UWATA CE SANADI ©Maimunah Tijjani Iyam Bismillahir rahmanir rahim ina Mai farawa da sunan Allah mahaliccina Wanda cikin ikonsa,amincewar sa,yardar sa tare da Aron numfashin daya bani na rubuta wannan littafin nawa UWATACE SANADI.ya Allah ka tsare min hannaye na wajen rubuta abin da zai zama cutarwa ga al'umman musulmai tare da tarbiyarsu. GARGAƊI Ban yadda wani ko wata suyi ƙoƙarin sauyamin littafi ba,ba tare da iznina ba Duk Wanda yayi ƙoƙarin aikata hakan ALLAH YA ISA BAN YAFE MASA BA. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 0⃣1⃣ Littafin ƙaddarar rayuwa ta cike yake da babi-babi na ƙuncin dana taso,na tsinci kaina a cikin tun kafin nasan kaina. Kamar yanda jini yake yawo cikin duk wata sassan jikin ɗan adam misalin yanda ƙunci yayi kane-kane cikin rayuwa ta. Kowani ɗa yafi kusanci da mahaifiyar sa saɓani nida ta wa uwar take ƙoƙarin nisan ta kanta dani,rashin dace da samun nagartacciyar uwa shi yaja ragamar rayuwa ta izuwa ga ƙunci da baƙin ciki. Bansa menene farin-ciki ba,bansan ya ake yinsa ba,bansan inda ake samun sa ba,wasu lokutan nakan zauna nayi kuka da hawaye anya akwai mai irin ƙaddara ta kuwa?. Tabbas kowani bawa da irin tashi salon ƙaddarar da kuma yanda take zuwa masa amma tawa ta fita daban. Suna na Hibba labarin rayuwata Mai matuƙar girgizarwa ne,firgitarwa,gami da kiɗimarwa. Duk wata zuciyar da Allah ya dasa imani acikin ta sai ta raunana domin jin labarina,yayin da idanuwa da yawa zasu zubda hawaye yayin da suka saurari labarin rayuwata. Nice ɗiya ta farko a wajen mahaifina ta bangaren mahaifiyata kuwa ta kasance, ta taɓa aure kafin mahaifina ɗanta ɗaya da tsohon mijin nata YAYA FAWAS,amma duk tare muke zaune dashi. Mahaifiyarmu haj.Juwahir ba inda munanan halayyarta basu jeba kowa ya shaideta da rashin ta ido wato kunya,ta bangaren Abbana kuwa juya shi takeyi son ranta kasancewar ta fishi abin duniya. Duk dawainiyar gidanmu ita takeyi,Abu daya daya ke rushe mata wannan aikin alkhairin shine gori domin ko ruwa. Ta saya a gidan nan sai ta wuni tana yiwa Abba gori,ta gaza fahimtar nauyin igiyoyin aurensa uku dake kanta, ta wofantar da nauyin tarbiyanmu dake kanta ta zaɓi duniya sama da inganta lahilarta. Yanda ake dama koko a cikin kowani gida na kirki haka Umman mu ke dama giya a tsakar gidanmu wai da sunan Sana'a. Safiya ce datake cike da sanya nishaɗi yayin da faffaɗan bishiyar tsamiyar dake dashe,a madaidaicin filin tsakar gidan mu ke kaɗa iska ko'ina.Yanayi ne mai tafiyar da zuciya kasancewar daren jiya kwana akayi ana zabga ruwa,hakan ya sanya garin ƙara sanyaya. Zaune nake a madaidaicin ɗakin yake mallaki na,katifa ce wacce take yashe a ƙasa sai kuma bahon kaya daga can gefe guda su kenan a cikin ɗakin. Shirin tafiya makaranta nakeyi ina saka safa yaya Fawas ya shigo ɗakin bakinsa ɗauke da sallama, da fara'a a saman fuskata nake amsa sallamar.A gefena ya zauna tare da karɓan safan dake hannuna ya fara ƙoƙarin sanin yana cewa. "My cute angle har yanzu baki gama shiryawa ba ko so kike muyi latti?". Cikin murmushi nace"A'a yayaa Fawas ai nakusa gamawa ma fa ka shigo". "Ba wani kin kusa gamawa bayan kullum sai nazo na taya ki shiryawan". Yana gama sanin safan ya riƙo hannuna muka fito,A kwance akan tabarma muka hango Umman mu ta lumshe idanunta kamar mai bacci, a hankali muka ƙariso inda take cikin ƙasa-ƙasa da murya yaya Fawas ya kamo kunne na yana cewa, "Ƙanwata mu tashe tane ko kuma mu tafi?". Nace "yaya Fawas inmuka tashe ta faɗa zata mana gwara mu tafi kawai". "To". Kawai yaya Fawas yace tare da ƙara riƙo hannu na muka dauƙi hanyar fita daga gidan. Kamar daga sama muka ji muryan Umma ta daka mana tsawa a firgice dukkaninmu muka juyo yayin,da lokacin ɗaya jikinmu ya ɗauki rawa bansan sanda nasaki wani razanannan ƙara ba saboda duk na tsorita inda abin dayake saurin gigitani to tsawa ne. Kamoni yaya Fawas yayi sosai cikin zubda ƙwalla yace "kin nutsu ƙanwata kinji". Cikin wani tsawan umma ta cigaba da magana tana cewa,"Munafukan banza ina da kuke shirin tafiya yan iska jarababbu salon kujawa mutum abin magana a gun wannan sakaran uban naki ko?". Cikin raunanniyar murya yaya Fawas ya shiga faɗin "Umma dama munga kina bacci ne kuma bamason mu tashe k......" Wani tsawan ta kuma dakawa yaya Fawas Wanda yasa shi yayi shiru ba tare da ya ƙarisa maganar da yakeyi ba. Cikin zafin rai Umma take maganan tamkar zata kaiwa ya Fawas duka take cewa"Dalla rufe min baki munafikin banza, Ku wuce kuje Ku ɗauko abinci kuci kafin Ku tafi". A hankali na wuce kitchen naje na ɗauko mana abincin, hawaye tunin ya fara wanke min fuska muka fara cin abincin. Ai kuwa kamar jira Umma takeyi mu fara cin abincin.Muna kai spoon ɗin farko ta fara zazzaga mana gori.Wani dariyar ƙeta tayi sosai har sai da idanunta suka kawo ƙwalle kafin tace,"Uhm abin da kuka iya kenan daga Ku har lusarin uban naki shine ci kudai sai dai infita innemo muku,in dafa,in baku Ku zauna Ku hau ci ko? daman shine aikin.ba komai ai Allah yana ganin duk abin da sule yakemin a cikin gidan nan duk ɗawainiyar gidan nan ya gibge shi a kaina tsabaragen lusaranci irin nasa". Sai data numfasa sannan ta cigaba da faɗin"Bashi da aikin sai yawo a cikin unguwa daga wannan masallacin sai wancen". Da hawaye fal a idona na takaicin furcin Umma na miƙe daga cin abincin cafko hannuna yaya Fawas yayi shima idonsa cike da hawaye yace"A'a ƙanwata ki zauna mugama cin abincin kar ki ja mana wani abin maganan". Tabbas akwai wata irin so da shaƙuwa tsakani na da yaya Fawas,a lokuta da dama nakan mance dacewa ba mahaifinmu ɗaya da shi domin ko Kaɗan Abba baya nuna bambamci a tsakaninmu. A hankali na dawo na zauna tare da ɗaura kaina akan cinyar yaya fawas ina kuka.Mukam wacce iriyar uwa Allah ya