyar itace Iblis ɗin wannan ƙauye, yanxu tsabar shaharan yarinyar nan, a fanni Rashin hankali har ki dirƙawa mutane katangar tollet ɗinsu, cewa Ilu yayi. " Shiga ka jawo ta kaci Uban ta, wannan ɗan iskan bakin nata wanda kullum yake cikin ƙazanta, ka tabbatar kayi rugurugu dashi. Daga cikin ɗakin Indo tace, " Nidai wlh ba Uba na ba ehe. " Zaro Ido mustapha Yayi, yace. " Sai Uban waye kenan.? Babu tsoro fiskar INDO ta mayar masa da amsa. " Sai Uban Wanda ya tsargu. Kallon ilu yayi yace. " Ka shiga ka sanja mata kamanni nace maka. Tare ƙofar Innah tayi tace, " Naga shegen da zai wuce cikin ɗakin nan, munafiki, idan banda munafurci, meya fito da kai daga ɗakin ka, sai ya fasa mata bakin mu gani. Jawo Innah mustapha yayi😄 suka hau kokuwa, yayin da ya riƙe mata Hannayen ta gam yana cewa, Ilu ya shiga. Ganin da INDO tayi da gaske, Ilu zai damƙe ta, yasa ta daka tsalle sai ƙarƙashin gadon Innah, can ƙarshe. Neman Indo Ilu yayi sama da ƙasa ya Rasa, ko motsin ta, baiji ba cikin ɗakin, fitowa Yayi cikin Huci yace, ta fah ɓace babu ita cikin ɗakin nan. " Babu ita kamar Yaya cewar Mustapha, Yanxu na hango yarinya, kace bata nan ta ɓace sai kace Aljana. " Wlh Babu ita, kaxo ka duba ka gani. Sake Innah mustapha yayi, yasa kansa Cikin ɗakin, bai ganta, dube dube ya hau yi Amma Babu INDO sama da ƙasa, ko a ransa bai kawo INDO zata shige ƙarƙashin gado ba. " Haba ai daman *Biri yayi Kama da Mutum* yanda yarinyar nan, take dole tana Aiki da Aljanu ne, Idan ba Aljani ba waye zai ɓace ɓat lokaci ɗaya. Kallon sa ya mayar kan Ilu yace kaje kayi hkr, kawai ka barta da Allah dan yarinyar nan tafi ƙarfin mutum sai dai Aljani. Shigewa Ilu yayi yana cewa wlh ido na Idon INDO, sai na mata shegen Duka. " Kama kashe ta idan kaga dama, cewar Hajiya Innah kuma zanje har wajen Ubanka naji idan shiya turo ka gidan nan kamin rashin mutunci. Ficewa waje shima mustapha yayi ba tare daya kalli Hajiya Innah ba. Ɗakin ta shiga, tace. " To fito ja'ira marar Kunya nasan ai kina cikin ɗakin, ashe daman Bala'i kika nemo shiyasa kika shigo a guje, har nima kika Sani gudu, yau da sun kamaki sai dai wani bake ba wlh, daman haushin ki, suke ji. Fitowa INDO tayi tana dariya, tace " To ya suka iya dani Innah, ni ɗin tsayuwa zanyi su jibge ni, ni dai yanxu Innah ki bani taliyar turawan Nan, naje gida na tafasa, dan baxan tsaya gidan nan ba, ya mustapha yaxo ya ritsani. " Ai kuwa kinga ɗauki wannan, kwalin ki kaiwa Uwar taki ta tafasa muku keda ƙannen ki. Ɗauka Indo tayi tana cewa, shiyasa nake sonki Innah, kodan wannan taliyar, ficewa tayi tana waige waige kar Ilu ko mustapha su riƙota, cikin sa'a kuwa har ta shiga cikin gidan bata haɗu da suba. Zaune mlm sa'idu mahaifin Hansai yake gaban mai gari, yayin daya kawo ƙarar INDO kan Abunda ta shiga cikin gidan sa ta masa. Nisawa mai gari yayi tare da cewa. " Ita Indon ce tayi wannan ɗanyen Aiki, umurtan Dogari yayi akan cewa yaje yaxo masa da Mlm Musa mahaifin INDO. Da sauri dogari ya tafi aiken da mai gari ya masa. Sallama Dogari ke kwalawa a ƙofar gidan su indo, Yayan Indo Tanimu shine ya fito, jin sallama da ake yi, Dogari ya gani tsaye. " Lafiya kuwa Dogari, cewar Tanimu. " Lafiya lau mlm Musa Nake nema, mai gari ke kiran sa, yanzu a fada. " Me gari kuma, Allah dai yasa lfy. " Koma menene idan yaxo yaji, ka shiga kamin Sallama dashi. " Baya nan Amma bari naje kasuwar na kira sa, zaizo yanzu insha Allah. " Shikenan bari na koma, ka tabbatar yaxo yanzu. " Insha Allah zaizo. Tanimu bai koma cikin gida ba, ya shige, kasuwa wajen, mlm Musa, yana zaune bakin shagon nasa na tireda, yana jin rediyo, yaga Tanimu ya masa Sallama. Amsa Sallamar yayi yace. " Tanimu kaine cikin shagon nawa, yaushe ka dawo daga wajen Raken naka. " Yanzu na dawo Baba bamma daɗe da dawowa ba, naji sallamar dogari, shine yace min mai gari na son ganin ka yanzu. Mlm Musa baiyi mamakin jin kiran mai gari ba, yasan *Tatsuniyar Gizo bata wuce ta Ƙoƙi* wannan kiran da mai gari ya masa bazai wuce wata maganar Indo ta jawo masa a gari ba, tashi yayi ya kulle shagon nasa ya cewa, Tanimu muje. An taro fadar mai gari, ana jiran isowar mlm Musa, sai Kuma ga shi ya iso, zama yayi tare da gaishe da mai gari, sannan mai gari ya dubi, mlm Sa'idu yace " Maimaita masa Abinda ke tafe dakai. Duban mlm Musa, mlm Sa'idu yayi tare da fara jero masa tijarar da, Indo ta masa cikin gida. Ya ƙarasa zancen da cewa, na gaji kawai mai gari ya min tsakani da Indo da Kuma ƴata, babu mu Babu ita, ko a hanya taga Hansai, karta ƙara koda kallon ta. "Allah ya huci Zuciyar ka, mlm Sa'idu, duk Abinda kace Indo tayi banda musu ko ja akan haka, fiye da haka ma zata aikata, Kuma insha Allah daga yau na maka Alƙawarin cewa, Indo ko ƙofar gidan ka, bazata ƙara kallo ba, duban sa ya mayar kan mai gari, yace yallaɓoi dan Allah Ayi hkr insha Allah hakan bata ƙara kasancewa ba. Nisawa mai gari yayi yace, " To mlm Sa'idu kaji bayanin mlm Musa, nima ina ƙara baka hkr, tabbas kam yarinya bata kyauta ba, kayi hkr, gaba idan ta sake zamu ɗauki ƙwaƙwaran mataki a kanta. " Shikenan mai gari, Nayi hkr, Allah ya yafe mana duka. Godiya mlm Musa yayiwa mlm Sa'idu da mai gari, sannan yacewa Tanimu ya tashi su tafi. Tanimu Allah Allah yake, ya isa gida ya samu Indo, wlh yau kam mai ƙwacen Indo a hanun sa Sai Allah. Cikin Sa'a kuwa Tanimu suna shiga shiga cikin gidan itama Indo tana shigowa, da kwalin Indomie ɗinta a kayi, karɓar kwalin Tanimu yayi ya ajiye a gefe sannan yaja Indo har ɗakin da Mama ke kiwon tumaki, rufe ƙyauran Tanimu yayi, Mlm Musa na ganin haka, yayi murmurshi tare da shigewa cikin ɗakin sa, dan yasan yau Indo ta shiga Uku hanun Tanimu. Kallon Tanimu Indo tayi tace. " Me zamuyi Anan ɗin yaya, naga ka rufe ƙyaure, kayi sauri ni zanje na dafa taliya tace. Tanimu bai tanka Indo ba, sai ma sunkuyawa da yayi ya ɗauki bulala, ya hau zabgawa Indo, ihu Indo take tana ƙoƙarin riƙe bulalar Amma Tanimu bai bari ta riƙe bulalar ba, sosai Tanimu yake dukan, Indo, ita kuwa sai cewa take. " Allah ya isa zai kasheni mungu, azzalumi, wayyo Mama, yaya zaiyi kisan kai cikin gidan nan, ka sakeni shege mugun banxa. A jiye bulalar Tanimu yayi ya daki bakin Indo da ƙarfi sanda ya kawo jini, take kuwa bakin ya kunbura suntum, sannan ya buɗe ƙyauren ya fice, yabar Indo tana birgima tare da ihu, Mama da Mlm Musa ya sanar da ita abunda ya faru, ko kollon inda Indo take Mama bata kalla ba saima, ɗage kwalin Indomie da tayi ta mayar gefe, tasan baxai wuce Hajiya innah bace ta bata taliyar. Har dare Indo tana zaune ɗakin tumakin nan taƙi fitowa, zagi kuwa Babu irin wanda Tanimu baisha ba, Jauɗo kuwa ƙaninta daya leƙa da duwatsu ta jefe sa. Babu wanda yace mata fito, kowa harkar gabansa yake, koda Mama ta gama abincin dare ma Indo ƙinci tayi, mama dai mayar da abincin ta tayi cikin madafi, cikin dare kuwa da yunwa ta Addabi Indo Babu wanda ya sani ta zaga ta ɗauki Abincin taci. Washe gari da safe Mustapha ya fito cikin shirin shi na komawa cikin dutse dake Garin Jigawa, Hajiya Innah ya samu tana cin ɗumamen tuwon ta, zama yayi gefen ta, tare da Gaishe ta, Amsawa tare, dace. " Muhammadu har ka fito baxaka bari kayi karin kumallo ba. " A'a innah idan na koma gida na karya, kuɗi ya ciro dubu ashirin ya ajiyewa innah, tare da mata sallama. " Allah ya kiyaye hanya ta masa ka gaishe da iyayen naka, habibu kam wannan karon baka haɗamu munyi magana ba, tare da basa su daddawa kuka harda kuɓewa bushashiya tace gashi ka kaiwa uwar taka sayi Amfani dashi. Karɓa yayi yace innah kwana biyu wayar Habeeb idan na kira bata tafiya, ina ga babu network ne cikin garin naku. " Shikenan to sai Allah ya ƙara dawo dakai ka haɗamu. Har zauren gidan ta rakosa sannan ta koma. Mustapha ya buɗe motar sa da niyar shiga kenan yaji Muryar Indo na cewa. " Masoyina komawa zakayi kuma, ni dai wlh ban gaji da ganin kaba ka bari sai gobe ka koma, kafin nan zan maka kafi tsire sai ka kai tsaraba gidan ku. Juyowa Mustapha yayi a fusace da niyar make Indo, sai kuma yayi tozali da bakin Indo dake kumbure sun tum harya sanja mata kammani, dariya ce ta kwacewa Mustapha yana nuna Indo, yace yau kuma waye ya iya jada Aljana. Gaskiya ku ƙara yawan sharhi ko na ajiye Alƙalamina, domin bakwai sharhi mai tsawo. *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman*✍🏻 *(Ummu Nasmah)* [1/3, 8:05 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty Fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gare Ni, domin ke ɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake, Allah ya barmu tare Aunty nah. *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P* 5️⃣ ➡️ 6️⃣ Taɓa bakin ta indo tayi tace. " Oh wannan Azzalumin ne ya Tanimu, yamin haka da baki, Kuma wlh na rantse da Allah sai na bawa tumakin sa maganin ɓera sunci sun mutu, badai shi azzalumi ba. Wlh saiya gwammace bai taɓa ni ba. Zaro idon sa, Mustapha yayi, Yace. " Ke mahaukaciya, ke yanzu idan aka barki sai ki kashe masa tumaki, dake kema tinkiyar ce, hankalin ku ɗaya da tumakin, amma dai Allah ya Kawo Miki shiriya, dan wlh iyayen ki suna fama da ɓakin cikin ki, sai dai Allah ya basu hkrn zama dake, iya gama faɗin haka ya buɗe motar sa da niyar shiga, indo tayi carap tace. " Dan Allah ya Mustapha karka tafi wlh ban gaji da ganin ka ba. Tsuka Mustapha yaja tare da shigewa motar sa, yaja da ƙarfi, duk ya bule Indo da ƙura, bin motar Indo tayi da gudu tana. " Ya Mustapha ka tsaya dan Allah na manta bance maka, *kifiyar Sonka ta soke ni a ƙirji na, Wlh ina Sonka sosai har cikin ƙahon Zuciyata*. Shi kam Mustapha baima san tana yiba, dan tuni yayi gaba Abinsa, juyawa Indo tayi Ranta a haɗe, cikin takaicin tafiyar Mustapha, gashi wannan zuwan da yayi basu wani haɗu sosai ba, dawa Allah zai haɗa Indo idan ba Zainabu ba, can ta hango Zainabu tsaye ita da, Hansai suna zance, lallaɓawa Indo tayi yanda Zainabu baxata ganta ba, bare ta gudu, ita ko Zainabu sam bata wani lura da Indo ba sai ji tayi an tsakomo ta. Ware idonta Hansai tayi cikin jin tausayin Zainabu. " Uban waye na kama dan kutumar ubanki, ƴar durun uwa, da kin zata kin tsokaneni a banxa ne, to wlh yau na lahira saiya fiki jin daɗi. Ƙoƙarin kwacewa Zainabu take hanun Indo sai dai ina Indo tafi ƙarfin ta, dukan Zainabu Indo take tsakanin ta da Allah, yayin da ta wurgar ta kasa, ta ɗane ruwan cikin ta, sai dukan bakin ta take tana cewa. " Dan ubanki akanki zan huce haushi na yau, gobe Uwar ki Hali zata ƙara zuwa gidan mu kai ƙarata, na kuma ƙara tareki naci ubanki, karku fasa karna fasa, muga nida ku waye zai gaji. Sannan ta sauƙa da ruwan cikin Zainabu. Harara ta zabgawa Hansai tace. " Ke kuma matsa ki bani waje, kema kinyi Sa'a, Wlh da Mai Gari ya kama Baba na, da kema naci naki uban. Ita dai Hansai bata kula Indo, ba har tayi tafiyar ta. Hansai ce tace " Ki tashi kiyi hkr, kema Zainabu meya kaiki tsokanar Indo, kinsan dai Indo tafi ƙarfin ki, maza ma yaya suka ƙare da ita bare kuma ke. Kuka Zainabu tasa, cikin jin haushin dukan da Indo tayi mata, Rabuwa sukayi da Hansai kowa ya kama hanyar gidan su. Da kuka Zainabu ta ƙarasa wajen Goggo Hali. " Lfy Zainabu meya same ki, zaki shigo min gida da kuka, cewar goggo Hali. " Ba Inda bace, ta kama ni da duka, wai gobe ma ki ƙara kai ƙaranta gidan su, itama ta ƙara kamani da duka. Sallallami Goggo Hali ta ɗauka, sannan tace. " Kinga Zainabu ki haƙura ki bar Indo da Allah domin kuwa Indo shaiɗaniya ce, Babu mai iyawa da ita sai ALLAH. Tura baki Zainabu tayi tace. " To Allah ya isa na Wlh. " Shikenan zai kuma isar Miki. Misalin ƙarfe Uku na Rana Mustapha ya shigo cikin dutse, Shango Estate na gani Rubuce a mashigar Inda zai shigan, gidaje ne da yawa cikin Estate ɗin, wani gida mai shegen kyau naga Mustapha ya shiga, yara biyu ya samu a compaunt ɗin gidan suna ƙwallo, da gudu yaran suka taho wajen sa, suna Oyoyo yaya Mustapha, parking ɗinsa ya gyara, sannan ya fito yana dariya, ɗaya bayan ɗaya Mustapha ya ɗaga su yana cewa. " Autan Momy, yau Babu islamiyya ne, na ganku a gida. Sharif ne yace. " Babu yaya, malamin namu baban sa ya mutu, wai sai anyi Uku mu dawo. " Ayya Allah ya jiƙansa da rahama, ina Momy? Ishaq ne yace, " Tana ciki yaya, Aunty *RAUDA* ma taxo jiya take tambayan ka, Momy tace, ka tafi ƙauye wajen *Hajiya Innah*. " Sannun ta da zuwa to, Tare suka ƙarasa makeken falon, wanda ya tsaru da Adon pink da purple, falon yayi kyau sosai, idan ka ɗaga kanka sama kuma, tozali zakayi da wani ƙaton Elagement, Kama ce tsantsan tsakanin su kamar a raba ruwa biyu, haka suke, basu da wani banbanci, koda ta yatsa ne, gefe ɗaya anyi Rubutu da manyan baƙi, *MUHAMMAD MUSTAPHA AND MUHAMMAD HABEEB*, sai kuma gefe duka Family ɗin gidan, wata kyakkyawar mata na gani fara sol daga ganin ta kasan bafulatanar Asali ce, sai wani Dattijo shima kyakkyawa wankan tarwaɗa, sai kuma wata yarinya ƙarama, da kuma ƴan biyun ta Hudu Habeeb Mustapha sai Sharif da Ishaq. Muryar Momy yaji a bayan sa tana cewa. " Mustapha yaushe ka shigo. Murmurshi yayi yace. " Yanxun nan shigowa ta, na same ku lfy. " Lfy lau yasu Hajiyan ka barta. " Tana lfy sai darun tsufa ni wlh Momy na gaji da zuwa wannan ƙauyen gaskiya, Daddy ya daina tura ni, kullum naje ƙauyen nan da ciwon kai nake dawowa. Murmurshi Momy tayi tace. " Mustapha idan bakaje ba waye zaije, kasan dai *Sharifa* baxata iya zuwa ita kaɗai, haka kuma Sharif da Ishaq sunyi ƙanƙanta, Habeeb kuma baya ƙasar ma gaba ɗaya, tunda kaine babba, ai dole kuma kaje ka. *RAUDA* ce ta fito daga kitchen ɗin Momy hanun ta riƙe da cooler, dariya tayi tare da cewa yaya Mustapha sannu da dawowa, Haɗa Ransa Mustapha yayi, yace " Yawwa sannu, tare da kawar da kansa gefe. Jikin *RAUDA* ne yayi sanyi ganin irin amsar da Mustapha ya bata cikin hadewar fuska, gashi ita kuma Allah ya ɗaura mata jarabawar soyayyar sa, amma sam Mustapha baya sake mata fiska Asali ma idan tana waje bai cika zama ba, ta rasa Meye aibun ta da Mustapha ke gudun ta. Shigewa tayi, daining ta ajiye, foodplast ɗin dake hanun ta, ta ƙara komawa kitchen ɗin domin kwaso sauran Abincin. Shigewa ɗakin sa yayi, ba tare daya ƙara wata magana ba. Ran Momy sam baiyi daɗi ba, domin kuwa bata jin daɗin abunda Mustapha ke yiwa RAUDA, gashi ita kuma tana da burin ganin sun haɗa kansu kodan ƙudirin dake ranta na Son haɗa su, Aure. RAUDA jikin ta a sanyaye tace Momy na haɗa komai a daining bari na shiga ɗakin ya Mustapha, na share masa. To Momy tace mata sannan ta haura sama ita kuma RAUDA tayi ɗakin Mustapha. Fitowar shi kenan daga tollet, ɗaure da towel, a ƙugun sa, yaga mutum Zaune gefen gadon sa, ta ƙurawa pic ɗinsu shida Habeeb ido. Tsuka yaja mai ƙarfi wanda ya dawo da RAUDA cikin hankalin ta. " Me kike nema a nan? ya jefo mata tambaya. " Babu komai, daman ɗakin zan gyara maka sannan na sanar da kai, Food is ready. " Na gode to, amma sharar bana buƙata, abinci kuma na ƙoshi, kina iya tafiya. " But amma ya Mustapha. Da katar da ita Mustapha yayi ta hanyar cewa, sorry Please leave me alone, kaina ciwo yake ina buƙatar hutu. Cikowa idon RAUDA yayi da hawaye Cikin tausayin kanta na *Son Maso wani* 🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻 Afwan Fan's wlh yau na wuni a makaranta ban samu na muku typing mai yawa ba, ku biyo ni next page gobe. *Yawan comments yawan typing* *Share* *And* *Comment* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/5, 2:39 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ T̸͟͞o̸͟͞* *Ä̤ṳ̈n̤̈ẗ̤ÿ̤ F̤̈ä̤ṳ̈z̤̈ä̤ ÿ̤ä̤r̤̈ ä̤m̤̈ä̤n̤̈ä̤* ṳ̈ẅ̤ä̤ m̤̈ä̤b̤̈ä̤d̤̈ä̤ m̤̈ä̤m̤̈ä̤ k̤̈ä̤ṳ̈n̤̈ä̤r̤̈ k̤̈ï̤ d̤̈ä̤b̤̈ä̤n̤̈ ẗ̤ä̤k̤̈ë̤ g̤̈ä̤r̤̈ë̤n̤̈ï̤, d̤̈ö̤m̤̈ï̤n̤̈ k̤̈ë̤d̤̈ï̤n̤̈ s̤̈ḧ̤ṳ̈g̤̈ä̤b̤̈ä̤ c̤̈ë̤ d̤̈ä̤k̤̈ë̤ ä̤d̤̈ä̤l̤̈c̤̈ï̤ g̤̈ä̤ d̤̈ṳ̈k̤̈ n̤̈ä̤ k̤̈ä̤s̤̈ä̤ d̤̈ä̤k̤̈ë̤. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* Aunty Hauwa Maman Uswan, ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *Godiya* Gareku masoyana, a gaskiya banda bakin da zan muku godiya domin kuwa kun nunawa wannan book ɗin nawa ƙauna fiye da tunani na. Allah ya bar ƙauna, ina muku godiya a duk inda kuke, da wanda nasan su da wanda bansan suba. *P* 7️⃣ to 8️⃣ Mai ya shafawa jikin sa, sannan ya zura jallabiya, wayar sa ya ɗaga, ganin kiran ɗan uwan sa, Habeeb. " Mutanen India, kwana biyu kun manta da mu fah. Dariya Habeeb yayi cikin zolaya yace. Ni waye na isa da mantawa da ɗan uwana na haihuwa, kasan dai kaima hakan baxata kasance ba, rai ya mata da rai. " Ba wani nan cika min baki kake yi kwana biyu ka jini shuru ai zaka neme ni meya faru. " Nafa nemi layin ka naji unable to connection, na kira Momy take cemin, ai ka tafi ƙauyen dasina, wajen *Tsohuwa mai Ran Ƙarfe Hajiya Innah*, Gaskiya nayi missing ɗin tsohuwar nan, kasan rabo na da ita, 8yrs. " Ƙauyen Dasina ko ƙauyen masifa, kullum naje wannan ƙauye sai na dawo da ciwon kan wannan mahaukaciyar Aljanar yarinyar. Dariya mai sauti, Habeeb yayi, yace. " Gaskiya zanso ganin wannan, Aljanar taka, da kullum nake shan labarin ta, *umm Waya ga Musty Angon Aljana INDO* zanso ganin Ranar da zaka cewa INDO *I love You* " Amma dai Allah ya isa tsakanina da kai Habeeb, ashe kuwa zaka mutu baka ga wannan Ranar ba, Allah ya kiyashe ni, ɗiban yayi, kaga ma sai Anjuma naga Alamu, yau da baƙar Fata ka tashi, kafin bakin ka yayi tasiri kaina gara na kashe waya ta. Dariya ce sosai Habeeb yake tun yana kan kujera saida ya sauƙo ƙasa, yanda Mustapha ya hasala kai kace, ance gobe za'a ɗaura masa Aure da INDO, duba wayan yayi yaga harma ya kashe wayar. " Mustapha Sarkin Zafin Zuciya, gaskiya duk matar da ta Aure ka, zata sha wahala kafin ta gane halin ka, domin sanin Halin ka sai wanda yayi dogon Zama da kai. Tashi yayi daga ma daidaicin falon da yake ya shige bedroom ɗinsa tare da turawa Mustapha saƙo kamar haka 👇🏻 Allah ya huci Zuciyar ka ɗan uwana, sannan ka shirya tarbata gobe ina hanya insha Allah, zanzo hutu. Murmurshi mustapha yayi bayan ya karanta saƙon Habeeb, tura masa yayi da cewa. Kai amma gaskiya naji daɗi sosai Allah ya kaimu goben da rai da lafiya, bari ma naje na fara yiwa Momy Albishir. *DASINA* Kwanan Mustapha Uku da tafiya, Indo dai tsiyar tata da sauƙi, domin kuwa yau har ruwa Mama ta samu Indo ta jido mata, Bayan ta gama ɗibawa mahaifiyar tata Ruwan ne, cikin girma da Arziki tace Mama na tafi gidan Innah. A dawo lfy Mama ta mata, sannan Indo ta fice daga gidan zuwa na Innah, a hanya ta gamu da Baffah mahaifin, Hansai, har ƙasa Indo ta sunkuya ta gaishe shi, mamaki ne ya cika, Baffah ganin Indo a nutse, har mutuncin gaisuwa