[11/20, 2:59 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwa ne, idan kinsan baki biyaba dan Allah karki karanta, bazan miki Allah ya isaba koban fad'a ba dama Allah ishashene kowa sani, dan haka idan kinga daidaine seki karanta* 0 Dukda nasarar shigewar da Abu huraira yae hakan be hanawa murfin motar dakar k'afarshi ba, da sauri ya rufe motar suka soma zarar ido suna bin halittar datayi burki tana kallonsu harshe a waje, bazasu iya gano ko wace halitta bace ba amma tabbas bazaki bane ba, hasken dake nan na farin wata baze basu damar ganin abun da kyau ba, sedai koma miye muguwar halittace kuma taso cutar dasu, haka tafi 1 hour tana zagayen su su kuwa se had'a gumi sukeyi dukkansu acikin mugun tashin hankali suke mara misaltuwa, daga bisani dabbar ta wuce abunta kuma, dukda haka sun kasa sakin jikinsu gashi k'afar ta Abu Huraira tana masa zogi, Allah ne ya taimakeshi amma ya bugu da kyau, Tawayen sane yaja masa qafar gaba man zafi haka sukai masa luddan gaske suka rage glass na motar sabida ventilation ya shigo sosai. ************* Yau daikam baccin ma babu wanda yayi shi acikinsu, da asuba haka suka daure suka cire tsoro suka sakko sukai alwala sukai salla, sun jima suna adu'o'i har gari ya waye sannan suka k'urawa inda suke ido, kowa hankalinsa atashe yake "Abu Huraira ni wlhy tsoro nakeji, nagaji kuma inaso inje gun Mom ma" dama yasan halin rikicin d'an uwansa shi arayuwa bayason takura ko rayuwan wahala sam "Haba Twin? Kayi hakuri mana, ya zaka sako zancen gajiya agun dababu alamun mutane ma bare musamu maceci? Wannan wurin abu d'aya zan sanar daku ku saka aranku cewan Allah ne kawai ze fitar damu a wannan jejin, so acire zancen zuwa gida yanzu, Allah dai ya rufa mana asirin mu ya nuna mana hanyar barin wannan gun acikin sauqi" Kallonsa kurin yae amma bece qala ba, hankalinsa atashe yake dan shima ya hango abin, ga basuda mai isashe danko rabin tanki basu dashi.... *********** "Haj na sanar dake yaran nan suna lafiya, mesa kike hakane wai?, ni kinga yau zanje ghana tafiyar nan ta aikice ba fashi, bazanji dad'i ba ace wai na barki a wannan halin, ki kwantar da hankali, na tura su barde mota biyu da sojoji tare dashi mukaje kaita wancen lokacin yasan k'auyen inyaso su duba idan sun baro ne se aduba ko ina, bana tunanin komai amma an sanar dani wai wataqil sun saki hanyane, dan inka shiga jejin rud'u ne dashi amma babu namun jeji sosai a wurin dan haka kiyita adu'a, kinji" Nisawa tae yanzu kam "To hakan ma yayi Allah ya tsare munkai su kuma ya bayyanar dasu cikin qoshin lafiya" murmushi yae ya shafi gefen fuskarta "Ayita adu'a hajiyan general, Allah ya bayyanar mana dasu" Murmushi ta rakashi dashi kurun harya bar gidan. ******'''''''******'''''''******* Tafiyar nan dai anyita babu ji ba gani, amma ba alamun gari agaba ko kuma abayansu abu huraira, basuda wata torchlight seta waya, gabaki d'ayan hankulansu sun tashi, tuni man motarsu ya k'are qaf, gasu a tsakiyar jeji ba hanyan gaba babu na baya, suna gudun su taka konan dacen ne azo kuma idan anga abun tsoro ba wurin b'uta, acikin k'ank'anin lokaci duksun rame sun zagbe "Bana tunanin shawarace me kya barin gun motar nan da yamman nan, kurun mu kwana kaman yanda muka saba, inyaso da safe semu soma cin kasar" jinjina kai Dawud yae cikin gamsuwa da bayanin Abu sufyan "Hakan yayi, mu kwana amma fa idan muka cinye cake da wancen bushashen donut ko shakka banayi se yunwa ta hallakar damu idan bamu b'ulle tafiyar jejin nanba gobe, sabida bamuda sauran wata madafa" Girgiza kai Abu hurairah yae "Allah yasoma acikin k'aramar jakar cen ta baya akwai cookies me yawa da cyama ta mana, bamuko tab'a shiba, idan zaku tafi mu kwashe bread da Baba ladi ta bari dukda ya soma sandarewa" Babu wanda yae magana yammakam acikin bayan motar suka kwana dukansu a takure rayuka ba dad'i. *********** Sallan Asuba kurun suka idar suka kama hanyar dasuke tunanin itace me b'ullewa, badan zukatan su sunyi na'am da bin hanyar ba sedan basuda wani zab'in daya wuce wannan. *********** Zaman shiru ne ya ratsa wurin na kusan dak'ik'u sama da hamsin kasamcewar hanyar dasuke tunanin itace har sukai tattakin binta ta b'acewa ganin su, mamakin ganin agaban wannan babban Tekun sukeyi tunda yake sun sandai mota bata tsallaka ruwa, kuma su sam basu bi wannan hanyar ba, agogo Abu sufyan ya kalla dake d'aure a wutsiyar hannunsa k'arfe biyar da rabi na yammaci, tun asuba suka kamo hanya da k'afa kasamcewar motarsu ba mai, gasu d'auke da kayan abinci na flour da ruwan sha, ga daddumar sallah, sun gaji iya gajiya idan ba wannan hanyar bace ba ana nufi juyawa zasuyi su koma baya kenan? Subar jejin yaushe? Koda yake har suka iso nan babu wara dabba dasuka had'u da ita idan ba tsuntsaye da k'adan garu ba,se kulb'a dasuka gani so d'aya jal! Shiru kowa da abinda yake sak'awa aranshi secen Abu Huraira yace "Ku tashi mu mik'i hanya muga ko zamu kai k'arshen kogin nan, bana tunanin ma a Nigeria muke yanzu kam watak'il tunda kukaga ruwa idan muka tsallaka zamu samu hanyan b'ullewa mu fita daga cikin wannan doguwar hanyar mara hanyoyin b'ullewa danni fa a gaskia na sare ma da rayuwar gabaki d'ayanta" Nannauyar ajiyar zuciya Dawud ya sauke "Hakane mu zagaye mugani, tunda akwai ruwa da ikon Allah zamu akwai gari a kusa" Haka suka mik'i hanyar zagayen babban ruwan dabashida iyaka dan basako hango k'arshen sa takowane kwana. Sunyi kusan awa d'aya babu labarin k'arshen ruwa ga magrib tayi duhu ya sauka sallah suka tsaya sukayi, da ruwan sukai alwala bayan sun idar suka karanci alkur'ani me girma sannan suka suka zauna suka jira zuwan isha suna idarwa suka kunna torchlight ta wayan Dawud dama irin me hasken nan ce ga wayar tana baiwa wata wayar charge ma suka qarayi gaba, basa so su kwana abakin teku, so suke suga wuri me yalwar fili sabida tsaro. ************** Hankalin sarkin atashe yake sabida yau saura kwana bakwai ayi sacrifice da rayuwar wani me tsautsayin tsallakar tekun ya shigo garin su, gashi har yanzu shiru, wani daga garin be tsallaka ba gashi wani daga wani garin be fito ba, idan har sati ya zago batare da ansamu wanda za'a sadaukar ba shi za'a yanka, kuma a k'ona iyalanshi da ransu, shekararsa ashirin da uku kan mulki wannan ne karon farko dayazo saura kwanaki bakwai batare da ansamo me tsautsayin daya tsallako ba koya fita ba, sun tura jirgi yakai bakwai amma shiru kakeji kanshibya matuk'ar d'aure....se zagaye yake a d'akin shishi kad'ai yana zare idanshi, batun yauba yaso ya kashe wannan bak'ar al'adar amma be samu dama ba har yanzu, duk yanda yaso bokan garin baya barin sa, shikad'aine sarkin dayae shekaru masu yawa ma, sauran duk basa wuce uku biyar zuwa bakwai, cikin damuwa matarsa ta kallesa da yaren dabaka gane wane iri ne tace dashi "Nayi mafarki wani zezo ko saura kwana d'aya ne, kayi hak'uri k'uru" kallonta yae cikin damuwa "K'uruwa, idan kuma ba haka bane fa, rayuwar mu duk k'arewa zatayi " "Shekaru da yawa kanayi, kaine me tarihi kayi shekaru da yawa kanayi, ko yanzu zakayi" zama yae kusa da ita "K'uruwa idan yakai saura kwana d'aya bezoba zamu gudu da dare, nasan hanyoyi da yawa bani bari akashe mu" Cikin damuwa tace "Ze mazo kaji?" Shiru dukkansu sukayi ba wanda ya k'ara cewa komai, Lawuri dake kwance tana jin me suke cewa ta share k'wallan daya zubo mata, ita tasan mutuwa ma zasuyi ko basu gudu ba ita zata gudu gobe gobe ma, bazata bari a kashe ta a banza ba........ ****** Littafina na kud'ine, dan Allah idan baki biyaba karki karanta mun, idan kinaso kinsiya ki tuntub'i wannan lambar...07084161619. ********** Wannan daren a zaune suka kwana dukkansu, babu wani wanda ya iya runtsawa acikin su, ga mamakin su safiyar Allah suna tashi sega jirgin ruwa abakin teku, basuga wanda ya kawo ba, kurun dai suna tunanin cewar daga wata gab'a yazo nan koda yake ba kusa da tekun suka kwanta ba, sunga yana hawowa idan yazo da gudu watak'il wasune suka ajiye in hakane su ara kawai su tsallaka ruwan, a gurguje sukayi sallah, sunyi mintuna goma suna adu'a kafin su shiga jirgin suka d'auki falankan da ake turawa dake shinfid'e acikin jirgin suka somayi kamar yanda suke gani anayi a film..... ******** Lawuri kuwa ta gama shirinta tsaf acikin dare taje bakin tekun, tana jiran zuwan saurayinta Mik'aru, shine ze taimaka mata subar garin sabida a tsorace suke, sun gano kashe sarki za'ayi lokacin mutuwar sa yayi, kuma idan har aka kashe sa to kuwa tabbas ita mazajen garin zasuta amfani amfani da ita layi layi harseta mutu, kasancewarta mace kuma 'yar fari, sauran 'yan gidan kuma za'a qonasu, idan akayi amfani da ita so 100 bata mutu ba to da ranta za'a binne ta, acewar su tun daga ka kanin ka kanni idan sarki ya gagara kawo wanda za'a sadaukar idan ba'a kashesa da iyalansa ba wani mugun abu ze faru a garin wanda ze iya kashe kowa da kowa ma. Mom Nu'aiym 03 [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* 01. Ko kad'an bazaka ce ya tab'ayin dariya bama idan ka kalli fuskar sa yayi wani kici kicin da fuskar nan sekace wanda aka aikowa da manzon ranar mutuwar sa, cikin tsare gida mahaifin sa ke kallon sa "Yaya zakace bazaka ba? Ni kakeso naje kokuma so kakeyi ka mayar dani sa'anka sarai ka sani bana sauya hukuncina, baiwar Allah nan tayi shekaru masu yawa bataje gidansu ba, sabida haka kai da kuma Abu huraira kune zakuje ku kaita idan yaso ku dawo city ku jirata daga nan baya ta kammala adadin kwanakin data gaya muku zatayi seku koma ku d'akko ta tunda yake tafiyar akwai nisa daga nan DOGUWAR HANYA ce zakubi" Be isa ya k'arayin gaddama dan haka cikin girmamawa yace "Kayi Hak'uri dad, dama ban fahimci manufar kaba ne se yanzu, yaushe zamu tafi to?" Kallon sa uban yae "Kuje ranar Juma'a da safe" iyakar abinda General ya fad'a kenan ya mik'e cikin isa dajin mulki ya haura saman sa ransa ad'an b'ace, besan meyake sa Abu Sufyan yake da kafiya ba akan al'amura wataqil kuma halin sane daya gada yakeso ya masa fintinkau akan halin. Abu sufyan yana mik'ewa hanyar waje ya nufa, sojoji se k'ame masa sukeyi kkallon su beyi ba yau ran maza ya b'aci, kurun shi dad baze saurari uzurin mutum ba seya wani kafe akan seyayi abu, yana da hidimomin gabansa yazece seyaje har wannan garin abin haushin ma acikin k'auye irin wannan tafiyar wahala ce zasuyi yasani tabbas dan kuwa akwai direbobi masu tulin yawa agidan, sesuje da ita mana amma dan wani neman rigima dad har yace ita zata fad'i adadin kwanakin datakeso su duk uzurinsu ya zamto na banza kenan? Haba dad sam baya adalci wasu lokutan wlhy, figar motar yae ya soma gudun fanfalaqi akan titin na birnin Tarayya ranshi a b'ace. *********** Amma General kana ganin hakan ya dace kuwa, yaran nan dukan su sunada uzuri ni samma se nakeji ajikina tafiyar ba alkhairi bace ba sam" Harara ya wurga mata "Se uzurin su yafi aiken dana musu? Sesuke had'e kai sunawa mutane shashan ci da girmansu da komai shekarunsu nawa yanzu? Haba Haj Adama, mesa newai ke har yanzu kike biyewa shirmen yaran nan da yawo suke so suje inane bazasu jeba dan Allah? Wlhy bazan janye maganar tafiyar nan tasu ba jibi jibi, dole ne sukai mun uwata har garin su su kuma jirata tayi adadin kwanakin datakeso tayi sannan su dawo da ita, mutunci d'aya zan musu shine su koma cikin gari su kama hotel su kwana kafin ta kammala sesu koma k'auyen su d'akkota su dawo" Nisawa tae "Shikenan tunda haka kace, ina musu fatan Alheri Allah ya kaisu lapiya ya kuma dawo dasu lapia" "Ameen" itace kurun kalmar da general ya furta ya mik'e yabar d'akin, yana fitowa motoci suka jeru burjik da sojoji se sare masa akeyi shi kuwa dama fara'a bawai damun sa tae ba ya wani sha mur bako alamun rahama a fuskar sa. ************ "Dude kana ina?" Ya tambaya bayan tawayen nasa ya d'aga wayar sa "Ina Green tea" tsaki yae ya juya akalar motarsa zuwa cen batare dayace masa komai, cikin mintunan dabasu wuce sha biyar ba se gashi a wurin, k'arisawa yae ya baiwa Abu huraira hannu shida wani abokin shi suka gaisa yace "Kai Musty shine zaka gudo ka barni da Dad kaga wani had'a rai da yae yanata mun masifa sekace wani abu" Murmushi yae dayake shi dama be cika shariya irin na Abu Sufyan ba shi bama shida yawan surutu "Bansan mezan ce masa bane ba, kuma kaima nace karkace masa haka ka hak'ura da bikin kawai tunda ba dole, amma ka kafe aika jaraba, halin dad ka manta kaima kasani wlhy baze tab'a bari mu tsaya biki mubar aikensaba kona waye" Tsaki Abu sufyan yae "Amma bro aikasan ana iya d'age lokacin tafiyar nan, dama Allah ya taimakemu zamu samu wannan program na mata wanda za'ayi thursday night kaga Bashir bazeji zafinmu sosai ba" Kishin gid'a yae ajikin kujerar dayake kai cikin takaici "Allah ya mana jagora, ni gabaki d'aya tafiyar se idan na tunata k'irjina yake bugawa wlhy, Doguwar hanya ce zamu bi fa" murmushi yae "Nan zuwa garin aiba nisa karka wasu 'yan damu inshaa Allah zamuje lapia mu dawo lapia, kuma zamuji dad'in tafiyar nan" murmushi kurun yae yana tunanin tafiyar, dole yaje Shops nasu yaga tafiyar al'amuran yau tunda yake gobe thursday tafiya kuma friday ne, ranshi a jagule ya mik'e "Abu Huraira zanje Building materials shop, sekaje tile making company ka had'a abubuwan nan, sauran kuma Cyama taje, tunda yake tana gari" jinjina masa kai Abu huraira yae yayinda ya mik'e ya musu sallama shida Friend d'inshi Dawud ya wuce. *********** Hanifa kam tayi kici kicin da fuskarnan se rigima take masa akan tafiyar nan "Amma yaa abu huraira da gasken wai tafiya zakayi, tayaya kakeso naci bikin nan baka nan" murmushi ya sake mata "Hanny kiyi hak'uri banida wani zab'in daya wuce nabi umarnin dad,indai baso kike ya fasamun kai da gun ba toki dena wannan rigimar" Turo baki tae "To naji amma karku wuce 2days plss" murmushi ya sakar mata "Inshaa Allah my hanny karki damu kinji" Langwab'ar da kanta tae "Ban maka alqawarin cewan baran damu ba, amma zan kwatanta" Murmushin dake fuskarsa ya fad'ad'a "To my hanny barinzo in wuce yanxu dai, kinga gobe da sassafe zamu cira kuma ga gajiyan biki yau, Abu sufyan yanata kirana a waya ma" Fuskar ta sam ba dad'i tace "Ina maka fatan Alheri Yaa Huraira kace ina gayar da yaa sufyan, zan muku waya so 20 akowace rana amma zancen motar fa?" Murmushi yae "Tana waje ai, habu ya kawo tuni, yanzu zanje na daukeshi kese ki shigo da ita, and plss karki mun wasa da motana, kar kuma na dawo na tarar tayi datti ko wani scratch ajikinta" murmushi yanzu kam tae "Yaa Abu kacika rigima indai akan motane, inshaa Allah ma biki kurun zanje dashi sena dawo na ajiye" murmushi yae "Nizan wuce muje gate seki karb'a ko?" Haka ta tako shiyaja motarsa har xuwa gate suka rabu zuciyoyin su ba dad'i, itadai haka nan hankalinta be kwanta da tafiyar nan ba ajikinta setage ka tamkar akwai wani abu daze faru da yayyunta abinda bazata iya d'auka ba kenan har abada, jikinta amace ta k'arisa cikin gidan, kallonta Baba saude tae "Hanifer na yada fuska haka ne? Naga duk kinyi wata kalar tausayi" kwanciya tae ta kwantar da kanta asaman cinyar Baba "Baba hakanan hankalina ne kwanta da tafiyar su yaa Abu ba, ni tunda nake banji tafiyan dabe kwantamun ba kaman wannan" murmushi irin na manya Baba saude tae, dukkuwa da yake cewan itama tafiyan ba wani yi mata yae ba sam, jitakeyi tamkar tawa General magana akan a fasa tafiyar da yaran a bata kud'in mota aitasan hanya inyaso seta tafi abunta, batayi tsufan daza'ace bazata iya tafiya da kanta ba amma Tarasa meke damu General yacika kafiyan tsiya yanzu koda cewa tae zata mai magana ma baji zeyiba ranta ne kurun ze b'aci "Hanifer a sanya alkhairi acikin zuciya, a k'ullawa zuciya salama, adu'a itace abun buk'atar su yanzu, Allah ya kaisu lafiya ya dawo dasu lafiya kurun zakice kinji" murmushi tae "To Baba, ni ki sosamun kaina yana mun k'aik'ayi" sosa mata kan tahauyi batayi magana ba, tana tunanin yanda yafiyar nan ta yara zasu kasance, kosu sunce basason tafiyar, mahaifiyarsu ma haka mesa General ze kafe ne? Tana musu fatan alheri aduk inda suke" ********** Dukkaninsu suna durk'ushe agaban mahaifiyar su sunyi shiru suna sauraraenta amma shiru batace dasu komai ba, yanayin shigarsu ya karb'esu sosai shadda ce brown me duhu da hula brown amma light sunsha d'inkin zamani d'an cakwai yayi cas ajikinsu, komai nasu iri d'aya ne banda abu d'aya shine agogon hannunsu wannan nashi fatar kalar baqi ce wuluk yayin da d'ayan ke sanye da kalar fari k'al, wanda wannan shine kad'ai abinda zesanya ka banbanta su sabida tsananin kamanin dasukeyi, ko iyayensu idan ba ta wurin idanunsu ba basa banbance su se abu d'aya na halayya koda yake dukkaninsu basuda yawan magana bare kace ka gane su sedai kurun d'ayan yanada hak'uri sosai yayinda d'ayan sam bashida hak'uri komai k'ank'antar laifi abin masifa ne a gunshi, amma yafi wancen sauk'in kai sabida baya rik'ewa mintuna k'alilan sun wadace shi ya manta da abu komai b'acin ran daya sakashi "Kyautar Allah inaso aduk inda kuke kuji tsoron Allah, ku sani dukkkanin abinda kuke aikatawa Allah yana ji yana kuma ganinku, bakuda abinda shaku shamakance Lillahi daga ganin ku a komai dakukeyi, karkuga kaman kunyi nisa da gidan kuce zaku aikata abinda bashi bane halayyar ku ta asali, karkuyi abu koku bari danni kuyi dan Allah ku kuma bari dominshi, shikad'ai yasan ladan daze baku, kuna k'ok'ari sosai kuma ina matuk'ar jin dad'i ina kuma yabawa sosai akan hakan, sedai ku k'ara, kuma ku rik'e adu'a ku yawaita yin adu'a, musamman idan zaku fita da kuma duk wani abun k'i daya tinkaro ku kubishi da ambaton Lillahi inshaa Allahu zakuga haske komai yawan duhun daya taso muku, kuci gaba dason juna tafiya ce ta sati d'aya nake ga, dukda koni a raina banson tafiyar amma babu yanda zamuyi, awurin Allah sati ai kaman yau ne zakuga kun dawo, fatan kuje ku kuma dawo lafiya" A tare suka had'a bakinsu wurin cewa "Mungode sosai Mom, Allah ya saka da alkhairi, kuma inshaa Allahu zamu kiyaye" Dafa kan Abu hurairah tayi ta masa adu'a sannan ta sake ta dafa kan Abu sufyan ta masa sannan sukai mata sallama suka fita" A waje suka tadda general ya murtuke fuskar nan tamkar be tab'a dariya ba, k'arisawa Abu sufyan yae kusa dashi yace "Dad yanzu zamu tafi" kallonshi yae kanya kai kallonshi zuwaga zoben hannunshi sabida yanaso ya gano ko waye, shi kanshi idan bada zoben nan ba to baya tab'a banbantasu, shisa tun suna yara suna k'ara girma yana sanyawa ana musu zobuna masu sunayensu d'aya me d'igon bak'i d'aya kuma me d'igon fari, agogon hannunsu kuwa sune dan kansu suke sakawa sabida abokanan su da sauran mutane "Abu sufyan?, kun fito kenan ina Baba ladin?" Sadda kanshi yae a k'asa "Tanawa mom sallama ne, yanzunnan zata fito" Jinjina kanshi yae "Zaku d'auki *DOGUWAR HANYA* k'auyen kuma babu gari irin haka akusa dashi sam se jeji tako ina, shekarun bayan nida kaina na kaita amma ita da kanta ta dawo, nasan yanda hanyar take seku dinga adu'a akoda yaushe" godiya dukkansu sukayi sannan suka juya wa kotocin Abu Huraira shine ya zauna gefen direba se Abokinsa Dawud dayace seya bisu yawo, se Abu sufyan daya zauna abaya sekuma Baba ladi a gefenshi motace suka d'auka k'irar hilux fara qal sabida yanayin hanyar, da adu'a d'auke a bakunan su suka hau *Doguwar Hanyar* se d'aga musu hannu Cyama keyi yarinyar dake tsananin kamanni dasu, agidan nasu bazaka iya cewa game kama daban ba kowama kama yake da d'an uwansa Baran ma hasan da Usaini (Abu sufyan da Abu Huraira) suda bakama iya banbancesu aduk duniya mahaifiyarsu ce kurin kallo d'aya take gane waye wannan acikin su. ************* Yanayin shirun da motar ta d'auka kurun zaka kalla ka gano babu mejin dad'in tafiyar, jefi jefi Baba Ladi kan wurgo zance dayike ita macece me tsananin son raha kuma Abu sufyan shine yake yawan biye mata wannan dalilin ke sanya tana saurin ganesu itakam kota hanyar gaisuwar suma, ga mamakkinta yau koshi tsit yake sedai idan tayi maganar ze bata amsa cikin sakin Fuska, haka suka naushi hanyar har suka isa babban garin, Tsayawa Abu Huraira yae lokacin k'arfe sha biyu ta gota yaceda sauran "Abu Mage bana tunanin zamu iya nausar hanyar garin nan a wannan daren, so kawai inaga mu nemi k'aramin hotel mu kwana gobe muje mu kaita da asuba haka semu dawo kaga man motar ma yaje down baze mana kyau ba mu naushi jeji a haka gaskia" Murmushi yae jin sunan daya kirashi dashi yace "Abu takobi zancen ka dutse ne, hakan shine shawara me kyau, yanzu wane hotel zamu sauka?" Kallon agogon hannunsa ya qarayi kan ya yamutsa fuska "Bawani sanin garin mukayi ba, inaga mu tambaya semuje takusa sosai,inyaso ma mu ajiye kayanmu anan mu semu tafi muna dawowa munsan inda muka sauka" Da tambaya suka isa wani hotel me kyau da tsari, ya had'u ainun, d'aki me suit suka kama susu uku se Baba ladi da suka kamawa k'aramin d'aki ita kad'ai, sun siya kayan abinci suka k'araci sannan sukayi sallan isha suka hau hirar duniya sosai da sosai se dariyarsu kakeji a wannan daren kam sun rabashine suna hirarrakin duniya. *Washe gari* K'arfe bakwai na safe suka fito, inda suka tarar Baba azumi harta rigasu bakin motar, sunyi breakfast awurin inda suka biya wani wurin suka kwashi kayan snacks musamman cake dai suna sanshi sosai babba d'aya suka siya da qananu se donuts da sauransu, Baba Ladi kam har bread tasa aka siya mata kusan k'waya 4 da kayan shayi akan idan taje tariqa yin kalacin safe, komai sun tanadarwa kansu, daidai da ruwa sun nemi carton na faro me 24 aciki, drink ma haka, daga nan gidan mai suka nufa sukayi wa motarsu full tank, hadda siyan wani a jarka, dukda kuwa Abu sufyan yana ganin had'arin d'aukar fetur a hanyan dabasu san yama take ba, haka Abu huraira yace dashi basusan nisan wurin ba, ya tsani short na mai a mota, kuma sun samu anwa jarkar d'aurin kazar kuku an d'aure sosai, beside bama boot bane ba irin haka ai a bud'e bayan yake kayan Babane kurun da en tsarabe tsarabenta se suka rufe da k'yalle sabida k'ura....da adu'o'in tsari d'auke abakunansu suka d'auki hanyar k'auyen na b'ingirau dake cikin jeji me nisan gaske. ************ Sosai suka gajiya da nisan hanyar dasukebi, gashi dai garin maman ba cikin wannan nahiyar ba, ace tafiya tun bakwai na safe sukeyi har yanzu k'arfe biyu da rabi ta gota, sukam yaushe suka ajiyeta har suka juyo zuwa masauki, Tsaki kuwa Abu sufyan yayi yafi so hamsin, har ita Baba ladi da kanta ta kula da k'osawar da yae, ita da kanta taso General ya barta ta hau motan kasuwa amma ya kafe, sassanyan ajiyan zuciya ta sauke ganin sunzo hanyar dazasu yanki jejin daze sadasu da K'auyen na B'ingirau, da hannu ta nuna musu suka kuma karkata akalar motarsu zwaga wannan b'angaren Abu huraira ya juye baki da harshen turanci yace da Abu sufyan "Abu Takobi kaga wannan jejin kuwa, kasan wai jikina ya soma mutuwa, a gaskiya dazaran mun ajiyeta mu juyo sabida ina jiye mana yin dare a wannan muguwar hanyar" Kawar da kanshi yae gefe d'aya ya kaiwa agogon hannunshi kallo "Dama munsan hakane aida yaseen a motan haya zamu d'urota, yanzu fa uku saura mintuna biyar kacal, dama mun juyo ne mu soma timing amma wannan masifar har ina?" Dawud ne ya karb'e zancen da cewa "Ba masifa bane ba kadena kira mana ita, idn dai kan wannan hanyar ne ai inaga zamu juyo dare be mana ba" shiru dukkansu sukai, zuwa hud'u saura kwata sun k'arisa garin, mafiya yawancin mazauna garin fulani ne kamar Baba ladi, harkokin su suke gudanarwa cikeda aminci, sun gaggaisa da mutane kansu tsaye suka nemi yin salla azahar da la'asar kansu ce zasu koma, duk yanda akaso suci abinci sun gagara tsayawa se wuraren biyar da rabi ma sukai shirun tahowa duk saurin dasukayi...wani mutum ne me tsananin kamanni da Baba ladi yazo ya kalli Abu sufyan daya karb'i tuk'in motar ganin kamar Abu mage ya gaji yace dashi "Yaro dazaku bi shawarata dakun hak'ura da tafiyar nan zuwa asubahi, komu damuke da garin nan bama yi masa fitar yamma, koba komai kuna baqi seku saki hanya ai" kallon Abu Sufyan yae cikeda takaici yace "Kamana adu'a lafiya lau zamu fita mun gama haddace hanyar inshaa Allah" jinjina kanshi yae alamun gamsuwa yace "Idan kuka miqi hanya zuwa gabashin nan, karku neki ko washe hanya sheta kudu, kunayin kudu kuka raba jejin masarau biyu seku yamma kuyi arewa se titi kuma, kushkure d'aya jal je sanya ku shaki hanya, kuma shakin hanya a wannan daren baze muku da kyau ba, ina muku fatan alheri kaji ko" jinjina kanshi yae yana sakaya murmushin yak'e kansu d'aga musu hannu subi hanyar daya dace... ************** Shiru dukkansu sukayi kowa da abinda yake sak'awa aranshi, jin kafewar tayar motarsu ne ya sanya suka kalli juna shida Dawud dake gaba yayinda Abu Huraira ke kwance abaya yayi matashin kai da wani trow pillow daya zame masa abun yawo duk inda zashi, shi d'inma d'gowabyae yace yadai?" Cikin sanyin jiki yace "Ga duhu ya soma sauka, ji nake fa kaman laka ne muka mak'ale aciki, amma ai d'axu bamu bi wata hanya me laka haka ba ko?" Wasu yawu Masu d'acin gaske ya had'iya kanyace "Ko kusa bamu wani shiga laka ba gaskia, amma kaja da kyau mana" Iyakar dagewar shi yaja ya taka totor amma sam motar taqi ta motsa, kashewa yae suka fito dukkansu, babu wanda jikinshi be b'aci ba, lakar ce kuwa tsaki Abu Sufyan yaja ya koma cikin mota sukuwa suka ja baya suna me karkad'e k'afansu daya lalace da tab'o, giya ya sauya zuwa me iya fitar da motar daga wurin, dama Allah ya imakesu Hilux ce seta fito daga cikin Lakar lafiya, duhu ya soma sauka wannan ya sanya dawud ya ciro wata k'atuwar waya a aljihunsa ya kunna torchlight dake jikinta me hasken gaske, kai tsaye ta mamaye lakar da haske arziqi ma sukayi irin me zurfin gasken nan ce, cikin damuwa Abu Sufyan yace "Dawud anya bamu sake hanya ba kuwa? Nifa sam babu wannan lakar a inda muka biyo ni gaskia na tsorata" Dafe kai sukayi dukkansu kansu d'akko ruwan faro dasukai guzurinshi su wanka k'afansu dashi sannan su koma kotar, sunyi adu'a kafin su d'auki hanyar dasuke tsammanin ita zata fitar dasu kan titin dabeda maraba da babu.... K'arfe takwas ta gota sanda Dawud cikin damuwa yace "Abu sufyan ka kwatanta ka gani, uku saura mintuna biyar muka yanki jejin nan d'azu, kuma koda hud'u saura kwata tayi fa mun isa qauyen kaga tafiyar 45 mns ta kaimu, yanzu kuwa tun biyar da rabi muke zagayar jejin nan, ko shakka banayi wlhy b'atan hanya mukayi" wani dogon burki yaja ganin k'aton maciji agabansa gudun karya taka shi, bakinsa har rawa yake ganin macijin ma yaja burki ya d'ago kai yana kallon haske fitilar motar sekace yana ganinsu "Abu Huraira maciji" Lek'owa shima yae shida Dawud, lokaci d'aya suka shiga ambaton mahalicci, basuko matsaba kuwa kaman yanda basu d'aga da motar ba konan dacen ganin yanda macijin kr kallon su kaman wani mutum. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: 🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na kud'ine dan Allah idan baki biyaba karki karanta, idan kinaso ki biya kudi ki riqa samu a kud'inki* 02 Adu'ar tsari dukkansu ke karantawa har suka ga macijin ya wuce abunshi batare dayayi ta kansu ba, dukda Ac dake kunne a motan hakan be hanawa dukkansu tsiyayar da zufaba "Abu sufyan ina wannan kalan macijinne ke had'iye mutum?" Wasu yawun wahala ya had'iya kafin yace "Ni gaba d'aya na rikice ma, jikina yae sanyi sosai da tafiyar nan, ina roqon Allah ya mana shamaki daduk wani abun k'i" cikin damuwa Abu huraira yace "Yanada girma amma da wannan macijinne aida motar gaba d'aya xe had'iya sedai fa aganina mu juya gwara mana kwana a k'auyen nan da mu lula acikin wannan jejin, ko shakka banayi mun sake hanya sosai" Nisawa Abu sufyan yae "Bazan iya tuk'in nan ba, mu juya kawai kaikaja" cikin damuwa Dawud yace "Kai yanzu seka sauka ku juya, kana ganin wannan mucijin, idan kuma be tafi bafa, kaidai ka juya kurun" haka ya juya akalar motar sa sukaci gaba da tafiya........ ********** "Bana samun number yaran nan koyaya na gwada, rabon danayi wayama dasu tun da rana dasukaje ajiye Baba ladi, ga garinsu babarma ba Ntwrk inaga dan wayanta itama a rufe" Kallonta General yae cikin takaici "Ko? Toki musu adu'a inshaa Allah suna nan lafiya lau, maybe basu juya da wuri bayan sun ajiyeta inaga basuda caji, kuma k'aninta ya sanarmun sun ajiyeta harsun juya tun yamma, Glo kurun ke aiki a k'auyen, kinga mtn take using soba lallai ki samu ba" Ajiyan zuciya ta sauke hankalinta sam baya jikinta amma batace dashi komai ba se kwantawan datayi jiki a mace. ********* Duk yanda taso tayi bacci abun ya gagareta, bazata iya hak'ura da rashin jin yayyun nataba, shak'uwace me tsanani a tsakaninsu, Fuskar wayarta ta kalla da sunayen su a k'alla ko wanne ta kira wayanshi yafi so hamsin amma baya tafiya, duk iyakan k'ok'arinta not reachable ake cewa da ita to ina suka shiga? Wannan itace tambayar da takewa kanta amma bata samu amsaba har wannan lokacin. *********** Wayanshi ya danna gefen key haske ya bayyana, agogon wayan ya nuna k'arfe goma da rabi hadda mintuna uku na dare gumi ya sharce dan a zahirin gaskia a tsorace sosai yake, yawun bakinsa ma ya k'afe sam bayada wani abu dayae saura daze had'iya a bakin "Abu Sufyan nashiga dana sani fa, dana sanin hanyar nan damuka d'akko cikin wannan daren damun sani damun kwana a k'auyen, gwara zazzab'in cizon sauro da wannan tashi hankalin damuke ciki, idan dai har daidai muka biyo hanyarnan tokuwa da tuni munzo wurin lakar damuka fad'a ciki d'azu, amma gashi yanzu shiru kusan sa'o'i biyu da matasan mintuna sun shud'e amma shiru kakeji, ina fatan ba wata hanyar muka k'ara cafka ba mara b'ullewa" Cikin damuwa Dawud yace "Wannan kam tabbas wata *Doguwar hanya* ce muka d'akko me matuk'ar wahalar b'ullewa" "Tuk'in nan danake tafiya ne kurun nakeyi amma wlhy bana gane kan hanyoyin nan, ban magana bane dankar na tsoratar daku amma hanyar seta rik'amun iri d'aya duk inda zanbi, ya dace musan abinyi gaskia" Yawun wahala Dawud ya had'iya ya tuna maganar mahaifuyarshi sanda ze fito gida "Yanzu kai me zaka cewa kabeer? Kaine babban abokinsa amma akan ka tsaya hidimarsa kafiso kaje gantale, su sunada hujja dan ubansu ne ya aikesu kai kuma kanada wata hujjar ne, haba Dawud? Ya dace kawa kanka fad'a gaskia" Nisawa yae tunawa da ansan daya bata "Umma ki gane tafiyan nan tunda Twins zasuyita nima dolene inje, bazan ganewa komai ba idan basa nan bikin ba wani dad'i zemu mn ba, nidai kimun kurun ita nake buk'ata" Adu'ar tamasa ya juya abunsa kuwa yabar gidan. "Afu sufyan kasan me, Nemi wuri med'an fili kayi parkin motar nan kurun, mu kasheta mu sauke glass ko yayane, ka kunna mana karatun alqurani me girma, idan gari ya soma wayewa semu kama hanya, dan kar mui nisa inda bazamu ganeba koda akwai yalwar haske" Kallon juna sukai shida twin d'inshi ya kad'a masa kanshi akan hakan shawarace me kyau, cikin sanyin jiki yaja gefe yae parking adaidai wata bishiyar tare da janyo wayarshi ya kunna karatun alk'urani me girma a hankaki ya zuge glass na gaba duka biyu na baya d'aya kawai kwanciya yae jikin sit na kujerar ya lumshe idanshi tare da soma rero duk wata adu'ar datazo bakin sa ta tsari, haka suma sukeyi a hankali.... *********** Hasken Rana shine abinda ya farkar da Abu Sufyan dayan daga nannauyan baccin daya d'auke dukansu batare dasun shirya zuwan saba, wayarsa kuwa har cahrge ya d'auke sabida ya da take kunne, karon sa na farko kenan tun bayan daya girma da wani abu me kamada yin salla asuba ba'a cikin lokaci ba ya same shi, kallon Dawud yae dake gefenshi,baccin sa shima yake cikin nutsuwa sedai badan dad'i ba kod'an da yake a zaune yakene oho, ko shakka ba yayi sun kai nisa 5 kafin baccin ya sacesu dabadan hakan ba ba abinda ze hanawa d'ayansu farkawa adaidai lokacin daya saba tashi sallan asuba, hannu yakai yad'an bubbugi kafad'ar Dawud inda a hankali ya bud'e idanshi d'auke da salatin annabi a bakin sa, Abu Huraira ma farkawa yae suka kalli juna cikin mamakin baccin dasukayi, kan su sakko daga motar dukkansu su soma shirin d'aura alwala da d'an ruwan dasuka zo dashi na Faro.... Se bayan da suka sallaci sallolin dabasu samu sunyiba data asuba sannan suka yi addu'ar neman yafiya kan daga bisani su mik'e suna ninke carpet dake hannun su wanda dama anxo dashi, Abu Huraira ne yawa wurin kallon tsafta sosai kan daga bisani ya nisa yace "Ko kunsan cewan kwata kwata ba alamun sawun mutane nabi nan hanyar ko zancen wata mota kaiko babur da keke banaji suna bi" Jikin motar Abu Sufyan ya jingine cikeda damuwa yace "Abinda ya kamacemu shine mu qarawa motar nan mai mu kama gabanmu yanzu Alhamdulillah safiyane inshaa Allah zamu gano hanyar" kallon tausayin kansu Abu huraira ya mai kanyace "Abu Sufyan kasan Allah, wlhy a madifar tsorace nake, dabadan da Hilux mukazo ba da ba abinda ze hanamu shan bak'ar wahala tun daren jiya, yanzu kuma tsorona Allah banga inda zamu biba, ko ina yakoma mun iri d'aya" Mamaki ne sosainya bayyana a idon Dawud "Kaima ka kula kenan? Na zata d'emuwane ya kamani ai" Hannunsa ya zura a lajihunsa d'aya jal "Nikaina ban fahimci komai ba, kasan me dana farka senaga kaman jiya banan na ajiye kan motar ba" shiru ne ya ratsa wurin na wuccin gadi kafin daga bisani Abu sufyan yace "Allah ya gani iyayen mu mukewa biyayya mukazo wanan jejin, da yardar Allah da qarfin adu'ar su bazamu tab'e ba, kuzo mui lalube inshaa Allah zamu b'ulle" cikin damuwa suka d'akko man fetur suka zube ajikin motar sannan suka koma ciki suna tashe tax wannan karon Dawud ne ya karb'i Tuk'in, Abu sufyan yana baya ya kwanta yana me lumshe idansa, yunwa yakeji ma sosai dan haka ya janyo musu cake da drinks ya baiwa kowa yanka suna tafi sunaci badan dad'i ba, gabaki d'ayansu hankulansu a tashe suke kasancewar basu tab'a tsintar kansu a jeji ba se wannan karon........ ******** Yajima tsaye a kanta yana nazarin yanayinta, samsamsam ya kasa gane kan Haj Adama,tunda aka gagara samun lambobin wayoyin yaran nan jiya ko abinci tak'i taci, zama yae kusa da ita ya rik'o hannun ta "Haba hajiyar general mesa kike hakane? Ai duk yayinda kikaji shiru tokuwa da yardar lillahi lafiya ce take kawo hakan, nifa inaga yarannan dan kurin sunyi tafiyar nan ne basaso suka kama suka rufe wayoyinsu, suna kan fushi har yanzu, amma zasu bud'e ne" d'ago idanta tae dasu kae ja ta kalleshi, cikin takaici tace "Bana tunanin na d'aura kyautar Allah akan wata turba masiffanciyar wannan, da kansu bazasuyi fushi da iyayen suba akan abinda yafi wanan ma bare wannan abin dabe taka kara ya karya ba, girman nak'uda yawane dashi koda bazaka yarda dani ba kasani koyaya matsala take kad'an tokuwa tabbas itace ta hanasu bud'e wayoyinsu kokuma a samesu" Sauke nannauyar ajiyan zuciya yae "Bamuda wani zab'i daya wuce mu musu adu'a arayuwa, da damuwar nan tana maganin wani abu data miki Haj, ina baki shawara kurun ki musu adu'a zatafi saurin isa garesu akan wannan damuwar dakika sanyawa kanki, kici abinci ki miqawa Allah lamuranki inshaa Allah zakiga haske" Batace masa komai ba harya mik'e yabar mata d'akin. ********* Duk yanda sukaso su gano kan hanyar abun yaci tura, sunyi zagaye sunyi kwana har sun gaji amma sam basu gano komai ba, zuwa yanzu man motar tasuma yayi qasa sosai ga yamma tayi cake kurin sukeci se sallah dasuke idan time yayi, alwala ma se sun riqe sabida ruwan su saura roba bakwai kurin, kansu ya kunce ainun. Tunda magrib tae musu a wannan jejin suka sare da fita aciki a wannan ranar, to save there remaining fuel kurin sukae parking sukai sallah skaci cake se dabino suka sha lemo sa ruwa suka hau karatun alqur'ani me girma, sun jima sunayi har suka kintaci lokacin sallan isha suka tashi sukayi sannan suka shinfid'a qatuwar dadduma ajikin bayan motar su, suka koma suka kwanta acen cikin budadd'en booth d'in dasuka shinfid'a dandumar, sama dukkansu ke kallo bayan sunyi pillow da trow pillows dake cikin motar farin wata ya haske sararin samaniya bakajin sautin komai se bugawar zuciyoyin su dakuma sautin kukan tsuntsayen dake tashi lokaci zuwa lokaci, Abu sufyan ne ya kai hannunshi ya rik'o hannun Abu Huraira cikin muryan damuwa ya furta "Brother am really scared please pray for us" Matse hannun nashi danashi cikin tausayi yace "Keep reciting Ayatul kursiy brother, everything will be alright ok?" Yafad'a yana me duban face d'inshi acikin d'an hasken na farin wata, dawud ma a hankali ya soma adu'a ba k'akk'autawa........ Kuka suka soma jiyo tamkar na zaki, a tare suka miqe a zaune dukansu, se zare ido sukeyi yayinda kukan ke qara kusan tar inda suke, da gudu suka sakko suka bud'e motar, amma ina kafin sukai ga shigewa har abun ya qarado inda suke..... Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* 04 Sojojin basu isa garin nasu Baba ladi ba se bayan 2 days,haka suka wuni a garin bayan an tabbatar musu sun juya, amma wannan karon tare da Baba ladi suka juyo, sabida ta kaisu wannan Hotel dasuka sauka aji kosun koma, ga mamakin su basu koma ba tun ranar, ga kayansu ma dasuka bari anan kuma kud'in sati suka biya gashi yanzu kusan 6days babusu babu labarin su sam, sojojin hankalinsu ya tashi, anan sukawa kansu masauki washe gari suka juya k'auyen nasu Baba ladi da guzurin man fetur me yawa kaman yanda sukeyi idan zasuje jeji aiki. K'anin Baba Ladi yae gyaran murya yace da Oga Shamsu "Ranka ya dad'e kamar dai yanda ka sani wannan yankin namu muna boader da k'ashashe kusan uku, kuma idan ka lura da kyau zakaga cewar bama kusa da mutane sam, mun yanko jeji sosai munbar gari da nisa, itama sanadi ne ya fitar da ita daga garin nan dabadan haka ba bana tunanin akwai wamda ya taso ba'a nan ba, Hanyoyine muke dasu masu rikitarwa sosai anan jejin, dagazaran ka saki hanya da kuskure d'aya tokuwa tabbas zaka yanki wata uwar *Doguwar Hanya* ne dabakasan sanda zaku rabu da itaba, acewar kakan ninmu, hanyoyin kana isa zasu koma maka iri d'aya kuma da gabas da yamma da kudu da arewa duk zasu zame maka alqibla d'aya ne, sa'n nan kuma bazaka gane inda ka dosa ba, duk inda ka duba zaka ga kamar nan kafito, seka bi seta dulmiyar dakai, acewar su ko namun jeji basa zama a jejin duk wani naman daji daka gani agun tokuwa tabbas aljanine dansu kad'aine ke iyawa da gun" Wani tashin hankaline ya ziyarci Oga shamsu ya kalleshi cikin takaici yace "Yanzu kenan bamuda ikon shiga jejin neman su?" "To nidai bazance bakuda ikon shiga ba, ikon shiga kam aikowabyanada shi, ikon fitowa ne babu kaga anan zab'i nakune,tunda mutane suke shiga jejin ana zuwa nemansu, Barde ne ke zuwa kafin a haifeshi kakanshi keyi, yazo Baban shi nayi yanzu shiya gada jikan sarkin malamai ne anan garin, babu wanda aka tab'a samu da ranshi ajejin, kowanne zaka tarar gawa aka tsinta kokuma alamun yaje jejin, baka tab'a samun tarihin wanda yaje ya fito, idan ma ansamo mutum tokuwa zakaga dawani ciwon ze dawo, to idan ma mutum yakai gab'ar kogin ko Barde baya shiga wannan ruwan zaka hau su bakada tabbacin sauka kuma idanma ka saukan baza'a k'ara samun labarin kaba, mahaifin Barde ma daya tsallaka haryau shiru kaga akwai matsala kenan?" Hular kansa ya zare cikin mutuwar jiki yace "Lallai wannan doguwar hanya ce, to amma shi barden baya zuwa tare da wasu ne? Kaman yanzu yajagoran cemu?" Murmushi yae "Yakanje tare da mutane matsalan shine ko kabishi ba amfanin ka bishi dan ba'a kagana a jejin, kana yi kana dulmiyewa, bafa k'aramin mugun abu bane a wannan wurin, koda kuna tare kanshi kurun yake iya baiwa kariya sabida haka gwara karkuje, ku koma ku bashi aiki ya muku acikin kwana uku yake dawowa da bayanin wanda yaje nema, ko rai ko babu idan ma mutum beje ba ze gane, idan yaje kuma ze gane meya sameshi koda ya tsallaka kogi ne kuwa, matsalan d'aya ne baya wa kowa aiki seya bashi damin hatsi 20, na dawa 20 na masara ma haka, sannan ga tsaban kud'i jaka talatin" Kallon shi oga yae "Nawane jaka talatin?" "Dubu shida fa, shiyasa wasu idan d'an uwansu sun tafi basa iya biyan barde wlhy" murmushi yae "Ba kud'in bane abinji mu zamu ma qara masa ninkin ba ninkin, mu cetosu mukeso yayi, gashi kuma kace baya iya baiwa wani kariya, yazeyi to idan ya gansu?" Murmushi yae "Yasan yanda zeyi ai, masu rabon fitowar sukan fito tare dashi, wannan aikin sane, ku bari muje gunsa inyaso kunga semui magana dashi idan ze iya jagoran tarku ko?" Hakan kuwa akayi sedai ya sanar dasu shi sam se laraba yake zuwa jejin dan haka tunda yake yau alhamis sedai su jira nanda kwanaki shida, yakuma musu alqawarin inshaa Allah zeje tare dasu indai zasu biyashi kud'in aikin nasu... Ba b'ata lokaci sukai na'am da wannan sabida basuda yanda suka iya haka dole suka juya zuwa gida domin sanarwa da mahaifiyar yaron bisa jagorancin wani d'an k'auyen gudun kar hanya ta k'ara saka subi doguwar hanya mara b'ullewa. *********** Ruwan yanda ya taso da k'arfi sekace had'iyesu zeyi, idan ana zancen tsorata sam baza'a kawota anan dan abinda sukeji azukatansu a wannan lokacin yafi k'arfin tsoro, dukkaninsu sun sare da rayuwa se Abu sufyan ne kurun ya soma adu'a cikin muryar sa me dad'i, ilahirinsu d'auka sukayi babu wanda abakinshi ba adu'a yake ba, jirgin se tangal tangal yakeyi dasu kaman ze kife, suda sukeda niyyan tsallakawa seya juyar da akalan jirgin zuwa mik'ewa ata tsakiyan ruwan tsaye, duk yanda sukaso su juyo abin ya faskara, da k'arfin adu'a cikin iyawar Allah suka samu suka daidaita kan jirgin zuwa tsallakawa, hakan ce ta basu damar samun yar nutsuwa a hankali suka ci gaba da tuk'a jirgin har zuwa sanda sukazo gab'ar Tekun suka gangara suka ajiye shi suka sakko daga kai suna me zaunawa, ilahirin jikinsu ruwa ta gama jiqashi gashi kala d'aid'aya dama suka zaro daga kayansu gudun kota kwana, wannan najikinsun tun ranar dasuka zo yake, gyara jikinsu sukayi suka shirya dukkansu cikin qananun kayan sannan suka ninke wancen suka mayar a qatuwar jakar bayan dasuke juyawa daga wannan zuwa wancen. Tafiya suka somayi suna mamakin ikon Allah azukatansu, wannan shine Allah d'aya amma gari banban, ka kalli nisan dabe wuce sa'o'i uku ba daga shigarsu jirgin su tsallako wannan wurin har sunga sauyin yanayi, babu wani gari dasuka hanga amma tabbas wurin ya k'ayatar, sabida ga 'ya'yan itatuwa nan burjik se kalan wanda bakaso dogayen itatuwa sunwa wurin k'awanya wurin ya burgesu sosai dukda zukatansu ba dad'i hakan be hanasu yada zango anwurin ba suyi sallah azahar harma da la'asar kasancewar su matafiya an halatta musu aikata hakan, bayan sun idar sukaci dabino da lemo harma da korawa da ruwan robar dabe wuce musu saura roba uku ba yanzu suka kama hanya bayan sunji cikinsu ya musu nauyi suka naushi hanyar suna tafe suna bin karatun alqur'ani me girma dake tashi daga k'aramar wayar Abu Huraira, yayinda suke tsintar lemon zak'i dakuma Tufa da suka taradda itaciyar kowannen burjin agun suna wurgawa a jakarsu wasu kuma a hannayensu..... Ganin su da yarinyar tae ne yabata damar k'ara fitowa daga jikin itacen data bu'ya ta k'ura musu ido, shigar jikinsu kurun take kallo tana mamakin wad'an nan wane irin muta nene haka? Tun tashinta tana k'arama duk shekara se k'addara ta kad'o wani garin nasu amma wannan ne karanta na farko dataga masu irin wannan shigar kuma ga alama mazane ma, Dawud ne ya fara ganinta seda yaja baya ya rik'o hannun Abu Huraira " Abu Huraira kalli wata aba!" Ya furta cikeda tsoro dan harga Allah shi kallon aljana yake mata, Atare suka d'aga suka kalleta kowa yae turus yana kallon ta ita d'inma su take kallo bata ko k'iftawa amma tafi nacewa kallon Abu Huraira da tawayensa kasancewar tana musu kallon aljanai gasu iri d'aya komai nasu iri d'aya tosu waye? Ta tambayi kanta "Dawud mugodewa Allah mun had'u da mutum, wannan mutanene masu rayuwa jeji bakaga yanayin shigartaba?" Sauke ajiyar zuciya yae "Toni naganta kaman daga sama kuma ta wani tsaya ta kafemu da ido ko k'iftawa batayi" Murmushi Abu sufyan yae yace "Muda muke tare da tsarewar Allah, kai banda ikon Allah ka isa kazo nan wurin da ranka, koma aljanar ce magana zam mata niba ruwa na" takawa yae har zuwa inda take seda ya k'are mata kallo sannan yace "Baiwar Allah dan Allah nand'in inane? B'ata mukayi wlhy muba en nan nahiyar bane" kallon sheqeqe ta masa sarautar da mulkin suka motsa dan dama ita ba'a kallonta a garin kwata kwata, baka isa ka kalli 'yar sarki ba, k'wak'ulemaka ido d'aya akeyi musamman mazan garin, cikin yaransu dabayaji ta sanya hannu ta tankad'a shi yae baya yaje taga taga ze fad'i seda Abu Huraira ya rik'eshi sannan tace "Kai waye dazaka kalleni ido cikin ido? Zan saka a kashe ka fa" kallon juna sukai da tawayen nashi, shi Abu huraira ya fahimci sam batajin yaransu suma kuma bawai gane komai sukayi dangane da yaran nasu ba, hard'e hannaye Dawud yae ya langwab'ar da kanshi gefe d'aya ba tsinta dukaba, amma tabbas magana takeyi akan kisa dakuma fad'an yana kallonta, ko shakka bayayi yarbanci takeyi sedai banbancin kalamai da wurin furtasu daya kula akwai da yaren shida yakeyi, matsawa yae kusa da ita ya juye yaran bakinsa, cikin harshen na yarbanci ya soma bata amsa "Kiyi Hakuri baze k'araba kinji" kallonsa su Twins suka tsaya yi sun gano yarbanci tae sedai suma natan ya musu wani iri, dukda yake sunsan abokin nasu Mahaifanshi duka yarbawa ne zama acikin hausawa yasa suka riqa, gasu musulmai ne kuma sosai tun kakaninsu shisa har komai nasu ya juye zuwa al'adun hausawa sedai kam sukanyi yarbanci sosai agidan nasu. Kallanshi tae ya sauke k'wayar idanshi k'asa da sauri yanaso ya gane idan ya fahimceta sosai kallon natane ba'ayi, murmushi tae "Wane magana yake haka? Bana ganewa?" Ta tambayi Dawud kanshi a k'asa yace "Yaren sa kenan" Murmushi ta k'arayi "Bayan yamura yarenmu sekuwa yamura kawal susu kad'aine yaruka biyu aduniya kuma duk na iya, ya akayi nashi bako d'aya aciki" D'an kallonta kad'an yae ya fahimci sosai bata san annabi ya faku ba, ko yanayin shigar tama ya nuna rayuwar dabbobi suke a jeji "Akwai yaru kan dabaki saniba ne ai, duniyan yanada fad'i sosai yaruka sunfi a irga" Wata dariya ta kwashe dashi, sannan tace "Ni babu inda ban saniba aduk fad'in duniyar nan, ko ina nasani kuma ina zuwa ko ina ma, Sarki k'uru shine mahaifina tare muke zaga duniya dashi" JINJINA kanshi yae bece qalaba, kafin wani yae magana acikinsu har wasu qartin mazaje sun zagaye su sun shiga d'aurinsu da igiyoyi, mamakine ya hanasu magana haka aka jasu tabi bayansu tana murmushi, dukda saurayinta ya b'ata mata rai, amma hakan be hanata murmushi ba, idan sukabar garin sama ina zasuje? Yanzu kam an samu na sadaukar wa ta huta.... Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwane idan kinason ki karanta kibiya kud'i, ida kika karanta baki biyaba kuma toh...idan kinaso ki siya ki nemi wannan number 07084161619. 05 Acikin sojojin nan Barde da mutane bakwai ya tafi jejin nan, a mota suka tafi dukda yake yace shi baya shiga jejin a mota, amma suka lallab'ashi ya amince musu. *********** Hankalin su Dawud a tashe yake musamman shi Dawud dayakan tsinci abinda suke fad'a acikin wak'ar dasuke rerawa da harshen su me kamada yarbanci, dukda yake ya kula akwai banbanci sosai acikin yaren nasu, ko shakka baya yi wannan wani ikone na Allah amma yarbancinne dai, tunda har ya iya yin magana da ita,gashi kuma yakan gane abinda suke nufi, se turasu sukeyi sekace sun kamo bayi "Abu sufyan wlhy zancen Sacrifice sukeyi fa, kanajin abinda suke cewa a wannan wak'ar dasuke inajin wani abun kaman yarbanci suke, mun shiga uku munzo garin matsafa" cikin tashin hankali Abu Huraira yace "Dena gayamun mun shiga Uku Dawud, inshaa Allah bamu shiga komai ba se Alheri, sunada k'arfin tsafi munada k'arfin ikon Allah, kaci gaba da addu'a da karatun alqur'ani inshaa Allah zamu kub'uta" shikamma Abu sufyan ya dena gane komai, gaba ki d'aya ya gagara furta wata kalma banda gumi babu abinda yake had'awa haka aka tankad'a k'eyar su har zuwa wani babban fili me zubin yashi kawai ba itatuwa, a tsakiyar yashin aka ajiyesu aka d'auresu kowa baya fuskantar d'anuwansa dan a had'e aka d'auresu sedai bayansu dake gugar juna,a nan aka barsu har rana ta fito ta fad'i bako ruwa gashi an k'wace musu jankunkuna an ajiye angefensu har wannan lokacin kuwa wayar Dawud tana rero karatun alk'urani seda k'yar ya janyota a aljihunsa ya kashe sabida gudun k'arewar caji. ********* Yamma lik'is mutanen garin suka firfito aka zo aka ajiye kujera koda a k'auyen dake dokar jeji ne kana gani zaka hango cewan harkan saraki ne, haka aka jere kujeru sassak'ar katako sunkai k'waya bakwai mutanen gari suka zo sukazo suka jeru bame wata sutura se kayan fata da kuma wasu ganye sun rufe iya farjinsu maza da mata, matayen kuwa zuwa k'irjinsu ma arufe yake da kayan fata, zuwa akayi aka zagayesu da wani abu kaman cage amma na kara, kaman k'ananun ramukan dake gun dama jira suke dankuwa acikinsu kurun ake kafe abun ana zagayewa har aka kammala Wani wanda ko ba'a gaya musu ba sunsan sarkine da ahalainsa suka iso gun an d'akkosu acikin wani cage na itace shima k'arti sun d'akko ko wanne susu hud'u d'auke dashi Kowa sujuda yae harseda sarkin da ahalinsa suka zauna sannan suka mik'e tsaye dukansu, gasunan da tsofaffi da kowa, wani ne yafito da jawabinsa na cewan Er sarki Lawuri itace ta kamo mutanen da zasu ceci babanta da danginta batare data tsallaka ruwan ba anan aka d'auki tafi da sowa saurayinta sr murmushi yake yayinda ko kallonsa batayi ba sabida taji haushin yanda bezo ba, Cikin takunta na k'asaita ta k'arasa cikon hilin tare da rakiyar muqarabanta mata masu kula kula da ita. Kunce mata su akai duk aka mik'ar dasu tsaye, lokaci d'aya Abu Sufyan ya nemi zubewa k'asa sabida azabar kishirwa da kuma wuni a dunk'ule gu d'aya, da sauri Abu huraira ya rik'oshi "Sannu Sufyan, menene?" Ya furta cikeda tashin hakali "Ruwa nakeso Huraira, kuma k'afana baya iya d'aukana" jakarsu ya janyo da sauri ya zaro roban ruwa, wurin kowa yayi tsit ana kallon su har Lawuri ma, bud'ewa yae ya jonama mai robar a abaki, sosai yakeshan ruwan jiyake kaman ze iya had'iye kogi ma akan tsabar kishin dayakeji, hannu Lawuri ta saka ta karb'e roban ruwa ta tuttular da sauran a k'asa sannan ta wankawa Abu Huraira mari ta turw sufyan a k'asa " kai waye dazaka mana k'aud'i, ka isa kaciyar dashine?" Dafe kuncin sa yae cikin mamaki ya bita da ido beyi aune ba yaji dirar k'asa a idan sa "Ni wannan abun ze kalla ido cikin ido? Kai d'an iskan inane dazaka kalleni ido cikin ido? Tabbas inaga kaine zamu yankawa Raminus a wannan shekarar" murza idanshi ya hauyi ga k'asar ya shiga masa sosai haka ya dinga murzawa ya rasa inama ze sanya rayuwar sa, Abu sufyan ne ya rik'oshi ya soma hure masa idan sa, haka yae ta masa kowa yae tsit daga k'arshe ya janyo roba daga jakars ya bashi ya wanke masa fuakarsa da idansa seda yaga ya samu nutsuwa sannan ya rik'e hannunshi yaja yayan shi bayan shi ya had'e hannayensa gu d'aya alamar rok'o kan cewar suyi hak'uri, wata mahaukaciyar dariya ta kwashe da ita sannan ta sanya hannu ta d'auki robar ruwan daya ajiye takai bakinta ta k'wankwada, wani iri taji daban kaman an sanyawa ruwan rake lumshe idanta tae ta shanye duka sannan ta kalli Dawud, tace dashi cikin yaren data fahimci yana ganewa "Ruwan meye wannan?" D'agowa yae ya kalleta amma be bari sun had'a idoba yace "Ruwan shane" atak'aice. Murmushi tae masa "Amma ba irin namu bane, ina ku kuka samo?" shid'inma kafirar k'ishi yakeji seda ya hadi'yi bushashen yawunsa sannan yace "Dashi mukazo daga garinmu, ku taimaka kubarmu mu koma gida, badasan ranmu mukazo nan ba, hanya ce ta b'ace mana" Hannun ta takai taja gashin gemunsa seda yae k'ara sannan tace "Wannan zan saka a soma askewa, kaf garin nan babu wanda yakeda daman ajiye wannan se Sarki k'uru naka yayi yawa" Bece komai ba se jakar shima daya janyo ya zari robar rowan da itace ta k'arshe ya kwankwad'a sosai yakusa shanyewa ma kanya ajiye, warcewa tae ta k'ara shanyewa kamar wata mahaukaciyar zakanya. Matsawa tae kusada Abu Huraira ya k'ura mata