[ 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 1&2 Please🙏🏻kuyi _____ 'Yanmata ne guda biyu suke tafiya cikin nutsuwa,kana ganinsu kasan bazasu wuce shekaru goma sha takwas ba,d'ayar tana Sanye cikin uniform na islamiya,tanada duhun fata kad'an,a hankali ta juya ta Kalli qawar tata, wadda take Sanye cikin kayan gida,babu uniform din ajikinta saide dogon hijab irinna d'ayar,wanda yazo mata har qasa,kalar hijabin ruwan toka yayi mutuqar qawata farar fatarta,Wanda kana gani kasan cewa hutu dakuma Jin dadi ya ratsa fatar tata. Jiddah tace"MAWAHIB,kiraba mana musu dan Allah" Ahankali tajuyo dara daran idanunta wanda yayi kama Dana mejin bacci, ta Kalli qawar tata, sannan tace"musun me Jiddah?" Wadda aka Kira da Jiddah tace"wallahi musu muke dasu Hassan da Hussainin gidanmu,nace duk unguwar Nan sukadai ne 'Yanbiyu matasa, shine sukace min wai Yaya ASHRAF din gidanku Shima 'Yanbiyu,nikuma nace ba 'Yanbiyu bane, Yaya Ashraf ne kadai yayanku,saboda nide tunda nake dake,Kuma duk yanda nake qawance dake,baki taba cemin kunada 'yanbiyu a gidanku ba" Saida ta yatsina kyakykywar fuskarta mai cikeda gashin gira alamun batason maganar, sannan ta motsa dan qaramin bakinta Mai launin pink,tace" 'yanbiyu ne,d'ayan baya zuwa sosai shiyasa baki sanshi ba,ai kinsan Yaya Ashraf dinko?,toshima d'ayan kamar kinsan shi,yanda kikaga Yaya Ashraf Shima haka yake,yana Nan kullum yana fama da uniform,basuda banbancin kamanni, komai nasu iri dayane,nikaina idan suka hadu su biyun bana Iya banbance su,saboda komai iri daya suke sakawa,kawai de hali ne kowa da irin nasa" Cikin mamaki Jiddah tace"ashe Ana Samun 'yanbiyu maza manya kamar Yaya Ashraf,? Amma Mawahib baki taba bani labarinsa ba" Cikin sauri Mawahib tace"menene hadina dashi dazan baki labarinsa? wannan marar imanin inani inashi?, halinsa daya da mahaifiyarsu,duk yanda kike tunaninsa yawuce Nan,miskilancinsa yayi yawa,baida fara'ah,kenifa bari Kiji Infada miki na tsaneshi, tun saudaya dana ta6a yimasa laifi ya Sumar dani, daga ranar naji nasake tsanarsa" Cikin sauri Jiddah ta zaro ido(😳) Tace"nashiga uku Suma fa kikace?" Cikin tabbatar wa Mawahib tace"suma kuwa,Ina zaune Yaya Ashraf yazo yacemin naje nagyara masa dakin su,Wai ashe shine zaizo daga Abuja,nikuma bansan ranar zai dawo ba,dana gama gyaran saina dan kishingida akan gadon su,nadan dora kaina a wani fillo Mai laushi,Bansan lokacin da bacci ya daukeni ba,daya dawo yaganni a'inda yake kwanciya,kuma nadora kaina akan fillonsa, shine ransa ya6aci,daya damqi gashin kaina bansan lokacin dana saki ihu ba,shine yasaka kaina a cikin sink din toilet dinsu yabude ruwan,nide nasan yasakani a ruwa,amma daga Nan bansake sanin inda kaina yakeba,Sai farkawa nayi naganni a kwance a gadon dakina" Cikin tashin hankali Jiddah tace"innalillahi....amma Abbanki baice komai ba?" "Jiddah mezaice tunda sun dauki power sun bashi?,haka itama NABIHA yata6a jimata targade ahannu,shiyasa nida ita bamaso yazo gida, musanman ma ni,na tsaneshi Jiddah" Jiddah tayi ajiyar zuciya tace"A a Mawahib,kidena fadar haka,koba komai ai dan'uwan ki ne, gidanku daya,sannan kobabu wannan dangantakar,shidin dan'uwan ki ne musulmi, Kuma babu dadi ka dinga cewa ka tsani mutum,Amma Kuma nayi mamakin yanda naji labarinsa a wajanki,saboda su Hassan din gidanmu har cemin sukai idan yazo har kudi yake rabawa mutane abakin get dinku, wani lokacin ma harda kayan abinci,toke menene ma yakaiki kwanciya a gadonsa?" Cikin sauri tace"Gadonsa ne shi kadai?gadon su ne shida Yaya Ashraf" Jiddah tace"duk da haka nide Ina kokonto akan wannan halaiyar tasa dakika fadamin,mutumin dazai dinga yin Alkhairi da kudinsa na aljihunsa shine za'a yi masa wannan shedar?" Cikin taqaici Mawahib tace"to Jiddah aikuma Sai kiyi,ya Ina fada miki mutum bashida Imani kina min maganar wani kudi,kudinsa na banza da wofi...? ni Kinga tafiya ta" Tana gama wannan maganar tayi gaba tabar Jiddah a tsaye a wajan cikeda mamaki,Jiddah tasaki ajiyar zuciya tabi Bayan Mawahib da kallo, meyake damun qawarta ne?aiko wani taji yana aibata dan'uwan nata kamata yayi ace Sai inda qarfin ta Yaqare,amma suna gida daya,ana Samun wannan matsalar?(🤔) ****** Tana shiga gida, cikin fara'ah megadinsu dayake zaune a kofar get din gidan yace"yanmatan Mamy har andawo daga islamiyar?" Cikin ladabi tace"Baba Musa nadawo, sannu da aiki" Bata jira amsar saba taci gaba da tafiya tana qarewa manyan motocin gidan kallo Wanda suke sheqi da daukar ido tundaga ma'adanar su, taqaraso get na biyu, tabude tashiga,anan zahirin gidan yake, gidane hadadde wanda ya amsa sunansa gida,saide bashida fadi sosai,duk da hakan an qawatashi da adon furanni Masu kyawun launi,anan compound din gidan taci karo da mutanan gidan a zaune,manyan mata ne guda biyu, saikuma wata yarinya wacce bazata wuce sa'arta ba, cikin sakin fuska tayi sallama, Nabiha da hankalin ta kekan wayar dake hannun ta, tadago kanta da sauri Jin muryar yar'uwar tata,qawa, Kuma aminiyar ta. tace"Mawahib Kin dawo? Ya Sayyadi yayi dorin karatu?" Cikin tsokana tasaki wani irin murmushi,murmushin yayi mutuqar yimata kyau har hakan yasa dimple dinta guda biyu suka futo sannan tace"anyi dori,Kuma anbada number,tunda yau da niyya kikaqi zuwa" Hajiya KILISHI datake zaune gefe kan kujerar roba,lokaci daya tabi Mawahib dawata irin harara kamar idonta zai fado qasa,cikin izza da gadara,tareda tsantsar iko tace" 'ya'yan ma'aikata andawo Kenan,INA GANIN IKON ALLAH NI KILISHI,anfita angama yawon gantali andawo,nikam naga mijin wannan yarinya,Kuma fa ahakan ake neman miji nagari..." Lokaci daya jikin Mawahib yayi wani irin sanyi,Nabiha ta sunkuyar da kanta qasa,alamun bataji dadin furucin hajiya Kilishi Akan Mawahib dinba,cikin sanyin jiki Mawahib tadubi Hajiya Kilishi,babbar mace ce Mai kimanin shekaru Hamsin da biyar,fara ce tas,batada digon baqi a jikinta, hutu dakuma Jin dadi ya boye shekarun ta, bazaka ce takai adadin wannan shekarun ba,tana kyau sosai,saide fuskar ta cike take da qunci da rashin walwala, cikin ladabi ta russuna tace"sannu da hutawa Momy" Hajiya Kilishi ta kawarda fuskarta gefe batareda ta amsa gaisuwar ba Mawahib tasaki murmushi Mai ciwo, sannan ta dubi d'ayar matar datake zaune kusa da Nabiha, wadda a shekaru bazatafi Mamyn taba, tace"Mama sannu da hutawa" Cikin sakin sakin fuska wadda aka Kira da mama tace"sannu Mawahib" Cikin sanyin jiki tashige kitchen,kasancewar tasan yau girkin mamyn tane, Kuma Bata dawo da wuri daga wajan aiki ba, tasan har yanzu tana kitchen bata gama wasu ayyukan ba,tana shiga kitchen din kuwa taganta a tsaye tana duba farfesun ganda Wanda qamshinsa yagama cika kitchen din,kallo daya zaka mata ka tabbatar da cewa mace ce Mai aji dakuma tsari,uwa uba yar boko maiji da gayu, komai nata tana yinsa a nutse,manya manyan zobuna ne a hannunta na gold sunkai guda uku,Riga da zanine ajikinta na leshi kanta yana daure da dan kwali Amma duk da haka jelar kitsonta ya sauko harkan gadon bayanta, black beauty ce, kokadan bata kama da Mawahib, launin fatarsu daban, saide sanyin hali dakuma dabi'arsu da tazo daya, a hankali tace"Mamy sannu da aiki" Batare data kalletaba tace"sannu da zuwa ya makaranta?" Cikin rashin walwala tace"Lafiya kalau Mamy,bari inje in cire kayana inzo natayaki" Kallonta tayi a Karon farko ta karanci akwai damuwa a fuskar 'yartata, amma Bata nuna mata komai ba,cikin hikima tace"A a,aina gama komai,dauki wannan salat din kawai kije ki yanka min,Abbanki yace ayi masa kwadon salat kafin yadawo" Ahankali tasaki ajiyar zuciya,sannan tacire hijabin dake jikinta,doguwar rigar gown din dake jikinta ta atamfa ta baiyana,rigar ta kama jikinta sosai har hakan yasa shape dinta futowa fili,hips dinta yacika rigar dam,saida ta bubbude girkin da mamy din tayi tagani bayan farfesun ganda,harda fried rice,da Alalan dankali, da fried cabbage with meat,a hankali tadauki salat din ta futo daga kitchen din tanufi hanyar part dinsu, Hajiya Kilishi tabi bayanta da kallo,ta Kalli yanda uban Hips dinta suke juyawa acikin rigar kamar da niyya take kad'asu, ta watsa mata wata irin harara tace"ina ganin ikon Allah ni Kilishi"(😂) Tajuya ta Kalli matar datake gefenta tace"Sadiya,dole zanyi wa ALQALI magana yaje yasamu shugaban makarantar islamiyar yaran nan ayi masa magana,ai bazai iyu abar yara suna zuwa makaranta babu uniform ba,suci wannan uwar kwalliya suna juyawa malamai kwankwaso,Kuma ahakan ake neman miji nagari....,bazan Iya cigaba da zama anan ba Sadiya,baqin cikin wannan yarinyar zai Iya illata ni,idan Kinga zaki Iya cigaba da Zaman jiran abincin, to bismillah Nina tafi,wannan horon yunwa har Ina? ai sai asa ulser ta tatashi". tana wannan sababin ,tajuya cikeda iko da izza irinta yayan mulki ta wuce part dinta. Mama Sadiya tayi murmushin qarfin hali a hankali tace"Allah yarufa asiri" Sannan tadubi yarinyar ta Nabiha dake gefenta tana daddanna waya, tajuya taga tabbas Hajiya kilishi tashige part dinta, sannan tace"Nabiha yi maza kije kitchen idan akwai aiki a wajan Mamyn Mawahib ki taimaka mata" Nabiha ta amsa cikin ladabi, sannan tashige kitchen din, Mama Sadiya saida tasake kallon part din Kilishi ta tabbatar de Hajiya Kilishin bataga lokacin da Nabiha tashiga kitchen dinba,sannan tasaki ajiyar zuciya ta wuce nata part din,tun dazu taso tatura mata Nabiha,domin ta taimaka mata da aiki tunda Mawahib din taje islamiya,to amma tsoro dakuma shakkar Hajiya Kilishi yahanata. Tana shiga falonsu ta ajiye salat din ta wuce dakin ta tayi sauri ta watsa ruwa,ta futo Sanye da riga da wando,ta zauna adaya daga cikin rantsatstsun kujerun falon Masu launin ruwan toka,Sai qananun fillo dasuke Kai,ta dauki remote din esi ta kunna, sannan tafara yanka salat din cikin qwarewa,batafi minti ashirin da zama ba mamy ta shigo falon, tun daga bakin qofa ta qarewa 'yar tata kallo,tana ganin irin dirin da Allah yabata,Riga da wando ne a jikinta baqaqe, wandon gaba dayansa Iya gwiwarta yatsaya,rigar Kuma batada banbanci da vest saboda ko hannu Bata dashi,sai farar hula shara-shara Wanda kana Iya hango tulun gashin da Allah yabata, Wanda ta gajeshi a wajan mamy, a hankali tasaki ajiyar zuciya tace"kin kunna esi kinzo kin saka wannan kayan, banason shirme tashi kije ki sauya kaya,idan sanyi ya kamaki fa" Cikin shagwaba tace"Mamy Ana Kiran sallah zancire fa" Cikin tsare gida tayi mata kallo daya,babu musu ta ajiye wuqar hannun ta ta wuce dakin ta domin sauya kaya. Lokacin sallah nayi kowa yashige dakinsa domin gabatar da sallar magrib,tana idar da sallar ta dauko Alqur'ani tabude tafara karanta inda aka biya mata dazu a islamiya,Bata dade da fara karatun ba mamy taturo qofar dakin ta shigo hannun ta daukeda counter tana dannawa,ta dubi Mawahib tace"kije kikaiwa su Yaya Abinci" Badan tasoba tarufe Alqur'anin,tafice daga part din nasu zuwa babban kitchen din gidan,ta dauki abincin mama Sadiya tashiga part din tareda sallama,falon nasu yatsaru Iya tsaruwa da kujeru nasu launin dark green,babu tarkace sosai Bayan kayan kallo dayake falon, Kai tsaye ta wuce dinning dinsu ta ajiye abincin, sannan tashige dakin Nabiha,tana zuwa tazube akan gadon ta tace"sarkin danna waya,kina Nan kina sana'ar taki" Nabiha tayi murmushi tace"to saina zauna shiru dan Allah? aigara indinga danna wayata" Mawahib tace"hakane Kam,Nima yanzu tunda mungama exam ai yanzu zan maidata qawata" Nabiha tace"Mawahib yaushe Yaya Ashraf zai dawo?" Saida ta juya idanunta Mai kamadana Masu Jin bacci sannan tace"wallahi bansaniba Nabiha,jiyama bayan munfuto daga last paper nayi masa flashing, amma bai kirani ba,kikirashi mana idan magana zakuyi" Ajiyar zuciya Nabiha tayi,cikin ranta tana jinjina maganar Mawahib datace ta kirashi,tayaya ne zata samu qwarin gwiwar kiransa bayan bataga fuskar hakan awajansa ba? Cikin basarwa tace"to shikkenan,babu damuwa" Cikin sauri Mawahib tatashi tace"bari inje inkaiwa Momy kilishi abincinta karnayi laifi" Nabiha tace"wallahi kuwa,bare keda dama kamar qiris take jira" Sallama tayi mata ta futo daga part din, takoma kitchen dinsu ta dauki abincin hajiya Kilishi sannan tawuce part dinta,gabanta yana tsinkewa. Da'ita taci karo tana Bude kofar falon,qiris yarage subugi juna, cikin sauri Mawahib taja baya Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"Ina ganin ikon Allah ni kilishi, ai saiki dinga nocking kafin kishigo, idan anbaki iznin shigowa saiki shigo tunda bakida iko da part din bare kidinga shigowa Kai tsaye haka" Ahankali ta sunkuyar da kanta qasa cikin ladabi tace"kiyi haquri momy, dama abinci ne nakawo" Batareda ta kar6i abincin ba tace"bude nagani" Cikin nutsuwa ta sauke kwandon dake hannunta, sannan ta bubbude mata abincin,Nan da Nan qamshin girkin yacika wajan,abincin ya tsaru kana gani, kasan girki ne nazamani. Yatsina fuska tayi tace"wanne irin gantalallen abinci ne haka zaki debo jiki kikawo min,?da alama kema haka zakije kinayi a gidan naki mijin....,kinga koma dashi kawai" Babu musu Mawahib tarufe abincin sannan tadauko tanufi part dinsu dashi, tanajin yanda Hajiya kilishi take rufo qofar part din nata da qarfi. Tana zuwa part dinsu dayake babu Nisa a tsakani, anan taci karo da Mamy tana zaune tana kallo,cikin mamaki mamy ta kalleta tace"yanaga kindawo da abincin?" "Mamy nakai mata tace in dawo dashi" Cikin yanayi na rashin damuwa Mamy tace"to Bari inkai mata dakaina" Mamaki yacika Mawahib, babu musu tabata kwandon abincin, mamy ta karba tafice daga nasu part din tanufi part Hajiya Kilishi. Tana zuwa tatura kofar falon tashiga bakinta dauke da sallama,falo ne har falo,yaji kayan qawata gida da lafiyaiyun kujeru milk color,tareda kafet Mai mutuqar laushi dawani daddadan qamshi dayake tashi gamida sanyin esi,can gefe inda dinning yake, anan ta hangi Hajiya Kilishi tana qoqarin hada tea, Kai tsaye ta nufi wajanta tace"yaya ga abincin angama, Mawahib tacemin kince adawo dashi, kiyi haquri Yaya yau dinne munsamu marasa lafiya a asbiti dayawa,Ina shirin tahowa aka kawo wata mata tana naquda,nice natsaya nakula da'ita harta haihu,sannan nataho gida shiyasa na Makara bandawo da wuri nayi abincin ba, amma kiyi haquri Yaya" Hajiya Kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni Kilishi,nace kinyi wani laifi ne Maryam?kawai abincin naki ne yau bazanci ba,kinyi wata shinkafa haka a tsatstsaye bata dahuba,kiyi mana abincin da muka saba Namu na gargajiya kinqi, saina ki na Yan zamani, kega ma'aikaciya,wannan naman gandar daga ganinsa ko silala baiyi ba bare ayi batun dahuba" Cikin ladabi tace"kiyi haquri Yaya, me kikeso nadafa miki yanzu?" Hajiya Kilishi ba tace komai ba, tajuya tabar mamy a tsaye a wajan tashiga dakinta,mamy tasaki ajiyar zuciya ta wuce takai abincin dinning, sannan ta futo daga part din. Tana komawa part dinsu taga Mawahib a zaune tanashan farfesun data gama a hankali cikin yanga kamar batason ci,Wanda a zahiri ba yanga takeba,haka cin abincin yake, hankalinta yana kan TV, tana ganin shigowar mamy, ta ajiye plate din dake hannun ta takoma kusa da ita ta zauna, ta dora hannayen ta akan cinyar mamy, sannan ta kalleta cikin damuwa tace"Mamy, Wai dan Allah meyasa Momy Kilishi bata sona?menayi mata Mamy?" Cikin kwantar da hankali mamy taqarewa 'yartata kallo tana ganin tsantsar yanda take kama da mahaifinta, a hankali tace"tana sonki mana,itace tace miki bata sonki?" "Mamy bata sona,dazu har cewa tayi wai itakam taga irin mijinda zan aura...,Mamy ahaka zamuci gaba da zama ne komai akai kinayin shiru?har cemin fa tayi wai nima ahaka zan qare danawa mijin idan nayi aure" Cikin sauri mamy tace"insha Allahu ba'ahaka zaki qareba,mijinda zaki aura lafiya kalau zaki zauna, ba zakiyi irin wannan rayuwar ba" Ahankali Mawahib tasaki ajiyar zuciya Jin furucin mahaifiyar tata,sannan tace"to Mamy meyasa ke bata sonki?" "Wai waye yace miki bata sona? Kawai halintane haka, banason tambaya Mawahib,kitashi kije ki kwanta" fan's ya kwana biyu?🤔 Amnah is back💃🏼 Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 3&4 Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin samun Audio Novel's👇🏻 https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels ____ Ba dabi'arta ce yin musu da mahaifiyar tata ba,danhaka babu musu tatashi ta dauke sauran farfesun datake ci takai d'an qaramin kitchen dinsu dake cikin falonsu,sannan ta futo tazo dining tazuba wata uwar madara a cup, tazuba ruwan zafi kad'an, tad'auki cornflakes d'in dake gefe tazuba acikin madarar, sannan ta wuce dakinta. Mamy tana ganin shigarta daki tasaki ajiyar zuciya,yanzu har Mawahib yarinya 'yar shekara sha takwas tagane tsanar da Hajiya kilishi tayi mata harta fara sata agaba tana tambayarta dalili? Itakam meta tsarewa matar nan ne? aikin gomnatin datake ne yazama matsala? kokuma wannan ne sakayyar dazata mata bayan rainon yaranta datayi mata Abaya? Labarinsu: GIDAN ALQALI....,sunan da ake Kiran gidan dashi Kenan. Duk unguwar inde kace gidan Alqali to kowa yasan cewa gidansu Mawahib ake nufi,Alqali mutun ne shi mai ra'ayi d'aya, baya magana biyu,yanada dattako,kowa nasa ne, yanada faram-faram da mutane,kowa shedar kirki yake masa,amma duk da wannan sakin fuskar tasa hakan bai hana yakasa gudanar da gidansa yanda yakeso ba,shine yake kafa doka agidan,duk abinda yabada umarni shi akebi,kasancewar shine babba a gidan,sai qannansa guda biyu Alhaji khaleed dakuma qaramin su Alhaji Isah. Alqali fari ne tas,zaka Iya cewama ba bahaushe bane, amma bahaushe ne cikakke mutumin garin kano, yanada sauqin kai, kuma baya goyon bayan rashin adalci,tun yana qaramin ma'aikaci yake kokarin yin aikinsa da gaskiya da amanah,har Allah yabashi matsayin Alqali,wanda yazama abun koyi a wajan sauran Alqalai,babu ruwansa da kar6ar cin hanci, aiki kawai....🤗 su uku ne rak a wajan iyayensu wanda suka mutu suka bari,Alqali Ibrahim shine babba,da matarsa daya tun auren saurayi da budurwa wato HAJIYA KILISHI,lokacin da akayi auren sunsha surutun mutane ganinta fara tas kamar ba yar hausawa ba, shima kuma fari, wannan yace anhada kyau da kyau za'a ga irin yaran dazasu haifa,ire iren wannan surutun tun yana damunsu harya dawo yazame musu jiki, suna zaune lafiya tsawon wasu shekaru,Hajiya kilishi itace take kula da duka gidan zatayi girki Alhaji khaleed da Alhaji Isah zasuzo suci abincin su sutafi harkar gabansu. Tsawon lokaci shiru shiru babu haihuwa, tun 'yan gulma suna saka ran ganin abinda zasu haifa har suka haqura, saida aka dauki wasu shekaru kafin ubangiji ya azurtasu da samun haihuwa, karon farko Hajiya kilishi ta haifi yaranta 'yanbiyu dukansu maza,lokacin da akayi haihuwar kai tsaye Alqali yace a dinga 6oye yaran,saboda Allah yayi musu kyau kamar 'ya'yan larabawa,Kuma bakin mutane wani bazai furta Alkhairi ba, sun dauki kyan uwa dakuma na uba sun hada waje daya, sunada mutuqar shiga rai babu wanda zai gansu baiji aransa yana qaunar yaran ba, ranar suna aka sakawa babban sunan mahaifinsu Alqali wanda yarasu,sai suke kiransa da ASHRAF,sai qaramin wanda aka sanya masa sunan mahaifin Hajiya Kilishi, suna kiransa da ARYAN.... Tun lokacin da kilishi ta haihu,take nan-nan da yaranta,kwata kwata batason abinda zai ta6a mata lafiyar 'yanbiyun ta, tanaji dasu kamar ranta,musanman ARYAN, wanda yaci sunan mahaifinta,ta dauki duk wani hope d'inta, ta dorashi akan ARYAN,idan har ta yiwa Alqali laifi to ta hanyar yaran yake hukuntata, saboda yariga yagano cewa yaran nata sune weakness dinta,tun suna zama Hajiya kilishi take gane-gane, yau taga maciji gobe kunama,idan d'aya yana kuka tad'aukeshi tana lallashinsa shima dayan saiya fara kuka,tarasa yanda zatayi ta lallashe su duka su biyun saboda haka saita ajiye d'aya idan d'ayan yayi shiru saita lallashi d'ayan,to duk ranar datayi hakan abincin gidan baya ciyuwa,haka zata dinga sakawa abinci wuta qarshe saide ayi asarar sa,data gane saitake had'asu duka su biyun take lallashin su,d'aya abaya,daya a hannu, daga lokacin bata sake ganin kunama ba,sai lokacin dasuke rarrafe idan sukai ta'adi tad'an dakasu alamun abinda sukai ba daidai bane,tana barin wajan taga wata baqar kunama,sai wata aminiyarta tabata shawara akar6o musu abincin maqota azuba musu akan murfin tukunya bazata sake ganin komai ba,haka akayi kuwa taje maqota takar6o abinci, tadauko murfin tukunya zata zuba musu Alqali yace karta fara, wannan duk canfi ne na mutane, Allah ne kawai yake kawo kunama amma ba yayansa ba,duk surutun mutane ne. a hankali rayuwa taci gaba da tafiya 'yanbiyu suka fara tafiya har suna fita kofar gida wasa,ba'a Isa adakesu ba yanzu Hajiya kilishi zata sa6a mayafi koda sanin Alqali ko babu saninsa,zataje har gidan yaron daya dukar mata 'yanbiyu tarama musu, sannan takamo 'ya'yanta sudawo gida, wannan halaiyar kwata kwata Alqali bayajin dadinta. Amma hajiya kilishi inde akan yaran nan ne, to zaka Iya Jin kanta dakowa, kasancewarta yar sarauta idan aka taba su Ashraf,mantawa take ita yar sarauta ce taje ayi wacce za'a yi,kokadan batason abinda zai ta6a mata lafiyar su,lokacin da aka haifeta, a lokacin a kayiwa mahaifinta sarauta, shiyasa mahaifinta ya Sanya mata suna KILISHI. tashin datayi a gidan sarauta yasa take wa kowa kallon raini da Kuma nuna Isa da taqama da izza,kana ganin yanda take gudanar da al'amuranta zakasan cewa jinin sarauta yana yawo a jikinta,ahakan ma saboda Alqali a tsaye yake agidansa, shiyasa take rissinawa. Bayan Alqali Ibrahim Sai qaninsa na biyu Alhaji KHALEED,adede wannan lokacin yayi aure, yaso yazauna agidansa shi kadai amma Alqali yace babu inda zaije, ya zauna a gidan duk suyi zamansu tare babu wanda zaibar cikin gida, Alhaji KHALEED ya auri Mama Sadiya mace mai kawaici da kawar dakai akan komai, kasancewarta mace mai tsoron fitina yasa zamanta da kilishi ya d'ore,bata Isa tayi komai ba saida iznin Kilishi, komai zatayi saita tambayeta,hakan yasa kilishi take qarajinta asama,kanta yana sake kumbura tana jinta eh lalle ita d'innan fa yar sarauta ce. Alhaji Khaleed baifi wata shida da aure ba, Alhaji ISAH shima yataso da batun nasa auren,wato d'an qaramin su, babu abinda yayi na aure komai Alqali da Alhaji Khaleed ne sukai masa kasancewar sa shine qarami a cikinsu,kuma sunaji dashi tun bayan rasuwar iyayensu,to duk abinda Isah yace yana so suma shi suke so, tun yana yaro suka shagwa6a shi abinda yakeso shi suke masa,alokacin Maryam, wato Mamy tagama degree dinta nafarko fannin Nursing,yar asalin garin maiduguri, ganin wahalar datasha a karatun ta yasa ta fad'awa Alhaji Isah cewa itafa bayan auren nan zatayi aiki, bazata bar karatun ta yatafi ahakaba,tanaso tabawa yan'uwanta mata gudunmawa ta fannin karatun ta,Alhaji Isah yasamu yayunsa su Alqali yafada musu qudurin Maryam, Nan take Alqali yace ai babu komai,aikin nata ai 6angaren lafiya ne,inde har tana son d'an'uwan nasu to babu matsala tazo tayi aikinta. Wannan mataki da Alqali ya dauka yayi bala'in qonawa kilishi rai, tayaya suna zaune agida,za'a bar yarinya tazo cikinsu tana aikin gwamnati? me suka rasa agidan daza'a zo musu da wani fi'ili na aikin gwamnati? hukuncin Alqali baiyi mata dadi ba, daga nan ne matsalar tafara faruwa tsakanin Mamy da Hajiya Kilishi. Bayan Maryam, wato Mamy tayi sati buyu a gidan Alqali, a lokacin Alqali ya tarasu duka su ukun yayi musu maganar girki, tunda harkarsuce tacikin gida Yaya suke ganin zasu tsara girkin? Nan take Mamy tace tunda tana aiki, tana ganin kawai kowa yayi nasa girkin,ba zai iyu ace saita dawo daga wajan aiki sannan zata dafa musu abinci ba, lokaci daya Alqali yace hakan bazai iyu ba, shida qannansa qwaya biyu rak a duniya bazai iyu su raba girki ba,hakan yana nufin kenan dan autan su Alhaji Isah haka zata dinga barinsa da yunwa harsai ta dawo aiki ne zata dinga dafa masa abinci, a lokacin Mamy saita nuna masa cewa inde cikinsu ne daga ita Sai mijin ta Alhaji Isah,bazata bar mijin ta da yunwa ba, amma Alqali yace Bai yarda da wannan batu nataba,dole zasu hade girkin su, sai Mamy tace to tunda ita tana fita aiki, tana neman Alfarmar su Hajiya kilishi da Mama sadiya abar mata Iya weekend su sai suyi sauran ranakun, nan take Hajiya kilishi ta watsawa Mamy harara tace bazai iyu ba, a dinga yi kwana bibbiyu, babu wani weekend daza'a barmata,Alqali baiji dadin furucin kilishi ba, amatsayinta na babba a cikinsu kamata yayi ace taja matan qannan nasa a jikinta, su zama qawayenta kuma qannanta, koba komai matar autan nasu alfarma tanema akan su bar mata weekend din,kuma babu wanda yawuce yanemi alfarma, to har zai dauki mataki saiya fasa ganin harkar suce ta mata, daga haka taron ya tashi. Ko wata uku ba'a yi ba,Hajiya kilishi taga Mamy bata musu girki akan lokaci, saita dawo daga wajan aikinta sannan ne zata fara shirin dora musu abinci, sauqinsu daya idan aikin yamma takeyi, to shine kafin tatafi take musu girkin,kuma Mamy Bata girkin gargajiya,saboda tana aiki da kudin ta take kashewa tayi girki mai rai da lafiya,wanda duk wanda yaci, saiya so ranar girkin ta yasake zagayo wa, to daga nan ne Kilishi tayiwa Alqali magana yakamata asake zama akan batun girkin nan, Maryam bata musu abinci akan lokaci idan aikin safe ne da'ita saita taso wajan karfe uku na aana sannan za'a fara shirin dora musu abinci,tosu yanzu sun yafe gara ta dinga yi da weekend din kawai,(😂) Alqali yayi murmushi bai tanka ba,tun farko abinda yahango musu kenan, shiyasa yaso subata weekend din, tunda Alfarma ta nema,sannan itace qarama a cikinsu kuma matar dan autansu, kamata yayi su ja yarinyar a jikinsu musanman ma ita Hajiya kilishi tunda itace babba, amma mugunta ta rufe mata ido, takasa gane hakan tun farko. Haka Alqali yayi mursisi yaqi saka baki akan maganar girkin. Mamy tanada masifar haquri,zaiyi wahala kaga 6acin ranta,tana zaune da kowa lafiya a cikinsu Kuma da zuciya daya, tanajin dadin yanda Mama Sadiya take janta ajiki,nan da nan sai suka saba, suka zama kamar qawaye,duk lokacin da Hajiya kilishi ta 6atawa mamy rai, Mama sadiya ce take bata haquri, kuma Mamy bata ta6a fadawa mijinta ba, saide tabar abun aranta. Tunda tazo gidan ta lura kwata kwata Hajiya kilishi bataso su Ashraf suzo wajanta,koda wasa taga sunyi hanyar part din Mamy toda gudu zataje ta janye su, abun baya yiwa Mamy dadi, tana bala'in qaunar yaran, amma babu damar daukar su saide tadinga leqensu daga nesa. Hajiya kilishi ganin Alqali yaqi kula maganar ta dangane da girki, hakan yasa wata rana Mamy tana girki Hajiya kilishi taje ta sameta a kitchen din tayi mata tatas,Mamy ko uffan batace mataba, ganin Mamy taqi tanka mata yasa tafara zaginta, tayi mata zagi nacin mutunci,hartana fada mata yar gidan talakawa wadda take aiki saboda talaucin iyayenta, juya....wacce bata haihuwa tunda tazo gidan ko 6ari bata ta6a yiba(😥) Mamy bata ramaba saide kuka da takeyi duk da hakan tana bata haquri,ashe duk abinda ake Alqali yana ganinsu yazo wucewa,cikin 6acin rai yayiwa kilishi magana cikin tsawa,itama 6acin rai ya rufe mata ido tarama,nan take babu 6ata lokaci Alqali yabawa Hajiya kilishi jan Kati, yayi mata saki daya(🙆🏻‍♀️) Sannan agabanta yaje yadauko Ashraf da Aryan yace yabawa Mamy su halak malak(😳) A wannan lokaci kilishi hauka ne kawai batayi ba,taji tsanar Mamy tasake nunkuwa aranta,tanaji tana gani haka tabar 'yanbiyunta a hannun matar data tsana tafice tabar gidan Alqali. A lokacin Mamy tajasu ajiki sosai kamar 'ya'yanta,musanman yanda takeson haihuwa amma gashi Allah bai bataba, idan taje asbiti taga mata sun haihu tadinga kula da yaran kenan bata kyamatarsu, hakan ne yaja mata farin jini a wajan aikinta,dama hajiya kilishi ce tayi mata iyaka da 'yanbiyun, amma tana sonsu sosai, Alqali yana danqa mata su kuwa tabude bakin aljihu tadinga yimusu siyaiya, shikuma yaro inde za'a bashi, musanman kayan chocolate to yanzu zaka siyeshi, tun basa sakin jiki da'ita har suka dawo suka saba da'ita,sune suka fara kiranta da MAMY, tun suna yara Mamy ta lura Aryan baya son surutu,yafison ya zauna yanata game da wayarta,koda tajashi da zance irin dan surutun nan na yara saide taga yace mata eh kokuma a a,saide in yanason abu zaice Ma-my inason sweet, kokuma Ma-my ruwa, kai tsaye de yace Mamy,ba zakaji yafadi hakaba, wannan saide Ashraf, amma shide Aryan a rarrabe yake kiran Sunanta. Tayi amfani da hikima sosai wajan shawo kan yaran,haka kawai tana dawowa daga wajan aiki zata cire uniform dinta tasa qananun kaya tadinga goyasu sunata wasa saide Alqali yajiyo su sunata qyalqyala dariya,da yamma haka zata musu wanka ta shirya su tsaf suyi kyau, sufuta wajan wasan yara takai su suyi wasa son ransu, sannan su dawo gida,harta kai takawo idan zata fita aiki ma dasu take tafiya, kowa yasan su a wajan aikinta,qawayenta na wajan aiki har chocolate suke kawo musu, wasu Kuma kayan wasa suke kawo musu,mutane dayawa suna tunanin ma yaranta ne, saide su din farare ne sosai kuma identical twins kwata kwata baka banbance su,amma ita kam sarai tana ganesu, kai tsaye zata nuna Ashraf tace wannan ne babba, shikuma Aryan rashin surutun sanema yakesa nan da nan aganeshi, amma kuma idan shida Ashraf ne har mamakin yanda yake surutu take,inde dagashi sai dan'uwan ne yanzu zakaji yanata masa magana, daga qarshe a kaure da fad'a, saide fadan nasu baya zuwa ko'ina zakaga sun shirya, Mamy tasan halin kowa a cikinsu, Ashraf gaba daya halin Alqali yad'auko, babu ruwansa, inde yazo waje sai kasan yazo,haka idan tahada musu tea dasafe, gashi de tea din bawani zafin kirki gareshi ba,haka Ashraf zai dauka yasha abunsa, yayinda Aryan yadebo halin Hajiya Kilishi gaba d'aya,tun yana qarami Mamy ta fahimci yanada son girma, baya son raini, gashi de shine qarami amma Ashraf bai Isa yace ya girmeshi ba,kuma kokadan bayason zafi,shide kawai sanyi, idan tahada ruwan dumi zata musu wanka nan da nan zai fara kuka shi bazata masa da ruwan dumi ba saide na sanyi, ita kuma tana tsoron kar ruwan sanyin yayi masa illah, haka zata riqeshi yana kuka yana cewa ruwan da zafi, ahaka suke wankan kullum, idan Ashraf yaga Aryan din yana kukan ruwan zafin saiya saka hannunsa acikin ruwan, ya kalli Aryan din yace kaji ruwanfa babu zafi(😂) Darana kuwa taci karo dawata baqar kunama a qofar dakinta,cikin tsoro tajuyo aguje,suma suka bita da gudu suna dariya,mamaki ya kamata,tadauko abu zata kashe Ashraf yace shine zai kashe,yasaka hannu ya dauki kunamar shima Aryan yace saiya bashi,shikuma Ashraf yahana,lokaci daya kunama tahada su fada, ganin ana qoqarin fada akan kunama kuma gatanan tana ganinta qiri qiri a hannun Ashraf lokaci daya Mamy ta suma a tsaye, batasan lokacin data saki qaraba,tariga tabayar kunamar zata cutar dasu. ganin tana kuka yasa suka dawo wajanta suma suna kuka,saida tagama kukan tafara lallashin su anan taga babu kunamar a hannun su babu dalilin ta,haka tayi shiru da bakinta bata tambayesu Ina take ba. Haka Mamy tadinga kula dasu, yanda take kaffa-kaffa dasu yasa su kayi mugun sabo da Mamy, yanda suke liqe mata saika rantse itace ta haife su,ko dare yayi bazasu kwanta ba saide a jikinta, haka zata tofesu da Addu'ah har suyi bacci, saide cikin dare ta lallaba ta gudu wajan Alhaji Isah,suyi abinda zasuyi (🙈) kafin ace sun farka sun fahimci bata wajan su zata dawo cikinsu suci gaba da baccin, kuma hakan kokadan baya damun Alhaji Isah saboda qarancin kulawar dayake samu a wajanta, saima dadi da yakeji yanda take riqe 'ya'yan dan'uwansa kamar itace ta haife su. Sun kwashi watanni a wajan Mamy,yau suyi fad'a tadinga rabiya, gobe azauna kalau ahaka har sukayi mugun sabo da'ita, komai Mamy,bakajin komai a bakin su sai maganar Mamy, ta rainesu yanda ya kamata, raino wanda zaiyi wahala yaro ya manta da uwar rainon sa. Ganin Alqali yayi mursisi baije bikon Hajiya kilishi ba, hakan yasa tadinga yiwa yan gidansu magana har sukuma suka yiwa Alhaji Khaleed da Alhaji Isah magana, suka basu haquri akan laifin kilishi suka roqesu Alfarmar suyiwa yayansu Alqali magana akan dawowar kilishi dakinta,domin sude bazasu Iya tunkarar sa da maganar ba, domin kuwa Alqali akwai kwarjini,hakan akayi kuwa, Alhaji Isa da Alhaji Khaleed sune suka shige gaba, aka maida auren Hajiya kilishi da Alqali Ibrahim,suka sake bawa yayan nasu haquri akan katsalandan din dasuka masa, badan Alqali yaso ba, haka yayi haquri kilishi ta dawo dakinta, bayan alqawari data dauka masa cewa hakan bazata sake faruwa ba. Mamy kuwa tayi tunanin ganin hajiya Kilishi tadawo zaisa su Ashraf su koma wajanta, saitaga yara sunyi mursisi sunqi komawa wajan Hajiya kilishi,irin murnar nan ma taganin uwa sude ba suyi ba, saida Alhaji Isah yasata tahada musu kayansu sannan yace tarakasu wajan mahaifiyar su, a lokacin data gama hada musu kayan harda kukanta, a lokacin yarinta tasa basu fahimci kukan me takeba,Ashraf ne yafara matsowa yana goge mata hawayen,amma shikam Aryan da bai Iya lallashi ba shima saiya kwanta a cinyarta yafara kuka (😂) Haka tarakasu wajan Hajiya kilishi, tayi mata sannu da zuwa ta amsa mata da qyar, itade Mamy ahaka ta futo tabarsu tareda mahaifiyar su. Tunda Hajiya kilishi tadawo taji suna kiran Maryam da Mamy,babu 6ata lokaci tahanasu fadar sunan, saide suce Anty, sukuma basu saba da Anty ba, da Mamy suka saba, dan dolansu babu yanda suka Iya shine suke kiranta da Anty Mamy,maimakon suce Anty kadai,sai suka hada mata duka biyun suke kiranta da Anty Mamy Bayan wasu shekaru suna kammala primary school dinsu Mama Sadiya ta haifi yarta mace, aka sanya mata sunan Mahaifiyar su Alqali, suna kiranta da NABIHA, adede lokacin Alqali yafitar dasu qasar waje karatu,saida karatun su yayi nisa sosai sannan Allah yabawa Mamy ciki,ta haifi yarta mace mai tsananin kyau kamar balarabiya,mahaifinta ya sanya mata suna RUQAYYA,Mamy kuma take kiranta da MAWAHIB. ma'anah (MAI YAWAN KYAUTA). Mawahib tun tana qaramarta Allah yayi mata diri,tanada jiki mai daukan hankalin samari, tanada sanyin hali kamar Mamy, kwata kwata batada hayaniya,Allah yayi mata baiwar hips kamar ita ta sakawa kanta,saide batada cikar qirji, boobs dinta ba manya bane kuma ba qananu bane, 'yan madedetane hakan ne yasa suke a tsaye qyam.... Mamy da Abbanta sunaji da'ita,sosai Mamy take siyo mata qananun kaya daga nashan is'ka harna bacci, haka zata saka kayan ta tayi uzurinta Iya part dinsu babu wanda yake mata magana, haka 6angaren kayan kwalliya ma ba'a barta abaya ba,idan Mawahib ta dauki kwalliya babu musu zakace mata yarinyar Momy da Daddy ce,saide bahaka bane,kawai Mamyntace ta tsaya mata take shigar ta yanda taga dama, tunda samarin gidan bawani zama suke ba. Aqasar waje su Ashraf sukai secondary school dinsu,suka dora da jami'ah,bayan sungama jami'ah suka nunawa Alqali cewa suna so suzo gida, yace su dakata suyi masters tukunnah,duk tsawon wannan shekarun Mamy tana nan a ransu, tun basa fahimtar mahaifiyar su Hajiya kilishi bata son Mamy, har suka dawo suka gane,idan suka tambaye ta awaya Ina Mamy nan da nan Hajiya kilishi zatayi kicin kicin darai ta nuna musu batason mu'amularsu da wannan matar. Haka sukai haquri basuzo gidaba saida suka kammala karatun su kamar yanda Alqali yakeso, sannan suka dawo gida, anan sukaga an sauya tsarin gidan, ansake masa fasali, anyi masa get biyu,gida yakoma gidan zamani ankashe masa dukiya, a wannan lokacin Alqali yayi ritaya,yana zaune agida yana hutawa,duk wani nauyin kula da gidan yakoma kan Alhaji Khaleed mahaifin Nabiha, saikuma Alhaji Isah mijin Mamy, gida de ya sauya, saide halin Yan gidan dabai canja ba(😂),tunda suka dawo Ashraf yaga Nabiha da Mawahib shikkenan yake jansu a jikinsa, musanman Mawahib din Mamy, yana bawa Mawahib kulawa yanda ya kamata, jinta yake aransa kamar me,duk abinda takeso nan da nan zakaga yaje yasiyo mata,amma kwata kwata baya bawa Nabiha wannan damar, tsakanin sa da'ita saide gaisuwa amma fuska asake yake amsawa, shikuwa gogan ko a jikinsa, daga Mawahib din,har Nabihan, gaba dayansu baya shiga sabgarsu, kwata kwata baya son raini, suma su Mawahib da sukasan halinsa koda wasa basa shiga harkar sa. Bayan sunyi bautar qasa Ashraf yasamu aiki a NNPC dake Rivers state,shikuma Aryan dama burinsa yasamu aikin soja,kuma yasamu, har yakai matakin CAPTAIN,shiyasa su Mawahib suke kiransa da YAYA CAPTAIN, yana aikinsa a Abuja,bai cika zuwa gida sosai ba, Ashraf ya fishi zuwa gida. Kamarsu daya da Ashraf sak,zaiyi wahala ka banbance su idan suka saka komai iri daya,suna fad'a ajunansu,saide fad'an nasu babu inda yake zuwa nan da nan zasu shirya, idan Ashraf yayi budurwa shima Aryan yana ganinta zaiji yana sonta, daga dawowar su daga qasar waje zuwa yanzu dasuke aiki Ashraf yayi 'yanmata dayawa, amma wai irin ya nunawa dan'uwansa sabuwar budurwar da yayi, sai shima Aryan din yace wallahi sonta yake (😲) Babu yanda Ashraf zaiyi saide ya haqura da yarinyar tunda bazai iyu su auri mace daya ba, sunyi haka yakai sau biyar,kuma shima Ashraf din dan masifa kamar anyi masa dole muddin yasamu budurwa saiya nunawa Aryan ita,shikuma yana ganinta kai tsaye zai fada masa wallahi Shima yana sonta,haka Ashraf din zaiyi haquri yabar masa yarinyar kokuma su barta duka su biyun,shikuma captain Aryan baya kula yanmata bare ayi tunanin zai samo wata, yana zaune saide in dan'uwan yasamu, yace shifa duk duniya shima wannan yarinya yakeso,haka zasu haqura da yarinyar gaba dayansu. Ashraf yanason ruwan zafi,halinsa sak irinna Alqali, shiyasa koda yaushe yake ta'ammali da tea,kuma babu ruwansa da zafin tea dinnan haka zaisha abunsa, amma captain Aryan bahaka bane, kokadan baya hada hanya da ruwan zafi, yafison ruwan sanyi, duk sanyin da ake agari bazaiyi wanka da ruwan zafi ba, dana sanyi zaiyi, wannan dabi'arsu ce tun suna Yara. Har zuwa wannan lokacin Hajiya kilishi bataso su ra6i Mamy,amma har yanzu suna sonta,kuma suna mu'amula da'ita dan dole Hajiya kilishi ta haqura tabarsu. Fatan Alqali da Hajiya kilishi shine su samu mata suyi aure, Hajiya kilishi ta dauki buri ta dorawa yanbiyunta kawai so take su samo mata yanmata nagani nafada na kece raini suyi aure irin auren 'ya'yan Masu dashi dakuma 'ya'yan masu mulki, amma har yanzu basu kawo kowacce yarinya gida ba,har gara Ashraf yana dan kula Mawahib,yana Jin dadi idan yaganta, yana sakata aiki kamar gyaran dakin su,girki marar wahala,yana wasa da dariya da'ita, amma baya kula Nabiha sosai, amma ita kullum tana tasa,bata da aiki sai tambayar Mawahib yaushe Yaya Ashraf zai dawo,? Sunyi waya da Yaya Ashraf? Cigaban labari: Dasafe Mamy tagama shirinta tsaf domin tafiya wajan aiki, tashiga dakin Mawahib taganta a kwance a gadon ta tayi d'aid'ai tana bacci,dogon gashin kanta duk ya barbaje akan katifar,tana sanye cikin wata yar 6ingilar rigar bacci gaba daya rigar iyakarta rabin cinyarta,hakanne yasa fararen cinyoyinta suka futo muraran,babu bra ajikinta amma yan madaidaitan boobs dinta suna nan a tsaye cak har kana Iya hango tsinin nipples dinta. Mamy bata damu da kayan dayake jikin Mawahib ba, asalima itace take siyo mata su,tana duba agogon dake daure a hannun ta,mai mutuqar tsada, sannan tasaki dan qaramin tsaki tace"Mawahib tashi daga baccin nan haka, kina sana'ar taki ta bacci ko gidan baki gyaraba" Cikin shagwaba tace"Mamy ramuwar baccin exam nake fa..." "kitashi haka kiyi break fast kar yunwa ta kamaki,akwai kudi agefen gadona Abban ki yace ki dauka kije gyaran jiki,karki yarda kidawomin gida da wannan gashin naki babu gyara" Idonta a lumshe tace"to Mamy saikin dawo" Bayan Mamy tafita a hankali tazuro qafafunta qasa, tashafa shafaffan cikinta,sannan ta wuce toilet tayi brush, ta futo ta gyara musu part din nasu, ta kunna turaren wuta, ko'ina yadauki qamshi, sannan takoma daki tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga Abaya,wadda ta bude daga qasa, daga sama kuma ta fitar da shape din qirjin rigar, abincin tazuba tafara ci a hankali kamar bataso, adede lokacin Alhaji Isah Yafuto cikin shirin fita aiki,cikin sauri ta gaida shi, cikin mamaki yace"a a,karfe nawa yanzu baki tashi kinci abinciba sai yanzu kike break fast? meyake damunki ne Ruqayya? " Saitayi wani sororo kamar bada ita yake magana ba,saboda ita kanta mantawa take Sunanta Ruqayya, saboda Mawahib din da'ake fada mata ya6oye Ruqayyan. Cikin shagwaba tace"Abba bacci nakeji sosai shiyasa" Kansa ya girgiza yace"kiyi sauri kifuto Ina jiranki saina saukeki kafin in wuce" Bai jira amsar taba yawuce, cikin sauri tahada tea tasha, sannan tadauko hand bag dinta yar qarama mai kyau, tazuba kudin da Abban yabata, sannan ta futo, key tasa tarufe part din nasu, sannan ta wuce part din Hajiya Kilishi kamar yanda Mamy takafa mata doka kullum taje part din kowa ta gaishe su, tun kafin ta qarasa part din taji wani qamshi mai dadi ya bugi hancinta,a hankali ta lumshe Idonta, sannan ta bude, qamshin yayi mata dadi, cikin nutsuwa tatura kofar falon tashiga, dashi tafara yin tozali da alama saukar dare yayi, shiyasa batasan da zuwan sa ba,kyakykywan saurayi ne mai kyau da aji kana ganinsa kasan zaikai shekara 37,sumar kansa sai wani sheqi take,ga wani saje daya sake qawata farar fuskar sa,yanada dan qaramin lips launin ja. tun kafin tagama qarasowa cikin falon Hajiya kilishi tafara watsa mata wani irin mummunan kallo,duk da tana shakkar Hajiya Kilishi, hakan baisa ta 6oye murmushin ganin Yaya Ashraf ba, cikin ladabi ta tsugunna tace"Momy Ina kwana?" Daqyar Hajiya kilishi ta amsa,murya can ciki tace"lafiya..." ta amsa tana qarewa surar jikinta kallo, shikuwa Ashraf kamar wanda tatafi da imanin sa tana shigowa haka yabita dawani irin mayen kallo,shi kansa baisan lokacin dayabita da wannan kallon ba,da alama yama manta da'inda yake zaune(😲) Tun kafin Mawahib ta gaida Ashraf,Hajiya kilishi tace"Ina ganin ikon Allah ni kilishi.....ke Kuma irin tarbiyar da uwar taki take baki kenan? bazaki Iya jira akaiki gidan miji ba tun a titi zaki fara nunawa duniya jikinki? Kuma ahakan kuke neman miji nagari ko? banga sallaman man dazai kwasa ba...."(😢) Cikin sauri Ashraf ya runtse idonsa,bayason wannan furucin datake yiwa Mawahib,bayajin dadinsa ko kadan. domin ya katse zancen, ya Kalli Mawahib wadda ta sunkuyar da kanta qasa tana wasa da dogayen yatsun hannunta, qiris yarage tafashe da kuka, yace"Mawahib zaki fita ne?" Cikin sanyin jiki tadaga masa kai batareda tace uffan ba,domin kuwa bazata Iya magana ba, inde tace zatayi magana to kuka ne zai biyo baya,a hankali tatashi ta futo daga falon. Tana fita Hajiya kilishi ta kalleshi Cikin fada tace"Ashraf kafita daga harkar yarinyar nan,banason Jin wata magana daga baya,koda wasa banason ganin wani abu yashiga tsakanin ku,naci buri akanku sosai,sonake kuyi aure nagani nafada auren kece raini,shiyasa ARYAN yake birgeni, saboda baya shiga sabgar wannan yarinyar" Ashraf yayi murmushi tareda shafa sumar kansa yace" kiyi haquri Momy" Tana barin part din Hajiya kilishi qunci da damuwa yasa ko kallon part dinsu Nabiha batayi ba bare tashiga, wani irin kuka ne ya taho mata,to amma data tuna Abban ta yana jiranta a waje, zai gane tayi kuka, Sai tayi sauri tadaga fuskarta sama, tana kokarin maida hawayen,tarasa me matar nan take nufi da'ita, nafarko ita batace tana son 'ya'yantaba, tarasa meyasa tasata agaba,kuma Mamy taqi fada mata Dalili..... Yaya Ashraf anya kuwa? 🤔🤔 Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 7&8 Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,za'a fara dora muku Audio Novel's👇🏻 https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels Cikin sanyin jiki ta qarasa shigowa falon,tazauna kusa da Mamy tace"Mamy me a kayiwa Yaya Ashraf tunda yashigo naga kamar yana fishi" Cikin basarwa Mamy tayi murmushi tace"Fada yake saboda kinfara tsayawa da saurayi, baisan su Alhaji ne suka bawa Nabil damar zuwaba,tun ranar da mukai waya da Yaya Mustapha Abbanki yaje yasamu Yaya Alqali yafada masa komai" Ahankali Mawahib tasaki ajiyar zuciya tazauna,tabawa Mamy ledar hannunta cikin dari-dari tana tsoron kartayi mata fad'a,cikin murmushi Mamy ta kar6i ledar tace"Kawo miki yayi?" Tace"eh, saida nace yabarshi shine yace zai fad'a miki" Mamy tace"to inbanda shirme menene naqin kar6a? koba maganar soyaiya Nabil ai yayanki ne,dani da mahaifinsa uwarmu daya ubanmu daya,bazanyi fad'aba danya baki wani abu,bari mugani menene aciki" Tafadi hakan tana bude ledar,kayan kwalliya ne aciki masu tsada harda turarukan da chocolate dayawa,sai wata 'yar qaramar Envelope da dubu goma aciki,cikin murna Mamy tace"lalle Nabil,wannan uban kaya haka ai kinci qarfin albashin nasa,Allah yasanya Alkhairi,amma ya kikagan shi? ya miki?" Cikin tsananin kunya taturo dan qaramin bakinta gaba tace"kai Mamy dan Allah....nide kidena min wannan maganar" cikin sauri tamiqe zatabar wajan, Mamy tana dariya tace"dawo ki dauke kayan ki,kije kikaiwa 'yar'uwar taki itama" Cikin shagwa6a tadawo tabude kayan tadibawa Nabiha komai,sannan tatafi zatakai mata. Nabiha tagama dudduba kayan da Mawahib takawo mata, cikin mamaki tace"Gaskiya kinyi sa'ah Mawahib,yaya Nabil da qarfin sa yafuto,kuma da alama da gaske yake tunda gashi ta wajan iyaye yafara neman,kuma daga gani bashida rowa,gashida fara'ah masha Allah, kinsan wannan kayanfa tsada ne dasu" Mawahib tayi murmushi tace"nima shiyasa naji yafara birgeni,tunda yazo yaketa bani dariya,gashi bashida shekaru sosai irin mijinda nakeso,ke kinsan meyafaru dazu da yamma kuwa?Yaya Ashraf yadinga yiwa Mamy fad'a saboda na saurari Yaya Nabil,kuma fa Abbana yasan da zuwan nasa" Nabiha tayi shiru tana sauraron Mawahib,tunda Mawahib d'in tafara magana dayake ita tafita shekaru da wayo, nan da nan ta dauki haske akan dalilin fadan Yaya Ashraf din, tayi shiru saida tagama jin qarshan zancen sannan tayi ajiyar zuciya tace"kinsan abinda nake tunani? Yaya Ashraf fa Ina zargin sonki yake" gaban Mawahib yayi wata irin faduwa,cikin tashin hankali ta zaro idonta tace"dan Allah Nabiha? Innalillahi...naga takaina" Nabiha tace"menene abun wani innalillahi...? kinsan Allah sonki yake,kuma zakice nafada miki" Mawahib tace"ai yanzu yaga Yaya Nabil,nikam babu ruwana, bazai ma fadamin ba, babu ruwana da Momy kilishi" Cikin bada qwarin gwiwa Nabiha tace"kinsan Allah,ki ajiye wannan haqurin naki irinna Mamy agefe ki fuskanci rayuwa, wani lokacin idan biyaiya tayi yawa anfi yima is'kanci,kina mata biyaiya kamar itace takawo ki duniya,ni bakiga idan tana sababin tama wayata nake dauka ba?" Cikin rawar murya Mawahib tace"bazan iyaba Nabiha,itama kamar uwa ce awajanmu, watarana ai sai labari,nan gaba kadan ma zanbar mata gidan har abada inkoma wajan Yaya Nabil maiduguri" Nabiha tace"to ai shikkenan,saiki daina rawar jikin" Sai a lokacin Mawahib ta Lura jikinta rawa yake tunda Nabiha tace mata Yaya Ashraf yana sonta, sun dade suna fira daga baya tayi mata sallama tatafi. Washegari da safe takama weekend ne, Mamy tana gida bataje ko'inaba,itama Mawahib tun safe data gyara musu part din nasu takoma dakinta tagyara shi,tarasa meyasa tun safe gabanta yaketa faduwa,sai Addu'ah taketa maimaitawa aranta, tana gama gyara dakin Yaya Nabil yakira wayarta,tayi zamanta adakin suna wayarsu, Mamy ce taqwala mata kira cikin sauri tayi sallama dashi tafuto,ganin Mamy tayi dauke da wani yaro yana kuka kad'an-kad'an, ita kuma Mamy sai jijjigashi take,Mamy ta kalle ta tace"d'auko hijabin ki kikai wannan yaron gidan Maman Fati,yanzu ta aiko shi nayi masa allura kuma naga yaron daya kawo shi kamar bazai riqe shi dakyau ba,nace yaje yaturo babba adaukeshi,kuma kinji shiru babu wanda yazo" Tace"to Mamy" Sannan tajuya dakinta tadauko hijabi tafuto,hayaniyar datake ji a waje ne yabata mamaki tarasa me'akeyi haka,Mamy ta nufo bayanta da yaron tace"yi sauri ki goyashi kikai matashi yaro yanata kuka tun dazu" tafad'i hakan tana dora matashi abayanta, Mawahib tasa zanin goyon tana kokarin goya yaron, tace"Mamy wai hayaniyar menake ji a waje? kosu Daddy ne suke rabon zakka?" Cikin sauri Mamy tace"riqeshi ki goyashi ni,kin dameni da tambaya sauri nake,CAPTAIN ne yazo, inaso inyi sauri inyi masa ferfesu med'an sauqi" tana fad'ar haka tayi d'akinta tabar Mawahib atsaye a wajan Haushi yakama Mawahib,tabi bayan Mamy da kallo gabanta yana dukan uku uku,cikin ranta tace"mukam yau munshiga uku, bala'i yadawo" tajuya ta kalli yaron dayake goye abayanta yana qishin-qishin din yin kuka,cikin haushi kuma a fili tace"Yanzu fisabilillah Mamy saboda wannan mutumin jikinta yake rawa haka? saikace wani mutumin kirki za'a je anayi masa wani farfesu? wahalalle yanzu haka da wannan uniform din nasa na kullum-kullum yazo"(😱) tasake juyawa ta kalli yaron dayake goye abayanta,tatuna maganar qawayenta 'yan makarantar su dasuke cewa goyo yana zubar da Nono, cikin fad'a tafara qoqarin sauke yaron daga bayanta tareda fadin"kaikuma sauko,wallahi bazan goyaka ba" tasake rage muryarta taci gaba da fadin"Salon d'an nonon nawa duk su zube mijina yarasa na kamawa...."(🙊) Qamshin turaren daya bugi hancinta,wanda bata gama tantancewa nawaye ba yasa tajuya bayanta dasauri....,lokaci d'aya idonsu yahad'u dana juna,gabanta yayi wata irin fad'uwa,atake gumi yafara rufe mata fuska,idonta yayi tsilli-tsilli qarara tsoro ya baiyana a cikinsu,Addu'ah take aranta Allah yasa baiji maganganun datayi ba, kallonta yake fuskar nan tasa murtuk babu alamun fara'ah,amma hakan bai hana kyawunsa baiyana ba,kyakykywane ajin farko,kamar kullum yana sanye cikin kakinsa na Soja,kayan yayi mutuqar yimasa kyau,farar fatar jikinsa tabada hadin kai wajan qawata uniform din a jikinsa,agaban rigar bangaren hannun dama an rubuta CAPTAIN ARYAN,gefen hannun hagu kuma an rubuta NIGERIAN ARMY. Jikinta ne yadauki rawa,cikin sauri tacire idonta daga nashi,gani take kamar wani abu ne yake futowa daga cikin nasa idon yana shigewa cikin nata idon,da sauri ta matsa ta bashi hanya, tayi wuf tafice daga part din nasu,saura qiris ta doka tuntu6e takayarda yaron hannunta,kai tsaye ta nufi get tafice daga gidan, saida taje bakin get din nasu sannan taga sauran mutane sunata daukar kayan abinci kama daga shinkafa har zuwa taliya da macaroni,gakuma wasu sojoji a tsaye agefe kowanne hannunsa daukeda bindiga, cikin sauri ta wuce kai tsaye taje takai yaron gidansu, sannan tadawo gida,tanaji tana gani part dinsu ya gagareta shiga,sai part dinsu Nabiha ta wuce. Duk yanda sanyin esi ya ratsa dakin Nabiha, hakan bai hana Mawahib cire hijabin jikinta tana sake firfita dashi ba,Nabiha tace"meyake faruwa ne Mawahib naga sai gumi kike hadawa?" Cikin rawar murya tace"nida Yaya Captain ne...,maganganu nasaki baki inata fada,bansan yana bayana ba,bansani ba yaji abinda nake fada ko baiji ba,amma kunya ta kamani, na aikata abinda ba halina bane Nabiha" Cikin sauri Nabiha tace"innalillah....Yaya Captain kuma?to me kikace? wacce maganar kikayi?" Mawahib tayi shiru tana tunanin me zata cewa Nabiha? nayi maganar nono kuma Yaya Captain yajini?kokuma nagama zaginsa tsaf kuma yajini? Cikin sauri ta girgiza kanta tace"kede abar kaza cikin gashinta,amma na tabbatar inde yaji abinda nafada,babu abinda zai hanashi dukana" Nabiha tace"to yau kin janyo mana ruwa, kinganni nan? tunda naji hayaniya a waje nasan cewa shine yazo,shiyasa naqi fita ko nan da can" Mawahib tace"to yanzu yaya zanyi Nabiha?" Nabiha tace"wai akenki yayi kikaqi zuwa ne?" Cikin rawar murya Mawahib tace"nace miki kidena tambayata abar kaza cikin gashin ta,ni wallahi yau babu inda zanje daga nan" Tana fadar haka ta kwanta a gadon Nabiha tareda shigewa cikin bargo,gaba daya sai taji zazza6i yana neman rufeta. Ba'ita ce tabar part dinsu Nabiha ba, saida aka kira sallar magrib, taji gidan shiru alamun duka mazan gidan suntafi masallaci, sannan ta lalla6o ta wuce part dinsu da gudu. da daddare suna zaune afalo da Mawahib da Abba dakuma Mamy suna kallo, Mawahib tana sanye cikin doguwar riga ta bacci amma mai kauri, su Mamy suna kallo suna fira kad'an kad'an, amma Mawahib gaba daya tunaninta baya kansu, shawara tagama yankewa aranta gara tahada kayanta tatafi maiduguri idan taji labari Yaya Captain yatafi, saita dawo, kokad'an bataji dadin zuwansa ba, ga kuma rashin kunyar data gama yimasa wanda bata saniba yaji ko baiji ba. Abbanta yayi magana yaji shiru bata saka baki, a hankali yajuya ya kalle ta yace"yanmatan Abba, babu matsala deko?" Kallansa tayi cikin ladabi tace" Abba babu matsala,amma inaso idan ka amince zanje maiduguri" Abba Yajuya ya Kalli Mamy yace "lafiya zata tafi?" Mamy tace"Alhaji nima sai yanzu naji zancen tafiyar" Cikin mamaki yace"meyafaru zaki tafi,kuma tafiya babu shiri baki sanarda mahaifiyar kiba?" Wani irin murmushin qarfin hali tayi sannan tace"Abba dama inaso naje hutu ne kafin hutun mu yaqare" Abba yace"A a Ruqayya,yaushe kukai hutun ai baki gama hutawa ba,sannan ga yayanku yazo d'azu da yamma, kowa yana gida,bai kamata kitafi ba,ni kinyi masa murna ne akan karramawar daya samu?" Wani irin qullutun taqaici ne yakama Mawahib,yanzu saboda Allah dan Yaya Captain yazo sai ahanata tafiya hutu maiduguri? Cikin kwanciyar hankali ta shimfidawa Abbannata qarya tace"eh dazu mungaisa nayi masa ala sanya Alkhairi" Tana rufe baki, aka turo qofar part din nasu aka shigo,wani irin qamshi mai dadi yadaki hancin Mawahib,sanin datayi cewa irin qamshin dazu ne, hakanne ya tabbatar mata da cewa Yaya Captain ne, hakanne yasa koda wasa batayi kuskuren dago kanta ba,cikin sallama suka shigo falon,dukansu su biyun sanye sukeda wando three quarter, da riga marar hannu alamun kayan shan is'ka ne a jikinsu tunna yamma,gaba daya sai suka saje suka zama abu d'aya,saide fuskar mutum daya data kasance babu wasa akanta. Mawahib tayi mutuwar zaune kamar ruwa ya cinyeta,saika rantse bata cikin falon. Cikin farinciki Mamy tace"yan samari" Captain yad'ora hannunsa akan daya daga cikin kujerun falon yace"Anty Ma-my...." yakira sunanta a rarrabe,cikin murmushi tace"Captain" Yaya Ashraf yace"Anty Mamy akwai sauran kunun madarar nan na dazu?" Mamy tace"akwai, yana dinning bari in dauko muku" Tafadi hakan tana kokarin tashi, Abba ya Kalle ta yace"yakamata kiyiwa 'ya'yanki fad'an ajiye iyali Maryam" Mamy takawo musu kunun madarar wanda yaji kwakwa aciki har lokacin da zafinsa,tazuba musu a cup tabawa kowa,ta zauna a kujera tana fadin"to gasunan de Alhaji,inajin saimun fara tallarsu a yanar gizo" Adede lokacin Yaya Nabil yakira wayar Mawahib,a hankali tasaki wata irin ajiyar zuciya,dama atakure take a wajan,idan tatuna maganar Nabiha datake cewa Yaya Ashraf yana sonta, tasake tunawa da kato6arar datayiwa Yaya Captain dazu, gaba daya saitajita atakure, a hankali tamiqe tanufi hanyar dakinta,Captain Aryan yana shan kunun madara yad'ago da manyan idonsa a hankali yabita da kallo,karaf idonsa ya sauka akan hips dinta,cikin sauri yad'auke kansa. Shikuwa Yaya Ashraf kasa daina kallonta yayi, har saida yaga ta shige dakinta tareda rufowa. Mamy tayi ajiyar zuciya ganin Mawahib tabar wajan,gaba dayansu tana lura dasu yanda suka bi yarinyar da kallo, musanman Ashraf da tun shigowar su ya kafeta dawani irin kallo,to shikuma Captain Aryan kallon na menene? a hankali gabanta yafara faduwa,amma data tuna da maganar Nabil, saitaji hankalin ta ya kwanta harta sake sukaita firarsu. Sun dade a part din Mamy sannan suka tafi dakin su,Ashraf yafara gyara musu lafiyaiyen gadon su,Captain yana danna wayarsa,d'ayar wayar tasa ce tayi qara, yadauka yana magana a hankali kamar da mace yake magana,Ashraf yayi tunanin Captain din yayi sabuwar budurwa ne, a hankali yadago yana kallon sa saiyaji yana cewa"A a bamu da irin wannan bindigar,idan zaka shigar da bayanan ka rubuta muna buqatar irinta,musanman saboda sababbin ma'aikata wanda zasu kar6i horo ok?" Daga dayan 6angaren aka amsa masa, sannan ya ajiye wayar. Ashraf yace"bansan yau zaka shigo gari ba, da nasa yaran nan sun gyara mana dakin,duk yayi datti wallahi" Hankalinsa yana kan waya yace"nima bansan zan taho ba,kawai nagaji ne,kuma inason ganinka kaida Momy, shiyasa kawai nataho,toko muje gidanka mu kwana tareda wad'ancen sojojin?" Ashraf yace"Rigima boy kenan....babu matsala mu kwanta kawai gobe saisu gyara mana,wai kasan yarinyar nan Zulaihat kuwa har yanzu tana nan tanata nacin kirana?" Captain ya ajiye wayar hannunsa yace"karabu da'ita kawai,dan nima ganin farko danayi mata naji tamin..."(😲) Ashraf yace"but... tabani tausayi, tana kuka tana tambayata meyasa zan yaudareta?" Cikin rashin damuwa Captain yace"toya zatayi? Kashareta kawai kanemi wata" Ashraf ya zauna abakin gadon ya kalli Captain yace"amma kasan idan nasake yin wata budurwar kace kana sonta saika raina kanka?" Captain yace"to idan aka dace Ina sonta ya zakayi? zamu auri mace d'aya ne?" Ashraf yadauki fillo yadora a cinyarsa sannan yace"wai kai baka ga Mawahib bane?" Saida ya yatsina fuskarsa sannan yace"wace hakan?"(😲) Ashraf yayi masa wata irin harara sannan yace"Mawahib d'in Anty Mamy mana" Cikin rashin kula Captain yace "Oh..." Ashraf yace"kamarya oh.....? wai kana nufin har yanzu kana nan kanaqin yarinyar nan?,ko saboda Anty Mamy yakamata kadena nunawa 'yarta qiyaiya...." Cikin damuwa ya lumshe idonsa yabude sannan yace"Bansan jin maganar marar kunyar yarinyar nan Ash...,at all ma nibata gabana,ni maqiyin qasata shine maqiyina ba wannan qwailar ba...."(🙊😳😱) (cin mutunci😲Captain mungode) Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 5&6 Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,za'a fara dora muku Audio Novel's👇🏻 https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels ____ Bayan tagama abinda take bata dawo gidanba saida ta daidaici lokacin dawowar Mamy daga Asbiti yayi, sannan itama tadawo gidan, gashin nan nata kuwa yasha gyara sai qyalli yake,jikinta yayi sumul dashi kamar ka latsa jini yafuto, koda ta nunawa Mamy gyaran da'aka mata koda wasa bata fad'a mata yanda sukai da Hajiya Kilishi ba. Washegari da daddare suna zaune afalo gaba dayansu,Mawahib tana sanye cikin kayan bacci riga da wando mai santsi,wandon dogone har qasa, sai 'yar qaramar riga, tayafa dan qaramin mayafi a jikinta,amma kana Iya hango yanda sumar gashinta ta kwanta a goshinta. Abba ya ajiye cup din hannunsa mai daukeda fruit salat, yad'auki remote yana canja channel tareda fadin"dazu su Yaya Ibrahim suka tafi Abuja,sunyi min magana kozan samu zuwa to ayyuka sunmin yawa a office shiyasa nima ban bisu ba,yauce ranar da za'a karrama su ARYAN,yana d'aya daga cikin wanda shugaban qasa zai karrama su saboda qwazonsu a wajan aiki" Mawahib dake danna wayarta tayi shiru tana Jin abinda Abbanta yake fad'a,a wannan baqin halin na Yaya Captain tarasa yanda akai harya samu yashiga jikin manya gashi hardashi za'a karrama. Cikin murna taji Abbanta yana fadin"Alhamdulillah Maryam kinga ma gashi suna nunawa a wannan tashar" Cikin farinciki Mamy Tace"masha Allah,aikam gasunan,Alhamdulillah, Allah yasanya Alkhairi" Cikin Jin dad'i Abba yace"ni gaba d'ayama sainaga Mawahib tana juyewa tana yin kama dashi,da idon,da hancin, da bakin,gaba daya na Captain Aryan ta d'auko" Yajuya ya Kalli Mawahib da hankalinta yake kan waya ko inda TV take bata kalla ba,yace"koba hakaba 'yanmatan Abba?" Ahankali tasaki wani murmushi mai kamada yaqe... Sai a lokacin ta kalli tv,idonta ya sauka a kansa,kamar kullum yana nan da kyansa,kwantaccen sajen daya zagaye bakinsa irinna Yaya Ashraf yasake qawata farar fuskarsa kamar balarabe,jan lips dinsa d'an qarami mai mutuqar laushi sai sheqi yake kamar ya shafa musu lipstick,fuskar nan tasa ad'aure kana gani kasan babu wasa kamar ma baya farinciki da karramawar da akayi masa,yana tsaye qyam ya qame waje d'aya,ga shugaban qasa da kansa yana sake gyara masa rank dinsa,ga manya manyan sojoji daga gefe kowa ya qame a tsaye, saida shugaban qasa yagama gyara masa rigarsa,sannan shikuma yasara masa,sannan aka fadi irin jajircewar dayake akan aikinsa, tareda kyautar kudi Naira million arba'in,anan aka buqaci daya daga cikin familynsa yazo su kar6i kyautar tare,kai tsaye Alqali yatura Ashraf,cikin nutsuwa Yaya Ashraf yataka yaje gaban Aryan din suka kar6i kyautar tare,bama sai anyiwa mutane bayani ba,ana ganin ashraf wanda basu san cewa Captain Aryan 'yanbiyu neba, yau kam sun sani,tsirarun 'yanmata wanda suka samu damar zuwa wajan taron lokaci daya kallon su yakoma wajan Ashraf da Captain Aryan,kowa mamaki yake dama wannan miskilin Sojan 'yanbiyu ne? Mawahib tagama qarewa Captain Aryan kallo, taga babu wata kama dasuke kamar yanda Abbanta yafada, banda fari dayake dashi irinnata ita bataga wani abun birgewa a wajan Yaya Captain ba bare har taji dadi dan ance suna kama. Ganin yanda sauran sojoji suke qara girmama shi kamar wani nagaske,hakan yasa Mawahib taji wani irin baqin ciki,sai yanzu ne tagane dalilin zuwan Yaya Ashraf gida,a hankali tatashi ta wuce dakinta. Abba yabi Mawahib da kallo harta shige dakinta,yajuyo ya kalli Mamy yace"madam ya kamata fa asamawa Ruqayya qanne,naga tatafi daki kamar tana fishi,kuma nasan ba fishi take ba, kawai shagwa6a take ji ba'a tafi da'ita wajan taron nan na yayansu ba,shiyasa tatafi d'aki"(🙊) Mamy tayi murmushi batace komai ba,shima Abba yayi dariya yace"emanah,tana ganin itace qarama a gidan shiyasa take shagwa6a son ranta,inda tanada qanne ai zata rage shagwa6ar" Mamy tayi murmushi tace"Alhaji kenan,babu wani shagwa6a ita tasan meyake damunta" Cikin jin dadi yabi ilahirin jikinta dawani irin mayen kallo sannan yace"Allah koh?" Itama murmushin tasake yi batace dashi uffan ba,saboda tasan ma'anar kallon dayake binta dashi(🙈) Washegari Hajiya kilishi ce ta kar6i girki,a qa'ida kuma inde itace tayi girki babu wanda take kaiwa part dinsa,saide kowa yaje yadauka,saboda itace babba,Mawahib bataje ta d'auko musu nasu abincin ba,saboda Mamy tana wajan aiki,shima Abba yafita bai dawo ba,ita kadai ce kuma ba yunwa take ji ba, tun safe aketa sallama a gidan,ana zuwa anayi wa Hajiya kilishi murnar karramawar da Captain Aryan yasamu,sai hayaniya akeyi, tana kwance afalonsu tana chat da Yaya Nabil,wani d'an kawunta dake maiduguri tana jiyo surutun mutane kala kala,bata fita d'aukar abincin ba saida taji hayaniyar mutane ta ragu a lokacin itama tagama chat d'inta,rana tayi sanyi, sannan ta futo,tana sanye cikin doguwar riga marar hannu,yadin rigar yanada laushi, daga gaban rigar anyi mata ado da baqin leshi,sai dan qaramin mayafi data d'ora akanta,babu kowa atsakar gidan,kai tsaye ta wuce kitchen tad'auko nasu abincin,futowar ta kenan daga kitchen din adede lokacin Hajiya kilishi tafuto daga part d'inta itada wata babbar mace da alama qawarta ce, cikin ladabi ta rissina tace"Momy Ina wunin ku" Hajiya kilishi ta amsa a taqaice tace"lafiya" Ita kuma d'ayar cikin murmushi ta amsa tana bin Mawahib da kallo harta shige part dinsu, saida taga shigewar Mawahib sannan ta maida kallonta wajan Hajiya kilishi tace"Matar Alqali,Ina kuka samo 'yar kyakykywar yarinya haka?" Hajiya kilishi tace"Hajiya Mariya baki ganeta bane?" Wadda aka kira da Hajiya Mariya tace"ina zansan wannan yarinyar? duk zuwan danake bana ganinta,anya anan gidan take kuwa? Kina ganin yarinya jajir da'ita kamar wankan inji? Kiduba kiga wannan uban diri kamar ita tayi kanta,badan da 'yanbiyun samarinki a gidan ba aida nayiwa Farouq d'ina kamu..." Hajiya kilishi tace" 'yar wajan Maryam cefa,da wanne samarin zaki had'ata?,inaaa! bade 'yanbiyu naba,har abada babu had'i, yanda kika gantannan kullum haka take yawo tana nunawa mutane jiki,ita ga tantiriya,kuma uwarta ce take koya mata komai,idan na kuskura nabari yarinyar nan ta auri d'ana aina kashe kaina, tun yanzu ma kafin ayi mata aure bad'ala iri-iri uwarta take koya mata,to inaga anyi aure? tana saka irin wannan kayan yanzu,idan tayi aure kuma wanne iri kike tunanin zata saka?kinsan 'yar maiduguri ce uwar, idan 'yarta ta auri dana kuma ai shikkenan sai yanda aka min dashi, kiduba kigani de yanda tashiga tafita a wajan malamai da bokaye saida tarabani da 'yanbiyu nah,basu Isa suzo gidan nanba saide kiga sunje part dinta sun tare,Ashraf ma dayazo shekaran jiya danyaga na tsaye masa ne, na Kuma saka masa ido,amma da abinci ma Infad'a miki saide yaci awajanta, to inda nakejin dad'i sauqina d'aya,yarinyar bata gabansu duka su biyun, musanman ma ARYAN...." Cikin sauri Hajiya Mariya ta katse ta" ke dakata matar Alqali,wai kina nufin yarinyar nan ce 'yar wajan Maryam tagirma haka?" Hajiya kilishi tace"hmm ai Ina ganin ikon Allah Hajiya Mariya,itace wallahi,ai kallon tsoro kikai mata,bakiga uban nonuwan taba" Hajiya Mariya tayi ajiyar zuciya tace"to aikuwa matar Alqali tun wuri kitashi tsaye,inba hakaba kiyiwa kanki sakiyar daba ruwa..." Cikin sauri Hajiya kilishi tace "wa?, Allah yatsare ni,ai har abada babu alkhairi a tsakanin ta da 'yanbiyu na,to Ina alkhairi ga yarinyar da batayi gadon haihuwa ba? Ita kad'ai uwarta tahaifa daga ita babu qari, ita kuwa bana tunanin ma idan tayi auren zata haihu, tunda batayi gadon haihuwa ba,to waima INA UBANTA?, har zuwa yanzu mude bamu ganshi da idonmu ba"(😳🙆🏻‍♀️tofa) Hajiya Mariya tayi ajiyar zuciya tace"tabdi, aikuwa matar Alqali saiki dage,kuma kisawa 'ya'yanki ido sosai, kinsan maza da jarabar tsiya,da gane-gane, suna qyalla ido idan suka ganta shikkenan,musanman idan wannan dirin nata ya rud'esu,kina zaune saide kiji Ashraf yana cewa shizai aure ta shima Aryan yana fad'in shi zai aure ta...."(😂) Hajiya kilishi tayi ajiyar zuciya tace"kada ubangiji ya nunamin wannan baqar rana....to Hajiya Mariya ai bakisan wani abuba,gaba d'ayansu su biyun fa har yanzu basuda tsayaiyar budurwa,abun har tsoro yake bani, shekaru sunata tafiya sunqi aure, musanman Aryan, shi bashida magana, bansan yaya zaiyi yasamu mace ba" Hajiya Mariya tace"tokode baqar aljana ce ta aure shi?" Cikin sauri Hajiya kilishi tace"aiko farar aljana ce dole zaiyi aure shima ya ajiye zuri'ah" "wannan gaskiya ne" cewar Hajiya Mariya, daga nan tarakota get dinsu na farko, sannan tadawo. ****** Da daddare Mamy tagama cin abinci suna zaune afalo gaba d'ayansu, yayanta dake maiduguri Alhaji Mustapha yakira wayarta, bayan sun gaisa yace"Maryam yaronki ne yasani wannan waya, kinganshi nan zaune tun yamma yazo yasani agaba lalle saina kiraki nafada miki shifa yanason Mawahib,yace nafada miki yanason ayi masa izni yafara zuwa wajanta zance " Mamy tayi murmushi,tasan cewa yayan nata bashida wani da namiji Sai guda daya, sauran duka mata ne, cikin Jin dadi tace"Nabil kenan,yanzu nice nazama haka awajansa? bazai Iya kirana yafadamin da kansa yanason Mawahib ba saide yasaka kakirani kaida kanka Yaya?" Gaban Mawahib ne yayi wata irin faduwa Jin maganar akanta akeyi,dama Yaya Nabil sonta yake shiyasa taga kwana biyu yana matsa mata da magana idan tahadu dashi a chat? Bata gama tunanin datake ba taji Mamy tana cewa"a a, batada kowa Yaya, amma Nabil aina gida ne,Allah yasanya Alkhairi, Allah yasa rabon sa ce" Bayan sungama wayar,cikin jin dadi Mamy ta Kalli Alhaji Isah tace"Abban Mawahib kaji wai Nabil din Yaya Mustapha ne yace afada mana yanason Mawahib" Abba yayi murmushi ya Kalli gefenda Mawahib take zaune kamar ruwa ya cinyeta,cikin tsokana yace"yanmatana wai zaki aure shi kigudu kibarmu?" Cikin kunya tatashi da sauri tafice daga part din nasu, tatafi wajan Nabiha. Alhaji Isah yayi murmushi yace" To Alhamdulillah, gaskiya naji dadi sosai, Nabil ai yanada hankali,zansamu su Yaya inyi musu maganar,shima saiki fada masa yazo suyi magana shida Mawahib din,idan sun sasanta kansu shikkenan, idan Allah yayi auren dashi,saita qarasa karatunta adakin mijinta" Mamy tayi murmushi tace"hakane,amma gaskiya ni naso ace saita kammala karatunta sannan zatayi aure,banason irin neman aure da wurin nan,duka-duka ma nawa Mawahib din take?shekara goma sha takwas Alhaji wanne irin aure ne wannan zasuyi?" Abba yayi murmushi yace"wanne karatu Maryam?yaushe tafara karatun? ko level two bata shiga bafa yanzu tasa qafa a karatun,kicire wannan tunanin aranki inde harshi Nabil din zai barta tayi karatunta ai Alhamdulillah, batun shekaru kuma bawata matsala bane,tawani fannin ma gara hakan, mijinta zai koya mata soyaiya da kansa, sannan kuma kinsan abinda mu iyaye mukeso akan yayanmu qaddara tana zuwa ta sauya shi,kiga abinda mukeso din bai faruba, ke kinaso ace tagama karatu, taqara shekaru, sannan tayi aure,nikuma abinda yake Raina shine naso ace ta auri Yayanta CAPTAIN ARYAN,dukansu dagashi har ita Ina musu sha'awar junansu" Gaban Mamy ya yanke yafadi,cikin sauri tace"Alhaji kadena wannan maganar Dan Allah, Allah yasa Nabil din yazame mata mafi Alkhairi" Cikin Sanyin jiki Abba ya amsa mata da "Amin" ****** Tana zuwa dakin Nabiha tace"Nabiha nadena zuwa wajanki daga yau, ke bakida aiki saiki ki shige daki ki dauki wayarki,gaba daya kin manta dani" Cikin murmushi Nabiha tace"to yi haquri,nadena, shikkenan? meyake faruwa naganki yanzu goma saura?" Saida ta yatsina fuskarta sannan tace"kinsan me?wai Yaya Nabil ne yasa kawu Mustapha yayiwa Mamy magana wai yana sona" Nabiha tanajin haka tagyara zama tace"ke dan Allah?" Mawahib tace"wallahi,Nina rasa yanda zanyi,gaskiya ni bana sonshi,amma zan aure shi kodan Momy kilishi, idan tadena ganina ai shikkenan, bazata sake fada mana magana nida Mamy naba" Nabiha tayi ajiyar zuciya tace"hakane kam, amma gaskiya nide Mawahib nafi miki sha'awar Yaya Ashraf,saboda naga kamar yana ra'ayinki" Cikin sauri Mawahib tazaro idonta(😳) tace"Rufamin asiri Nabiha,inani Ina 'ya'yan Momy kilishi?,sannan kuma yamin girma,banason tsoho, gara yaro dan ashirin dawani abu" Nabiha tayi murmushi tace"lalle yarinyar nan, Yaya Ashraf ne tsoho? to bari Kiji wallahi irinsu akeso,sunfi yaran Iya soyayya....wallahi innice ke ko,yanda Yaya Ashraf dinnan yake kulaki,wallahi sainayi soyayya dashi Inga Yaya Momy kilishi zatayi,Yaya Captain nede dama bamu Isa mugwada hakan ba" (😂) Mawahib tace"Nabiha ko amafarki bana fatan nayi soyaiya da 'ya'yanta, zama lafiya aiyafi zama dan sarki" Haka suka dinga tattauna zancen har shadaya nadare,sannan Nabiha tarakota, sukai sallama ****** Washegari tun kafin tatashi daga bacci Nabil yakira ta yakai sau biyar tana bacci bata dauka ba,kuma wayar tana silent, saida tatashi taga messages dinsa dayawa,kusan guda hudu, duka babu wanda bai zuba mata kalaman soyaiya ba,kasancewar ta farin shigan soyaiya tafi minti ashirin tana daga kwance tanata aikin karanta saqonnin nasa,daga baya kuma tatashi tayi wanka ta shirya ta futo ta gyara musu gidan,bata dade da gama aikin ba Mamy tadawo kasancewar yau juma'ah da wuri take dawowa,sai bayan ansauko daga sallar juma'ah sannan Nabil yakira ta,sun dade suna waya tun Mamy tana mamakin Mawahib harta dawo ta daina ganin yanda take magana qasa qasa ita Ala dole da saurayi take waya, da abun ya isheta saita Kalle ta tace"Mawahib kije daki kiyi wayar mana"(😂) Babu musu tawuce dakinta,saida sukazo sallama dashi ne sannan yake fada mata zaizo gobe,me takeso yataho mata dashi, ta nuna masa batason komai, daga qarshe sukai sallama. Saida daddare take fadawa Mamy Yaya Nabil zaizo gobe,Mamy tayi murmushi tace"Allah yakawo shi lafiya" Washegari da sassafe taje tatashi Nabiha daga bacci,cikin Jin dadin bacci Nabiha tace"dan Allah Mawahib ki barni nayi bacci na" Mawahib tace"kitashi dan Allah Yaya Nabil ne zaizo anjima, yamin waya yana hanya wallahi" Cikin sauri Nabiha tatashi zaune tace"wai daga maidugurin zaizo?" Tace"eh,bansan me zanyi masa ba,nahada masa drinks kawai yayi?" Nabiha tace"haba Mawahib,ya mutum zaizo tundaga maiduguri amma mu bashi lemo, kinsan me? fita zamuyi muyo cefane muyi masa girki mai dadi, kinsan yau momy kilishi ce zatayi girki ba Mamy ba bare muce zamu bashi abincin gida,kuma wallahi momy kilishi abincin gargajiya takeyi, kawai kije kifuto muje driver yakaimu kasuwa muyo cefane mudawo" Mawahib ta jinjina kanta tace"eh hakane kuma,to bari inje in shirya, kema kitashi dan Allah" Cikin sauri suka shirya suka fita,driver yakaisu suka siyo abinda suke so, sannan suka dawo gida, suna dawowa ko zama ba suyi ba suka fada kitchen, kasancewar kayan maqulashe suka hada masa nan da nan suka gama kafin ma ace Hajiya Kilishi ta shigo kitchen din, Mamy de taga anata jera girke girke afalo cikin ranta tace"ikon Allah,zamani kenan" Sai wajan qarfe uku na yamma yazo,kasancewar sa ba baqo ba a gidan yasa kai tsaye Mawahib ta shigo dashi falo,saurayi ne matashi bazai wuce shekara ashirin da bakwai ba. batayi kwalliya mai yawa ba,kawai light makeup tayi,tasaka riga da siket na leshi,tayafa mayafi dan madaidaici mai kyau, bayan sun gaisa ta gabatar masa da kayan ciye ciye, babu kunya yaci abunsa sosai, sannan takira masa Mamy suka gaisa, Mamy tadan dade a zaune tana tambayarsa 'yan'uwanta mutanan maiduguri, sannan ta koma daki tabarsu shida Mawahib din. Cikin nutsuwa yafara yiwa Mawahib magana cikin sigar jan hankali domin kuwa ya lura bata taba soyaiya ba,a hankali a hankali harya dinga janta da zance harta sake dashi,nan da nan ya dinga sakata dariya sai gashi tun kafin yatafi taji ya kwanta mata arai kasancewar sa mutum mai barkwanci, maisata nishadi. bai dade sosai ba yace zai tafi, kasancewar tafiyar akwai nisa,sai a lokacin takira masa Nabiha suka gaisa,dazata tafi yadauki 5k yabata, Nabiha tayi masa godia sosai, sannan tatafi, ita kuma Mawahib suka qarasa tattauna wa sannan ta futo zata rakashi,sunzo get nafarko ya kalleta yace"to Amarya ta,zan tafi,sai yaushe kenan?" Kalmar daya fada ta amarya ta, itace tasa Mawahib dariya,har dimples dinta suna futowa, adede lokacin musa megadi ya budewa Ashraf get yasako hancin motarsa ciki,dasu yafara cin karo,tun daga nesa ya hangota tana yiwa wani qato murmushi, lokaci daya yanemi annurin fuskarsa yarasa,ko gama daidaita parking baiyi ba yafuto daga cikin motar ya nufi get na biyu,fuskar nan tasa a murtuke, Mawahib data dago daga dariyar datake lokaci daya tayi ido biyu dashi, mamaki ya kamata,kode Yaya Captain ne yadawo? to ai kuma idan shine yadawo dole zata sani,da tuni qofar gidansu ma yacika da jama'ah, to meyasamu Yaya Ashraf yayi irin wannan daure fuskar?gaba daya saiya koma mata Yaya Captain sak. Koda wasa baima kalli inda suke ba yabude get din zai shige,Nabil ya kalle shi cikin mutuntawa yace"barka da shigowa Ina wuni?" Ba tareda ya kallesu ba yace"lafiya" kamar anyi masa dole, yana shigewa ciki Nabil ya Kalli Mawahib yace"Sojan gidanku yadawo ne? naga shine baya fara'ah, kinsan niba ganesu nakeba" Mawahib tayi wata dariya Mai kamada yaqe, tace"shine...," Saide cikin ranta tana mamakin sauya war Yaya Ashraf zuwa fishi, idan ta cewa Yaya Nabil bashi bane zai Iya tunanin wani abu, shiyasa tayi masa qarya cewa Yaya Captain ne. Nabil yayi ajiyar zuciya yace"rannan naga bbc sunyi posting din karramawar da'aka musu,naga photon sa shida shugaban qasa, Allah yasanya Alkhairi" Kanta aqasa tace masa "Amin ya Allah" Motarsa yabude yadauko mata wata babbar leda fara, yabata yace "ki shiga da wannan ciki,babu yawa yar qaramar kyautata ce izuwa gareki" Cikin sauri ta girgiza masa kai tace"A a,Mamy zatamin fada,babu ruwana ka barshi" Murmushi yayi yace"naji, to ki kar6a zankirata awaya inyi mata magana" Saida taji haka sannan ta kar6a tayi masa godia,yace zaije suyi sallama dasu Alqali sannan yawuce,tayi masa Addu'ah,sannan tajuyo zuwa cikin gida. Tana shiga part dinsu, ta tsinci muryar Yaya Ashraf cikin fishi yana fadin"Amma Anty Mamy yaushe tafara karatu da zaku barta tafara sauraron samari yanzu? waye yabata damar kula samari haka anyhow....?" baima tsaya jin amsar da Mamyn zata bashi ba yajuya cikin 6acin rai zai fice daga part din,yana ganin Mawahib abakin qofa a tsaye da U uwar leda a hannunta yazo wucewa ta gefenta qiris yarage ya bigeta, cikin sauri ta matsa gefe, tsananin mamaki ya cikata dama shima yana fishi haka?(🤔) Mamy takasa magana tabi Ashraf da kallon mamaki harya fice daga part din,a hankali tasaki murmushi ganin wannan qarfin hali nasa, gaba daya tagama gane inda yadosa,kuma hakan bazai ta6a iyuwa ba,koda ace Mawahib din tana sonshi dole zata haqura dashi, haka inma mazan gidan sukace zasu qullah to bazata yarda ba,saide wannan karon a saketa har abada tafice tabar familyn Alqali. (wata sabuwa🥺😱) Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 9&10 Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin Samun Audio Novel's👇🏻 https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels Captain Aryan yaci gaba da fadin "please kadena min maganar ta" Ashraf yace"dole inyi ma maganar ta kuwa, saboda Ina sonta, najira kadawo ne infara yima maganar,banason kai tsaye in yiwa su Daddy maganar, kaima kuma kadawo kace kana sonta" Captain Aryan dayake kwance cikin wani irin fargici ya tashi zaune yace"inso wa? ni...? Inrasa wazan aura sai wannan abar?" Cikin zafin rai Ashraf yace"yauka fara? sau nawa Ina nemo yarinyar dazan aura kana cewa kaima ita kakeso? ban'isa inyi sabuwar Baby ba, kaima saika sota, 'yanbiyu mata masu kama daya kakeso insamo mana? shiyasa nafara fad'ama maganar,kar inje infad'awa su Daddy inason Mawahib kaima ka dage kace kai sai ita..., inkasan kana sonta to tun wuri inyi shiru da maganar" Cikin taqaici Captain Aryan yace"kaga Ashraf,dan Allah idan zakayi zancen 'yanmata, toka dena saka yarinyar nan aciki, idan zaka so kowacce irin yarinya tonima zan'iya sonta,saboda jinin mu ahad'e yake,zan'iya son dukkan 'yanmatanka,amma banda ita..."(🙆🏻‍♀️) Ashraf yayi shiru yana qarewa dan'uwan nasa kallo, tunda yacewa Mawahib qwaila yake tantama aransa anya Aryan yana cikin hankalin sa kuwa?kokuma de ya makance? Ahankali yasaki ajiyar zuciya yace"kagama?" Kai tsaye Captain yace"ban gamaba,inaso kasani batada abubuwan dazaija hankali na har'insota,bazan ta6a sontaba har abada,nawuce ajinta,bata cikin tsarina,bata Isa takama qafar irin matar dazan aura ba, sannan kaima Ina gargadinka,karka bari Momy taji maganar nan ,kuma abinda ya shafeni kaima yariga ya shafeka,bana qaunar ta,saboda haka dole kaima karabu da'ita tunda bana sonta...." Ashraf yace"saboda kaine kakawo ni duniyar ko? to saina aureta,inyaso ka mutu" Cikin sauri Captain Aryan yace"saide kaika mutu,kuma baka Isa ka auretaba INDE INA RAYE" Ashraf yace"tosaika hana mugani" Yafadi hakan tareda sakin tsaki, ya dauke fillonsa yamaida shi qafafun Aryan,ma'ana sukai kaida qafa. Kusan minti biyar dukansu sukai shiru babu wanda yasake yin magana, sai can Captain Aryan shima yasaki tsaki yadauke fillonsa yadawo dashi kusadana Ashraf.(😂) Ashraf yana jinsa yayi shiru ya qyaleshi,Captain yaji shiru Ashraf bai kula shi ba duk da yadawo da fillonsa wajansa,a hankali yace"Ashraf..." Ashraf yayi shiru yaqyaleshi, yasake sakin dan qaramin tsaki yace"Ashraf katashi kayi Addu'ah" Babu musu Ashraf yatashi yafara Addu'ah,saida yagama addu'ar sannan ya kalli Captain Aryan yace"kai kayi addu'ar ne?" shima Captain Aryan yanajin Ashraf din yayi shiru yarabu dashi(😂) Ashraf yasan sarai yana jinsa,sai yayi murmushi kawai yad'ora hannunsa akan lallausar sumar Aryan din batare daya qara magana ba,yanajin lokacin da Aryan din yafara bacci, amma shi bai fara bacci ba yana tunanin yanda zai 6ullowa iyayensu akan maganar aurensa da Mawahib,har wajan qarfe biyu nadare yana tunanin mafita,yanajin yanda Captain Aryan yaketa juye-juye kamar akwai abinda yake damunsa,ahankali ya rufe idonsa har bacci yayi nasarar daukar sa. Cikin dare Captain Aryan yafarka dawani irin ciwon mara,tun yana daurewa harya fara ciza lallausan lips dinsa, ga esi yanayi adakin amma Captain Aryan sai gumi yake had'awa,ahankali ya runtse idonsa yana tuna shawarar da likita yabashi akan wannan ciwon cikin nasa yakamata ace yanemi mace yayi aure hakanne zai kawo qarshan jinyar,ahankali yatashi zai dauko maganinsa yaji bazai Iya miqewa ba. Cikin sauri yafara tashin Ashraf, yace"Ash,tashi!!" Cikin bacci Ashraf yabude idonsa a hankali,ganin Captain Aryan a zaune sai had'a gumi yake hakan yasa yatashi cikin sauri, yadora hannunsa a kafadar Captain din sannan yace"meyake damunka?" Saida ya cija lips dinsa sannan yace"magani na,bani maganina" Cikin sauri Ashraf yasauko daga gadon,yabude yar qaramar jakar da Captain din yazo da'ita ya dudduba sannan yaga maganin,wutar dake gefen gadon su ya kunna saida ya karanta yaga maganin menene, sannan yabashi,yaje fridge ya dauko masa gorar ruwa, cikin sauri Captain Aryan ya 6alli maganin yasaka a bakinsa, sannan yakafa gorar ruwan a bakinsa saida ya shanye shi tas, sannan yafara maida numfashi ahankali. Ashraf ya dafashi yace"Aryan...,nayima magana kadena shan maganin nan,gara kazauna haka idan kayi mafarki shikkenan zakaji sauqin abinda yake damunka" Captain Aryan da kansa yake sunkuye yad'ago ya kalli Ashraf yace"kullum zan zauna kenan banida aiki sai mafarki? ni bazanyi asarar abuna ba,na matata ne...."(🙈🙊) Yaqarasa maganar cikin sigar shagwa6a kamar ba Soja ba Dariya takama Ashraf,amma dayake yasan halin dan'uwan nasa akan wannan dariyar yanzu saiya fara yimasa masifa, saiya danne dariyarsa yayi murmushi yace"tokayi aure" Cikin shagwa6a yace"niba wacce nakeso" Ashraf yace"Okay...mugunta ce tasa kake rabani da 'yanmata na kenan ko? kai baka auraba niban aura ba" Captain Aryan baice dashi uffan ba,yaja fillonsa ya rungume tareda runtse idonsa yana numfashi sama-sama har baccin wahala yadaukeshi. Ashraf yana zaune yana kallonsa saida yaga yayi bacci sannan shima ya kwanta agefensa yayi bacci. Dasafe bayan sungama buga ball dakinsu suka dawo kowa yayi wanka,gaba dayansu suna daure da farin towel a qugunsu sai wani d'an qarami guda d'aya kowa yana goge sumar kansa, Ashraf yad'auki wayarsa ya dokawa Mawahib Kira, a lokacin tana zaune tanashan tea tagama gyaran part dinsu kenan, har zuwa lokacin Mamy bata tashi ba kasancewar yau weekend ne bata tashi da wuri, mamaki ya kamata,kiran Yaya Ashraf da wannan safiyar lafiya? gaba daya sai taji tsoron daga wayar kartaje tunanin Nabiha yazama gaskiya idan kiranta yayi domin yafada mata yana sonta mezatace masa? haka ta kasa daukan wayar harta katse, daga nasa 6angaren yasake kira akaro na biyu,sai a lokacin ta dauka cikin ladabi tace"yaya Ashraf barka da safiya" Saida yasaki wani murmushi najin dadi sannan yace"yawwa Mawahib idan kingama abinda kike please kizo ki gyara mana dakin nan..." Cikin ladabi tace"to Yaya" Daga nan yakashe wayar yad'auki mai zai fara shafawa, Captain ya kalle shi yace"yanzu kai bakaji kunya ba?kasa yarinya agaba kana wani kashe murya saika ce kasamu wata babbar mace,wannan abun kunya har'ina "(😖) Ashraf yayi murmushi yace"kaine kake ganinta amatsayin yarinya,amma Mawahib tanada abinda wata babbar ma batadashi,ka nemi mace kayi aure kaqi, ka dameni da juye-juye cikin dare dashan magani, kawai ka lalla6ani inbarma Mawahib,ninasan abinda nagani, kaima kuma idan ka qarewa yarinyar kallo zakasan akwai kayan alatu" Captain Aryan yasaki wani irin tsaki,cikin 6acin rai yace"Ash...nifa yarinyar nan batada wani abu wanda zangani har inji sha'awarta" Ashraf yabi Captain Aryan da kallon mamaki,to kodai saboda rashin zuwansa gida akai-akai shiyasa baisan yaya Mawahib din take ba? girgiza kansa yayi, da alama dan'uwan nasa baisan yarinyar ba. Captain Aryan yace"kuma a'irin wannan yanayin nawa kwanaki wani me magani yakai office dinmu, a lokacin inajin kasala,bana yin gym kamar yanda nasaba" Ashraf ya zauna abakin gadon nasu yaci gaba da shafa mai a jikinsa,shikuma Captain Aryan yana goge jikinsa da dan qaramin towel din hannunsa,cikin aji kamar bayaso yaci gaba da fadin"naji me maganin yana cewa da maiqo da zaqi da kasala duk maganin yana yi,to nima inajin kasala, sainayi tunanin nima irin nasu ne,nakar6a nasha,inashan maganin nan daga nan labari yafara sauyawa,nakifa kaina qasan table sai hada gumi nake,na riqe mara,da farko nafara jurewa, danaga abun bana qare bane ahaukace naje wajan mai magani najashi gefe,nafada masa abinda nakeji,shine yacemin ai yayi tunanin inada aure, maganin masu aure ne, yaje yanemo min wani abu kamar goro, nide ban tsaya na tantance menene ba nafara ci,shine naji dama dama..." Ashraf ya kwashe da dariya,yace"tokaima kawai daga ganin suna shan magani kaima saika sha?" Adede lokacin Mawahib tazo kofar dakin nasu,a lokacin Captain Aryan baibawa Ashraf amsa ba, ita Kuma Jin shiru tayi tunanin basa cikin dakin,ahankali tatura qofar dakin ta shigo, gabanta ne yafadi ganin murd'ad'd'an jikinsa abaiyane,cikinsa har wani hawa-hawa yake alamun yana motsa jiki,ga faffadan qirjinsa wani irin gashi mai laushi ya kwanta,bata ta6a ganin namiji hakaba,gaba daya saita diririce jikinta yadauki rawa taqame awajan, adede lokacin Captain Aryan wanda bai lurada zuwan Mawahib dakinba,yasaki wata irin dariya wadda tunda Mawahib take, bata ta6a ganin yayi dariya haka ba,cikin dariya yacewa Ashraf "ta'inda ake hawa batanan ake sauka ba?,inacin abinda yabani najini nadawo Normal,daga ranar ban sake cewa zansha ba" Suka saki dariya gaba dayansu,yajuya zai goge kunnansa na hannun dama, karkatawar da zaiyi yaganta a tsaye idonta yayi tsuru-tsuru, lokaci daya annurin fuskarsa ya sauya,ya wullar da towel din dake hannunsa,cikin 6acin rai yadaka mata wata irin tsawa yace"stupid girl....mekikeyi anan!!!?" tun kafin yagama rufe bakinsa Mawahib tajuya da gudu tabar wajan,yanda yaga uban Hips dinta suna kad'awa saboda gudun datake hakanne yasake 6ata masa rai, 'yar qanqanuwar yarinya hartasan tayi ciko...