ya samu, Amsawa yayi ta shige, abunta gidan Innah. Baffah ne yace, " Allah dai yasa *ba nutsuwar kwantan ɓauna tayi ba* Indo ta samu Innah sai shan Baccin ta takeyi hankali kwance, bata tashe ta ba, saima tsintsiya da ta ɗauka ta sharewa Innah gidan ta tsaf, tare da wanke mata kwanukan ta, sannan ta hura wuta, ta dafa taliyar ta, sanda taci ta ƙoshi tayi gyatsa sannan tace " Alhamdulillah, to bari na lissafa aikin ladan da nayi yau, na farko dai, nayiwa Mama ɗiban ruwa, na gaishe da Baba, na kuma gaishe da Baffah, yawwa sai yanzu da nayiwa Hajiya Innah aiki, wataƙil zan iya samun, lada, guda *ɗari da tamanin* ko haka na tsaya a cikin satin nan na samu, yawwa to yanzu bari na tashi Innah ta bani Naira hamsin na tafi shagon ɗan tasi na sayo maganin ɓera, dariya tayi tace, ya Tanimu nida kai shege ka fasa cikin wannan ƙauyen, tashi Innah ta hau yi, da salati a bakin ta, Innah ta farka, washe baki Innah tayi tace. " Kaji ƴar Albarka ina mafarkin ki, sai kuma gaki. Naɗe kafar ta Indo tayi tace dan Allah Innah gaya min me kika ganni inayi cikin mafarkin. Dariya Innah tayi tace, " Ganin ki nayi, a Makeken gidan da Muhammadu Mustapha ya gina, kina zaune hakince, komai sai dai kisa amiki, ga kayan ciye ciye kala kala, ke harda fah ƴarinya na ganki wai harkin haihuwa. Rufe idon ta Indo tayi wai ita a dole taji kunya, ance an ganta da yarinya ta haihu, cigaba da cewa Innah tayi. " Kinga wasu maka makan kujeru dake cikin ɗakin ki, harda wani ƙaton tebi. Dariya Indo tasa tace. " *Wayyo Allah, Allah ya Kai damo ga harawa ko baici ba yayi ɓarna chap Innah waya ga INDO A BIRNI, za'a ga tsiya Aradun Allah, dan zan tsula ciyata son Raina, kinsan Innah, nifa Idan na Auri ya Mustapha ya daina fita kenan, karma wata shegiya ta gansa tace tana sonsa*. dariya Innah tayi tace. " Idan kin hanasa fita naga shegen da zai nemo muku abinci kuci, bare ma kekam mai cin tsiya, nifah nama fi sonki da Habibu, domin kuwa yafi wannan mai zafin ran tsiya, sauƙin kai. Tura baki Indo tayi tace. "Kinga Innah Idan kina son mu zauna lfy ki daina zagin ya Mustapha, waye ma habibu, sunan ma ko daɗi Babu, wai *HABIBU* nidai ya Mustapha nake so. Kama bakin ta Innah tayi, tace " Ikon Allah, wai damma ba kyale ki yake yiba kullum yana cikin Hantarar ki, da tsangwama. " Naji nidai yanxu bani Hamsin, tunda sharar da nayi miki ma baxaki gode min ba, sai ki bani ladar shara na da wanke wanke, dan nayi ne domin ki biyani. Sai lokacin Innah ta lura da sharar da Indo tayi mata, fes ta share gidan ya fita, dariya Innah tayi, tace. " Sannu ƴar Arziki Irin Albarka, ai ɗari ma zan baki ba hamsin ba, laritarta Innah ta buɗe ta ɗauko gudan Ɗari ta bawa Indo. Aiko kuɗin nan na shiga Hanun Indo ta tashi a guje, sai shagon ɗan tasi, maganin ɓera tace ya bata na hamsin, karɓar kuɗin ɗan tasi yayi, tare da danƙa mata maganin ɓerar. A hankali Indo ta shigo cikin gidan nasu tana leƙen, gidan domin bata son kowa yasan ta shigo gidan, cikin Sa'a kuwa Babu kowa tsakar gidan, ɗakin tumakin ta shiga, suna ɗaure sunfi goma, dusar dake gaban su ta zazzagewa maganin ɓerar, sannan ta dama shi sosai, kallon tumakin tayi tace. " Kuyi hkr fah tumaki ba da son raina ba zaku mutu, wanda ya ɗaure ku shine ya jawo muku dan haka sai ku ɗauki hkr, wuf tayi ta fice tabar gidan kafin kowa ya ganta, a dakalin ƙofar gidan nasu ta zauna, zuwa azhar kafin ta shiga cikin gidan nasu. Fitowar Mama daga ɗakin ta, zatayi madafi ne, sai taji tumaki na wani irin gurnani, leƙa ɗakin tayi, sai tagan su gabaki ɗaya kwance, bakin su kuwa sai fitar da kunfa yakeyi, zaro ido Mama tayi, da sauri tayi ɗakin Tanimu ta kira sa tare suka fito duka harda Baba, Salati Baba ya ɗauka, cikin mamaki yake cewa " ikon Allah dobbobi kamar wanda suka ci guba, maxa Tanimu, tafi ka kira idi mahauci yaxo ya siyi dabbobin nan dan Wlh mutuwa zasu yi. Da gudu Tanimu ya fice daga gidan, a gigice, INDO dake zaune taga ficewar Tanimu, Dariya tayi, tace. " Lallai magani ya fara aikin sa. Tare Tanimu suka dawo da idi mahauci, ko Kafin su iso ma tuni tumaki kam sun mutu, gaba ɗaya ko ɗaya bai tsira ba, shuru Tanimu yayi tare da zamewa ya zauna a ƙasa, sai Kuma hawaye ya fara bin idanun sa, Mama ma taji tausayin sa ainun, domin kuwa ko wani rago ɗaya zaiyi dubu Arba'in, Baba kuwa, Haƙuri ya fara bawa Tanimu da cewa ya ɗauki ƙaddara. INDO da ta shigo cikin gidan ne, ta samu Tanimu na zaune sai famar kuka yake, salati ta ɗauka tare da cewa. " *Subhanallah me zan gani haka, GARDI da kuka, sai kuma tasa dariya, Allah sarki daɗi na da gobe saurin zuwa, haka Nima jiya iwar haka, ka Sani kuka, sai gashi nima yanxu Allah ya saka min.* Jin furucin INDO yasa Mama, zargin kodai Indo ce tasawa dabbobin nan wani Abu suka mutu. " Zo nan Indo cewar Mama. " Naxo kuma Mama me zanyi ni Kuma? " Kixo nace ko, idan kuma baxaki zoba, sai ki faɗa min. Tahowa Indo tayi, kusa da mama, tace " Gani nan tana tura baki tayi maganar. " INDO kece kika kashe dabbobin nan koh? Saurin ɗago kansa Tanimu yayi jin abinda Mama ke furtawa. Cikin rashin tsoro, Indo tace. " Ni kuma Mama, akan me zan kashe masa dabbobin sa?, nikam bani bace. Murmurshi Mama tayi kasancewar tasan Halin Indo, indai kin haɗa ta da Allah to zata faɗa miki gaskiya, sannan tace. " Dan Allah dan Annabi na roƙeki da Allah ki faɗa min idan kece kika kashe dabbobin nan? " Shikenan tunda kince Allah, ai kin gama magana, dole zan gaya miki gaskiya. Har ga Allah Mama ganin da nayi Ya Tanimu haka kawai jiya yata jibgata akan wata banxa lami, Babu wanda ya hanasa cikin gidan daga ke har Baba, shiyasa ganin da nayi bani da gata cikin gidan nan, ba'a sona yasa ni ƙwatawa kaina ƴanci ta hanyar, zuwa gidan Innah nace ta bani hamsin, tana bani kuwa nayi shagon ɗan tasi na sayo maganin ɓera, kuna cikin uwar ɗaka, na shiga na juye maganin ɓarar cikin Abincin dabbobin, Amma fah Kafin na saka musu saida nace dabbobin su yafe Min ai. A fusace Tanimu ya tashi zai rufe Indo da duka. Dakatar dashi Baba yayi ta hanyar cewa tsaya Tanimu. Kallon Indo yayi yace. " Haba yanzu dan Allah akan ɗan dukan, da ɗan uwan ki, ya miki jiya shine shine zaki masa wannan mungun Aikin, kisan Asarar da kika masa kuwa, haba Indo meyasa bakya jin magana ne, innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, yanxu Indo, tsiyar taki, harmu ma baki barmu ba, to wa zaki bari, iyayen kima baki kyale ba, bare Kuma Wasu, kiji tsoron Allah Indo ki gyara alaƙar ki da al'umma. " Haba Baba wacce nasiha zaka tsaya yiwa wannan shaiɗaniyar, Ka kyale ni kawai yau na koya mata hankali cikin gidan nan na karya ta, ta zauna kowa ma ya huta da bala'in ta, dan Indo masifa ce. Mamace tace. "Subhanallah, haba Tanimu, ƴar uwar taka kake kira da masifa, baxaka nema mata sauƙi ba, sai kake binta da mungun baki, to karna sake jin ka kirata da masifa, da kake cewa a barka ka koya mata hankali, jiyan da ka doke tan, meya jawo maka yanzu, Bayan Asarar da tayi maka, a yanzu ni kaina Uwar Indo lamarin ta ya fara bani tsoro, idan kace ma dukan ta zakayi, gobe sai ta maimaita maka abinda yafi na yau, addu'a kawai ya dace mu bita dashi, Allah daya bamu ita, shi zamu roƙa ya shirya mana ita. Baba ne yace. " Tabbas Maganar mahaifiyar ku gaskiya ce, addu'a shine mafita tsakanin mu, da Indo. Kallon ta Mama tayi tace. " Kinyi sallar Azhar ne? " Banyi ba cewar Indo tana haɗa rai tare da hararar Tanimu. " Jeki ki ɗauki buta maza kiyi Alwala, kiyi Sallah. *Ni fah Mama ba yanxu nake yin Sallah ta ba, sai da isha'i nake haɗa Asuba magriba Azhar da kuma isha'i.* Kuyi hkr da rashin jina jiya da bakuyi ba, hakan ta faru ne ta sanadin bana typing Ranar Asabar, fans ɗina dake group ɗin Sara da Sassaqa sun san hakan. *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/6, 4:33 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ T̸͟͞O̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni, domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* Aunty Hauwa Maman Uswan ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya.🙏🏻 😄😄😄😄 Sara da Sassaqa fan's kuyi hkr wlh ban manta daku ba, ina nan ina typing ɗinsa, za kuma kuga posting, gobe insha Allah. *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*•••••••9️⃣ ➡️ 1️⃣0️⃣ Tsawa Mama ta dakawa INDO tace, " Maza ɗauki buta kije kiyi Alwala kiyi Sallah maxa, sannan ki ɗauko uniform ɗinki, na boko ki wanke gobe Litinin kuna da makaranta, Anjuma kuma zakije makarantar Allo. " Nifa Mama Babu wani wanki da zanyi, haka zansa uniform ɗin, ni bokon ma ba wani damuna tayi ba. Tanimu dake jifan Indo da mungun kallo ne ya tashi ya fice daga cikin gidan, domin Wlh ji yake kamar ya shaƙe wuyan ta, sai dai babu damar yin hakan sakamakon hanasa da Mama tayi. INDO tana haɗa rai haka ta ɗauki buta tayi alwala, bayan tayi sallar ne, ta ɗebo uniform ɗin bokon nata, ta wanke su, tas kuwa ta wanke, domin Indo badai iya wanki ba, sai idan bata ga dama ba, tayi jiƙa jiƙa. Jummalo ce ƙanwar INDO ta shigo cikin gidan hanun ta ɗauke da ledar shinkafar da Mama ta aike ta, ta siyo mata shagon ɗan tasi, da Sallama jummalo ta shigo, amsawa Indo tayi, tare da cewa. " Zona aikeki jummalo ɗakin Mama ki ɗauko min ɗankwalin uniform ɗin nan. Babu musu jummalo ta shige ɗakin Mama, tana sallah ta same ta, ajiye ledar tayi tare da duba cikin kayan wankin Indo, da ƙyar jummalo ta samo ɗan kwalin, ficewa tayi ta miƙa mata, cikin neman faɗa Indo ta fara cewa jummalo. " Wato ke kuma jummalo tsabar baƙar mugunta, shine jiya kika wanke uniform ɗinki ko ki haɗa da nawa ki wanke, kinyi Asara ai ke kam, *mai shegen wariyar Launin fata*, To gashi ai na wanke yanxu banga abunda ys ya cinye ni ba. " Kiyi hkr na duba uniform ɗin naki ne ban gani ba shine yasa na wanke nawa kaɗai, Amma ai kinsan kullum nice nake wanke mana uniform koh. " Kuma haka ne, kinsan nifa idan ana min abu kullum Rana ɗaya banga ammin ba, ji nake kamar ba'a taɓa min ba, shikenan jeki, nima na gama gari zan shiga dan wlh ba xanje makarantar Arabbi ba yau. Ita dai jummalo shigewar ta tayi ɗakin Mama ba tare da ta tankawa INDO ba. Washe gari da safe jummalo tayi shirin makarantar ta, kunu da ƙosai taci, sannan tayiwa Mama sallama ta tafi, ita ko Indo bata da Alamar, zata makarantar ma, dan ko karin kumallon ma batayi ba, tana zaune, kawai tayi shiru. Mamace ta dube ta tace. " INDO baxaki makarantar bane, jummalo har ta juma da tafiya, takwas fah yanxu, ko karin kumallo baki yiba. " Zani mana, nafi son sai sun gama wannan tsayuwar tukunna, mema yake da suna, asandabilyu, ko Assambly, oho sai sun gama tukunna. " Tashi maxa kisa uniform ɗinki, kixo kici abinci, ki shige makaranta, bana son shashancin banxa, ko dan kinga ina kyale ki, shine kike min abunda kika ga dama dan ubanki, ki tashi nace, cikin tsawa Mama take maganar. Tashi Indo tayi tana ƙunƙuni tasa uniform ɗin, ko karin kumallon ma ƙinyi tayi, ta fice daga gidan. " Allah ya shirya ki Indo cewar Mama. A hanya Indo ta ɓelɓelce, ba ita ta shiga cikin makarantar tasu ba, sai ƙarfe tara na safe. Taxo daidai bakin window na ajin nasu taji for master nasu yana kiran sunan ta. " *Ashatu Musa* Daga jikin window INDO ta amsa da ƙarfi. " *Labbaika Present Sir Naxo, gani nan ma a nan*. Gabaki ɗaya Ajin juyo da kallon su sukayi zuwa ga Indo, yayin da Mlm Sani ke cin dariya, suma Ajin dariyar suka ɗauka. Cikin dariyar ne, Mlm Sani yace. " Sannun ki da zuwa to, sai ki samu damar ƙarasowa koh. Shigowa Indo tayi ba tare da tsoron lattin da tayi ba, tsayawa tayi gaban mlm Sani tace. " Mlm gani. " Meyasa kika zo a latti? Me kuma yasa kika amsa min sunan ki daga waje? Wa kuma yace kin amsa sunan ki sau biyar? Mlm Sani ya jefo mata tambaya tare da ƙara gyara zaman bulalar sa, a hanun sa. Haɗa fuska tayi, tana kallon bulalar hanun sa, kafin tace. " Mlm duka wannan tambayar zan amsa ni kaɗai. Ɗago bulalar Mlm Sani yayi, tare da cewa zaki amsa min koh saina lillisaki tukunna. " Zan baka ta fada masa tana turo bakin ta gaba. " Ina jinki, tell me. " Mlm to ka fassara min Abunda kace na ƙarshen, toll ma, meye ne shi da Hausa. " Murmurshi Mlm Sani yayi kasancewar yasan Indo tana da ƙoƙari, indai akayi darasi bata fahimta, ba, to fah sai tayi tambaya, kuma dags wannan lokacin ta riƙe kenan a kwakwalwar ta, gaskiya Indo badai brench ba. " Tell me, yana nufin cewa faɗa min. Kin gane. Kaɗa kanta INDO tayi alamun ehh ta gane sannan tace. " Mlm Abunda yasa nayi latti tsakani da Allah bana son tsayuwar asandabilyu ne, na biyu kuma, na amsa ne saboda bana son ka samin banxo ba, sai na Uku kuma, da nace *Labbaika* wai dai Mlm na maka *Larabci ne* dan kasan na iya, *Present Sir* kuma wai na amsa maka ne da yaren turanci, sai kuma *Naxo* da Hausa na maka. Kaga Mlm ai nayi ƙoƙari dana iya Yaren Uku koh. Kaɗa kansa Mlm sani yayi tare da jinjina shirme irin na Indo, da yarinta, wato dai Kowa da irin tasa yarintar, duban ta yayi yace. " Dan Allah INDO daga yau duk ranar monday ki dinga zuwa kina halartar Asembly yana da amfani sosai, sannan daga yau ki daina amsa suna daga waje, ki bari sai kin shigo class tukunna, sannan daga yau idan an kira sunan ki, ki amsa da Present kawai kinji. " Naji Mlm kuma baxan sake ba in Allah ya yarda. Muga farcen hannu ki, da kuma kitson ki, uniform dai naga kin wanke. Miƙo masa hanun Indo tayi, wayyo Allah, farcen Indo sunyi zaƙo zaƙo sai kace wacce bata taɓa yankan farce ba, tunda uwar ta, ta haife ta, kayin ta kuwa da ta buɗe Babu abunda yake tashi sai tsamin datti, kitson ta kuwa tsabar daɗewa har ba'a ganin tsagun. " Subhanallah cewar Mlm Sani, meye haka INDO, wani irin ƙazanta ne wannan, ki dubi farcen ki, da kayin ki babu ko daɗin gani, haba Indo kike tsafta dan Allah. Kinji, kinga yanda kike babbar yarinya haɗaɗɗiya, da zaki ke tsafta haba wa, karki ga kyan da zakiyi. Su Indo Mlm Sani ya fasa mata kai, cikin dariya tace " Allah Mlm ni kyakkyawa ce. Dariya Mlm Sani shima yayi domin a iya zaman sa da Indo ya gane idan zaka bita a hankali tana da sauƙin kai, za kuma ka ribance ta, idan kuma da faɗa kake binta, baxata taɓa gyarawa ba. " Sosai ma kuwa, a wani fitowar kyan naki ma, sai kin yanke farcen ki, kin tsefe kanki kin wanke, kije kiyi kitso, ai Babu mai gane ki Indo tsabar kyan ds da zakiyi. Ƙara washe yellown hakwaren ta Indo tayi, tace " Wlh Mlm yau zanyi kitso, na yanke farce na, har ƙunshi sai nayi, Allah sarki ashe ni kyakkyawa ce, nake ɓoye kyawuna. Murmurshi Mlm Sani yayi cikin jinjinawa yarinta irin na Indo yace. " To Allah ya kaimu jeki zauna maxa zamu fara lesson. Rasa wajen zama Indo tayi sakamakon cika teburin zaman da akayi, sai dai ta zauna a ƙasa, hango Zainabu Indo tayi zaune ita da su Hansai, wajen nasu ta nufa, cikin gadara da bata rai, tace, ke Zainabu tashi ki bani waje na zauna. Saurin tashi Zainabu tayi, kasancewar tana tsoron taƙi, tashi, Indo taci uban ta. Ta koma ƙasa ta zauna. Girgiza kanta Hansai tayi ganin fin ƙarfin da Indo tayiwa Zainabu. *ⓓⓤⓣⓢⓔ* Dariya sosai RAUDA keyi, har tana riƙe ciki, tace. " Wlh ya Habeeb ka bani dariya, wai yaushe zaka gane ka girma ne, wai camma, London ɗin haka kake musu irin wannan calikancin. Dariya shima Habeeb yayi tare da cewa. " Zan girma amma sai randa nayi Aure dan har yanzu a matsayin Yaro nake. Momy dake sauƙowa daga step ne take cewa. " Kai kam baxaka girma ba, tunda har yanxu ka gagara yin hankali, kullum wasa shine cinka da shan ka. Murmurshi Habeeb yayi, yace " Kai Momy kema abunda zakice kenan, Momy ai rayuwa saida wasa da Dariya, har yaushe kullum mutum zai zauna cikin haɗe fuska, gaskiya ni baxan iya wannan rayuwar ba. RAUDA ce tace. " Shiyasa Rayuwar ka take burgeni ya Habeeb, kana komai cikin sauƙin kai saɓanin ya Mustapha da baya sakewa da kowa, daga Momy sai kai. Dariya sosai Habeeb yayi yace. " Bros sai a hankali haka yake tun tashin mu, bai cika sakewa akan komai ba, so kar wannan ya dameki, domin *A JININ SA YAKE*. Momy ce ta nisa tare da cewa. " Abinda nake faɗi mata kenan, ta daina damuwa da Halin mustapha, Amma ta kasa ganewa wataƙil idan ka faɗa mata, sai ta gane naka. " Hmm RAUDA Amaryar mustapha, tun yanxu kin tsoron sa, ina kuma ga anyi Auren, ya faɗa mata tare da kanne mata ido😉. Murmurshi RAUDA tayi tare da cewa. " Ya Habeeb kaima dai da tsokana kake, nine muke soyayya da ya Mustapha, lallai zolayar ka bata baka dai dai ba. Dariya Habeeb yayi yace. " Shikenan *Abar Kaza cikin gashin ta* Amma nidai nasan abinda ke wakana. Jin motsin mutum ne yasa Habeeb juyawa, Mustapha ya hango yana sauƙowa daga step, cikin haɗewar fuska, dariya Habeeb yayi ganin kallon da Mustapha ke aikawa RAUDA, kallon wulaƙanci. Sanda ya zauna kusa da Habeeb sannan yace " Sannu da hutawa Momy. " Yawwa sannu sai yanxu ka fito, Tun ɗazu ɗan uwan ka ke jiran ka, kuma kasan dai Daddyn ku, yace by four ku samesa kasuwa. " Sorry Momy wlh bacci ne ya danne Ni, amma yanxu ma bata ɓaci ba, zamu tafi, kallon Habeeb yayi yace, muje bros. " Muje ina ai idan kaga na tashi anan sai Momy ta mana Shari'a, Momy gani ga Barrister mustapha, ki mana Shari'a. " Ina sauraron ku kaji iyayen faɗa badai ku haɗu ba sai kunyi cece kuce tsakanin ku, cewar Momy. Dariya Habeeb yayi Yace. " Momy cewa fah nayi gobe muje ya rakani DASINA wajen Hajiya Innah, amma bawan Allah nan yace baxai jeshi ba. Murmurshi Momy tayi tace. " Yana da gaskiya Habeeb, kwata kwata kwanan sa uku da dawowa, kuma gashi ya koma bakin Aikin sa, kaga kuwa kai kaɗai zakayi tafiyar ka. Dariya mustapha yasa tare da cewa. " Yes Momy daɗi na dake Adalci, Mlm Habibu Angon Hajiya Innah, tafiya DASINA ya kamaka kai ɗaya, sai ka tashi mu dangana zuwa ga Daddy. RAUDA ko Babu abunda take sai kallon mustapha Kamar wacce zata haɗiye sa, shiko suna haɗa ido zai maka mata harara. *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/7, 5:31 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ T̸͟͞O̸͟͞* *Aunty fauza ƴar amana* Uwa mabada mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* Aunty Hauwa Maman Uswan, ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya🙏🏻. *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ___________________________________ Masoyana bani da bakin da zan muku godiya, na gode na gode sosai, da ƙaunar ku gare Ni, yanda kuke Son book ɗin *INDO A BIRNI* abun ba'a cewa komai, waɗanda suka min magana ta privet cewa na sasu a group ɗin *INDO A BIRNI* suyi hkr dan Allah wlh group ɗin ya cika, ku nema a wani group nasan baxaku rasa ba.