ido, Dawud dayaga kowa baya iya kallonta sosai ya fahimci ba'a kallonta seya sanya hannu ya rufe masa ido, hannun nasa Abu Huraira ya bige ya sake sanya idanshi a nata, matsawa sosai tae kusa dashi tace da macen dake gefenta "Wannan nakeso abayar wannan shekarar, banason yanda yake kallona, na tsaneshi sosai, da inada hali bazasu sako musu zakiba, shi zan tura" murmushi tae mata "Lawuri aike ta dabance, koma wani zakin ya zab'a semu mayar wannan" Murmushi tae daya mugun k'arawa fuskar ta kyau ta tab'e baki had'e da d'age kirarta d'aya "Muje" tafad'a bayan ta juya tana takun k'asaita babu ko takalmi a k'afarta kafatanin garin ma bame takalmi harshi kanshi sarkin, harsun juya ta kuma waigowa ta kalli jakar su dake wurin tacewa d'aya "D'akkomun abinda ke jakar cen nacikin irin wancen seki bar musu abunsu agun" dubawa tae bame fari seme baqi haka ta d'akko coke d'in d'aya tabar jakar anan, bayan sun gama maganganun dasuke suka ruf'e qofar cake d'in bayan da suka sako musu wani qaton zaki wanda ya sanya Abu sufyan sakin fitsari a wando ya koma bayan tawayen shi, se ihu mutanen garin keyi ganin yanda suka rud'e anata zabgawa zakin kirari, lokaci d'aya ya soma rura yana zagayen su, yayinda su kuma suka had'e gu d'aya suna adu'a had'e da kukan zuci haukace suke dukkansu. Wurin Abu huraira yae gadan gadan, shi kuwa yae maza yana k'araso jikinshi ya kwanta k'asa ya dakarwa zakin ciki ya hankad'ashi bayan shi seda ya mulmula, tasowa zakin yae ya karkad'e jikinsa ya k'arayi kansa, nan ya soma adu'a dakiran sunan Allah ya k'ara kaimasa naushi ajikin wuya inda ya kuma zubewa, koda zakin ya d'ago sega idanshi yakoma ja kaman jini jikinsa ya koma kalar baki qirin, atake suka fahimci zakin na tsafine "Ku d'auki ayar Allah Dawood wlhy ba zakin asali bane ba" haka suka had'a baki suna rero ayatul kursiyu da duk wata adu'a da karatun alk'ur ani me girma dayazo bakin su, hakan ce ta sanya zakin ya gagara dogon motsi ya zube agun yana zabga rura, daganan ya soma shure shure, itaciya d'aya Abu huraira ya zaro daga cikin wanda aka kafe akai cage dashi yace "Allahu Akhbar!!" Ya dab'a mai aciki take agun zakin ya mace beko shura ba, mik'ewa tsaye sarki yae ya kallu k'uruwa yace "Bala'i ya samemu ance me tarwatsa garin nan shine me kashe zaki, wannan akashesa da ruwan jikin zakin shine kad'ai maganin sa" Itad'inma rikicewa tae tace "Hakane, daya tarwatsa garinmu gwara mu kashe sa, tunda susu ukune akashe makashin Lamme" haka suka d'auki kuka gaba d'aya garin ana wak'a aka kwashesu suda gawar zagin akai cikin gari dasu, a hanya sukejin labarin za'a jiqa Lamme (zakin suke kira haka), seya kwana ajik'e se'a baiwa wanda ya kashe zakin ruwan yasha shima ya mutu idan ba haka ba, garin ze kama da wuta danme tarwatsa gari ya karkashe su ne yazo idan be mutuba su zasu mutu...... Dawuda dakejin wannan yaren ya sanar dasu me ake cewa suka hau adu'a, yanzun ma a cage d'aya aka ajiyesu akaje domin aje a jik'a gawar lamme akashe Abu huraira. *Littafina na kud'ine idan kinsan baki biyaba karki karanta dan Allah, idan har kinaso ki siya akan farashin 200 kacal ki nemi wannan lambar 07084161619* ********* Da sassafe sauya agogon hannunsu sukai da sufyan da zobe harma da rigarsu dayake dama ba kala d'aya bace ba, suka shirya idan an kawo yayi bismillah so 21 shi yasha sun kula tsafine kawai Allah ne kawai ze kub'utar dasu......... Lawuri duk yanda taso tayi bacci abun ya gagareta, abinda taji suna karantawa da k'arfi shine yake mata amsa kuwa acikin kunnuwanta, ko shakka babu so takeyi ta k'ara sauraren wannan abun, bazata iya bacci basam so take ta rik'aji sunayi koda mutum d'aya ne yana mata, mesa takeson ta saurari wannan abun? Mesa ma takeson yanda wannan yake kallonta? So take taje ita yama k'ura mata idanshi, kodan sabida ba'a saba kallonta bane ba takejin hakan? Tana tsananin son taga idanshi a nata, Kalmar sa ta karshe itace tafi kowacce yi mata yawo sabida yawon datake mata harta haddace "Allahu Akhbar!!", matsafane ko shakka batayi wannan ruwan datasha sun mata wani stafin ne aciki amma bari tabi daren nan taje gunsu ya mata wannan karatun dayake koma su duka su mata. ******** Shirinta tsaf tayi taje inda aka ajiyesu a sace, akwai masu gadinsu a wurin amma setayi magana akan zata gansu ne, suka bata hanya tashiga bukkar, tunkan ta k'arisa gun kage d'insu take kiyo sautin muryoyinsu suna wannan abin irin na d'axu, zama tayi batare data k'arisa inda suke ba tafi 3 hours seda taji shiru sannan tabar wurin, jikinta yana mata wani nauyi mesa bataso suka dena ba? Mesa batajin bacci, ya akayi acikin muryoyin nasu take gane muryan me kallonta ido cikin ido? Mesa ya tsaya mata arai, tsafi ko? Ta ayyana a ranta idan hakane zata gwada cin ubansa tun kafin dare yae mata. ************* Washe gari dabino sukaci da cookie's da lemo roba d'aya kowa ya kurb'a, gwara sui manage kafin k'aryarsu ta k'are, sunaji ajikinsu cewar tabbas da yardar Allah zasu kub'uta. Da shirinta tsaf tazo gunsu, itada muqarabanta, fitowa dasu akasa tayi dukda ya sauya kaya kallo d'aya sukawa juna ta gane cewar shine, dariya sosai tayi kafin tace amayar da sauran shi abarshi, sosai suka tsorata naba gaira ba dalili, suna mamakin yanda ta gano lagonsu da wuri haka, kodai wani yaga sanda suke sauya kaya ne? Kai tsafine dai danba wanda ya gansu. Kallon juna suke ko k'iftawa basayi daga shi har ita, seda ta gaji ta janye idanta, hannunta takai inda gefen k'irjinta na hagu naji yanda wurin ke harbawa sauri sauri kaman ze faso k'irjinta ya fito da sauri tace a mayar dashi...lallai tsafine, so yakeyi ya kasheta, me kenan haka takeji a k'irjin ta? ******** "Bana tunanin baza'a gane wannan shirin namu ba, ina tsoron azo asamu matsala gaskia, kar su cutar dakai Abu sufyan, tun jiyan nan seda na sanar dakai banso wannan shirin ba, dan Allah ku taimaka na mayar da komai nawa, idanfa mutuwar ce k'addarata anan tabbas sena mutu kome sabarar ku, dan Allah ku sauya tunani" Dawud ne ya karb'e zancen da cewa "Nasan tsafine shisa nace kuyi hakan, idan tsafinsu akan wanda ya kashe zakin ne kaga baze kama Sufyan ba, tunda muka fito gida muke had'uwa da hatsarin rayuwa iri iri, kuma adu'a ce take bamu kyakyawar kariya ko yanzu adu'ar zamuyi" haka suka zauna suka dinga zuba adu'a kaman ba gobe kafin a kawo Jiqaqqen ruwan zaki. *kark karantamun littafi idan baka biya ba, idan ka karanta kuma toh.....idan kanason ka siya ka kira wannan number 07084161619* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Lillatfina na kud'ine idan baki biyaba karki karanta dan Allah idan kin karanta kuma toh, masu son su siya ga number dazaku tuntub'a 07084161619* 06 Kwana d'aya sukayi kafin su tarar da inda motarsu Abu Huraira take ajiye, ganin motar ya tabbatar musu da cewar lallai nan suka bi, amma suna ina? Shine tambayar da suka gagara baiwa kansu ansa, barde ne ya jagoranci ci gaban tafiyar sabida ya tabbatar akwai dalilin su na ajiye motar, kuma amaimakon baya gaba sukayi, dankuwa ko yanzu bayan aka tsinci motar. *********** Shirye shirye kurun akeyi na yanda za'a gabatar da bikin sadaukar war da za'ayi nanda kwanaki hud'u masu zuwa, yayinda aka jiqa gawar Lamme (zaki) ana so yacika lokacin da akeso a baiwa Abu Hurairah, Lawuri dukda jikinta a mace yake hkan be hanata murna ba, za'ayi maganin wanda ya Rainata, yacika son stoma idanshi acikin nata,tunda take kuwa babu namijin daya tab'a kallon k'wayar idanta seshi, agarin tagwaye so d'aya aka haifa 'ya'yan albarka ake musu suma maza ne kowa yanaji dasu amma suma basu tab'a kallonta haka ba, yanzu ta fahimci irinsu d'aya da wad'ancen bak'in, shirinta tsaf tayi tayi kwalliyar daidai yanda ta saba, taja layi itada masu take mata baya zuwa filin daza'a shayar da Abu huraira ruwan, burinta kawai taga da kanta tana tsaye yasha ruwan harya mutu agabanta taga yanda idan na raini ze kalleta....... Duk yawan yalwar iskar safiyar dake kad'awa hakan be hanawa Abu sufyan had'a gumi ba, baze iya kallo akashe masa d'an uwansa ba amma tabbas a tsorace yake, shi kanshu Huraira baya cikin nutsuwar sa ko kad'an, banda adu'a babu abinda suke aransu dawud ma haka ba wanda zuciyar sa bata tsere wurin dukawa amma hakan be dakatar dasu daga ambaton Allah daneman kariyar shiba. ********** Mom yaukan tafi ko yaushe rikicewa, kwanaki nawa suka shud'e? Lokaci yanata kwaranya ba daddy babu kuma labarin shi dama 2 weeks zeyi ga wannan mutanen kusan sati da tafiya amma shiru, bata samun wayan kowa acikin su, ta kasa gane meke faruwa, Cyama dake zaune kusa da ita itama cikin damuwa ta kalleta tace "Mom please yaran nan inaga da adu'a kika dage kina musu daze fi musu amfani akan wannan damuwar, mom wai kinga yanda kika rame kuwa mom? Dan Allah niki rufamun asiri ki tashi muje k'asa kici abinci semu zauna mu musu adu'a" A raunane ta kalli yarinyar "Cyama wazan gaywa kukana dacen banda Allah?, kowane lokaci kika ganni a damuwa shi nake gayawa, ko yanzu shina duk'ufa nake gayawa ina yin adu'a na tabbatar Allah ze amsa mini sabida shi maji roqon bayin sane" Rik'o hannun mom d'in tae "Tunda kinsan hakan mom seki rage damuwa, kinyi imani da Allah tokuwa tabbas zakiga ribar imanin, dan Allah kici abinci, ban isa ince karki shiga damuwa ba dankoni ma ina cikin damuwar amma baxanji dad'i ba ace bakyacin binci" Jinjina kanta tae "Shikenan Cyama muje, inshaa Allah zanna rik'aci Allah ya miki albarka" . ********** A filin aka ajiye Abu sufyan shishi kad'ai su Abu huraira kamma suna cen gefe an ajiye su, ruwan aka kawo inda sarki k'uru yae bayani akan yanason ya cikawa 'yarshi Lawuri burinta, ta shayar da ruwan ga mugun da kanta, take agun aka yarda da hakan manyan garin sukace shine daidai hakan. Kallonsa takeyi sosai amma shi sam yaqi ya had'a idanshi da nata, a yanayin data kula dashi ma kaman tsorace yake, batajin fad'uwar gaba, kazalika batajin wannan idan daya gagara had'a ido da ita mamallakin gangar jikin ne ya gagara had'a idanshi da nata, mesa takejin daban? Ya akayi takeji cewan ba wannan bame makashin zakin? Idan hakane kenan sanjiya sukai? Kenan so suke su juyar musu dakai, tajima tana tsaye amma kanshi a k'asa duk yanda taso ya d'ago ya kalleta amma abun yaci tura, waigawa tae ta kalli Babbar yarinyarta hadimarta me suna Linta tace "Kicewa aakam ya kawo d'ayan yaron me kamada wannan" sunkuyawa tae ta amsa sannan ta juya cikin sassarfa, bata dawo ba se tare da Abu Hurairah jerasu akai gu d'aya tabisu da ido bata ko k'iftawa, kafeta da ido shina Abu Hurairah yae cikeda tsana, kallo d'aya ta masa tagano Abu sufyan bashi bane ainahin me kisan Lamme, bashi bane me sanya zuciyarta na harbawa so dubu saba'in acikin daqiqa d'aya ba, idan hakane mezai faru idan da an baiwa wannan ruwan? Amma ita sam bazata iya tonawa wannan me kallon nacin asiri ba, bazata iya furtawa da bakinta tace shi bane ba wannan me kamadashi ba "Ku mayar dashi" shine abinda ta furta jikinta ba k'wari cikin murya me tsananin rauni, batasan wane kalan tsafi yae akanta ba, wannan waiko aljanai ne? Ta tambayi kanta, da kanta tayi tsaye seda taga yasha ruwan adadin yawan da ake buk'ata tana mamakin wace kalma ce yake furtawa kafin yasha ruwan menene yake furtawa haka?..... Ihu suka hau yi ganin yagama shanye adadin copunan da akeso yasha, jira kurun suke suga macewar shi, amma shiru shiru har akafi tsawon mintuna talatin!! Ganin hakanya sanya barade soma dukanshi kaman ba gobe da manya manyan itatuwa, tun yana iya kaiwa kanshi kariya da hannunshi harya galabaita ya durqushe, Dawud da Abu Huraira se ihu suke suna k'ok'arin k'wacewa amma an rirriqesu, duka aka masa bana wasa ba, harseda ya dena numfashi, haka suka d'aukesi akan wani abu me kaman dogon baro amma wannan shanaye suke turawa sukai ta zaga garin dashi daga k'arshe sukai bayan gari dashi. ************ Duk yanda Dawud yaso ya basu hak'uri akan su basu koda gawar Sufyan ce abin yaci tura, acewar su sun jefar dashi ma acikin jejin da naman jeji ze cinyeshi, kuma ma tunda yasha wannan ruwan narkewa zeyi. Abu huraira kuka wannan ma ya gagareshi, idanshi ya weqashe duk shi ya janyowa d'an uwanshi mutuwa,daya sani dashi yaje yasha, duk sa'in daya tuna da yanayin dukan da akamai akanshi seyaji hankalin shi ya tashi, yana jiyo amon sautin muryarshi yana furta "Huraira ka taimakeni, huraira zasu kasheni" runtse idanshi yae sosai ya k'udurta aranshi seya nemo d'an uwanshi, jikinshi be bashi cewan ya mutu ba kuma a wannan daren ze fita. ******** Littafina na kud'ine kada ka karantamun idan har baka biya ba, idan ka karanta kuma tam. Me buqatar siya ya tuntub'i wannan lambar 07084161619 ********** Dare yana rabawa kuwa Huraira beko tashi Dawud ba ya bige bukar dasuke ciki ya fito, yayi sa'ar babu wanda ya ganshi ya lallab'a yabi sawun d'an uwanshi dukda yake besan inane aka kaishi ba takamaimai........ Acikin duhuwar daren yake haska fitilar k'aramar wayarshi dake daf da d'aukewa duka sabida rashin cajin ta, tafiya sad'af sad'af cikin tsoro yana me fatan had'uwa da d'an uwan sa koda amacene kuwa, baze so yayi mutuwar wulak'anci hakaba, ko kad'an! Motsin dayaji ne ya bashi dama tsayawa k'yam ya waigo domin ganin ko miye, abinda ya haskane ya firgitar dashi ya kusan suma awurin.. Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na kud'ine idan ka karanta baka biya ba kuma tam.meson ya siya ya tuntub'i wannan lambar 07084161619.* 07 Sauke abinda ke kanshi yae yace "Karka tsorata Hurairah Dawud ne, dama ina bayanka, na rufe fuskatane na sace kayan jikin d'aya daga cikin masu gadin mu, shiyasa kamun nisa ma, naga suma haka suke yawon dare da ganye akai shine na d'ora" Ajiyan zuciya me nauyi sosai Abu Huraira ya sauke yace "Kayi hakuri Dawud, banda nutsuwar zama acen nabar d'an uwana a uk'uba koda hakan ce sun kasheshi gwara amai salla Dawud, basusan darajar mutane ba" Rik'o hannunsa Dawud yae "Kashe fitilan wayar nan muyi adu'a kar wani ya hango haske, mutafi inaga nanne hanyan bayan gari, sabida nan sukace sun kaishi sun wurgar kuma akwai naman jeji inaga fa" shiru yae baya ya kashe suka rik'e hannun juna sannan sukai gaba cikin sand'a, seda sukaji sun dena yawo ajikin bishiyoyin sannan suka kunna fitilar wayar su, lokacin har gari ya soma wayewa, sunyi nisa sosai harsun k'araso wurin ruwan suka hangoshi yashe ko motsi bayayi, da sauri sukai kanshi, d'an uwanshi ya tallafo kanshi sosai ya d'aura asaman cinyar sa yana zubar da k'walla, ganin yanda duk kanshi ya kukkunbura harma da jikin sa sabida azabar duka, kwantar da kanshi yae jikin k'irjinsa yaji yana zuciyar sa na bugawa amma cen maqale, hannunsa ya d'aga ya rik'e ta wutsiyar da kan yatsunsa yaji purse nashi ma ba laifi sedai a hankali sosai komai yayi law sosai "Dawud yanada ranshi duba mana jirgi mubar nan gun dashi kawai" D'aga kai Dawud yae amma ba alamar jigin k'asa ko d'aya, wannan alamace ta cewar wancen jirgin ma da sani aka turashi gun hanyar ba wacce ake yawan bi bace ba, kai ba'a ma bi ruwan yayi yawan da bazasu iya tsallakawa ta hanyar aiki da jikin suba "Abu Huraira babu jirgi anan, sedai da ace a farke yake zamu iya amfani da manyan icen cen kowa ya rik'e d'aya mubar nan jejin tun muna shaida juna" ruwa ya ebo a hannunsa ya wankewa Sufyan Fuska dashi, seda yae kusan so uku sannan ya farfad'o sedai ba k'arfi, suka tashesa a zaune yana buqatar ruwa ba abin shansu, haka suka dinga ebowa da hannu suna bashi harya k'oshi, Shiru sukayi dan sunga garin ya soma washewa sosai, tabbas kuwa se anbi bayansu, dan zuwa yanzu dole ansan basa nan "Ka bari na sanya Al-hasan a bayana mu tafi, biyo sahu zasuyi kuma tabbas sesun tarar sun fimu sanin hanya" Tashi tsaye sukayi ya sanya Abu Sufyan a bayan shi suka kama hanya cikin sassafarwa, agefen ruwan dabasuda tabbacin zasuga k'arshen sa. Basufi 30mns suna tafiya ba aka zageyesu, cikin takaici Abu Huraira ya k'walla k'ara ya sauke Abu sufyan a k'asa yabi k'artin da kallo, matsowa Lawuri tae sosai suka had'a ido da Abu Huraira kallon dayake mata kawai ya isa ya nuna tsantsar tsanar dayake mata a k'wayar idansa, hannunta takai ta rik'e masa hannu, yanayin rik'on datamai bega alamar na fad'a bane wanan ya sanya yae sororo yana kallonta, jira yake kurun yaga me take nufi da wannan salon iskancin kuma, Abu sufyan ta nuna da yatsanta tace "Ku bashi yasha" Da sauri gardawan sukai kanshi suka tashshi zaune suka d'ago kanshi suna shirin qyanqyama mai ruwan, kallon Dawud tae tace "Dashine ya kashe lamme (zaki) da tuni ya mutu, nasan wannan ne me hanani nutsuwa ya kashe sa, shisa na kawo masa magani inba hakaba shima dafin ruwan a hankali a hankali ze zagaye jikinsa harya mutu" kallon Abu Huraira yae cikin sauri yace "Barshi yasha Abu Hurairah magani ne, ta gano bashi bane ya kashe wancen zakin kaine" bece komai ba se kallon cikin k'wayar idanta dayakeyi, Abu sufyan yana shaye ruwan ya singa aman jini ya jima sosai yanayi kafin ya tsagaita, ruwa tasa aka bashi yasha sekuma gashi ya mik'e asaman k'afafuwanshi, kallon muk'arabanta tae maza da mata, babu wanda yasan tafito tasan bayanta zasu biyu musamman dayake baqi ma sun gudu, koda yake seda ta sumar da masu gadin su, hannun Abu huraira taja "Kujagirancemu mu rakasu hanyar barin gari me sauki, wacce muke bi da sarki" Zaro ido wani daga cikin su yae kanshi a k'asa ya soma bata hakuri akan ta dubawa Danginta da mahaifinta tabar biyu su tafi amma d'ayan na sacrifice a barshi ya koma" kallonsa tae tace "Naji muje semu dawo da d'ayan, ainima bazanyi hakan ba" haka suka kama hanya cikin sauri harsu har ita, koda yake duka ya lankwashe Sufyan seda wani gardi ya goyeshi ma. ************** Sarki K'uru bebi takan suba yau, bekuma bi takan 'yarsaba idan da sabo ma yarigada ya saba da yawan yawon ta na tsiya, zema iya cewa tafishi sanin wannan garin nashi da kewaye, shidai hankalin shi ya kwanta tunda ya samu wanda zeyi garkuwa dasu. Maganin baccin data baiwa masu gadin shi kuwa ta dumar dasu juju ne na garinsu, ze iya sumar dakai kwana biyu ma, sabida haka babu wanda yasan meya faru seda mekai musu abinci yaje ya tarar suna bacci zuwa,kumama be tashesuba ajiyewa kurin yae ya juya abinshi wannan ne ya sanya babu wanda ya nemesu. ************ Gardawan nan ilahirinsu tace su juya zatazo tare da Dawud bayan sunyi tafiya me nisa data tabbatar cewar bazasu iya qarisawa gidaba se cikin dare, yarinyar ta Barbo kurun tace zasu dawo tare, babban cikinsu ne ya mata gaddama akan bazata iya juyawa ita kad'ai ba, take ta sharara masa mari "Dacen danake zuwa jeji nai kwana biyu tare muke zuwa? Ina ruwanka? Nace ka koma ban gayawa kowa na fitaba hankalinsu seya tashi" duk'ar da kanshi yae "To kozamu koma tare da wannan d'inne?" Ya tambayeta yana nuna Dawood, harara ta wurga masa "Ni zanzo dashi da kaina nace, kuma idan kaje kace wad'annan duka biyu sun mutu, dama ai ana tsammanin wannan ya mutu ko?, to kace bamu ganshi ba yabi ruwa wannan kuma kace dukanshi kukai bayan ya gudu akazo da tsautsayi ya mutu kanaji ba?" Cikin girmamawa yace "to" suka juya aka barta itada Baiwarta Barbo kurun. Abu Huraira shine ya koya d'na uwansa tajagorancesu cikin sassarfa acikin wannan mugin jejin, banbancinsa da wancen shine akan had'u da 'ya'yan itatuwa kala kala asha. ******* *Littafina na kud'ine, idan har kika karanta baki biyaba keda Allah, idan kinason siya ki tuntub'i wannan lambar 07084161619* *********** Duk iyakar qoqarin da sojojin nan zasuyi sunyi suda Barda tabbas Barde ya sanar dasu sun tsallaka ruwa ne, kuma wannan ruwan shima mahaifinsa ya tsallaka be dawo ba, sabida haka shikam baze shigaba, sannan ba jirgi dan acewar kakansa lokaci zuwa lokaci suke aiko da jirgi k'walli d'aya jal tamkar abun tsafi, dan haka idanma bi zakayi sedai kai kazo da jirgin ka, wannan ruwan kogi ne babba, wanda yake had'a gari zuwa gari bakasan ina ya tsaya ba" Shiru Oga shamsu yae yarasa bakin magana dankuwa shida kanshi duk yawan dazukan dasuka shiga bega kamar wanan ba, ba naman jeji ko d'aya ba 'ya'yan itatuwa kuma ba ruwa se wannan, abin akwai hatsari, Sir munir ne ya dafa kafad'arsa yace "Dolene semunyi ta soja, yanzu kasan mezai faru? Komawa zamuyi gida amma akan hanyarmu ta komawa kowane itace muka gani mu shafa penti gudun b'acewar hanya, sannan adawo da jirgi me saukar Angulu k'waya hud'u da motar yak'i k'waya biyar, a samo motarmu k'waya biyar sannan azo da mayak'a, muzo da floating bridge mu tsallaka wannan ruwan inaga wannan shi kad'aine solution" Nisawa yae sannan ya sakar masa murmushi "Munir kaime basirane sosai, dole hakan zamuyi dan general baze d'agamuna k'afaba" da wannan shawarar suka juya zuwa gida. ******** Ansha fama kam wurin tafiya, koda wancen suka ankara har sunyi tafiya me nisan gaske, sarki yashiga tashin hankali dole yace abi bayansu da gudun fanfalaqi, acewarsa zasu cutar masa da 'yarsa tunda dukansu mata ne. A b'angaren su Abu sufyan kuwa mamaki sosai suke yanda take leading nasu tana musu bayanin so take ta fitar dasu daga garin gaba d'aya yanda baza'a kowa acikin su ba, har take baiwa Dawud labarin abinda ake da mutane idan an kamasu a k'arshen shekara, yasha jinin jikin sa har yakewa maimaitawa Abu Huraira labarin data bashi shida kanshibya tsorata, ta qara da cewar bata san dalilin dayasan takejin bazata iya kallo akashe suba musamman Abu Huraira sedai kome ze faru ya faru, tana kuma son wannan maganar dasuke had'a baki sunayi susu duka idan sunayi setaji sanyi, wannan ne karon farki da Dawood yae murmushi tun zuwansu wannan Doguwar hanyar yagano karatun alk'ur'ani me girma take nufi hakan abu ne dake nuni da yanda takeson addinin nasu alamace dacewar zasu zama wani Haske ga wannan al'ummar idan Allah yaso..... Tunda sukazo wannan d'an k'aramin garin suka sake tsorata, Babu wanda ya kulasu agarin bakuma suji kowa na magana ba har yarama kowa shiru yake, Lawuri ta kalli Dawud cikin tashin hankali tace dashi "Ni bantab'a had'uwa da wannan garin ba, ga alama nima na b'ace hanya ne, dan gaskia yaci ace mun isa hanyar dazaku hau jirgin ruwa zuwa wani wurin ni bansan kowane yare bama se biyu, kuma wancen garin banan hanyar bane ba, gaba da namune sosai, wannan mutanen kuma waye su?. Turus suka tsaya suna kallon mutanen dasukayi tamkar ma basu san anyi ruwan tsiyar su bama. Suna nan har yamma ta qarayi duhu na fara sauka suka soma ganin mutanen garin na sharara uban gudu suna shigewa k'ananun bukkokin su, kowa kuma tsita bame magana amma se ruwan gudu ake ana b'oyewa hakan ce ta sanya su Dawud suma rugawa su adana kawunansu cikin wata bukkar dasuka kula babu wanda ya shiga acikinta, Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Book nawa na siyarwa ne, plss inkinsan baki biyaba karki karantan book nawa, idan kinason ki siya ki tuntub'i wannan lambar 07084161619* 08 Yanayin suturar jikinta ya kalla ya d'auke kanshi gefe d'aya, yana bak'in cikin wannan rayuwar tasu, kalli mace tsirara ace wai wannan fatar sune sutura, kallonshi itama takeyi cikin wani yanayi dabazata iya fassar ko meye ba, abu d'aya ta sani bazata barshi ya tafi ya barta ba, koma yayane seta bishi har inda zashi koda zasu ci gaba da magana ne irinna kurame, batasan dalilin ta na bijirewa iyayenta ba ta cutar dasu akan wannan abun, abin takaicin ma shine takasa gane dalilinta nason tabishi to akan me?...... Kowa yae shiru tsit kakeji acikinsu, babu wani abu dake tashin sauti se bugawar zuciyoyin su dake tserereniya wurin fitar da sauti sauri da sauri. Wuta suka fahimci ana zagayen bukkar tasu dashi, kallon kallo suka shigayi, me hakan yake nufi kenan? Wannan kuma wace *Doguwar Hanya* ce suka k'ara b'ullowa aciki? Kodai wani sabon ajalin ne ke kiransu? Tunda Allah ya kub'utar dasu na wuccin gadi daga wancen gidan, suna nan har aka wuce su batare dasun koda motsa ba, hankalinsu duk atashe yanda sukaga rana haka sukaga daren ranar, suna ganin haske ya soma fitowa sukai taimama sukai Sallan Asubahi dukansu sannan suka fito daga wannan bukkar, yauma kamar jiya babu wanda ya kallesu ma bare yasan suna gun,sun dai kula ana gasa mutum lafiyayye bayan an cire masa kai, to me hakan yake nufi? Wannan ne ya sanya sukai hanzarin barin garin sukai doshi wata *Doguwar Hanyar* dababu me tabbacin zata b'ulle acikinsu, tafiya sukai me nisa sbida har k'arfe biyu tayi lokacin yunwa ta soma galabaitar da Lawuri an saba dacin me kyau, kallon ta Abu Hurairah yae cikin tausayi yace da Dawood "Yarinyar nan yunwa takeji Dawood, bansan mesa ka barta take ta binmu ba, mu kanmu bamuda tabbacin fitar mu a wannan k'uncin bare kuma mu iya kare su, mata kasani sunada rauni matuk'a abubuwan dazamu iya karo dasu mu daure ya kake tunanin su zasuyi, kumama wai shin mesa suke binmu? Akan me?" Ta kula fad'a yakeyi kuma ta tabatar akansu ne, kallon sa shima dawood keyi tunda ya soma magana, dafa kafad'arsa yae "Ka kula yarinyar nan addinin Allah ne yake shirin janyo ta izuwa garemu, yaya zamu bari hasken musulunci ya gagara ratsa ruhinta alhalin munada damar yin hakan?" Sauke nannauyan ajiyan zuciya yae yace "Ya akai kai ka gane cewan musuluncin ta biyo?" Murmushi yae ya shiga nodding kanshi a hankali "Na tabbatar kaima kaga abinda na gani, sedai idan bakason gaskiyar ne kawai, kaga wannan dabanne, sena umarce ta akan ta koma kawai" cikin damuwa yace "A yanzu dai gwara ta koma gaskia sabida bamida tabbacin bata wata kariya, ka duba fa ka gani yanda ake gasa mutum da kaman ana gasa kasa, kuma wancen garin baka kulaba bewa wani magana, dani dakai duk bazamu iya cewa ga dalilin shirun na kowa ba, mu kanmu kuramen k'arfi da yaji muka zama" Cikin fusata Dawood yace "Mesa kakeda sankai ne wai? Yanzu itama tace damu ta b'ata, idan ta koma wancen gari suka yankasu fa? Kai wane irin mutum ne wai?" Kasa cewa da Dawwod komai yae ya k'urawa Lawuri ido cikeda tausayi besan dalilin sa najin matuk'ar tausayin taba, besan me gaba ta tara ba "Shikenan