bamu,kullum tinani na shine wani irin laifi muka aikatawa umma datake nuna mana wannan zallar kiyayya tamkar ba ita ta haife muba. Shafa kaina yaya Fawas yayi cikin Ƙarfi hali yace"Ya isa haka Hibba ki tashi mu tafi kinga ma munyi latti". Tashi nayi na fara tattare kwanukan abincin na kai kitchen.Umma nake kallo yayin da ita kam ma hankalinta ba'a kanmu yake ba sai al'amuran gabanta takeyi. Wasu hawaye ne naji sun shiga ambaliya a fuska na wato ita kukan damukeyi ma bai dameta ba,.kitchen na shiga domin ajiye kwanukan daidai lokacin daxan fito daga kitchen din najiyo muryan yaya Fawas yana cewa."Umma xamu tafi". Cikin ɗaga murya Umma tace" to Fawas Dan zaku tafi me kakeson namuku kenan?na goya Ku nakai Ku makarantar ko kuma yaya kake son na muku?". Cikin sanyin murya yaya Fawas yace" A'a Umma dama kuɗin nafef zaki bamu kinga munyi latti". Harara Umma ta watsa masa sannan tace" nizan baku kuɗin nafef ɗin? Ai da niyyar ficewa kukayi daga gidan ba tare dakun sanar dani ba indai sai nabaku kuɗin nafef sai dai, Ku fasa zuwa makarantar ai dama ba dole bane". Tana kawowa nan ta cigaba da abinda ke gabanta.Fitowa nayi daga kitchen ɗin na nufi inda yaya Fawas ke tsaye riƙo hannun shi nayi ina cewa"Yaya na mu tafi kar muyi latti". Durƙusawa yaya Fawas yayi tare da ƙara riƙo hannu na dukka biyu hawaye nabin fuskar sa yake cewa"Hibba ko zamu haƙura yau da zuwa makarantar,kinsan da nisa in mukace zamuje da ƙafa bazamu isa akan lokaci ba,gashi kuma Abba baya nan balle inyana dashi ya bamu". Wani marayan murmushi nasaka Wanda iyaka cinsa fuska dan baikai har ga zuci ba kafin nayi ƙarfin halin furta. "A'a yaya Fawas muje kawai". Shima murmushin ya saka yana cewa" Ƙanwata mu tafi da ƙafa bazaki gaji ba?".kaina na ɗaga masa alamarar e. Share hawaye fuskan shi yayi tare da riƙo hannu na muka tafi.A hankali muke tafiyar kamar babu laka a jikin mu,tunda muka fito daga gidan cikinmu ba Wanda yayi magana. Kowa da abinda yake tinani acikin ransa.Muna cikin tafiya muka hangi Abba zaune a bakin wani masallaci,ya zabga tagumi hannu bibiyu. Hannunsa riƙe da carbi yana tasbihi amma kallo ɗaya zaka masa ka tabbatar wa kanka,cewa hankalinsa ba akan tasbihin daya ke yi yake ba. Ina hango Abba nasaki wani nauyayyan ajiyan zuciya nasan wahalar mu ta ƙare matuƙar yana da kuɗi zai bamu. Mu ƙarisa makarantar ƙafafuna har jinsu nakeyi tamkar ba'a,jiki na suke ba dan tsabar gajiya kawai,daurewa nake har ya fawas ya gane hakan. Da sallama muka iso inda Abba ke zaune,a hankali ya ɗago kansa daga tagumin da yayi yana binmu da kallo yace"Hibba Fawas me kuke yi har yanxu Baku tafi makarantar ba?". Tunin idanuna sun kawo ruwan ƙwalla nace "Abba wallahi Umma ce tace bazata bamu kuɗin abin hawa ba wai sai dai mu tafi da ƙafa,Ko kuma mu fasa zuwa makarantar". "inna lillahi wa inna ilaihir raji'un!wannan wani irin rashin tausayi ne haka,tun daga nan zaku tafi har makarantar kuma da ƙafa?". Jijjiga kansa yayi tare da ciro naira ɗari biyu daga aljihunsa,ya miƙawa yaya Fawas tare da faɗin"Ga wannan Fawas ko hau nafef,Ku tafi makarantar".Karɓa yaya Fawas yayi tare da yi masa godiya sannan muka tafi. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam __________________________ Free page Page 0⃣2⃣ Asalinmu A jahar yobe muke da zama ƙaramar hukumar potiskum, unguwar tandari. Asalin sunana Fatima naci sunan kakata ta wajen abba shiyasa Abba yake ƙirana da Ummul-khair. Abba Dan asalin kano ne cikin ƙauyen gano, kasuwanci ya kawo shi potiskum.A lokacin ya mallaki komai najin daɗin rayuwa kafin Allah ya jarabce shi da karayan arziki,auren soyayya sukayi da Umma amma tun daga lokacin da karayan arziki ya sameshi komai ya canza na daga zaman dasuke yi. Anan garin potiskum suka haɗu da Umma lokacin ta fito daga gidan mahaifin yaya fawas.A wajen kakarta take saboda iyayenta sun daɗe da rasuwa,bayan wani ɗan lokaci ma Allah yayiwa kakarta ta rasuwa. A haka Abba ya aure ta ya kuma riƙe yaya fawas tamkar ɗan daya haifa. Abba baya wasa akan duk wani lamarin daya shafi harkan karatunmu tun muna nursery school suke private school har kawo yanzu,duk da halin dayake ciki na babu bai taɓa gajiyawa,ba ko nuna gazawa wajen biya mana kuɗin makaranta ba. Burinsa ɗaya ne a duniya shine muyi karatu ta yanda zamu tsaya Da ƙafafunmu ko bayan bashi.Ina jss 3 ya Fawas yana ss 2 a unity model school dake nan cikin potiskum. Yau kam idan nace na gane abinda aka mana a makaranta to nayi ƙarya,dan tun da muka isa hankali yake ga tinani,har aka tashi muka dawo. Tun daga nesa muke hangi mutane keta shige da fice a gidanmu,wani baƙin ciki ne naji ya tsaya min a raina dana tino mummunar sana'ar Umma na sayar da abinda da Allah ya haramta. Manyan mutane,yan siyasa da ma'abota dukiya suke siyan giyan da umma keyi da sunan Sana'a. Da sallama muka shiga cikin gidan amma ba,Wanda ya kula da shigowarmu cikin gidan balle musa rai ga za'a amsa sallamar da muka shigo da ita.Gidan cike yake da mata da maza, karuwai da kuma ƴan daudu kowa abin da ke gabansa shi yakeyi. Ga wani mummunar shigar da matan sukayi,Umma na zaune a kan garduma tare da wasu mutane biyar uku maza biyu mata.Suna buga caca riƙo hannuna yaya Fawas yayi sosa tare da rufe min idona da tafukan hannunsa wai dan kar na kalli abin da Umma keyi. Muka wuce muka shiga ɗaki yaya Fawas yace."Kiyi wanka kihuta kafin lokacin islamiya yayi kinji ƙanwata " "To yaya Fawas". Fita yayi ya nufi daƙinsa,wanka nayi sannan nayi salla na kwanta ina kwanciya yaya Fawas ya shigo. A gefena ya zauna yana cewa" Hibba kinci abinci kuwa?". "A'a yaya Fawas kaima ai nasan baka Ciba"na faɗa ina tsaida idanuna akan fuskar shi. Ajiyan numfashi yasaka kafin yace,"Hibba inason muyi wani magana dake". Gyara zamana nayi