🙏🏻 *P*••••••1️⃣1️⃣ ➡️ 1️⃣2️⃣ Kauda kanta RAUDA tayi cikin ƙunar rai, ta rasa menene ya gaxa a jikin ta da mustapha yake mata wannan wulaƙancin, gashi Dai Mamy tace mata malamin ta, ya tabbatar mata cewa Mustapha zaiso ta, amma har yanzu shuru, sai ma uban wulaƙanci da take fuskanta a wajen sa, yau dai ta ƙudurce a ranta, dole sai ta koma gida, kodan Mamy tasan halin da ake ciki, domin kuwa baxata iya Rayuwa Babu mustapha ba, shine numfashin ta, taya to rayuwa zata kasance Babu numfashi, dole ma sai ka soni mustapha, dole ne. Maganar da Habeeb ke mata shine ya dawo da ita daga duniyar tunanin data faɗa. " Dan Allah Sis RAUDA anjuma ki haɗa min Abinci, mai kyau, ai kinsa abubuwan da nafi buƙata. " Ba komai ya Habeeb zan haɗa maka insha Allah, adawo lfy. " Habeeb ne kawai ya amsa da Ameen shikan mustapha, kallo ma bata isheshi ba, bare kuma ya amsa sai ya dawon ta. Sallama sukayi wa Momy sannan suka wuce wajen daddy kasuwa. RAUDA kallon ta, ta mayar wajen Momy tace. " Momy bari na haura sama na ɗan miƙe, kafin Anjuma na sauƙo na ɗaurawa ya Habeeb girki. A fito lfy ta mata, sannan ta haura sama. Kwanciya RAUDA tayi akan gadonta tare da ɗaukar wayan ta ta dannawa mamyn ta Kira. Da sallama Mamy ta Amsa, tace RAUDA lfy naji Muryar ki kamar wacce taci kuka. " A'a Mamy ba kuka nayi ba, kawai raina ne yake ɓace, Mamy na shiga Uku, ya Mustapha baya sona, Mamy ko kallo na, baya sonyi, ya zanyi Momy, ta ƙarasa maganar cikin kuka mai tsuma Zuciya. " Ya isa Haka RAUDA, ki daina kuka, domin kuwa muddun ina numfashi dole sai Mustapha ya durƙusa a gaban ki da gwiwwowinsa yana roƙarsa soyayyar ki, Dani yake zancen, tunda shi butulu ne, baisan Alkairi ba, ai yana da tarihin Halaccin da mahaifin ki yayiwa ubansa, ki kwantar da hankalin ki, zai shigo hanu, sai kin juyasa kamar wainar tanda. Cikin farin ciki RAUDA tace. " Promise Mamy, wlh ina son ya Mustapha, fiye da yanda nake son kaina, jiya ma ya Habeeb yake cemin, zasuxo Anjuma su gaishe ki. " Okey Allah ya kawo su lfy. Da Ameen RAUDA ta amsa sannan sukaci gaba da zancen Duniya. Menene Asalin Mustapha? Menene alaƙarsu da RAUDA? Menene Dangantakar su da ƙauyen su Indo? 🤔🤔🤔🤔🤔 *Dangantakar su* Alhaji Mamman babban limami ne, a cikin ƙauyen *DASINA* mutum ne mai karancin da mutunci, ana girmama sa, sosai cikin wannan garin, Yana da matar sa ɗaya mai suna Harira yaran ta suna kiran ta da INNAH, yaransa biyu, Haruna shine babba, sai Hindu wacce ake kiran ta da Hinde a cikin ƙauyen, Mlm Mamman takaka ne sosai, wani sa'in abincin da zasu Ci ma gagarar su yake, kasancewar ya samu matar rufin Asiri, bata taɓa nuna gajiyawar ta akan Rashin Abincin gidan Mlm Mamman ba, haka zata san dabarar da zatayi, yaran ta, su sami Abinda zasu Ci, maƙocin Mlm Mamman, Mlm Hadi mutum ne, mai kyautatawa maƙoncin sa, duk da shima bawai yana dashi bane sai dai rufin Asiri, amma yawanci idan yayi cefenen gidan sa, to sai yayiwa, Mlm Mamman, zumunci ne mai ƙarfi tsakanin su, matan Mlm Hadi, Safiya, da Rabi, suna zumunci sosai da INNAH, musamman Rabi, kusan zaka iya kiransu ƙawaye da INNAH, Rabi tana da ɗanta ɗaya mai suna Musa, Musa da Haruna ɗan Innah kusan komai tare suke yinsa, shaƙuwace mai ƙarfi, tsakanin su. Tafiya suke suna, zance, dawowar su kenan daga, makarantar Allo, Haruna ne yake cewa Musa. " Musa ina ganin fah xan tafi birni neman kuɗi, dan kaga mun gama Secondary School, Bamu da Halin da zamuje gaba da Secondary, Kuma gaskiya ni, ina da burin cigaba da karatu, kodan na taimaki rayuwar iyaye na, da ƙanwata. Shiyasa na yanke wannan shawarar, idan kaima kana da wannan burin, sai mu haɗa hanya. Shuru musa yayi kafin yace. " Gaskiya Haruna ni bani da burin cigaba da karatun Boko, iya Secondary ɗin ma, da nayi ya isheni, gara na nemi sana'a na fara, tunda kai kayi niya, kaje ka, Allah ya baka Sa'a yasa ka shiga, birni a Sa'a. " Shikenan Musa na gode sosai, kuma baxan taɓa manta Addu'ar ka gare niba, Haka Abotar ma baxata taɓa yankewa ba. Har suka iso gida tattaunawa suke kan tafiyar Haruna birni, da la'asar Haruna da musa suka sami iyayen su, a majalisar su, na dattawa da maganar tafiyar, Haruna birni, domin neman kuɗin da zaici gaba da karatunsa, da farko Mlm Mamman yaƙi, yarda, da tafiyar Haruna birni, sai da Mlm Hadi yasa baki tukunna, nan ma daƙyar mlm Mamman ya Yadda, bayan ya amince masa ne, suka nufi wajen Innah, domin sanar da ita, dan shi Haruna a niyarsa gobe yaƙe son wucewa, birni. A zaune suka sami Innah bakin murhu tana iza wuta, tsugunnawa sukayi, tare da mata barka da gida. Kallon su Innah tayi tace. " Musa kune tafe yanxu, ya Rabin take. " Lafiyar ta ƙalau Innah, tace ma na gaida ki. "Ayya Ina amsawa, Haruna ka shiga ɗaki na akwai abinci rufe ku ɗauka kuci koh. Da to Haruna ya Amsa tare da cewa " Innah idan kin gama, muna son zamuyi magana ne, dake. " Ba damuwa kuje kuci abincin ina zuwa nima. Bayan sun gama cin abincin ne Innah ta shigo cikin ɗakin, tare da zama. Musa ne ya dube ta, tare da sanar da ita ƙudirin Haruna, na son zuwa burni neman kuɗi, ya kuma sanar da ita yanda sukayi da Mlm Mamman. Innah bata wani hanasa ba, illa ma cewa da tayi. " Tunda har Mlm ya yarje maka, ni babu abinda zance, sai dai a duk inda kake Haruna ka kasance mutum mai ruƙe amana tare da haƙuri, ka kuma ji tsoron Allah, ka zauna da duk mutanen da kayi tarayya dasu, Allah ya baka Sa'a yasa ka sami Abinda kaje nema, kake zayartar mu, duk lokacin daka samu zama, hakanne zai nuna mana kana lfy. Haruna yaji daɗin addu'ar mahaifiyar sa sosai, cikin farin ciki da murna suka fice daga cikin gidan. Washe gari da safe Haruna ya ɗauki dangwalin sa, tare da yiwa ƴan uwa da abokan Arziki sallama, har bakin gari, Musa ya raka Haruna da ƙyar suka iya rabuwa cikin kewar juna, kafin musa ya dawo cikin ƙauyen shi kuma, Haruna ya kama hanyar tashar mota domin hawa motar da zata kaisa birni. Cikin sa'a kuwa Haruna ya shiga birni da farko ya fara sana'ar sharan shago ne a kasuwa, a biyasa ɗari hamsin, a wuni yana samun Dubu biyu kullum, na sharar shagon, akwai Ranar da Haruna yake yiwa Wani Alhaji sharan shago, sai tsinci kuɗi, wajen dubu goma rafar su, komawa Haruna yayi ya kawowa Alhajin kuɗin yace gashi tsinta yayi, yana masa shara, shiko Alhajin ashe da sanin sa, ya ajiye kuɗin domin ya gwada amanar Haruna, kasancewar yana son ɗaukar sa yaron shago, Alhaji muktar yaji daɗin samun, Haruna daga cikin masu Amana, daga nanne fah ya ɗauki, Haruna, yaron shago suna saida Atampopi, akwai ɗan Alhaji muktar, Bello, zai ɗan girmi Haruna kaɗan sanshi a lokacin ma yana da mata, muktar da Haruna, jinin su ya haɗu sosai, shaƙuwace mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu, inda kullum suke tare. Akwana a tashi Babu wuya wajen Ubangiji, Alhaji muktar ya yadda da amanar Haruna sosai, inda hakan tasa ya ɗauke sa ya kaisa gidan sa da zama, tare da sashi, kawo takaddun sa, ya nema masa University. Alhamdulillah Rayuwar birni tayiwa Haruna daɗi, tunda gashi, yana sana'ar sa, kuma yana zuwa makaranta, haka ƙauyen suma yana kaimu musu ziyara sa'i da lokaci, bai Kuma manta da abokin sa, Musa ba, inda yakan yawan nasa Alkairi. Haruna cikin nasara ya gama karatunsa inda ya fito da good result, wato first class, Babu ƙyashi Alhaji muktar ya basa Aron kuɗi kimanin, 20 millions yace ya buɗe shagon sa na kansa, idan yaso yake biyansa kuɗin sa da kaɗan kaɗan, Haruna yaji daɗin alkairin da Uban gidan nasa ya masa. Cikin ikon Allah, kasuwa rake jawa Haruna inda ya samu ninkin kuɗin da Alhaji muktar ya basa aro a cikin shekara ɗaya. Fili Haruna ya saya tare da fara ginawa, ya kuma fara neman, Auren A'ishah wacce suka haɗu da ita taxo siyan zani shagon nasa, soyayyah mai ƙarfi ne ta shiga tsakaninsu. Cikin ikon Allah kuma yayi nasarar samun Auren, A'ishah, inda Alhaji muktar shine ya karɓi Auren bisa umarnin Mlm Mamman, ƴan ƙauyen Dasina suka zo Aure. Harda Musa ma ya sami Halartar Taron ɗaurin Auren. Bayan shekara Uku. A'ishah matar Haruna ta haifi yaranta, maza kyawawan gaske, Hatta Hajiya Innah ta halarci wannan sunan, inda yara sukaci sunan, Muhammad Mustapha, da Muhammad Habeeb. A lokacin ne kuma Musa Nasa Auren ya tashi, Haruna kusan shine yayi hidimar bikin, Musa, Tare sukaxo da matar sa A'ishah, da ƴan biyun sa, sunan matar da Musa ya Aura Maryam itama ƴar cikin ƙauyen nasu ne, bayan bikin ne Haruna suka koma cikin Birni, da matarsa A'ishah. Inda ya buɗewa Musa shagon sai da kayan tireda. Acikin wannan shekarar ne, Allah ya ɗauki Rayuwar mahaifin su Haruna da mahaifin musa tsakanin su sati ɗaya ne kacal, sunji zafin mutuwar sosai, Innah kuwa tasha kukan ta, har ta godewa Allah. Haruna ya ɗauki kanwar sa, Hindu ya koma da ita birni yaso ya tafi da Innah, amma Innah taƙi, tace Babu inda zata, a barta anan ƙauye har mutuwar ta. Bayan shekara biyu da mutuwar mahaifin Haruna, ya biya musu kujerar hajji, dashi da Innah da kuma matarsa A'ishah, suka sauƙe falari, a cikin shekarar. Ƙanin Alhaji muktar, Usman shine ya auri Hindu, inda ya tafi da ita birnin Istanbul kasancewar acan yake aiki. Shekaru sunja rayuwa sai tafiya take, yanxu ƴaƴan A'ishah biyar bayan ƴan biyun ta na farko, ta sake haihuwar Mace mai suna Sharifa sai kuma ta sake yin wasu ƴan biyun, ishaq da Sharif, inda zumuncin Haruna da Bello tayi ƙarfi sosai, har ta kai ga Bello yakan ɗauko ƴarsa RAUDA ya kawo ta weekend, gidan Alhaji Haruna, Inda ita kuma RAUDA ta taso da tsantsan ƙaunar Mustapha, wanda shi yake ɗaukar hakan a matsayin, Hauka take yi. A lokacin su mustapha sun gama karantunsu a ƙasar London, har sun kama aikin su, inda Mustapha ya karanci Lawyer shi Kuma Habeeb ya karanci medical doctor, Hospital ɗin da Habeeb yayi practical, suka ɗauke sa. Aiki Shima Musa yanxu yana da yaran sa, biyar, Tanimu, INDO, jummalo, Abubakar sai kuma Haruna mai sunan Abokin nasa. Haruna da iyalansa suna ziyartar mahaifiyar sa, sosai wacce yanxu suke kira da Hajiya Innah. Wannan shine tushen labarin su. Ku biyo Alƙalami na gobe insha Allah domin komawa cikin labarin *INDO A BIRNI*. *Share* *And* *Comment* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/8, 5:26 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ T̸͟͞O̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya.🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 🙏🏻🙏🏻🙏🏻😩😩😩😩 Ya Ubangiji ina roƙo gareka daka sa *Farisa* ƴar sister Ladingo marubuciyar matar GwamnaTana hanu na gari, Allah ka kareta a duk inda take, ka Bayyana ta cikin gaggawa. Ameen 🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻 *P*•••••••1️⃣3️⃣ ➡️ 1️⃣4️⃣ *Mu Dawo cikin labarin mu* 🏃🏻‍♀ Yau Indo tun dawowar ta daga makaranta, ta nemi Ruwa a baho da dutsin goge kaushi, ta jiƙa ƙafarta, yayin da kuma reza ke riƙe a hanun ta tana yanke farcen ta, ita dai Mama tana tsaye gefe tana kallon ikon Allah, ɓarawo da bacci, wai yau Indo ce ke yanke, farce harda gugar ƙafa, yarinyar da ko zaka mutu kana cewa Indo wanke ƙafarki baxata wanke ba, sai dai ki mutun, bare kuma gugar ƙafa, yau kuma sai gashi ita ɗayan ta, tanayi ba tare da kowa ya sata ba, bayan ta gama yanke farcen Hanun nata ne, sai Kuma tahau gugar ƙafa, cikin mamaki Mama ke kallon ƙafar Indo, yanda ta fita fes, Babu wani alamar kaushi, ashe daman datti ne, yasa kafar Indo fita hayyacinta, yanke farcen ƙafarta, tayi, sannan ta dubi Mama tace. " Mama tsammin Omo na wanke kayina dan Allah, ina son zanje gidan Laure ne, kitso Anjuma. Zaro ido Mama tayi tace. " Me kika ce, zaki kitso gidan Laure, ke ɗin kuma yau Indo, kece zakiyi kitso. Dariya Indo ta kwashe dashi tace. " Eh wlh Mama, Mlm Sani yace idan na yanke farce na, nayi kitso, ba ƙaramin kyau zanyi ba, sai nafi duka ƴan matan garin nan kyau, tana fari da Ido take yiwa Mama maganar, kuma yace gani ƴar ɗagwas ɗagwas kyakkyawa son kowa ƙin wanda yarasa,. Dariya ce ta suɓucewa Mama ganin yanda Indo ta dage, wai a dole ita kyakkyawa ce, haba ai daman wannan tsaftar bata Allah da Annabi bace, dole da biyu, cikin dariyar Mama ta nunawa Indo gun wanke wanken ta, tace " Jeki ki ɗauko gashi can kixo na wanke miki kayin, tsifar ma ni sai nayi miki, Mlm Indo kyakkyawar garin nan, Mama ta faɗa tana cin dariya. Indo dai bata Wani damu da dariyar da Mama ke mata ba, ta shige ta ɗauko Omon, tas Mama ta wanke mata kayin tana zolayar ta, tsifa Mama tahau yi mata, gashin Indo yana da masifar tsayi, ga yawa, kuma yana da ɗan tauri kaɗan, runtse idon ta, take, tana jin zafin yanda mama ke figar gashin nata, cikin fara gajiya da jin zafin tace " Mama ki daina min da mugunta Mana, wannan ai mugunta ce, sai jamin kike da ƙarfi. " Nice kuma nake miki muguntar Indo, cewar Mama. " Yo to Mama, gani nayi sai jamin gashi kike da ƙarfi, dole nace munguta mana, ai sai kimin a hankali, Allah kika cigaba da jamin gashi zan fasa kitson ma, sai nabar gashin a haka. " Wannan shegen taurin gashin naki, daya kusan wata biyar baiga kitso ba, ai dole aja shi da ƙarfi, idan kuma bakya so to sai na ƙyale ki, adunga miki kallon ƙazama, mummuna, kinga yanxu ma yanda kika fito fes dake ƴar ɗagwas ɗagwas kyakkyawa. Ta ƙara zugata. Washe baki Indo tayi tace. " Wasa fah nake miki Mama, kedai ita jan gashin zanyi hkr, kuma wlh Mama yau har ƙunshi zanyi, a gidan Hajiya Innah ma zan kwana nayi ƙunshi na, mai shegen kyau, bari ma jummalo ta shigo na aiketa gidan su Zainabu ta siyo min gam ɗan yanka, ina zaki bani kuɗin koh Mama harda na kitson ma. " Dole na mah kuwa, ai yau komai kike so zan baki shi cikin gidan nan, Hajiyar kyau. Jummalo da ta shigo gidan ne, ta ga Indo anyi fes, sai faman tsifa suke yi, dariya ne yaso ƙwace mata, amma sanin Halin Indo da tayi kamar yunwar cikin ta yasata maida dariyar ta ciki, tasan tana dariyar nan, to yau kuma ta shiga Uku mai kwatarta hanun Indo sai Allah, ƙara sowa tayi wajen nasu tare da cewa. " Ganan aiken naki nan, Mama wai inji innar talatun kuma, ki aiko da kuɗin dashen naki, harda na wancan satin. " Kinga jummalo shiga ɗaki, cikin samira ta, na ukun nan akwai kuɗi ciki, ki ɗauko dubu ɗaya, ki kawai innar talatun, kixo ga ashirin ki karɓowa, Indo gam a wajen Goggo Hali. Cikin mamaki Jummalo tace, " Gam kuma Mama, me Indo kuma zatayi da gam, chap Abun mamaki, wai da gaske ƙunshin nan zakiyi ne. Ko kafin Mama ta bawa jummalo Amsa Indo ta mayar mata da cewa. " *Ubanki zanyi da Gam, kinji shegiya dai, har wani tambaya ta kike mai zanyi da gam har da wani mamakin ki, to kyau zan fuki dan uban.............* Buge bakin Indo da Mama tayi ne ya hanata karasa maganar tata. " Wai Indo me yasa baxa kiyi hankali bane, yanxu uban naku kike zagi dake ke baki da mutunci, kedai ba'a zama dake lfy wlh, sai kin nemo masifa, yanxu dan ta tambaye ki, shikenan sai ya zama laifi. Tura baki Indo tayi tace. " Tambayar Rainin wayo fah tamin, kuma na rantse da Allah, sai na yiwa jummalo shegen duka yau cikin gidan nan, badai kin daki baki na akanta ba. Sake mata kai Mama tayi,tare da cewa. " Tashi kije ki kashe ta, baki dake ta, ba tunda ke baki da mutunci, kuma naga wanda zai biya miki kuɗin gam ɗin dana kitson, marar mutunci. Cikin Rau Rau da baki Indo tace. " Idan kin hanani sai me, *ko a kwalar Rigata tunda Innah tana duniya ai dai baxan ga baƙin ciki ba, ehe* Kan jummalo tayi da gudu yayin da itama jummalo tayi waje da gudu, Rufa mata baya Indo tayi, kira Mama take ƙwala musu, amma basu ma san tanayi ba. A kofar gidan, Ɗan Birija, Indo ta ritsa jummalo da duka, sai kokuwa suke yayin da yara suka cika suna musu waƙa. Jin hayaniya da Ɗan Birija yayi ne, ƙofar gidan sa, ya sashi fitowa, Indo ya gani tasa JUMMALO gaba sai duka take, kamar wacce ta samu jaka, kasancewar ƙarfin su ba ɗaya ba, ya indo tafi ƙarfin jummalo. Da ƙyar Ɗan Birija ya ɓanɓare Jummalo daga hanun INDO, huci Indo take tana cewa. " *Ko yanxu kinji A jikin ki, harda dukan Asarar kuɗin da Mama zata bani, kika min bakin ciki na miki, gobe ma ki sake shiga safga ta*. Juyawa jummalo tayi tana zabgar kuka, ta koma gida, yayin da ita kuma Indo tayi hanyar gidan Hajiya Innah tana zagin ɗan birija ƙasa ƙasa, ya jita sarai amma ya ƙyaleta saboda yasan ba kunya gareta ba, ta basa Kunya cikin mutane ba abu bane mai wahala wajen ta. " Innah !! Innah !! Innah !! Innah dai wai ina kika shiga, ina kiran ki, kinyi shuru, idan baxaki amsa ba, sai nayi tafiyata Wlh. Innah da ta fito daga banɗaki ne, tace. " To Uwar ƴan marassa hakuri, saboda ina tsoron ki, Uwata karki tsine min na shiga duniya, sai na taka dokar Ubangiji na amsa miki ina daga cikin banɗaki, Uwar ƴan mita. " Mtss, wannan kuma matsalar kice, ni yanxu kuɗi zaki bani na tafi kitso gidan Laure kinga na yanke farce na, Idan na dawo daga kitson kuma zaki bani Lalle na ƙunsa. " Muje ɗaki na baki, yau kuma aljanun tsafta ne, kenan suke kusa. " Kinga Innah idan zaki bani ki bani, idan baxaki bani ba, shikenan, sai na haƙura, basai kin tsaya kina jero min magana ba. "Muje nace ai na baki ko, Uwar marassa Kunya. Tura baki Indo tayi, suka shiga, Innah ta bata ɗari ɗaya. Ficewa Indo tayi tana cewa Innah sai na dawo. Adawo lfy Innah ta mata, bayan fitar indon ne Innah tace. " Ikon Allah yau kuma A indon ta take, to Allah dai ya raba yaran gari da shiga gonar ki, dan Wlh yau duk Wanda ya shiga gonar ki yau baxai fito lfy ba. *Dutse local government* Sai wajen ƙarfe tara na dare, su mustapha suka shigo cikin gidan, tare da mahaifin nasu Alhaji Haruna. Zubewa mustapha yayi saman kujera tare da cewa. " Wash Allah Wlh yau na gaji Momy, kaina ke ciwo. " Momy gaskiya Rayuwar ɗanki akwai gyara cikin ta, ace mutum shi a rayuwarsa baya ƙaunar Hayaniya, tun ɗaxu yake mita, cikin kasuwar nan. Cewar Habeeb. Daddy ne yayi murmurshi cikin ƙaunar yaran nasa, yace. " A'a Habeeb bana son takura, kasan dai kowa da yanayin sa, dan haka karka takura min Yaro. Dariya Mustapha yayi tare da cewa, " Yawwa daddy gaya masa dai ko zai gane, tunda ya kasa fahimta ta, har yanzu. Tsumewa Habeeb yayi, tare da tura baki yace. " Na dai gane cikin gidan nan, ba'a sona anfi son mustapha, RAUDA kawai ke kulawa dani cikin gidan nan. Dariya RAUDA tayi tana satar kallon Mustapha tace. " Sannu da dawowa Daddy. " Yawwa sannu RAUDA, ya kike jin zaman gidan namu, ina fatan dai baki da wata matsala, idan akwai kuma kiyi gaggawar sanar dani, domin magance miki shi. Shuru RAUDA tayi tare da duban mustapha tana jin a cikin zuciyarta kamar ta sanar da daddy buƙatar ta, na son Auren Mustapha, sai dai kuma tana jin nauyin Daddy baxata iya sanar dashi wannan zancen ba. " Babu wata matsala daddy, ina