dawood muje" Haka suka d'unguma cikin wahala ga uban k'ishiruwa Abu sufyan dai baya Cewa da kowa uffan shi ta kanshi ma yake yi dan bayajin lafiya sam ajikinsa wannan dukan ya masa raunika sosai ajikinsa, tafiya suke shiru shiru kamar wasu kurame, Har sukazo wani k'aton fili wanda bashida maraba da sahara danko banda yashi babu komai aciki, gashi kuma ba bishiya ko d'aya se k'walleliyar rana, basason su tsaya a samu matsala, haka suka dinga cin wannan yashin me tattare da wata uwar Doguwar hanya mara b'ullewa, Lawuri da Barbo dai ankaisu k'arshe dan har gwara Barbo su dama sun saba abinci d'aya a wuni ruwa idan lokacin damunane so d'aya, lokacin sanyi ma so d'aya amma lokacin zafi so uku a rana, to yanzu dai damina ta soma sauka amma akan kwanaki ma ba ai ruwan ba.... Kasawa tae takai zaune ga yamma tayi sosai, shikansu Sufyan ya gaji sosai, Abu Hurairane ya rik'o d'an uwansa suka zauna suma ba laifi yashin ya soma d'aukar sanyin yammaci yace "Sannu Twin, jikinne ko?" Hawayen dayaketa k'ok'arin adanawa ne suka zubo masa yace cikin wata murya me rauni "Abu Huraira tsoro nakeji, gani nakeyi tamkar bazan k'ara ganin Momyna ba, kuma daddy shine bezo nemanmu ba, ga babban wayana ma yana waccem jakar naga ban ganku da shiba" Dafe kanshi yae "Jakar kam bamuda damar dok'arta amma wayarka gata a aljihuna, na kashe maka ita dama cajin ba yawa sufyan, ka manta tun sanda muka saka karatun alk'urani me girma mukai bacci ta d'auke seda kai cajinta da wayan dawood cajin ba yawa gaba ntwrk me zakai da ita ne?" Wasu yawu ya had'iya masu d'acin gaske yace "Bro kishi nakeji, da yunwa sosai, nakusa in mutu wlhy" Shi kanshi kukan yake yanzu kam "Munshiga tashin hankali mara misaltuwa Twin, kayi hakuri ka dena ambatar mutuwar nan inshaa Allah dukkaninmu zamu kub'uta da yardar Allah zamu b'ullewa wannan doguwar hanyar, Allah daya kawomu nan shine ze kub'utar damu" shiru sukai dukkansu dagacen yakai dubanshi zuwaga Lawuri duk ta fita hayyacinta, tausayinta yakeji matuk'a, matsawa yae kusa da ita besan dawane yaren ze mata magana ba se kawai yace da ita "Sannu" Murmushi ta sake masa amma batace masa komai ba dan ba gane me yake cewa take ba, ya jima dirk'ushe a inda take kafin ya mik'e taimama ya somayi, itama tazo ta somayin kaman yanda taga sunayi, kallonta yae ya sakar mata lallausan murmushi itama murmushin ta mayar masa batare datace komai ba, haka sukai sallah agun yanata mamakin yanda tabisu bayan ance ta tsaya baya ya sani ba sallan ta dan batamasan me suke ba, bayan sun idar ta kalli Dawood dakejin yaranta tace "Wannan maganan dakuke idan dudduk'awa kuna burgeni ina sanshi sosai ka koyamun" murmushi yae "Idan Allah ya fitar damu lapia aishi kenan, sena koyar dake ko Abu Sufyan dankuwa shine ogan mu gaba daya, amma yanzu kowa tsorace yake" murmushi tae batace komai ba" *************** "Alummomi daban daban a sassan na duniya kaf d'inta, gaba d'aya sunada wasu mutane na jeji wanda basuda addini ma kwata kwata, dazakace musu akwai wata al'umma bayan suma bazasu yarda ba, basuda abinda suke bautawa se tsafi a wannan yankin dasuka bi akwai irin wannan al'ummar da dama, bana tunanin zasu tsallake kaidinsu dansu kansu kad'ai suka sani, karkuyi saurin tsallakar wannan ruwan ku bundiga ne daku, amma a ire iren wuraren nan dama ai tsafi yafi yawa, kuje da jirgi me saukar angulu sekun gama zagaye area kaf, anyi stodying na wurin nima zan shirya muje daku" Nisawa oga shamsu yae cikin takaici kan yace "Ba damuwa General, zamuyi yanda kace amma inaga zamuyi hanzarin zuwa sabida me rakamu a jejin wanda ya san hanya laraba laraba kurun yake zuwa, gashi yau kaga sunday idan mukai wasa seyace se wata larabar gashi kace mahaifiyar suma batada lapia, gwara musan me ake ciki" Jinjina kanshi yae "Zan shirya dani zakuje yaushe zaku tafi?" "Yau nake shirin mu rage hanya" ya bashi amsa cikin girmamawa, nisawa yae yace "Koda 12:pm zatayi ku zama a bakin mota zn fito nima" haka sukai sallama akan zasu shirya tafiyar. ********** Anan suka kwana a tsorace seda asuba sukai sallah sannan suka nemi yi gaba, Alhamduliillah basu jima da soma tafiya ba suka soma barin saharar, suka had'u da wuri me yalwar itatuwa da 'ya'yan itatuwa masu yawan gaske, Bismillah sukai suka zauna sukaci tufa dasukagani burjin awurin had'e dayin uban guzuri dn kuwa Abu Huraira rigarshi ya cire ya cikata fam da Tufa da Mango sannan sukaja yana goye da rigar. Kuma ba jimawa suka had'u da ruwa, anan suka sha ruwan kowa da hannunshi sannan suka huta sukai azahar da la'asar sanan suka mik'i hanya dan yanzu ba laifi kowa cikinsa ya d'ago, rana ta k'wale se dukansu take gashi yanzu kam sunkai wurin wasu ciyayi masu yawan Gaske anan Lawuri ta taka k'aya, k'ara ta k'walla me k'arfin gaske aikam da sauri Sufyan yayo kanta, baze manta taimakon datamai ba har abada matsawa yar ya rik'o k'afar tata ya zaunar da ita seda ya cirw mata k'ayar sannan ya tasheta tsaye, takalmin k'afarsa ya zare ya nuna mata su akan tasaka, kallonshi tae kowa yayi turus acikinsu bame cewa komai, ganin bata saka ba ya sanya da kanshi ya tsuguna ya saka mata, sannaj yaja hannunta sukai gaba....agaba suka wuce da k'yar take tafiya da takalmin sabida rashin sabo shi kuwa Abu Hurairah besan mesa beji dad'in yanda Abu sufyan yae ba, sukse yaji ma jikinsa yae sanyi, ranshi yana d'an sosuwa a hankali a hankali musamman daya kula lokaci zuwa lokaci sukan kalli juna su sakarwa juna lallausan murmushi meke nan hakan yake nufi?... A b'angaren Lawuri kuwa burge ta yakeyi takula yafi d'an uwanshi sakin jiki yafishi kirki kuma, sannan suna burgeta sabida sunason taimakon wani, yanayin dayake rik'e da hannunta kuwa yana tayata tafiyar danya kula bata iya bane, se abin yake sakasu dariya dukkansu har suke manta damuwar su, dazaran tad'anyi wani taku ba daidai ba seya nurmusa itama kuma hakan. ******** Sunyi tafiya me nisan zango, yayinda sukeda tabbacin ana biye dasu, koda yake sun b'ace hanya suma bare mabiyan su, K'arar da Lawuri ta k'walla ne ya mayarda dukkan hankulan mazajen uku akanta harma da Baiwarta Barbo, tahau surfafa yare tana sambatu tana nuna k'afarta had'e da yarfe hannayenta duka biya, Abu sufyan da har lokacin suna tafiyane agaba yae sauri mayarda dubanshi ga k'afar har lokacin duhu be sauka ba, k'atotuwar kunama ya gani agefenta, da sauri ya janyeta a wurin yace "Dawood kunama ce ku kalleta k'atotuwar gaske" shida Abu Huraira duk suka kalli gun ita kuwa kunamar da sauri ta shige acikin ciyayi tae tafiyarta, yayinda Lawuri se k'ara take, sunkuyawa yae yana duba inda harbin yake, seda suka janyeta daga wurin ciyayin dannan aka zare takalmin a saman babban d'an ya tsantane ta harbeta amma a yanda suka kula dukta soma haye mata sama tama rasa ina zata nuna, Abu sufyan rigarshi ya cire ya ya yageta da sauri dukda k'arfin datake dashi ya daure yatsan, sannan ya zari k'aya ya caki gun ya sanya bakinshi ya tsotse jinin tatas, yana zubar wa a k'asa, se gumi take had'awa suna mata sannu, Abu Huraira yayi sororo yasani abinda qaninsa yae taimakone amma mesa yakejin ba dad'i a ranshi? Menene yasa bayaso yaga ana taimakon wannan baiwar Allah alhali shi kuma ya tabbatar har k'asan zuciyarsa yana tsananin jin tausayin yarinyar. Abu sufyan kuwa dukya tashi hankalin sa, gashi macece bare ya goyeta gashi basason duhu yae batare dasun isa inda ya dace su isaba, san wannan wurin an sma da kunama inata ga kuma dare yayi, dole sui sauri su bar gurin, ganin taimakone kuma babu wata hanya se wannan ya sanya yace ze goye ta, harara Abu Hurairah ya wurga masa cikin takaici yace dashi "Kai kana haukane zaka ce zaka giyeta abayanka?" Kallon sa yae cikin mamaki "To anan zamu tabbata Bro, kana gani fa bazata iya tafiya ba, idan dare ya mana anan an soma da kunama ya kake tunanin zata k'are? Kokuma Waze goyetan to? Wannan macece bazata iya d'aukar taba" cikin b'acin rai yace "Nizan goyeta bakai ba kamaji na gaya maka matsamun agun!" Ko motsawa Abu sufyan beyiba zabida mamakin kalaman yayan nashi kuma tawayenshi meke damunshi haka?... Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafin doguwar hanya na siyarwane, idan kina son ki siya seki tuntib'eni ta wannan lambar wayar 07084161619* 09 Mik'ewa tsaye yae yana mamakin Brother shi kanyace "Ur over reacting bro, calm down mana menene yasa zakace kaine zakayi, open all wahalan daka sha akaina, tun yaushe kake tafiya dani a bayanka? Gaskia tunda naji sauk'i nine zan d'auketa" Sauke ajiyar zuciya hurairah yae "Kaida Bakada lafiya yaya kuma zaka k'arawa kanka ciwo, dubi kanka fa har yanxu da sauran k'umburi ga k'afarka ma haka" Dawood ta kalla cikin damuwa sosai tace "Kamar fad'a suke ko?" Girgiza kanshi yae yace "Abu sufyan ne ya kafe akan ze d'aukeki kinga kuma bashi da lapiya, shine, Abu Huraira yace dakanshi ze d'auke ki amma fad'a suke ba zancen kenan" murmushi tae tace dashi "Dan wannan aibama sesun wahala ba, zan iya tafiya ai sekace maciji?" Jinjina kanshi yae "Da gaske zaki iya?" Ya tambayeta "Allah zan iya, Barbo tayani in kik'e kawai, haka suka shige gaba ita da Barbo, tafiyar shiru kakeji wannan karon har duhu ya sauka basui magana ba, seda taradda fili sannan suka samu zaunawa sukai sallah, sukaci tufa da mango sedai ba ruwa, Haska fitila Abu Huraira yae yana nazarin wurin, tabbas Filine amma bame zaunuwa ba har a wani kwanta, ramukan dake wurin filin sunyi yawa ko ina ramuka ne gasunan burjik, kamar na macizai dan haka ya jagoranci tafiyar dauke da Adu'a a bakunan su suka k'ara nausawa cikin hanyar sunkai 11:pm na dare suna tafiya kansu tadda ruwa, badan huraira yasoba sukai masauki agun, ga dare gashi basusan me ruwan ya k'un sa ba. ********** Haka tafiyar su General ta yiyu acikin kwana d'aya suka isa k'auyen, inda jiragen masu saukar angulu suka rigasu zuwa jejin suna me zagayar gun sun tabbatar bayan an tsallake ruwan akwai garuruwa kusan bakwai dasu kaga mutane suna rayuwa aciki, amma basu san wanne ne ba, da wannan suka koma akan idan ma me sh8ga jejin bazeje ba zasuwa jejin saukar aradu zasu fara da garin dake manne da ruwan dazaran an tsallaka, wannan ya sanya suka shirya helicopter har 4 suka nausa da manya manya bindigoginsu a garin. Tunda suka sauka a garin suke shan mamakin yanda mutanen garin suke kallon su, wasu mamaki qarara a fuskar su wasu se rugawa suke sa gudu jin k'arar jirgin, haka sun kula yaren nasu yasha banban danasu, takawa sukai har cikin garin da k'yar wani ya tsaya yin magana dasu, sun fahimci yare yake kamar yarbanci sedai ba duka bame yarbancin da wannan ya jagorance su zuwa gun sarki bayan ya sanar dasu sarki yau kwana uku beda lapia sabida b'atan 'yarsa, wanini me suna geoge da wani kanu suke magana dasu dan sune yarbawa. Sun sanar dasu akan tabbas sunzo amma sun sace 'yar sarkin sun gudu Kafin kace meye wannan sun nemi kawowa sojojin hari basusa meye bundiga ba, seji sukai an soma mayar da martani jini yana zuba gasu su qananun wuqaqenw dasu dana katako wanda ake feqewa, aikam lokaci s'aya k'auyen ya rikice aka hau gudu ana ihun cewar dama ance garin ya kusa mutuwa. Sojojin basu b'ata lokacin suba suka juya gun general suna so su gaya mai cewar ga abinda sukaji daga garesu. ************ Washe gari da asuba sega wani me tuk'in jirgi koma ince jiragen ruwa sunkai 10 wasu sun kawo passengers wasu kuma empty sukazo, abin mamaki fulatanci suke wannan abun ya burge su Hurairah dan kuwa yarem momy kenan sunaji sosai,mutanen suka sanar dasu akwai rugar fulani a gaban kad'an kuma sannan akwai 'ya'yan itatuwa dasuke zuwa d'eba anan suna kaiwa cikin gari siyarwa, itatuwa a zube suke a jejin na Allah, haka suka shiga jirgi d'aya dama sunada kud'i a aljihunsu sedai bame yawa ba amma ba laifi suka biya ya gangara dasu bakin ruwan bekoda wani tsayi sosai, shisa mutane sukai yawa ba jimawa suka taradda rugar fulani ga shanaye nan burjik babu iyaka ga gonaki nan malale k'auye me yalwar ni'ima, anan akai musu iso gun me garin bayan sunmai bayanin abinda ya samesu yace a baiwa matan suturu yana mamakin dama anan kusa dasu akwai garin maguzawa har haka, acikin Nigeria nan ya dace aje musu da addinin islama dai kam...dattijo me karamci d'aki aka basu bukka d'aya sedai far sunada nisa da cikin gari, matsalar ma jiya mota ta tashi yanzu se bayan sati biyu zata dawo dama haka takeyi, bama wannan ba akwai garuruwa uku dazasuje dole kfin Allah yasa sukaiga inda motar take, wannan labarin be musu dad'i ba sam idan akwai abinda suke buk'ata shine su isa gida kafin wayewar garin gobe, amma koda wannan rufin asirin Allah ya barsu sun gode masa. Lokacin da dare ya tsala sun shiga takura sosai, sabida da farko dai da k'yar suka samu suka iya shan zallan Nonon da aka basu susha sabida k'arnin nonon, sannan kuma bukkar kyasone kurun aciki gata qarama gasu susu biyar ne, Cikin tausayi ganin su Lawuri a takure Abu sufyan yace da Abu Huraira "Mu kwanta a waje mana, inyaso da safe semu shiga ciki, yaya zasu samu nutsuwar bacci a tare damu?" Kallon shi Huraira yae "Bakan tunani ne me kyau, mu basu wuri, haka suka fita ranar kuma aka sheqa ruwan sama, sunsha wuya, badan sun soba suka kwana a bukkar tare dasu, da Asuba bayan sunyi sallah Abu Hurairah ya kalli Dawood yace "Naga kamar ana kamun kifi a bakin rafin cen, mezai hana muje mugani ni zaman tunanin duniyar nan ma ya ishen wlhy" kallon mamaki ya masa yace "Kaida nasan bakasan k'arnin kifi kuma?" Mezaisa kaje wurin?" "Nidai zanje, idan bazaka ba se naje ni" "Bro Nima zanje zan bika" Atare suka mik'e Dawood na mitan kafiya irin na Hurairah, ya sani k'arnin kifi har amai yake sakashi amma ya kafe akan seyaje aise yayi tunda yaji yakuma gani... ********** Mommy kam jiki yayi nisa, sam batada lapia ko kad'an, duk yanda taso tacire abun aranta lamarin yafi k'arfin tunaninta, Cyama da Hanifer sune suke jinyarta dan har ankwantar da ita ma, ita Cyama babu abinda yake damunta irin rashin lafiyan mamanta, batasan meya samu 'yan uwantaba gakuma momy a kwance, hanifer ma haka, Abu huraira take so kamar ranta ze fita, tunda ta nemeshibta rasa kuwa bata cikin nutsuwarta da kwanciyar hankalinta, haryau tana tuna yanda sukai sallama bayan daya bata aran motar sa, lumshe idanta tae kurun cikin tsananin damuwa. *********** General yayi shiru yana nazarin jejin, tabbas yaranshi suna shirin tashin hankali mara misaltuwa, da wannan ya yanke shawarar ashiga jejin gadan gadan dankuwa shi kad'aine solution agaresu, da wannan sukawa wani fili saukar angulu suka soma tafiya da k'afa agaban jejin domin nemansu. Sunyi tafiya me nisa harta kwana biyu dayike su sojojine basu sha wahala ba kamar su, suna iya yin tent na wuccin gadi su zauna, a hankali harsuka isa garin nan da ake cin naman mutane, da wannan suka samu damar tambayar en garin kosun gansu, amma ga mamankisu kowa sukai qoqarin yiwa magana baya amsa musu, ko kallonsu ba'ayi, sunsha mamaki sosai na wannan rayuwar to kodai aljanaine wannan garin, General ne yae umarni akan tunkan dare yae musu sui gaba dn wannan garin tabbas ba lafiya acikin sa, haka suka yi nisa wa garin sosai sannan suka yada zango awani fili me yalwar yashi, hankalin general be kwanta da garin ba still dan haka sukace zasu koma cikin dare sui bincike yana ganin kamar ko yaranshi suna garin ne, da wannan sukai shiga irinta soja suka nausawa garin cikin sand'a. Gani sukai wasu mutane suna yawo sa wuta suna zagayar d'akunan mutanen garin, sannan daga bisani suka cinnawa wata bukar wuta sega mutanen ciki sunfito da gudunsu suna qoqarin guduwa, suna kallo suka sassaresu su kusan hud'u, sannan suka d'aukesu suna rera wak'a abakunan su suka rawa, general jikinsa yae sanyi suna nan a b'oye har safiya ta soma yi suna kallo aka hasa wuta aka d'add'auresu ajikin ice aka soma gashin su, kansu ya masifar d'aurewa mekenan ake nufi, komawa sukai inda suka fito suke baiwa sauran labari, sabida akwai mamaki akasheku kuma makasanku suzo suna gashinku acikin gari sannan babu yako d'aga ido ya kallesu me za'ayi da naman? General dai duk dauriyar sabyau seda yae kuka yana tsoron indai ba ankashe masa yaran saba, tunda wancem garin sun sanar cewar sun gudu kuma anzo nemansu ba'a samesu ba. Shawarar kaiwa garin hari akayi amma koda suka bazama sesuka tarar kowa naman nan ake yanka masa yana ci, cikin tashin hankali sukai gaba, dan duk yanda sukaso babu wanda ya kulasu, kenan gudun da mutanen garin keyi gudu ne na gudun kar a yankasu a gasa? To amma shirun fa? Na meye? . General yasha kuka sanda suka bashi akan sunada yaqinin yanda basu kulasuba suma bazasu kulasuba koda sunzo dan haka sunyi gaba, da wannan suka k'ara ci gaba da tafiyar dasuke. ************* Sunyi enjoying rayuwar su abakin ruwan, har kamun kifi sukayi, sannan suka hasa wuta suka dafa shi, suka yanke shawarar kurun suje su kaiwa wannan matan dasuka baro, sunga yanda duk suka rame akwanaki qalilan kenan. Kwanansu hud'u agarin suka nemi hanyar yi gaba inda Me garin ya basu 'yan rakiya susu biyu suka jagorance su har suka isa bakin ruwa daganan ma seda suka tsallaka dasu sannan suka dawo, anan ma sunci karo da wata rugar fulani masu karamcci an karrama su ba kad'an ba agarin, seda suka kwana uku sannan suka bar garin, a haka a haka har suka isa inda motar zata tashi zuwa cikin gari nanda kwanaki uku masu zuwa, sedai ba kamar sautan garuruwa ba dole ce ta sanya su kwana a tasha. ********* General kuwa yasha wuya shida yaranshi kafin su taradda wannan ruwan, basu wani sha wahalar tsallaka ruwan ba suma suka isa garin,anyi sa'a general da kanshi yake jin fulatanci, bayan doguwar tambaya aka sanar masa tabbas sunzo anma sun wuce yafi da sati motar ma da ake saka ran su hau nanda kwanaki uku zata tashi, da wannan ya bada umarni akan manyan su koma inda jiragen shida wasu zasu bi sahun su twins, amma se wani ya bada shawarar su bari suje gaba d'aya inyaso se aje da wasu jiragen a d'auki wancen tunda garin dake kusa dasu naman mutane ne abincin su, hakan kuwa akayi jirgi uku suka hau a ranar suka naushi d'ayan garin. ********** Zazzab'i sosai Lawuri keyi amma bata sanarwa kowa ba, tarasa dalilinta najin yawan fad'uwar gaba me tsanani aduk sanda ta tuna mahaifanta, da 'yan uwanta anya ta kyauta kuwa? Yanzu harse yaushe zasu samu wani sui sacrifice dashi? Idan akace basu smu bafa hakan yana nufin ta kashe iyayenta da 'yan uwanta da hannunsu, ada tana tunanin tamkar yin hakan ba komau bane mma yanzu ta hango tsantsar rashin kyautawar dabatayi ba, amma yazatayi da rayuwar ta? Tsari d'aya kenan dayazo mata, batasan yazatayi da ranta na akan wannan al'amarin, taso ta yakicewa zuciyarta amma batasan meke hanata ba akan yaran nan, ita kanta bazata iya cewa ga takamaimai abinda yasanya take binsu ba, bata tsammani akwai ranar dazatazo rana d'aya ta guji danginta ba haka kawai, anya bazata koma ba kuwa? Amma idan kuma wani abun ya same tafa? Ta tabbatar wa kanta yanda suke murna sun baro wannan bala'in bazasu yarda su rakata ba bare kuma har sun tarardda wurin da ake gasa mutun, kai koma ba hakan ba ita bazata komaba ta rasa me mata wannan maganar dasuke susu uku, ga kayan da aka sanya mata ma a wancen k'auyen a bingili suke ga masifaffen sanyin dake ratsa ta sabida zazzab'in datakeji tako ina, tarasa nutsuwarta da farin cikin ta, gefen k'irjinta na hagu zafi sosai yake mata, Barbo cema ta fahimci batada lafiya harta gayawa Dawwod data kula shishi kad'ai yakejin yaren su, anan suka taimaka mata sun neki chemist amma babu haka suka kwana tanashan wahalar sanyi. *******Bayan kwana uku* Ba k'aramin sanyi sukaji ba a ransu dasuka samu hawa mota for the first time tun bayan dasuka bar motarsu a wannan jejin, abin takaicinsu d'aya sama suka samu asaman kayan amfanin gona suda wasu Fulani masu qarnin tsiya, sunyi sa'a sosai sedai fa hanyar batada kyau sam, sunyi tafiya ta kusan awa uku kafin su tarar da wani titin dasukeda tabbacin tun zamanin mulkin soja aka shinfid'ashi, duk ya gama mutuwa sedai sufa hakan wata rahama ce agaresu dankuwa yaushe suka saka ran zasu ga qara ganin titi ma a rayuwar su? Ai basu zataba sam. Su General koda suka zo ansanar dasu ai motar tafi sa'o'i uku da d'aga wa, kuma tabbas samari uku da 'yan mata biyu sun samu shiga kotar, sedai shi general baze iya jiran zagowar makon nin biyu ba kafin ya koma gida dn haka ya nemi wata hanyar musamman yasa azo masa jirgi me saukar angulu yawa hanyar k'aura, atake wani bafillatani yace dashi shi yana motar sama, kurun k'a'idane sati bibbiyu ake zuwa kuma hanyar ce ba kyau, take general ya tilas ta masa kaisu cikin garin zema k'ara masa kud'i akan wanda ake biyanshi. Tafiyar tasoma gajiyar dasu sanda aka taresu, wasu mutane masu furka a rufe da qyalle sa manya manyan bindigogi ne suka tare motar, take dulanin nam suka soma salati suma su Dawood suka hau yin salatin, duk inda kake kanajin qarar bundigar sanda wanin su ya harbata a sama, hankula sun matuk'ar tashi musamman twins dake tsammanin wahalar su ta k'are ashe ashe tsugune bata gama k'are musu ba!!!! Sunfi 4 hours suna binciken su snin hanyar bame bi ba soja ba 'yan sanda kafin daga bisani su soma shirin barinsu anan suna qoqarin tafiya da motar cikin jeji sabida dama kayan amfanin ginar suke so, da kudad'en dasuka zo dashi, Abu Hurairane ya shiga musu magiya akan su taimaka su barmusu motar, yaya zasu bar wannan *Doguwar hanyar* idan babu mota dan Allah su taimaka......aikam take agun wani daga cikinsu Ya dage bundigarsa ya danna masa harsshi take ya xube agun kowa yae tsit se Abu sufyan daketa faman kuka yana rik'e dashi, suna kallo suka bar wurin bayan har wayoyinsu sun karb'e suka kuma tafi da motar, cikin azaba Abu huraira ke mayar da numfar fashi sama sama, sauran se kuka suke Abu sufyan cikin kuka yace "Daddy kana inane haka? Gashin mun shiga halaka ka turomun wannan *Doguwar Hanyar* mara b'ullewa, daga wannan bala'in se wancen Allah ka kawo mana d'auki, Allah ka ceci ran d'an uwana ya Allah, kowa kuka yakeyi cikin tashin hankali.... *Littafina na kud'i ne idan baki biyaba karki karanta, idan kinaso seki tuntub'i wannan lambar 07084161619* Mom Nu'aiym [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwane idan kanaso ka biya ka karanta idan karantamun littafi baka biyaba kaida Allah, idan ma biyan kai kayi sharing kaida Allah. Me buqatar biyar litattafanmu ya tuntubi wannan lambar 07084161619* 10 Haka ya dinga zubar jini yana juyi agun, lawuri ta kalli Barbo tace da ita cikin yarensu "Yana zubar da jini da yawa, naga kaman akwai ganye aja anan wurin da sauri ki tsinkamun" Batare da Barbo tayi magana ba ta juya da gudu cikin jejin, seda ta had'o ganyaye kusan uku sannan ta dawo, ba wani ruwan dazasu wanke ganyayen hakla ta murje ganyayen da hannunta ta ta kama k'afar da aka harba ta cura su tana nan manne da wurin sesa taga jinin ya dena zubowa, sannan abu sufyan ya qara yagar rigarsa aka d'aure k'afar "Mubar nan wurin, nizan goyeshi, mu taimaki kanmu kar daren yae mana anan, bamusan mezai faru ba" Driver kuwa kallon su yae yace da hausarsa ta fulani "Sa'a suka samu daganan zuwa cikin gari ba wani nisa, ko'a mota befi mana saura mintuna 25 ba, sunsan kota bata zuwa k'auyen nan se bisa tsautsayi dan haka mutaka, bana tunanin nanda awanni biyu ma bazamu isa koma qasa ga hakan" jinjina kai dawood yae "Bakajin dad'i abokina, barin goye shi idan na gaji ka tayani, ni asibiti nakeso mui rushing muje" shidai Abu Hurairah bayama cikin hayyacinsa azabar dafin billet daya ratsa shi kawai ya ishesa, haka suka rankaya Dawood yana goye dashi suka ci gaba da yankan doguwar hanyar, taimakon da Allah ya musu ma titine ba kwana ko shiga gona ko jeji bare ka b'ata. *********** Sunyi tafiyar kamar awanni biyu kafin suka taradda babban gari anata hada hada, kai tsaye asibiti suka wuce dukda bame waya acikinsu babu kuma wanda yakeda ko k'wandala,wahala sosai sukasha akan sesun kawo police report kafin a karb'eshi daga k'arshe kuma akace baza'a musu aiki ba kud'i ba, a binciken da Abu sufyan yae kuwa garin dasuka sauka ko kusa beda alaqa da garin dasuke yanzu, tafiyace ta tsawon kwanaki kafin ka isa wancen garin dasuka baro kayansu kuma ATM card d'inshi yana cikin kayan sa, dama Na huraira ne suka fito dashi kuma ya b'ata tuni, ajakar dasuka baro k'auyen su Lawuri yake, dafe kanshi yae ganin yanda jini ke zubar masa cikin ma an tsare dana hausa gashi harya suma ma sabida azaba "Dawood yanzu ina zamu samu kud'i anan? Yaya zamuyi ni kaina ya d'aure wlhy" kallonshi yae shima cikesa damuwa "Bansan yanda zamuyi ba? Bansan wasu irin k'addarori bane marasa dad'i suke bibiyar mu, na rasa gano inda al'amarin ya dosa" shiru sukai dukkansu suna tunanin mafita ************ Sun tsaya da motarsu ganin jini akan titin, inda d'aya daga cikin sojojin wanda likitan soja ne shi ya Duba jinin, kallon general yae yace "Baze wuce 3 hours ba da faruwar abun, abun kuma jinin na mutum ne" Nisawa yae cikin tashin hankali ya kalli dirensu yace "Dama ana fashine anan?" Asuwakin dake bakinsa ya goga hak'waranshi dashi "Sosai kau, sabida ai sunsan a wannan ranar kad'ai mota ke wucewa se kuma bayan sati biyu irin ranar, kuma kayan abunci suke karb'ewa sedai kuma sukan tafi da motar ne, wani zubin ma sekaga sun ajiye motar abakin titin nanda en kwanaki, kuma idan akai gaddama sukanyi harbi gaskia" Shiru General yae kanshi ya k'ulle, duk abinda ya faru da yaran nan laifin sane, besan mesa ya kafe akan sesunyi tafiyar nan ba, mahaifiyar suma tace hankalinta be kwanta da tafiyar ba, shi har yanzu mamakin kanshi yake wlhy, yanda ya dage yanzu wa gari ya waya? "Amm yanzu mintuna nawa zasu kaimu cikin garin?" Kallonsa yae "Ai munzo, mintuna ashirin zuwa ashirin da biyar sun wadatar, an kusa zuwa cikin garin ai" bece komai ba ya koma mota sukai d'auki hanyar cikin garin, bayan da duka isa yace da General "Yanzu tashar mu zamuje semuji