ina cewa" to yayana inajinka". Cigaba da magana yayi yana cewa "ƙanwata kinga irin rayuwar da mahaifiyar mu ta zabawa kanta ko?" jinjina kaina nayi alamar ina fahimtar maganan tasa,sannan ya ɗaura da faɗin. "To Hibba banason koda wasa ne koda ace ni da Abba bamu numfashi cikin duniya,wataran kiyi sha'awar irin rayuwar da kikaga umma nayi,my cute angle kinga ke macece". Cikin nutsuwa nace" In sha Allah yaya Fawas zan nisanta kaina daga dukkanin ɗabi'un da umma take aikatawa.Amma abinda yake damuna shine in har tasan baza ta so mu ba to meyasa ta haifemu?". Gyaran murya yaya Fawas yayi kafin yace "Hibba Umma tafi karfin musata acikin jerin maƙiyanmu,ita tayi silar zuwanmu duniya ta nuna mana dukkanin ƙauna tinda har ta haifemu kuma bana son na ƙarajin,ki furta cewa Umma bata son mu kinji my cute angle?". " To ya Fawas in sha Allahu bazan ƙara ba". Shafo kaina yayi yana cewa" yauwa my cute angle nizan tafi shago in lokacin islamiya yayi ki shirya ki tafi kinji ko". Turo baki nayi kana nace" yaya Fawas ban iya hadda ba bazan jeba". Murmushi yayi Wanda sa ka fararen jerarrun hakwaran sa suka bayyana, yaya Fawas badai kyau ba dan mahaifinsa buzu ne ɗan nijar. "To shikenan amma in Abba ya dawo yasame ki a gida ba ruwa na" yana gama faɗin haka ya fice. Kallo nabishi dashi yayin da take ficewa daga daƙin,ina ƙara jinjina irin shaƙuwar dake tsakaninmu da yaya Fawas komawa nayi kwanciyata. Sai dab da magriba sannan na tashi nan naji gidan gaba ɗaya yaɗau kiɗa ta ko'ina sauti ne kawa ke tashi. A hankali na buɗe ƙofan ɗakin na fito wajen,dan gane ma idano na meyake faruwa.Maza da mata ne sun haɗe sai tiƙar rawa suke babu ko kunya,gefe guda masu shan taba sunayi,masu sha wiwi sunayi,mai shan shishi nayi. Can gefe kuwa masu caca ne suma sun haɗa nasu daban sunayi. Umma kuwa tana ta dama giyarta ga masu saya sun mata cirko-cirko akanta,sai sauri take taga ta sallame su lokaci ɗaya muka haɗa ido da ita. Sauri nayi na kawar da kaina gefe tare da share hawayen dake shirin zubowa daga idona. "Yauwa Hibba zo ki sallame waɗannan". Tunin ƙwalla suka fara bin fuskata nace"Umma alwala zanyi fa an ƙira salla". Ashar Umma ta shiga ɗuramin masu nauyin maimaitawa sannan tacigaba da cewa"Ƴar iska Mai halin ubanta ni zaki cewa salla? zakiyi ko muɗin ce miki akayi bama sallan,zaki yi gadon tsiya matuƙar kikace zaki gado halin ubanki wuce ki bani waje shashasha". A hankali nake daga ƙafata na wuce naje nayi alwala sannan na koma daƙi nayi salla. Ina iddarwa na kwanta akan sallayar wani azababban yunwa nakeji har sai da naji kamar zazzabi yana neman rufe ni,lokaci ɗaya jikina yaɗau rawa tashi nayi nashiga banɗaki nayi wanka sannan na dawo kan sallayata na,kwanta bansan sanda wani baccin wahala ya ɗauke ni ba. Sai bayan sallan isha'i sannan Abba da yaya Fawas suka shigo kamar night club haka gidanmu yake a kowani dare,suna shigowa suka hango Umma ta zage sai buga caca yakeyi,ga wani sautin daya ke tashi cikin ko wata kusurwa acikin gidan. Kai tsaye Abba ya nufi inda Umma take yace."Juwahir taso innason magana dake". Ko ɗago kai batayi ta kalle shi ba balle tasan da mutum awajen ta cigaba da cacan ta. Cikin zafin rai Abba ya sake magana a karo na biyu" Juwahir wai ba magana nake miki bane". A harsale Umma ta juyo tana cewa,"Haba!sule wai ya kake son nayi da rai nane kazo ka tarar dani ina Abu to ba sai kayi wucewar ka ba". Ɗaga hannu Abba yayi da nufin zabga mata mari,cikin sauri yaya Fawas ya riƙe hannun Abba cikin muryar kuka yace."Dan Allah Abba kayi haƙuri taci alfarma mu". Cike da takaicin daya gama cika Abba yace,"Juwahir Allah ya shiryeki" sannan ya wuce daƙin sa. Yaya Fawas ya shigo daƙi na kwance akan sallaya ya tarar dani a hankali ya zauna gefe na,mafici ya ɗauko ya fara min fifita gani yanda naketa haɗa gumi. Wani wahalallan ajiyan zuciya na saka lokacin,dana ji iskan na ratsani hijabin dake kaina ya fara ƙoƙarin ciremin. A hankali nafara buɗe idona ganin yaya awas ne yasa na fara,sakin murmushi yayin da nake ƙoƙarin tashi. Da fara'ar sa yace "my cute angle yunwa ce tasaki baccin nan ko?". UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________________ Free page Page 0⃣3⃣ Sunkuyar da kaina ƙasa nayi ina cewa"A'a yaya Fawas naci abinci". Ɗago kaina yayi yana cewa,"Hibba ko wani motsi kikayi nasan me hakan yake nufi baki ci abinci ba ko ƙanwata?". A hankali nace" e ya Fawas ban Ciba". Wata Leda ya miƙo min wacce ya shigo da ita yace."Gashi kici Abba ne ya taho mana dashi". Jawo ledan nayi gaba na na buɗe ƙosai ne a ciki Wanda baifi guda bakwai ba,tunin na fara hawaye na buɗe baki zanyi magana kenan yaya Fawas ya dakatar dani ta hanyar cewa. "Nasan bazai ishemu ba kici ke ɗaya kinji my cute angle". Bai jira amsar dazan bashi ba ya fice daga daƙin. Inaci ina hawaye haka har na gama na tashi naje nayi alwala sannan nazo nayi sallar isha'i,ina iddarwa yaya Fawas ya shigo yace Abba na ƙira na. Cikin sauri na miƙe nabi bayansa muka nufi daƙin Abba.Yana zaune akan sallaya muka sameshi wuri muka nema muka zauna,gyaran murya Abba yayi kafin yace "Ummul-khair da Fawas". Cikin nutsuwa dukkaninmu muka amsa sannan ya cigaba da maganar. "Kunsan halin da muke ciki a wannan gidan abinda yake damuna yanda ƙiyayyar da juwahir kemin har ya shafeku,amma bana son kusa wannan damuwar a ranku har akai ga wataran kun ɓata mata rai,a cikin ko wani yanayi kar Ku na mantawa da cewa ita ce silar ku nazuwa duniya babu abinda zaku yi mata Wanda zai biyata wahalar nishin naƙudar ku datayi.Tsakanin Ku da ita sai addu'a Allah ya shirya mana ita". "Amin "duk kaninmu muka amsa dashi. Nasiha Abba yake mana sosai akan irin girman hakkin da umma take dashi akanmu. Muna cikin haka umma ta bankaɗo labulen