(😱) Ashraf ya ajiye manda yake shafa wa yataso yaduba baiga kowa ba,cikin damuwa yace"miye haka Aryan? Mawahib ce tazo kakoreta ko?" Cikin 6acin rai yace"tayaya yarinya zatazo taganni ahaka ta rainani?" Ashraf yace"nina kirata tazo tagyara mana dakinfa" "ta barshi,kaima idan bazaka gyaraba kabarshi" Ashraf yace"kaine qarami,kaine zaka gyara" Aryan yace"minti nawa kabani?" Ashraf ya harare shi yace"au Allah? to ko zamuje a tambayi Momy?" Cikin sauri Aryan yace"muje" Kamar wani abun arziqi zasuyi haka suka shirya cikin sauri kai tsaye suka nufi part din Hajiya Kilishi,suna shiga Ashraf yace"Momy" Shima Aryan din yace"Momy" Tasan duk lokacin dasuke mata irin wannan kira to musu sukeyi a tsakanin su,cikin sanin abunda ya kawosu Hajiya kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,shekaru ko? nasani, dan Allah kurabu dani zuwa yanzu yaci ace kun daina wannan musun" Alqali dayake zaune yanashan tea yakallesu yayi murmushi,wankan shadda su kayi mai launin light blue,banda shine ya haifesu to zaiyi wahala ya banbance su saboda hatta agogonsu iri daya ne, hular dake kansu ma iri dayace,koda yaushe yana alfahri da 'ya'yansa,tsugunnawa sukai suka gaida shi, sannan Hajiya kilishi tafara hada musu tea din suma, Ashraf yanacin sultan Chips din dake gabansa yana turawa Mawahib text naban haquri,sannan yasake roqarta akan taje tagyara musu dakin itada Nabiha, Mawahib tana ganin text din ta fadawa Mamy, sannan taje tasamu Nabiha, suka nufi dakin su Yaya Ashraf din,suna zuwa suka fara gyara dakin,duk wani kaya dasuka ganshi babu ninki suka ninkesu, suka adana musu shi,saida suka wanke har toilet din komai yayi tsaf, a lokacin aka kira wayar Nabiha, ta amsa wayar tafita, Mawahib kuma ta dauki air freshener tana fesawa a dakin,tabude fridge din dakin tasake gyara lemuka da ruwan dasuke ciki,glass cup din dasuke kan fridge din suma tasake gogesu tana gyara musu zama, adede lokacin suka shigo dakin duka su biyun,Aryan yana ganinta ya daure fuska yanuna mata hanyar fita daga dakin, cikin tsawa yace"get out...." Tsawar da yayi matane yasa ta tsorata batasan lokacin data saki cup din hannunta ba, nan take yafashe,bai damu da yanayin datake ciki na tsorata ba yasake daka mata tsawa yace"zoki fice nace" cikin 6acin rai shima Ashraf yace"Mawahib karki fita" Cikin sauri Captain Aryan ya'iyo kanta gadan-gadan,cikin sauri tayi gudu ta6uya a bayan Yaya Ashraf,ganin Captain Aryan yana tattare hannun rigar sa hakan yasa Ashraf yasaka hannu zai kareta,Mawahib kuwa tana ganin Yaya Ashraf ya tareta tayi qasa tarage tsawon ta, tafice da gudu daga dakin. Cikin 6acin rai Ashraf yace"wai dan Allah menene damuwar kane da yarinyar nan? Aaka kawai yarinya tana walwalarta harka tsorata ta kasa tafita babu nutsuwa" Captain Aryan yana jinsa ya shareshi, Ashraf yaci gaba da fadin "meta tsare ma? haka kawai kasaka yar mutane agaba bakada buri wanda yafi ka zalunceta?" Cikin 6acin rai Captain Aryan yace"wai Ashraf saboda wannan abar kakemin masifa?kanamin masifa saboda ita kamar wanda ka haifeni?" Lokaci daya jikin Ashraf din yayi sanyi,koda suke fadansu saide akan abinda ya shafesu,amma basa fada saboda wani, bazaka ta6a Jin kansuba inde akan wani ne,saide akan abinda ya shafesu su biyu,to yanzu kuma ga Mawahib tana nema tashiga tsakani, cikin damuwa yasaka hannunsa yadafe goshinsa(🤦🏻‍♂️) Sannan ya kalli Captain Aryan yace"meyasa naga kamar kana cikin damuwa ne?,meyake damunka?" Cikin damuwa Captain Aryan yace"no,babu abinda yake damuna,kawai de banajin dadin yanda yarinyar nan take nema tashiga tsakanina dakai,kadena son abinda nakeso saboda ita,banajin dadin zaman,gara in tafi " Cikin sauri Ashraf yace" babu inda zakaje" sannan yakama hannunsa suka zauna abakin gado,ya Kalle shi yace"inajin wani iri wannan zuwan naka Aryan,may be idan katafi sainayi rashin lafiya kamar yanda nasaba,kokuma kai kayi" Captain Aryan yace"kadena tunanin komai,babu abinda zai faru insha Allah,bani kad'ai nazo ba,akwai yaran dasuke tare dani,yakamata inkoma next time idan nazo nikad'ai saina huta sosai" Cikin sanyin jiki Ashraf yace"to Allah yasa,yau ba muje wajan Anty Mamy ba" Captain Aryan ya yatsina fuskar sa yace"inason ganin Anty Ma-my, but banason ganin wannan yarinyar..." Ashraf yalumshe idonsa ya bude tareda girgiza kansa baice komai ba. Haka suka wuni a daki babu inda suka fita,saide suje sallah sudawo,Captain Aryan baya gajiya da zance inde tareda Ashraf ne,suyi fada su shirya kansu da kansu babu wanda yajisu. Da daddare suna kwance sunyi shirin bacci Captain Aryan yadauki wayarsa yakamo wani hadadden gida gari guda kamar ba'a qasar yake ba,yabawa Ashraf wayar yace"Ash kaga aikin gidan nan har sun gamashi,ansaka komai aciki,wannan komawar da zanyi a cikinsa zan sauka,matata ma nasa sun saka mata komai da komai kawai clothes ne babu,shima dan bansan size dinta bane danayi mata order ansaka mata kafin tashigo gidan, but....naso ace tareda ita zamu fara shiga" Ashraf ya kalli photunan gidan yace"Wow...,gaskiya yayi kyau,banbancin sa da nawa na nan garin kadanne,naka farin fenti nawa brown,to amma kayi auren mana saika tafi da matarka kushiga tare tunda haka kakeso" Captain Aryan ya girgiza kansa kawai sannan ya basar da zancen alamun bayaso,yace"nima kayan ciki har windows din duka brown ne,yayi kyau sosai,inaso wannan shekarar gaba daya yan gidannan sutafi aikin hajji,daga nan kawai saika taho muje muyi zamanmu a gidan muhuta kafin su dawo" Cikin farinciki Ashraf yace"babu damuwa Allah yakaimu,sannan bazaka samu lada kai kadai ba,kai kabiyawa su Daddy nikuma su Momy,sannan gaskiya ni bazan tare agidana yanzu ba,saina jira na auri Mawahib tukunna,sai mu koma tare rana daya,duk wasu yan'uwa zan basu sati daya sugama zuwa ganin amarya, daga nan kuma zan rufe gidan in fara amarci na hankali na kwance" Cikin yatsina fuska Captain Aryan yace"mekace? kayi aure kuma kana kallon amaryar har tsawon sati daya?kayi aure bakayi komai ba a wannan ranar saika ce wani kidahumi?" Ashraf yace"menene yakawo maganar kidahumi kuma Aryan?,kana nufin kai bazaka Iya jiran sati daya ba kenan? kaide matarka taga ta kanta wallahi,zan fadawa Daddy yayima aure" Cikin rashin damuwa Captain Aryan yace"gaskiya kam,because nide babu wasa,cikin kwana biyu ma zan'iya yimata ciki" Ashraf yanajin haka yakai masa dukan wasa,yariqe kunnansa yace"bakajin magana Aryan" Dahaka sukai addu'ah suka kwanta cikin farinciki. Washegari yahada kayansa tsaf zaikoma bakin aikinsa,jikin Ashraf duk yayi sanyi,kokadan bayason tafiyar Aryan din baisan meyasaba,saida sukayi sallama da Hajiya Kilishi,bayan ya ajiye mata wasu manyan kudade a gabanta, sannan sukaje yayiwa Mama Sadiya sallama,itama ya ajiye mata kudi masu yawa akan kujera, sannan suka d'unguma suka tafi part din Mamy. Suna shiga part din Mamy suka tarar da'ita tareda wata baquwa, babbar mace ce sosai tana zaune akan kujera da wayarta a hannunta tana dannawa, Cikin farinciki Mamy tace"Captain har tafiyar tatashi?" Captain Aryan yayi murmushi ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa,yace"Anty Ma-my barka da safiya" Ta amsa masa cikin girmamawa tareda shige wa dan qaramin kitchen din dake falon ta. Ashraf ya kalli babbar matar dake zaune afalo yace"ina kwana" Cikin walwala tadago kanta tace"lafiya kalau yagida" Kafin Ashraf yabata amsa shima Captain Aryan cikin sauri ya rissina yace mata "Barka da safiya" Ta kalleshi tace"masha Allah,yawwa sannunku" Adede lokacin Mamy tafuto daga kitchen hannunta daukeda leda,tabawa Captain Aryan tace"ga dambun kaza" Ya kalli ledar hannunta cikin shagwa6a yace"haba Anty Ma-my, gaskiya ni bazan tafi dashi a leda ba,saikace wani marar gata,Allah nide saide ki sauya min,haba Anty Ma-my kina d'an girmama ni mana,amma haka abu aleda?" ya qarasa maganar cikin shagwa6a kamar zai fashe da kuka. Mamy tace"naqi,bazan sauya maba, kaje kayi aure sai matarka ta dinga saka maka a flask" Captain Aryan yayi shiru yana kallon wannan leda,duk girmansa Anty Mamy bazata sake girmama shi tazuba masa a qayataccen food flask ba?bai Isa yayi magana ba komai sai tace yaje yayi aure(😔) Ashraf yayi murmushi yazuba musu ido yana kallon wannan drama tasu, adede lokacin Mawahib tafuto daga dakinta tana sanye cikin riga da siket 'yan kanti, amma tasaka mayafi a jikinta, ganinsu yaya Captain a falon yasa taja ta tsaya daga nan bakin qofar d'akinta. Ashraf yana ganin futowar ta yamaida kallonsa gareta,yazuba mata manyan idonsa yana kallonta cikeda so. Qawar Mamy dake zaune agefe tana ganin abinda yake faruwa tayi dariya tace"Maryam wannan kamar yaran nan naki dakika yayesu ko?" Cikin sauri Captain Aryan yajuya yana sake kallon matar, tunda yaji tana maganar lokacin da Anty Mamy ta yayesu yasan cewa tabbas babbar mace ce,kuma tasan yarintar su,yagama qarewa matar kallo kenan yajuyo zai maida kallonsa wajan Mamy anan idonsa yasauka akan Mawahib,sai akayi dace idonsa ya sauka cikin nata qwayar idon,lokaci daya bugun zuciyar su yasauya,cikin sauri kowa ya janye idonsa. Mamy tayi murmushi tace"Sister Hadiza sune wallahi, gasunan duk sun girma" Babbar matar da aka kira da Sister Hadiza tace"ikon Allah,kinga duk sun girma sun taroki kamar wasu qannanki, waye kwa me tsoron ruwan zafi acikinsu lokacin da aka musu kaciya?"(🙊🙈😂🙆🏻‍♀️) Mawahib ta dago kanta da sauri ta kalli Sister Hadiza. Cikin sauri Captain Aryan ya runtse idonsa, saboda yasan akansa ake maganar, shitake tambaya, yatuna Mawahib fa tana cikin falon nan,shikkenan matar nan tagama dashi,ta kunyata shi agaban wannan yarinyar, cikin sauri yafuto daga falon da ledar dambun kazansa a hannu yanaji kamar ya nutse awajan dan kunya(😂) Ashraf yayi dariya shima yabi bayansa (Sister Hadiza baki kyauta mana ba🤣 asauka lafiya captain 🙏🏻) Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗 (Hot luv) Writing By Amnah El Yaqoub 11&12 Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,za'a fara dora muku Audio Novel's👇🏻 https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels *Last free page*🙏🏻 Mawahib tayi murmushi tashige dakinta, cikin ranta tana fadin su Yaya Captain anji kunya. Yana fita qofar gida mutanan da su kasan da tafiyarsa duk suna tsaye,suna ganinsa kuwa suka fara yimasa addu'ar sauka lafiya,saida yayi musu ihsani kamar yanda yasaba duk tafiyar da zaiyi, sannan ya qarasa wajan iyayen nasa maza duka su ukun suna gefe a zaune,Alhaji Isah mijin Mamy ya kalle shi da fara'ah yace"Captain har zaka koma aikin bazaka zauna ko sati d'aya kayi manaba?" Murmushi yayi,duk da kawu Isah kawunsa ne sunada damar dazasuyi wasa da dariya a tsakanin su amma basa wasan, yanajin girman kawun nasa sosai akwai mutuntawa a tsakanin su,amma kuma idan shida Ashraf ne haka zaka gansu suna wasa da dariya kamar yaya da qani, cikin murmushin yace"eh kawu,saboda nataho da wadancen ne shiyasa zan koma akan lokaci" yafadi hakan yana juyawa yana kallon sojojin dasuka rakoshi su hudu, Alhaji Isah yace"eh hakane kuma,to Allah yakaiku lafiya,Allah yatsare hanya" Cikin ladabi ya amsa da "Amin" Sannan ya qarasa wajan Alhaji Khaleed da Kuma mahaifinsa Alqali, sukayi sallama, anan ne yake musu albishir din tafiyar su aikin hajji wannan shekarar gaba dayansu wanda zasu biya musu shida Ashraf, sunyi farinciki sosai,Alqali yasanya musu albarka duka su biyun,suna qarasowa jikin mota Captain Aryan ya rungume Ashraf wanda jikinsa yayi sanyi sosai akan tafiyar Aryan din, sannan yasake shi,Ashraf yariqe hannunsa yace"meyasa bazakubi jirgi bane?" Captain Aryan yayi murmushi yace"saboda muma kanmu tsaron ne,muda ya kamata mubawa yan qasa tsaro idan muka fara gudun hanya yaya kenan? dani kadai ne sainabi jirgi Ash,amma yanzu duk wanda yaganmu ahanya zaiso yabiyo bayanmu saboda yasan zai samu tsaro da kariya awajan mu,insha Allah babu damuwa" Ashraf yasaki ajiyar zuciya yace"to shikkenan,sai munyi waya" Captain Aryan yagyada kansa sannan yashiga mota sukaja suka tafi. Suna tafiya ahanya yana tuna irin kunyar da matar nan qawar Mamy tabashi agaban yarinyar nan Mawahib,koda wanne ido zai sake kallonta oho,danma ba sabgarta yake shiga ba bare tasake samun damar rainashi,sai yanzu ne yatuna dukansu matan gidan yabasu kudi amma banda Anty Mamy saboda ya futo cikin kunya ko sallamar kirki ba suyi ba,already yanada account number dinta, cikin sauri ya laluboshi yayi mata transfer, sannan yamaida wayarsa aljihunsa tareda lumshe idonsa,motar shiru babu surutu kasancewar sunsan cewa ogan nasu bayason surutu. ****** Har motocin su Captain Aryan sukai nisa aka dena hangosu Ashraf yana tsaye a wajan yakasa dena kallon hanyar, mamaki yakama Alqali, da alama akwai abinda yake damun Ashraf,qarara ga damuwa nan ta baiyana a fuskarsa,yana kallonsa saida ya dade atsaye a wajan sannan yajuya yashiga gida,shima kansa Alqali sai zaman qofar gidan ya gagareshi, Ashraf din baidade da shiga gidaba shima yad'oru abayansa ya shige, kai tsaye dakinsu Ashraf din yanufa,Ashraf yana ganin mahaifin nasa a dakinsu mamaki ya kamashi,saboda babu abinda yake kawo shi dakin saide in yanason ganinsu yakira su suje, zama yayi abakin gadon cikin fuskarsa ta kamala yadubi Ashraf yace"babu damuwa deko?" Babu 6oye-6oye Ashraf yace"Daddy banason tafiyar Aryan,kuma nafada masa banaso yatafi shine yarabu dani ya shirya yayi tafiyarsa,nikuma inaji kamar wani abune zai sameshi" Alqali yayi ajiyar zuciya yace"ka kwantar da hankalin ka,kayi masa addu'ah insha Allahu babu abinda zai faru sai alkhairi,kasaki jikinka kayi walwala kaji ko?" Sai a lokacin Ashraf yasaki wata irin ajiyar zuciya,Alqali yasake kallon fuskarsa yagade har zuwa lokacin kamar akwai sauran magana, cikin hikima irin tasu ta iyaye yayi murmushi yace"tosaime kuma?" Cikin kunya Ashraf yafara sosa kunnansa yace"Daddy dama....dama inaso inyima magana Daddy inaso ka nemamin auren Mawahib a wajan Kawu Isah,wallahi Ina sonta Daddy" Tsananin mamaki yakama Alqali,kowanne irin so Ashraf yake yiwa Mawahib ya tabbatar badan qarami bane,tunda bai tsaya Iya cewa a nema masa auren ba, saida ya dubi tsabar idonsa yasake cewa yana sonta, Alqali yayi murmushi tace"to wannan aiba abun damuwa bane,abun farinciki ne ai wannan,saide kasan mahaifiyar ka batayi da mahaifiyar Mawahib din ko? to saboda kwanciyar hankalin ita yarinyar, yakamata kaje kasamu mahaifiyar ku da maganar idan har ta nuna tana son Mawahib din kaga babu damuwa koda ka aure ta zasu cigaba da zama lafiya a tsakanin su" Ashraf yace"eh Daddy zanyi mata maganar ,ita naso nafara fadawa ma, to sai nafara yiwa Aryan maganar,dafarko yanuna bayaso, saidaga baya naga yabar maganar, amma nasan Momy zataso abinda nakeso" Alqali tace"to Alhamdulillah,naji dadin wannan maganar taka,koba komai aurenka da Mawahib din zai Iya kawo shiryawar mahaifiyar ka da mahaifiyar ita Mawahib din,zan samu Alhaji Khaleed da shi Alhaji Isah akan maganar,Allah yayi maka albarka" Cikin jin dadi Ashraf yace"Amin ya Allah Daddy" Cikin sigar tsokana Alqali yace"shikkenan hankali ya kwanta?" Cikin kunya Ashraf yace"eh Daddy" Alqali yasaka hannu yashafa sumar kansa, sannan yafice daga dakin tareda rufowa. ****** Tafiyar su tayi nisa sosai har zuwa lokacin Captain Aryan idonsa a lumshe suke,kamar an jefo musu wani abu haka wani babban mutum sanye da farar shadda gamida babbar riga sai maiqo shaddar take yafado gaban motarsu Captain,lokaci daya direban su Captain Aryan yataka wani mahaukacin birki wanda yasa Captain din bude idonsa cikin sauri, motar tana tsayawa mutumin yanufo murfin motar tasu yana kokarin budewa yanayi yana waigen bayan sa, lokaci daya suka fara jin qaran harbi, cikin sauri Captain da sauran sojoji suka bude motar suka futo, Captain Aryan yadubi mutumin yana tambayarsa "meyake faruwa?" Kwata kwata tashin hankali yahana Captain Aryan gane tsananin kamar da wannan mutumin yake da Mawahib,daga idonsa har cikakkiyar girarsa gaba daya basuda banbanci dana Mawahib, fari ne tas kamar ka latsa jikinsa jini yafuto, kafin mutumin yabashi amsa kamar daga sama sukaji taaaassss an iyo musu harbi, cikin tsananin tashin hankali mutumin nan yadubi Captain Aryan yace"ka taimaka min yaro, zasu kasheni, zasu kasheni ka taimaka min mubar wajannan basuda Imani zasu kasheni...." Captain Aryan yanajin haka ya juya ya kalli sojojin dayake tare dasu, kallo daya yayi musu, suka gane abinda yake nufi nan take suka fitarda bindiga suka fara sakin wuta, lokaci daya wajen ya karade da qaran bindiga, har zuwa wannan lokacin Captain Aryan baiyi harbi ba, yana tsaye yariqe wannan babban mutumin ya 6oyeshi a bayansa Daya daga cikin wanda suka kawo harin ne yazo daga bayansu Captain zai harbi mutumin,wannan mutumin yana ganin haka nan take ya lumshe idonsa yafara karanta kalmar shahada, saboda yagama tabbatar da cewa harbin da'aka iyo daga bayan nan yariga ya sameshi, yasan cewa yau tasa taqare mutuwar sa tazo,Captain Aryan dayake riqe dashi yajuya da sauri saboda qaran harbi dayaji, yana juyawa adede lokacin har bullet din yazo wajan su,cikin sauri yature wannan mutumin,yana tureshi adede lokacin bullet din yazo kai tsaye harbi yasauka agefen qirjin Captain Aryan, cikin sauri yasaka hannu yadafe wajan,yasaka hannunsa na dama ya dauko 'yar qaramar bindigar datake aljihun wandonsa babu 6ata lokaci shima yarama harbin,nan take kuwa wancen din yafadi qasa babu alamun numfashi atare dashi. Sauran maharan suna ganin ankashe ogansu,suma suka gudu kowa yayi ta kansa, wannan babban mutumin kuwa yana ganin yanda Captain yatare masa harbi lokaci daya jikinsa yadauki rawa,yadora hannunsa aka kamar ba babba ba yafara kuka wiwi, cikin kuka yake fadin"lahaula wala quwata illa billahi aliyal azim,yaro meyasa kayi haka? meyasa baka bari sun kasheni ba? meyasa zaka sadaukar da rayuwarka saboda ni?" Duk wannan maganganun dayake Captain Aryan baya jinsa, hannunsa dayasa yatare inda yaji shigar bullet din jikinsa gaba daya hannun ya6aci da jini,yawan jinin daya zubane yasa nan take jini yafara daukar sa, idanunsa suka fara lumshewa, atake jiri ya debeshi yazube a wajan,sauran sojojinsa suna ganin halin da Captain yashiga cikin sauri suka saka shi cikin mota,shima wannan mutumin cikin sauri yafada cikin motar sukaja da mugun gudu sukabar wajan,kai tsaye nasarawa state suka qarasa dashi saboda tafi musu kusa akan Abujan,wani private hospital suka qarasa dashi,motocinsu suna tsayawa wannan babban mutumin yabude motar yafuto sai hawaye yake kamar ba babban mutum ba, farar shaddarsa wacce take maiqo gaba daya ta6aci da jini, ganin yanda babban mutum kamar sa yake kuka wiwi, yasa hankalin ma'aikatan asbitin yadawo kansa, cikin sauri aka kawo musu dauki, aka turo dan qaramin gadon daukan majinyata zuwa gaban motarsu, cikin sauri aka dora Captain Aryan akai, wanda yake kwance babu alamun numfashi atare dashi nurses suna tura gadon zuwa dakin tiyata dasauri amma wannan babban mutumin cikin kuka yake bin gadon yana fadin"likita ka taimakeni,kada yaron nan yamutu ta sanadi na,katemakeni likita" Yana wannan surutun baisan ma sun qaraso zuwa dakin tiyatar ba,suna zuwa suka dakatar dashi sukuma suka shige ciki da Captain tareda rufo qofar ****** Da yamma Nabiha tana dakin Mawahib suna firar su,Nabiha tace"Mawahib Yaya Ashraf kuwa yafada miki yana sonki?" Mawahib tace" Dama tunanin kine,ni har yanzu banga alamun hakaba,muna de mutunci kamar baya" Jikin Nabiha yayi sanyi,ahankali tace"Mawahib Yaya Ashraf yana sonki...." Cikin sauri Mawahib tace"koda yafadamin ko, bazan ta6a aurensa ba, saboda dan'uwansa yaya Captain baya sona,sannan mahaifiyar su Momy kilishi itama bata sona, to wanne irin zaman aure zanyi dashi?, kidena min wannan maganar Nabiha,Allah yamin tsari da auren 'ya'yanta" Nabiha tayi murmushi tace"to shikkenan Mawahib yawuce" Abba da Mamy suna zaune afalo Abba ya Kalleta yace"ina yarinyar nan take ne?" Mamy tace"Mawahib? tana daki itada Nabiha tun dazu" Kafin yasake magana saiga Alqali da kansa shida Alhaji khaleed acikin falon nasu, mamaki yakama Abba da Mamy, cikin sauri Alhaji Isah yatashi tsaye yana cewa "Yaya kaida kanka? aida kun kirani nazo" Alqali yayi murmushi, suka nemi waje suka zauna,cikin ladabi Mamy ta tsugunna ta gaishe su,cikin ranta tana mamakin menene yakawo su Yaya Khaleed da Yaya Alqali har part dinsu yau? Ahankali tajuya tashiga kitchen domin tahado musu dan abun motsa baki. ****** Ashraf yayi wankansa ya shirya tsaf cikin qananun kaya nashan is'ka kamar yanda yasa ba, wayarsa yadauka yakira Captain Aryan saide wannan karon ma wayar taqi shiga,tun azahar yake kiransa yanason yaji kosun sauka lafiya amma wayar taqi shiga yarasa meyasa? a fili yace"insha Allah lafiya...." Sannan yafuto iai tsaye yatafi part dinsu, Hajiya kilishi tana zaune akan kujera tana waya cikin iko kamar yanda tasaba, Ashraf ya zauna agefenta yana sake try number Aryan... Cikin wayar yaji tana fadin"banason atamfofi tsofaffi fa,masu tsada nakeso ki bayar akawo min guda goma,amma guda bibbiyu kala daya,kayan lefen 'yanbiyu na nake hadawa banason asaka kaya masu araha acikin lefensu". Ashraf yayi murmushi ya jinjina kansa alamun lalle Momy da gaske take (😂) Can saiyaji tace"to shikkenan ki gaida Asalamiyya,saita kawomin din" Yanajin takashe wayar ya Kalleta cikin zaquwa yace "Momy" Cikin kulawa tace"Na'am Ashraf, yanaganka cikin farinciki ne ko an samomin sirika ne?" Cikin murna yace" kamar kinsani Momy,ai harna fadawa Daddy ma a nemamin auren ta" Hajiya kilishi ta gyara zamanta ta kalleshi dakyau, sannan tadaga hannunta sama tace"Alhamdulillah, Allah abun godia,saura Aryan kuma" Tajuya tasake kallonsa tace"yar gidan waye afadin qasar nan?" Cikin rashin damuwa yace"Momy Mawahib cefa...." Hajiya kilishi saitaji kamar bataji bataji abinda yafada daidai ba,cikin son tabbatar wa tasake kallonsa sosai tace"wakace?" Ashraf yayi murmushi yace"Mawahib din Anty Mamy cefa" Cikin sauri Hajiya kilishi tamari fuskarta,incase in mafarki take tota farka (😂) saida tasake marin fuskarta akaro na biyu taga de tabbas ba mafarki takeba babban danta Ashraf shine a zaune agabanta yana fada mata yanason jinin Maryam, cikin son tabbatar wa ta kalleshi tace"Ashraf kaine kake fadamin kanason ka auri 'yar gidan Maryam?" Cikin sauri ya sunkuyar da kansa qasa,kafin yadago yabata amsa yaqa ta miqe tsaye, cikin sauri yadago kansa yace"Momy Ina zakije?" Bata saurari abinda zaice mataba tanufi qofar fita daga part din nasu,cikin sauri Ashraf ya riqo hannunta,yace"Momy ki tsaya muyi magana Ina zakije?" Hajiya kilishi gaba daya idonta ya rufe, burinta kawai taganta a gaban Mamy, ko sauraren Ashraf batayi ba tafizge hannunta tanufi part din Mamy ****** Tunda suka shiga dakin tiyata dashi har yanzu basu futo ba,wannan babban mutumin banda zagaya wajan babu abinda yake, hular kansa tana hannunsa yana firfita da'ita, gumi duk ya jiqa masa jiki, idanunsa yayi jajir har zuwa yanzu hawaye yake,sai zagaya wajan yake yana fadin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..." Gashi mutane sun kasa zuwa kusa dashi su bashi haquri saboda sojoji guda hudu dasuke tsaye a wajan kowanne a cikinsu hannunsa yana dauke da bindiga,kana ganin yanda suke zare ido suna zagaya wajan,zakasan cewa ba qaramin mutum suka kawo asbitin ba. Cikin sauri wannan mutumin yadauki wayarsa yayi kira,daga dayan 6angaren aka daga akace"ALHAJI MA'ARUF.... Ina kashiga ne naje gidan gonarka bansamekaba?" Cikin kuka wannan babban mutumin wanda aka kira da Alhaji Ma'aruf cikin tashin hankali ya goge hawayen idonsa yace"Alhaji Bala akwai matsala,muna asbiti, yaro zai mutu a dalilina,kazo kasameni yanzu" Alhaji bala daga nasa 6angaren yace"Yanaji kana kuka? gani nan zuwa, kayi haquri gani nan zuwa yanzu-yanzu, kuna wanne asbiti?". ****** Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci kayanmu daga Ethiopian ne prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil anti dandruff shampoo serum bdy cream hand cream magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkomin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Abba yadubi yayansa Alqali yace"to yanzu Yaya, Yaya zamuyi da maganar Nabil?" Alqali yace"Nabil ai tambaya yayi yana so yafara zuwa wajanta zance,ba izni ya nema a bashi dama yakawo kayan neman aure ba,inda ace yakawo wani Abu gida,kokuma iyayensa sunzo sun sameni munyi magana dasu baki da baki, to bazan goyawa Ashraf baya ba,sannan inda ya shirya da tuni iyaye sun shiga cikin maganar" Alhaji khaleed yace"to Yaya koda ace sunzo munyi magana ma,ai munada damar dazamu hana auren mubawa danmu,saboda gida bai qoshi ba,ai baza'a bawa daji ba, Yaya muna ganin yarinya me hankali da tarbiya, zamu bari wani daga nesa yazo ya dauketa 'ya'yansa dashi kansa su mori wannan tarbiyar tata, bayan mukuma gamu da samari agida har guda biyu ace mun kasa qwato wannan tarbiyar tadawo cikin gidanmu? nima Ina ganin tunda maganar Nabil din batayi nisa ba, abawa Ashraf din kawai..." Kafin Alhaji khaleed yayi magana Hajiya kilishi ta bankado kofar falon tashigo idonta yarufe da masifa ko ganinsu Alqali dasuke zaune a falon batayi ba, Ashraf ma yabiyo bayanta yana kokarin riqe hannunta musanman shida yaga iyayensa maza a zaune a falon,Hajiya kilishi ta fizge hannunta ta qarasa shigowa cikin falon. Cikin masifa tadaga murya tafara qwalawa Mamy kira"Maryam! Maryam!! kina Ina?" Mawahib da Nabiha dasuke zaune adaki suna kalle kallen video a Instagram din Nabiha sunajin wannan kiran da akewa Mamy sukasan cewa yau gidan ba lafiyaba, cikin sauri sukai wulli da waya suka futo,saide suna ganin su Alqali a wajan sai sukai turus suka tsaya abakin kofar dakin Mawahib din. adede lokacin Mamy takawowa su Alqali wani hadadden cake jikinta duk yayi sanyi tun lokacin data farajin mazan gidan suna tattauna maganar auren Mawahib da Ashraf, wanda a zahiri bazata yarda da wannan auren ba. Cikin Masifa Hajiya kilishi ta tunkari Mamy tace"Maryam kinji dadi,yau burinki yacika,kinshiga kin fita kin rabani da d'ana,naji dadi kuma na godewa Allah dayasa baki hada da CAPTAIN ba,shima dakin mallakeshi da yanzu 'ya'yana biyu suna fada akan AGOLAR 'YARKI" Cikin sauri Mawahib ta kalli Hajiya kilishi tana maimaita kalmar 'Agola' acikin ranta.... Ashraf ya sunkuyar da kansa qasa yana tunanin kode Hajiya kilishi bata cikin hayyacin tane shiyasa take kiran Mawahib da Agola? a'iya saninsa Mawahib de Uncle Isah ne ya haifeta. Mamy tana Jin furucin Hajiya kilishi lokaci daya hawaye ya wanke mata fuska,kokadan takasa daga idonta ta kalli mutanan falon,wani irin kukan baqin ciki ne ya kamata take taci gaba da kuka harda shashsheka. Nabiha tadinga rarraba ido tana ganin mutanan falon gaba daya jikinta rawa yake tashiga shock sosai saboda basu ta6a ganin tashin hankali irin wannan ba Alqali dayake zaune ransa idan yayi dubu toya 6aci,baqin cikinsa a gaban qannansa maza matarsa tazo tashigo babu da'a duk da tana ganinsa a zaune a wajan kokadan bashida kwarjinin dazai hana Kilishi ciwa Mamy mutunci kenan? koda tayi niyyar zagin Mamy ai idan ta ganshi a zaune ya kamata ace tayi haquri tabari yabar wajan tukunna, cikin baqin ciki yatashi tsaye baiyi wata-wataba yadauke Hajiya kilishi da mari (🙆🏻‍♀️😳) Cikin sauri Ashraf yadago kansa ya Kalli iyayen nasa,baqin ciki ya kamashi yau Daddy ne yake marin momy? shi kuwa wanne irin yaro neshi da yayi silar da mahaifinsa zai daga hannu yamari mahaifiyar sa? Cikin qunci Hajiya kilishi ta kalli qwayar idon Alqali tace"qarya nayi? Ina ubanta? har yau kun ganshi da idonku ne? to billahillazi dana Ashraf bazai ta6a auren SHEGIYA ba" Cikin sauri Mamy da fuskarta tagama jiqewa da hawaye tace" 'yata ba shegiya bace Yaya...,kiyi haquri nima ko bayan ranki bazan bari 'yata ta auri danki ba" Mawahib tanajin furucin Mamy ta tabbatar da cewa kenan maganar Hajiya kilishi gaskiya ne, cikin tashin hankali tace"Mamy?" Bata Iya sake magana ba wani kuka yataso mata, cikin sauri ta shige cikin dakinta tashin hankali yasa har tana bige Nabiha bata sani ba, cikin sauri itama Mamy tabi bayan Mawahib din cikin kuka. Alhaji khaleed mahaifin Nabiha yatashi tsaye saboda bazai Iya jure ganin fadan yayan nasu shida matarsa ba, cikin sauri yafice daga falon, Nabiha ma da idonta yayi jajir cikin gudu tafice tabar part din. Alqali ya Kalli Hajiya kilishi yace"kinji dadi? kin tonawa yarinya asiri kinji dadi ko? yanda kike qoqarin ganin kin tozarta wannan yarinyar kisani Allah zai saka mata ta'inda baki ta6a zato ba,saboda bata tsare miki komai ba" Alhaji Isah yatashi tsaye cikin sanyin jiki yace"yaya kayi haquri,yaya kilishi kema kiyi haquri insha Allah wannan maganar anbarta" Cikin sauri Ashraf ma da jikinsa yayi sanyi ya kalli mahaifin nasa yace"Daddy kuyi haquri,tunda Momy bataso zan haqura" Cikin 6acin rai Alqali yace"Aure babu fashi sai anyi shi inde Ina raye,saide in Mawahib ce dakanta tace bataso" Daga nan yasakai yafice daga falon cikin fishi babbar rigar nan tasa sai tashi sama take. Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"haka Nima muddin Ina raye, wallahi dana bazai ta6a auren wannan yarinyar ba" itama tafice daga falon ko rufo musu qofar batayi ba, Alhaji Isah yaja Ashraf jikinsa ya rarrashe shi, sannan ya bubbuga bayansa alamar lallashi, yajuya yabi bayan Mamy wadda tashiga dakin Mawahib. Tarar dasu yayi dukansu suna kuka daga Mawahib din har Mamy. Cikin kuka Mawahib tace"mamy da gaske ni shegiya ce banida mahaifi? Abba ba shine ya haifeni ba?" Cikin sauri Mamy tarufe mata baki tace"karki sake kiran kanki da wannan sunan,ke yar halak ce kamar 'ya'yanta" Alhaji Isah yayi gyaran murya yace"Maryam kudena wannan koke koken dan Allah,Mawahib de koda ace batada mahaifi nime tsaya matane a kowanne hali take ciki,barema kunadani, bazan ta6a bari kuyi kukaba, kuyi haquri kudena kuka,ki rarrasheta tayi shiru," Yana fadar haka yafuto daga dakin cikin sanyin jiki. Mawahib ta Kalli Mamy cikin kuka tace"Mamy waye mahaifi na? kibarni natafi wajansa ko Momy kilishi zata daina yimin gori Mamy" Mamy ta goge hawayen idonta tace"karki sakemin maganar mahaifin ki Mawahib,babu abinda zai kaiki wajansa,zan maye miki gurbin sa ako'ina" ****** Cikin tashin hankali Ashraf yakoma dakinsa, yana zuwa yakama kansa dayake masa barazanar rabewa gida biyu,cikin tashin hankali yafurta"innalillahi wa Inna ilaihirraji'un...." Cikin sauri yadauki wayarsa yafara kiran Captain Aryan, saide har yanzu wayar kwata kwata bata shiga, cikin baqin ciki yayi wulli da wayar yadafe kansa da hannunsa (🤦🏻‍♂️) ****** Basu futo daga dakin tiyatar ba sai qarfe biyu nadare,kai tsaye dakin hutu aka turashi,aka hana kowa shiga inda yake,Alhaji Ma'aruf yakasa zaune yakasa tsaye,sai leqen Captain yake ta glass din kofar dakin yana kwance andaura masa qarin jini babu riga a jikinsa, ansaka masa audiga da bandeji a'inda harbin ya sameshi, fuskarsa tayi wani irin fayau lokaci guda. Har aka kira sallar asuba shida sojojin nan idonsu biyu,abokinsa Alhaji Bala shine de yake dan gyangyadi a zaune. Saida gari yawaye sannan likita yazo inda suke,hannunsa daukeda file,ganin Alhaji Ma'aruf yana kuka tunda sukazo,kuma yahana kansa sukuni,sannan gashi fari tas kamar yanda Captain Aryan yake,shiyasa yayi tunanin ko shine mahaifinsa, kai tsaye yace "Alhaji kaine mahaifin marar lafiyar?" Cikin sauri Alhaji Ma'aruf yace"eh nine,likita babu matsala deko?bai mutu ba yana nan da ransa ko?" Likitan yabude file din hannunsa ya kallesu gaba daya yace"menene sunan marar lafiyar?" Daya daga cikin Sojojin nan take yace"Captain Aryan I. Alqali" Likita yayi rubuce rubuce a file din sannan ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"kazo ka sameni a office" Cikin sauri yabi bayansa zuwa office din,suma sojojin suka doru abayansu,Likitan da baisan menene a tsakanin suba ya juyo ya kalli Sojojin yace"babu damuwa,zamuyi magana ne dashi kawai" Jin hakan yasa suka dakata daga bakin qofar. Suna zama a kujera likita ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"Alhaji yaronka yasamu harbi a haqarqarinsa,ma'ana qasan qirjinsa daga gefe, amma bullet din bai shiga canciki sosai ba, Alhamdulillah yanzu ma zamu Iya sallamar sa idan ya farfado daga dogon suman dayake, saide akwai matsala guda daya,Alhaji kayi haquri yaronka yasamu matsala bazai Iya haihuwa ba,saboda bullet din baishiga cikin qashin haqarqarin ba amma yagogi qashin wajan , shikuma wannan qashin da bullet din ya goga, maniyin namiji yana fara samuwa ne daga cikin jinin dayake yawo daga tsakanin qashin haqarqari zuwa qashin baya,zaiji sha'awa normal kamar yanda yasaba, but idan yayi aure yanzu, bazai samu maniyi mai lafiya kuma me kaurin dazai bawa matarsa ciki ba,saboda bullet din yariga ya gogi qashin wajan, amma zamu dorashi akan magani,sannan kuma ya kiyaye cin abinci barkatai,saide megina jiki,yakiyaye cin maiqo,saboda cin abu mai maiqo zaisa yasake samun qarancin maniyin, (low sperm count),amma idan yafara shan maganin da zamu dorashi akai,lokaci zuwa lokaci yana gwada mu'amular aure da matarsa insha Allah sperm dinsa zai dawo Normal,harma yasamu ciki...." Cikin sauri Alhaji Ma'aruf yafashe da kuka yace"likita karka qarasa, karka qarasa likita shikkenan nacuci yaron nan...." haka yataso yafuto daga office din kamar mahaukaci kamar wanda baya hayyacinsa ya nufi kofa zai fice daga Asbitin,Alhaji bala yabi bayansa cikin sauri yana tambayar "Alhaji Ma'aruf Ina zakaje? Meyasamu yaron?" Alhaji Ma'aruf bai kula shi ba saida yafuto harabar asbitin kuka yaci qarfinsa yazube a farfajiyar asbitin yana kuka,nan da nan mutane suka taru a kansa ana bashi haquri, dayawa daga cikin mutanan sunyi tunanin mutuwa aka masa,Alhaji bala dayayi tunanin Captain Aryan yarasu ya tsugunna yace"Haba Alhaji Ma'aruf shi mamaci ai addu'ah yake buqata,ba kuka zaka masaba, addu'ar mu yake buqata yanzu haka"(😳) Alhaji Ma'aruf yace"kabarni inyi kuka Alhaji Bala,banta6a jin na tsani kaina nayi tir da halina ba tun bayan barin Maryam cikin rayuwa taba sai yau" Alhaji bala ya runtse idonsa sannan yabude yadafa kafadar Alhaji Ma'aruf sannan yayi qasa da murya yace"akwai mutane anan,kayi haquri ka tashi dan Allah" Alhaji Ma'aruf ganin mutane suna masa kallon wanda aka yiwa mutuwa hakan yasa cikin sauri yatashi tsaye kamar wanda aka tsikare shi yafice daga harabar asbitin yana doka sauri kamar wani mahaukaci,tuni yagama yanke hukunci acikin ransa. shima Alhaji Bala cikin sauri yad'oru abayansa suka fice daga asbitin. ****** ahankali yafara bude idonsa harya gama budeshi gaba daya,yaqarewa dakin dayake kwance kallo,ya kalli kayan jikinsa,sai a lokacin yatuna da abunda yafaru,ahankali yasake lumshe idonsa sannan yabude,babu wani alamun Jin ciwo yatashi zaune kamar ba aiki ne a jikinsa ba,sojojin dasuke tsaye daga waje suna hangoshi ta glass din dakin cikin sauri daya daga cikinsu yakira likita, likitan yana zuwa tare suka shiga dashi,likita yana ganin Captain a zaune nan da nan da yashiga taitayinsa saboda yasan cewa asbitin nasu ya kar6i baqin fuska masu ban tsoro, ahankali yafara dudduba shi, sannan yahada allura yayi masa a hannunsa, ya kalleshi yace"yaya kakejin wajan ciwon?" Cikin miskilanci yace" banajin komai doctor,zaka Iya sallama ta yanzu?" Cikin sauri yace"za'a baku sallamar insha Allah,amma akwai magungunan da zakasha yanzu,tukunna" Baice dashi komai ba sai d'aga kansa da yayi kawai alamun yaji. Likitan yabawa daya daga cikin Sojojin kati sannan yace"muna buqatar wannan magungunan" Daga nan yafuto daga dakin. Captain Aryan ya dudduba gefensa baiga wayarsa ba yadago ya kalli sojojin dasuke tsaye yace"whare is my phone?" Cikin sauri daya daga cikinsu yasara masa sannan yabashi wayar cikin ladabi yace"mun rufe wayar ne oga,saboda kada hankalin yangida yatashi" Cikin 6acin rai yace"kamarya kada hankalinsu yatashi?,idan mutuwa nayi ma haka zaku kashe waya bazaku Kira gida kufada musu halinda nake ciki ba?" Kasa bashi amsa sukai saboda babu girma yana fada suna fada, cikin sauri ya kunna wayarsa,yafara neman wayar Ashraf ****** Ashraf yana zaune cikin damuwa, Alqali ya kalleshi yace"Ina tunanin nima akwai abinda yake faruwa,tun jiya Ina kira gaba daya nakasa samunsa" Alhaji khaleed yace"yaya Ina ganin fa gara ka barshi yaje wajan aikin nasu yagano koba lafiya ba" Adede lokacin kiran wayar Captain yashigo cikin wayar Ashraf, cikin sauri Ashraf dayake zaune yatashi tsaye yana fadin"gashinan yana kira Daddy" Yadauki wayar tareda sakata a amsa kuwwa,cikin muryar sa maicikeda aji murya can qasa yace"Ash..." Cikin sauri Ashraf yace"Aryan Ina kakai wayarka tun jiya da yamma Ina neman ka?" Lumshe idonsa yayi,a hankali yace"ka kwantar da hankalin ka,munsamu tsautsayi ne a hanya harma nasamu harbi...." Alhaji khaleed da Alhaji Isah tareda Alqali sunajin haka suka saki wani irin Salati Cikin sauri Ashraf yace"harbi? innalillahi garin Yaya? saida nacema karka tafi,yanzu kana Ina? Yaya Harbin naka da sauqi?" Gaba daya ya rikice,kwata kwata baya cikin nutsuwarsa sai tambaya yake jerowa Aryan din Captain Aryan yayi murmushin qarfin hali yace"Ash..." Kafin yaci gaba da magana Alqali ya kar6i wayar yace"kuna wanne asbiti....?" ****** Alhaji Ma'aruf da abokinsa Alhaji Bala suka turo kofar dakin suka shigo gaba dayansu su biyun duk jikinsu yayi sanyi kalau, adede lokacin Captain Aryan yagama waya da yan gida ya ajiye wayar agefensa,Captain ya zuba musu ido yana kallon su musanman Alhaji Ma'aruf wanda har zuwa wannan lokacin rigar jikinsa tana nan da sauran jini ajikinta,sai yanzu Captain yaqare masa kallo yaganshi fari tas idan ba hausa yayi bama zaka dauka ba bahaushe bane,Alhaji Ma'aruf ya kalleshi, tun kallon farko daya masa yasan cewa wannan acikin sojojin ma akwai tsare gida, zama yayi agefen gadon yace"yajikin naka?" Ataqaice yace"Alhamdulillah" Daga nan sukai shiru gaba dayansu,Alhaji Ma'aruf yarasa ta'ina zai fara,gaba daya yaron yayi masa kwarjini, daqyar yasamu qwarin gwiwar kallon sojojin yace musu "Dan Allah kuyi haquri kud'an bamu waje inaso zanyi magana dashi" Sunajin abinda Alhaji Ma'aruf yafada amma ko kadan basu motsa daga inda suke ba,saida Captain Aryan ya kallesu sannan suka fice daga dakin. Alhaji Ma'aruf ya kalli abokinsa Alhaji Bala yace"Alhaji bala zauna mana" Alhaji Bala dayake tsorace da ganin sojojin yaqaraso ya zauna akan kujerar dakin. Alhaji Ma'aruf ya kalli Captain Aryan yace"Captain Aryan ko?" Fuskar Captain Aryan babu wasa Ataqaice yace "yes" Alhaji Ma'aruf yayi ajiyar zuciya yasake kallon Captain Aryan cikin tausayawa yace"Aryan kayi haquri nayi maka babban laifi,bansanka ba, kaima baka sanni ba, amma ka za6i ka sadaukar da rayuwarka saboda ni,da nasan cewa abinda zai faru dakai kenan bayan tare harbin nan dakayi,da wallahi gara ni in mutu, akan wanna masifar tasameka" Captain Aryan yayi shiru yanajin Alhaji Ma'aruf yana masa bayani,yarasa menene dalilin yin wannan dogon bayanin,aikinsa shine ya kula da yan qasarsa,bai dauki wannan abun da yayi abakin komai ba. Alhaji Ma'aruf ya goge zufar daya fara sannan yaci gaba da fadin"likita yace sakamakon wannan harbin daya sameka, ba lalle sperm dinka ya iya samarda haihuwa ba,amma zai doraka akan magani idan kafara shan maganin insha Allah watarana za'a dace" Cikin sauri Captain Aryan ya Kalli Alhaji Ma'aruf,cikin ransa yafara furta Kalmar nan ta"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...." Ya lumshe idonsa yaci gaba da maimaita kalmar acikin ransa,Alhaji Ma'aruf yasake kallonsa sannan yaci gaba da fadin"Ina roqon alfarmarka kadubi girman Allah da darajar sa, kayafemin,nasan cewa nine sanadi,ta dalilina hakan tafaru dakai,sakamakon hakane yasa yanzu-yanzu naje masallaci nida Aminina Alhaji Bala,NA 'DAURA MAKA AURE DA 'YATA RUQAYYA" (😳🙆🏻‍♀️🙊😱) Captain Aryan da idonsa yake lumshe yana maimaita Kalmar innalillah aransa,cikin sauri yabude idonsa ya zabura daga inda yake zaune,gabansa banda dukan uku uku babu abunda yake,wacce irin masifa ce ta sameshi haka? daga taimako? Alhaji Ma'aruf ya kalleshi,cikin sanyin jiki yaci gaba da fadin"nasan yanda kakeji aranka,kuma nasan nime laifi ne awajanka,nasan cewa duk matar daka aura taji labarin cewa ga lalurar data sameka,zaiyi wahala ta zauna dakai,idanma ta zauna dakai to watarana zata gorantama akan hakan wannan dalilin ne yasa nabaka 'yata tacikina, nasan cewa 'yata bazata ta6a goran tamaba har abada,saboda nasan cewa mahaifiyar ta batayi mata irin wannan tarbiyar ba,idan babu damuwa inaso ka had'ani da iyayenka zanyi musu bayanin komai" Captain Aryan ya runtse idonsa cikeda damuwa,sannan yabude su,idanun sunyi jajir,gabansa banda faduwa babu abinda yake,kansa ya dauki ciwo kamar zai rabe gida biyu, cikin tashin hankali ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"please ko zaka bani space?" Ganin yanda yake cikin damuwa komai zai Iya faruwa hakan yasa babu musu Alhaji Ma'aruf yatashi,yasaka hannu cikin aljihunsa yad'auko wani d'an qaramin kati ya ajiye agefen Captain Aryan sannan yace"wannan shine katina,duk lokacin da hankalinka ya kwanta,kaji kana buqatar matarka,kakirani,zankawo ma matarka..." Masha Allah...Mawahib de Allah yayi ta Auri miji nagari 😂 Yaya batun saka ranar Ashraf da Mawahib? 🤔 Shin Nabil zai haqura? 🤔 menene zai faru idan Captain Aryan yasan cewa wannan qwailar itace matarsa?🤔 Mamy tace kobayan ranta bazata bari Mawahib ta auri 'ya'yan Hajiya kilishi ba,mezai faru idan labari yazo wajanta? 🤔 Alqali yace inde yana raye Ashraf saiya auri Mawahib,shin kuna ganin Captain Aryan zai saketa ne?🤔 Da alama yanzu ne Hajiya kilishi zataga ikon Allah 😂 Alhaji Ma'aruf rashin sani yasa ya qulla qullalliya a gidan Alqali 💃💃 Yanzu labarin yafara,karki bari ayi bake ki, kibiya kudin ki, ki antayo paid group din Mawahib atafi dake💃💃💃 Alhamdulillah....anan nakawo qarshan free page's dina, duk meson cigaban littafin MAWAHIB, yabiya naira 500 kacal👌🏻 Yanzu kwamacalar tafara,akwai rikici agaba kala kala duk a gidan Alqali, koda kudinka saida rabonka 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Insha Allah zaku dinga Samun posting biyu arana,wani lokacin kuma posting daya, kamar de yanda mukai daku a SHAHAAB, sai kunzo 🙏🏻 Zaki turo 500 ta wannan account din 👇🏻 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻[7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: *Page 78* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Bayan sunfuto daga dakin kai tsaye wajan payment sukaje Alhaji Ma'aruf yabiya kudin komai harda na magunguna ta hanyar atm dinsa, sannan suka futo daga asbitin,Alhaji Bala ya dubi abokinsa yace"Alhaji Ma'aruf kana ganin abinda ka zartar kuwa babu matsala? idan mahaifiyar yarinyar tayi mata aure fa? sannan idan yarinyar tana soyaiya dawani kuma kai karaba wannan soyaiyar ai kamar da cutarwa aciki" Alhaji Ma'aruf yace"ni ina ganin wannan ba matsala bane,koda RUQAYYA tana soyayya dawani dole zatayi haquri tabarshi ta rungumi wannan sojan,saboda shi d'a na halak dole zaiso mutumin daya taimaki mahaifin sa,zan kira MARYAM Infada mata abinda na yanke" Alhaji Bala yace"to shikkenan Alhaji Ma'aruf,Allah ya shige mana gaba" ****** Kasancewar jirgi suka biyo hakan yasa cikin sauri suka qaraso asbitin,gaba daya mazan gidan ne suka taho cikinsu harda Hajiya kilishi datake kuka wiwi,Mamy ce kawai bata taho ba itada Mama Sadiya,amma dukansu sun taho. Suna shiga asbitin d'aid'aikun mutane suketa kallonsu,ganin yanda Hajiya kilishi take kuka har lokacin babu tantama zakayi tunanin mutuwa aka musu. Sojojin dasuke tareda Captain suna ganin zuwansu Alqali suka musu iso zuwa dakin da Captain din yake, suna shiga Hajiya kilishi ta rungumesu shida Ashraf din gaba dayansu tana kuka, gaba daya saita bawa mazan gidan tausayi. Alqali yayi gyaran murya yace"Kilishi kukan ya'isa haka,tunda yana raye to Alhamdulillah,Allah zakiyi wa godia" Yajuya ya kalli Sojojin yace"muje wajan likitan" Cikin sauri suka juya suka rakasu har office din likitan,da Alqali da Alhaji khaleed da Alhaji Isah,su ukun dukansu suka shiga office din likitan,Bayan sun gaisa Alqali ya kalleshi yace"likita,mune iyayen yaron nan da aka kawo muku wanda yasamu harbi" Cikin girmamawa likita yace"Sojannan?" Alhaji Isah yace" qwarai shi,ya ake ciki ne dangane da jinyar tasa? shikkenan babu damuwa zamu Iya tafiya dashi yanzu sai acigaba da kula dashi a asbitin mu nacan?,kokuma zamu sake barinsa ne yasake warwarewa?" Cikin mamaki Likita yace"ikon Allah,wai dama wancen mutumin ba shine mahaifinsa ba?" Alhaji khaleed yace"wanne mutumi?" Mamaki cikeda fuskar likita yace"mutumin daya kawo shi,nayi tunanin shine mahaifinsa shiyasa ma nayi masa bayanin komai" Alqali yace"kai likita,mune iyayen Captain Aryan,kayi mana bayanin meyake faruwa" Likita yayi ajiyar zuciya yace"wato abunda yake faruwa shine....." Nan take yasake yimusu bayani kamar yanda yayiwa Alhaji Ma'aruf. Lokaci daya gumi ya rufe Alqali,Alhaji Isah mijin Mamy yacire hular kansa yafara firfita da'ita,Alhaji khaleed ne ya dinga maimaita salatin Annabi a fili, sannan yasamu qwarin gwiwar yiwa likitan magana yace"yanzu likita menene abunyi? zamu Iya fitar dashi qasar waje ne a nema masa lafiya kokuwa akwai wani abu wanda zaku iyayi basai anfitar dashi ba?" Likita yace"Alhaji no need ace anfitar dashi wata qasa saboda duk maganin dazai buqata munada shi anan qasar,sannan zamu dorashi akan magani idan yafara shan maganin lokaci zuwa lokaci yana mu'amular aure da matarsa to zai gani idan Sperm dinsa yazama normal kamar yanda yake abaya,idan har yadawo normal to zai Iya samun ciki da matarsa,idan kuma yaga yanayin Sperm din bai sauya ba,to dole zaici gaba dashan maganin sa" Alhaji khaleed yace"likita Captain Aryan bashida aure,tayaya zamu gane ya warke idan yafara shan maganin sa yanzu?" kai tsaye likita yace"saikuyi masa auren,kuma Ina baku tabbacin inde yafara shan maganin akan qa'ida kamar yanda nafada muku,to insha Allah bazai dauki dogon lokaci ba zai warke" Alhaji khaleed yasaka gefen babbar rigarsa ya goge gumin fuskarsa, sannan yace"mungode likita,yanzu zamu Iya tafiya dashi ne?" Likita yace"Why not?" Daga nan sukai masa godia suka futo daga cikin office din jikinsu a sanyaye. Daga waje Sojojin suka tsaya,su Alqali suka qarasa cikin dakin, Captain Aryan yana ganin yanayin jikinsu yasan cewa sunji komai, Alqali yanemi waje ya zauna, Alhaji khaleed da Alhaji Isah suna tsaye,Hajiya kilishi data kama yaranta ta riqe duka su biyun kamar za'a qwace mata su, cikin sanyin jiki ta kalli Alqali tace"Alhaji.....yana ganku jiki a sanyaye? lafiya?" Alqali yayi ajiyar zuciya yace"akwai matsala kilishi,yaron nan yasamu matsala......" nan take yabata labarin komai kamar yanda likita yafada musu. Tun kafin yagama yimata bayani take hawaye harya gama,amma bai fada mata yanda sukai da likitan akan shawarar daya basu ta batun auren Aryan dinba,ajiyar zuciya ta sauke sannan ta share hawayen idonta tace"hasbunallahu wani'imal wakeel,Ina ganin ikon Allah ni kilishi,wacce irin masifa ce wannan Alhaji?" Alhaji Isah yasaki ajiyar zuciya yace"Yaya kilishi kiyi haquri,kowanne bawa baya Iya kaucewa qaddarar sa,Ina ganin kutashi muyi shirin tafiya kawai" Adede lokacin shima doctor yashigo dakin, shida Ashraf sune suka fara qoqarin kamashi,cikin muryarsa kamar bayaso yace"zan'iya Doctor" Dakansa yatashi kamar ba ciwo ne a jikinsa ba,suka futo yabawa Sojojin sa umarnin suwuce Abuja kawai,zai taho daga baya, cikin girmamawa suka sara masa, sannan suka wuce, sukuma gaba dayansu suka nufi Airport suka dauki hanyar dawowa gida Tun kafin su koma gida labari ya Isa unguwar kowa yaji abinda yafaru,suna sauka kuwa sukaga mutane sun tattaru abakin get din gidan gaba dayansu ire-iren wanda yake yiwa Alkhairi ne idan yazo, sosai mutanan sukai musu jaje tareda addu'ar Allah yakiyaye gaba,sun dade a bakin get din, sannan suka samu nasarar shiga gida. Agidan ma kai tsaye suka wuce part din Hajiya kilishi, Mama Sadiya da Mamy da Nabiha nan take sukaje sukai masa sannu,amma Mawahib bataje ba,suma su Mamyn dasukaje Hajiya kilishi ko d'ago ido batayi ba bare ta kalli inda Mamy take. Tun safe dasuka zo Captain Aryan yayi shiru baya cewa um bare um um, saide in anyi masa Addu'ah Allah yakiyaye gaba yace Amin, daga haka babu qari, iyayen nasa sun lura yana cikin damuwa,sai suka dauki hakan amatsayin maganar rashin haihuwar sane take damunsa,abunda basu saniba shine maganar haihuwar kokad'an bata damunsa tunda ba cewa akai gaba daya har abada bazai sake haihuwa ba, yanasa ran shima zuwa gaba idan Allah ya qaddara zai iya haihuwa shima,maganar auren nan ce kawai take damunsa, yarasa wazai fad'awa yaji dad'i ko zai samu shawarar data dace. tun saukar su Hajiya kilishi bata zauna ba,dakanta tadafa musu abinci shida Ashraf takuma hanasu fita ko nan da can,sai yamma Ashraf yaje dakinsu yayi wanka sannan yadawo falon wajan Aryan. Ya zauna ya kalli Captain Aryan dayayi shiru kana ganinsa kasan yana cikin damuwa, yace"muje daki kayi wanka?" Kafin yayi magana Hajiya kilishi tace"bari inhada masa ruwan wankan a toilet dina saiya shiga yayi" tafadi hakan tana shigewa cikin dakinta,Ashraf yabi bayanta da kallo tareda murmushi yajuyo ya kalli Captain Aryan yace"d'an autan Momy" Captain Aryan baice komai ba Sai idonsa daya lumshe kawai Batafi minti biyar ba tadawo tace"Ashraf rakashi yayi wankan" Sai a lokacin ya bude lumsassun idonsa yace"zan'iya Momy" Daga nan yatashi ya shige dakin nata,yana shiga yawuce toilet yacire rigar jikinsa zai fara wankan. Hajiya kilishi ta dubi Ashraf dake zaune agefenta tace"dauko masa kayansa Ashraf" Kafin Ashraf yatashi sai qara suka jiyo daga toilet din Hajiya kilishi Cikin sauri Hajiya kilishi ta nufi dakinta tana fadin"Aryan lafiya?meyasa meka?" Yana daga cikin toilet d'in cikin shagwa6a yace" Momy zafi ruwan...." Ashraf yasaki d'an qaramin tsaki yafice daga dakin,yayi tunanin ma faduwa yayi shiyasa yashigo d'akin aguje(😂) Hajiya kilishi ta dafe kanta da hannunta(🤦🏻‍♀️) tace"Aryan anya hardakai akai training din aikin nan naku kuwa?" Yanajin abinda tace yayi shiru, badan yaso ba haka ya runtse idonsa yashiga ruwan,cikin ransa yana jinjina zafi irinna ruwan. Da daddare suna d'akinsu shida Ashraf,Captain Aryan yana zaune akan gado dagashi sai gajeren wando,wandon yanada laushi sosai hakan yasa mutum zai Iya ganin shacin komai(🙈) Baqin gashin dayake faffad'an qirjinsa ya kwanta luf asaman farar fatarsa,Ashraf kuwa yana sanye cikin kayan bacci wata doguwar riga mai kyau. Yazo bakin gadon ya zauna kusada Captain Aryan sannan yace"wai damuwar ce har yanzu? banajin dad'in yanda kake yawan tunanin nan Aryan,idan de magana ce akan haihuwa bagani ba, sai indinga haifo mana yaran" Captain Aryan yayi shiru yana tunani,kwata-kwata ba wannan ne damuwar saba, tunanin aurensa yake baisan yaya zai fadawa su Momy ba. Ashraf yaga yayi magana amma kamar ma Captain Aryan din baya tareda shi,ahankali yasaki ajiyar zuciya sannan yaja fillo ya kwanta agefen Aryan din,Captain Aryan kuwa yanata tunani saida yadawo daga duniyar tunanin nasa sannan ya kalli Ashraf yace"yanaga kaima kayi shiru? tunanin me kake?" Ashraf ya kalleshi yace"Ina tunanin abubuwan dasuka same mune dagani har kai cikin kwana biyun nan,kaiga qaddarar data sameka,nikuma Momy batason aure na da Mawahib,shekaran jiya fa anyi tashin hankali a gidan nan, inata kiran wayarka bata shiga,qarshe ma Daddy har marin Momy yayi" Cikin sauri Captain Aryan yace"mari kuma? tome ta masa?" Cikin sanyin jiki Ashraf yace"hakane,kayi haquri kayafemin nasa Daddy ya mari momy,amma yanzu dasauqi rashin lafiyarka yasa wancen rikicin ya kwanta,amma gaskiya Ina cikin damuwa,yanzu Momy bazata barni in auri yarinyar danake soba kenan?,wai ashe ba uncle Isah ne ya haifi Mawahib ba,Ina tunanin akwai abinda yafaru a gidannan wanda bamu saniba lokacin da muka fita karatu, kuma babu wanda yasanar damu, idan ba uncle Isah ne ya haifetaba waye mahaifinta to? yaushe Anty Mamy ta haifeta awani wajan kuma duk bamu sani ba?,amma ni koma waye ya haife ta inason ta ahaka" Captain Aryan yayi shiru bayan yagama Jin labarin da Ashraf yabashi,to Mawahib ma dasuke gida daya Momy tatashi hankalin ta tace baza'a aure taba,inaga shi da ko yarinyar ma baisaniba?🤔 Cikin damuwa yasaki ajiyar zuciya sannan yace"naka mai sauqi ne Ash..."(😂) Ashraf dabai fahimci me Captain yake nufi ba cikin sigar tambaya yace"kamarya?" Kafin Captain Aryan yayi magana Mamy tashigo dakin bakinta daukeda sallama, suna ganinta suka saki murmushi, Ashraf yace"Anty Mamy kece?" Mamy tayi murmushi tace"nice nazo dakin tuzurai, nasan basuda dan abun ta6awa shine na kawo musu" Captain Aryan yayi wani d'an qaramin murmushi mai aji, cikin sauri ya gyara zamansa ta hanyar had'e qafafunsa,sannan yad'auki fillo yad'ora akan cinyarsa saboda kar Anty Mamy taga abubuwan dasuke 6oye(🙈🙊😲) Ashraf daya lura da abinda yayi, cikin sauri ya kawar da kansa gefe yana murmushi,gashi ko riga babu a jikinsa, bazai iyu yasaka riga ba saboda audigar da'aka saka masa a wajan harbinsa. Mamy kuwa batamasan wainar dasuke toyawaba tanemi waje agefen gadon ta zauna tareda bude plate din hannunta mai daukeda sweet potato banana bites, tace"kuzo kuci" Babu musu Ashraf ya matso ya zauna agefen hannunta na hagu, shikuma Captain Aryan yana gefen hannunta na dama,sai suka sakata a tsakiyar su kamar wata yayar su, Ashraf yasaka hannu yafara ci yana lumshe idonsa, Mamy ta kalli Captain Aryan wanda fuskarsa take cikeda damuwa sannan ta d'auko daya tanufi bakinsa dashi, babu musu yabude mata bakin tasaka masa sannan yafara ci, Ashraf ya kalleta ya Sosa qeyarsa alamun kunya shime suruka, sannan yace"Anty Mamy nifa" Mamy ta girgiza kanta sannan tadauki daya shima tasaka masa a bakinsa sannan tace" Captain dazu Alhaji yafadamin abinda yake faruwa,kayi haquri ka kwantar da hankalinka,komai mai wucewa ne, watarana sai labari, sannan ya kamata idan kagama warwarewa koda a Abuja ne kasamu qwararren likita,nasan sunada likitoci masu kyau, inde suka doraka akan magani, abun zai zama tarihi " Ahankali yace"to Anty Ma-my zanje" Daga haka yayi shiru baisake cewa komai ba. Wayar Mamy ta dauki qara alamun kira yashigo,zuciyarta daya ta kalli wayar nan take taga sunan sa yafuto 6aro-6aro a fuskar wayar, mamaki ya kamata, cikin zuciyar ta ta maimaita sunan wanda yake kiran, MA'ARUF?,tome Ma'aruf zai fada mata? har abada bata fatan wani Abu yasake shiga tsakani ta dashi, batare da tunanin komai ba tayi rejecting Kiran (🙆🏻‍♀️) Saida takai wajan qarfe goma tana sake lallashin Captain Aryan, sannan tayi musu sallama ta futo daga dakin. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Washegari da yamma Mawahib da Nabiha suna Hanyar dawowa daga islamiya Nabiha tace"Mawahib yau qawar ki Jiddah bata zoba" Mawahib tace"eh wallahi nima nayi mamaki amma bari muqarasa gida saina kirata inji ko lafiya?" Nabiha tace"Mawahib kinji abinda yasamu Yaya Captain ko? wai likita yace bazai Iya haihuwa ba,saboda harbin da aka masa" Mawahib tace"naji wallahi,inaji lokacin da Abba yake fad'awa Mamy, ai gara hakan, dama menene amfanin haihuwar Yaya Captain? shiyasani,garama ya zauna hakan saboda may be idan ya haihun ma yaran suyi irin halinsa,saboda haka canta matse masa, ni abinda yake damuna ma ya'isheni" Cikin sauri Nabiha tace"meyake damunki?" Mawahib tace"Nabiha tunda abun nan yafaru nasan cewa niba yar gidanan bace wallahi bana baccin kirki,sai yanzu ne nasan dalilin dayasa Momy kilishi bata qauna ta,sannan na cewa Mamy na tabarni na koma wajan mahaifi na inde yana raye, tace karna kuskura nasake yimata maganar sa,gaba daya narasa yanda zanyi, gashi inajin gabana yana yawan faduwa kusan kwana hudu kenan, haka kawai sai gabana yadinga faduwa" Nabiha tace"innalillah...,toki dinga Addu'ah,amma maganar tafiya kima dainata Mawahib, kema kinsan idan kika tafi nima bazanji dadi ba" ****** Alhaji khaleed mahaifin Nabiha, yadubi sauran yan'uwansa yace"koda ace likita bai bamu shawarar muyiwa Aryan aure ba, dole ne dukansu ayi musu aure,saboda gudun kada wata matsalar tasake faruwa,inda ace tun farko sunyi aure da wuri,da yanzu daga shi Ashraf din har Aryan din babu wanda baida d'ansa na kansa,to amma mun zuba musu ido, munbar yara suna zaune babu aure" Alqali yace"wannna hakane,nima nayi wannan tunanin,kuma munyi magana da mahaifiyar su,nariga nafada mata auren Mawahib da Ashraf babu fashi,to itama takawo wata magana cewa shi Aryan din tasamo masa yarinya,yar wajan qaninta wato Asalamiyya,saboda haka yanzu gaba dayansu su hudun za'a hada ayi auren su,itama Nabiha akirata aji idan akwai wanda takeso" Alhaji Isah yace"wannan shawarar tayi Yaya, Allah yabasu zaman lafiya" Alqali yace"Amin Amin, yanzu kiramin ita Mawahib din" Yajuya ya Kalli Alhaji khaleed yace"kaima Khaleed kiramin Nabiha" Babu 6ata lokaci Alhaji Isah yadauki wayarsa yakira Mamy,tana dauka yace"turomin yarinyar nan bakin get yanzu yanzu" Mamy tanajin haka tasan cewa akwai abinda yake faruwa, kuma bazai wuce maganar Mawahib din da Ashraf ba,to amma bata tabbatar ba,dole zata masa biyaiya ta tura Mawahib din dan taji ko menene dalilin kiran. Mawahib tana zuwa taga Nabiha agaban iyayen nata a zaune,cikin ranta take fadin to lafiya? Ta qarasa itama ta zauna tareda sallama. Alqali ya dubeta yace"Mawahib munyi magana da iyayenki gasunan a zaune,muna so muhada aurenki da Ashraf,to amma muna so muji ta bakinki,kina sonsa kokuwa?" Gaban Mawahib ya yanke yafadi,tayi tunanin tunda akayi tashin hankalin nan da Hajiya kilishi ai magana ta wuce,harga Allah batason Yaya Ashraf,koda wasa batason tashin hankali gara ta nesanta kanta da Momy kilishi, to amma yaya zatayi? tayaya zata kalli idon mutanan dasuka riqeta tsakani da Allah tun tana yarinya suka ciyar da'ita suka tufatar da'ita, suka shayar da'ita tace musu batason d'ansu? jin tayi shiru yasa Alhaji Isah yace"kinyi shiru Mawahib koda matsala?" Cikin sanyin jiki tace"Babu matsala Abba Ina sonshi" Alqali yayi murmushi yace"to Alhamdulillah,Allah yayi miki Albarka,tashi kije" Ahankali ta amsa sannan tatashi tabar wajan. Alqali ya kalli Nabiha tace"Nabiha kefa? akwai wanda kike tare dashi ne yanzu?" Nabiha tayi shiru tana tunani,mutumin datake qauna tun tana 'yar qanqanuwarta hankalinsa da zuciyarsa suna wajan Mawahib,kuma itada Mawahib kamar abu dayane,dole zatayi haquri dashi ta auri wani koda kuwa hakan zai cutar da zuciyar ta. Ahankali tadago ta aalli Alqali sannan tace"A a Daddy babu" Alqali yace"kin tabbata?" Cikin sanyin jiki tace"eh Daddy" Yace"to shikkenan,zamuyi magana daga baya, tashi kije" Cikin nutsuwa tatashi tatafi tanajin zuciyar ta tana karyewa kamar ta fashe da kuka,daqyar ta'iya qarasa wa part dinsu, tana zuwa tun daga falo taji zuciyar ta tana mata zafi,lokaci daya tasaki wani irin kuka maicin rai tafada jikin Mama Sadiya tana fadin"Mama wallahi Ina sonshi" Mama Sadiya ta dinga binta da kallon mamaki tace"ke kalau kike kuwa? wani abun su Alhajin suka fada miki?" Cikin kuka tace"wai Mawahib zasu bawa Yaya Ashraf,Mama wallahi Ina son Yaya Ashraf...." Mama Sadiya tadago Nabiha daga jikinta cikin sauri tace"Nabiha kanki daya kuwa? kirasa wanda zaki so sai d'an Yaya kilishi? kirufamin asiri banason tashin hankali,ko ba'a kan idonki komai yafaru ba shekaran jiya jiyan nan?" Cikin kuka Nabiha tatashi tashige d'akinta, Mama Sadiya tabita da kallo tana tafa hannu tana sallallami. ****** Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Cikin damuwa tasake goge hawayen idonta tace"Mamy dan Allah kibarni natafi....,ni bazan Iya auren Yaya Ashraf ba,Momy kilishi kasheni zatayi, kibarni natafi wajan mahaifi na Mamy" Mamy da ranta yayi baqiqqirin tace"kinsan bakya so dan me zaki amince musu? babu inda zan barki kije,ko Ina halin hauka bazan bari kikoma wajan mahaifin kiba,bare kuma inada hankali,ki daina 6ata lokacin ki kina kuka itama mahaifiyar tasa bazata bari ayi auren ba,konima nan har abada bazan yarda ki auri yaron Yaya kilishi ba, gara kitafi maiduguri kiyi zaman ki acan, kokuma Alhaji yasakeni mutafi gaba daya, amma nima bana goyon bayan wannan auren " Mawahib tanajin abinda Mamy tafada taji hankalin ta yadan kwanta,ko banza tasan baza ayi auren ba tunda gashi tasamu goyon bayan Mamy, hakan ne yasa hankalin ta yadan kwanta hartaje daki ta kwanta ****** Washegari da safe suna zaune a dining ng suna break fast su hudu,Alqali da Hajiya kilishi, da Ashraf da Aryan,Hajiya kilishi ta kalli Aryan taga banda ruwan black tea babu abinda yakesha, cikin damuwa tace"Aryan bakasan cin abinci,kacire damuwar nan aranka kadauki qaddara komai fa mai wucewa ne" Cikin sanyin jiki yace"to Momy" Alqali ya ajiye cup din hannunsa ya kalli yaran nasa yace"mungama magana da iyayenku,zuwa jibi za'a saka muku ranar aurenku,Ashraf Mawahib, kaikuma Aryan za'a hada auren ka da Asalamiyya 'yar gidan kawunku Tafida" Cikin sauri Aryan dayake shan tea yaqware,lokaci daya yariqe qirjinsa yafara tari. Cikin sauri Hajiya kilishi tatashi tafara bubbuga bayansa tana masa sannu. Alqali yasan ma'anar tarin da Aryan yakeyi,yana nufin bayason auren, kuma bazai lamunci jin wata magana ba,dolen dole yayi aure kodan neman lafiyarsa. Yana gama wannan tunanin yatashi yabar wajan. Yana ganin tashin Alqali ya kalli Hajiya kilishi yace"Momy nifa banason auren nan..." Cikin sigar lallashi tace"yanzu Aryan menene laifin Asalamiyya?" Cikin tsananin damuwa ya lumshe idonsa yabude,su Momy bazasu gane ba,tayaya ne zai fada musu cewa shifa yana aure batare da sun sake qaqaba masa wani auren ba? Cikin damuwa yatashi daga dining d'in yafuto daga part din gaba daya. A compound din gidan yatsaya yarasa Ina zai nufa? wa zai fadawa halin da yake ciki yabashi shawara? gaba daya kansa yadauki zafi jiyake lallausar sumar kansa tana tiriri,bayan yagama yankewa kansa shawara kai tsaye yanufi part din Mamy. Yana zuwa falon yaga babu kowa sai qarar TV datake yi,zama yayi acikin daya daga cikin kujerun falon yayi tagumi hannu bibbiyu tareda zubawa tv ido,amma azahiri ba kallon yakeba,ya lula ne cikin duniyar tunani, saida yagama tunani yaga bashida mafita sannan yasaki ajiyar zuciya, yajuya gefensa anan yaga wata yar madedeciyar brezia akan kujera, ya qarewa breziar kallo ya yatsina fuska,yasan aikin Mawahib ne,ya kalli qoqon breziyar yana tunanin yanzu boobs dintane yake cika duk wannan qoqon? bazai iyuba, saide in cuko take,duka duka nawama take dazata saka wannan? dama duk ciko ne,za'a bawa dan'uwan sa fake,shikuma Ashraf duk ya rangauce jiyake abubuwan ne (😲🙊) Adede lokacin Mamy tafuto daga dakinta taga Captain yana kallon brezia,mamaki ya kamata meyake damunsa ya zauna shi kadai anan yana tunani? Cikin sauri taqaraso wajansa ta zauna tace"Captain meyake faruwa ka zauna anan kana tunani?" Shiru yayi yakasa bata amsa,harta fitar darai ba zaiyi magana ba, sai can kuma yace"Babu komai" Mamy tayi shiru tana tantama aranta tabbas akwai damuwa,akwai abinda yake damun Captain, tajuya ta kalli breziyar Mawahib data sameshi yana kallo, ta qwala mata kira.... Tana daga cikin dakinta ta amsa tafuto da sauri,tana sanye cikin riga da wando,sai hula mai girma data saka akanta, kwata-kwata baka ganin baiwar dogon gashin kanta, wandon na jeans ne sai kuma rigar yar qarama mai launin ja,hips dinta yacika wandon taf... sai rawa sukeyi, cikin sauri Captain yadauke idonsa daga kanta. Mawahib tana qarasowa falon ganin Captain a zaune tayi tunanin Ashraf ne,shiyasa tad'an saki ranta tayi murmushi har dimple dinta suna futowa tace"laa Ya Ashraf yaushe kashigo?" Binta yayi da kallo cikin ransa yace"dama tana murmushi?"(🤔) Kafin yayi magana Mamy tace"banason shashanci Mawahib,dauke wannan abar daga anan...yayun nakima har gobe kin kasa ganesu" taqarasa maganar tana yi mata nuni da breziyar ta dake gefen Captain,sai a lokacin Mawahib tashiga taitayinta,tanajin furucin Mamy tasan cewa toba Yaya Ashraf bane, Yaya Captain ne,nan take tashiga hankalin ta,tasa hannu ta dauki breziyar ta sum-sum takoma cikin dakinta. Mamy ta kalli Captain tace"muje daki?" Babu musu ya daga mata kai,tatashi tayi gaba shikuma yabiyo bayanta har cikin d'akinta, suna zuwa ta zauna abakin gadonta shima ya zauna, ta kalleshi dakyau, cikin sigar lallashi tace"meyake faruwa? wani abunne yasake ya faruwa kuma?" Bude bakinsa yayi zaiyi mata magana amma saiya kasa,saboda raunin da zuciyarsa tayi,ahankali yadora kansa akan kafadarta,babu wata-wata yasaki wani irin kuka (😳🙊🙆🏻‍♀️) Gaban Mamy yayanke yafadi, ta tabbatar akwai babbar matsala, Captain da kuka? yaushe rabon dataga yana kuka? zata Iya cewa tun suna yara Ajiyar zuciya ta sauke tadora hannunta akan lallausar sumar kansa tafara shafawa, sannan tamaida hannunta kan gadon bayansa tafara bubbugawa alamun lallashi, batace dashi uffan ba, saida tabarshi yayi kukan, yaji sauqin rad'ad'in dayake damunsa, sannan tad'agoshi daga kafad'arta tace"fad'amin meyake faruwa?" "Anty Ma-my....su Daddy ne sukace zasu saka mana rana jibi,nikuma banason auren" Mamy ta lumshe Idonta tabude, sannan tace"yanzu Captain banda shagwa6a kawai saboda bakason aure saika fara kuka?meyasa bakason auren?,ko akwai yarinyar dakake so?" Cikin sauri ya girgiza kansa sannan yace"ni babu yarinyar danakeso Anty Ma-my" Mamy tace"to meyasa?" Duk da gabansa yana faduwa hakan bai hanashi baiyana mata gaskiya ba,may be zai samu shawarar dayake nema a wajanta,kai tsaye yadago kansa ya kalle ta sannan yace" SABODA INADA AURE" Cikin sauri Mamy tace"What...?" (Ina ganin ikon Allah ni Amina😂 kowanne irin matsayi abokiyar shawara zata koma bayan Aryan yagano itace sirikar tasa? 🤔 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Taredashedar biya ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: *Page 19&20* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Captain Aryan yayi shiru yana kallonta ganin yanda ta tsorata takuma d'auki zafi akan maganar,to inaga Momy kilishi Kuma? Cikin tashin hankali Mamy taci gaba da fad'in"innalillahi...to garin Yaya hakan tafaru? meyasa kayi hakan Captain?" Ahankali Captain yafara yimata bayani tiryan-tiryan yanda abubuwa suka faru harya gama sannan yace"ni bansan Yaya zanyi da Momy ba" Mamy tayi firfita da hannunta alamun garin yafara yimata zafi tace"Hasbunallahu wani'imal wakeel, toshi mahaukacin inane zaiyi ma aure babu sanin iyayenka?" Captain Aryan yayi shiru yakasa bata amsa ganin yayi shiru hakan yasa ta fahimci bashida amsar dazai bata, tasaki ajiyar zuciya tace"wannan ba maganar daza'a yi shiru bane,maganar aure aita wuce wasa,zanje In samu Yaya kilishi Infada mata komai" Cikin sauri Captain yace"a a Anty Ma-my,kada kisake yin wani laifin a wajanta, zan fad'a mata" "to Ashraf yasani ne?" "A a ban fad'a masa ba" tace"toka sameshi kafad'a masa,kuje kusamu Daddynku da Yaya kilishin kufad'a musu komai " Cikin gamsuwa ya girgiza mata kansa alamun amsawa, sannan yatashi yafuto daga dakin itama tabiyo bayansa gaba daya jikinta yayi sanyi,qwaqwalwar ta tatsaya cak tarasa gane tunanin me zatayi.... ****** Abba yana zaune afalo yana ganin labarai,ya kalli Mamy yace"kiramin Ruqayya" Mamy tatashi tashiga d'akin Mawahib a lokacin tana zaune akan sallaya tana karatun qur'ani, Mamy ta kalleta tace"kizo" Saida takai qarshan ayar datake karantawa sannan tarufe qur'anin tafuto, tana zuwa ta zauna cikin ladabi tace"Abba gani" Alhaji Isah Yadauki remote yarage qaran tv sannan yace"gobe muke shirin saka ranar ku keda Ashraf,Ina fatan de babu wata matsala ko?" Kafin Mawahib tayi magana Mamy tace" Alhaji matsala ta nawa kuma? nifa dakun bar wannan maganar tazauna tajira Nabil din har zuwa lokacin dazai shirya" Abba ya gyara zamansa sosai Yajuya yana kallon Mamy yace"saboda me? shi jinin nawa ne bakya so 'yarki ta aura kinfi son taje ta auri d'an d'an'uwanki?" "bahaka bane Alhaji" Cikin zafi Abba yace"to menene Maryam?tunda munkira yarinya jiya kuma ta amsa mana da bakinta tanaso to meyasa zaki dauko wata maganar kuma?" Mamy tace"Alhaji, kaida kanka kasan cewa uwar yaron nan bata qaunar hadin nan,tunda Mawahib take cikin gidannan banta6a ganin Yaya kilishi tayi mata kallon arziqi ba,tayaya ne inaji Ina gani zan bari adauki yata qwalli daya akaita wajan Yaya kilishi bayan nasan cewa idan akwai wadda Yaya kilishi ta tsana a duniya to baiwuce nida Mawahib ba?" Abba yace"Okay to yanzu hukuncin da muka zartar nida Yaya Alqali shi zaki warware kenan saboda kina taqama Ruqayya 'yarki ce?" Mawahib tanajin haka idonta yaciko da qwalla,bata ta6a ganin Mamy da Abba suna sa'insa ba,sai gashi akanta hakan tana faruwa,ahankali tatashi tabar wajan takoma dakinta tana share hawaye Mamy ta kalli Abba tace"Amma wanne irin hukunci ne wannan?,bayan kunsan abinda yake faruwa saboda me zaku hada aurensu? nide Alhaji bana maraba da wannan auren,idan kuma kuka dage sai kunyi tozan tattara kayana nabar muku gidanku" Tana fadin haka ta miqe zatabar wajan. Abba yace"to aikuwa dagake har Yaya kilishi,baku Isa kuhanamu abinda mukai niyya ba,idan kuma zaku fara toga wajan nan" ****** Da daddare suna d'akinsu,Ashraf sai waya yake da abokansa na wajan aiki yana fada musu very soon zai zama ango Captain yana zaune agefen gado yana kallonsa, saida yabari yagama yin wayar sannan yayi ajiyar zuciya yace"Ashraf" Ashraf dayake tsaye yana danna waya yadago yace"ya'akayi?" Cikin damuwa Captain yace"magana zamuyi" Mamaki yakama Ashraf,yadawo kusada Aryan ya zauna sannan yace"meyake faruwa? Ko wani abune yakema ciwo?" Captain ya girgiza kansa yace"Ash...inada damuwa,narasa yanda zanyi inyi magana dasu Momy,but nayi maganar da Mamy, tace insameka muyi magana dakai sannan muje mufad'awa su Momy komai" Ashraf yace"meyake faruwa? fadamin " Cikin damuwa yace"Ash nifa anbani mace..." cikin rashin damuwa Ashraf ysce"nasani ai,koba Asalamiyya ba?" Captain yasaki dan qaramin tsaki sannan ya lumshe idonsa yabude yace"inama maganar serious kana min zancen wata Asalamiyya ni banma san yarinyar nan ba,Ina nufin inada aure Ash" Cikin sauri Ashraf ya kalleshi yace"kana hayyacinka kuwa?" Captain Aryan ya kalli Ashraf cikin damuwa yace"da gaske nake,anbani mace" Cikin sauri Ashraf yace"to Aryan kode kafara shan wani abu ne bansani ba? tayaya zakace min kanada aure in yarda? yaushe kayi aure? kuma a'ina?" Cikin sanyin jiki Captain Aryan yace"niba ni nayi ba,qaqaba min akayi,har yanzu bansan yaya yarinyar take ba,shi kansa wanda yamin auren bansan ko waye shiba" Ashraf yace"mekake san cewa?" Captain Aryan ya kwashe komai tun daga farko har qarshe ya fadawa Ashraf, sannan yaci gaba da cewa"bawai damuwar haihuwa ce tasa nake tunani ba Ash,wannan maganar auren ne,bansan ta'ina zan fara yiwa su Daddy maganar ba,nikuma gaskiya banda ra'ayin yin mata biyu,shiyasa nashiga damuwa,idan nayi shiru hakan yana nufin zasu sake daura min aure da Asalamiyya,bayan itama waccen yarinyar bansan yaya take ba,kaini yanda banason kowacce yarinya ma inde nasake had'uwa da mahaifinta banason damuwa gaskiya zan sakar masa 'yarsa...."(🙆🏻‍♀️) Lokaci daya gumi ya wanke fuskar Ashraf,cikin sauri yasaka hannunsa ya goge sannan ya doka tagumi hannu bibbiyu(🙉) Yayi shiru yakasa magana. Captain Aryan yaci gaba fa fadin "kuma ni gaskiya bazan Iya tunkaran Momy da wannan maganar ba,kuma banason su sake liqa min wata yarinyar, gaba daya narasa yanda zanyi da raina,Ash... inaji araina dama banzo gida ba,kwata kwata wannan zuwan nawa bashida dadi,komai ya lalace min, kamar a film nake ganin komai yana faruwa akaina" Ya qarasa maganar sannan shima yayi tagumi hannu bibbiyu kamar yanda Ashraf yayi. Har zuwa lokacin Ashraf yayi shiru yakasa magana,shi kansa daba shine hakan tafaru dashi ba,gabansa faduwa yake, toshi kuma Aryan din yaya yakeji kenan? Cikin rashin qwarin gwiwa Ashraf yace"tunani na yatsaya cak,bansan ma yaya zamuyi ba, amma abinda yafi kawai mu fadawa Daddy gobe,shidin yad'anfi Momy sauqi " Captain Aryan yadaga kansa alamun amsawa sannan yasamu yacire tagumin da yayi yajuya ya kwanta tareda rufe idonsa badan yanajin baccin ba. ****** Washegari da safe daga Aryan har Ashraf babu wanda yaje part din Hajiya kilishi yin break fast, gaba dayansu suna zaune a dakinsu kowa yayi shiru, shi Captain yana zaune agefen gado yayi tagumi, shikuma Ashraf yana tsaye daga gefen window hannunsa harde a qirjinsa shima yayi shiru, Hajiya kilishi dataji shiru basuzo cin abinci ba saita hado musu komai tabiyosu dashi dakinsu,kai tsaye taturo qofar dakin tashigo, saita gansu kowa gabansa, kuma duk sunyi shiru, cikin mamaki tace"kukuma lafiya kuka zauna ad'aki ku kad'ai bakuzo kunci abinci ba?" Ashraf ne yayi kokarin bata amsa yace"bamajin yunwa Momy" Cikin mamaki ta kalleshi sannan tasake kallon Aryan, tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi tome aka muku?"(😂) Yanzun ma Ashraf ne yabata amsa yace"babu komai..." tata6e bakinta tace"cikinku..." Tajuya ta kalli Aryan tace"kasha maganin kane?" batare daya kalleta ba, yabata amsa a taqaice yace"nasha" Kilishi tasaki ajiyar zuciya tace"wai saboda batun Asalamiyya ne kake ta wani d'aure fuska? to babana kadad'e baka d'aure fuska ba,dan aure babu fashi" tajuya ta kalli Ashraf dayake tsaye har lokacin, tace"kada Allah yasa kuci abincin, kanku kuka yiwa " tajuya ta fice daga dakin. Tana fita Captain ya kalli Ashraf cikin shagwa6a yace"kanaji abinda Momy take fada ko?" Ashraf yace"rabu da'ita, zamu fadawa Daddy ai" shiru suka sake yi,kusan awa daya babu wanda ya kula abincin data kawo musu, kamar wasa Ashraf dayake tsaye jikin window yaga wani abokin Alqali yashigo gidan hannunsa daukeda goro,cikin mamaki yabude bakinsa zaiyi magana saiya ga Alqali yashigo shida wani maqocinsu da Alhaji khaleed mahaifin Nabiha, dakuma Alhaji Isah mijin Mamy, sai fara'ah sukeyi dukansu sunsha manyan kaya kamar yaune ranar d'aurin auren. Cikin sauri yajuya ya kalli Aryan yace"Aryan sunzo,wallahi gasu Daddy can sun wuce part din Momy da goro,Ina tunanin fa ranar nan zasu saka, taso muje muyi musu bayani" Cikin sauri Captain Aryan yatashi kamar wanda aka tsikare shi,Ashraf ya dauko masa riga da wando na qananun kaya yasaka, shikuwa Ashraf d'in jallabiya ce a jikinsa yau hankali ba'a kwance yakeba babu wanda yayi tunani saka kaya iri daya a cikinsu.(😂) Suna zuwa falon suka tararda iyayen nasu sun zazzauna sunata sake gaishe-gaishe,suma suka nemi waje suka zauna,Alqali yabisu da kallon mamaki, saide kafin yayi magana suka sake Jin wata sallamar, yan'uwan Hajiya kilishi ne sukazo wato dangin Asalamiyya,nan aka sake sabuwar gaisuwa,sannan kowa yayi shiru Ana jiran Alqali ya zartar da komai. Alqali ya kalli yaran nasa yace"Ashraf meyake faruwa ne naganku anan?" Daya daga cikin yan'uwan Hajiya kilishi yayi murmushi yace"Alhaji arabu dasu mana, suma ai zasu ga yanda akeyi ko?" Alhaji khaleed ya kalli wanda yayi magana yace"zumudi ne da rashin haquri kawai irin nasu,mezai kawosu wajan saka ranar aurensu Alhaji Sammani?" wanda aka kira da Alhaji sammani yayi murmushi yace"to Alhaji khaleed aida an qyale su,Asalamiyya ai 'yar gida ce....danma batason zumunci ne aida zaku dinga ganinta a gidan koda yaushe,shima angon aida bazaiyi d'okinta har hakaba...."(😂🙊) Captain Aryan da yaji wannan furucin lokaci daya ransa yayi baqiqqirin,idan za'a kasheshi baimasan Yaya Asalamiyya takeba bare ace wai yana d'okinta,gaba daya maganganun nasu ma sai suka sake 6ata masa rai, cikin dakiya irin tasu ta sojoji yadago kansa ya Kalli Ashraf yace"Kafada musu"(😂) Shima Ashraf ya kalli Captain yace"A a,kaika fada musu" Alhaji Isah yayi murmushi yace" yanbiyu meyake faruwa ne? kuyi magana mana" Adede lokacin Hajiya kilishi takawo wa baqi ruwa da lemuka, anan taga ansaka Aryan da Ashraf agaba ana cewa suyi magana, cikin mamaki taja ta tsaya tanaso taga menene yake faruwa,dama tunda tagansu a dakinsu sunyi shiru tasan akwai abinda suke qullawa. Ashraf da Aryan kuwa suna ganin Hajiya kilishi ta tsaya gaba dayansu sai suka sunkuyar da kansu, sunma kasa dago ido bare su kalli iyayen nasu. Hajiya kilishi data gama tabbatar wa akwai abinda yaran suke 6oyewa, ta kalli su Alqali sannan ta kalli su Ashraf tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,toko kunzama kurame ne ana magana kunyi shiru?" Alqali yazuba musu ido yana kallonsu,duk da bayason had'in auren Aryan da Asalamiyya fatansa daya kada Aryan ya kunyatashi agaban wad'annan mutane yace bayason Asalamiyya saboda tun ranar daya fada musu zai musu aure yake ganin take takensa. Alhaji Isah yayi gyaran murya cikin sigar lallashi yace"Ashraf kaine babba fad'amin meyake faruwa? karka 6oye mana komai menene yake faruwa?" Ashraf yadago kansa ya kalli Alqali sannan yayi qasa da kansa, yasosa qeyarsa yace"Uncle dama...dama Aryan ne yace kar asa ranar nan dashi, saboda shi yanada mata, kuma....." Tun kafin Ashraf yagama magana gaba d'aya mutanan falon suka hada baki sukace "la'ila ha illallahu,Muhammadu rasulillahi" Hajiya kilishi datake tsaye cikin sauri tazo tafara jijjiga kafadar Captain, cikin tsananin mamaki tace"Aryan...?" Sannan tafara tafa hannayen ta tana sallallami. Alhaji Isah yacire hular kansa yafara firfita da'ita, Alqali kuwa duk esin da yakeji afalon hakan bai hana yatashi tsaye yacire babbar rigarsa ba. Alhaji khaleed ne yagoge gumin goshinsa ya kalli Captain da kansa yake qasa har lokacin yace" Aryan,meyasa kayi haka? yanzu muna iyayenka bamu Isa muyi ma aure ba saide kaje kayi auren sirri? menene ribar hakan? mu muna gida kullum muna fatan ace kasamu mace kayi aure ashe kai kayi auren ka mukake rainawa wayo?" Cikin sanyin jiki Captain yace"Uncle wallahi bahaka bane,yanda kuke tunani bahaka abun yake ba,abinda yafaru shine tun ranar dana samu harbi mutumin daya kaini asbiti likita yayi masa bayanin rashin lafiya ta,shine shikuma yayanke hukunci yace ya d'auramin aure da yarsa tunda shine sanadin samun matsala ta.... " Hajiya kilishi tanajin magana daga bakin mai ita tad'ora hannunta aka tasaki kuka, cikin ihun kuka tace"nikam nashiga uku na,ni kilishi Ina ganin ikon Allah,wanne marar mutuncin ne yayi maka aure babu saninmu Aryan?" Alhaji sammani wakilin Asalamiyya ya kalli Hajiya kilishi yace"Kilishi kiyi shiru kidena wannan koke koken,ai shi bawa babu inda ya'isa yawuce qaddarar sa " Yajuya ya kalli Captain Aryan yace"kai Aryan,yanzu Ina mutumin daya yi ma auren yake? kasan inda zamuje mu sameshi?" Captain ya girgiza kansa alamun a a Alhaji Isa mijin Mamy yace"wanne irin shirme ne wannan? bai nuna maka yarinyar ba kawai ya daurama aure yatafi?" Captain Aryan ya kalleshi yace"ni har yanzu banga yarinyar ba,yabani katinsa de yace duk lokacin danake buqatar matata in kirashi..." Alhaji Isa yace"to Alhamdulillah, yanzu Ina katin yake?" Captain Aryan yatashi yafice daga falon, dukansu suka bishi da kallo, kai tsaye dakinsu yaje, cikin bed side drower dinsu yabude yadauko katin yazuba masa ido kamar yana ganin wani Abu ajikin katin, sannan yafuto daga dakin yakoma falo,har zuwa lokacin Hajiya kilishi tana zaune agefe tana goge hawaye, mazan falon kuwa kowa yayi shiru, kowa da abunda yake saqawa aransa Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 *** Suna nan zaune har Captain yadawo. Alhaji Isah ya dubi Aryan yace"bani katin " Babu musu Captain Aryan yabashi katin, sannan ya zauna kusada Ashraf. Alhaji Isa yadauko wayarsa yakira number Alhaji Ma'aruf, sannan yasaka wayar a amsa kuwwa yanda duka mutanan falon zasu ji abinda yake faruwa, wayar da farko qin shiga tayi, saida yasake kira a karo na biyu sannan tashiga, bugu uku kuwa yadauka tareda sallama, Alhaji Isah yace"muna magana dame wayar ne?" Daga dayan 6angaren Alhaji Ma'aruf yace"eh nine,me wayar ne, dawa nake magana?" Abba yace"kana magana ne da Alhaji Isah, daya daga cikin iyayen CAPTAIN ARYAN" Alhaji Ma'aruf yanajin haka yatashi zaune tareda fadin "Alhamdulillah, Allah nagode maka,tun ranar da muka rabu da wannan yaron nake tunanin halin da yake ciki,kuma ni banyi azanci na kar6i number saba..." Alhaji Isah yace"yanzu de ba wannan ba bawan Allah,muna nan zamu sakawa Aryan ranar aure sai yake fada mana wata magana, yace kayi masa aure,munyi mamaki tayaya zaka yiwa yaro aure batare da sanin mu iyayensa ba" Alhaji Ma'aruf yace"wannna maganar bata waya bace Alhaji,tun ranar danabar Captain Aryan a asbiti nake zaune nake jiran ranar dazai kirani inzo har gida in roqi iyayensa gafara suyi haquri akan hukuncin dana yanke" Alhaji Isah yace"ta tabbata de kayi masa auren kenan,yanzu Ina yarinyar take? ka tabbatar shi Aryan din yanason yarinyar ne kokuma kawai hadin aure ka'iya?" Alhaji Ma'aruf yanajin wannan furucin jikinsa yayi sanyi, ya tabbatar kuma tabbas iyayen Aryan ransu ya6aci akan hakan,cikin sanyin jiki Alhaji Ma'aruf yace"to nide Ina mai sake baku haquri akan kuskure na, maganar yana sonta ko baya sonta kuma duk basu taso ba, nide daukan yarinyata nayi na bashi kyauta,kuma duk da bansan halin danku ba inada yaqinin zai riqemin yata tsakani da Allah" Alqali dayake zaune dukansu sunajin yanda take kayawa tsakanin Alhaji Ma'aruf mahaifin Mawahib,dakuma Alhaji Isah wani mahaifin nata(😂) Alqali ya daga murya yace"isah kace dashi yazo shida yartasa munasan ganinsa" Alhaji Isah yace"to idan babu damuwa kazo munasan ganinka tareda 'yartaka" Daga dayan bangaren Alhaji Ma'aruf ya kalli Agogon dake daure a farar fatar hannunsa yace"yanzu karfe goma da rabi na safe,zanyi kokari nabiyo flight din dazai taso yanzu sainazo,kuna wanne gari?" Abba yace"muna cikin garin kano" Cikin mamaki Alhaji Ma'aruf yace"a a, ikon Allah, to ai itama yarinyar tana kano,kaga shikkenan takwana gidan sauqi,idan nazo saimu qarasa daku muje inbaku yarinya" Cikin damuwa Abba yace"Okay yarinyar bata tare dakai kenan,tanada auren kabata iznin tafiya wani garin" Jikin Alhaji Ma'aruf yayi sanyi,meyasa wanna mutumin yake gwa6a masa magana ne kamar akwai wani abu aqasa?🤔 Yayi murmushin qarfin hali yace"gani nan zuwa" Batare daya jira amsar Alhaji Isa ba yakashe wayar,kai tsaye wajan Abokinsa Alhaji Bala ya nufa,yafada masa abinda yake faruwa,daga nan suka wuce Airport domin tahowa kano, tun ahanyarsa ta tafiya Airport yake kiran Mamy,amma koda wasa bata dauki wayar ba, haka ya dinga kiranta har zuwa lokacin da jirgin su zai tashi sannan ya haqura da kiran. ****** "sister Maryam kina gani tun dazu ana kiranki amma kinqi dauka, kiyi haquri ki dauka mana ko marasa lafiya ne suke kira" Mamy tayi ajiyar zuciya tace"Sister Bilkisa ba kowa bane yake kira Ma'aruf ne,me Ma'aruf zai fadamin? banason Jin muryarsa ko a mafarki" Sister Bilkisa tayi murmushi tace"Sister Maryam nasanki da haquri amma bansan meyasa har yanzu kikaqi yafewa Ma'aruf ba,shekara nawa? yakamata ace komai yawuce, ki dauki wayarsa kiji dalilin kiran" Cikin damuwa Mamy tace"bazaki ganeba,damuwar danake ciki ma ta'isheni basai nahada data Ma'aruf ba,mazajenmu sunacan agida suna kokarin saka ranar Mawahib dina da yaron Yaya kilishi,kwata kwata banason wannan hadin,bansan Yaya zanyi inhana faruwar hakan ba,amma muddin suka saka ranar nan to nima zan saka mana rana nida Mawahib saide su nememu surasa a gidan, maiduguri zamu tafi" Sister Bilkisa tayi murmushi tace"kitafi kibar gidan aurenki saboda wata kilishi? haba Maryam karki bada matan maiduguri mana, kishiya bata koreki daga gidan miji ba sai wata can facala ce zata koreki? babu inda zakije zama daram a gidan Isah,ita de yarinya yanzu ne zaki samo mata hanyar guduwa, amma fa idan kinso" Cikin mamaki Mamy tace"kamarya? mekike nufi?" Sister Bilkisa tayi murmushi tace"kidauki wayar Ma'aruf kiji menene yake tafe dashi, daga nan kiji Ina yake da zama yanzu? dazaran yafada miki to ki hadawa Mawahib kayanta takoma wajan ubanta,hakan ai zaifi" Mamy tayi shiruuu tana nazari akan maganar abokiyar aikin ta, sai can tace "kumafa hakane, ni kwata kwata ma bankawo wannan tunanin arainaba,saide Ina fatan ace zuwa yanzu Ma'aruf ya sauya halaiyarsa" Tana gama wannan maganar ta kirashi,adede lokacin Alhaji Ma'aruf da Alhaji Bala saukarsu kenan a Airport din malam Aminu suna kokarin tare taxi,yana ganin kiran nata yayi sauri yadauka, cikin damuwa yace"Haba Maryam, me yayi zafi haka? amma ko babu yarinya a tsakanin mu ai zanci darajar kasancewata musulmi ki dauki wayata kiji abinda yake tafe dani ko? kinsan halin dana shiga saboda haka? Inda nasan gidan da kike aure wallahi da tuni kin ganni " Cikin damuwa Mamy ta lumshe idonta sannan ta bude tace"Ma'aruf inajin ka meyafaru?" Kai tsaye yace mata"ina Ruqayya? Inason ganinta" Cikin mamaki tace"au dama kadamu da'ita ne?" Alhaji Ma'aruf ya runtse idonsa, yace" Maryam, yanzu ba lokacin tone tone bane,inaso naga Ruqayya " Mamy yace"Ina wajan aiki,Mawahib tana gida" Alhaji Ma'aruf yacika da mamakin Mamy, har abada halinta mai kyau bazai canza ba,gashi de sunan mahaifiyar sa yarinyar taci, amma shi kai tsaye yake kiranta da sunan,amma gashi Maryam har wani suna daban tasaka mata,hakan yana nufin har yanzu tana ganin darajar mahaifiyar sa,tunda gashi ta kasa kiran sunan kai tsaye, yayi ajiyar zuciya yace"toki yi mata magana tahada kayanta gani nan zuwa" Cikin mamaki Mamy tace"bangane ba" Yace"idan mun hadu zanyi miki bayani,tahada kayan de zanzo har gida In dauketa" Yana fadin haka yakashe wayar. Sister Bilkisa tace"meyake faruwa kuma?" Mamy tafada mata duk yanda sukai dashi, sister Bilkisa cikin mamaki tace"kode yaji labari ne za'a aurar masa da yarinya?" Mamy yace"Ina zansani sister Bilkisa?amma bana tunanin haka gaskiya" Sis Bilkisa tace"to ai zama bai ganki ba, ki kama hanya kije gidan, idan kunhadu dashi duk wacce za'a yi sai ayi" Cikin sauri Mamy tace"to shikkenan" Daga nan ta dauko jakarta, tacire dan qaramin hijab dinta na ma'aikatan asbiti, tasaka wani babban hijab me tsawo shima fari, sannan tanufo gida. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Direban taxi yana zuwa inda aka yi masa kwatance ta waya yayi parking sannan yajuya ya kalli su Alhaji Ma'aruf yace "Alhaji munzo" Alhaji Ma'aruf yace"Okay nan suka kwatanta ma?" Dan taxi yace"eh nan ne gidan Alqali" Alhaji Bala yayi masa godia sannan yadauki kudi meyawa yabashi, bayan yatafi suka qarasa wajan Musa megadi Alhaji Ma'aruf yace"kashiga gidannan kace musu sunada baqi a waje" Musa megadi yashiga ya'isar da saqon,nan take Alhaji khaleed mahaifin Nabiha yamiqe yabiyo Bayan Musa, yana zuwa ya gansu su biyu atsaye abakin get,yana ganin Alhaji Ma'aruf yaga kamar Mawahib atare dashi, Alhaji khaleed yamiqa musu hannu yace"baqin namu ne? sannunku da zuwa,ku qaraso mana,ku qaraso daga ciki..." Alhaji Ma'aruf yace"to mungode" Daga nan suka shigo cikin gidan, kai tsaye suka wuce part din Hajiya kilishi, har zuwa lokacin gaba dayansu suna nan a zaune,Hajiya kilishi kuwa takafa ta tsare tana so taga waye yayi mata katsalandan acikin rayuwar d'anta,Captain Aryan yana ganin Alhaji Ma'aruf yasaki wata irin ajiyar zuciya,Alhaji Ma'aruf kuwa cikin fara'ah yafara bawa duka mazan falon hannu suna gaisa wa, sannan ya zauna yamaida kallonsa ga Alqali ganin shine babba a cikinsu, yace"Alhaji kuyi haquri nasaku kuna jirana,ni Sunana Alhaji Ma'aruf,dan asalin jigar Kebbi,kuma nine wanda na aurawa 'yata Captain Aryan bisa shaidu da wakilai kamar yanda addini ya tsara,amma nayi hakanne badon komai ba saidon ganin nine silar dayasa yaron nan yashiga matsala,kuma inada tabbacin yata batazata ta6a yimasa gori akan batun haihuwa ba,amma...ina roqon ku da kuyi haquri kuyafemin, haqiqa nasan nayi kuskure,sannan yarinya ta na bashi ita halak malak, saide in shine yaga bata yi masa ba to zai Iya sauwake mata,amma amatsayina namai laifi Ina qara baku haquri amatsayin ku na iyayensa,idan har baku haqura ba to duk hukuncin dazaku min kuyimin inde zaku huce akan abinda na muku" Alqali yayi shiru yanajin dogon bayanin da Alhaji Ma'aruf yayi,gaba daya sai jikinsa yayi sanyi,ada yayi niyyar yashiga qara tareda duk wanda yayiwa dansa aure ba tareda saninsa ba,amma bayan yaji bayanan mutumin sai yaji bazai Iya masa komai ba,yasaki ajiyar zuciya yace"to Alhaji Ma'aruf munji bayanin ka, kuma mungode, adade nayi tunanin ko duk abinda na mallaka zai qare to sai inda qarfina yaqare akan mutumin da yayi min auren d'ana, to amma bayan naji bayananka saina gamsu da maganganunka,haka ubangiji ya tsara masa,Allah yasa hakane yafi Alkhairi, yanzu Ina yarinyar take?" Alhaji Ma'aruf yadauko wayarsa daga aljihu yace"bari nakira inji inane address din gidan sai muje daku a dauko yarinyar"(🙆🏻‍♀️) Cikin sauri yadokawa Mamy Kira,bugu biyu Mamy data dawo daga wajan aiki tadauka, Alhaji Ma'aruf yace"gani akano, inane address din gidan" Mamy tace"akawoka gidan Alqali,duk wanda ka fadawa yasan gidan" Cikin tsananin mamaki Alhaji Ma'aruf yace"a a, gidan Alqali kuma? to ai Ina cikin gidan" Yajuya ya kalli mutanan falon daduk suka zubo masa ido suna kallonsa yace"yanzu dan taxi yace mana nanne gidan Alqali, koba nan ne gidan ba?" Ya qarasa magana yana kallon yan falon Gaba dayansu sukace" Nanne" Alqali ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"kafada musu suzo cikin gidan Alqali yanzu yanzu part din matar Alqali" Alhaji Ma'aruf yacewa Mamy "to Ina cikin gidan Alqalin,gani ga mutanan gidan kuzo keda ita, Ina jiranku" yana fadin haka yakashe wayar Mamaki yakama Mamy, kamarya suzo gidan Alqali? to Ma'aruf yariga yazo gidan kenan kome? waye yafada masa a gidan take? Tadaga kanta ta kalli Mawahib datake tsaye a gaban tv tana qoqarin kashe kayan kallo, tana sanye cikin doguwar riga abaya mai kyau, tace"ke zomuje part din yaya kilishi" Cikin sauri Mawahib tace"Mamy lafiya?, inaso ne inje gidansu Jiddah munyi waya tacemin zasu tashi sunkoma gombe dazama gaba daya" Mamy tace"muje nace" Babu musu tabiyo bayan Mamy suka tafi part din Hajiya kilishi,tun abakin qofar sukaga takalma dayawa hakan ya tabbatar wa Mamy mazan gidan suna ciki kenan, da sallama Mamy tashigo falon,Mawahib ma tashigo, gaba d'aya sai kallo yakoma kansu,cikin sauri Hajiya kilishi tatashi tsaye tace"Rainin hankali....idan an'isa in nutse anan,ni za'a rainawa hankali?" Cikin tsawa Alqali yace"Kilishi meyake damunki ne?" yajuya ya kalli Mamy dabai san dalilin zuwansu ba yace"maryam meyake faruwa?" Kafin Mamy tabawa Alqali amsa Alhaji Ma'aruf yace"Alhaji ai itace wadda nayi waya da'ita yanzu,itace mahaifiyar 'yata Ruqayya wadda na aurawa d'anku Captain Aryan...." Cikin sauri Ashraf yatashi tsaye yace"What....?" Gaban Captain Aryan yayi wata irin muguwar fad'uwa,ya runtse idonsa afili ya furta "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un,Hasbunallahu wa ni'imal wakeel...,ko ba'a fada masa wacece Ruqayya ba yasan Mawahib suke nufi tunda itace yarinyar Anty Ma-my" Mamy tanajin furucin Alhaji Ma'aruf,saita tuna lokacin da Captain Aryan yake fada mata wani mutum yamasa aure da 'yarsa,ta tabbata de dolen dole sai yarta ta auri jinin Yaya kilishi, cikin tsananin damuwa tadafe kanta da hannunta (🤦🏻‍♀️) Mawahib data gama rikicewa tana ganin abu kamar a film,cikin ranta tana fatan ace bade da'ita Ruqayyan sukeba, cikin rawar murya tace"Mamy meyake faruwa?" Alhaji Ma'aruf ya kalleta, tsananin kamar datake dashi shine yasake tabbatar masa da cewa tabbas itace Ruqayyansa yace"Ruqayya nayi miki aure,na aura miki Captain Aryan nasan insha Allahu....." Kafin yagama magana Mawahib takoma bayan Mamy da sauri ta rirriqeta,lokaci daya hawaye ya wanke mata fuska,jikinta yadauki rawa tafara girgiza kanta alamun rashin yarda Hajiya kilishi ta kalli Mamy wadda har yanzu hannunta yana goshinta takasa dago kanta, cikin masifa tace"Maryam kinji dadi....wato dana nuna miki baza'a bawa Ashraf Mawahib ba saida kika koma kikai kutun-kutun kika liqawa Aryan ita, to billahillazi bazai iyu ba" Tana fadin haka tanufi Captain Aryan wanda kansa yake sunkuye yanaji kamar a mafarki wannan abubuwan suke faruwa, tana zuwa takama hannunsa tatashe shi tsaye ta nuna masa Mawahib tace"gatanan saketa yanzu yanzun nan, maza yimata saki uku"(😳🙆🏻‍♀️) Alqali dayake zaune yana ganin ikon Allah yayi murmushi ya kalli Captain yace"kai Aryan....dauki matarka kubar gidannan" Mawahib tanajin wannan furucin tasaki ihun kuka ta qanqame Mamy tana cewa"Mamy zan mutu,wallahi banason sa,bagarama Yaya Ashraf dinba..." Hajiya kilishi ma tanajin furucin Alqali tayi maza tazo bakin qofar tatare tace"Babu inda zasuje saiya saki wannan yarinyar" Alqali yatashi tsaye yanufi qofar,Alhaji khaleed da Alhaji Isa ma suka Isa qofar, Alqali yasa hannu ya matsar da kilishi gefe,yakamo hannun Mawahib yasaka acikin tafin hannun Aryan,sannan ya kalli Aryan d'in yace" d'auki matarka ka koma bakin aikinka" (Kai wata dramar Sai a gidan Alqali,yau Hajiya kilishi tana ganin ikon Allah tsagwaron sa😂😂) mutara zuwa gobe🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Tsawar daya matane yasa tajuya cikin dakin da gudu tana sakin wani irin kuka mai ciwo. Jakar kayanta data futo dasu daqyar,gaba d'ayansu guda ukun yadagasu da hannusa guda daya,ya watsa mata su cikin dakin sannan ya rufe kofar yajuya cikin dakinsa cikin damuwa,yana zuwa Yafada kan gadon sa tareda hargitsa sumar kansa yana Runtse idonsa, lokaci daya yaji wani ciwon kai yana neman kamashi, bayason damuwa kokadan. Cikin kuka tajanyo wayarta takira Mamy amma takasa cewa komai banda kuka babu abinda take, daga dayan 6angaren Mamy tayi shiru tanajin yanda Mawahib take kuka,adede lokacin tana kitchen, tasaka hannu takashe gas din sannan tabar kitchen din takoma dakinta ta zauna, bata hanata kukaba saida tabarta tayi kukan sosai, sannan tace"ya'isah haka" Sai a lokacin Mawahib takejan zuciya alamun taci kuka ta qoshi,Mamy ta dafe goshinta alamun damuwa, ta tabbatar akwai abinda yake faruwa a gidan yaran, cikin sigar lallashi tace"meyake faruwa?" Saida tarage kukanta sannan tace"Mamy ni gida zan tafi,Yaya Captain zai kasheni,mugune...." Mamy tanajin wannan furucin gabanta yafadi,tayi tunanin ko takurawa yarinyar yake ta 6angaren auratayya,to amma kuma tana shakku akan hakan,cikin rashin sani tace"mekike nufi? meya miki?" Cikin muryar kuka tace"yana takuramin,ni banason yana shiga harkata,ni kawai kowa yayi rayuwar sa,amma saiya dinga cin zalina yana sakani Ina faduwa,ni Mamy nagaji bazan iyaba" Mamy tasaki ajiyar zuciya,tayi tunanin matsalar ta wuce haka, ashe Iya haka ta tsaya,duk da tana cikin dakinta saida ta rage murya sannan tace"Mawahib, keda Captain gaba dayanku nasan halinku ciki dabai, babu wanda zai kawomin qaran dan'uwan sa acikin ku bangane waye marar gaskiya ba,kinyi masa laifi ne?" Cikin muryar kuka tace"Mamy ni banyi masa koma ba,Ina goge kitchen ban shiga sabgar saba yazo yaje far min da goran ruwa,Ina shara yasamin qafa nafadi,menayi masa dazai dinga cutata" Mamy tayi murmushi marar sauti,gaba daya cikin bayanan na Mawahib tagama gane cewa da niyya Captain din yayi mata haka,soyake ta kula shi amma Kuma taqi kula shi ta nuna masa itama miskilar kanta ce,tasan cewa tun yana yaro bayason raini,Ashraf ma daya bashi Yan awanni kokadan bayason yaji Ashraf yana cewa ya girmeshi yanzu saisu fara musu har aje Ana tambayar kilishi waye Babba,gaba daya su biyun daga Mawahib din har Captain din kowa Yana buqatar ajashi ajiki a lallasheshi,shide dama tun yana yaro tasan cewa bai iya lallashi ba bare tasaran zai lallashi Mawahib,Shima kansa lallashin yakeso. Cikin nutsuwa tace"Mawahib mekika dauki aure ne?" Saida taturo dan qaramin bakinta gaba sannan tace"to Mamy dole ne saiya shiga harkata? kowa yayi rayuwar sa" Mamy tace"karna sakeji kin fadi haka, kina qarqashin ikonsa ne yanzu,Sai abinda yace dake, duk cikin bayanin ki banji inda kikace kin gaishe shi ya mareki ba,banji inda kikace haka kawai kina zaune yazo ya rufeki da duka ba,Mawahib tayaya zakiga yayanki bazaki gaida shi ba? Kuna rayuwa gida daya kubiyu dole zaki gaishe shi,dole zaki tambayeshi koda abinda yake damunsa, idan kinzo gidama Abbanki a ranar zai maidake" "to Mamy dole ne hakan? ni banason shi, banason auren nan,dole ne sai nayi masa magana?"(🙆🏻‍♀️) Kai tsaye Mamy tace"dole ne,kishiga hankalinki Mawahib banason shirme,kina tunanin zai zauna ya dinga lalla6aki ne kamar Abbanki? Kece zaki masa biyaiya kimasa abinda yakeso saboda aljannarki kike nema,daga yau, gaisuwa kullum safe da yamma,girki kullum Kuma ba Kala dayaba,shara kullum mopping kullum, kinji abinda nace? Karna sakejin wata matsala makamanciyar wannan kuma" Qit....takashe wayarta, Mawahib ta Kalli wayar da idonta,itace zata tambayi Yaya Captain meyake damunsa? tayaya? mutumin da inde ta zauna kusa dashi jikinta yadinga karkarwa Kenan ta'ina taga qwarin gwiwar yimasa magana?. ****** Washegari da sassafe yadawo daga motsa jiki, yana Sanye cikin Riga wacce take hade da hula, sai dogon wando qafarsa tana Sanye cikin farin kambos,yana shigowa gida dadan sauran gudunsa adede lokacin Nabiha tagama share musu compound din gidan gaba daya,kallo daya yayi mata yadauke kansa, Nabiha dabata lura dashi ba,kamar daga sama taji yace"kikai min abinci anjima" Bai saurari abinda zata fada ba yawuce ciki,cikin sauri tabi bayansa da kallo tasaki wani irin murmushi sannan ta wuce part dinsu. Darana takai masa abincin kamar yanda ya buqata, tajuya zata futo yace"zonan" Babu musu tadawo ta zauna aqasansa, shikuma yana zaune akan gadon su, ya kalleta batareda da damuwa ba yace"Nabiha nasan bakyason auren nan,dole ce za'a miki,toki kwantar da hankalin ki Nima banaso,bazan 6oye miki ba, idan nasamu yarinyar danake so zan aureta,kema nabaki dama daga Nan zuwa lokacin da za'a liqa wannan aure,idan Kinga wani Wanda kikeso, toki sanar dani namiki alqawarin dakaina zanje nasamu su Daddy Nafada musu a dakatar da maganar auren nan,idan Kuma yanzu ma kinada Wanda kikeso toki sanar dani,Sai afasa wannan hade-haden"(🙆🏻‍♀️) Nabiha tayi shiru tafara tunani cikin sanyin jiki,itade tasan cewa tun tashinta ba kula wasu samari takeba,asalima yanda gidansu yake da tsaro da wahala kaga saurayi yazo yana Neman su,abinda tasani shine tatashi da soyaiyar Yaya Ashraf acikin ranta, komai yayi birgeta yake,saide shi hankalinsa yana kan Mawahib,yanzu idan ta nuna masa batada saurayi kamar zai dinga yimata kallon wacce aka liqa masa yadinga hantarar ta,cikin dabara tace"inada saurayi amma bai shirya aure yanzu ba,makaranta yakeyi" Cikin farinciki Ashraf yace"Alhamdulillah,tokinga ta kwana gidan sauqi,idan Naga yarinyar danake so,zan aureta,kema duk lokacin daya gama makarantar kifadamin, zan sauwaqe miki kije kuyi aurenku" Mamaki yakama Nabiha,yanzu harya yarda da wannan qaryar data shirya masa? tayaya zata yarda yarabu da'ita bayan ya aureta? Cikin ladabi tace"to Yaya Ashraf nagode" Cikin sauri Shima yace"ki godewa Allah, zaki Iya tafiya" Babu musu tayi masa sallama tafuto daga dakin. ****** tsawon sati biyu Kenan Mawahib bata sake saka Captain a'idon ta ba, Bata futowa sai taji baya gidan,zata futo ta dauki lemo ko madara da biscuit takoma dakinta, Shima Koda wasa bai nemetaba,yauda daddare daqyar tagama cin biscuit din,saboda ya'isheta, Kuma Mamy tace ta dinga yiwa Yaya Captain girki, ita Kuma qyashin yimasa girkin take,amma dole gobe zatabi umarnin Mamy tayi,kodan cikinta ma, wannan cin biscuit din babu inda zai kaita,shiyasa tayi sauri tayi wanka sannan tasaka kayan bacci ta kwanta saboda tana son tashi da wuri tayi gyaran gida tayi girki. Acan dakin Captain kuwa bayan yagama abinda zaiyi Shima yayi shirin bacci, wayarsa tayi qara yana dubawa yaga Ashraf ne, cikin sauri yadauki wayar, Ashraf yace"yanaga kadauki wayar da sauri haka? Aryan anya kuwa? Kode baka zama da matarka ne kullum Ina kiranka saikayi caraf kadauka kod'an irin Ina zuwa zan kiraka dinnan babu?" Cikin taqaici Captain Aryan yace"dan Allah kadena min maganar yarinyar Nan Ashraf,ni gaba daya na manta da'ita ma,tunda nabata abinci shikkenan na sallameta"(😲) Ashraf yayi murmushi yace"kayi haquri mana,koba dan itaba, kodan Anty Mamy" Captain Aryan yace"yanzu haka zanyi ta zama da'ita Kenan? Banson ganinta wallahi"(🙆🏻‍♀️) Ashraf yace"to ya zakayi? Nima wallahi banason ganin Nabihan nan,but ni matsala ta tawuce, nace Koda bayan bikinne zan sauwaqe mata ta auri Wanda takeso" Cikin sauri Aryan yace"yes hakan yayi,Nima zanyi tunanin Yaya zanyi da yarinyar nan" Ashraf yace"kaikam Mawahib aita zame ma dole,zaka saki yarinyar Anty Mamy ne Kuma kadawo gidannan kaje wajanta? aikai auren zobe aka muku,nine de bazan dauki wannan auren nasu ba"(😲) Captain Aryan yace"alaqa ta da Anty Ma-my daban,wannan yarinyar Kuma banda alaqa da'ita, saboda ita har yanzu Momy bata daukan kirana" Cikin sauri Ashraf yace"what...? Amma Meyasa baka fadamin ba?" "bansan tadama hankali ne,nabari ne idan nazo bikinka Sai muyi magana da'ita" Ashraf yace"to shikkenan Nima zan bata haquri kafin lokacin insha Allah,wajan aiki zan tafi gobe da sassafe Nima, but kafin nawuce zanje nakai mana dinkunan mu insha Allah" Captain Aryan yace"nima kwanciya zanyi, zanfita aiki da wuri gobe,sauqi nama kwana biyu Bata damuna da wannan kukan nata. Ashraf yayi murmushi sannan yace"Bye" Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Sassafe tatashi ko dogon hijabin datayi sallah dashi bata cire ba,tafuto Kai tsaye tawuce kitchen tashareshi tayi mopping, sannan tafara shirya abincin breakfast, ta dauki dankalin turawa tahada Chip salad,da pancake, sai tea Wanda tasaka kayan qamshi aciki sosai,tayi sauri tagyara wajan dining table din ta gogeshi, sannan ta dauko abincin ta jerasu akai, takoma kitchen tasake gyara shi, gashi de bawani girkin kirki tayi ba amma duk qamshi yacika gidan. tadawo falo ta share tafara mopping. Adede lokacin Yafuto daga dakinsa yayi masifar kyau cikin uniform dinsu na sojoji,kamar kullum yar qaramar bindiga tana soke a aljihun wandon sa nabaya,tun kafin yasako qafarsa kan Stairs yaji wani qamshin girki yadaki hancinsa,Mawahib kwata kwata bataji futowar sa,tasaka mopper akan stairs din zata fara gogewa taji alamun takun mutum,bata tsammaci ganinsa ba hakan yasa tanajin takun ta zabura cikin tsoro,hakan yasa santsi ya dauketa zata zube a wajan,kamar wasa tajita acikin jikinsa, shi kansa baisan menene ya fusgeshi ba harya tareta daga faduwar da zatayi,Mawahib kuwa cikin tsoro taqi bude idonta, kawai jira take yasaketa tafadi a wajan kamar yanda yayi abaya. Batare da tunanin komai ba Captain yatsaida ta, saida yaga ta tsaya da qafafunta sannan yasake ta, yazo ya ra6a ta gefenta zai fice daga falon,fuska babu alamun wasa yace"kikula" Abinda yace da'ita Kenan yakama handle din qofar falon zai fice,Mawahib dabata gama dawowa daidai ba daga tsananin mamakinsa, ganin zai fita cikin sauri tace"ina kwana?" Baice da'ita uffan ba yabude qofar falon,tasake bin bayansa da kallo tace"break fast..." Kai tsaye yace"no" Daga haka ko waiwayen ta baiyi ba yafice cikin sauri,Sai dirin motarsa taji alamun yafice daga gidan. Tasaki ajiyar zuciya tayi sauri ta qarasa aikin datake, sannan ta hau Sama tayi wanka,ganin baya gidan yasa tasaka wata yar 6ingilar Riga marar hannu,gaba daya tsawon rigar Iya gwiwar ta tatsaya, tawuce ta bararraje a dinning tafara yin break fast dinta cikin kwanciyar hankali tanaci tana danna waya,tunda tazo gidan yaune Karon farko data ta6a girki,kullum batada aiki saicin lemo da biscuit,shiyasa taci abincin sosai,tatashi takoma sama tasako zumbulelen hijabi akan rigar jikinta, hijabin dogo ne har qasa,ta dauki sauran abincin data rage takaiwa megadinsu maisuna David,bayan tagaidashi ta bashi abincin,cikin girmamawa ya kar6a,saitayi mamakin yanda yake bata girma kamar wata matar wani, harta tafi David yana binta da kallo yana sake jinjina wa oga Aryan akan yanda ya murji amarcinsa hankalinsa kwance(😲) tunda sukazo gidan shida Madam kullum suna ciki saiyau yata6a ganin tafuto,ya tabbatar wannan yarinyar yanda ta keda kyannan Sai yanda tayi da oga Aryan. Zuwansa wajan aiki da awa uku,suka shirya fita ganin wani daji zasuga yanayinsa kafin atura rundunar sojoji zuwa dajin. Futowa sukai susu ukun suna tafiya zuwa ma'adanar Helicopter dinsu, ga wasu sojoji a bayansu kowa fuskarsa a daure kamar Wanda aka musu albishir da mutuwa. Tun kafin su qarasa wajan helicopter din mai launin army green driver ya tadashi, babu wata-wata suka shige ciki duka su ukun. Tunda suka shiga idon Captain Aryan yana waje,yana ganin yanayin yanda hanyar take,basu yi tafiya mai nisaba suka qaraso dajin mai cikeda duhuwa dakuma bishiyoyi. Jirginsu bai sauka ba,kawai a'iya wajan yake zagaye. Major Abdullahi ya Kalli Captain Aryan yace"Captain wannan ne dajin damuke tunanin yana cikeda yan bindiga" Cikin zafin nama Captain Aryan yace"Okay sir..." Colonel Abdul wahab yadora da fadin"dole Sai kunyi taka tsantsan dashi,kamar yanda labari yazo mana suma labari zaije musu zamu kawo musu hari" Cikin biyaiya Captain Aryan yace"angama Sir" Daga Nan suka Bawa driver umarnin Yajuya dasu. Bayan sunkoma kai tsaye office dinsa yawuce yadauki takardar taswirar dajin yana sake qarewa wajan kallo ta yanda shida rukuninsa zasu cinmusu kafin yan bindigar su ankara. Tsawon sati uku Captain Aryan yadauka yana sake horar da rukunun sojojinsa dayake aiki dasu, saboda dajin dazasu fuskanta, har zuwa wannan lokacin Mawahib kullum saita tashi da safe tagyara gidan tayi masa girki amma ko saudaya bai ta6aci ba,tun tanayi dashi hartazo ta daina tadinga dafa wa itada David Maigadi. zaiji qamshi yacika gidan amma acewarsa bazaici jagwalgwalon taba. Adede lokacin bikin Ashraf yazo,bai tafi da wuri ba kasancewar kullum yana bawa Yara horo, Sai ranar daurin auren yaje, tunda yaje kwata-kwata basu zaunaba shida Ashraf din,duk da bawani farinciki sukeda auren ba, hakan bai hanasu yin kyauba,farar shadda suka saka tareda babbar riga,komai iri daya sukasa, tundaga kan takalmi har hula da Agogo da links din dayake hannun rigar, babu Wanda yake gane waye angon a cikinsu,acikin masallacin suka zauna da sauran abokan su yan unguwa,har limamin unguwar yadaura auren Ashraf da Nabiha Akan sadaki naira dubu dari lakadan ba ajalanba. Basu samu shiga gidaba Sai can dare wajan qarfe goma da rabi zuwa lokacin mutanan gida baqi sunyi sauqi Sai Wanda baza'a rasaba,kai tsaye part din Mamy suka shiga,tana zaune tana kallo afalo taci kwalliya cikin leshi Riga da zani Sai walwali take kamar ba dare ba,falon nata tsaf Sai tashin qamshi yake,ita kadaice takeyin kallon, Sai baqi Yan kwana datayi yan'uwan mama Sadiya, suma Kuma suna dining tazuba musu abinci sunaci, tana ganin shigowar su Ashraf da Aryan ,cikin fara'ah tace"A a angwaye" Ashraf yayi murmushi, atare suka hada baki suka gaisheta,Captain kuwa fuskarsa babu murmushi,daga gaisawar nan yayi qasa da kansa(😂) Ashraf yace"Anty Mamy yunwa mukeji" Mamy tayi murmushi tace"to bari insama muku wani abu sai akai muku daki,ahado muku da coffee ne?" Ashraf yasake bata amsa yace"eh ahado" Ta miqe tsaye zata wuce kitchen ta Kalli Captain Aryan da kansa yake qasa Koda wasa yaqi kallonta,cikin ranta tace Allah karimun waheedun yau nice nazama dodon Aryan,tun ranar da Mawahib takirata tana kuka Bata sakejin kansu ba kosun shirya kansu kokuma sunacan sunacin mutuncin juna oho musu,tace masa"Captain ya Abuja?" Fuskarsa babu yabo babu fallasa yace"Alhamdulillah" Daga nan baisake cewa uffan ba. Ashraf yace"Anty Mamy kicewa mama Sadiya Wanda suka raka yarinyar Nan su zauna su kwana tareda ita,zan kwanta anan tareda Aryan" Cikin fahimta Mamy tace"to shikkenan bari in kawo muku abincin saina wuce part dinta Infada mata" Captain Aryan yana jinsu,yana ganin shigewarta kitchen yatashi tsaye yace"tashi mutafi" Ashraf yayi murmushi yatashi suka futo,part din Hajiya kilishi suka nufa tundaga bakin qofar falo sukejin hayaniyar mutane, alamun akwai sauran Wanda basu kwanta ba, Hakan yasa suka juyo suka koma cikin dakinsu, suna zuwa Ashraf ya kwashe da dariya yana qoqarin cire babbar rigarsa,ya Kalli Captain Aryan cikin dariya yace"wai Kai kunyar Anty Mamy kakene?" Captain Aryan ya yatsina fuska yace"kunya Kuma?" Ashraf yace"ni zaka rainawa wayo? tunda mukaje kayi kidis dakai kamar wani baqo,saini kadai nake mata magana " Cikin damuwa Captain Aryan yace"niba kunyar ta nakeji ba" Ashraf yace"kunya kakeji mana,kazo gaban surukarka, tun yanzu kana irin wannan kunyar idan kunfara amarci gidan zaka daina shigowa Kenan?" Captain Aryan yadaure fuskarsa tareda girgiza kai yawuce toilet domin watsa ruwa,bayajin har abada wannan abun da Ashraf yake fada zai faru tsakanin shida wannan yarinyar, yana shige wa toilet adede lokacin Mamy takawo musu abincin sannan tayiwa Ashraf saida safe tafice daga dakin. Sama Sama sukaci abincin sannan Ashraf ya kalli Aryan yace"kaga saqon dana turawa Mama Sadiya yanzu" Yafadi haka yana bawa Captain Aryan waya. Captain Aryan ya kar6i wayar yafara karanta saqon a fili kamar haka "Mama nasan Nabiha batason auren nan,Nima kuma kinsan hakane,to tasanar dani akwai Wanda take jira,Ina miki alqawari babu abinda zai samu Nabiha,bazan ta6a miki yarki ba,yanda kuka kawota haka zata auri Wanda takeso, daga Ashraf" Captain Aryan yana gama karantawa yace"eh tura mata,dansu tabbatar wannan aure auren dasuka qulla mana babu inda zaije, ko Nima in turawa Anty Ma-my irinsa?" Ashraf yace"karka tura,gara nawa hadin da sauqi akan Naka, kaifa ta ko'ina adaure kake, baka Isa kasaki yarinyar Anty Mamy ba, nidin de daba dogon mutunci nakeyi da Nabihan ba to zan'iya tura musu, tashi muje wajan Momy" Haka suka nufi part din Hajiya kilishi. Alokacin da Mama Sadiya taga saqon saitayi murmushi ta nunawa Mamy, itama ta karanta, Mamy tayi dariya tace"to bari mugani ayi Zaman auren, tunda kikaga haka da Aryan din sukai wannan shawarar, bazai turo ba sai Aryan yasani, duk su biyun zamu gauraya ne, dani suke zancen" shabiyu saura,suka qarasa part dinsu, Alqali yana zaune afalo yana duba hisnul Muslim yaga shigowar su, Kai tsaye wajan sa suka nufa tun a wajan daurin aure rabon su dashi, kasancewar ko acikin duhu suke zai banbance su shiyasa Kai tsaye ya Kalli Ashraf cikin rashin wasa yace"mekake baka tafi gidanka ba?" Cikin ladabi Ashraf yace"Daddy dama Naga akwai baqi a gidan ne dangin mamanta,shine nace su kwana tare Nima zan kwanta anan tareda Aryan" Jin wannan bayanin nasa yasa ya gamsu,baisake cemasa komai ba Yajuya wajan Aryan yace"yaka baro iyalin naka?" Captain Aryan yace"Lafiya kalau Daddy" Alqali yace"babu damuwa deko?" Kai tsaye yace"babu komai" Alqali ya jinjina kansa sannan yace"Kariqe yarinyar nan amana,nasan babu Wanda yakeson auren acikin ku,amma karka duba wannan,Koda yaushe karka manta mahaifiyar ta ta rungume ku a lokacin da bakwa tareda taku mahaifiyar,saboda haka ko bayan raina karka kuskura kasani hannunta" Lokaci daya jikin Captain yayi mugun sanyi,cikin sanyin jiki yace"to Daddy" Alqali yace"zaku Iya tafiya" Cikin sanyin jiki suka nufi dakin Hajiya kilishi,tana zaune adakin ita kadai tagama saka turaren wuta adakin Kenan, kasancewar ba'a Dade da gyara mata dakinba sakamakon baqi dasuka wuni adakin. Zama sukai agefen gadon sukai shiru,Hajiya kilishi ta Kalle su tace"Lafiya?" Ashraf yace"Momy ashe fishi kikeyi da Aryan" Tajuyo ta Kalli Ashraf tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi, sakoka yayi agaba Kenan kazo Kamin duka saboda Ina fishi dashi?" Cikin sauri Ashraf yace"Momy bahaka bane bafa...,kiyi haquri dan Allah,Kinga fa duk ya rame wallahi,ni rakoshi nayi yabaki haquri" ya qarasa maganar yana zungurin qafar Aryan Cikin sauri Aryan da yaji abinda Ashraf yamasa ya kalleta yace"Momy kiyi haquri idan nayi miki laifi kiyafemin,banajin dadi idan banji muryar kiba,fishin ki zaiyi tasiri akaina har hakan yashafi aikina" Cikin 6acin rai kilishi tace"au cewa kake idanma Kamin laifi? Saboda angama shanyeka ko Babana? bazan ta6a Jin sauqin zuciyata ba harsai karabu da yarinyar Maryam,har abada bana fatan ace jinina yana auren jinin Maryam,karka sake Kiran wayata inde kasan baka saki yarinyar nan saki uku ba,naji dadi da Allah yasa ba haihuwa zakayi ba bare harka hada jini da wannan yarinyar...." jin kalaman nata sunyi tsauri dayawa yasa Ashraf yafara hawaye, cikin sauri yafice yabar dakin. Captain Aryan idanunsa suka kada sukai jajir amma shi baiyi kukan ba, cikin ladabi yace"to Momy zanyi yanda kikace,amma kiyi haquri kiyafemin" Yana fadar haka Yafuto daga dakin nata jikinsa a mutuqar sanyaye,Alqali baya falon,Kai tsaye saiya wuce dakinsu,yana zuwa yaga Ashraf har lokacin yana goge hawaye,zama yayi kusa dashi cikin dauriya yace"wai kukan menene Ashraf?" Hawayen idonsa yagoge gaba daya sannan yace"toya zakayi? Ya sukeso kayi? shi Daddy yace karka saketa,ita tace saika saketa saki uku,yanzu saboda Mawahib har Momy zatayi alfahri da rashin haihuwar ka saboda karka hada jini da'ita? Ni bazan iyajin wannan fadan nataba,zuciyata saita buga" Ya qarasa maganar wani Hawayen yana zubo masa,Captain Aryan ganin Ashraf da gaske de kukan yake hakan yasa yadaure yazo kusa dashi yafara cewa "kayi shiru mana,aini bana kukan,kamar mace kana kuka Ashraf to waye zai lallashi Amarya bayan sati daya?"(🙈🙊😂) Cikin sauri Ashraf yadauki fillo yadoka masa shikuma yana dariya,dahaka yayi nasarar lallashin Ashraf harsukai warware kamar babu abinda yafaru. Washegari da yamma yayi shirin komawa Abuja,sunyi kyau sosai cikin baqin yadi Mai tsadar gaske,Sai hasken fatarsu yasake futowa sosai,kana ganinsu kaga angwaye,kafin yatafi sukaje wajan Hajiya kilishi,Ashraf Sai dauke Kai yake, suna gaisheta ya kawar da kansa gefe saboda abunda yafaru jiya da daddare. Cikin sanyin jiki Captain yace"Momy zan wuce kimin Addu'ah" Daqyar tabude baki kamar bataso tace"Allah ya tsare hanya" Cikin sanyi jiki yace"Amin" Yasaka hannu a aljihun rigarsa ajiye mata damin kudi guda biyu, sannan yasake bata haquri,suka futo daga dakin. a gurguje Ashraf ya rakashi part din Mamy,ta dauko masa wata gumba dataji hadi irinna Yan maiduguri tasaka acikin baqar leda ta bashi tace yakaiwa Mawahib,cikin ladabi ya kar6a da hannu biyu,saida yaga tajuya sannan ya ajiye mata kudi dami daya akan kujera daga Nan suka futo. abakin get ya hadu da iyayen nasa maza,yayi musu sallama, Alqali yasake jinjina masa akan ya riqe Mawahib da kyau, sannan suka shiga Mota da Ashraf yakaishi Airport shikuma yajuyo gida. Sai qarfe shida na yamma yasauka a Abuja, suna Sauka Ana Kiran sallar magrib. David yana ganin dawowar oga Captain yayi sauri yabude masa get cikin rawar sauri, saboda yasan yau bai kwana agidaba. Matar gidan kuwa batasan baya nanba,idan yana nan dinma Sai suyi kwana da kwanaki basu haduba, shiyasa yanzun ma Batasan cewa yaje kano ya kwana ba,Kuma suma yan gidan babu Wanda yace mata Yaya Captain yazo gida. Yana Bude falon nasu wani qamshi mai dadi na turaren wuta da air freshener yadaki hancinsa,qamshin yamasa dadi hakan yasa ya lumshe idonsa sannan yabude kai tsaye yahaye Sama ya shige dakinsa, zubewa yayi akan gadon sa yana maida gajiya,saida yahuta sosai sannan yakira Yan gida Yafada musu yasauka,fridge din dake cikin dakin yabude yadauki ruwa yasha sannan yaje yayi wanka yadauro alwala yazo yagabatar da sallah sannan ya zauna yana azkhar. Yadade a zaune har wajan qarfe tara nadare sannan yatashi yacire farar jallabiyar jikinsa yasaka rigar bacci doguwa kalar dark blue,rigar iyakar tsawonta gwiwar sa,daga gaban rigar abude take kana Iya hango gashin dake kwance a faffadan qirjinsa. Yana kwanciya akan gadon yaga ledar da Anty Mamy ta bashi yakaiwa Mawahib,dan qaramin tsaki yasaki yatashi ya dauko ledar batareda yadamu daganin menene aciki ba,Yafuto daga dakinsa yanufi dakinta Adede lokacin tafuto daga wanka, kasancewar tasan baya ta6a shigowa dakinta hakan yasa taqi rufe dakin da key,ta tsaya a gaban mirror tana shafa humra ajikinta. Sauke towel din dake jikinta tayi yayi qasa gaba dayansa,surar jikinta da dukkan dirin jikinta ya bayyana muraran batada komai ajikinta, ta dauki turare spray tana feshe duka jikinta dashi, adede lokacin yaturo qofar dakin zuciyarsa daya yashigo(🙆🏻‍♀️😳🙈) Idonsa bai sauka a ko'inaba Sai akanta,gabansa yayi wata irin faduwa,a zahiri, Kuma agabansa, bai ta6a ganin mace babu kaya ba Sai yau. Idonsa qyam akan nashanunta Wanda suke atsaye cif,ya Kalli bajajjan hips dinta cikin ransa yace"yahaka?, dama natane? dama jikinta ne ba cuko ba?" zai Iya cewa akaf tarihin rayuwarsa bai ta6a ganin yarinya me qananun shekaru dakyan jiki kamar taba. Lokaci daya yaji wani abu zirrrr tundaga qwaqwalwar sa har zuwa tafin qafarsa,duk saiya nemi jarumtarsa yarasa, Sai jikinsa yafara rawa. Mawahib tana dago kanta ta ganshi a tsaye,lokaci daya tasaki wani irin ihu ta tsugunna qasa tareda wawuro towel din data jefar aqasa tarufe jikinta dashi,tuni hawaye suka 6alle mata afuska,ta qudundune a waje daya tana raskar kuka. Kukan tane yasa yagama dawowa hayyacinsa, cikin sauri ya ajiye mata ledar a wajan, Yajuya yafice daga dakin cikin sauri. Yana zuwa dakinsa Yafada kan gado yana maida numfashi kamar Wanda yayi gudu. Lumshe idonsa yayi tareda dora hannu akan sumar kansa yashafa sumar zuwa fuskarsa, haushin kansa yakeji meyakaishi? meya aikata haka? Wanne kallo yarinyar nan zata dinga masa? Cikin sauri yaja bargo yarufe jikinsa dashi har kansa, ya Runtse idonsa tareda karanto addu'ar bacci,cikin ikon Allah bacci ya dauke shi,saide ko awa biyu cikakke baiyi ba yafara ganinta cikin baccinsa a'irin wannan yanayin daya ganta dazu. Cikin taqaici yatashi yazauna tareda sakin wani irin dogon tsaki, afili yace"a a, waiya haka ne?" Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Mrs Usman✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Cikin kuka Mawahib tafara tirjewa tana kiran sunan Mamy, har zuwa wannan lokacin Mamy kanta yana dafe da hannunta, saide ruwan hawaye dayake gangarowa har zuwa tsintsiyar hannunta, tanan ne zaka fahimci kuka take,shikkenan komai yaqare, yau Mawahib dinta ce ta auri dan Yaya kilishi,Ma'aruf ya cuceta duniya da lahira, Abba yayi murmushi yazo saitin kunnanta yace"Maryan shikuma wannan ikon Allahn yaya zakiyi dashi kenan?" bai jira amsar ta ba yajuya yabi bayan Mawahib da Captain Aryan,Captain dayake riqeda hannun Mawahib tana masa ihun kuka jiyaje kamar yadauketa da mari(🙆🏻‍♀️) Alhaji Isah yayi sauri ya tarar dasu,kai tsaye yabude musu mota yakira driver yace"zoka kaisu Airport" Mawahib tanajin maganar Abban ta ta qwace hannunta daga cikin na Captain tatafi da gudu ta rungume Alhaji Isa cikin kuka tace"Abba banaso,dan Allah Abba karka bari yatafi dani,zan mutu Abba" Alhaji Isah yayi murmushin qarfin hali yaja hannunta yasakata cikin mota, sannan yakama hannun Aryan da idanunsa sukai jajir shima yasaka shi a motar sannan ya rufe musu motar yajuya cikin gida yanajin zuciyarsa tana karyewa saboda kukan Mawahib din Acan dakin Hajiya kilishi kuwa,Alhaji Ma'aruf yajuya ya kalli Mamy yace"Maryam meyake faruwa ne?" Mamy batace dashi uffan ba tajuya tatafi part dinta idonnan nata yayi jajir saboda kuka. Alqali ya kalli kilishi cikin daure fuska yace"wuce daki" Haka ta wuce daki saikace mahaukaciya, tayaya ne tanaji tana gani za'a bawa Aryan Mawahib,Aryan din dataci buri akansa shine za'a hadashi da wannan tantiriyar yarinyar dabata da aiki Sai nunawa mutanan gari jikinta,inde tanada iko akan Aryan tosaiya saki wannan yarinyar. Alqali yanemi waje ya zauna sannan ya kalli Alhaji Ma'aruf da Ashraf dasuke tsaye yace"duk ku zauna" Bayan sun zauna ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"Alhaji Maryam acikin gidannan take,sannan mutumin dakuke waya dashi akan maganar auren nan shine mijin ta,wato Alhaji bazamu kira abinda kayi amatsayin kuskure ba,abinda kayi ka kyauta, kuma muma kahutar damu, saboda mu a wajan mu da Ashraf da Aryan duk dayane,kaga wannan yaron dayake zaune?" Yafadi hakan yana nuna Ashraf, Alhaji Ma'aruf yajuya ya kalli Ashraf sannan yace"naganshi Alhaji,amma yanaga haka? yanaga kamar wancen dayan? kode yanbiyu ne Alhaji?" Alqali yace"yanbiyu ne,kuma dukansu 'ya'yanane, wannan shine Ashraf, shine babba,sai Captain Aryan shine qarami,yanzu haka zaman da kaga munyi anan da wannan goro dakake gani nasaka ranar Ashraf ne da Mawahib,Captain Aryan kuma muka yanke shawarar zamu hadashi da yar'uwarsa Asalamiyya,to shine shida dan'uwan nasa suka samemu da wannan maganar cewa kayi masa aure kaji dalilin dayasa muka kiraka domin musake tabbatar wa da abinda suka fada mana,tunda muke da Maryam bata ta6a nuna mana mahaifin Mawahib ba,tun bayanda yan tashin hankali suka faru abaya har Allah yasa aka samu saki a tsakanin ta da mijinta tabar gidannan tsawon wasu shekaru daga baya kuma Allah yayi zata dawo gidannan Isah yaje aka sake daura musu aure, sai muka ganta da wannan yarinya, muka kar6i yarinya muka riqeta da hannu bibbiyu,saboda mun yarda da Maryam mun tabbatar bazata haifi yarinya bata hanyar aure ba,ita bata kawo mana uban yarinya ba,muma Kuma bamu tambayeta ba,to abinda yake faruwa anan gidan shine iyayen yaran Nan mata basa jituwa,hakanne yasa muka dage kan hada auren Ashraf da Mawahib domin asamu sasanto a tsakanin su,to ashe Kai kariga kabata Captain Aryan,amma duk da hakan babu matsala,suje Allah yabasu zaman lafiya da zuri'ah tagari" Gaba daya falon aka amsa da "Amin" Alhaji Ma'aruf yace"ikon Allah,lalle ubangiji yayi hukuncin sa anan,to Allah yabasu Zaman lafiya,amma ni idan Naga wannan dinma ai Sai in dauka Captain Aryan dinne" Ya qarasa maganar yana kallon Ashraf. Alqali yayi murmushi yace"haka suke,tun suna yara ba'a cika banbance suba" Alhaji sammani wakilin Asalamiyya yace"to yanzu Alhaji, Ina maganar saka ranar Asalamiyya da Aryan ta tsaya?" Kai tsaye Alqali yace"Sammani tunda wannan abu yafaru, Ina ganin abar maganar Asalamiyya agefe, idan Captain ya zauna da matarsa sunga halin juna, yaji yanada ra'ayin qara aure,idan har Asalamiyya din tamasa saiyazo su daidai ta idan har zuwa lokacin batayi aure ba" Alhaji Sammani yayi qasa da Kai cikin ladabi yace"to ai ranka yadade atawa shawarar Ina ganin mezai hana Ashraf yamaye gurbin dan'uwansa Captain Aryan,kamar yanda Shima Captain din qaddara tasa yamaye gurbin Ashraf?" Alqali yace"da nayi wannan tunanin,to daga baya saina yanke shawarar Shima Ashraf din zan hadashi aure da qanwarsa NABIHA" Jikin Alhaji sammani yayi sanyi, gashi babu damar dazai kushe Nabiha, kokuma yayi musu da Alqali tunda ga mahaifinta nan a zaune,cikin danne damuwar sa yace"eh hakane,hakanma ai yayi,to Allah yasanya Alkhairi,Allah yabasu Zaman lafiya gaba daya, mu bari muwuce" Alqali yace"Allah ya maida ku gida lafiya" Alqali dayake babban mutum ne Kuma Wanda yake mu'amula da mutane sarai yagane halinda Alhaji Sammani yake ciki,shikuma da hankalin sa bazai iyu yahada dansa aure dawani dangi na kilishi ba,shima kansa haquri yake da'ita tayaya zai sake qoqarin hada iri dasu?(😳🙊🙆🏻‍♀️) abinda yasa ya amince mata da auren Asalamiyya afarko ma saboda tabar Ashraf ya zauna da Mawahib lafiya shiyasa Shima yace ya amince Aryan din ya auri Asalamiyya,amma yanzu tunda ubangiji yayi hukuncinsa yanda yakeso sai abar maganar Asalamiyya,Yara kuma suje gidajen su su qarata, acan saisu daidaita kansu. Ashraf yanajin abinda Alqali yayanke yayi qasa da kansa yana tunani,shide Dama Mawahib yakeso, to Aryan ya aureta,maganar ta tariga ta wuce,amma Nabiha de baya sonta,tunda yake da'ita kallon qanwa yake mata, bai ta6a tunanin aurenta ba,Kuma yasan ta'inda zai 6ullo mata cikin ruwan sanyi zai sallameta.(🙆🏻‍♀️) Alqali ya Kalli maqocinsa daya zama mutum mutumi zaune, sannan ya Kalli amininsa yace"ga abun saka Rana nan, ga mahaifin Nabiha nan, kusaka musu ranar daya dace, tunda su wadancan mutum biyun anriga an daura" Nan take sukai abinda zasuyi, aka tsaida ranar auren Ashraf da Nabiha,sati biyar Masu zuwa,Ashraf yanajin haka yatashi yafice yabar falon cikin rashin damuwa saboda yasan abinda yagama qullawa aransa. Alhaji khaleed yakira Mama Sadiya yabata umarnin takawo musu abinci,Nan take tasaka hijabin ta takawo musu abinci,already Hajiya kilishi takawo musu lemuka da ruwa,zata juya tatafi Alqali yace"dauki wannan goron kije ki rabawa dangin ki da sauran yan'uwa, nasaka ranar Ashraf da Nabiha ne" Mama Sadiya taji maganar banbarakwai,Ashraf ba Mawahib za'a bashi ba? ganin mutumin daya Bata umarnin bawanda zata tsaya jayaiya dashi bane, Hakan yasa ta dauki goron tareda cewa "Allah ya tabbatar da Alkhairi" Bayan tafita Alhaji Bala abokin Alhaji Ma'aruf,shine Yazuba musu abinci, sukaci su kasha kowa yana farinciki, Alhaji Ma'aruf yasaka hannu a aljihunsa yadauko rafar kudi dami daya,wadda zata Kai kimanin dubu Dari, yabawa Alhaji khaleed yace"Kudin sadakin Ruqayya ne,Wanda abokina gashinan a zaune Alhaji Bala shine yabiyawa Aryan, amatsayin sa na waliyinsa" Alhaji khaleed ya kar6i kudin tareda godia,Alhaji Ma'aruf ya Kalli Alqali yace"inaso zanyi magana da Maryam da mijinta kafin muwuce" Alqali yadauki wayarsa yakira Abba yace"inason ganinka kaida maryam" Bayan wasu min tuna suka shigo shida Mamy amma idonta yayi jajir har yanzun kuka take, zama sukayi, Alqali ya kalleta yace"Maryam kukan ne har yanzu?" Cikin kuka Mamy tace"yaya wannan mutumin ya cutar dani,Kuma ya dauki yata yamata aure babu sanina, bayan baisan wahalar taba, baisan cintaba baisan shanta ba, baisan Yaya take rayuwa ba" Alqali yayi murmushin manya yace"to ayi haquri mana,Maryam shekara da shekaru ai ya kamata ace kin yafe masa haka ko?" Alhaji Ma'aruf da jikinsa yayi sanyi yace"hakane Alhaji, haqiqa nime laifi ne awajan ta,acikin Zamana da Maryam zan'iya cewa nine na cutar da'ita,ashekarun baya banida wata sana'ah data wuce fashi da makami,da'ita nake cinyarda Maryam da mahaifiyata wadda ta Ruqayya taci sunan ta, kafin Allah yamata rasuwa,har Allah yabawa Maryam ciki ta haihu na sakawa yarinyar sunan mahaifiyata,bayan haihuwar ne Maryam ta kamani Ina waya taji duka sirri na,munyi tashin hankali da'ita, tace na daina nace wannan sana'ar tawa babu fashi, wannan dalilin ne yasa tace tona zaba kode in daina sana'ah nadena ciyar dasu da haramun mu zauna nida ita da yarmu, kokuma na sauwaqe mata, alokacin idona ya rufe da kudi, hakan yasa nace na zabi sana'ar fashi akansu, daga ranar Maryam ta dauke Ruqayya, bansake sanin Ina sukeba, saide number ta itace de bata sauya ba,lokaci zuwa lokaci Ina kiranta amma bata taba dauka, haka na haqura nadena kiranta,har kawo wannan lokacin Ina Nan Ina sana'ah ta tafashi da mamaki nariga nazama shugaba, kwanaki munje gidan wani Alhaji munyi masa fashi ban biya yarana kudin da suke so ba, wannan dalilin ne yasa suka hademin kai suka kawomin hari zasu kasheni, shikuma Captain Aryan yatemake ni, tunda naga dan mutane yana qoqarin rasa ransa akaina, daga ranar nayi tir da halina,naji na tsani kaina saboda Koda nake harkar fashi na niban yarda da kisan kai ba, bayan nabar asbiti naje duk wata dukiyata da nasan cewa ta fashi ce nakaita gidan marayu, gidan da zan'iya tunawa Kuma Natura musu kudin su tareda neman yafiyar su,a yanzu na daina wannan dabi'ar ta sanadin danku,sanadin danku na shiryu nazama nagari, yanzu Iya kudina na halak nake rayuwata dashi,wannan dalilin yasa ban nemi Ruqayya ba, saboda ban Dena fashi ba, idan na nemeta da haramun din zanci gaba da ciyar da'ita, Kuma nasan Maryam batason haka,yanzu da ubangiji ya nufeni da shiryuwa gashi nazo har gida na nemi yata amatsayinta na matar aure" Dukkannin mutanan falon sukai shiruuuu Bayan sungama jin dalilin mutuwar auren Mamy,wannan ne dalilin dayasa taqi nuna musu mahaifin Mawahib kenan tsawon wannan lokacin. Alkali yayi ajiyar zuciya yace"ikon Allah,Allah Mai yadda yaso,Allah de ya nufa Kaine zaka haifi Mawahib ba qanina ba, saboda auren ta na farko anan gidan muke da'ita,muna Zaman mu yau dadi gobe babu dadi Har na fitar da Ashraf da Aryan qasar waje karatu, to a wannan lokacin ne suka samu matsala da me dakina kilishi,alokacin Bana Gari munje meeting din Alqalai Abuja,to maganar gaskiya ni kaina shedane Maryam tanada haquri, to ranar ankaita maqura hakan yasa taciwa matata mutunci tarama abinda aka mata, to daga Nan qanina Alhaji Isah yamata saki daya,a ranar tabar gidan Nan tatafi maiduguri,Bayan nadawo nasamu labari nayiwa Isah wankin babban bargo, nasashi agaba mukaje maiduguri, muka basu haquri, sai mahaifanta suka bamu haquri cewa bazata koma ba, haka muka dawo gida duk jikin Isah yayi sanyi,Bayan tsawon watanni bamuji labarin taba,sai daga baya suka sake haduwa da Isah anan yaganta da yarinya, tafada masa tayi aure amma sun rabu da mijin,anan Isah ya nuna yanason tadawo dakinta saboda tsawon wannan lokacin bai sake aure ba,Maryam tace bazata aure shi tabar yarinyar taba, shikuma yayi mata alqawari zai riqe yarinyar kamar yarsa ta cikinsa, Isah ya sameni da maganar Nima na amince, to wannan ne dalilin dawowar ta gidan Alqali Akaro na biyu,gata han har yanzu muna tare" Alhaji Ma'aruf yace"ikon Allah,dama can Allah ya qaddara saboda samun Ruqayya ne yasa tashigo cikin rayuwata ba" Yajuya ya Kalli Mamy da kanta yake qasa yace"Maryam kiyi haquri, ki yafemin, sannan akwai kadarorinta dasuke wajena wanda nasiya mata da kudina na halak dakuma Wanda mahaifiya ta tabata kafin tamutu, idan komai ya Lafa zanje Abuja muyi magana da'ita, amma Dan girman Allah ki yafemin ki manta baya" Mamy batace masa uffan ba, sai Abba ne yayi ajiyar zuciya yace"babu damuwa Alhaji Ma'aruf, Allah yayafe mana baki daya" Gaba daya falon suka amsa da "Amin" Daga Nan sukai shirin tafiya, suka sake musabahar rabuwa, gaba dayansu mazan suka futo domin yimusu rakiya, Mamy Kuma ta wuce part dinta, suna zuwa get nafarko adede lokacin direban dayakaisu Mawahib Airport yadawo, Alqali yasashi yasake daukansu Alhaji Ma'aruf suma yakai su Airport din domin tafiyar su jihar Kebbi. ****** Acikin jirgi suna zaune hankalin Captain yanakan window,tunani yake aransa yanzu shine aka hadashi da wannan jaririyar,shikkenan daga taimako taimako yazame masa masifa,? Yatuna lokacin da suke zancen aurensu shida Ashraf har yana fadawa Ashraf cewa tayaya ne zaiyi aure baiyi komai ba a wannan ranar kamar wani kidahumi? Shide yasan bazai ta6a neman wannan yarinyar da sunan mu'amular aure ba,ba ajinsa bace,bazai ta6a sunkuyar da kansa awajanta ba har abada bare har hakan yakaisu ga wata mu'amula ta aure,yanzu ta tabbata Kenan shine kidahumin,tunda gashi ga matar tasa amma saide kallo. Wata zuciyar tace dashi idan hakan tafaru ma aiba haihuwa zakayi ba,saikasha magani sannan ne zaka gwada ko Allah zai baka haihuwar,idan kuwa saboda Mawahib zaisha magani gara ya tabbata babu haihuwa.(🙆🏻‍♀️) kukan datake ne yadawo dashi daga dogon tunanin daya Lula,cikin tsawa yajuyo ya kalleta yace"kokimin shiru kona wanka miki mari...stupid" Tsit,Mawahib tayi shiru, ita kanta jitayi ta nemi kukan tarasa Sai jikinta dayake karkarwa saboda tsawar daya mata. Wanda yake zaune agaban kujerarsu yaji tsawar tayi yawa hakan yasa yajuyo ya kallesu, to ganin suna kama hakan ya tabbatar masa da cewa may be qanwar sace,danhaka baice komai ba Yajuya yaci gaba da karatun jaridarsa. Suna sauka tabiyoshi abaya idanunta harsun fara kumbura saboda kuka,yana hango Sojojin dasuke jiran saukar sa kamar yanda ya musu text Yafada musu yanufi inda suke,suma suna ganinsa suka Sara masa, daya daga cikinsu yayi sauri yabude masa motar,ganinsa tareda mace yasa itama suka bude mata daya gefen tashiga,mamaki ya kamasu ganin ogan nasu tareda mace,Kuma tafiyar tasu kamar babu Shiri,babu jaka babu kwalliya gashi fuskar ogan nasu a daure, basu ga yana fara'ah ba bare a tambayeshi aji ko sunyi suruka ne. Ahanya ma baice dasu uffan ba,sojan dayake Jan motar ne ya kalli Captain ta madubi yaga fuskarsa a daure yana kallon gefen titi, Yajuya yaga Mawahib itama kanta yana kan window, wannan ne Karon farko da tazo Abuja,amma tashin hankali yahanata kallon garin yanda ya kamata,Sojan ya daure yayi gyaran murya sannan ya Kalli Captain Aryan yace"Oga zamu wuce barrek ne kokuma muwuce gidanka?" Saida yayi maganar gida sannan Yatuna lokacin dasuke fira da Ashraf yana nuna masa hadaddan gidan daya gina Har yana cewa yaso ace da matarsa zasu fara shiga,meyasa qaddarar sa take zuwa masa ajuye? meyasa yanda ya tsara rayuwar sa Bata zuwa masa daidai? yanzu duk yanda yakeji da sabon gidan Nan nasa hakan yana nufin tareda Mawahib zasu fara shiga Kenan? gashi ya debe komai nasa daga barek yamaida gidansa Dama yanda ya tsara shine yana dawowa yasauka asabon gidansa, cikin taqaici kamar Wanda aka qwato maganar daga bakinsa yace"gida" Sojan da yayi masa tambayar Wanda harya fidda rai zai samu amsa cikin sauri Yajuya kan motar suka nufi sabon gidan Captain Aryan. Dayan Sojan dayake zaune a kujerar me Zaman banza shine ya turawa wasu daga cikin Sojojin su text,sannan yamaida wayarsa cikin aljihunsa. Suna zuwa gidan kuwa Mawahib taga sojoji ta ko'ina,shi kansa Captain Aryan yayi mamakin ganinsu, daga baya saiya gane aikin Sojojin dasuka dauko shi ne, tundaga Compound zaka tabbatar ba qaramin kudi aka kashewa gidan ba,gidane ginan zamani kamar an dauko shi andora a wajan,ginin beni ne sama da qasa,anyi masa farin fenti, daga qasa akayi wata yar qaramar ma'adanar motoci,manya manyan motocinsa guda uku kowacce tana adane aciki, duka windows din gidan brown color ne, daga Saman Benin akwai wani waje kamar balcony ansaka wasu kujeru na hutawa a wajan,motarsu tana tsayawa ya futo, ganin tare yake da mace yasa wani yayi saurin Bude mata motar, gaba dayansu cikin girmamawa suke gaida shi, saikuma abokan aikinsa Wanda matsayin su dayane sune suke dan tattauna wa tareda yimasa addu'ar kiyaye wa gaba, dangane da harbin da'aka masa, dayawa daga cikinsu Sai satar kallon Mawahib suke wadda take tsaye ajikin motar kana ganinta kasan a tsorace take, tunda take Bata ta6a ganinta cikin sojoji haka ba,to sunriga sunsan cewa Captain Aryan shiba ma'abocin kula yanmata bane,mata dayawa suna tatashi amma shi kokadan baya kulasu, Kuma sude basuji labarin yayi aure ba bare suce, Kuma baitaba zuwa da qanwar sa gidan ba,gashi fuska a daure babu damar tambaya(😂) Wani Captain Ilyas ne yayi qasa da muryarsa sannan yace masa"munyi Amarya ne?" Kai tsaye yace masa"hakane" Daga haka babu qari, yawuce cikin gida,shikuma Captain ilyas yakoma yafadawa sauran, nan da Nan labari ya watsu Captain Aryan yayi aure. Yana shiga gidan itama ta doru abayansa,babbar qofa ce tashiga falon,suna shiga taci karo dawani babban madubi abakin qofar,dawani table agabansa ansaka flowers agabansa anyi ado dashi, Sai sauran falon an qawata shi da wasu kujeru Masu launin brown,gawata Uwar plasma agefe, Sai kitchen da dinning table maicin mutum hudu,falon yayi kyau sosai bnda wannan kitchen din babu wani daki aqasa,daga bakin qofar shigowar falon akwai matakalar beni wacce Bata wuce Hawa goma ba,kowanne step guda daya akwai glop din wuta daga fuskarsa ba wajan da zaka taka dinba, daga fuskarsa anan aka jerasu Kuma kowanne akwai Haske Mai daukar hankali a jikinsa, kana gama Hawa daga hannun hagu akwai dakuna guda biyu ajere, Sai dan qaramin falo Wanda aka qawatashi da kujeru Masu kyau, da fridge aciki dakuma kayan kallo amma bekai na falon girma ba, daga falon ne zaka fita zuwa balcony ta yanda zaka dinga ganin gidan gaba dayansa ta Sama, daga bangaren hannun Dama anan dakin oga kwata kwata yake,duka dakunan akwai kayan amfani aciki, kawai kayan sakawa ne babu,gini ne madaidai ci ginin dan Boko mecin mace daya, suna shigowa yahaye sama yabarta a falon qasa,Mawahib tagama qarewa falon kallo yanzu anan Yaya Captain yake rayuwa kamar ba'a Nigeria ba? Shiyasa yakejin kansa kamar shiyafi kowa yadauki girman Kai ya dorawa kansa? Ahankali tasamu daya daga cikin kujerun falon ta raku6e aciki,ta dauki lokaci Mai tsawo anan falon, taga alamun maigidan bazai Mata nuni da makwanci ba, ahankali tatashi tafara hawa matakalar benin hartaje takama handle din dakinsa zata bude Sai taji alamun yana magana awaya, cikin sauri tacire hannunta, takoma dakin dayake hannun hagu, tana turawa yabude, babu tunanin komai kawai tafada ciki tareda rufowa,zama tayi akan gadon tareda tagumi hannu bibbiyu Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** "Maryam kidena kukan nan haka,farinciki zakiyi Allah yayi auren yarki,Kuma tasamu miji kamili Mai kwarjini Wanda kowacce uwa tagari zatayi fatan ace shine mijin yarta" Cikin shashshekar kuka Mamy tace"bahaka bane Anty,naci buri sosai Akan auren Mawahib,meyasa Ma'aruf zaimin haka? nasha wahalar yarinya haka kawai yazo yadauketa yabada ita inda banaso? niba haka naso aurenta ya kasance ba,banaso tayi rayuwa irin wacce nayi,nafiso taje tayi aurenta hankalin ta ya kwanta kamar kowacce yarinya" Daga dayan bangaren Auntyn tace"to Yaya zakiyi da qudurar Allah Maryam? Ki kwantar da hankalin ki kiyi mata Addu'ah Dan Allah, karki biyewa facala kudinga tashin hankali kamar bakusan tauhidi ba,Dan Allah na roqeki kiso auren Nan, Kuma kiyi mata Addu'ah insha Allah watarana Sai kinyi alfahri da auren Mawahib" Mamy ta share hawayen idonta tace"to shikkenan Aunty, nagode, insha Allah zanyi yanda kikace " "yawwa Maryam haka nake sonki, Allah yayi miki Albarka" Bayan sungama wayar mama Sadiya datake gefe tace"ni bansan meyake faruwa ba,saida Alhaji Yamin waya inkai musu abinci sannan naji yace ansaka ranar Ashraf da Nabiha,harga Allah nide banason hadin Nan, banason tashin hankali, tunda Yaya kilishi ta nuna bataso hankali na yaqi kwanciya da hadin" Mamy da idonta yayi jajir tace"ai yaran nata basuda laifi,sunada kyakykywan hali,Nima ita nafiji,ita din mahaifiyar suce, zata Iya basu kowanne umarni akan matan su" Mama Sadiya tace"to saide muyi haquri Maryam,ya zakayi da hukuncin Allah? Idan kace lalle lalle baza'a yi ba zaka Iya mutuwa Kuma qarshe ayi auren,yanzu ita data dage Ashraf bazai auri Mawahib ba, ba gashinan abun Yaqare Akan dan lelentaba, aiko da wasa batayi tunanin abun zai juye hakaba,dazu Naga likita yashiga part din nata, saida na tambayi baban Nabiha Sai yake cemin itace zazza6i ya rufeta"(😳🙊🙆🏻‍♀️) Mamy tace"Allah yabata lafiya,dazu Yaya khaleed yacemin na shirya zamuje can Abujan,zakije kine kema?" Mama Sadiya tace"yafadamin Nima, amma bandani aka shirya tafiyar,inajin muma saidaga baya zamuje, Dan Allah Maryam idan kinje, ki taushi Mawahib sosai,tariqe mijin ta tamasa biyaiya karta Bawa mahaifinta kunya" Cikin damuwa Mamy tace"to Maman Nabiha insha Allahu" ****** Har dare babu Wanda yasake saka dan'uwan sa a'idonsa,baisan a halin datake ciki ba, yana kwance agadon sa yana waya da Ashraf,yana Sanye cikin rigar wanka fara qal, wadda tsawonta bai wuce Iya gwiwar saba. Cikin damuwa Ashraf yace"ya hanya" Captain Aryan yace"lafiya,bayan munzo saida nafita wajan aiki, sannan nadawo, yanzu nede na kwanta" Ashraf yayi ajiyar zuciya yace"yajikinka? Ciwon dasauqi ko?" "dasauqi sosai,banajin ciwon komai,but duk da haka zan dan huta na kwana biyu kafin nafara aiki" Ashraf yace"zaka huta ko zakayi amarci?" Cikin sauri ya Runtse idonsa Kai tsaye yace"Ash.... zan saki yarinyar nan,bazan Iya zama da'ita ba" Ashraf yace"kayi dace da mace tagari, meyasa zakace zaka sake ta?saboda me?" Cikin shagwa6a yace" Ash Banasonta,ni bazan Iya hada Shimfida da'ita ba,neman maganin ma nafasa,wallahi gara in zauna haka,sannan kaima kana sonta,meyasa ni zan zauna da'ita?" Ashraf ya lumshe idonsa yabude yace"kadena damuwa dani,dama ni nasaba,saina Samo mace saika qwace,yanzu ma gashinan...dama ai kace inde kana Raye ban'isa in aure taba hakane?" Cikin sauri yace"Ash...,kadena tunamin please,banason maganar yarinyar nan" Ashraf yayi murmushi yace"nabar ma ita har abada Aryan,tanada kyawawan halaye nasan duk daren dadewa zakasota, Wai Nima Bayan kuntafi Daddy yace zai bani wannan Nabihan nanda sati biyar " Captain Aryan yatashi zaune yace"wai Dan Allah meyasa su Daddy suke so su dinga janyo mana raini a wajan yaran nanne? Ita wannan yarinyar zata Iya kulawa dakai ne?" Ashraf yace"takula dawa? Idan nazauna da'ita Kenan,kakira Momy kayi mata sannu, batajin dadi tana zazza6i" Captain Aryan yace"innalillah, bari inkira ta" Yana kashe wayar yafara neman layin Hajiya kilishi,saide harya gama yimata 5 missed call kosau daya bata dauka ba, haka ya kwanta cikeda damuwa. ****** Misalin qarfe daya na rana suna zaune a gaban Alhaji khaleed da Alhaji Isah Wanda suka zo gidan bisa jagorancin Captain Aryan,dagashi har Mawahib wadda idonta yake cikeda hawaye ganin Mamy dukansu suna zaune sunajin yanda Alhaji khaleed yake musu fada akan haquri dakuma Zaman lafiya,Mamy Kuma tana daukan jakankunan kayan Mawahib tana Hawa mata dasu Sama,tanajin duk fadan da ake musu, babu buqatar ta zauna tatofa albarkacin bakinta, duk wani Abu dazata fada musu Alhaji Isah da Alhaji khaleed sun fada musu, shiyasa ta maida hankalinta wajan Hawa da kayan Mawahib Sama,duka kayanta Mamy tahado mata shi, daga manyan kaya irinsu atamfofi, Har dogayen rigunan datake yawan amfani dasu, dakuma qananun kayanta nashan is'ka, Sai fici-ficin kayan baccin ta, babu abinda tabar mata agida, tariga ta kar6i qaddara da hannu bibbiyu,zata yiwa yarta fatan Alkhairi da Addu'ar Zaman lafiya itada mijin ta. Bayan takai mata kayan tadawo falo ta zauna,a lokacin angama yimusu Nasihar,Captain yafita yayo musu takeaway na abinci, sukaci suka qoshi, sannan sukai shirin tafiya,mazan sukai gaba sukabar Mamy da Mawahib abaya ko zasuyi wata maganar,Mawahib tana ganin sun tafi tasake rungume Mamy, cikin rawar murya tace"Mamy Bana sonsa,wallahi tsoron sa nakeji Mamy zai kasheni" Mamy tasake rungume ta tace"kiyi hakuri Mawahib,ko baki ji fadan da Abban ki yagama yimuku ba yanzu? kiyi shiru kidena kuka babu abinda zai miki kinji?" Cikin sauri ta goge hawayen idonta sannan tadagawa Mamy kanta alamun amsawa, Mamy tace" idan kin duba kayanki zakiga wani magani aciki, kidinga Sha kullum karki yi wasa dashi,akwai turare zaki ganshi a kwalba kidinga shafawa kullum da daddare idan zaki kwanta" Saida ta share hawayen idonta sannan tace"to Mamy" yarinta tasa kwata kwata Bata gane menene amfanin abubuwan da Mamy din tace ta dinga amfani dasu ba. Futowa sukai tarakota har gaban Mota, tana ganin shigar Mamy Mota tajuyo da gudu tana kuka tadawo cikin gidan. Saida sukaje Airport zasuyi sallama dashi Mamy tace"Captain nasan bakason auren Nan, kayi haquri, Kuma ka dinga haquri da shirman da Mawahib zata dinga yima,yarinya ce Batasan wani abun ba,idan tayi ba daidai ba kayi mata hukuncin daya dace" Captain Aryan bai Iya cewa Mamy komai ba, Sai kansa daya sunkuyar kawai,shi kansa yana buqatar ace Mamyn ta rungumeshi, ta lallashe shi.(😂🙆🏻‍♀️🙊) Amma yanzu gaba dayama Yakasa sakewa da'ita,yakasa kallonta, tazama kamar wata baquwar sa. tun Bayan tafiyar su Mamy gidan yayi shiru bakajin motsin kowa,tana zaune a dakinta batada aiki Sai tunani, ga wayarta nan agefe amma batada sukunin daukar wayar harta dinga dannawa, haka suka wuni ranar babu Wanda yasake saka kowa a idonsu har dare,Kuma Har lokacin Mawahib bataci komai ba, rabon ta da abinci tun akano,yau kwana daya Kenan, dazu daya siyowa su Mamy Koda wasa bataci ba, saboda ba tajin dandano a bakinta,Shima Captain yana dakinsa, Bayan tafiyar su Mamy ma haka ya dinga Kiran Hajiya kilishi amma Bata dauki wayarsa ba, haka yaja Computer sa ya kunna yana ganin ayyukan office ko hakan zai rage masa tunani,Washegari ma haka suka wuni babu Wanda yaga kowa, gidan tsit bakajin motsin kowa, yauma wuni tayi tana kuka, gaba daya ta kasa sakewa a gidan. A 6angaren Captain kuwa gaba daya ya manta da Mawahib,rayuwarsa yake kansa tsaye, kasance war baya ganinta yasa shaf ya manta da wata halitta a gidan,damuwa ta masa yawa Kuma babu Wanda zai jashi ajiki bare yaji damuwarsa ya lallasheshi,kana ganinsa zakasan hankalinsa ba'a kwance yakeba saboda rashin daukan wayarsa da Hajiya kilishi taqi yi,bayason ya fadawa Ashraf Sai Shima yashiga damuwar. Da daddare yayi shirin bacci wajan shadaya da rabi nadare,yana Sanye cikin kayan bacci Riga da wando, rigar yar qarama ce mai gajeren hannu,wandon Kuma dukansa iyakarsa Rabin cinyarsa,farar fatar jikinsa tayi fresh Sai sheqi take, qasa-qasa yakejin kuka yana tashi,mamaki ya kamashi waye a gidan har ake masa kuka da wannan Daren? Cikin sauri yabude dakinsa Yafuto, yana futowa dayaji daga inda kukan yake tashi saiya tsaya yayi turus tareda dafe kansa da hannunsa, kwata kwata ya manta da yarinyar nan. Fuskar nan tasa adaure ko alamar annuri babu haka yatura kansa cikin dakin, anan bakin qofar dakin yaci karo da'ita, yatsaya Yazuba mata ido hannayen sa duka biyun suna zube cikin aljihun dan qaramin wandon baccin dake jikinsa,tana zaune ta dora kanta Akan cinyarta tana kuka, abayar jikinta ce tun wacce tazo da'ita gidan Bata sauya wani kayan ba,dakin ya qarewa kallo yaga babu abinda tayi amfani dashi kayanta da Mamy tashigo mata dashi yana Nan inda ta ajiye mata su da alamun Bata Bude kayan ba, saida yagama qare mata kallo sannan yayi ajiyar zuciya cikin dakewa yace"kindameni da kuka,kitashi kifice daga gidannan kije waje kiyi,kin takuramin zaki hanani bacci, banason hayaniya" Tanajin maganar sa tadago fuskarta dake cikeda hawaye ta kalleshi, ganin fuskar tasa babu Rahma yasa cikin sauri ta maida kanta qasa tace"ni yunwa nakeji" Yanajin haka ya girgiza kansa Yafuto yabar mata dakin, yanzu fisabilillah saboda yunwa kawai ta zauna take masa ihu a kansa? Komai kuka towa zata yiwa kuka? Bata barshi da damuwar dayake ciki ba zata qara masa wata damuwar? Shimafa dazai samu kukan nan zaiyi ko zaiji sauqin abinda yakeji aransa (😲🙊) Yana gama wannan tunanin yadauki key din Mota yafice yabar gidan, bai dauki dogon lokaci ba yadawo gidan hannunsa daukeda takeaway guda daya,Kai tsaye dakinta yawuce yana zuwa yajefa mata ledar, abincin dayake ciki yawatse ajikinta, kadanne yayi saura acikin ledar, bai saurari komai ba ya rufe mata dakin da qarfin gaske,zafin abincin ne yasa Mawahib tatashi da sauri tana karkade jikinta,shinkafa ce jallop Sai wainar qwai da cinyar kaza guda daya,amma duka ta watse agabanta, qofar tabi da kallo taga harya Riga ya rufe, haushi yasa ta dauki sauran nacikin ledar ta wulloshi jikin qofar dakin Shima ya watse anan, tatafi da gudu tafada kan gado tana kuka,ahaka baccin wahala ya dauketa. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Washegari tun sassafe yunwa tatashe ta,Bayan tayi sallah tayi karatun qur'ani kamar yanda tasaba, tagyara dakin tsaf yadawo hayyacinsa, sannan tashiga toilet tayi wanka ta shirya cikin Riga da siket na Atamfa sannan tasaka hijab tafuto zuwa falon qasa,Kai tsaye kitchen ta nufa, Bata tsaya qarewa kitchen din kallo ba saboda jiri jiri take ji saboda yunwa,jikinta har wata karkarwa yake,Kai tsaye tabude fridge din data gani aciki,anan taci karo da lemuka da ruwa harda madarar Hollandia, cikin sauri ta dauki kwali biyu tarufe fridge din takoma Sama, tana zuwa tarufe dakin tasaka key sannan takafa Kai a madarar Nan saida ta shanye kwali daya sannan tafara maida numfashi,ahankali tatashi ta kwanta akan gado tana lumshe idonta, Sai yanzu ne tafara jinta tana dawowa hayyacinta. Wannan lemukan data dauko suta wuni tanasha bata Bude dakin Bama bare tafuto,Washegari ma haka tayi, sauka tayi tasake dauko wasu, anan taci karo da kayan abinci a kitchen din, duk wani nau'in kayan abinci saida ta ganshi, tabude babban fridge din dayake gefe taganshi da nama danye Kala Kala harda kaji saide duk sun daskare alamun kamar sun dade acikin fridge din. Kwanansu uku babu Wanda yaga wani, kullum dasafe zata futo ta dauki lemo takoma daki, bata yarda suhadu. Yauda safe tafuto daukar lemo taga kitchen din yana buqatar gyara, da hijabi ajikinta tafara gyara kitchen din, tafara mopping Kenan yashigo kitchen din da dan gudunsa sai hada gumi yake yana Sanye cikin kayan gym singlet da gajeren wando irin singlet din,kai tsaye fridge ya nufa yabude yadauki gorar ruwa guda daya Mai sanyi yafara Sha,gaban Mawahib yafadi,ta gefen ido ta kalleshi taga yanda murdadden jikinsa yake shinning yana hada gumi da alama daga motsa jiki yadawo,ga yanayin garin akwai sanyin safiya amma ahaka yake shan ruwa sanyi ga jikinsa babu suturar arziqi da alama sanyi baya damunsa, ganin zai juyo yasa tayi saurin yin qasa da kanta, saida ya shanye ruwan tas Sannan ya wullar da gorar ruwan anan,zuciyarsa tayi baqiqqirin alamun 6acin rai,ganin Mawahib ko gaisuwa ta gagara yimasa. Ita kuwa gaba daya a tsorace take dashi,cikin sauri tazo zata dauke robar ruwan daya Jefar a wajan,santsin ruwan dabai gama bushewa ba ya dauketa tatafi luuuu zata fadi, cikin sauri Captain Aryan yayi sauri yaruqota,kallon fuskarta yayi yaga ta Runtse idonta alamun ta tsorata da faduwar da zatayi,zuba mata ido yayi yana kallonta, wata zuciyar tace dashi yarinyar dabata Iya gaisuwa ba ka taimaka wa? Lokaci daya ransa yasake 6aci,Kai tsaye yasake ta tafadi qasa warwas a wajan, hannunta ya hadu da tiles din kitchen din yabugu,lokaci daya tasaki qaran azaba,Captain ya juya yafita, yana jinta amma Koda wasa bai juyo ya kalleta ba bare yaga halin datake ciki. Cikin sauri tatashi tana yarfe hannu tareda hura iska a'inda taji ta bugun,daga kanta tayi ta Kalli kofar kitchen din acan ta hango Captain yana hayewa Sama,cikin ranta tace"mugu...." Kai tsaye ta wuce dakinta tafara dudduba cikin kayan ta kasancewar ko agida Bata rasa magani Mamy tana zuwa da wasu gida, anan taga paracetamol, ta6alla tasha sannan ta wuce toilet tahada ruwan dumi tayi wanka dashi, cikin ikon Allah Sai taji ta kalau,taso tafuto tashare falon ta gyarashi, to amma ganin ya Captain yana gidan yanzu shiyasa ta yanke shawarar gara ta kwanta idan taji alamun yafita zuwa yamma saita futo tagyara falon,doguwar Riga tasaka marar nauyi, ta kwanta agado Nan da Nan bacci ya dauketa. Da yamma wajan karfe uku taji gidan shiru,tasaka hijabin ta madaidaici akan doguwar rigar data saka dazu,tafuto kamar yanda ta tsara zata gyara falon,zuciyarta daya tasauko qasa tana zuwa Sai tayi turus ganinsa afalon yabaje takardu ga Kuma computer agabansa yana dannawa, yana Sanye cikin Riga da wando,rigar milk color, wandon Kuma na jeans ne,Sai yanzu ne ta ganshi ta kayan arziqi tunda tazo gidan, kullum yana cikin kayan shan Isa ko tsoron sanyi ba yayi. Mazewa tayi ta wuce ta dauko tsintsiya a kitchen batace dashi uffan ba, yanajin saukowar ta, yanajin lokacin data wuce tasake dawowa, Shima baice da'ita uffan ba. Sharar tafara cikin sauri sauri danta gama takoma daki, saida tagama share ko'ina tas sannan tadawo inda yake zata share, ta sunkuya tafara Sharar,mamaki yasake kama Captain,yaga alamun gaba daya tagama rainashi,yana gaba da'ita amma tafi qarfin ta gaidashi, ya kalleta ta gefen ido,yagama Lura kan yarinyar yana rawa, Kuma bazai dauki raini ba, dole zai sauke mata duk wani Iya shege datake ji dashi. zuciyar ta daya tazo gab dashi da Sharar ganin yana zaune a wajan yasa ta miqe zata tsallake inda yake zaune,tashin Nan da zatayi tana daga qafarta Captain yasaka qafarsa a wajan da niyya,aikuwa saita harde tafadi a wajan, yana ganin tafadi ya kalleta tareda ta6e baki yaci gaba da typing din dayake a computer. Mawahib Batasan lokacin data saki wani irin kukan taqaici ba,tatashi tana riqe da goshinta dayake mata zafi tayi wulli da tsintsiyar sannan ta wuce daki da gudu tana kuka. Sosai take kuka Kuma kuka Mai sauti kamar Wanda akayi mata mutuwa, jakunkunan kayanta guda uku Wanda suke ajiye d'om,suta fara janyowa da qyar gaba dayatafuto dasu gaban dakinta ta jirgesu anan kofar dakinta.(🙆🏻‍♀️) Jin kukan nata yayi Yawa Hakan yasa yasaka hannuwansa ya rufe kunnuwansa duka biyun,amma yanajin kukan, cikin 6acin rai ya kawar da computer sa gefe yatashi yanufi Saman, yana zuwa tundaga kan matakalar benin nasu ya hango jakar kayanta a adane agefe,bai damu dasuba ya tsallake su yanufi dakin nata, yana kama handle din dakin zai Bude saiya jiyo muryarta cikin ihun kuka tana fadin"Nabiha wallahi gida zan tafi,Kuma Allah saina fadawa Mamy abinda yakemin,banason wannan auren,zuciyata zafi takemin inajin mutuwa zanyi" ta qarasa maganar tana ruskar kuka Daga daya 6angaren Nabiha tace"Mawahib karki fadawa Mamy,kinsan kan Garin Abuja ne da zakice zaki taho ke kadai? kiyi haquri Dan Allah koma meya miki kibarshi da Allah, Kuma Allah saiya saka miki" Cikin kuka tace"idan nasake kwana agidan Nan tobana numfashi Nabiha...."(😳🙆🏻‍♀️) Tana fadar haka ta kashe wayar tafuto daga dakin, tana Bude kofar dakin ta ganshi a tsaye a wajan ya harde hannunsa a qirjinsa, fuskarsa a daure yamiqa mata hannunsa yace"bani wayar nakira miki Anty Ma-myn" Bata kalli inda yakeba ta sunkuya tafara kinkimar jakar kayanta(😳) Cikin 6acin rai yadaka mata tsawa yace"go back" Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: *Page 47* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Tsawon lokaci ta dauka tana kuka awajan,gaba daya takasa tashi daga wajan gani take tana miqewa zai sake dawowa yaganta tsirara, ta dade awajan saida tagama kuka a yanda take a tsugunne sannan cikin gudu tatashi tarufe dakin daga jiki, sannan ta murzawa dakin key. jikinta sai karkarwa yake kwata kwata bata samu qwarin gwiwar saka kaya ba,haka tahau kan gado tashige cikin bargo tana kuka. Adede lokacin Mamy takira wayarta,tana cikin bargon tayi sauri ta dauki wayar,Mamy tanajin yanda tayi sallama tasan cewa kuka tayi,batayi mata tambaya akan yanayin muryarta dataji ba,tace"Captain yakawo miki saqo?" Cikin muryar kuka tace"Eh Mamy yakawo" Mamy tayi ajiyar zuciya tace"gumba ce kidinga ci kullum" Saida tayi ajiyar zuciya alamun tasha kuka sannan tace"to Mamy" Mamy taba tambayi dalilin kukan ba,tasan mata da miji Sai Allah, suna gama magana tayi sauri takashe wayar. Da sassafe tatashi zata futo tadora abinci,ta kirma wani uban hijabi ita kanta tasan wannan hijabin yafi qarfinta,tana futowa daga dakin tayi turus ta tsaya ganin Yaya Captain a tsaye a falon Yajuya bayansa yana magana awaya kamar bayaso, ahankali tafara ja da baya dan karya ji takunta harta dawo sama,abinda bata saniba shine tun futowar ta yajita, yaqi juyawa ne saboda bayason suhada ido,gani yake zata dinga yimasa kallon fassara saboda halin daya ganta aciki jiya,Wanda har zuwa wayewar gari yana danasanin shiga dakin nata saboda masifar da hakan taja masa,(🙈🙊) Tana gabda shiga dakinta taji yana cewa"toya zanyi? duk inda soja yake yasan cewa dole ne ya dinga sadaukar da ransa ayaqi,dole ne zamu fuskanci maqiyan qasa da abokan gaba komu kashe ko a kashe mu,wannan shine mataki na qarshe...." Lokaci daya jikinta yayi sanyi, Ina zaije yake maganar kisa? sanin babu mai bata amsa yasa tashige dakinta tare rufowa,dama saboda cikinta zatayi girkin tunda shide idan tayi bayaci,gara ta haqura da girkin da'ace tafita tahada ido da Yaya Captain,hijabin jikinta tacire tayi kwanciyar ta tana duba wayarta. Bata sake futowa daga dakiba Sai azahar,gidan shiru kamar kullum,saida ta leqa taga babu motarsa guda daya sannan tasaki ajiyar zuciya ta wuce kitchen tahada abinci mai sauqi, tafuto da abincin daga kitchen ta wuce dining,anan taci karo da rafar kudi Yan dubu daya, kimanin dubu dari,da wata takarda aqasan kudin,abincin hannunta ta ajiye, sannan tajanye kudin taduba takardar "BANDA FITA YAWO" Abinda aka rubuta a takardar kenan,tadauki kudin tadinga juyashi a hannunta tana tambayar kanta mezatai da kudi to? menene ma'anar wannan rubutun? Meyake nufi? Tunda tazo duniya bata ta6a riqe kudi mai yawan wannan ba,ba'a bata kudin daya wuce dubu ashirin,sai wannan kudin ya tsoratata, ta ajiye shi agefe tareda takardar tafara cin abincinta. Wayarta dake gefe tafara qara,tana dubawa taga Nabiha ce me Kiran,cikin sauri ta dauka tace"Nabiha" Nabiha tace"na'am Mawahib ashe Yaya Captain suntafi wani daji kamo yan bindiga" Mawahib tayi shiru tana tunani,Kenan shine ma'anar barin wannan kudin da wannan takardar. Cikin rashin damuwa tace"nima yanzu nakeji a wajanki" Cikin mamaki Nabiha tace"wai kina nufin bai fada miki zai tafi ba?" Mawahib tace"to menene hadina dashi dazai fadamin zaiyi tafiya? Kinga kowa rayuwar sa yake a gidannan,tsakani na dashi gaisuwa" Nabiha tayi ajiyar zuciya tace"ta6di, lalle muna ruwa Mawahib,to aike gara ke ko Yaya ne,kina ganin Yaya Captain, nifa tunda aka fara hidimar bikinnan,aka gama, aka kawoni gidannan,wallahi har yau banga idon Yaya Ashraf ba,gida nikadai kamar mayya, Kuma wallahi duk lokacin daya dawo saiya raina kansa" Cikin sauri Mawahib ta zaro ido(😳) Tace"mekikace Nabiha?Yaya Ashraf dinne zai raina kansa? ke kuwa Nabiha nawa kike dashi a account dinki?" Cikin damuwa Nabiha tace"wai me kike nufi ne Mawahib? auren nan namufa babu fashi,kina ganin dan mun nuna bama so Daddy Alqali zaisa su sakemu ne? Idan sun sakemu mun koma gidan mun zauna suma sundawo gidan hakan dadi zaiyi? gara tun wuri muyiwa kanmu fada, muriqe mazajenmu tun kafin wasu matan su qwace mana su" Cikin damuwa Mawahib tace"anya zan'iya? kinga Yaya Captain ba kamar Yaya Ashraf ba,kuma ni har yanzu banajin sonsa araina ko kadan,nifa banqi muyi shekara da shekaru ahaka ba,yayi harkarsa inyi tawa" Nabiha tace"Mawahib bakida wayo, kwata kwata yarinta tamiki illa,to kodan Momy kilishi aikya yiwa kanki fada,amma kiyi tunani" haka Nabiha takashe wayar tabarta cikin tunani,gaba daya sai taji abincin datake ci yafita aranta,kanta yafara ciwo,cikin damuwa tatashi tabar wajan tahau sama. Dan qaramin falonsu dayake Sama Wanda yaraba dakinta dana Yaya Captain,nan tashiga,tayi tagumi hannu biyu tana tunani tayaya ne zata Iya sauya zamansu da Yaya Captain bayan kokadan bata jinsa aranta? tayaya zatayi hakan bayan tasan cewa shima awajansa itada banza duk daya? Ajiyar zuciya tayi tafuto balcony din wajan tafara qarewa gidan kallo tana shaqar wata is'ka mai dadi,ta dade awajan sannan takoma falo ta kunna kallo. Satinsu daya adaji,tunda yatafi hankalin Mawahib a kwance,bata tunawa dashi kokadan bare tayi tunanin halin dayake ciki, rayuwarta take tama manta dashi,tana zaune afalon Sama tana kallo tabude data tahau Facebook anan taci karo da wasu sojoji da bbc ta dora tana bayanin cewa Sojojin Nigeria sunyi nasarar kama Yan bindiga Wanda suka addabi yankin kudancin qasar. Mawahib tasake karanta labarin,lokaci daya ta tasaki wani irin murmushi,tunda tazo gidan yaune karon farko da tasan tayi murmushi. ****** Tunda akai bikinsu kusan kwana takwas Kenan Sai yau Ashraf yadawo daga Rivers,tunda yashigo gidan yawuce dakinsa, bai nemi inda Nabiha take ba,ita kuwa tanajin zuwansa tayi sauri tashiga kitchen tafara kokarin yimasa hadadden girki,bata gamaba har bayan magrib,ta wuce dakinta tayi wanka ta shirya cikin shadda Riga da siket ta tsara kwalliya tagani tafada, sannan ta wuce dakinsa tafara qwanqwasa wa, cikin mamaki Ashraf yabude qofar,nan take yayi tozali da kwalliyar da Nabiha tazuba,bai nuna mata komai ba Kai tsaye yace"lafiya?" Cikin sanyi tace" Yaya Ashraf akwai abinci,kafuto kaci abinci" Lokaci daya ransa yadan 6aci,shi wannan yarinyar zatazo tana yiwa Kiran miji Yafuto yaci abinci? har zai fara masifa, saiya tuna ai itama bason auren take ba, akwai Wanda takeso agefe, saiya fasa Yasaki ajiyar zuciya yace"to" Bai jira amsarta ba yamaida qofar ya rufe. Jikin Nabiha yayi sanyi,tajuya fararen idonta tareda sakin ajiyar zuciya,Yaya zatayi da son wannan bawan Allah? a'ido ma basai an fada mataba tasan cewa Yaya Ashraf baya sonta,ta wacce hanya zatabi ta janyo hankalinsa gareta? Cikin sanyin jiki tajuya zuwa falon ta zauna awajan abincin tana jiransa, saida yagama yangarsa son ransa sannan yayi wanka, zai saka gajeren wando da yar qaramar riga saiya fasa dayayi tunanin Zaman nasu bamai dorewa bane menene abun sakewa da yarinya har yana saka gajeren wando duk tagama ganeshi ciki da bai sannan su rabu, saiya janyo jallabiyar sa yasaka Yafuto falon. Hangota yayi a zaune ita kadai tasa abincin agaba ga waya a hannunta tana dannawa, Kai tsaye zuwa yayi ya zauna yafara bude abincin wani daddadan qamshi ya dakeshi, ya juya ya kalleta yace"to yanzu ke Nabiha kya gajiyar da kanki akaina? inake Ina wani girki muda zaman namu bamai dorewa bane?"(😲🙆🏻‍♀️) Nabiha tace"yaya Ashraf ai girki ne,ko agida amatsayina na qanwar ka aiba laifi bane dannayi ma girki" Ashraf yayi shiru yatafi dogon tunani, Sai can yace"hakane Kuma,amma de duk da hakan, kidena,karki sake takura kanki akaina" Cikin ladabi tace"to yaya" Daga Nan tatashi tafara zuba masa abincin ****** Da daddare wajan qarfe takwas ta dinga jiyo murya sama sama ana magana,sai hayaniya ake wasu suna ihu,cikin sauri tabude qofar dakinta tafuto, anan tafijin hayaniyar sosai,har zataje ta bude qofar falon taga menene Sai tsoro ya kamata, saita shiga dakin qaramin falonsu na sama, tafita ta balcony din gidan anan taga sojoji dayawa a compound din wasu a tsaye wasu a zaune,dawani abu agabansu sunaci Batasan menene ba,Yaya Captain yana gefe yana danna wayarsa kamar baya wajan,tun lokacin data fara leqensu yaganta tagefen idonsa,Sai yaqi dagowa yaci gaba da danna wayarsa. Mawahib takoma gefe tana qare musu kallo batareda sun sani ba. Daya daga cikin Sojojin ne yaharba bindiga sama,Mawahib datake tsaye tanajin qaran bindiga tayi sauri tarufe kunnuwanta tareda tsugunna wa awajan. Kai tsaye Captain yadago kansa, ya kalleta yaga bata wajan, yamaida idonsa kan wayarsa a hankali yace"matsoraciya" da alama bata ta6ajin qaran bomb ba,dagajin wannan qaran harta tsorata. Mawahib kuwa cikin gudu tabar wajan takoma daki,cikin ranta tace sundawo kenan. Wayarta ce tafara qara, tana dubawa taga Mamy ce, cikin sauri ta dauka tareda sallama, Mamy tace"sannu Mawahib, yakukaji da jama'ah Kuma?" Cikin rashin fahimta tace"jama'ah wanne iri kenan Mamy?" Mamy tace"mijinki yadawo daga cikin dokar daji kina tambaya ta wacce jama'ah? Mutanan arziqi mana Masu zuwa muku murna" Cikin halin ko'inkula tace"inajin sunzo sunyi masa,ni har yanzu ban hadu dashi ba" Cikin tsananin mamaki Mamy tace"dawaye baki hadu ba? Kanki daya kuwa?" Lokaci daya idonta yakawo ruwa,yanda taji Mamy tana maganar tasan cewa babu wasa a fuskarta, kan kace kwabo har hawaye sun fara zubowa a fuskarta cikin hawaye tace"Mamy ni wallahi banason shi..." Cikin 6acin rai Mamy tace"banason sakarci Mawahib,cemiki akai shi yana sonki ne? da bakina da nashi yafadamin bayason kowacce yarinya, da komai ya bayyana gaskiya tafuto fili shine mijinki kinji yayiwa iyayensa tijara ne bayason auren? Meyasa ke bazaki kwantar da hankalin ki kizauna adakin mijinki kiyi shiru ba? saikin nunawa duniya da Yaya kilishi cewa bamu baki tarbiya ba kamar yanda take fada?" Zuwa wannan lokacin Mawahib kuka take harda shashsheka, cikin kuka tace"Mamy konayi masa girki bayaci,baison magana dani..." Cikin damuwa Mamy tace"toya zakiyi tunda ubanki ya janyo miki? Idan bakiyi haquri kin zauna ba so kike yasakeki kidawo muzauna Yaya kilishi taji dadin goranta miki? Shikkenan,Kici gaba tunda haka kikaga yafi miki" tafadi haka tareda kashe wayar. Kifa kanta tayi akan gado tafara ruskar kuka kamar marar lafiya,tasaka hannunta biyu tarufe fuskarta dashi tana kuka, cikin kuka take tunani gani ga Yaya Captain agida daya, idan kasheni zaiyi saide ya kasheni babu wanda ya damu daba Shiri nake dashi ba, itama Mamy tadawo tana bin bayansa,meyasa takeso ta tilastani zama da wannan mugun me muguwar zuciya? yanzu shikkenan itama Mamy tadena sona? Kuka taci gaba dayi, saida tayi mai isarta Sannan ta kwanta Koda wasa batayi kuskuren futowa daga dakinta ba. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Washegari dasafe takama Asabat ne babu aiki,Captain yana gida, tun sassafe yazo falo ya zauna yana dan aiki kadan kadan a computer sa,har wajan qarfe goma baiga futowar taba,abincin datake futowa tayi wa kanta ma yau baiga tafuto ba,tambayar kansa yafara yi kode ta tsorata sosai ne da qaran bindiga shiyasa takasa futowa? Cikin sauri ya ture computer dake gabansa yatashi yayi dakinta,da gudu-gudu yahau matakalar benin, ya qarasa gaban qofar dakin ta yadora hannunsa akan handle din dakin zai bude, saiya kasa budewa cak yaja yatsaya yana tunani, idan yasake ganinta a'irin yanayin rannan fa? mezai cemata? a hankali ya janye hannunsa daga kan handle din dakin yana tunani menene damuwar sa? cikin sauri ya fasa budewa Yajuya yabar wajan. Mawahib tana cikin dakinta tana aiki tun safe, kayanta da Mamy takawo mata daga gida wanda suke ajiye d'om ko ta6asu batayi ba,shi ta bude tafara jerawa a wardrobe,kayan sakawa ta ware musu wajan su daban, kayan shan is'ka suma wajansu daban,kayan bacci ma wajansu daban,saida tagama jera kayanta tas, sannan taga maganin da Mamy tace tasako mata aciki da turare,ta dauki ruwan tsumin dabatasan menene amfanin saba tasha sosai kamar ruwan sha,sannan tatashi ta ajiye shi acikin bedside drower dinta,turaren ta bude ta shaqa taji qamshin yanada dadi,tarufeshi tasaka shi a gaban mirror inda ta jera kayan shafarta,gumbar da Yaya Captain ma yakawo mata tabude tasaka hannunta taci yar kadan, da taji dadi saita gyara zama dama bataci komai ba,ta zauna taci gumba Iya yanda takeso sannan ta ajiye ta akan mirror da nufin zuwa anjima tasake sha saboda taji tanada dadi sosai(🙆🏻‍♀️😳) Cikin ranta tanata mamaki meyasa Mamy tabata wannan tarkacen. Saida tagama shirya komai tsaf,sannan tasake gyara dakin ta wuce toilet tayi wanka,ta zauna tafara karatun qur'ani har yamma,kokadan bata futo falon ba yau,karatun qur'ani takama ko hakan zaisa taji sauqi sauqi aranta, idan tadanji yunwa saita tashi taci gumba tabude dan qaramin fridge dinta tasha ruwa(🙆🏻‍♀️) Tun yamma Alhaji Ma'aruf yakira wayar Captain Yafada masa gasunan zuwa suna hanya,basu saukaba Sai wajan magrib,ana Kiran sallar magrib yafice zuwa masallaci, daga nan sukai waya dasu yaje ya taro su a hanya suka dawo gidan tare,tun a compound din gidan Alhaji Ma'aruf ya jinjina kansa, tabbas yarsa tayi sa'ar duniya saura ta qiyama Kuma,Captain ne yabude musu kofar falon suka shigo suka zauna,sannan yasake gaida su cikin girmamawa,yatashi yawuce gaban tv ya kunna musu kallo sannan yace"bari akirata" Alhaji Bala yayi murmushi yace"to ba laifi" Cikin sauri Captain yahau sama, kai tsaye yatura dakin nata yana Addu'ah Allah yasa yaganta cikin sutura kartayi Masa haramiyar baccinsa nayau, yana turawa yaji a rufe, saiyayi mata nocking, Mawahib kuwa tun lokacin daya shigo yaganta babu kaya tadaina barin dakinta abude,cikin nutsuwa tatashi tabude qofar, tana Sanye cikin hijabi hannunta daukeda Alqur'ani,kallo daya yayi mata yatuna yanayin daya ganta kwanaki, cikin sauri yadauke kansa sannan yace"ana kiranki" Daga Nan Yajuya yasauko qasa, mamaki ya kama Mawahib to waye zaizo musu itadaba kowa tasani ba? Qur'anin ta ajiye sannan ta biyo bayanshi tafuto,tana zuwa taga mahaifinta zaune afalo shida abokinsa,yayi kyau sosai cikin shadda blue color, cikin ladabi ta tsugunna qasa tace"Abba sannunku da zuwa" Cikin Jin dadin sunan data kirashi dashi yace"yawwa Ruqayya, Kuna lafiya ko?" Tace" lafiya kalau" Alhaji Bala yace"Yaya baqunta? ai yanzu kinzama yar Abuja kinsan gurare dayawa ko?" Mawahib tayi qasa da kanta tace"eh" Captain Aryan Yazuba mata ido yana kallonta,lokaci daya tsoro ya kamashi ganin ta takure a waje daya tana amsa musu babu sakin jiki atare da'ita,karfa yarinyar nan ta kunyatashi a gaban mahaifin ta, suyi tunanin wani abu yake mata, kana ganinta kasan a takure take. Kallo yayi kallo, yayi nisa acikin kallonta lokaci daya yatafi tunani,wannan ne Karon farko daya ta6a qarewa kyakykywar fuskarta kallo, Sai yanzu yasake yaganowa da wanda take kama, wato Alhaji Ma'aruf,pink lips dinta dan qarami,idanunta,girarta,gaba daya irin na mahaifinta ne. yatuna lokacin dasuke primary school kafin su tafi qasar waje karatu,Ashraf yacewa Mamy ta haifa masa Baby mekyau itace matarsa,shikuma yacewa Mamy ta haifa masa mai kama da'ita. Alhaji Ma'aruf ya kalleshi yace"Captain...." sai a lokacin Captain Aryan yayi firgigit yadawo daga duniyar tunanin daya lula. ****** shiryawa yayi zaije gida ya gaida Momy yakuma sake bata haquri akan fishin datake da Aryan,cikin sauri yadauki key din motarsa ya futo yana so yadawo da wuri karya yi dare acan, Nabiha tana ganin futowar sa tasan cewa yanzu haka idan yafita bazai dawo ba saide yabarta ita kadai takwana a gidan, cikin sauri ta d'oru abayansa haryazo yashiga mota, zai rufe murfin motar Sai ganinta yayi agabansa. Cikin mamaki yafasa rufewa ya kalleta fuska babu alamun wasa yace"lafiya?" Cikin damuwa yace"Yaya Ashraf dan Allah inzo na rakaka?" Mamaki yakama Ashraf, ya Kalli Agogon hannunsa na azurfa yaga qarfe bakwai da minti takwas, ya kalleta yace"kirakani kuma? babu inda zanje, zanje gidane" Cikin sauri tace"to yaushe zaka dawo?" Cikin halin ko'inkula yace"idan nasamu kaina..." Nabiha tana jin furucin yanda yake mata magana tasan cewa ta takura masa,da alama bayason maganar,cikin wani irin salo da kissa tafara bubbuga qafafunta awajan cikin shagwa6a tace"nide Allah Yaya kadawo da wuri ni gidan tsoro yake bani idan baka nan" Ashraf da kansa yake qasa cikin sauri yadago kansa ya kalleta,sai yayi saroro yana kallonta yaji gaba daya shagwa6ar tata ta dakeshi. Baisaba da hakan ba,babu macen data ta6a tsayawa agabansa babu hijabi bare mayafi,ga kyan diri, tatsaya agabansa take zuba masa shagwa6a sai yau yagani,lokaci daya yaji wani irin yanayi yana kamashi, dan karta gano halinda yake ciki, cikin sauri ya amsa mata yace"to" Sannan ya rufe motar yafice yabar gidan. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Cikin sauri Captain yace"na'am Abba" Yanda yaji Mawahib din tafada,Alhaji Ma'aruf yayi murmushi,yaji dadin yanda Captain ya kirashi da wannan sunan,hakan yana nufin ya kar6eshi amatsayin uba kamar yanda yabashi 'yarsa, idan ya Lura yanzu ya kar6i auren nasu da hannu bibbiyu,kuma bisaga dukkan alamu Captain din yafara fadawa cikin tarkon 'yarsa,tun dazu suna magana amma idonsa yanakan matarsa ko qiftawa bayayi yatafi tunani. Yayi ajiyar zuciya yace"akwai kadarorinta dasuke wajena Wanda na mallaka mata su tun tana qarama,idan kunsamu lokaci Sai kuzo, zan danqasu a hannunka, da nayi niyyar kaiwa mahaifiyar ta, to amma yanzu tunda tayi aure,saina yanke shawarar zan bawa mijin ta,saikusan Yaya zakuyi dashi kaida ita,tunda yanzu haqqin kula da komai nata yana wajanka" Kansa aqasa cikin ladabi yace"to Abba insha Allah" Alhaji Ma'aruf yace"Yaya aikin naku,? naga Ana posting a media kun yaqi wasu 'yan ta'adda, Allah yaqara kiyaye wa gaba" Cikin biyaiya yace"Amin ya Allah" Adede lokacin Mawahib takawo musu ruwa,lokacin qarfe takwas da kwata nadare,ta ajiye cikin nutsuwa sannan tajuya zata koma kitchen, anan taji Abbanta yana cewa "Yaya maganar ganin likita?" Cikin sauri tashige kitchen batason jin suna masa maganar ganin likitan nan, gaba daya sun d'aga hankalinsu akan rashin lafiyar sa,ko idan yaga likitan wacece zata haifa masa yaran oho(😳🙆🏻‍♀️) Captain Aryan yace"har yanzu de ban ganshi ba,tunda na warke nadawo bakin aiki bansamu zama bane shiyasa" Alhaji Ma'aruf da Alhaji Bala suka hada baki wajan fadin "Allah yasa adace" Kafin Captain ya amsa musu, adede lokacin Mawahib takawo musu abinci,ta ajiye agabansu, sannan takoma tadauko babban plate tabude abincin zata zuba musu, wani irin qamshi yadaki hancin Captain,cikin sauri yakai idonsa kan abincin yaga yana turiri, jallop din macaroni tayi musu saboda babu lokaci,tasaka carrot aciki da hanta dakuma ganye,gaba daya ta juye musu macaronin, Sai Kuma farfesun kaza data sake ajiye musu agefe, Alhaji Ma'aruf ya matso ya kalli Alhaji Bala da Captain Aryan yace"Bissmilah muci abinci" Captain Aryan ya kalli abincin yafara tunani aransa gashide yana qamshi,anya kuwa abincin yarinyar nan zaiyi dadi? ganin ga mahaifinta a zaune tareda abokinsa kada sugane baya son cin abincin, saiya saduda yadauki spoon badan yaso ba, yadebo abincin dan qadan,sannan yakai bakinsa, lokaci daya ya lumshe idonsa,baisan lokacin dayakai hannunsa yafara Sosa kunnansa ba,girkin yayi mugun dadi kamar Anty Mamy ce tayi,rabonsa dacin girki maidadin wannan tun ranar auren Ashraf da Anty Mamy takai musu abincin dakinsu. Alhaji Ma'aruf da Alhaji Bala sunji girki sai suka fara zance suna hadawa da farfesun kaza. Captain Aryan kuwa uffan baicewa kawai girki yake kwasa,kafin kace me,daga macaronin, har farfesun sai gashi sun tashi dashi gaba d'aya.(😳) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Mutara zuwa yamma🙏🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻[7/9, 5:59 PM] AMINA KABIR CAPS: *Page 24&25* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki. ____ Alhaji Bala yadauki tissue yafara goge bakinsa yana cewa"masha Allah,Captain girki yayi dadi" Captain Aryan dayake riqeda spoon a hannunsa yana nadama dama abincin bai qareba,yayi murmushi sannan ya ajiye spoon din yana shafa sumar kansa. Alhaji Ma'aruf ya ajiye gorar ruwan datake hannunsa yadaga murya yanda Mawahib datake kitchen zata jiyoshi yace"Ruqayya kina inane, futo zamu tafi" Cikin nutsuwa tafuto daga kitchen din,har lokacin taqi yarda ta Kalli Captain Aryan,Alhaji Ma'aruf da Alhaji Bala suka miqe, Shima Captain ya miqe, Alhaji Ma'aruf yasake kallon Mawahib da kanta yake qasa tana jan yatsun hannunta yace"Babu damuwa deko?" Manyan idanunta me kama Dana masujin bacci irinnasa ta dago ta zuba masa ido sannan yace"Babu komai Abba" Cikin Jin dadi yasaka hannunsa a aljihunsa yadauko rafar kudi Yan dari biyar biyar guda uku yabata yace "Ruqayya, girki yayi dadi sosai, ga tukwicin girkin ki, saiki bayar a ajiye miki" Tanajin abinda yace tagane nufinsa,cikin ladabi ta kar6a tace"to Abba nagode, Allah yaqara budi" Cikin jin dadi yace"Amin Ruqayya,Allah yayi miki Albarka,Allah yabaku Zaman lafiya" Alhaji Bala dayake gefe yace"Amin,Amin ya Allah" Mawahib taqaraso a hankali tamiqawa Captain Aryan kudin,yabi kudin da kallo aqalla zasu Kai dubu dari da hamsin,ya Kalli dogayen hannunta dasuka riqe kudin sirara dasu da tsawo gwanin sha'awa. Alhaji Bala Yazuba musu ido yana kallon tsantsar dacewa awajan,yaga alama Ruqayyan har yanzu kunyar Captain take ji,dubada yanda taqi hada ido dashi tunda sukazo,da alama Captain din yadaga mata qafane bai gama cire mata kunyar amarci ba(😲🙈) gyaran murya yayi,hakan yasa Captain ya kar6i kudin da Mawahib din take bashi,yasaka su cikin aljihunsa. Alhaji Ma'aruf yafara tafiya suma suka biyoshi abaya, har suka futo harabar gidan sannan yace"to zamu wuce,zamuje gwarumfa mukwana,gobe dasafe zamu wuce insha Allah" Captain Aryan yace"Allah yakaimu Abba" Suna tsaye shida ita su Alhaji Ma'aruf suka shige cikin motar,direban Captain yaja suka tafi. Har sukabar gidan,idan Mawahib yanakan motar,duk da bawani sabo tayi dashi ba, taji babu dadi dazai tafi,uba ubane ko Yaya yake. Atare suka jiyo sai akai dace idanunsu ya hadu waje daya,cikin sauri ta janye idanunta tajuya ciki da sauri,Captain Aryan yabita da kallo hannunsa zube cikin aljihun wandonsa. Washegari dasassafe tatashi kamar yanda tasaba,qafafunta tazubo qasa yayinda take zaune akan gado,kayan bacci ne ajikinta Riga da wando light pink,wandon dogo ne yayinda rigar ta kasance yar qarama marar hannu kamar shimi,kayan me santsi ne sosai ya kwanta a lallausar fatarta luf. Tagumi tayi da hannu bibbiyu,tana tunani,Nabiha da Mamy ne take Samun sassauci awajansu,to suma sun dawo suna cewa ta kula da rayuwar auren ta,idan Yaya Captain yasaketa kodan gorin da Hajiya kilishi zata mata bata Isa ta tunkari kano ba saide Kai tsaye tanufi kebbi wajan mahaifinta,idan taje wajan mahaifinta batasan wanne hali zai shiga ba idan yaji ansaketa yanda taga yana farinciki jiya,gara ta sakawa kanta salama ta rungumi aurenta tayi zaman aure kamar kowacce mace tunda tasan saki de babu maganar sa tsakanin ta da Yaya Captain,tasaki ajiyar tareda cire tagumin datayi,dole de akeso ta zauna da wannan mutumin,zata sauke duk wani haqqi nasa,idan an tilasta mata zama dashi ai baza'a tilasta mata tasoshi ba. Ahankali tayi miqa,sannan tasauko daga gadon,tasan ai yau ba aiki,ba lalle yatashi da wuri ba,hakan yasa ta dauki dan qaramin mayafi siriri ta daura akanta ta wuce toilet tayi brush,sannan ta wanke fuskarta tarufe toilet din,sanin yana bacci yasa batareda tunanin komai ba tafice ahaka,yau ko hijabin babu. Kitchen tawuce tafara tunanin abinda zata dafa,bata saniba idan ta dafa dashi zaiji ko bazai ciba,tasan na jiyama datayi wa su Abbanta baici ba, tunda shide tunda suke zamansu ko sau daya beta6a cin abincin taba,wata zuciyar tace da'ita kiyi komai domin sauke haqqin dayake Kanki,ko awajan Allah kin fita. Ajiyar zuciya tasaki,ta dauki wayarta ta kunna data tafara browsing tana ganin ire iren abincin sojoji Wanda yake qarawa sojoji lafiya yagina musu jiki,datar ta rufe sannan tafara qoqarin girkin. cikin kwanciyar hankali tafara girkinta tana qarfafawa kanta gwiwa akan Wanda takewa girki saboda baso take ba,tursasa kanta kawai take, cikin sauri take komai dan tagama da wuri takoma sama tayi wanka. Girkinta yayi nisa qamshi yafara baiyana,adede lokacin yagama gym yadawo gidan,yana Sanye cikin gajeren wando da yar qaramar Riga wadda ta bayyana qaqqarfar surar jikinsa,kamar yanda yasaba idan yadawo zai shiga kitchen yasha ruwa,yau ma yana shigowa falon Kai tsaye yawuce kitchen, tun kafin ya qarasa yaji wani daddadan qamshin girki yana tashi,hakan ya tabbatar masa tana ciki,cak yaja ya tsaya abakin qofar gabansa yayi wata irin faduwa sakamakon kayan jikinta wanda yayi tozali dashi,wanda tsantsin kayan nata yasa kayan ya kwanta luf ajikinta kana ganin tsantsar dirin da Allah yamata. tabashi baya batasan ya shigo ba,aikinta kawai take hankali kwance,shikuwa yazuba wa bajajjan hips dinta ido wanda yake dan rawa kad'an-kad'an saboda yanda take motsa jikinta wajan aikin,kamar da niyya take kadasu,zuciyarsa ce tafara zillo,yaji wani irin abu yana masa yawo tundaga qwaqwalwar kansa zuwa ilahirin jikinsa,gabansa ya tsananta faduwa yana so ya dauke idonsa daga wajan amma yakasa,mamaki yake wannan qanqanuwar yarinyar ce da wannan abubuwan? towai tayaya ta mallakesu?. dankwalin kanta ya kunce yafado kafadarta,dogon gashinta data hadeshi waje daya shima ya baje, cikin sauri ta wanke hannunta sannan takama gashinta ta daure,tamaida dankwalin tarufe kanta, Captain Aryan dayayi mutuwar tsaye yabi dogon gashinta da kallo cikin ransa yake tambayar kansa to kode ba'ita bace?