jin daɗin zaman cikin gidan nan sosai. Alhamdulillah daddy yace, haka ake buƙata. Kallon Momy yayi yace. " A'ishah muje ki haɗa ruwan wanka ina son zan kwanta da wuri, bacci nake ji, kai kuma Habeeb, karka wuce DASINA ba tare da mun haɗu ba, saboda akwai saƙon da zan baka. Da to Habeeb ya amsa sannan daddy suka haura sama shida Momy. RAUDA ce tace. " Ya Habeeb ganan abincin naka yana daining. " Yawwa RAUDA na gode sosai bari na cika tunbi na kafin na haura sama, wannan bawan Allahn kan sunci abinci da Momy ta aika kasuwa, ya nuna Mustapha da hanu. Taɓe bakin sa Mustapha yayi tare da cije lips ɗinsa, ya tashi yana ƙoƙarin haurawa sama, sai idon sa ya hango masa Sharifa tana zaune tasa, su ishaq da Sharif gaba sai buga games suke, tsawa ya daka masu. " Keeeeeeee. A gigice su Sharifa suka ɗago idon su, jin muryar Dodon nasu Mustapha, Uban ƴan takura, cewar Sharifa. " Uban me kuke Anan, yanxu. Shuru sukayi, suka kasa ce masa game suke yi. Tsawa ya ƙara daka musu a karo na biyu. " Ba magana nake muku bane kunyi min shuru. Cikin rawar murya Sharifa tace. " Game muke yi. " Game kuke yi, ya maimaita maganar, amma me nace muku kuke yi daidai wannan lokaci? " Karatun ƙur'ani ta mayar masa da Amsa. " Okey shine saboda kun Raina ni, shine kuke Game koh. " A'a yaya kayi hkr zamu ɗauko littafin yanxu muyi karatun baxamu sake ba. Shigewa yayi yana cewa. " Kuma sake kuga matakin da zan ɗauka a kanku cikin gidan nan. Ajiyar Zuciya Sharifa ta sauke ganin sunsha, dariyar Habeeb taji a daining yana cewa. " Barrister Mustapha babban yaya, Ango na RAUDA. Murmurshi RAUDA tayi jin daɗin sunan da Habeeb ya kira, *ANGON RAUDA* Allah ya tabbatar da bakin ka, RAUDA ta ayyana a Zuciyarta. Wayyo Allah sister's kuyi hkr da wannan, Wlh naso nayi muku typing yafi haka yawa, sai dai uzuri sunyi min yawa yau akaina. 🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻ya Ubangiji ina roƙo gareka daka bayyana ƴar gidan Ladingo, wato Farisa, Allah kasa tana hanun na gari, ba mungu ba, Allah ka bayyana ta cikin gaggawa. 🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻 *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/11, 3:49 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty Fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *Ina ƙaunar ku masoyana* Na gode sosai da ƙaunar ku gareni, kwana biyu kawai da banyi typing ba, kun damu sosai, har ta privet masoya ke min magana, wasu kam ma bansan group ɗinsu ba, gaskiya na gode sosai, hakan ya nuna min yanda kuke ƙaunar wannan book ɗin. *P*•••••1️⃣5️⃣ ➡️ 1️⃣6️⃣ Yana shiga ɗakin nasa wanka ya faɗa, Bayan ya fito daga tollet ɗinne ya mulke fatar jikin sa, da mai da turare, sannan yasa gajeren wando Wato 3cutter da best sannan ne ya faɗa saman gadon sa, tare da jawo system ɗinsa, ya buɗe, yana jin shigowar, Habeeb bai ɗago kansa ba, shima dai Habeeb bai kulasa ba, saima shigewa wanka da yayi, bayan ya shirya ne, ya dawo saman gadon nasu ya faɗa, tare da rufewa, mustapha system ɗinsa, sai a lokacin mustapha ya ɗago ya kalle sa, yace. " Ya haka Malam, da rufe min system? " Saboda Magana nake so muyi dakai. " Okey ina sauraron ka, Allah yasa mai amfani ce, nasan Halin ka, da zolaya, domin itace ɗabi'ar ka. Murmurshi Habeeb yayi, tare da cewa. " Wannan maganar mai muhimmanci ce, mustapha. "Okey ina sauraron ka. " meyasa kake nunawa kamar baka san RAUDA na Sonka ba? Wannan yarinyar fah tayi nisa a cikin Sonka, amma kai nunawa kake bakasan tanayi ba, Bayan kuma nasan Kasan tana Sonka, ka sani fah walaƙanta ɗan adam baida amfani duk mai Sonka yafi maƙiyin ka, ko yaya yake, komai kuma muninsa, bare kuma RAUDA bata da wani muni daga fuska har dirin jikin ta. Why mustapha, Please Answer my Questions? Cije lips ɗinsa yayi, wanda ya zama masa jiki a rayuwarsa, yana son cije lips ɗinsa, magana ya fara. " Saboda bana sonta, bata min ba, nifa kaga RAUDA bata daga cikin kalar matar da nake bukatar aura, sannan kuma bata da aji tunda har zata iya furtawa namiji cewar, tana sonsa, mace mai aji neman ta, ake ace ana sonta ba, ita bace zata nema tace tana son. Da kake maganar diri, koka manta da cewa shi so Babu ruwan sa, da kyau ko muni, idan kana son mutum baka ganin munin sa dan haka ni kyan mace ko munin ta, baya daga cikin ra'ayina nafi son mace mai kamun kai da nutsuwa tare da ilimin zamani dana Addini, idan har na samu mace mai wannan suffar komin munin ta, zan iya Auren ta, idan har ina sonta, sai amsar tambayar ka, ta ƙarshe itace, bani nace ta soni ba, bare kuma har tayi zurfi cikin soyayya ta, wannan damuwar tace ba tawa ba, idan kana tausayin ts mai zai hana kai ka Taimake ta, ka Aure ta, ai ina ga kamar Babu banbanci tsakanin mustapha da Habeeb, dukan su Abu ɗaya ne, kaga kuwa duk wanda yaso mustapha dole zaiso Habeeb, kodan tsantsar kaman dake tsakanin mu. Murmurshi Habeeb yayi cikin jinjina tsatstsauran ra'ayi Irin na, Mustapha, shi wlh yana mungun tausayin RAUDA, domin kuwa yasan ba ƙaramin so take yiwa mustapha ba. " Kai take so ba Habeeb ba, kamar muce kawai ɗaya, amma halayyar mu, ta banbanta, wata ƙil badan kyan fuskar ka take sonka ba, wata ƙil tana sonka dan wani abu dake tattare dakai may be yanayin kane yake burgeta, kokuma Halin ka, ko kuma haka kawai take sonka, amma tunda kace, Allah ya zaɓa muku Abunda yafi Alkairi. Ameen Mustapha yace tare da jawo system ɗinsa ya buɗe, yana cewa Habeeb. " Shiyasa fah jiya da kace muje gidan su, ka gaida Mamy nace maka baxan jeba, Saboda wannan shegiyar ƙanwar Tata mai shegen bakin tsiya, kana zuwa zata fara tambayar ka, ya soyayyar ka da RAUDA kamar ni nace mata ina soyayya da RAUDA. Dariya Habeeb yayi yace. " Ni kam ai zanje na gaishe ta, dole na, kodan yawan kira na da take a waya, tace min idan ta kira ka, baka dagawa sai kaga dama. Dariya shima mustapha yayi, tare da cewa. " Haka tace maka kenan, Duk kiran da zata min akan damuwar ƴarta ne, shiyasa ban damu da ɗaga kiran ta ba. " Allah sarki Habeeb yace, tana taya ƴarta neman soyayyar kane, shiyasa, kasan uwa da tausayin ɗanta. Ni ya maganar case ɗin khabeer da uwarsa Momy sarah ne, naji SADIQ yana cewa court ɗinku zai kai su? Danni rabona da khabeer tun sanda yaje London kamo wani Alhaji. Ɗago kansa Mustapha yayi, ya kalli Habeeb kafin yace. " Wlh banda masaniya dan gaskiya na daɗe, rabona da khabeer, tun randa mukaje gaishe sa, daya kwanta rashin lfy, wajen shekara ɗaya kenan. " Daman can ba shiri kuke ba, kaga bari na kwanta, dan mun daɗe muna hira har 12. " Allah ya tashe mu, lfy nikam ba yanzu ba, sai na gama aiki na, akwai wani bincike da nake yi. Itako RAUDA ta kwanta tayi lamo akan gado, ta rasa meke yiwa rayuwar ta daɗi, pic ɗin mustapha ta zubawa ido wanda ta tura a wayar Habeeb, ta daura kan wayar ta, wannan wacce irin soyayya ce nake maka Mustapha, soyayyar ka ta zama cuta ce a gare Ni, why !! why !! why baka sona, menene bandashi menene Aibu na, daka tsaneni haka, Allah ka sassauta min soyayyar mustapha cikin zuciyarta, ko zan samu sauƙin ciwon dake damuna cikin ƙirji na. Ahaka bacci ɓarawo yayi nasarar capke RAUDA, cikin damuwar da take ciki na tsanar da mustapha ke gwada mata, inji ta da faɗa. Washe gari da safe, momy ta riga kowa tashi kasancewar zata yiwa Daddy breakfast, zai fita kasuwa da wuri, a kitchen ɗin RAUDA da Sharifa suka taradda Momy, gaishe da Momy sukayi ta amsa tare da cewa. " Sai yanxu kuka tashi kenan, dana biye ku, yau da saidai Daddyn ku, ya tafi kasuwa ba tare da yayi breakfast ba. Murmushi RAUDA tayi tace. " Ehh Wlh Momy, bayan nayi sallar Asuba ne bacci ya ɗauke Ni, kije ki zamu ƙarasa aikin, fita Momy tayi tana ce musu. " Kudai yi da jikin ku, dan daddyn ku zai fita kasuwa yau da wuri. Wajen wanke wanke Sharifa ta shige yayin da RAUDA ta tsaya kan girkin. Cikin 30 minute suka haɗa komai suka jera saman daining, Mustapha da Habeeb tare suka sauƙo, kafin Momy da daddy su fito suma. Gabaki ɗayan su, a daining suka haɗu yayin da RAUDA tayi seving ɗin su, kafin RAUDA ta iso kan Mustapha, yayi saurin cewa, Sharifa tayi seving ɗinsa, ɗago kanta RAUDA tayi cikin jinjina irin ƙiyayyar da mustapha ke gwada mata, wato tsabar tsana, abincin ma, bazan zuba masa ba, duk motsin Mustapha akan idon RAUDA ne, yayin da shi kuma ko inda take bai kalla ba, bayan sun gama breakfast ɗin ne, RAUDA tacewa daddy, " Daddy ina son Anjuma zan koma gidan mu. Kafin Daddy yayi magana Momy ta rigasa ta hanyar Cewa. " Zaki koma gida kuma RAUDA, keda kikace zakiyi mana sati biyu, kwatakwata fah kwanan ki biyar ne, shine kike zancen komawa gida, kodai akwai Abunda muke miki ne, idan akwai ki faɗa mana. Cikowa idon RAUDA yayi da hawaye, ita har ga Allah babu wani Abunda suka mata, kawai gajiya tayi da kallon tsana da wulaƙanci da Mustapha ke mata, gara kawai ta koma gidan su, ko zata samu mafita wajen mahaifiyar ta. " Babu Abunda aka mini Momy kawai dai zan koma gida ne. " Kin tabbata Babu Abunda aka miki RAUDA, cewar daddy. " Wlh Babu komai daddy kawai so nake na koma gida. Ɗago kansa Habeeb yayi yana kallon RAUDA cikin tuhuma, kasancewar yasan dalilin daya sa, zata koma gida, sunkuyar da kanta ƙasa RAUDA tayi, ta ɗauke idon ta, daga na Habeeb, shi Kuma Mustapha yana jinsu, bai ɗago kansa ya kalle su ba, bare ma susa ran zaiyi magana, tashi yayi tare da cewa su Momy. " Ni zan shige office, Habeeb ka gaida Hajiya Innah idan kaje, sai Allah yayi dawowar ka. " Okey Babu damuwa zataji. Cewar Habeeb, amma baxaka tsaya mu fita tare ba. " A'a hanyar mu ba ɗaya ba, kawai Allah ya kiyaye hanya. Daddy ne, ya tsayar da mustapha ta hanyar cewa. " Ka tsaya RAUDA ta shirya sai ka sauƙe ta, a gidan su, kafin ka shige office ɗin. Ɓata ransa mustapha yayi, yace. " Daddy ni na riga na shirya, zan shige office kuma sauri nake yi, tunda ga Habeeb zai fita bai shirya ba, idan yaso saita jirasa ya sauƙe ta. Momy ce tace. " Habeeb baxai sauƙe ta ba, kaiɗin kaine zaka sauƙe ta, ka zauna ka jira ta har ta shirya, sai ku fita tare. " But amma Momy...... Ɗaga masa hanu Daddy yayi tare da cewa " Ya isa ka zauna ka jirata, ke kuma RAUDA jeki shirya maza karki ɓata masa lokaci. Tashi RAUDA tayi tare da haurawa sama yayin da Mustapha ya bita da kallon ƙiyayya, da kuma harara. Ran Mustapha idan yayi dubu toya ɓaci, akan me za'a zaunar dashi ace dole saiya jira wannan abar, shiya kawota gidan ne, koko zaman sa take cikin gidan, Habeeb ne, yazo daidai kunnen sa ya sunkuya, tare da cewa. " Ka zauna kayi jiran Amarya yaro, don naga alama momy na sonka da RAUDA, sai kayi hkr, ka zauna jira. Yana gama fadar haka ya ɗaga kansa tare da haurawa sama, yana yiwa Mustapha dariyar mugunta, harara mustapha ya bi Habeeb dashi ba tare daya tanka masa ba. Har Habeeb ya fito, Daddy ya basa saƙo wajen Mlm Musa da Hajiya Innah, tare suka fice da daddy suka bar Mustapha Zaune yana jiran RAUDA. Momy ce ta tashi tare da cewa, bari na haura sama naga maiya tsayar da RAUDA haka tun ɗaxu. Shidai Mustapha baice komai ba, yana Zaune cikin haɗa fuska, yana ganin RAUDA da Momy suna sauƙowa, ya ɗauko baƙin glass ya manna a idon sa, tare da ficewa waje, cikin motar ya shiga ya zauna jiran ta, har bakin motar Momy ta rako RAUDA, tana cewa. " To RAUDA ki gaishe da Hajiya Turai ɗin kice Mata, ina zuwa nima insha Allah, Allah ya kiyaye hanya mun gode sosai. " Zataji RAUDA tacewa Momy, sannan ta buɗe gaban motar ta shiga, jan motar mustapha yayi ba tare daya kalleta ba. Ƙira'ar malam Ibrahim Abdulrasheed Mustapha ya kunna cikin wayar yana bi a hankali. Muryar RAUDA yaji tana cewa. " Ya mustapha meyasa baka sona, menene Aibuna, kasan irin soyayyar da nake maka kuwa.......? " Enough RAUDA, bana buƙatar jin muryar ki, cikin motar nan. " Saboda ka tsaneni baka sona koh, dole ai kace nayi shuru, wani irin tsanane wannan, kodan nace ina sonka shine kake wulakanta Ni. Dariyar takaici Mustapha yayi, tare da yin wani wawan burki, cikin tsawa yace, " Fita min daga cikin mota, ki fita min nace daga cikin mota, sau nawa zan faɗa miki cewa bana sonki, ko ana soyayyar dole ce, fice min daga cikin mota. Murmurshi mai ciwo RAUDA tayi tare da sa hannun ta, ta buɗe motar ta fice, cikin tsanar Zuciyarta data ke son Mustapha. Tsuka mai ƙarfi Mustapha yayi, sannan yaja motar sa, tare da bule RAUDA da ƙura, yayi gaba abunda. Share guntun hawayen daya cika mata Ido tayi, tare da tare mai adaidaita sahu. *DASINA* A hankali INDO take tafiya, ita a dole tasha gayu, ansha lalle da kitso harda, wanka aka sha, tafiya take a hankali, wai zatayi tafiyar ƴan gayu, wani yaro ne ya taho da bokitin ƙullin koko, a kayin sa, sanda yazo daf da INDO cikin tsautsayi, yayi tuntuɓe da ƙaton dutse, sheƙowa ƙullin kokon yayi gaba ɗaya jikin Indo ya wanke mata jiki, tun daga kayi har ƙafifin ta. " *Kutumar Uba* dan ubanka tsinanne, shine zaka min wanka da ƙullin koko, tsabar kana baƙin cikin nayi wanka, to wlh yau sai naci kutumar ubanka, shaƙo wuyan sa, Indo tayi, haba wa, sai kokuwa, dakuwa suke sosai yayin da yara suka taru a kansu suna rera musu waƙa " *Ku tasu arna ku tasu ku tasu ba mai raba ku, kai mu raba ace munyi zamba, ku tasu arna, ku tasu dai ba mai raba ku* Aiko kamar zuga Indo suke yi, ta dage sai jibgar juna suke. Habeeb da shigowar sa kenan, cikin ƙauyen ya hango yara cike sai zabgar kokuwa ake, parking yayi, tare da fitowa daga cikin motar ya nufo wajen nasu. " Kai baku da Hankali ne, kuke kokuwa. Juyowa Indo tayi cikin masifa da rashin Kunya, wa zata gani idan ba Mustaphan ta ba, fit tayi shuru tare da sake yaron tana dariya, tace " *Tafi abunka kaci albarkacin masoyina mustapha jeka na tafe maka ya Mustapha yaushe ka zoka sannu da zuwa kaga yanxun nan Innah ta shiga cikin gidan mu bari na kira maka ita*. Zaro ido Habeeb yayi jin ta kirasa da mustapha, kuma masoyina, daga bayan sa yaji yara na cewa lallai yau tasi'u Allah ya ƙwace sa a hanun Indo. " *INDO Habeeb ya furta sai kuma ya kwashe da dariya tuno labarin Indo da mustapha yake basa, Ashe Itace ALJANAR MUSTAPHA LALLAI BARRISTER MAI ƳAN MATA KALA KALA*. __________________________ Bana typing Ranar asabar yauma ganin da nayi kwana biyu banyi typing ba, yasa na daure nayi muku🙏🏻 *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/13, 3:29 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take a gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*••••••1️⃣7️⃣ ➡️ 1️⃣8️⃣ Cikin dariya Habeeb yace wa Indo. " To jeki kira Hajiyan, idan kin kirata sai ki wanke jikin ki koh, dan kin Zama dodo. Sake baki Indo tayi tana kallon Habeeb cikin mamaki wai yau mustapha ne yake mata magana cikin sakewar fuska, mutumin da baya dariya, kullum cikin faɗa yake, ƙara leƙa fuskar tasa ta Indo tayi. " Lafiya kike leƙen fuska ta, cewar Habeeb. Wangale yellown hakwaren ta Indo tayi, tace wa Habeeb, gani nake kamar ba kai bane ya Mustapha, shifa ya Mustapha yana da faɗa kuma kullum cikin haɗewar rai yake, kai kuma naga kana dariya kuma baka faɗa. Dariya Habeeb yayi Yace. " Nine mana na sanja miki ne, Hajiya Indo. " *Aradun Allah ya mustapha ka sauya kodai ka fara sona ne, yanda kake min murmurshin nan dafe ƙirjin ta Indo tayi tace har ji nake wasu kifiyoyin sonka na harbi na, a ƙirji na, Wayyo Allah Wlh ya Mustapha sonka yamin ɗaurin huhun goro ina sonka ya Mustapha na dan Allah kaima kace kana sona ko zanji daɗi* Dariya sosai Indo ta bawa Habeeb dariya yake sosai, domin shi Wlh yarinyar ma, comedy ɗinta burgesa yake. Cikin dariyar yace. " Jeki ki kira Hajiyan ni na wuce, gidan nata idan mun sake haɗuwa zan gaya miki, motarsa ya koma yaja shi zuwa ƙofar gidan Innah. Da gudu Indo ta shigo cikin gidan har tana tuntuɓe. " Hajiya Innah !! Hajiya Innah. Innah da suke zaune da Mama suna firar duniya, tace. " Lafiya Indo kike min wannan kira kamar wacce kike bina bashi. Mamace tace. " Hajiya ai kinsan Halin Indo babu hankali sam a tare da ita, kullum cikin shashanci take, bata da nutsuwa sam. Tura baki Indo tayi tare da ɗaukar bokiti, tayi wajen randa tana cewa. " Ya mustapha ne, yaxo, shine yace na mishi kiran sa, idan kinga zaki iya zuwa kije idan kuma bazaki iya ba, Sai ki zauna ni dai wanka na zanyi naje *musha fira da masoyina*. Salati Mama ta ɗauka tana cewa. " Lallai Indo rashin kunyar taki ta shahara yanxu gaban mu kike kiran masoyi, Allah ya shirya ki, to waima ke a hakan za'a soki baki da hankali da nutsuwa, ga rashin mutunci, da fitsara, babu wanda baki iya ba, ciki, Babu mai sonki a haka. Dariya Hajiya Innah tayi tana cewa. " A'a maryama aiko INDO sai tafi ƴan matan garin nan farin jinin Samari kinga indodo na maza jeki kiyi wankan ki, rabu da maryama. " Ai nima Innah yau banda lokacin ta, bare naji haushin zancen ta tunda ya Mustapha yamin dariya Kuma yace naxo zaice min yana sona. Zaro ido Innah tayi tace mustaphan, ne yace miki haka, wannan ɗan bakin Halin tsiyar, ikon Allah, naga wata sabuwar yaudara gurin Muhammadu, anya ma kuwa mustapha ne, yaxo garin nan, gani nayi kwatakwata satin sa ɗaya da zuwa, amma ban sani ba ko ubansa Haruna ne ya aiko sa, maryama bari naje gidan na gani. " To Innah na gode a huta gajiya. Cewar Mama. INDO kuwa wankan ta, ta shige tabar Mama zaune tsakar gida. Da sallama Innah ta shiga cikin gidan Habeeb ta hango Zaune bakin ƙofar ɗakin ta, daga nesa itama INNAH tayi zaton mustapha ne, sanda ta ƙaraso daf dashi, taji Habeeb ya sureta yana hajijiya da ita, domin tasan shi kaɗai ne, mai mata wannan yahudancin, rufe idonta Innah tayi gam, tana zagin Habeeb. " Ka sauƙe ni dan ubanka Haruna, kaji ɗan iskan Yaro zai ƙarasa ni. Cikin dariya Habeeb ya sauƙe Innah tare da cewa. " Missing ɗinki nayi fah Amarya ta, an juma ba'a haɗuba, yanxu na ganki kuma ai dole na juyaki. Dariya Innah tayi tace. " Ja'iri Habibu aini nasan babu mai min wannan iya shegen sai kai, yaushe ka dawo ƙasar, kullum saina tambayi Muhammadu, kai sai yace min ai baka da Ranar zuwa ɗan albarka Ashe kaine kake tafe, ni fah nayi mamaki da naji Indo tace min Muhammadu ne yaxo. Dariya Habeeb yayi yace. " Nine nan Innah nayi nayi mustapha mu taho tare wlh wannan bawan Allah yaƙi, wai ba yanxu ba, ko dai kina basa ciwon kaine Innah. " Toni ina ruwa na, dashi idan yana soma karya ƙara zuwa waje na, daga nan har abada, dan ubansa. Dariya Habeeb yayi Yace. " Ni Babu ruwana a tsakanin ku, kunfi kusa, nine bare tsakanin ku, bari naje nayi wanka, akwai kaya cikin but ɗin mota, bari nayi wanka saina nemo yara su kwashe, yace akwai wanda za'a kai gidan Mlm Musa. To saika fito cewar Innah, ɗakin da mustapha yake sauƙa inda yaxo garin shima Habeeb nan ya sauƙa. Wanka Habeeb yayi tare da kwantawa baccin gajiya. Wanka Indo tasha fes da ita, ta taho gidan Innah, Innah tana zaune tsakar ɗakinta Indo ta shigo tana leke leƙen ta ina zata ga mustapha, ɗakin Innah taxo ta zauna tare da cewa Innah, ina yaya Mustapha yake. Dariya Innah tayi, tace. " To shasha wannan ba Muhammadun bane, Habibu ne, ɗan uwan haihuwar sa, kamace kawai suke, sai banbancin hali da suke dashi. " *Haba haba daman dai akwai walakin goro a miya, nidai nasan mustapha bai taɓa min dariya ba, wannan kuwa yana dariya, harma da kula mutum, kallon jikin ta, tayi yanda tasha wanka harda ɗige ɗige da tasha a fuskar ta, sai kuma tasa kuka 😩 tace yanxu kenan nayi wankan banxa, wlh danasani banyi wannan wankan ba*. Dariya sosai Innah tayi tace. " Yanxu ke INDO baza kiyi wanka danjin daɗin jikin kiba, sai dan wani, amma dai kinji kunya Wlh. Ƙara sautin kukan ta Indo tayi, tsakanin ta da Allah take kuka tana yiwa Innah masifa, cikin ɗaga murya. " *Ni ki ƙyaleni nayi kuka na, Wlh banyi niyan ƙara wanka ba, sai wani sati Ranar juma'a shine ya cuceni yasani nayi, har yasa naji kifiyar Son ya Mustapha ta sokeni ashe ba shi bane, Kuma wlh wankan Allah ya isa nayi, tunda banyi niya ba, kuma Innah kiga fah yanda na zage nayiwa fuska ta kwalliya, duk dan ya Mustapha yace nayi kyau*. Habeeb da tun sanda yaji hayaniyar Indo ta hanasa bacci ya fito, ya tsaya gefe yana kallon shirmen Indo, shi Wlh burgesa take idan tana wasu abubuwan. " To kukan ya isa haka. Taji Muryar Habeeb daga bayan su. Tsale Indo tayi ta diro gaban Habeeb tana ƙara sautin kukan ta, tana cewa. " *Baxan yi shuru ba Wlh yau wuni zanyi ina kuka, kuma Na wuni ina zan Allah ya isa, dan ancuce ni Wlh.