daƙin tare da shigowa daƙin tsaki ta saka kafin tace. "Haka dai ka iya sule baka da aikin yj sai dai ka tara yaran nan kana tusa musu ƙiyayya ta a cikin ransu.Wa kai a hakan kafi kowa son su bayan ba ɗaya daga cikin ɗawainiyar, su Wanda kakeyi sule kai kam ka tsoraci ranan da Allah zai tambaye ka irin kulawar daka bawa iyalinka". A hankali Abba yace" ummul-khair da fawas Ku tashi kuje Ku kwanta". Duk jikin mu yayi sanyi muka tashi muka fita bayan munyi wa Abba sai da safe. Miƙewa Abba yayi tare da faɗin"Juwahir nagaji da abinda kike min a cikin gidan nan,daga rana mai kaman ta yau indai na amsa sunana na matsayin miji a gareki to kin daina wannan sana'ar,sannan kuma bazaki ƙara taramin maza a gida na ba". Wani shewa umma ta saka kafin tace"Sule gidanka ko gidana? kai ko kunyar faɗa bakayi ba?kuɗin hayan dani nake biyansa". Cike da takaici Abba yake faɗin "juwahir ni kike gaya haka koda yake bazan yi mamaki ba domin Ku mata kunada saurin manta alkhairi,kin manta lokacin dana auro ki duk da kasancewar dangi na basuyi na'am dake ba juwa". Cikin matuƙar ɗaga murya wanda ya zamto ɗabi'ar ta,a duk sa'in daza tayi magana tace. "Na faɗa ma sule nace na faɗa ɗin yo sule da miji irinka a gwara babu,idan ka cika dan halak a cikin iyayenka ka ficemin daga gidana sai sanda ka sama zuciyar neman na kanka sa ka dawo,mu cigaba da zaman yanzu kai idan za'a lissafo maza za'a saka a cikine sule". Kallon ta kawai Abba yakeyi yama rasa me zaice mata a hankali yace. "Juwahir duniya ce ta tafi gabaruwa iya jima kije kiyi inkina ganin zai haifar miki da ɗa mai ido". Ficewa yayi daga daƙin ya shigo daƙin yaya fawas har yayi bacci ya same shi,juyowa yayi ya shigo daƙina inajin shigowar sa amma na rufe idona kamar bai bacci dan duk abinda yake faruwa inajinsu. Zama yayi gefen lamutsatstsiyar katifa ta kallona yake yi sosai yana shafa kaina yana hawaye yace. "Mama na Allah ya muku albarka keda ɗan-uwanki inason kasancewa tare daku amma dole zan barku". Addu'o'i yashiga min yashafa min sannan ya fice daga daƙin. A hankali nabi bayansa da kallo ina ƙoƙarin fahimtar inda maganganunsa suka dosa,umma na tsaye a ƙofar daƙin ta lokacin da Abba ya fito daga daƙina. Yatsina fuska tayi kana tace "Dan Allah sule inka tafi karka dawo har anaɗe duniya,inka tafi ma ai ni wahala ka ragemin umma ta gaida aisha a sauƙa tsiya lafiya". Ficewarsa yayi ba tare da ya kalli ko inda take ba,tsaki tasaka tare da komawarta daƙi. Tsawon Daren wannan ranan ban runtsa ba kamar yanda ban iya,tsayar da ruwa hawayen da ido ke tsiyarwa ba. Washe gari da wuri muka yi shirin tafiya makaranta, umma na zaune a ƙofar daƙin ta muka fito as usual tare da yaya fawas hannunmu saƙale cikin na juna. Durƙusawa muka yi muka gaishe ta amma ko ɗago kai batayi,ta ganmu ba balle tasan da mutum awajen. Miƙewa nayi na ɗauko mana abincin mu a kitchen cikin sauri mukayi muka gama ci. "Yaya fawas yau tinda na tashi banga abba". "Haka ne nima naje daƙin sa da asuba mu tafi masallaci amma da mamakina sai ban ganshi ba,amma karki damu my cute angle akwai kuɗi a wajena sai muyi amfani dashi mu tafi makarantar". "To yaya na" na faɗa tare da sakin murmushi. Sallama mukayi a umma muka tafi ƙarfe uku saura muka iso gida bamu sama umma a gida ba amma gidan a buɗe muka same shi. Cire uniform ɗina nayi, nayi wanka nayi salla sannan na shirya cikin uniform ɗin islamiya na fito. Ina fitowa ma yaya fawas ya fito zai tafi shagon da yake zuwa koyan ɗinki,murmushi na jefa masa cike zolaya ina faɗin. "Allah my yaya irin kyau haka anya ka duba madubi kuwa kaga irin kyan da kayi?". Na ƙarishe maganar tare da kashe masa ido ɗaya. Matsuwa yayi ya shafo ƙuncina tare da faɗin. "Haba!hibba ta kyau ya wuce wanda kikayi a yanzu na tabbatar ko gasar kyau kikaje,a haka babu abinda dazai hanaki ki cinye gasar". Turo baki nayi tare da kai masa dukan wasa a kafaɗunsa nace. "A hakanne zanci gasar kyau yaya fawas?". Na ƙarishe maganar ina duban uniform ɗin jiki na da har canza launi,suka yi daga ainihin kalar su saboda tsabar tsofan dasukayi. Ganin yanayi na daya sauya yasa yaya fawas cewa "Sosai ma kuwa ƙanwata". Dariya mukayi sosai kafin muka fito a tare sa daya rakani,har islamiyar sanna ya wuce shagonsu. ƙarfe Biyar muka tashi daga islamiya sanda na iso gida har izuwa lokacin umma bata dawo ba,uniform ɗina nacire nayi wanka sannan na fito. Na fito na shiga kitchen na fara dube-dube kozan sama abinda zanci amma babu komai a ciki,fitowa nayi na nufi daƙin umma amma ƙofar daƙin a rufe yake. Wani nauyayyan ajiyan zuciya na saka na fito ƙofar gida ina jiran dawowar Abba da yaya fawas. Can na hango ya fawas cikin sauri na isa gareshi tare da karɓan ledan dake hannun sa, cikin sakin fuska yace. "Ƙanwata umma bata dawo bane naganki a waje?". Ya tsina fuska nayi nace" e ya fawas bata dawo ba,Abba ma kuma mai dawo ba". Kallo ni yayi yana murmushi ya riƙo hannuna kafin ya shiga faɗin. "Karki damu zasu,dawo ai dare ma baiyi ko ummul-khair ɗin abban ta". Murmushi nasaka ina sunkuyar da kai na ƙasa daya kira ni da yayi da ummul-khair sai naji kamar Abba ne,domin shi kaɗai ne ke ƙira na da wannan sunan. Da haka muka ƙarisa cikin gidan tabarma na ɗauko na shimfiɗa mana,sannan na shiga kitchen na ɗauko Kofi na juye kunnun da yaya fawas ya taho mana dashi. Sannan muka fara sha muna hira,muna zaune umma ta shigo tamkar bataga ƴan Adam awajen ba tasa kai zata shiga daƙinta. Yaya fawas ne yayi saurin cewa" umma sannu da dawowa". A hankali ta juyo tare da ƙare mana kallo sannan tace. "Yauwa fawas sannun ku har ka dawo daga, shagon kenan?". Cikin jin daɗin yanda umma take masa magana yace"E wallahi umma yau da wuri na dawo". Nima da fara'ata nake faɗin"Umma tun ɗazu da muka dawo daga