(🤔) jiyayi yanayinsa yana sauyawa,marar sa tadan murd'a, ahankali yasaki ajiyar zuciya. Cikin sauri tajuya cikeda tsoro tace"wayyo Allah na..." tafadi haka cikin tsoro tana matsawa gefe,batayi tunanin akwai mutum a kitchen dinba,tana ganinsa ta lumshe idonta tareda sakin ajiyar zuciya,takalli ingarman jikinsa wanda yake a murde saboda d'aga qarfe,sannan takalli kayan jikinta cikin sauri ta sunkuyar da kanta qasa,tadaure fuskarta,taci gaba da aikin cikin sauri. Ganin zata kamashi yana kallonta cikin sauri yanufi fridge yabude yadauki gorar ruwa guda daya,maimakon yafice daga kitchen din, saiya tsaya yaqi fita yafara qoqarin bude gorar ruwan. Ta gefen ido ta Kalle haka kawai yau ta tsinci kanta da rashin fargaba dakuma tsoron sa,tunda tasan bayason auren itama bataso bataga amfanin daure mata fuskar dayake ba dukda dama hakan dabi'arsa ce, to amma itama gara takoya daga gareshi tadaure tata fuskar itama inyaso ayi wacce za'a yi, batare data kalli inda yake ba tace"ina kwana?" Bai amsa mataba yad'ora gorar ruwan a bakinsa yafara sha,yana satar kallonta qasa-qasa. Mawahib dataji bai amsa ba saitayi shiru taci gaba da aikinta saide duk ta takura saboda tsayawar sa awajan, tarasa menene dalilin tsayuwar tasa, duk saita kasa sauri kamar yanda takeyi kafin yashigo. Saida yagama shanye ruwan tas, sannan yajuya yafice daga kitchen din. Kai tsaye dakinsa yawuce ya watsa ruwa yafuto yana goge jikinsa,yana so yafita da sauri saboda yau babu aiki ogansa yamasa waya zasuyi ganawar sirri a Danjam hotel saboda wani qalubale dayake tunkaro su. Jikinsa yake gogewa da dan qaramin towel amma ita yake gani a'idonsa lokacin daya ganta naked babu kaya,tsayiyun breast dinta suka fado masa,dan qaramin tsaki yasaki tareda jefarda towel din hannunsa, ya zauna akan gadon dagashi sai guntun towel din dayake daure a qugunsu,yadafe kansa da hannunsa cikin damuwa yake tambayar kansa meyake damunsa ne? Wayarsa ce tafara qara, ba tareda yaduba yaga me Kiran ba yadauka yakara wayar a kunnan sa, daga dayan 6angaren Ashraf yace"A&M....." Yanajin haka yagane tsokana ce take damun Ashraf din,wato Aryan da Mawahib,idonsa a lumshe yace"Ash kana lafiya" Ashraf yace"lafiya,Ina Mawahib?" Captain Aryan ya runtse idonsa,Ashraf baisan halin dayake ciki ba yarinya tasashi agaba tana masa gashi ta qarqashin qasa amma shi ita yake tambaya(🙊) Cikin taqaici yace"bansani ba,bakada number tane?"(🙆🏻‍♀️) Ashraf yayi murmushi yace"idan inada number ta inkirata inyi mata mene?" Captain Aryan yace"oho" Ashraf yace"kishi kake?" Cikin sauri Captain Aryan yace"akan wa kenan zanyi kishin? wait....Ashraf, wai ita kakira kaji kokuma nika kira kaji lafiya ta?" Ashraf yace"kaina kira" wata irin ajiyar zuciya Captain yasaki sannan yace"yaushe zakazo?" Ashraf yace"Ina zanzo Ina tareda wannan jarababbiyar yarinyar? tayaya zan tafi nabarta? Ina tafiya zata fara kuka nikuma inajin tausayin ta, saide kaikazo"(😲) Captain yace"bazan Iya zuwaba Ashraf,gaba daya tsoron zuwa gida nake saboda Ina tsoron Momy" Ashraf yace"to shikkenan idan nasamu lokaci zanzo ko daga wajan aiki ne saina qaraso" Captain Aryan yace"nima idan nasamu lokaci inde bakazo dinba zanzo ok?" Daga Nan sukai sallama, wayar daya gama da Ashraf itace tasa yarage tunawa da surar jikinta, harya samu nasara cikin sauri ya shirya cikin qananun kaya riga da wando yayi mutuqar kyau kamar ba gobe. Wanka yayi da turare sannan Yafuto yana bulbula qamshi zuwa falo, adede lokacin tagama shirya komai na abincin zata koma sama tayi wanka,Koda wasa qin kallonta yayi saboda yana tsoro kar yaje gaban ogansa kuma asamu matsala(🙈) yagama lura yau tashin hankali takeji shiyasa taqi saka hijabi, shikuma bai shiryawa wannan tashin hankalin ba,yana zaman zamansa nema take qarfi da yaji tasa azo ana abun kunya atsakani,shikuma bayason raini,kokadan hakan bazata ta6a faruwa ba. ganin zai fice daga falon kamar yana sauri hakan yasa ta kalleshi tace"ga abinci" Batareda ya kalleta ba fuska a daure yace"no,Ina sauri" dan qaramin bakinta taturo gaba,Kenan duk wahalar da tayi tatashi a banza,ita kanta Batasan ya akai ba,kamar an qwato maganar daga bakinta saiji tayi tace"bakaci komai bafa.... " Cak yaja yatsaya yaji yakasa fita,kuma yakasa dawowa. Tunani yafara tunda yaga ta dage yau, gara yasamu ladanta yaci ko kadanne,may be jiya saboda yanajin yunwa ne shiyasa yaji abincin yayi dadi, juyowa yayi zaije yaci abincin, mamaki ya kama Mawahib, Anya Yaya Captain dinne kuwa? itace zata masa magana Kuma yadawo yayi abinda tace? ganin da gaske abincin zaije yaci,yasa tayi sauri tahaye sama. Zama yayi a dining din yabude abincin yana gani,bawani abincin kirki tayi ba, daga ita Sai shi kawai tadafa musu Iya cikin mutum biyu. qamshin da yaji ne yasa yayi Addu'ah Allah yasa yanda yake qamshi Shima girkin yayi dadi duk dade bawani ci zaiyi sosai ba kawai de danya samu ladan tane,abincin yafara ci tundaga spoon din farko yafara jinjina kansa alamun komai yaji. yaci rabi yana tunanin rufewa saiyaga gara yadan qara kadan de,yasake qarawa ya cinye,dayaga sauran wanda ya rage din bashida yawa kawai saiya cinye (🙆🏻‍♀️🙊) Saida yagama cinye abincin sannan yatuna babu saura fa gaba daya ya cinye abincin, yazuba wa Empty plate's din gabansa ido yana kallo,da alama de yarinyar nan itace tasamu ladansa,idan tazo taganshi da wanne ido zai kalleta?(🤔) Cikin sauri yatashi yafice daga falon. Tana hawa sama taga wayarta tana haske alamun anyi mata missed call,tana dubawa taga Mamy ce,tayi mamakin kiran,saboda tasan cewa da weekend Mamy tana dadewa bata tashi daga bacci ba,kiranta tayi,bayan sun gaisa tace"Mamy Ina kitchen lokacin dakika Kira,sai yanzu Naga kiranki" Mamaki ya kama Mamy, yau yaushe tana waya da Mawahib amma babu kuka babu alamun damuwa? Hamdala tayi cikin ranta,tasan cewa addu'ar datake ce Allah ya amsa mata, ajiyar zuciya tasaki tace"kuna lafiya ko?" Tace"lafiya kalau,jiya Abba yazo shida abokinsa da yamma,sai dare suka tafi" sarai tasan Ma'aruf take nufi,amma saita nuna mata bata saniba tace"waye Abba?" Jikin Mawahib yayi sanyi,tace"Abbana,har kudi ma yabani amma nabawa Yaya Captain" Cikin gwasalewa tace"ashe Abban kine" Mawahib tayi shiru cikin sanyin jiki batace komai ba, Mamy ma da taji tayi shiru saitabar maganar tace"babu matsala de kinayi masa girkin kina kuma gaidashi ko?" Cikin sanyin jiki tace"inayi Mamy,yanzu ma nayi masa break fast" Mamy tace"to yayi kyau,ki daina barin gidan da datti kullum kidinga gyarawa,sannan duk lokacin daya dawo daga wajan aiki kidinga kar6ar abun hannunsa,sannan basai Yanemi wani Abu ba kamar abinci ko ruwa,yana zuwa kidinga bashi dan abunsha mai sanyi" Cikin sanyin jiki ta amsa mata, aranta tana tunanin menene ma Yaya Captain yake zuwa dashi dazata kar6a banda bindiga? a fili tace"to Mamy insha Allah" Mamy tace"shikkenan to sai anjima" Cikin sauri Mawahib tace"yawwa Mamy wannan abun nawa yakusa qarewa ki qaromin wani,wannan abun da kika bawa Yaya Captain yakawo min, saura qiris yaqare" Cikin sauri Mamy ta zaro idonta(😳) Sannan tace"wai menene yakusa qarewa? gumbar daya kawo mikin ce harta qare?" Dan qaramin bakinta taturo gaba cikin shagwa6a tace"jiya ma shina wuni inasha,naji da dadi ne,dan Allah ki qaromin wata" Mamaki yakama Mamy,Anya Mawahib kanta daya kuwa?gumbar daya kamata ace ta dade tana amfani da'ita itace take fada mata jiya wuni tayi tanasha Kuma tawaye kalau da'ita bataji labarin tana asbiti ba? to ai ko'ita kanta idan tasha yar kadan,tanaji ajikinta idan tashiga hannun Alhaji(🙈🙊) tanaso ta tambayeta datasha din lafiya kalau suka waye itada Captain din kokuma yakira mata likita ne tazo gida ta dubata? amma Kuma tarasa ta yanda zata mata tambayar kasancewar ta mahaifiya a wajanta. Cikin shan ciki tace"to za'a kawo miki wata robar, nan gaba saina dinga aiko miki babbar roba,amma de bakyajin tsoron kwana ke kadai ko?" Cikin sauri Mawahib dabata gane kan tambayar ba tace"tsoron me Mamy?,Ina gama abinda nake zanyi wankana inyi shirin bacci in kulle dakina intayin bacci na"(🤦🏻‍♀️) Mamy tayi murmushi,ganin cikin ruwan sanyi taji abinda takeson sani, tace"toki gaida Captain din,sai anjima" Tana ajiye wayar tafara tunani,wanne irin zama yarannan suke yine?suna zaune gida daya Kuma su biyu amma ace har yanzu shiru? tasan Captain yanada matsalar haihuwa har sai yasha magani to amma ai ba'a ce yanada matsalar jin sha'awa ba,meyasa bazai nemi matarsa ba? dalilin bazai wuce ace saboda baya son yarinyar bane,ajiyar zuciya tasaki, batada ikon dazata sa Captain yaso Mawahib, amma tanada damar dazata yi musu Addu'ah idan har zaman auren nasu akwai Alkhairi, to ubangiji ya sanya musu soyaiyar junansu acikin zukatansu. Tana ajiye wayar tafasa shiga wankan,kamar yanda Mamy tayi mata magana akan gyaran gidan, duk da bashida datti saida tasake gyara shi, tasaka turaren wuta, tafesa abun qamshi,sannan ta kunna esi afalon,ta wuce dining zataci abinci saide tana zuwa data zauna zataci abinci saitaga wayam babu komai,mamaki ya kamata a fili tace"A a, Ina yakai abincin to?" Wata zuciyar tace da'ita ya cinye mana(😂) Qugunta ta riqe da hannu biyu a fili tace"toni meyake so inci? dama yanason abincin amma girman kai yahanashi ci?, idan nace ga abinci, saiyace no..." tafadi 'no' din tana gwada yanda yake mata magana yana cika yana batsewa ganin babu Captain babu dalilin sa awajan kawai ihu take bayan hari, hakan yasa takoma kitchen ta dauko biscuit sannan tazo tahada tea Mai kauri tasha dashi,tadebe kwanukan wajan takai kitchen ta wankesu ta adana sannan ta koma dakinta tashiga wanka, a lokacin Kuma qarfe goma shadaya na safe. ta dade tana wanka,sannan ta wanke kanta wanda rabon dataje wajan wankin kai tun kafin tazo Abuja,tafuto sanyeda farar rigar wanka mai jikin towel,tadaura dan qaramin towel din akanta,Kai tsaye tafuto falonsu na sama tabude d'ayar qofar falon tafuto tafuto balcony,taduba bakin get taga David baya nan da alama yana cikin dakinsa, tayi maza ta warware towel din dake kanta, sannan ta baje dogon gashinta tana sake warware shi dan tasha is'ka Karkatar da kanta tayi zuwa gefen hannun hagu,gashinta yadawo gefen hagun gaba daya,tasaka towel din tana goge gashin nata,adede lokacin Captain ya danno hancin motarsa cikin gidan,kokadan bataji qara ko alamun shigowar saba,tunda yashigo ya hangota daga inda take,parking ya gyara yafuto daga cikin motar,har zuwa lokacin tana tsaye tana goge gashinta,wayace akare a kunnansa saide bakajin abinda yake fada, yatsaya daga inda yake wayar yana qarewa dogon gashin ta kallo, kamar wasa taji magana qasa qasa, tana dagowa sukai ido biyu dashi, cikin sauri ta janye idonta, ta6ata fuskarta kamar de shi, sannan ta maze taci gaba da abinda take, sannan tajuya tabar wajan. Magana yake awaya amma tunani yake cikin ransa, meyasa take sauyawa ne? gashinta yanada tsawo sosai kamar na Anty Ma-my but meyasa bai ta6a lura da hakan ba saiyau? Ya lura tanada miskilanci sosai,kuma dole zai gyara mata zama bazai lamunci wannan ba. harya shigo falo wayar tana kunnansa yanayi,adede lokacin itama tafuto daga falon sama,ganin yashigo falon yasa tasake gyara towel din kanta,tadaure shi akanta, sannan tasakko zuwa falon, Shima adede lokacin yazauna afalon cikin daya daga cikin qayatattun kujerun falon, fuskarsa tana nan kamar ko yaushe adaure,bata tsaya yimasa magana ba ta wuce kitchen hankalinta kwance,Captain dayake zaune yana waya yana waya yabita da kallo qasa-qasa, rigar wankan tayi mata kyau,manyan hips dinta ya baje sosai acikin rigar, duka tsawon rigar Iya karta gwiwar ta,saida tashige kitchen din gaba daya sannan ya janye idonsa daga kallonta. Fridge ta bude ta dauko masa ruwa Mai sanyi kamar yanda Mamy tasata,sannan ta dauko glass cup ta taho wajansa kanta tsaye. Tana zuwa ta ajiye ruwan agabansa, sannan ta sunkuya ta tabude ruwan tafara zuba masa a cup,sunkuyawar datayi tana zuba masa ruwan hakanne yasa idon Captain yasauka akan madedetan nashanunta,cikin sauri ya runtse idonsa,gabansa yana faduwa,saide daya runtse idon ma wani 6angare na zuciyarsa fizgarsa yafara yi akan yabude idon, ahankali yasake bude idonsa, har lokacin tana sunkuye yasake dora idonsa akansu ko kyafta ido ba yayi,baisaba ganin wannan abu a zahiri haka ba, qare musu kallo yake tsaf, yana tunani aransa dama haka suke,?(🤔) Kwata-kwata ya manta waya yake(🙆🏻‍♀️) Ruwan taturo gabansa, sannan ta miqe zata bar wajan, adede lokacin mutumin dayake magana awaya Yace"Captain ina magana kayi shiru kana Jina kuwa?" Cikin sauri yayi firgigit yadawo hayyacinsa a lokacin Mawahib harta bar wajan, batayi masa sannu da zuwa ba saboda taga yana waya. Gyaran murya yayi sannan yadauki ruwan cup din ya shanyeshi tas, cikin sarqewar murya yace"Inajin ka, sorry,nasha ruwa ne" Daga dayan 6angaren mutumin yayi murmushi,tunda yasamu labari Captain Aryan yayi aure tundaga lokacin yayi masa uzuri zuwa nanda wasu watanni(🙈) Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Har qarfe shadaya nadare yana zaune yana aiki a computer, yaso ace yagama aikin tun kafin weekend yawuce,to amma bai zauna ba, shiyasa ya takura kansa yanason yau komin dare ace yagama aikin. Nabiha tana dakinta,tagama waya da mamanta kenan bayan tagama bata shawarwari akan yanayin zaman nasu, tashi tayi tashiga wanka ta shirya cikin wata yar qaramar rigar bacci doguwa,rigar tayi shara-shara dayawa kana Iya hango komai,Kai tsaye falon tafuto anan taganshi inda ta barshi tun dazu, kitchen ta wuce tahado masa coffee, sannan tazo ta zauna agefensa ta ajiye masa coffee din tace"yaya Ashraf ga coffee" Cikin sauri yadago kansa ya Kalli coffee din sannan ya kalleta,yana ganin yanayin datake ciki cikin sauri yadauke kansa yamaida kan computer yana cigaba da aikin da dayake. Bata damu da rashin maganar saba ta zauna dab dashi tana kallon yanda yake danna computer cikin salon qwarewa, har shabiyun dare suna zaune afalon, shi yana aiki ita kuwa harta fara gyangyadi, ta juya ta kalleshi da idanunta mecike dajin bacci, tana lumshe idonta cikin wani irin salo tace"yaya Ashraf bacci....,please muje muyi bacci" Ashraf ya juya ya kalleta,tasake lumshe idonta cikin jin bacci tace"muje kajiiii" tafadi maganar tajan Kalmar qarshe,zuba mata ido yayi yana kallonta,kayan dake jikinta Wanda dashi da tsirara duk daya,shine yafara fizgarsa,yaji bazai Iya yimata musu ba,ahankali yadaga mata Kai sannan ya rufe computer yatashi tsaye,itama tashi tayi tareda yin wata irin miqa wadda tasa jikin Ashraf yafara rawa,kallon qirjinta yake yanda taturo su gabansa yaji kamar yadora hannunsa akansu, to amma daya tuna yarjejeniyar su da'ita dakuma message din daya turawa mama Sadiya sai yayi sauri yawuce dakinsa. Kai tsaye itama tabishi cikin dakinsa,yana shiga yacire rigar jikinsa, yajuya zai ajiye rigar saiya ganta abayansa, mamaki ya kamashi, kanta daya kuwa? meyake damunta yau?. Ganin yana kallonta fuskarsa adaure nan tagane korarta zaiyi, nan take tafara kukan qarya da kissa,cikin 6acin rai Ashraf ya rufe kunnansa sannan yabude yace"kin dameni,fita" Ya qarasa maganar yana nuna mata qofa,cikin shagwa6a tamatso dab dashi tace"yaya Ashraf ni wallahi tsoro nakeji,ni anan zanyi bacci na" Taqare maganar tana hada jikinsa da nata, saiga Ashraf yayi shiru, Yakasa yimata musu,ganin yayi shiru yasa tadora manyan boobs dinta abayansa, ta zagayo da hannayenta tariqe cikinsa sannan tadora kanta abayansa, cikin muryar kissa tace"ni bacci nakeji" Ashraf yayi shiru yanajin yanda tudun breast dinta yake mintsininsa,nan take yanayinsa yasauya, amma ya gagara yimata komai,numfashinsa yafara fita da sauri da sauri,sai hada gumi yake. Daqyar ya'iya fuzgo magana daga bakinsa cikin yanayin sha'awa yace"wai lafiya?" sake rungume shi tayi, tahade jikinsu tayi shiru alamun bacci take,cikin sauri ya fusgota tadawo gabansa,Nabiha tabude idonta dasauri Jin yanda ya fuzgotan kamar ba fusgowar me hankali ba,kafin tayi yunqurin yin wani abu, yadora bakinsa a wuyanta yafara sakar mata wata irin kyakykywar sumbata,hannunsa yakai kan yar qaramar rigar jikinta yayi kasa da'ita, cak ya dauketa yajefata kan gadon sa,sannan yabi ta yafara kissing din ko'ina najikinta,ganin yanda yake abu da qarfi kamar za'a qwaceta yasa hankalinta yatashi, tafara yunqurin tashi, tayi masa hakan ne danta ja hankalinsa yasaki jiki da'ita harsu fara bacci tare, bawai takawo masa kanta yayi wani abu bane, Ashraf kuwa ganin zata tashi yasa yasake riqeta sosai a jikinsa, hannunsa yana yawo a ko'ina najikinta,cikin fargaba tace"yaya Ashraf yarjejeniyar mu,kayi haquri, niba haka nake nufi ba" Kwata kwata baiji abinda take fadaba, cikin rashin fahimta yace"yarjejeniya,tame?" hannunta yake qoqarin ja yanason dora mata shi aqasan mararsa,cikin sauri ta fizge hannunta,baidamu da hakan ba yadora bakinsa cikin nata,yayinda hannunsa yake kan manyan nashanunta,babu 6ata lokaci yanemi hanya yashigeta cikin fitar hayyaci,Nabiha tasaki wani irin kuka tafara dukansa abayansa amma Yaya Ashraf idonsa yana lumshe yana zubarda hawayen dadi, kokadan Yakasa magana kawai nishi yake kamar Wanda akayiwa dukan tsiya, bata zaci abun zaizo ahaka ba,cikin aza6a take Kiran sunan sa, amma Ashraf kawai abun gabansa yake,tun tana Kiransa cikin muryar ta datake fita, har muryar ta ta dashe kamar me mura saboda kuka,kukan zuci kawai take tana hawaye, tana tunanin itada sake zuwa dakinsa har abada(🙆🏻‍♀️) kusan awarsa daya dawani abu,sannan ya qanqameta yana sakin wani irin numfashi,rungume ta yasake yi a jikinsa sosai idonsa a lumshe yana jin kamar yasake maimaitawa (🙆🏻‍♀️) Cikin muryarta dabata fita tace"Mama nashiga uku na, Yaya Ashraf yakashe ni" Sunan MAMA dayaji ta ambata shine yadawo dashi cikin hayyacinsa, cikin sauri yasaketa yatashi zaune tareda dafe kansa da hannu bibbiyu,salati yafara maimaitawa aransa yana tambayar kansa meya aikata haka? Nabiha cefa wadda sukai yarjejeniya a tsakanin su, wadda yayiwa mahaifiyar ta alqawari babu abinda zai faru. Cikin kuka tace"kamaidani gida,mutuwa zanyi wallahi, kakaini wajan mama,ni kayi haquri zanbar ma gidanka tunda dama baka sona" Cikin sauri Ashraf ya kalleta yace"to meyasa kikazo dakina bayan kinsan ga yarjejeniyar damukai daku?"(😂) Nabiha tayi shiru tana goge jajayen idonta da tasha kuka. Ashraf yasake dafe kansa cikin damuwa,sannan yasake kallonta yace"yanzu dakikazo mukai wannan abun mekikeso na fadawa mahaifiyar ki?"(😂🙊) Nabiha tayi shiru takasa magana, domin kuwa radadin datakeji a qasanta ma kadai ya isheta,batasan meyafaru tsakaninsa da maman taba, kuma batada qwarin dazata tambayeshi. Tashi yayi yadafa ta cikin tausayawa yace"taso muje kiyi wanka" Cikin kuka tace"ni bazan Iya tashi ba, kawai ka maidani wajan mamanah" ganin acikin duhu suke, hakan yasa bai damu dasaka komai a jikinsa ba ya dauketa cak, suka shige toilet ****** Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Dasafe tagama aikin komai kamar yanda tasaba,tayi masa breakfast tashirya komai yanda yadace, ta wuce sama tayi wanka tashirya cikin gajerar riga,hannun bakin less ne da rigar,daga wuyanta zuwa qasan qirjinta duka da milk din less a kayiwa rigar ado,daga qasan qirjinta Kuma rigar ta bude har zuwa qwiwarta,ganin Yaya Captain ba harkarta yake shigaba, ba kallonta yake ba,kuma bahanata shigar datake so yakeyi ba,datasa hijab datasa qananun kaya duk dayane awajansa, hakan yasa tagyara kanta, ta shafa masa mayuka gashinta yadauki sheqi yana walwali,ta fesa turare tafuto falon ko hula bata saka ba bare mayafi, saitayi kyau kamar kasaceta ka gudu. Falon tafuto ta zauna akan kujera tayi tagumi hannu bibbiyu,tunda tafara sakkowa daga sama Captain dayake Sanye cikin uniform dinsu yanayin breakfast cikin jin dadi yazuba mata ita yana kallonta,gaba daya saitayi masa kama da yar larabawa,dogon gashinta ya dauki hankalin sa sosai,har tazo ta zauna afalon idonsa yana kanta, cikin sauri yadauke kansa yaci gaba dacin abincin sa. Tana zama a kujera tayi tagumi hannu bibbiyu,dama haka auren yake? yanzu ita kenan batada aiki sai gyaran gida dayin girki aikin kenan? Idan a gidane Mamy ce zatayi komai saide tataya ta dawani aikin, yanzu kuwa komai itace zatayi babu me taimaka mata da komai,lokaci daya kewar mahaifiyar ta ya kamata,tayi nisa cikin tunani a hankali taji hawaye ya silalo daga idanunta zuwa fuskar ta. Cikin kwanciyar hankali yagama yin breakfast dinsa,shida kansa yaga abincin yaje yazauna yaci, yau ko tayi batayi masa ba, yazo wucewa yaganta tana hawaye, yanason yaji menene damuwarta amma yarasa tayaya zai fara? kokadan bayason ganinta da wannan qananun kayan datake sakawa, takura masa suke,sannan bazai Iya hana ta sakawa ba saboda kartaga kamar tana daukan hankalinsa, wucewa yayi ta gabanta yad'auke kansa,bazai yi kuskuran kallonta daga qarshe kallon yazo ya dagula masa lissafi ba,cikin sauri yanufi qofa zai fice, saikuma yaja ya tsaya awajan cak, tunani yafara aransa, yarinyar nanfa amana ce awajansa,duk da cewa ba lalle ne zaman nasu yadore ba,bai kamata ace yaganta tana kuka,Kuma yawuce yabarta ba,itama wani lokacin tana kyautata masa tunda gashi yanzu ma tabashi kulawa ta hanyar yimasa girki,ajiyar zuciya Yasaki, fuskarsa kamar kullum babu fara'ah yajuyo yadawo falon yazo kanta ya tsaya baice da'ita komai ba,Mawahib tadaga kai ta kalleshi, cikin sauri ta goge hawayen idonta,ta6ata ranta itama,kallonta yayi da fuskar nan tasa ta sojoji yace"lafiya?" Cikin sauri ta girgiza masa kanta, sannan tace"bakomai" Shiru yayi yazuba hannunsa cikin aljihun wandonsa,sannan yazuba mata manyan idonsa yana kallonta,yafara tunani,bayason damuwa kwata kwata,tazauna tana kuka,ya tambayeta lafiya tace babu komai metakeso yamata? shibe saba lallashi ba, be'iyaba. kallon qwayar idonta yayi wanda wani sabon hawayen yake sake taruwa amma taqi basu damar zubowa sai qifqifta ido take,wata is'ka ya furzar daga bakinsa, ahankali yatako gab da'ita, kusancin yayi kusanci a hankali ya tsinci kansa da zama dab da'ita har jikinsa yana gogar nata. (kode lallashin ne yatashi bamu saniba?🤔) Mutara zuwa gobe🙏 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki. Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/10, 10:20 AM] AMINA KABIR CAPS: *25&26* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki. fuskarsa yadan saki,amma duk da hakan ba walwala ce ta bayyana a fuskar ba,saide tafi dazun sakewa,sake nutsuwa yayi ya tausasa murya sannan yace"meyafaru?" hawayen datake riqewa ne yayi nasarar zubowa, tasa hannu ta share,cikin muryar kuka tace"ni Mamy nakeson gani" Shiru yayi yana nazarin maganar ta,baga irinta ba? idan ance sudena yiwa qananun yara aure aga laifin mutum,yanzu irin haka dame yayi kama? wannan ficiciyar yarinyar anrabata da mahaifiyarta,anzo ankawo ta nan an ajiye. yanzu metakeso yace? tayaya zai Iya lallashin mace? Mawahib datake share hawayen idonta,jin Yaya Captain yayi shiru saita fara tunanin kozai lallashetane yace zai kaita wajan Mamyn. Ajiyar zuciya yasauke, bayan yagama tunanin cikin rashin walwala yace"sannu" tanajin abinda yafada baqin ciki da taqaici suka kamata, sannu? ta maimaita Kalmar aranta, lokacin daya ta rushe da muka tadora kanta akan qafafunta taci gaba da kuka kamar Wanda ya daketa. Captain yabi dogon gashinta da kallo wanda ya kwanta a gadon bayanta,yasaka hannu yadafe kansa,metakeso yace mata bayan haka? be'iya lallashi ba tayaya zai fara lallashinta? hannunsa ya janye daga goshinsa bai sake cewa komai ba yatashi yafice daga falon. Wuni tayi tana kuka,gaba daya kewar mahaifiyarta take ji, tagaji da zama waje daya,sai wajan shabiyu na safe tatashi taje ta wanke idonta sannan tadawo falon ta kwanta akujera ta kunna kallo dan dole tanayi. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** wuni tayi tana kuka yau,tana zaune afalo ta bubbude qafafunta kamar zaman masu ciki,idanunta sun kumbura sosai saboda kuka,ga tea nan agefenta amma kokadan taqi sha,hawaye yana sake zubo mata lokaci zuwa lokaci, Ashraf dayake zaune agefe yayi shiru yana kallonta, yayi lallashin harya gaji amma taqiyin shiru, cikin sigar lallashi yace"yanzu mekikeso? mekikeso nayi miki kidaina kukan nan,kinason goyo?"(😳) Cikin kuka ta girgiza kanta tace"nide gida nakeso, kakaini gida, bazan cigaba da zama a gidannan ba" Cikin damuwa yace"shikkenan Ina zuwa " Yana fadar haka yamiqe Yafuto daga falon nasu zuwa compound din gidansa. Wayar Captain Aryan yakira,a lokacin yana tsaka da aiki a office, yadauki wayar, Ashraf yace"Aryan ya zanyi ne,yarinyar nan kuka take ta dameni saina kaita gida" Captain Aryan yace"Okay baki suka hada da yarinyar nan kenan?" Ashraf yace"kamarya?" Captain Aryan yace"yauda safe lafiya kalau fa tasauko,shine kawai ta zauna tana kuka wai Anty Ma-my takeso,nafuto nabarta,bansani ba kota taho wajan Anty Ma-myn bayan nabar gidan" Ashraf yace"Mawahib shagwa6a takeji, lallashinka take buqata" Captain Aryan yace"babu wannan maganar,ban'iyaba,kuma bazan fara akanta ba,idan tagaji da zaman tatafi gidansu qofa abude take,itama kaje kasa driver yakaita gida kokuma kaje kakai musu yarsu,menene aciki? ba'ita ce takeson zuwa ba?" Cikin damuwa Ashraf tace"Aryan bazaka ganeba,yarinyar nanfa komai yariga yafaru daren jiya,inkaita gida ince musu me?" Cikin sauri Captain Aryan yace"what? innalillahi....Ashraf kaje kayi abu kasa inajin kunyar kaina,kaida kake fadamin maganar babu kunya a'idonka amma ni yanzu haka kasa kunya nakeji,wai Dan Allah in tambayeka? meyasa baka kunyar qananun yaran nanne? baka gudun ta rainaka?" Ashraf yace"ni shawara zaka bani ba wani maganar kunya ba,gaskiya ni bazan Iya rabuwa da yarinyar nan bayan abinda naji ba,bansan haka akeji ba,kawai yanzu damuwa ta shine mahaifiyarta" Cikin taqaici Captain yace"Okay bazaka Iya rabuwa da'ita ba bayan abinda kaji?" Cikin sauri Ashraf yace"yes" Cikin haushi Captain yace"maye,saikaci gaba ai" Yace"zanyi,kai har yanzu zubawa Mawahib ido kayi kana kallonta ko?" Captain ya runtse idonsa yana tuno yanayin jikinta,cikin sauri ya bude idonsa yace"Ashraf banda lokacin wannan abun, saina samu wacce nakeso, zanje wajan likita in nemi magani,sannan ne zan zama namiji..." Ashraf yace"Aryan Kenan,shikkenan Allah yakaimu, ni yanzu Yaya zanyi?" Cikin aji yace"inde kasan kanajin zaka Iya zama da'ita Kaci gaba daga inda ka tsaya to karka yarda ka kaita gida,kuma kokaje gida karka yarda kahadu da mahaifiyar ta,nasan zata Iya kiranta awaya tafada mata komai" Cikin gamsuwa Ashraf yace"Okay nagane,to shikkenan bye bye" Daga nan suka kashe wayar. ****** Sai magrib yakoma gida,agajiye yake sosai, yana shigowa falonsu yazube a kujera yafara 6alle botiran gaban rigar sa harya cireta, farar singlet ta bayyana a jikinsa daga saman singlet din kana hango baqin gashi mai laushi wanda yake kwance a faffadan qirjinsa, yasaka hannu yacire takalmin qafarsa, yayunqura zai tashi sai gata,tana Sanye cikin riga da siket atamfa,tayi daurin dankwali simple amma gashinta duk ta barshi abude tayi ado dashi, rigar kasancewar yar qarama ce Kuma ta kamata shiyasa kake ganin nashanunta daga saman rigar, tun tana tahowa ya tsareta da idonsa yana kallonta a6oye,ganin tana sake tunkaro shi yasa yayi saurin janye idonsa,amma ko second daya baiyi ba yasake maida idonsa kanta, shibe tashi ba, shibe koma ya zauna ba,tambayar kansa yake meyasa kowanne kaya yake mata kyau? hartazo gabansa bai janye idonsa ba, ganin kallon dayake binta dashi yayi yawa duk saita takura, cikin ladabi tace"sannu da zuwa,kawo kayan" Ta qarasa maganar tana kar6ar rigarsa da takalmin sa daya cire,babu musu yasakar mata kamar wani soko. Cikin tafiyarta kamar yanda tasaba tajuya tana tafiya hips dinta suna juyawa kamar da niyya takeyi,tafiya take amma gabanta faduwa yake,meyasa yake mata wannan kallon? data tuna Iya kallon nede Shiba sonta yakeba Sai hankalinta yadan kwanta, tanufi dakinsa tabude tashiga akaron farko tun zuwanta gidan. Yana ganin shigewarta dakinsa yadawo cikin hayyacinsa,lumshe idonsa yayi yakoma cikin kujerar yazube, tareda hargitsa sumar kansa, ya lumshe idonsa gaba daya Yarasa meyake damunsa, da yana niyyar hanata saka qananun kaya to yau tasaka manyan amma gashi dan abun kunya yakasa dauke idonsa akanta. Yana wannan tunanin idonsa a lumshe baisan tadawo ba, Sai qamshinta yaji akusa dashi, cikin ladabi tace"akwai Abinci,akawo nan?" Idonsa a lumshe suke har yanzun bai budeba, tunani yafara daga zuwansa daga wajan aiki bayan gajiyar daya kwaso,babu wanda zai taimaka masa yayi wanka, saide abinci, Iya abinda yake Iya samu kenan kullum, kawai koda yaushe abinci abinci (😲😂) yatsina fuska yayi yace"no kibar wannan jagwalgwalon naki, later" yatashi da sauri batareda ya kalleta ba yawuce dakinsa domin watsa ruwa, Mawahib ta bude bakinta tabishi da kallon mamaki harya shige dakinsa,cikeda jin haushi a fili tace"abincin nawane jagwalgwalo?" Zama tayi a kujerar,tana tunanin zata daina yimasa jagwalgwalon saiya gani idan jagwalgwalon yana amfani. Tana zaune awajan ya futo Sanye da kayan shan is'ka,wandon yadan wuce gwiwar sa da kadan,rigar kuma me gajeren hannu,gani yayi ta zubawa TV ido tana kallo amma fuskarta ahade ta6ata ranta,yaga alama yanzu yarinyar nan gani take kansu daya, kwana biyu yaga sai daure masa fuska take, duk kujerun wajan bai zauna a ko'ina ba sai inda take zaune shima ya zauna dab da'ita, idonta yanakan tv duk da taji zuwansa,taji zaman da yayi kusa da'ita bata daga kai ta kalleshi ba,saide kusancin nasu yasata shiga cikin wani hali na faduwar gaba,atsora ce take sosai kawai mazewa tayi bata nuna masa hakan ba,tarasa meyasa yake mata haka, yau dasafe ma kafin yafita haka ya zauna tanajin jikinsa yana gogar nata,qiris yarage ta suma a zaune, shine yanzu ma yasake zama. kallonta yayi yata6e baki sannan yace"zansamu abinci?" Bata Isa tayi gigin yimasa musu ba duk da baqar maganar daya fada mata akan girkin,cikin shagwa6a taturo dan qaramin pink lips dinta gaba, tatashi ta wuce dining din tana buga qafa aqasa kamar zatayi kuka. Captain Aryan yadaga kansa yana binta da wani irin kallo,shagwa6ar tata tayi masa kyau sosai,batare daya saniba yasaki wani irin murmushi.(🙊😳) abincin takawo tazo gabansa ta tsugunna ta ajiye, tasake komawa ta dauko ruwa ta tsugunna zata ajiye,idonsa ya sauka akan nashanunta da suka furfuto tasaman rigar,tana gyara kwanukan bata saniba shikuwa ya shagala a kallon nashanunta yana ganin yanda suke sosai a zahiri,tashi tayi takoma kan kujera ta tazauna yabita da kallo nan take yaji wani irin yanayi me dadi yana fuzgarsa sakamakon nashanunta dayaga sun danyi rawa saboda zaman datayi jagwab akan kujera ba zamane na nutsuwa wanda zai hanasu motsawa ba,yaga alama har yanzu fishi take, kokuma maganar Ashraf ce ta tabbata may be shagwa6ar take ji,idonsa ne suka yi wani iri, kana kallonsu zakasan acike sukeda tsagwaron fitina,sai sukai wani iri kamar yanajin bacci,kallanta yayi,cikin wata irin murya qasa qasa kamar me rada yacemata "waye zai zuba min?" shi kansa tsintar kansa yayi dayi mata tambayar,baisan Yaya akai maganar ta futo daga bakinsa ba,sai yaji kamar an fuzgota daga bakinsa. tsananin mamaki yakama Mawahib,yau kuma? anya yau kalau Yaya Captain yake? Sai magana yake yana zama kusada ita anya ba Yaya Ashraf ne yazo ba shikuma yakoma kano? kallonsa tayi dasauri saboda itade tunda take dashi a gidan doguwar magana irin wannan bata ta6a hadasu ba,aikinta kawai tayi abinci ta ajiye idan yagani inzaici zai dauka,jiyama abinda yasa tazuba masa ruwa dan Mamy tayi mata fada ne akan haka shiyasa, gaba daya atakure take awajan, tunda yadawo maimakon yawuce dining yaci abincin acan shine yasake dawowa inda take, sotake ta gudu daki saboda bazata sake tayi kallonta yanda takeso ba, saide in photon mutane zatake gani amma bazata fahimci komai ba. Cikin nutsuwa ta sauko ta tsugunna tafara zuba masa abincin,Basmatic Rice ce tadafa jallop dinta amma tayi daidai bata caku6e ba, tasaka green beans aciki da carrot,Sai Kuma paper chicken agefe,tunda tafara zuba shinkafar yabi dan siririn hannunta da kallo Wanda yake ganin kamar idan yayi mata qwaqwqwaran ruqo zai Iya karyata, ahankali idonsa ya sauka akan kyakykywar fuskarta, kasancewar idonta yana qasa Sai gashin idonta dasuka hadu waje daya suka sake qawata fuskar tata,idonsa ya gangaro zuwa abinda yafi daukar hankalinsa,idonsa suka fara lumshe wa, baisan meyasa yakejin wannan yanayin ba duk lokacin daya kasance tareda ita,wani irin saliva yafara hadiyewa adede lokacin data zuba masa lemon kwakwa da madara tadago tareda tura masa komai gabansa tace"Gashi" Bata koma kan kujeraba saita zauna aqasa kamar yanda yake ta raku6e agefe daya kanta yana qasa,jira take yagama ta dauke kwanukan tabar wajan. Bai janye idonsa akanta ba sai lokacin data tashi takoma gefensa ta zauna sannan yayi saurin dauke idonsa,yadan sake daidaita fuskar sa takoma yanda take babu wasa,spoon yasaka yafara cin abincin, sannan yasake juyawa ya kalleta yace"saboda kin rainani shine kika kawomin abu kika ajiye min ko?" Ya qarasa maganar cikin sigar tambaya da lallashi. Kanta ta sunkuyar qasa tana kallon yatsun qafarta, mezata ce masa? tabude baki zata ce masa yi haquri Sai wayarsa dake gefenta tafara qara,ahankali tadauki wayar zata bashi, sunan dataga yana yawo a screen din wayar ne yabata mamaki, ASALAMIYYA, batare da damuwa ba ta ajiye masa wayar agefensa sannan tace"gashi" Wayar ya kalla,sannan ya dauka tareda sallama,ahankali Mawahib ta miqe tabar wajan danta bashi damar dazai yi wayarsa, Captain yabita da kallo tareda kashe wayar, yana tambayar kansa meyasa tatashi? Tana shiga dakinta tafara qoqarin cire kayanta zata shiga wanka,dakin ta kulle sannan tacire komai da komai,tadaura towel tashiga wanka domin shirin bacci,bata jima a toilet dinba tafuto tafara shafa mai ajikinta sannan ta fesa turare Kala Kala,tayi parking dogon gashinta sannan ta nannade shi a'inda ribon din yake gaba dayansa,takashe wutar dakin zata kwanta adede lokacin Nabiha takirata,cikin farinciki ta dauka tareda cewa"Nabiha bakiyi bacci ba?" Nabiha tace"ban kwanta ba wallahi,kwana biyu yakike yagida?" "lafiya kalau Nabiha,Ina Yaya Ashraf?" Nabiha tace"hmm yana dakinsa Nima Ina nawa,Ina Yaya Captain?" Mawahib tayi ajiyar zuciya tace"nabarshi afalo yanzu,yanacan yana waya,dazu yagama nunamin halin nasa,Nabiha wai girki nane jagwalgwalo?" Nabiha tace"shine Yafada miki haka?" Cikin damuwa tace"shine wallahi,bazai ta6a sauya halinsa ba,kullum haka yake" Nabiha tace"yaya Captain daba magana yake ba shine ya tanka miki? kuma mekika masa?" Cikin rashin damuwa tace"mezan cemasa Nabiha? aisaina zauna awajan ma bare yasake gasa min wata maganar,nabarshi yana can yana waya da Asalamiyya" Cikin sauri Nabiha datake kwance tatashi zaune tace"kikace me? kinsan me kike fada kuwa Mawahib? wata shegiya takira wayarsa kika taho kika barsu sukadai?" Mawahib tayi murmushi tace"to Nabiha menene aciki? tunda yana sonta saiya aure ta ai,ni sonsa nake? tayaya zan hanashi kula wadda yakeso?" Nabiha ta girgiza kanta cikin fada tace"kina bani mamaki Mawahib,waiku sai yaushe ne zaku zubar da wannan makaman qiyaiyar dakuke yiwa juna? dan bakya sonsa hakan saiya baki damar dazaki bar mijinki kara zube kowacce bola ta kulashi? Idan zaki nutsu kiriqe aurenki dakyau toki nutsu,kinaso ko bakyaso babu saki a auren ku saboda gaba da baya adaure kuke,duk iyayenmu kowa yazubawa aurenku ido aga yaya yanayin zaman naku zai kasance? kisawa zuciyar ki salama kiso mijinki, saboda bazaku ta6a rabuwa ba, Yaya Captain bazai ta6a sakinki ba saboda Mamy, Yaya Captain bazai ta6a sakinki ba saboda Daddy Alqali,Yaya Captain bazai ta6a sakinki ba saboda mahaifinki,idan kika bari yasakeki ma kinsan haduwarki da Mamy,kinsan ba zataji dadi ba saboda kowacce uwa fata take Allah yazaunar da yarta lafiya a gidan mijinta,ga makaman yaqi a hannunki amma kin tsaya kina wasa da damarki,taqamar Momy kilishi de shine Yaya Captain din, kuma aure yariga ya dauru, saboda haka Ina baki shawara ki kama Yaya Captain da hannunki, idan kika riqe shi shine zaki zauna lafiya a gidanki, idan kikai wasa kukaci gaba da zama ahaka bai soki ba, Ina tabbatar miki wataran Momy kilishi tanayi masa maganar auren Asalamiyya to zai amince da auren ta, idan Yaya Captain ya auri Asalamiyya kuwa wallahi kin kade,watarana korarki zaiyi daga gidansa,kuma kidawo gida kusa da Mamy nanma taci gaba da gasa muku baqar magana,tana takura miki, ni bance kisoshi dole ba,amma yanada kyau, ki janyo hankalin mijinki kanki...." Cikin sauri Mawahib tace"amma Nabiha kina ganin hakan zai iyu?,ance ana musu allura karnaje allurar sojojinsa tatashi akaina,Yaya Captain nefa kina ganin...." Kafin ta qarasa magana cikin sauri Nabiha ta katse ta,tace"nasan Yaya Captain ne,shi Yaya Captain din waliyi ne?,kikama shi, kokuma kibarwa sauran mata...." Tana fadar haka ta kashe wayarta,Mawahib tazubawa wayar ido tana tunani Anya zata Iya?🤔 (Nabiha da alama akwai wani tsohon qulli tsakaninki da Captain shiyasa kika bada wannan shawara,...😂) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/11, 9:36 AM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki. Tunani tafara acikin shawarar da Nabiha tabata babu ta yarwa,to amma tayaya ne zatayi hakan bayan bata sonsa sannan kuma baijata ajikin dazata sake dashi harta Iya yimasa wani abu ba? tabbas dan hakin dakai raina shine tsone maka ido,idan bata damu da kiran da Asalamiyya take masaba tabbas wataran zata jita acikin gidannan amatsayin matar sa. Ahankali tasaki ajiyar zuciya,tazuro qafafunta qasa, sannan tatashi tsaye tafuto daga dakin,ahankali take sakkowa tayi tunanin har zuwa wannan lokacin wayar yake,saita hangeshi da computer agabansa idonsa yanakan computer yana aiki,tun kafin ta qaraso qamshin turarenta yagame falon,idonsa ne yake fuzgarsa ya kalleta, amma kuma yakasa,wasu takardu yake gani da'aka turo masa su ta email dinsa,saide yana karantawa ne kawai, amma baya fahimtar komai, tana zuwa falon taga babu plate din dayaci abincin, tajuya ta wuce kitchen anan taga yakawo matasu duka ya ajiye,mamaki ya kamata dama yana aiki?. yanajin shigarta kitchen ya lumshe idonsa yabude, meyasa zuciyar sa take kwadaita masa son ganinta ne? Ajiyar zuciya yasauke,cikin sauri kamar an tsikareshi yatashi yawuce kitchen din shima,yana shiga yaganta a tsaye tana goge abinda data zuba masa abinci da alama wanke su tayi,shigar jikinta ya kalla yaga tasauya wata zuwa kayan bacci ba shigar d'azu bace,ta nannande dogon gashinta abayanta,wata irin ajiyar zuciya yasauke saboda ganinta,kamar wanda yadad'e baisata a'idonsaba, tanajin ajiyar zuciya abayanta tajuya da sauri,yana ganin juyowarta shima yabude fridge zai dauko ruwa,Mawahib tazuba masa ido taga yana dube dube,Kuma shibe mata magana ba,ta tsaya sosai tana kallonsa yayinda shikuma yarasa mezai dauka sai dube dube yake, itace ta katse musu shirun tace"meza'a kawo?" Cikin sauri ya kalleta sannan yadan kawar dakai gefe yace" ruwa" Tace"to" Sannan ta nufo fridge din,cikin sauri ya juya yafice zuwa falo, tana dubawa taga ga gorar ruwan nan dayawa amma Kuma taga shi Sai dube dube yake kamar baiga ruwan ba,amma ko marar gani ne yasaka hannu ya laluba zaiji ruwan,to tunanin meyake dayahanashi ganin ruwan? Wata zuciyar tace da'ita tunanin Asalamiyya (😂) Girgiza kanta tayi sannan ta dauko masa ruwan tareda cup, tadawo falon ta zauna agefensa sannan ta bude ruwan ta zuba masa tace"gashi" Idonsa yanakan computer yayi qarfin halin mazewa bai kalleta ba yace"thanks" shiru sukai na wani lokaci ita tana kallo maganganun Nabiha suna mata yawo a kanta, shikuma yana karanta takardun cikin ransa yana mamakin zamanta. Kuma kokadan yaqi kallonta,cikin zuciyarsa yanason ya kalleta saide Kuma yana kunyar hakan. tana cikin kallon bacci ya dauketa kasancewar da wuri take kwanciya kullum saboda tashi sassafe datake yi, baisan tayi bacci awajan ba,saida yagama karance karancen sa, sannan ya rufe computer zai tashi, yana juyawa yaga ta dora kanta akan kujera tana bacci cikin kwanciyar hankali, mamaki ya kamashi, daga kallo Sai bacci? Kasancewar falon nasu akwai haske sosai hakan yasa Yazuba mata ido yana qare wa halittarta kallo a Karon farko arayuwarsa, ajiyar zuciya yasaki yaharde hannunsa a qirjinsa,yabi bajajjan hips dinta da kallo duk da tana zaune,yamaida kallonsa zuwa ga madaidatan qirjinta Wanda babu brezia amma gasunan atsaye qyam,ya Kalli gashinta dayake da duhu sosai kamar na Mamy,nan take maganar Ashraf tafara dawo masa acikin ransa,(yarinyar tanada qira mai kyau) tambayar kansa yafara meyasa yakeson yawan kallonta cikin kwanakin nan? meyasa yakejin sanyi acikin ransa duk lokacin daya jishi akusa da'ita? Idonsa ya lumshe sannan ya motsa jan lips dinsa yanason yakira Sunanta tatashi amma yakasa,tunda yake da'ita bai ta6a Kiran sunan taba,daga ke,shikkenan saide Kuma yafadi maganar sa Kai tsaye batare daya Kira sunan nataba,yanzun mezai ce? Ahankali yafara dukan kujerar sannan cikin murya qasa qasa yace"ke...,tashi" Cikin baccinta taji kamar ana magana,saitayi juyi ta banqaro qirjinta tana so tajuya tagyara zamanta. Cikin sauri ya kawar da kansa gefe,gabansa yafara faduwa yanajin yanayinsa yana son sauyawa. Ahankali yafara kawo hannunsa jikinta,ya Runtse idonsa sannan yasaka dayan hannun ya dauketa cak yamiqe tsaye, Sai yajita shafal babu nauyi,cikin bacci tasake gyara kanta a faffadan qirjinsa tayi luf, yanda ta motsa kanta a qirjinsa hakan yasa gashinta data daure abaya ya kunce yazubo akan farin hannun Captain wanda yake cikeda gashi baqi,tsayawa yayi cak Yazuba mata ido yana kallonta,yasake gyara mata ruqon da yayi mata, garin gyaran ruqon hannunsa ya damqi hips dinta,lokaci daya yaji wani irin shock ya kamashi,ahankali cikin rashin kuzari yafara taka stairs din zuwa dakinta, da hannu daya ya riqeta, yasaka dayan hannun yabude dakin nata,wani irin qamshi mai dadi yadaki hancinsa,jin yariqeta da hannu daya saitaji kamar zata fadi hakan yasa tasaka duka hannunta tayi masa wata irin kyakykywar runguma (🙆🏻‍♀️) Lokaci daya Captain ya kar6i saqon,nan take suka zube akan gadon nata,rabin jikinsa yafada kanta,jan lips dinsa yasauka akan dan qaramin pink lips dinta,cikin shagwa6a tabude idonta tanaso tayi kuka. ganin zata masa kuka yasa nan take ya rikice,cikin sauri yadagata,gaba daya ya dimauce banda jikinsa dayake wata irin mahaukaciyar rawa,cikin sauri yace"Sorry, sorry okay? sleep...." Nan take Mawahib ta wartsake daga baccin datake,gabanta yayi wata irin faduwa,cikin sauri tayi qasa da kanta cikin wata irin matsananciyar kunya,takasa hada ido dashi. Cikin sauri Shima Yajuya yafice yabar dakin zuwa nasa dakin. Yana zuwa dakinsa yazauna akan gado tareda dafe kansa da hannunsa(🤦🏻‍♂️) meyasa tafarka? yasaka hannu yashafa lips dinsa, yanzu data ganshi tayaya zai Iya sake kallonta?. Kwanciya yayi ko falon baisake komawa ba bare yadauko computer sa,daqyar yasamu bacci ya dauke shi sakamakon wata irin sha'awa data dameshi cikin dare,wadda tasa asubar fari yayi wanka sannan yagyara jikinsa yafita zuwa masallaci. Bayan yadawo kawai wanka yashiga ya shirya, sannan yafice cikin sauri yabar gidan saboda kunyar hada ido dayake da'ita(😂) Mawahib kuwa jikinta tagama qarewa kallo taga de babu alamun wani abu ajikinta,sannan tasamu nutsuwa takoma ta kwanta, saide baccin gaba daya ta nemeshi ta rasa,anya ba sauya Yaya Captain akayi ba? shine yadauke ta da hannunsa? mamaki yahanata bacci da wuri, hakanne yasa ta makara bata tashi da wuri ba,saida gari yayi haske sannan tayi sallah, bata sake gigin komawa bacci ba,tayi azkar sannan tafuto tafara gyara gidan kamar yanda tasaba,ganin har qarfe tara na safe bataji motsin Yaya Captain ba hakan yasa ta leqa ta window anan taga babu motarsa guda daya, hakan ya tabbatar mata da cewa yafita aiki ne. Tunda abun Nan yafaru Captain yafara qauracewa Mawahib,baya yarda su hadu kwata kwata,duk yanda zuciyarsa takeson ganinta haka yake faman yakice tunanin aransa,yanaji idan baiyi nesa da'ita ba wataran zai Iya tafka abun kunya, bayan kuma bada ita ya tsara hakan ba,ya tsara cin amarcinsa ne bayan yasamu wadda yakeso, cikin kwanakin aiki yasaka agaba kawai,idan zai fita Sai yaji babu motsin ta sannan zaiyi sauri Yafuto. Anata 6angaren kuwa hakan bai dameta ba,saima sabuwar rayuwa data budewa kanta tana cin abinda takeso, tana shan abinda takeso, sannan tasaka kayan datake so tayita yin kallo, aikinta kenan, kusan satinsu biyar suna wannan halin 6oyewa junan. Kamar kullum yauma bayan tagama girkin rana,saide ta makara bata gama da wuri ba,Sai wajan qarfe hudu na yamma sannan tagama,David mai gadi ta zubawa sannan tafuto Sanye cikin abaya mai launin pink, tun zuwanta gidan bata cika saka Abaya ba saboda dama tafi sakawa ne idan zata fita, Kuma Abuja tunda tazo ko nan da can bata fita ba,dankwalin abayar ta yana akanta,sannan ta dauko abincin tafuto zuwa compound din gidan. Captain Aryan da abokin aikinsa Captain Shu'aibu suna tsaye a can gefe wajan adana motocinsa, sun baje wata babbar takarda ta taswirar wani daji Wanda aka tura Captain Shu'aibu tareda wasu rukunun sojoji, Kuma shi Captain Shu'aibu shine Wanda zai jagorancesu zuwa dajin, Kuma baisan kan dajin ba, bai ta6a zuwaba, shikuma Captain Aryan yasan ciki da wajan dajin saboda yata6a zuwa can shekarun baya kuma sunyi nasara sosai ansamu abinda akeso, shine yabiyo Captain Aryan din har gidansa yana sake yimasa bayanin wasu abubuwan, Captain Aryan yazage yana zuba bayani yaji shiru Captain Shu'aibu baya magana, yana dago idonsa saiyaga gaba daya hankalin Captain Shu'aibu yanakan Mawahib data futo hannunta daukeda abincin David,tayi fresh da'ita kasancewar babu inda take fita,Mawahib kuwa kwata kwata batasan ma suna gidan ba, saboda bata Kalli inda suke bama. Captain Aryan da yaji shiru Captain Shu'aibu baya responding nasa yadubeshi yace"Captain...." Amma inaaaa Captain Shu'aibu yayi nisa, Captain Aryan yabi inda yake kallo da idonsa anan yayi tozali da'ita,gabansa yayi wata irin faduwa ganin tasake cika farinta yasake futowa,saiyaga tasake girma ma a'yan kwanakin nan da baya ganinta. Ransa yayi wani irin baqiqqirin,Kishi ya kamashi, dama koda yaushe fuska a daure, kuma aka sake 6ata masa rai, yayi wani irin huci cikin tsawa yace"Captain..." Sai a lokacin Captain Shu'aibu yajuyo da sauri ya Kalli taswirar gabansa cikin kame kame yace"na na...na'am, abokina cigaba da bayani" Captain Aryan ya ajiye biron hannunsa cikin 6acin rai, sannan ya Kalli Mawahib cikin tsawa yace"ke,ajiye abun hannunki kikoma ciki, akwai rana" Cikin sauri Mawahib tajuya gefen hannun hagunta,anan taga Yaya Captain da wani dukansu da kayan sojoji a jikinsu,ganin yakoma mata sak Yaya Captain dinta na'asali kuma bataga wani abu datayi ba dazai mata tsawa, hakan yasa ta6ata fuskarta tayi masa wani irin kallo, ko taku daya bata qaraba ta ajiye abincin anan inda take, sannan tajuya cikin sauri. Captain Shu'aibu ya kalli Captain Aryan sannan yace"wacece wannan ne Captain?" Cikin 6acin rai dakuma kishi daya rufe masa ido wanda shi karan kansa baisan da hakan ba, ya dubi Captain Shu'aibu yace"She's my wife...idan kagama kallon saika wuce" Yana fadar haka yabar Captain Shu'aibu a tsaye awajan batare da ya qarasa masa bayanin ba, cikin sauri Captain Shu'aibu yabiyo shi yana kiransa amma Captain Aryan ko juyawa baiyi ya kalleshi ba. Yana shigowa falonsu yafara dube dube yaga batanan, cikin masifa yabita sama, kai tsaye yatura dakinta yashiga, tana zaune agefen gado a tsorace,amma saita dake tadora qafarta daya kan daya tana girgiza qafa kamar gaske, tasan sarai yaga hararar data masa, kuma tasan zaizo gareta bazai raga mataba, kuma itama bazata juraba. Dakin yatura yashigo, ya kalleta idonsa fal 6acin rai, sannan yafara kad'a yatsun hannunsa a fuskarta yatsun suka had'u suka bada wata qara d'as d'as, cikin fishi yace"idan kika kuskura,nasake ganin qafarki awaje,Sai ranki yayi mummunan 6aci,keko nanda kofar falo nasake ganin kinje,saina kakkarya qafafuwanki naturasu kano" ganin yanda ransa ya6aci, hakan yasa tsoro ya kamata amma bata nuna masa ba, cikin 6acin rai itama ta kalleshi tace"toni menayi Yaya Captain?" Idonsa ya zaro mata,ya sunkuyo da fuskarta daidai tasa sannan yaciro bindigar datake aljihun wandon sa yace"to qaramar marar kunya,idan kika sake nasake kafa miki doka kika tsallake toda wannan zanyi maganin ki" Ya fadi haka yana nuna mata bindigar hannunsa. Yana fadar haka yafuto daga dakin tareda rufowa, jikake qofar tabada wani irin qara baram! Mawahib taja baya da sauri saboda tsoro,idonta yayi tsilli tsilli jikinta yafara rawa,taga alama yau a Captain dinsa yake,metayi to? ko wani ne yace masa tayi wani abu?, meyasa yake mata wannan fadan tokode allurar tasu ce ta motsa?, ahankali ta dafe kanta da hannunta wanda yafara yimata ciwo nan take,hawaye masu zafi suka sulalo daga cikin idanuwanta. idan ba allurar suce ta motsa ba ya za'ai da yamma irin wannan zaice wai da rana?, qarfe hudu na yamma wacce irin rana,?wacce irin rayuwar aure take yine? Zamanta tayi adaki bayan tagama shan kukan ko kofar daki bata futo ba,da daddare yana zaune afalo yana cin fruit ko inda abincin data dafa yake bai kalla ba,fruit din yakeci amma masifar Kishi yakeji aransa,sai karkada qafafunsa yake fuskar nan tasa kamar anyi masa albishir da mutuwa, har yakai shadaya nadare a zaune baiga futowar taba Kuma bai nemetaba, wayarsa ce tayi qara yana dubawa yaga Ashraf ne,bayan sungama gaisawa Captain Aryan yace"har yanzu fa Momy bata daukan wayata,Bansan Yaya zanyi ba" Ashraf yace"kayi haquri insha Allah wataran zata sakko,nima Ina bata haquri,amma de ai lafiya kalau Mawahib din ko? Ina nufin babu wata matsala" Ta6e bakinsa yayi yana jijjiga qafarsa daya alamun har yanzu da sauran 6acin rai aransa, yace"Ina zansani da matsala ko babu,tana dakinta Ina falo" Ashraf ya lumshe idonsa yabude yace"Aryannnn...." yaja sunan nasa, sannan yace"kadinga jan yarinyar nan a jikinka please, Kai kadai tasani fa agarin" Cikin 6acin rai Captain yace"Ashraf Sokake in dinga goyata Ina zagaya gari da'ita? nafarko yarinyar nan ba tajin magana ta, Kuma batamin biyaiya,saboda ta rainani, idan Ina zaune bazatazo ta zauna ba,wayarta tafini muhinmanci"(😲😂) Ashraf yayi murmushi yace"to ai kasan yarinya ce,saika koyi lallashi" Captain Aryan ya lumshe idonsa qit yakashe wayar,Ashraf zai sake bashi wata damuwar ne. Har yagama zamansa bata futo falon ba,hakan ba qaramin sake kunnashi yayi ba,gaba daya haka ya kwanta baccin baiyi masa dadi ba. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Washegari yagama shirin sa yafuto zai wuce office,yana zuwa falon yayi tunanin zaiganta amma ko alamar ta bai gani ba, ya kalli dining dinsu nanma yaga wayam babu abinci kodaya, haushi ya kamashi, wato saboda yamata fadane Kenan, tafison yabarta tana nunawa qartin maza jikinta,bazai dauki wannan sakarcin ba,idan tayi wasa falon ma hanata saukowa zaiyi gaba daya(😳🙆🏻‍♀️) Awajan aikin ma gaba daya saiya kasa sukuni, abu kadan saiya 6ata masa rai,idan ya tuno abinda yafaru agida saiya saki tsaki shi kadai, gaba daya sai tunani yahanashi ta6uka komai,cikin damuwa yabar wajan aikin nasu yadawo gida a lokacin qarfe biyu na rana,zuciyarsa sai azalzalarsa take, wani irin sauri yake yana fatan ace yaganta a falon, yana yaqara sowa falon, yaga bata nan, saiya tsaya yayi turus,yajuya ya Kalli ko'ina amma ko motsin ta babu,sama yahau, ya Kalli dakinta kamar zai shiga saiya fasa yashige nasa dakin,yawatsa ruwa yafuto cikin qananun kaya riga da wando yayi masifar kyau sosai, fita yayi yanemo abinci yadawo, zama yayi afalon yabude abincin yafara ci saide ko spoon biyu baiyi ba ya ajiye saboda kwata kwata abincin babu dadi,tariga ta 6atashi da daddadan girkinta,tunani yafara yarinyar nan kuwa lafiya? Cikin sauri yatashi kai tsaye yanufi dakinta,ahankali yatura dakin yashiga, yana shiga ya hangota can qasan gado akan tiles ta lubga bargo akanta tana kuka sha6e-sha6e, gabansa ne yafadi cikin sauri yashigo dakin ya qarasa wajanta ya yaye bargon wani irin zafi yadakeshi,tun abayar jiyace ajikinta,nan take damuwa ta wanzu a fuskar sa,cikin sauri ya birkitota yace"lafiya? meyake damunki?" Cikin kuka Mawahib tace"yaya Captain zanmutu...." gabansa yasake faduwa Jin furucinta,ahankali yakai hannunsa jikinta kamar yana tsoron ta6ata,dagota yayi zaune saitayi sharaf tazube a faffad'an qirjinsa, hawayen datake yafara sauka a qirjinsa,hannunsa ne yafara karkarwa ahaka yasaka hannun a wuyanta yaji zafi rau,cikin damuwa yace"bakida lafiya?meyake damunki? ko zazza6i ne?" gaba daya ya rikice sai tambaya yake zuba mata, idonta ta runtse, hawaye yasake zubowa, batada bakin dazata masa bayani,kwata-kwata bata cikin hayyacinta,cikin tsananin azaba takama hannunsa dayake wuyanta,laushin da hannun nata yake dashi ne yasa yaji wani irin shock,Mawahib kuwa dabatasan halin dayake ciki ba taja hannun nasa Kai tsaye ta dora akan mararta(🙊🙈😳) yanajin hannunsa awajan yakoma ya zauna jagwab aqasan tiles din,kallonta yayi da sauri kuma yakasa janye hannunsa daga wajan,cikin kuka tace"zan mutu,ka taimakeni" Yanajin haka yadawo cikin nutsuwar sa,cikin rashin kuzari ya dauketa cak suka futo daga dakin,motarsa yasaka ta sannan ya zagaya yaja motar suka bar gidan cikin gudu Zuwa asbiti mafi kusa, suna zuwa aka kar6eta,dayake mata ne suka kar6eta tuni suka gano bakin zaren,taimakon gaggawa suka bata ta hanyar yimata allura sannan suka daura mata ruwa,saida ta samu bacci sannan yasamu ganin doctor,likitan ya kalleshi ganin suna yanayi yace"kaine yayanta ko?" Cikin sauri yace"eh doctor,meyake damun tane,? na tsorata da rashin lafiyar,ban ta6a ganin tayi haka ba" Doctor yayi murmushi,yace"karka damu bawani ciwo bane babba,ciwon mara ne wanda mata sukeyi a lokacin da zasuyi menstruation,idan tafarka zaku Iya tafiya,but akiyaye a dinga bata magani aduk lokacin da hakan yazo," Cikin gamsuwa yace"but doctor baza'a Iya yimata wani abuba wanda zaisa tadaina kwata kwata? banaso tasake shiga wannan halin" ganin damuwa qarara a'idon Captain Aryan, hakan yasa doctor yayi tunanin kode saurayinta ne, kokuma sunada kusanci sosai shida marar lafiyar, cikin rashin damuwa yace"akwai sosai ma,idan tayi aure may be zata Iya dainawa idan tayi mu'amular aure da mijin ta" Gaban Captain yafadi,cikin sauri yace"babu wata hanyar?" Doc. Yace"gaskiya babu" Captain Aryan yace"komin qanqantarta babu wata hanyar?" Doctor yace"babu" Cikin sauri yatashi daga kan kujerar yabashi hannu suka sake yin musabaha sannan ya nufi qofar zai fice,Doc. Ya kalleshi yace"yawwa idan kun koma gida ahada mata black tea tasha,sai abata magani" Cikin sauri Captain ya amsa,sannan yafuto daga office din gaba daya jikinsa asanyaye,idan ya fahimci maganar likitan nan yana nufin fa sai sunyi sex shida yarinyar nan,idan hakane kuwa akwai matsala gagaruma,tayaya ma zai bari haka tafaru a tsakanin su? hakan bazata ta6a faruwa ba gara de ya tambayi wani likitan Koda wata Hanyar amma banda wannan hanyar, bazai iyaba,yana zuwa dakin yaga ruwan yaqare amma har yanzu tana bacci,zama yayi yazuba mata ido yana kallonta,fuskarta tayi fayau,karon farko dayaji tausayinta ya kamashi, yanzu haka zata zauna da wanna ciwon kenan? Sun dade a asbitin tana bacci, sai dare suka dawo gida hannunsa daukeda magungunan ta,yaruqota tana tafiya a hankali saide kowa yaqi kallon idon kowa (😂) Kai tsaye dakinta yakai ta,tashiga toilet zatayi wanka shikuma yafice zuwa masallaci,suna idar wa bai tsayaba yadawo gida,Kai tsaye kitchen yashiga yafara dafa mata tea a karon farko arayuwarsa da yayiwa wata mace girki, bayan yagama tea din Yazuba a cup,yasaka mata suger sannan yanufo dakinta,yana shiga yaganta a kwance idonta a lumshe, tarufe jikinta gaba daya da bargo, qarasa wa yayi wajanta sannan ya zauna a bedside drower ya kalleta yace"ga tea kisha" Ahankali ta bude idonta sannan tayaye bargon tagyara zama ta jingina da gadon,cikin sauri ya kawar da kansa gefe ganin shedaniyar rigar datake jikinta wadda yake ganin nipples dinta ta wajan rigar kamar zasu masa magana, hannunta ta kawo ta kar6i tea din,hannunsu yahadu dana juna, bata damu da hakan ba, ta kar6a sannan takai bakinta tasha, cikin sauri ta furzar dashi sannan tabashi cup din da sauri. kar6a yayi ya kalleta sannan ya Kalli tea din yace"meyafaru?" lips dinta ta goge ta nuna masa tea din, hawaye yazubo daga idonta,tasa hannu ta goge sannan tace"gishiri" Ganin hawaye a'idonta ba qaramin rikicewa yayi ba, cikin sauri"gishiri?" yakai tea bakinsa yayi sipping dan kadan yaji yacika uban gishiri a maimakon suger, runtse idonsa yayi cikin sauri yafice daga dakin, sai gashi yadawo da lemon kwali dawani cup din,yazauna abakin gadon sannan ya 6allo mata magungunan ta yabata, yazuba mata lemon Shima yabata, cikin kulawa yace"sorry,bansani bane" Daqyar ta'iya hadiye maganin tana runtse idonta sannan tayi sauri tasake shan wani lemon abakinta, tasha lemon sosai kasancewar bataci komai ba,tana gama sha tafara maida numfashi dasauri dasauri, ba tasan lokacin da tadora kanta akafadar sa ta hannun hagu ba,ta lumshe idonta tana maida numfashi kadan kadan haryaji numfashinta yayi nauyi alamun takoma bacci,yanajin tafara bacci yatafi tunani, yanzu haka zata dinga fama kenan da wannan ciwon every month? wanne irin ciwo ne za'a ce maganinsa shine sex? ai dolene inde anyi bincike asamo maganinsa wanda shima zai samu yabata tasha tadaina yin wannan kukan,amma wanne likita zai sake tambaya, koya tambayi Anty Mamy? But yace mata me? Ajiyar zuciya yasaki sannan yagyara mata kwanciya kanta yadawo tsakiyar qirjinsa,ya Kalli agogon dake daure a farin hannunsa mai cikeda gashi,yaga qarfe goma da rabi,cikin ransa ya ayyana zuwa shadaya kafin nan tayi nisa a bacci saiya zame ya kwantar da'ita shikuma yatafi dakinsa. haka ya zauna yayi shiru banda qaran esi babu abinda yakeji,dogon gashinta ya sakko ya rufe mata fuska,ahankali yasaka hannunsa ya janye mata gashin,yazubawa kyakykywar fuskarta ido yana kallonta,pink lips dinta yake kalla dan qarami yanajin kamar ya gwada tsotsa yaji yanda akeji,saide wata zuciyar tana gargadinsa,yana aikin kallon nata baisan lokacin da bacci yayi awun gaba dashi ba,mararta ce taji tadan tsikareta cikin alamun jin ciwo tadan yatsina fuskarta sannan tasaka hannuwanta duka biyun ta rungumeshi sosai,cikin baccin batareda yasani ba Shima yasake gyara mata kwanciya a jikinsa tareda rungume ta qam qam kamar wani zai qwace masa ita(🙈) (asuba tagari Rukyn Aryan 💃🏼💃🏼💃🏼) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/11, 9:36 AM] AMINA KABIR CAPS: *13&14* wani irin bacci sukai wanda gaba dayansu basu ta6a bacci mai dadin wannan ba,tunda suka shige jikin juna babu wanda yasake motsa wa,baccinsu suke cikin kwanciyar hankali wanda yasa ko kiran sallar asuba basujiba,hannunsa yana jikinta, yayinda tashige jikinsa tayi luf kamar mage,Captain Aryan bai tashi farkawa ba sai qarfe shida da rabi nasafe(😲🙆🏻‍♀️) Ahankali yafara bude idonsa cikin jin dadin bacci,ganinta a jikinsa ga dogon gashinta duk yabazu a fuskarsa hakan yasa cikin sauri yaware idanuwan sa,gabansa yayi wata irin faduwa,shida yake jira minti talatin tayi kafin nan baccinta yayi nisa saiya tafi dakinsa, meyake yi anan? agogon hannunsa ya kalla karfe shida harta wuce saide ace bakwai saura,yatuna baije masallaci sallar asubaba yau,dayayi wata irin zabura yatashi zaune yafara jada baya, hakan yasa itama cikin sauri tafarka,tana ganinshi itama saitayi baya da sauri tana gyara hargitsatstsan gashinta. Kanta yana qasa takasa kallonsa,shima kasa kallonta yayi,cikin sauri yafara saukowa daga gadon yana dana sanin zuwansa dakin gaba daya,batare daya kalleta ba yace"sannu" Cikin sauri ta kalleshi,kode yafara jin tausayin tane? Shi kansa saida yafada yake mamakin kansa,meyasa yake girmamata, meyasa yake tausayinta shi kansa baisani ba,kafin tagama tunanin taji yace"yajikin" Cikin sanyi jiki tace"dasauqi" Duk wannan maganar dasuke babu wanda ya Kalli dan'uwansa,cikin sauri yabar gaban gadon zai fice daga dakin,saida yaje bakin qofa sannan ya kalleta yace"karki dafa komai" Bata Iya magana ba saboda gaba daya mamakin sa yagama daure mata kai, sai kanta kawai data daga masa alamun amsawa. Yana ficewa daga dakin tasaki wata irin ajiyar zuciya menene ya sauya shi haka? dukkan tambayoyinta babu me bata amsa,hakan yasa tasauko daga gadon takashe esin dakin sannan tagyara shi tsaf, ta wuce toilet ta kunna ruwan zafi domin wanka. bayan tagama wankan shiryawa tayi cikin doguwar riga ta material,bata shafa komai a fuskarta ba,falon tafuto ta zauna tana dan daddanna waya kadan kadan, ba tajin ciwon komai yanzu,saide jikinta babu qarfi sosai, David ne yayi nocking tatashi tabude,babbar Leda yabata yace oga Aryan ne yace akawo mata, ta amsa tareda juyowa, zama tayi tabude ledar taga abinci ne kusan kala biyu sai Kuma snacks shima daban, cikin mamaki tabude daya taci dan kadan, sannan takoma sama ta dauki maganin ta tasha. Falo ta dawo ta kwanta a kujera tana tunanin jiya da daddare, itade tasan tabbas ciwo da rashin qwarin jiki yasa ta jingina a jikinsa, amma batun kwanciyar su tare batasan Yaya akai hakan tafaru ba, lumshe idonta tayi tanajin har lokacin kamar qamshin jikinsa yana nan ajikinta. Baidawo gidan ba sai dare,a lokacin tana dakinta a zaune tayi shirin kwanciya tana Sanye cikin riga da wando amma masu kauri,snack ne agabanta tanaci kad'an kad'an kamar bataso. Kai tsaye dakinta yawuce,tana ganin shigowar sa ta kalleshi sannan ta janye idonta tace"sannu da zuwa" Yana tsaye daga bakin qofar dakin yace"yajikin" Kanta aqasa tace"dasauqi" Daga nan bai sake yimata magana ba ya juya yafice daga dakin,dakinsa yashiga yayi wanka,sannan yasanya farar jallabiya,yadawo dakin nata,tsayawa yayi yana waya da Ashraf, Ashraf din yana fada masa yasake musu sabin wayoyi zai turo masa tasa yagani,zama yayi dab da'ita saide bai had'a jikinsa da nata ba, a lokacin tagama cin samosa kenan,yana wayar yana kallonta tagefen idonsa. tun shigowar sa dakin jikinta yayi sanyi taji batada wani sauran kuzari,ahankali tasaka hannunta ta dauki maganin ta ta6allo zatasha,cikin sauri yayi sallama da Ashraf, ya ajiye wayar a tsakanin su, sannan ya kalleta cikin kulawa yace"sannu" kanta ta daga masa sannan tasaka maganin a bakinta ta runtse idonta tasha tafara maida numfashi kad'an kad'an adede lokacin wayarsa dake gefensu ta dauki haske kasancewar yasakata a silent,ganin sunan Asalamiyya a fuskar wayar tana kiransa sai hakan yatuna mata da shawarar Nabiha datake cewa muddin Asalamiyya tashigo gidan Yaya Aryan to haqiqa tata taqare,batasan Yaya zatayi tashawo kan Yaya Aryan zuwa gareta ba,saboda bata sonshi,kana kokarin shawo kan Wanda kakesone zuwa gareka ba Wanda bakaso ba,ahankali tafara yamutsa fuska ganin tunanin yana Neman saka mata ciwon kai, Captain Aryan daya dauki wayarsa zai amsa ganin yanda take yatsina fuska Sai hankalinsa yadawo kanta,ya ajiye wayar ya kalleta da kulawa, cikin rad'a yace"lafiya? ko jikin ne?" Batace masa komai ba amma ta daga masa kanta alamun haka ne,Sannan ta tagyara fillo zata kwanta Cikin damuwa ya sunkunyo daidai kunnanta yace"komu koma asbiti?" Sanin datayi babu abinda takeji cikin sauri ta girgiza masa kanta ma'ana basai sunkoma asbitin ba,hannunsa yadaga zai ta6ata, saikuma yayi sauri yafasa ya janye hannunsa tareda dunqule hannun,wayar ce tasake yin haske akaro na biyu, Mawahib tana ganin kiran ta jinjina kanta tana mamakin wasu matan, zaka kira mutum bai dauka ba, kuma kira da daddare awajan me mata, amma bazasu fasa kiran ba,ta6e bakinta tayi sannan muskuta ta gyara zatayi kwanciyar ta, ahankali tace"wash..." Bata qarasa rufe bakinta ba taji Captain yaruqota gaba daya arikice yafara cewa"Akira miki Anty Ma-my ne kinason waya da'ita?" nanma batace masa komai ba Sai girgiza kanta datayi,ganin yariqeta a jikinsa hakan yasa cikin dabara tafara qoqarin raba jikinta da nasa. Captain Aryan kuwa yayi tunanin ciwon ne yadawo shiyasa take yatsina fuska,hakan yasa bai damu da kasancewar ta a jikinsa ba, yasan sha'anin rashin lafiya ne,da kalau take kokadan bazai aikata hakan ba,yanajin yanda takeson zare jikinta daga nashi, amma bai bata damar hakan ba,sake rungume ta yayi kamar yana tsoron wani zai ganshi,sai gashi ba'a dauki wani lokaci metsawo ba bacci ya dauketa,Captain ya kalleta yaga tayi bacci, ahankali yafara qoqarin kwantar da'ita akan gadon saboda bayaso yasake yarda abinda yafaru jiya yauma yasake faruwa.😂 Cikin dabara yafara qoqarin zareta ajikinsa,tanajin haka tabude idonta,Shima yana ganin haka yafara bubbuga bayanta alamun takoma taci gaba da baccinta,baccin takoma kamar wata Baby, saida takai kusan minti talatin tana bacci, baccinta yayi nisa sosai sannan tajuya tasake gyara kwanciyar ta tahanyar sake riqeshi,Captain Aryan Yasaki wani irin numfashi saboda yanda yaji tasake shigewa jikinsa, ahankali ya matse qafafunsa saboda kartaga halin dayake ciki gashi da jallabiya kuma azo aji kunya girma yafadi,numfashi yake saukewa da sauri da sauri yana kuma jin azaba taciki,🙈 yayinda fuskarsa tacika da gumi sosai,Kuma yakasa raba jikinsa da nata,ahaka yayi kwanan zaune, Mawahib kuwa tayi baccinta cikin kwanciyar hankali. ****** tunda suka tashi yau yaji jikin nata babu sauqi,dalilin wannan qananun zazza6in datake ne yasa ko wajan aiki bai tafi ba wanna satin, kuma taqi yarda suje asbiti,ganin yau jikin nata yayi zafi sosai yasa cikin tsantsar soyaiya da kulawa yasake gyara mata kanta dake kwance a qirjinsa yace"sweet nace muje asbiti kinqi,gashi tun dazu kina kuka,kitashi muje muga likita" Hawaye ne ya zubo mata, cikin kuka tace"dan Allah ya Ashraf kakaini gida Naga mamana karna mutu tunda mukai aure fa banjeba" Runtse idonsa yayi yabude sannan cikin damuwa yace"banason jin wannan maganar,karki sake cemin zaki mutu kibarni kinji ko?" Cikin sauri ta daga masa kanta Yasaka hannu ya share mata hawayen idonta sannan yace"shirya muje gidan,amma dazaran kin ganta,asbiti zamu wuce kin amince?" Cikin sauri ta amsa masa amma cikin ranta tariga ta yanke babu inda zata dawo saita warke,kusan sati uku Kenan kullum cikin qananun zazza6i take, ga tashin zuciya,uwa uba Yaya Ashraf baya daga mata qafa,idan tashiga hannunsa baya yimata ta sauqi,tana fama da zazza6i amma idan yafara abu daya bayason bari, yacika fitina dayawa har bataso weekend yazo yadawo gida(🙆🏻‍♀️) Tsaf ta shirya yariqe hannunta suka futo zuwa cikin motarsa, suna tafiya ahanya tana kallon yanda yake driving cikin kulawa tana sake godewa ubangiji daya mallaka mata abinda take Qauna a Duniya,kai tsaye gida suka wuce,a lokacin qarfe tara da kwata nasafe,Mamy tafuto cikin shirin tafiya aiki tayi tsaf cikin uniform dinta saita gansu sun shigo,ganin yanda Nabiha take tafiya tana hada hanya hakan yasa taja tatsaya turus tace"Ashraf lafiya? meyake damunta?" Momy kilishi data futo daga kitchen itama ta tsaya tana kallonsu,Ashraf ya Sosa kansa sannan yace"Anty Mamy ba tajin dadi ne, zamuje asbiti Sai tace mufara zuwa taga mama tukunna,amma tunda gaki ma shikkenan Sai muje asbitin gaba daya" Mama Sadiya tafuto daga part dinta,cikin sauri Ashraf ya sunkuyar da kansa qasa yace"Ina kwana?" Cikin fara'ah tace"lafiya kalau Ashraf,kune a gidan yau?" Ashraf bai bata amsa ba ya qarasa yagaida Hajiya kilishi. Mamy taja Nabiha jikinta cikin farinciki tace"Amarya...meyake damunki ne?" Nabiha ta rungume Mamy,wani irin hawaye yazubo mata, adede kunnan Anty Mamy tafara mata magana qasa-qasa, "Mamy karki bari yatafi dani Dan Allah,zazza6i nakeji sosai Allah zai kasheni,bashida tausayi Yaya Ashraf mugu ne...."(😳) Gaban Mamy yayanke yafadi,tuni ta gano inda matsalar take,lokaci daya jikinta yayi sanyi,to Ashraf ma Nabiha tana masa kuka,Mawahib datake hannun Soja, awanne hali take ciki kenan?🤔 ganin mama Sadiya tana wajan karta fahimci komai hakan yasa cikin lallashi tafara bubbuga bayanta tana cewa"ya'isa to, kukan ya'isa,zakiji sauqi insha Allah" Hajiya kilishi ta kalle su tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi....,kukan metake to? ko kukan jin dadi ne kukan ganin uwa?" Mamy tayi murmushi cikin sauri tace"A a Yaya,ba tajin dadi ne zazza6i ne yake damunta,amma yanzu ma zasu wuce asbiti saisu ga likita" Mama Sadiya tace"Subhanallah,to amma Maryam bagaki ba? kiduba ta kawai saita zauna tahuta inyaso saiya siyo mata magungunan ko a chemist ne" Mamy tace"to shikkenan," Ta Kalli Nabiha tace"meyake damunki?" Nabiha taja hancinta alamun tasha kuka,cikin murya qasa qasa tace"Mamy zazza6i nakeji,kuma komai naci sainayi amai,kuma nasha magani zazza6in yaqi tafiya" Cikin farinciki Mamy tasake kallonta tace"masha Allah,to Ina zuwa" Tasaketa tashige part dinta, ta dauko wata roba dawani dan qaramin tsinke (pt strip) Sannan tabata robar tace"jekiyo fitsari anan kikawo min" Hajiya kilishi tanajin abinda Mamy tace saitaja ta tsaya tana so ta tabbatar da abinda idonta yake gani,meyake shirin faruwa kenan? Nabiha taje dakinta nada tayi abinda Mamy tasa ta,Sannan tadawo,Mamy tayi gwaje gwajenta ta dudduba idon Nabiha, sannan ta Kalli Ashraf da Mama Sadiya tace"Alhamdulillah,ciki ne da'ita,Nabiha tasamu ciki,zanje asbiti da sauran fitsarinta sai aduba agani wata nawane" Cikin sauri Ashraf ya sunkuyar da kansa qasa gabansa yana faduwa,ga Mama Sadiya awajan, shida yayi alqawari bazai ta6a mata yaba yanzu gashi ciki ya bayyana,wata irin kunya ta rufeshi yaji dama baizo gidan ba,yarasa tayaya zai tashi yafice yabar gidan. Cikin sauri Hajiya kilishi tajuya ta Kalli Ashraf da kansa yake qasa tace" yanzu kai Ashraf kaida kanuna min bakason aure shine daga ganin 'yar mutane saboda tsohuwar jaraba harka lalla6a ka d'kirka mata ciki?"(🙊🙆🏻‍♀️) Ashraf yayi shiru yakasa cewa komai Kuma yakasa dago kansa,gashi Aryan baya Nan bare yatare masa, haka yakasa dago kansa sai qeyarsa dayake sosawa cikin kunya. Cikin farinciki Mamy ta Kalli Hajiya kilishi tace" Yaya wannan ai abun farinciki ne" Cikeda masifa Hajiya kilishi tace"kyace haka kam,gara da Allah yasa Aryan baya haihuwa,shima nasan da yanzu ancika masa gida da 'ya'yan wasu anfake dacewa abin farinciki ne"(🙆🏻‍♀️) Maganar tata tadaki Mamy sosai,taso tayi haquri kamar yanda tasaba, to amma bazai iyu tayiwa 'yarta qwaya daya jal mummunan Fata irin wannan tayi shiru ba, ahankali tayi wani irin murmushi mai ciwo tace"Yaya kenan,Aryan ai Addu'ar ki yake buqata,kiyi masa Addu'ah Allah yabashi lafiya,shima ya haifi dansa na kansa koba ta hanyar 'yataba, idan Kuma ta hanyarta yasamu haihuwar babu yanda zamuyi da hukuncin Allah, dama yariga ya tsara akwai haihuwa a tsakanin su" Cikin sauri Hajiya kilishi tace"Kinga dakata Maryam,karki yiwa dana Aryan fatan hada zuri'ah dake,saide yarki taje can wani kwararon tasamo cikin,amma bata hanyar dana Aryan ba" Cikin sauri Ashraf ya kalleta yace"Haba Momy...,meyayi zafi ne har haka?" Hajiya kilishi ta Kalle shi tace" kaida Allah rufe min baki, shashasha,meka sani dahar zaka tsomo mana baki, da Aryan ya haihu da wannan yarinyar gara in mutu inbar duniya,dana bazai ta6a hada iri da wannan mayyar ba, saide in shegu za'a liqa masa" Ashraf ya sunkuyar da kansa qasa hawaye ya sulalo daga idonsa, Nabiha kuwa kuka take sosai takama Mama Sadiya ta riqe gani take duk itace silar wannan tashin hankalin, data sani batasa Yaya Ashraf yakawo taba,da wannan tashin hankalin gara tabi mijin ta su koma gidansu inma kasheta zaiyi ya kasheta, yanzu gashi tajawa baiwar Allah Mawahib zagi nacin mutunci. Mamy ta kalli Hajiya kilishi,cikin 6acin rai tace"Mawahib bazata haifi shegeba,dan halak zata haifa kuma tareda Captain Aryan,meta tsare miki? yarinyar nan batason auren nan,nima banaso,amma haka nayi haquri itama na tilastata tayi haquri saboda nariga na yarda da hukuncin Allah, ba zanyi jayaiya da qaddarar da Allah yariga yahad'a ba, shiyasa nayi haquri nabarsu, Yaya tunda nake acikin gidannan ban ta6a qin yaranki ba,Ina daukar su ne kamar Mawahib,amma yanda kike nunawa yata qiyaiya nima bazanso ace ta auri danki ba,banda ubangiji yahada aurenta da Aryan wallahi tallahi gara ace Mawahib ta auri mahaukaci data hada zuria dake" Cikin masifa Hajiya kilishi tace"haka kikace?" Mamy tace"haka nace Yaya" Hajiya kilishi tace"yau zan nuna miki raino ba haihuwa bace,zan kira Aryan yazo yasaki yar taki saki uku akan idonki,inyaso kije kibata mahaukaci" Cikin 6acin rai Mamy tahade hannunta waje daya tace"Allah yabaki sa'a yaya"(🙏🏻) Daga Nan tajuya tashige part dinta cikin qunan rai. Hajiya kilishi tabude wayarta tafara qoqarin kiran wayar Captain Aryan. Ashraf kuwa cikin kuka yafice yabar gidan Kai tsaye yaje yasamu mazan gidan dasuke waje,yafada musu komai, sannan yafara qoqarin kiran wayar Aryan.... Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Yana wajan aiki bayan yagama waya da Momy saiga kiran Ashraf,yana dauka cikin sauri Ashraf yace"Momy zata kiraka, karka dauka,kayi sauri kakashe wayarka karta kira tasameka" Captain Aryan yace"aina dauka,munyi magana da'ita tace tana son ganina nida Mawahib yanzu yanzu,Ashraf tunda akai auren nanfa Momy bata daukan wayata,tayaya yau zanga kiranta inki dauka? meyasa zakace karna dauka akwai abinda yake faruwa ne?" Ashraf ya dafe kansa tareda fadin"ya Salam,meyasa zaka dauka?" Alqali dayake gefe yanajin abinda yake faruwa yace"kace masa sutaho din,zanyi maganin matsalar" Ashraf yace"shikkenan,kutaho inji Daddy" Captain Aryan yayi shiru yana tunani bayan sungama wayar,meyake faruwa a gidan? haka kawai rana tsaka ace sutaho gida meyafaru? Ajiyar zuciya yasaki sannan yadauki excuse yataho gida, yana zuwa gida afalo ya zauna ya lumshe idonsa,baisan meyasa ba haka nan yakejin bayason tafiya gidan,yafison suyi zamansu su kadai anan ba tareda sunyi nesa da juna ba(🙈) Mawahib tafuto daga kitchen ta ganshi a zaune,mamaki ya kamata yau shine yadawo da wuri? Kitchen din takoma tahado masa fruit da ruwa takawo masa tace"sannu da zuwa" Cikin sauri yabude idonsa ya kalleta,tana Sanye cikin doguwar riga bubu ta leshi,ruwa kawai yadauka yasha dan kadan sannan yace"ki shirya zamuje gida" Cikin murna Mawahib tace"gida?, wayyo Allah, to bari in shirya" Bata jira amsar saba tahaye sama da gudu cikin murna,yabita da kallo yana mamakin murnar ta,kenan so take sutafi gida ta barshi? 😢😂 Meyasa shi bayason tafiya gidan?🤔 yana nan zaune tafuto hannunta daukeda qaramar jaka hand back,bai damu da cire uniform din jikinsa ba yatashi suka fice daga gidan jikinsa a sanyaye. Kusan awarsu daya a airport sannan suka tashi, acikin jirgi yana kallon window yana satar kallonta yaga sai walwala take,tunda tazo gidan sa, bai ta6a ganinta tana walwala ba, hakan yana nufin atakure take dashi Kenan, lokaci daya ,jikinsa yasake sanyi. Suna sauka yakira direban gidan yaje airport din yadauko su,direba sai satar kallonsu yake ganin yanda sukai mutuqar kyau da dacewa da juna,suna zuwa gida sukaci karo da Mamy da Alhaji Isah a compound din gidan kan Mamy aqasa Abba kuma yana mata magana da alama fada yake mata, cikin murna Mawahib tayi wani irin gudu ta rungume Mamy, Captain Aryan yayi sauri ya sunkuyar da kansa qasa cikin ladabi yabawa Alhaji Isah hannu suka gaisa,Alhaji Isah yace"Captain kun qaraso Kenan,kana aiki antasoka ko?" Captain yayi murmushi yace"babu damuwa uncle" Yajuya ya Kalli Mamy yace"Anty Ma-my" Mamy tasaki fuskarta babu yabo babu fallasa tace"sannunku da zuwa Aryan,ku qaraso ciki " Tafadi haka tana musu nuni da qofar Hajiya kilishi,gaban Mawahib yafadi,daga nan jikinta yayi sanyi saboda tasan zuwa part din Momy kilishi ba Alkhairi bane"😂 Cikin takunsa na sojoji Kuma ingarman namiji maiji da kansa, yayi sauri yawuce gaba zuwa part din mahaifiyar tasa,yana shiga yaga iyayen nasu gaba dayansu,Nabiha ce kawai bata nan amma kowa Yana falon,zama yayi yagaida kowa,suma su Mamy suka shigo Mawahib tana jikin Mamy ta riqeta kamar za'a qwace ta,Alqali yayi ajiyar zuciya sannan yace"Kilishi kece dalilin Zaman mu anan,Ashraf yafada mana cewa zakisa Aryan yasaki matarsa saki uku menene dalili?" Cikin sauri Mawahib tadago kanta ta Kalli Captain Aryan,adede lokacin shima yadago kansa idonsu ya sarqe dana juna,cikin kamewa ya janye idonsa,ahankali itama tayi qasa da kanta bazatace ga yanayin datake ciki ba, itade tasan cewa batason sa,saide azaman dasuke gudanarwa na yanzu bazatace yanayi mata abinda bataso ba, daidai gwargwado yana bakin kokarin sa, soyaiyar sa cede bataji aranta har yanzu,cikin sanyin jiki ta sunkuyar da kanta qasa, tasan cewa tabbas wani abu yafaru. Hajiya kilishi tace"Alhaji kasan de bana qaunar auren nan,kawai fin qarfina akayi,saboda haka idan de nice na haifi Aryan, inaso abani damata ta mahaifiyar sa d'ana yamin abinda nakeso" Tajuya ta Kalli Captain Aryan da kansa yake qasa har lokacin yana tsugunne ko zama baiyi afalon ba, sannan taci gaba cewa"gashinan a zaune tun auren Ashraf na bashi umarnin yasaki yarinyar nan,idan yasan bai sake ta ba,to karya kuskura yasake kirana,amma saboda ban Isa dashi ba, shine yadaina kirana kwata-kwata yaza6i yazauna da wannan tijararriyar yarinyar akan yabi umarnina,kuma muddin Ina raye bazan ta6a daukan wayarsa ba saiya cikamin umarnina,gashinan a zaune, itama yarinyar gata nan a zaune yasaketa,uwarta taje ta aura mata mahaukaci..." Mamy kanta yana qasa,tunda sukazo falon batadago kanta ta Kalli kowa ba,tana jira ne kawai Alqali yayanke hukuncin wannan aure,wani irin hawaye mezafi yazubo daga idon Mawahib, tasaka hannu ta share,ta tabbatar akwai abinda yafaru agidan yau,ta tabbatar anciwa Mamyn ta mutunci yau,meyasa Hajiya kilishi bata sonta? a gaban kowa da kowa taza6i taci mata mutunci saboda qiyaiya. idon Ashraf yayi jajir qiris yarage yafara hawaye. Wayar Captain Aryan tafara qara alamun Kira yana shigowa, yasaka hannu yayi rejecting kiran. A'irin wannan lokacin bashida qwarin gwiwar daukan waya. Kansa yana qasa bai dago ya kalli iyayen nasaba,saide yarasa dalilin dayasa yakejin mummunan faduwar gaba atare dashi. Alqali yayi ajiyar zuciya yace"to kilishi ki kwantar da hankalinki,insha Allah yau wannan matsalar taku zatazo qarshe,dama can abinda yasa mukayi tunanin hada Ashraf da Mawahib aure, saboda wannan sa6anin dakuke samu ne keda Maryam, munyi tunanin idan danki, ya auri yarinyar Maryam,rikicin naku zaizo qarshe,kika nuna baza'a yi wannan aure ba, Kuma daga qarshe Allah da ikonsa Sai ubangiji yayi ikonsa akan Aryan,mukayi haquri bamu bashi umarnin yasaketa mu aurawa Ashraf itaba saboda Allah yariga yayi ikonsa,Sai muka kar6i tsarin Allah da hannu bibbiyu mukayi haquri muka bisu da Addu'ah,amma tunda har yanzu kin nuna bakyason auren,amatsayin ki na uwa,dole zamu baki damar ki,idan de har rabuwar auren shine kwanciyar hankalinki,to zai sake ta" Mawahib tadaga kanta,tajuya ta kalli Captain Aryan taga kansa yana qasa baka gane yanayin dayake ciki, ta Kalli Mamy taga kanta yana qasa har yanzu, Mamy kuwa tariga ta saduda,tasan cewa auren Mawahib yaqare yau,qarshan cin mutunci de yau Hajiya kilishi tamata,tunda gashi agabanta za'a saki yarta,menene yafi wannan ciwo? Menene amfanin zamanta awajan? Ahankali tatashi tafice daga falon gaba daya,Abba bai hanata ba. Alqali ya Kalli Captain Aryan yace"Aryan...kaji yanda mukai da mahaifiyar ka,tanaso kasaki Mawahib" Captain Aryan yaji kamar an doka masa guduma akansa,cikin damuwa yadago kansa ya kalli Hajiya kilishi yace"Momy saki bakyau..."(🙊😳) Gaba daya sai falo yayi tsit,maganar Captain tabawa kowa mamaki,a yanda suka sanshi da miskilanci dakuma sanin cewa baya son auren, ba suyi tunanin zai fadi wannan maganar ba. Cikin Masifa Hajiya kilishi tace"haka Kuma ubangiji ya halasta shi, gatanan a zaune kasaketa" adede lokacin aka sake kiran wayarsa akaro na biyu,yayi shiru ya runtse idonsa yarasa mayake masa dadi,yayinda Alqali yazuba masa ido yana kallonsa yanaso shi Aryan din da kansa yakawo musu qarshan wannan tashin hankali,Ashraf ya kalli halin da dan'uwan nasa yake ciki,yaga kowa yazuba masa ido yana kallonsa anason aga mezai yanke ,cikin sauri dabara tafado masa yadaga murya yacewa Captain "kaje kadauki wayar kadawo" Cikin sauri yadago kansa ya kalli Ashraf,kallo daya Ashraf yamasa nan take Captain yadauki haske,cikin sauri yadaga wayar wadda take shirin katsewa tareda fadin"oga inajinka" Sannan ya silale yabar falon. Hajiya kilishi ta Kalli Mawahib ta watsa mata wani irin kallo,cikin sanyin jiki Mawahib tatashi tafuto daga falon idonta yana tsiyayar da hawaye,sai yanzu ne tasan dalilin kiran nasu, tana futowa daga part din adede lokacin Captain Aryan yagama maganar dayake awaya yajuyo,ahankali yatako yazo gabanta yatsaya,itama tana ganinsa ta tsaya tayi sauri ta goge hawayen idonta,zuba mata ido yayi yana kallonta yakasa cemata komai,yanda yaga hawaye a fuskarta ba qaramin ta6a zuciyarsa hakan yayiba,da'ace ya'iya lallashi da babu abinda zai hana ya lallasheta,baisan Yaya zaiyi da'ita tacire damuwar Momynsa aranta ba,wani 6angare na zuciyarsa ne yake zigashi akan ya rungume ta(🙆🏻‍♀️) kallon compound din gidan yayi, ganin babu kowa hakan yasa ahankali yasake takawa gab da'ita har sunajin hucin numfashin juna,ahankali yasaka hannunsa ya rungume ta sosai a jikinsa har yanajin yanda tudun nashanunta suke ta6a qirjinsa,lokaci daya yafara sakin ajiyar zuciya kamar yaron daya shekara baisha nonon uwarsa ba,hannunsa daya rungume tan yafara motsawa yana shafa bayanta ahankali,hakan yasa Mawahib ta kwantar da kanta a faffadan qirjinsa tayi luf idonta yana tsiyayar da hawaye. cikin wata irin muryar rad'a,data hadu da kasalar jikinsa sukasa muryar tasa tasake yin wani irin laushi,yadora bakinsa asetin kunnan ta yace"Sorry,are you ok?" Adede lokacin Mamy tafuto daga part dinta zataje part din Hajiya kilishi sakamakon kiran wayarta da Alqali yayi,(🙆🏻‍♀️) Kokadan basuji takun tafiyar taba,Mamy tana dago kanta ta gansu a wannan yanayin,gabanta yafadi,cikin sauri tajuya takoma part dinta. Cikin kuka Mawahib tace"please kakaini wajan mahaifina,ni nagaji..." Cikin sigar lallashi yace"kinaso mutafi?" Cikin sauri ta daga masa kanta,yace"Okay let's go" Yana fadin haka yakamo hannunta suka futo sukabar gidan(🙆🏻‍♀️) Suna zuwa bakin get Captain yacewa driver "kaimu Airport" Cikin sauri direba yabude musu Mota suka shiga yadauki hanyar Airport. Mamy tajima afalo hannunta dafe da qirjinta, wacce irin rashin kunya su Aryan suke da ranar Allah kuma a filin tsakar gida basa tsoron a gansu? kasa fita tayi saita window ta leqa,taga basa nan, sannan tafuto takoma falon Hajiya kilishi,har lokacin suna nan a zaune yanda suke,Alqali ya kalli Ashraf yace"ina Aryan din yakene? baigama wayar bane har yanzu? jeka kirashi haka" Ashraf yatashi ya futo ya dudduba ko'ina bai gansu ba, yakoma ya zauna yace"Daddy ban ganshi ba" Alqali yace"to Ina yayi? kirashi awaya kace masa muna jiransa" Ashraf yadauki wayarsa yakira Aryan,wayar tana shiga yabawa Alqali yace"Daddy gashi tashiga" Alqali yace"A a,sakata a speaker inaji" Ashraf yabude waya kamar yanda Alqali yasa shi,saida takusa katse wa Aryan ya dauka, Ashraf tace"Aryan kana inane? tun dazu fa su Daddy suna jiranka" Kai tsaye Captain Aryan yace"Ashraf gaskiya natafi..."