meya faru awurin direban" jinjina ka shi yae yana mamakin yanda gabaki d'aya kanshi ya dena aiki, har suka k'arisa bece komai ba. Sunyi sa'ar ganin direban kuwa inda suke basu labarin meya faru, har abinda ya faru da en bunnin nan, hankalin General ya tashi matuk'a dajin wannan zancen "Yanzu wane asibitin sukaje?" Rike baki Direban ya "Sunce su bak'ine basu tab'a zuwa nan garin ba, nima kuma ban tab'a sanin wani asibiti ba anan, amma dai gabas sukayi danko kud'in dazasu hau adaidaita basuda shi" Godiya General ya musu sannan ya nemi gidan soji na nan garin ya karb'i mota da direban su, kana ya soma yawon asibito cin garin kaf neman yaranshi. *********** "Koyaya naso nai tunani sena gagarayi, zuciyata tana mun tserereniya akan abinda ze faru ga d'an uwana Dawood, ina cikin tashin hankali mara misaltuwa bansan waze taimakemu ba, asibitin nan basuda imani suna ganin mutum helpless su taikeshi bashi bane a ransu se zancen kud'i?" Kallonshi Dawood yae cikin damuwa yace "Ga bamuda waya, gabansan number kowa aka ba" cikin zaquwa yace "Nasan number mom aka, muje gun kiran waya na kud'i kokuma ma mu ari wayar likita anan ko wani staff" "Hakan yayi muje" hakan sukaje suka samu wata mace a reception suka ari wayanta suka kira mom, haka sukayi ta kiranta a waya bata d'agawa har kusan so ba adadi, cikeda damuwa ya wurgawa dawood idanshi "Bata d'auka ba wlhy" ya fad'a cikeda damuwa "Ita kad'aice number dakake da itane?" Shiru yae nad'an lokaci kanyace "Se Number Ayusher, barin gwada neman ta muji" kiranta yae ringin biyu ta d'aga kuwa, cikin muryanta me dad'i tace "Hello" guntun tsaki yaja "Badai zaki dena ba kenan ko?" Tashi zaune tayi cikin mamaki "Father sword da gaske kaine, where have you been? Hav bn trying ur number all this while but its not going through" dafa goshin sa yae cikin qosawa da zancen nata yace "Ayusher saurareni mana" shiru tae dan tasan seya datse kiran yanzu "Ina cikin problem and bayaga number mommy banida number kowa aka bayan naki, so zanje wurin first mony agent zan qara kiranki a waya, u transfer 150k in to their acc inyaso sesu taimaka su bani cash" Nisawa tae "Meya faru dakai hakane Farher sword?" Haushinta ya somaji "Look Ayusher banida time na dogon bayani, just do as i say, u makesure that kin ajiye wayanki a kusa dake, zn kiraki da wani layin daba wannan ba yanzun nan ba jimawa, sena tura miki acc details d'in" murmushi tae "Alright Pure hrt bye" ta kashe wayan, neman gun first money agent sukai, sunsh fama dasu kafin su yarda, sabida acewar su sedai ka bada kud'i a tura ma waninka, koka basu ATM su cira da kansu su baka, da qyar gashi weekends ne suka yarda da wannan shawarar, suka taimaka yashirata ta turo mai kud'in aka bashi sannan suka koma asibiti. ************ Alhamdulillah anyi masa aiki an cire bullet d'in lokaci bullet ne ma, na irin bundigar nan ta farauta, alamun dai qauyawa ne, aka saku damar gayar k'afar kuma anyi sa'a da aikin dan kuwa zuwa dare harya farfad'o, shi kuwa General beyi tsammanin zasuce asibiti ta garin babba ba, sedabya gama karad'e asbitocin garin kaf da clinics be samesu ba sannan ya nemi makwanci badan yaso ba, se washe gari ya soma neman Su a teaching hospital ta garin. Besha wahala ba gun gano har d'akin dasuke, koda Abu sufyan ya ganshi a d'akin kasa koda k'wak'waran motsi yae ya k'ura masa na mujiya kawai yana kallon sa!, a hankali ya taka gun gadon na Abu huraira ya kalleshi yana bacci tausayin yaron ya sanyashi kuka, gashi kuma duk Abu sufyan yafita hayyacin sa, banda wahala babu abinda kake hangowa a fuskokin su, seda Abu Sufyan ya rungumeshi suka sha kukansu kafin su zauna baiwa juna labarin abinda ya faru, shirin tafiya gida yae musu ba b'ata lokaci sabida mahaifiyar su dake cikin halin ciwo ba qaqqautawa. *Ban saniba ko iyakar tsawon hanyar kenan, ban saniba ko sun gama shan wahalar rayuwa kokuma da saura, bana tunanin nasan mezai faru agaba, abu d'aya na sani shine yanxu aka soma wasan, wasan na manya ne, wasan me wahala ne, dani daku semun daurewa bin Doguwar hanyar nan atare kozamu samu madafar b'ullewa* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwa ne, idan kanso ka biya ka karanta idan ka tsinta a waje ka karanta baka biyaba kaida Allah... Me buqatar siya ya nemeni ta wannan number . 07084161619. 11 "Menene yanzu yake damunta?" General ya wurgawa Cyama wannan tambayar acikin waya "Batacin abinci jininnkuma har yanxu be sauka ba inji Dr." Nisawa yae yace "Kibata wayar tam zan mata magana ne" mik'a mata tae tace "Mom, dad ne ze miki magana" karb'a tae ta kara a kunnen ta "Adaman General ya jikin ki?" Murmushi tae jin abinda yace "Naji sauk'i Daddyn Twins" ta fad'a tana me k'ok'arin nuna masa bata cikin wani ciwo "Na samo miki yaranki, ki gayawa jinin nan ya sauka da sauri, ga Abu sufyan ma ze miki magana" Da sauri ta tashi zaune tana dafe kanta "Da gaske kake?" Amaimakon taji muryan General setaji muryan Abu sufyan "Mom sannu da jiki ya jikinki?" Mayar da numfarfashi tasomayi sauri da sauri kantace cikeda farin ciki "Sannu Sufyan, ina kuka shiga haka kuka nemi d'agamun hankali mahaifiyar Dawood ma tashiga damuwa me tsanani" murmushi yae "Mom ki kula da kanki kawai da lafiyanki mufa muna nan lafiya lau, wayoyin mune kurun aka sace mana duka, amma dukanmu muna cikin qoshin lafiyax harma tare da dad zamu dawo, please kiji sauqi kinji?" Ya k'arashe maganar cikin shagwab'a, tabbas ko wannan halin ya isa ya nuna cewan Abu sufyan d'intane, murna awurinta ba'a magana haka sukaita hira daga bisani sukai sallama bayan ya sanar mata Hurairah yana wanka gudun karta gano bashida lafiyane. *********** Shirinsa tsaf yae shida Dad da dawood sannan aka kwashesu zuwa airport dan da jirgi zasu koma abuja, tafiyar dabata wuce 40 mns ba ta sadasu da Abujan, Rahama wacce basu tab'a shiga acikintaba suka tsinc8 kansu aciki ganinsu a babban birnin tarayya, da wheelchair aka d'auki Abu Huraira, su Lawuri se zare ido suke, dama haka duniyar take da ababen kallo iri iri, kalli motoci kaman ba gobe dama haka rayuwar take suke cikin mugun jejin cen basu masan abinda ake ciki ba, kodai wai mafarki ne takeyi? Kokuma shin aa Aljanaine suka sato ta? Tama rasa me zatai tunani akai a haka har aka umarcesu da shiga motar suka d'unguma dukkansu zuwa gida. ************ Abu Huraira kam asibiti aka wuce dashi inda suka k'ara duba k'afar alhamdulillah aiki yayi kyau, sedai fatan samun lafiya, Abu sufyan kuwa shida sauran dukansu gida suka wuce, kai tsaye d'akin su ya wuce ya shiga toilet yafi 2 hours yana dirxar jikinsa, yasha mamakin yanda gashi ya masa yawa sekace wanda ya shekara baya cikin al'umma, koda gake ba abin mamaki bane tunda yaga yanda gaba d'aya Abu Huraira yazama sekace wani tsohon zaki jikinsa duk gashi, bashida nutsuwar daze wani b'ata lokacin gun kwalliya dukda haka ya shirya tsafi acikin k'ananun kayan sa shirt blue da wando fari qal, hannunsa ya wurgawa kallo bemasan dunuyar da agogon sa ya shiga ba kuma dashine ake ganeshi, zoben dai yana nan, murmushi yae ya fito daga d'akin nasa bayan ya feshe jikinsa da turaruka masu tashin k'amshi me sanyi da sanyaya zuciya. A k'asa yaci karo da Hanifer bayan daya sakko, zuwa tae tana masa murmushi yabkalleta cikeda kulawa "Hanny Baby, kina lafiya?" "Ka rikitar dani yaa Sufyan nasan kaine ma, gashinan kanamun wannan kallon" murmushi yae "Naji nine ya akayi?" "Duk ka canja fa, kwata kwata kaman ba kaiba" gemun daya masa tsawo ya shafa yana murmushi bece komai ba "Yaa Huraira fa?" Kallonta yake har yanzu "Huraira zazzab'i yake yana asibiti ma, daga zaran nayi aski gunshi zanje, ku da dare sekuje yanzu wannan bak'in ki nuna musu sui wanka ki basu abinci da lemo me sanyi sannan ki wadata su da suturu wannan kayan jikinsu ai destroying nasu ki baiwa gate man ya qonasu" Jikinta duk yae sanyi "Yaa Sufan kace ina gayar da yaya huraira plss" Ta qarashe maganar wane zatai kuka jinjina kanshi yae ya juya kawai. Kai tsaye shagon aski yaje yae askin san sannan ya wuce gun mom, murna awurinta ba'a ma magana, bayan sun gama gaisawa take tambayar sa Huraira yace ciki zolaya "Lallai mom inaji dake, toba zagwad'in ganinki ya sanya gaba d'aya na manta ban sanar dake ba, kinsa halin Brother zazzab'i ya kamashi fa yanzu haka yana kwance agidan amma yace a gaisheki, idan naje gida zan kira kui magana danki tabbatar yana lafiya, yamaso yazo nace kasan Mom bazataji dad'i ba idan har ta ganka kana layi kuma kazo dubata" Murmushi tae "Allah ya bashi lafiya, waime ya faru dakune Kyautar Allah nashiga damuwa fiyeda tunaninka, sekuma naganka fes fes amma karame sosai fa" kallon ta yae cikin murmushi "Mom ya bazan rame ba bayan banida abinda zanci, kin sani nifa idan bake kika girka abuba ko Baba ladi bana iya cinshi, shisa nayita shan yoghurt kawai harna rame" ya k'arashe maganar cikin tsananin shagwab'a har yana d'aura kanshi asaman kafad'arta, hannu ta sanya ta tureshi da wasa, tana dariyabta kally Cyama "Cya zanga ranar da yayanki ze girma, kalli shifa gotai gotai dashi yake so ya k'arasa 'yar tsohuwa" murmushi Cyama tae "To mom tun yaushe rabon daya ganki mom? Ni yaa Sufyan kurun ka hau cinyar tama" Dariya sukai dukkansu sannan suka shiga hirar duniya, anan yaci abinci sosai sannan yace zeje gida, bayan nan gun Huraira ya wuce, suka zauna sukaita hira yake gaya masa yanda yae da mom, qaramar wayar daya siya ya zaro ya kira mom ya baiwa Huraira jin yana lafiya ba qaramar nutsuwar ya saukar mata ba, take cewa base yazo ba ya zauna abinshi seyaji sauqi. ************* Su Lawuri agun wanka ma ansha fama dasu dankuwa Hanifer har mamakin wannan gidadancin take, to suwaye ga basajin Hausa, se Sighn language (yaren kurame) suke amfani dashi, da k'yar ta tsaya sukai wanka ta basu dogwayen riguna na material nanma tasha fama seda ta saka musu kuma sesuka kasance a takure dan basu saba ba, abinda ma takula dashi shine basa jin dad'in kayan, abinci kuwa ansha fama dasu, shinkafa da miyane amma ko yanda zasuci basu sani ba, gaba d'aya kan Hanifer ya d'aure seda ta zauna ta ebo nata tanaci suna gani sannan suka ci, bazasuce basuji dad'i ba amma dai basu sababa kam, hakan datakula basu maci da yawa ba ya sanya ta kawo musu 'ya'yan itatuwa ba laifi sukam sunsha sosai, bayan nan kuma d'aki ta kaisu suka kwanta sabida rage gajiya, ita baiwar komai d'ari d'ari takeyin sa, danko gadon kasa kwanciya tae kusa da uwar gijiyar tata se a qasabta kwanta babu wanda ga mayar da tsawon 30mns acikinsu batare da yayi bacci ba. ******** Sufyan kuwa bayan nan Gidansu Ayusher ya wuce, a waya yae kiranta tafito tana tafiya cikeda yanga ta d'aukar hankali, sanye ajikinta farar doguwar jallabiya ce da mayafinta ja, agaban rigar ko ina an rubuta Ayusher da manyan haruffa da jajayen duwatsu, agogon hannunta ma fari ne qal, shima jikin fatar rad'am zaka hango an rubuta masa Ayusher da jajayen duwatsu takalmin k'afarta jane gaba d'aya, ta zuba asalin kyau dan har bayan rigar ta Ayusher ne zane da red stones, tana tafiya tana taunar cingom, se wani murmushibtake fesa masa yayinda ya kawar da kanshi gefe d'aya azuciyar sa yana jin haushin halayen Ayusher, bud'e mab'allin motar tae tashiga gefen me zaman banza ta zauna, k'amshin turarukansu suka daki hancin juna kowannen su seda ya lumshe idan sa, watsa masa kallo tae "Yau da kanka a gidanmu pure heart?" Gajeran tsaki yaja cikin takaici "Kewai when zakiyi hankali ne?, kinzo mun ba sallama kin shigo ba gaisuwa kin soma zuba surutu akaina" Sadda kanta tae, mantawa take dawa yake gabanta ta manta masifar shi "Am so sorry , Assalamu Alaika kuma ina wuni?" "Alaikissalam, sorry dama kud'in nan na kawo miki sauri nake da inda zani" cikin mamaki ta kallesa "Wane kud'in kuma pure heart?" Murmushi yae "Look Ayusher banzo nan mui wasa ba, kud'in dakika turamun nagode sosai, shine na dawo dashi" a yamutse ta kalleshi cikin hargitsi "Haba Father sword mesa ni kome zan maka arayuwa bazan burgeka bane ba? Kud'in kaman banida shi zakace zaka dawomun dashi?" B'ata fuska ya k'arayi "Nasan kinadashi shisa nace ki bani aro ai, Ayusher plss karki b'atan lokaci, nagode sosai da kulawa da kuma taimako, so ki karb'a kud'in nan" Jikinta yae sanyi inda sabo tasan halin Sufyan kozata mutu tunda beso karb'a ba baze karb'a ba, cikin takaici ta karb'a tace "Thank u" murnushi ya sake mata "Zan kiraki anjima idan na nutsu, karki kirani dan Allah da kaina zan kiraki" kallonsa tae yanxu kam har k'walla ya taru a idanta "Amma sufyan kasan yanda mutane ke sona, kasan yawan samarin dake tururuwa akaina kaine kad'ai kake wulaqanta ni, yanzu meye laifi idan ni na kiraka fisabilillah" abinda yake had'ashi da ita kenan "Kin iya jinjina yawan masoyanki, kinga Ayusher dan Allah jeki" Cikin fusata tabar cikin motar, tsaki yaja shikan yae gaba da motarsa zuwa gida. ********* Abin duniya ya soma damun lawuri, tarasa inda zata tsoma ranta, baccin ma datayi da tulin mafarkai barkatai tayishi, dukda mahaifiyarta hankalinta ya koma gida, gida takeso taje taga me suke ciki amma batasan hanya ba, lallai seta koma gida bazata juri rashin mahaifiyarta ba, amma ko Wancen ze bita kuwa?. Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwa ne, idan kanso ka biya ka karanta idan ka tsinta a waje ka karanta baka biyaba kaida Allah... Me buqatar siya ya nemeni ta wannan number . 07084161619. 11 "Menene yanzu yake damunta?" General ya wurgawa Cyama wannan tambayar acikin waya "Batacin abinci jininnkuma har yanxu be sauka ba inji Dr." Nisawa yae yace "Kibata wayar tam zan mata magana ne" mik'a mata tae tace "Mom, dad ne ze miki magana" karb'a tae ta kara a kunnen ta "Adaman General ya jikin ki?" Murmushi tae jin abinda yace "Naji sauk'i Daddyn Twins" ta fad'a tana me k'ok'arin nuna masa bata cikin wani ciwo "Na samo miki yaranki, ki gayawa jinin nan ya sauka da sauri, ga Abu sufyan ma ze miki magana" Da sauri ta tashi zaune tana dafe kanta "Da gaske kake?" Amaimakon taji muryan General setaji muryan Abu sufyan "Mom sannu da jiki ya jikinki?" Mayar da numfarfashi tasomayi sauri da sauri kantace cikeda farin ciki "Sannu Sufyan, ina kuka shiga haka kuka nemi d'agamun hankali mahaifiyar Dawood ma tashiga damuwa me tsanani" murmushi yae "Mom ki kula da kanki kawai da lafiyanki mufa muna nan lafiya lau, wayoyin mune kurun aka sace mana duka, amma dukanmu muna cikin qoshin lafiyax harma tare da dad zamu dawo, please kiji sauqi kinji?" Ya k'arashe maganar cikin shagwab'a, tabbas ko wannan halin ya isa ya nuna cewan Abu sufyan d'intane, murna awurinta ba'a magana haka sukaita hira daga bisani sukai sallama bayan ya sanar mata Hurairah yana wanka gudun karta gano bashida lafiyane. *********** Shirinsa tsaf yae shida Dad da dawood sannan aka kwashesu zuwa airport dan da jirgi zasu koma abuja, tafiyar dabata wuce 40 mns ba ta sadasu da Abujan, Rahama wacce basu tab'a shiga acikintaba suka tsinc8 kansu aciki ganinsu a babban birnin tarayya, da wheelchair aka d'auki Abu Huraira, su Lawuri se zare ido suke, dama haka duniyar take da ababen kallo iri iri, kalli motoci kaman ba gobe dama haka rayuwar take suke cikin mugun jejin cen basu masan abinda ake ciki ba, kodai wai mafarki ne takeyi? Kokuma shin aa Aljanaine suka sato ta? Tama rasa me zatai tunani akai a haka har aka umarcesu da shiga motar suka d'unguma dukkansu zuwa gida. ************ Abu Huraira kam asibiti aka wuce dashi inda suka k'ara duba k'afar alhamdulillah aiki yayi kyau, sedai fatan samun lafiya, Abu sufyan kuwa shida sauran dukansu gida suka wuce, kai tsaye d'akin su ya wuce ya shiga toilet yafi 2 hours yana dirxar jikinsa, yasha mamakin yanda gashi ya masa yawa sekace wanda ya shekara baya cikin al'umma, koda gake ba abin mamaki bane tunda yaga yanda gaba d'aya Abu Huraira yazama sekace wani tsohon zaki jikinsa duk gashi, bashida nutsuwar daze wani b'ata lokacin gun kwalliya dukda haka ya shirya tsafi acikin k'ananun kayan sa shirt blue da wando fari qal, hannunsa ya wurgawa kallo bemasan dunuyar da agogon sa ya shiga ba kuma dashine ake ganeshi, zoben dai yana nan, murmushi yae ya fito daga d'akin nasa bayan ya feshe jikinsa da turaruka masu tashin k'amshi me sanyi da sanyaya zuciya. A k'asa yaci karo da Hanifer bayan daya sakko, zuwa tae tana masa murmushi yabkalleta cikeda kulawa "Hanny Baby, kina lafiya?" "Ka rikitar dani yaa Sufyan nasan kaine ma, gashinan kanamun wannan kallon" murmushi yae "Naji nine ya akayi?" "Duk ka canja fa, kwata kwata kaman ba kaiba" gemun daya masa tsawo ya shafa yana murmushi bece komai ba "Yaa Huraira fa?" Kallonta yake har yanzu "Huraira zazzab'i yake yana asibiti ma, daga zaran nayi aski gunshi zanje, ku da dare sekuje yanzu wannan bak'in ki nuna musu sui wanka ki basu abinci da lemo me sanyi sannan ki wadata su da suturu wannan kayan jikinsu ai destroying nasu ki baiwa gate man ya qonasu" Jikinta duk yae sanyi "Yaa Sufan kace ina gayar da yaya huraira plss" Ta qarashe maganar wane zatai kuka jinjina kanshi yae ya juya kawai. Kai tsaye shagon aski yaje yae askin san sannan ya wuce gun mom, murna awurinta ba'a ma magana, bayan sun gama gaisawa take tambayar sa Huraira yace ciki zolaya "Lallai mom inaji dake, toba zagwad'in ganinki ya sanya gaba d'aya na manta ban sanar dake ba, kinsa halin Brother zazzab'i ya kamashi fa yanzu haka yana kwance agidan amma yace a gaisheki, idan naje gida zan kira kui magana danki tabbatar yana lafiya, yamaso yazo nace kasan Mom bazataji dad'i ba idan har ta ganka kana layi kuma kazo dubata" Murmushi tae "Allah ya bashi lafiya, waime ya faru dakune Kyautar Allah nashiga damuwa fiyeda tunaninka, sekuma naganka fes fes amma karame sosai fa" kallon ta yae cikin murmushi "Mom ya bazan rame ba bayan banida abinda zanci, kin sani nifa idan bake kika girka abuba ko Baba ladi bana iya cinshi, shisa nayita shan yoghurt kawai harna rame" ya k'arashe maganar cikin tsananin shagwab'a har yana d'aura kanshi asaman kafad'arta, hannu ta sanya ta tureshi da wasa, tana dariyabta kally Cyama "Cya zanga ranar da yayanki ze girma, kalli shifa gotai gotai dashi yake so ya k'arasa 'yar tsohuwa" murmushi Cyama tae "To mom tun yaushe rabon daya ganki mom? Ni yaa Sufyan kurun ka hau cinyar tama" Dariya sukai dukkansu sannan suka shiga hirar duniya, anan yaci abinci sosai sannan yace zeje gida, bayan nan gun Huraira ya wuce, suka zauna sukaita hira yake gaya masa yanda yae da mom, qaramar wayar daya siya ya zaro ya kira mom ya baiwa Huraira jin yana lafiya ba qaramar nutsuwar ya saukar mata ba, take cewa base yazo ba ya zauna abinshi seyaji sauqi. ************* Su Lawuri agun wanka ma ansha fama dasu dankuwa Hanifer har mamakin wannan gidadancin take, to suwaye ga basajin Hausa, se Sighn language (yaren kurame) suke amfani dashi, da k'yar ta tsaya sukai wanka ta basu dogwayen riguna na material nanma tasha fama seda ta saka musu kuma sesuka kasance a takure dan basu saba ba, abinda ma takula dashi shine basa jin dad'in kayan, abinci kuwa ansha fama dasu, shinkafa da miyane amma ko yanda zasuci basu sani ba, gaba d'aya kan Hanifer ya d'aure seda ta zauna ta ebo nata tanaci suna gani sannan suka ci, bazasuce basuji dad'i ba amma dai basu sababa kam, hakan datakula basu maci da yawa ba ya sanya ta kawo musu 'ya'yan itatuwa ba laifi sukam sunsha sosai, bayan nan kuma d'aki ta kaisu suka kwanta sabida rage gajiya, ita baiwar komai d'ari d'ari takeyin sa, danko gadon kasa kwanciya tae kusa da uwar gijiyar tata se a qasabta kwanta babu wanda ga mayar da tsawon 30mns acikinsu batare da yayi bacci ba. ******** Sufyan kuwa bayan nan Gidansu Ayusher ya wuce, a waya yae kiranta tafito tana tafiya cikeda yanga ta d'aukar hankali, sanye ajikinta farar doguwar jallabiya ce da mayafinta ja, agaban rigar ko ina an rubuta Ayusher da manyan haruffa da jajayen duwatsu, agogon hannunta ma fari ne qal, shima jikin fatar rad'am zaka hango an rubuta masa Ayusher da jajayen duwatsu takalmin k'afarta jane gaba d'aya, ta zuba asalin kyau dan har bayan rigar ta Ayusher ne zane da red stones, tana tafiya tana taunar cingom, se wani murmushibtake fesa masa yayinda ya kawar da kanshi gefe d'aya azuciyar sa yana jin haushin halayen Ayusher, bud'e mab'allin motar tae tashiga gefen me zaman banza ta zauna, k'amshin turarukansu suka daki hancin juna kowannen su seda ya lumshe idan sa, watsa masa kallo tae "Yau da kanka a gidanmu pure heart?" Gajeran tsaki yaja cikin takaici "Kewai when zakiyi hankali ne?, kinzo mun ba sallama kin shigo ba gaisuwa kin soma zuba surutu akaina" Sadda kanta tae, mantawa take dawa yake gabanta ta manta masifar shi "Am so sorry , Assalamu Alaika kuma ina wuni?" "Alaikissalam, sorry dama kud'in nan na kawo miki sauri nake da inda zani" cikin mamaki ta kallesa "Wane kud'in kuma pure heart?" Murmushi yae "Look Ayusher banzo nan mui wasa ba, kud'in dakika turamun nagode sosai, shine na dawo dashi" a yamutse ta kalleshi cikin hargitsi "Haba Father sword mesa ni kome zan maka arayuwa bazan burgeka bane ba? Kud'in kaman banida shi zakace zaka dawomun dashi?" B'ata fuska ya k'arayi "Nasan kinadashi shisa nace ki bani aro ai, Ayusher plss karki b'atan lokaci, nagode sosai da kulawa da kuma taimako, so ki karb'a kud'in nan" Jikinta yae sanyi inda sabo tasan halin Sufyan kozata mutu tunda beso karb'a ba baze karb'a ba, cikin takaici ta karb'a tace "Thank u" murnushi ya sake mata "Zan kiraki anjima idan na nutsu, karki kirani dan Allah da kaina zan kiraki" kallonsa tae yanxu kam har k'walla ya taru a idanta "Amma sufyan kasan yanda mutane ke sona, kasan yawan samarin dake tururuwa akaina kaine kad'ai kake wulaqanta ni, yanzu meye laifi idan ni na kiraka fisabilillah" abinda yake had'ashi da ita kenan "Kin iya jinjina yawan masoyanki, kinga Ayusher dan Allah jeki" Cikin fusata tabar cikin motar, tsaki yaja shikan yae gaba da motarsa zuwa gida. ********* Abin duniya ya soma damun lawuri, tarasa inda zata tsoma ranta, baccin ma datayi da tulin mafarkai barkatai tayishi, dukda mahaifiyarta hankalinta ya koma gida, gida takeso taje taga me suke ciki amma batasan hanya ba, lallai seta koma gida bazata juri rashin mahaifiyarta ba, amma ko Wancen ze bita kuwa?. Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na kud'i ne idan baki biyaba kika karanta keda Allah, idan kinaso ki tuntubi wannan number 07084161619* 12 *Bayan kwanki biyar* Har akai kwanaki biyar Lawuri bata cikin nutsuwar ta sam, komai baya mata dad'i ga yawan yin mafarkai da mahaifiyarta, mafarkin datayi yau yafi komai firgitata, sabida mafarki tae da mahaifiyarta an cinna mata wuta tana ihu tana neman taimakonta amma ita ta gagara zuwa ta tallafeta, ganin haka ya sanya ta soma tunanin lallai tabbas iyayenta basu samu wanda zasu bayar matsayin sadaukarwa ga abin bauta ba,kuma tabbas an kashe su. A bayan gidan take zaune ita da kuyangarta Barbo furanni da 'yan shuke shuke dake gun suna d'ebe mata kewa, Kuka takeyi na abubuwa kala kala, na farko tunda suka dawo bata k'ara sanya mutanen uku a idanta ba dukansu, tarasa to zamanme take ne, ga wannan yarinyar da wannan tsohuwar ma yaransu sukejiba ga rayuwar takura su a jejin dasuke ko rijiya babu a kogi suke ebo ruwa, a jeji suke kashi, amma wannan komai ya sauya komai basu iyaba hatta yanayin cimarsu daban da tasu, bakinta be saba ba sam! Kallonta barbo tae cikin kulawa tace "Lawure shugaba ya dace mu koma gida fa, yanzu nasan K'uru da k'uruwa suna cikin damuwa kamar yanda kema kike ciki yanzu" "Barbo wataqil ma an kashe su fa, idan fa basu samu sadaukarwa bafa sune za'a kashe, anya Barbo na kyauta kuwa" sadda kanta k'asa tayi "Nasan Baki kyautaba amma ni inaga kaman zuciyanki kika bi, kuma akwai abinda kikeso agun mazan garin nan" D'agowa tae suka kalli juna "Inaso insan halinda Iyayena suke ciki, amma banso na koma cen, so nake nasan menene ake ciki bansan ya zan ba" Barbo batace komai ba sega Abu Sufyan akansu, murmushi d'auke a fuskar sa ya kallesu "Sanunku" shine abinda ya fad'a yana kallonsu, ganin yana murmushi ya sanya ta sakar masa murmushin itama, cikin ido ta kalleshi tana share k'wallan idanta, da hannu ya mata alamar tambaya akan menene yana b'ata fuskar sa akan menene yake sanyata kuka, nanma take ta fahimcesa dan haka da kanta ta masa alamar ba komai lokci d'aya k'walla yana kwaranya daga idanta, b'ata fuska yae yashiga nodding kansa alamar bayaso ta dena, bayan hannunta ta sanya ta share k'wallan daya silalo tana k'ok'arin sanya murmushi a fuskar nan, da hannu ya mata alama akan tabiyo bayanshi, haka suka rankaya har babban parlor gidan, zama yae ya nuna mata da hannu akan ta zauna, zama tae ya nunata da hannu sannan u Yakai hannunsa a bakinsa alamar cin abinci yana tambayar ta ko taci abinci? Lokaci d'aya ta fahimci meyake nufi ta shiga gyad'an kanta alamar taci, jinjina kansa yae ya mayar da dubanshi akan TV yana jiran k'arasowar Dawood dakuma Abu huraira yau an sallamaeshi a asibiti mommy ce kawai basu sallama ba acewar su jinin keda sauqin hawa amma saukar se'a hankali, suna nan jigum jigum har sukaji sallamar su, zamanta a gidan na kwanaki biyar ta fahimci cewar idan Akayi wannan maganar shigowane za'ayi haka harta soma haddace yanda suke amsawa dan haka kafij yae aune harta furta "Amin wa Alaikumussalam" da sauri dukkansu suka kalleta suna mamakin dukda kalmar tayi wani iri abakinta yanda ta iya furtashi, yaushe tazo harta iya ansa sallama hakan nan rad'au a bakinta, Mik'ewa tsaye tayi tana kallon Abu Hurairah tana zuba masa murmushi, kallonsu take shida Dawood har suka k'araso acikin tsakiyan palon, seda tayi jim kantace dasu "Sannunku" kamar yanda Abu sufyan yace dasu d'azu, sannan yanda taga Cyama da Hanifer suna gayarda Baba ladi kullum shine itama tace "Ina kwana Baba ladi" a zatonta duka gaisuwar ce har Baba ladi, yanzu kam dariya dukkansu suka saka mata suna jinjinawa Hikimomin Allah yanda ya halicemu da magana amma kowa da yarensa dayakeji, Dawood ne yace mata cikkn yarensu dashima akwai banbanci "Ina kwana, shine ainahin gaisuwar Baba ladi, sunan matar dasuke gayarwa kenan baya cikin gaisuwar kamar ke ai sunanki Lawuri ko?" Gyad'a masa kanta tayi alamar eh yace "Yauwa to idan zan gayar dake senace "Ina kwana Lawuri" idan fa da safe ne kenan, idan kuma da rana ne ko yamma sena "Ina wuni Lawuri? Kingane ko?" Murmushi tae tace dashi "Tokai menene sunanka?" Yana murmushi yace "Ni sunana Dawood" ya nuna Abu Sufyan da d'an yatsansa yace "wannan kuma sunan Abu Sufyan", ya qara Nuna Abu Hurairai yace " Wannan kuma sunansa Abu Huraira" Jinjina kanta tae cikin gamsuwa tana me k'ok'arin nanata sunayen a bakinta cikin dabaru dan basui daidai ba zaka ka gane dai "Menene sunan wannan mtan to?" Kallon sufyan yae yace "Matan nan gidan take tambayar sunansu, wakenan ne?" Numfashi sufyan ya sauke cikin yanga yace "Cya ne da hanny ko?" Se yaran qanana inaga" kallonsa ya mayar zuwaga reta "Cyama kenan d'ayar kuma Hanifer" yamutsa fuska tae "Sunanku wahala ne dashi, yaushe zan koma gidanmu ne" kallon mamaki ya mata amma seyace da ita "Se sanda kika yarenmu yanzu dai ba inda zaki" batace dashi komai ba se zama datayi a saman kujerar tamkar wata er koyo sanye da jar atamfa d'inkin doguwar riga tayi kyau sedai kanta ba d'ankwali, gashin kan har yau yana nan jiya iya yau "Yau mamanmu zata dawo fa, yadace dai asan abinyi" Abu sufyan ya fad'a "Dama Mom batasan komai ba kenan game da abinda ya faru da wannan yaran?" "Ba abinda na sanar mata sabida banason ta tashi hankalinta sedai ta dawo ta gani, amma me zamuce mata?" Dawood ne ya sharb'e zancen da cewa "Ba abinda zamuce mata se gaskiya, idan muka damu kanmu akan hakan ai bamu godewa Allah kuma ai daddy yana nan ko, shima ze iya mata bayani da kanshi" jinjina kansu sukai cikin gamsuwa da bayaninsa Hanifer ce tazo ta sauri taje ta hugging yayanta Hurairah, cikin d'okin ganinsa "Oyoyo swt bro na, i really really missed u" D'agata yae daga jikinsa "Halin ya motsa ne se yaushe zaki girma ne wai, yanzu gand'a memiya dake sekizo kina tab'ara anan hadda wani rungumeni ko" ya furta cikin kafeta da manya manyan dara daran fararen idansa, Turo baki tae tahau doddoka k'afa a k'asa "Allah yaya nifa bana tab'ara, koda kadawo asibitin ma gunka se Yaa sufyan ya hana inje ma ance kana zazzab'i kuma shine kum....." Shiru tae ganin k'afarsa a d'aure da sauri taje k'asa gaba d'aya ta dafe k'afar a hankali "Subhanallah bro menene a k'afanka haka" Cikin zafi Abu sufyan yace "Hanifer please mana, karki ishemu da surutu kaman aku, badai gashi kinga yaji sauk'i ba ki godewa Allah, sabida da abin yazo da tsautsayi se mutuwa kurin ba ajali se rabon shan wahala harbin b'arayi sukayi a gun" Anan ta zube tanata faman kuka duk rararrshin duniya sunyi tak'i tae shiru "Seda fa nagayawa yaa Huraira ni Banson tafiyar nan sam, na sanar masa hankalina be kwanta ba" ganin haka ya sanya Sufyan ya mata masifa sosai seda tabar parlon hurairah murmushi kawai yae aranshi yana mamakin K'aunar da Hanifer ke masa irin wannan idan da agaban saurayinta tae aita taro match....Lawuri kuwa fuskar nan ta sauya setaji haushin wannan Hanifer ma meye na wank zuwa ki dinga kuka anan koda batajin me suke fad'a ta fahimci lallai zancen dai akan raunin k'afarsa ne take kuka to meye hakan?..... ************* Murna sosai ake agidan, ga Abu Huraira ya dawo ga kuma mom ta dawo, General ma yana gidan anyi girke girke kala kala, zakasha mamakin yanda ma akai aikin har wanka da kwalliya yaran gidan sukai idan ka gansu zaka d'auka wani bikinne ya tashi, mazajen sune suka d'akko mahaifiyarsu daga asibiti, Abu Hurairah kam tunda ta ganshi crouches hankalinta ya nemi tashi "Menene ya sameka haka ban saniba Na fari?" Ta tambaya tana kallonshi cikin ido, murmusawa yae cikin nuna ba komai bane "Mom calm down mana bafa komai bane ba, gogewa nae a k'afa ga gocewar qashi shikenan ne, bakiga nazo d'aukan ki da kaina ba?" Dukda bata yarda ba amma bata tankaba se "Allah ya tsare na gaba" kurun data iya furtawa cikin muruwar jiki. Kallon wannan Family kurin zakayi ka tammabatarwa kanka cewan lallai suna ciki tsantsan farin ciki, sedai mom ta k'asa tsayae da zuciyarta gu d'aya akan wannan matan data gani takuma rasa waye ma zata tambaya game dasu, seda ta kalli cyama da hanifa bayan sun kammala cin abinci tace dasu "Kuje da bak'in nan ciki zamuyi magana da yayyunku" Ba musu suka ja hannunsu zuwa ciki, anan mom ta nemi sanin su waye, abu hurairah shine yae jarumtar gaya mata tundaga farkon maganar har k'arshen sa, Koda ya gama kuka sosai takeyi na tausayawa halin dasuka shiga ciki, gefe d'aya tana godewa Allah akan ni'imar sa na kub'utar da yaranta daga hanun azzalumancen da sharrin jeji, haka aka dinga jajantawa juna sedaga bisani ta kalli Abu huraira tace "Wannan yaran dakuka saki jiki suka biyoku, ina kuke tunanin zaku kaisu, acikinku wayene ze mayar dasu ga iyayen su, a duk labarin wannan *doguwar hanyar* dakuka d'auka banaji kunzo da hankulanku a yayin dawowa yaya ma zaku daddage ku kwaso mana *maguzawan jeji!!* alhalin bakui tunanin ainahin dalilin dayasanya suka biyoku ba? Kokuma ku dalilin daya sanya ku kuka kwaso mana annoba ba, kai Na fari sarai kasan halina bana d'aukar ire iren wannan haukan wannan yaran dakuka kwaso sekusan nayi dasu, danni bazan bari ku bisu su koma garin suba bakuma zan lamunci su zaunamun a gidana ba ehe" kallonta General yae dama yasan a rina yasan halin zafin ta gata itama ta iya kafiya akan hukuncinta "Ba'ayi haka ba adama, ni ina ganin haske musulunci ne ya janyo yaran nan, itace fa 'yar sarkin garinsu wannan baiwar tace, kinga alamar zata wuce 16 yrs ne ko'a haihuwa? Batada alamar wayau ma, idan mukai musu rashin mutunci irin haka sesu d'auka addinin mu ba tausayi" idanta harya k'ada yayi ja sanda take kallonsa tace cikin takaici "Sunsan addini ne? Matsafa ne fa General, kanada dalilin mayar dasu gida ai, ka sanya a d'aukesu da jirgi me saukar angulu a mayar dasu inda suka fito danni dabadan dare bane ko kwana bazasuyi agidana ba, kanaji fa har ruwan mugun zakin gawar safa suka baiwa sufyan nawa wlhy suda Allah" General dasu sun rasa bakin nata hak'uri duk yanda suka so su d'auki abun da sauki mom ta kafe, se turjiya takeyi me ban mamaki dankuwa basu zata hakan zatayi ba. ************** *Washe gari* Mahaifiyar Dawwod ma kafewa tae akan lallai sesun bar gidan, shi kuma General da asuba yabar gidan kwata kwata yama bar garin zuwa sokoto akwai aikin dasuke da shi acen sokoton, sun yanke shwara korar yaran dazaran su Sufyan suka saki jikinsu akan zasu barsu, tunda sunyi ta lalama abun ya faskara, haka suka nuna wa sufyan kaman ba komai, Abu Huraira dake da ciwon k'afa ma haka ya d'aukesu a mota harsuka isa salon na gayarn gashi da k'afa, a mota yajira seda yaga an gyare Lawuri tsaf! Har baiwar ma ba laifi kud'i sosai aka cake sa dankuwa ko farce basa yankewa, k'afan uban datti, koda ta fito dukse ya soma hangowa hasken fatrata da kyau, yana murna ya mayar da ita gida, kowa yasha mamakin kyawun datayi daganan suka sake wanka ta sanya jallabiyan dake jikinta, washe gari suka shiga sabgoginsu tunda shima k'afar tayi sauk'i alhamdulillah yaji garau, mom kuwa dama shirinta kenan, da driver ta had'asu tace seyayi nisa yabar cikin garin Abuja dasu an yanki jeji ya ajiyesu su k'ara gaba yanda zasu fita harkar gidanta har abada!!!! *Ni kaina tuna nina ya tsaya cak akan wannan al'amarin! Bana fahimtar yaren mom, anya bata nemi tarwatsa mana farin cikin mu ba kuwa? Ko shakka banayi mun qara lulawa ne wata *Doguwar Hanya* mara b'ullewa.........* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na kud'ine, idan kana buk'atar ka siya seka biya ka siya, me so ya tuntub'i wannan lambar 07084161619* 13 Kallon Khaleed Oga Shamsu yae "Kabi mana ghali da yarancen, karsu wuceka fa, koma dai muje taren ja muje" Haka suka ja suka bi bayan ghali dasu Lawuri, ganin ya d'auki hanyar fita gari ya sanya suka sha gabansa damai alamar ya tsaya, sauka yae daga kan titi ya gangara k'asa, suka paka gaba d'aya Oga Shamsu yace dashi bayan sun firfito "Ina zakaje da yaran nan?" Cikin tashin hankali yace dashi "Hajiya ce tace na saki cikin gari zuwa barin gari, idan munje a jeji na saukesu na dawo" Girgiza kanshi yae dan dama general yace ya sanya mai ido akan su "Ka koma dasu gida, kuma ko bana nan aka k'ara sakaka aikata wannan mugun abun ka sanar dani tukunna, kaji dai abinda nace ko?" Girgiza kanshi yae ya shiga motar sa da sauri, shima kuma suka juya suka rakasu har gida, koda suka Dawo Mom hankalinta a kwance tayi sa'a ta rabuda k'aya agidan ta, Oga shamsu ne ya shigo tare dasu da sallamar sa, amsawa tae tana me kallonsa cikeda mamakin ganin su Lawuri a bayansa "Shamsudeen lafiya dai?" Matar oga ma oga ce sabida haka ya russuna cikeda ladabi yace "Yarannan dalilin su aka barni agarin nan hajiya, dukda yake tafiyar nan ta aikice ko oga bashida halin hanani yinta amma tunda yake ya isa seya mun umarni da kwana tsaye k'yam akan kulawa dasu, kada ki manta basu san *Doguwar hanyar* da akabi akazo nan ba, basusan Allah ya halicci wata aba wai ita mota ba, zama acikinta ma tsoro yake basu, maza ma dasuka shiga jejin da hanyar garin su take sun girgiza sun tsorata bare kuma mata, hanyar garin nasu bata Abuja ake biba sam cen wata nahiyar ce, na tabbatar bazasu shekara anan ba, General seya saka an mayar dasu gida, ina rok'on alfarma kiyaye hana su fita konan dacen idan bani akeso na musu wani abinba da kaina kokuma wanda suka kawo su nan garin" Cikin Takaici ta kalleshi yaunya hango b'acin rai sosai a idanta game dashi "Zan kiyaye ubana, sedai kuma kai seka kiyaye gayawa wani wannan maganar, kakuma tabbatar ka baiwa uban gidanka shawara akan kwashemun tarkacen maguzawa agidana dazaran ya dawo dan banason ganin su" murmushi yae irin na matar soja se soja "Angama hajiya, yana dirowa agarin nan zan bada wannan shawarar sabida ki samu salamar zuciya, amma yanzu dai abasu masauki" "Ka koma gunku naji" Mik'ewa yae su kuma duk sunsha jinin jikinsu musamman wata uwar harara data bisu da ita kafin ta haura samanta ranta babu dad'i, koda batajin yarensu tana fahimtar dalilin fad'an su akansu ne, takula sam matar tunda ta dawo bata na'am da ita sam! Hankali ya tashi ainun wannan ya sanya a darare ta zauna a Cikin parlor zuciyarta babu dad'i tana tunanin wannan bak'ar rayuwar data wurgo kanta aciki. ************ Duk juyin sa d'aya da tunaninta yake kwana yake kuma tashi baya k'aunar abinda ze sanya yae nesa da Lawuri kome k'ank'antar sa, ya gagara sukuni yakuma rasa mecece ainahin damuwar sa da ita? Idan abinda yakeji a zuciyar sa game da ita shine so to tabbas kuwa so beyi masa adalci ba, mesa acikin dukkansu seshi kad'ai? Mesa zega jarabawa akan wannan *DOGUWAR HANYAR?*, be samu bacci ba se bayan asuba wannan ne ya sanya shi makara bayan nan, be farka ba se after 11, seda yae wanka da komai ya kimtsa sosai cikin kayan da Abu sufyan ya ciro masa sannan ya fito ya fito waje, ya takure ya taradda su acikin parlor susu kad'ai suna zare zaren ido, kai tsaye kusa da ita yaje ya zauna ya ajiye sandarsa dayake doddogara k'afa sannan da hannu ya tambayeta alamar lafiya? Murmushi ta k'ak'aro cikin yak'e ta girgiza sa masa kanta alamar ba komai, sam be yarda ba wannan ya sanya ya nuna bakinsa alamar cin abinci sunci kuwa? Amaimakon ta bashi amsa seta sadda kanta k'asa kurun, Barbo ya kalla ya tambayeta ta girgiza kanta alamar aa, cikin tsananin mamaki ya mik'e da sandar sa zuwa kitchen "Sannu Baba Ladi, me ake girka mana ne?" Ya tambayeta yana me sakar mata murmushi "Yauba wani abinda mukai se kunu da k'osai seko soyayyan dankalin hausa, zaka ci kona sauya maka zuwa wani abun?" Girgiza kanshi yae "Ina hanifer da cyma? Mesa ne yarancen basuci abinci ba?" Dafe baki Baba ladi tae "Toh nidai Hajiya ce tace dani tun safe karna girka dasu, shiyasanya kaga ban girka d'inba" B'ata fuska yae mesa mom take haka ne? Ta sauya da yawa d'an adam ai ba'a horonsa da yunwa fisabilillah, gaskia beji dad'i ba "Baba kozaki girka mana Indomie da k'wai dukanmu plss, kinga zaman da yunwa ba dad'i ko?" Jinjina kanta tae "Mezai hana kyautar Allah? Mintuna goma sha biyar zakaga na had'o na kawo da yardar Allah, ta furta bayan ta juya zuwa store, shid'inma gunsu ya koma ya zauna dukkaninsu suka k'urawa TV ido kowa da abinda yake sak'awa aranshi ko shakka babu seta nemi hanyar gida wannan shine abinda takeso tayi yanzu, shi kuma tunanin yanda ze rufe mata jikinta yake, sumar kanta ma duk a waje ba d'ankwali ba hijabi, dole ya kaita gun mace me hankali ta rik'a kimtsa masa ita. *********** Zaman office d'in baze masa inhar beji halin da Lawuri take ciki ba, ina ze iya wannan badak'alar ta tashin hankali, besan mesanya wuya ta zab'e saba hankalinsa kaf da nufsuwar sa baya tare dashi seya ganshi kusa da yarinyar nan, kodai tsafi sukai masa? Banda haka inashi Abu sufyan ina Lawuri? Yaje ina da ita? Zuciyar sa se azalzalar sa take akan ya tashi yaje gida ya ganta, ko shakka bayayi batada abokin hira shishi kad'ai ne ya iya yarenta da kurmanci, danshima bekosan yanda akai suke gane maganganun juna ba, takardunsa ya harhad'a ya fito daga office d'in, yana hurzo iska me zafi daga bakinsa, kai tsaye Airport ya soma nufa inda ze karb'o sak'on agogon hannunsu da aka k'ara yin sababbi kowa da kalar nasa, dama shi Baki yake using Abu Huraira ke amfani da fari, daganan gida ya wuce ya shiga ciki a sukwane, yanxun ma susu kad'ai ne a parlor d'in tarasa yanda zatayi da rayuwarta matar gidan ko k'ara sakata a ido basuyi ba, ga 'yan matan dake kula dasu ma ba kowa acikin su, ita bata gane kan gidanba tun zuwan matar cen da Dawood yace mata mahaifiyar suce. Sallama yae ta amsa masa sabida ta haddace da fara'a d'auke a fuskar sa ya k'arasa ciki, kallo d'aya ta masa ta gane shi cikin sakin fuska tace "Aboo shufyan sannu" murmushi yae "Lallai Lawuri an gwanan ce, irin wannan rik'e abubuwa haka ba wuya" kaman taji meyake cewa setayi murmushi, da hannu yamata alamar sunci abinci, gyad'a masa kanta tae alamar e, yana murmushi ya mik'e yake nuna mata yana xuwa. Wanka yae a sukwane ya kimtsa cikin kayansu na yamma, yana mamakin yanda Huraira baya gidan, yasan halinsa seyaje tile making company d'inan dukda yace dashi ya zauna shi zeje da kanshi tunda ya sani k'arfin hali kurin yake amma bashida lafiya. Sakkowa yae yazo ya zauna suna kallon atare, ya fahimci baya gane komai dan haka ya mayar musu tashar yarbawa lokaci d'aya yaga ta mayar da hankalin ta har tana murmushi idan akayi abun murmushin, kallonsa tae tanaso ta tambayeshi abu game da film d'in batasan ya zatayi ba, ga yunwa tun safe bata qara ci ba, kalma d'aya ta rik'e da ake yawan ambata "Baba ladi kawomun abinci" kallon sufyan tae tace "Aboo Shufyan Baba ladi kawonun abinshi" duk yanda yaso ya b'oye seda yae dariya me sauti "Lallai Lawuri anji garau, kirawo Baba ladi yaje yae ya dawo tare da ita, ya nuna Barbo da d'an yatsa yace "Barbo" ya k'ara nuna Lawurin yace "Lawuri" ya nuna kansa yace "Abu sufyan" sannan ya nuna Baba Ladi yace "Baba Ladi" murmushi tae sabida lokaci d'aya ta fahimci abinda yake nufi, k'ara nuna ta tae tace "Baba ladi" murmushi yae yana tafa mata alamar ta haddace, sannan ya zauna itama ta zauna bayan ya gayawa baba ladi ta kawo mata abincin, koda ta kawo shiya karb'a ya kalleta yana nuna abincin yace da hausa "Abinci" jinjina kai tae Ta maimaita kalmar abakinta, ya kuma tura plate d'in agabanta yana murmushi, gyara zamanta tae lokacin Barbo tabi Baba ladi kitchen kasancewar ta mata alama da hannu akan tazo, ta sanya hannu ta ebo shinkafar tana shirin kaiwa bakinda ya rik'e mata hannu da hannunsa na hagu, ya ebo abincin da spoon da aka kawo mata ta janyeshi gefe ya Furta "Bismillahi" kafin yakai bakinsa ya tauna, tare da sake mata hannunta, bata fahimce saba ta k'ara yunk'urin kai lomar bakinta ya rik'o hannun da sauri "Bismillahi" ya fad'a da k'arfi kad'an, nuna kanta tae da d'an yatsanta "Bishmillahi" sake mata hannun yae ta kai lomar bakinta murmushi ta msa sanda ta k'ara ebo wata lomar ta k'ara cewa "Bishmillahi" kafin taci murmushi yae ya nuna d'an yatsansa manuni yace "Bismillahi" bata gane ba dai sabida haka ya k'yaleta duk loma d'aya setayi Bismillah ya zauna yana zuba mata murmushi harta cinye tatas sannan ya tashi ya haura sama gun mom. ************ Wani kallo hanifer ta watsawa Lawuri cikin tsana, b'ata rai sosai tayi cikin baqin ciki, tamkar zata saka kuka ta soma yayyafa masifa tana nunata da d'an yatsa "Ke wace irin jakace wai? Jahilar inace kene ehhh? Mesa bakida hankali so nawa zan nuna miki yanda ake amfani da kayan toilet d'innan, kalli wani salon iskanci yanda kikai wasa da kashi, kashi a k'asa dan bala'i, wannan yarinyar nan ji nake tamkar in shaqe ki shegiya kowa ya huta" kuka wiwi Lawuri ta saka, koba komai a k'alla Hanfer zatayi 22yrs yayinda ita take teenage age nata sam sam bazata shallake 16 yrs ba inma tayi "Wuce muje wlhy sekin tattare kashin cen da tissue, dan bawai gyara shi zanba, er mutan jeji shegiya kawai" Bata fahimceta ba seda ta nuna mata hanyar toilet da hannunta, sumsum ta wuce tana sharar k'walla, Barbo ma tabi bayanta tana jan jiki, tissue ta ebo ta mik'a mata tace "Kwashe shi?" Bata fahimtar hausar ta sabida ha ta karb'a tayi mata tsuru da ido kurun, wata tissue ta yaga ta nannad'e hannunta da leda ta tsuguna ta kwashe d'an kad'an d'in kashin dayake gun ta hurga tissue d'in a WC na toilet d'in tana mejin qyanqyamun hannunta,sannan ta nuna mata ta duk'a ta kwashe, tsaye tsayi k'yam seda ta gurfanar da ita, ta juta tana yayyafa masifa akan lallai ta tabbatar ta kwashe shi itada baiwar ta ta barmusu tissue anan, haka ta fito tana yamutsa fuska, su kuma suka tsuguna Barbo tana cewa ta bari tayi amma bata bati ba, garin kwashe kashin duk suka bar layi layin kashi dasuke ja da tissue basu goge da kyau ba, kuma wurin wurga kashin a WC suka b'ata WC (water closet) d'in, seda suka wanke hannunsu sannan suka fito dama wanka zatayi da towel d'aure ajikinta tashiga da zmar tae flushing na waccen qazantar tae wanka, kurun taji warin yana tashi koda ta duba gaba d'aya basu wanke gun ba gashi farin tile ne, basu kuma goge da kyau ba hasalima garin goge war sun shafa hadda inda babu da, a fusace ta fito daga toilet d'in ta soma wankama Lawuri mari tana zage zage, fita tae da gudu tana hargowa yanda yarbawa keyi tana bada hak'uri Baiwarta ma se rarrashi take, amma ina se wanka mata mari take da duka tako ina, wannan yayi daidai da shigowar abu huraira, cikin tashin hankali yae kanta, da lafiyayyen mari "Hanifer kina haukane? Meta miki dazaki dinga dukanta, ko baiwar gidan kuce aka gaya miki?" Dafe kincinta tae cikeda mamaki take kallon sa, tazo iya wuya baqin ciki da kataici sun mata katutu, harta soma k'walla, murya na rawa tace "Yaa Huraira wasa fa tae mana da kashi a toilet" cikin qarajin dabata tab'a yayi ba yace "To sai me? Is that reason enough to beat her like this? Are u mad? Sekace bakida hankali?" Kalmomin sa sun mata ciwo ainun, dama yanada zafi sosai shi kam, hanifer ranta yayi zafi ita kanta, tunda take da Abu Huraira be tab'a kwatanta yi mata tsawa haka ba, ko duka, duk azababben son nan datake masa wanda harta kasa b'oyewa ya sani kuma tasni itama shi bata gabansa amma beta nuna mata qiyayya ba, kome take so yana mata, daidai da zance ma idan ta roqa zuwar mata yake, bata tab'a ganin fushin sa akanta ba, duk akan wannan banzar Lawurin? To akan me wlhy setayi sanadin barinta gidan har abada.... *Inshaa Allahu zan riqayin post biyu a rana, kuyi hakuri masoyana yanayin jikinne ke hanani sukuni.* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Book nawa na siyar wane idan kinsan bki biya ba karki karanta dan Allah, idan kika karanta baki biyaba kuma Allah yana kallonki, masu taya masu fitarwa yad'awa kuma kuji tsoron Allah, me buk'atar karantawa ya nemi wannan lambar 07084161619* 14 Hannu ya sanya ya tashi yarinyar tsaye duk jikinta rawa yakeyi tashiga rud'ani tunda take 'yar gatace ba'a tab'a dukan ta ba, ko yaya duka yake seta shiga tashin hankali, jiyake tamkar ya rungumeta k'irjinsa, dukda yake yasani k'aramar yarinya ce amma ya tabbatar ta wuce ya rungumeta matsayin sa na musulmi, tana rik'e a hannunsa ya haura saman sa da ita, a bakin kujrar parlorn su ya ajiyeta ya shiga ciki ya watso ruwa ya sanya qananun kaya ya dawo ya zauna kusa da ita, hannayensa duka biyu ya hard'e alamun rok'o akan tayi hak'uri, murmushi tae ta shiga nodding kanta alamun ya dena mana, Abu sufyan yafishi iya magana da ita dukda haka tanajin dad'in yanda shima yake kulawa da ita sosai, bata gajiya da kallon sa ko kad'an, yanda yake kafe ta da ido abun yana narkar da ita batasan metake jiba amma takan kasance cikin nutsuwa. Da hannu ya mata alama akan taje tae wanka, jinjina kanta tae cikeda tsoro, mik'ewa yae yana mejin zafin dukan da aka mata, kai tsaye d'akin su cya ya wuce, acen ya tarar tana zaune ta rafka uban tagumi kallo d'aya zaka mata kasan ranta a jagule yake, kusa da ita yaje ya zauna ya rik'o hannunta "Hanny am so sorry kinji" k'wallan datake ta rik'ewa ne ya silalo mata tace muryanta yana mata rawa "Yaa Mage nifa ba fushi nai ba" nutsuwarsa ya tattare a gunta "Meta miki hakan nan to?" Cikin sheshekar kuka tace "Yaa Huraira tunda sukazo gidannan nake wahala dasu akan komai ma, baka ganin yanda nake kulawa dasu shine yaran nan zasu mana wasa da kashi a bayi, naje da kaina na nuna musu yanda zasu gyara mana gun shine duk suka gama b'atawa, rainane fa ya b'aci kurun sena daketa shine fa kaikuma kazo ka dakeni" hannunsa yakai ya shafi gefen kumatunta, ga yatsunsa nan sun kwanta akan farar fuskar ta rad'au gun yayi ja sosai "Am so sorry pretty hanny, bazan qara ba, kuma zan kaisu gun horo kinsan ba yaranmu sukeji ba dole se hak'uri" batace masa komai ba yakuma cewa "Ki sanyo mayafi kizo muje ki rakani wani gun" batae musu ba ta d'akko yalolon mayafi dama wanka ta gama ta yane kanta dashi, har lokacin kuka takeyi, hannunsa ya sanya ya share mata hawayen nata "Haba k'anwata? Yanzu ni laifin daban sabayi ba dan nayi so d'aya seki dinga kuka anata zubamun fushi haka to kiyi hak'uri inshaa Allah bazan k'ara ba" Murmushi tayi tana hawayen "Yaa huraira nifa na dena ruwan idona ne ya gagara denawa" murmushi yae "To suma ki basu hak'uri zan siya miki New phone shikenan fushin ya k'are" murmushi tayi ta sanya hannunta ta share k'wallan duka "Laptop fa mukai magana dakai, ni wayana befi 4month inajin dad'in amfani dashi kurun ka siyan Laptop d'in" jinjina kanshi yae ."ba dakuwa zan siya shikenan?" Gyad'a masa kanta tae alamar eh "To bansan ganin kukan kinnnan, maza maza ki share wannan k'wallan" haka ta share suka fito seda ya janyo Lawuri da Barbo sannan suka bar gidan, mommy dai fushi take ta zama amaryar kulle a d'aki komai acen ake kai mata, dama zaman babban parlor bawai ya dameta bane ba bare yanzu dabatasn ganin fuskokin maguzawan cen..... ************* Shop na wata mata yaje dasu bayarbiya, bayan sun gaisa da turanci yake kora mata bayanin sa nason susan rayuwar cikin gari da yaruka biyu Hausa da Turanci, kallon sosai tae masa sannan tace "Ni shop nawa salon ne kawai kuma kaga hausan be wani rik'eni ba, amma akwai wata 'yar uwata dakejin hausa sosai, inaga cen zaka kaisu setana rik'a musu yarbanci ta fassara da Hausa, from dia seka kaisu sechool" Jinjina kansa yae alamar gamsuwa "Wane school za'a karb'su ai sunyi girma" shiru tad'anyi kafin tace "Ka nemi nursery school anty, ka roqeta tamusu na 6month with extra care, ana kammalawa ka kaiwa parimary 1 anty for 2 month haka haka dai, kafin ka kaisu na gaba" kallonsa hanifer tae cikin takaici tamkar zatayi kuka "Yaya wainikam yaran nan ba garin su zasu koma bane? Menene na cewa sesun iya hausa kuma ko wani turanci?" Wani kallo ya wurga mata daya sanya tasha jinin jikinta "Amm kozaki tayani yin mata magana da kanki, hausar ce damuwata ni yanzu ba turancin ba" jinjina kanta tae "Idan zaka dawo dani shop zan raka ka mana, sema muje yanzu" haka suka rankaya rayuwar hanifer ba dad'i ko kad'an, yayinda matar kewa Lawuri bayani da harshen Yarbanci akan abinda yakeso su iya da inda zasuje, takula yarukan sunada banbanci sedai ba cancan ba. ************** Kaman wani wawa haka yashigo gidan a sukwane, kai tsaye kuma d'akin su Hanifer ya wuce, Lawuri yakeso ya gani akwai inda yakeso suje yau,a hanya yaci karo da mom tafito daga d'akin kallon sosai ta masa fuskar ta ba yabo bakuma fallasa "Ina xakaje ne?" Ta tambaya, shida kanshi yau yasha jinin jikin sa da yanayin tambayar ta da kallonta harma da fuskarta "Gun Cya zanje mom" "Zakaje gun bamaguzar cen kai, yanzu Sufyan adalci kenan dakake ganin zakumun? Haka muka saba daku, kashigo gidan amaimakon kaje guna yanda kuka saba shine zaka zo neman wasu Arna" Jikinsa ne yae matuk'ar sanya ya matsa sosai kusa da ita ya d'aura kanshi saman kafad'arta ya rik'e hannunta d'aya "Kiyi hakuri bazan k'araba mom kinji" kawar da kanta tae gefe d'aya "Amma yaushe zakuwa Daddyn ku magana ya sanya soja su mayar dasu garinsu nifa sam hankalina be kwanta dasu ba" "Idan haka ze baki nutsuwa ki bari ya dawo zan mai magana a mayar dasu kinji mamana?" Murmushi tae "Naji kamaci abinci kuwa?" "Yanzu na dawo mom, Cya dama zance tazo ta dafan chips" Murmushi tae "Cyama bata nan hanifer ma haka, har baqinku ma sun fita da Huraira inji Baba ladi, kaje zan maka, with fried egg zakaci?" "Ea, nagode mom" ya furta had'e da sake ta ya juya zuwa part d'insu, zama yae ya zaro wayarsa ya danna wayar Hurairah ringing biyu ya d'auka "Twin ya akai?" Jingina jikinsa yae da kujerar dayake kai "Seka gudu baka nema na sam, narasa meke d'auken hankalin ka