makaranta muka samu bakyanan". Cikin sakin fuska tace "wallahi na fita wata unguwa ne hibba ya makarantar taku?". Cikin nishaɗi na amsa mata da alhamdulillah umma. "Yauwa maman abbanta Allah ya taimaka" dukkaninmu muka amsa da amin. Tashi tayi zata shiga ɗakinta cikin sauri, maganar da yaya fawas ya fara ne yasata juyowa. "Umma wai yau ina Abba yaje ne tun safe baya gidan nan?". Kamar bazata amsa ba sai data jima a tsaye kafinta dawo ta zauna tare da faɗin. "Amma fawas ai kasan gidan nan bana sabane ko?". A hankali yaya fawas daya jinin jikinsa ya amsa da cewa. "Kiyi haƙuri umma nasan,da haka dama kawai na tambaya ne naga tun safe baya nan". Sai data turo ɗaurin ɗan kwallin ta irin ɗaurin da akewa laƙabi da ture kaga tsiya,izuwa gaban goshin ta wanda in tayi hakan ƴan daudun ta da sauran tarin,matan datayi silar rabasu da gidan iyayen su. Suke mata kirari da"Magajiya kinci dubu sai ceto,kinfi ƙarfi yaro walla sai dai baban yaro ƙadangaren bakin tulu kike abarki ki lalata ruwa,a kashe ki a fasa tulu". Chewgum ɗin dake bakin ta ta tauna da ƙarfi,sai da tayi wata ƴar ƙara kash!. Sannan ta fara warware mana zare da abawa abinda ya faru a daren jiya,wasu hawaye marasa control ne nayi sun shiga ambaliya daga idona yana sauɗa akan fuskata. Harara umma ta watsa min tana faɗin. "Dalla kaji banza marar tinani to dan ya tafi sai me?,Dama meyake tsinana miki a cikin gidan?". Kuka yaya fawas yake yi sosai muryansa Ƙasa- Ƙasa yake cewa"Haba!umma Meyasa bakya tausayawa halin da muke ciki ne?, umma mufa ƴaƴankine Abba kuma mijinki ne amma Sam k....." Watsa masa mari umma tayi hagu da dama ta ɗaura da faɗin. "Shashasha fawas har kai ka isa ka faɗamin abinda ya dace na aikata?.Gida dai nice mai biyan kuɗin hayan nan dan haka duk wanda baiji daɗin hukuncin,dana yi ba to shima sai yabar min gida". Tana kawowa nan ta miƙe ta shige ɗakinta. Ɗaura kaina nayi akan cinyoyin yaya fawas tare da sakin wani irin wahalallan kuka,mai cin rai kuka nake da iya ƙarfina ina faɗin. "Wannan wani irin rayuwa ne yaya fawas?,Meyasa mu kuma ƙaddarar mu take zuwa a haka?,Meyasa Abba zai tafi ya barmu?,Meyasa umma zata mana haka yaya fawas meyasa yaya fawas?". Ɗago kaina yayi idanunsa taf! da ƙwalla cikin sigar lallashi yake cewa. "Hibba ƙanwata ki daina kuka kinji,kukan ki na ɗagamin hankali sannan yana karyar min da zuciya naji tamkar bazan iya ba dan Allah ki daina". Muryana can ƙasa-ƙasa nace" yaya fawas shikenan fa Abba ya tafi kenan?". Komar da kaina nayi kan cinyarsa na cigaba da kukana,shima yaya fawas hawaye basu daina zuba daga idanunsa ba haka muka kwana a wajen muna kuka. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________________ Free page Page 0⃣4⃣ Washe gari na tashi da matuƙar zazzaɓi ko makaranta bamuje ba,yaya Fawas ya sanar da Umma halin danake ciki,naira hamsin ta bashi wai yaje ya siyo min paracetamol. Jikinsa sam babu kozari ya karɓa kuɗin cikin sanyin murya yaya Fawas yace "Umma inaso muyi wani magana dake". Tana daga kwance tace,"menene inajinka Fawas?". Sai daya sauƙe ajiyan numfashi kafin ya shiga faɗin. "Umma dan Allah inason nasani ne ke kika haife mu?, kuma wani laifi muka aikata miki a cikin duniyar nan wanda yasa bakya sonmu?". Cike da mamaki Umma ta juyo tana watsa masa wani irin kallo kafin tace"Fawas kamar ya bani na haifeku ba?banason surutun banza,ka wuce ka je ka sayo mata maganin". "Amma Umma muka fa ƴaƴanki ne, amma ko kaɗan mu a rayuwar mu,bamusan daɗin uwa ba haba um....." Tsawa Umma ta daka masa sai da jikinsa ya ɗau rawa,cikin zafin rai take faɗin" kafice min daga ɗaki Fawas". Jiki a sanyaye yaya Fawas ya fito daga ɗakin.gefe na yazo ya zauna cike da kulawa yace"Ƙanwata kiyi haƙuri yanzu zanje na siyo miki". Gyaɗa masa kai kawai nayi sannan ya fice.Haka rayuwa tacigaba da zuwa mana da ƙalubale iri-iri,ga tsangwaman da umma take mana Kullum hau-hawa yakeyi. Nikam kullum cikin kuka nake,rayuwa duk ta mana zafi gashi bamu da dangi a kusa balle muje wajensu. Duk dangin Abba a kano suke da zama,ita kuwa Umma duk iyayenta sun rasu inna (kakarta) ma ta Daɗe da rasuwa. Yaya Fawas kuma dangin mahaifinsa ƴan nijar ne,koda sukazo nigeria a azare suke na jahar bauchi. Haka muka cigaba da rayuwa abinci ma umma sai jifa-jifa take bamu, ahaka har yaya Fawas ya gama secondary school lokacin ni kuma zan shiga ss 2. Cikin ikon Allah yasama admission a university of Maiduguri (unimaid),course ɗin daya kasance burinsa cikin ikon Allah shiya samu mass communication. Nan Umma tace"ita bazata iya cigaba da mana dawainiyar karatun muna,sai dai ɗaya daga cikinmu ya haƙura ta cigaba da biyawa ɗaya". Yaya Fawas yace "shi ya haƙura zai cigaba da zuwa shagon dayake zuwa koyan ɗinki ni ta cigaba da biya min". Ranan nayi kuka daya zarce a misalta shi na yadda naka sai naka.Nace" A'a yaya Fawas nina haƙura da karatun kai kayi". Kamo hannu na yayi yana hawaye yana faɗin"A'a Hibba ke kiyi burin Abba ne,muyi karatu duk da kasancewar Abba ba mahaifina ba amma bai taɓa nuna bambamci tsakani na dake ba,sai yanzu dan bayanan zan shiga tsakanin ki da burinsa my cute angle kiyi karatu ki cikawa Abba burinsa kinji Ummul-khair ɗin Abbanta". Kallon shi kawai nakeyi ƙwalla nata gudana a saman kunci na, bakina na rawa nace"Nagode yaya Fawas In sha Allah bazan baka kunya ba zan maida hankali ga karatu na". Shafo fuska na yayi tare da sakin wani murmushi wanda yafi kuka ciwo da raɗaɗi yace "yauwa ƙanwata". Haka yaya awas ya sadaukar,da burinsa nayin karatu saboda ni nayi. Burin yaya Fawas ɗaya ne a duniya ya zama dan jarida dan haka,nasa a raina matuƙar ina numfashi a cikin duniya sai na tabbatar da wannan,burin bai mutu ba cikin zuciyar yata Fawas ba. Lokacin da mukayi jamb mass communication na zaɓa a matsayin course ɗin danake son karanta,a duk choice huɗu na zaɓar institution da jamb ɗin ke bayarwa. Haka yaya Fawas ya cigaba da zuwa shagon ɗinki,har shima ya gware a sana'ar. Haka na gama secondary school na cikin ikon Allah na sama admission a yobe state university (YSU),na koma sama course ɗin danake so. Murna wajen Rabin jikina yaya fawas ba'a magana,dan lokacin tafiyata jami'a tayi,kusan komai yaya Fawas ne ya siyamin hatta sutura sai daya sauya min.Dan yanzu alhamdulilla yana samu sosai a shagonsu. Ranar dazan tafi tun safe na gama shiri na,na fito da kayayyakina ƙofan gida Ina tsaye yaya Fawas ya shigo fuskarshi da fara'a yace" A'a ysu student har kin fito"?. Murmushi na saka nace"E wallahi yaya fawas umma ma nake jira,ta dawo muyi sallama dan tun ɗazu data fita har yanzu bata dawo ba". "Haba!