(😲) Cikin sauri Ashraf yace" Ina katafi?" Captain Aryan yajuya ya kalli Mawahib datake gefensa tayi luf a jikinsa tana goge hawaye da bayan hannunta, sannan yayi qasa da murya yace"nakoma bakin aikina" Ashraf yace"kakoma aiki kuma? Mawahib dinfa?" Captain Aryan yace"gatanan muna tare,itace tace mutafi,damuwa zatasa mata ciwon kai Ashraf,daga zuwanmu har face dinta yarame,kafada musu mun wuce,ka nuna musu anmin kiran gaggawa ne a office"(🙆🏻‍♀️🙊😂) yana fadin haka yakashe wayar,Ashraf daya saka waya a speaker duk mutanan falo sunajin abinda Captain yake fada saiya qame da waya a hannu yakasa dago ido ya Kalli kowa. (asauka lafiya Captain😂🙏🏻) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/11, 7:47 PM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Kibiya ki karanta cikin salama,yafi sauqi akan abinda za'a barki da ubangijinki Alqali yayi murmushi cikin kunya,ta tabbata de abinda yake zargi yagama tabbata,Aryan yanason matarsa,shiyasa yadauki wuqa da nama yabawa Yaron,tunda shine me aure saiya yanke abinda yake daidai,Alhaji khaleed yayi murmushin jin dadi duk dade maganar Aryan din shima tasashi kunya,Mamy tasaki wata irin asirtacciyar ajiyar zuciya,tana hamdala aranta Hajiya kilishi tanajin abinda Aryan Yafada tadora hannunta aka ta rusa uban kuka tatashi tsaye tace"shikkenan....maryam kin cuceni,kingama da dana, wallahi bazan ta6a yafe mikiba sai Allah yayi mana sakayya dake" Cikin kuka ta wuce dakinta tafara kiran yan'uwanta awaya tana fada musu abinda yake faruwa. Alqali yayi gyaran murya ya Kalli Alhaji khaleed da Alhaji Isa yace"to Alhamdulillah,ban tauyewa kowa haqqinsa ba,Aryan ya nuna mata yanason matarsa,saboda haka Maryam karna sakejin anyi wani tashin hankalin dan Allah,Yara Kuma mubisu da Addu'ah Allah yabasu Zaman lafiya" Gaba daya falon suka amsa da "Amin" Alqali yasake dubawa ya kalli Ashraf da kansa yake qasa har yanzu,kawai jira yake yabar falon yakira Aryan yafada masa komai,yace"kai tashi kaje kadauki matarka kutafi gidanku,Allah yasauketa lafiya" Cikin kunya ya sosa kansa sannan yace "Amin Daddy" yatashi yafice daga falon cikin sauri, daga nan sukai Addu'ah taro yatashi. ****** Suna sauka agida tabude murfin motar tafuto idanunta sun kumbura saboda kukan datasha kafin su qaraso,kokadan taqi yarda tahada ido dashi. bayanta yazubawa ido yana kallonta harta shige ciki, sannan Yasaki wani irin huci mai zafi, hannunsa yazuba cikin aljihun wandon sa sannan yafara takowa ahankali zuwa cikin gidan,yana zuwa falon yaga batanan,kai tsaye yabita sama batare da tunanin komai ba yatura yashiga dakin. Tana zaune agefen gado ta jingina kanta da jikin gadon tafada duniyar tunani, batasan cewa hawaye ne yakebin fuskarta ba, wacce irin qiyaiya Momy kilishi take mata haka? meyasa bata santa? saboda ta kasance agola? haqiqa maganar Nabiha tanakan gaskiya datace muddin tabari Yaya Captain yasaketa to daga ita har Mamy sun shiga ukun su. qamshin turaren Captain data shaqa wanda kokadan batasan ya zauna akusa da'ita ba, shine yasa tatuno irin rungumar dayayi mata agida,dama shima ya'iya irinna yan film? bata ta6a ganin hakan a zahiri ba,Sai gashi yau tagani akanta,ashe yadade yana mata Alfarma bata saniba,ashe andade dabashi umarni yasaketa shine yaqiyin hakan? tasan cewa baya sonta,Kuma bazai ta6a sonta ba,soyaiya bazata sa yaqi sakinta ba, shin saboda Mamy ne yasa yaqi sakinta kokuma saboda mahaifinta? ganin tunda yazauna yaga ko motsi batayi ba kawai tunani take tana faman hawaye hakan yasa yayi gyaran murya,sannan ya'ajiye mata wani farin handkerchief Cikin sauri tadawo hayyacinta,tasaka bayan hannunta ta goge hawayen,sannan tagyara zamanta,shiru sukai duka su biyun,kusan minti biyar sannan yaga sai ajiyar zuciya take, cikin aji kamar baison magana yace"kiyi shiru, keba matar soja bace?" Cikin sauri ta kalleshi cikin ranta tana tunanin sunan daya fada mata, matar soja. ganin tana kallonsa yasa shima yajuyo yasake fuskantar ta dakyau sannan ya Kalli cikin idonta mai kama dana mejin bacci yace"yes...kizama jaruma, kidena tsoro, ba komai akewa kukaba,lalle Anty Ma-my na haquri,haka take haquri da kukanki? bakece kike murna zakije gida ba? yanzu nabaki za6i guda biyu,koki zauna a gidan mij...mijin...mijinki, kokuma kano" Yafadi sunan mijinki din a daqyar kamar yana shakkar fadar hakan, sannan yadauki handkerchief din daya ajiye mata ya dorashi akan cinyarta, yatashi yafice daga dakin gaba daya,Mawahib tabishi da kallon mamaki, dama yana doguwar magana haka? gidan mijin ta? Yana nufin yayarda kenan yanzu shine mijin? tashi tayi tashiga toilet tayi wanka,tasake gyara kanta, sannan takoma kan gadon ta ta kwanta tayi shiru tana tunanin rayuwar aurenta, ita kuma tata qaddarar kenan Uwar miji bata qaunar ta,wayarta ce tayi qara taduba taga Mamy ce, saida tayi ajiyar zuciya sannan tace"Mamy" Mamy tace"Na'am, ya hanya, kun sauka lafiya?" Cikin sanyin jiki tace"lafiya kalau Mamy,munzo tun dazu" Mamy tace"to Alhamdulillah,Allah yahuci gajiya,kidinga haquri de,Kici gaba da yiwa mijinki biyaiya,kina ganin de abubuwan dasuke faruwa,kuma kun tafi bamuyi sallama ba,dakin tafi da gumbar ki ai,nace Anty Kulsum ta aiko miki wata daga maiduguri,saide idan anyi sai abayar akawo miki" Yatsina fuska tayi tace"wai Mamy maganin menene?" Cikin basarwa Mamy tace"kawai magani ne,ko a barshi kar akawo?" Cikin sauri tace"A a kikawo min, yanada zaqi sosai, ni dayan ma banasha" Mamy ta girgiza kanta tace"kici gaba dasha yanada amfani,gobe qawata zatazo taganki, tare muke aiki da'ita anan daga baya sai suka dawo Abuja" Tace"to Allah yakaimu Mamy" Daga nan sukai sallama. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ******* Da daddare tasake wani wankan saboda yanayin period datake ciki,tafuto tashafa mai sannan tafeshe jikinta da turare Kala Kala,tasaka wata irin shedaniyar rigar bacci,wadda kake hango farar fatar jikinta,qirjin rigar bashida girma sosai hakan yasa tayi mata daidai madaidaitan nashanunta suka cika rigar,tagyara kanta sannan ta daure shi, tana tunanin ya kamata ace taje wajan wankin kai,batajin yunwa saboda yanayin damuwar datake ciki na Hajiya kilishi, saide ta samawa Yaya Captain wani abun marar nauyi,futowa tayi daga dakin Sai zuba qamshi take, tasauko tanufi kitchen,a lokacin yana kwance a doguwar kujera yadora computer asaman cikinsa yana browsing,baiga futowar taba sai qamshin ta yaji, kafin yadaga kansa harta shige kitchen, ko minti talatin batayi da shiga ba, tafuto hannunta daukeda plate wanda tadafa masa indomie da dafaffan qwai,yana daga kwancen tunda tafuto daga kitchen yazuba mata ido yana binta dawani irin mayen kallo, kwata kwata yakasa janye idonsa akanta,har itama ta tsargu da kallon nasa, cikin sauri ta sunkuyar da kanta qasa sannan ta qaraso gabansa ta ajiye masa plate din tace"gashi" Computer ya ajiye sannan yatashi zaune ya Kalli abincin yace"banaci" Cikin sauri takalleshi, yadaga girarsa daya yace"Anty Ma-my tasani, banacin indomie banacin dafaffan qwai, saide Ashraf..." Cikin sauri tatashi tadauki plate din tace" bansani ba,zan dafa wani yanzu" Captain Kam baiji meta ce ba, saboda gaba daya tunda tafara magana yazubawa dan qaramin bakinta ido yana kallo,saida yaga bata wajan sannan yadawo cikin tunanin sa,Yasaki wani irin numfashi yabi hanyar kitchen din da kallo,kasa haquri yayi, ahankali yatashi yabi bayanta zuwa kitchen din, yana zuwa ya tsaya abakin qofar kitchen din yaharde hannunsa a qirjinsa yana qare mata kallo,yanda take girkin birgeshi takeyi,tanayin komai a nutse babu sauri bare gaggawa, kasancewar dare ne yasa ba zatayi abu me nauyi na, Banana pancake tafara hada masa,tadauko Zuma ta ajiye agefe tana so idan tagama tazuba masa zuman akai. kallonta yake har lokacin,fuskarsa babu fara a kamar de kullum,tunani yake meyasa duk lokacin datake kusa dashi yakejin komai yana masa daidai?(😲) Baisan dalilin hakan ba,amma yana fatan ace ba sonta yakeba, kunyar Ashraf ma kadai ta isheshi, tayayama za'a ce sone? tayaya zai fara sonta? no kawai sabo ne(🥺) Ajiyar zuciya yasaki, kamar daga sama taji yace"dame zan tayaki?" Cikin sauri tajuya a tsorace,bai damu da tsoratar tataba yatako ya qaraso wajanta yatsaya dab da'ita. Lokaci daya ta rikice,yana ganin yanda hannunta yake karkarwa,cikin rawar jiki tace"nagama" Tafadi hakan gabanta yana faduwa,zuman ta dauka zata zuba yasaka hannunsa ya kar6a, sannan yazuba son ransa,suka futo daga kitchen din, tana gabansa, yana bin bayanta idonsa akanta. Suna zuwa falo bata zauna batawuce sama,wannan baqin halaiyar na Yaya Captain yanasa ruwan kanta yatsaya cak,yana ruguza mata duk wani kuzarinta,tana zuwa daki ta kunna esi sannan tashige cikin lallausan bargonta ta lumshe idonta. Harta haye sama akan idonsa,saida yadena ganinta sannan yasauke numfashi tareda shafa sajen fuskarsa, yafara cin pancake din,yadauki wayarsa yakira Ashraf, yana dauka yace"kasamu kanka Kenan,shiyasa kasamu damar kirana" Murmushi yayi yace"nasamu kaina bayan brother na ya ku6utar dani, Momy rigima,yakuka qare?" Ashraf Yasaki dariya yace"kasan mene? Wallahi karka Kira Daddy,dan sunji komai, wayar nan a speaker Daddy yace nasaka, Kuma dukansu sunji yanda mukai dakai,wallahi kasa kallonsu nayi marar kunya kawai" Cikin sauri yace"what? yasalam,shikkenan magana ta qare, amma Anty Ma-my de bata bata wajan ko?" Ashraf yace"tana nan wallahi,to ya zasuyi? share kawai,yanzu de kafara murna munkusa zama Daddy's,Nabiha tanada ciki" Captain yace"wow kace qwallo tashige...." Gaba dayansu sukasa dariya. Ashraf yace"Ina Mawahib,ka lallashe ta sosai, tasha kuka" coffee din gabansa yasha kadan, sannan yace"yanzu tawuce daki, shiyasa nasamu damar kiranka, datana nan nasan kallonta bazai barni inkira kowa ba, bansan meke damuna ba Ash...,idan tana tare dani inajina cikin jin dadi,zuwa wannan lokacin acikin hayyaci na nake komai,but..idan naci gaba da ganin yarinyar nan, bazan Iya riqe kainaba..." Ashraf yayi dariya yace" ai tun lokacin danaga ka'iya kallon idon Momy kace mata saki babu kyau,daga Nan nasan cewa kakamu,wallahi sonta kake" Captain dayakai pancake bakinsa cikin sauri ya ajiye fork din hannunsa yace"kai a a, tayaya?,bahaka bane,niba sonta nake ba" Ashraf yace"to menene?, Aryan katsaya ka nutsu, ka fuskanci rayuwar aurenku,maganar gaskiya so guda dayane Kuma kanason Mawahib" Sumar kansa ya hargitsa da hannunsa daya Wanda bai riqe wayar dashi ba,ya runtse idonsa tareda fadin "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un....,tayaya?, meyasa nayi wannan saken?,tayaya yarinyar nan taci galaba akaina?" Ashraf yace"to menene aciki? nasan bakai ne kayi dacen mata kadai ba, itama tayi dacen samun miji nagari,ka riqe matarka,kasameta kafada mata kana sonta" Cikin rashin sanin abunyi kamar wani yaro yace"kenan sai Infada mata Ina sonta?" Ashraf yayi dariya yace"emanah,kafada mata" Yace"tayaya? bazan iyaba Ashraf..." Ashraf yayi ajiyar zuciya yace"Aryannn,ka nutsu mana,kaifa Sojane,a 6angaren soyaiya ma inaso Kaci gaba da zama soja,kayi yaqi akan soyaiyar ka harsai kasamu abinda kakeso,karka bani kunya Kai namiji ne,karka koma Kaine kake tsoron Mawahib a yanzu,ka tunkareta...." Jin kalaman Ashraf yasa yaji qwarin gwiwa a jikinsa,cikin sauri yadauki coffee din gabansa, shida bayason zafi a wannan Karon bai damu da zafin dayake dashi ba yadaga duka ya shanye, sannan yafara maida numfashi yace"insha Allah, zanyi yanda kace" Cikin farinciki Ashraf yace"kokaifa" Daga nan suka kashe wayar, Captain Aryan yadoka tagumi hannu bibbiyu,gaba daya ya manta dawani pancake dayake gabansa,Kenan duk alamomin nan da yakeji akanta shine soyayya? wato yanmatan dayake qwacewa Ashraf abaya duk ba sonsu yakeba,yanzu ne zai fara soyayyar kenan, tayaya zaija hankalinta gareshi? tayaya zai birgeta? tayaya zai Iya kallon idonta yafada mata yana sonta? tayaya zai goge laifinsa a wajanta??? (irin wannan quations tsaya na tambayoma fan's din Amnah 🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻[7/13, 5:41 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Washegari da sassafe tatashi tagama aikin komai, tayi masa breakfast tabarshi a dining sannan takoma dakinta tayi wanka tashirya,tafuto Sanye cikin doguwar riga ta material dinkin bubu mai fadi,tayafa dan madaidaicin mayafi taruqo yar qaramar handbag dinta a hannunta, bazaka ta6a cewa tanada aure ba, sakkowa tayi qasa Sai zuba uban qamshi take, a lokacin yana zaune a dining yanacin Yam kebabs din data hada masa, saikuma kunun gyada, tana sakkowa yazuba mata ido yana kallonta, fuskarsa ba'a sake takeba,harta qaraso inda yake idonsa yana kanta, yana kallon yanda taci gayu kamar zataje wajan dinner,Kuma ga jaka a hannunta, saida tazo dab dashi sannan Yasaki ajiyar zuciya ya janye idonsa,zama tayi a daya daga cikin kujerun dining din sannan tayi qasa da kanta tace"ina kwana" Kallanta yayi qasa qasa, sannan yace"lafiya" yazuba mata ido yanacin abincin yana aikin kallonta,jinsa yake cikin nishadi duk da bamagana suke ba,wani irin dadi yakeji aransa saboda ganinta ta tabbata kenan dai son yarinyar nan yake. Mawahib da kanta yake qasa a hankali tadago kanta ta kalleshi,cikin sauri ya janye idonsa akanta saide ya makaro, tariga ta kamashi yana kallonta,bata damu da kallon ba saboda tasan cewa ba komai bane danya kalletan,tasan daga kallon de babu wani abu,ahankali tabude dan qaramin bakinta tace"Yaya Captain...dan Allah idan babu damuwa inaso naje a wanke min kaina" Tunda tafara magana yazubawa lips dinta ido yana kallo,har wani lumshe idonsa yake yana sake kallonta,cikin jin dadi yace"kishirya muje nakaiki" Cikin sauri ta kalleshi tace"aina shirya,nagama komai" fuska babu fara'ah kamar kullum ya girgiza kansa yace"kikoma ki sauya shiga,idan kingama ki sameni a Mota" Mawahib tabi kayan jikinta da kallo taga rigar da fadinta sosai,kokadan bata nuna shape din mutum,menene aibun shigar? ganin babu damar tambaya hakan yasa batayi masa musu ba tatashi takoma dakinta tasaka wata rigar,tafuto,tana zuwa falon taga baya nan,cikin sauri tafuto zuwa compound din gidan, yana tsaye yana waya ajikin motarsa,tunda tafuto Yaqare mata kallo tana Sanye cikin dogon hijab jalbab har qasa,baka ganin rigar data saka, tasaka glass medan fadi jan duhu a fuskarta, tariqe Jakarta a hannunta na dama, kasancewar ta fara tas, Sai glass din yayi mata kyau yasake qawata fuskarta,tana zuwa kusa dashi ya janye idonsa daga kanta, sannan yakashe wayar yabude mata motar da kansa,Mawahib ta qame awajan, tana tunanin kansa ya budewa Mota kokuma ita ya budewa?, kallonta kawai yayi, sannan yajuya yakoma dayan side din yabude yashiga, daga kallon da yayi mata anan ta fahimci cewa yana nufin tashiga, shiyasa cikin sauri tashige sannan tarufe motar suka tafi, David Sai daga musu hannu yake. Suna daukan hanya batare daya kalleta ba yace"cire glass dinnan" Cikin sauri tasaka hannunta tacire, tabude Jakarta tasaka shi aciki, babu wanda yasake magana a cikinsu, har sukaje wajan wankin kai, wanda ita de batasan inane ba, shine ya kaita da kansa, suna tsaya tabude zata fita,taji yace"qarshan number Anty Ma-my" Cikin sauri ta juyo ta kalleshi saitaga atm dinsa yake bata,tana so tace masa akwai kudi a Jakarta to amma tana shakka ganin yanda yahade fuskarsa, babu musu ta kar6a sannan tace"thanks" "idan kingama kikirani" Kallonsa tayi sannan tace"to" tafuto tarufe masa motar, sannan tashige wajan, tana jujjuya atm din nasa a hannunta tana tunani ,qarshan number Mamy ne pin dinsa? wacce irin shaquwa cene a tsakanin sa da Mamy? Saida yaga shigewarta sannan yaja motar yana fatan ace Karta sake maida wannan glass din idonta saboda ba qaramin kyau yamata ba. Ta dade awajan sosai kasancewar gashin nata yanada yawa,kuma saida aka mata harda fulawa ta baqin lalle a hannunta, sannan tabasu atm din suka cire kudin su,ana gama wanke mata lallen takira wayar Mamy bayan sun gaisa zuciyarta daya tace"Mamy dan turomin number Yaya Captain,naje wajan wankin kai yace idan nagama nakira shi" Mamy tayi shiruuuu tana tunani,mata ce take tambaya aturo mata number mijin ta wai yaran nan anya Zaman nan nasu kuwa babu gyara? kina zaune da miji wata da watanni amma bakida number sa wacce irin rayuwa ce wannan?ajiyar zuciya tayi, cikin ranta tace akwai matsala, da sauran gyara,a fili saitace "to bari inturo miki,kingama ne yanzun?" Tace"eh nagama,inaso na koma da wuri saboda baquwarki da kikace zatazo Kuma Kinga har azahar tayi" Mamy tace"to shikkenan Allah Yakiyaye hanya" takashe waya tatura mata number Captain,sannan takira qawarta Hajiya Saudat,bayan sun gaisa Hajiya Saudat tace"yanzu nake shirin kiranki dama, ki turomin address din gidan zanfita yanzu" Mamy tayi ajiyar zuciya tace"Sister Saudat akwai matsala,Zaman yarinyar nan taki akwai gyara, idan kinje inaso kisha cikinta sosai tafada miki duk abinda yake faruwa Sai kiyi settling komai,Ina aiko mata maganin mata tana tambaya ta maganin menene, sannan yanzu haka da'ita nagama magana tana tambaya ta number mijin..." Sister Saudat tace"haba sister Maryam,to tayaya zakibarta haka bazaki kirani da wuri ba Kuma yarinya tana zaune a'irin wannan garin, gari garin 'yan boko Kuma mijin ta me yawan fita salon yaje yagano wata a waje?" Cikin damuwa Mamy tace"Saudat bazaki gane ba, naci buri sosai akan auren Mawahib,nabaki labarin yanda auren ya kasance de,a yanda na tsara maiduguri naso turata duk su koya mata komai ayi mata gyaran jiki kamar ma wata biyu,to komai yazo a baibai, Ma'aruf ya ruguza min komai" Sister Saudat tace"to shikkenan, yanzu de ki kwantar da hankalinki,zanje gidan ai, duk yanda ake ciki zakijini" Daga nan sukai sallama tareda kashe wayar. ****** Wani soja ne yazo ya dauketa ya maida ta gida, tana zuwa tacire hijabin jikinta tafara qoqarin girkawa baquwar tata abinci,bata gama ba Sai yamma, saboda tahada harda girkin Captain tayi komai gaba daya,tayi wanka ta zauna afalon kenan, David yashigo yasanar da'ita tanada baquwa,ta bashi umarnin yashigo da'ita,saida yakawo ta har falo sannan Yajuya, Mawahib tatareda cikin farinciki,sister Saudat ta rungumeta tana kallon tsarin gidan nasu cikin ranta tana yabon kyan gidan, zama sukai a kujera Mawahib ta gabatar mata da abincin da tayi mata tareda lemuka da ruwan sha,ta kunna musu kallo sunayi, sister Saudat tadage tana kallon duk da ba ma'abociyar kallon bace,amma dan Mawahib din tasake da'ita yasa tasaka kallon agaba sunayi suna fira kad'an kad'an har yamma,saida taga Mawahib din tasaki jiki da'ita sannan tace"karatu yafara nisa Kuma gashi Captain yagudo dake Abuja" Cikin murmushi tace"A a baiyi nisa ba,ai yanzu ne zamu shiga level 200" Sister Saudat ta jinjina kanta sannan tace"hakane fa,to amma ai zai barki Kici gaba da karatun ko?" Tace"bansani ba wallahi,ban ta6a yimasa maganar ba" kafin sister Saudat tayi magana Captain yashigo falon,gaba dayansu qofar suka kalla,Mawahib tana ganinsa tayi qasa da kanta, tace"sannu da zuwa" bai amsa mataba ya tsugunna cikin ladabi yacewa sister Saudat"sannu da zuwa,barka da yamma" Cikin farinciki tace"yawwa sannu da zuwa,ya aiki?" Kansa a qasa yace"Alhmdulillah" Daga nan yatashi yawuce sama,Sis Saudat ta bishi da kallo cikin ranta tana fadin lalle 'yar tasu tayi dacen miji irin wanda kowacce mace take burin samu. Mawahib tadago kanta taci gaba da kallo ko inda Captain yake bata kalla ba, cikin mamaki sister Saudat tace"bazakibi mijin naki bane?" Zaro idonta tayi sannan tace" la'ila...aibana zuwa" Sis Saudat ta jinjina kanta sannan tace"Meyasa?" Mawahib tace"ai agida ma bayaso muna zuwa dakinsu,nikuma tsoro nakeji" Cikin shan ciki Sister Saudat tace"eh Kuma hakane,dole Kiji tsoro,babu dadi ka takura wa mutum,amma idan yanason wani abu fa yakuke?" Mawahib tace"ai girki ne kawai,idan nayi masa na ajiye masa shikkenan,zaizo yaci,girkin ma da bayaci, shine Mamy tace inci gaba dayi masa" Sister Saudat ta zubawa Mawahib ido tanajin komai, tace"amma duk dadin girkin ki bayaci? yanzu yanaci sosai ko?" Tace"yanaci yanzu,idan yaci zai fita wajan aiki" Sis Saudat tace"to idan yadawo yana sake fita ne? kokuma zama kukeyi agida?" Tace"wataran yana fita,amma ba sosai ba,nide dakina nake tafiya inyi bacci shikuma yana aiki a falo" Sis Saudat ta Zaro ido tace"bacci?" Mawahib tace"eh,saboda nagaji,kullum sainayi gyaran gida da girki" Sis Saudat ta kalleta ayanda tadanji zancen nata ta fahimci abubuwa dayawa,cikin sigar dabara tace"to yanzu kitashi kije dakinsa kiji koda abinda yake buqata, Kinga yadawo daga wajan aiki,Kuma Ina zaune afalon,bazai Iya futowa yazo yazauna ba, kije kiyi masa sannu da zuwa idan akwai abinda yakeso sai kizo kikai masa" Mawahib tace"to" Sannan tatafi sama cikin ranta tana mamakin wannan baquwa,Kuma daga zance saita turata dakin Yaya Captain? to taje ta masa me? Sis Saudat tabi bayan Mawahib da kallo ta girgiza kanta,da alama girman qashi ne da'ita kawai,amma batada wayo,tuni matan bariki zasu Iya qwace mata mijin... tana zuwa bakin qofar dakin takama handle din dakin ahankali tatura tashiga a karo na biyu tunda tazo gidan,wani irin sanyin esi da daddadan qamshi ya daki hancinta,adede lokacin ya futo daga toilet yasaka hannunsa biyu yana gyara sumar kansa,murdaddan jikinsa ya baiyana sai sheqi fatarsa take,tana ganinsa tayi sauri tajuya baya tareda runtse idonta tana jiran taji saukar duka kamar yanda yata6a cewa zai daketa lokacin dataje dakinsu. Kallonta yayi,yana mamakin zuwanta dakin, ahankali yatako yazo dab da'ita,kamar zai rungumota tabaya,yadan karkatar da kansa dede kunnanta cikin rada yace"lafiya?" Cikin sauri ta girgiza masa kanta,jitake zaiyi mata masifa saitaji sa6anin haka,saima magana daya mata cikin rad'a. ganin batason hada ido dashi ne yasa yajuya yazauna abakin gadon sannan yace"bani mai" rikicewa tayi,cikin sauri tajuya wajan mirror ta dauko masa wani mai batasani ba shi yake shafawa koba shi bane, ta qarasa wajansa kanta aqasa taqi kallonsa tace"gashi" Kallon fuskarta yayi yaga idonta a runtse,da alama a rikice take,wani dan qaramin murmushi yayi cikin jin dadi yasake cewa "bani kayana" Cikin sauri tasake juyawa tabude Wadrob din tarasa wanne kaya zata bashi? ganin yamma ce Kuma tasan yafi saka kayan shan is'ka saita dauko masa qananun kaya,ta bashi, yana kar6a tayi sauri zata fice daga dakin taji yace"zonan" gabanta ne yafadi,mekuma zata masa? Ahankali tajuya taqarasa wajansa ta tsaya kanta aqasa tana wasa da hannunta, kamar wasa taji ya fuzgota saigata d'are d'are akan cinyarsa,idonta ta runtse hannunta na hagu ta dorashi akan qirjinsa da fatar jikinsa tayi sanyi sosai, kallonta yayi yaga idonta a runtse,dan qaramin bakinta Sai motsi yake amma takasa magana,meyasa ne wasu lokutan take tsorace dashi? ya kamata ace yafara qoqarin cire mata wannan tsoron nasa, hannunta dayake kan qirjinsa ya kalla ahankali yasaka hannunsa ya janye hannun nata,sannan zubawa fulawar hannunta ido yafara murza hannun, wani iri Mawahib tafara ji ajikinta, wani irin yanayi wanda tunda take bata ta6a Jin irin wannan yanayin ba,amma idonta a runtse yake har lokacin,daina murza mata hannun yayi,cikin sigar rad'a yace"yaushe aka miki wannan abun?" Sarai tasan da zanen lallan hannunta yake,batareda tabude idon ba tace"awajan wanke kai" Cikin wata irin murya qasa qasa kamar meyin rad'a yace"shine baki nunamin ba? i luv it..." Yafadi haka sannan yakai hannun saman lips dinsa,ya lumshe idonsa yasakar mata wani irin kiss Cikin sauri tabude idonta ta kalleshi,a lokacin shima yabude idonsa suka zubawa juna ido tsawon yan sakwanni,cikin ranta take mamaki dama yana lura da wannan abun? cikin sauri tafara motsa wa zata bar jikinsa, bai hanata ba yabarta tatashi,saide tana zuwa bakin qofar dakin tun kafin tabude taji yace"wait.." Cak taja ta tsaya awajan,amma koda wasa batayi kuskuren juyowa ta kalleshi ba, tashi yayi yasaka kayansa, yafesa turare sannan yatako yazo wajanta,kudi yabata me yawa yace"kibata tasha mai" Kanta ta gyada masa sannan tace"to Allah yasaka da Alkhairi" Yaji dadin addu'ar data masa,baice da'ita komai ba, yakamo hannunta suka futo, saida sukazo falon qasa sannan yasaki hannunta yafice daga gidan gaba daya Sister Saudat taga yanda yaruqo hannun Mawahib din amma saita maze ta nuna bata gansu ba har Mawahib kusa da'ita tazauna, tana zama taji tana wani qamshin turaren daban,tayi murmushi cikin jin dadi da alama akwai abinda yafaru,taji dadin hakan sosai,Mawahib tabata kudin tace"gashi yace kisha mai" Sister Saudat takalli wannan uban kudi cikin ranta tafara tunani irin wannan kudi haka ai dole nema ta hurewa yarinyar nan kunne Shima yaga canji(🙊) Cikin farinciki tadauki kudin sannan tace" kice nasa d'an namu wahala,to kice masa nagode sosai" Tamatso kusada Mawahib din sosai takama hannunta duka biyun tace"toki saurareni dakyau kina Jina?" Mawahib tadaga kanta dasauri tana kallon cikin idonta,hannunta na dama yanakan na hagu tana shafa inda Captain yasakar mata kiss dazu,har yanzu tanajin abun acikin jikinta. Sister Saudat tace"akwai kayan dana taho miki dasu suna cikin mota, su zaki dinga sakawa karki sake shiga irin wannan tajikinki,wannan kayan kine tunna gida karki sake sakasu,kuma kidaina kwana adakin ki ke kadai,kidinga tafiya dakin mijinki Kuna kwana tare,abinci kidinga sakashi agaba yanaci yana kallonki kokuma ki zauna kuci tare,banaso nasake ji kince idan kikaje dakinsa wai bayaso ko agida, gida daban Mawahib,can gidanku ne gaba daya, nan Kuma gidanki ne kekadai Sai abinda kika tsara sannan zaiyi,sannan magungunan da mahaifiyar ki tabaki kici gaba da amfani dashi kullum kinji abinda nace?" Cikin sanyin jiki tadaga kanta, sister Saudat tace" yawwa,muje ki rakani ni tafiya zanyi" Tashi sukai tarakata har wajan motar ta,tabude motar ta janyo mata wata uwar jaka tabata sannan sukai sallama tatafi,Mawahib ta janyo jakar tajuyo cikin gida jikinta a sanyaye tana tunanin maganar sister Saudat, kai tsaye dakinta ta wuce da jakar tazauna akan gado tabude duk tafitar da kayan ciki,wasu irin shedanun kayan shan is'ka ne dana bacci abun babu dadin gani inji ustaz. kayan ta d'ad'd'aga tagama kare musu kallo, tasan cewa tun agida Mamy tana siyo mata qananun kaya tana amfani dasu amma wannan kayan na daban ne,tayaya zata Iya saka su taje dakinsa? anya bazai yimata fadaba? (sister Saudat Captain yana godia💃) Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Kasancewar yasan akwai baquwa a gidan hakan yasa bai dawo ba sai dare,saide harya dawo gidan yana mamaki aransa menene yakawo ta dakinsa dazu? wani tunani yayi Kode wannan baquwar ce taturo ta? Idan kuwa hakane zuwan ta yamasa dadi zai so ace Koda yaushe tana kawo musu ziyara(😂) Murmushi yasaki yashafa sumar kansa a lokacin daya rufe motarsa Yafuto, wayarsa ta dauki qara,yana dubawa yaga abokin aikinsa ne, Kuma abokinsa, suna mutunci sosai dashi, ya karanci halaiyar Captain Aryan hakan yasa suke mutunci sosai, yana dauka Bayan sun gaisa abokin nasa yace"Captain nayi shiru nazuba ma ido naga har yanzu bakada niyyar kawo mana Amarya mugaisa, to yanzu madam dina tamin magana da kanta,tace akawo mata qawarta su gaisa kada suhadu awani wajan Kuma ayi abun kunya" Captain Aryan dayake cikin walwala yace"karka Captain Habib tunda gobe babu aiki insha Allah zamuzo" Cikin farinciki Captain Habib yace"amma da munji dadi sosai,Allah yakaimu goben, zan fadawa Madam" Batareda yace komai ba yakashe wayar. Yana shiga falon yaga bata nan, da alama tana dakinta, Kai tsaye dakin nata yanufa adede lokacin tagama maida kayan da sister Saudat takawo mata ta adanasu,tana gwada kiran wayar qawarta Jidda,Sai gashi yashigo, tana ganinsa kiss din dazu yafado mata arai, cikin sauri ta sunkuyar da kanta qasa tace"sannu da zuwa" Kallonta yayi batareda ya amsa ba yabata ledar hannunsa, cikin ladabi ta amsa sannan tace"nagode" Kallonta yayi yanaso su kasance tare amma yarasa yanda zaiyi yafada mata hakan, kuma shiba ma'abocin surutu bane bare yajata da zance,haka dan dolensa ya haqura,harzai fice saiya sake dawowa yace"kishirya gobe zamuje unguwa" Batare data Kalli qwayar idonsa ba tace"to Allah yakaimu" Idonsa ya lumshe sannan ya futo daga dakin badan ransa yaso ba. Yana fita daga dakin tasaki ihun murna tafada kan gadonta,dama tagaji da wannan zaman,cikin murna tasake sakkowa tabude ledar daya kawo mata,kayan gyaran gashi ne masu tsada,mamaki ya kamata,wai meyake damun Yaya Captain ne? Murmushi tasaki sannan tasake duba kayan tanata jujjuyasu, sannan ta dauke ta ajiyesu a'inda ya dace. harta kwanta ta tuna da maganar sister Saudat datace karta sake kwanciya ita kadai,tasaki ajiyar zuciya ta Kalli kayan jikinta,idan taje yace me yakawo ta, me zata cemasa? girgiza kanta tayi,tawuce inda ta 6oye tsimin ta da Mamy tabawa Yaya Captain yakawo mata, tadaga gorar gaba daya ta shanye shi tas 🙆 Sannan takoma gadonta ta kwanta. Kasancewar yawon takeso hakan yasa sassafe tatashi tagyara gidan kamar kullum sannan tashiga kitchen tafara kokarin hada musu breakfast,potatoes crush take hadawa,tana soya naman dazata hada aciki yashigo kitchen din,dagashi sai gajeren wando da singlet,itama rigar baccin tace ajikinta bata cireba,doguwar rigace har qasa, saide Kuma jikin rigar yanada santsi sosai, ko Yaya ta motsa Sai jikinta ya nuna,tanajin shigowar sa tajuya ta kalleshi, cikin sauri ta janye idonta tace"ina kwana" Kallonta yayi yadage girarsa daya batare daya amsa ba,yatsaya daga bakin qofar kitchen din yanajin wani irin farinciki yana lullu6eshi,amma fuskarsa bata nuna hakan ba, tana nan adaure kamar kullum,cikin sigar rada kamar bayaso wani yaji abinda yakeson fada yace"bani ruwa" Cikin sauri tasaki spoon din hannunta tabude fridge din zata dauko masa ruwan, mamaki ya kamashi, saurin metake haka kamar Wanda zatayi laifi idan taqara seconds bata bashi ruwan ba? Meyasa har yanzu takasa sakewa dashi ne? Yaya zaiyi da'ita? bai gama tunanin ba tanufoshi da sauri zata bashi ruwan garin sauri tatake gaban doguwar rigar ta tatafi luuu zata fadi,ko qafarsa bai motsa daga inda yake ba cikin sauri yasaka hannunsa yataro ta, madedetan na shanunta dabata saka musu bra ba suka sauka cikin tafin hannun Captain(🙆🏻‍♀️) yanda yayi niyar riqe jikinta dakyau dan karta fadi, haka yakaiwa nashanunta wani irin ruqo. Lokaci daya numfashin Mawahib yake neman tsayawa cak, tazaro idonta waje.(😳) Captain Aryan kuwa laushin nashanunta da santsin rigar jikinta yasa yaji ilahirin jikinsa ya kar6i wani irin kyakykywan saqo Wanda yasa ya lumshe idonsa nan take, Kuma yakasa sakin abinda ya riqe din(🙈) zuciyarsa ce take zigashi akan ko sau dayane ya matsa ko kadan ne yaji abinda akeji, saide kafin yagama yanke shawara Mawahib data ji shiru yaqi sakinta, cikin sauri tafara qoqarin raba jikinta da hannunsa,cikin sauri shima yasake ta,yakai dubansa ga gorar ruwan data fadi,anan idonsa ya sauka akan gaban gajeren wandonsa yaga halin dayake ciki, cikin sauri yajuya yafice daga kitchen din batare dayasha ruwan ba,yana zuwa dakin sa yazube kan gado yayi kwanciyar rub da ciki ko hakan zai rissinar da halin dayake ciki,yajima ahaka, sannan yatashi ya shige toilet din dakin. Mawahib kuwa aikin take amma gaba daya jikinta karkarwa yake,ta Kalli rigar jikinta tanajin kamar ta yageta ta zubar saboda taqaici,da tasaka yar qarama daduk haka bata faru ba,takai hannunta tashafa breast dinta guda daya Wanda Captain yariqe,tunda take babu Wanda yata6a kuskuren Kai hannunsa wannan wajan,amma yau a Karon banza Yaya Captain ya kama matashi,wani irin taqaici da haushin kanta ya kamata,haka tayi abincin a gurguje ko yayi dadi ko Kar yayi haka de tagama tareda tea, takai musu dining sannan ta wuce dakinta domin watsa ruwa. Bayan tayi wanka ta shirya cikin leshi mai launin purple dinkin riga da zani,tazauna ta tsara kwalliya sosai tayi kyau, tunda tazo gidan bata ta6a zama tayiwa kanta zanen kwalliya sosai kamar yau ba,ta kalli dan qaramin agogon hannunta irinna mata taga qarfe goma shadaya da kwata,da niyya taqi sauka qasa da wuri saboda batasan ganin Yaya Captain,ta lura yanacin galaba akanta sosai akan abubuwa dayawa,yaganta tsirara haihuwar Mamy,yanzu kuma abun yawuce gani da ido yakoma ta6awa, to tun kafin abun nasa yakoma matsawa gara tafara ja baya dashi,saida takai shadaya da rabi sannan tafuto hannunta riqeda mayafinta dakuma jaka da wayarta,a hankali take sakkowa daga stairs din kamar batasan taka qasa,a lokacin yana zaune yana cin abincin data hada musu,tun tana sakkowa yazuba mata ido yana qarewa shigar jikinta kallo,meyasa kowacce shiga take mata kyau ne? waye yakoya mata gayu haka? Wata zuciyar tace dashi Anty Mamy, kwalliyar idonta ya kalla cikin ransa yace"Beauty" Zama tayi a kujera tana duba agogon hannunta,kallonta yayi yace"zonan" Kasa kallon idonsa tayi,ahankali tatafi kanta aqasa taqaraso wajansa ta tsaya tana murza hannunta,kallon hannun nata yayi Wanda yaji baqin lalle, yaso ya maze saide Kuma bazai Iya hana zuciyarsa abinda takeson ta6awa ba,dan haka yakai hannunsa kan nata hannun ya janyo ta dab dashi sannan yace"zauna Kici abinci" Saitaji wani iri banbarakwai,tayaya zai sata cin abinci agabansa bayan kowa abincinsa yake ci? bata gama tunanin ba yaja mata kujera fuskarsa a tsare yace"seat..." Babu musu ta zauna,yana ganin zamanta yatashi da kansa yazuba mata komai sannan yatura gabanta,yazuba mata ido yana kallonta. Jikin Mawahib yayi sanyi tarasa gane meza tayi? Tunda take dashi basu ta6a Zaman cin abinci tare ba,asalima tun agida ma basu saba hakan ba,dago idonta tayi ta kalleshi,Yajuya manyan idonsa yayi mata nuni da abincin,babu yanda ta Iya tasa fork tafara cin potatoes crush din,tanaci ahankali kamar bataso tana juya dan qaramin bakinta,amma koda wasa taqi kallonsa,wayarsa yake dannawa yana turawa Captain Habib saqon cewa gasunan zuwa,zuciyarsa tana azalzalarsa akan yaci gaba da kallonta, saide bayason yawan takura mata da kallon,ya lura har yanzu akwai sauran rashin sakewa a tsakanin su,wanda dole shine zai yi maganin wannan matsalar da kansa. Dan kadan taci,tasha ruwa tace"nagama" Dago kansa yayi ya kalleta,baice da'ita komai ba yadauki tissue guda d'aya yanufeta dashi,dan zaro idonta tayi, gashi babu damar musu fuskarsa a tsare take kamar kullum,tana ganin yakawo fuskarsa dab da tata tayi sauri ta runtse idonta gabanta yana faduwa,zuba mata ido yayi yana qarewa kwalliyar tata kallo,kusancin nasu yayi qaranci dayawa har tanajin yanda hucin numfashinsa yake sauka akan fuskarta,lips dinta dayasha janbaki ya kalla,ahankali yafara kawo bakinsa dab da nata yanaso ya shanye mata shi ya Kuma yimata last warning karta sake sakawa inde zasu fita,cikin sauri zuciyarsa ta gargadeshi akan aikata hakan,cikin kasala yadan ja baya kadan, sannan yadora tissue din akan lips dinta yafara goge mata janbakin, saida ya gogeshi tas, idonta yana runtse,tanajin yagama goge mata kwalliyar ta wani irin hawaye ya silalo daga fuskarta,kallon hawayen yayi, yasaka yatsansa guda daya yagogi hawayen sannan cikin rada yace"why?...." Cikin sauri ta sunkuyar da kanta qasa ta goge hawayen idonta sannan tace"ka 6atamin kwalliya ta" wani irin murmushi yasaki Wanda bai shirya ba,cikin ransa yana sake tabbatar da maganar Ashraf lalle Mamy tagama shagwa6a yarinyar nan,but... yaji dadin shagwa6ar,idan tana masa irin haka tayaya zai iya riqe kansa? Hannunta yakama yace"muje" Cikin sauri tatashi sai turo dan qaramin bakinta take gaba, ahaka suka qarasa wajan motar,shida kansa yabude mata tashiga, sannan yazagaya yaja sukabar gidan. Har sukai nisa da gidan babu wanda yace komai,kallonta yayi yace"me kika za6a?" Kallonsa tayi fuska a cunkushe tace"name?" Shiru yayi yana nazari tayaya zaice mata meta za6a zaman gidansa ko zaman kano? bai sake magana ba, Kuma bai bata amsa ba, saide ita cikin ranta tana tunani Kenan yanaso yaji shita za6a kokuma kano? Kafin ta bashi amsa suka qaraso bakin get din gidan Captain Habib,horn yayi maigadi yazo yabude masa,yana ganin sa Yasaki murmushi ya russana yana kwasar gaisuwa,Captain Aryan yasaka hannunsa yabude wani waje a motar yadauki kudi yabawa megadin,mamaki ya kama Mawahib,shin duka sojoji ne sukeda kyauta kokuma de shine ahakan shiyasa yake siye zuciyar mutane? Yana kashe motar yacire belt dinsa, itama tafara kokarin cire nata,kallonta yayi yaga belt din yana Neman zame mata daurin dan kwalinta,to yagoge janbaki ma tana masa kuka karkuma yanzu belt din motarsa yacire dan kwali shikuma ta masa ihu, hakan yasa cikin sauri yace"wait..." Cak ta tsaya,ya matso dab da ita yafara janye belt din,yanda ya matso din har tanajin yanda numfashinsa yake sauka a wuyanta,belt din yakeson cire mata amma idonsa yanakan qaramin lips dinta yanaji kamar yahade bakinsu waje daya, daddad'an qamshin turaren tane ya rinjayeshi,lokaci daya yafara fitar dashi daga hayyacinsa,har baisan lokacin daya dora dogon hancinsa akan wuyanta ba,yafara yawo da hancinsa a dukkannin wuyanta yana shaqar qamshin nata,yayinda idonsa yake a lumshe, kwata kwata ya manta da inda suke. Gabanta ne yafara faduwa,anya Yaya Captain kuwa yana cikin hankalinsa kwana biyun nan? Meyasa yake mata irin wannan abubuwan ne? Cikin sauri tayi gyaran murya,sai alokacin yayi firgigit yadawo hayyacinsa,cikin sauri yacire mata belt din,sannan yabude mata motar,tana ganin haka kuwa cikin sauri tazuro qafafunta waje,shima futowa yayi,suka shiga cikin gidan jikin Mawahib a sanyaye. suna qarasowa falon matar tasa tataho da sauri ta rungume Mawahib,kana ganinta kaga wayaiya,Captain Habib yabawa Captain Aryan hannu suka gaisa cikin farinciki sannan suka qarasa shigowa cikin falon suka zauna, matar tasa ta Kalli Mawahib tayi murmushi tace"Amarya bakya laifi" Mawahib tayi murmushi tare sunkuyar da kanta qasa Captain Habib ya Kalli matarsa yace"Nusaiba kawo musu ruwa mana" Cikin farinciki tatashi tayi kitchen domin kawo musu ruwan,batafi minti uku ba sai gashi tafara kawo musu abun motsa baki dangin snacks tasake kowama kitchen din,Captain Habib ya Kalli Mawahib tace"Amarya kin rikita mana angon naki gaba daya mun kasa ganeshi, Captain Aryan baya Makara wajan fita aiki amma tunda ya aureki sai ahankali,idan yaje wajan aikinma bashida nutsuwa yana ta6a dan aikin dan kadan ko ba'a bashi excuse ba saiya gudu gida,ga jarabar tunanin ki dayak.... " kafin ya qarasa cewa dayake,Captain Aryan yafara tarin qarya(😂) Sosai yariqe qirjinsa yana tari kamar gaske,tunda yafara zuba wata irin kunya takama Captain Aryan yanaji kamar ya nutse awajan saboda kunya,Captain Habib baisan yanayin auren nasu da yarinyar bane harya saki baki yake wannan surutun? baisan cewa ko agida Shiba ma'abocin yin wasa dasu bane saboda baya son raini? da farko yayi tunanin zancen nasa bazai miqeba, amma dayaga yana qoqarin tona masa asiri shiyasa ya qirqiri tarin qarya Adede lokacin Nusaiba takawo musu ruwa,Captain Habib yayi sauri yadauki gorar ruwa yabashi Sai sannu yake masa. Mawahib kuwa mamaki ne ya kamata,kwata kwata bata yarda da wannan maganganun na Captain Habib ba,ba akanta yake magana ba,Yaya Captain da baya sonta shine zaiyi tunanin ta awajan aiki? Nusaiba ta kallesu cikin farinciki ta gabatar musu da abubuwan data kawo musu tace"to bismillah ga ruwa" Mawahib ta dauki lemon kwali ta tsiyaya a cup tasha dan kad'an,ganin idon Nusaiba akanta yasa tasake daukan irin lemon datasha din tazuba wa yaya Captain,tabashi cikin ladabi, yamiqo hannunsa zai kar6a, maimakon yariqe cup din sai yahada da nata hannun da cup din yariqe yakai bakinsa yasha lemon, Captain Habib Yasaki murmushi, Nusaiba kuwa saitayi quriii da'ido tana ganin soyayya, kamar ba Captain Aryan ba,damafa masu shiru shirun nan akwai soyayya. Captain Aryan kuwa yayi hakanne saboda karsuyi wani tunani akan zaman nasu,saboda yaga har yanzu taqi sakin jiki dashi, to zasu Iya gane wani abun ataraiyar su harsu saka musu alamar tambya. Mawahib kuwa gaba daya al'amarin Yaya Captain yagama daure mata kai, idan yayi mata wani abun kawai yanayin rayuwar su ta kano take tunowa,sai taga kamar an sauya shi gaba daya. haka sukaci gaba da zantuka kad'an kad'an daga wannan lemon dasuka sha,babu wanda yasake cin wani abu a cikinsu,shide Captain Aryan wayarsa ce a hannunsa yana dannawa, Mawahib Kuma suna magana da Nusaiba kad'an kad'an. Kitchen tatafi domin ganin girkin datake yi,tana kitchen din Yaron ta yatashi daga bacci yafara kuka, Captain Habib yace"bari in dauko mufid yatashi a bacci" Mawahib tayi murmushi yace"bari in dauko shi" Captain Habib yayi murmushi yace"to Amarya,ainaga lokacin sallah ma yayi bari inyi alwala" Yana fadin haka ya shige toilet din dake cikin falon, Mawahib ma tatashi tashige dakin datake jiyo kukan Yaron,tana shiga kuwa ta ganshi yana cikin dan qaramin gadonsa, Yaron fari kyakykywa dashi gashi 6ul6ul dashi,jijjigashi tafara yi adakin tana lallashin sa, bataso tafuto falon tasan Yaya Captain ne kawai a zaune,batasan su kasance su biyu takura take yi sosai. Acan falo kuwa Captain Habib yana gama alwala yafuto yadaga toilet din yana daura agogon hannunsa ya kalli Captain Aryan yace"Captain shiga kayo alwala mu wuce masallaci,idan kagama Ina compound, zan amsa waya" Captain Aryan ya kalleshi tareda gyada kansa,ya shige toilet din dan dama yana buqatar kama ruwa saboda kafin su shigo gidan tun amota Mawahib ta 6ata masa tsarkinsa(🙈) Saida tajima adakin har Yaron yayi shiru sannan tabude qofar dakin ahankali taleqo taga Yaya Captain baya falon, sannan tafuto daga dakin,Agogo ta kalla ganin lokacin sallah yayi hakan ya tabbatar mata da cewa sun fita masallaci, ahankali tacire mayafin jikinta,tacire agogon hannunta, sannan ta ajiye mufid tanufi toilet din falon zatayi alwala(🙆🏻‍♀️) Zuciyarta daya tatura tashiga toilet din adede lokacin Captain Aryan yagama gyara jikinsa ya miqe tsaye zai maida gajeren wandon sa jikinsa,idonta ya sauka akan abunsa(🙈🙊😳) Cikin sauri tazaro idonta waje,jikinta yadauki karkarwa gaba daya,Shima Captain Aryan da baiji budewar qofar ba sai ganinta yayi cikin sauri ya zaro idonsa waje(😳) Lokaci daya ya runtse idonsa,kuma ya gagara maida wandon,meyasa yau yake kunya ta kansa ne awajan Mawahib? numfashin tane yake neman daukewa zata sume masa a toilet din,akaf tarihin rayuwar ta bata ta6a ganin wannan abun ba,abun ma na manya, manyan ma ingarman namiji jajirtacce kamar Yaya Captain wanda kana gani kasan nashi bana wasa bane(🙈) Ganin zata fadi a toilet din yayi sauri ya maida gajeren wandon sa sannan yariqeta ta tsaya da qafafunta, saide daga gani bata hayyacinta,gaba daya gumi ya jiqa mata fuska, tanajinta a tsaye, tayi sauri tabude qofar tafice aguje(😂) Captain Aryan yabita da kallon mamaki,yaja qofar ya rufe yadora hannunsa akan goshinsa dayan hannun Kuma yariqe qugunsa dashi,cikin ransa yace"yasalam" Yanzu shikkenan yarinyar nan taga girmansa? irin wannan abun kunyar yana faruwa tayaya ne zai Iya kallon idonta harya fada mata cewa yana sonta? gaba daya tasake tsorata dashi duk saboda ganin wannan abun to ranar daya batashi a hannunta yaya zatayi Kenan? Kansa ya girgiza kawai,yadauro alwala sannan yafuto daga toilet din yana sauke hannun rigarsa qasa fuskarsa kamar Koda yaushe tana nan a daure,kallon cikin falon yayi anan yaga Mawahib tacire dan kwalin kanta tana firfita dashi duk da esin dayake aiki a cikin falon,kansa ya girgiza yaqarasa ficewa daga falon,baisan lokacin daya saki murmushi ba,duk me yayi zafi haka? kode ta manta ba'a gidansu suke ba? ahaka Nusaiba tadawo ta sameta bayan tagama ajiye girkin data musu,tace"Amarya zafi kike jine?" Cikin sauri tadaga kanta sannan tayi wata irin dariyar yaqe tace"eh wallahi" Nusaiba ta dauki mufid tace"to taso muje dakina saikiyi sallah kafin su dawo muci abinci" Babu musu tabita dakin nata, domin kuwa bazata Iya sake shiga wannan toilet din na falo ba,gani zatayi kamar zata sake ganin abun Yaya Captain (🙈) Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Suna shiga dakin Nusaiba tajata gefen gado suka zauna, tatashi ta dauko mata wani magani sannan tadawo kusa da'ita ta zauna tabata maganin tace"nasan idan sundawo ba lalle su barmu musake ba,kiyi amfani da wannan maganin nasan zakiji dadinsa,tunda yanzu de nasan Captain ya maidake yar gari,kidinga sakawa a yogurt kinasha, zaisa jikinki yayi fresh sosai,amma kuma saikin sake daurewa,idan kuka hadu da oga ba sauqi, duk da nasan cewa matan sojoji muna qoqari,suna nuna mana qarfi kamar sun manta cewa mudin ba sojoji bane" Atare suka saka dariya saide ita Mawahib dariyar yaqe take,gaba daya bata cikin nutsuwar ta,Nusaiba tace"shiga kiyo alwalar to,bari in Shimfida miki darduma" Mawahib tace"to nagode" ta ajiye maganin kusada agogon ta, Sannan tashige toilet, tana shiga ta jingina da jikin qofar toilet din, gumi yana sake futo mata a goshinta,lumshe idonta tayi amma wannan abun na Yaya Captain take gani, cikin sauri tabude idonta, maganar Nusaiba tadawo mata cikin ranta,idan ta fahimceta maganin mata tabata,kenan dama Mamy ma maganin mata take aiko mata dashi Kenan? Shine tadage tuquru tanasha jitake abun arziqi ne? wato kowa burinsa tasha maganin mata Yaya Captain yaji dadi kowa sonsa yake babu wanda zai lura da cewa shiba sonta yakeba, ita ba sonsa take ba,ajiyar zuciya tasaki tafara zuba ruwa a fuskarsa harta samu nutsuwar ta tadawo, sannan tayi tsarki ta daura alwala tafuto tatada kabbarar sallah. falon suka dawo suka zauna har lokacin su Captain basu dawo ba, bata daura dankwalin taba sai mayafin data yafa har kanta, mufid yana hannunta tana wasa dashi Sai qyalqyala dariya suke,tana son yara kasancewar gidansu basuda qananun yara,duk da tana tuna abinda yafaru a tsakanin su da Yaya Captain hakan bai hana ta sake suna wasa da Yaron ba,adede lokacin suka dawo daga masallaci, hannunsa yana zube cikin aljihun wandon sa, fuskarsa kamar kullum tana daure,tun daga bakin qofar falon yazuba musu ido itada yaron yana kallonsu,sun birgeshi sosai kamar ya dauketa itada yaron sutafi gidansu ko zai samu yadinga ganin wannan kyakykywar dariyar tata kullum(🙈) Har suka zauna a kujera Mawahib bata dago kanta ta Kalle su ba,tanata wasanta da mufid,Nusaiba data gama zuba musu abinci ta kalleta tace"Mawahib kinason yara,kema zaki haifi naki,may be ma naki Yaron yafi mufid kyau da fari tunda mijinki fari ne kema haka, kokuma ki haifo mana 'yanbiyu, tunda shima 'yanbiyu ne" Captain Aryan daya faracin abinci ya saci kallonta,saiyaga tayiwa mufid kiss a goshi sannan tace"banason farin yaro" Wani irin murmushin gefen baki yayi,batare da kowa yasani ba,matarda taga abu duk ta rikice tana tsoro jikinta yana rawa itace hartake da za6i akan yaron dazata haifa, a wannan tsoron nata tayaya ma zata saki jiki harta samu yaron? . Captain Habib yayi dariya yace"to saide in dangi dan naku zai iyo,amma iyayensa de duka gakunan farare ne" Murmushi tayi dan kadan bata sake cewa komai ba,har suka gama cin abincin,basu sake zaman awa dayaba,Captain yace zasu wuce,badan sun soba haka suka musu rakiya har Mota, Nusaiba Sai rada take yiwa Mawahib akan kartayi wasa da wannan maganin,daga nan sukai sallama maigadi yabude musu get suka fita. tunda suka dauki hanya babu wanda yace da dan'uwan sa uffan, Mawahib gaba daya hankalin ta tamaida kan window tana kallon yanayin garin,ahankali yajuyo ya kalleta yaga kokadan taqi kallon inda yake,dan qaramin murmushi yasaki baice da'ita komai ba,suna zuwa gida tabude motar tafuce tanufi gida sai sauri take kamar zata tashi sama, kallonta yayi yasaki wani irin numfashi tareda zuba hannunsa cikin aljihun wandon sa yabi bayanta ahankali. har zuwa dare Mawahib bata yarda tahadu da Captain ba,shima bai takura mata ba ya qyaleta,saide har zuwa dare yana tunani akan matsalar haihuwar sa,idan yatuna zuwa gidan Captain Habib dasuka yi,saiya dinga ganinta a'idon zuciyarsa itada wannan yaron,bai ta6a jin yanason haihuwa ba sai yau din dayaga yaron yamata kyau,bai ta6a jin ciwon rashin lafiyar sa ta tsinkakken maniyi ba sai yau,yaga alama tabbas tanason yara, yakamata ace yabata nata Babyn itama saita dinga wasa dashi, bai fargaba saida yakai kusan qarfe biyu nadare yana tunani, ajiyar zuciya yasaki yatashi yawuce toilet yayi alwala yazo yafara nafilfili, yadade yana Addu'ah yana roqon Allah yakarkato masa hankalin matarsa kansa,Allah yabasu zaman lafiya da zuri'ah tagari,Allah ya daidai ta tsakanin mahaifiyar sa dakuma matarsa, Allah yasa koba yanzu ba, watarana mahaifiyar sa taso matarsa kamar yanda take sonsa,saida yagama shafa Addu'ah sannan sannan yadauki wayarsa yasake turawa Hajiya kilishi saqon ban haquri da neman yafiya, sannan yayi addu'ar bacci ya kwanta. Washegari sassafe yayi wanka yafice yabar gidan,kai tsaye Maitama general hospital yaje,bayan yayi duk abinda yadace yasamu ganin doctor,saida suka sake yimasa wasu gwaje gwajen, sannan likitan yayi masa rubuce rubuce akan katin sa yabashi katin sannan yace"kanemi wannan magungunan yanzu yanzu,sannan karka yi wasa da shansu,inde kana shansu bisa qa'ida insha Allah cikin qanqanin lokaci sperm din zai koma daidai kamar yanda yake ada,but karage cin abu me maiqo, sannan dazaran kafara amfani da maganin saika sanar dani yaya kake ganin yanayin sperm din, idan da yiyuwar asauya magani sai asauya ma wani" Cikin gamsuwa Captain Aryan yabashi hannu suka sake gaisawa, sannan sukai exchange din number,yafuto daga office din,kai tsaye magungunan yaje ya siya sannan ya futo daga asbitin yabude motarsa ya ajiye maganin,shima yashiga yaja motar yanufi gida. 50/50,Ali yaga Ali 😂🙈 (Captain de ya lalla6o neman magani dakansa 😂🤣) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [7/13, 5:41 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Banji dadin yanda wasunku suke fitar min da littafi naba, ada har Ina murna Ina cewa Allah yahadani da fan's din MAWAHIB yan amanah,asheni bahaka bane nice nake yaudaran kaina,wasu writer's din idan suna novel har sha'awa suke bani saboda bazaka ta6a ganin littafin su yana yawo ba,amma ni bansan meyasa akemin hakaba, littafin nan na kudi ne,kudi kukasa kuka siya, meyasa bazakubar duk wanda yakeso Shima yasiya da kansa ba? kusa aranku idan kune kuka hana kanku bacci, kuka hana kanku sukuni,domin ganin kun farantawa masoyan ku rai kawai sai kuka ga littafin ku yana yawo a group zakuji dadi? nasan wasu daga cikinku sunsan yanda typing yake,yanda typing yake da wahala idan Marubuciya tace Allah ya'isah billahillazi sai Allah yasaka mata, kullum posting biyu nakeyi saboda kada kudinga jira muyi muyi mugama kowa hankalinsa ya kwanta amma jiya jiya Ina posting cikin mintuna qalilan sai gashi Har kun fitar min dashi, group fa ba mutum dayane aciki ba, wani group dinma yatara sama da mutum 600 menene ribarki idan kin fitar dashi ne? Bafa komai zasu miki ba watama saide tace miki 't' wato tnx, tun farko saida nace idan kinsan cewa zaki sai littafi nane danki dinga fitar min dashi to nahadaki da girman Allah karki siya, bana buqatar kudin ki, ni aganina ko 100 ce dani gara in fadawa mutum inaso, idan ya siyar min shikkenan in karanta cikin kwanciyar hankali yafi ace anbarni da Allah, masu cewa Wai idan ba'a share nasa tayaya ne wasu zasu gani su siya Toni nagode da wannan share din, Iya free page din danayi posting Wanda suka gani suka siya sun Isa, Allah yayi masa albarka, ko a addinin musulunci ciniki babu dole, idan kin siya Mawahib ne danki fitar min dashi kiyi left, zan miki transfer din kudin ki 🙏🏻 [7/13, 5:41 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 yana komawa gida ya ajiye ledar aqasan carpet din falo ya kwanta akan doguwar kujera yakira wayar Ashraf. Alokacin suna zaune afalonsu yadora Nabiha akan cinyarsa hannunsa yana cikin rigarta yana shafa cikinta wanda yafara dan tasawa kad'an. Daukan wayar yayi, daga 6angaren Captain yafara magana qasa qasa kamar yanda yasaba yace"Ash naje naga doctor yanzu" Ashraf yayi murmushi,yadora hancinsa akan qirjin Nabiha yana goga mata dogon hancinsa irinna Aryan sannan yace"kayarda da magana ta kenan,yanzu za'a fara fafatawa" Idonsa ya lumshe sannan ya budesu a hankali yace"bahaka bane Ash...,kawai naga tana son Baby ne" Ashraf yayi murmushi yace"kafada mata kuwa?" Cikin sauri yace"nakasa Ashraf,nikaina kunyar kaina nakeji,bansan Yaya zan tunkareta da maganar ba" Ashraf ya lumshe idonsa yace"meyake damunka ne?kacire komai aranka kayi abinda yadace" Cikin sanyin jiki yace"Okay ,jarababbe sai anjima" Ashraf ya Kalli wayar da sauri yana murmushi bayan yaji Captain din yakashe wayar,hakan yana nufin yagane da Nabiha yake tare kenan. Yana kashe wayar yashiga email din wani gidan abinci yana magana dasu,daga dakinta tafuto tayi kwalliya tana sanye cikin doguwar riga ta atamfa fitet gown,daurin dankwalin nata yayi mata kyau sosai,tana qarasowa falon ta ganshi a kwance yana danna waya,qarasowa tayi ahankali tana zuwa kusa dashi qamshin ta yanayi masa sallama, kallon fuskarsa tayi wadda babu fara'ah kamar kullum, sannan ta janye idonta ahankali saboda karsu hada ido,tace"Ya Captain Ina kwana?" Kallonta yake cikin wani irin shauqi,yana qarewa shigar jikinta kallo a taqaice yace"kin tashi lafiya?" Mamaki ya kamata,yau Kuma salon gaisuwar tasa kenan,tasaba Koda yaushe saide yace mata lafiya, a taqaice. Kanta aqasa tace"akwai breakfast" wayar hannunsa ya ajiye sannan yatashi yace"Okay" dining suka qarasa,yadora hannunsa akan kujera yana tsaye, itama daga tsayen tafara zuba musu abinda tadafa,kallonta yake cikin zuciyarsa yana yaba irin nutsuwar yarinyar,harta gama zubawa ta ajiye masa agabansa,itama ta ajiye nata agabanta,abincin ya dauka yabar inda yake yadawo kujerar kusa da ita ya zauna har jikinsu yana haduwa dana juna,ta kalleshi ta gefen idonta,sannan ta dauki fork tafara cin arish din dake gabanta ahankali,kad'an kad'an tanajin gabanta yana faduwa amma saita dake,babu wanda yayi magana duka su biyun,saida suka kusa gamawa batare daya kalleta ba yace"ya tsoron jiya?" Lokaci daya Mawahib ta qware, tafara tari,meyake damun Yaya Captain ne? tasamu tafara mantawa shikuma yana qoqarin tuno mata da wannan tashin hankalin. ganin yanda taqware yasa ya danyi murmushi kad'an, saboda ya tabbatar dalilin tambayar ne yasa ta qware, tashi yayi tsaye yadauko gorar ruwa yazuba a cup, sannan yadora hannunsa a bayanta yana shafa wa, yadora mata cup din abakinta, cikin sauri ta shanye ruwan,tafara maida numfashi,gumi ya rufe mata fuska,Captain yana kallonta yana murmushi qasa qasa,yanason ganin wannan tsoron na idonta, birgeshi yakeyi, ahankali yasaka dayan hannunsa yajata jikinsa ba tareda musu ba ta kwantar da kanta luf acikin qirjinsa, wata irin ajiyar zuciya yasauke wadda tabawa Mawahib mamaki sosai, bayanta yake shafawa ahankali,dankwalin kanta yazame yafadi qasa,yabi dogon gashinta da kallo, ahankali yasaka hannunsa yafara tattare mata gashin,Mawahib tanajin yanda yake hade mata gashinta batayi kuskure ko yunkurin hana shiba,wayarsa dake kan dining tafara ringing, atare suka Kai dubansu izuwa wayar, sunan Asalamiyya ne yake yawo akan screen din wayar,kokadan Mawahib bataji komai ba akan kiran,tasan budurwar sace,Kuma batada ikon dazata hana shi mu'amula da'ita saboda yar'uwarsa ce,wani Kishi da akeji kokadan bata jishi ba,saima damar daga wayar data bashi, ta hanyar raba jikinta da nashi,ta sunkuya zata dauki dankwalinta daya fadi qasa. Captain Aryan ya lumshe idonsa cikin taqaici,yarasa me yarinyar nan take nema awajansa,batada aiki Sai kiran wayarsa Kuma bawani zancen arziqi zata fada masa ba saina tsiya, kullum de maganar itace tanaso taganshi tanaso taganshi to idan taganshi uban me zai mata?(😳) Yanzu gashi yana cikin nishadinsa tayi masa haramiya(🤦🏻‍♂️) bai dauki wayarba harta katse,Mawahib taware dankwalin ta zata yafa akanta cikin sauri yariqe dankwalin yace"no barshi haka,kinfi kyau" Gabanta ne yayi wata irin faduwa,tafi kyau? me hakan yake nufi? bai bata damar cigaba da tunanin ba,yadauki fork din datake cin arish dashi yadauko guda uku,yanufi bakinta dashi,gabanta ya tsananta faduwa,meyake shirin faruwa ne? me hakan yake nufi? Meyasa yake mata abubuwa kamar wani saurayi da budurwa? Cikin sigar rada yace mata"please bude bakin..." Wani irin zirrrr taji ajikinta Sakamakon yanda yayi mata maganar cikin rada hakan ba qaramin tasiri yake acikin gangar jikinta ba,ahankali tabude dan qaramin bakinta yasaka mata arish din guda daya,tafara taunawa ahankali,sannan shima yasaka sauran guda biyun bakinsa,saide idonsa yana kanta,yakasa raba idonsa da dan qaramin bakinta,Mawahib kuwa mutum mutumi tazama awajan,gani take kamar bashi ba,gashi fuskarsa babu walwala bare takawo masa wani wargi. Ahaka ya dinga basu har suka kammala,cikin sauri tatashi zatakai plate din kitchen,Shima yadauki wasu yabiyo bayanta dashi,ganin kitchen dinma ya biyota hakan yasa cikin sauri tajuya zata fice,yajuyo ya kalleta ganin duk ta rikice,hartaje bakin qofar fita daga kitchen din yace"bakiji ba" Cak taja ta tsaya awajan,ya harde hannunsa a qirjinsa yace"kishirya da yamma zamu fita" Kanta kawai ta daga masa sannan tayi wuf tafi ce daga kitchen din tayi sama,murmushi yasaki yabude fridge ya dauki gorar ruwa yakoma falo yabude magungunan sa yafara sha. tana rufe dakinta ta jingina da bangon qofar gabanta yana faduwa har kana hango yanda na shanunta suke sama da qasa saboda yanda take sauke numfashi, lumshe idonta tayi tana so ta daidai ta kanta, meyake damun sane? ga budurwarsa agefe shida ya kamata yayi farinciki da kiran ta shine yake neman ya hargitsa mata lissafi,gashin kanta ta hargitsa tana barbaza shi ko zataji is'ka tana shiga cikin gashin nata saboda yanda yadauki zafi. qarfe hudu na yamma yayi wanka ya shirya cikin qananun kaya riga da wandon jeans, rigar ruwan toka tana hade da hula,yasaka glass wanda yasake qwata kwalliyar tasa, falon yafuto yana zuba uban qamshi,Mawahib kuwa tun safe data shige dakinta taqi futowa falon bare tahadu dashi. ganin bata falon yasa yafita compound yana waya qasa qasa,saida yagama wayar sannan yaduba number ta,number yazubawa ido yana kallo kamar yana tunanin wani abu,har zai kirata saiya fasa yatura mata text cewa yana jiranta. tafuto daga wanka kenan tana shafa turare taji alamun shigowar saqo wayarta, "I'm waiting for you" duk da batayi saving number ba tasan cewa shine zai turo mata saqon,cikin sauri ta qarasa shirin datake tazira abaya ta dauki Jakarta tafuto,tana zuwa compound ta hango shi kusada motarsa yana danna waya, cikin sauri ta qaraso wajansa, yanajin qamshin ta yadago ya kalleta, sannan yabude mata mota da kansa, babu musu tashiga, yazagaya yashiga yatada motar suka fita,suna hanya tana tunanin irin sabin halayen dayake nuna mata a yanzu,duk da batasani ba yana sonta ko baya sonta,saide abinda tasani daga nata 6angaren shine har yanzu batajin sonsa acikin zuciyar ta,saide bata tsaneshi ba,batajin tsanarsa kokadan aranta,wajan shopping sukaje,saida suka tsaya sannan tagane dalilin futowar tasu,kallonta yayi yace"muje" Babu musu tafuto suka shiga tare,tunda suka shiga tsirarun mutane suke kallonsu,fuskarsa tana hade kamar koda yaushe,itace agaba yana binta abaya yana turo mata kwandon zuba kaya,Sai zagaye suke tarasa mezata dauka,ganin tunda tazo gidan yakawo kayan abinci da kayan maqulashe baisake siyowa ba,tasan may be wannan shine dalilin dayasa yace tashirya sutaho tare saboda taza6i abinda take yawan amfani dashi,kuma miskilanci yahana yayi mata bayani. kayan shayi tafara dauka tajuya tazuba masa acikin kwandon,wasu yanmata su biyu sunzo wucewa suka kalleshi harda waiwaye,ganin wannan hadaddan gayen ne yariqe mata kwandon yana binta abaya kamar wata sarauniya,saide babu fuskar yimasa magana ganin yanda fuskarsa take ahade danma yasaka glass shiyasa baka gane zahirin yanda fuskar tasa take, sai zagayayyen sajensa daya qara qawata fuskar tasa kamar wani balarabe. suka zagaya wajan turaruka tadauki wanda takeso,shima ta dauka masa,Sai wajan kayan miya anan tafi 6ata lokaci,sai naman kaza, bata dauki Jan nama ba saboda suna dashi dayawa,fridge din gefe ta kalla sannan tasaci kallon Yaya Captain taga hankalinsa yana kan waya,cikin sauri tazuge glass din fridge din, ta dauko robobin ice cream masu yawa, shima ta zuba, sannan ta kalleshi tace"yaya Captain nagama" Cikin sauri yace"Okay" Yatura sukaje yabada atm dinsa suka dauki kudin su,sannan yadauko kayan suka koma mota. Daga nan wani boutique sukaje,yasake kallonta yace"muje" Kanta tadaga, tafuto suka shiga ciki, tun kwanaki yaga wata doguwar riga suna tallarta,kuma rigar tamasa kyau,zata dace da irin dirin Mawahib,tunda yanzu sun riga sun futo gara su sayi rigar saisu koma gida gaba daya. d'aya daga cikin ma'aikatan wajan ya nunawa rigar,cikin sauri tareda girmamawa ya musu iso wajan da rigar take,doguwar riga ce fara mai kama data amare,duka jikin rigar anyi masa ado da qananun stone masu walwali,dogon hannu ne da rigar sai mayafin ta madedeci mai shara-shara,rigar tana jikin mutum mutumi, Mawahib tasaki jiki da baki tana kallon rigar, duk yanda take daukan wankan dogayen riguna sai wannan rigar tatafi da imaninta, batasan mutumin daya rakosu wajan rigar yatafi ba,sai gani tayi yadawo yabawa Captain Aryan rigar acikin kwalinta, Captain ya duba kudin rigar yabashi atm dinsa, mutumin yajuya yabarsu awajan. Captain Aryan yabata kwalin rigar yace"gashi" Mamaki ya kamata,cikin tsananin murna ta kalleshi tace"yaya Captain nawane?" Captain Aryan ya Kalli qwayar idonta yace"yes,kiyi kwalliya dashi" Cikin sauri ta ajiye kwalin rigar, cikeda tsananin murna ta qarasa jikinsa tayi masa wata irin runguma,cikin farinciki tace"nagode Yaya Captain, Allah yaqara arziqi,thank you so much" Captain Aryan dabaiyi tunanin wannan rungumar ba saiya qame awajan,dama tana fara'ah har haka? yanda yakejin tudun nashanunta yana mintsinin qirjinsa hakan yasa ya lumshe idonsa,nan take yafara shiga cikin wani irin yanayi,ahankali kamar yana tsoron ta6ata, yadora hannunsa akan hips dinta yasake rungume ta sannan yagyada mata kansa,kwata kwata yakasa magana, Koda zaiyi maganar ma toba lalle muryarsa tafita ba(🙊😎) Mawahib bata lura da yanayin dayake ciki ba kokadan,jin takun dawowar wannan mutumin daya basu rigar hakan yasa tasake shi cikin sauri. Saide ta riga ta makara , mutumin yariga ya gansu,yayi murmushi yabawa Captain atm dinsa, sannan yajuya yabar wajan,Captain Aryan yadan daidaita kansa sannan cikin shaqaqqiyar murya ya kalleta yace"muje" Cikin sauri tadaga masa kanta, tadauki rigar ta suka futo daga boutique din,yabude mata motar tashiga, sannan suka dauki hanyar gida. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 A hanya yana lura da'ita sai farinciki takeyi,sa6anin shida yahad'a uban gumi saboda har yanzu yanajin rungumar nan a jikinsa saboda bai ta6a zaton hakan daga gareta ba,suna zuwa gida David yataso da sauri suka dauki kayan shida Captain Aryan,ko tsinke bai bari ta dauka ba. Kai tsaye kitchen tawuce tashirya duk abinda suka siyo sannan takai nata kayan daki sai wani farinciki takeyi, turarukan data siyo musu ta ajiye nata,sannan tashiga wanka,bayan tafuto adede lokacin ana kiran sallar magrib,saida ta gabatar da sallah sannan tadauki nasa turaren takai masa dakinsa,bata tarar dashi adakin ba tasan yafita masallaci ne,dakin nasa tsaf yake a gyare kamar dakin mace,qasa ta sauko tahada musu fruit salat,tadebi fulawa yar kadan tahada musu meat pie manya guda biyar tasaka isasshen nama aciki,sannan takai falo ta ajiye tadauki fruit salat dinma takawo, tabude fridge tadauko qanqara ta jefa acikin fruit salat din,tana qoqarin barin falon Sai gashi yashigo yana magana a waya qasa qasa,abincin data hada masa ya kalla, yazauna a kujera yagama wayar, sannan ya kalleta fuskarsa kamar koda yaushe yace"dawo kici abinci" Babu musu tadawo tazauna dama sallar isha'i zataje tayi,saita haqura tazauna suka faracin meat pie din,yadauki remote yana sauya tasha,sosai yakejin dadin zaman nasu,baiqi ace sun qare daren yau ahaka ba. Guda daya taci taji ta qoshi, tafara shan fruit salat din ahankali tana jiran yagama ta dauke komai tagudu sama,shikuwa yariga yagane so take tagudu tabarshi, hakan yasa yakeci kamar bayaso,ganin suna neman yin awa daya dawani abu hakan yasa yafara goge bakinsa da tissue, tana ganin haka tatashi takai komai kitchen,bata dawo wajan dayake ba tanufi sama zata tafi, yana ganin zata tafi cikin sauri yace"bakiji ba" juyowa tayi tace"na'am" "bani magani a dakina" Cikin ladabi tace"to" Sannan tawuce dakinsa tafara dube dube,can ta hango wata farar leda, tana dubawa taga magungunan aciki masu yawa, mamaki ya kamata, me Yaya Captain yake da wannan magungunan? bashida lafiya ne? Hannu tasa acikin ledar ta dauki guda daya taduba tagani,ta6e bakinta tayi ganin bata fahimci maganin kona menene ba, tafuto tarufe dakin sannan takawo masa,takoma kitchen tadauko masa ruwa takawo masa,bata tashi daga wajan ba tana satar kallonsa saida yasha Kala kalar magani sunkai guda biyar, sannan tadauko ledar tawuce sama. Har qarfe shadaya da rabi nadare idonta biyu batayi bacci ba,sai yanzu ne abubuwan da Yaya Captain yake mata suke sake dawo mata arai, meyasa yake mata haka? yaudara ce kokuma yan'uwan taka? tasan cewa de soyaiya kam babu ita, Yaya Captain bazai ta6a sontaba, to amma meyasa yake qoqarin ganin ya faranta mata a kwanakin nan? Wayarta dake silent tayi haske alamun shigowar saqo,cikin mamaki ta kallo agogon wayar taga qarfe shabiyu na dare,waye zai mata saqo,? Number data gani ce tasa gabanta faduwa,a fili ta furta Yaya Captain? saqon tabude taga yaturo mata "kin kwanta ne?" Cikin mamaki tace anya lafiya kuwa? bai ta6a turo mata saqo ba, Kuma a'irin wannan lokacin. Acan dakin Captain kuwa a zaune yake a gadon yasaka wayarsa a gabansa yana jira ta masa reply,bazai Iya Samun nutsuwar bacci ba sai yaji daga gareta, yanason su dinga fira ta wayar ko yasamu bacci ya daukeshi. Saqo ne yashigo, cikin sauri ya rarumi wayar zai duba saqon, bai bude ba saida ya kwanta sannan yabude yaga taturo masa "no,but zan kwanta yanzu" mezaice mata Kuma? Bawani surutu suke yiba,shibe Iya zance ba, da Ashraf nede saita gaji, to amma shi mezaice yanzu? Cikin jin haushin rashin surutun sa yayi mata replay da "Ok sweet dream nd take care of yourself...." Wayar yazubawa ido yana jira ko zata ce masa wani abu, shiru shiru bata turo masa komai ba, haka ya haqura shima yakife wayar tashi sannan ya lumshe idonsa yafara karanta Addu'ah ta bacci. Washegari sassafe tatashi tayi ayyukan komai ta ajiye masa breakfast takoma sama ta kwanta takoma bacci, saboda tasan yau Monday zai fita aiki da wuri. Captain kuwa yana dawowa daga wajan motsa jiki kawai wanka yayi,yafuto yaci abinci yazauna afalon yana shan magungunan sa yana kallo kad'an kad'an,yau babu inda zai fita yariga yanemi excuse,har qarfe goma na safe bata futo ba, yayi mamaki sosai,yadade yana falon har wajan goma da rabi, sannan yakashe kallon yadauki fillon kujera guda daya yadora a cikinsa ya rungume shi, sannan ya lumshe idonsa yafara bacci. Mawahib bata tashi farkawa ba sai wajan qarfe goma shadaya na safe,tayi wata irin miqa sannan tawuce toilet tayi wanka a nutse,tashirya cikin riga da wando tasaka hula akanta,riga da wandon sunada dan fadi tasake acikin kayan sosai,haka yadin kayan yanada santsi amma ba sosai ba,qasa ta sauko domin cin abinci, batayi tunanin yana falon ba,tana zuwa saitayi turus ta tsaya tana kallonsa,tayi sauri taduba wayarta taga de yau Monday,amma yata ganshi a kwance anan? tajuya gefe taga magungunan sa awajan, ta tuna jiya ma yace tabashi maganin zaisha,Kuma Bayan ta kwanta yamata text yana tambaya ko tayi bacci to Kode bashida lafiya ne? Ko ciwon ne yasa yaqi fita aiki shida baya wasa akan zuwa wajan aiki? Kokuma jikin nasa ne yatashi shiyasa yake tambayar ta a text yana nufin idan bata wani abu taje ta taimaka masa? Shi miskilancinsa yamasa yawa, bazai futo fili yafadi abinda yakeso ba,to amma kuma aiyace mata ta kwanta tayi bacci medadi. Matsowa tayi kusada kujerar dayake kwance,takai hannunta zataji jikinsa koda zafi,saitayi sauri ta janye hannunta tafasa, ta kalli tulin magungunan dasuke gefe tasan cewa ba kalau ba, matso da fuskarta tayi dab da tashi fuskar ko zataji jikinsa da d'umi. Captain Aryan yana jinta tun lokacin datazo wajan yafarka saboda qamshin ta daya shaqa, yanajin qamshin turaren yafarka amma bai bude idonsa ba,yanda yaji numfashinta yana sauka a fuskarsa sai hakan yake qoqarin jefashi awani irin yanayi, Mawahib kuwa da taji bataji wata alama ta zafi ba saita dago kanta kad'an, tamaida kallonta kan kyakykywar fuskarsa,zallar kyansa take gani,jan lips dinsa ta kalla tafara tunani, Yaya Captain yanada kyau sosai, amma tarasa meyasa takasa jin sonsa aranta kamar yanda sauran mutane suke sonsa. Ajiyar zuciya tasauke zata tashi tawuce kitchen,Captain Aryan dayaji zatabar kusa dashi cikin sauri ya fuzgota tafado jikinsa,cikin tsoro tasaki wata yar qaramar qara,cikin sauri yasaka hannunsa ya rufe mata bakinta sannan yazubawa fuskarta ido yana kallonta,itama shi take kallo,fuskarsa da bacci da rashin bacci koda yaushe haka take babu fara'ah, cikin muryarsa tame bacci yace"me kike kallo?" girgiza kanta tayi sannan ta janye hannunsa daga bakinta tace"dama....dama..damafa nayi tunanin bakada lafiya ne,shin...shine" saitayi shiru takasa qarasawa,ta sunkuyar da kanta qasa tana kallon yanda tayi male male akan jikinsa kamar tasamu katifa. Wani irin dan qaramin murmushi yayi,har zaice shine daga tunanin rashin lafiya kika tsaya kina qaremin kallo,? to kuma sai yayi shiru yashareta,idonsa ya lumshe sannan yabude ya kalleta yace"lafiyata kalau,karki yi girki yau,idan kingama abinda kike,qarfe biyu zamu fita" Cikin sauri ta daga masa kanta, sannan tafara kokarin tashi daga jikinsa,yanda take motsa jikinta anasa hakan yasa yayi saurin lumshe idonsa yanajin wani irin dadi,fatansa daya, Allah yasa idan sun fita ya'iya kallon idonta ya bayyana mata abinda yake cikin ransa ko zai samu ta yafe masa takuma amshi soyaiyar sa. yanajin tatashi,shima yatashi yayi sama saboda daga haduwar nan tasu tasashi cikin yanayin da bazai Iya tunkaran masallaci batare da wanka ba(🙈) kamar yanda yafada qarfe biyu daidai suka fita,yau wankan laffaya tayi,baqar laffaya ce me adon stones,kasancewar ta fara hakan yasa laffayar tayi mata kyau sosai,shikuma yasaka manyan kaya na shadda, saide baisaka babbar riga akai ba,bata ta6a ganinsa da manyan kaya a Abuja ba,kullum saide qananu kamar ba bahaushen mutum ba,amota babu wanda yake magana,Mawahib tana tunanin yau Kuma inane zasuje dahar yaqi zuwa aiki saboda fitar tasu? shikuma yana tunanin yanda zai fada mata yanda yakejin ta acikin ransa. wani wajan cin abinci sukaje,wajan yahadu sosai an qawatashi Iya qawatuwa,babu kowa awajan,haka duk kujerun dasuke wajan iya kujera daya ce aka shirya shirya abinci da lemuka akai, hakan ya tabbatar mata wajan yakama gaba daya kenan, Captain Aryan ya Kalli ko'ina yaga tsarin yamasa kamar yanda sukai magana dasu ta Email,wajan zaman suka qarasa yaja mata kujera ta zauna sannan shima yazauna,kallonsa tayi taga yanata walwala,dakansa yatashi yafara zuba mata komai, cikin sauri tace"yaya Captain kabarshi zan zuba dakai...." Kafin ta qarasa cewa dakaina,yadora hannunsa akan qaramin lips dinta yace"shiiiit" Babu musu tayi shiru,shine yazuba mata komai yatura mata gabanta, sannan shima yazuba,d'aya daga cikin ma'aikacin wajan yazo cikin ladabi yace"yalla6ai akwai abunda kuke buqata aqaro ne?" Hannu kawai Captain yadaga masa alamun cewa babu komai, cikin girmamawa yajuya yabasu waje. Abincin sukaci cikin nutsuwa,har yanzu Mawahib tana tunani aranta meyasa yau suka futo cin abinci? ko natane bashida dadi? gaba daya mamakin sa yagama kashe ta,gaba daya gani take kamar an sauya mata shi. Sun dade dagama cin abincin harta yi tunanin ko wani yake jira,saita ga yatashi yadawo kusada ita ya zauna,cikin sauri ta kalleshi,bai damu da kallon nataba yakama hannayenta duka biyun yariqe, sannan ya Kalli qwayar idonta yace" I'm sorry" Cikin mamaki Mawahib ta kalleshi sai rarraba idanuwa take,cikin rawar murya tace"for what...?" Yakalli qwayar idonta sannan ya sassauta murya tace"for everything...,kiyafemin,nasan nayi miki laifi abaya,ba daya ba, ba biyu ba,kuma kina kallo na da wannan abun aranki, amma na kar6i laifi na,na kar6i kuskure na,inaso kiyafemin please..." Jikin Mawahib yayi wani irin sanyi,meyasa Yaya Captain yake mata wannan abubuwan ne? waye ya sauya shi? bazata Iya qin yafe masaba,duk da ba soyayya ce a tsakanin suba yanzu zaman nasu yafi na baya,yana kokarin kyautata mata,kallonsa tayi, cikin sanyin jiki tace"nayafe ma Yaya Captain" Cikin sauri yace"are you sure?" Murmushi tasaki tace"very sure" Idonsa ya lumshe yana hamdala aransa,saura Kuma batun soyaiya,but kar tayi tunanin saboda soyayyar sane yasa yanemi yafiyar ta,yanemi yafiyar tane saboda yafara wanke kansa a wajanta,hakan yasa ya haqura bai fada mata cewa yana sonta ba,Mawahib ta Kalli idonsa taga bakinsa yana motsi kamar yanason yafadi wani abu, har lokacin hannunta yana cikin nasa hannun,yadago kansa ya kalleta yace"muje gida?" Cikin sauri ta daga masa kanta,dama atakure take awajan,takasa sakewa har yanzu, tarasa dalilin sa na neman wannan yafiyar, amma dole zata tambayi Nabiha. Hannunta cikin nasa suka futo daga wajan,yabude mata mota tashiga sannan yashiga yaja suka dauki hanyar gida. basu qarasa gida ba sai qarfe hudu da kwata, hakan yasa yana ajiyeta yajuya yatafi masallaci,itama sallah tayi, tacire laffayar jikinta ta watsa ruwa, sannan tasaka yar qaramar riga tafuto falon qasa,saitake jin ranta fes, kamar ansauke mata wani abu data dade yana damunta, hakan yasa tashiga kitchen ta dauko robar ice-cream guda daya tayi zamanta afalon tafara Sha,Yaya Captain bai dawo ba sai wajan qarfe biyar,yana zuwa yaganta afalon tabaje tana shan ice-cream yayi murmushi yawuce sama, ko banza tunda yanemi yafiyar ta yasan hakan yayi tasiri sosai tunda gashi harta Iya fara zama afalon duk da tasan yana gida zai Iya shigowa kowanne lokaci,amma ahakan tazauna bata gudu daki ta kulle kanta ba, hakan ya nuna tafara dan sakewa dashi. Qananun kaya yasaka yafice motsa jiki,bata bar falon ba saida taji anfara kiran sallar magrib, tatashi tayi sama,ta gabatar da sallah sannan tabude qur'ani tana karantawa har zuwa lokacin sallar isha'i. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Bayan ta idar da sallah tasauko tayi masa abinci marar nauyi dan kadan dede cikinsa,sannan takoma dakinta,Captain Aryan kuwa yana dawowa daga masallaci yaci abincin sa, ya kunna kallo sannan yasaka computer sa agaba yana aiki saboda yau bai fita aikin ba, bai tashi daga wajan ba sai qarfe goma da rabi,da computer yawuce sama ya ajiyeta, sannan yacire jallabiyar jikinsa yashiga wanka. Mawahib kuwa ta dade a kwance a gadonta tana chatting,tayi luf cikin bargo,wayarta ce tafara vibration,cikin mamaki taga sister Saudat qawar Mamy data kawo mata ziyara itace take kira,dauka tayi tareda sallama, Sister Saudat tace"kuna lafiya deko?" Mawahib tace"lafiya kalau Anty,harna kwanta bacci ma naga kiranki nayi tunanin koba lafiya ba" Sister Saudat tace"harkin kwanta bacci kamar Yaya? kin kwanta bacci kokuma kun kwanta bacci?" Tace"na kwanta Anty" Cikin sauri sister Saudat tace"Mawahib meyasa bakya jin magana ne? na hanaki kwana ke kadai saida mijinki bahaka Nafada miki ba?" Cikin sauri tace" Hakane Anty but..." "but what Mawahib? banason jin shirman komai kitashi kisaka kayan dana kawo miki kitafi dakin mijinki yanzu yanzun nan kokuma nakira Mamyn ki nafada mata" Cikin 6acin rai tace"to Aunty" ita tarasa meyasa matar nan takeson turata awajan Yaya Captain bayan ba saba zuwa tayi ba,fisabilillah taje wajansa tace masa me? duk ranta babu dadi tatashi tana tura bakinta gaba tabude jakar kayan taga duka babu na arziqi,gaba dayansu idan tasaka sai anga komai nata, hakan yasa taduba wata qwaya daya medan dama dama data gani me dogon hannu,tanada dan fadi rigar,amma tsawonta Iya duwawunta ya tsaya,sai wandon rigar shima dan qarami ne gaba dayansa Iya tsawon rigar ya tsaya shima,duka cinyoyinta a waje suke, daga gaban rigar akwai botir daga sama har qasa, amma botir guda biyar na sama anciresu, tundaga wuyanta har breziyar ta gaba daya yana waje, daga qasan breziyar ne akabar botiran rigar har qasanta, ta dauki turaren da Mamy ta bata wanda tace idan zata kwanta ta dinga shafawa ta shafashi sosai, ta kalli kanta a madubi taga yanda gaba daya fararen cinyoyinta suka bayyana,a fili tace"anya kuwa?, tayaya zanje wajansa ahaka? Ahakan ma shine me dan sauqi sauqi ita Ina tasamo wannan kayan ne?" tasake kallon gaban rigar taga inda babu botir din gaba daya kana ganin na shanunta dasuka cika madedeciyar breziyar har suna futowa ta waje,girgiza kanta tayi,bazai iyu taje wajansa hakaba,tasaka hannunta tacire ribon din dake kanta, dogon gashinta ya sauko,ta tattare gashin gaba daya ta dawo dashi gefen kafadarta na dama,hakan yasa yadan 6oye qirjin nata,sannan tafuto kai tsaye ta nufi dakinsa amma kana ganin fuskarta zakasan cewa dole aka mata,kana gani kasan cewa ranta a6ace yake, Ahankali tatura qofar dakin tashiga, wani irin qamshi yabugeta, ga sanyin esi yana ratsa jikinta,wutar dakin a kunne take,amma baya cikin dakin da alama wanka yake, ga computer sa nan agefe,cikin sauri ta nufi gadon zata kwanta tashige bargo dan karya ganta da wannan sallamanmu kayan, saide tana dora hannunta a gadon da niyyar kwanciya,sai wayarsa tafara qara,idonta ya sauka akan sunan me kiran taga Asalamiyya (😂) batasan dalili ba haka kawai taji ranta yayi wani irin mugun 6aci, dama tashigo da nata 6acin ran,saita fasa kwanciya tatashi ta Kalli agogon dakin taga qarfe goma shadaya nadare,kar kuma abun nasu yazama da rainin hankali,tabarshi yana mu'amula da'ita, tabarshi yana waya da'ita acikin gida duk da shawarar da Nabiha ta bata, rannan suna breakfast ta kirashi,da rana tana kiransa, yanzu ma da dare saita kira shi? Karfa ace Momy kilishi ce take turowa Yaya Captain wannan Asalamiyyan,tayaya harta bari tayi sakacin da wata zata kira mijin ta qarfe goma shadaya na dare? duk da bata sonsa bazai ta6a iyuwa ayi mata wannan cin kashin ba,idan auren ta zaiyi yaje ya aure ta inyaso Momy kilishi tasashi yasaketa (🙆🏻‍♀️) Tana gama wannan tunanin wayar tasake ringing akaro na biyu, cikin sauri ta dauka tace"wai ke bakisan lokacin dazaki dinga kiran mutum me iyali bane?" Asalamiyya tasaki dariya tace"ina ruwan masu iyali,ke harkin samu damar da bakinki yabude dahar zaki hanani kiran dan'uwana? kokin manta matsayin mahaifiyar sa awajena? yaushe aka haifeki? yaushe ki kasan dad'in mijin dahar zaki min shamaki da kiransa? yanzu nafara kiran Yaya Aryan kuma bazan daina ba sainaga ganni acikin gidansa amatsayin matarsa,matsayin uwar yayansa,kibari idan kuka samu yancin kanku keda mahaifiyar ki saiki fara iko da mijin" Mawahib ta jinjina kanta, lalle ta riga tayi sake, cikin 6acin rai tace"ko? to saiki bari idan ya futo daga wankan Sunnah saiya kiraki"(🙊😂) Tana fadin haka takashe wayar tayi wulli da'ita kan gado,Captain Aryan daya mace atsaye yana kallon surar jikinta, cikin jin dadi yasaki wani irin murmushi,meyake gani a fuskarta kamar fa kishin sa take, idan kishin sa take hakan yana nufin tafara sonshi ne? wani irin dadi ya kamashi,tun lokacin data daga wayar yafuto daga toilet yanajin su,yanda take nuna cewa shidin mijin ta ne hakan ba qaramin dadi yayi masa ba,sosai ta birgeshi,saide furucinta na qarshe yabashi dariya,shida zai samu ma ta bashi hadin kai yayi wankan Sunnar aida tagama masa komai (🙈) Mawahib data dafe kanta da hannunta cikin 6acin rai tanufi hanyar barin dakin,tun farko ita taqi shawarar Nabiha, da tun lokacin da Asalamiyya tafara kiransa tayi maganin abun da abun bekai hartazo tana fadawa Mamyn ta magana ba. cikin sauri Captain Aryan yajefar da dan qaramin towel din dayake goge fuskarsa ya nufeta tareda ruqo hannunta,yanda ya matso jikinta hakan yasa turaren data shafa wanda Mamy tabata yafara fizgarsa,cikin laushin murya yace"Ina zaki?" Hannayen ta taharde a qirjinta ba tareda tajuyo ta kalleshi ba tace"dakina" Kasancewar ta bashi baya hakan yasa cikin sauri ya rungumota tabaya,har tanajin yanda danshin ruwan dake qirjin sa yake ratsata, fuskarsa ya matso dab da tata fuskar, tanajin yanda numfashin sa yake sauka akan fuskarta,yanda tayi furucin tace zata tafi dakinta cikin fishi hakan yasa gaba daya ya rikice,yasaka hannunsa duka biyun yariqe fuskarta cikin sigar lallashi yace"meyafaru zaki tafi? fadamin me kikeso?,nine na 6ata miki rai?" Cikin sauri ta girgiza kanta alamun a a Cikin damuwa yasake yin qasa da muryarsa yace"bakinyi mata warning ba? bazata sake kiraba, shikkenan?" Yanzun ma batace masa komai ba, kawai de ta daga masa kanta alamun amsawa, sannan tasaka hannu tacire hannunsa daya riqe mata fuska sannan takama handle din dakin zata fice, cikin sauri yasake fuzgota tadawo jikinsa, kamar wani sakarai ya kalleta yace"nabaki haquri fa" Batare data Kalli inda yake ba tace"aina haqura" Fuskarta yasake riqewa ya kalli qwayar idonta, cikin muryar rad'a yace"to meyasa zaki tafi?,kina fishi danine?" ganin yanda ya rikice yake jero mata tambayoyi,hakan yasa takasa kallonsa,tayi sauri ta lumshe idonta,gaba daya ranta a6ace yake da wayar datayi da Asalamiyya, Yaya Captain din de mijinta ne, amma har ita Asalamiyya zata kira tana fada mata baqar magana haka kawai saboda tana taqama da Momy kilishi, wani irin hawaye suka silalo daga idanunta,yana ganin haka baiyi wata-wata ba, ya lumshe idonsa sannan yadora harshan sa akan fuskarta yafara shanye hawayen. Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/13, 6:16 PM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki tanajin yanda yake lashe mata fuska jikinsa har wata rawa yake kamar wanda baya hayyacinsa,kwata kwata ranta baya mata dadi,jitake ta tsani komai dama batazo dakinba,hakan yasa gudun hawayen nata yasake qaruwa,ahankali yasaka hannunsa yafuzgota ya rungume ta tsam a jikinsa,kanta yanakan faffadan qirjinsa tanajin yanda bugun zuciyarsa yake bugawa cikin sauri, yasaka hannunsa yakashe wutar dakin,sannan yadauketa cak yanufi gadonsa da'ita,bai damu da towel din dayake jikinsa ba,kuma bai nemi riga yasaka ba,ya kwantar da'ita a gadon sannan ya kwanta yasakata cikin jikinsa,qamshin turaren data saka ne yake fuzgarsa hakan yasa yadora hancinsa akan wuyanta yana shaqar qamshin,cikin wata irin muryar rada yace" I'm sorry please stop crying" Yana fadin haka ya lumshe idonsa yayinda hancinsa yake yawo a'iya wuyanta yana shaqar qamshin jikinta, d'is....yaji hawayenta ya d'iso akan fuskarsa, ahankali yasaka hannunsa ya goge mata hawayen, sannan ya laluba yadauko wayarsa, yacire security din sannan yace mata "kallah..." Ahankali yafara bude idonta harta gama budeshi fes akan screen din wayarsa,akan idonta yakamo number Asalamiyya yayi blocking dinta, sannan ya kalleta da idanunsa dasuka gama qanqancewa yace"shikkkenan?" Cikin sauri ta gyad'a masa kanta, yace"toki daina kukan" Cikin sauri tasaka bayan hannunta ta goge duk wani hawaye dayake fuskarta,wata irin wawiyar ajiyar zuciya yasaki sannan yamaida kansa cikin wuyanta yana cigaba da shaqar qamshin turarenta, kasancewar tayi kuka hakan yasa tafara jan zuciya alamun tagama kukan, cikin wata irin muryar fitar hayyaci yace mata"nine nasaki kuka ko?" Gyada masa kanta tayi batare da tayi magana ba. Cikin shagwa6a yace" bazan sakeba kinji? " Yanayin yanda yayi shagwa6ar yasa taji wani irin yanayin shauqi yana Neman kamata, bata Iya bashi amsa ba sai kanta data sake gyada masa. Hancinsa ya gangaro zuwa qirjinta yaji inda qamshin yafi yawa, yashaqa yace" waye yabaki wannan turaren?" Cikin rawar murya tace" Mamy ce" Daga nan bai sake cemata komai ba, cikin jin dadi yamaida hancinsa zuwa cikin jikinta yana shaqar lungu da saqo najikinta, Mawahib tana jinsa tayi shiru tunanin ta ya tsaya cak! saide gabanta faduwa yake,tanajin yanda yake hade qafafunsa gaba daya yakasa nutsuwa yadena motsi, hancinsa yana cikin wuyanta, ahaka wani irin bacci me dadi ya dauke shi,tanajin yanda ya qanqameta ko motsin kirki takasa yi,gaba daya saita nemi baccin idonta tarasa,tayaya zata iya bacci ya qanqameta haka? badan gidansu daya da Yaya Captain ba, babu makawa yau datace shi maye ne,bata ta6a sanin anashan hawaye ba sai yau. Motsi tayi zata juya tafara bacci amma cikin sauri yasake ruqota, hakan yasa tahaqura,batasan lokacin da bacci ya dauketa ba. Sunyi wani irin bacci me dadi wanda su kansu basusan tsawon lokacin da suka dauka suna baccin ba,koda wasa basuji kiran sallar farko ba,haka lokacin da aka shiga sallah a masallatai ma basujiba,aka idar basu jiba,saida gari yayi haske sannan Mawahib tafarka,ahankali tafara bude idonta harta budeshi gaba daya tas a fuskarshi,baccinsa yake hankali kwance har lokacin,ahankali tafara qoqarin tashi ganin gari har yayi haske,motsin tane yasa shima yafarka, yana bude idonsa yasauke shi akanta,ahankali yasaka hannunsa yashafa gashinta,idonsa yana kanta sannan yashafa fuskarta yace"jiya kinyi kuka,kanki yana miki ciwone muje asbiti?" Ahankali ta girgiza kanta Sannan tayi qasa da idonta,ta yunqura zata tashi yasaka hannunsa ya riqeta baice da'ita komai ba kawai kallonta yake,kasa kallonsa tayi, ahankali tace"lokacin sallah yawuce fa" Agogon dakin ya kallah sannan yatashi, itama tatashi tana gyara gaban rigar ta,Sannan tasake gyara gashinta daya barbazu, duk yana kallonta, saida yasake qarewa shigar tata kallo, cikin ransa yana fadin fine girl, sannan yasauko daga gadon ya shige toilet. Cikin sauri itama tafice daga dakin takoma dakinta. Bayan ta idar da sallah babu abinda tayi, kawai saukowa tayi tafara qoqarin hada masa abinda zaici kafin yafita aiki. saboda tasan ya makara wajan fita aiki saita hada masa iya tea da bread sai wainar qwai,taqara dafa jallop din soyaiyar taliya 'yar kad'an tadora masa da soyaiyan naman kaza agefe,tana jera abincin a dining yafuto cikin uniform dinsu yana tafiya yana kallon agogon hannunsa, baiyi tunanin harta gama abinci ba adan qaramin lokaci haka,kai tsaye wajanta ya qarasa yadora hannunsa akan kujerar dining din cikin girmamawa yace mata "Ina kwana?" Kallonsa tayi cikin mamaki,Allah yaso ba'acikin mutane yake mata wannan gaisuwar ba,sai mutane suyi tunanin wani abun take masa,babba dashi amma shine yake fara gaishe ta,cikin kulawa ta amsa masa, sannan tazuba masa jallop din taliya wadda taji kayan ganye dasu carrot tatura masa gabansa,ya Kalli taliyar yahadiye wani irin saliva,sannan yaja kujerar baya yazauna yasaka fork yafara ci yana lumshe idonsa,tana daga tsayen tana satar kallonsa yanda yake lumshe ido, da alama abincin yayi masa dadi amma miskilanci bazai barshi yayaba mata ba,wainar qwan tasake tura masa gabansa, tabude bread ta dauko slide hudu ta ajiye, sannan tabude flasks tazuba shayi tahada masa shi yayi kauri, sannan tabar wajan takoma kitchen,gyara kitchen din tayi, tafuto cikin sauri zata fara gyaran falon yataso daga dining din, taku uku yayi zuwa hudu yasaka hannunsa ya fuzgota tafada jikinsa,baice da'ita komai ba yadauketa cak yawuce dining din, bai mata mazauni a ko'inaba sai akan cinyarsa,cikin sauri ta kalleshi tace"yaya Captain zan gyara kitchen..." Cikin sauri yagirgiza mata kai yace"bakya gajiya ne?kici abinci first" Kafin tayi wata maganar yafara bata abincin a bakinta,ya 6ata lokaci sosai wajan bata abincin,yana bata tea wayarsa tafara ringing,dauka yayi batare da yayi magana ba, daga dayan 6angaren akace"Captain Aryan lafiya jiya baka shigo office ba, yauma shiru" Saida yabata tea din sannan ya Kalli wayar yace"Captain Habib Ina hanya" Captain Habib yayi murmushi yakashe wayar. Saida ya tabbatar ta qoshi,sannan yadauki tissue yana goge mata bakinta, Mawahib tayi zugud'um tana kallon ikon Allah,gaba daya al'amarin yaya Captain daure mata kai yake,yakamata tayi waya da Nabiha,saboda abun nasa yawuce tunanin ta,tana cikin wannan tunanin taji yasakar mata kiss a wuyanta,cikin sigar rada yace"kiyi haquri akan abinda yafaru jiya,zan fita,ki kulamin da kanki...." Gabanta ne yayi wata irin faduwa rasss! lokaci daya Yaya Nabil yafado mata,shine yake fada mata wannan kalaman,tasan cewa shikuma soyaiya suke, amma Yaya Captain fa? Kanta ne ya daure,harya ajiyeta zai fita jikinta a Sanyaye yake,tasan de yayi mata magana, amma batasan meyace ba harya fita,yana fita ta zauna jagwab a kujera tareda dafe kanta. Bayan yarage ayyukan office yadauki wayarsa yakira Hajiya kilishi,saida yayi mata 5 missed call bata dauka ba, ya lumshe idonsa tareda ajiye wayar, akwai babban qalubale acikin rayuwar aurensa, yarasa tayaya zai warware wannan matsalar, sai yaushe ne Momy zata sauko tadaina fishi dashi? Yaya zaiyi da ransa? Ashe haka Ashraf yaji lokacin dayake qoqarin fahimtar dashi irin soyaiyar dayake yiwa Mawahib? haqiqa soyaiyar Mawahib kamar jarabawa ce da ubangiji yayi masa, Koda wasa bai ta6a tunanin cewa shi Aryan zai so Mawahib ba, soyaiya ma mai tsanani kamar wannan,baya tunanin akwai wani abu wanda bazai Iya sadaukar mata dashiba, ciki harda ransa,agefe guda ga Momy tanaso yasake ta, idan yasake ta Yaya zaiyi da soyayyar ta? wayarsa yadauka yakira Ashraf,bayan yadauka cikin damuwa yace"Ashraf yaya zanyi da matsalar Momy ne?,bata daukan wayata, dama ranta ya6aci,kuma zuwanmu gida bayan umarnin data bani hakan yasa tasake yin fishi dani,narasa yanda zanyi da raina,idan nasaketa yaya zanyi da soyayyar ta Ash? tayaya zan fadawa Momy soyaiyar yarinyar nan tasa bana gane komai?" Ashraf yayi murmushi yace"dan soyaiya,ya'isa haka" "Ashraf bazaka ganeba,idan Ina tareda ita manta komai nake wallahi,ciki harda kaina, ina mantawa dani ko waye gaba daya sai inzama kamar yaro sai yanda tayi dani" Ashraf yace"ka kwantar da hankalin ka,Momy fa tana sonmu,zata huce,amma wai ya ake ciki ne? kafada mata kana sonta kuwa?" Dan qaramin tsaki yasaki"nakasa fada mata,bazan iyaba,koda nayi niyar fada mata saitamin kwarjini,bansan Yaya zanyi ba" Ashraf ya kwashe da dariya yace"serious.... Aryan, wai kaine kake tsoron mace? kaga karka bani kunya,qanina yafi qarfin kowacce irin mace,kayimin alqawari yau zaka fada mata" Cikin sauri yace"amma Ash..." Dasauri Shima Ashraf din ya dakatar dashi yace" no,banason jin komai,kafada mata,na tabbatar dole zata kar6i soyaiyar qanina,saboda kyakykywan saurayi ne" Captain Aryan yayi murmushi yace"naji,niba saika zigani ba,nayima alqawari" Suna sallama yasaki wata irin ajiyar zuciya me nauyi yanajin kamar yasauke wani tarin kaya me nauyi daga kansa. Bayan tagama gyara gidan ko'ina yayi tas ciki harda dakinsa, ta kunna turaren wuta,gida yadauki qamshi. tayi wanka tafuto falon ta dauko ice-cream tasa agabanta amma takasa sha, abubuwan da Yaya Captain yake mata shine yake damunta,dole de yakamata ace takira Nabiha. Wayarta ta dauka tadokawa Nabiha kira,alokacin tana zaune tasaka taura da magarya agabanta tanataci, dauka tayi tace"mutanan Abuja" Mawahib tace"meciki,ya Babyn mu?" Nabiha tace"gashinan lafiya kalau,yakike kwana biyu Ina Yaya Captain" "yana lafiya Nabiha,ke kinsan meyake faruwa? Shekaran jiya Asalamiyya takira Yaya Captain,lokacin muna breakfast, to inaga saboda ya ganni ne shiyasa bai dauki kiranta ba,jiya da daddare ma wajan shadaya dawani abu tasake kiransa,na dauka nayi mata magana,qarshe de baqin ciki yasa na kashe wayar,shima gashi duk narasa gane kansa,sai wasu abubuwa yakemin kamar ba Yaya Captain ba" Nabiha tace"aina fada miki, kece kikaqi yarda, amma tun kafin kuzo ranar da akai tashin hankalin nan nabaki shawara,haba Mawahib wacece wata Asalamiyya, mezata fada miki? abinda take dashi kema kinada shi saide ma ki nuna mata wani abun, amma idan kika tsaya kallon ruwa kina gani kwado zai miki qafa, kija mijinki ajikin ki,saboda tun ranar da'aka ce yasakeki yaqi sakin ki na tabbatar Yaya Captain sonki yake, inba haka ba ke kina ganin akwai me sauya Yaya Captain ne? Kinde San halinsa babu me Iya masa sai Allah, banda yana sonki babu abinda zai hana a ranar yacika umarnin mahaifiyar sa,saboda haka kidinga kiyaye wa da Asalamiyyan Nan, ni daga ita har Momy kilishi tsoro suke bani" Cikin sanyin jiki Mawahib tace"to shikkenan Nabiha,saimun sake magana" Tana kashe wayar takira Mamy suka gaisa, tasake kiran Abba suka gaisa sannan takira babanta na kebbi, ta ajiye wayar tayi shiru tafada duniyar tunani, meza tayi dan tasaka Yaya Captain aranta kodan ta watsawa Hajiya kilishi qasa a'ido? To amma da gaske ne maganar Nabiha Yaya Captain sonta yake? Idan sonta yake Yaya zatayi da qiyaiyar Hajiya kilishi? Ta wani Fannin gara ace karma yafara sonta, saboda idan de har yana sonta to ita ya kuntowa ruwa, ta tabbatar mahaifiyar sa bazata ta6a sonta ba. Ajiyar zuciya tasaki tabude ice-cream din tasha dan kad'an taji duk yafita daga ranta danhaka tamaida shi fridge. Qarfe uku na yamma tashiga kitchen tadafa musu jallop din cous cous ta yaiyanka hanta aciki,sannan tahada lemon ginger,tayi musu farfesun jan nama d'an kad'an, tawuce sama tasake wanka tasaka riga da wandon jeans,tadawo falo tayi zamanta tana chatting. Har aka kira sallar magrib tana wajan sannan takoma sama domin yin sallah,Captain Aryan bai dawo da wuri ba kasancewar baitafi aiki da wuri ba, Kuma jiya baije ba,bai dawo gidan da wuri ba sai da yatsaya awaje yayi sallar ishai'i sannan yashigo gidan, alokacin tana dakinta bataji shigowar saba,daya shigo falon yaji wani irin qamshi yadakeshi, ya lumshe idonsa sannan ya Kalli dining saboda wata irin yunwa yakeji Kuma yaqicin komai kawai girkin matarsa zaici, cikin sauri ya haye sama anan yaga irin gyaran data yiwa dakin nasa,sai yau yasake tabbatar wa duk gyaran namiji idan mace tayi nata dole kaga banbanci,wanka yashige yafuto yayi shafa, sannan yafeshe jikinsa da turare, yasaka kayan bacci, yafuto daga dakin nasa, adede lokacin itama tafuto daga dakinta tana Sanye cikin daya daga cikin kayan da sister Saudat takawo mata,tana ganinsa gabanta yafadi tayi turus ta tsaya abakin qofa, tayi tunanin baya gidan shiyasa tafuto da wannan shigar tana so tayi sauri taci abinci saita gudu dakinta ta kwanta. Captain Aryan kuwa qamewa yayi awajan yazuba mata ido kamar yau yafara ganinta,numfashinsa ne yafara sauyawa lokacin da idonsa yasauka akan farar fatar jikinta wadda take wani irin sheqi,gabansa yafara faduwa kamar yau yafara ganinta,rigar Iya karta Rabin cinyarta,tanada hannun brezia sannan qirjin rigar akwai breast cup dan qarami wanda madedetan nashanunta suka cika breast cup din har suna futowa waje,shara-shara ce rigar babu abinda baya gani hatta dan pant dinta na rigar shima yana ganinsa,haka kan nipples dinta ma yana ganinsu, tahade gashinta waje daya ta daura ribon kalar kayan,wani irin yanayi ne mewuyar sha'ani yake fuzgarsa,fatan sa kawai yajita a jikinsa,cikin sauri tajuya zata koma dakinta,baisan lokacin daya fuzgota ba,batayi masauqi a ko'inaba sai a faffadan qirjinsa, tanajin yanda yake fitar da wani irin numfashi kamar wanda yayi tseren gudu,yanda yayi mata kyakykywar runguma a jikinsa hakan yasa yayi mata runfa da faffadan qirjinsa,yadora hancinsa akan wuyanta yana shaqar qamshin jikinta,gabanta yafara faduwa Ganin kamar besan meyake ba yasa cikin sauri tafara qoqarin raba jikinta da nasa,lokaci daya yayi saurin daidaita kansa,cikin shaqaqqiyar murya yace"muje nabaki abinci?" Cikin sauri ta daga kanta saboda so take yasaketa, bai qara cemata komai ba yadauketa cak suka nufi dining,Mawahib tayi shiru tana tunanin maganar Nabiha da tace Yaya Captain yana sonta,wannan abubuwan sune soyayya? to amma saboda me zai sota bayan abaya baya qaunar ta? Suna zuwa dining a cinyarsa ya ajiyeta dukda tashin hankalin da hakan ya haifar masa,abincin yake bata shima yanaci amma gaba daya idonsa yana kan nashanunta,Mawahib tanajin yanda yake yawan motsa cinyarsa amma batayi tunanin komai ba.(🙈) ko cokali goma bataci ba tace masa ta qoshi, tatashi daga jikinsa da gudu tayi daki, dawani irin mayen kallo yabita,shima baici gaba da zamaba yakashe wutar falon sannan yabita dakinta. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Mawahib kuwa tana zuwa dakinta tahaye gadonta gabanta banda faduwa babu abinda yake, sauri kawai take tashige cikin bargo, tadaga bargon zata rufa sai gashi yashigo dakin, cak ta tsaya tazuba masa ido qirjinta sai bugawa yake. Akusa da'ita yazauna,sannan yajuyo ya kalleta yace"RUQAYYA...." Cikin sauri ta kalleshi,saboda tunda take da Yaya Captain, tsawon shekaru suna gida daya, bai ta6a cewa Mawahib ba,idan yafada ma to ba'a gabanta bane, amma yau shine yake kiranta da RUQAYYA? meyake faruwa haka? Meyasa taga jikinsa yayi sanyi? Kode bashida lafiya? Kallonsa tayi cikin sanyin jiki tace"na'am" Matsowa yasake yi dab da ita har jikinsa yana gogar nata,yakama lallausan hannayenta duka biyun yariqe sannan ya sassauta murya yace"kiyi haquri..." Cikin mamaki ta kalleshi, batasan haqurin meyake bata ba,cikin idonsa ta kalla tace"meyafaru?" hannunta yariqe gam,sannan yazube gwiwoyinsa aqasa,yayi kneel down,cikin raunin murya yace"nasan cewa nime laifi ne a wajanki,amma inaso kimin kowanne irin hukunci idan har hakan zaisa kisoni...." Gabanta ne yayi wata irin faduwa,lokaci daya ta zaro idonta waje,Yaya Captain ne ya tsugunna mata aqasa yake fada mata wannan maganganun? Cikin sauri tafara girgiza kanta tana qoqarin qwace hannunta,yana ganin haka yatashi daga kneel down din da yayi,yamiqe tsaye tareda fuzgota tadawo jikinsa,idonta ne ya furfuto waje cikin tsananin tsoro da faduwar gaba take kallon qwayar idonsa, fuskarta yakama yariqe da hannunsa biyu,cikin tsananin tashin hankali yace"Ruqayya bakya sona? kin tsaneni ko? bazaki yafemin ba? fadamin yaya kikeso nayi da soyayyar ki? kinaso narasa rayuwata ne saboda soyaiyar ki?..." Cikin sauri tafara girgiza masa kanta hawaye yana ta ruwa a'idon ta, amma bata bashi damar zubowa ba. Yana ganin ta girgiza masa kanta ya lumshe idonsa take yaji wani irin hawaye yana zuba daga idonsa,bai damu daya goge hawayen dayake ba yayi sauri yasaki fuskarta ya rungume ta tsam a jikinsa tareda dora kansa akan kafadarta,tanajin yanda hawayen sa yake d'iga a gadon bayanta (Sorry Captain....😭😭😭) Kuyi haquri da wannan bayawa, muhadu zuwa yamma insha Allah 🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/13, 6:16 PM] AMINA KABIR CAPS: *19&20* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad itama hawayen tafara,kuma shine yasata kukan,saboda bata ta6a ganin babba kamar shi yana kuka saboda soyaiya ba,hawaye take yayinda shima nasa yana d'iga ajikinta,jin danshin lema agefen wuyansa hakan yasa yagane itama kukan take,ahankali yasaka hannunsa ya dauka cak,suka kwanta akan gadonta,duk da yanajin yanda sha'awar sa take sake bijiro masa hakan baisa yanuna mata maitar sa a fili ba,yana kokarin samo soyaiyar sane tukunna,akan jikinsa ya d'orata, sannan yafara shafa dogon gashinta kanta yana kwance luf akan qirjinsa,dukansa sunajin bugun zuciyar junansu, shi nasa bugun zuciyar saboda tsantsar soyaiyar dayake matane dakuma sha'awar dayake ji,jiyake kamar yakai hannunsa yakama nashanunta dasuke kwance a qirjinsa amma yahana kansa hakan, nata bugun zuciyar kuma na tsoro ne da mamakin wai yau Yaya Captain ne ya furta mata Kalmar soyaiya, saitakeji kamar a mafarki, Yaya zatayi? Idan ta amshi tayinsa Yaya zatayi da tsanar da mahaifiyar sa tayi mata? Tana wannan tunanin taji yasaka hannu ya goge mata hawayen idonta, yasake matseta gam a jikinsa ta yanda zai dinga jin nashanun nata yana gogarsa,kad'an yarage tasaki kuka yanda ya matsetan,wani irin numfashi tasaki hakan yasa ya sassauta mata ruqon,yadora bakinsa akan kunnanta, cikin wata irin murya mai cikeda shauqi dakuma tsantsar sha'awa yarad'a mata cewa "i really love you..." Sannan yasaka matar kiss a kunnan,lokaci daya Mawahib tayi mutuwar kwance,wani irin abu taji ya ratsa ta, wanda bata ta6a jin irinsa ba,kanta yaci gaba da shafawa har wani bacci me dadi ya dauke su. Yauma saida suka makara,saboda bacci ne yake me dadin gaske yariga ya fitar da abunda yake cikin zuciyarsa,Kuma gashi gata tana cikin jikinsa yanajin dukkan albarkatun jikinta acikin jikinsa,yayinda Mawahib tayi baccin rashin sabo, bata ta6a yin bacci akan namiji ba,amma yau gashi Yaya Captain yazame mata Katifa. Atare suka farka,saboda duk yanda daya yayi motsi to dayan yanajin dan'uwan sa,kallonta yayi itama ta kalleshi cikin sauri ta runtse idonta,murmushi yayi yacire ribon din data daure kanta cikin murya qasa qasa yace"i luv you..." Cikin sauri tasake 6oye kanta a jikinsa,gashin kanta daya bazu a jikinsu yafara wasa dashi yana mayar mata dashi baya, yayi jifa da ribon yace"kidena sakawa,haka nake sonshi...." Mawahib tayi shiru har yanzu mamakin ta yaqi qarewa,tashi yayi yadauketa cak yakai ta toilet dinta, ta sunkuyar da kanta qasa ganin yanda yake sake qarewa surar jikinta kallo,ahankali yarufo mata qofar sannan yanufi nasa dakin,kai tsaye toilet yashiga yafara wanka ya tsarkake jikinsa sannan yayi alwala Yafuto yatada kabbarar sallah. awajan break ma yana zauna yana ganin yanda take zuba musu abincin harta gama taja kujera zata zauna yamiqa mata hannunsa tareda fadin"zonan" Ahankali tatako taqaraso wajansa,hannunsa yabata, babu musu tadora nata hannun acikin nasa,yajata ya d'orata akan cinyarsa, sannan yace"daga yau karki sake zama a ko'ina, nan ne wajan zamanki, kingane?" Kanta ta daga masa,yadauki fork yafara yadauko chips yasaka mata a bakinta tafara ci sannan shima yafara ci,saida yaga ta ware tanaci sannan yasake daukowa guda hudu zai saka mata a bakinta, cikin sauri tafara girgiza kanta tace" Yaya Captain yayi yawa..." Cikin murya qasa qasa yace"A a baiyi ba,bude bakin" dan qaramin bakinta tasake budewa yasaka mata duka guda hudun,ganin da gaske yamata yawa yasa ya sunkuyo da kansa dab da fuskarta sannan yadora bakinsa akan nata bakin yakaryi sauran chips din yafara ci idonsa yana cikin qwayar idonta. Mawahib taqame a zaune a cinyarsa,anya kuwa Yaya Captain ne? kunun gyada yadauka a cup yanufi bakinta dashi tasha, sannan shima yasha,yasake bata,garin sha wani dan kad'an yazubo mata akan lips dinta, cikin sauri ta meqa hannu zata dauki tissue ta goge bakinta yayi sauri yariqe hannun sannan yakama fuskarta yariqe yace"cloth your air..." Cikin sauri ta lumshe idonta,kafin tafara tunanin meyasa yace tarufe idonta saijin saukar lips dinsa tayi akan nata, yana lashe mata wajan da kunun gyadar yazubo mata,cikin sauri ta bude idonta ta kalleshi, shima idonsa yana cikin nata saide bai fasa tsotsar lips din nataba saboda wani irin laushi da yaji lips din nata yana dashi,yasake haduwa da nasa laushin lips din,tun yana kallon fuskarta baisan lokacin daya lumshe idonsa yakama duka lips din nata na qasa yana tsotsa ba,bai ta6a irin wannan kiss dinba tunda yake,hakan yasa yamasa mugun dadi har baima san lokacin daya sake ruqo kanta ba,yariqe kanta da duka hannunsa biyu yana tsotsar bakinta,Mawahib da idonta yake bude ta kalleshi,gabanta banda faduwa babu abinda yake,tarasa meyake damun Yaya Captain, cikin sauri tafara qoqarin cire bakinta daga nashi, ahankali yabude idonsa ya kalleta, cikin wata irin murya mai Sanya kasala yace"please...." Sannna yasake maida idonsa ya lumshe,wani irin dadi yakeji wanda bai ta6a sanin cewa idan ana irin wannan kiss din haka akeji ba, yayinda Mawahib ta runtse idonta tanajin yanda yake tsotse mata baki ciki da bai,wani irin yanayi tafara ji ajikinta wanda tarasa gane na menene,numfashinta yafara sauyawa, cikin sauri tayi qoqarin qwace bakinta,lips dinta har wani zafi zafi suke mata. Kallonta yayi da jajayen idonta,yasake janta jikinsa ya rungume ta yana sake sauke numfashi,gaba daya ta tsorata dashi,dama haka yake? ganin lokaci yana tafiya hakan yasa tayi dabara tace"zaka makara aiki" Kansa ya gyada mata, sannan ya sauketa daga cinyarsa yace"Ina zuwa" Bayansa tabi da kallo, tagade gashinan tsaf cikin uniform dinsa yagama Shiri meyasa zai koma daki? Yana zuwa dakinsa yacire uniform din duka, yashiga wanka,saida yasake watsa ruwa sosai a jikinsa, sannan ya futo yasauka sabon boxer saboda wancen yariga ya lalace(🙈🙊) Sannan yamaida uniform dinsa yasauko,alokacin harta gama dauke kayan dasukaci abinci tana kitchen tana wanke wa,kitchen din yabita ya rungumota tabaya sannan yadora hannunsa akan cikinta yace"ki kulamin da kanki kinji?..." Cikin sauri ta gyada masa kanta. Yadora bakinsa akan kumatunta yasakar mata kiss sannan yace" I luv you..." Ya juya yafice daga falon, saida Yafuto compound din gidan ya Kalli rana ta kalleshi, sannan yasan cewa yauma ya sake tafka wani lattin(😲) Tana ganin fitarsa tasaki wani irin numfashi tareda dora hannunta akan lips dinta tana shafawa, Yaya Captain haka yake dama? jiki a sanyaye datagama aikin komai sannan takoma falon sama tayi zamanta acan,bata zauna afalon qasa ba. Kamar yanda bai fita da wuri ba,tayi tunanin zai dade kafin yadawo,saide tunanin ta bai tabbata ba, saboda da wuri yadawo gida harta kasa 6oye mamakinta,tunda yadawo gidan yahanata sakat, bai barta ta zauna ita kadai ba, tana zaune a jikinsa,tun tana jin hakan wani iri harta haqura tafara sabawa da Zaman jikin nasa. haka zamansu ya kasance tsawon sati biyu, babu abinda ya canja daga kulawar dayake bata, har zuwa wannan lokacin Mawahib bata furta masa cewa tana sonshi ba,saide yanda yake janta a jikinsa, yake mata masauqi a jikinsa hakan yasa tayi mugun sabo da jikinsa,koda yaushe zaka gansu manne da juna yayi mata runfa da faffadan qirjinsa,a tsawon sati biyun nan tun ranar da yayi mata kiss a dining bai sake yimata ba, saide a hannu idan zai fita aiki, kokuma a goshinta kokuma kumatunta,yadage tuquru wajan ganin yaja hankalinta gaba daya domin ya siye zuciyarta da zallar soyaiyar sa,tun lokacin dayaje dakinta suka kwana basu sake kwana tare ba,da wuri take guduwa dakinta tarufe tayi kwanciyar ta,sabida qarfi dayaji nema yake yakarya duk wata Garkuwa ta jikinta. Ta 6angaren maganinsa kuwa baya wasa dashi, kullum yana cikin sha kamar yanda likita ya dorashi akai,kuma har zuwa wannan lokacin babu wanda ya fadawa yaje wajan likita sai Ashraf... yafison iyayen nasu duk suga result ajikin matarsa(🙈) Kamar yanda suka saba yauma bayan sungama komai tawuce zata tafi daki,saiji tayi yayi sama da'ita,bai zame ko'ina dasu ba sai dakinsa,bata tada hankalin taba, saboda tasan cewa babu abinda zai mata,tsawon wannan lokacin tun lokacin daya furta mata Kalmar soyaiya bai ta6a yunqurin yin wani abu da'ita ba,illa iyaka kiss, dagashi babu qari, hakan yasa ta kwantar da hankalinta,tana kwance a jikinsa kamar yanda yasabar mata har bacci yafara fuzgarta taji yana sauke wani irin numfashi. Fuskarsa cikeda gumi yarasa yanda zaiyi da tarin sha'awar ta datake addabarsa,amma bazai Iya yimata komai ba harsai yasan Yaya matsayin sa yake a wajanta,har yanzu yana lura da'ita baiga alamun tana sonshi kamar yanda yake sonta ba,bai San menene acikin zuciyar taba, haka kuma taqi bude masa zuciyar tata yasan Yaya matsayin nasa yake,kokadan taqi bashi damar dazai gano inda ta'ajiye shi. runtse idonsa yayi yana matse qafafunsa waje daya, ahankali tabude idonta ta Kalle shi,cikin mamaki tace"Yaya Captain kana lafiya?" Kansa yadaga mata,sannan yariqe fuskarta yadora harshensa akan lips dinta yafara lasa, duk da hakan bata tsorata ba,saboda dama inde wannan ne yasaba, hakan yasa batayi yunqurin hana shi ba,tana jinsa tun yana lasar lips dinta harya gangaro yadawo yahade bakinsu waje daya. ahankali yakama harshanta yana sha idonsa a lumshe,sosai yake aika mata da zafafan kiss,Mawahib tayi shiru tanajin yanda jikinsa yake rawa tun yanashan bakinta ahankali har yafara fita hayyacinsa yafara abu da zafi zafi kamar za'a qwace masa ita,jitayi yana qoqarin tura hannunsa cikin rigar ta, hakan yasa tafara tureshi,daqyar ya'iya daina kissing dinta yabude idonsa dasuka gama lumshe wa da fitina yace"bakyaso ne?" Babu musu tadaga masa kanta,yayinda hannunta yake kan qirjina ta danne rigarta tana tsoron karya sake qoqarin saka mata hannu,cikin sigar lallashi yace"tokiyimin,ni inaso" Cikin sauri ta kalleshi,tayaya zata Iya kama bakinsa tasha? kallonsa tayi tace"no" Idonsa ya lumshe,sannan yasauke wani irin numfashi yace"Okay" Daga nan yajuya mata baya tareda lumshe idonsa,batace dashi uffan ba itama ta lumshe idonta saboda gaba daya a tsorace take da al'amarinsa,yanzu daya saka mata hannu a cikin rigarta mezai faru kenan? Kasancewar yariga yasaba mata da kwanciya cikin jikinsa hakan yasa cikin bacci batasan ta lallabo tashige jikinsaba,shima yasaka hannunsa yasake rungume ta,duk da suna bacci,atare suka saki ajiyar zuciya. Da asuba suna farkawa suka gansu manne jikin juna,batare daya saketa ba yace"meyasa kikazo jikina?" dan qaramin bakinta taturo gaba cikin shagwa6a tace"to meyasa ka rungume ni?" Murmushi yasaki yana mamaki lalle bakinta yafara budewa tunda gashi yana fada tana bashi amsa. tashi yayi zai shiga toilet wayarsa tafara qara,cikin mamaki ya juyo,Mawahib tayi sauri ta bashi wayar itama tana mamakin meyasa Yaya Ashraf yake kira a'irin wannan lokacin? Saboda taga shine me kiran. Dauka yayi sannan yazauna abakin gadon yace"Ash..." Cikin damuwa Ashraf yace"tun qarfe uku nake kiranka fa,ina kasa wayarka ne? Momy batada lafiya cikin dare Daddy yamin waya muka tafi asbiti,yanzu haka muna asbitin,jikina yayi sanyi da rashin lafiyar ta Aryan..." Cikin sauri yatashi tsaye yace"what innalillahi...,meyake damunta to? meyasameta? kode saboda nine?" Ashraf yace"tun ranar dakukazo gida tace kasaki Mawahib,yan'uwanta sukazo har gida suka lallashe ta, tun daga ranar tadaina kula kowa,daga nan kuma sai zazza6i kad'an kad'an,nafi tunanin tasaka abun aranta ne,dazu tana aman jini har mukazo asbitin" Dafe kansa yayi da hannunsa sannan yace"Ash inada laifi awajan Momy,nasan cewa bazata yafemin ba saboda banbi umarnin taba,bansan Yaya zanyi ba" Ashraf yace"Aryan,kadena wannan tunanin,Momy zata so aurenku,kuma insha Allahu watarana zatayi alfahri da aurenku" Cikin damuwa yace"Allah yasa,zamu taho yanzu" Wayar ya ajiye ya Kalli Mawahib da jikinta yayi sanyi,saboda duk taji abinda yafaru a wayar,lokaci daya, kuma karon farko da taji tausayinsa ya kamata, cikin sanyin jiki yace"Allah yabata lafiya" Kansa ya gyada yace"Amin,kiyi sallah zan dawo daga masallaci saimu tafi" Ta amsa masa sannan tafuto daga dakin nasa tawuce nata dakin, wanka tayi sannan tatada sallah, tana idarwa tatashi ta shirya cikin doguwar riga ta abaya,ta dauki abinda zata buqata tasaka ajaka sannan tafuto falo,shima yana idar da sallar gida yataho,sai waya yakira ya fadawa Captain Habib komai, yana zuwa ya shirya suka futo, lokacin har gari yafara Haske, magana yayi da David sannan yadawo suka wuce airport. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Qarfe tara daidai a Airport ta musu,kasancewar sun dade kafin jirgin yatashi, Ashraf ne yaje Airport din daukosu,tundaga nesa yahango su yaga sun qara wani fresh kamar daga wata qasar suka dawo,suna qarasowa wajansa Aryan ya rungume shi, sannan suka shiga mota,duka su biyun suna gaba, Mawahib tana baya,saida suka fara tafiya sannan ta gaida Ashraf, ya amsa mata cikin sakin fuska. Gida suka fara zuwa,suka ajiye Mawahib, sannan suka wuce asbitin, Mamy tana kitchen itada Mama Sadiya kasancewar weekend ne sai ganin Mawahib sukayi,cikin murna taje ta rungume Mamy. Mama Sadiya tace"mutanan Abuja,kun qaraso kenan?" Cikin farinciki tace"mama munzo wallahi, Ina Nabiha?" "Nabiha tana gidanta,itace ma take fadamin Ashraf yakira Aryan din ai yasanar dashi, shine nace to yau Kuna hanya" "hakane tun asuba muka futo daga gida fa,yame jikin?" Mama Sadiya tace"jiki da sauqi za'a ce,yanzu zan koma asbitin ma" Zata sake magana Mamy tace"sannunku da zuwa" tace"sannu Mamy, Mamy yunwa nakeji" "ga abinci nan dauki kije kici" Mama Sadiya tayi murmushi tana sake qarewa Mawahib din kallo taji tana maganar yunwa kode sun samu qaruwa ne,to amma data tuna da matsalar Captain saita daina tunanin" abincin ta dauka sannan ta Kalli Mamy tace"Mamy ina na Yaya Captain?" Mamy ta kalleta cikin mamaki,kode tafara sonsa ne? Kafin tabata amsa Mama Sadiya tace"kizo ki zuba masa mana Mawahib,saiki kai masa dakinsa" Ta amsa mata sannan tafuto daga kitchen din,Mamy ta Kalli mama Sadiya tace"Maman Nabiha Kinga zamani?" Mama Sadiya tace"ai Mawahib da sauqi,ni Nabiha kallon cikin idona takeyi take cewa ita tana son mijin ta" Mamy tayi murmushi ta girgiza kanta sannan ta dauko wani flask din tazuba wa Aryan din,kasancewar yau itace da girki tasan cewa basai an sake yimasa wani girkin daban ba, girki ne na zamani wanda zai birge wanda yaci. Tana shirin futowa daga part din Mamy saiga Mamy din tashigo, abincin ta bata tace"gashi saiki ajiye masa" Kar6a tayi tajuya ciki,itama tazubo abincin ta zauna kusada Mamy tanaci, kana ganinta kasan cikin farinciki take,tana gama cin abincin suka dasa sabuwar fira,har yamma su Captain Aryan basu dawo gidaba,Mamy tana lura da Mawahib taga koda wasa bata kira mijin nata tayi masa maganar yazo yaci abinci ba,Bata kirashi tayi masa tambaya Yaya jikin mahaifiyarsa ba, bata kirashi taji Yaya lafiyar saba, daga nan tasan cewa har yanzu ba lalle Mawahib tana sonsa ba,inda tana sonsa ko awa daya ba zatayi ba dole ko acikin magana ne saita sako maganar sa, amma koda wasa banda tambayar abinci, babu abinda tayi wanda ya danganci Aryan,daga nan tasan cewa akwai sauran rina a kaba. Sai qarfe goma shadaya nadare suka dawo gida tareda Alqali,kai tsaye Alqali part dinsu yawuce, shikuma Captain Aryan da Ashraf suka shigo part din Mamy, alokacin suna zaune itada Mamy, cikin farinciki Mamy tace"sannunku da zuwa" Captain Aryan ya Sosa kansa yace"Anty Ma-my,barka da dare" "Yawwa Captain,yame jikin?" Ashraf yace"jiki da sauqi Mamy,mun taho de tasamu bacci" Mamy tace"Allah yabata lafiya,aida safe munje nida Alhaji,to dazan dawo gida sai muka taho da maman Nabiha saboda tatafi musu da abinci, ku zauna bari akawo muku abinci, kun wuni bakuci komai ba" Ashraf yace"eh wallahi,Allah yasa ba Mawahib ce tayi jagwalgwalo ba,girkinki kawai zamuci Anty Mamy" Mawahib ta Kalli Yaya Ashraf cikin shagwaba taturo bakinta gaba tace"Mamy wai nice nake jagwalgwalo?" Mamy tayi murmushi tace"Kinga tashi ki basu abinci dan Allah" Tashi tayi tanufi dining,Captain Aryan yana jinsu baice komai ba sai dan qaramin murmushi da yayi,yarasa meyasa yakejin nauyin Mamy yanzu. Abincin ta ajiye musu, sannan tazuba musu,ta kalli Captain tace"Yame jikin?" wani irin kallo yayi mata yace"Alhamdulillah" Daga haka bata sake cewa komai ba,tatashi tawuce dakinta,Captain yabita dawani irin kallo,Ashraf yana ganin haka yayi sauri yata6o shi,cikin sauri ya sunkuyar da kansa, saide Mamy tana kallonsa ta gefen idonta,yanzu kam tagama tabbatar wa Mawahib bata bawa Captain kulawa,bataga wata soyayyar captain mashahuriya acikin idon Mawahib ba. Sun dade a part din suna firarsu da Mamy sannan sukai mata sallama suka tafi,directly wajan Alqali sukaje alokacin shima yana cin abinci, sallama suka masa, sannan Ashraf yaraka Captain dakinsu, shikuma yayi masa sallama yatafi gida. Kwanciya yayi adakin shiru shi kadai,tunani rashin lafiyar Hajiya kilishi yake,tunda sukaje asbitin oxygen ne a hancinta ko magana basu samu damar yida itaba. Idan har sakin Mawahib shine zaisa Momy ta warke Yaya zaiyi kenan? tunani ne yayi masa yawa,kuma Ashraf yatafi bare suyi magana akan matsalar,juyi yasake yi yashafa gefen sa yau bata nan,tsaki yasaki yatashi ya zauna yana tunanin tayaya zai Iya bacci shi kadai batare da'ita ba? Tayaya zai Iya bacci bayan tariga tasaba tana shige wa jikinsa laushin fatarta yanasa yayi dogon bacci cikin nutsuwa? Agogon dakin ya kalla yaga shabiyu nadare,amma kokadan bayajin alamun bacci a'idonsa,wayarsa yadauka yadoka mata kira,alokacin tana bacci tayi daidai tana shan esi tana Sanye cikin doguwar rigar bacci irin kayanta nada wanda take amfani dashi kafin ayi musu aure, wayarta ce take vibration cikin bacci ta laluba ta dauka takara a kunnanta batare data kalli me kiran ba,shiru yayi tsawon lokaci baice komai ba, itama batace komai ba,yanajin yanda numfashinta yake sauka tacikin wayar. Wani irin numfashi ya sauke yace"kinyi bacci?" tanajin muryar sa tabude idonta,cikin muryar bacci tace"um" "zaki Iya baccin ne?" Juyi tayi, tasake riqe wayar tace masa"um" Cikin kulawa yace"Okay,gud night" Batace masa komai ba yakashe wayar,bayan ya ajiye wayar shiru yayi tsawon lokaci,yasake daukan wayar yakirata. Saida wayar takusa katsewa sannan ta dauka,cikin wata irin murya yace"are sure zaki Iya bacci batare dani ba...?" Cikin shagwa6a irinta masu bacci tace"yaya Captain bacci nakefa" Cikin lallashi yace"no kitashi kitaho..." Wani irin kukan shagwa6a tafara zuba masa,ya lumshe idonsa sannan yakashe wayar batare da yayi magana ba,tashi yayi yasaka jallabiya kai tsaye yanufi part din Mamy(🙆🏻‍♀️) Yana tura qofar falon yaji shi abude,cikin sauri yanufi dakinta,yakama handle din dakin yabude yashiga,wutar dakin ya kunna yaganta tana baccinta cikin kwanciyar hankali,doguwar riga ce ajikinta amma mai kauri,zama yayi agefen kanta yafara shafa fuskarta,sannan yayi kasa da kansa yadora fuskarsa akan nashanunta yafara yawo da fuskarsa akansu yana shafasu da fuskar, cikin rada yace"kitashi mutafi" Wani irin zabura tayi jin fuskarsa tana yawo akan na shanunta,cikin sauri yariqe fuskarta, murmushi yasaki yace"muje dakinmu?" Cikin sauri tace"yaya Captain su Mamy fa..., agida muke fa" Cikin sauri yadora hannunsa a kan bakinsa, ya kalleta da idanunsa dasuka fara qanqancewa yace"shiiiiit" Sannan yasaka hannu yadauketa cak,suka futo daga dakin. Adede lokacin Abba da Mamy sun futo daga dakin Mamy din zasu koma dakin Abba su kwanta kamar yanda suka saba,Abba ne yafara ganinsu, cikin sauri yaja hannun Mamy sukai baya,basu yarda su Captain sun gansu ba, saida sukaga fitarsu sannan Abba ya Kalli Mamy yace"meyasa baki tura ta wajan mijin taba?" Mamy tace"Alhaji ai danaga abun da kunya,duka muna gida daya?" Murmushi yayi yace"a a,kibar yaro yaji dumin matarsa,adena barin ta tana kwana anan,inde baso kike yadawo nan suna kwana tare ba" Mamy tace"amma Alhaji fisabilillah kunsan da irin wannan lokacin amma tun farko baza'a tura yaran nan wani gidan ba? " Cikin tsokana yace" a a gara kusa damu danki gane da kyau yarki jarumi ta aura,yarona babu daga qafa"(😂) Wata irin hararar soyaiya tayi masa, sannan tawuce dakin nasa shima yabi bayanta. Suna zuwa daki yadireta agadon yace"yi baccin anan" Kwanciya tayi agadon tana turo bakinta gaba cikeda shagwa6a,jallabiyar jikinsa yacire,yarage dagashi sai gajeren wando sannan yakashe wutar dakin, yahau gadon yajata ya rungume ta yana sakin wata irin ajiyar zuciya,lokaci kankani bacci yadauke su gaba dayansu. Kiran sallar farko akan kunnan Mawahib akayi,cikin nutsuwa tafara zare jikinta daga nashi,yana jinta yabude idonsa yace"Ina zakije?" Rigar jikinta data dan tattare ta gyara sannan tace"tafiya zanyi,ni tsoron Mamy nakeyi, karta tashi taga bana Nan" Murmushi yasaki yace"muje nakaiki to" Yafadi hakan yana qoqarin tashi,cikin sauri tace"A a,zanje dakaina" Murmushi yayi yace"kishirya qarfe takwas zamuje asbiti" Cikin sanyin jiki tace"to" Sannan tafuto daga dakin cikin sauri takoma part din Mamy,tana zuwa tashige dakinta tareda rufowa. itace takai masa breakfast dinsa daki lokacin yana wanka, sannan itama taje taci, Mamy ta shirya mata wanda zata tafi dashi asbitin takaiwa Maman Nabiha,kamar yanda yafad'a qarfe takwas suka yiwa Mamy sallama suka shiga Mota suka tafi,suna zuwa asbitin shine yariqe kwandon abincin suka qarasa ciki,itace take binsa abaya jikinta yayi sanyi saboda batasan Yaya wannan zuwan nata asbitin zai qare ba,suna shiga dakin taganta a kwance likita yana yi mata gwaje-gwaje,Mama Sadiya tana gefe a zaune,agefe guda ta raku6e kana ganinta kasan akwai wani abu aqasa, likitan yadubi Captain Aryan yace"jikin nata yana sake warwarewa,hawan jini ne yake damunta saikuma ciwon zuciya dayake son kamata,munyi magana da Alhaji ta waya shima na sanar dashi komai,amma insha Allah zamuyi Iya kokarin mu akan hakan,akwai buqatar aqara mata jini, zamu duba jinin nata sai mu duba idan muna dashi sai azo asaka mata" Captain Aryan yabashi hannu suka sake gaisawa, sannan likitan yafita, gadon ya qarasa ya sunkuya daidai kanta yariqe hannunta yace"Sannu Momy,Allah yabaki lafiya" Ahankali ta lumshe idonta sannan ta bude alamun amsawa,Mawahib dake gefe adan tsorace tace"Momy Allah yaqara afwa" Hajiya kilishi tayi shiru bata amsa mataba,saide kallonta datake yi, mama Sadiya datake gefe ta girgiza kanta,me hali de baya fasa halinsa,Ina laifin wanda yatako yazo inda kake domin ya duba jikinka? ta kalli Mawahib tace"Mawahib qaraso ciki mana" Ahankali taqaraso dakin, taja kwandon da Captain ya ajiye ta turawa Mama Sadiya gabanta tace"ga abincin ku inji Mamy,tace tana mata yajiki" Mama Sadiya tace"jiki da sauqi, tun cikin dare tafarka saide bakin shiru babu magana saide tana amsawa da idonta,har zan kira su Ashraf ma saina fasa tunda dare ne, saina fadawa likitocin" Cikin sanyin jiki Mawahib tace"Allah yabata lafiya" Mama Sadiya da Captain suka hada baki suka amsa tare. Mama Sadiya tazuba abincin sannan ta matsa tadago Hajiya kilishi tafara bata abincin,ko spoon uku bataci ba, tafara kwara amai wanda yake tahowa harda jini acikin aman, gaba dayansu tsorata sukai da Amman nata ganin yanda take zubar da jini dayawa,lokaci daya kuma aman nata ya tsaya cak, tafara maida numfashi,dukansu kanta sukayi suna mata sannu. Mama Sadiya tafara qoqarin cire mata kayan, Mawahib ta matso suka cire mata,duka kayan ya6aci da jini,cikin rashin qyanqyami Mawahib tacire dankwalin abayarta ta daura shi akanta,sannan ta dauki kayan tanufi cikin toilet din dakin tace"bari na wanke mata kayan" Mama Sadiya tace"to sannu Mawahib,Allah yayi miki Albarka" Tafadi hakan tana sakawa Hajiya kilishi wani kayan. Tsaf Mawahib ta wanke kayan, sannan ta dauko wata mopper tazo tagyara wajan, tabude Jakarta ta dauko turare ta fesa awajan, Hajiya kilishi babu abinda take sai kallonta. Captain Aryan kuwa dayake gefe banda ido babu abinda ya zuba mata, wacce irin yarinya ce ita? Meyasa har yanzu taqi ta amshi tayin soyaiyar sa? Mezai mata arayuwa taji dadi kodan wannan kulawar data ba mahaifiyar sa? Menene acikin ranta har tsawon wannan lokacin data kasa kar6ar tayi soyaiyar sa? Yana wannan tunanin yaga tafita da kayan zataje ta shanya su. Bayan fitar ta Ashraf da Nabiha da Alqali da Mamy da Abba da Alhaji khaleed,sukazo asbitin saboda duka sunji labarin ta farka. tasha wahala kafin tasamu inda ta baza kayan saboda batasan kan asbitin ba. Bayan tagama shanya kayan tadawo dakin, tana shigowa taga duka Yan gidan sunzo, gaida su tayi takoma kusada Nabiha ta tsaya,likita ne yasake duba ta sannan ya kalli Alqali yace"Alhaji munrasa irin jininta wallahi,bamu dashi yanzu,saide mufara gwada naku idan yayi daidai sai asaka mata,idan baiyi ba sai mu tura asiyo da wuri saboda idan yawuce awa biyu ba'a saka mata ba maganar gaskiya zuciyarta zata samu matsala" Cikin sauri Captain Aryan yace"wanne irin jini ne da'ita? zamu bata nida Ashraf" Likita yace"O negative ne da'ita" Alqali yace"ba irin nasu bane,da Ashraf dani da Aryan duka irin jini nane dasu,saide a gwada na khaleed da Isah" Likita yace"babu damuwa zamu Iya tafiya" Lab sukaje aka dauki jininsu,sannan suka dawo dakin suka zauna kowa sai sannu yake mata. Mamy tayi shiru tana tantama aranta kode tafada musu irin jinin Mawahib ne? to amma Hajiya kilishin zata so hakan ne? Ba lalle ne taso asaka mata jinin Mawahib ba,saboda tsanar data mata, danhaka tayi shiru ta bari adauki nasu Abban Nabihan sai asaka mata. Mawahib kuwa tunda taji anfadi irin jinin Hajiya kilishi gabanta yafara faduwa saboda tasan cewa irin jininta ne,tadaga kanta tana kallon mutanan dakin,ta kalli Hajiya kilishi taga idonta yayi wani irin yallow,gashi ta qara fari dama Kuma gata fara tas,ahankali tafice daga dakin,duka Yan dakin sunga fitar ta saide kowa yayi tunanin wani uzurin ne yafiyar da'ita,Captain Aryan yabi bayanta da kallo yana tunanin inane zataje Kuma? Tana futowa daga dakin tafara dube dube ko zata ga likitan,tafiya takeyi da baya saitaji tayi karo da mutum, tana juyawa taga likitan ne,cikin sauri tace"doctor jinin nasu yayi?" Cikin damuwa yace"wallahi ansamu matsala,baiyi ba, kinsan irin jinin nata ne akwai wahalar samu gaskiya, gashi kuma matar nan tana cikin had'arin gaske" . Cikin rashin damuwa tace"doctor irin jinina gareta,kad'auka kasaka mata" Cikin sauri likitan yasake kallonta yace"are sure babu damuwa su Alhajin sun sani?" Tace"babu damuwa doctor" Lab din suka juya,yadauki jinin nata yagwada danya sake tabbatar wa, yajira results yafuto yagani zata Iya bata, wani dakin daban sukaje ta kwanta a gadon wata nurse tana tsaye agefensu,likitan yasaka wani qaton sirinji suka fara daukan jinin,tsawon lokaci yadauka yana tsaye saida yagama daukar jinin sannan yabarta da nurse din yatafi dakin da ahalin Alqali suke. Yana zuwa mamaki ya kamasu ganinsa da jini a hannu,Alhaji khaleed yace"doctor muna jira kazo da result din gwajin jininmu domin mugani zamu Iya bata kokuwa, amma kuma yaya muka ganka da jinin? ko kunsamu ne awani wajan?" Likita yayi sauri yajonawa Hajiya kilishi jinin,ya daidaita gudun shigar jinin sannan ya kalli Alhaji khaleed yace"kamarya? tacemin Alhajin yana sane taje wajena,dama ba kune kuka turo taba?" Gaba daya mutanan dakin sai suka zubawa likita ido suna kallonsa. Cikin sauri Alhaji khaleed yace"muka turo wa?" Cikin mamaki likita yace"yarinyar dana gani dazu anan me doguwar riga abaya ai itace tasameni yanzu tace adauki nata jinin asaka mata saboda irin jininsu daya" Mamy tanajin haka tasan cewa Mawahib ce,Hajiya kilishi datake kwance tana magana da ido wannan lokacin bayan tagama jin abinda likita yafada lokaci daya ta qame takasa motsa idon natama. Cikin sauri Captain Aryan yatashi tsaye gaba daya idonsa yarufe ya manta iyayen nasa suna cikin dakin,ya kalli likitan tace"yanzu tana Ina? tana wanne hali?" (Ina masu sirika me halin Hajiya kilishi? Shin zaku Iya sadaukar war da Mawahib tayi kokuma Allah yabata lafiya? 🤔🤔) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻[7/14, 1:55 PM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB *Page 19&20* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Doctor yace"tana next roo...." Kafin ya qarasa cewa room,Captain yafice daga dakin,ganin Captain Aryan yatafi hakan yasa Mamy ko kuskuren fita daga dakin batayi ba. Alqali yace"bamu saniba doctor, aida nima bazan bari ba saboda kada yarinyar tashiga matsala" Likita yace"idan ba'a saka mata akan lokaci ba itama marar lafiyar zata Iya shiga matsala Alhaji,kuma naduba naga tanada isasshen jini, shiyasa nadauka" Mamy takalli Alqali yace"Yaya ai babu damuwa,Mawahib ma ai daya suke dasu Ashraf..." Hajiya kilishi tanajin furucin Mamy wata irin kunya ta kamata,yau itace a kwance a wannan halin amma yayanta na cikinta basuda ikon taimaka mata sai gashi Mawahib din datake qi itace yau tabata jini,itace ta tsaftace mata jikinta lokacin da tayi amai harda jini,ahankali ta lumshe idonta wani irin hawaye ya silalo daga idonta, babu wanda ya lura da hakan. ****** Yana zuwa dakin yaganta a kwance a gadon,tariqe hannunta da aka dauki jinin ta danne wajan da audiga,mayafin abayar yafadi akan gadon,dogon gashinta ya baiyana,cikin sauri ya qaraso gadon yafara tatta6a jikinta baima lura da nurse din datake tsaye ba,yariqe fuskarta da hannayen sa cikin damuwa yace"meyasa kikai haka?, bakyajin magana ko? idan kikai rashin lafiya fa? Yanzu inane yake miki ciwo?" Kallonsa tayi ganin yanda ya rikice yake jero mata tambaya tace"Yaya Captain banajin komai" Ashraf ne da Nabiha suka shigo dakin,nurse din ta kalli Aryan tace"yalla6ai asamo mata fruit da maltina saitasha kafin tatashi,zai qara mata kuzari" Captain Aryan yadago ya kalleta, sannan yashafa fuskar Mawahib ya miqe tsaye,ya Kalli Ashraf,batare da yayi masa magana ba suka juya suka bar dakin, itama nurse din tafita, Nabiha ta zauna agefen gadon tace"Mawahib?,sannu Mawahib,gaskiya kinyi kokari,bakya tsoron kisamu matsala?" Murmushi tayi tace"Nabiha likita yace zuciyarta zata samu matsala idan ba'a saka mata ba,kuma irin jini nane,dan Allah nabata ai,badan halin datake nunamin ba" Nabiha tace"eto hakane, aikuwa yanzu wallahi saitaji kunya,ai tanaji likitan yace kece kika bata jinin,zamuga ya zatayi idan ta warke " Mawahib tayi murmushi tace"Allah ya shiryeki Nabiha,Nabiha wai tayaya kike gane Yaya Ashraf idan suka hadu da Yaya Aryan? ni yanzu dasuka hadu duk saina kasa gane menene banbancin su, har yanzu bana ganesu,saide idan Naga fuskar mutum daya adaure to shine zan gane" Nabiha tayi dariya tace"idan zamu futo wani turaren daban nake fesa masa ba irin Wanda suke amfani dashi shida Yaya Captain ba,to zoben hannunsu iri daya,kuma a'irin dan yatsa daya,sannan su saka kaya iri daya, hula daya, agogo daya,turare daya,waya iri daya, tayaya zan ganesu idan suka hadu? Yanzu kuwa tunda gida daya nake dashi wallahi sauya masa turare nake, Kuma baya cewa komai," Mawahib ta gyara kwanciyarta tace" to idan qamshin turaren ya sheqe fa?" Tace"to daga nan kuma saina barwa Allah sauran"(😂) Mawahib tayi dariya adede lokacin suka dawo dakin, Captain ya zauna kusada ita yabude mata maltina sannan yatashe ta zaune, yajanyota jikinsa kad'an, sannan yafara bata,saida tasha kusan rabin gongoni sannan ta kawar da kanta tace"ya'isa" Cikin sigar rada yace"kin tabbata?" Kanta ta daga masa. Ashraf dayake tsaye agefensu yace"sannu Mawahib,Allah yasaka miki da Alkhairi" Murmushi tayi batace komai ba. Ashraf ya Kalli Captain yace"muje wajan Momy tunda ga Nabiha suna tare" Cikin gamsuwa yadaga kansa,sannan ya sunkuya yasakar mata kiss akumatunta,yariqe fuskarta da hannunsa biyu, yayi qasa da muryarsa yace"karki sake irin haka,because idan kika samu matsala Nima matsalar ki tashafeni" Qasa tayi da idonta batare da tace komai ba, ahankali yasaki fuskarta sannan suka fice daga dakin. Nabiha tasaki wata nauyaiyar ajiyar zuciya tace"irin wannan soyaiya haka Mawahib?" Cikin mamaki Mawahib tace"soyaiya kuma?" Nabiha tace"emanah, gashinan duk kin rikita Yaya Captain ko kunya ta baiji ba yake miki kiss" Mawahib ta girgiza kanta tayi shiru,tana tunani,har yanzu bazatace ga sahihin abinda take ji akan Yaya Captain ba,tasan cewa de bata tsanar sa. Nabiha tadawo kusa da ita ta zauna sannan tafara bata fruit din dasukazo dashi. Kusan awarsu biyu itada Nabiha adakin, doctor yazo ya tambaye ta ko akwai abinda takeji tace masa babu damuwa, bayan yafita suma suka futo daga dakin,ta kalli Nabiha tace"rakani muje nadauko kayan Momy dana shanya dazu" Nabiha tace"muje dama nagaji da zaman" kayan sukaje ta dauko ta ninke su, sannan suka juyo,zasu koma dakin Hajiya kilishi sukaga wata mata ankawo ta tana murqususu cikin naquda,jikin Nabiha yayi sanyi tace"nashiga uku Mawahib wannan haihuwa zatayi" Mawahib tace"tabdi lalle abun na gaske ne,kingafa daqyar take tafiya baiwar Allah,wannan wahala ahaka matar abokin Yaya Captain take cewa zan haifi yanbiyu? bazan iyaba" Nabiha tace"aikuwa tunda mijinki yanbiyu ne ko baki haifa yanzu ba, agaba saikin haifa" Murmushi Mawahib tayi tace"kema haka ai" Daga nan suka shiga daki,kamar dazun har yanzu duka mazan gidan nasu suna cikin dakin,harda Mamy da mama Sadiya,Ashraf da Aryan suna gefen Hajiya kilishi. Duk yanda Hajiya kilishi ta addabi duka 'yan gidan Alqali da tashin hankali,hakan baisa sun gujeta ba,tun safe gaba dayansu suna cikin dakin sun sakata agaba kamar idan suka matsa zata koma halin jinyar. Suna ganin Mawahib sukayi mata sannu ta amsa,Alqali ya kalleta cikin kulawa yace"bakyajin komai de ko?" Cikin ladabi tace"banajin komai Daddy" Kafin yasake magana ta kalli Hajiya kilishi dake zaune akan gadon tanashan Yagourt,amma takasa dago kanta ta kalli kowa, cikin ladabi ta qarasa tabawa Mama Sadiya kayan Hajiya kilishi,sannan ta zauna kusada Mamy tadaga kanta tasake kallon Hajiya kilishi sannan tace"sannu da jiki Momy" Cikin sanyin jiki Hajiya kilishi tace"Sannu Mawahib,Allah yayi miki Albarka"(😳🙆🏻‍♀️😲) Cikin sauri mutanan dakin suka juya suna kallon Hajiya kilishi,babu wanda furucin Hajiya kilishi bai bawa mamaki ba,Captain Aryan yaji wani irin dadi aransa,Ashraf kuwa murmushi yayi. Mamakin su bai gama yankewa ba sukaji Hajiya kilishi tana cewa Mamy "Maryam nagode,Allah yasaka da Alkhairi" Mamy tayi murmushi tace"babu komai Yaya,Allah yabaki lafiya" Sun dade adakin sannan sukai shirin tafiya,Captain Aryan yadauki wayarsa yaturo wa Mawahib saqo,wayarta tana hannunta taga shigowar saqo,dubawa tayi taga yaturo mata "idan zasu tafi karki bisu kijirani" wani irin taqaici taji aranta, saboda taso tabi Mamy su tafi gida, kamar tafashe da kuka ta jefa wayar acikin jaka ko replay batayi masaba. Bayan su Mamy sun tafi itada Nabiha ne suke dan zance qasa qasa suna kallon wayar Nabiha, idan Nabiha zata mata gulma saita rubuta mata ta wayar ita kuma saita karanta. Basu bar asbitin ba sai dare,Nabiha tabi Ashraf, shikuma Captain Aryan yadauki Mawahib suka yiwa mama Sadiya da kilishi sallama suka tafi. Yana driving yana juyowa yana kallonta,ita kuwa luf tayi acikin kujera saboda tagaji sosai,abakin titi ya Parker motar yatsaya, sannan ya juyo ya kalleta,yaruqo hannunta yace"meyake faruwa?" Cikin yanayin gajiya tace"inajin gajiya ajikina ne kawai" Cikin kulawa yace"kinajin jiri ne?" Girgiza kanta tayi tadan lumshe idonta tace"kawai gajiya nakeji" Fuskarsa cikeda damuwa yarage sautin muryarsa yace"meyasa kika bada Jininki?" Cikin sanyin murya tace"tana buqatar jinin itama,ka manta kaima ka temaki mahaifina?" Idonsa ya lumshe sannan yabude yafara kallonta, yarasa wanne matsayi zai bata acikin zuciyarsa, abinda yasani shine tariga tazama komai nasa,baisan menene acikin Zuciyarta game dashi ba,baisan meyasa tabawa Momynsa jini ba, soyaiyar datake masa ne kokuma tsabar tausayi ne? Hannunta yasake riqewa sannan ya kalli cikin idonta yace"MAWAHIB...." Wannan ne Karon farko da taji ya kira Sunan Mawahib a bakinsa bayan Ruqayya, cikin gajiya ta sake lumshe idonta, sannan ta kalleshi da idonta me yanayin bacci, tace"um.." Lokaci daya idonsa ya kada yayi jajir kamar zaiyi kuka sannan yace"meyasa bakya sona? mekikeso nayi miki kisoni?" Idonta ta lumshe cikin damuwa, sannan ta bude tace"Yaya Captain inajin bacci kuma nagaji" Cikin sauri yagyada kansa, sannan yace"I'm sorry,bari muje gida,zakiyi baccin yanzu kinji?" Kanta ta daga masa, sannan yasaki hannunta yaja motar suka bar wajan, kafin su qarasa gida saida yatsaya yasai mata kaji gasassu,sannan yasake tsayawa awani store yabude boot din motar aka saka masa katan katan din maltina ta gwangwani, sannan yakoma motar yaja suka tafi gida. Da taimakon maigadi aka shigar mata da kayan daya siyo mata part din Mamy,Mamy tana zaune sai ganinsu tayi ita dashi,gakuma megadi yana shigowa da kaya. Mawahib zubewa tayi a kujera, shikuma ya tsugunna tareda sunkuyar da kansa qasa cikin girmamawa yace"Anty Ma-my barka da hutawa" "yawwa Captain,ita kuma wannan menene yake damunta?" ta qarasa maganar tana kallon Mawahib. Kallon Mawahib din yayi yace"tace tanajin gajiya ne,kuma tanajin bacci " Mamy ta bude idon Mawahib ta kalla sannan tace"jinin data bayar ne,kuma batasha maltina dayawa ba,kamata yayi tasha sosai, tashi kije fridge akwai sauran maltina me sanyi saikisha kuje ki kwanta zuwa safe zakiji ki normal" Kansa ya sosa kadan sannan yace"Anty Ma-my, tayi baccin tare dake" Mamy tace"to shikkenan rakata dakinta,bari na kawo mata Maltinar" Bai tashi ba saida yaga Mamy tanufi fridge dinta tabasu baya,kawai yasaka hannu ya dauketa cak, yanufi dakinta da'ita,kwantar da'ita yayi akan gadon sannan yashafa kanta,yace"sannu" Daga masa kanta tayi,Mamy taturo dakin tashigo takawo mata maltina, sannan ta fice tabarsu,yana ganin fitar ta yatashi yadawo gadon yadauke ta ya d'orata akan cinyarsa, sannan ya kwantar da kanta akan qirjinsa yabude maltina yafara bata, saida ta shanye daya, sannan yasake bude wata, taqara sha kad'an, sannan tafara girgiza kanta tace"naqoshi" Cikin sigar rada yace"dan qara wannan dan kadan" Sake sha tayi,ta kawar da kanta,yasake bata maltinar cikin lallashi yace"sha wannan to dagashi shikkenan" Kukan shagwaba tasakar masa,ya lumshe idonsa yabude,sannan cikin dabara yasake bata tasha, ya ajiye sauran tareda kwantar da kanta a qirjinsa, yana shafa kanta,sun dad'e ahaka har bacci ya dauketa me nauyi, saida ya tabbatar tayi bacci sannan ya kwantar da'ita, ya sunkuya yadora bakinsa akan lips dinta,yayi kissing dinta, sannan ya futo daga dakin. Yana futowa yaga falon babu kowa,cikin sauri yafice yanufi dakinsa yayi wanka sannan ya rungume fillo a qirjinsa ya lumshe idonsa yana tunanin ta har bacci ya dauke shi. Washegari takama Monday,tun asuba Captain yake faman kiran wayarta yanajin yanayin jikin nata, ta kuma tabbatar masa ta warke ras. Saida gari ya waye sannan yashiga part din,tare sukai breakfast shida ita da Mamy da Abba,tanajin yanda yake ta6o mata qafarta da tasa qafar ta qasan table din dasuke zaune, amma saita maze bata nuna komai ba, saide tadan kalleshi kad'an sannan ta kawar da kanta. Abba yatashi zai tafi aiki, Mamy ma tayi shirin tafiya asbiti tadauki abincin su Hajiya kilishi, Abba zai fara kaita asbitin takai musu abincin, sannan ya rakata wajan nata aikin sannan shima yawuce nasa. Su kadai suka bari afalon,hakan ba qaramin dadi yayiwa Captain ba,domin kuwa suna tafiya yasaka ta a jikinsa, ahaka suka wuni,banda shagwa6ata babu abinda yakeyi,bai tafi asbiti ba sai yamma dede lokacin da Mamy ta dawo kenan, bai yarda yabarta ita kadai a gidan ba,acan asbitin ya tarar da Ashraf,basu dawo gida ba sai dare kamar kullum. haka rayuwar gidan Alqali ta kasance har tsawon sati daya,tsawon wannan lokacin Mama Sadiya ce me zama da'ita,Mamy kuma kullum zata kai musu abinci sannan tawuce aiki,zuwa wannan lokacin jikinta ya warware sosai,saide rama irinta rashin lafiya kafin jikinta yagama komawa daidai. Azaman Aryan da Mawahib kuwa babu abinda ya sauya,bai ta6a tunanin neman haqqinsa awajan taba,koda yaushe kokarin ganin ya kyautata mata yake,kuma bai ta6a jin haushinta dan taqi baiyana masa menene acikin zuciyar taba. yau aka sallamo Hajiya kilishi,mutane sai sintirin zuwa gidan suke ana yimata yajiki,gaba daya sanadin wannan rashin lafiya yasa Hajiya kilishi ta sauya kamar wanda aka sauya ta,tazama shiru shiru kamar ba'ita ba,cikin ranta kuwa tsantsar nadama ce take damunta,dama ance baka gane masoyinka sai kana halin jinya,tunda Maryam tazo da yarinyar nan cikin gidan Alqali shedan yake kitsa mata abubuwa marasa kyau cikin ranta, bayan babu abinda yarinyar ta tsare mata,ubangiji ya nuna mata Ishara akan danta Aryan mafi soyuwa aranta,Allah yahada aurensa da Mawahib, duk da haka bata saduda ba,ajiyar zuciya ta sauke bayan tagama tunani ta Kalli Ashraf da Aryan dasuka sakata agaba Ashraf yana zaune aqasan kujera yana game awayarsa Aryan kuma yana zaune agefenta akan kujera yayi shiru. Kallonsa tayi tace"Baba na kamar kanada damuwa, meyake faruwa?" kallonta yayi yana shakkar yimata maganar abinda yake ransa, cikin sanyin jiki yace"Momy dama inaso zanyima yarinyar nan lefe ne" Cikin sauri tace"Mawahib?" Kansa ya sosa yace"eh Momy" Tace"kuyi musu mana,nima akwai wasu kayan awajena,idan kun gama sai ahadasu gaba daya" Ashraf yadaga kansa ya kallesu yace"Momy to guda nawa zamu siyo?" Hajiya kilishi tace"toku bawa Maryam kudin saita hado muku komai mana"🤭 Ashraf yace"shikkenan ma, yafi sauqi" Captain Aryan ya6ata fuskarsa cikin shagwa6a yace"Momy...gaskiya nide gara kihada min da Kanki" Hajiya kilishi tayi murmushi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,au bazaka bawa surukar ka tahada muku gaba daya ba? yanzu Baba na inani Ina shiga kasuwa? ita Maryam din de itace yar zamani duk zata sako muku abinda yadace, amma tunda baka so toka bawa Sadiya saita hadoma" Cikin sauri yace"eh zan bata" Murmushi tayi tajashi jikinta tana shafa kansa. Adede lokacin Alqali yashigo falon, yana ganinsu yayi murmushi yakalli Hajiya kilishi yace"Kilishi maman biyu,kede kawai burinki kisa yaranki a gabanki kina lailayasu kamar jarirai" Ashraf yayi murmushi yace"Daddy Aryan takewa haka,shine yaro" Cikin sauri Captain Aryan yadago kansa daga kafadar Hajiya kilishi yace"waye yaron? Momy kidena bari yana cemin yaro" Hajiya kilishi tace"yazan masa ne Aryan? kutashi muje kurakani part din Maryam" Alqali yayi murmushi yace"lafiya deko?" Cikin sanyin jiki tace"ai harda kai zamuje Alhaji,zan sake bawa Mawahib haquri,tunda gashi an sallamoni nadawo gida" Gaba dayansu su ukun kallonta sukai cikeda jin dadi,Ashraf yayi wulli da wayar hannunsa yace"muje Momy" Cikin jin dadi suka nufi part din Mamy gaba dayansu. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Mamy ta kalli Mawahib tace"tunda Yaya kilishi ta warke nasan kun kusa tafiya ko?" Mawahib da hankalinta yake kan waya tace"wallahi bansani ba Mamy,banyi maganar dashi ba" Mamy tace"to kafin kusa ranar tafiya saiki fara zuwa wajan gyaran jiki,nayi magana da Hajiya Balaraba,saiki fada masa zaki fara zuwa gobe,kona kwana biyu ne a miki kafin kutafi " Tace"to Mamy zan fada masa" "magungunan dasuke wajanki wanda na aiko miki sun qare ko?" Mawahib ta kalleta,sai yanzu nema da Mamy tayi mata maganar magani sannan ta tuna da maganin da Matar Captain Habib tabata,yana cikin Jakarta,ta kalli Mamy tace"duka na shanye,turare ne bai qareba,yana can" Mamy tace"to turaren babu qamshi ne? ko bayaso kina amfani dashi?" Murmushi tayi tace"Yaya Captain din? besan ma Ina amfani dashi ba" Mamy ta jinjina kanta daga haka bata qara magana ba,saide tunanin ta yagama bata Mawahib da Captain babu abinda yata6a hadasu, idan kuwa sunyi mu'amular aure toda kanta zata nemi maganin saboda yanada kyau sosai,idan taga Aryan din yana rawar jiki akanta lokacin da zata nemi wani ma babu wanda yasani. Adede lokacin su Hajiya kilishi suka shigo falon,cikin farinciki Mamy ta kallesu tana tashi tsaye tace"sannunku da zuwa,Yaya meyasa kika taso keda bakyajin dadi aida kinmin waya nata so" Hajiya kilishi tace"A a jiki ai yayi kyau Maryam,babu komai wallahi" Mamy ta kalli Mawahib tace"kawo musu ruwa" Sannan ta kalli Alqali cikin ladabi tace"Yaya Bissmillah" Zama yayi a kujerar, sukam su Ashraf tuni sun zauna,Mawahib takawo musu ruwan takoma zata dauko lemo Hajiya kilishi tace"Mawahib dawo ki zauna,Maryam kibarta ta dinga hutawa mana" Cikin sauri Mawahib ta kalli hajiya kilishi sannan ta nemi waje ta zauna, Mamy ta sunkuyar da kanta qasa tanata mamakin Hajiya kilishi. Hajiya kilishi tajuya ta kalli Mawahib tace"Mawahib wajanki nazo, zuwa nayi nasake yimiki godia akan taimakon dakika min a asbiti,haqiqa naga aya,kuma na dauki darasi,inaso ki yafemin duk abubuwan dasuka faru abaya, Sharrin shaidan ne,kiyi haquri kiyafemin kodan mijinki Aryan" gaba dayansu sai jikinsu yayi sanyi,Alqali yayi shiru yana sake godewa Allah acikin ransa, ashe yana raye zaiga irin wannan ranar, kafin yagama tunanin sa yaji Mawahib tace"babu komai Momy, nayafe miki" Hajiya kilishi tace"Allahu Akbar,haqiqa ni kilishi Naga ikon Allah,rayuwa kenan,Allah ya miki Albarka Mawahib" Ahankali Mawahib tace"Amin" Hajiya kilishi tajuya takalli Mamy tace"Maryam kiyi haquri,daga yau namiki alqawari insha Allahu bazaki sakejin wani tashin hankali awajena ba, abubuwan dasuka faruwa Dan Allah na roqeki ki manta dasu, ki daukeni amatsayin yayarki daga yau" Cikin farinciki Mamy tace"wallahi babu komai Yaya, yawuce, Allah yayafe mana baki daya" Cikin farinciki Hajiya kilishi tace"nagode Maryam" tajuya tasake kallon Mawahib da kanta yake qasa tace"Mawahib...? Allah yabaku Zaman lafiya " Cikin jin kunya Mawahib tatashi tawuce dakinta, Captain Aryan yayi murmushi yabita da kallo. Sun dan jima afalon,har Abba yadawo ya gansu,shima yazauna sukaci gaba da firarsu gwanin sha'awa, sannan Alqali ya rufe musu taro da Addu'ah suka tafi nasu part din. Da daddare suna zaune a dining itada Mamy bayan sungama cin dinner,tadauki wayarta tatura masa saqo "Yaya Captain inaso gobe zanje wajan gyaran jiki" Alokacin da saqon yashigo wayarsa yana wajan Mama Sadiya yana fada mata irin kayan lefen dayake so a hadowa Mawahib,saqon nata yaduba yagani yayi murmushi, sannan yayi mata replay yace"send me your account number" tura masa tayi sannan ta ajiye wayar,Mamy tafuto daga dakinta tabata magani a cup tace"ungo shanye kiban cup din" Ganin yanda Mamy ta tsareta yasa babu musu ta shanye maganin sannan tabata cup din. Alert ne yashigo na dubu dari cikin wayarta, mamaki ya kamata, ta nunawa Mamy alert din tace"Mamy nafada masa shine yaturo min wannan kudin" Mamy tace"har dubu dari? lalle Captain gyaran jiki yakeso dakyau" Mawahib taturo bakinta gaba tatashi tawuce dakinta cikeda shagwa6a, Mamy tayi murmushi takira Hajiya Balaraba tafada mata bayan gyaran jikin ayi mata hadin magunguna masu kyau hadin amare ta zaunar da'ita tasha komai agabanta, yanzu zatayi mata alert. Hajiya Balaraba tanajin zancen alert tasan Mamy ba wasa,cikin tabbaci tace"karki damu Hajiya Maryam,ai tunda kin kawo ta wajena kingama komai,inde nayi mata gyaran jikin nan ko mijin ta kasa ganeta zaiyi,sannan zanyi mata hadin nafi qarfin reni,ina tabbatar miki daqyar mijinta zai iya kallon wata yarinyar amatsayin mace,saina sata ta gigitashi banida sasssauci ta wannan fannin" Mamy tayi murmushi tace"to shikkenan saita zo,zakiji alert yanzu yanzun nan" Daga nan sukai sallama Mamy tawuce daki,tana jiran zuwan Abba Ashraf yakirata awaya yake fada mata maganar lefensa, suka tattauna abinda zasu tattauna sannan sukai sallama Kamar yanda Mamy ta tsara washegari tun sassafe Mawahib tabar gidan,tatafi gidan Hajiya Balaraba,bata dawo ba sai yamma lis,tun aranar yau din Mamy tafara ganin canji,farar fatar Mawahib din taqara yin fresh,kasancewar tana dadewa bata dawo da wuri ba, hakan yasa tana zuwa gida take kwanciyar ta tayi bacci,Mamy tana lura da shige da ficenta kokadan taqi bata damar da zata hadu da Captain,tafi son agama yimata gyaran jikinta tsaf,sannan ta tattara ta sukoma Abuja. kwananta biyar tana zuwa kuma yaune qarshe,tana dawowa tawuce part dinsu cikin kasala saboda kwana biyu wannan magungunan da ake bata yasa take yawan jin feeling ajikinta. Acikin kwana biyar dinnan su Mamy suka gama hada komai na lefe, apart dinsu Nabiha suke ajiye komai wajan Mama Sadiya. ****** Hajiya kilishi ta Kalli akwatunan dasuke gabanta guda ashirin,tace"wanne ne na Mawahib?" Captain Aryan ya sosa kansa yace"wannan ne guda takwas,na Ashraf kuma guda shabiyu" Cikin sauri ta kalleshi tace"guda takwas ai yayi kad'an,guda shabiyu zaka mata,kaikuma Ashraf kasake tura mata wani kudin asiyo da kayan baby,Babanah kaikuma kafitar da kudi akaro mata wasu akwatunan guda hudu, sai aqara musu da kayan wajena" Cikin tsananin mamaki Captain Aryan ya kalleta,yayi tunanin zatayi fada shiyasa lokacin da mama Sadiya tace asiyo shabiyu yace a a saboda kar Momy tayi fada asiyo guda takwas, amma abun mamakin gashi itada kanta take cewa yayi kad'an, lalle Momy ta sauya. Sumar kansa ya shafa yace"to Momy" Kafin tasake magana wayarsa tayi qara,ganin Captain Habib ne mekiran yasa yadauka cikin sauri, bayan sun gaisa Captain Habib yace"yaushe zaka shigo ne? akwai damuwa fa" Captain Aryan yace"meyake faruwa? Ina tunanin mafa hutu zan dauka gaskiya" Captain Habib yace"saboda kayi amarci dakyau kenan" Saida yasaci kallon Momy kilishi yaga hankalinta baya kansa sannan yace"eh wallahi" Captain Habib yayi murmushi yace"hakan yanada kyau,amma yanzu de ya kamata shirya kataho anyi mana rashi wallahi,dazu muka samu labari ankashe Captain Shu'aibu awajan yaqin da'aka turashi" Cikin sauri Captain Aryan yatashi tsaye yace"what...? innalillahi Captain Shu'aibu yarasu? ninefa nayi masa bayanin yanda kan dajin yake,lokacin ya biyoni har gida....kai Hasbunallahu wani'imal wakeel...." yafadi haka tareda dafe kansa da hannunsa(🤦🏻‍♂️) Hajiya kilishi ta kalleshi da sauri tace"wayene yarasu?" "abokin aiki nane Momy" Ashraf yace"Allah yaji qansa da Rahma" Jikin Momy kilishi yayi sanyi, lokaci daya idonta yacika da hawaye, tace"ni Babana wannan aikin naku tsoro yake bani,a dinga kashe rai kamar ansamu kiyashi" Ta qarasa maganar hawayen yana zubowa. Kallonta yayi cikin kwantar da hankali yace"Momy duk wanda kikaga yarasu dama lokacin sane yayi,kowanne bawa baya wuce qaddarar sa,Allah yaji qansa da Rahma" Gaba daya suka amsa da "Amin" Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Washegari Ashraf yasake yiwa Mamy da Mama Sadiya magana akan maganar qarin lefen,saboda Captain Aryan yana busy,waya yake tayi da ma'aikatan su saboda rashin da'aka musu,sai Ashraf ne yaci gaba da kula da batun kayan lefen saboda shi Captain Aryan yana tunanin yakamata ace sun koma Abuja. Haka su Mamy da Mama Sadiya suka sake fita suka karo kayan kamar yanda suka fada. Washegari yan'uwan Hajiya kilishi sukazo gidan kowa yaga kayan lefe sai yabawa yake,akwatunan Mawahib guda shabiyu, saikuma qarin akwatuna guda uku irin wanda Hajiya kilishi take siya take 6oyewa saboda hada lefen 'yanbiyun ta. Bayan sungama ganin kayan aka kaiwa Nabiha nata part dinsu, suka sake daukan na Mawahib ma suka kai, alokacin tana dakinta tana jiyo hayaniyar mutane afalon amma bata futo ba,saida yamma ta futo har lokacin akwatunan suna jere afalon Mamy. lemo ne a hannunta tanasha tana danna wayarta, Mamy ta kalleta tace"Mawahib ga kayan lefenki fa Captain yayi kokari sosai" Ba tareda ta kalli kayanba tace"to Mamy" tanemi waje ta zauna tafara kallo, Mamy tana jira taga Mawahib ta bude kaya taga ko ajikinta harkar gabanta ma take, inda akwatunan suke ma bata kalla ba. Ta girgiza kanta cikin ranta tace"Allah yarufa asiri" Da daddare suna dakinsu shida Ashraf,abinci suka gama ci,Aryan yatashi yadauko magungunan sa sannan yabude yafara Sha, Ashraf ya dauki kwalin maganin ya karanta sannan ya kwashe da dariya. Captain Aryan ya kalleshi yace"miye haka? menene abun dariya?" Ashraf yace"miye na wani daure min fuska? ganinayi kadage da shan magani, Naga alama Sokake su Daddy saide suga Mawahib da ciki" Captain Aryan yagama shan maganin yace"maganin ma yaqare bari nakira doctor naji" Ashraf yaci gaba da ganin magungunan yana karanta wa,Captain yakira doctor yasaka wayar a speaker,bayan sun gaisa yace"doctor naje gida ganin family na, but drugs dina sun qare, zan'iya neman irinsu anan ne inci gaba da sha kokuma wani daban zaka rubuta ka turomin kota message ne saina nema infara Sha?" Likita yace"masha Allah,gaskiya kayi kokari sosai haka akeso,to yanzu Yaya kake ganin yanayin sperm dinka? yana nan yanda yake lokacin daka samu matsalar kokuma yakoma asalin farko yanda yake kafin kasamu harbin,?" Ashraf ya Kalli Captain Aryan yanaso yaji amsar dazai Bawa likitan ,Captain Aryan yace"kamarya doctor?" Doctor yayi murmushi yace"Ina nufin sperm din naka Yaya kaga yanayin fitar sa? yanada kauri ne kokuma har yanzu wani babu banbanci?" Kallon juna sukai shida Ashraf,har likitan yaji shirun yayi yawa yace"hello" Ashraf ya zunguri Captain Aryan alamun yayi magana, cikin kame kame Captain Aryan yace"doctor nifa... ni....maganar gaskiya" Jin yana kame kame yasa doctor yace"Ina nufin Yaya kaga yanayinsa? da kauri ko babu kauri? idan kaduba kaga yanda yake, saika fadamin sai insan akan maganin daya kamata nasake doraka" Cikin rashin sanin abin fada yace"doctor tayaya kenan?" Likita yayi murmushi yace" Ina nufin ta hanyar mafarki idan ka farka zaka gani,kokuma ta hanyar sex, but Captain I think you're not single right?" Cikin sanyin jiki yace"yes" Doctor yace"idan kagani saimu yi waya" Qit likita yakashe wayarsa. Captain Aryan yayi shiru yana kallon Ashraf,Ashraf yace"toni sai kallo na kake,matarka zaka kalla bani ba,yanzu tsawon lokacin nan Aryan haka kuka zauna? ko kanada matsalar haihuwa ai kanada lafiyar yin sex,ya za'ai ka zuba wa yarinya ido kana kallonta,inda ace daga lokacin bikinku kafara shan magani to zuwa yanzu yaci ace kayi mata ciki"(🙈) Idonsa ya lumshe sannan yabude cikin damuwa yace"Ashraf bazaka gane ba,har yanzu Mawahib fa bata sona,nina rasa yanda zanyi da sonta, kullum qaunar ta sake qaruwa take acikin raina, nafison ace taji aranta cewa tana sona,sai inyi abinda yafi sex ma" Ashraf yayi ajiyar zuciya cikin damuwa Shima yace"Allah yarufa asiri,toka zuba mata ido kana kallonta tayaya zata Soka? idan ba zakayi sex da'itaba kasabar mata da romance sosai yanda ko baka nemetaba inde tasaba ita da kanta zata kawo kanta,amma inaso kasani muddin baka cire wannan ra'ayin naka nawai saita Soka sannan zakayi sex ba to akwai matsala,idan ba haihuwa kayi Momy taga yayanku ba, bana tunanin komai zai wuce a gidannan, saboda haka kayi abinka kawai,saika kirashi kafada masa" Captain yaja wani irin dogon numfashi, kafin yayi magana Colonel dinsu yakirashi, cikin mamaki ya kalli Agogo yaga goma shadaya saura,daukar wayar yayi cikin girmamawa, daga can bangaren colonel yace"Captain Aryan anbani umarni daga sama cewa gobe dasafe zaka tafi dajin da aka tura Captain Shu'aibu Kaci gaba da jagorantar sauran sojoji" Gabansa ne yafadi,bawai tsoron dajin yakeba,tsoron rabuwa da Mawahib kawai yake,cikin girmamawa yace"sir da Ina shirin daukar hutu ne,saboda bana Samun damar zama da iyal...." Kafin ya qarasa cewa iyali na, colonel yace"umarni ne daga sama Captain,kai kadai ake tunanin zakaji da komai" Cikin girmamawa yace"angama Sir" Sannan yakashe wayar, cikin sanyin jiki ya Kalli Ashraf yace"akwai matsala,anturani wajan yaqin da Captain Shu'aibu yarasu,zanci gaba da jagorantar sauran Sojojin,Ina tunanin mutuwar Captain Shu'aibu, gani nake nine nayi silar mutuwar sa saboda banyi masa bayanin wajan yanda ya kamata ba,Kishi ya rufe min ido bangama yimasa bayani ba na sallame shi saboda yazo harcikin gidana yana kallon Mawahib, nikuma bazan Iya Jura ba, yanzu dole gobe zan wuce da sassafe,zamu tunkare su komu kashe, kokuma Nima a kashe ni " Jikin Ashraf yayi sanyi yace"wai wajan da aka kashe abokin aikinka shine suka sake tura ka wajan? Ya za'ai kanaji wani yamutu kaikuma zaka tafi?" Captain Aryan yace"wannan shine aikin soja Ash...,bazan Iya qin bin umarnin suba" Cikin tsananin tashin hankali Ashraf tace"babu inda zakaje,tayaya wani yamutu,sannan su rasa wazasu tura saikai? idan kamutu fa mu sukayi wa asara basu ba, babu inda zakaje" Captain Aryan Yariqe hannun Ashraf yace "Ash....,mutuwa fa dole ce muna so bamaso,kayimin Addu'ah mana,idan banje ba sauran Sojojin dasuke dajin su basuda iyaye da yan'uwa ne?, dan Allah na roqeka kayi shiru karka fadawa kowa wajan yaqi aka turani musanman Momy,gida ya nutsu yanzu, kowa Yana cikin farinciki, idan Momy taji cewa inda wani yamutu Nima aka turani bazata kwantar da hankalin taba,kuma kaga bata dade da tashi daga jinya ba, kayimin alqawari zamu bar maganar nan mu biyu,Kaci gaba dayi min Addu'ah" Hawaye ne suka zubo daga idon Ashraf,jikinsa yayi sanyi kalau, tun suna qasar waje yake yaqi da wannan qudurin na Aryan akan yaja hankalinsa yadena son aikin soja, amma Aryan yaqi, saboda ajininsa yake son aikin,cikin sauri yaja Aryan ya rungume shi,shima Aryan din qwalla ya goge daga idonsa, Ashraf yadago kansa ya kalleshi yace"kaje kadauko matarka kasauke haqqin dayake kanka,karka tafi da tunanin wannan abun aranka" Hawaye yashare kamar ba Captain ba yace"Ash...bazan iyaba" Shima Ashraf hawayen yashare yace"zaka Iya" Yana fadar haka yafice daga dakin yana kuka,ya Kalli part din Momy da Mamy da Mama Sadiya, suna cikin farinciki gida yayi dadi yanzu yaushe zai fara fada musu antura Aryan yaqi? dole zai riqe alqawarin dan'uwan sa. Ficewa yayi yabar gidan yatafi gidansa. Yadade yana hawaye adaki shi kadai,gabansa ne yake faduwa gani yake kamar yarabu da Ashraf kenan har abada,bai ta6a jin shakka ko tsoron tunkaran dajin da zasuyi yaqi ba sai yau,takarda yadauka yayiwa Mawahib dogon rubutu ajiki, sannan yabude bedside drower yasaka takardar aciki, yashare hawayen idonsa yadauki wayarsa yakirata,alokacin harta fara bacci,cikin bacci ta dauki wayar taga qarfe daya da kwata, mamaki ya kamata lafiya Yaya Captain bai kwanta ba? Cikin sauri ta dauki wayar,cikin wata irin murya yace"i want to see you please" Yanda taji muryarsa hakan ya tabbatar mata ba kalau yake ba,kashe wayar tayi, sannan tafuto daga dakinta tana Sanye cikin yar qaramar rigar bacci Iya gwiwar ta, sai zani data daura akan rigar, Ficewa tayi daga part din tatafi dakinsu,tana zuwa tatura dakin tashiga, ta ganshi a zaune abakin gado yakama kansa yariqe da hannu bibbiyu,dakin ta rufe sannan ta qaraso kusa dashi ta zauna jikinta a sanyaye tace"yaya Captain..." Dago idonsa yayi ya kalleta, cikin sauri ta zabura ganin hawaye a'idonsa,kafin tayi magana yariqe hannunta duka biyun yace" MAWAHIB....i need you" Gabanta ne yayi wata irin faduwa, kanta ya Sara, lokaci daya kanta yafara ciwo tafara girgiza masa kanta cikin tsoro tace"acikin gidannan? kayi haquri Yaya Captain Dan girman...." Cikin sauri yaruqo ta tareda dora hannunsa akan lips dinta yace"shiiit...,ya'isa,ahankali zanyi miki, bazan miki da zafi ba kinji? ki nutsu kidena tsoro" Mawahib tatuno lokacin dataga abun a zahiri,gabanta yasake faduwa tasake girgiza masa kanta,tacire hannunsa daya riqe mata hannaye tace"kayi haquri,ni banason wannan abun,tsoro yake bani,kayi haquri pl...." Kafin ta qarasa cewa please, ya fuzgota tafada jikinsa, sannan yariqe kanta da hannunsa daya, yadora bakinsa cikin nata yafara nuna mata yanda yake cikeda zallar sha'awar ta, bakinta take kokarin qwacewa amma yahanata wannan damar,tsotsar lips dinta yake kamar yasamu yasamu sweet, kuka tasaki tafara tura shi, ahankali yacire bakinsa daga cikin nata cikin muryarsa data gama cika da buqata yace"please, karki hanani, zan mutu" Yana fadin haka yasaka hannayen sa ya yaga rigar jikinta tundaga sama har qasa, yana ganin nashanunta yakai musu wata irin damqa yana matsawa,sannan yadora bakinsa akan guda daya yafara tsotsa da qarfi,yayinda hannunsa yake murza dayan,zafin da taji ne yasa tafara dukansa amma Sojan nata ko a jikinsa,runtse idonta tayi tanajin kamar zai tsinke mata kan nono,cikin kuka tace"Yaya Captain zaka kasheni,zaka cire min abuna,kayi haquri dan Allah,natuba.." Jin abinda take fada yake sama sama saboda yanda yadauki caji, bai tabajin dadi irinna yau ba,ahankali yazare bakinsa daga kan dayan yamaida kan dayan nashanun nata yafara sha, sannan yatura hannunsa cikin pant dinta yafara shafa mata wajan, yanda yaji wajan yamasa irin yanda yakeso hakan yasa yafara wani irin hawayen dadi,gaba daya yagama ficewa daga hayyacinsa cikin sauri yacire pant din nata ya wullar dashi aqasan dakin, sannan ya wara qafafunta yafara neman hanyarsa. Tun kafin yashiga wajan,yadena hawaye, yadawo kuka wiwi,jikinsa banda rawa babu abinda yake,yakasa cewa komai kawai kuka yake yana kokarin shigar ta,amma kwata kwata babu hanya, kasancewar ta budurwa Kuma tasake Samun gyara wajan Hajiya Balaraba, hakan yasa wajan yasake rufewa,Mawahib ta girgiza kanta hawaye yana zuba akan fillon datake kai,yanda yake kokarin shiga yakasa hakan yasa taji gaba daya ya gurje mata wajan, banda radadi babu abinda takeji,jitake kamar ansaka mata barkwano awajan. Tana jinsa yana kokarin shigar ta daqyar taji wani irin qarfi yazo mata, ta yunqura tatashi tafara dukansa zata tureshi daga kanta,da hannu daya yasa yariqe duka hannayen ta biyu, sannan yadora bakinsa cikin nata yahanata kukan, yasake bude qafarta yadanna yashiga daqyar, a zabar da taji ne yasa batasan lokacin data saki ihu ba ta qwalla qara tace"Mamy,!!!" Sanadin ihun nata yasa gaba daya gidan saida ya amsa. Hajiya kilishi da part dinta yake kusa da dakin su Aryan din, ta zabura tatashi zaune,tana salati, tajuya ta kalli Alqali dayake bacci tafara tashinsa tace"Alhaji, tashi Ina tunanin yan fashi sun shigo mana gida"(😂🙆🏻‍♀️) Cikin sauri sauri yatashi yace"subhanallahi bani rigata" Acan part din su Mamy kuwa Mamy tanajin wannan kiran tatashi tafuto daga dakin Abba tawuce dakin Mawahib,tana shiga dakin taga wayam babu Mawahib, cikin sauri ta nufi qofa, Abba da yaji futowar ta shima ya biyo bayanta yace"Ina zakije?" Acan dakin Captain kuwa,wani irin sambatu yafara shi kansa baisan a'ina yakeba,hankalinsa ya gushe, tunaninsa ya 6ace,yana cikin wata irin duniya wadda baya fatan ace yadawo tamu duniyar,gaba daya yafita daga hayyacinsa, kukan datake tana tureshi shine yaqara masa qaimi tun yanayin abu a nutse yadawo yanayi cikin sauri harda dukan katifa, ,Mawahib dataji kamar anqara zigashi hakan yasa tasake sakin ihun kuka akaro na biyu tana fadin"nashiga uku na,Yaya Captain zan mutu,kayi haquri,Mamy zai kasheni" Cikin kuka dakuma fitar hayyaci yake tambayar ta "inyi haquri?, inyi haquri?" Kuka yake yana maimaita Kalmar inyi haquri kwata kwata bayajin ta. Mamy datake tsaye bakin kofar falo tana jiyo magangun Mawahib gabanta yafadi,cikin sauri ta kalli Abba tace"Alhaji Mawahib cefa" Abba yakama kafadarta yariqe yace"tana tareda mijinta,Ina zakije? kokin manta nima lokacin dakika so taramin mutane?" Cikin tausayi Mamy tace" Alhaji ita din yarinya ce" Cikin sauri Shima Abba yace"to ya zamuyi? kibar su suyi daren farkon su,kinzaunar da yarinya Koda yaushe kina yiwa danki tattali da tanadi Kuma yana yana kar6ar kyautar dakika masa duk kin shiga damuwa?" Hararar wasa tayi masa, sannan tajuya dakinta jikinta asanyaye. Alqali kuwa rigar sa a hannu yafuto da'ita, kilishi tanabin bayansa a tsorace,tana leqo kanta ahankali kamar za'a kamota, suna zuwa compound sukaji daga inda kukan yake,adede lokacin Captain Aryan yasaki wani irin ihun dadi yana sake kiran sunanta cikin fitar hayyaci. Lokaci daya Mawahib ta suma,bata sake sanin inda kanta yakeba. Alqali yajuya ya kalli kilishi yakasa cemata komai,itama bayansa tabiyo tana share hawaye,suna zuwa dakinsu Alqali yakoma gado ya kwanta, Hajiya kilishi tazauna agado tana kuka(🙆🏻‍♀️) Alqali ya kalleta yace"Kilishi kukan na menene ne?" Cikin kuka tace" Alhaji Ina ganin ikon Allah yau ni kilishi,Babana zai kashe musu 'ya" Alqali yace"to yanzu kukan dakike mezai hana?kidena kuka may be rashin sabo ne kawai,ahankali zata saba komai zai wuce" yafadi haka tareda kwanciya. Hajiya kilishi kuwa kasa bacci tayi, a zaune take daram tana tunanin wannan abu,wannan yawuce ace rashin sabo,qarfi kawai yake nunawa yarinyar nan. Saida ya dauki lokaci madedeci bayan Sumanta, sannan yasamu yayi satisfied,duk wani abu daya dade yana tarawa yafitar dashi, yawan mafarki dayake abaya saboda wannan abun Shima yasamu yabiya buqatar sa,yawan kallonta dayake a Abuja da yanda take tunzurashi da zafafan shigar ta Shima yamaida kwadayinsa,yasaka hannu ya rungume ta tsam a jikinsa. saida yagama maida numfashi sannan yasakar mata kiss yace"i luv you so much,Allah yayi miki Albarka" Jin shiru bata Motsi hakan yasa yatashi cikin sauri yafara jijjigata, yata6a fuskarta yaji shiru, cikin sauri yadauketa yayi toilet da'ita, ruwan dumi ya kunna,yasaka ta aciki,ruwan bashida zafin kirki amma kasancewar shi bayason zafi hakan yasa yaji ruwan yamasa zafi sosai,tanajin ta acikin ruwan tafarka tareda sakin kukan azaba,sosai take kuka duk lallashi dayake mata bata saurare Shiba, saida yamata wanka Shima yayi, sannan yadaukota suka dawo dakin,zanin gadon yayi kaca-kaca da jini hakan yasa yacire shi yasaka wani, sannan ya kwantar da'ita, yasake gyara gadon, yadauko rigarsa yasaka mata, sannan shima yasaka jallabiya, yakawo hannu zai ta6ata cikin 6acin rai tace"karka ta6ani,mugu kawai" Idonsa ya runtse,sannan yabude ya kalleta yaga gaba daya jikinta karkarwa yake,tsoro ya bayyana qarara a'idon ta,gashi idon nata ya kumbura yayi luhu-luhu saboda kuka,sai ajiyar zuciya take tana goge hawaye,ta zame daqyar ta kwanta a gadon tana runtse idonta cikeda azaba. Qafafunsa yazuba aqasa yayi kneel down sannan yace"kiyi haquri,nasan nayi miki laifi babba,amma inaso kisani bada san raina hakan yafaru ba,dole ce tasa,na tabbatar agaba zaki gane hakan,a yanda na tsara shine bazan ta6a yimiki komai ba harsai lokacin dakika furta min cewa kina sona,bansan Yaya zanyi da soyaiyar kiba,Ina sonki, amma ke nasan cewa bakya sona,ban damu da hakanba saboda ni Ina qaunar ki,nabar hakan amatsayin jarabawa da ubangijina yakemin akanki saboda abinda yafaru abaya,azaman danayi tare dake bansan mekika aikata min ba, abinda nasani shine kin koyamin yanda zan soki fiye da yanda zanso kaina, dukkan abinda nake buri, da dukkan abinda nake fata, da dukkan abinda nake buqata shine na kasance atare dake,bansan Yaya zan misalta miki farincikin danake jiba aduk lokacin dana jiki ajikina, zanyi tafiya me nisa Mawahib, bansan yaushe zan dawo ba,bansaniba zan dawo dinma kokuma bazan dawo ba, amma inaso kisani Ina sonki,Koda yaushe kece acikin tunani na daga safiya har dare,kuma Ina Addu'ah Allah yasa ki kasance acikin tunani na har abada..." tunda yafara magana take kuka,inda ace hawaye suna Qarewa babu makawa yauda nata sunqare,tana jinsa ya sunkuya yayi kissing dinta a goshi adede lokacin aka fara Kiran sallar asuba. yadade bai dauke bakinsa daga goshinta ba,sannan yadago ya kalleta yace"duk abinda kike buqata karki tambayi kowa ki tambayi Ashraf...,koda bana raye ki kalleshi,kisa aranki kamar ni kike kallo,kiyafemin..." Yana fadin haka yasaka hannu yagoge hawayen idonsa, sannan yatashi cikin sauri tana ganinsa yacire jallabiyar jikinsa ya sauya kaya, sannan yafara kallonta yana tafiya da baya da baya yana kallonta haryaje bakin qofar dakin, sannan yakama handle din dakin yabude, yajuyo yasake kallonta, cikin sauri yafice daga dakin tareda rufowa, yana zuwa compound baiga kowa ba,amma yana zuwa get yaganshi a bude alamun su Daddy sun fita masallaci,fita yayi yakira wayar Ashraf suka hadu yazo ya dauke shi yakai shi airport,acan Airport din sukai sallar asuba shida Ashraf saide babu Wanda yake magana a cikinsu,kowa jikinsa asanyaye yake, wayarsa yadauka ya turawa Daddy da Momy kilishi saqo yawuce wajan aiki anyi masa kiran gaggawa, sannan ya turawa Mamy saqon yatafi yakoma bakin aiki, taje takula da Mawahib, tana buqatar taimako. ko minti ashirin basu qaraba, jirgin su yatashi, Ashraf baibar Airport dinba saida yaga tashin jirgin su, sannan yajuyo gida jikinsa a asanyaye. (Allah yakaika lafiya Captain 😭) (Allah yabaki lafiya Mawahib 😭😭) Mutara zuwa gobe🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/15, 10:44 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki. Mamy bata dauki wayarta ba saida ta'idar da sallah tayi azkar sannan tayiwa Mawahib Addu'ah, cikin sanyin jiki tatashi tafara ninke hijabin jikinta Zuciyarta fal da tunanin halin da Mawahib take ciki,wayarta ta dauka zata shiga kitchen tana duba wayar taga text din Captain,cikin sauri taduba time din daya turo taga tun kafin atada sallah a masallaci,tana gama karanta text din tazauna agado jagwab tafara Salati meyasa bata duba wayarta da wuri ba ga yarinyar ta can awani hali? Cikin sauri tatashi tafuto daga part din tanufi dakinsu Captain, abakin qofa sukaci karo itada Hajiya kilishi data kasa runtsawa, Hajiya kilishi tace"Maryam kema kinji ihun nata ne?" Cikin sanyin jiki Mamy ta 6oye damuwarta, saboda kar mutanan gidan suyi tunanin wani abu,tace"A a Yaya,Captain yamin text ne yace inzo indubata" Cikin tsananin mamaki Hajiya da bata kalli inda wayarta take bama bare taga saqon da Captain yaturo mata na sallama tace"kamarya kizo? to ina yatafi?" Mamy tace"anyi masa kiran gaggawa ne awajan aikin su" Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"zancen banza zancen wofi,ya za'ai yatafi yabar yarinya tana wannan ihun kukan?" Bata jira amsar Mamy ba tatura dakin suka shiga atare,tun kafin su qarasa gadon sukaci karo da wandonta daya cillar dashi qasa,ga rigarta daya yaga acan gefe kusa da bedsheet din daya cire,Mawahib tana ganin Mamy tasaki wani irin kuka. Hajiya kilishi kuwa tana ganin bedsheet din dayake qasa duk gashinan jini ya 6ata shi, ga idanun Mawahib sunyi jajir saboda kuka,saita dora hannunta akanta tasaki kuka, Mamy ta kalleta tace"haba Yaya kidena kuka mana" Cikin kuka Hajiya kilishi tace"dole nayi kuka Maryam,wannan rashin imanin har ina?" Mamy ta qarasa wajan Mawahib ta zauna ta rungume ta tace" ya'isa, yi shiru, kukan ya'isa haka" Cikin kuka tace"Mamy zan mutu," Wannan Kalmar da Mawahib tafada itace tasake sa Hajiya kilishi fashewa da kuka, sai jijjuya kai take cikeda tausayi, Mamy ta dagata zata kaita toilet,anan taga jallabiyar Captain dinma datake jininta itama jini ya6ata ta,cikin sauri Mamy ta runtse idonta, takama jallabiyar tacire,Hajiya kilishi tayi sauri tawuce toilet tahada mata ruwan zafi. Mamy Kuma takamata tace"tashi muje kishiga cikin ruwan zafi" Cikin hawaye tace"Mamy bazan Iya takawa ba" Hajiya kilishi ta qaraso da sauri suka kamata su biyun, suka kaita toilet, sannan Mamy ta sakata cikin ruwan zafi, tana shiga cikin ruwan tasaki wata qara zata tashi, saboda wanda Yaya Captain yasakata bekai wannan zafi ba, Mamy ta maidata ta koma tazauna, Hajiya kilishi ta goge hawayen idonta tace"duk yanda akai Aryan bai sakata acikin ruwan dumi yanda ya kamata ba saboda shi dama baya son ruwan zafi, gani zaiyi itama zafin zai mata yawa" Mamy tace"toya za'ai Yaya,ai sai haquri" Saida suka sauya mata ruwa sau uku,sannan suka kamota suka futo,Hajiya kilishi ce ta riqeta Mamy Kuma tasake gyara gadon sannan suka kwantar da'ita daga gefe,ahankali Mamy ta tsugunna ta bude qafafun Mawahib taduba wajan sannan ta miqe tsaye tace"dole sainayi mata dinki Yaya" Hajiya kilishi tace"dinki? innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, Ina ganin ikon Allah ni kilishi...." saita saki kuka. Mamy tace"Yaya kidena kukan nan kada mutanen gida suji" Cikin kuka tace"ji na nawa Kuma Maryam? yanda ya haiqewa yarinyar nan waye acikin gidan nan zaice baiji ihun kukan taba? Aryan baya hayyacinsa,inajin maganin maza yasha" Mamy tace"babu wani magani Yaya, tunda kikaga haka gardama ta masa,inda ta tsaya koda zataji ciwon bazai kai har hakaba,tayayane zata nunawa soja itama me qarfi ce?, bari inje daki in dawo" Mawahib tanajin yanda suke tattauna wa,hawaye ne kawai yake zuba daga idonta. cikin kuka Hajiya kilishi ma tafuto daga dakin tawuce part dinta, Mamy tabita da kallo kamar cewa akai Captain din yakashe Mawahib,ta girgiza kanta tatafi part dinta da sauri. Hajiya kilishi tana zuwa falonta tazauna a kujera tadafe kanta tana share hawaye tareda ajiyar zuciya. ****** Abba daya dawo daga masallaci yanzu, ya Kalli Mamy ganin tana hada wata allura yace"meyake faruwa ne?" Cikin damuwa tace"Alhaji yarinyar nan taji ciwo ne sosai,zanyi mata dinki" Cikin sauri yace"subhanallah...kode zamu tafi asbiti ne?" Tace"A a babu matsala zanyi mata komai, idan munje asbitin ma zasu dinga surutu ne suyi tunanin rape ne akayi mukuma muka 6oye" Cikin sanyin jiki yace"yanzu tana wanne hali?" ****** Alqali da Ashraf suka nufo part dinsu, Alqali yana tambayar Ashraf "meyake faruwa kazo gida haka sassafe kabar iyalinka?" Ashraf yace"naraka Aryan Airport ne" Alqali ya kalleshi yace"eh naga yaturo min saqo dazu,yatafi Abuja,Allah yakaishi lafiya, shiyasa jikinka yayi sanyi kenan? Ashraf anya rayuwa zata iyu dahaka kuwa? inde dan'uwan ka zaiyi tafiya saika saka damuwa aranka? Ina Abuja Ina kano? idan kanason ganinsa basai kaje ba?" Ashraf ya Kalli mahaifin nasu,shi kadai yasan inane Captain zai tafi,shi kadai yasan Ina aka tura qanin nasa. Meyasa Aryan yabashi ruqon wannan babban alqawari? tayaya zaiyi shiru da bakinsa shi kadai ba tareda iyayensu sun san cewa yaqi aka tura shi ba? Dan Kar Daddyn nasu ya fahimci wani abu hakan yasa yasaki ajiyar zuciya yace"to Daddy insha Allah" Alqali yace"yawwa kokaifa, Allah yayi muku albarka" Kafin Ashraf ya amsa suka shigo dakin anan suka tarar da kilishi tana zaune tana share hawaye, gaban Ashraf yafadi kode taji labarin Ina Aryan yatafi ne? Cikin sauri suka qarasa wajanta Alqali yace"Kilishi meyake faruwa?" Cikin muryar kuka tace"Yakashe ta" Ashraf yazaro idonsa waje(😳) Yace"wa aka kashe?" Tace"Mawahib,Aryan yayi mata kaca-kaca babu dadin gani,Ashraf Ina imanin dan'uwanka yatafi? yarinya qarama yakasa binta a sannu tun cikin dare muke jiyo ihun kukanta babu damar dauki,nabar su acan itada Maryam zata mata dinki bazan Iya ganin wannan a zabar ba" Alqali ya zauna yace"dinki?" Hajiya kilishi tace"dinki za'a mata,yarinyar duk ta rame dare daya abun tausayi ido duk ya kumbura" Ashraf ya sunkuyar kansa qasa yana sosa qeyarsa,saboda maganar ta masa nauyi. Alqali yace"amma yasan da wannan danyan aikin yatafi Abuja yabarta? Wanne irin aiki ne za'a yi da bazai jira gari yawaye yabawa yarinya kulawa ba kafin yatafi?" Hajiya kilishi tace"ni ban yarda ma kiransa akai ba,nasan halinsa sarai kawai guduwa yayi saboda shi yasan abinda ya aikata" Alqali ya girgiza kansa yace"Allah yarufa asiri,kitashi kihada mata tea saiki kai mata tasha" Hajiya kilishi tatashi tsaye tanufi dining dinsu tana fadin"zaizo yasameni,wato shiga me qarfin doki" Ashraf yasake yin qasa da kansa yana sosa kansa,yasan cewa yana magana zata rufeshi da fada tace ai tare suke qulla komai,bayan kuma hakanne tare suka qulla din. (😂) ****** Mamy da Mama Sadiya ne adakin wadda tazo yanzu saboda itama tun ihun farko tasan cewa gidan ba kalau ba, itace take miqowa Mamy abinda take buqata, ita kuma Mamy tana mata dinkin,duk da Mamy tayi mata allura kafin afara dinkin hakan bai hanata jin zafi ba, saida mama Sadiya ta riqeta,Mamy tayi mata dinkin cikin nutsuwa. Zuwa wannan lokacin Mawahib kasa kukan tayi, saide hawaye dayake zarya a'idonta,bayan angama Mama Sadiya tace"bari naje nahada breakfast sai akaiwa Abban Mawahib dinma tunda ke kina nan" Mamy tace"to shikkenan,ai yau ba zanje asbitin bama,zanyi musu waya" Mama Sadiya tace"ai abun da tausayi, bazai iyu abarta ita kadai ba" tafadi hakan tana ficewa daga dakin. Mamy ta Kalli Mawahib tace"kidena kukan mana" Mawahib tana jinta tayi shiru,amma bata daina hawayen ba,saboda ita kadai tasan metake ji ajikinta. Hajiya kilishi tashigo da tea a hannunta tace"kungama dinkin Maryam?" "angama Yaya,gata nan kwance" Tea tabata tace"toga tea me kauri nahado mata zataji dadin cikinta insha Allah" Mamy ta kar6i tea din tace"to Yaya angode" Hajiya kilishi ta Kalli Mawahib datake zubar da hawaye tace"sannu Mawahib,yarinyar nan kin adda azaba,kiyi haquri kidaina kuka,shima duk inda yaje zaizo yasameni" Mamy ta Kalli Mawahib tace"kici gaba da kukan, idan ruwan hawayen naki yaqare sai naga da wanda zakici gaba da kukan,tun asuba kina kuka anyi lallashi anyi ban haquri kinqi kiyi haquri,kowa da haka yafara saide na wata yafi na wata, amma bazakiyi haquri ba kamar akanki aka fara kar6a budurci?" Hajiya kilishi tace"um um Maryam...,kibarta tayi kukanta,irin wannan abun de, kuma acikin wannan gida,to akanta aka fara,saboda nima ko ubansa bai ganamin wannan azabar ba" (🙊) Mamy tayi shiru ta dauki tea din tabata,a hankali ta kar6a tafara sha,kad'an tasha zata ajiye Mamy tasata ta shanye shi duka. Ashraf ne Alqali yazo yaga jikin Mawahib din,dakin yaturo yashigo shida Ashraf, idon Ashraf yasauka akansu, yagansu sun sata atsakiya ga qafafun ta a bubbude ,kansa yadan sosa sannan ya sunkuyar da kansa yace"Anty Mamy Ina kwana" "lafiya Ashraf,ya Nabiha?" "tana nan kalau wallahi, yame jikin?" Mamy ta Kalli Mawahib tace"gata nan sai langwai take jiki da sauqi,dauketa kakaimin ita dakina dan Allah,sai a rufe nan din" Cikin sauri ya girgiza kansa yace"A a" Hajiya kilishi ta kalleshi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi Mawahib dince bazaka dauka ba?" Kansa ya shafa yaqi cewa komai,Hajiya kilishi tayi ajiyar zuciya tace"ai shikkenan" Mamy tayi murmushi tace"to Ashraf Mawahib datana da aure dabata aure ai qanwar ka ce" Abba ne yayi sallama yashigo dakin ya shirya tsaf zai fita aiki, yagaida Hajiya kilishi, Ashraf ma ya rissina ya gaishe shi. ya Kalli Mawahib yace"sannu Ruqayya" Daga masa kanta tayi alamun amsawa amma batace uffan ba. Abba ya Kalli Mamy yace"zanfita aiki Maryam, saina dawo" Tace"to Alhaji Allah Yakiyaye hanya, ko zaka dauki Mawahib mukoma can?,Ashraf yaqi daukarta" Abba ya kalli Ashraf yayi murmushi ya qaraso ya dauketa cak, suka futo daga dakin,Mamy ta Kalli Mawahib datake goge hawaye tace"bazaki daina wannan qananun kukan ba? aida kinyi shiru ganin ubanki ne yasa zakici gaba da kukan" Hajiya kilishi tace"kai Maryam sai fada kike yiwa yarinyar nan dame zataji ne?" ta kalli Abba tace"isah kaimin ita dakina,zanyi jinyarta" Abba de yana jinsu baice komai ba yayi murmushi yajuya yakai Mawahib har cikin dakin Hajiya kilishi, sannan suka futo daga dakin. Mamy tawuce dakinta tayi breakfast sannan tawuce kitchen tadafa mata farfesun kifi,takai mata,alokacin tana kwance da apple a hannunta tana karya ahankali,farfesun tabata taci sosai, sannan ta kalleta tace"babu inda yake miki ciwo bayan wajan dinkin ko?" Idontane yacika da qwalla amma taqi basu damar zubowa tace"bacci nakeji kuma nakasa yi" Mamy ta jinjina kanta, sannan tafuto taje part dinta tahado allurar bacci tazo tayi mata, ko minti biyar bata sakeba, wani irin wahalallan bacci ya dauketa. Ta dade tana bacci har azahar, Hajiya kilishi data idar da sallah adakin tajuya tana kallonta tana azkar,hannunta ta daga zata fara Addu'ah taji Mawahib tana cewa "Yaya Captain zan mutu....kayi haquri,wayyo!!..." tafadi wayyo din da qarfi tareda firgita tabude idonta. Cikin sauri Hajiya kilishi ta ajiye carbin hannunta sannan tafara yimata magana tace"Mawahib..,kin tashi ne?" Cikin idonta dake cikeda da bacci tace"um...." tareda lumshe idonta taci gaba da baccin. Hajiya kilishi tasaki ajiyar zuciya tana girgiza kanta, lalle yarinyar nan tasha wahala a hannun Aryan,har cikin bacci ma yarinya tana firgita wacce irin rayuwa Aryan ya daukar wa kansa? Mutane suna cewa ko awajan aiki ana cewa danta Aryan jarumi ne, bata tabbatar da hakaba sai yanzu,haqiqa taga jarumi ganin idonta(😂) Tsawon sati daya Mawahib ta dauka Hajiya kilishi tana bata kulawa,acikin kwana bakwai dinnan kullum saita shiga cikin ruwan dumi haka bata aikin komai Hajiya kilishi tahana,zuwa kwana bakwai dinnan tagama warkewa ras,babu abinda yake mata ciwo,saide duk lokacin data tuno irin gumurzun da sukai itada Yaya Captain saita ji tsoro yasake kamata,idan ta tuna yana Abuja har wani nishadi takeji. Hajiya kilishi Kullum saita gwada kiran wayarsa, amma bata shiga wayar tana kashe,haka Alqali Shima yakira yakira yaji shiru. A6angaren Ashraf kuwa yafi kowa shiga damuwa saboda rashin samun Aryan awaya,idan yazauna yayi shiru ko agida ko awajan aiki maganar Aryan dince take fadowa ransa lokacin dayake cewa zamu tunkaresu, komu kashe ko akashe mu,idan ya tuno wannan furucin nasa saiya ji qwalla tacika idonsa. Har yanzu bai fadawa kowa ga inda Aryan yatafi ba. Haka sukaci gaba da nemansa har tsawon sati biyu, amma babu labarin Captain Aryan. Alokacin Mawahib takoma part din Mamy tana rayuwa acikin dakinta,tsawon sati biyun nan tayi tunanin Yaya Captain zai kirata yaji awanne hali take ciki, amma taga shiru bai kirata ba,tunani tafara Anya kuwa soyaiyar dayake kuka yake fada mata yana sonta Anya da gaske ne? yasanar da'ita zaiyi tafiya amma wacce irin tafiya ce zatasa yakasa kiranta!? ta dauki wayarta ta kirashi akaro na biyu tun aurensu,saide tana kira taji wayar akashe. Haka tayi haquri tabari har zuwa yamma tasake kira nanma taji waya akashe, mamaki ya kamata Anya Yaya Captain lafiya kuwa? tasan cewa baya kashe wayarsa,cikin damuwa tafuto daga dakinta takira Yaya Ashraf tace"Yaya Ashraf yau tun safe Ina kiran wayar Yaya Captain amma bana samunsa" Ashraf yayi shiru yana tunani to Mawahib sai yau takira Captain kenan,gyara muryarsa yayi yace"may be baida caji ne,zan kirashi zuwa anjima idan munyi magana saina fada masa ya kiraki" Tace"to shikkenan" Ta ajiye wayar jikinta yadan fara sanyi. Hajiya kilishi kuwa ganin sati biyu shiru Aryan bai kirasu ba,kuma idan sun kirashi basa samunsa,hakan yasa hankalinta yatashi,da farko tayi tunanin saboda abinda yayiwa Mawahib ne yasa yakashe wayar yaqi kunnawa harsai sun huce,daga baya kuma dataga shirun yayi yawa daga nan tasan cewa akwai matsala. Da daddare suna zaune da Alqali ta kalleshi tace"nikam Alhaji shirun Yaron nanfa yayi yawa babu waya babu wata magana qwaqwqwara akan ahaka" Alqali yace"nikaina abun yafara damuna, yau satinsa biyu kenan, dazu munyi magana da khaleed da Isah, Isah yace zaije Abujan yagano to nahanashi zuwa saboda yanayin aikinsa, sai muka yanke zamu tura Ashraf yaje yagano mana ko lafiya. Hajiya kilishi tasaki ajiyar zuciya yace"yawwa,amma shirun ai ya'isa haka,ko a wayar wani ai yakamata yakira mu idan tasa wayar ce bazai budeba" Bayan kwana biyu Mawahib tana kwance a dakinta sai juyi take tana so tayi bacci amma kuma takasa, ko Yaya ta lumshe idonta shi take gani, kuma tasan rashin baccin nata baya rasa nasaba da yanda Yaya Captain din yasabar mata da kwanciya a jikinsa, wayarta tadauka tasake gwada kiran wayar Captain Aryan,taji waya a kashe,mamaki yasake kamata, shekaran jiya Yaya Ashraf yace zai masa magana, jiya ta wuni tana kira wayar a kashe,yauma haka. Tashi tayi tanufi dakin Mamy tana zuwa tazauna jagwab akusa da'ita, Mamy ta kalleta tace"kekuma lafiya kikazo zaki sani agaba kifara min wannan jarababban kukan naki?" Cikin damuwa tace" Mamy ba kuka zanyi ba, Kingani kullum idan nakira wayar Yaya Captain bata shiga,shekaran jiya nakira shi, jiyama, yauma haka,Mamy ke kunyi waya ne?" Jikin Mamy yayi sanyi tace"Mawahib ai Captain yau sati biyu da kwana biyu kenan wayarsa a kashe,nikaina tun ranar daya tafi nake kiransa amma bana samunsa,babu ranar da zatazo tawuce ban kira Captain ba,tun tafiyar sa da kwana biyar danaji wayarsa a kashe jikina yabani ba lafiya ba,to babu wanda nafadawa saboda kada na tada hankalin iyayensa" bakinta tabude cikeda damuwa sannan tasaki wani irin numfashi tatashi tafuto daga dakin kamar an tsikare ta, Mamy tabita da kallo cikin tausayawa dan da alama tunda Mawahib tafara nuna damuwa akan Captain haqiqa tafara sonsa ne. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Mawahib tana barin dakin Momy takoma dakinta tazauna a gadon tafara tura masa saqo Kala Kala,sannan taci gaba da kiran wayarsa, takira wayar har babu adadi, amma bata sameshi ba. Har yamma tana kiran wayarsa amma shiru,daganan kuma jikinta yayi sanyi, gabanta yafara faduwa, tatuna lokacin dazai tafi, tatuna kalaman sa a gareta lokacin dayake fada mata cewa zanyi tafiya me nisa,bansan yaushe zan dawo ba, bansani ba zan dawo dinma kokuma bazan dawo ba, amma inaso kisani Ina sonki... duk abinda kike buqata karki tambayi kowa ki tambayi Ashraf,koda bana raye ki kalleshi, kisa aranki kamar ni kike kallo ki yafemin.... tana gama wannan tunanin gabanta yayanke yayi wata irin faduwa,jikinta yafara karkarwa,a fili ta furta "Ina yatafi?" Cikin sauri ta dauki wayarta takira Nusaiba matar Captain Habib abokinsa wanda sukaje gidansu suka kaimusu ziyara. Tana dauka cikin tashin hankali ko tsayawa batayi sun gaisa da'ita ba tace"Aunty Nusaiba,dan Allah inaso ki turomin number Abban mufid zan tambayeshi naji Yaya Aryan ko lafiya muna kiran wayarsa bata shiga, koda yaushe a kashe" Cikin mamaki Nusaiba tace"kamarya? Mawahib wai bakisan antura Captain Aryan wani daji zasuyi yaqi ba?"(🙆🏻‍♀️) tanajin haka taqame a zaune tareda sakin wayar tata tafadi qasa,gabanta yayanke yafadi,hawaye yafara zuba daga idonta, tadora hannunta aka tasaki wani irin ihun kuka tace"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...." Mamy datake kallo afalo, cikin sauri ta miqe tsaye tace"yau naga takaina yarinyar nan kode tahadu da matsalar aljannu ne?" tatashi da sauri zata nufi dakin Mawahib Hajiya kilishi da mama Sadiya dasuka jiyo ihun nata suka fado cikin falon cikin sauri,Hajiya kilishi tace"Maryam Mawahib qonewa tayi ne da ruwan zafi?" (🙆🏻‍♀️) Mamy tace"tana dakinta,nima Ina nan najiyo ihun nata" gaba dayansu suka saka kai cikin dakin Mawahib,har yanzu hannunta yana kanta tayi baza-baza da gashinta tana kuka kamar mahaukaciya. Mamy tace"Mawahib menene?, me aka miki?" Cikin kuka tace"yaya Captain ne..." Cikin sauri Hajiya kilishi tace"yakiraki ne? meyace miki?" Cikin kuka tace"wai antura shi yaqi...,dama yacemin qila bazai dawo ba yatafi kenan...,Mamy dan Allah kice masa yadawo wallahi yanzu inason mijina zanyi masa duk abinda yakeso"(😭) Hajiya kilishi tanajin haka ta jingina da bango tafara silalewa qasa zata zauna. Cikin tashin hankali Mamy tace"yaqi kuma?" (Sorry Mawahib 😥🙏🏻) Mutara zuwa yammah🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/15, 4:20 PM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB *13&14* Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Mama Sadiya tace"ai bamuga ta zamaba kamata yayi a fadawa su Alhaji atashi tsaye da Addu'ah in saukar Alqur'ani za'a masa ma sai ayi, ko kwanakin baya dasuka tura shi ai yana Samun damar kiran waya kota minti daya ce" Hajiya kilishi data silale awajan ta zauna tayi shiru kamar bata cikin hayyacinta, duk maganar da Mama Sadiya tayi kokadan bata jitaba, Mamy tacewa Mawahib "to ai Addu'ah zaki masa yanzu tunda de har anji inda yatafi" tajuya ta kalli hajiya kilishi "Yaya kiyi haqiru,in Allah yayarda Captain yana cikin qoshin lafiya" Cikin sanyin jiki Hajiya kilishi tace"rannan yacemin ankashe abokin aikinsa awajan yaqin....ina tsoro kar'akashe shi Shima " tafadi hakan hawaye yana zuba daga idonta . Mawahib tanajin haka tasake fashewa da kuka tadora kanta akan qwiwoyinta,sai yanzu ne take nadamar abubuwan datake masa abaya,sai yanzu ne take dana sanin meyasa takasa nuna masa soyaiya? Fita sukai daga dakin Mamy da Mama Sadiya suka ruqo Hajiya kilishi datake ji kamar bazata Iya taka qafafunta ba,compound suka hadu da mazan gidan kowannensu yadawo daga wajan aiki,cikin mamaki Alhaji khaleed yake cewa"meyake faruwa ne?" Mama Sadiya ta kalleshi "Alhaji yanzu Mawahib take cemana wai yaqi aka tura Captain tsawon wannan lokacin,gashi tunda yatafi Alhaji kana gani bamu ta6a Samun wayarsa ba" Alhaji Isa dayake tsaye da brief case a hannunsa yace"yaqi? Hasbunallahu wa ni'imal wakeel, amma Captain yayi shiru yakasa fada mana? bari nakira Yaya" Yadauki wayarsa yakira Alqali,yace"Yaya kana inane?" Alqali yace"Ina tareda Ashraf zai shirya yaje Abuja" Alhaji Isah yace"basai yajeba Yaya,kudawo gida akwai matsala" Alqali yanajin haka suka juyo zuwa gida, afalon Hajiya kilishi suka tararda duka mutanan gidan banda Mawahib. Ashraf yanemi waje ya zauna, Alqali ya kallesu yace"meyake faruwa? yanaga ana gogewa kilishi gumi?" Alhaji khaleed tace"yanzu muke samun labari awajansu wai Mawahib tace musu antura Captain wajan yaqi" Cikin sauri Ashraf yadago kansa ya kalli surukin nasa, Yaya akai Mawahib tasani? tayi waya dashi ne? Tayaya akai maganar tafita? Alqali yanemi waje ya zauna yace"to akwai matsala kenan,to aini yanzu nake shirin tura Ashraf Abuja yaje yagano ko lafiya,toda ace yajema dada wannan mummunan labarin zai dawo kenan" Alhaji Isah yace"idan munje masallaci anjima sai muyi magana da liman asaka shi cikin Addu'ah" Mama Sadiya tace"Abban Mawahib nida cewa nayi mezai hana ko sauka ce ayi?" Ashraf da kansa ke qasa yadago kansa ya kalleta yace"Mama nasa anayi masa sauka duk sati tun lokacin danaga yayi kwana biyar bai kirani ba" Alqali yace"yafada maka maganar yaqin ne?" Kansa ya sunkuyar yace"muna tare dashi aka masa waya lalle lalle yatafi Abuja dasafe, akwai abokin aikinsa dayake jagorantar sauran Sojojin ankashe shi,shine sukace kada ya6ata lokaci yaje yamaye gurbin wancen,naso nasanar daku tun ranar daya tafi, to amma yace nayi masa alqawari kada nafada muku saboda kada hankalinku yatashi" Hajiya kilishi tanajin inda aka tura Aryan wani hawayen yazubo mata, shikkenan shima qila kashe shi zasuyi. Alqali ya kalli Ashraf yayi shiru,sai yanzu yagane dalilin dayasa jikinsa yayi sanyi lokacin da Aryan din yatafi, ashe su akwai abinda suka 6oye. Yajuya ya kalli Mamy "waye yafada mata cewa antura shi yaqi?" Mamy tace"Yaya wallahi bansani ba,ihun ta muka jiyo daga daki muna zuwa saitake fada mana, da alama awaya taji labarin" Girgiza kansa yayi yace"insha Allahu zamuyi abinda yadace,ubangiji Allah yakare shi aduk inda yake" Gaba dayansu suka amsa da "Amin" Tun daga ranar Alqali da sauran qannansa suka yiwa limaman unguwar magana idan aka idar da kamsa salawat ake saka shi acikin kowacce Addu'ah. Duk gidan kowa idonsa yanakan wayarsa ko zaiga kiran Captain kokuma saqon sa,tun suna zuba idon ganin wayarsa har tsoro yagama wanzuwa a zukatansu, ganin sati na hudu kenan ya shude babu labarin Captain, babu dalilinsa. Mawahib duk ta rame sai fari kawai,hatta hips dinta saida suka ragu, haka breast dinta,idan tasaka riga da siket wanda abaya kamata yake, yanzu zuruf siket yake wucewa. Mamy tana lura da'ita amma babu yanda zatayi da'ita kullum cikin haquri take bata,dakuma lallashi. Idan ta tuna da maganganun daya fada mata adaren dasukai first night dinsu saide taji hawaye yazubo mata. Acikin sati na biyar ne cikin dare tana bacci tafarka takasa komawa baccin, ahankali tatashi tafuto daga dakin ko tsoro bataji kai tsaye tawuce dakinsu Captain,dakin yana rufe tun ranar da Abba ya dauketa yakai ta part din Hajiya kilishi,tsaf dakin yake a gyare ,rigar jikinta tacire tabude kayansa ta dauki jallabiyarsa tasaka, Sanna ta kwanta akan gadon tareda rungume fillo tanajin kamar Yaya Captain ne,ta dade tana juyi tana tuno irin yanda ya sangartata da daddadar soyayyarsa, ahaka wani bacci me dadi ya dauketa. Da asuba Mamy taga bata nan, taduba toilet dinta taga bata ciki,cikin sauri tafuto tazo dakinsu Captain anan taga Mawahib tana bacci cikin kwanciyar hankali jikinta Sanye da kayan Captain,murmushi tayi tarufe mata dakin ba tareda ta tashetaba saboda rashin isasshen bacci datake fama dashi. Tun daga ranar tadena kwana a dakinta tadawo kwana dakinsu Captain,tun mutanan gidan basu ganeba har suka gane,wani lokacin ma da Hajiya kilishi da Mamy da Mama Sadiya idan suna compound din gidan a zaune a kujerun roba haka zatazo ta wuce su tashige dakin tayi kwanciyar ta,Hajiya kilishi saide tayi murmushi,tasan shima rasa kunyar dayana nan haka zai qetare su yashige dakin tunda harya Iya kasa haquri da jarabarsa ya lalla6a ya danne yarinya acikin gidansu.(🙊) Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** yauda tatashi da asuba tayi sallah adakin, komawa bacci tayi, bata tashi ba sai qarfe tara na safe,tashiga toilet din dakin tagyara shi,sannan tadawo dakin shima tafara share shi,wata takarda ta sharo aqasa gado ta tsaya da sharar ta duba taga kamar takardar Yaya Captain ce, tadora takardar akan gado, sannan taci gaba da shara saida tagama ta kunna turaren wuta adakin tajuya zata fita,ta hango wannan takardar data bari akan gado, tadawo ta dauketa tabude bedside drower zata sakata aciki,bindiga tagani aciki,ahankali ta tsugunna ta dauki bindigar tafara jujjuyata tana gani, bata ta6a riqe bindiga a hannunta ba sai yau, saide tahangeta daga nesa-nesa awajan Yaya Captain. Ajiye bindigar tayi anan taga wata farar takarda da rubutu ajiki takardar tana bude ba'a ninke taba. Zama tayi awajan tadauka tafara karantawa, tun lokacin da idonta yakai inda taga yasa RUQAYYA gabanta yafara faduwa. Cikin sauri tafara karanta abinda ya rubuta "RUQAYYA kiyi haquri,antura ni yaqi zan maye gurbin Captain shu'aib,kiyi min Addu'ah,idan Allah yasa nadawo shikkenan, idan ban dawo ba kici gaba dayimin Addu'ah,naso ace nabarki har sai nadawo zuwa lokacin idan Addu'ah ta takar6u may be kinfara sona,to amma bazan iyaba...,inason koda sau daya ne nima na kasance da matata naji abinda sauran maza masu aure sukeji,ayau zan kar6i haqqina a wajanki,nadade inashan magungunan da likita yabani saboda matsalar rashin haihuwa ta, idan Allah yasa kafin nadawo kinsamu ciki idan namiji kika haifa asaka masa sunan ASHRAF,idan mace kika haifa asaka mata sunanki, saboda keda Ashraf kune mutum biyu danake so duk duniya sama da kowa bayan Momy na, kiyafemin..." Yana kawowa nan rubutun yaqare,zuwa wannan lokacin da Mawahib take karanta wannan takardar, tuni takarda ta jiqe da hawaye. Dama magungunan dataga yanasha na matsalar sane? takardar ta cukwikwiye tarufe idonta da'ita tana wani irin kuka mecin rai,sosai take kuka kamar anyi mata albishir da mutuwa. Mamy da taji shiru Mawahib batazo tayi breakfast ba tafuto zuwa dakin cikin damuwa,Hajiya kilishi data futo daga kitchen taga Mamy tana sauri zata wuce tace"maryam lafiya kuwa?" Mamy ta kalleta"Yaya Mawahib ce naji shiru bata futo ba,har zan fita aiki banga tazo tayi breakfast ba,shine zan duba" Cikin damuwa itama tace"muje,yarinyar nanfa saimun tashi tsaye akanta" Suna zuwa dakin suka sameta tana rusa kuka,idanunta sunyi jajir,cikin sauri suka qarasa Hajiya kilishi ta zauna abakin gadon ita Kuma Mamy ta tsugunna taja Mawahib jikinta tana bubbuga bayanta alamun lallashi, cikin rawar murya kamar zata fashe da kuka itama Mamyn tace"kiyi haquri mana,Mawahib Addu'ah zaki masa ai" Cikin kuka ta nunawa Mamy takardar tace"Mamy wasiyya ya barmin fa....,yanzu Ina shara nagani,dama yasan tafiya zaiyi yabarni bazai dawo ba meyasa bazai tafi dani ba?" ta qarasa maganar idonta yana tsiyayar da hawaye. Hawaye yazubo daga idon Mamy takasa cemata komai tadaiyi kokarin rungume ta ajikinta. Hajiya kilishi ta dauki takardar ta karanta lokaci daya itama tafara kuka,tasaka gefen zaninta tana share hawayen,cikin kuka tace"kimasa Addu'ah Mawahib...." daga haka takasa cewa komai tafuto daga dakin tana ruskar kuka. Mamy da Mawahib kuwa sun dade adakin babu mai lallashin wani,sannan Mamy tasamu qwarin gwiwar goge hawayen ta takamo Mawahib din suka futo daga dakin. Tundaga wannan ranar saiya kasance abincin ma tadaina ci,saide ruwan shayi,idan ta zauna ba zatayi magana ba saide tayi shiru tana tunani,har Mamy tafara tsoro kar cutar damuwa ta kamata. Da daddare Mamy tahanata zuwa dakin Captain Aryan tadawo da'ita dakinta suna kwana tare,acikin kwanakin dasuke itada Mamy kullum basa bacci sai sun gabatar da nafila cikin dare sunyi addu'o'i sannan Mamy ta kwanta, Mawahib kuwa idonta biyu ras bata jin bacci,shiru take tana tuna irin rayuwar dasuke a Abuja itada Yaya Captain. Har akira sallar asuba idonta biyu,gari yawaye amma ko gyangyadi batayi, Mamy data lura bata Iya bacci hakan yasa take yimata allurar bacci,shine zata dade tana bacci har asamu qwaqwalwar ta tahuta. Hakan yasa washegari Mamy taje part din Hajiya kilishi,ta tarar har Alqali ma yana nan, bata 6oye musu komai ba akan matsalar Mawahib tafada musu komai,anan Alqali yace zaisa ayi mata rubutu ko Allahu zaisa tadawo hayyacinta takuma fauwalawa Allah komai, sannan yace Mamy ta matsa mata akan Addu'ah dakuma karatun qur'ani. Mamy taji dadin maganganun Alqali,koba komai itama Hajiya kilishi asamu tadawo nata hayyacin, tunda daga ita har Mawahib din ansara gwara gwara a cikinsu. Kwana biyu dayin wannan maganar Mamy tana zaune afalo itada Abba da Mawahib suna ganin labarai, Mawahib da Alqur'ani a hannunta tana karantawa,kwata kwata hankalinta baya kan abinda su Mamy suke gani,tana Sanye cikin hijab, Abba da Mamy kuma suna ganin Labaran, saide kowa yayi shiru da alama suma kawai kallon sukeyi gudun karsuyi tunani. Ashraf da Hajiya kilishi da Alqali suka shigo falon,Mamy tayi musu sannu da zuwa, Mawahib ta Kalle su tace"ina kwananku?" Alqali ya amsa mata cikin murmushi, zama sukai Alqali ya kalli Abba yabashi wata gora cikeda ruwan Addu'ah na rubutu yace"isah wannan na Ruqayya ne,ta dinga sha safe da yamma" Cikin girmamawa Abba ya kar6a yace"to Yaya insha Allahu za'a bata,ai jikin nata naga da sauqi ma, tunda gatanan tadena zaman daki da'ita muke zama afalo saboda kada ta yawaita tunani..." Kafin Alqali yayi magana gidan talavision din dasuke watso labari suka sako photunan wasu sojoji guda uku,cikon na hudun kuwa Yaya Captain ne,Mawahib da idonta yakai kan Sojojin nan tana ganin fuskar Yaya Captain ta ajiye qur'anin hannunta tazubawa tv ido gabanta yana faduwa,gaba daya suma su Alqali sai suka maida hankalin su kan labaran, inda me bada labarin yake cewa"rundunar Sojojin Nigeria wadda aka tura yaqi domin qwato dubban mutanan da yan ta'adda sukai garkuwa dasu sun samu nasara akan yan ta'addan inda suka qwato dukkan mutanan, sannan suka kashe mafi yawan yan ta'adda bisa jagorancin Captain Aryan I. Alqali,kada mutane su manta ba qaramin yaqi bane wannan, musanman dajin da wannan Yan ta'adda suke ciki,shide wannan daji ya kasance mafi munin daji acikin dajujjukan damuke dasu afadin qasar nan,tsawon wata uku kenan da'aka tura Captain Shu'aibu tareda rundunar sojin Nigeria,inda Allah yayi qarar kwanan sa a wannan daji, daga baya gwamnatin Nigeria tabada umarnin atura wasu Sojojin inda hukumar Sojan qasan Nigaria tatura mutane hudu,daga cikinsu akwai Captain Aryan I. Alqali, wanda muke samun labarin mutuwar sa yanzu haka daga majiya mai qarfi inda yasamu harbi agefen zuciyarsa, har yanzu de hukumar Sojojin Nigeria takafa ta tsare wajan ganin......" Dif idanun Mawahib ya rufe tadena ganin komai sai duhu,ahankali Hajiya kilishi ta lumshe idonta tafara qoqarin maida qwallar dazata zubo mata,bataso kokadan tayi kuka,wani abu mai tauri yazo ya tsaya mata a maqoshi tana so taja numfashi amma takasa, saide har lokacin tahana kanta zubar da hawaye ko daya. Ashraf yasaka hannu yagoge hawayen idonsa kansa aqasa ya gagara dagowa bare ya kalli fuskar dan'uwan nasa da'ake nunawa. Alqali yatashi tsaye ya goge gumin fuskarsa ya kalli Abba da idanunsa sukai jajir yace"isah muje musamu khaleed saimu wuce Abujan" Cikin sauri Abba yagyada kansa amma yakasa cewa komai saboda yana bude bakinsa kuka zai Iya qwace masa. Shiru falon yayi bakajin motsin kowa sai kukan Mamy data kasa riqe kukanta ta sunkuya ta dora kanta akan hannun kujera tana kuka kamar ranta zai fita. Hajiya kilishi data lura Mawahib bata motsi cikin sauri tatashi tafara kiran Sunanta tace"Mawahib!" Taji shiru, tasaka hannunta duka biyu tafara jijjigata cikin rawar murya wadda take gab da fashewa da kuka tace"Mawahib!!" tagado ta kalli Alqali da Abba dasuke shirin fita tace"Alhaji kuzo ku duba kar itama mu rasata" (So Sad 😭) (matan sojoji Allah yakare muku mazajenku,🤲🏻,Wanda suka rasa mazajensu ubangiji Allah yabasu haqurin rashin su,🤲🏻😭) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad👌🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/18, 5:57 AM] AMINA KABIR CAPS: *Page 78* Abba ne yasunkuya ya tatta6a fuskarta yana kiran sunanta "Ruqayya! Ruqayya bude idonki" Shirun da yaji ne yasa yata6a qirjinta yaji bugun Zuciyarta yana nan, sannan yace"suma tayi" Ya kalli Mamy ko zata bata wani taimakon yaga Mamy sai faman kuka take ko kallon Mawahib dinma batayi ba. Ya kalli Ashraf yace"bamu ruwa Ashraf" Tashi yayi fuskarsa tana tsiyayar da hawaye yaje fridge yadauko gorar ruwa guda daya yabawa Abba, yakar6a tareda budewa yazuba a hannunsa sannan ya shafa mata dan kadan a fuskarta, amma bata farfado ba. Hajiya kilishi tace"mutafi asbiti kawai" Mama Sadiya da Alhaji khaleed ne suka shigo falon, Mama Sadiya sai kuka take tana salati. Gaba daya itada Mamy sai suka sa duka mutanan falon kuka,amma abun mamaki Hajiya kilishi har yanzu batayi kuka ba,idonta de yana cike tab da qwalla, kuma tana magana kanajin muryarta tana rawa alamun tana dab da fashewa da kuka. Abba ya kalli Ashraf yace"karomin wani ruwan" Ashraf yasake bude gorar zai zuba masa ruwan, wayarsa ta dauki qara alamun kira yashigo, cikin sauri yaduba wayar,gabansa ne yayi wata mummunar faduwa a fili yace"Aryan...." Cikin sauri Mamy tadago kanta ta kalleshi,Mama Sadiya datake goge idonta ta dankwalin kanta itama ta dakata duk suka zuba masa ido,Alqali ya kalli Ashraf daya qame a tsaye yakasa daukar wayar, yatashi yakar6i wayar, yana fadin"ina tunanin mutuwar zasu fada mana" Yadauki wayar yazauna a kujera sannan yasaka wayar a speaker yace"Assalamu Alaikum" Daga can 6angaren cikin muryar nan tasa me aji yace"Ash...." Cikin sauri Alqali yatashi tsaye yace"Aryan...Aryan kana jina? kaine kake magana ko kunnuwana ne?" Murmushi yayi yace"nine Daddy...." Lokaci daya fuskar jama'ar falon ta washe,Hajiya kilishi tasaki wata irin ajiyar zuciya,sai alokacin wani irin hawaye yazubo mata. Mamy tafara goge hawayen idonta tana murmushi,kowa ya matsu abashi wayar, kafin Alqali yayi magana Alhaji khaleed yace"Aryan yanzu mukaji labarin mutuwar ka,kaganmu nan hankalin kowa yatashi iyayenka sai kuka suke" Cikin mamaki yace"Uncle mutuwa kuma? rumors ne kawai,babu wanda yarasu acikin mu,basu gama tantance labari bane suke yad'ashi" Alhaji Isah yace"Alhamdulillah Alhamdulillah, Allah abun godiya.... Yanzu kana Ina? yaushe zaka taho? kokuma de mu muzo gaba dayanmu muganka ko hankalin mu zai sake kwanciya?" Captain Aryan yayi murmushi yace"Uncle yau zan taho gida komin dare insha Allah,yanzu haka muna Abuja shiyasa nasamu damar kiranku,munfuto wajan network" Abba yace"to Alhamdulillah,ubangiji Allah yakawo ku lafiya Aryan,Allah yatsare ku" Ya amsa masa da "Amin" sannan yace"Ashraf...." Alqali yayi sauri yabawa Ashraf wayar,Ashraf dayake goge hawayen idonsa na farinciki ya kar6i wayar yace"Aryan" Captain yayi dan qaramin murmushi jin Ashraf din kuka yake,danya kwantar masa da hankali yace"Whare is my wife...?" Ashraf ya goge hawayen idonsa sannan ya kalli Mawahib dahar lokacin take kwance bata farfadoba,yasake goge hawayen idonsa danya kwantar masa da hankali yace" She's sleeping..." Ajiyar zuciya Captain yasauke me nauyi sannan yace"kakula min da'ita kafin nazo itada Momy, saina qaraso" Ashraf yace"to Aryan" Gaba daya falon sai bakin kowa yabude, falo yadauki surutu,Hajiya kilishi tasake goge idonta ta kalli Mamy tace"Maryam tunda kinji labarin dannaki yana raye zoki duba tawa yarinyar" Dariya suka saki gaba dayansu,ta taso takarbi gorar ruwan da Ashraf yakawo tabude bakin robar ta kwara mata,cikin sauri Mawahib tasaki wani irin numfashi tareda jan numfashi,Mamy ta kamota ta rungume ta ajikinta,ahankali tafara bude idonta harta budeshi ras,tana ganin mutanan falon ta tuno abinda yafaru,cikin d'acin zuciya tasaki wani irin kuka tace"Mamy da gaske yaya Captain yatafi yabarni?,meyasa saida yabari nafara sonsa zai tafi yabarni? meyasa mutuwa bata daukemu tareba,? Mamy nima mutuwa zanyi..." Cikin lallashi Mamy tace" Mawahib Captain yana nan,bai mutu ba,yana nan da ransa yanzu muka gama waya dashi" Hawayen idonta ta goge tace"Mamy dan karna mutu shiyasa kika fadi haka ko? da idona nagani ance yamutu" Ashraf yayi sauri yakira Aryan,bugu daya yadauka yace"Aryan ga Mawahib tana so taji muryarka" Yafadi haka tareda bawa Mamy wayar,daga can 6angaren Captain Aryan da beyi tunanin a speaker aka saka wayar ba, cikin sigar soyaiya yace"Baby bakya kewata ko...?" tanajin haka ta kalli wayar da sauri,sannan ta kalli Mamy,cikin sauri ta 6oye fuskarta ajikin Mamy, Mamy tayi murmushi tabawa Ashraf wayarsa, Ashraf yafice daga falon da wayar a kunnansa. Alqali yayi murmushi ya kalli Mawahib yace"shikkenan kuka yaqare ko Mawahib?" Cikin sauri ta juya bayanta anan taga duka iyayen nasu maza da kowa da kowa na gidan duk suna falon,cikin sauri tacire jikinta daga na Mamy tatafi dakinta da gudu cikeda kunya(🙈) kan gadonta tafada tasaki wani irin murmushin farinciki,fillo taja ta rungume a qirjinta tana sakin murmushi ita kadai, cikin sauri tatashi tafada toilet tayi wanka wanda ta dade batayi irinsa ba, sannan ta dauro alwala tazo tafara gabatar da sallar nafila tana sake yiwa Allah godia daya dawo mata da mijinta gida lafiya. mutane suna jin labarin nasarar su Captain aka fara sallama a gidan ana yiwa mutanan gidan barka. Su Daddy kuwa suna idar da sallah suka wuce wajan limamai suna sake yimusu godia akan irin taimakon dasuka basu na Addu'ah. Ashraf kuwa gida yawuce yadauko Nabiha suka dawo gida. tun yamma Mamy da Mama Sadiya suka shiga kitchen tare suka fara gabatar da abincin da za'a tar6i Captain Aryan,Nabiha kuwa tana wajan Mawahib sai tsiya take mata. Zuwa magrib su Mamy suka gama komai, Hajiya kilishi tace"sukai komai da komai part dinta ahadu acan gaba daya aci abincin" can suka kai abincin tareda taimakon Mawahib da Nabiha, Mawahib gaba daya hankalin ta ya karkata kan bakin get,gani take kamar bazai dawo ba,bayan sungama jera komai a part din Hajiya kilishi compound suka dawo gaba dayansu kowa ya zauna a kujerun roba dasuke tsakar gidan nasu. Amma Mawahib a tsaye take takasa zama,tana daga tsaye ta dora hannunta akafadar Nabiha, tayi kwalliyarta madedeciya tana sanye cikin riga da siket na leshi, har dare suna Compound din gidan,mazajen gidan su Daddy harsun shigo gida kai tsaye sukace wuce part din Hajiya kilishi. Mamy ta kalli Abba tace"Alhaji bai qaraso bane har yanzu?" Abba yace"sun sauka tun dazu,Ashraf yaje dauko shi" Mawahib tanajin haka tayi wata irin asirtacciyar ajiyar zuciya,ta sunkuyar da kanta. Ko minti ashirin ba'a yi da shigowar su Daddy ba,Yaya Ashraf yashigo sannan Yaya Captain,yana Sanye cikin uniform dinsu na sojoji,Mawahib tana ganoshi ta saki ihun murna tatafi da gudu ta rungume shi(🙈🙊🙆🏻‍♀️) Ihun dasu Abba suka jiyo yasa suka futo anan sukaga Mawahib rungume da Captain Aryan. Sosai ta rungume shi kwata kwata ta manta da wata aba kunya,murmushi yasaki shima baiyi wata wata ba yadora hannunsa akan hips dinta ya rungume ta sosai yana sakin ajiyar zuciya,hawaye take na farinciki ta dora kanta akan faffadan qirjinsa tayi luf tana zubar da hawaye, cikin kuka ta dago ta kalleshi tace"ina sonkaaaa!! ". Wani irin farinciki ya kama Captain, Murmushi yasaki sannan yadan sunkuya daidai tsawonta yadora bakinsa akan kunnanta cikin sigar rad'a yace"I miss you...,kiyi shiru mana,bagashi nadawo ba?" Cikin hawayen tadago kanta ta kalleshi sannan takai masa wani irin dukan soyaiya a qirjinsa. Cikin sauri Mamy dataga alamar kamar sun manta iyayensu suna wajan tayi gyaran murya tace"sannu da zuwa Captain"(😂) Ahankali yasaki Mawahib ya qaraso cikin gidan yana dan sosa qeyarsa, ya kalli iyayen nasu da duka fuskarsu ta cika da farinciki, sannan ya tsugunna yasake sosa qeyarsa ya gaida su, cikin farinciki suka amsa, Hajiya kilishi data cika da farinciki ta kalleshi tace"Baba nah? aikasan yanda ake rubuta takardar barin aiki ko?" Alqali yayi murmushi yace"kai taso muje kayi wanka muci abinci kowa da kowa kai yake jira" Cikin kunya yatashi suka wuce part din Hajiya kilishi,acan yayi wanka sannan Ashraf yakawo masa kayansa yasaka,suka futo falon hannunsa cikin na Ashraf,dukansu suna zaune a dining kowa jiransa yake, yana zuwa kuwa suka zauna shida Ashraf, Nabiha tana gefen Ashraf, Mawahib kuma tana kusada Mama Sadiya, Hajiya kilishi tana daya gefen nata, sun sakata a tsakiyar su,Mamy ce tazubawa kowa abinci,saida tafara zubawa mazan sannan iyayensu mata saikuma su yara, abinci aka faraci Alqali yana kallon kowa yanajin dadi aransa,ranar dayake fata yake buri yau gata tazo, Allah yahada masa kan iyalansa gaba daya, babu tashin hankali babu fitina, ko yanzu yafadi yamutu yasan cewa bai bar baya daqura ba. Captain Aryan yanacin abincin yana satar kallon Mawahib,ita kuwa qin dagowa tayi ta kalleshi kasancewar tana fuskantar sane, gata ga Hajiya kilishi Ina ita Ina rashin kunya agefen suruka? idan tabiye masa babu abinda bazai faru ba,tundashi bazai Iya daina kallonta ba togara ita tadan nutsu. Qare mata kallo yake ganin tarame sosai tafada, saide fari data qara,jiyake kamar ya janyota jikinsa,cin abincin nan dayake jinsa yake kamar akan qaya yake. Ashraf daya ga gaba daya hankalin Captain yana kan Mawahib yaturo qafarsa ta qasan table din ya zungureshi. Sai alokacin yadawo hayyacinsa,yaci gaba dacin abincin har suka kammala gaba daya,yar fira sukai cikin farinciki kowa yaana tofa albarkacin bakinsa har wajan qarfe goma nadare sannan Mama Sadiya da Alhaji khaleed sukai musu sallama suka tafi Part dinsu, Nabiha ma tatashi tabi bayan Mamanta. Sannan Mamy da Abba ma sukai musu sallama suka tafi,cikin nutsuwa itama Mawahib tabi bayan iyayenta tanajin yanda idon Yaya Captain yake yawo ajikinta,amma bazai iyu ta zaunaba dole zasu barsu da iyayensu ko zasu tattauna wata maganar. Tana zuwa dakinta wanka tashiga tasaka rigar bacci doguwa tanada dan kauri,sannan tafara shirin kwanciya saboda tasan yau Yaya Captain yana tareda Momy kilishi,kwanciya tayi adede lokacin goma da rabi nadare,saqo ne yashigo wayarta tana dubawa taga Yaya Captain ne yaturo mata, karantawa tayi sannan ta girgiza kanta cikin murmushi tatashi tasaka hijabi takashe wutar dakin nata, tafice tatafi dakinsa. Tana turo qofar dakin ta ganshi a tsaye yana fuskantar qofar dakin yana sanye cikin kayan bacci riga da wando,yana ganinta yabude mata hannunsa alamun tataho wajansa. Kanta ta sunkuyar qasa ahankali tataka har tashige cikin jikinsa tareda kwantar da kanta a qirjinsa,atare suka saki ajiyar zuciya,idonsa ya lumshe yayinda itama nata idon yake a lumshe, haka suka tsaya tsawon lokaci babu wanda yayi magana,ahankali yatura hannunsa cikin hijab d'inta sannan ya damqi hips dinta da duka hannunsa biyu cikin muryar rad'a mecikeda tsananin buqata yace"meyasa abuna suka rame haka?" Yafadi hakan yana matsa mata mazaunan ta,Mawahib taji wani irin zirrrr ajikinta,batasan lokacin data sake rungume shiba, saide takasa bashi amsa. janye hannunsa yayi daga wajan,doguwar rigar dake jikinta yafara dagewa sama har saida yakawo yakawo rigar dede cikin ta,ya kasance duka cinyoyinta suna a waje daga ita sai qaramin pant din dake jikinta,yatura hannunsa cikin rigar tata yakama nashanunta sannan yamaida yatsansa kan nipples dinta yafara murzawa a hankali,numfashin tane yafara yin sama sama tanajin wani irin dadi,ahankali tasake qanqame shi, cikin muryar jin dadi wadda tacika da sha'awa yace"Baby kinyi missing dina?" Cikin jin dadin abinda yake mata tasake lumshe idonta sannan tadaga masa kanta, ahankali yacire hannunsa daga kan qirjinta,rigar jikinta ta sauko qasa tarufe mata jikinta, yakama fuskarta da hannunsa biyu Sannan yace"to nunamin" Ahankali tadaga kanta tadora lips dinta akan nasa tasakar masa kiss, yanajin lips dinta akan nasa ya cafke bakinta yafara yimata wani irin kiss,ahankali tafara maida masa martani, tariqe lips dinsa naqasa tana tsotsa ahankali, yayinda shikuma yakama lips dinta nasama yanasha, sunyi nisa sosai cikin kiss banda numfashin su da kakeji babu abinda kakeji yana tashi adakin. Ashraf yayi gyaran murya ganin basu maji qaran bude qofar da yayi ba,cikin sauri Mawahib ta qwace bakinta,wata irin kunya ta kamata taji kamar ta nutse awajan. hannunsa ya harde a qirjinsa sannan yace"tsuntsayen soyaiya ya'isa haka,mu zamu wuce gida" Cikin gudu tashige toilet din dakin tareda rufowa, Captain Aryan yabita da kallo yasaki murmushi sannan ya kalli Ashraf yace"kaga kasa ta gudu,bansan ka shigoba wallahi" Yafadi hakan yana sosa kansa. Ashraf yakama kunnansa guda daya yariqe yace"wallahi kabi 'yar mutane a sannu,inba hakaba zaka hadu da Momy..." Cikin sauri yadora hannunsa akan kunnansa yace"Auch...Ash wallahi babu abinda zan mata" Ashraf yacika kunnansa sannan yayi murmushi yace"to saida safe" "muje na rakaka" Cikin sauri Ashraf ya dakatar dashi yace"no,yi zamanka,ka kwanta kahuta" Yafadi haka tareda ja musu qofar, Captain Aryan yawuce toilet yayi nocking ahankali tabude tafuto,bai jira wannan tafiyar tata ya yangaba yasaka hannu ya dauka cak, yakashe musu wutar dakin sannan suka haye gadon yayi mata rumfa sannan yamaida bakinsa cikin nata(🙈) Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Qofar motar yabude mata ya kalleta ganin tana tafiya daqyar kamar batason taka qasa yace"kode Baby na yana damunki ne in dauke ki?" Nabiha ta kalleshi cikin shagwa6a tace"Sweet dan Allah kabarmu mu kwana agida" Jingina yayi da motar yana kallonta yace"to fadamin,tareda qanina da matarsa kikeso muhadu mu kwanta gado daya? Kokuma zaki biyoni Part din Momy? Kokuma ni in biyo ki part din mama sai muyi kwanciyar mu? kinsan de bazai iyu muna gida daya muraba wajan kwana ba ko?" Cikin shagwa6a tace"sweet...." Murmushi yayi yanuna mata cikin motar, babu musu tashige,shima yashiga yaja suka tafi gida. Acan dakin Captain Aryan kuwa ganin yanda Mawahib take maida masa martani hakan yasa ahankali yafara zame mata kayan jikinta harya cire mata rigar gaba daya yarage daga ita sai brezia da pant,sannan shima yacire nasa kayan,yasake sakata cikin jikinsa, ahankali yazare lips dinsa daga nata sannan yaja blanket ya rufe su, tanajin yanda yacire mata riga tasake shige wa jikinsa,cikin jin dadi yafara yimata rada a kunnanta koda wani yana cikin dakin ba lalle yaji abinda yake rada mata ba,cikin rad'ar yace"Honey na fadawa Daddy gobe zamu wuce Abuja hakan yayi?" Cikin sauri ta kalleshi tace"Abuja kuma?" Hannunsa yasaka ya 6alle mata brar dake jikinta tabaya sannan yace"yes,amma yace saide muyi haquri mutafi jibi, ko so kike na kashe kaina da sha'awar ki? kinsan halin dana shiga batare dake ba? tsawon kwanaki nawa banji ki ajikina ba? Kina tunanin zan'iya jurewa ne Ina ganin ki acikin gidannan batare dana jini aciki ba?"(🙈) Cikin rashin fahimta tace"kamarya?" Murmushi yayi yazare mata breziyar ya cillota qasa,sannan yatura hannunsa cikin bargon yadora hannunsa akan cinyarta yace"Ina nufin cikin nan" Cikin sauri tasaka hannunta tazare masa nasa hannun daga cinyarta jin yanda yake mata waiwayi awajan, murmushi yayi yadauke hannunsa sannan yace"nayi kokari, bazan Iya sake kwana uku batare dana kasance dake ba,Ina tsoron insake yin hakan acikin gidannan saboda karki taramin mutane" Cikin sauri tayi murmushi sannan ta 6oye fuskarta acikin qirjinsa,shima murmushin yayi yadora hannunsa akan nashanunta yana shafawa cikin dabara sannan yace"Ina sonki Honey....,tundaga ranar da muka kasance abu daya,daga ranar na maida miki sunan ki Honey,you're so sweet...kinada dadii sosai,Ina sonki Kuma zanci gaba da sonki har abada" Idonta ta lumshe saboda yanda yake wasa da nashanunta ahankali babu zafi hakan ba qaramin dadi yake mataba, cikin jin dadi tace"nima Ina sonka Yaya Captain...,Ina qaunar ka" Cikin sauri ya kalleta yace"sosai?" Daga masa kanta tayi ba tareda tayi magana ba. " to fadamin yaushe kika fara sona?" Cikin shagwa6a tace"ni de banason wannan tambayar" Murmushi yayi a bayyane, yaja hannunta cikin dabara yadora akan mararsa,lokaci daya hannunta yafara karkarwa takasa koda qwaqwqwaran motsi da hannunta,ganin yanda ta rikice yasa yafara qoqarin kwantar mata da hankali, cikin salon jan hankali yace"shiyasa kika rame?" Cikin sauri ta daga masa kanta hawaye yazubo daga idonta,cikin sauri yasaka harshansa ya lashe mata hawayen sannan yace"bagani nadawo ba,?kidena kuka,yanzu zansa wannan abubuwan nawa su dawo yanda suke da harma sufi nada yawa" yafadi haka yana shafa breast dinta da hips dinta. Cikin kunya ta rufe fuskarta da qirjinsa,ahankali tace"bazaka sake tafiya ba?" Captain Aryan ya kalleta da sauri yanajin wani irin dadi yanda take nunawa yanzu fa tanayi dashi, yace" ki kwantar da hankalin ki,insha Allah Ina tare dake a kowanne lokaci kinji?" Ahankali ta daga masa kanta sannan tace"i miss you" Murmushi yayi yace"really?" Daga masa kai tayi, cikin jin dadi yace"nima nayi kewarki,nayi kewar komai naki,bana fatan nasake kwana daya batare dakeba, please ki riqeni amana kinji,karki bari kowa yashiga tsakanin mu" Cikin sauri ta gyada masa kanta. Kansa ya sunkuyar yayi kissing wuyanta,ahankali ya gangaro zuwa qirjinta yadora bakinsa akan nashanunta yana tsotsa ahankali idonsa a lumshe,jin yanda yake mata komai nutsuwa da hankali hakanne yasa tafara sakin wani irin numfashi ahankali,badan qaran esi dake dakinba babu abinda zai hana kajiyo yanda take sauke numfashi,hannunsa yatura cikin bakinta ahankali takama tafara tsotsa, tun yana shan nashanunta sai gashi yadawo yanashan ko'ina najikinta,jikinsa yafara rawa yana mazari, Mawahib tana jinsa kokadan batayi yunqurin hana shi ba,yadora hannunsa akan nata hannun dayake aqame waje daya takasa ta6uka komai. Zuwa wannan lokacin Captain yafara tsiyayar da hawaye ajikinta,yayinda Mawahib taji duniyar tafara mata zafi sakamakon abinda yake cikin hannunta,ganin tafara qin sakin jiki dashi hakan yasa yarada mata a kunne cewa"babu komai, babu abinda zan miki,nasan ai muna gida,idan kinaso muyi bacci to kimin koma menene...." tanajin abinda yafada sai kanta ya kulle, tarasa gane meyake nufi data masa komai,jin tayi shiru bata fara masa komai ba yasa yaja hannunta cikin hikima ya gwada mata abinda yake buqata,ahankali tafara yimasa komai cikin tsoro harta dawo tasaki jikinta ganin ko inda pant dinta yake bai nufa ba,hakan yasa tasaki jiki dashi tana masa duk abinda ya gwada mata, yayinda shima nasa wasan yayi nisa har yayi tsaurinda Mawahib takasa yin shiru saida tafara sakin wani irin nishi, yayinda shikuma yake tsiyayar dawani irin hawaye. Bai rabu da'ita ba saida ya tabbatar daga ita harshi sunji dadin wasan, sannan ya rungume ta dukansu suna maida numfashi,saide gaba daya sun gama lalata jikinsu(🙈) Mawahib tayi luf a jikinsa tana tunani aranta ai inde Iya wannan abun Yaya Captain zaiyi mata badata matsala saboda yanada dadi,amma wancen dayan kam bazata yarda dashi ba. Sun dade a kwance tsawon lokaci kafin yaji qarfi a jikinsa yadauketa suka wuce toilet,tare sukai wankan duk da yanda take kawar da idonta daga kansa hakan bai hana yacusata cikin jikinsa sunyi wankan tare ba. Basu kwanta bacci ba sai wajan qarfe uku nadare,wani irin bacci medadi ya daukesu. Asuba tagari masoya🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub ✍🏻 [7/18, 5:57 AM] AMINA KABIR CAPS: Koda wasa basuji kiran sallar asuba ba duk da ga masallaci nan a kusada gidan Alqali. Amakare yaje masallaci lokacin ana sallama yana tada tashi kabbarar sallar,baiyi kuskuren kallon inda su Daddy sukeba, yana idarwa yadan zauna kad'an sannan yataso yafice daga masallacin. Yana komawa dakin alokacin ta idar da sallah kenan tatashi tana Sanye cikin hijab zata fita daga dakin, hannunsa ya harde a qirjinsa yace"whare...." Kafin ya qarasa tambayar ta Ina zataje tatari numfashinsa tace"dakina zan tafi,kar Mamy ta lura bana nan" Cikin shagwa6a yace"to batasan mijinki yadawo ba?" Yana fadin haka yadauketa cak suka koma kan gado,hijabin yacire mata sannan yazare mata rigar,shima yacire jallabiyar jikinsa yatsaya dagashi sai gajeren wando,yasaka ta cikin jikinsa yana shafa kanta,ahankali bacci yayi awon gaba dasu,sosai sukai bacci musanman Mawahib da bata Iya bacci saida allura,yau kuma tasamu baccin hakan yasa ba qaramin nisa baccin nasu yayi ba,basu tashi ba sai qarfe goma shadaya nasafe, atare suka bude idonsu suka zubawa juna ido babu wanda yake kokarin janye idonsa, ahankali ya motsa lips dinsa yace"Ina kwana" Kunyace ta kamata ta6oye kanta a jikinsa tace"nide gaskiya ka daina gaidani" "why?" "nice qarama" Murmushi yayi sannan yace"Ina miki kallon sarauniya tane,saboda haka dole zan baki wannan matsayin" Yana fadin haka taji ya 6alle mata huge din brar ta, cikin sauri ta kalleshi, yadora hannunsa akan lips dinta alamun tayi shiru,tana jinsa yamaida kansa cikin bargon ya rufe har zuwa qirjinta, kawai kanta ne a waje,bakinsa yadora akan wuyanta yana kissing dinta harya gangaro zuwa qasan wuyanta, ahankali tafara sakin numfashi kad'an kad'an,tanajin yanda yake lashe komai na qasan wuyanta, Mawahib da kanta yake waje tanajin saqon dayake isar mata batasan lokacin data lumshe idonta ba,ahankali ta motsa hannunta dake cikin bargo ta dorashi a kansa tariqe kansa da hannayenta duka biyu alamun tanajin dadin abinda yake mata kada yadaina,yanajin haka yayi mata wani irin Salo wanda tasa Mawahib sakin nishi me qarfi tareda shafa lallausar sumar kansa, batasan lokacin datake shafa masa kansa ba,abinda tasani shine tanajin wani irin yanayi me dadi wanda take fatan ace Yaya Captain yaci gaba dajiyar dasu wannan yanayin,yanajin yanda take shafa sumar sa cikin fitar hayyaci yasan cewa saqon nasa yana zuwa inda yadace,ahankali yasaka hannunsa guda daya yafara shafa cinyarta, zabura tayi tabude idonta tasauri sannan tafara kokarin dauke hannunsa daga kan cinyarta,ahankali yadena kissing dinta cikin muryar jin dadi yace"bari mana...." Kanta ta gyada masa badan ta yarda dashi ba,amma abun mamakin baiyi qoqarin yimata komai ba saboda yanason tagama sakin jikinta dashi,kawai shafa mata fararen cinyoyinta yake, hakan yasa taji hankalinta ya kwanta, ganin tayi shiru yasa yasake maida kansa cikin bargo sannan yaci gaba da bata horo(🙈) cikin wata irin murya tace"Yaya Captain..." Yana daga cikin bargon yace"um...." Kansa tasake rungume wa a qirjinta tasake cewa "Yaya Captain...." Jin kamar batasan tana kiran sunansa ba hakan yasa yafara yimata komai da sauri sauri,cikin wata irin murya wadda tayi kama data yar maye tace"wayyo Mamy...." Murmushi yasaki yana daga cikin bargon,ahankali yace"meyafaru?" cikin fitar hayyaci tace"please cigaba" Dariya ce taso kamashi, amma saiya yi shiru yamaida hankali kan abinda data umarceshi dashi,har yaji tasake rungume shi, sannan kuma jikinta yasaki alamun saqonsa yagama kar6uwa,ahankali yatsaya cak yadena abinda yake. Sannan yafuto da kansa daga cikin bargon yazuba mata ido,ahankali tabude idonta ta kalleshi cikin sauri ta6oye fuskarta a jikinsa. Murmushi yayi yace"saura ni" Zaro idonta tayi waje ta kalleshi,yadage mata girarsa guda daya yace"yes" Cikin shagwa6a tace"tota yaya" Yace"ta yanda namiki" Idonta tarufe tace"ba yanzu ba" "sai yaushe?" Kai tsaye tace"saimun koma Abuja" Gashin kanta yashafa yace"kinyi alqawari?" Tagyada masa kanta alamun tayi, wata irin ajiyar zuciya ya sauke sannan yace"muje muyi wanka" Cikin sauri tace"A a,zanyi adakina" tajuya ta kalli agogo taga shabiyu saura minti biyar, cikin sauri tace"innalillah Yaya Captain azahar tayi" Kallonsa yakai kan agogon dakin,cikin sauri yatashi yace"kai har shabiyu tayi?"(😂) Ahankali yayaye musu bargon, sannan yadauki brar ta yamaida mata, ya sunkuya yayi kissing breast dinta ahankali ta sauko daga gadon shikuma yatashi zai wuce toilet yace"kibar wayarki akusa dake please" Kanta tagyada masa cikin sauri tagyara dakin sannan ta fice bata bari ya futo daga toilet dinba,Addu'ah take aranta Allah yasa karta hadu da kowa,gani take gaba daya kamar kowa zaisan abinda sukayi, tunanin da tayi yau akwai aiki Mamy tatafi asbiti hakan yasa tadan kwantar da hankalin ta. Bataga kowa a compound ba, hakan yasa cikin sauri tawuce plat din Mamy tatura qofar tashiga, tana shiga falonsu taga Abbanta da Mamy a zaune afalon, wata irin kunya ta kamata taji kamar tajuya takoma aguje. Abba yayi murmushi yace"yanmata na antashi?" Cikin sauri ta girgiza kanta kuma takasa koda daga qafar ta ne tawuce dakin. Mamy ta kalleta ganin ta ras babu alamun rashin lafiya hakan yasa taji hankalin ta ya kwanta. Cikin rashin damuwa tace"kin tsaye kiwuce kije kiyi wanka kizo kici abinci" Ai kamar dama jira take cikin sauri tayi wuf tashige dakinta,Abba yayi murmushi yace"Ruqayya kenan,ai dazu Yaya yake cemin gobe zasu koma Abuja wai mijin nata yace yau zasu wuce shine yace yabarshi de zuwa gobe saisu tafi" Mamy tace"ai gara sutafi Alhaji,suje can su qarata,agabanmu ana rungume rungume idan aka hanasu tafiya ai zamuga abinda yafi haka" Abba yayi murmushi yace"toya za'ai" Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Bayan tayi wanka ta shirya qin futowa tayi,zamanta tayi adaki suna exchange messages itada Yaya Captain,shine yake fada mata yazo gaida su Mamy bai ganta ba,anan take sanar dashi tana cikin dakinta tana tunanin sa. Mamy da taji shiru Mawahib taqi futowa ta dauko abincin tabiyota dashi daki tace"tunda zaman daki ya aureki ga abincin nan" Bata Iya kallon Mamyn ba,saboda kunyar ta takeji,kawai abincin ta kar6a tafara ci. tun yamma Mamy take hada mata magunguna na qarin ni'ima wanda zai taimaka mata wajan rage radadi koda sunkoma Abuja. Da daddare tasata agaba saida taga tasha kala kalar magunguna masu kyau da inganci,sannan tayi mata fada sosai akan bin miji, ta kuma sata kullum idan sunkoma ta dinga cin fruit. Har dare tana tareda Mamy saida Mamy taga tagama hure mata kunne tsaf akan kula da Captain sannan tabarta tatafi dakinta da magungunan ta, tasaka su cikin jakar kayanta, tagama hada kayanta tsaf,sannna ta kwanta,tun safe data bar dakinsa bataga Yaya Captain ba,tasan yana can yana fama da mutane masu zuwa yimasa sannu da zuwa, uwa uba kuma abokinsa, amininsa, dan'uwan sa Yaya Ashraf Shima bazai bari surabuba, hakan yasa tayi baccinta cikin jin dadi tana tuna irin dadin dayasa taji yau dasafe.(🙈) Da Mamy da Mama Sadiya,da Momy kilishi,da Ashraf,da Nabiha,da Captain da Mawahib,gaba dayansu suka tafi Abujan zasu raka Amarya dakinta tareda duka kayan lefenta. Gidan Captain yau saiya zama kamar gidan biki,Nusaiba ma da taji labarin sunzo haka tasa Captain Habib yakawo ta gidan, tun safe tana gidan tareda su,saida azahar tatafi, Mawahib taji dadin zuwan gidan tareda su,itada Mama Sadiya da Mamy ne sukai girki, sannan suka gyara gidan tsaf, banda Nabiha saboda tayi nauyi. Atare sukaci abincin gaba dayansu,kana ganinsu zakasan cewa familyn yagama cika da farinciki,sai qarfe biyar na yamma jirgin su yatashi zuwa kano, Mawahib kawai aka bari a gidan, shikuma Captain yamusu rakiya Airport. Bai dawo gidanba saida yabiya ta asbiti yayiwa doctor bayanin halin dayake ciki, dakuma yanayin yanda kake ganin sperm dinsa,ya rubuta masa wasu magungunan,sannan ya siyo yadawo gida. Yana zuwa gidan yaji shiru kamar yanda yake ada,falon yayi tsaf ko'ina yana tashin qamshi,tana jiyo dirin motarsa daga sama tafuto daga dakinta cikin wani irin arnan kayan bacci wadda Sis Saudat takawo mata,komai na jikinta kana ganinsa,da gudu tasauko tazo tashige jikinsa, baisan lokacin daya saki ledar magungunan saba ya rungume ta yana sakin ajiyar zuciya, haqiqa sai yanzu ne yasan cewa shima Ana qaunar sa. Shiru sukai a tsaye rungume da juna,cikin rada yace"duk wanda yace zaizo kifada masa bakya nan..."(🙈) Wani irin kallon soyaiya tayi masa, sannan taja hannunsa tace" muje kaci abinci" Hannunsa ya qwace yadauketa cak, sannan yadauki magungunan sa yayi sama da'ita yace"ga babban abinci na" Cikin sauri tarufe fuskarta a qirjinsa,kai tsaye dakinsa yanufa da'ita,ya kwantar da'ita akan gadon, sannan yawuce toilet yayi wanka, wayarta ce a hannunta tana dannawa, tana ganinsa bayan ya futo yanufi fridge yadauko ruwa yabude maganinsa yasha, sannan yadauko man dazai shafa yanufi gadon dashi yabata yace"bissmillah" Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Kallan man tayi sannan ta kallashi, tayaya ne zata Iya shafa masa mai banda de neman magana irinna Yaya Captain? Kallonta yayi da idonsa suka qanqance yace"mekike jira ne?" Ahankali tasaka hannunta takashe wutar dakin,duhu ya mamaye dakin sannan tatashi ta matso jikinsa tafara shafa masa man a dantsan hannunsa,shiru yayi yanajin yanda yatsun hannunta suke sake birkita shi,sake zubo man tayi a hannunta zata shafa a qirjinsa yayi sauri ya fizge towel din jikinsa sannan yakai hannun nata kan cinyarsa yace"shafa anan" Babu musu tafara shafa masa ahankali, wani irin nishi Yasaki yafada kan gadon,tanajin yanda yake qoqarin Jan hannunta zuwa wani waje me girma na daban. Jikinta ne yafara karkarwa,ta kalleshi da sauri taga idonsa a lumshe gaba daya yasakar mata ragamar komai,hakan yasa gudun 6acin ransa tayi abinda yake buqata, lokaci daya taji Yasaki wani irin ihu,adede lokacin wayarsa tafara qara,kallon wayar tayi taga Hajiya kilishi ce take kira,ahankali ta dauka tareda bashi tace"Momy ce" Idonsa a lumshe yace"Momy.." Hajiya kilishi tace"Aryan kana jina? wallahi tallahi kabi yar mutane a sannu, banaga kanka yana rawaba idan kakashe musu yarinya kaima kasheka za'a yi,kadawo hankalinka ba Soja ka aura ba" Mawahib ganin idonsa a lumshe yanajin abinda Hajiya kilishi take fada hakan yasa tayi tunanin hankalinsa baya kanta,cikin wani irin Salo tasake zuba man a hannunta taci gaba da shafa masa daduka hannunta biyu,lokaci daya Captain Aryan ya qame. Hajiya kilishi data ji shiru tace"kana jina aiko?" Idonsa a lumshe daqyar yace"to Momy" Sannan yakashe wayar karta gane halin dayake ciki. Wulli yayi da wayar cikin jin dadi yace"Honey zaki kasheni faaaa" Yaja faaaa din dawani irin Salo,ganin abinda take masan yasamu kar6uwa hakan yasa tafara yimasa wani irin salo ita kanta batasan ta'iya ba,ta sunkuya ta dora bakinta a qirjinsa , tayi masa kamar yanda yayi mata agida. Ko minti biyu batayi da farawa ba yaji bazai jure ba,cikin sauri yasaka hannunsa yafarka rigar jikinta,ya birkitota tadawo qasansa, sannan yafara kissing dinta kamar mayunwacin zaki,ganin yanda ya birkice kamar bashi ba hakan yasa tafara tsorata dashi,musanman lokacin da taji yabuda cinyoyinta, cikin sauri tahade qafafunta, gabanta yana faduwa tatuna a zabar datasha a karonsu na farko,hawaye ya zubo daga idonta tasan cewa yauma bazai qyale taba,girgiza kanta tafara yi da sauri,cikin kuka tace"bazai iyu bafa...." Cikin wata irin murya mecike da buqata yafara kokarin shiga jikinta ta hanyar neman hanyarsa yace"inji waye bazai iyu ba?" Kuka tafara sosai,cikin sigar lallashi yashare mata hawayen idon nata amma yakasa cewa komai ba,ahankali yatura yashigeta da qyar,wani irin qara yasaki yayinda Mawahib ta kawar da kanta gefe tana tsiyayar da hawaye,sosai take jin bala'in zafi,kamar babu banbanci dana farkon,Captain kuwa yagama nutso ajikinta kokadan baisan tana wannan kukan ba,maganganu yake mata barkatai marasa kan gado,hakan ne yasake tabbatar mata baya cikin hayyacinsa,bata bari yaji kukan nata ba,saide hawayen nata duk ya jiqa fillon, yadade yana abu daya sannan yasamu nutsuwa, fuskarsa sharkaf da hawaye,ya rungume ta jikinsa yana kissing dinta,sake cusata yayi a jikinsa yanaji kamar yamaida ta cikin jikinsa. Idonsa ya lumshe sannan yace"Allah yayi miki Albarka" Ajiyar zuciya tayi duk da taji ajikinta,bata yarda yagane ba,batayi masa ihu da kwakwaro ba kamar na farko,tayi shiru duk da tanajin kamar ta mutu haka tayi shiru saide ruwan hawaye. Kanta tagyada masa alamun amsawa. Murmushi yayi yace"Allah yaqara miki...." Ta kalleshi, suka zubawa juna ido duk da duhun dakin, yayi murmushi yace "meyasa baki tambaye niba?" Ahankali tace"mezai qaramin?" Sunkuyawa yayi yadora bakinsa kan kunnanta cikin rad'a yace"Dadi..." Murmushi tasaki batace komai ba,yazuba mata ido yana ganin yanda murmushi yake mata kyau,yace"mekike yiwa murmushi?" kallonsa tayi tace"mezance Yaya Captain? bansan ta yanda zanyima bayanin murmushin dake kan fuska taba,abinda nasani inde kana tare dani zanci gaba yin wannan murmushin har qarshan rayuwata, naji dadin sakamin albarkar dakayi sosai, Allah yaqara maka lafiya kaci gaba da jiyar dani irin wannan yanayin kullum..."(🙈) wani irin murmushi yasaki me sauti,da alama yaji dadin maganar tata,Mawahib ta kalli yanda yake cikin walwala saboda maganar data masa,kuma tafadi hakan ne danyaji dadi amma bawai dantaji dadin abunba😳😂🤣 asalima banda azaba data kar6a babu abinda taji,tafijin dadin wasan sosai fiye da wannan abun. Saida yagama murmushin sannan ya kalleta cikin jin dadin maganar tata sannan yace"Allah ya shiryeki...." sannna cikin jin dadi yace"kinaso kenan?" Domin yaji dadi hakan yasa tadaga masa kanta alamun eh tanaso,kuma tanada tabbacin shima yanason maganar,shine yawani wayance wai Allah ya shiryeta(😂) Asuba tagari 'ya'yan Hajiya kilishi....🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼 Zaki turo 500 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/18, 5:57 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki sunyi bacci irin wanda suka dade basuyi me dadinsa ba,Mawahib baccin wahala take domin kuwa ba qaramin jin jiki tayi ba,yayinda Captain yayi baccinsa cikin kwanciyar hankali kuma me dadi. Kamar yanda yafada kafin su tafi yanason ya dauki hutu hakan ce ta kasance,babu inda yake zuwa koda yaushe suna manne da juna,ya shagwa6ata yanda ya kamata, yamaida ta kamar zinariya sai abinda tace, a yanda ta lura dashi shine kokadan babu daga qafa a al'amarinsa,safe rana dare duk lokacin data motsa masa haka zaiyi yadda yakeso da'ita, wannan dalilin yasa tarame,saide bayan sister Saudat tasake kawo musu ziyara hakan yasa tajata daki tacire kunya tafuto fili tayi mata fada tareda bayani filla filla akan hakan,taja hankalin ta akan cire tsoro takuma gargadeta akan saka abun aranta. Cikin ikon Allah datayi amfani da shawarar data bata saita ga canji,hakan yasa ta kwantar da hankalin ta,sukaci gaba da cin amarcinsu hankali kwance. A6angaren Captain yanaci gaba dashan magungunan sa,kuma yana ganin cigaba sosai,ita kanta Mawahib yaga sai wata qiba take hadawa ta musanman sakamakon yanda ta kwantar da hankalin ta. Tsawon sati biyar kenan suna amarci,kullum ana abu daya hakan yasa tafara sabawa dashi,uwa uba Yaya Captain din ba baya bane wajan Iya kula da mace,kokadan batada damuwar komai yanzu,fatanta daya Allah yabawa mijinta lafiya suma su samu Babynsu,yau shiryawa sukai cikin manyan kaya suka futo a asalin hausawan su, suka nufi jihar kebbi,wajan mahaifinta,shida kansa yaje Airport ya daukosu,tun ahanya yake jansu da fira sunata dariya shida Captain kamar ba surikinsa ba,kai tsaye gidansa ya wuce dasu hadadden gida mai tsananin kyau da qawa,Mawahib ta qarewa gidan kallo tana tunanin da yanzu Mamyn ta tana ciki, jikinta yayi sanyi,suka shiga ciki, zama sukai a kujera Abbanta ya kalleta yace"Ruqayya shiga kitchen ki dauko muku lemo kinsan baban naki shi kadai ne" Murmushi tayi, tatashi tacire mayafin jikinta tashiga kitchen din gidan ta ganshi tsaf babu abinda babu na buqata,ruwa da lemuka tafara kaiwa, itama ta zauna tafara shan lemon,tun tanashan lemo a hankali harta ware ta shanye gora daya,tasake daukan wani tafara sha,Alhaji Ma'aruf ko a jikinsa baima lura da'ita ba,yayinda Captain Aryan yake satar kallonta gabansa yana faduwa wanne irin shan lemo take haka?,danma gida sukazo,da'awani wajan ne cewa za'a yi ba lafiya ba(😂) Tunanin sa baigama yankewa ba yaga ta dauki gora ta uku,tanasha ta kalli babanta tace"Abba da wannan lemon zan tafi" Captain Aryan yazaro idonsa,(😳) Karfa tasa mahaifin ta yayi tunanin baya bata lemo agida. Cikin jin dadi Alhaji Ma'aruf yace"akwai a store ai Ruqayya,saiki tafi dashi, suna nan dayawa a store idan kin shiga kitchen zakiga wata qofa kibude akwai kayaiyaki aciki ki dauki duk abinda yamiki" Cikin sauri Captain Aryan yace"Abba ai akwai irinsa a Abuja, idan muka koma sai asiya,a gidan nede babu saboda bana siyo lemo me gas" Mawahib ta kalleshi tace"ni wannan nakeso,bana Abuja ba" Captain yabita da kallon mamaki,bata lura da irin kallon dayake mataba tatashi tawuce kitchen ko kallon inda Captain yake batayi ba,store din tashiga taga komai, sannna ta dauki tukunya ta wanke tadora musu abinci,jitayi tana sha'awar tuwo, hakan yasa tatuqa musu tuwon shinkafa da miyar ridi ta yaiyanka naman kaza aciki,tun daga falo suke jiyo tashin qamshin girkin. Kafin tagama aka kira sallar azahar,su Captain suka fita sallah ita kuma takawo musu abincin ta ajiye,sannan takoma tagyara kitchen din,tafuto tayi sallah tana azkar tana tunani meyasa tasha wannan lemo haka saikace wanda tayi kwana da kwanaki batasha ruwa ba? tashi tayi tacire mayafin jikinta bata jira su ba, tazuba wani uban tuwo tasaka miya, tafara ci,suna shigowa Abban yaga abincin data zuba yayi murmushi cikin ransa yana jin dadin yanda aure yayi albarka da alama tanada juna biyu,musanman daya ga tasake hada wata Uwar qiba ba kamar lokacin da sukaje gidanta ba shida abokinsa Alhaji Bala. Captain Aryan kuwa kawai kallonta yake, yasan cewa bazata Iya cinye wannan abincin ba,kawai shirme ne irin nata,yasan ko yankata za'a yi bazata Iya cinye waba,yazuba mata ido yana ganin yanda zata qare. Shine yazuba musu nasu shida Abban ta,suka faraci, Abbanta ya kalleta yace"Ruqayya waye ya koya miki girki ne, ko Maryam ce?" Murmushi tayi tace"A wajanta nakoya Abba" Jinjina kansa yayi tace"ai Maryam ta'iya girki sosai,tanada haquri da kawaici,lokacin datana gidannan nayi tunanin bude mata gidan abinci, to kuma Allah baiyi zamu zauna ba,mahaifiyata tayimin fada sosai akan rabuwa ta da Maryam,kafin Allah yayi mata rasuwa saboda dukansu acikin gidannan muke zaune kafin nasa a rushe shi, namaida shi ginan zamani" Mawahib tace"to Abba yanzu kai kadai kake zaune akwai tsaro ne a gidan?" Captain Aryan yajuya ya kalleta shima tambayar dayake son yimasa kenan,plate din gabanta ya kalla yaga wayam tacinye duka tuwon gabanta, lokaci daya yakasa 6oye mamakinsa har fuskar sa ta nuna. Alhaji Ma'aruf yace"ni kadai nake zaune,babu abinda yake faruwa ai unguwar akwai tsaro,akwai gidan wani kawunki acan cikin gari zamuje daku yanzu ku gaisa dashi,kamar Yaya yake awajena,idan nagaji da zaman nan Ina zuwa can nayi kwana biyu,shi kadai yarage min yanzu a dangin, duk sun rasu" Captain da Mawahib suka hada baki sukace "Allah yaji qansu" Ya amsa musu da "Ameen" Ya kalli Captain yace"anan zaku kwana ne?" Captain Aryan ya sosa kansa yace" a a Abba yau zamu wuce,jirgin qarfe biyar na yamma zamubi mukoma" Cikin gamsuwa Alhaji Ma'aruf yace"to bari in turawa Alhaji Bala text yazo muje na nuna muku gidan gonar Ruqayya,dakuma sauran kadarorinta, saina baka takardun katafi dasu" Cikin ladabi Captain Aryan ya amsa masa. Wajanda sukaci abinci tagyara,sannna tadawo falon ta zauna suna jiran zuwan Alhaji Bala,a wannan dan Zaman jiran bacci me dadi ya dauketa, saida Alhaji bala yazo sannna suka tasheta suka tafi. Sunje taga gidan kawun nata, matarsa tayi musu tar6a mai kyau,sunji dadin yanda tayi musu hidima takama Mawahib ta riqe kamar zata maidata ciki, daga nan sukaje sukaga gidan gona wanda yahada da shanu da kaji raguna wani yanki naciki kuma akayi shuke shuken kayan fruit. sukaje yanuna musu gonakinta wanda mahaifiyar sa tabata, dakuma filaye wanda shine yabata su,basu dawo gida ba sai qarfe hudu,suna zuwa sukai sallah, sannna sukai haramar tafiya. Sunfuto compound wata mata tashigo gidan aqalla zatakai shekara Arba'in, gaida su tayi, Abba ya kalleta cikin murmushi yace"Murjanatu kece a gidan yau?" Cikin ladabi tace"eh wallahi,naje gidan Anty ne shine tabani wannan saqon tace na kawowa Ruqayya" Cikin fara'ah Alhaji Ma'aruf yace"ikon Allah,itade bata gajiya harda wahala kuma?, toga Ruqayyan nan" Yafadi haka yana nuna mata Mawahib sannna ya kalli Captain Aryan yace"qanwar matar yayana ce,gidan damuka baro yanzu" ta qarasa wajan Mawahib tace"Amarya gashi,sai yaushe zaki dawo kimana kwanaki kuma?" Cikin jin dadi Mawahib tace" zan dawo insha Allahu" tace"to ga wayata sakamin number ki saimu dinga gaisawa" Mawahib ta kar6i wayar tasaka mata number sannan suka rabu cikin mutuntawa. Har Airport Alhaji Bala da Alhaji Ma'aruf suka kaisu Mawahib,sunyi sallama zasu rabu tajuya ta kalleshi tace"Abba" Cikin mamaki ya juyo yace"na'am" tadawo baya ta qaraso wajansa,Alhaji bala yayi murmushi yabasu waje, yayinda Captain ma yayi gaba yana jiranta,ta kalleshi cikin damuwa tace"Abba to yaushe zakayi aure?" Murmushi yayi yace"aure kuma Ruqayya? da girmana ai yanzu aure mun barwa Yara" Wani irin kallon shagwa6a tayi masa tace"Abba tobaga Anty murjanatu nanba,naga kamar batada aure" Ajiyar zuciya yasaki tace"eh murjanatu batada aure amma Ruqayya murjanatu ai bazata yarda ta aureni ba saboda namata tsufa" Cikin sauri tace"Abba dan Allah kafada mata" Murmushi yayi yace"to shikkenan tunda haka kikeso,zanje gidan kawun naki saimu yi magana da yayarta idan batada manemi sai ayi abinda kikeso" Cikin farinciki tace"to Abba nagode" Alhaji Ma'aruf yasake kallon cikin jikinta yace"to Ruqayya,Allah yakaiku lafiya,kidinga kula de kinji ko?" Kwata kwata bata fahimci meyake nufi da maganar sa taqarshe ba,kawai de ta amsa ne. Acikin jirgi ta dora kanta akan kafadar Captain suna zance kad'an kad'an har bacci ya dauketa,saida suka qarasa Abuja sannna ya daukota cak a hannunsa, lamarin daya bawa kowa mamaki,kuma babu damar tsegumi saboda fuskar Captain din a Captain dinta take(😎) Bayan sunyi wanka sun kwanta,Mawahib tashige jikinsa tana shafa bayansa ahankali,hancin ta yana yawo a fuskarsa,cikin mamaki ya kalleta yau kuma itace da kanta take neman abun? yabude baki zaiyi magana yaji tahade bakinsu,mamakinsa ya tsaya cak inda yaji itada kanta take masa komai,hakan yasa ya lumshe idonsa yanajin yanda take masa komai an maidashi dan gata. Cikin wata irin shaqaqqiyar yace"zaki Iya baki gaji ba?" Cikin muryar shauqi wanda ita kanta mamakin kanta take meyasa takejin wannan tsananin sha'awar bayan da bahaka take ba? meyasa takejin idan baiyi mata abinda takeso ba akwai matsala? kallonsa tayi cikin yanayin sha'awa tace"nide kayimin bangaji ba" Ahankali yadaga kansa sannan yace"no,tunda ke kika faramin saide kici gaba" Cikin sauri tadaga kanta sannna taci gaba da abinda take,Captain Aryan ya lumshe idonsa yanajin wani irin dadi yanda take masa komai,yasaba koda yaushe shine meyin komai yau kuma gashi yasamu zata masa tayaya ne zai yarda yayi wani abu?(🙈) nishinsa kawai kakeji adakin yana wani irin numfashi,jin zaiyi mata ihu yasa tarufe masa baki,sannan tamaida hankali kan abinda takeyi, itace take gudanar da komai,yayinda Captain yakejin kamar yamutu dan dadi,ganin tana abu ahankali yasa ya kwantar da'ita yaci gaba dayi cikin sauri,sai ihu yake yana kuka. Yayinda Mawahib tasakar masa jiki tana tayashi abinda yake,hakan ba qaramin dadi yamasa ba,jiyake yau tafita daban,jinta yake ta musanman saboda wani irin dadi data qara,hakan yasa bai tsaya Iya round daya ba, saida yayi nabiyu,anabiyun ma haka yaji irin dadin farko bata sauya ba,yayi tunanin zata masa shagwa6a kokuma mita tagaji, amma abun mamaki saiyaji shiru (🙊) Washegari tatashi babu ciwon komai,kai tsaye kitchen tawuce tayi musu tuwo,Captain ya shirya ya futo zaiyi breakfast yazauna yaga tafara zuba musu tuwo, ya kalleta yace"yau tuwo muka samu?" Tace"naji Ina sha'awar sane" Kansa ya gyada mata yaci tuwon daidai misali,yayinda Mawahib ta zauna tafaraci kamar ba gobe, kallonta yayi ya tattara duka nutsuwar sa akan ta yace"dama kinason tuwo haka amma bakya yi?" Cikin sauri ta kalleshi tace"ni wallahi banaso,shiyasa ma banta6a yiba, yanzun nede naji inason sa, may be danna dade banci bane" Ajiyar zuciya ya sauke tace"eh may be hakanne" Ya kalli agogon hannunsa yace"zan fita, zuwa yamma zan dawo,akwai abinda kikeso?" "A a, saika dawo" Bayan yafita sosai taci tuwon ta,ta dauko lemo me gas tasha sosai, ta kwanta afalon tana bacci cikin jin dadi,bata farkaba sai la'asar, cikin sauri tatashi ta kalli Agogo taga irin dadewar datayi tana bacci, afili tace"subhanallah,wanne irin bacci ne wannan?" Wayarta ta kalla taga yakirata har sau hudu,Nabiha tamata kira sau biyu,Mamy sau daya,cikin sauri tatashi tayi sallar azahar da la'asar, sannna ta wuce kitchen tasake dora musu tuwon semo miyar ku6ewa tasaka Jan naman Rago acikin miyar sosai. Captain baidawo gidan ba sai magrib,alokacin tagama komai tana shirin kiransu Mamy sai gashi yashigo,tana ganinsa tatafi da gudu ta rungume shi,cikin damuwa yace"Ina kikabar wayarki inata kira?" "bacci ne ya daukeni wallahi,Naga harda kiran Mamy da Nabiha, suma yanzu zan kirasu" daukar ta yayi cak suka qarasa kujera tana cikin jikinsa yace"Nabiha ce tahaihu,tasamu Baby boy,nasan shine abinda zasu fada miki,nima shina kira in sanar dake" Cikin sauri ta kalleshi fuskarta cikeda farinciki tace"dan Allah Yaya Captain?" Cikin sauri yadora hannunsa akan lips dinta yace"banason sunan nan,daga yau nayi cancel dinsa, asauya min wani" Murmushi tayi tashige cikin jikinsa,tasake rungume shi,sannan tafara kiran Nabiha,tana dauka cikin farinciki tace"Nabiha sannu" Nabiha tace"Mawahib Ina kikabar wayar inata kiranki, Baby Aryan yana Neman second Mom dinsa" Mawahib tace"wallahi Ina bacci Nabiha,yajikin naki? duk kuna lafiya?" Cikin farinciki tace" lafiyar mu kalau, kinganni agida,Ina dakin Mamy itace ta kar6i haihuwar tamin komai" Cikin farinciki tace"to Allah yaraya,kice inyi shirin zuwa Inga Sabon mijina, ashe sunan sa za'a saka" Nabiha tayi murmushi tace"Sweet yace shi sunan Yaya Captain zaisaka,dazu yagama cewa Mamy wai shima soja zai zama kamar Yaya Captain" Mawahib tayi dariya tace"kice nazama matar soja maman soja" Nabiha tace"kuma surukar soja insha Allah" Dariya sukayi dukansu sannan tabawa Mamy wayar suka gaisa,daga nan sama suka wuce ta taimaka masa yayi wanka, sannan suka sauko qasa zasuci abinci,yana sauya Channel tana zuba masa abincin, yajuyo yaga yanzun made tuwon tasake yi,ya kalleta baice komai ba suka faraci, tun zubin farko yace ya qoshi,Mawahib kuwa saida tasake zuba wani. Washegari dasafe yana zaune a dining ita kuma tana tsaye zata zuba masa abinci,yaga tafara zuba musu tuwo(🙆🏻‍♀️) Saiya ajiye wayarsa agefe yayi tagumi hannu bibbiyu yana kallonta, tagama zubawa ta kalleshi tace"yanaga kayi tagumi?" Cikin sanyin jiki yace"yauma tuwon muka samu?" kallon shagwa6a tayi masa tafara bubbuga qafafunta aqasa zata saki kuka, cikin sauri yace"a a, ya'isa haka shikkenan,zoki zauna, zanci" Zama tayi, babu musu yafara cin tuwon yace"yanzu honey mundawo rayuwar cin tuwo kenan?,danayi magana kifara kuka?" Bakinta taturo gaba tace" toni shinake so" sai hawaye, yana ganin hawaye a'idon ta yace"yaisa,shikkenan to kidaina kuka,taso nabaki tuwon dakaina" qin tashi tayi daga inda take,sai shine yatashi ya daukota ya d'orata akan cinyarsa, sannna yadebo tuwon da spoon yace"bude bakin nabaki" Wani irin hawaye ne yasake zubo mata tace"ni bazan ciba" Yace"meyasa?" Cikin shagwa6a tace"ni lemo zansha me gas,kuma duka na shanye na kitchen din yau babu wanda zansha" Idonsa ya lumshe sannan yabude yace"Honey banason kisaba dashan irin wannan lemukan,meyasa yau kike jin rigima ne?" Kuka tasake saki tace"Allah nide shinake so nasha" Tuwon daya debo a spoon ya ajiye sannan yakama fuskarta yariqe da hannunsa biyu, ya kalli yanda idonta yake tsiyayar da hawaye, ya sassauta murya yace"Honey...,meyake damunki ne?" Kanta ta girgiza masa alamun babu komai. cikin sigar lallashi yace"lemon kikeso kisha?" Kanta tadaga masa da sauri. Ahankali yace"inbaki nawa lemon zakisha?" Cikin rashin fahimta tadaga masa kanta. Yasaka hannu yagoge mata hawayen idonta,sannan ya sunkuyar da kansa qasa yadora lips dinsa akan nata,sannan yazura harshan sa cikin nata, cikin sauri takama tafara tsotsa,atare suka saki wani irin numfashi, yayinda Mawahib takejin wani irin dadi ta lumshe idonta, aka nemi kuka aka rasa. Basu Iya kai kansu dakiba, anan kujerar dining din akayi komai aka gama,Captain yaji tasake yin wani irin dadi fiyeda jiya,hakan yasa ya kalleta yaga har lokacin idonta a lumshe, yayi kokari yatashi ya dauketa suka wuce dakinsa,saida yasake yin wani akaro na biyu, sannan sukai wanka suka sauko qasa,bai koma dining dinba saida yafita ya lodo mata lemuka masu gas, sannan yadawo gidan sukaci tuwon tare. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 tun Captain yana complain akan tuwo harya dawo yadaina,saide yarasa gane kanta,kullum tuwo da lemo megas abun har tsoro yake bashi,saide inya gaji dacin tuwon yasha lemo ko madara da biscuit,amma inde Mawahib ce zata musu girki to tuwo ne, kuma yayi magana tafara yimasa kuka,abinda zai mata tayi shiru kuwa shine yajata a jikinsa ya jiyar da'ita dadi kamar yanda yasaba mata,saide wani lokacin yana mamakin yanda bataqin abun kokadan, ko zaiyi yakai sau biyar babu abinda zata ce, qarshe ma itace me taimaka masa,hakan yasa ya kwantar dakai yake kwasar dadinsa. Cikin lokaci qanqani yaga tasake hada wata uwar qiba,to amma ganin yanda take cin tuwo kullum babu qaqqautawa hakan yasa yayi tunanin may be tuwon ne yake sata take hada wannan qibar. Ranar sunan Nabiha shine kawai yaje, bai barta tajeba,agida akai taron suna inda yaro yaci sunan Aryan. A part din Mamy sukaci abinci shida Ashraf,sosai yazage yake cin abincin abun har mamaki yabawa Ashraf,shikuma Captain Aryan yasan cewa idan beci abincin bama idan yakoma yasan cewa tuwo ne, shiyasa yaci abincin sa sosai. Mejego tayi kyau sosai tashiga tafita yanda ya kamata,anyi musu pictures kamar ba gobe,Hajiya kilishi takafa ta tsare yaro yana hannunta sai nan nan take dashi,Nabiha tasan cewa kawai haifar lil Aryan tayi, amma raino da wankan sa da kula dashi duk suna hannun Mamy da Momy kilishi, basu bar Mama Sadiya tamata komai ba. Sai dare Captain Aryan yakoma gida tareda tarin kayaiyakin suna daya kawo mata,alokacin tana zaune afalo ta'idar da sallar isha'i kenan tana azkar,tana juyo qamshin turaren sa ta juya ta kalleshi tatashi da gudu tatafi zata rungume shi,rigar jikinta ya kalla wadda tayi mata kyau sosai anan yagane rigar daya siya mata a boutique ce yau tayi masa ado da'ita, cikin jin dadi yabude mata hannayen sa,saide kafin ta qarasa jiri ya debeta tazube awajan. Cikin sauri yasaki ledar hannunsa yadauketa yasaka ta a jikinsa yafara tatta6a fuskarta yace"Honey...,Honey" Yaji shiru bata amsa ba kuma fuskarta a rufe, cikin tashin hankali yasake ta6a fuskarta yace"Honey bude idonki" nanma yaji shiru, cikin tsananin damuwa ya dauketa cak, ya futo yasakata a mota sannan yanufi asbiti cikin wani irin gudu. (ga posting din safe Nan ayimin afwa yauba na yamma zan dan huta, nagode 🙏🏻) Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻[7/18, 10:14 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Asbitin dayake ganin likita nan yakaita,wata qwararriyar likita ta kar6eta, bayan taimakon gaggawa dasuka bata ta farfado,likitan ta dauki jininta da fitsarinta tatafi lab dashi. Captain dake zaune agefe yakama hannunta yariqe yace"bakyajin komai ko?" Kanta tagyada masa tace"banajin komai,dazun ma jiri kawai naji ya daukeni, sai dan zazza6i da nakeji" Hannun nata yayi kissing yace"sorry..., zakiji sauqi kinji?" Kanta tagyada masa alamun amsawa Sannan ya sunkuya yasake kissing goshinta, yafara shafa kanta ahankali. Likitan ce tashigo dakin tareda wani babban doctor, Captain Aryan yana ganinsa yatashi yabashi hannu suka gaisa, likitan ta kalleshi cikin farinciki tace"congratulation Captain,matarka tana daukeda juna biyu" Mawahib dake kwance ta zaro idonta waje, cikin ranta tace ciki? Cikin tsananin farinciki ya kalli doctor bakinsa a bude. Doctor yayi murmushi yasake bashi hannu yace"masha Allah magani yayi kyau,Congratulation" Cikin sauri ya girgiza kansa,wani irin hawaye yazubo daga idonsa,suna ganin haka suka fice daga dakin. Juyowa yayi ya kalleta sannan yayi sauri ya goge hawayen idonsa ya zauna agefen gadon yadora bakinsa akan lips dinta yasakar mata kiss,tanajin yanda hawayen sa yake d'iga akan fatar idonta, ahankali tadora hannayen ta duka biyun a kansa tafara shafa sumar kansa, cikin sigar lallashi tace"yaya Capt..." Cikin sauri ya rufe mata baki danashi yafara kissing dinta cikin nutsuwa,babu musu ta tafara maida masa martani,saida suka dauki lokaci me tsawo suna kissing junansu, sannan yazare bakinsa daga nata yace"nagode Honey,bansan da wacce Kalma zanyi amfani wajan gode miki ba, kingama min komai arayuwa,kinbani Kanki,rayuwarki,kulawar ki,bansan dame zan saka miki ba, kin zauna tare dani duk da kinsan cewa ba lalle ne kisamu Baby dani ba" yafadi haka yana sake zubar da hawaye. Cikin sauri ta goge masa fuskarsa sannan tace"kadena fadar haka,kaifa dan'uwana ne, kuma mijina,koda bazaka ta6a haihuwa ba zan kasance atare dakai har abada" Cikin sauri yadaga mata kansa, sannan yadauki wayarsa yakira Ashraf, yana dauka yace"Ash..." Ashraf yace"meyafaru kake kuka?" Cikin sauri yace"Mawahib she's pregnant..." Cikin tsananin murya Ashraf ya kalli Momy kilishi datake yiwa lil Aryan wanka yace"Momy Mawahib tasamu ciki" Hajiya kilishi ta ajiye lil Aryan tasaki wata irin gud'a,tafuto compound din gidan tana fadin"Alhamdulillah....,Allah yabawa Babana lafiya" Mamy da Mama Sadiya dasuke gyara kitchen saboda aikin suna da'aka yi, su naji mama Sadiya tafuto da sauri sunata farinciki, Mamy tayi murmushi batace komai ba, tana cikin aikin taga saqon Captain yashigo yana fada mata Mawahib tasamu ciki, wani murmushin tasake yi ta girgiza kanta tace"Allah ya sauketa lafiya" tafuto daga kitchen din bayan ta qarasa aikin datake,anan ta tarar harda su Alqali a tsaye a compound din kowa yana maimaita magana daya. Wuce su tazo yi Hajiya kilishi tace"Maryam dannaki fa babu zaman lafiya yakusa zama uba" Mamy tayi murmushi tace"yaturomin text ya fadamin Yaya,Allah yasauketa lafiya" Hajiya kilishi tace"Amin ya Allah,ai sai yakawo ta gida idan tagama laulayin cikin saita koma" Ta kalli Ashraf yace"kiramin shi" Alqali yayi murmushi yace"dakin barsu ai kilishi,shima zai Iya kulawa da'ita" Cikin sauri Hajiya kilishi tace "a a Alhaji,Nabiha ma abinda yasa bance akawo taba saboda akusa take, amma wannan idan wani abu yasameta kafin muje ai komai yagama lalacewa" Ashraf yabata wayar bayan Aryan yadauka, cikin farinciki yace"Ash..." Cikin sauri Hajiya kilishi tace"nice Aryan,kanajina ko? kadauko Mawahib kakawo ta gida idan tagama warkewa saiku koma" Gabansa ne yafadi yace"Momy gida kuma?,amma Momy she's fine fa" Ya qarasa maganar kamar zai fashe da kuka. Hajiya kilishi tace"Aryan haquri fa zakayi,laulayin ciki ai sai mace yar'uwarta,idan tanason dan abun sha'awa na marmari anan duk zamuyi mata koba hakaba?" Cikin damuwa yace"Momy tuwo tafi so sai lemo,anan ma tanayi" "tana laulayin ciki tana girki,tana kula dakai bazai iyuba,kaji abinda nafada ma" ta qarasa maganar tana kashe wayarta. Dafe kansa yayi da hannunsa yana salati cikin ransa, tayaya zai Iya rayuwa babu Honey? har suka dawo gida jikinsa yana sanyaye,kasancewar dare yayi hakan yasa bata lura da yanayin dayake ciki sosai ba,sai washegari data gama bacci ta sauko qasa,ta ganshi ya zauna yana tunani,cikin jikinsa ta shige babu musu yafara shafa gadon bayanta. Cikin kulawa yace"Honey kin tashi?" Kanta tadaga masa sannan tasaka hannunta tadora akan kumatunsa guda daya tace"Baby meyake damunka?" Cikin damuwa ya kalleta"Momy ce tace saina kaiki gida" "gida kuma?," Kansa yagyada mata,bakinta taturo gaba tace"Gaskiya nide Baby um um,to tayaya zan dinga bacci bayan bakanan?"(🙈) tafadi maganar cikin 6oye abinda yake ranta, saboda tafi son koda yaushe yana cikin yiwa shukarsa bayi. maganar tata ta bashi dariya hakan yasa yayi murmushi,sai yanzu yagane dalilin dayasa takesan kasancewa dashi a kowanne lokaci,idan kuwa hakane yaji dadin abinda cikin nan yasata,Babynsa na cikinta ya kyauta wa babansa,haka kuma sai yanzu ne yasan dalilin cin tuwon ta. yariqe fuskarta yace"toya zamuyi?mekikeso ayi yanzu?" Cikin shagwa6a ta kalleshi"nide gaskiya saide muzauna acan hardakai" Cikin sauri yabude bakinsa sannan yasaka dariya yace"Honey? ashe kuwa za'a samu matsala,kinsan meyasa nake cemiki Honey?" Cikin sauri ta girgiza masa kanta. Yadora kansa a kunnanta yace"saboda you're so sweet" Cikin sauri tarufe fuskarta cikin kunya. yadago kanta yace"zan nemi excuse idan anbarni saimu tafi gaba daya ko?" Cikin sauri ta daga masa kai cikeda murna tasake rungume shi. tunda Hajiya kilishi tayi masa maganar zuwan Mawahib take zuba ido taga shiru bai kawo taba har tsawon sati daya,acikin sati dayan daya qara kuwa banda shagwa6a Mawahib babu abinda yake, kasancewar itama batason tafiyar hakan yasa yayi biris da maganar Momy Kilishi,kawai sha'anin su sukeyi,Koda yaushe yana jiyar da'ita dadin datake so, saide duk lokacin dazatasha fruit kokuma wani magani shima bashi take yanasha duk da baisan na menene ba, shi kansa bayason tafiyar ta saboda shi kadai yasan meyake ji ajikinta,jiyake kamar zai rabu dawani sashin jiki nasa. Saida sukai kwana goma bayan maganar Hajiya kilishi sannan suka shirya suka taho gida,ranar da sukazo part dinta suka fara zuwa,abinci ne agabansu ta zuba musu sunaci,Captain Aryan de sosai yakecin abincin sa,Mawahib kuwa kad'an takeci kana gani kasan batason abincin. Hajiya kilishi ta kalleta tace"meyasa bakyacin abincin ne Mawahib ko bakya so?" Cikin sauri tace"Momy cheese nakeso" Cikin sauri Captain Aryan ya juya ya kalleta,cikin ransa yace yau kuma? Mamy ce tayi sallama tashigo falon dawowar ta Kenan daga wajan aiki,tana ganin Mawahib tayi turus ta kalli hajiya kilishi tace"yaya yanaganta kalau kamar bame laulayi ba?naga tahada uwar qiba" Hajiya kilishi tace"irin laulayina takeyi ai,nima lokacin danake laulayin su Ashraf kalau nake,zanci abinci na inqoshi,saide za6e, banida aiki saide inta za6ar abubuwa Inaci na kwadayi,itama gashinan yanzu daga zuwansu tace cheese takeso" Mamy tayi murmushi tace"to Allah yaraba lafiya,bari insa driver ya siyo mata" tajuya tafita,bayan sungama cin abincin zama sukayi Captain Aryan yadauki wayarsa yatura mata saqo, tagani tayi murmushi itama tamasa replay. Suna musayar saqo Mamy tadawo da nbabbar ledar cheese gaba dayanta,Mawahib taja ledar tabude, sannan ta dauko guda daya tafara ci. Captain Aryan yace mata "danbani" Hajiya kilishi tace"karki bashi,yanzu haka a Abujan ma komai qwace mata kake kanaci" Kansa ya sosa yayi shiru. Mamy tayi dariya yace"Haba Yaya,yana qwace mata abunta shine zatayi wannan qibar? gashinan tana nema takamoni jiki" Ashraf ne yashigo falon cikin farinciki yabashi hannu suka tafa yace"Boy kun qaraso kenan" Captain Aryan yace"munzo tun dazu,Ina kabar wayar taka Ina kiranka baka daukaba" Qyafta masa ido yayi,sannan yace"banga kiranba" Captain Aryan yayi murmushi yasan cewa yanzu haka yana tareda matarsa,kuma hakanne domin kuwa yanacan dakin Mawahib inda Nabiha take zaune kafin ta zubar da wanka. Zama yayi yafaracin abincin da suka rage, Mawahib ta gaida shi ya amsa,ya kalli Captain Aryan yace"amma zaka dade ko?" Cikin sauri yace"no,da daddare zan wuce,zanbi jirgin qarfe takwas,na tambayesu amma babu damar hakan, akwai ayyuka dayawa" Fira sukaci gaba dayi cikin farinciki, sannan Mamy tatafi part dinta,yayinda Hajiya kilishi taketa kallon Mawahib yanda takecin cheese kamar ba gobe,tatuna lokacin datake dauke da cikin su Ashraf haka Alqali zai sata agaba ya dinga kallonta tana faman cin gyada,ko ridi,saide duk lokacin data tuno baya tana sake jinjina wa irin qoqarin da Alqali yayi mata alokacin, saboda cikin yazo mata da jaraba,kullum suna daki itada Alqali suna abu daya,dasafe kafin yatafi aiki saiya yi mata zai fita,haka za'a dinga kiransa a kotu ana sanar dashi masu kawo qarafa suna jira(🙈). Tasaki ajiyar zuciya tana fatan ace Mawahib nata cikin baisa mata wannan jarabar ba,saida taci cheese kusan guda biyar, sannan ta goge bakinta,ta dauke cheese zatakai kitchen din Hajiya kilishi ta kalli Ashraf da Aryan tace"bazakuci cheesenf ba?" Ashraf yayi murmushi yace"A a,ci abinki Mawahib" Hajiya kilishi tace"Ashraf kam nasan dama bazaici ba, amma shi de wannan dayan zaici, bashi qwaya daya kikai kitchen ki ajiye kayan ki" Dariya Mawahib tayi ta dauki qwaya daya jal tabawa Captain Aryan,ganin qwaya dayan tabashi yasa ya harareta. tana ganin hararar dayake mata tafara qoqarin maida abunta cikin leda(😂) yana ganin haka yayi sauri ya qwace,daga nan suka fita shida Ashraf. Itama bayan tafuto daga kitchen din part din Mamy tawuce,tana zuwa tashige dakinta da sauri tadauki Babyn Nabiha kyakykywan yaro kamar mahaifinsa, kankana Nabiha take Sha itama tasaka hannu sunasha, tana daukar yaron photo da wayarta, daga nan fira ta 6alle aka fara bawa Mawahib labarin haihuwar,kasancewar taga Nabiha hakan yasa bataji kewar Yaya Captain sosai ba,sai dare wajan qarfe bakwai da rabi yazo yayi sallama da kowa sannan yawuce dakinsa yakirata,daukan lil Aryan tayi suka tafi Nabiha tana mata tsiya, tana zuwa dakin ya rungume su itada Babyn, sannan yafara shafa cikinta yace"yaushe nima zaki bani nawa?" Cikin sauri tadora hannunta akan nasa hannun dayake cikinta tace"kwanan nan,zan haifo ma mekama dakai kamar lil Aryan" Cikin sauri yace"no, nafison me kama dake" yafadi haka yana kar6ar yaron daga hannunta, ya kwantar dashi akan gado sannan yadora goshinsa akan nata,yayinda hannunsa yake matsa hips dinta yace"zan tafi" Kanta ta gyada masa tace"tosai yaushe?" Cikin damuwa yace"duk lokacin dakikaji kinason ganina kimin waya kawai" Cikin sanyin jiki tagyada masa kanta. Hips dinta yasake shafawa cikin shaqewar murya yace"wannan abun meyasa kullum yake sake bajewa ne?" Idonta ta lumshe tanajin dadin yanda yake mata,cikin shagwa6a tace"bakaine kasa yayi hakan ba,gashinan kasa Mamy tana cewa nakusa kamota" Murmushi yayi yatura hannunsa cikin rigarta yaciro nashanunta guda daya yafara sha ahankali, cikin sauri tasake lumshe idonta ta riqe kansa tana shafawa,cikin jin dadi tadago kansa tace"Baby bakasha dayanba"(🙈) Cikin wani irin sauri yasake ciro dayan shima yadora harshansa akai yanasha,lokaci daya tsaiwar tafara gagararsu. Adede lokacin Ashraf yafara kiran wayarsa,cikin wani irin yanayi yacire bakinsa, ahankali tamaida su cikin rigarta, sannan ta dauko Aryan suka futo hannunsa cikin nata,saide yakasa cemata komai saboda yarasa meyake masa dadi, har mota tarakashi, sannan tadawo gida. Da daddare tanajin yanda Nabiha da Babyn ta suke bacci cikin kwanciyar hankali, amma ita takasa baccin,sai juyi take tana tunanin mijinta, har aka kira sallar asuba idonta biyu, saida suka idar da sallah sannan ta kwanta tafara bacci, baccin daya dauketa tsawon lokaci tanayi. Tana tashi Hajiya kilishi takawo mata farfesun kayan ciki itada Nabiha,ta kalli Mawahib tace"ko akwai abinda kikeso kuma?" Ta kalli hajiya kilishi tace"saide tuwo Momy" Cikin sauri tace"to Sadiya tana kitchen bari insa tayi miki,kefa Nabiha?" Nabiha tace" a a Momy banason komai" Tace"to shikkenan" tajuya tafita,Nabiha ta kalli Mawahib suka hada ido tace"ni Nabiha yau ninake ganin ikon Allah, wai Momy kilishi ce take shagwa6a mu haka" Mawahib tayi dariya tace"ikon Allah din kenan" Bayan angama tuwon part din Hajiya kilishi takoma taci, anan ta wuni Hajiya kilishi tana mata gata iri iri sai abinda takeso take kawo mata, Alqali yana ganin yanayin zaman nasu, sosai yakejin dadin hakan aransa. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Mamy tana kula da Nabiha yanda ya kamata,da kudinta take siyan kayan gyara tana bata saboda takoma dakin mijinta tsaf babu raini, duk wani abu daya shafi maganin mata idan Mamy tabawa Nabiha tare suke sha da Mawahib,Mamy tana fita Mawahib zata dauka itama tasha,azaman da tayi tsawon sati daya kullum suna cikin waya da Yaya Captain, haka zata shige dakin Hajiya kilishi su dinga wayarsu,chatting kuwa duk dare suna tare a online tana yaudarar sa da salonta najan hankali wanda hakan zaisa ta janye hankalinsa daga kallon wasu matan. Da gaske Hajiya kilishi take kulawa da'ita, ita kanta Mawahib sai yanzu ne tasan cewa gida yafi dadi saboda yanda da tayi wani motsi Hajiya kilishi zata ce koda abinda takeso babu abinda take nema tarasa, sai abu daya kewar mijinta,wanda yake rikice mata awaya kamar qaramin yaro saita 6ata lokaci wajan lallashi. Alhaji khaleed da Alhaji Isah dakuma Alqali gaba dayansu babu wanda baya jin dadin irin kulawar da Hajiya kilishi take bawa Mawahib, kokadan bata laulayin komai saide dan ciwon kai ko zazza6i wanda baza'a rasaba. Daqyar ya'iya yin sati uku a daddafe, da yamma suna zaune a compound kamar yanda al'adar gidan take watarana, sai ganinsa sukayi shida Ashraf wanda shima yatsaya a rivers tsawon sati daya,saiya biya masa suka taho tare, Mawahib ta baje a zaune sai shan kankana takeyi kamar ba gobe,ganinsu Mamy da Hajiya kilishi ne yasa takasa rungume shi, shima kallonta yake qasa-qasa idonsa akan cikinta wanda yafuto sosai girmansa yawuce watanninsa,dakinsa yawuce bayan sun gaisa Mawahib tayi shiru tana so tatashi,kuma tana kunya(😂) Mamy tanaso tace mata tatashi ta bishi ko yana buqatar wani abu,amma tana tsoron laifi awajan Hajiya kilishi,mama Sadiya tayi murmushi ganin yanda Ashraf yasaka hannu ya dauki lil Aryan yawuce dashi falon Mamy yajuyo ya kalli Nabiha yace"Ina Abinci?" baijira amsar taba yayi gaba, ma'ana tabiyo shi(😂) Hajiya kilishi ta kalli Mawahib tace"ku yaran zamani kun sangarce miji zai dawo bazakubi bayansaba saide yanemi abinci da kansa, ya nemi ruwan wanka da kansa, bazaku kama mazajenku ku riqe hannu bibbiyu ba sai wata ta qwace muku shi kudinga kishin is'ka,kuje kubasu abinda suke buqata mana" Mawahib tasaka tafin hannunta aqasa sannan tafara qoqarin tashi kamar yanda masu ciki sukeyi,Nabiha ma tatashi tayi kitchen,basu ce mata uffan ba,batasan cewa suma suna son ganin mazajensu ba ganin boss kilishi tana wajan ne yasa kowa yayi fuska(😂) Saida taga shigar Mawahib dakin Captain taga shigar Nabiha dakin Mamy sannan tasaki ajiyar tace"bari intafi dakina nahuta nima,duniya juyi juyi kahaifi yaro acikinka amma yau shine yake shigewa daki da mace wai har ya girma,shi Ashraf kokunyata babu ya kalli matar wai babu abinci?,babu abinci ko babu lokacin sa?"(😂) Mamy da Mama Sadiya sukai dariya, tace"yo haka yake nufi mana" Daga nan tawuce tayi falon ta. Mama Sadiya da Mamy suma suka wuce part din Mama Sadiya. Nabiha tana shiga Yaya Ashraf yace"kuma har sati daya bana nan shine bazaki shigo da wuri ba?" Cikin shagwa6a ta kalleshi "Sweet Momy tana wajan fa" Ajiye Aryan yayi ya fuzgota jikinsa yace"aitasan nadawo" Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 ****** Mawahib kuwa tana shiga dakin ta ganshi yana zagaye dakin,juyowa yayi ya kalleta yace"Honey kode bakiyi kewata bane? meyasa bazaki taho ki rungume niba?"(😳) Murmushi tayi tashige cikin jikinsa, ahankali yasaka hannunsa ya rungume ta,yayinda hannunsa yake shafa cikinta. Mawahib tasaki wata irin ajiyar zuciya tace"sannu da zuwa" Idonsa ya lumshe yana shafa cikin yace"Baby na yasake girma sosai Honey,kuma tauri,me kike bashi?" Murmushi tayi tadago kanta ta kalleshi tace"danma babansa baya nan ne,dayafi haka girma" Cikin jin dadi yace"serious?" Kanta tadaga masa sannan tace"zauna nabaka abinci nasan kanajin yunwa, ko wanka zaka fara?" Cikin shagwa6a yace"Honey wanne abinci? ai kece abincin yau"(🙈) Murmushi tayi tace"kasamu" "da gaske?" Tace"sosai" Yace"muje inyi wanka to" Babu musu taja hannunsa zuwa toilet. Tun a toilet yaso sufara gudanar da harka taqi yarda saboda tasan yanda yake idan tafiya tayi nisa ya dinga surutai da ihu kenan, kuma tasan cewa yanzu kowa zai Iya jinsa,hakan yasa taqi yarda sai zillewa take daqyar yatsaya akai wankan suka futo,abinci tabashi yaci adede lokacin yakira Ashraf suka fice sallar magrib saboda muddin zai sata agabansa yana kallonta to za'a yi abinda bai kamata ba. Itama part din Mamy tawuce,anan ta tarar da Nabiha tana tunani, zama tayi akusa da'ita tace"Nabiha lafiya?, tunanin me kike?" Cikin damuwa tace"Mawahib Ina tausayin Yaya Ashraf wallahi,yanzu fa kuka yagama,inaso na qare wankan nan mu koma gidanmu,yayi yayi dani naqi yarda,yanzu muna part dinku, ga Mamy, ga Abba,sukuma maza babu ruwansu idan zan yarda sai muzo muna jin kunyar iyayenmu daga baya,Ina bakin qoqari na wajan yimasa yan dabaru to yacemin hakan baima sa ba, narasa yanda zanyi" Mawahib tasaki ajiyar zuciya tace"to Nabiha ki amince masa mana tunda kinada tsarki kawai wankan ne baku gamaba,sannan hakan ba laifi bane awajan Allah,laifin shine yaje yakai kansa wajan wata" "Mawahib to ai ba'a gidanmu muke ba,murasa inda zamuyi wannan abun sai acikin gidan iyayenmu?aida nauyi" Mawahib tayi wani murmushi mai ciwo,tace"to Nabiha ni ince me?nida yamin abinda kowa yasani, babu wanda baisan meyafaru dani ba acikin gidannan" "Mawahib aiba acikin part din daya daga cikin iyayenmu kukayi ba, a dakinsu ne,kuma ni yanda naji a zabar haihuwa ma Mawahib bazan yarda na koma abun nan da wuri ba" Mawahib tace"to saiki dinga lallashinsa harku koma gidan,ai danma kin kusa qare wankan,dasauqi" haka suka dinga tattauna maganar daga baya suka tashi suka gabatar da sallah, bayan sallar isha'i Mawahib tayi shirin kwanciya ta kwanta a gadon,Nabiha ta kalleta tace"Amma de tafiya zakiyi ko?" Mawahib tace"ina zanje? rabu dashi babu inda zanje, kwanciya ta zanyi" Nabiha tayi murmushi tace"rufamin asiri karkisa Yaya Captain yazo dakin nan cikin dare,kije wallahi nasan yana can yana zuba idon ganin ki" Kafin Mawahib tayi magana kuwa yakirata,tadauka tana sauraren sa tana murmushi da alama wani abun farinciki take saurara daga wajansa. Wayar ta ajiye takalli Nabiha tace"saida safe" Nabiha ta kwashe da dariya tace"nida nasani,nima bari nakira Yaya Ashraf nasan fishi yake dani saboda abunda nahanashi dazu" Mawahib tayi mata saida safe tafice. Tana zuwa dakin nasa ta tarar dashi yana waya,kai tsaye gadon ta haye ta kwanta tareda lumshe idonta. Saida yagama wayar sannan ya qaraso gadon shima ya kwanta,yajata jikinsa ya rungume ta yace"bani labari" Kwanciyar ta tagyara tafara bashi labarin yanda tayi kewar sa, da yanda take kasa bacci,da yanda Momy kilishi take kulawa da'ita. Yayi shiru yazuba mata ido yana kallon qaramin bakinta wanda take juyashi ahankali kamar karta daina maganar. Bayan tagama bashi labarin shima yabata nasa,da yanda yakejin gidan nasu yamasa fadi saboda bata ciki,dakuma kewar tuwon ta(😂) Dariya suka saki gaba dayansu, tayi wani irin fari da idonta sannan tace"shikkenan?" Kansa ya girgiza mata yanayin idonsa yana sauyawa Izuwa ja,banda qanqancewa dayake. hannunta tadora akan wuyansa ya kasance kansa yana cikin tsakanin hannunta, sannan tace" to fadamin sai me kayi kewa bayan girki?" Hannunsa yadora akan cikinta yashafa cikin sannan yace"nayi kewar Babyna" Murmushi tayi tace"tosaime kuma?" Idonsa ya lumshe yabude shi sannan ya kalli qwayar idonta yaqi magana,sannu ahankali yafara yin qasa da hannunsa, har yakai hannunsa zuwa wani waje me girma cikin shaqaqqiyar murya yace"sai nan..." wani irin numfashi suka saki atare,cikin wani irin yanayi tace"sai in..." kafin tagama cewa sai Ina,yadora bakinsa acikin nata, wata irin soyaiya suka fara gudanar wa wadda tasa hankalin kowannen su yabar jikinsa,kowa kokari yake yaga ya birge dan'uwan sa, kasancewar andade ba'a hadu ba, gakuma abubuwan data sake Sha awajan Nabiha,hakan yasa taqara yimasa wani irin mugun dadi wanda yasa yafara sakin nishi me qarfi,Mawahib kuwa batasan yanayi ba,ita kanta hankalin ta baya jikinta, sai yanzu ne tasan cewa abaya Yaya Captain yafita jin dadi shiyasa take samun damar datake Iya toshe masa baki saboda kar mutane su jisu,kwata kwata yau takasa daga hannun tama bare ta'iya rufe masa bakin,hakan yasa gaba dayansu tunaninsu ya gudu,hayyacinsu ya gudu,suke sakin wani irin ihu a gidan kanaji zakasan cewa ihun jin dadi suke.(🙈) Hajiya kilishi da part dinta yafi kusa dasu ahankali tabude idonta tatashi ta zauna tana tunanin ihun menene wannan? Ahankali ta zuro qafafunta waje tafuto falon sannan tabude qofar falon ahankali,anan taji inda ihun yake futowa,gabanta ne yafadi,dama yaran nan ne? wasu irin maganganu taji Mawahib tana saki hakan yasake tabbatar mata cewa jin dadi ne yasa take wannan maganar,kenan ta tabbata de gaba daya irin laulayinta Mawahib take yi,domin kuwa ko itama alokacin dan Alhaji khaleed da Alhaji Isah basu yi aure bane basu cika zama agidan ba shiyasa basuji kunya a'idonsu ba,ahankali tasaki ajiyar zuciya takoma daki ta kwanta. har tsawon awa daya Hajiya kilishi bata daina jiyo ihunsu ba, ahankali tafara tashin Alqali,yatashi ya kalleta yace"Kilishi lafiya?" "Alhaji yaran nanfa sun hanani bacci wallahi,kamar wanda suka shekara basu hadu ba? idan iyayen yarinyar nan suka jiyo su tayaya Aryan zai Iya kallonsu da safe?" Alqali yace"saboda ne zai kasa kallonsu bayan kece kika riqe masa mata? ni narasa gane dalilin ki nayin hakan kilishi, yarinyar nan tunda ba jinya take ba kibarta takoma dakin mijinta,ai yayi kokari sati uku babu mace Ina kikeso yaje? yanzu gashi yakasa haquri daga shi har ita suna iface iface,ki barsu su tafi kawai shima kansa abinda yake cikin ta zaifi samun isasshiyar lafiya" Hajiya kilishi ta jinjina kanta tace"aikam dole su tafi, wannan abun kunya har Ina?" Alqali yayi murmushi ya kwanta yaci gaba da baccinsa. Hajiya kilishi kuwa saida tarufe kunnanta sannan ta'iya bacci. Washegari a part din Hajiya kilishi suke breakfast dukansu da Mawahib da Captain Aryan da Alqali. Hajiya kilishi ta Kalle su taga dukansu sai walwala suke,ta tabbatar tashiga haqqin yaran dayawa, ta kalli Captain Aryan tace"Babana yaushe zaka koma ne?" Kansa ya sosa yace"bansani ba Momy" Alqali yayi murmushi yaci gaba dashan tea dinsa ganin da gaske de kilishi ta dage. Hajiya kilishi tace"aida bakazo jiya bama cikin wannan satin dama nayi niyyar saka Ashraf yakai maka Mawahib,amma yanzu tunda kazo ai saiku shirya anjima kutafi ko?" Cikin sauri suka kalleta gaba dayansu, Mawahib tayi qasa da kanta cikin kunya, tasan dakin Momy kusa yake da dakinsu Yaya Captain to kode Momy tajiyo ihunsu jiya? Captain Aryan yace"Momy yau kuma? da wuri haka?" Hajiya kilishi ta ajiye cup din hannunta ta kalleshi tace"emana,zaman ai ya'isa haka Babana,saiku shirya anjima kutafi" Kafadarsa yadaga cikin rashin damuwa yace"to Momy" Mutara zuwa gobe 🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/19, 8:13 PM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 dubun godia ga members na Mawahib paid group 💯 Ina qaunar ku har cikin raina ❤️ Mawahib tarigashi gamawa, wayarta ta dauka tatura masa saqo, sannan ta kawar da kanta kamar ba'ita ce taturo masa saqon ba, dayake wayar tasa tana ajiye agabansa saqon yana shigowa Captain ya karanta "Momy fa tajimu yau" Cak yaja yatsaya da taunar abincin dayake, kansa yana qasa ahankali yadago Iya idonsa ya kalli Momy kilishi, cikin sauri yadauki tissue yagoge bakinsa sannan yadan sosa kansa yatashi yabar dining din yadawo falo yazauna a kujera ,yana qoqarin yimata replay, itama tana ganin yatashi tatashi zata bar wajan, Hajiya kilishi tace"ina zakije? zauna ki qara bake kadai bace " Badan tasoba ta zauna taqara dan kadan, sannan tawuce part dinsu tana kallon gefen da Yaya Captain ya zauna hankalinsa yana kan waya, tana futowa daga part din kuwa taga replay dinsa" da gaske kike tajimu?" Cikin sauri tamaida masa da amsa," tunda kaji haka nasan tajimu wallahi" Cikin sauri yace"innalillah toki hada kayan ki mubar musu gidansu" Murmushi Mawahib tayi ganin irin amsar daya bata, sannan tawuce part dinsu. Da yamma duka mutanan gidan suka futo za'a musu rakiya,Mawahib tana riqeda Aryan a hannunta, yayinda Captain Aryan yadauko mata jakar kayanta, Ashraf da Nabiha ma sun futo, amma shi Ashraf zai musu rakiya zuwa Airport,gaba dayansu suna cikin walwala da farinciki adede lokacin Asalamiyya tashigo gidan. Mawahib tana ganinta ta dauke kanta tafara yiwa Aryan dake hannunta wasa. Asalamiyya tana ganin Ashraf da Aryan ta tabbatar Captain yana gida kenan,Hajiya kilishi tace"Asalamiyya yau kece agidan namu?" Cikin sauri Captain Yajuya ya kalleta saboda dama baisan taba, Mawahib tadaga ido ta kalleshi taga yana kallon Asalamiyya cikin haushi tadauke kanta,Captain Aryan kuwa qarewa Asalamiyya kallo yayi yana mamakin nacin datake masa awaya kwanaki. Yasaki ajiyar zuciya sannan ya dauke kansa ya kalli Mawahib,harara ta watsa masa yayinda tayi kicin kicin da fuskarta tayi gaba. Mamy tabi Mawahib da kallo tayi murmushi cikin ranta tana fadin yau mata suna Kishi... Asalamiyya tayi murmushi sannan ta kalli hajiya kilishi tace"Dama zuwa nayi na gaishe ki, ashe su Captain Aryan suna nan, aiban saniba danazo mun gaisa" Hajiya kilishi tace"Aryan baya nan shima jiya yazo, yanzu hakama tafiya zasuyi, ya samari suna Nan kalau ko?" Asalamiyya tayi murmushi cikin kunya tasaci kallon Captain Aryan sannan tace" ai babu" Hajiya kilishi yace"Allah sarki, kinsan komai ai lokaci ne, kema Allah yabaki nagari Kisamu saurayi kiyi aurenki bame mata ba,ai komai yanada lokaci, da aure da mutuwa duk lokaci ne" Cikin sanyin jiki Asalamiyya tace"Amin, bari in tafi dama wucewa zanyi" Hajiya kilishi tace"to Allah yakaiki lafiya ki gaida gida" Ashraf yayi murmushi yana ganin drama Momy kilishi da Asalamiyya, afakaice magana tafada mata, Allah yabata saurayi bame mataba Kenan ba Aryan ba tunda shi yanada mata. Hajiya kilishi kuwa Bayan Asalamiyya tabi da kallo cikin ranta tana mamakin Asalamiyya lokacin da akace Captain yamutu Koda wasa batazo gidan ba, bare tamata jaje awaya duk kusancin su, tayaya ne zata yarda yanzu ta auri Aryan,yanzu kam tagane gaskiya. Ahankali Captain Aryan Yasaki ajiyar zuciya sannan ya kalli Ashraf yace"muqarasa motar" Kai tsaye suka musu rakiya wajan motar anan Captain yaga Mawahib harta shiga tana zaune abayan motar tana danna wayarta, yabude motar yasaka jakar kayanta, sannan yashiga motar suka tafi duk yan gida suna daga musu hannu, Ashraf yana tuqa motar, yayinda Mawahib da Captain suke baya,tunda yashigo yaga ko kallonsa batayi ba, ya kalleta tareda dora hannunsa akan nata amma saita janye hannunta,girarsa guda daya ya sosa sannan yayi murmushi yaharde hannunsa a qirjinsa yana kallon window. Yariga yasan ganin Asalamiyya ne yasa take wannan fishin,itama window ta kalla yayinda Captain Aryan yakejin bazai Iya jure wannan fishin nataba. Ahankali yadan Matso kusa da'ita sannan yayi qasa murya yace" I'm sorry" Cikin fishi ta juyo ta kalleshi tace"for what...?'' Ashraf dayake driving yana jiyosu yayi murmushi baice komai ba. yanaso yajata jikinsa ya lallashe ta amma yanda yaga tahada rai, saita masa kwarjini, gashi zuciyarsa sai zigashi take akan ya janyota ya lallashe tan, gashi Ashraf yana motar bazai iyu daga lallashi yaje ya shagala ba, hakan yasa ya kalli Ashraf din yace"Ash bari in dawo gaba" Babu musu Ashraf yatsaya, Captain yafuto yakoma gaba, sannan sukaci gaba da tafiya, dalilin haka yasa Mawahib tacika tayi fam.... Suna zuwa Airport dinma gaba tayi, Ashraf bai tafi ba saida yaga tafiyar su sannan yadawo gida, acikin jirgin ma kasa yi mata magana yayi, kanta yana kallon window yayinda ta harde hannunta a qirjinta, Captain kuwa kasa tanka mata yayi saide ya kalleta yayi murmushi. Suna qarasa wa gida tawuce tabarshi awajan tanajan jakar kayanta cikin sauri harta qarasa shiga falon nasu,taku kadan yayi yakamo ta saiji tayi ya fuzgota zuwa jikinsa, kanta ta kawar cikin 6acin rai, yasaka hannunsa na dama ya rufe falon nasu sannan yadora hannunsa akan cikinta yace"kiyi haquri mana,tun agida nabaki haquri amma sai fishi kike dani,yakike so inyi ne?" Cikin taqaici tafashe da wani irin kuka tacire hannunsa daga kan cikinta tace" Nika rabu dani,kakoma wajanta mana, tunda katsaya kana qare mata kallo" Ganin kukan ta yasa cikin tsananin damuwa shima ya tsugunna yakamo fuskarta da hannunsa biyu sannan yace"niban kalleta ba, waye yace miki na kalleta?" Cikin fishi tace"to meyasa ka tsaya awajan?" Cikin damuwa yasake riqe fuskarta yace"Honey...,duk da natsaya awajan ba'ita nake ganiba, ke nake gani a'idona,kidena tsoro ko tantama akaina nariga nabaki amanar kaina babu wadda zan bawa wannan matsayin bayanki" Hawayen idonta ta goge tace"kayi alqawari?" Cikin sauri yace"nayi miki Honey,please kidena min asarar hawayen ki" Kanta tagyada masa,tana sake share hawayen. Kallonta yayi cikin sigar rada yace"kin haqura?" Sake daga masa kai tayi, cikin gamsuwa yace"to nunamin" Ahankali tamatso jikinsa tayi kissing wuyansa, cikin sauri ya rungume ta yana sauke numfashi. cikinta ya shafa yace"Honey irin wannan kishin zaki barni in qara aure kuwa?" Cikin sauri takai masa wani irin dukan soyaiya, yasaki murmushi yadauketa cak suka qarasa shigowa falon,yana ajiye ta tatashi tafara qoqarin gyara gidan,Shima kayanta kawai yakai mata sama, sannan yarage kayan jikinsa Yafuto suka cigaba da aikin tare,kokadan bai barta tayi wani aikin kirki ba, duk shine yayi ayyukan,saida suka gyara gidan tsaf, sannan yayi wanka ya shirya yafita, itama wankan tayi tashirya ta sauko falon tana kiran wayar Yan gida. Captain Aryan ne yashigo falon hannunsa daukeda take away dayawa, abinci ne yashigo musu dashi ciki harda tuwo kamar yanda yasan cewa tana so. Afalon suka baje sukaci su kasha, sannan Captain yajata jikinsa yana shafa cikinta, kallonsa tayi tareda dora hannunta akan nasa hannun tace"Baby baka gajiya da shafa cikin nan ne?" Kissing din wuyanta yayi yace"to awa nawa bamu gaisa dashi ba? bayan kinmin haramiyar dumin jikinki tun muna Mota?" Bakinta taturo gaba tace"bayan kaine ka koma wajan Yaya Ashraf karabu dani , saboda na nuna Ina kishin mijina akan Asalamiyya" Murmushi yayi yace"Honey bazan Iya jinki ajikina hannu na yatsaya haka kawai ba, kuma kinga Ash yana cikin motar, but please kiyi haquri bazan sake ba" Cikin sauri tabude bakinta tace"Amma ai a jirgi...." Cikin sauri yadora bakinsa cikin nata yahanata yin mitar datake shirin yi, sai gashi Mawahib tayi dif kamar an dauke wuta, ta manta da batun fada suka fara shagalinsu. Tunda suka dawo Abuja Captain ya sangarta Mawahib,kokadan baya barin ta tayi aiki me yawa,koda yana wajan aiki yanzu za'a ga yadawo gida duk da lokacin tashin nasu beyi ba,jarabar da cikin yasata ne yasa Captain Aryan shima har wata murjewa yake saboda yanda yake samun ta yanda ya kamata,koda wasa bai ta6a gajiya wa da'ita akan haka ba,ganin yanda yake mata qoqari yasa tadage musu da shan fruit, ko kallo suke saita hado musu fruit adan plate suna kallon sunasha. Kokadan basuda wata sauran damuwa hankalinsu yana kwance suna gudanar da rayuwar su yanda suke so,kwata kwata Captain bashida lokacin kansa saina Mawahib saboda yanda yake bala'in tausayin ta,ko tafiya yaga tanayi saide yayi shiru yana binta da kallo jikinsa a sanyaye, tausayin dayake mata ne yasa yake hanata aikin komai saide shi yayi, haka yadage mata lokaci zuwa lokaci suna zuwa asbiti tana ganin likita daga nan ayi mata awo su dawo gida har cikinta yasake girma sosai. Bayan sun shafe wasu watanni a Abuja tafiyar mutanan gidan Alqali zuwa Saudia tatashi,kamar yanda su Captain suka tsara, da Alqali da Alhaji khaleed, Alhaji Isah, da Momy kilishi, da Mama Sadiya, da Mamy, gaba dayansu iyayen nasu sukai shirin tafiya, ya kasance gidan babu kowa,su Mawahib basuje sallama ba,Ashraf da Nabiha ne kawai suka rakasu Airport daga nan suma suka wuce Abuja wajansu Mawahib da niyyar yimusu weekend. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Ranar babu wanda yakai Captain Aryan murna shida Mawahib, ita tana murna Nabiha zatazo, shi yana murna Dan'uwansa Ashraf zaizo. Itace tayi musu girki lafiyaiye da taimakon Captain,suna sauka a Airport Captain yaje ya dauko su ita kuma tana gida. Kallo ta kunna tanayi kadan kadan har sukazo gidan, tun a compound take jiyo dariyar su Yaya Captain shida Ashraf,ahankali tatashi tanufo qofar falon, tun kafin ta qarasa suka shigo, Ashraf yana ganin Mawahib yaji ta bashi tausayi, saboda cikin nata badan qarami bane, kona Nabiha kafin ta haihu bekai nata girma ba. Captain yana daukeda Lil Aryan a hannunsa yaronda yake tsananin kama dashi. Nabiha ta rungume Mawahib tace"sannu Mawahib" tafadi maganar tana kallon cikin jikinta,cikin murmushi Mawahib ma ta rungume ta tana amsawa. qarasa wa sukai falon suka zauna sannan suka sake gaishe gaishe, Mawahib ta yunqura zata tashi tace"bari in kawo muku lemo" Nabiha tayi sauri tace"yi zamanki, zan dinga yin komai har weekend yaqare mutafi" Babu musu takoma ta zauna, Nabiha ta gabatar musu da komai, sannan suka zauna aqasa kowa yafara cin abinda yakeso sai dariya suke gaba dayansu su hudun kana ganinsu kasan cike sukeda farinciki, yayinda Lil Aryan yake kwance akan kujera yana daddaga qafa irinta jarirai yana kallon p.o.p din falon. Har yamma suna zaune babu inda sukaje, saida daddare ne sannan sukai wanka suka shirya suka fita zuwa shan ice cream sannan suka zaga gaari, basu dawo da wuri ba sai can dare sannan. Dayan dakin dayake kusa dana Mawahib nan su Ashraf suka shige suka kwanta cikeda gajiya, sannan Mawahib da Captain ma sukai shirin tafiya, ganin yanda take tafiya daqyar hakan yasa yadauketa gaba dayanta, suka shige dakinsa, yakashe musu wuta suka kwanta. Ko minti goma ba suyi da kwanciya ba, taji yana shafarta, tasan sarai abun yakeso, duk da itama tana buqatar hakan amma dole zasuyi haquri yau, juyowa tayi ta kalleshi tace"no Baby,banda yau" Cikin lumshe ido yace"meyasa?" Idonsa ta kalla sannan tace"saboda su Yaya Ashraf mana,kaida baka komai bakinka arufe tayaya hakan zai iyu?" Cikin shaqaqqiyar muryarsa yace"Honey ko sau dayane please...,cemiki akai sudin ba zasuyi ba?" Hannunta tasa takama fuskarsa ta riqe tace" Baby...banason rigimarka,muyi haquri mana kaji?" Ta qarasa maganar cikin sigar lallashi. Cikin shagwa6a ya kalleta bece komai ba, Mawahib tayi murmushi ta rungume shi tana shafa sumar kansa alamun lallashi hartaji numfashinsa ya sauya alamun yayi bacci, sannan itama ta samu nutsuwar yin baccin. Washegari da safe bayan sungama shiryawa kai tsaye kebbi suka tafi bayan saqon gaiyata dasuka samu daga wajan Alhaji Ma'aruf na walimar da abokan sa su Alhaji Bala suka hada masa saboda yayi sabon aure bayan tsawon shekaru daya dauka babu aure. Dawuri suka sauka hakan yasa aka fara gudanar da walimar suna nan,sai bayan azahar sannan aka tashi daga wajan walima,daga nan Mawahib da Nabiha suka dawo gidan kawun ta, inda yayar Murjanatu amaryar Alhaji Ma'aruf tahada su dukansu Nabihan da Mawahib din ta basu magungunan masu kyau irinna Yan kebbi, sannna tasake yimusu fada sosai akan Zaman haquri da juna, daga qarshe kuma ta qare tana sake wayar musu da kai akan rayuwar aurensu, sosai suka sake daukan darasi a wajanta,Nabiha kuwa har tambaya take mata akan wasu abubuwan daya shige mata duhu, babu kunya matar tayi mata bayani sosai, amma Mawahib bata tambaye ta komai ba kasancewar Sister Saudat dama tagama hure mata kunne akan kula da Captain din. Sai yamma sukai shirin tafiya bayan ankai Amarya Murjanatu gidan Alhaji Ma'aruf, sannan suka sake sallama da Alhaji Ma'aruf din suka tafi. Sai gab da magrib suka dawo gida,Ashraf da Aryan kuwa basu shigo gidan ba masallaci suka wuce, bayan sun idar da sallah Nabiha tashiga kitchen tahado musu maganin da Matar kawun Mawahib ta basu, ta kawowa Mawahib nata tana cewa "yanda take ziga maganin nan bari de musha muji inda gaske take" Mawahib tayi murmushi itama ta shanye magani,daga nan suka gabatar da sallar isha'i, sannan suka zauna afalon. Sai qarfe tara su Captain suka dawo gidan,Nabiha ta Kalle su tace"ko ahado muku abinci?" Captain Aryan ya kalli Mawahib yace"no na qoshi,daga nan yawuce sama" Mawahib tana ganin kallon da yayi mata tasan cewa kiranta yake, Ahankali tatashi tabi bayansa,sai Ashraf da Nabiha ne kawai afalon. Tana shiga dakin ta ganshi a kwance tace"koka gaji dayawa ne?" Kallonta yayi yamiqa mata hannu, babu musu taqaraso jikinsa, ajiyar zuciya yasaki yace"nagaji sosai Honey" Fuskarsa ta shafa tace"sorry, muje kayi wanka" Babu musu yatashi suka shige toilet, already tayi wanka kafin tayi sallar magrib, amma haka yasata saida tasake yin wani wankan, tun a toilet din takasa gane masa, har suka futo taga duk inda tayi binta yake, Ahankali tajuyo ta kalleshi tace"Baby, yanzun nan fa kagama cewa kagaji,muje kayi bacci mana" Cikin shagwa6a yadan kalleta yakasa yimata magana,ganin jiya ta hana shi yauma karta sake hana shi ta kwana cikin tsinuwar mala'iku hakan yasa dakanta taja shi zuwa gadon takashe musu wutar dakin sannan ta kalleshi cikin duhu tace"da sharadi..." Cikin sauri yace" naji koma menene na yarda" Jin yanda ya rikice mata tun ba'a je ko'inaba, hakan yasa tayi murmushi tace"babu kuka,babu surutu saboda su Yaya Ashraf..." Kansa yadaga mata alamun ya amince, daga nan salon labari ya sauya. da farko yayi kokarin ganin yacika mata sharudan data gindaya masa, amma da tafiya tafara nisa yaji tasake sauyawa sakamakon maganin mutanan kebbi, baisan lokacin daya fara sakin qara ba, Mawahib tanajin haka tayi sauri tarufe masa bakinsa,saide tana rufe masa bakin tasake jiyo wani ihun na daban wanda ta tabbatar na Yaya Ashraf ne, ganin tahana mijinta ihu amma tanajin ihun mijin Nabiha, hakan yasa tasaki bakinsa yaci gaba da abinda yakeso ko hakan zaisa tadaina jin na Yaya Ashraf. Gaba daya sai suka haukata saman da iface iface cikin rashin sanin su kansu sunayin ihun, hakan ya tabbatar musu da cewa lalle maganin da su kasha yanada kyau sosai. Bai sarara mataba sai can cikin dare kafin su kayi wanka suka kwanta,dasafe baccin gajiya Mawahib take ramawa domin kuwa ba qaramin gajiyar da'ita yayi ba, batasan a halin da Nabiha take ba, baccinta tayi sosai bata tashi ba tun bayan da tayi sallar asuba sai wajan qarfe goma nasafe,wanka tayi sannan ta sauko qasa. Anan taga Nabiha tana kallo tanacin abinci, Lil Aryan yana kwance agefenta. Qarasowa tayi ta zauna itama tafara cin abincin Nabiha tace"Harkin tashi?" "wallahi na tashi yanzu,bansamu bacci bane shiyasa, saida asuba sannan naji wani bacci me dadi yasake daukana" Nabiha tace"nima ban dade da saukowa ba,qarfe tara na sauko shine nashiga kitchen nayi mana wannan abincin" Mawahib tace"tosu Yaya Captain me sukaci? banji motsin suba ko sun fita ne?" Nabiha tace" nakira Sweet yacemin sun fita, duk inda sukaje saisu ci abincin acan,naso in tashi dawuri inyi mana wani abun amma idona yacika da bacci,dama kuma ga gajiyar hanya data wajan walima,kawai sainayi bacci na, dana tashi naga bayanan kawai saina dafa mana Iya ni dake, Shima yaja musu basuyi break fast agidaba tunda shine ya hanani bacci jiya,amma aida zan tashi inyi mana wani abun dawuri" Cikin sauri Mawahib ta kalleta tana tunani kode tajiyo Yaya Captain itama? Amma bata tambaye ta ba saitace"kema baki kwanta dawuri ba?" Nabiha tayi murmushi tace"Yaya Ashraf ne ya hanani,amma yanda nagaji naso inyi bacci na" Mawahib tazuba tea tafara Sha tace"toya za'ai sai haquri,jiya haka mukai da Yaya Captain nahanashi komai nace muyi bacci" Nabiha tayi murmushi tace"nikam ban hana shi ba,kuma Koda wasa banyi kuskuren rufe masa baki ba, dade ace Aryan dina ya girma ne dole zan dauki mataki akan hakan, amma yanzu Kinga Aida saura,Mawahib a rayuwar Nan banajin akwai abinda nasan cewa zaisa Yaya Ashraf yaji dadi banyi masa Shiba, saboda shi din kamar kyautar Allah ce agareni,tun bansan menene soba nake qaunar sa,alokacin hankalinsa yana Kanki, hakan yasa nayi haquri ban baiyana ba naci gaba da Addu'ah, daga qarshe Kinga na mallakeshi, to mutumin dana tashi da soyaiyar sa, ban ta6a tsammanin zan sameshi ba, kuma sama taka na sameshi, tayaya ne zan hana shi jin dadin sa? ko a gidanmu barin sa nake yayi abinda yaso" Mawahib ta ajiye cup dinta tagyara zama tace"Nabiha? Wai kina nufin dama duk yawan tambaya ta dakike yaushe Yaya Ashraf zai dawo dama sonsa kike? Amma meyasa baki fadamin ba?" Kai tsaye Nabiha tace" saboda shi din dan'uwana ne, dole zan tayashi son abinda yake so, ke yakeso alokacin, dani dake kuma duka abu gudane Mawahib, shiyasa nake qoqarin Cusa miki ra'ayinsa" Mawahib tace"nikam bansan wacce irin soyaiya Yan gidanku suke nunamin ba Nabiha, amma haqiqa kunmin komai, yanzu saboda farincikina saiki sadaukar min danaki farincikin?" Nabiha tace"to ba gashi naga sakamakon sadaukar war danayi mikin ba?" Mawahib ta karyi bread tace"kenifa dama nafada miki bana sonsa, bare kuma Yaya Captain da bana saka shi a lissafi, amma gashi Nima cikin hukuncin ubangiji Allah yadora min masifar qaunar Yaya Captain, yanda nakeji araina Nabiha, idan babu Aryan, to babu Mawahib" Gaba dayansu suka sa dariya, Nabiha takira musu mutanan Saudia ta vedio call suna magana dasu harda Mawahib din, sun dade suna Waya sannan sukai sallama suka kashe Mutara zuwa gobe🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/20, 10:13 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Sis Uzaimat Mlm murja Nana Asma'u ab Sis Asma'u Rahma delight Fatima Baban Fatima iddah Salma Ameeeeenah Sis firdaus(writer) Mai mahamane kagana Sis nmera Sis Ummi ❤️ Maman hunai Amina Bamu Mom Asas Maimunat Muhammad Umaima Aisha musa Mabaruka Deeja@rh Bilkisu saulawa Bintu abyher Haly jasheru Nazifa Fatima Abdullahi Ummu Maryam Bilkisu bej Mrs Adam yar la6e😜 Ruqayya a kawu takwarar Mawahib Mmn yzeed Sadiya Bala zakr Ruqayya maje HauwaBima Ummu Irfan Amina kabir Hafsat iliyasu 'yar malama me bibiyar shahaab da alama tafi tsoron bindiga akan hukumar efcc. Bazaku qareba fa,duk wadda batada sunan taba zata gani a next page, Ina Alfahri daku💃🏼 Su Yaya Ashraf basu dawo gidan ba sai bayan azahar, alokacin Nabiha tagama yimusu girki sun sake wanka sun shirya tsaf cikin kyakykywar shiga, Mawahib doguwar riga ce ajikinta ta leshi me fadi, yayinda Nabiha tasaka riga da siket, lil Aryan yana wajan Mawahib tana wasa dashi,zama su Captain sukai a falon suna cigaba da tattauna maganar data shafi aikinsu. Nabiha ce ta gabatar musu da abinci, yayinda Mawahib tatashi ta zauna tana dan yatsina fuska saboda yanda taji cikinta yana dan mata motsi kadan kadan. Cikin kulawa Captain ya kalleta yace"babu matsala deko?" Kallonsa tayi cikin soyaiya tace"babu komai, Ina lafiya" Tare sukaci abincin gaba dayansu,bayan sun gama sukaci gaba da firarsu kad'an kad'an, saide Captain Aryan wayarsa ce a hannunsa yana turowa Mawahib kalamai tana karantawa, Nabiha sai ganinta tayi tana murmushi ita kadai. Washegari Monday su Ashraf suka shirya suka tafi, har Airport su Mawahib suka kaisu,bayan sun dawo suka biya shopping sannan suka dawo gida. Tun daga wajan mota yadauketa, yayinda ta saqalo hannunta ta wuyansa, har falo yakaita ya kwantar da'ita, sannan yakoma yadauko kayan dasuka siyo awajan shopping, dawowa yayi wajanta ya zauna aqasa, yayinda take kwance akan kujera yace"akwai abinda kike buqata kuma?" Cikin kulawa tadora hannunta akan fuskarsa tace"bana buqatar komai Baby,kai kadai kamaye min gurbin duk wani abu dazan buqata" Kansa ya gyada mata batare da yayi magana ba, ya shafa cikinta yace"dazu Naga kina runtse ido bakyajin komai yanzu?" Cikin sauri tace" a a banajin komai" Zama ya gyara yadora kansa akan kujerar datake zaune yayinda hannunta yake shafa lallausar sumar kansa. Tsawon sati biyu Kenan kusan kullum Mawahib sai taji cikin yana yawan yimata motsi, ko bacci take haka zata farka, amma ganin abun baiyi mata tsananin ba yasa tayi shiru bata fada masa ba, haka sukaci gaba da kulawa da cikinsu hankali kwance, suna kuma Addu'ah Allah ya sauketa lafiya, har su Mamy suka dawo daga Saudia, basuje musu sannu da zuwa ba saita waya suka musu saboda Mawahib tayi nauyi sosai. Washegari da safe bayan sungama break fast yana shirin fita aiki yaga tana yatsina fuska, cikin kulawa ya kalleta yace" babu matsala deko?" Kafin tabashi amsa taji cikinta yayi wata irin juyawa, cikin azaba tafara yarfe hannu tace"cikina" Arikice yadora hannunsa akan cikin yace"ciwo yake miki? me kike ji?" idonta ta runtse tace"jinake yana juyawa" Zaro idonsa yayi yace"juyawa?" Bai jira amsar taba ya dauketa sai Mota, asbitin datake ganin likita nan yakaita,suna zuwa kuwa likitan sa ya hadasu dawata doctor mace, cikin kulawa ta duba Mawahib sannan tace zata mata scanning, Captain Aryan yana zaune agefen gadon da Mawahib ta kwanta hannunsa yana kanta yana shafa wa gabansa faduwa kawai yake tunda yaji tace ciki yana juyawa. scanning din aka fara idon Captain da Mawahib yana kan Dr. suna kallonta, juyowa tayi ta kallesu tace"masha Allah, baby's dinku suna cikin qoshin lafiya,bawata matsala bane juyawar datakeji suna motsi ne" Cikin sauri Mawahib tazaro idonta tareda bude baki, Captain Aryan kuwa zama ya gyara cikin farinciki yace"Dr. naji kamar kince Baby's" Cikin farinciki ta kallesu tace"emana,yanbiyu ne acikinta ai,haba kukuwa bakuga cikin da girma ba? gashi ku kalla kuga yanda suke motsi" Cikin sauri suka kai idonsu wajan,Mawahib tazubawa tv ido tana kallon wannan abubuwan duka acikinta suke,? ahankali tashafa cikinta, saide atsora ce take da batun yanbiyun Nan. Captain Aryan Yasaki murmushi yace"wallahi yanbiyu ne, Alhamdulillah, Allah nagode ma,yanzu Dr. wacce shawara zaki sake bamu akan wannan cikin, banaso baby's dina su samu matsala, kuma Ina tausayin maman su, ko tashi zatayi saita runtse idonta" Dr. tayi murmushi cikin ranta tace yau nahadu da dan soyaiya, tajuyo ta fuskance su tace"wannna tausayin daka fada kuwa dole zaka rageshi ka dinga tilasta mata kullum ta dinga motsa jiki saboda cikin nata ya girma,hakan zai taimaka mata wajan sauqin naquda,tadena zama haka kawai yanada kyau ta dinga motsa jikinta koda yaushe, sannan ahankali zata daina jin ciwon motsin harta saba daga Nan Har zuwa ranar dazata haihu, idan basa motsin ai akwai damuwa" Cikin gamsuwa yace"Insha Allah Dr. zamu kiyaye" Dr. tajuya ta kalli Mawahib tace"Maman twins bakya magana,ko bakya murna da ganin yaranki?" Cikin sanyin jiki tace"Dr. mata ne?" Dr. tajuya tasake dubawa sannan tace"maza ne, saide bamusan Yaya Allah zaiyi hukuncinsa ba, amma anan de abinda nagani dukansu maza ne" Kallon photon yaran tasake yi tace"kuma zan'iya haifar Yara biyu?" Likita tayi murmushi tace"idan kikai Addu'ah fiyeda biyu ma saiki ga kin haifa, komai yana wajan Allah" Daga nan sukai shirin tafiya amma har lokacin jikin Mawahib bai rage sanyi ba, suna futowa sukai sallama da dayan likitan daya hadasu da matar data musu scanning sannan suka futo hannunta cikin nasa, adede lokacin aka wuce da wata mata akan gado Ana tura ta da uban ciki da alama naquda take, Mawahib tana ganinta saita fashe da kuka tashafa cikinta. Captain Aryan yajata ya sakata a Mota sannan ya rufe yaja suka bar asbitin, har sukai nisa a hanya bata daina kukaba,cikin damuwa yataka birki yaja yatsaya sannan ya juyo ya kalleta yace"Honey kode bakya so nane yanzu?" Cikin kuka ta dago ta kalleshi tace" dole kace bana sonka mana tunda natsaya kamin ciki gashinan kana gani ana mutuwa awajan haihuwa,idan na mutu ba shikkenan kahuta ba"(😂) Murmushi yasaki yakama hannunta yariqe yana ganin yanda hawaye suke gudu a fuskarta yace"tunda akace yanbiyu zamu haifa naga hankalinki yatashi, waye yace miki ana mutuwa a haihuwa? Momy ta mutu ne? bakiga gashi ta haife mu kuma gashinan har yanzu da ranta ba? duk wanda kikaga yamutu kwanan sa ne yaqare Honey" Wani hawayen ne yasake zubo mata tace"to meyasa zaka min cikin yanbiyu, bayan Nabiha ta fadamin guda daya ma qafar mutum daya lahira daya tana duniya" Hannunta yasaki yasake matsowa yariqe fuskarta yace"Honey toni tayaya zansan namiki cikin yanbiyu ko dan daya? idan Allah yayi kowacce haihuwa yanbiyu zaki dinga haifomin Yaya zanyi ni?" Tanajin haka tasake fashewa da kuka, ahankali yasaka harshensa yafara lashe mata hawayen tundaga kumatunta har idonta, sannan yahade bakinsu waje daya, saide har lokacin hawayen take zubarwa, ahankali yadago kansa ya kalleta sannan yazare bakinsa daga nata yace"menene matsalar kuma?" Cikin kuka tace"ni tsoron haihuwa nake" Cikin kwantar da hankali yace"zaki haihu lafiya kinji? insha Allah Allah yana tare damu yanda Momy ta haife mu lafiya nida Ash kema haka zaki haifomin sababbin Ashraf da Aryan kinji?" Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta goge hawayen idonta,yasake kallonta yace" shikkenan komai yawuce?" Dago idonta tayi ta kalli wata bishiyar mangoro agefensu reshen bishiyar duk ya sakko qasa, tace" ni mangoro zansha" Cikin sauri yace"shikkenan muje Super market kidebi duk yanda ya miki" Cikin shagwa6a tace"ni wannan danyen nakeso" Kallon bishiyar yayi yace"Honey danyan mangoro kuma? kinsan zaki nemi danyan mangoro meyasa tun kafin muyi aure bazaki fadamin ba ashuka miki acikin gidanki?" Cikin shagwa6a tace" to kafin muyi auren baka tsaneni ba" Cikin sauri yace"kinga, toya Isa,nina manta, basai kinmin wani tone tone ba, bari inciro miki" Yafice daga Motar tana kallonsa ya dinga ciro mata mangoron sannan yadawo yabata, yashiga yaja motar suka tafi gida. Suna zuwa gida suka zauna afalo yadauke mangoron yaje ya wanko mata su ganin zata faraci ko wanki babu, dawowa yayi yakawo mata sannan shima ya zauna, anan yaga qafafunta duk sun kumbura, ya miqe qafafunsa yaja qafar tata yadora akan cinyarsa yana matsa mata su, wayarsa yadauka yakira Momy kilishi, bayan sun gaisa yace"Momy munje wajan scanning ance Mawahib yanbiyu ne" Cikin sauri Hajiya kilishi tadafe qirjinta tace"yan biyu?, har yanzu de Ina ganin ikon Allah ni kilishi,gaba daya de a zabar danasha irinta yarinyar nan take sha, to tunda saura Yan satittika tasauka ko zaka kawo ta gida saita haihu anan?" Cikin sauri yace" Momy Anty Mamy tataho mana,ba mazajenta za'a haifa ba?" Hajiya kilishi tayi murmushi tace"to Maryam din gatanan tanajin abinda kafada kuma bazata zo ba" Cikin sauri yazaro idonsa sannan yakashe wayar. Hajiya kilishi ta kalli Alqali tace"Mawahib fa takusa sauka Alhaji,shine nake tunanin ko zai kawo ta gida ta haihu anan?" Alqali yace"naji kince yanbiyu ne ko?" Tace"eh haka yake fadamin yanzu" Yace"toki rabu dasu idan tashiga satin haihuwar saisu dawo gida,da Ina tunanin Sadiya taje ta zauna dasu, to amma yanzu tunda yanbiyu ne gara sudawo gida ta haihu agabanku,zasufi Samun kulawa, zan kirashi insha Allah" Cikin farinciki Hajiya kilishi tawuce part din Mamy zata sanar da'ita. Captain Aryan bai bar Mawahib agida ita kadai ba ranar baije wajan aiki ba zama yayi tareda ita yana aikin matsa mata qafafu. Kamar yanda likita tafada Washegari bayan yadawo daga wajan aiki hannunta ya kama suka fita compound din gidan ta dinga yawo, kawai gidan suke zagaya wa bai barta ta zauna ba, aikuwa kafin tagama duk ta hada uban gumi, sannan suka dawo ciki yakamata tana taka stairs dinsu daqyar, dakinta yakaita tayi wanka, tasauko qasa tashiga kitchen tafara kokarin hada musu abinci,zama yayi a falo yana qoqarin waya da Ashraf, sai qaranta yajiyo a kitchen, aguje yashiga kitchen din yaga ta riqe dan yatsan qafar ta tana yarfe hannu. Hannunta ya janye daga kan yatsan nata yace"meyake faruwa?" Tace"plate dinnan ne ya fadomin a qafata" Yakai kallonsa wajan plate din shibega abun kuka anan ba, yadauki plate din a hannunsa yaga idan ya masa kyakykywan ruqo zai Iya karyashi,ya kalli idonta yace"akwai zafi ne?" Cikin sauri tadaga masa kanta, cikin kulawa ya kamota yace"muje falo ki zauna,yau zanyi mana girkin" Badan ta yarda ba tazauna shikuma yashiga kitchen din yadauki wayarsa yayi browsing girke girke sannan yafara yimusu, tana zaune afalo sai ganinsa tayi ya ajiye mata plate din abincin agabanta, yace"taste it..." Murmushi tayi ta dauki spoon taci dan kad'an ta yatsina fuska, saita ga yanayinsa ya sauya jikinsa yayi sanyi, sai tafashe da dariya tace" yayi dadi, dama gwadaka zanyi" Dariya yasaki yazauna akusa da'ita tareda riqe kafadarta, adede lokacin cikinta yafara motsi, ta dauki hannunsa ta dora akan cikin tace"kaji suna motsi" Cikin farinciki Shima yasaka hannunsa yanaji, dayan hannun nasa kuma yafara bata abincin. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Haka suke gudanar da rayuwar su cikin farinciki,hatta kwanciya saiya kwantar da'ita yayi mata Addu'ah, sannan shima zai kwanta, kullum idan yadawo daga wajan aiki baya zama sai sun fita ta motsa jikinta kamar yanda likita tafada,duk yanda yakaiga son kasancewa da'ita haquri yake,saboda girman cikin, hakan yasa suka rage yin abubuwa saide bayan kwanaki suyi, saide tazarar kwanakin dayake bata baya komai hakan yasa idan suka kasance tare yake kasa controlling kansa harsai yaji yanda yakeso sannan yake rabuwa da'ita. Kamar yanda Alqali yatsara kwanakin haihuwar ta suna cika, yasa Captain yakawo ta gida, bayan sunzo gida a part din Hajiya kilishi ta sauka, kowa sai sannu yake mata cikinsu harda Nabiha data taho gidan tun safe itama. anan gida ta wuni tareda Mawahib wadda tunda ta zauna bata motsa ba,Nabiha ce take nuna mata tsarabar su ta Saudia sai murna suke kamar su aka jewa Saudian. Saida Captain Aryan yayi kwana biyar Mawahib bata haihu ba, hakan yasa yashiga damuwa saida Mamy tasake yimasa bayani cewa dama Ana wuce watannin, sannan hankalinsa ya kwanta harya samu damar komawa wajan aiki. Bayan yatafi ma saida yayi sati biyu a Abuja kullum yana waya yana tambayar halinda ake ciki, amma saide yaji shiru babu batun haihuwa. Yau tun asuba tatashi da naquda Mamy taduba tagani tace"dasaura" Hajiya kilishi tana gefen ta ta riqe hannunta sai sannu take mata, yayinda Mamy tagama shiryawa tsaf domin kar6ar haihuwar jikokinta,tun qarfe shida na safe Captain Aryan yake kiran wayar Mawahib amma no answer, da farko yayi tunanin ko bacci take, saiya haqura, wajan qarfe takwas yasake kira yaji shiru bata dauka ba, alokacin Mawahib batasan inda kanta yake ba, naquda ta sakata agaba gadan gadan. Captain bai haqura ba yasake kiran wayar Momy kilishi itama yaji bata dauka ba, yakira Mamy ma shiru, yakira Mama Sadiya itama bata dauka ba, tun daga nan jikinsa yabashi ba lafiya ba, kai tsaye ya shirya yanufi Airport ya taho gida. Baizo gidaba sai qarfe tara da rabi na safe, yaji gidan shiru babu kowa,da alama mazan gidan basa nan, kai tsaye yanufi part din Mamy yaganshi a rufe, cikin sauri yatafi part din Momy kilishi anan yaji maganar matan gidan gaba dayansu a dakin Momy kilishi,yana dosar dakin yaji Mama Sadiya tana cewa"yi nishi Mawahib" Gabansa yayi wata irin faduwa,yasaka kansa cikin dakin yatsaya abakin qofar dakin yana kallon azabar da Mawahib takesha gaba daya dogon gashin nan nata ya hargitse tajiqe sharkaf da gumi banda kuka babu abinda take, jikinsa ne yayi sanyi kalau yayinda gabansa yake faduwa baisan lokacinda ya jingina da jikin qofar dakin ba. Mamy datake tsugunne a gaban Mawahib tace"Mawahib kiyi nishi mana,zaki kashe masa yara fa..." Hajiya kilishi data fashe da kuka tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi waiku malaman asbitin nan meyake saku masifa ne? kiyi mata haquri mana da wannan uban cikin zataji koda masifar ki?" Mama Sadiya ta shafa kanta tace"daure Mawahib, daure Allah yasauke ki lafiya" Wani irin nishi tayi takama hannun Hajiya kilishi ta riqe kamar zata 6allata saiga kan da yafuto, akan idon Captain yaga yanda Mawahib take haihuwa lokaci daya ya silale yayi qasa ya zauna jagwab, daga nan baisake sanin meyake faruwa ba yasume a zaune (🙆🏻‍♀️) Jama'ah a taimako da ruwa yau soja ya gaza😂 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/21, 11:44 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Godia ta musanman ga: Ayesha✨🥰 Safeena Ummu hafsah Hauwa Umar Hauwa'u Bilkisu bej Saratu Hassan Nusaiba maga Hafsat Zainab jaaf Asiya Bashir Mummy A10 Babyj Ummi Gumi Mrs Hauwa Ameenah🥰 Ramatu shehu Umm Hafs shareef Matar mijin Ummu mujitapha Zainab Aisha Queen Rashida kham Maman walid Murjanatu Maryam Teemah Baba Khadija Muhammad Hareesa taneem🌹🌹 M@m@n Aish@ Maman samha Reemah Shamsiya A.g Abdullahi Ummu kulsum Ina Alfahri daku akoda yaushe ❤️💃🏼 Mama Sadiya da Mamy da Hajiya kilishi ne suka juya jin motsin mutum a bayansu, amma babu wadda tabi takansa sun san cewa tsorata yayi da alama baisan yanda akeyi ba. Mawahib kuwa bataga shigowar saba, saida ta haifi na farko sannan tafara maida numfashi,Mamy tabawa Mama Sadiya yaron, Mama Sadiya tafara gyara shi, hawaye suka zubo daga idon Mawahib tanajin wata sabuwar qaunar Mamy aranta, bata gama kukanba wani sabon ciwon yataso, wannan karon kam kasa yin shiru tayi kuka take sosai harda ihu, kafin ubangiji yabata damar haihuwar dayan lafiya. Shikuma Hajiya kilishi ce ta kar6eshi tana hamdala afili idonta fal hawaye, ba komai take tunawa ba sai lokacin data haifi su Ashraf, suma haka taji kamar ta mutu, Mamy kuma tamaida hankali tafara kula da Mawahib, tsawon awanni suka dauka adakin zuwa lokacin harsun gyara yaran tsaf dasu masha Allah farare masu mutuqar kama da juna,Mama Sadiya tayiwa na farkon alama, yanda za'a gane waye babba a cikinsu, Mamy kuwa sai yanzu hankalinta ya kwanta bayan taga tagama gyara yarta tsaf harda dinki tamata, sannan ne Mawahib tafara yin baccin wahala. Mamy ta kalli Captain Aryan tayi murmushi tace"to sojoji sun fadi sun suma, shi Ashraf inda yagani shikuma Yaya kenan?" Cikin farinciki Hajiya kilishi tace" rabu da wannan dannaki Maryam Aryan aiba soja bane awajan matarsa" Mama Sadiya ce ta dauko ruwa ta zuba masa, sai alokacin yazabura yabude idonsa yafara bin dakin da kallo yayinda gumi yahadu da ruwan da aka zuba masa yasa kayan jikinsa suka jiqe, gadon ya kalla yaga Mawahib tana bacci ga yaran nan an shirya su tsaf acikin fararen kaya suma suna bacci. Ahankali yaji hawaye yana zubowa daga idonsa,yanzu irin wannan wahalar Momy tasha itama kafin ta haife su? wacce irin kulawa zai bawa matarsa saboda wannan azabar datasha? Cikin sanyin jiki ya qarasa wajan Momy kilishi yadora kansa a cinyarta yafashe da kuka yace"Momy kiyafemin" Mama Sadiya ta girgiza kanta cikeda tausayi, yayinda Mamy tafara bashi haquri. Hajiya kilishi ta shafa kansa tace"Babana bakamin komai,duk abinda yafaru abaya ai yariga yawuce, Allah zaka yiwa godia bisa kyautar da yayi maka" Cikin sauri yatashi daga kan cinyarta yana goge hawayen idonsa, sannan ya qarasa kan gadon ya kalli yaran masha Allah ba qananu bane,suna baccinsu cikin kwanciyar hankali suna nema su kashe masa mata, bai dauke suba, yakama hannun Mawahib yariqe sannan ya shafa kanta yadora bakinsa akan goshinta yayi kissing dinta, cikin kunnanta yarada mata "Allah yayi miki Albarka Honey" Yasaka hannunsa yana sake goge hawayen idonsa, Mamy tayi murmushi tatashi tafice,tana fadin "bari inje in bugawa Yan maiduguri waya Infada musu" Mama Sadiya ma tatashi tafita, Hajiya kilishi kuwa wayarta ta dauka takira Alqali yana dauka tafara fada masa, sannan itama tabar dakin, Captain Aryan yana jiyota daga falo tana buge bugen waya tana fadawa mutane. Shida kansa yakira Ashraf yafada masa, inda Ashraf din yabashi tabbacin yau zai baro wajan aikinsa yazo yaga yaran shima, Mama Sadiya kuwa itace ta fadawa Nabiha. Ta dade tana bacci yayinda Captain Aryan yana zaune agefe yana aikin kallonsu itada yaran yanajin wani irin farinciki aransa wai ita da yaran duka nasa ne,kallon yaran yake tundaga kan yatsun qafarsu iri dayane babu banbanci, kamar de shida Ashraf, ahankali yasake jin wani hawayen yana zubo masa, yasaka dan yatsansa ya goge, sannan ya sunkuya yayi kissing dinsu, yasake komawa gefen Mawahib. Nabiha ce tashigo dakin cikin farinciki tana ganin Mawahib tana bacci saita fara takowa a hankali dan karta tasheta, yaran tafara kalla ta sunkuya ta dinga kissing dinsu cikin farinciki sannan ta gaida Captain Aryan daya kafa yatsare yaqi zuwa ko'ina, sannan tafuto daga dakin. Nabiha tana fita bayan minti talatin Mawahib ta farka, ahankali tafara bude idonta harta gama bude shi fes a kansa, hannunta yana cikin nasa, cikin kulawa ya sunkuya yayi kissing dinta sannan yace"Sannu Honey,Allah yayi miki Albarka..." Ajiyar zuciya ta sauke ta kalleshi tace"Yaya Captain..." Cikin sauri yace"Honey yau ba Baby?" Bakinta taturo gaba tace"nadena haihuwa" Hawayen tausayin tane yazubo daga idonsa,ahankali tasaka hannu ta share masa hawayen, cikin hawayen yace"nima bazan bari kisake haihuwa ba, wannan ma sun'isa,wahalar tayi yawa,nayi tunanin mutuwa zakiyi, kingansu nan ban dauke su ba,nabari saikin tashi mu dauki yaranmu da kanmu atare" Fuskarsa ta shafa tayi murmushi tayunqura tatashi daqyar, yayi sauri yasaka mata fillo a bayanta, sannan yadauko yaran yadora mata su ajikinta gaba dayansu, sannan ya hadasu ya rungume su wani sabon hawayen yana sake zubo masa. Kallon Yara take tanajin yanda take tsantsar qaunar su acikin ranta, ahankali ta kalleshi tace"wana fara haifa?" Cikin sauri ya nuna mata nafarkon,ta sunkuya ta sumbaceshi, ta sumbaci dayan ma tace" Allah yayi musu albarka" Hawayensa ya share yace"Amin" Dago kanta tayi tasake kallonsa,ganin yana share guntun hawaye hakan yasa ahankali ta dora harshanta akan fuskarsa ta share masa hawayen tas, kamar yanda yake mata, Mamy ce tashigo dakin cikin sauri Captain Aryan yayi baya tareda sosa qeyarsa. Mamy bata nuna musu komai ba ta qaraso gadon ta zauna tana qoqarin daukar yaran daga cinyar Mawahib tace"wai har yanzu basu tashi daga baccin bane?" Mawahib tace"basu tashi ba" Mamy tadan jijjigasu tace"maza kutashi ba bacci kukazo yiba,baccin awa nawa zakuyi, kutashi gasu Yaya khaleed can afalo sunzo suga abokan su" Hajiya kilishi ce tashigo dakin da tuwon dawa miyar kuka wadda taji Jan nama aciki, sai man shanu da'aka zuba akan tuwon dakuma kunun kanwa, mama Sadiya ma tashigo da farfesun nama duk suka ajiye mata, Hajiya kilishi takalli Mamy tace"wai har yanzu basu tashi bane?" Mamy tace"gasunan sun kama ido sun rufe sunata bacci ko tsoron ganin mu suke oho" Hajiya kilishi tace"tashe su"(😂) Babu musu Mamy tafara tashin su. Hajiya kilishi ta juya ta kalli Mama Sadiya tace"Sadiya kice su Alhaji su shigo mana,su shigo kawai" Adede lokacin kuwa Mamy tatashi yaran, nan da nan kuwa suka fara kuka, Captain Aryan ya kallesu cikin jin dadi ya sunkuya yayiwa Mawahib rada yace"kinji kukan su" Murmushi tayi tanajin dadi aranta. Adede lokacin Alqali da Abba, da Alhaji khaleed suka shigo dakin,har rige rigen daukan yaran suke saboda farinciki,Alqali ya dinga kallonsu sai suka tuna masa da shekarun baya lokacin da kilishi ta haifa masa yanbiyunsa. Hajiya kilishi takalli Mawahib tace"sauko kici tuwo saiki basu susha" Mawahib tace"Momy ni banason tuwo" Captain yayi sauri ya kalleta yace"yau kuma?" Mama Sadiya tace"dama ai cikin ne yasa take cin tuwon shiyasa ga yaran nan masha Allah 6ul 6ul dasu kamar ba haihuwar farko ba" Captain Aryan yayi kasa da kansa yana tunanin maganar Mama Sadiya cikin ransa yana fatan Allah yasa iya cin tuwon tadaina banda daya abun 🙊🙈 Hajiya kilishi tace"tuwo ai dole ne Mawahib,idan kikaci tuwon kika Sha kunun kanwar nan yanzu yanzu ruwan nono zaizo, suma yaran saisu samu abinci" Badan taso ba tatashi daqyar ta sauko sai taji cikinta sakayau kamar an debe mata komai haka tafara cin tuwon ahankali tana tunanin yanda take masifar son tuwo kafin ta haihu amma yanzu tuwon ne bataso, taci tuwon daidai misali sannan tafara shan kunun kanwa,Alqali yayiwa yaran Addu'ah,yabasu ruwan zam-zam sukasha, sannan ya kalli hajiya kilishi yace"Kilishi yanzu kinsamu sabin angwaye ba Zaman lafiya" Momy kilishi tace"A a bana wannan auren, ba nayi Sam Alhaji,Ina mazaje anan tunda suka zo suke aikin bacci" Alhaji khaleed yace"A a Yaya baza'a yi hakaba" Hajiya kilishi tace"tun yaushe?" Dukansu dariya sukai, Nabiha tashigo dakin tana sake kunna turaren wuta. Daga nan su Alqali suka fita, Nabiha ma tasake fita taje takawo mata fruit, sannan ta zauna tana mata sannu. Saida taci ta qoshi Mamy tahado mata tea me shegen kauri shima tasha, sannan Hajiya kilishi ta kalli Captain Aryan tace"bata su tabasu susha" Ahankali yadauki guda daya yabata, ta kar6eshi, Hajiya kilishi ta fice, Mamy ma ta dauke sauran kwanunkan da Mawahib tagama cin abinci tace"Nabiha zo muje ki kawo wa Captain abinci" Nabiha tatashi tabi bayanta, Hajiya kilishi ta kalli Mamy cikin jin dadi yanda take kula da yaranta,Koda bata Raye ta tabbatar Mamy zata kula mata da yaranta, gashi de yazo tundaga Abuja babu wanda yayi tunanin bashi wani abun yaci, ciki harda ita, sai Mamyn ce tayi tunanin bashi. Captain Aryan yana ganin ficewarsu ya matso da daya yaron a hannunsa ya kalli Wanda yake hannun Mawahib sannan ya kalleta yace"kibashi mana" Ahankali tazuge zif din rigar ta tafuto da nonon ko brezia babu tafara bashi, Captain Aryan ya kalli breast din yanda suka sake cika yahadiye wani irin Saliva yana kallonsu da birge wa, ahankali ta runtse idonta tace"yanasha da zafi Yaya Captain" Cikin sauri yace"Honey wai bazaki dena cewa Yaya Captain dinnan ba?" Kallonsa tayi cikin wata irin hararar soyaiya, cikin shagwa6a tace"to ba Kaine kasa Ina zaman zamana yaranka sukazo suna neman kasheni ba, gashi yanzu suna shamin abu da zafi" Murmushi yayi cikin jin dadi yace"zaki daina jin zafin Honey,kiyi haquri please muntuba" Kallonsa tayi tace"Allah da zafi" Cikin kulawa yace"sorry,basu ahankali to" Haka ta daure taci gaba da basu duk da zafin datake ji. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Sai yamma Ashraf yadawo, kai tsaye suka dauke yaran shida Captain Aryan suka futo falo dasu wajan Hajiya kilishi, Mawahib kuma suka barta da Nabiha adakin,Ashraf yasake qarewa yaran kallo yace"Momy wannan ne babba,saboda haka shine Ashraf" Cikin sauri Captain Aryan yace"inji waye? saboda Kaine babba kuma yanzu ma saika za6i babban kace shine Ashraf?, to bazai iyu ba, suma suna girma haka babban zai iyo halin ka ya dinga cewa shine gaba da Aryan, saboda haka na sauya, yanzu Aryan ne babba, Ashraf qarami" Hajiya kilishi tace"Dan Allah sai yaushe zaku girma kudena musu akan waye babba waye qarami? Akan yayan naku ma saikun gwada halinku?, to duk ku barsu, uwarsu saita za6a da kanta waye zai zama babba waye qarami"(😂) Wannan furucin natane yasa sukai shiru tunda tabarwa uwar yaran wuqa da nama a hannunta. tunda akai haihuwar duk wasu masu zuwa barka anan falon Hajiya kilishi suke ganin yaran, Mawahib kuma tana cikin dakin tana hutawa, saide in yunwa suke ji sai Nabiha takawo mata su susha. Kwanan ta uku da haihuwa Alhaji Ma'aruf yazo yaga yaran, bai hadu da Mamy ba alokacin tana wajan aiki,duk wata kulawa data dace Hajiya kilishi tana bawa Mawahib,koda yaushe tana sakata tana zama acikin ruwan dumi saboda dinkin da'aka mata, tsakanin ta da yara saide in suna jin yunwa kawai, da rana haka zasu wuni suna bacci, da daddare kuma su hana Mawahib da Hajiya kilishi bacci da kukan su. Ana gobe suna suna zaune da Hajiya kilishi da Mamy da Mama Sadiya dukansu adakin Hajiya kilishin,Mawahib taci kwalliyar ta cikin riga da siket na leshi tayi kyau sosai duk da dare ne,ruwan tea takesha Abba yashigo dakin yadauki yaran Wanda idonsu yake qur akan hasken dakin, cikin kulawa Abba yace"suna tayaku fira kenan" Hajiya kilishi tace"wadannan? lumbu lumbu kenan, Ana jimawa zasu fara kuka kamar wanda ake zigasu, daya yana fara kuka Shima dayan zai farka yafara har tausayi uwar tasu take bani,haka zan yi juyi inganta daram a zaune tana faman jijjigasu, to sai in dauki daya in tayata Nima, amma bama bacci wallahi, nikuma lokacin danayi goyon su Ashraf bahaka nayi ba, kalau muke bacci" Abba yace"toku dinga hanasu baccin da rana mana Yaya" Hajiya kilishi tace"ana musu wanka ma idonsu a rufe yake, saide in wankan yayi wanka shine zasu farka,amma wannan kukan nasu yayi yawa, kamar hadin baki Yara kudinga ihun kuka cikin dare" Kafin Abba yabata amsa megadinsu yadoko sallama yafara ajiye wasu hadaddun akwatuna agabansu, mamaki ya kama su, kafin suyi magana Ashraf da Aryan ma sun shigo da wasu, wasa wasa saida suka ajiye akwatuna guda goma, na yara shida, kowa uku uku, na Mawahib kuma guda hudu. Abba ya kallesu yace"wannan kayan menene?" Ashraf yace" kayan Baby's ne dana mejego" Cikin sauri Abba yace"ba Maryam tasiyo wa yaran wasu kayan ba?, meza suyi da kayan har haka?" Captain Aryan da kansa yake qasa yace"Uncle ai basuda yawa" Abba yayi murmushi ya girgiza kansa sannan yafice daga dakin. Hajiya kilishi ta kalli Mama Sadiya tace"Sadiya bude mana kayan mugani" Kayan Mama Sadiya tafara budewa suna ganin hadaddun kayan baby's Kala Kala masu masifar kyau, Captain Aryan ya kalli Mawahib yanaso su ke6e amma babu dama, alama yayi mata akan ta duba wayarta, sannan suka fice daga dakin shida Ashraf. Ahankali ta dauki wayarta taduba taga yayi mata alert din kudi ko zatayi wasu buqatun dashi na suna. Saqo tafara tura masa tana masa fada akan yawan kudin dayake kashe musu, nan take ya tabbatar dashi da abunda ya mallaka duka mallakinta ne tayi yanda takeso dasu, haka suka dinga musayar saqo sai murmushi take saki ita kadai. Washegari akayi taron suna,yara sukaci sunan Ashraf da Aryan, kamar yanda mahaifiyar su ta za6a itama, saide babban tace a sakawa sunan Ashraf,a ko'ina babba babba ne, haka tatoshe kunnanta bayan kallon harara data samu daga wajan Yaya Captain bayan yaji hukuncin data yanke. Alhaji Ma'aruf yazo suna,shida matarsa murjanatu, Mamy taja murjanatu ajiki kamar qawarta, ganin yanda murjanatun take kulawa da Mawahib adan Zaman dasuka yi na wunin ranar,Mawahib tasha wanka yanda ya kamata, gida yacika dam da baqi, wasu dangin kilishi, wasu dangin Mama Sadiya, wasu kuma dangin su Alqali, wasu kuma dangin Mamy ne Yan maiduguri, idan kaga jama'ar da gidan Alqali ya dauka zaka rantse aure akeyi ba bikin sunaba. Captain Aryan yayi kokari sosai kuma ya kashe kudi kamar banza wajan ganin an wadata kowa da abinci da sha, yayinda Mamy ta dauki nauyin duk wasu abubuwan daza'a rabawa mutane na kyauta. Hajiya kilishi kuwa kasa zama tayi, anjima ki ganta acan, anjima kisake ganinta acan tana kula da baqi. Yayinda Mama Sadiya da Murjanatu matar Alhaji Ma'aruf dawata mata daga maiduguri suke kula da yaran, duk baccinsu kuwa yau ba suyi baccin ranaba saboda hayaniya dakuma yanda ake yawan daukar su. Murjanatu da Alhaji Ma'aruf basu tafi ba, saida suka kwana, dasafe da Murjanatu akai aikin gyaran gidan da komai, sukai suyar naman suna, suka gyara kitchen sannan da yamma sukai shirin tafiya itada Alhaji Ma'aruf, kafin su tafi saida Alhaji Ma'aruf yasake neman yafiyar Mamy ta kuma tabbatar masa komai yawuce, sannan suka tafi kebbi. Saida Captain Aryan yayi sati daya bayan suna, sannan ya shirya yatafi Abuja, Mawahib kuma sukaci gaba da wanka 6angare daya kuma yana tareda matarsa da baby's dinsa ta vedio call, kullum saiya gansu yakejin dadi. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 A wannan zaman wankan da Mawahib tayi,tasamu kulawa sosai,6angaren Mamy bata wasa da'ita wajan bata magunguna masu kyau na mata, amma Koda wasa bata ta6a bata maganin a gaban Hajiya kilishi ba, saide idan sun ke6e zata sata agaba saita sha duk wani magani na mata da tasan cewa zaiyi wa Mawahib din amfani,Mama Sadiya ma ba'a barta abayaba, ganin yanda Mamy ta zage dantse ta kula mata da Nabiha lokacin haihuwar ta ba tareda ko sisinta ba, hakan yasa itama tazauna da kanta tayi mata hadin kaza da nonon raqumi tasata agaba tacinye kazar tas, cikin sati uku kuwa saiga Mawahib tasake cika tayi wani fresh kasancewar ko cikin rana ba shiga takeba, hips dinta suka sake girma haka breast dinta ma, tana kula da yaran ta sosai bata gajiya da kukan su, haka dan dolenta tamaida tsarin baccinta yadawo irin nasu, da rana suyi bacci da daddare kuma ido biyu. Captain Aryan koda wasa baiyi kuskuren zuwa gidaba, saboda shi kansa yasan anbawa Mawahib tsaro yanda ya kamata, bai Isa ya tunkare taba. saide duk lokacin dasuke vedio call tana ganin irin ramewar da yayi. Hakan yasa suna zubarda wanka ya taho gida,afalon Hajiya kilishi ya sauka Mawahib tatashi tagabatar masa da abinci kala kala wanda tashiga kitchen da kanta tayi masa, duk inda tajuya kuwa idonsa yana yawo ajikinta kwata kwata ya manta da zaman Hajiya kilishi afalon, idan Mawahib tana wajan ita yake kallo, idan tabar wajan hankalinsa saiya dawo kan yaransa, yanda yake ganinsu a vedio call saiya ga sunfi haka warware wa, yadaga kansa ya kallo Hajiya kilishi yace"Momy yaran nan me ake basu ne naga sun qara girma haka?" Hajiya kilishi tace"babu abinda ake basu Babana,nonon uwar ne me kyau,kullum basuda aiki sai shan nono, shiyasa aikuwa gatanan duk sun tsotseta sai rama take" Cikin sauri Captain Aryan ya kalli Mawahib yaganta 6ul6ul masha Allah komai yacuko yayi girma, Yaya Momy takeso tazama kuma bayan haka? yaga alama jarabar shan nonon da yaransa sukeyi shine yasa Momy zata huce akan sa, kuma nono yanzu tafara bayarwa dan shima gashi yadawo yazama cikon na uku(🙊) Murmushi yayi a fili daga nan baice komai ba, Mawahib ta tsugunna tafara zuba masa abincin sannan ta dauke yaran daga cinyarsa shi kuma yafara cin abincin, Hajiya kilishi tazuba masa ido tana kallonsa cikin tausaya wa, yanda taga ya rame ta tabbatar ba qaramin qoqari yayi ba, musanman yanda taga yakama abincin da gaske yanaci, hakan yasa tagama yanke shawarar bashi matarsa yau su tafi dakinsa saboda da alama yana qirga kwanakin wankan Mawahib din duba da yanda bai qara mata ko kwana daya ba yadawo, ga wannan kallo dayake binta dashi, tajuya ta kalli Mawahib taga wayarta a hannunta tana dannawa, itade bataga iyayen nata su Sadiya da Maryam sun dan bata wani abu tasha ba, gashi shi Captain yariga yadawo, hakan yasa ta miqe tashiga kitchen din falon ta, tabude fridge dinta tana tunanin irin hadin dazata bawa Mawahib din domin tayiwa danta gata kasancewar ya rame dayawa tasan cewa yayi kokari, kankana ta yanka tahada da dabino, da cocumber , da ayaba, da kwakwa, tazuba peak ta ruwa gongoni daya, sannna tayi Blanding dinsa tajuye tasaka mata a fridge, tadawo falon ta zauna. Captain Aryan yana gama cin abinci yafice daga falon saboda idan yaci gaba da zama za'a Iya Samun matsala, kuma ga Momy akusa. Hajiya kilishi tana ganin yafita ta kalli Mawahib tace"kije fridge kidauko dan fruit nahada miki ki shanye shi duka" Mawahib ta kalleta da sauri,tasan batasan su Mamy da Mama Sadiya sun bata wannan abubuwan ba, har zataqi zuwa tasha saita ga kuma Hajiya kilishin zata Iya tambayarta dalili, hakan yasa babu musu tawuce taje ta dauka ta shanye tana mamakin irin qaunar dasuke wa Yaya Captain. Har qarfe goma nadare Captain bai shigo ba,Mawahib tana shirin kwanciya Hajiya kilishi tace"A a dauke su kutafi,mijinki yadawo Ina zaki kwanta anan,dauke su kuje shima yau yadana rashin baccin" Mawahib tayi murmushi ta dauki yaranta suka tafi dakin Yaya Captain, kwantar dasu tayi, tafara qoqarin kwanciya sai gashi yashigo dakin. Cikin sauri yaqaraso yasaka ta a jikinsa, yafara kissing dinta ahaukace,dagashi har ita wata irin ajiyar zuciya suke saukewa, bai bari tacire kayantaba yasaka hannunsa yayagasu. yanda ya birkice mata ne yasa ta garara yimasa magana, saida tafiya tayi nisa sannan tace"Baby munyi dakai fa bazan sake haihuwa ba" Cikin sauri yace"amma ai bamuyi dake ba zamuyi wannan abun ba..." Zata sake magana yahade bakinsu waje daya,sannan ya dauketa cak suka qarasa gadon, yanda yaji ta tsaf yanda yakeso hakan yasa daya fara surutansa tarufe masa baki, cikin ikon Allah bata barshi yayi musu tonon sililin daya sababa, saide abunda ya daurewa Mawahib kai ganin yaronsu ko guda daya babu wanda yafara alamun kuka, bayan komai yalafa sukai wanka yasaka ta a jikinsa ita kuma tasaka yaran agabanta tana masa mita itade karya yi mata wani cikin, shikuma gaba daya ya lalace awajan lalla6a ta, baccinsu sukai me dadi amma wani qarin mamakin Yara kamar sunsan ubansu yazo sun barshi yayi baccinsa yayinda suma sukai baccin. Da asuba bayan yadawo daga masallaci ya dauketa suka koma zasuci gaba da bacci kamar yanda suka saba, sai alokacin yara sukace basu san zance ba, Mawahib ta dauki daya tana lallashi, shima Captain yadauki daya, har gari yafara Haske suna kuka, Captain Aryan ya kalleta yace"wai haka suke wannan kukan?" Cikin sanyin jiki tace"haka suke,bama bacci da daddare nida Momy,yau dinma nayi mamaki da basu hanamu bacci ba" Cikin damuwa yace"inaga daga min qafa sukai" Dariya taso kama Mawahib saita fuske, hannunta yakamo yace"zauna kidan basu ko kadanne saimu kwanta wallahi bacci nakeji, kuma ni bazan Iya bacci Ina ganinki ba tareda naji ki ajikinaba" Babu musu tazauna, tafara bawa Ashraf nonon, cikin sauri yakama yafara sha. Captain Aryan yasaka hannunsa yaciro dayan tayi tunanin Aryan dinta zai bawa nonon saitaga yadora bakinsa yanasha ahankali, cikin jin dadi ta lumshe idonta tana sake riqe kansa. Aryan dayake hannun Captain Aryan yasaki wani irin kuka, cikin shaqaqqiyar murya Mawahib tace"Baby ka barshi yasha" bakinsa yadauke ahankali, sannan yasaka hannunsa yacire dayan datake bawa Ashraf, ya ajiye Ashraf din akan gado sannan yace "kibashi wannan mana" Yafadi hakan yana maida kansa yaci gaba da sha shima, Mawahib ta kalleshi ta girgiza kanta, taga alama nema yake dagashi har yaransa so suke su qarar da'ita. Ganin yaran sunyi shiru hakan yasa suka kwanta, saide bacci yana fara dadi suka sake sakin sabon kuka, cikin damuwa Captain yace"waiba sunsha nonon bane? me suke so kuma?" Mawahib tace"to ai baka barsu sunsha sun qoshi ba, kahanasu" Cikin damuwa yace"duk wannan dadewar dasukai sunasha be ishesuba sai d'an wanda nasha ne zaisa sukama kuka,? nasu ne ko nawane? hado musu kayansu daga yanzu sun koma wajan Momy da kwana"(🙊🙆🏻‍♀️😂) Babu musu tatashi ta dauki dan kayansu da tazo musu dashi, ta dauki Aryan yadauki Ashraf suka futo,itace agaba tana zuwa qofar daki taci karo dawata qatuwar kunama, cikin sauri tayi baya yace"Yaya Captain kunama" Cikin rashin damuwa yace"ki dauketa mana" Kallonsa tayi tace"haka kawai saika ce wanda nayi gamo zansa hannu na in dauki kunama?" Kansa yashafa, sai yanzu yatuna ashefa ba Ashraf bane,ya kalli yanbiyunsa, sannan yazo yawuce tagabanta ya dauke kunamar, Mawahib ta matso da sauri takama hannunsa tace"ina kunamar? bata cijekaba?" Baice mata komai ba yace"muje" Kanta ta daga masa suka futo daga dakin, alokacin gari harya gama wayewa safiya tayi, Hajiya kilishi tafuto zata shiga kitchen da flaks din tea a hannunta sai ganinsu tayi da yara a hannu, ga jakar pampers dinsu da sauran kayan buqata a hannun Captain, cikin mamaki ta tsaya tace"lafiya naganku sassafe? meyafaru?" Kafin su bata amsa Mamy tafuto daga kitchen din da alama itace take qoqarin hada break fast, itama taja ta tsaya, babu kunya Captain Aryan ya kalli hajiya kilishi yace" Momy dama sun dawo wajanki ne,mun bakisu"(😂🙆🏻‍♀️) Mamy tanajin haka ta kwashe da dariya, cikin sauri Captain da Mawahib suka juya, ganin Mamy yasa yayi saurin sunkuyar da kansa yana sosa qeyarsa. Mamy ta qaraso wajansu takalli Hajiya kilishi tace"Yaya yanaga kin bude baki kina kallonsu, ko bakyason kyautar da'aka miki?" Hajiya kilishi tace" Ina ganin ikon Allah ni kilishi, yanzu kai Aryan shine kasakota agaba kukazo kukawo min yara wato ni karna yi bacci ko?" Mamy tayi murmushi ta kalli Captain da Mawahib tace"kafin kuyi aure kuyi bacci, bayan kunyi aure ma kuyi bacci, waye yace muku yanzu lokacin bacci ne? ai wanda kukai abaya kunyi Iya rabonku,banda shirme wannan qananun yaran ne za'a rabasu da uwarsu ace sun koma wani waje? toku bani tunda bakwa so" Tafadi hakan tana meqa musu hannu, Captain da Mawahib suka hada ido,cikin sauri suka juya Sum sum suka koma dakinsu da yaransu. Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻 [7/22, 11:25 AM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Suna komawa daki Captain yayi tagumi hannu bibbiyu yana kallon yanda Mawahib ta goya Ashraf, Aryan kuma tana jijjigashi, wani irin tausayin tane ya kamashi, lalle in hakane Momy tayi qoqari, ahankali yatashi ya kar6i Aryan yafara jijjigashi yana zagaye dakin dashi. Cikin kulawa tace"Yaya Captain kakawo shi saika kwanta kahuta" Shiru yayi bai tanka mataba, tasake kallonsa tace"please" Kallonta yayi yace"kidena fadamin sunan nan mana Honey" Murmushi tayi tace"to Baby, Baby na kawo shi ka kwanta kahuta" Sunkuyawa yayi yadora Aryan abayansa sannan yafara jijjigashi yace"da'inada damar dazan dauke ciwon naquda dana dauke miki Honey,meyasa rainon yaranmu zan barki kiyi ke kadai?" Murmushi tayi cikin ranta tana jin yanda soyaiyar mijinta takesake nunkuwa acikin Zuciyarta, haka suka dinga lallashin yaran har sukai nasarar sakasu bacci sannan suka kwanta gaba dayansu sukai baccin. Kwanan Captain Aryan uku agida sannan sukai shirin komawa Abuja,Hajiya kilishi tahada wa Mawahib kayan tsaraba sosai musanman abubuwan girki,Mamy tasake yimata nasiha akan kula da mijinta, bayan sun futo zasu wuce Mamy tayi mata sallama saboda gobe zata wuce maiduguri wajan bikin Nabil. Ashraf da Nabiha ne suka rakasu Airport, saida jirgin su yatashi sannan suka dawo gida. Da daddare suka sauka agida, gaba dayansu dakin Mawahib suka wuce suka gabatar da sallah sannan Mawahib tacire kayan jikinta tafara gyaran gidan, ganin yaran basa kuka hakan yasa shima Captain yazage sukai aikin tare, sai wajan qarfe tara suka gama aikin komai, kayan Yara ma suka adanasu inda yadace,batayi girki ba sai fita yayi yanemo musu abinci, sunacin abincin yaran suna gefen su kwance akan kujera, bayan sungama cin abincin tagyara wajan sannan tadawo falon, tun kafin ta zauna Captain Aryan yabata hannunsa, babu musu tasaka hannunta cikin nasa, yajata jikinsa tazauna akan cinyarsa, yayinda tadora kanta akan qirjinsa tayi luf. Sunkuyawa yayi, yayi kissing dogon gashinta, sannan yasaka hannunsa ya sarqe musu hannun cikin na juna yace"Honey kode muyiwa Mamy magana asamo mana wadda zata dinga tayaki raino?" Cikin sauri tadago kanta ta kalleshi tace"me raino kuma? haka kawai daga zuwa rainon yara takoma rainon mijina?" Cikin sauri Captain Aryan yayi dariya yace"waye yace miki akwai wacce zataci gaba da raino na bayan ke?,Momy da Mamy sungama nasu, har abada kece zakici gaba da raino na nida yarana,Ina tausayin aikin dakike ne,kinashan wahala Honey..." Kanta ta girgiza takama fuskarsa ta riqe tace"zanci gaba da kula daku har abada,bana fatan wata daban tashigo cikin rayuwar mu harta zama silar Samun sa6anina da mijina, Allah n daya bani su yasan zan kula dasune shiyasa,karka manta ubangiji baya jarabtar bawa da abinda bazai iyaba" Kansa ya daga mata alamun gamsuwa da maganar tata,ahankali takoma cikin jikinsa ta kwantar da kanta akan qirjinsa, hannunsa yasaka yafara shafa dogon gashinta, yadaga kansa ya kalli yaransu da Mawahib tasaka musu kan fida a bakinsu sai tsotsa suke, dukansu idonsu biyu. Mawahib tace"Baby da tuni nasa Mamy tamin allurar planning fa" Cikin sauri ya kalleta yace"saboda me? meyasa?" Dagowa tayi ta kalleshi tace"saboda munyi dakai mundena haihuwa" Idonsa ya lumshe sannan yabude yace"yanzu de tayi miki kokuma bata miki ba?" Kai tsaye tace"batamin ba" Wata irin ajiyar zuciya ya sauke sannan ya rungume ta yace"bazamu yi planning ba, insha Allah zanyi bakin qoqari na Inga nayi abinda yadace baki samu ciki yanzu ba" Ajiyar zuciya tasauke tasake shige wa jikinsa, ahankali yafara shafa jikinta yana shaqar qamshin jikinta, cikin wata irin murya yace"Honey yarannan basa kuka yanzu,please inyi?" Babu musu tadaga masa kanta, anan falon suka fara sha'anin su gaba dayansu sunfi ta daga hayyacinsu, Captain Aryan bai samu qwarin gwiwar daukanta zuwa sama ba, afalonsu suke gudanar da komai, yayinda tabar masa bakinsa abude itama tabude nata suka dinga zuba ihu San ransu, saida tafiya tayi nisan gaske, sannan yanbiyunsu suka fara kuka, Aryan ne yafara kuka shima Ashraf yafara, gaba daya yaran suka kaure da kuka sakamakon bakin fidarsu daya fice daga bakinsu, sai falon na Mawahib yakaure da kuka Kala biyu,yara suna kukan neman ceto, manya suna najin dadi, Koda wasa daga Mawahib har Captain babu wanda ya'iya yunqurin haquri da daya domin adauki yaran, suna jin kukan yaran sama sama,amma basu haqura da juna ba saida suka samu nutsuwa, Captain Aryan ya kwanta awajan yana sake maida numfashi, yayinda Mawahib tayi kokari tatashi zaune ta dauki yaran tafara basu nono, Captain Aryan kuwa idonsa a lumshe suke yana maida numfashi har lokacin, yana jin yanda take lallashin yaran amma yakasa Koda qwaqwqwaran motsi ne. Washegari da safe Captain bai fita aiki ba, tun safe Mawahib take aiki saboda abokan Captain daza suzo domin ganin Yara, sai azahar sukazo sunji dadin yanda Mawahib ta karbesu, sunci sunsha sunyiwa Yara pictures, daga Nan sukai shirin tafiya inda suka ajiye wa yanbiyu kyaututtuka sosai. Bayan sun tafi Mawahib tabar yaran wajan Captain Aryan tagyara gidanta tsaf,sannan tahau sama duk wani kayan sakawarta manya ta lodeshi waje daya, sai rigunan sallah data ware da hijabai na sallah, duk wasu manyan kaya datake amfani dasu ta ajiyesu sai qananun kaya saboda rainon yanbiyu. Captain Aryan yashigo dakin hannunsa daukeda yaran, ya kwantar dasu a gadon shima ya kwanta, ya ajiye mata wasu kudi akan gadon,sannan shima ya kwanta. Wayar Mawahib datake gefen Captain tayi qara,yadauka zai bata sai idonsa ya sauka akan sunan b me kiran, lokaci daya ransa yayi baqiqqirin tun kafin ta qaraso ta dauki wayar ya wullar da wayar akan gadon. Mawahib ta kalleshi cikin mamaki ganin lokaci daya yanayinsa ya sauya, wayar ta kalla taga sunan Yaya Nabila yana yawo a fuskar wayar, ajiyar zuciya tayi ta dauka suka gaisa tayi masa ala Sanya Alkhairi akan aurensa sannan takashe wayar, tadawo gefen Captain ta zauna takama hannunsa ta riqe tace"meyafaru naga yanayin ka ya sauya?" Cikin 6acin rai yace"oho" Murmushi tayi tace"saboda Yaya Nabil yakirani?,bafa komai yacemin ba, kawai fadamin yayi cewa yayi aure yau,nayi masa ala Sanya Alkhairi shikkenan fa" Cikin wata irin masifa yace"to saboda me zai kiraki? daya kiraki danme zaki dauka? saina futo fili nafada miki banason kina waya da wannan yaron sannan ne zaki fasa amsa wayarsa? cemasa akai bakisan bikinba? kokuma dole ne sai yaji muryarki sannan zai iya zaman auren?" Mawahib ta girgiza kanta cikin damuwa,ashe yasan auren Nabil din amma koda wasa bai nuna mata ba,cikin damuwa tace" Yaya Captain Yaya Nabil yayanane fa" Cikin sauri Shima yace"nima Asalamiyya ai yar'uwa tace" Lokaci daya ranta ya6aci jin yakira sunan Asalamiyya,wayarta tabude ta bashi number Nabil din sannan tace"gashinan rufe number sa" Babu musu ya kar6i wayar yayi blocking number Nabil sannan ya ajiye wayar. Ta kalli kudin gefensa tace"wannan kudin menene?" Murya ciki ciki yace"nakine" Kallonsa tayi taga har lokacin baisa ki fuskarsa ba,tace"mekace?" Cikin 6acin rai yace"nace miki nakine ha'a" Dariya ce taso kamata,saitayi fuska ganin yanda yahade rai,cikin rashin sani tace"nawa kuma? yaushe nabaka kudi?" "na Abbah" Shine kawai abinda yace mata,lokaci daya ta dauki haske,wato kudin da Alhaji Ma'aruf yabata ne tun lokacin dayazo gidansu shida abokinsa harta bashi ajiya. Murmushi tayi ta matso kusa dashi tadauki kansa ta dora akan cinyarta, ta sassauta muryar ta cikin sigar lallashi tace"fishin ne har yanzu?" Shiru yayi yarabu da'ita, tasake sassauta murya tace" I'm sorry" Cikin damuwa yajuya kansa gefe,tasaka hannu ta riqe kansa tace"me kakeso?" Juyowa yayi yace"ke nakeso Honey" Cikin jin dadi tace"amma kake fishi da Honeynka?" Cikin shagwa6a yace"bakinsan menake soba?" Murmushi tayi tadora bakinta akan nasa tafara kissing dinsa, ahankali yamiqo hannunsa yakama breast dinta,sun dade a wannan halin saida ta tabbatar yadena fishin sannan ta rabu dashi. Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼 Tundaga wannan rana Mawahib tadena saka manyan kaya,kullum tana cikin qananun kaya gajeren wando kokuma dan qaramin siket, riga kuwa saide tasa marar hannu yar qarama, kokuma doguwar riga wadda tsawonta bai wuce cinyarta ba, dan dolenta ta qware wajan yimusu wanka, haka cikin sauri take shirya su sannan ta basu susha takama ayyukan gida, kwata kwata batada lokacin kanta saina yaran, idan tana girki taji sunfara kuka haka zata kashe gas din tafuto ta basu nono, sannan ta jijjigasu suyi shiru takoma kitchen, haka zata sakasu agaba ta dinga magana dasu kamar suna jin abinda take fada. Da weekend tana aikin gida da girki Captain Aryan yadauko sauran kayan wankin yaran wanda ake saka musu nashan is'ka yasaka su cikin washing machine yana tayata wankin, kuka suka fara hakan yasa yabar wajan wankin kayan nasu yadawo yadauke su yafara yimusu wasa amma sukaqi yin shiru,saida Mawahib tazo suka hadu suka lallashesu sannan sukai shiru. Haka suke gudanar da rayuwar su gwanin sha'awa,idan weekend yazo komai tare sukeyi, ranakun aiki kuma yana tayata da wasu abubuwan idan baigaji ba. Watansu uku tafara koya musu zama, har tsawon wannan lokacin basuje gidaba,sun maida hankali wajan kula da yaran su yanda yadace. Adede lokacin sukai shirin tafiya Umara shida Ashraf da Nabiha da Lil Aryan, saikuma Mawahib da yanbiyun ta,saida su Ashraf da Nabiha sukai kwana daya a Abuja sannan Washegari suka shirya tsaf suka tafi Airport domin wucewa Saudia. Sunyi mutuqar kyau gaba dayansu musanman Mawahib da Captain Aryan. Mawahib tasake girma da fari, daga ita har Captain Aryan sun saka glass a fuskarsu, tana riqeda Aryan, yana riqeda Ashraf, yayinda Ashraf yake riqeda Lil Aryan, Nabiha kuma tana waya da mutanan gida, babu wanda basu birge ba a Airport din, duk inda suka juya kallonsu ake. Satinsu biyu a Saudia suka dawo, anan Abuja suka sauka saida suka huta tsawon kwana biyu sannan su Nabiha suka tafi, Mawahib tahada mata tsarabar Yan gida duka tatafi musu dashi. Watansu Ashraf da Aryan hudu, zamansu yayi nisa sosai,Mawahib bata takura musu da saka kaya me nauyi kullum cikin qananun kaya yaran suke,zuwa wannan lokacin kuwa sun daina kukan dare, kalau suke baccinsu yayinda Captain Aryan yake sha'anin sa cikin dare son ransa, har yanzu Captain Aryan baiyi kuskuren da Mawahib zata samu ciki ba, yana bakin kokarin sa wajan kaucewa abun dazai zuba mata domin tasamu cikin kamar yanda Manzon Allah yakoyar, saide idan abun ya qwace masa babu yanda ya'iya kasa jurewa yake, amma duk da hakan suna nan kalau babu alamun ciki, Nabiha ma shiru babu ciki. Ganin Zaman yanbiyu yayi qwari hakan yasa Captain Aryan yasiyo musu wata kujera kowa tasa, kujerar daga Samanta akwai abun wasan Yara dayake qara yana yawo, idan Mawahib tana so tayi aikinta cikin kwanciyar hankali zata saka kowa acikin tasa kujerar ta barsu afalo ita kuma tashige kitchen, haka zasu dinga daga hannu suna qoqarin kamo wannan abun wasan, dahaka take yaudarar su tayi aikinta hankali kwance. yauma bayan tagama aikinta itama shiryawa tayi tsaf, tadawo falo ta zauna a kujera tana kallo cikin jin dadin yanda tagama aikin komai na gida, tagyara gida gidanta yana tashin qamshi, ga kuma girki tagama a dining, ta kalli yaranta dasuke Sanye da pampers aqasan Capet Aryan yana wasa Ashraf kuma yakifa cikinsa yana qoqarin karya gwiwa yanason yin rarrafe, ganin yakasa yin rarrafen yasa ya kalleta yafashe da kuka, ta ajiye remote din hannunta tadaukeshi tasaka masa nono a bakinsa tana fadin "toyi shiru sha nononka karka ragewa Aryan" Lokaci daya yaron yayi shiru yanashan nonon, yakai hannunsa yaja dankunnanta, cikin azaba tace"Ashraf cikamin kunne karka yagamin shi" Aryan dayake wasa aqasa yadago kansa yana kallonsu, ta sunkuya ta dauke shi tace"kaima taho kasha" Tana miqa masa hannu ya taho, tadaukeshi shima taciro dayan nonon ta bashi, shima yana farasha yafara tsone mata ido, ta janye hannunsa tace"kubari bazaku nakasa niba" Adede lokacin Captain Aryan yadawo daga aiki, zama yayi agefen ta ya kalli yanda take shayar dasu duka su biyun, ya kalleta cikin soyaiya yace"akwai zafi?" Kanta ta girgiza masa tace"babu zafi Baby,yanzu kam ai nadade da sabawa" Tana fadar haka tacire musu nonon daga bakinsu tabawa Captain Aryan su, sannan tatashi tace"muje kayi wanka Kaci abinci" Tashi sukai suka tafi sama yaran suna hannun Captain gaba dayansu. Itace ta taimaka masa yayi wanka, sannan suka dawo falon, tahadowa yaran Custard,shima Captain tahado masa nasa abincin, tana zuwa zata zauna yajata tazauna akan cinyarsa, babu musu tazauna tadauki spoon tafara bashi abincin, suma tasaka nasu qaramin spoon din irinna Yara ta zaunar dasu sosai tana basu ahankali, Captain Aryan ya kalleta cikeda soyaiya ganin yanda gaba dayansu su ukun take ciyar dasu cikin nutsuwa, kafin ace yagama tauna nabakinsa ya cinye, harta bawa yanbiyu nasu, suma kafin su shanye tadawo tasake bawa Captain Aryan nasa,cikin jin dadi yasake jin nutsuwa dakuma qaunar ta suna sake shigar sa saboda yanda ubangiji yayi masa baiwar Samun ta amatsayin mata, ahankali yazura hannunsa cikin rigar ta ya damqi nashanunta yana matsawa, kallonsa tayi suka saki murmushi atare tashige jikinsa tana murmushi, sannan tadago taci gaba dabasu abincin. Da daddare adakinsa suka kwanta gaba dayansu, tasaka yaranta agaba yaran suna baccinsu cikin jin dadi, ita kuma duka jikinta yana cikin bargo itada Captain, amma kansu zuwa qirjinsu a waje yake,qaran esi ne yake tashi adakin sai nishin da Captain Aryan yake saki ahankali, kansa yana cikin wuyanta yana shaqar qamshin ta,sha'anin su suke hankali kwance,yana daga bayanta yana abunda yakeso, yayinda Mawahib ta lumshe idonta tana sake tayashi sai nishi take itama, akwai tazara tsakanin ta da yaran hakan yasa yanda Captain Aryan din yake motsa mata jiki bai tashi yaran ba,ahaka ya dinga sha'anin sa har zuwa lokacin dasuka samu nutsuwa ya dinga kissing wuyanta. *Bayan wasu shekaru* Wajan taron Sojojin cike yake da manyan baqi kama daga iyaye yan'uwa da sauran manyan qusoshun gomnati, sai kuma sojoji manya da yaran su. Cikin wanda suka halarci wannan taro harda jama'ar gidan Alqali gaba dayansu, tundaga kan Alqali,Alhaji khaleed,Alhaji Isah, Hajiya kilishi, Mama Sadiya, Mamy, Ashraf da Nabiha da lil Aryan din Nabiha, saikuma wani jaririn yaro a hannun Nabiha fari tas dashi kyakykywan gaske, sai Mawahib da d'an qaramin cikinta, yanbiyunta suna ta wasa awajan sunqi zama waje daya, sai Alhaji Ma'aruf da matarsa Murjanatu. Kyautar girmamawa ake bawa manyan sojoji Wanda suka zage dantse wajan ganin sunbawa qasa tsaro da kulawa yanda ya kamata, kamar daga sama aka fara Kiran COLONEL ARYAN I. ALQALI. Farinciki ya wanzu akan fuskar familyn Alqali, musanman Mawahib da bakinta yaqi rufuwa sai tafi ake masa, tashi yayi yaje yasa rawa Mai basu award din, sannan ya kar6i nasa, babu abinda kake gani awajan sai hasken yanda Camera take aiki wajan daukar sa photo, Mawahib ta kalleshi tasakar wa hannunta kiss sannan tahura masa. Yana juyowa kai tsaye wajanta yanufa yazauna sannan yabata award din, kissing din award din tayi sannan tabawa su Hajiya kilishi, tajuyo ta kalleshi takama hannunsa ta riqe tace"ina Alfahri dakai mijina,a ko'ina na tsinci kaina zanyi Alfahri kasance wata matar soja,ubangiji Allah yakare min kai Yaya Aryan..." Cikin sauri yace"what...?, menene Yaya Aryan kuma? Honey Babyn ma bazan samu ba?" Murmushi tayi takama dantsan hannunsa na hagu ta rungume,sannan tamotsa qaramin lips dinta tayi masa kiss tahura masa, sannan tace"nadena, amma kasani,daga yau kabar Yaya Aryan,kabar Baby,kabar Yaya Captain,saide Yaya Colonel" Murmushin jin dadi yasaki bai duba irin jama'ar dasuke wajanba yadora kansa akan kafadarta,hannunsa yanakan d'an qaramin cikinta yana shafawa wanda yake fatan shima tasake haifo masa wasu yanbiyun.❤️ *TAMMAT BI HAMDULLAH* anan na kawo qarshan novel dina maisuna *MAWAHIB* Alkhairin dake cikin wannan labari Ina roqon Allah ya sadamu dashi, Sharrin dake cikinsa Allah yayi mana tsari dashi,Allah yabamu ikon yin amfani da kyawawan darrusan dake cikin wannan labari. Idan akwai wadda nayiwa laifi sanadin wannan labarin kokuma narubuta wani abu wanda ya6ata masa rai bai gamseshi ba, Ina roqon sa yayafemin dan'adam ajizi ne🙏🏻. Insha Allah bayan nahuta, nan bada jimawa ba zaku jini asabon littafi na maisuna ME 'DEBE KEWA ('yar me gwanjo) shina so nafara rubuta muku kafin MAWAHIB to amma ganin yanda yakeda yawa hakan yasa na jingine shi agefe saboda kada a dinga jirana dayawa,insha Allah jiran dakuka min a Mawahib bazaku sake irinsa ba,amma saina huta, Kunsan de Amnah tana daukan lokaci kafin tafara novel amma muddin nafara novel kafara karantawa to nasan cewa ko d'an kadanne sai labari na ya birgeka,kuma kullum sainayi posting,za'a jirani kafin nafara amma idan nafara posting babu tsaye-tsaye 😂 Kamar yanda wasunku sukamin complain cewa kudin Mawahib yayi yawa sbd yanayin rayuwa to insha Allahu zanyi kokari Inga kun samu ME 'DEBE KEWA kan farashi me sauqi 👌🏻 Amma ni aganina dan mutum yasai novel 500 inde labarin yayi dadi aiba laifi bane. masu tambayata novel dina nagaba free zanyi suma suyi haquri bazan Iya rubuta labarin ME 'DEBE KEWA free ba,saboda nasan salon rubutuna, bazan ziga labari naba saide mutum ya karanta da kansa saiya tabbatar da haka 👌🏻🥰 Alhamdulillah kowacce shekara Idan ubangiji yabani dama da lafiya da lokaci Ina rubuta novel guda biyu,☺️ 2022 narubuta BABBAN YAYA da SHAHAAB 2023 narubuta MAWAHIB, saura kuma ME 'DEBE KEWA insha Allah 💃🏼 Ina fatan ya birgeku fiyeda MAWAHIB zanyi missing dinku fan's,Allah yasake sadamu da Alkhairin sa🤲🏻😥 Yanda muka hadu a wannan group Ina roqon Allah yasa muhadu a aljanna baki dayanmu. saimun hadu acikin littafin ME 'DEBE KEWA🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ Koda yaushe Karku manta da sunan Amnah El Yaqoub,saboda nima akoda yaushe masoyana suna cikin raina, nagode🙏🏻 Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Idan kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki Amnah El Yaqoub✍🏻