kwata kwata" murmushi yae "Kayi hakuri Twin, zanzo ma gida yanzu idan kana nan" shafar sumar kansa yae zuwa bayan k'eya "Ina gidan kazo da sauri" murmushi yae kurin ya ajiye wayar, tunanin Lawuri yana damunshi soyake tazo sui hira, dukda yaren kurame suke amma yafi buk'atar yin hira da ita fiye da kowa a duniya. *********** Dawood kam mahaifiyarshi ta gama k'ank'ame abunta a gida, ta tsorata sosai da Lamarin daya faru, yauma kamar kullum zaune yake yana cin abincin sa cikin nishad'i suna hira da mahaifiyarsa, kallon sosai ya mata yace "Momy yaran nan damukazo dasu aina gaya miki yaren mu d'aya ko? Banbancin kad'anne kawai" murmushi tae "Yarena dai, kokabar hausan na Baban ka kuma?" Cikin raha yace "Auu hakane yarenki mom sorry, ni inaso su shiga hasken musulunci wlhy, gashi narigada na had'a alk'awarin aure da Cyama dabadan hakan ba daba abinda ze hanani aurarta in musuluntar da ita" kallon mamaki tae masa "Amma wasa kake ko? Ina haukane dazan barka ka auri er jeji, beside kai waye dazaka b'ata mu'amalan gidan nan dana gidan General? Cyama duk halaccin datama?" Sadda kanshi yae a k'asa cikin damuwa "Mom nifa bance haka bafa, nace daze yiyu kawai ko?" Harara ta wurga masa "To baze yiyu ba kaji na gayan maka, har abada wlhy, kamazo da salon raini" bece komai yasan halin mom, akan Cyama seya nemi d'aga masa hankalinsa gwara yae shiru kurun. ************ Yau tun 12:noon ya tashi daga office, beko lek'a ofishin Cyama ba ya wuce kanshi tsaye gidansu, yasan yanzu har mom tana gun aiki bakowa agidan nasu, A parlor gidan ya zauna sunata kwasar hira shida Lawuri, taji dad'in ganinsa har take masa bayanin Abu Huraira ya kaita wurin koyon hausa, kuma tana ganewa sosai ba kad'an ba, dan yanzu hartasan gaisuwa ma da wasu abubuwan yaren ba wahala sedai rubutu ne bata iyaba ko kad'an, anan take gaya mai rayuwar su akwai dad'i ba'a wahala kaman su, itafa noma take dukda zamanta 'yar sarki amma anan bataga gona bama, to ina suke samo abinci da nama, tunda bataga suna fita farauta ba" Dariya sosai yae har yana rik'e ciki, nan take ya mata bayanin komai dangane da rayuwar birni an dad'e sosai da barin wannan yamayi mamaki da ace duk wayewa bata kai musu ba har yanzu, aranshi yace watak'il hakan baya rasa nasaba da tsafin su waze iya zuwa garin... Sunsha hira sosai se raha suke Da sallama Cyama ta shigo gidan tayi mamakin ganin Dawood da Lawuri a parlor suna hira da dariya haka har basusan da zuwan taba, matsawa tae kusa dasu tace "D inata sallama fa" yanayin zaburar dayae kurun ya isa ya nuna mata cewan tabbas bashida gaskia, tasha mamakin wannan abin lokaci d'aya ya soma kallon agogon hannunsa, agogon dake manne a bangon parlor ta kalla cikin mamaki itama k'arfe biyu ta kwata ta mayar da dubanta zuwa gareshi "D lafiya dai? Ko bakai tsammanin ganina yanzu bane ba" wayancewa yae "Damafa ke nake jira, nayi mamakin yanda lokaci yae saurin gudu ne har haka" Rausayar da kanta tae "Amma shine kuma bakaje guna ba office, bayan secretary naka ya sanar dani tun 12:noon kabar office" sosa kanshi yae "Gida nakeso na ganki shisa nazo, aikin jaridancin zaki faramun ko?" Shiru tae ta harari Lawuri,taga alamar yarinyar nan seta mata saiti tukunna, D betab'a zuwa office beshiga sun gaisaba, shisa ma idan taga ya wuce time daya saba zuwa be zoba takan je da kanta dukda babu tsarin hakan akanta "Sannu de zuwa anty Cya" harararta tae "Yauwa sannu Laure" ta fad'a dan wancen sunan sun soma dena ambatar sa baso suke ba" Mik'ewa yae "Zanje nae sallah time ya tafi" da mamaki ta kalleshi "Auu sallan azahar ne kuma D bakai ba ka zauna wannan arniyar tana maka tatsuniyar gizo, har biyu ta gota" B'ata fuska yae sosai "Meye haka Cyama? Yaya zaki kalli mutum agabansa kice dashi arne? Daidaine hakan kike gani?" "To k'arya nai ita ba arniyar bace? Ko tana sallan ne? Idan da tanayi aida bazata zaunar dakai ba ayi sallah tun fin awa kana zaune" Shiru yae ya tsaya yana kallonta hartaja tsaki tae sama cikin fushi, girgiza kanshi yae yace da Lawuri zeje masallaci, itama saman ta haura gun Cyama, har k'asa ta tsuguna cikin fuskan tausayi tace "Anty Hakuri" Batako kalleta ba, wani azababben kishi takeji game da yarinyar ance bayarbiya ce yada kyau haka? Sewani haske take k'arayi, ko shakka babu seta rabata da gidansu da rayuwarsu gaba d'aya, take taken Dawood nuna mata yake cewan son yarinyar yake tun kwanakin baya ta kula da hakan, ta tsani yarinyar, tunda take dashi yace rana ta farko dayaje office harya fita be nemesu ba, a k'ark'ashin company d'in dad yake aiki yanxu itama kuma acen take. Da hannu ta mata alama akan ta tashi ta bata wuri haka ta mik'e jiki ba k'wari, ko shakka batayi tasan fad'a sukeyi kuma akanta ne, tarasa wannan mugun bak'in jinin dake bibiyar ta, tanason tasan ma'anar kalmar Arniya! So tari idan ana magana da fad'a akanta takanji ana yawan ambatarta da wannan kalmar, me wannan kalmar take nufi? Dama yau zataje gun d'aukar karatu da yamma seta tambayi Anty Risi akan hakan...... *Se mun had'u a shafin yamma inshaa Allah* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: 🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *please book nawa na siyarwa ne, idan kinaso ki karanta ki biya kud'in ki a sakaki a group, 07084161619* 15 K'uru zirga zirga yakeyi cikin tsananin tashin hankali, duk tsafin daya dace ya sanya ayi ya saka anyi amma har yanzun Lawurin sa bata dawo gida ba, anje garin kusa dasu ma amma shiru kakeji, tunda yae sa'a wani acikin bayinsa ya tsallaka ruwa ya samu sacrifice yake cikin murna sedai tashin hankalin rashin Lawuri, dole seya nemota amma besan akwai wata duniya ba bayan tasu data mutanen dake tsallako ruwa suzo, mutanen daya gani da wannan abun kashe mutum abun ya tsorata shi, ga K'uruwa ma ta dena cin abinci kullum zancen kenan Lawuri. "So nakeyi aje nemanta har waccen duniyar dabansan ya ake zuwa ba, ina buk'atar yarinyar nan ta dawo ko anaso ko ba'aso" Kallonsa Barden garin yar "Zamuje mu nemota, koda xamu mutu ne K'uru sarkin adalci ka kwanta kayi bacci dole zata dawo" haka suka shirya sunkai su 20 aka soma nausar jeji. ************* Rik'e take da book a hannunta ta k'urawa rubutun ido kurun amma sam bata gane komai, bazata iya rubutu ba ko karatu tasani har abada amma hausar dai tanaso ta koya, so take ta iya yaren Aboo Wurairai (In Lawuri's voice), ta rik'ayin hira dashi kafin ta koma garin su, kife littafin tae ta mik'e zuwa cikin gidan sabida tanaso tasha ruwa, zuwa yanzu tasoma sabawa da d'and'anon ruwansu me sanyaya zuciya, kai tsaye ciki tashiga bayan tayi sallama ba kowa a parlor d'in, kitchen ta wuce ta bud'a fridge ta d'akko robar ruwa d'aya ta shiga dudduba kofi, sedaga cen ta samu tana fitowa sukai karo da Hanifer cup d'in ya sub'uce mata dama na glass ne lokaci d'aya ya tarwatse, cikin tsoro taja da baya bata tab'a tsammanin abun yana tarwatsewa har haka ba "Hanty Anny hakuri kinji?" Ta furta muryanta yana rawa, tsaki hanifer tae "Dama mana Arniyar jeji, yaya zaki yi abu cikin nutsuwa wama ya baki damar d'akko cup na daddy kizo harki fasa? Wlhy yau keda mommy ne, zuwa zan na fad'a mata abinda kikayi idan akwai wanda kika tab'a ganin ya d'akko cup d'in daddy yana amfani dashi" ta gano masifar takeyi dukda bajin me takecewa duka take ba,jin ta ambaci momy ma ya k'ara firgitar da ita tasani kashinta ya bushe, kuka ta hauyi tana rok'onta amma da gudu ta juya saman, segata sun dawo tare da mom har lokacin kuwa Lawuri tana nan tsaye tana sharar k'walla, salati mom ta hauyi tana tafa hannu "Hanifer d'akkomun dorinan danake zane su Nu'aiym shida Khabbab kizo ki sameni a garden tare da ita zakizo" haka Ta wuce garden Hanifer kuwa ta wuce saman ta d'akko dorina ta kuma zo taja hannun Lawuri garin tsallakawa qatoton glass ya cake ta, k'ara ta kwalla yayinda hanifer ta tizgeta zuwa garden d'in cikeda fushi, d'ingishi ta somayi tana kuka amma ko kallonta hanifer batayi ba taci gaba da janta har garden, mom zama tae akan kujera hanifer ma haka "Hanifer tashi ki nuna mata yanda zatayi kneeldown" mik'ewa tae tayi kneel down agabanta tana nuna mata da hannu akan itama tayi, ba musu tayi harda d'age hannayenta sama yanda hanny tae, tana ganin tayi ta mike itama ta mik'e wanka mata mari hanny tae "Danla ki koma wayace ki mik'e?" Bata gane abinda take nufi ba ga glass a qafanta se kuka take tana ambatar kalmar ki Akuri da k'yar, duka sosai mom ta mata da dorina ta kira Dawood a waya "Ga wannan mejin yarbancin Arniyar yarinyar dakuka kawomun agida na, ka sanar mata glass cup data d'auka tasha ruwa harta fasa na daddy ne nxt time idan taga abu ta rink'a bincikawa danni ba lamuni zan mata ba" tana kaiwa nan ta kara wayar a kunnen Lawuri daga cen yayi Lawurin bayani akan shine ga abinda akace tayi ta rik'a kiyaye, tana kuka ta ansashi da ta dena zata nasu hak'uri amma a mayar da ita garin su "Zamuyi magana idan nazo Lawuri kinji, yanzu kiyi hak'uri" godiya ta masa sannan suka karb'i wayar dukai hanyar ciki ita duka barta nan "Allah Hanifer banajin dad'in yanda nakewa yarinyar nan, kurun dai na tsane ta ne so nake wuya tasa tabar gidan ba komai ba" jinjina kai hanifer tae "To mom harga Allah aibaki da laifi, tunda laifi tae kika hukuntata" Jinjina kai mom tae alamar gamsu kafin tace "Amma naga kaman Glass yashiga k'afanta kidubata da kanki" Jinjina kai Hanifer tae "To mom zan duba ta inshaa Allah" Barbo ce ta tattare kwalban ita kuwa hanifer tunda ta shiga hidimar girkin daza'aci na dare bata k'ara tunawa da wata Lawuri ba... ************** Tunda ta sanya kiran wayansa agaba be d'aga ba take cikin yamutsi, ta cab'a ado iya ado sedai babu walwalar zuci, mesa ne ita Pure heart yake mata haka? Meta masa ina laifin masoyinka? Shirin zuwa gun k'awarta tafito da amma se kurun ta karkata akalar motarta zuwa Tile making company nasu ta tabbatar yana cen yanzu. Kai tsaye office nashi ta nufa, akai mata iso ta shiga, fuskar nan babu walwala ya tarbeta "Me kika zo kimun anan?" Kallon sa tae har idanta sun sauya sunyi ja "Meye laifi na sufyan? Mena maka hakane wai? Na dinga kiranka kenan a waya baka d'agawa? Sannan kuma baka kirana, baka zuwa inda nake ni idan nazo seya zama laifi? Yaya kakeso nayi da rayuwata ne wai?" Hannunshi ya ssanya ya shafi sumar kansa "Na sanar dake ai banaso kike yawaita kirana a waya ko? Nakuma sanar dake ba girmanki bane ba ace kina kawomun ziyara da kanki" cikin damuwa ta furta "Amma idan nakira baka d'auka bafa? Kokuma idan na kira baka kirani back ba fa? Idan inaso na ganka amma bakazo bafa ya zanyi ehm Abu sufyan?" Ta k'arashe maganar cikin tausayawa kanta har tana zubar da hawaye, tausayi sosai ta bashi ya tashi daga kan kujerar da take yazo ya zauna kujerar dake fuskantar nata, cikin sanyin murya yace "Kiyi hakuri my Ayusher kinji? Ni abunda banaso missd col ya wuce 1, idan da kin kira so d'aya ban d'aukaba idan kika jirani zan kiraki back ne, zancen ziyara kuma naji, yanzu so nawa kikeso ki ganni a sati?" Share hawayen ta tae "Nagode sosai pure heart ni idan da wannan kalaman masu dad'i kurin ka barni zan gode maka" Murmushi yae "Gayamun mana so nawa kikeso ki ganni a sati?" "Niko sa d'aya ne ma kaji" murmushi yae "Nacire kwana uku kacal a sati, zaki ganni so 4, inshaa Allah muddin ina garin nan, kira waya kuma zanna riqa kiranki kullum safe da dare wannan fa ta miki?" Ya k'arashe maganar cikin sakin fuska sosai "Nagode pure heart" murmushi yae "Da driver kikazo?" "Da kaina nazo" mik'ewa yae "Muje gidan mom nayi wanka semuje yawon yamma" murmushi tae itama ta mik'e "Zaka sanya mom tace bana zuwar mata se idan kai ka kawoni ko" mirmushi yae "Idan bazakiba sena tafi abuna" Rike baki tai tana murmushi "Nina isa nace bazani ba? Aiban isaba ko pure heart?" Murmushi yae suka fita. Aqilu ya wurgawa key na motar Ayusher ya cafe yace "Ka kai motar gidan Su Ayusher ka baiwa gate man na gidan kace injita ya ajiye agunsa harta dawo" cikin girmamawa yace "To yallab'ai" Takardar dubu d'aya ya zaro ya mik'a masa "Kayi tranport zuwa gida daga nan" nanma godiya yae ya juya. ********** A b'angaren Lawuri kuwa yau duk kuka ta wuni yi, ta samu Barbo ta cire mata glass d'in amma sun duba a garden d'in babu wani ganye daze iya tsayar da jinin da k'afar keyi,wajen gidan Barbo taje ta duba ko akwai ganyaye irin na garinsu....... Zaman dirshan tae a bakin gate d'in tana jiran isowar Barbo sabida yanda jinin ke zuba, ga yau banda masu gadin gidan duka sojojin sun kama gabansu,Shigowar barbo yayi daidai da dosowar motar Abu sufyan gidan, parking yae ya fito daga motar ya bita da kallon mamaki kafin ya k'ara wurinta cikin azama, durqusawa yae ya tallafi k'afar ba laifi tasha faso da kirci na rayuwar jeji "Meya samu k'afar haka ne?" Amaimakon ta bashi ansa se kurun ta shiga rera masa kuka wiwi..... Nuni ya mata da hannu alamun ta mik'e a hankali ta tashi ta doma d'ingisawa tabi bayanshi zuwa ciki, Hanifer ya soma k'wallawa kira yama manta da wata Ayusher dasuka zo tare, da sauri ta sakko daga saman "Zoki treating wound na yarinyar nan, bansan meya same taba" tab'e baki tae "Yaa sufyan kofin dad ta d'akko na shan ruwa, shine kuma ta fasa shi garin gidadanci ta taka glass nisam nama manta mom tace na duba mata gun" Haukace mata yae da masifa, ita kuwa Ayusher tayi sororo tana jiyo su, haka ya dinga masifa har sanda ta shiga taitayinta, ya haura saman mom itama "Mom yanzu daidai ne dan Allah, yarin yarnan fa mom mutum ce fa? Amma ace kun barta da miki haka tun safe kuma akan glass cup ace hadda duka, Hanny ta gayamun kin dake ta kuma nima na gani duk jikinta ya fashe" Mik'e wa tae daga zaman datake "To ubana seka daken ai, nace seka daken, ni yanzu Sufyan ni kakewa magana irin haka acen wancen banzar, yaushe ta juyar mun da kanka har haka? Yaushe ma kai ka isa ka gayamun abinda ya dace ya wanda be dace ba?" Saukar da kanshi yae k'asa "Mom kiyi hakuri kurun naga an qyale tane acikin jini tun safe shiyasa" tsaki taja tafice daga d'akin gaba daya. Seda aka bata anti tetanus sannan akae dressing na gun se kuka take, lokacin ne barbo ta tallafeta zuwa d'akin su. Sun baiwa Ayusher tausayi sosai bako na wasa ba, bataso taga ana cutar da mutane ita kam,amma haka ta gaisa da mutane gidan ta zauna a darare har ya kimtsa suka fita, fitar ba dadi sabida fuskar babu wata walwala haka suka yishi. ********* Ana sallan isha Lawuri da Barbo suka sakko daga saman, sa'an dasukaci ba kowa ya basu daman zarcewa har gate, me gadin sun sansu dan haka babu wanda ya hanasu fita haka suka fice da zummar suda gidan har abada, Lawuri gida takeso taje dan haka ta nemi hanyar datafi mata sauk'i kawai, ta kula wannan mutanen kasheta zasuyi idan tayi wasa..... Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na siyarwane, idan kinaso ki siya, karki karanta idan baki biyaba 07084161619* 16 Tunda suka fito duk titin dazasu tsallaka sesunji jiki, sunsha bak'ar wahala kafin subar unguwar ma, tafiya dukayi ta kusan sa'o'i uku, sun jigata sosai, ga ciwon dake k'afar Lawuri, yanxu kam so suke su tsallaka babban titi sui ta kansu amma sunfi 30mns agun suna k'ok'arin tsallakar titin sedai kuma basu iyaba, sesunkai tsakiyar titin se kuma su dawo da gudun fanfalak'i, a garin hakan ne mota ta musu d'ebar karan mahaukaciya taje ta watsar gefen titi, matashiyar budurwa ma mallakiyar motar tayi azamab fitowa da saurinta bayan tayi parking inda ya dace tayi, Takalminta me d'an uban tudu tana tafiya cikeda yanga, bazaka ita cewa ga kalar taba ka kad'e mutane har biyu kuma kana tafiyar son rai? Sedai kumafa kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tashiga tashin hankali, a rud'e take sosai, ga alama iyakar saurin ta kenan a yanayin tafiyar ta, mutamen dabasu suka kad'e sunba har sun rigata isa gunsu, itama cikin azama ta k'arasa yanxu kam, abinda ta gani ya matuk'ar rikitar da ita sabida d'ayar gabaki d'aya fuskarta jinine ga k'afa ma haka she's unconscious ma, d'ayar ce ke ihu tana magana cikin yaren daba kowa ke ganewa ba, dafe goshi tae lokaci d'aya wani ya taimaka mata aka sanya daya a motarsa daya a motar ta duka lula asibiti mafi kusa dasu. Lawuri tafi Barbo shan azaban dan ita batako san wake kanta ba, Barbo kuwa ta k'arye a k'afa, ita Lawuri ba'a san iyakan ciwukan datajiba har yanzu, matashiyar budurwar data kad'esu se kuka take tana mamakin sanda sukazo gabanta batai auneba, kamar aljanu? Gidansu ta kira waya lokaci d'aya asibitin ta cika fam da mutanen gidansu. *********** Hanifer ta kula yaran basa d'akin su da dare amma tana mamakin ina sukaje? Taso ta ankarar da mutan gidan amma setayi tunanin suna garden, tunda k'auyawane ko tsakiyar dare saje garden ai, wannan ya sanya tana kammala ayyukanta tae shirin kwanciya, tana sakaran ta koma gidansu ma nanda 2days.......Cyama ma tayi mamakin rashin ganinsu amma hakan be sanya ta wani damuba dan itama tunani d'aya tae suna garden suna hira cox haka sukeyi dukda basu saba kai dare ba, da wannan ta watsar da tunaninsu tae shirin kwanciya abunta kamar yadda Hanny tae. *********** Duk mutan gidan sun hallara dining kasancewar General ya dawo, k'a'idane idan yana gari ko bakaso se dole ka fito cin abincin safe a dining dake babban parlor na gidan, sun shirya sosai abinci kala kala, ita kamma mom bata ko damu da rashin suba tama manta dasu, seda aka nutsu ana cin abincin kowa yayi tsit sannan General ya kalli Adama "Ina bak'in gidan ne ko kunya suke?" D'ago idanta tae ta kalleshi had'e da tab'e baki "Oho, ni yau duk ban gansu ba" Cyama ce tace "Dad jiya da dare ma basu zo d'aki da wuri ba, nazata ko suna garden sabida cenne gun zamansu shisa banyi magana ba har bacci ya kwasheni, yanzu mun wayi gari basa d'akin na tambayi hanifer ma tace bata gansu ba" Duka ya kaiwa table d'in da k'arfi "What?!!!! Kuna haukane shine bazaku sanar da wuri ba? Bama wannan ba da ban tambaya da bazaku sanar ba kenan" tsoro ya kama su Hanny tace "Dad na gayawa mom tinda na idar da sallan asuba, setace badai inda zasu waiko a garden suka kwana tunda sun saba kwanan jeji" Wani kallo ya wurgawa adama daya sanya ta sadda kanta k'asa ba shiri sannan ya kalli twins "Kai Huraira jeka ka duba mun lungu da sak'o na gidan ina yaran mutane suka shiga" A tare suka mik'e da sufyan dukkaninsu cikin tashin hankali mara misaltuwa, neman duniya sunyi agidan basu gansu ba, sedaga baya suka tambayi securities na gidan anan sukejin wai tun jiya da kusan isha suka fita babu kuma wanda yaga dawowar su gidan, hankalinsu ya tashi suka koma ciki suka sanar, mom dai ko gezau su hanny ma ganin dad a wani yanayin duk se ya rikitar dasu suka shiga taitayin su "Mesa nida gidana bazan kawo ajiyar abinda nake so a kular dashi ba? Shisa Captain yace zeje dasu gun matarsa bayarbiya na hana, yanzu a matsayin ki na uwa me kenan kikai? Kin burge kenan? Kin cinye kike gani? Yaran mutane dasuka fice dalilin masifar wlhy tlahi na baki awa ashirin da hud'u duk inda sukaje ki nemosu inba hakaba kinsan sauran" Mik'ewa tae cikin b'acin rai "Haba Muhammad, se yaushe zan girma ne a wurinka wai? Nina koresu? Koni nace su bar gidan? Banko san sun tafi tayaya zan nemosu? Idan har kace akan yaran nan zaka mun haka wlhy sena bar maka gidan, kaida ka kawosu sekaje cen ka nemesu danni babu ruwana" Kallonta yae cikin b'acin rai "Yanzu dama kafin na fita nakeso na duba CCTV nawa, an sanar mun har dukanta kikae a dining, suma securities sesunsha wuya a hannuna, yanda zasu bari su fita ba tare da sanin kowa ba, dan sunga shamsu baya nan" Juyawa tae rai a b'ace ta haura sama tana mejin zafin abinda ya mata agaban yara. *********** Lawuri unconcious take har washe garin, anma rasa gane meke damunta, dole yanzu ct scan za'a mata tunda yake ta samu rauni aka.... Yarinyar data kad'esu duk a rikice take tarasa nutsuwarta dukda kasancewar ta likita hakan be hanata shiga tsananin rud'u ba, musamman ganin wannan kamar zata mutu ma. Neman duniya anyiwa su Lawuri ba labarin su, Abu sufyan daren ranar bekoyi baccin kirki ba, yayinda Abu Huraira ya gagarayin baccin ma kwata kwata, hankalinsa ya tashi sabida yasani tabbas hanyar gidansu zata nema kuma bawai tasan hanyar bane ba, sedai ya kula tanada basira tabbas inda suka biyo tanan zata nemi komawa, sedai ta yaya? Tunda yake jirgi suka hau daga babban garin dasuka sauka zuwa nan garin Abuja, yashiga rud'ani sosai ya rasa tudun dafawa hankalinsa in yayi dubu to tabbas a tashe yake kuwa. ************ Banida zab'in daya fi in koma garin su Lawuri, banida zab'in dayafi inje garin nasu in binciketa inji kota gane hanya tazo, ai taji ana anbatar sunan garin dasuka hau jirgi sukazo wato OGUN state in hakane mota zata hau, taje cen sekuma ta nemi hawa wannan motar dasuka hau suka tafi wannan k'auyen na fulani, duk yanda akayi gida zataje amma bari ya bada sati d'aya idan ba'a samu labarin suba dole yaje garin koyaya ne kuwa!!!. *****Bayan sati d'aya* Har akayi sati d'aya babu neman dabasu musuba amma shiru kakeji, bame hotonsu bare su saka a media, general yayi bk'in cikin wannan abun, yanaso yarinyar ta karb'i musulunci yana so ya nuna mata cikar musulunci abun arziqi amma anzo an tilastata guduwa tabar gida sabida wani ra'ayin banza, damuwar sa d'aya ma besan hannun dazasu fad'a ba, nagari ko mugu?, yama rasa tudun dafawa! ********* Hankalin Twins baya jikinsu, Abu Hurairah be fahimci tsananin so da illar dason ya masa ba se yanzu, hankalinsa ya matuk'ar tashi ainun, har 'yar rama, wannan wace irin masifa ce wai? Yana cikin dubun tashin hankali akan wannan abun, sabida ya shirya sosai akan yanda ze shawo kan iyayensa ya musuluntar da ita ya aureta, amma shine za'a wani ce ta gudu? Lallai wajibine ya koma wannan *Doguwar hanyar* yasan abunyi akan Lawuri idan ma batacen duk inda tashiga aduniya seya nemota yaga cewar sun sake had'uwa itace farin cikin sa, itace komai na rayuwar sa yakeji dai........ A b'angaren Abu sufyan kuwa shisam bama shida lafiya, wani ciwo ne ya sameshi me wuyar magani, ya tabbatar rashin ganin Lawuri a rayuwarsa abu ne me shirin kasheshi har abada ba shiri, mesa yarinyar nan ta masa katutu a zuci ne wai? Meke damunsa game da ita? Ne kodai haukacewa yake shirin yine be shirya hakan ba? Duk iyakar tunaninsa ya rasa abinyi. Dawood yaji zafin wannan abin sosai Sedai shi bekaisu damuwa ba kasancewar ba wani d'ad'ashi da k'asa tayi ba, shidai kawai yana mata kwad'ayin musulunci ne, bayaga haka kuma yaso ya aureta ya sanyata a rigar musuluncin gaba daya, abu mafi damunsa shine besan hannun dazasu fad'a ba, sun shigo garine kurin batare dasun san waye mutanen birnin ba? Yana musu fatan alheri. ********* Duk wani shiri daya kamata huraira yae yayi abunshi na zuwa garin su Lawuri, babu wanda ya gayawa, se Sufyan daya kula tamkar da abinda yake b'oye masa yamasa shiru ne kurin yaga iya gudun ruwan sa. Ranar da ya fita aiki kuwa bekoma waiwayen gida ba ya Lula *Doguwar Hanya* wacce besan wane tanadi tae masa ba yanzu.......... Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Assalamu Alaikum masoya, litattafai namu masu suna kamar haka na kud'ine.