ƙanwata kinsan sai dare zata dawo,inki kace zaki tsaya jiranta zaki bata lokacin ki tafi kawai inta dawo sai na faɗa mata kin tafi". Yaya Fawas ya faɗa yana riƙo hannu na. Nace " To ya fawas amma Abba fa.....". Cikin sauri yasa hannun sa ya rufemin baki,yana faɗin"Hibba Abba zai dawo gare mu inajin haka ajikina". Wata leda ya Ciro daga aljihunsa, ya miƙamin Hannuna na rawa na karɓa na buɓe ledar,sabuwar wayace dal! ƙirar Android, kallon shi nake. Ina tambayar ta waye? Murmushi ya saka kafin yace"Ƙanwata naki ne kwanan nan muna samu ɗinkuna sosai a shago,shine na tara kuɗin da'ake sallama ta na haɗa da wanda umma ta bayar na biya miki registration sannan na miki wannan siyayyar,shine sauran na saya miki wannan wayar dan inki tafi in dinga jin muryarki my cute angle ko bakya so ne?". Bansan sanda hawaye suka fara zubomin ba,wayar ta burge ni duk da ba wata mai tsada bace hugging ɗin sa nayi cikin kuka nake cewa. "Nagode yayana Allah ya ƙara buɗi Allah yasaka maka da gidan aljanna,Yaya Fawas kai kaɗai nake dashi a duniyar nan bayan abba na,ina sonka yayana". Ɗagoni yayi yana faɗin"Hibba nima inason ki,inki tafi ki kulamin da kanki". Sausauta muryar shi yayi sannan ya cigaba da cewa"Ki rufamin asiri Dan Allah hibba kiyi abinda ya kaiki makarantar nan kinji my cute angle?". Yanda yayi maganar sai danaji tausayin sa nace" In sha Allah yaya Fawas bazan baka kunya ba" "Yauwa ƙanwata sannan banda biyewa samari kiyi abinda yakaiki". Murmushi nayi nace "Yo a ni yaya fawas ko aure zanyi,to sai wanda ka zaɓar min balle har na fara kula wani ba tare da Sanin ka ba". Shima murmushin ya maido min saboda yanda nayi maganar cike da shagwaba. Kuɗi ya Ciro daga aljihun sa 10k ya miƙo min tare da faɗin"Hibba ga wannan ki riƙe a wajenki". Wasu hawaye ne suka cikomin ido nace "nagode yayana". Share min hawayen ya farayi da hannun shi yana cewa."Ƙanwata ki daina kuka da kinsa yanda nakeji a zuciya na idan naga hawaye na zuba daga idanun ki,to dakin tausayamin ki daina,inki na haka sai naji kamar na kasa riƙewa Abba ke.Yanzu ki tashi ki tafi har yamma ta miki akwai yayan wani abokina lecturer ne a school ɗin munyi magana dashi zai ringa kulamin dake,ga numbern sa bari nasa miki". Wayar daya bani ya karɓa ya kunna ta yasamin number sannan shima yasamin nasa numbern daman ya sama min sim a cikin ta Har motor park yaya Fawas ya rakani sannan ya juyo. Ina isa cikin ysu na kalli fuskar wayata Wanda ya nuna ƙarfe goma da mintin arba'in. Lalle kam jami'a(freedom life),jama'a kala-kala kowa sai harkan gabansa yakeyi. Hostel naƙarisa daman yaya Fawas yagama min komai na registration, nashiga room ɗinmu. Mu huɗune a room ɗin tima,zubaida sai shahida zubaida ƴar gombe ce tima kuwa ƴar geidam ce shahida ce kawai ƴar potiskum. Sannan itace department ɗinmu yazo ɗaya da ita,Dan tima chemistry department take zubaida kuwa tana political science department. Sa yamma muka fito zamuje cafterian dake cikin school ɗin,makarantar babba ne sosai Dan nasha kallo. Tare muka fito dasu tima,indomie mukayi order cikin nishaɗi muka faraci inka ganmu zaka rantse mun jima da nisanin juna. Cikin haka yaya Fawas ya kirani hira mukayi sosa kafin mukayi sallama. Hostel muka wuce damuka gama Dan a lokacin bamu fara lectures ba. Sai da mukayi kwana uku da zuwa sannan muka fara lectures. Ranar da wuri muka shirya nida shahida muka fito,dan munada lectures ɗin 8:00 to 10:00am sannan zamu fito daga lectures ɗin. Sosai na maida hankali ga lectures ɗin, lecturer ɗin macece hakan nan kawai naji ta burge ni muna fitowa. Wayata na ciro daga cikin jaka ta na shiga dialing numbern lecturern da yaya fawas ya bani. Sai da kiran ya kusa tsinkewa sannan ya ɗaga,gaishe shi nayi ban masa wani dogon bayanin ni wacece ba,yace ya ganeni dama sunyi maganar da yaya fawas ya kwantamin office ɗin sa yace nazo. Tare da shahida mukaje sai damukayi knocking sannan ya bamu iznin shigowa,yana duba wasu takardu sanda muka shigo. Zama muka yi har ya gama sannan ya dago ya kallemu,sunan sane ajiye kan teburinsa DR.BASHIR MUHAMMAD AUWAL. Gaishe muka karayi ya amsa sannan yace "Hibba ko?" "E itace". Sannan ya cigaba da cewa"Muyi magana da fawas so duk da ni ƴan a chemistry department,nakewa lectures amma duk abinda ya shige miki duhu ki sanar dani in sha Allah zan yi iya ƙoƙarina". A nitse nace "nagode". Cikin yanayinsa na barkwanci Dana karanta yace "sunana bashir". Taƙaiceccen murmushi nayi kafin nace,"To nagode yaya bashir". Sannan muka fita,Haka rayuwa ta cigaba da tafiya nidai karatu na nasa a gaba baji ba ƙwauƙwautawa. A lokuta dama ina tuna furcin ya fawas"HIBBA DAN ALLAH Ki RUFAMIN ASIRI KIYI ABINDA YA KAI KI". Sam samari basa gabana Dan Bana ma sakar musu fuskar da har zasu min magana,kullum su tima cewa suke. "Wallahi ke hibba har yanzu baki waye ba". Bana damuwa da abinda suke faɗi dama wasu daga cikin course mate ɗin mu da suka ganin kamar,girman kai ke sakani yin haka. Na tabbatar dasun san irin ƙalubalen dana fuskan ta kafin su ganni a cikin wannan jami'ar,da bazan sumin wannan maganar ba. Bazan taɓa manta wani safiyar asabar ba,tin daga wannan ranar ƙaddarar rayuwa ta sauya. Ina kwance a hostel shahida tace inrakata ta sayo recharge card doguwar rigar abaya ce ajikina. Gyalen rigar nayi rolling akaina muka fito,muna tafe muna hira har muka isa wajen. 