* " 😆 Ikon Allah yau ni Habeeb ina ganin ikon Allah, to naji, idan kin wuni kina kuka ai kanki ma wuni zaiyi yana miki ciwo, to wai Allah ya isan wa kika jawa shi?. " *Kai kai na jawa Wlh, tunda kaine kayi kama da ya Mustapha na, shine harda cemin kaine ya Mustapha, ashe ƙarya kake min, KUMA NA JAMAKA YASIN DOGUWA, MAI JAN WANDO KUMA BULLUƘUTU BAƘAR MUTUWA TSAKANINA DAKAI ARADUN ALLAH BAN YAFE BA*. kaɗa kansa Habeeb yayi cikin jinjina yarintar Indo, Yace. " Badai akan mustapha kike jamin Allah ya isa ba, to zo na miki hoto saina kai masa gida yaga wankan naki, ba shikenan ba. Shuru Indo tayi tace. " A shagon waye zamuyi photon shagon salisu zamuje. " A'a a wayata zan ɗauke ki, wayar ya ciro daga cikin aljihun wandon sa, tare da cewa kin gani, fito waje na miki. Tana washe bakin ta, Indo, Indo ta fito, Innah kuwa haɓa ta riƙe tana kallon rashin mutunci da Indo ke tsulawa, Habeeb ya yiwa indo pictures wajen kala Uku kafin ya mata da Innah, sai kuma sukayi sulfie shida INDO, suka zo sukayi su Uku harda Innah. Cikin son zolayar mustapha Habeeb ya cewa Indo zo mamana, na miki video, ki faɗi saƙon ki, wajen masoyin naki, yana gani motsin bakin ki. Zaro ido Indo tayi tace. " Nice mamanka ƴar mitsitsiya dani, kai kuma ƙatoto dakai, nidai ka kira ni da indo na. Dariya Habeeb yayi Yace. " Nikam baxan kira sunan kiba, Saboda sunan mamana ke gare ki, idan kuma kince baxan kira ki da mamana ba, to na fasa miki video. " Shikenan to na yadda, ka shirya na fara. Dariya Habeeb yayi tare da saita Indo da wayarsa yana cewa ehh na shirya. Gyaran murya Indo tayi sannan ta fara jero kalamai. " *Assalamu alaikum yaya Mustapha ina kwana ya birni, da kuma mutanen cikin ta, yaya Mustapha yaushe zaka zo, Wlh nayi kewar ka, kuma gashi kullum kibiyar sonka harbi na, yake, ina sonka da yawa da yawa yaya Mustapha na, kaga wannan kwalliyar ma, kaine nayiwa, tana maganar tana fari da ido tare da washe haƙwara* Dariya sosai Habeeb yasa sanda yake kallon videon, kafin ya bude data ya turawa mustapha su. A wunin Ranar sabone sosai ya shiga tsakanin Indo da Habeeb. Kusan tare suka wuni Habeeb na cin dariyar indo, tana basa labarin soyayyar da takewa mustapha, sam Habeeb bai nunawa INDO ƙyama ba, yanda kika san ƙanwar sa ta jini haka suke mu'amala da indo. *Dutse local Government* Da gudu RAUDA ta shigo cikin gidan nasu, shige Mamy tayi a falo tayi ɗakin ta, a saman gadon ta, ta zube tare da sakin wani marayan kuka, mai tsuma Zuciya. Tana kukan mamy ta shigo cikin ɗakin, cikin tashin hankali, kusa da RAUDA ta zauna tare da ɗago kanta ta ɗaura bisa cinyar ta, tace " RAUDA menene meya faru, wani Abu aka miki, kika shigo min gida haka. Cikin matsanancin kuka, harda majina RAUDA tace. " Ya mustapha ne, Mamy ya Mustapha baya sona, ya tsaneni mamy ƙirjina nauyi yake min, soyayyar ya Mustapha zata kasheni Mamy, ki taimake ni Mamy, Wlh idan ban Auri ya Mustapha ba mutuwa zanyi Mamy. " Tsuka mai ƙarfi Mamy taja, tare da cewa. " Haba RAUDA ke baki da wani aiki sai Mustapha Mustapha kullum ke kenan wannan sunan ne a bakin ki, waye ma mustapha me yake dashi da kika liƙe masa yana wulaƙanta ki, ga samarin da suka fi mustapha suna zuwa miki amma kinƙi sauraron su, meya fiki dashi da zai ke wulaƙanta ki, *kyau ya fiki Asali ko gata, ba komai ba laifin ki bane laifin wannan shegiyar Zuciyar taki ce, mai nacin tsiya, zanje na nemo miki soyayyar mustapha koda kuwa komai nawa zai ƙare, dole zanbi shawarar Habiba, zanje Niger wajen malamin nan, mustapha sai yayi dana sanin wulaƙanta ki a cikin rayuwar sa, Mu zuba mu gani, nida kai shege ka fasa, domin kuwa karen bana shike maganin zomon bana* Kiyi hkr ki share hawayen ki, bari na ɗauki gyale na, naje gidan Hajiya Habiba mu tattauna. Ɗagawa mamy kai kawai RAUDA tayi, Mamy na ficewa daga ɗakin RAUDA ta tashi taje gaban babban ilajimen ɗin mustapha dake maƙale a bangon ɗakin, ta tsaya tana magana kamar wacce take gaban sa. " *Why mustapha why baka sona menene Aibuna, meyasa ka tsaneni, shin laifi ne danna soka, ko kuwa haramun ne, idan na soka,? tabbas nasan kasan zafin soyayyah, bai kamata ka Azabtar dani ba, kaji tausayi na, dan Allah ya Mustapha, ta ƙarasa maganar cikin kuka tare durƙushewa a wajen tana kukan hade da ajiyar zuciya*. Shiko mustapha yana zaune cikin office ɗinsa hankali kwance yake harkokin sa, yama manta da wata RAUDA cikin rayuwar sa, zama yayi tare da kunna ƙira'ar Mlm Ibrahim Abdulrasheed, yana sauraro tare da bin karatun, cikin suratul Muminun. Kamar wanda akace ya kunna datar sa, yana kunnawa saƙon Habeeb na shigowa. Buɗe wa yayi, sai kuwa yaga pictures ɗin Indo guda Uku tare da video, da kamar bazai buɗe ba, sai kuma wata Zuciyar ta sashi buɗewa. Duk tsare gidan mustapha da haɗe ransa sanda video nan ya basa dariya, sanda ya gama dariyar sa, sannan Yace. " *Wannan kece mahaukaciyar kam cikakkiya ma, Habeeb kuma an haɗu da indo, lallai Innah kema kin shiga Uku da shiririta, HABEEB HABEEB mutum ya girma amma har yanzu baisan ya girma ba, ita kuma shasha, waini tayiwa kwalliya, koda yake ance idan baka da hankali ka aikata komai.*.............. *YAWAN SHARHI YAWAN TYPING* *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)*[1/14, 3:19 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *BANSO YIN MAGANA BA, AMMA DOLE SAI NAYI MAGANA, HABA ƳAN UWANA YA KAMATA KUKE YIWA WRITERS UZURI, IDAN HAR KIN BIYO WRITERS PRIVET KINCE TA TURO MIKI BOOK, BATA KULAKI BA KAMATA YAYI KI MATA UXIRI HAR ZUWA WASHE GARI, KIGA IDAN BATA KULAKI BA, BAREMA IRINA DA YAU DUK SAƘONNI NA A WAITING MESSAGE SUKA ZO MIN KAƊAN NE WANDA SUKA ZOMIN A BUƊE, KU DAINA KIRAN CEWA WANE NADA GIRMAN KAI DAN ALLAH.* *DUK DA DAI BANI AKA ZAGA BA, AMMA DAI ƳAR UWATA CE WRITERS, KUMA ABUN YAMIN ZAFI, TAYA BAƘYA COMMENTS CIKIN GROUP ƊINTA, DAN TA CIREKI SAI YA ZAMA LAIFI ITA BATAJI GANDAN MIKI TYPING BA SAI KENE ZAKIJI GANDAN MATA COMMENT, TA CIREKI KUMA KIN BIYOTA PRIVET DA ZAGI, HAR KINA KIRAN CEWA, IDAN KINGA DAMA SAIKI MATA MUGUNTA KI ƁATA MATA SUNA.* *KIJI TSORON ALLAH DOMIN KUWA BABU ABUNDA ZAKI IYA MATA, SAI DAI IDAN UBANGIJIN TANE YA ƘADDARA MATA DOMIN IDAN UBANGIJIN TA BAI YADDA BA BABU ABUNDA KE KIKA ISA KI MATA.* *DUK WACCE NA ƁATAWA RAI SANADIN WANNAN MAGANA YAYI HKR 🙏🏻 NI DAI NA FAƊA NE DOMIN WACCE TAYI MAGANAR TASAN CEWA BABU MAI ƘADDARAWA MUTUM ABU SAI UBANGIJIN SA YA SO* *P*••••••1️⃣9️⃣ ➡️ 2️⃣0️⃣ Hanun sa yasa da niyar goge video da pictures ɗin sai kuma yaji kira a wayar tasa. daga kiran yayi tare da amsa Sallama. Ya daɗe yana wayan kafin daga ƙarshe naji yana cewa, shikenan Abdul Babu damuwa sai kazo goben, yana gama wayar. tana mutuwa Babu chage, tsuka yaja tare da tattara, kayan sa, ya kulle office ɗin, ya nufi motar sa, kasancewar lokacin tashin sa daga aikin yayi. " Kinga sharifa tashi ki ajiye wannan wayar da tun ɗazu kika sata gaba kin kasa min Aikin komai, tunda shi girkin nayi, aikuma dai zaki samu ki min gyaran kitchen ɗin koh. Ajiye wayar Sharifa tayi tana haɗa rai ta nufi kitchen ɗin, wayar ta Momy ta ɗaga tare da dannawa RAUDA kira, ringine ɗaya RAUDA ta ɗauka tare da cewa, barka da yamma Momy. " Yawwa RAUDA Barka dai, ya naji Muryar ki, kamar wacce kikayi kuka. Goge guntun hawayen ta RAUDA tayi tace. " A'a Momy ba kuka nake ba, ina ga ko network ne yake rawa, dan nima haka nake jin muryar ki. " Ayyah cewar Momy, ai network ɗin mtn sai a hankali, daman na kira naji kin koma gida lafiya ne. Murmurshi RAUDA tayi cikin jin daɗin yanda Momy take sonta tace. " Na koma lfy lau Momy, yanxu ma haka aiki nakewa Mamy ta fice unguwa. " Ayyah to bari na ƙyaleki kiyi aikin ki, kya gaida Mamyn naku idan ta dawo. " Zataji RAUDA tace tare da kashe wayar, sai kuma ta ƙara goge hawayen daya gangaro mata, sannan ta kira raihana ƴar aikin su, domin taya ta haɗa abinci a daining. Har Mamy ta dawo babu walwala a fuskar RAUDA. Dafa kafaɗar RAUDA Mamy tayi, tace ' ki kwantar da hankalin ki, insha Allah kin kusa samun mustapha a tafin hanun ki, munyi magana da Hajiya Habiba, tace bama sai naje ba, ita zataje mana chan Niger ɗin wajen malamin. Gyaɗa kanta RAUDA tayi tace. " Allah ya jiyar damu Alkairi, Mamy maganar kuɗin, wayar da nayiwa Abba har yanzu shuru yace zai baki ki bani, kuma naji shuru har yanzu. " Cap kin ganni da shiririta ko, ya bani kuɗin nan fah, dubu ɗari, suna cikin dressing mirror na, kije ki ɗauka, ina gama wataƙil abban naku gobe ya dawo. " Allah ya dawo dashi lfy, Sallah RAUDA ta shiga yi, yayin da itama Mamy tayi nata ɗakin. Sanda ya tsaya yayi sallar magriba kafin ya shigo cikin gidan nasu, a falo ya taradda duka family na gidan har Daddy. Gaishe dasu Daddyn yayi tare da ƙoƙarin haurawa sama, yaji Muryar Daddy ya kirasa. Dawowa yayi tare da zama ƙasa gefen ƙafar Daddyn. " Mustapha waiko ka manta da cewa kun girma ne, har yanzu banji kun fara maganar Aure ba, ya kamata kuma, yanxu haka kuna tare da iyalan ku fah, yanxu fah kuna da shekara 30 me kuke jira? Shuru mustapha yayi kasancewar shi harga Allah yanxu Babu maganar Aure a gaban sa, baya kuma neman ƴar Kowa, bai kuma shiryawa aure ba yanxu. Jin shurun yayi yawa ne yasa daddy cewa, " Ya naji kayi shuru, ko bada kai nake magana bane.? " Daddy kayi hkr, a yanxu kam gaskiya bana neman Aure, a ɗan ƙara mana lokaci, insha Allah ZAMU nema. " Allahu yasha, dan ya kamata ku fara nema tun wuri, tashi Allah ya maka albarka. " Ameen Daddy na gode. Kallon Daddy Momy tayi tace, " Alhaji ni Kuma ga wani shawara, me zai hana mu haɗa Auren yaron nan mustapha da RAUDA, kaga yarinyar tana da hankali, shikenan sai muyi tuwo na maina, hankali kwance, koya ka gani?. " To A'ishah baxan ce miki a'a ba, amma gaskiya da hakan zata kasance sai nafi kowa farin ciki, sai dai kuma karki manta da cewa su yaran yanxu ba'a musu dole cikin al'amuran su, mu barsu idan akwai rabon Aure tsakanin su, Allah ya haɗa su, ni bana son takurawa yaro cikin lamarin sa. Ɓata rai Momy tayi domin kuwa bata so haka ba, taso ne Daddy yabi bayan ta, sai kuma ya mata tozon raƙumi ya yasar da zancen ta gefe, shuru tayi bata ƙara cewa komai ba, domin kuwa tasan daddy kaifi ɗaya ne, baya magana biyu. Ƙarfe takwas daidai mustapha ya sauƙo suka ci abinci bai wani juma ba ya koma ɗaki kasancewar yanda yake jin marar sa, na famar ƙulle masa, kwanciya yayi tare da yin shuru, tun marar tasa na masa kaɗan kaɗan har ta dawo tana masa ciwo sosai, muƙurƙuso kawai mustapha keyi saman gadon sa, domin yasan Halin ciwon nasa, Babu Abunda ke sasa wannan shegen ciwon sai munguwar sha'awar da yake da Ita, gashi yanxu ya kai matakin da bazai iya tashi ya ɗauko tablet ɗin dayake amfani dashi ba, riƙe marar yayi sosoi, yana jin wani mungun felling na taso masa babu Abunda yake buƙata yanxu irin yaji mace kusa dashi, gashi shi Allah yayi shi da kyankyamin tsiya, bazai iya kusantar matar da batasa ba, yana cikin wannan Halin Allah ya jefo Ishaq cikin ɗakin, da hanu mustapha ya masa alamar yaxo, tahowa Ishaq yayi da sauri wajen yayan nasa, a hankali Mustapha yake masa magana cewa ya buɗe drower akwai tablet yellow ya kawo masa tare da ruwa a prich. Ɗaukowa Ishaq yayi ya basa, da ƙyar mustapha ya miƙe yasha maganin sannan ya koma ya kwanta, aikuwa bai juma da shan maganin ba, wani irin gumi ya yanko masa, duk jikin sa ya sake, a haka bacci ya ɗauke sa. *DASINA* Yau kwanan Habeeb huɗu a ƙauye dasina, sosai Kuma yake jin daɗin zaman garin, Zaune suke Shida Indo cikin gidan Hajiya Innah, tashi Habeeb yayi tare da nufar bishiyar maina dake tsakiyar gidan, hawa bishiyar yayi Yayin da Innah da indo suka zuba masa Ido, ƙaryo mainar yayi, sannan ya sauko yana gyara ta, sanda ya gyara ta, tsaf sannan ya kalli Indo yace. " Ungo karbi. Kallon sa, Indo tayi tace. " Bangane ungo ba, me zanyi dashi kuma. " Yawwa tambaya mai kyau, kinga dai na farko kince kina son Mustapha koh? Gyaɗa kanta Indo tayi alamar ehh, harda ɗan murmurshin ta. " Yawwa to kinga shi kuma mustapha yana son mace wacce haƙwaran ta, suke fari tas, kamar dai nawan nan, kinga ke Kuma naki hakwaren kin barsu sun ɓaci da datti, to shine naga cewa mai zai hana tunda nida ke, mun zama ƙawaye, na taimake ki, na taya ki, neman soyayyar mustapha, kuma ta yanda zamu fara dole sai mun fara da gyara ki tukunna, ki dinga wanka kina wanki kina goge haƙwaran ki, idan mustapha ya ganki fes, dole zai soki, kinga shi mace mai tsafta yake so, shiyasa ma, na ɓallo miki wannan iccen mainar dan ki fara goge bakin ki, kuma ba iya yau kawai zakiyi ba, kullum sai kinyi, ni Kuma na ɗau alƙawarin duk sanda na koma birni zan turo miki maclean da brush, wanda zaki dinga wanke haƙwaran ki dasu. Kin yadda? "Na yadda ai nasan kai kana sona baxaka cuceni ba, na yadda da kai fiye da yanda na yadda da Innah. Harara Innah ta dokawa Indo tace. " Kuji ja'irar yarinya, yo to ni ina ruwana dake, balle kuma yardar ki, shima Habibun wuyar sa, kukai Anjuma ne, sai an jiku a rana. Dariya Habeeb yayi tare da cewa. "Kinga rabu da Hajiya karɓi, ki fara goge bakin, ki goge fah sosai. Karɓa Indo tayi ta tauna sannan ta fara dirjan bakin ta, dashi, sosai ta dage take goge haƙwaran ta, har jini suke tana goge, sanda ta fara jin zafi tayi wurgi da magogin gefe tace. " *Kan bala'i Wlh ya Habibu kai mungu ne, kaji yanda bakina ke min zafi, kuma kasan yana zafin tsabar baƙar mugunta shine zaka bani kace na goge baki, to aradu baxan goge ba*. Haɗa Ransa Habeeb yayi sannan yace. " Nine mungun koh, shikenan na gode, daga yau kuma Babu ruwana dake, baxan ƙara taimakon kiba akan mustapha, daman akwai wacce take sonshi a can birni, kinga shikenan idan yaga ta fiki gaye da haɗuwa, mai fararen haƙware, tas tas dasu, sai ya sota, shikenan ke kuma kin tashi a *TUTAR BABU YA MANTA DA WATA INDO MA A DUNIYA, NI KUMA INA CAN INA WAJEN AIKINA BAZAMA KI GANNI BA, BARE MA KICE NA TAIMAKA MIKI* . Zabura Indo tayi cikin masifa da bala'i ta miƙe tsaye tayo kan Habeeb tana cewa. " *Ita yarinyar taci ubanta, kaji shegiya wai ya Mustapha take so, to Wlh ƙarya take ya Mustapha ƙwalelenta, yafi ƙarfin ta ya Mustapha na Indo ce, ita ɗaya, YASIN NASHA RUWAN ARADU DUK SANDA ALLAH YA HAƊANI DA ITA SAI NACI KUTUMAR UBANTA, SAITA GWAMMACE KIƊA DA KARATU, KAIMA HAR WANI MAIMATA WA KAKE KAMAR WANDA KA FAƊI ABUN ARZIKI, TO YASIN NA HAƊU DA ITA SAINA SANJA MATA KAMMANI, KAN UBAN CAN WAI YAYA MUSTAPHA NA, TAKE SO, LALLAI KAM, SANNU SARAN MAI BAƘAR TA KASHI GATA BULU GATA JAJA, SHEGIYA, KAWAI*. Sunkuyawa tayi ta ɗauko magogin tace, badai kan goge baki bane, *TO YASIN INDAN NA FARA GOGE BAKI NA, SAI YAFI NAKA HASKE, TA ƘARASA MAGANAR DA HARARAR HABEEB TAYI ƊAKIN INNAH TANA GOGE BAKIN*. Dariya ce ta kwacewa Habeeb ganin yanda Indo ta taso kansa da Bala'i kamar shine yace yana son Mustaphan. Kallon Innah yayi yace Hajiya. " Lallai kuna fama da indo cikin garin nan. Dariya Innah tayi tace. " Wai damma kwanan nan bata ɗebo magana, amma ai Indo Rana ɗaɗɗaya ne, bata jawowa iyayen magana da zagi a cikin gari, amma naga kai yanxu kana iyawa da Ita. Dariya Habeeb keyi, yaji wayar sa, na ringine, Bros ya gani manne a jikin screen ɗin wayar dariya Habeeb yayi ya ɗaga tare da cewa. " Allah ya taimaki Barrister sai yau aka ga sakon nawa ne. Murmurshi Mustapha yayi daga can Yace. " Badai kaje ka zaune wajen Hajiya ka manta da muba, kodai mu biyoka da sauran kayan kane. Dariya Habeeb yayi tare da cewa. "A'a kuyi hkr ba sai kun biyoni dashi ba zan dawo, jiya da daddare munyi waya ai da daddy, har ya bawa Momy wayar. Sai yanxu mustapha yayi dariya yace. " Ya sanar dakai kenan. " Meya sanar dani, ni babu wani Abunda ya sanar dani, taɗin duniya kawai mukayi ya kashe wayar sa. " Cewa yayi ya fara gajiya da mu, ya kamata mu nemo matan Aure. Dariya sosai Habeeb yayi sannan Yace. " Nine dai ya kamata na nemo matar aure ba kai ba, kai kam ai kana dasu, ko baka zaɓi sauran ba, ya kamata ka zaɓa cikin *RAUDA DA INDO, kaga daman kullum cikin felling kake, shikenan saika huta da shan tablet*. Tsuka Mustapha yaja tare da cewa. Daɗi na dakai kenan ba'a maganar arziki dakai, kaika sansu har kake tunawa dasu cikin rayuwar ka, kaga ni sai Anjuma ma. Dariya Habeeb keyi yace. " Allah ya huci Zuciyar ka, ga Innah zakuyi magana. Da gudu ya ƙarasa ɗakin Innah ya ɗaura wayar kunnen Indo, cikin raɗa yanda mustapha bazai jiba, yace kiyi magana mustapha ne. Cikin ɗoki da murna indo ta ƙankame wayar tare da cewa................. *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah)* [1/17, 6:16 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*•••••••2️⃣1️⃣ ➡️ 2️⃣2️⃣ " *Wayyo Allah daɗi kashe ni, ya Mustapha na, Aradun Allah ina sonka, kibiyar sonka ta soke ni, kaji wani irin daɗin da naji kuwa da ya Habibu yace ga mustapha na*. Jin shurun da tayi ne, yasata kallon Habeeb tace. Ya Habibu banji yayi magana ba, fah. Mustapha bai kashe wayar ba, shuru yayi yana jin su, domin kuwa yana jin sanda Habeeb yake, cewa Indo gashi mustapha ne kiyi Magana, shiyasa yayi shuru ba tare daya kashe wayar ba, yana jiran Habeeb ne ya karɓi wayar ya masa rashin mutunci. Karɓar wayar Habeeb yayi tare da dubawa, cikin mamakin ganin mustapha bai kashe wayar ba, kuma bayan yaji Muryar Indo, sa wayar yayi a kunnen sa, tare da cewa. " Bros ya kuma kayi shuru kana jin masoyiyar ka, tana sanar dakai yanda kifiyar sonka yake sukan ta kayi mata banxa. Murmurshi mustapha Yayi cikin jin takaicin yawan wasan Habeeb, shi dai komai zai iya yiwa mutum wasa akansa, koda kuwa mutum yana cikin Halin da baya buƙatar wasa. " Hmm to Uban ƴan neman magana, naji sai kuma akayi yaya, Sarkin ƴan neman magana na duniya, Kuma bari kaji na sanar dakai daga yau baxan ƙara neman ka a waya ba, har sai kabar wannan ƙauyen, Kuma karka Ƙara nema na, dan ko ka kira baxan ɗaga ba, tunda kaima kana son biye wannan shashashar ku zama iri ɗaya. Murmurshi Habeeb yayi, cikin serious ya cewa mustapha. " Bros naji abunda ka faɗa min kuma na ƴarda, sai dai ina son kasan Wani Abu guda ɗaya, kallon Indo yayi da ta mayar da hankalin ta wajen sa, ficewa yayi daga ɗakin Innah yayi nasa yana cewa. *Duk yanda mutum yake, bai kamata ka wulaƙanta shiba, domin kuwa, gobe baka san mai zai zama ba, sannan aini a tunanina, shi mai Sonka yafi maƙiyin ka, kuma bai cancanci wulaƙanci daga gare kaba, Amma kai Bros........