* *Sultan merah* *Kamar da wasa* *Doguwar Hanya* *Zafin rana* *Sanadiyya* *muna roqon duk wani me tsoron Allah da idan be biyaba karya karanta mana book koda marasa tsoron Allah sun fitar kuwa, yin hakan ganganci dan gashi munyi bayanin kanmu, idan kayi hakan kaida Allah mahalicci, munyi garab'asa gaduk meson duka biyar ya biya N500 kacal,meson 1 N200 kacal, me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300* ******** 17 Abu Hurairah bebi ta k'auyen su Baba ladi ba, ya kula hanyace me rikitar wa mara b'ullewa, jejin tamkar aljanaine aciki, da wannan ya samu isa OGUN STATE da yamma sakaliya, yayiwa wayoyinsa kisan gilla dan karma wani ya sameshi, shidai burinsa d'ayane shine ya samu Lawuri, rashin ganin babban tashin hankali ne agaresa, koda yake b'angarora da dama na zuciyar sa suna sanar masa tsabagen wowtar da yae na tunanin komawa wannan masifar, har wata zuciyar sa tana sanar masa tunda harshi ya kawo kansa tokuwa tabbas babu abinda ze sanya idan yae adu'a Allah ya amsa masa, sedai kuma a wani b'angarn yanaji ajikinsa cewar tabbas Allah ze nuna masa hanyar b'ullewa, dan kuwa bayaga soyayyar data janyoshi akwai kwad'ayin ya janyo musulunci a garin, abu d'ayane yamai tsaye arayuwar shi shine yarensu da bayaji? Yaya zeyi huld'a dasu, yaya zeyi communicating dasu? Ta ina ma ze fara? Daga wane b'angaren ze soma ? ....... ********** Ayusher yarinyace me matuk'ar tausayi tunda abin nan ya faru da yarinyar nan kullum setayi kuka ga yarinya a ICU dukta fita hayyacinta gashi batasan ina zataga iyayenta ba batasan inda ya dace ta dosa ba gun nemansu, kodai zasu d'auki hoton tane sukai sanarwa gidan tv da kuma sauran media flatform taga ko za'a dace? Da wannan shawarar yau ta kira Sufyan, yana d'agawa suka gaisa yace "Ayusher tunda kikai accident d'in nan ko nemana bakyayi duk kin nemi d'aga hankalinki a banza" murmushi tayi sannan tace "Kayi bak'uri nutsuwarce tamun k'aranci wlhy ina cikin tsananin damuwar rashin sanin iyayen wanda na kad'e" Nisawa yae "Haba Ayusher kema dai kunyi sakaci mezai hana kanki tsaye mana ki kai agidan tv na dad d'inku, a duk fad'in abuja wane gidan TV ne yafishi suna? Zakiga an dace ai" Nisawa tae "Shawara dana yanke kenan amma nace sena kira pure heart, barin gayawa mom kawai, yanxu kana ina" Nisawa yae "Ina OGUN STATE fa" wara ido tayi "Yinme pure heart?" Murmushi yae "Zan gaya miki daga baya kinji yanzu dai kiyi yanda nace d'in" sallama sukai sannan yaci gaba da tuk'insa. ********** Tsoro ya baiwa Abu hurairah sanda ya ganshi akan kwanar da ake d'aukewa aje wannan k'auyen na fulani, bashida dabarar dayafi ya gangara ya tsaya danya tabbatar yanda ya ganshi shima ya ganshi ido cikin ido, fitowa yae dama shi a tsaye suka kalli juna ido cikin ido, a hankali ya tako yazo ha rik'e hannun d'an uwansa cikin sanyin jiki yace "Al-hussain" amma seya gagara furta komai bayaga wannan kalmar, har wannan lokacin idonsu yana cikin na juna, Abu Hurairah yau duk dauriyarsa seda yae kuka besan sanda ya rungume d'an uwan saba yace cikin muryan kuka "Wlhy ina santa Al-hussain, rashin ta baze barni acikin sukuni ba, soyayyar ta tagama zagaye ilahirin jikina, dan Allah karkace zaka hanani zuwa nemanta kaji" murmushin takaici yae ya kula da wannan tunba yanzu ba shisa ya k'udirta a ransa koda soyayyar yarinyar zata hallakar dashi toze sadaukar da rayuwarshi akan d'an uwansa yaji dad'i, dukda shima yana shan wahala amma yasani beyi sabo da ita yansa za'ace baze iya barwa d'an uwansa ita ba "Nasani Al-hassan amma wannan baze barni in barka kabar wannan duniyar tamu zuwa wata duniyar ba me cikeda abun tsoro kala kala gakuma doguwar hanya me rikitarwa, iya kar wacce mukasha ta wadatar Al-hassan, sabida haka zuwa zakayi mu koma Abuja, idan nemanta kakeso aje semuje da soja yanda Dad amma kafito bakako nemi adu'ar iyaye ba ka ganta yaya? Ka gane ta aya? Shin kanada tabbacin taje garin nasu ne, karka manta Lawuri fa ko nan garin bata san sunan saba, kai koda ta sani ma tayaya zata zo nan? Ya zata iso har nan garin? Kay8 tunani mana, kokai aka bari kazonan da k'afa ta ina zaka fara? Karfa ka bari soyayya ta rufe maka ido, tasha makance ka daga ganin gaskia me amfaninka, ka nutsu kayi adu'a ka kuma nemeta a garin abuja da kewaye amma sam bata wannan Doguwar hanyar ba, nasan kalar tunaninka wannan ne ya sanya na biyoka tanan hanyar, agarin na kwana senawa nan hanyar sakkon asubahi, ina me fatar ganin ka dikda na kula sam ka manta da tracker dake jikin motarka dakuma agogon hannunka daka iya sanya nasan location naka aduk inda kake, hotel d'inma ban nem bane dana iso sabida gajiya" Nisawa Abu huraira yae "To yanzu Al-Hussain kana ganin zamu sameta a gari?" Murmushi yae "Nama alk'arin zanyi amfani da ilimina da basirata dakuma k'arfin ikon danake dashi wurin ganin na nemota, idan har kaga ban nemotaba Allah ya yanke had'uwa tsakaninmu da ita ne na har abada" Sauke nannauyan ajiyan zuciya yae "Yanzu gida zamu koma?" Murmushi Sufyan yae "Da jirgi ba,dama na mana booking akwai wani inyamuri abokina ne, ana garin yake zamu bar masa motocin nan, zanje inji nawa zamu bashi ya kawo mana su abuja" "Baka gudun ya gudu dasu?" Murmushi yae "Daze gudu dasu da bazan bashiba ai, yanada motocin jigila ne yana jarkar mota kuma ya siya ya aikama duk garin da kake, yanada qwararrun direbobi zasu kai mana ne mu biyasu" murmushi shima yae "Kasanni da mota subi a hankali ko gogewa tae bazan k'ara hawanta ba ka sani" Girgiza kai Abu sufyan yae Zaka rantse da Allah huraira me sauk'in kai ne amma komai nashi na gayu ne se high taste yafi kula da mota akan jikin sama, Abu huraira ze iya maka komai amma banda aron mota sam shi ko wankin mota yakai seya kasa ya tsare, tsaftar sa kuwa har takaici take baiwa sufyan wani zubin dukda shima ba baya bane gun tsaftar. ********* Abun sam bewa mahaifiyar su dad'i ba tun faruwar abun take cikin fushi da general, shikuwa yayi biris da ita har gashi yau kwana 8,abin mamaki Kyautar Allah duk basu kwana a gidaba, to ina sukaje? Hakan ba sabon su bane ba, me sukayi hakan kenan? Ina sukaje? Yanzu k'arfe d'aya na rana? .....sallamar sune ya katse mata tunaninta gaba d'aya ta d'ago a hargitse tana kallonsu, dukkaninsu tashin hankali suka shiga sunsan halin mom, zuwa sukai kusa da ita suka gayar da ita ta ansa cikin sakin fuska abinda ya masu mamaki kenan, batako tambayi inda sukaje ba, ta mik'e tabar wurin, kallon juna sukayi kafin suma su mik'e gwiwa a sace zuwa cikin gidan a b'angaren su. ************ Tun jiya ake zuba sanarwa amma har yau babu wanda yace yasan fuskokin mutane biyu, Ayusher dukta shiga damuwa, wayan Sufyan ta kuma kira, bayan sun gaisa tace cikin sanyin jiki "Pure heart beyi working ba wlhy, har yanzu fa shiru babu wanda yace ya sansu ma" nisawa yae ya kalli Abu huraira dayake kwance ya lumshe idansa kamar me bacci amma a zahiri ba baccin yake ba yace "Ina kince d'ayar karaya ce kawai, a baki ake karaya ne? Tayi magana mana" Nisawa tae "Yare takeyi kamar yarbanci kamar kuma wani abu daban" zabura yae ya kalli Abu huraira yaga bashi yake kallo ba yace "Kina ina yanzu?" "Ina asibitin mu" ta bashi amsa a tak'aice kashe wayar yae ya fice daga d'akin cikin hanzari, huraira yana wata duniyar dabemasan wainar da ake toyawa ba tukunna.... Kallon patient d'in yae cikin nutsuwa hankalinsa duk se ya tashi yace yana kallon Ayusher "Ayush baki gane wannan yarinyar ba wai?" Kallon mamaki ta masa "Ni ina zan santa bare na gane ta?" Shafar sumar kansa yae "Yarinyar dakika tarar agidan mu ta taka glass d'innan, danakewa hanifer masifa akanta" waro ido tae "Are you serious?" "Wlhy itace Ayush, kwana nawa muna nemanta, ni banmasan yanda akai ban gane ba tun sanda kika gayan" nisawa tae "Alhamdulillah yaa Allah, hankalina a tashe yake tun faruwar al'amarin, bansan madafa ba" yafita shiga farin ciki me yawa, daga bisani kuma ya shiga fargabar sanarwa Abu Huraira, ko shakka babu yanawa Lawuri Son so, duk kalaman daya fad'a dad'in baki ne kurin wa d'an uwansa bayaji ze iya sadaukar masa da soyayyar dayakewa Lawuri koda dawowa tayi arayuwar su kowa ya fanshi kansa agunta kawai, da wannan ya yanke shawarar barin hakan sirri na sanin makomarta. "Ayusher akwai taimakon danakeso kimun" kallon sa tae cikin mamaki "Name pure heart" Murmushi yae "Zanje da kaina nawa mom mgana akan yaran, muso muke su karb'i musulunci amma mom bataso ta barsu agidan mu, koda zata taimaka idan sunji sauk'i sesu xauna gunku, yaran danake gaya miki ne fa munzo dasu a hatsarin damuka shiga,kuma wannan ta taimakemu sosai, and please karta gayawa mom suna gunku" Nisawa tae "Pure heart dan wannan sekaje gun mom, karka damu bazan mace mata su bane, kurin zan dakatar da sanarwar kuma inshaa Allah zan nuna bamu samu iyayen suba zan rik'esu zuwa time daya dace kake kuma buk'atar su" godiya yae mata sukai sallama ya yafi. A hanya se murna yake akan ya samu Lawuri, ya k'udirta kuwa baze tab'a gayawa Abu huraira inda suke na. ************ *Bayan kwana biyar* D'awai niya sosai yake dasu har lokacin Lawuri se adu'a amma jiyan anyi nasara ta farfad'o, Dr. jalal shine mutum na farko datayi karo dashi tun bayan data farfad'o d'in, iyakar bincikensa akanta kuwa ya gano ta samu total lost of memory!!!!! Wanda tayi matuk'ar bashi tausayi duba da yanayin shekarunta. Yarinyar ta tsaya masa arai so yake ya taimaketa ta dawo daidai amma waze taimakeshi aikata hakan? Irin wannan fa dole se akwai wanda ya sanka cen baya, wacce suke tare ma tana samun sauk'i amma magana da ita ma wahala ne, shi kuwa da kanshi yakeso ya taimaketa, da kanshi yakeso ya daidaita tunanin ta zuwa duniyar ta ta baya, taji jiki ainun, da wannan yanemi Ayusher. Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* Litattafan mu ba free bane, na kud'ine dan Allah idan baki siyaba karki karanta,idan kuma kina buqatar daya daga ciki ki nemi wannan lambar 07084161619. Kamar da wasa (ummie Aisha) Sultan merah (fatima zarah) Doguwar hanya (Billy galadanchi) Zafin Rana (Ayusher muhammad) Sanadiyya (Maman khadyy). 18 Jinjina kai Sufyan yae bayan ya gama jin bayanin Dr jalal "Duk zan iya likita nidai fatana ta dawo cikin hankalinta kawai komai nata ya zama normal" "Idan akayi hakan zamu samu sassauci kaga tana samun difficulties wurin magana so dole semun d'auki mataki wannan ciwon maya buk'atar magani sedai ayita kulawa dasu ana koyar dasu abubuwa masu yawa" Sosai sufyan yae godiya kafin su rabu. *********** Murna awurin sufyan ba'a magana yana fatar karma memory d'in nata ya dawo sabida yanaso tasoshi shishi kad'ai batare da wani ba, yanaso ta manta da wani Abu Hurairah tun a wancen garin ya kula cewar tanason huraira shikuma baya fatan taso waninsa. Zama yae da kanshi yake bata abinci abaki, se murmushi yake zuba mata yana mata magana da hannu, kallonsa kurin takeyi bata fahim tarsa sam, language data iya shibawai ya iya bane ba ruwa ya bata tasha sannan yace "Lawuri?" Kallonsa takeyi sam bata gane ko waye bama tunaninta ya tsaya cak ta gagara tunanin komai ita kam "Sannu" shine abinda ya furta yana murmushi, ta gane kalmar tasan ta amma bata tunano komai ba, TV ya kunna ya zauna yana kallo yana nazarin kalmomin yarbanci daya soma koya a wurin Dawood da takarda da biro a hannun sa, so yake yariqa yin magana da ita shishi kad'ai, ya iya yaren su sabida kota kwana idan ma memory d'inta ya dawo shine abu huraira shi takejin yarensa kawai..... "Al-Hussain ina cikin tashin hankali, yaran nanfa hakk'in su yana kanmu, mune fa mukazo dasu wannan Doguwar hanyar batare da munyi wani dogon tunaniba, yanzu kana ganin daidai ne ace mu k'yalesu? Kana ganin daidaine mu fita sha'anin su bamusan hannun wa suka fad'a ba? Bamusan inda suke ba bayan ni dakai munada tabbacin cewar yaran nan basusan hanyar garin suba, ni inaga bamuwa kanmu adalci ba bakuma mu musuba" Nisawa yae yana me kallon yayan nasa "Twin ya kakeso muyi? Neman mutum a fad'in Nigeria nan ba abu bane daze mana sauk'i, munyi iyakar yinmu mesa newai kake k'ok'arin jefa rayuwar ka a hallaka akan wad'annan yaran? Kaga yanda ka rame kuwa? Dan Allah bro ka dena maganar yaran nan" kallonsa kawai Hurairah yake cikeda mamaki "Al-hussain yaushe ka dena damuwa da damuwar d'an uwanka? Yaushe ka soma sauyawa haka? Har yaushe ka soma manta wa da abinda nakeso? Ka manta soyayyar danakewa yarin yar nan kuwa?" Kallonsa shima yake cikin jin zafin jin wai yanason Lawuri har haka "Amma Al-hassan Hannifer kuma fa? Tun yaushe take dakon sonka? Tun yaushe take bibiyar ka, banji tausayinta ba matsayinta na mace sekai zanji tausayin ka, idan har akasan abinda kakeji game da ita babba ne ya kamata ka dubawa wannan yarinyar itama, ka ajiye son watacen dabaka masan inda take ba kaso k'anwarka ta jini" Gabaki d'aya ya gama rikitar dashi be saba yi masa magana haka ba, rana d'aya sukazo duniya amma yana matuk'ar girmamashi kasancewar shine yazo kafinshi "Al-hussain meke dmunka ne? Meya sameka hakane baka kallon damuwata seta wata hanifer?" Mik'ewa yae "Hanifer fa ce wata? Nifa bro damuwata d'aya wannan damuwar daka sanya kanka aciki, ka musu adu'a kurin shine abinda suka fi buk'ata a yanzu dai daga gunka" bece masa komai ba ya d'auki towel ya shiga wanka ya fito ya kimtsa se feshe feshen turaruka yake yana gyara sumar kansa yayi kyau matuk'a, kallon sa huraira yae sanda yake k'ok'arin barin d'akin "Twin ina cikin damuwar ne zaka fita ka barni ko kamun yanda ka saba kace nazo muje gun friends namu indan sake haka muka saba dakai?" Kallon agogon hannunsa yae "Bro da akwai inda zan biya ne gashi kaga ko wanka bakai ba, idn ka kimtsa kamun waya zan dawo na d'aukeka kaji" Bece komai se kishingida da yae "Twin ya canja sosai, ya fita harkarsa ya dena fita tare dashi ya dena damuwa da damuwar sa meya sameshi?" Da wannan shima ya kimtsa ya fice. ********** "Dawood mesa kaida sufyan bakwa tausayi nane wai? Kafi kowa sanin cewar ban tab'a samun yarinyar danace ma inaso ba idan ba Lawuri ba, amma sam ta b'ata kun wofintar da ita kun manta haqqin kulawa dasu yana rataye ne a wuyanmu" kallon nutsuwa Dawood ya masa "Nifa Abu Hurairah inaga adu'ar neman tsari ya kamata mu nema da wad'an nan mutane, bawai kai kad'ai ba nida kaina seda na fad'a tarkon ta, da momy ta kula ta dinga mun adu'a aka saka malamai ma sunayi sannan na samu lafiya akanta, abu na gaba kuma idan ka kula da kyau zakaga cewar bamune muka koresu ba da kansu suka bar gidan kuma Allah ya gani munyiniyakar yinmu, yanzu me kakeso muyi" Nisawa yae cikeda damuwa "Amma dukda haka baka ganin ya dace mu koma garinsu mu bincika kosun dawo, ka tabbatar fa cewar bawai sunsan hanya bane ba, bakuma wai sunajin yarukan garin bane, yarbawa kuma bawai lallai su taimaka musu ba" kallon tuhuma dawood yake masa cikeda mamaki da tunanin anya hankalinka d'aya kuwa "Kana haukane Abu Hurairah, yanzu kai Allah ya tsamoka daga hallaka sannan kace zaka koma, kasani irin azabar damukasha da *Doguwar hanyar* damuka bi Allah ne kad'ai yasa munada sauran shan ruwa agaba, kuma banda Allah babu me iya mana wannan, bari kaji idan harkai so ya rufe maka ido ni badaniba bazan tab'a komawa wannan hanyar ba, dan inada hankali na, ko dama nifa kurun ina sha'awar mukai musulunci agarin dababushi ne amma ban shirya hallakar da kaina akan mace ba" "Haba mana Dawood mesa bakwa tausayi nane wai? Mesa kakemun haka? Wlhy rashin ganin wannan yarinyar tamkar rasa wani b'angare ne ajikina, ka taimakeni" "Tausayinka nakeji wlhy d'an uwana, dole zanwa mommy magana ma anema maka magani kaima dan wannan abun tashin hankali ne, ace dai duk uquba da azabar damuk sha a wannan *DOGUWAR HANYAR* har kake iqirarin zaka koma?" Ai wannan kasan bawai aikine na hankali ba" Shiru kurun ya masa harya mik'e yabar masa d'akin gaba d'aya. ************ Tunda yake maganar general kallonsa kurin yakeyi, mamaki yake yanda yaron ya k'wallafa ransa akan yarinyar ya sani uwarsa koze mutu bazata yardaba, kuma yasani tabbas idan be masa abinda yake soba akwai matsala "Amma kai Huraira dolene sekaje da kanka? Idan neman yaran kakeso ayi kabari da kaina zan tura manyan soji suje garin amma bazan bari kai kaje ba" langwab'ar da kanshi yae ya marairaice fuska "Dad ka taimakeni aje dani, dan Allah na roqeka, kuma ni base ka gayawa mom ba kurun dai nika barni i promise u zan tsaya bayan sir shamsu akoma meye" Shiru yae yana nazarin maganar sa secen yace "Idan kun tashi kubi ta wannan ruwan, ta garin wannan fulanin wannan jejin yanada matuk'ar hatsri, zan maka adu'a kakuma tabbatar hadda yad'uwar musulunci ya sanya kakeso kaje da wannan Allah ze dafa maka" haka yae godiya ya tashi murna fal aranshi. ********** Tunda yaje gunta suke magana da 'yan kalmomin daya iya na yarbanci, komai shine yake shige mata gaba tanayi, sunyi shak'uwa me yawa, a hakan kuma yake mata hausa, lokuta da dama tare suke kulawa da ita shida Ayusher ko yanzu atare suke suna hausa suna yarbancin dasuma tsinta gwanin dariya, danma tanada kan kamawa sabida acikin 3 weeks harta soma iya mayarwa da hausar, ita kuwa Ayusher baiwar Allah har ita ake koyon yarbancin sabida tanaso taga Abu sufyan acikin farin ciki, kuma zaman yarinyar agidansu ya k'ara janyo kusanci a tsakanin su sabida kusan kullum yana gidan.. Mik'ewa yae ze tafi ya soma sallama dasu, kurun se Lawuri ta soma kuka akan zata bishi, hannunta ya rik'o duka biyu "Má binó Lawuri (kiyi hak'uri Lawuri)" Langwab'ar da kanta tayi cikin shagwab'a tace Igbawo lóma dé ? (Yaushe zaka dawo) Murmushi yae yaji me tace amma besan meze ce mataba da yarbancin se cewa "Da sassafe gobe" sarai ta fahimce shi setayi murmushi tace tana zare hannayenta "Odaró (seda safe) Ta furta tana me juyar da kanta alamun btaso ya tafi, takaici duk se ya kama Ayusher amma seta had'iye kurin itama ta soma rarrsahinta da hausa. Abu sufyan yabar wurin cikeda begen Lawuri yanaji aduniya baze tab'a iya yafewa waninsa itaba har abada. ********** Shirin tafiya sukayi akan shi Huraira zashi tafiyar aikine sokoto, adu'a sosai mahaifiyar sa ta masa sannan yabar gidan, inda akayi zasu had'u da sojojin anan suka had'u general ma yayi adu'a sannan suka kama *Doguwar hanyar* dasuke fatan binta a wannan karon ya zamar musu alkhairi. Niko nace Allah ya fitar ga A'i ga cinikin rogon ta kodai ta fad'i ko taci riba. ********* Mom Nu'aiym. [11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇* *Billy Galadanchi* *Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)* *Littafina na kud'i ne, dan Allah idan baki siyaba karki karantamun, kokimun ki tura wani gurin, bana Allah ya isa bane amma dai haqqina yana wuyan wanda ya aikata d'aya daga ciki, kuma koda ban fad'a ba duniya shaidace akan Allah isashene. Idan har kina buqatar karantawa ki nemeni ta wannan lambar 07084161619* 19 Zaro wayrsa yae daga aljihunsa cikin takaici dan sosai ta dameshi da ringing, ganin Al hussain da yae yana kiranshi yasa ya d'aga cikin mamaki "Mekenan haka kayi bro? Mesa zakamun haka?" Kishingida yae ajikin kujerar motar yana lumshe ido "Me kuma nayi maka?" Ya furta cikin mamakin kalaman d'an uwan sa "Dad ya gayamun komai, Amma na sanar dakai yaran nan basa garinsu fa mesa zaka nace akan sekaje?" Sumar kansa ya shafo zuwa sajensa har zuwa gemunsa yad'anja a hankali "Wane yaqini ne dakai nacewar basa garin su? Hakan yana nuni ne da cewar kasan inda suke kenan?" Se a sannan ya gano wowtar da yae na furta hakan "Da nasan inda suke yaya zan barka ka tafi a banza? Kurin dai ni nasan basu san hanyar bane ba ko alama, kuma naga k'afarka har yanzu kana d'ingisawa ai" "Wannan ba damuwa bane kaidai bakaso ka joining hand dani mu taimaki musulunci, baka kuma so in smu abinda nakeso so kayi abinda ya shafela plss ni zanyi nawa" mamaki sosai kalaman sa suka baiwa sufyan "Bro abin yakaimu haka mesa zakamun wannan maganar" tsaki Huraira yae "Sufyan plss pray for me if u can, babu abinda zaka gayamun yanzu, banaso mui wata doguwar magana yanzu plss" yasan halin huraira tunda yace fushin yake da gasken kuwa shiyake mutunci d'aya zewa kanshi ya barshi for now, da wannan yamai adu'a kurin yana mejin zafin zuciyarsa duk yanda yaso ya sanarwa d'an uwansa gaskia zuciyar sa ta hana. *********** Yau duk sukuku Sufyan yake har Lawuri ma ta fahimci haka seya kasance basu wani hira, tunanin d'an uwansa duk ya dameshi, shibesan meke damun saba, zama kusa dashi tae ta shagwab'e fuskar ta amma ta rasa ma me zatace masa, da k'yar ta tattaro kalmar "Kiló shiyé lèni "Meke damunka yau" be fahimta duka ba amma tabbas ya gane abnda take nufi, murmushi ya qaqaro "Ba komai fa Laure" Langwab'ar da kanta tae adaidai sanda Ayusher ta shigo d'akin da sallamar ta hankalin ta yana kan yanayin sa dakuma yanayin zamansu, zama tae ad'an nesa dasu idanta yana cikin nasa "Sannu" shine abinda tace dashi kurun ta kawar da kanta gefe d'aya cikin takaici "Menene damuwar kuma? Naga duk kin canja" ya tambayeta cikin nuna kulawa "Ba komai idan ka gama abinda kake zan jiraka a babban parlor akwai maganar danakeso muyi" jinjina kansa kurun yae "Muje a shirye nake, kallon Lawuri yae ya shafi sumar kanta "Zan dawo yanzu kinji?" Ya furta cikin harshen hausa, gyad'a masa kanta tae danta fahimci me yake nufi. "Dama akan abinda kakeyi da yarinyar cenne, kaga ka zire mata da yawa fa pure heart, bama wannan ba kaifa ka hanani hugging naka, shaking hand dakai amma yanzu se inga kana rik'ewa yarinyar cen hannu, kana matse wurin zama da ita anya hakan daidai kuwa?" Wani yamutsatsen kallo yabita dashi cikin hargitsi "Me kenan kike nufi da wannan maganar? Zargi na kike da yarinyar kome? "Wannan wace irin magana ce Yaa Sufyan? Ni yaushe nace wani zargi anan? Kurun ina gaya maka gaskia ne, mom ma tayi magana akan zaman yarinyar agidan nan, tunda an sallameta daga asibiti ka kaita gidanku kurin" cikin takaici ya kalleta "Sabida na nemi alfarma agunki shine zaki zomun da hauka? Mesa zakimun haka ne wai? Ni yanzu kin rainani idan da inason ta zauna gidan mu daban kawo ta nan ba ai sabida kanki ne cewar munada muhallin ajiyetan" Yanzu kam itama ta fusata "Sabida ina bautawa sonka seka mayar dani baiwarka? Sabida ina jarabtar sonka seka laftamun wata jarabawar, mayar dani wawiya kakeso kayi ko wacce batasan metake ba, idan hakane na dena damunka da zancnm soyayyata koda hakan ze zamo ajalina, ada roqonka nake kazo gidanmu amma sekayi wata kanamun yawo da hankali tunda kazo da wannan dangin mayun kake ziyartar gidannan wani zubin agunta kake wuni, an gayamaka banida zuciya ne? Daga rana me kamar ta yau na yafe duk wani abu daya dangance ka koya shafeka aiba kai kad'ai bane autan maza amma ka kwashemun dangin maguzawan cen daga nan gidan kaje dasu koma inane" yaukam mamaki Ayusher ke bashi iya mamaki, har wanda be tab'a tsammani ba, kwantar da murya yae "Karkimun haka mana Ayusher, ki tallafeni ki k'aramun lokaci wlhy dik abubuwan da kika lissafa bawai haka bane ba, tausayi kurin suke bani" k'ura masa ido tayi "Zan barsu su zauna, zan kuma yiwa mom magana akansu amma daga rana irin tayau karkai tunanin zan kula maka dasu, ka neki me aiki zasu koma b'angaren ma'aikata, karkuma ka k'ara zuwa inda take ka nemeni, ni bana mason ziyarar nabar mata" rarrashin duniya yayi amma haka ta kafe akan idan be yarda da hakan ba ya kwashe su agidan, badan yasoba yace ze duba me kulawa dasu d'in. ********* Seda suka zo k'auyen fulanin dazasu hau ruwa sannan sukai shiri suka ajiye motocinsu suka kama hanyar wacen garin fulanin na biyu, basu kwana ba suka kara tsalaka ruwa suka shige d'ayan garin inda aka musu karamci, sosai sukayiwa dattijon hakimin k'auyen bayanin dalilin dawowar su, jinjina kansa yae cikin jimami "Bana tunanin yaran nan sun dawo ta wannan hanyar gaskiya, kuma kunce basusan waccen hanyar ba, akwai gari idan an tsallaka ruwa anan yamma damu da suke cin naman mutane, abinda ya hanawa garin yawa ma kenan, sabida naman junan su ma ci sukeyi, yazamana aka shard'anta atsakanin su duk gidan dasukayi magana da juna so biyar arana agidan za'a d'auki mutum a yanka, idan baku manta ba na sanar daku kuma arziqi kukayi sabida zamansu matsafa, zakaga ko kallonka ma ba wanda zeyi a k'auyen ya kamata suma ku kula dasu sosai, rayuwarku da lafiyar ku itace tafi komai muhimmanci agareku, zancen musulunci dakukeso ku yad'a bazan hanaku zuwa isar da sak'on Allah ba, amma idan ba haka ba ku hak'ura wad'an nan matan dai basu dawo ta wannan hanyar ba sam" Abu sufyan ne ya tare da cewar "Babu damuwa Ranka ya dade, dukda hakan zamuje mu duba su, hankalina baze kwantaba sena tabbatar basuje d'inba, kuma na isar da sakon Allah" jinjina kai dattijon yae "Bari na baku aron mutane dasuka san kan jejin sabida tsaro" haka ya had'asu da fulani su hud'u suka shirya tsaf bayan sun basu ajiyar muhimman kayansu ciki jarda wyoyin salula suka lula doguwar hanyar.... ********* Cyama yauma kamar kullum se rarrashin mom take amma abun yanaso yafi k'arfin ta, general ya sanar mata inda Abu Hurairah yaje se kuka take akan ya cutar da ita, yaya zebar yaronta yaje wannan mugun wurin akan wad'an cen yaran "Cyama tun shigowar yaran nan arayuwata nake ganin jarabawa iri iri, wlhy halinsu ya isheni, nagaji da mugun abun dake bibiyata, daddynku kamar bashi ya haifi yaran nan ba, duk wata musiba ita yake jansu ya kaisu aciki, shi mesa bejeba in hakane?" Rufe mata baki Cya tae "Hana mom, mesa kike hakane wai? Ya dace kisan me kike fad'a gaskia, dad daya dage wurin ganin ya inganta rayuwar mu da taki ma, shine kuma yanzu kike zancen yayi kaza yayi kaza, sam be dace ace hakan daga bakinki yake fitowa ba gaskia, ki masa adu'a Allah yasa ya ganta kuma su dawo lafiya" wani hargitsatsen kallo mom tayiwa Cyama "Su dawo dawa? Idan ma mafarki kuke kedasu toku farka indai ina numfashi a doron duniyar nan wlhy kinmaji na rantse d'aya daga cikin yaran nan baze aure wannan shaid'aniyar 'yar maguzawar ba, koda bazasu auri matan dake sonsuba toko tabbas wannan shegiyar ma bazasu aureta ba" kame baki siyama tae sabida sanin halin mom tasani indai ta kafe akan abu ta kafe kenan, haka dai ta ringa rarfashi harta sakko. ********** Daren da yae musu ne a hanya ya basu damar kafa tent irin na soja suka kwanta aciki, Abu Huraira seya rasa meyake yawan fad'ar masa da gaban sa a wannan lokacin, da k'yar da sid'in goshi bacci b'arwo ya sace sa badan yaso bama, baccin sam bawai yana masa dad'i bane wannan ya sanya gari yana soma haske alamun sanyin asuba ya farka, shiya soma fita fitsari domin yasamu damar yae alwala yae sallah ya tashi sauran musulman dam tafiyar akwai arnan soji acikinta susu biyu, seda ya lula duniyar wasu itatuwa sannan ya tsaya ya soma fitsarin, kaman daga sama yaji an k'wala mar abu akai seda yae wata uwar k'ara daga nan ya some besan me ake ciki ba, Oga sufyan dayaji ihu ya duba tent baya nan seya fargar da sauran suka lula jejin nemansa. ************* Abu Sufyan tunda yabar gidan su Ayusher se wani zazzafan zazzab'i ya rufe shi, tunanin sa ya tsaya cak akan yanzu idan kuma garin wannan tafiyar Abu Huraira ya rasa rayuwar sa fa? Yace masa me? Mesa sanda sukai waya be sanar masa Lawuri tana nan ba yasan inda take? Tunanin d'an uwan sa sosai ya addabesa harya saukar masa da zazzab'i shi yasan yana son Lawuri amma ganin yanayin d'an uwansa kurin ya isa ya nuna maka cewan beko kama k'afarsa ba a soyayyar ta Lawuri, amma bayaji ze iya bar masa ita kam, sedai yanaso ya ganshi tare da d'an uwan sa, duk sanda ya tuna yanayin tsoro daya shiga a wancen lokacin dakuma wahalr dayasha se taimakonsa da Abu Huraira keyi seyaji zuciyar sa tana masa zafi akan abinda ya masa, ya tabbatar da Huraira yasan yana son Lawuri baze ma nuna masa yana santa ba sedai ya mutu dan nashi farin cikin kawai, abubuwa sun taru sunwa Sufyan yawa duk inda hankalin sa yake atashe yake... ********** Yanayin mutanen dake kan Abu Hurairah abun ya tsoratar dashi, duk jikinsu fenti ne, ja da fari, idanuwansu ma abun tsoro ne ja jajir anja musu layin bak'i a k'asansu, gasu suma k'arti bak'i k'irin dasu, yama rasa shi tunanin me zeyi, an tub'e masa kayan jikinsa gashi tsirara, besan wannan wace kalar al'umma bace kuma? Shidai yaga rayuwa se wasu surutai suke da sam baya gane komai akansu, hankalinsu yakai k'ololuwa gun tashi. *********** Wani daga cikin fulanin ne ke magana akan b'atan Hurairah "Al'ummar songai ne suka d'aukeshi, matsalar su kuma basa zama gu d'aya, yanzu Allah kad'ai yasan me zasu masa" shiru OGA shamsu yae yana tunanin komawa gida dazaran sun ganshi,musiba daga wannan se wancen gaskia shi bega amfanin haka ba, oga beyi tunani me kyau ba, wanban ba aikin qasa bane na ra'ayin sane. Mom Nu'aiym.