5 hundred shahida ta Ciro daga Jakarta ta mik'awa Mai shagon tace,"Gashi a bamu card na mtn na Dari bibiyu". Kallonta nayi nace"Kedawa na ɗari bibiyu?A'a wallahi shahida kibar kuɗin ki karki ɗaurawa kanki wata wahala". "Haba Hibba babu wata wahala,kedai sai dai inkin Rena ne to".Shahida ta faɗa,Murmushi na saka kafin nace,"To nagode". Wata mota ce tazo ta wuce ta gefenmu, tayi parking cikin parking space aka tanada cikin compound ɗin school. Buɗe ƙofar motar akayi tare da sauƙo da ƙafafunsa waje sannan shima ya fito Milk ɗin shadda ne ajikinsa,tsayin rigar dai-dai gwiwar sa ya ɗaura brown ɗin agogo a damtsen hannun sa. Kansa babu hula yayin da tarin sumar fuskar sa wanda tasha gyara sa sheƙi takeyi,haka nan sun kwanta luf a saman fuskarsa. Idanunsa sun boye cikin wani farin glass,sai wani ni'imtaccen ƙamshi ne yake tashi daga cikinsa. A hankali yake tafiya cikin cikakken nutsuwa ya nufo inda muke tsaye. ƙamshin shine ya bugi hancina, nan take na juya domin ganin Wanda yake tafe da wannan ƙamshin. Karaf muka haɗa ido dashi,sai a wannan lokacin nasama damar ƙarewa halittar fuskansa kallo. Round face gareshi skin color ɗinshi black ne amma mai irin kyau ɗin nan ne.Dan kowani mai farin fatan bazai nuna mishi kyan skin ba. Idanunsa manya ne ma'abota haske,yanada yalwan gashin eyes lid da eyes lashes bakin nashi Dan dai-dai. Yana da madaidaicin tsayi,lumshe idona nayi yayin da ƙamshin sa ke ƙara tsara ƙofofin hancina. Da sallama ya ƙariso wajen,a hankali yake motsa dan wannan bakin nasa yana tambayar mai shagon akwa recharge card na airtel?.Da rawan jiki Ma shagon yake cewa e akwai. Tsaki na saka nacewa shahida wacce ta naga shagalta da kallon wannan guy ɗin"Dan Allah ki karɓa chanjin mu tafi". Sai a sannan ta ɗauke idon ta daga kallon dake mishi Tace" Malam bamu chanjimu mu tafi". "Wallahi ba canji, sai dai kuje anjima sai Ku dawo Ku karba".Mai shagon ya faɗa lokacin dayake yagowa wannan guy ɗin recharge card ɗin. Dafe goshin ta shahida tayi tace"to ai zamuyi amfani da canjin ne yanzu ya za'ayi?". Sai a lokacin sannan guy ɗin ya ɗago kai daga latsa wayarsa da yakeyi,ya kalle mu murmushi yayi cikin sanyin voice ɗin sa yake cewa mai shagon "Kaga malam ka basu kuɗin Nasu kawaesai ka haɗa kuɗin card ɗin,da suka saya da nawa zan biya". Cikin fara'a shahida tace,"Mungode bawan Allah". Taƙaitaccen murmushi kawai ya saka sannan ya maida kallon sa ga wayarsa ba tare da yace da ita komai ba. Miƙowa shahida five hundred ɗin ta Mai shagon yayi,karɓa tayi tare da ƙara cewa,"mun gode bawan Allah". Sai a wannan karon ya ɗago kansa a hankali yana cewa"karki damu amma ita ƙawarta ki bata magana ne?". Washe baki shahida tayi Shahida tace" La!hibba ai wallahi haka take bata da yawan magana". Maimaita sunan kawai yakeyi Hibba!Hibba!!"Sunan ya burge ni ni kuma sunana habib bari nabaku complementary card ɗina". Wani card ya Ciro daga aljihunsa mai ɗauke da sunanan sa da phone numbernsa,ya miƙawa shahida karɓa tayi tare da ƙara yi masa godiya sannan muka bar wajen. Tsaki shahida tasaka tana faɗin"Wallahi hibba halinki yana bani mamaki ke Sam a rayuwarki bakya sakewa mutane fuska,to a haka wazai ce yanasonki?". Murmushi nayi kafin nace"Shahida kenan inda ace kinsan irin ƙalubalen dana,fuskanta kafin nazo nan da bazaki min haka ba karatu nazoyi ba sakewa samari fuska ba". "Amma fara'a ma ai wani abune, ko at list ki nuna mishi godiyanki akan alkhairin daya mana". A harsale nace,"shahida wai rokansa muka yi ne, ra'ayin kansa ne fa".Shiru shahida tayi dan tasan halina. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________________ Free page Page 5⃣ Hostel muka wuce,nasa recharge card ɗin da shahida ta saya mana na kira yaya Fawas. Ringing biyu ya ɗauka cike da so da kuma ƙaunar juna muka gaisa.Nace "ya Umma?". "Umma lafiyanta kalau yanzu ina shago,inna koma gida da dare zan haɗa Ku Ku gaisa". Cewar yaya Fawas Ajiyan zuciya na saka kafin nace,"yaya Fawas har yanzu Abba baizo gida ba?". Shima ajiyan zuciyar ya saka yana cewa,"Hibba har yanzu babu labarin Abba,yau kusan shekara uku kenan har baffa na kira ko yaje wajensu a kano amma suka shaida min bai zoba". A hankali naji hawaye yana bin fuskana. Bakina na rawa nace" Yaya Fawas yanzu shikenan ba zamu sake ganin Abba ba kenan na shiga uku nikam yaya Fawas". Wani kuka Mai ƙarfi na saka tare da kifa, kaina akan pillow ina fitar da numfashi a hankali. "Hibba ki daina kuka,matuƙar Abba yana numfashi a ciki duniya zai dawo garemu komai daren da daɗewa ki daina kuka kinji ƙanwata kukan ki na ɗaga min hankali"yaya Fawas ya faɗa cike da kulawa. Cikin dushashewar murya nace "Na daina yaya Fawas na daina kaji yayana".Cikin jin daɗin furci na yace,"yauwa ƙanwata". Yayin dayake hana hawayen dake cike fal a idonsa zubowa. Da haka muka cigaba da hirar mu,har sai da aka kira sallar magrib sannan mukayi sallama. Alwala nayi na gabatar da sallan magriba ina zaune kan sallayata shahida ta shigo tana cewa,"Hibba Dan Allah ina wayarki?". "Ga tanan meza kiyi da ita?".Matsowa tayi ta ɗauki wayar daga gaba na tana faɗin,"Wani waya zanyi mai muhimmanci wayata kuma ta mutu babu caji". Ban bata amsa ba, na cigaba da tasbihin da nakeyi yayin da ta koma ta kwanta akan gado tana wayanta. Suna na naji Shahida tana kira