* " Enough Habeeb bana buƙatar wani magana daga gare ka, cikin tsawa yace, *akan me zaka bawa wannan shashashar Iblis ɗin wayata, yarinyar data gagari Uban kowa cikin wannan ƙauyen, ƙazama marar Hankali da lissafi, idan har kaima ka koma shashasha, toni ban koma ba, da nawa hankalin a jiki na* Yana gama faɗin haka ya kashe wayar. Zuciyar Habeeb idan tayi dubu to, ta ɓaci domin kuwa yaji zafin maganar da mustapha ya faɗa masa, duk da yasan halin zafin zuciyar mustapha, zai iya yiwa kowa ihu idan ranshi ya ɓaci, sai dai baiyi tunanin, dan ya bawa Indo waya, ranshi zai ɓaci haka ba. Shigowar Indo ne, ya katse masa maganar zucin daya ke yi. " Ya Habibu ya kuma ka tafi baka bani wayar munyi magana da shiba, kuma har nasa raina zanji Muryar yaya Mustapha na, tana maganar ne tana tura baki. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " Babu network ne, shiyasa wayar ta tsinke, Amma ki bari sai gobe, idan ya sake kira sai na haɗaa ku. Tsumewa Indo tayi, tana murguɗe murguɗen baki, tace. " Nidai Wlh ya Habibu ban yadda ba, ai naji kuna magana dashi yanxu, shine ka gudo nan dan karka bani muyi magana, toni ban yadda ba, sai dai ka kira min shi yanxu ko Kuma kayi min video Irin na ranan sai ka kai masa tunda kace gobe zaka koma birni, idan kuma kaƙi min to Wlh *ALLAH YA ISA BAN YAFE BA JAMIN RAI DA KAYI*. Haɗa Ransa Habeeb yayi, ya gallawa ya Indo harara, tare da cewa. " Wato dai ke Indo baki da kunya, ni kika jawa Allah ya isa koh, ban girme ki bane da zaki jamin Allah ya isa, kamar wani sa'an ki, dan kinga ina kulaki koh, shine zaki zageni, Babu laifi nane da nake kulaki, shi mustapha ai da Baya kulaki baki zagesa ba sai Ni, ya karasa maganar cikin, haɗa fuska. Duk tsiyar Indo da iya shegen ta, sanda taji jikin ta, yayi sanyi, karo na farko da taji tayiwa wani rashin kyautawa, har taji tayi danasani, shuru tayi tare da cewa. " *KAYI HKR DAN ALLAH BAZAN SAKE BA*. Ƙin kulata Habeeb yayi, ya kuma kawar da kansa gefe, yace. " Ki tashi ki fita ki bar min ɗaki na. Zama Indo tayi daɓas gaban Habeeb tana masa magiya kan yayi hkr, amma ina Habeeb ko kallon ta baiyi ba, bare tasa ran zai kulata. To fah Indo ta fara ƙula, ganin yanda take bawa Habeeb hkr amma yaƙi kulata, cikin jin haushi tace. " *Shikenan to, tunda baza kayi hkr ba, inata baka hkr kaki kulani dan ma ka samu na baka hkr, Aradun Allah ban taɓa bawa Kowa hkr ba, har Mama, sai kai Kuma kace baxa kayi hkr ba, sai Kuma ta fashe da kuka tana Cewa, shikenan tunda kaƙi kulani kuma wlh baxan bar nan ba, ina Zaune har sai kace kayi hkr, da makarantar Allo zan tafi, Kuma na fasa zuwa tunda baxa kayi hakuri ba, tana kukan ne take wannan maganar*. Dariya Habeeb yayi cikin jinjina yarintar Indo, yama rasa dame zai fassara, wannan hali na Indo, da yarintar zai kirasa ko kuma da me zai kira, tunda dai yanxu Indo zatayi shekara goma a duniya, kamar dai ta wuce a kira shi da yarinta, ya kuma fuskanci yarinyar tana da sauƙin kai, idan zaka bita a hankali, tana kuma da fahimta, ya fuskanci Indo tana son mai kulawa da lamarin ta, tunda gashi yanxu har hkr take basa, da ace ni mazaunin kasar nan ne, to tabbas zan iya sauyawa Indo halayyar ta, kuma yarinyar da zata gyaru cikakkiyar mace za'a tayar, murmurshi Habeeb yayi, sannan yaci gaba da maganar zucin sa, zan nemi transfer daga London zuwa ƙasata ta Nigeria, duk wani weekend zan dinga yinsa cikin wannan ƙauyen, domin ganin na inganta rayuwar wannan yarinyar da ake ganin tafi ƙarfin kowa, domin kuwa *BABU GAGARARRE SAI BARARRE DA KUMA WANNAN YARINYAR INDO ZAN NUNAWA MUSTAPHA KUSKUREN SA NA RAINA ƊAN ADAM* . Kallon sa ya mayar kan Indo yace. " To tashi nayi hkr, maza kije ki tafi makaranta, idan kin dawo sai muyi video koh. Mai kuka ce, ta dawo dariya, tashi tayi tana dariya tace. " Yauwa yaya Habibu ko kai fah, a dai afuwa yana da daɗi, ni videon ma na fasa, bari naje na dawo ka kunna min kallo nayi a wayar ka. Dariya Habeeb yayi sannan yace. " Amma dai kije kiyi wanka tukunna, kuma kinga wannan aswakin, ki barsa a bakin ki, kina gogewa har ki dawo. " *Na shiga Uku ya Habibu wanka Kuma, Ranar da kaxo fah nayi, nidai gaskiya baxanyi wanka ba sai Ranar juma'a*. " Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yanxu Indo wankan ne, kike yinsa sati sati, Haba, ashe dai gaskiyar mustapha ne, da yace min, abunda yasa baya sonki ke ƙazama ce, kuma bakya jin magana, ashe da gaske yake, tunda yanxu maganar sa, ta zamo gaskiya, kinga Babu ruwana baxan ƙara cewa ya Aure kiba, tunda kinga ita wacce na gaya miki tana sonsa ƴar gaye ne, Kuma kullum sau biyu take wanka, to kinga mai zaiyi dake, mai wanka sati sati, ga mai yin wanka biyu kullum. Haɗa ranta tamau Indo tayi, shi kansa Habeeb haushin sa, take ji, idan taji ya ambaci sunan wata tana son mustapha, cikin jin haushi tace. " *YA HABIBU DAN ALLAH NA ROƘE KA*. Kunshe dariyar sa Habeeb yayi domin kuwa ya harbo jirgin Indo, indai kana son tayi abu cikin gaggawa to kace mata budurwar mustapha ta birni nayi, to yanxu zatace sai tayi wanda yafi nata, kuma daman dan tayi wankan ya mata haka. " Umhum ina jinki roke ni. " *DAN GIRMAN ALLAH DAN ANNABI MUHAMMAD (SAW) KA DAINA CEWA WATA TANA SON YA MUSTAPHA, KAGA KAIMA FAH HAR KASA NAJI HAUSHIN KA, SAURA MA KAƊAN NACE MAKA ALLAH YA ISA HAUSHIN DA KASA NAJI, KUMA SAI NA FASA CE MAKA ALLAH YA ISAN, AMMA YANXU ZANJE NAYI WANKAN INA DAI SHIKENAN KOH MAGANA TA ƘARE* " Dariya Habeeb yayi yace to karya nayi baida budurwar ne, ke dai kawai ki dage, ki fita wanka da wanke baki, ko zamu samu mustapha ya soki. Magana Indo zatayi Habeeb ya yace Mata. " Shit maza jeki kiyi shirin makaranta, kar lokaci ya ƙure. Shigewa Indo tayi, sanda taxo daf da Innah ta sunkuya gaban ta, tare da cewa. " Allah ya turo miki da malakul maut, ya ɗauke ki mu huta, ni yanxu na gaji da ganin ki, ni bani ashirin nayi kuɗin tara. Tashi Innah tayi tare da ɗaukar Salati. " Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yanxu Indo mena tare miki cikin wannan Duniyar, da kike neman Rayuwata, shikenan ni kuma yau baxanyi bacci ba, yarinyar nan tamin baki, nama isa na sake baki ina bacci na jini cikin barzahu, shegiyar yarinya, ja'ira, to bazan mutu ba, yanxu dan ubanki Musa sai naga mutuwar iyayen ki, naga taki naga ta jikokin ki, shegiya mai mungun baki. Habeeb jin mitar Innah daya sashi fitowa ne, ya tsaya yana cin dariyar ta, Innah da tsoron mutuwar ta. Ita kuwa Indo, dariya tayi tace. " Hajiya Innah ina ma zaki ga ƴaƴana bare kuma jikokina, ai kafin nan kin daɗe a lahira, ni ki bani kuɗin na tafi, kar kisa nayi latti. " Bazan bayar ba, kixo ki ƙwata dan uwarki, a hakan zan baki kuɗina kina neman Rayuwata, to bazan bayar ba. Ganin da Habeeb yayi, Indo da Innah zasu iya kaiwa magaruba, suna wannan faɗan bai damesu ba, yasa Habeeb Ciro kuɗi Naira dubu dubu ce,a jikin sa, ɗaya ya ɗauko ya cewa, Indo gashi karɓi maza kije kiyi sanji ki ɗauki, hamsin ki dawo min da sanji na, karfa ki hallaka kuɗin nan duka. Zuwa Indo tayi ta karɓa tare da cewa, yanxu ma zan kawo maka sanjin ka, kafin na wuce makarantar. Kallon Innah tayi tace, ke Kuma, yau ki jira zuwan malakul maut, dan sai kin mutu mutum ya tsufa ya tsofe amma bai son mutuwa, kuma mutuwa dole ce a kanki, . " Sai kixo ki kasheni ai dan uwarki, sai kici kanki ai mayya kawai. Dariya Habeeb yayi, kawai tare da shigewa ɗakin sa. Daddare hira sosai Indo da Habeeb suka sha, dan tun zuwan Habeeb mutanen gari suka samu sauƙi wajen Indo, wani sa'in wuni guda zatayi bata fito waje ba, tana maƙale gidan Innah tare da Habeeb. Innah kuwa yau taki kula Indo, haka itama Indo bata kula Innah ba. Tsakar dare gari yayi shuru, kowa yayi bacci babu Abunda akeji sai kukan tsuntsaye, Indo dake kwance ɗakin Innah ta tashi tare da ɗauko farin yadin da ta sayo da kuɗin da Habeeb ya bata, dan ƙin kai masa sanji Indo tayi, shima kuma ya manta da ya bata kuɗin, ware yadin Indo tayi tare da rufawa a jikin ta, tayi wajen gadon Innah, sanja Murya Indo tare da taɓa Innah, tashi Innah tayi, haba wa Innah tana buɗe Ido taci karo da mutum lulluɓe da farin yaji, baya Innah taja tare da cewa. " Waye ne? Wata irin murya Indo tayi tace. " Nine mala'ikan mutuwa naxo ne na ɗauki ranki, cikin Aminci, dan haka ki kwantar da hankalin ki. Rawa jikin Innah ya fara, ja da baya take tana magana da karfi tana cewa. " Wallahi bani bace wacce zaku ɗauki ranta, wayyo Allah, dan Allah mala'ika ka barni na ɗan kara kwanaki a duniya. Duk ta gigice ta fita hankalin ta. Habeeb dake kwance ne yaji ihun Innah ya fito da gudu, cikin tsoron ko wani abune ya sami Innah. Yana shiga ɗakin yaga Innah takure a gefe sai rawa jikin ta, keyi, haskawa Habeeb yayi da wayar sa, daga ƙafifin ta, ya gane Indo ce, baiyi magana ba, cikin tsabar haushin Indo, saima ɗauketa da wasu tagwayen maruka da yayi tare da nuna ta da yatsa yace Kuyi haƙuri da wannan wlh naso nayi muku typing yafi haka, sai dai kuma yau muna biki ne, na sister na, kuma wlh bawai ina jin daɗin jiki na bane, mu haɗu daku next page, Ranar Lahadi, in Allah ya kaimu, dan gaskiya bana typing Ranar Asabar. Gashi yau naso na dawo har cikin dutse, domin ganin halin dasu RAUDA suke ciki, amma ba damuwa mu haɗu next page, tunda Indo ta cinye wannan page d'in ita kaɗai.😄😄😄😄 *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻 *(Ummu Nasmah ce)* [1/20, 4:14 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*•••••2️⃣3️⃣ ➡️ 2️⃣4️⃣ "kin san me kika aikata kuwa, ki duba kiga yanda jikin wannan baiwar Allah ke rawa, ko kin manta da cewa tana da Hawan jini, so kike ki kasheta, idan mala'ikan bai kasheta ba, aike zaki kasheta, wani irin haline dake wannan, da baki san Wanda ke miki Alkairi ba, tsuka yaja tare da juyawa yayi kan Innah, gani yayi jikin Innah ya sake, da sauri ya kai kunnen sa kan ƙirjin Innah, ajiyar zuciya ya sauƙe jin suma tayi, juyowa yayi ya finciko Indo gaban Innah, Yace, gashi kin kasheta ai kin huta, shikenan Hankalin ki ya kwanta. Zaro ido Indo tayi, sai kuma ta fashe da kuka, tana Cewa. " Innah ki tashi dan Allah karki mutu, Wlh wasa nake miki, ya Habibu ka tashe ta dan Allah, wayyo Allah na shiga Uku na kashe Innah, shikenan yau kuma ni Indo na shiga Uku, sai kuma ta zauna daɓas a ƙasa, tana cewa, *Shikenan Babu ni Babu cin taliyar turawa tunda Innah ta mutu, Babu mai bani kuɗin kashewa na jawa kaina Asara, ni Wlh da akwai mai maye mini gurbin Innah bazan yi wannan kukan ba, wayyo Allah na, taliya ta kam shik.........* Tsawa Habeeb ya daka mata tare da cewa. " Rufe min baki, dallah dame zanji da ita Innah zanji koda masifar kukan ki, na banxa. Shuru Indo tayi tare da gallawa Habeeb harara, sai kuma ta tashi ta koma gefe ta zauna, tare da tsurawa Habeeb ido daya ɗauki ruwa yayi kan Innah. Yayyafawa Innah ruwa Habeeb yayi, kafin Innah taja numfashi mai nauyi, a firgice ta farka tana kalle kalle. Tausayi Innah ta bawa Habeeb gani yanda take leƙe leƙen cikin ɗakin, cikin taushin murya Habeeb yake ce mata. " Ki kwantar da hankalin ki, Innah mafarki fa kikayi, ba wani mala'ikan mutuwa daya zo cikin ɗakin nan, ki daina razana dan Allah. Cikin rawar murya Innah ke cewa. " Wlh Habibu ba mafarki nake ba, na ganshi cikin ɗakin nan, yace raina zai ɗauka, kuma Wlh bana son na mutu yanxu, ka tashi kawai Habibu mubar gidan nan, nikam na yafe zaman gidan nan. Ikon Allah cewar Habeeb. " Haba Innah nace miki mafarki kikayi ko, ga car INDO ki tambaye ta, kiji, itama ihun da kike cikin Bacci ya sata tashi, kinganta can kinsa itama ta kasa bacci kiyi addu'a ki kwanta ta ɓangaren daman ki, babu wani mafarki da zaki ƙara yi. Saurin kallon Habeeb Indo tayi ganin ya ɓoyewa Innah cewa itace ta mata wannan aikin, sai kuma ta sunkuyar da kanta, ƙasa tuno yanda jikin Innah yake rawa, tana kokarin maida dariyar ta, cikin ta, kar Habeeb ya ƙara jin haushin ta. " Shikenan Habibu, Indo kixo mu kwanta, amma dai nasan Baccin yau kam na rasashi dan ba iyawa zanyi ba, karna kwanta na ƙara wannan mungun mafarkin. " Yawwa to ko kefa Innah, kwanta itama Indo zata zo ta kwanta yanxu. Bayan Innah ta kwanta ne, Habeeb yayi, wajen Indo tare da sunkuyawa daidai kunnen ta, yace. " Na rantse da Allah kika ƙara tsorata tsohuwar nan, Wlh !! Wlh !! Wlh, kema yau tsakar gida zan wurga ki, na rufewa Innah ƙofar ɗakin ta, naga keda ita wa zai fara mutuwa yau ko kuma naga wanda zaifi wani jikkatuwa tsakanin ku, tunda ke, baki da mutunci. Tashi kije ku kwanta. Tura bakin ta Indo tayi ba tare data maidawa Habeeb Amsa ba tana hararar sa ta ƙasan ido, gadon Innah tayi tare da cewa. " Matsamin na kwanta kuma wlh karki matseni, kuma banda gwarti, dan kina hanani bacci ehe. Ita dai Innah bata tankawa Indo ba, dan yanxu bata da lokacin faɗa da indo a halin da take ciki, haka suka kwana har gari ya waye ba tare da Innah ta runtsa ba, idonta biyu har garin Allah ya waye. Da safe Innah ta aika Indo gidan talatu mai ƙosai siyo musu na karin kumallo, karɓa Indo tayi tana kallon Innah tana dariya ta fice daga cikin gidan. Ita dai Innah taƙi biyewa Indo yau, bare suyi ɗan Halin da suka saba. Gidan ƙosan cike yake da yara, kowa na jiran layi, itama Indo ajiye kwanon layin tayi, tare da samun gefe ɗaya ta zauna, kokuwa ne ya tirke tsakanin mariya da Garba, yayin da garba yafi jibgar mariya, anko rabasu garba yaƙi rabuwa, shiga mai taurin kan tsiya, haushin yanda garba ke dukan mariya ne, ya kama Indo, ta tashi taje tsakiyar su, tace. " Kai garba na sayi faɗan, rabu da ita mu gwabza dani naga jarumtar taka, ɗan mai taurin kan tsiya ka dage sai jibgar ta, kake dan kaga kafi ƙarfin ta. Sakin mariya Garba yayi yana kallon Indo cikin dariya yace. " Wanda suka fiki ma na gwabza dasu basu share ba bare kuma ke, idan kin shirya shigo mu fara kiga yanda zanyi dake, idan kina dukan wasu ki share to yau kam kin shigo hanuna, za kuma kiga yanda zaki sha wahala. " *Dariya Indo tayi tare da sunkuyawa ƙasa ta ɗebo ƙasa, a duka tafukan hannun ta, ta buɗewa Garba tace, ƊAUKI ƊAYA, GANA MASIFA GANA BALA'I, ZAƁI DA WANNE ZAMU GWABZA*. Na bala'in garba ya ture, ai kuwa take kokuwa ya kaure tsakanin Garba da indo, inda faɗa ya juya salo, ya zamana yanxu Indo ce, ke jibgar Garba, saɓanin ɗazu da garba ke jibgar mariya. Kokuwa suke sosai, inda garba yaji jiki sosai amma tsabar taurin kai irin na, garba yaƙi haƙura yabar faɗan itama kuwa Indo cewa tayi muddun garba bai haƙura ba, sai dai su wuni suna faɗan, da gyar da suɗin goshi aka raba garba da indo, ɗauko kwanon Indo talatu tayi ba tare da layin Indon yaxo ba, sa mata ƙosan da koko tayi tace gashi ki tafi. Karɓa Indo tayi tana cewa Garba. " *Ko wani shege ma waje ya samu, ka dage sai dukan ƴar mutane kake, ɗan iska ƙaton banxa, girman biredi tashin kofin shayi, gobe ka bawa wani labarin Indo*. Sanda Garba ya tabbatar da indo ta juya tana tafiya, ya taho da gudu ba tare da Indo ta ankara ba, ya ture ta, faɗuwa ƙasa Indo tayi daga ita har koko da ƙosan, shigewa da gudu Garba yayi yana cewa " Na rama kiji kema idan da daɗi. " Ihu ne, kawai Indo ba tayi ba, ganin Abunda Garba ya mata, Gashi Kuma ya tsere mata bazata iya kamo sa ba, tashi tayi cikin ƙwafa tare da cewa. " *Zamu gamu wata rana sai ka gwammace kiɗa da karatu, in kere na yawo zabo na yawa wata rana za'a haɗu* Ɗaukar kwanon nata tayi, ta koma gidan Innah. Ganin mutum Innah tayi a kanta, da kwano riƙe hanun nata, duk tayi futufutu da jikin ta, kallon ta Innah tayi tace. " Aya na ganki haka kamar an koroki, wai wanka kikayi da ƙasa ne, duba kiga yanda kika yi wata kala duk kin ɓata jikin da datti. " Tura bakin ta Indo tayi wanda ya zamo mata sana'a tace. " Faɗa mukayi da Garba, na masa shegen duka, shine da yaji haushi, ban ankara ba ya ture min koko da ƙosan ya zube ƙasa ko kaɗan bai saura ba. Habeeb ne daya fito cikin shirin sa, na komawa, cikin dutse ya girgiza kansa, yana jin Ikon Allah wajen Indo, wato ita duk Inda taje sai ta saida hali, Allah ya kyauta ya kuma shirye ki,. Cikin masifa Innah ke cewa. " Kan bala'i wato shi garban ne, ya zubar min da koko da ƙosan nawa da ubansa, to kuwa tashi zanyi naje har wajen shi uban nashi naji idan shine ya turo sa, tashi muje ki raka ni Indo. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " Haba yanxu ke idan an barki sai kije, kinsan Abunda ita indon ta masa ne, kuma idan banda Indo da rashin hankali kina mace ina ke ina faɗa da namiji, Babu kyauma ai, hararar Indo yayi yace, kindai ji jiki Wlh, tunda ke baza kiyi Hankali ba. Tashi Innah tayi tana cewa. " to Uban ƴan iya magana, a ina akace mace baza tayi faɗa da namiji ba, to tayi faɗan ke Indo, daga yau cikin garin nan, duk Uban da ya miki ki takasa ko ubanwaye ne, kuwa. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " Allah ya baki hkr Innah nikam ba baƙon zafi bane, tafiya ma zanyi yanxu, kallon Indo yayi Yace, muje ki rakani gidan ku, na gaisa da Mama da baba na wuce ina son shiga cikin dutse da wuri, ke kuma Innah shigewa zanyi daga can baxan dawo ba. " Bazaka tsaya kayi karin kumallo ba, zaka wuce da wuri haka. Dariya Habeeb yayi yace. " Dame zanyi karin kumallon Innah, bayan anyi tanbola da koko da ƙosan. Shikenan to ka gaishe da iyayen naka, ka cewa wannan ɗan baƙin Halin, ya aiko min da saƙona dan ubansa. Dariya Habeeb yayi cikin zolaya yace. " Babu ruwana tsakanin ki da mustapha sai Allah dan haka bazan shiga tsakanin kuba. " Karka shiga tsakanin namu, yanxu nasan idan ka tafi sai kuma tsawon rai kafin na ƙara ganin ka Habibu, sai kuma tasa kuka, Habibu Allah dai ya ƙaddara saduwar mu. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " Bazan dade ba, Innah idan na koma can wajen aikin nawa ma, bazan daɗe ba, zan ajiye musu Aikin su, na dawo gida na cigaba da aiki na, so bazan fi wata Uku ko huɗu ba, zan dawo insha Allah. Shikenan Habibu Allah ya kiyaye hanya ya tsare, ya sanyawa Rayuwar ku, albarka. Ita kuwa Indo haɗa fuska tayi jin ance Habeeb zai tafi, dariya Habeeb yayi tare da cewa. " Haba indodo na, meye na haɗa fuskar kuma bayan baxan daɗe ba, zan dawo. " Ya Habibu bana son ka tafi, amma tunda kace bazaka juma ba, shikenan, idan kaje ka cewa ya mustapha ina gaishe shi, kace masa ina sonsa kullum da sonsa nake kwana nake tashi. Murmurshi Habeeb yayi yace. " Insha Allah kuma zan isar miki da saƙon ki, Indo ki daure kike zuwa makaranta kinji, ki rage yawan rashin ji sannan kullum kike wanke bakinki kina gogewa kinji indona. " Ya Habibu xan rage, koda ƙaɗanne, zan kuma ke zuwa makaranta kullum, kuma kullum zanke wanke baki na. Bayan Habeeb sun shiga cikin gidan su Indo, ya gaishe da iyayen ta, duk da ma bai samu Baba ba, dubu ashirin ya ajiyewa Mama tana godiya tare da cewa ya gaishe da Hajiya A'ishah. Cikin jimami da bacin rai Habeeb da INDO suka rabu, yana ɗaga mata hanu tana daga masa, har yayi mata nisa, juyawa Indo tayi gidan su da niyar taje ta tafi makarantar Boko. *DUTSE LOCAL GOVERNMENT* Zaune suke sun gama breakfast kasancewar yau Daddy na gida bazai fita kasuwa ba, kallon Mustapha dake zaune yana game a wayar sa Daddy yayi tare da kiran sunan sa, amsawa yayi tare da kallon Daddy. " Mustapha ka shirya kaje gidan Alhaji ka karɓo min saƙo, kuɗi zai baka, idan ka karɓa ka shige bank ka ajiye min su cikin account ɗina, zai baka 20millions. Amsawa mustapha yayi da to, amma bawai zuciyarsa na ƙaunar zuwa gidan su RAUDA ba. Momy ce tace. " Yawwa bari na baka saƙo ka kaiwa RAUDA, daman akwai sarƙar da na saya mata, tunda zakaje saika tafi mata dashi koh. Haɗa Ransa Mustapha yayi Yace. Ki ajiye kawai Momy duk sanda taxo kya bata, karna manta ta cikin motata. " Bazan ajiye sai taxo ba, kai mata zakayi yanxu, ka manta kuma mu gani, sarkar ce, zaka manta, inbanda baka son kaimata ne Tashi mustapha yayi, cikin jin haushin aikan da Momy ta masa wajen RAUDA ya haura sama, yana mita cikin ransa, tare da jin haushin RAUDA, shidai har ga Allah haka kawai baya ƙaunar RAUDA cikin rayuwar sa, kuma bawai tana da wani Aibu bane ko wani mungun hali, a'a bata da ko ɗaya, shi kansa yasan RAUDA macece mai nutsuwa tare da biyayya ga duk na sama da ita, tana da kyawun ta dai-dai gwargwado, a fili yace. " Ajine kawai bata dashi, Tunda har zata iya furtawa namiji cewa tana sonsa, ai macen da takai mace, ita ake zuwa ace ana so, ba itace zata ke bin namiji ba, ko ita wannan INDOn da take cemin tana sona, daman can ita ba nutsuwa gareta ba, bare kuma a samu Class tare da, ita, ita ɗayan ta, ma Aljana ce, ita za'a iya mata uxirin rashin Hankali da rashin lafiya na aljanu da take fama dashi, amma ke RAUDA kina mace mai Class, har kin kai 3 Hundred level a JSU kixo kina zubar da ajinki wajen maza, banza jarababbiya kawai, tsuka yaja tare da shigewa tollet. Ita kuwa Momy da gangan ta aiki mustapha wajen RAUDA, duk neman yanda zata haɗa kansu, har shakuwa ta shiga tsakanin su, yanda zata samu sauƙi wajen haɗa su, aure. Sharifa Momy ta daga tace ta shigar da kwanuka kitchen, sannan ita kuma ta tashi domin zuwa gyarawa Daddy ɗakin sa, kasancewar shi Daddy yace baya buƙatar ƴar aiki cikin gidan sa. Cikin shirin sa, Mustapha ya fito, yana sanye da ƙananan kaya, Baƙin wandon jeans, da Red colourn riga, gashin kanshi kuwa kwance kasancewar mustapha ba ma'abocin Aski bane, sai Uban gyara da kuma mayuka da yake amfani dasu, wa kansa, toshe idanun sa, yayi da baƙin glass, ɗakin Momy ya nufa, bata ciki, fitowa yayi ya shiga na Daddy, tana gyaran ɗakin ya sameta, ki bani aiken naki Momy zan wuce. Murmurshi Momy tayi sannan, ta fito daga ɗakin Daddyn nasu, shi kuma mustapha na biye da ita har cikin ɗakin ta, bakin gadon ta ya zauna kafin, Momy ta ɗauko sarƙar tare da Zama kusa da mustapha. " Ga saƙon dan Allah ka tabbatar ka bata hanu da hanu, ka shiga har cikin falon nasu, ka gaishe da mamyn nasu, koh. Karɓa yayi tare da ce mata insha Allah zan shiga, sannan ya tashi ya fice Momy na masa a dawo lfy, tare da fatan Allah ya haɗa kansu da RAUDA, dan ta fahimci kamar akwai ƙiyayyar RAUDA cikin Zuciyar mustapha. A falo ma, a dawo lfy Daddy yayiwa mustapha, sannan ya fice daga cikin gidan. Hajiya Turai mahaifiyar RAUDA, suna zaune tare da Hajiya Hindatu, ta kawo mata saƙonta, na Niger, dariya Hajiya Turai tayi tare da cewa. " Amma dai Hindatu na gode sosai, Wlh ai daman nasan harkar ki Babu wasa cikin sa, kinsan yanda nake jin tausayin yarinyar nan, na rasa wani irin soyayya take yiwa wannan yaro, bata sauraron ko wani Saurayi ita dai kullum mustapha shine a bakinta, shiko ya maida ita shasha baya ma sauraron ta. Dariya Hajiya Hindatu tayi tare da cewa. ' to yanxu kam ya shigo hanu, dan wlh muddun kunyi amfani da wannan magani dai-dai to tabbas sai Mustapha ya shigo hanun ku, kunyi yanda kuke so dashi, na gaya miki, wannan cikin abinci za'a sa masa ku tabbatar yaci abincin, wannan kuma ƙofar ɗakin sa, zaku barbaɗa, shima ku tabbatar ya, tsallaka, sai wannan turaren kuma, RAUDA ta tabbatar ta shafa shi duk sanda zasu haɗu dashi. Idan kuka bi wannan dokokin dana lissafa muku, to kun sami mustapha kun gama, ina ita RAUDA take, taxo na ja mata kunne sosai ma tukunna. " Bata Nan ai Hajiya ta tafi makaranta, amma insha Allah yau tana dawowa, a gidan su zata kwana, domin ganin ta gabatar mana da wannan aikin. Yawwa da dai zaifi, bari na koma gida Hajiya, nabar sakina kwance zazzaɓi na damunta. " Ayyya Allah ya bata lfy, na gode sosai Hajiya Insha Allah zaki ganni duk abunda ke faruwa zakiji. Allah yasa muji Alkairi cewar Hajiya Hindatu. Har compaunt ɗin gidan Mamy ta rakata, Hajiya Hindatu na fita mustapha na shigo da hancin motar sa cikin gidan. Salim ƙanin RAUDA dake buga boll tsakar gidan Mamy ta shige zuwa cikin falon ta. Parking mustapha yayi ya ɗan juma kafin ya fito daga cikin motar, kiran salim yayi, da gudu salim ya ƙaraso. Tambayar sa Mustapha yayi ko Abban su nanan. " Ya mustapha yana nan, ka shiga yana nan ɗakin da suke ganawa da baƙi, yana tare dasu. Ɗakin Mustapha ya nufa, yana riƙe da hanun salim suka shiga. Mustapha bai daɗe da shiga ɗakin baƙin Abban nasu ba, itama RAUDA ta shigo cikin gidan, dawowar ta kenan daga school......... Kuyi manage da wannan🙏🏻🙏🏻🙏🏻 *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah ce)*[1/24, 10:06 AM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ Kuyi hkr masoyan Indo a birni na rashin jina kwana biyu da bakwayi, hakan ta faru ne, sakamakon tafiya da nayi zuwa garin Jigawa, gashi muna hidimar bikin, sister na, Please kumin afuwa zuwa ranar talata idan Allah ya dawo dani Gombe lafiya, sai mu ɗaura daga inda muka tsaya, karku gaji da jira na, abunda yasa kuma nake ɗan yin typing ɗin Sara da sassaqa, Saboda shi book ɗin na kusa gamasa ne, Please kumin afuwa, tare da addu'ar Allah ya dawo dani gida lfy. Please ku taya ni share ɗinsa domin ya samu ya isa zuwa ga masoyana. *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah ce)* [1/29, 11:53 AM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 _________________________ *Masha Allah my ƙawalliya ƙawar Arziki Zarahn Abdul, momyn Ahlan, ina tayaki murnar kammala wannan shahararren book ɗin naki wato (Shuhuda) Allah ya bamu ikon amfani da darusan dake cikin sa, Abunda kikayi kuskure kuma Allah ya yafe miki, congratulation momyn Ahlan🤝🏻* _________________________ *Alhamdulillah fan's gani na faso dole na daure nayi muku typing yau saboda ƙaunar da kuke yiwa wannan book, waɗanda suka kira ni, suka min murnar kammala book ɗina na Sara da sassaqa baya hana gamji toho da kuma waɗanda suka turo min text har zuwa kan waɗanda suka min murna ta online tare da fatan Alkairi, na gode sosai da ƙaunar ku gareni.* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*•••••••2️⃣5️⃣ ➡️ 2️⃣6️⃣ Cikin gajiya RAUDA ta shiga cikin falon nasu, a saman kujera ta faɗa tare da cewa. " Wash Wlh Mamy yau na gaji sosai, wani text mukayi mai zafi kaina ciwo yake ina gani ma, wanka zan shiga nayi na kwanta. " Amma dai ke RAUDA akwai malalaciya, yanxu kin dawo bazaki zauna kici abinci ba, sai kije kiyi wankan, idan yaso saiki kwantan, waya sani ciwon kan ma kona, yunwa ne. " Bafa yunwa bane Mamy, kawai text ɗinda mukayi ne, ya samin wannan ciwon kan. Shigowar Salim da gudu ne ya hana Mamy yin maganar da tayi niya, tace. " Lafiya ka shigowa mutane ɗaki da gudu salim cewar Mamy. " Mamy daman zan faɗawa Aunty RAUDA ne, ya mustapha yaxo yana ɗakin ganawar Abba yanxu haka. Murmurshi Mamy tayi domin kuwa mustapha yaxo mata a dai-dai, wannan shine first tagget ɗina akanka, daga yanxu zan fara wannan maganin, duk cikin Zuciyarta take wannan zancen, kallon salim tayi tace. " Naji koma wasan ka, manga na, ta masa maganar cikin sigar rarrashi, fita yayi abunsa, sannan Mamy ta dubi RAUDA tace, maza jeki ɗaki ki kwaskware fuskar ki, turaren da Hajiya hindatu ta bata wanda zata shafa a fuska, Mamy ta miƙo mata, tace maza ki shafa yanxu Hajiya hindatu ta kawo sa, tace indai kin shafa mustapha ya kalle ki, anwuce wajen, domin kuwa dole ya soki. Aiko cikin murna da zumuɗi RAUDA ta karɓi turaren tare da shigewa bedroom ɗinta da gudu, murmurshi Mamy tayi tare da yin kitchen domin yiwa Mustapha barbaɗe barbaɗe cikin ruwa da abinci, kasancewar tasan indai mustapha yaxo gidan Abba yana nan, dole saiya ci abinci, kafin ya tafi. Mustapha kuwa shigar sa, part ɗin bakin Abban ya samu saura mutum ɗaya ne, har ƙasa mustapha ya sunkuya ya gaishe su, kafin Abba ya masa nuni da gefen sa, yace yaxo ya zauna. Bayan Abba ya sallami bakon nasa ne, ya dubi mustapha Yace. " Muhammad Mustapha ne, ko Muhammad Habeeb, kasan bana gane ku, idan kuka haɗu waje ɗaya, gashi kuma Alhaji Haroun yace min shima Habeeb ya shigo ƙasar. Murmurshi Mustapha yayi yace. " Nine mustapha Abba, daman Daddy ne, yace naxo na karɓi sako wajen ka. " Ayyya Muhammad Mustapha, tashi mu shiga ciki to, sai kaci abinci, kafin na baka saƙon koh. Mustapha bai yiwa Abba musu ba, ya tashi ya bisa cikin gidan, a daining suka tarar da Mamy ta shirya abinci, gaishe da Mamy mustapha Yayi ta amsa cikin sakin fuska tana tambayar sa, mahaifiyar sa, tana lafiya yace mata, kafin Abba ya umurce shi da cewa ya zauna a daining ɗin, zaman kuwa sukayi, Mamy itace tayi seving ɗinsu, yayin da ta zubawa mustapha mai maganin, basu Kuma juma da zama ba, itama RAUDA ta fito cikin kwalliya, ta zauna kujerar dake kallon ta mustapha, wanda yana ɗaga idanun sa, ita zai kalla, tunda RAUDA ta zauna mustapha bai ɗago idanun sa, ba bare su haɗa da RAUDA, yadai ji Muryar ta, Abba ne ya kalli mustapha Yace. " Muhammad Mustapha, kaci abinci mana, an zuba maka Kuma. Sai a lokacin RAUDA tace. " Sannu da zuwa ya mustapha ina wuni. A dakile Mustapha yace. Lfy tare da ɗaukar spoon. Daga Mamy har RAUDA murna suke mustapha zaici abincin domin kuwa sunsan yana ci yaxo hanu. Ɗebo abincin mustapha yayi, har zai kai bakinsa sai yaji Ringtone din wayar sa, maida spoon ɗin yayi ya fasa kaiwa bakin nasa, tare da ɗaga wayarsa, ji nayi yace. " Ka samu bayanan, to tsaya dai-dai roat block ɗin gani nan zuwa yanzu, tashi mustapha yayi yacewa Abba. " Amin afuwa Abba, wlh wani sako zan karba mai mahimmanci, gun wani, gashi kuma baƙo ne, hanyace ta biyo dashi tanan garin zai shige, idan zai yiwu da an bani sakon saina samu na shige. Murmurshi Abba yayi yace. " Babu damuwa Muhammad Mustapha ai kana cin abinci cikin gidan nan, ke Turai jeki ɗauko masa wannan karamar jakar dana shigo dashi. Daga Mamy har RAUDA ji sukayi kamar an soka musu mashi cikin ƙirjin su, da mustapha ya tsallake wannan tarkon nasu, sunji mungun bakin ciki, haka dole Mamy ta shige ta ɗaukowa mustapha sakon ta basa, ƙarɓa yayi tare da yiwa Abba sallama, ya fice da sauri, tashi RAUDA tayi itama cikin sauri tabi bayan sa, tana cewa. " Ya mustapha baka jiba. Tsayawa mustapha Yayi daga buɗe murfin motar tasa, ya ɗago kansa, carap kuwa sukayi ido biyu da RAUDA, wani irin tsinkewa zuciyar mustapha yayi, kansa kuwa neman juye masa yake. " Subhanallah ya furta da ƙarfi tare da ambaton, innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, la'ilah ha'illah anta subhanaka inni kuntu minnazalimin, tare da zama cikin motar da sauri yana dafe da kansa, yafi 15 minute yana Zaune yana ambaton Ubangiji, Kafin yaji komai ya dawo masa normal, har lokacin kuma RAUDA na tsaye wajen, bai ƙara ɗago kai ya kalleta ba, saima wani tsawa daya daka mata. " Wai RAUDA me kike nema dani ne, kin dameni kin dami rayuwata, RAUDA duk wani take taken ki, na sani, Sona kike, to dan Allah zan roƙeki, ki ƙyale Ni, nikam bakya cikin matan da nake burin Aura, baki min ba, dan haka, ki sawa zuciyar ki, salama ki daina wahalar da kanki, iya gama faɗa mata haka, yasa hanun sa, ya dauko sarkar da Momy tace ya bata, ya wurgo mata tare da cewa idan kinga dama ki ɗauka Momy ce tace na kawo miki, sannan yaja motarsa da ƙarfi yabar wajen. Tsabar takaici RAUDA ta kasa motsi daga inda take, tsaye, hawaye kuwa ya wanke mata fuskar ta, sunkuyawa tayi ta ɗauki sarƙar sannan ta shige cikin falon nasu, tsayawa tayi ta goge hawayen ta, kafin ta shige su Mamy tayi bedroom ɗinta, Abba ne, ya kalli Mamy yace. "Turai Kamar akwai Abunda ke damun RAUDA koh naga yanayin ta, kamar ya sauya?. " Meka gani abban RAUDA, cewar Mamy. " Haka dai na gani kamar mood ɗinta ya sauya ba kamar yanda ta fita ɗazu ba. " To gaskiya ban sani ba dan ban lura da shigewar ta ba amma dai gaskiya Babu Abunda ke damunta. " Okey shikenan tunda haka kikace, bari na shige bedroom ɗina, ki samu kisa a gyara part ɗin baƙin nan. " Shikenan Abban RAUDA, za'a gyara. Bayan Abba ya shige bedroom ɗinsa ne, Mamy tayi bedroom ɗin RAUDA, tana kwance tayi rup da ciki sai kuka take mai tsuma Zuciya, hawaye kuwa harda majina, girgiza kanta Mamy tayi, tare da zama, ta fuskanci RAUDA tace. " Shikenan ke yanzu haka zaki zauna kullum kina yiwa namijin kuka, yanxu ke bazaki dage a matsayinki na mace ba, ki jawo hankalin mustapha, sai kace wacce kika fito daga ƙauye, ki tashi ki wanke fuskar ki, ki shirya zaki koma gidan su, mustapha da Zama har sai buƙatar mu ta biya, zan miki bayanin duk yanda zakiyi amfani da maganin, zamuyi nasara akansa insha Allah. Cikin kuka RAUDA take cewa. " Mamy na haƙura da ya mustapha domin ya faɗa cewa baya sona, Kuma mun haɗa ido shi, wannan maganin ƙarya ne Mamy, tunda Bayan mun haɗa ido dashi ne ya furta min cewa baya sona, na haƙura Mamy nasan mutuwa zanyi, domin soyayyar ya mustapha bazata barni nayi nisan kwana b........ Toshe mata baki Mamy tayi tace. " Ki daina furta waɗannan mugayen kalaman, dole ma mustapha ya soki kota Halin yaya, magani kuma yana da kyau, ki tashi nace kibi umurni na, ki shirya ki tafi, karkiyi zuciya akan abunda zuciyar ki, bazata ita haƙuri dashi ba. Tashi RAUDA tayi ba tare da ta kara cewa Mamy komai ba, tayi tollet. Shiko mustapha yana fita darect, wajen mutumin da sukayi waya yaje, wasu takaddu ya basa sannan sukayi Sallama ya wuce bank ya ajiyewa Daddy kuɗin sa, sannan ya dawo gida, a falo ya samu Habeeb Zaune yana danna waya suna game shida Sharif, ware idonsa mustapha yayi tare da cewa. " Yaushe ka dawo kai kuma. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " Tun ɗazu nakai 2 hours da dawowa. Zama mustapha yayi yana cewa. " Kace yau kabar Innah da kewa, ni nayi zaton ma ai sai mun bika da kayan kane. Dariya Habeeb yayi tare da cewa. " Wlh ƙauyen ne, yamin daɗi, mussaman dana samu Indo, gaskiya yarinyar tayi a rayuwa. Taɓe bakin sa Mustapha yayi, tare da cewa dake shashancin ku ɗaya ba, amma inbanda haka meye abun burgewa wajen, wannan taɓaɓɓiyar wacce ta addabi al'ummar garin, ni kaga bari na shige inada abunyi cikin ɗaki, tunda naga kaima baka da abun faɗa. Murmurshi Habeeb yayi tare da cewa. " A fito lfy daman ai nima bance ka zauna ba,. Shidai Mustapha bai tankawa Habeeb ba ya haura sama. Sharif ne ya cewa Habeeb. " Ya Habeeb, ya mustapha ya cika masifa, kullum yana cikin faɗa, ni tsoronsa ma nake ji wlh, kuma fah ya Habeeb ance duk mai faɗa mungu ne. Haɗa ransa Habeeb yayi tare da cewa. " Kul na ƙara jin wannan maganar a bakin ka, yayan naka ne, yake masifa, har kike cewa mungu, to wlh idan ya jika, wlh saina lahira yafika jin dadi kadai san halinsa. Tura bakin sa Sharif yayi tare da cewa. " Kayi haƙuri ya Habeeb bazan sake ba. Murmurshi Habeeb yayi yace. " Ya wuce Autan Momy, game ɗin suka cigaba dayi, sallama RAUDA tayi hanun ta janye da akwati. Amsawa Habeeb yayi cikin fara'a yace. " A'a baƙuwar muce ta dawo, kinga mun dawo a dai-dai kuwa, nima ban juma da shigowa, ba. Murmurshi RAUDA tayi kafin ta ƙaraso, tace Lallai munyi anko, kenan nima yanxu ina zaune naji kawai ina son dawowa, Sharif ne ya amshi akwatin nata, yana ƙoƙarin haurawa dashi, ita kuma ta zauna kusa da Habeeb suka cigaba da magana. Mustapha daya fito da key a hanun sane, yayi turus sakamakon ganin RAUDA Zaune yarinyar daya bari yanxu cikin gidan su, tsuka yaja tare da cewa. " Mayyah kawai, sannan yasa kansa ya fice ba tare daya kallesu ba. Girgiza kansa Habeeb yayi, cikin takaicin mungun hali irin na mustapha, da nunawa mutum ƙiyayya a fili. *DASINA* Tafe take riƙe da kara a hanun ta, tana raira waƙarta. " Ayya raye ayye ayye, ayyya raye ayye dije, zaman gidan wani tilas ne, ba'a kanki ne aka fara ba, ba'a kanki ne za'a ƙare ba, ƴar tsohuwa mai lallen zo yaki nan, kunsa mata amaryar nan n........ Maganar da malam Yakubu makaho ya mata shine ya katse mata waƙar tata, cikin murna tana dariya tace. " Lah Baba Yakubu kaine, Aradu ban lura dakai ba, ina zakaje da sassafen nan haka. " Yo Indo ina zanje kuwa idan ba Bara ba, bara zan fita mu sami na cefenen gida. " Kai Baba Yakubu yanxu yanda kake da tiƙeƙen ƙaton Yaron nan, Sani bazai je yayi sana'a ya kawo muku na cefenen ba, har sai kai da kake makaho kaje kayi bara ka Kawo kuma yaci, to aradu ni a gidan ya Tanimu shine yake bada kuɗin cefene, gashi kuma baban mu yana da idanunsa, amma dai Aradun Allah Sani yayi Asara. Dariya Mlm Yakubu yayi, domin kuwa yasan duk haukar Indo, yaudai maganar data faɗa tana kan hanyar gaskiya, sannan Yace. " To ya za'ayi Indo tunda shi bazai nema ba, aini dole na nema, kodan ƙananan yara. Kallon dubu ɗayan da Mama ta aiketa siyo kwanon shinkafa da rabin mudun wake tayi, sai kuma ta kalli Mlm Yakubu, ta sake kallon dubun kai tsaye tace. " kaga Baba Yakubu karka je barar nan, dan wlh na tsani barar nan, gashi kai Kuma ba ɗan jagora kake dashi ba, badai kuɗin cefene kake nema ba, ta gashi wannan dubu ɗayan kaje kayi cefene ba shikenan ba. " Ina kika samo dubun indodo, da zaki bani?, ya tambaye ta cikin mamaki. Ƙarya Indo ta zafgawa domin tasan idan tace masa kuɗin aika ne bazai karɓa ba, domin kuwa jinin Indo da Mlm Yakubu yaxo ɗaya sosai suke shiri, sannan tace. " Tsintarta nayi ɗaxo daman zan kaiwa Mama ne nace nayi tsintuwa, kaga tunda yanxu kai kana buƙata, saika karɓa. Karɓa Mlm Yakubu yayi yana shiwa rayuwar Indo albarka, kama sandar tasa Indo tayi tace muje Baba Yakubu na rakaka gida, sai ni kuma na wuce gida. Tafiya sukayi Indo ta raka Mlm Yakubu har ƙofar gidan sa, sannan ta ruga da gudu tayi gidan su. Mama na Zaune ta ɗaura ruwa a murhu tana zaman jiran Indo ta kawo mata shinkafa ta tsince ta saka cikin tukunyar, sai ganin Indo tayi ta shigo mata hanu ziƙau babu komai, tsayawa tayi akan Mama tayi shiru ba tare da tayi magana ba. Kallon ta Mama tayi sannan tace. " Ya kika tsaya a kaina ne, yiwa zaki bani magani ina aiken dana miki. Kai tsaye Indo tace. " shagon ɗan tasin a rufe ne. " Arufe kuma cewar mama, to bani kuɗin na aika jummalo gidan su, Hadiza ta sayo min. Kallon mama tayi tana turo baki gaba tace. " *Nayi miki sadaka da kuɗin* " Kinyi min sadaka da kuɗin, mama ta tanbaya, ban gane kinyi sadaka da kuɗi ba. " *Mama Baba Yakubu makaho ne, na haɗu dashi yanxu a gangare, zai tafi bara, shine yamin magana, yace zaije Bara ne, ya samo kuɗin cefene, shine ni kuma ya bani tausayi, na basa sadakar dubun taki, tunda ke kina da mai baki, ya Tanimu, shi kuma bashi da wanda zai basa, Sani ma shege ne, baya basa*. Kallon takaici Mama ke bin Indo dashi, domin kuwa yanxu ta fara tsoron lamarin Indo, kodai tana da aljanune a kanta, cikin haushi Mama tace. " Shikenan kin raya gidan wasu ke kuma kin kashe naku gidan, yau wasu zasu ƙoshi mu kuma zamu wuni da yunwa, yanxu Indo idan banda sakarci Irin naki kin taɓa ganin inda mutum yayi kyauta da abunda ba nasa ba, to Kuma Wlh yau sai kinsan kinyi kyauta da dubu, danko yau Babu mai hanani cin ubanki cikin gidan nan. Danƙo Indo Mama tayi, ta rufeta da duka, ihu Indo take tsakanin ta da Allah kamar wacce mama take yanka ta, Baba saude maƙwabciyar su, da taji ihun Indo yayi yawa ne, yasa ta, zagowa cikin gidan, daƙyar ta ƙwaci Indo hanun Mama tana cewa. " Haba mero yanxu wannan dukan da kike yiwa yarinyar nan ai yayi yawa, babu kyau fah yawan duka. " Ki barni mero na daki yarinyar nan yau ko zan huce, wlh na gaji da halin Indo, kullum da Abunda yarinyar nan take jawo min, masifar yau daban ta gobe daban, yanxu dan Allah Saude ki duba ki gani, tun da hantsi na ɗaura sanwar abinci, na aiki yarinyar nan Indo taje ta siyomin shinkafa na bata gudan dubu, jummalo na kwance bata da lfy, kinga har yanzu ƙarfe 1:00 na azahar ta dawo min, babu aiken dana mata, wai take cemin tayi sadaka da dubu ɗayan, sai kace ƴar gidan wani babban attajiri, da zakiyi kyautar dubu. " Ashsha haba yanxu ke Saboda baki da hankali, ki ɗauki kuɗin abincin ku, ki kyautar, baki kyauta ba, Indo dan Allah mero kiyi hkr, kibar maganar ta shige yaran yanxu ne saida hkr, duk yawanci haka suke. " Zan haƙura Saude sai wlh yau baxan bawa Indo abinci cikin gidan nan ba, sai daita kwana da yunwa, kallon Indo Mama tayi tace, zaki fice minne da gani kosai na taka miki wuya, shashasha marar lissafi. Ihu Indo ta ɗauko ta zunduma, sai kuma tayi waje da gudu tana ihu, girgiza kanta Baba Saude tayi, sannan ta kara bawa Mama hakuri ta koma cikin gidan ta. Tashin jummalo Mama tayi ta dauki ɗari biyar tace taje ta sayo musu shinkafa. Da gudu ta shiga gidan Innah tana ihu. " *Wayyo Allah na shiga Uku na lalace wayyo Allah Mama zata kasheni, wayyo Allah bayana ya kare* Jin ihun Indo yasa Innah fitowa da gudu rike da zani a hanu, tana cewa. " Subhanallah wani shegen ne, zai kashe ki? " Innah Mama zata kashe ni, ta karya min bayana, tamin duka saura kaɗan ma ta jefani wuta Allah ya kawo Baba Saude ta ƙwaceni kuma tace wlh yau bata bani abinci ba. " Ita mairon ce, tace haka, cewar Innah, me kika mata to, nasan dai ruwa baya tsami banxa. Tura bakinta Indo tayi tace. " Wai dan kawai ta aikeni da dubu, shine na haɗu da Mlm Yakubu, zashi bara, wai basu da kuɗin cefene, shine fah na mata sadaka da kuɗin nace yaje yayi cefene. Salati Innah ta ɗauka tare da cewa. " Yanxu daman akan ɗan wannan abun mairo ta miki wannan mungun dukan, dan kawai kin mata sadaka kin nema mata lada a wajen Ubangijin ta, to muje gidan naku naji dalilin da ta miki wannan dukan. Mayafinta Innah ta ɗauka tasa Indo a gaba tana mita har gaban Mama. Ganin Innah da Mama tayi ta tashi da sauri ta ɗauko mata taburma tana Cewa. " Sannu da zuwa Innah lale maraba. Cikin masifa Innah tacewa Mama. " Bana son sannu da zuwan ki, ki riƙeta, yanxu mairo kan dubu shegiya kika yiwa indo wannan dukan, saboda kawai ta nemo miki lada wajen Ubangijin ki, kunce bakin zanin ta, Innah tayi, ta ɗauko gudan dubu ta wurgawa Mama tace, ga kuɗin ki, ladan sadakar kuma Allah ya bawa Indo, duka kuma da kika mata kin daki Allah ya Isa. Murmurshin takaici Mama tayi sannan tace. " Kiyi hkr Innah, ki karɓi kuɗin ki, nikan bazan riƙe kuɗinki ba, Allah ya huci Zuciyar ki, kiyi hkr dan Allah. Harar Mama Innah tayi tace. " baxanyi hakurin ba, abinci Kuma kar Allah yasa ki bata, muje Indo kici abinci harki kyautar. Shigewa Indo tayi tana yiwa mama dariya harda gwalo, tabi Innah suka tafi, gidan ta. Girgiza kanta Mama tayi cikin jinjina ƙarfin hali irin na Innah, ita daya kamata tayiwa Indo faɗa wai itace take ɗaure mata gindi, ya Allah ka shirya min Indo cewar mama. A hanya Innah da indo suka bi wajen mahauta Innah ta saya musu nama, sanna suka dawo gida, zama sukayi Innah ta dubi Indo tace. " Ki saurareni da kyau kiji Abunda zan faɗa miki, duk cikin ƙauyen nan duk wanda ya miki ki masa karki bari, aci kashi a kanki, domin kuwa naga an fara samiki ido cikin garin nan. Dariya Indo tayi tace. " Innah yo dama wa zan ƙyale, yanxu ma jira nake Allah ya haɗani da garba naci ubansa la'ada waje zaisan yamin Asarar ƙosai da koko na, dan uwarsa. *Yawan sharhi yawan typing idan kunyi sharhi kaɗan nima kujini shuru sai bayan sati biyu, idan Kuma kunyi sharhi mai yawa kujini kullum tare da typing mai yawa*. *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah ce)* [1/30, 1:00 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽* 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻 *Na* *r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸* *(մʍʍմ ηαςʍα)* 👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻 *Marubuciyar* *Sauyin Rayuwa* *Nasmah ko Nasirah* *Sara da Sassaka* *D̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞i̸͟͞c̸͟͞a̸͟͞t̸͟͞e̸͟͞d̸͟͞ t̸͟͞o̸͟͞* *Aunty fauza ƴar Amana* Uwa mabada Mama ƙaunar ki daban take gareni domin keɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake. Allah yabar ƙauna. *S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢* *Aunty Hauwa Maman Uswan* Ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya 🙏🏻 TALLAH TALLAH TALLAH Ina kuke makaranta littattafan Hausa ku matso kusa ga dama ta samu, ni ɗinnan dai *(UMMU NASMAH)* na shirya tsaf domin gabatar muku da sabon Novel ɗina, wanda zai nishaɗantar daku ya faɗakar daku, yasa ku cikin tunanin, mai taken *(RUƊANIN ZUCIYAH BIYU)* Wannan littafin yasha banban da sauran littattafan dana saba gabatar muku, labarin yana tafe da Soyayyah mai ban tausayi, ƙiyayya ƙyama tsangwama, tausayi, littafin zai ruɗa tunanin ku, kudai ku cigaba da biyoni domin karku bari a baku labari da abaku gara ku bayar, karku manta da sunan sa *(RUƊANIN ZUCIYAH BIYU)* Nice taku mai son farin cikin ku a koda yaushe, *UMMU NASMAH CE*✍🏻 *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *P*•••••••2️⃣7️⃣ ➡️ 2️⃣8️⃣ " Kinga Indo tashi maza ki hura wutar nan, yau shinkafa zamuci da jar miya. Tashi Indo tayi, ta fara kici-kicin hura wuta, domin kuwa Indo babu laifi akwai ƙoƙarin zama tayi girki amma idan taga dama, fah. Suna aikin su suna taɗi har suka gama, cin abincin sukayi, saida akayi la'asar sannan Indo ta koma gidan su, siɗi siɗi ta shige ta ɗauki allonta tayi makaranta, tun biyar da rabi aka tashe su, tafe Indo take ita da Hansai, suna zance, Hansai ne tace. " Indo ɗazu da zan tafi makaranta naga lami ta dawo daga tafiyar da tayi, har take cemin Anjuma zata shiga gidan ku. Tsale Indo ta daka, cikin murna tace. " Tsakani da Allah Hansai da gaske kike lami ta dawo. " Wlh da gaske nake, ta dawo na ganta, da idanuna. "Wayyo Allah daɗi, aminiyata ta dawo, rugawa Indo tayi da gudu tare da mikawa Hansai allonta tace ki kaimin gida. Lami aminiyar indo ce ita da Hansai, itama lami hatsabibiyace sai dai bata kai Indo ba, shiyasa sukafi shiri da Indo fiye da Hansai. Aiko Indo kiciɓis sukayi da Lami a ƙofar gidan su, cikin murna suka ɗane juna, Lami tace. " Ƙawas andaɗe fa ba'a haɗuba, tun ɗazu naje gidan ku, Mama tace kinje makaranta, har gidan Innah naje tace bakya nan. " Kedai Lami bari Wlh bana jin daɗin garin nan da bakya nan, ayyya Lami ya mustapha na dai har yanzu baixo ba sai sau ɗaya kawai nanma bai daɗe ba ya tafi, amma inaga zan lallaɓa Innah muje Birnin nan, Allah indai har naje baxan dawo ba. Labarin Habeeb Indo ta dinga bawa Lami, har pictures ɗin da sukayi, ta karasa maganar da cewa. " Kinga wata shegiyar kama kuwa da suke yi, gashi yana da kirki, sosai ba irin ya mustapha ba, kullum yana cikin haɗiye rai. Shewa Lami tasa tare da cewa, " Ke ƙawata, kwantar da hankalin ki, ba sai kinje ba, tunda Innah tana cikin garin nan dole zaizo shi, dan haka sa ranki a inuwa, amma gaskiya naso haɗuwa da wannan Habibun, yanxu dai ba wannan ba, ina zamuje neman magana kinsan an daɗe ba'ayi ba. Shuru Indo tayi tana tunani, sai can tace. " Muje shagon Mlm Ibrahim ko zamu samu Garba, muci ubansa daman ina da cikin sa. " Muje Lami tace tare da kama Hanun Indo suka tafi. Aiko Garba dake zaune yana jirawa babansa shago, ya hango su Indo suna, zuwa, tashi Garba yayi ya ruga da gudu domin kuwa yasan muddun ya shiga hanun su Indo ya shiga Uku, rufa masa baya suma sukayi da gudu, amma ina kafin su iso Garba ya tsere musu. Haushi ne ya kama Indo cikin takaici, ta dubi Lami tace. " Shege ya gudu, Ranar mafah haka yamin ya tsere Min. Kallon shagon su Garba Lami tayi tace. " Kinga Abunda zamuyi kawai mu ɗebi, biskit da minti muyi gaba, shi kuma shikenan, ki barsa. Haka kuwa akayi suka shiga shagon suka ɗebi biskit da minti, sukayi tafiyar su, Indo kam a hanya, ta rabawa yara wanda ta ɗiba ko ɗaya bata ciba. Lami ce ta kalleta tace. " Ya kika rabar da naki baki ciba, bakya sone. " Ina so mana kawai dai bazan ciba ne, nasan yau sai baban garba ya kaimu ƙara wajen mai gari, akan kayansa, kinga basu da hujjar da zasuce na biyasu kayan su, sai suje su nemi yaran dana bawa su karbi Kayan su a hanun su. " Amma dai ke Indo akwai shasha, yo su kuma yara ina ruwan su, aida kici da karki ci, akan kene kika ci, garama kici idan yaso a miki hukunci da tushe. " Kan Uba cewar Indo, uban waye ya isa ya hukunta ni akan abunda banci ba, to wlh ba'a isa ba, *Uwar kuturu ma tayi kaɗan balle na makaho* idan kuma akace za'a hukunta ni to wlh shima kansa mai garin saiya gane kurensa. " Mtss matsalata dake Indo rashin wayo sai kitayi ni wlh saina ci, sai dai duk abunda zai faru ya faru. " Na Yadda banda wayon kuma wlh karkici kema ki rabawa yara, kamar yanda nayi idan kuma kikaci to wlh duk hukuncin da mai gari ya yanke mana, akanki ne ke ɗaya, dan wlh *Banci kaza ba baxanyi aman gashi ba* " Mtss sai kuma kiyi, tafiyar ta, Lami tayi tabar Indo tsaye a wajen. Itama Indo tsukar tayi, ta tafi tana zagin Lami cikin ranta. Gidan su, ta shige Mama ta samu zaune tana talge, kusa da jummalo ta zauna dake zaune tana, karkarwar zazzaɓi, sai hawaye dake zuba cikin idanunta, kallon jummalo tayi tace. " Sannu jummalo ya jikin naki. Hawaye ne, ya gangaro fiskar jummalo tace. " Mutuwa zanyi Indo, dan Allah ki nutsu ki daina ɓatawa Mama rai kinga ni zan tafi na barki da Mama, dan Allah ki daina ɓata mata rai. Kallon ta Indo tayi, sai kuma ta tuntsire da dariya, tace. " Kai jummalo duk zafin ciwon ne, haka, wlh yau da Innah kika faɗawa Maganar nan da kinsha zagi. Tana maganar ne, sai kuma taga Idon jummalo yana juyewa, sai kuma ta fara wani irin nishi, tsoro da Indo tajini yasata kwalawa mama dake madafi kira. " Mun shiga Uku mama kixo jummalo zata mutu, wai daman da gaske kike mutuwar, zakiyi, wayyo Allah. Da gudu Mama ta fito daga madafi, tayo kan jummalo tana girgiza ta, himar dinta mama ta dauko, tasa Indo ta kama mata, jummalo suka fito da niyar zuwa chemist amma ina kafin su ƙarasa fita daga gidan jummalo rai yayi halinsu, kallon Indo Mama tayi taga ita bata sanma jummalo ta rasu ba, cikin dauriya da ƙarfin hali tace. " Mu koma Indo mu ajiye ta, tayi bacci jikinta yayi sauƙi. Juyawa sukayi suka kwantar da jummalo, Mama tacewa Indo taje ta mata kiran Innah. INDO na fita Mama ta fashe da kuka, tare da rungumo jummalo a jikinta tana mata addu'a. Indo bata wani juma ba, suka shigo tare da Innah, da sauri Innah ta ƙaraso gaban Mama ganinta tana kuka tace. " Mairo lfy meya faru, kike wannan ajiyar Zuciya haka. " Innah jummalo ta rasu, ta tafi ta barni Innah. Daɓas Innah ta zauna a ƙasa tare da sakin kukan itama, sai aka rasa waye zai bawa wani hakuri tsakanin su. Allah sarki Indo, wato duk inda dan uwa yake yana son ɗan Uwansa, kasa kuka Indo tayi, ta zauna itama kusa da jummalo, sai kuma ta tashi ta fice da gudu, ashe Baba ta kira, tare suka dawo Baba yaxo ya same su sai sharbar kuka suke. " Haƙuri Baba ya basu tare da musu nuni da cewa, jummalo yanxu bata buƙatar kuka a garesu, addu'a take bukata, Allah sarki rai baƙon duniya, jummalo kwanan keso tayi, Indo da Innah kuwa kwana sukayi basuyi bacci ba, washe gari da misalin karfe goma aka kai jummalo makwancin ta, Indo tasha kuka Ranar har idanun ta suka kasa buɗuwa, Innah ce ta kira Baba tace yaje ya nemi waya ya sanar da Haruna rasuwar jummalo. Haka kuwa akayi Baba ya kira Abokinsa Haruna ya sanar masa. *DUTSE LOCAL GOVERNMENT* Hira suke ciki falon dukan su, suna zaune, har Habeeb, mustapha ne kawai baya cikin su, duban Momy Habeeb yayi yace. " Momy akwai maganar fah da nake son na sanar dake, shi Daddy na sanar masa. " Okey ina sauraron ka Habeeb. " Momy daman ina son jibi idan Allah ya kaimu zan koma London, saboda ina son zan sanar dasu cewa nabar aiki dasu zan dawo gida na cigaba da aiki, so idan na koma zan tattaro duk wani abu da yake nawa na dawo, bazanfi sati biyu ba zan dawo insha Allah. Murmurshi Momy tayi cikin murna tace. "Alhamdulillah, daman Abunda nake so kenan Habeeb, nafi son aikin ka, anan gida Nigeria, naji daɗin wannan Albishir da kaxo min dashi, Allah kuma ya kaimu jibin lfy. Murmurshi Habeeb yayi ya amsawa Momy da ameen sannan ya dubi, RAUDA yace. " Ke Malama, wai yau bazamu ci abinci a cikin gidan nan bane, naga kamar baku da niyar yi. Dariya RAUDA tayi tace. " Kai dai kace yunwa kake ji kawai idan banda haka yaushe ma akayi breakfast, ta inda ya mustapha yafika kenan, shi babu ruwan sa, da yawan ci. Dariya shima Habeeb yayi yace. Wai damma shi mustapha baya gari, da yau mun gwada mun gani nida shi waya fi wani ci. Kallon mamaki RAUDA tayiwa Habeeb, cikin Zuciyarta tace, haba shiyasa tun daya fita jiya shigota gidan nan banga ya dawo ba, ashe tafiya yayi, na shiga Uku anya wannan maganin namu akwai Sa'a cikin sa, kuwa. Sharifa ce, tace. " Momy da gaske ya mustapha tafiya yayi Babu Sallama yau. Murmurshi Momy tayi tace Sharifa. " Ehh shima baisan da tafiyar ba, sai da ya fita office ake sanar dashi, yaje inugu zasu gana da wani Criminal amma ina ga ya dawo gobe insha Allah. " Allah ya kaimu Momy ya dawo dashi lfy. Da ameen Dukansu suka amsa sannan Habeeb yace shi zai shiga ya kwanta. Tashi RAUDA tayi cikin ɓacin rai tayi kitchen ita da sharifa suka bar Momy zaune a wajen. Da dare bayan daddy ya dawo sunci abincin dare yake sanar da Momy mutuwar jummalo, sosai Momy ta taji mutuwar a jikinta, shi kanshi Habeeb yaji mutuwar domin yasan jummalo zuwan sa da yayi, yarinya ce mai nutsu da tarbiyya, gata da tausayin iyayen ta, daddy ne yacewa Momy. " A'ishah inaga Ranar Laraba, zaku shirya gaba ɗaya zamu tafi dasina ta'aziya, da jibi nayi niyan mu tafi, to sai kuma gashi Habeeb zai koma jibin shiyasa nace, gara mu bari idan ya tafi mu kuma washe gari sai mu tafi shi mustapha munyi waya dash daga inugu zai wuce Dasina zamu haɗu acan. " Shikenan Alhaji Allah ya kaimu jibin idan yaso saimu wuce dukan mu, har RAUDA. Nisawa RAUDA tayi tace. " MOMY ai ina da school babu Halin naje, zan dai koma gida idan kun dawo saina dawo nima. " Okey Allah ya kaimu cewar Momy. Haka kuwa akayi Ranar talata Habeeb ya wuce London tare da bawa Sharifa sakon idan taje, dasina Innah ta nuna mata Indo tace yana gaishe ta, Kuma yana mata ta'aziya, idan kuma ta samu network ta kirasa a waya ta haɗasa da Indo. Ranar Laraba da safe su Momy suka ɗauki hanyar DASINA, daddy ne yayi waya da mustapha yake tambayar sa yaushe zai iso Dasina, sanar dashi yayi cewa sai gobe idan Allah ya kaimu, sannan daddy ya kashe wayar sa, RAUDA suka fara sauƙewa a ƙofar gidan su, kafin suka ɗauki hanya, tare da direban Daddy.................... Dan Allah kuyi hkr da wannan wlh yau ina da makaranta, shiyasa ban samu nayi muku typing mai yawa ba. *Vote* *Share* *And* *Comments* *Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻* *(Ummu Nasmah ce)*