hibba!hibba!! Hibba!!!a harzance na juyo ina faɗin lafiya?. Ƙarisowa tayi gaba na tare da miƙamin wayan Tace,"Gashi HABIB ne zaku gaisa". Cike da rashin fahimta nake tambayar ta "waye kuma HABIB?". Tsaki ta saka kafin tace"Habib mana wannan guy ɗin daya saya mana recharge card ɗazu. Harara na watsa mata ina cewa"Haba Shahida daga haɗuwa da mutum sau daya shine har zaki kirashi wannan wani irin tusa Kaine?to nidai bazan gaisa da kowa ba". Inajinsa daga cikin wayar yana cewa, "just leave her alone,kar ki takura mata just extent my greeting to her". Bansan sanda nasaki wata doguwar tsaki bana,Fizge wayata nayi daga hannun Shahida "Daman wannan shine kiran dazakiyin har kike kiran sa mai muhimmamci?". Juya idanunta tayi cikin wani nishaɗantaccen murmushi tace"Hibba bazaki gane bane,guy ɗin ya haɗu over nake gaya miki he is very nice and cool". Cike da takaici nace"Shahida kinyi nisa Allah ya taro ki ". Ta bangaren Habib kuwa yana kashe wayar ya cilla ta kan bed ɗinsa sannan shima ya kwanta,yana ƙarewa ceiling ɗin bedroom ɗin nasa kallo. Da ƙarfi ya cije lips ɗinsa tare da shafa sumar fuskarta,sannan ya dafe ƙirjinsa saboda matsanancin bugun da take masa. Wayarsa ce ta fara ringing gani sunan DR BASHIR ya bayyana cikin screen ɗin wayar yasa shi sakin tsaki sannan ya ture wayar gefe. Ƙara kira akayi a karo na biyu,sai da ƙiran yakusa tsinkewa sannan ya ɗaga Koda ya ɗaga shiru yayi baiyi magana ba. "Afuwan mutumi na,wallahi fita ce ta same ni ta gaggawa shiyasa daka zu baka same ni ba".cewar Bashir A hankali cikin yanayinsa na rashin son yi magana mai tsayi yace"uhmm". Dr bashir yace "To yanzu yaushe zaka wuce katsina nan?". " Next tomorrow in sha Allah"ya faɗa yana gyara kwanciyar sa. "To Dan Allah gobe ka same ni a cikin school wallahi banason ka koma katsinan nan ne Baku haɗu da maryam Ba". Cikin ƙosawa da sauraron surutun sa Habib yace"okay Allah yakaimu goben and then if u wish ka ƙara ficewar ka nazo ban sameka ba kaga mezai faru". Yana kawowa nan ya kashe wayar yana sauƙe numfashi,can ya tashi ya shiga bathroom yayi wanka yayi alwala sannan ya fito ɗaure da towel a waits ɗinsa sai kuma wani ƙarami yana goge kansa dashi. Doguwar bakar jallabiya yasaka da hular ta,sai ka rantse da allah balarabe ne. Masallaci ya fito yaje nan ya zauna sai da akayi sallan isha'i sannan ya dawo wani part naga ya shiga Wanda yafi nasa girma. Da sallama ya shigo cikin palon Wanda aka ƙawata shi da abubuwan more rayuwa,kallo daya zaka yiwa furnitures ɗin dasuke falon Masu launin shuɗi ka tabbatar da an narka kuɗi wajen ƙawata falon. Wata matace zaune akan lausassun kujerun wacce zata kai kimanin shekaru shitta da biyar a duniya,ta amsa sallamar cike da fara'a. Kusa da ita ya zauna yana faɗin"Sannu da hutawa Granny". "Yauwa Babban mutum ga can abincin ka can akan dinning". Ya tsina fuska yayi yana ƙoƙarin ciro wayar sa daga aljihun sa Yace,"Bashi Granny banajin yunwa sa zuwa anjima zanci". Ba ta kula shi ba ta miƙe izuwa dinning arean ta zuba mishi abincin a plate,masa ne na farar shinkafa da miyar alayyahu Wanda yaji nama da kifi. Sannan ta tsiyaya mishi sanyanyan lemon kunnun a'ya a Kofi. A gabanshi ta dige plate ɗin ta zauna tana cewa" To gashinan oya kacinye mishi gaba ɗaya". Zaro idanunsa yayi yana faɗin,"Granny ina zankai dukka wannan abincin?". Ganin bashi da niyyar ci yasa ta fizge wayar sa ta ajiye a gefe. Da kanta ta dinga bashi abincin sai da tabbatar data cika mishi cikinsa sannan ta kyale shi. Sun ɗan taɓa hira da ita kafin ya tashi ya tafi part ɗinsa ya kwanta, bayan ya gama jero nafilfilinsa. WANENE HABIB? Habib Abubakar Galadima shine cikakken sunansa. Mahaifinsa alhaji Abubakar sanannan ɗan kasuwa ne bama a iya Nigeria ba gaba ɗaya faɗin Africa sunan sa ya zaga,kusan watace jaha a Nigeria yana company a jahar. Kasuwanci shine gadon gidansuSu uku ne a wajen mahaifansu Abubakar shine babban su,halima sannan suraj. Halima tun tana primary school Allah yakarɓi abinsa. Sun taso cikin kulawar iyayensu alhaji Galadima da Haj.hauwa wacce suke ƙira da Granny. A bangaren business Abubakar yayi karatum sa shi kuma suraj engeering ya karanta.Bayan kammala karatun sune suka dawo gida Nigeria. Inda Abubakar ya cigaba da kula da companies ɗin mahaifinsu.A nijer ya haɗu da mahaifiyar Habib ya aure ta Suka dawo Nigeria da zama. Bayan wani lokacin Allah yayiwa alhaji Galadima rasuwa,sunyi jimami sosai da wannan babban rashin dasukayi. Nan fa kula da kasuwancin mahaifinsun ya dawo hannun abubakar. Bayan wani lokaci Suraj ma yayi aure a katsina ya zauna da matarsa,kasancewar acan yake aikinsa. Amma shi Abubakar a damaturu yake tare da mahaifiyar su. Habib ne ɗansu na farko Wanda yaci sunan kakan sa na wajen uwa, daga shi kuma haihuwar ta tsaya. Tun haihuwar Habib aka haife shi da wannan cutar ta CARDIOMYOPATHY ma'ana raunin zuciya. Hakan yasanya tausayin sa a zukatan kowa,tashi ƙaddaran kuma kenan a yanda tazo. An mishi aiki a zuciyarsa aka bashi wasu magungunan dazasu taimaka wajen saisaita bugun zuciyar tashi. Sosai ahalin nasan suke kiyaye duk wani abin dazuka san sai ɓata masa rai. Simple life Habib ke yi dan sanin dayayi masu cuta irin tashi basu fiye tsawon rai a duniya ba,an masa aiki a zuciyar sa tare da jaddawa iyayen nasa suka kasance suna,masu Samar masa da farin-ciki Sosai duk ahalin suke gwada masa ƙauna. Suraj kuwa ƴaƴansa biyu sayyid Wanda yaci sunan Abubakar,sai kuma Yasira Wanda taci sunan mahaifiyar su. Habib yana da shekaru huɗu,Allah yayi wa mahaifansa rasuwa,a hanyar dawowarsu daga nijer. Nan riƙonsa tare da tarbiyar sa suka dawo hannun Granny. A jami'ar Abubakar Tabawa Ɓalewa ta jahar bauchin yakubu yayi karatun sa fannin kasuwanci,yana dawowa kuwa ya karɓi ragaman kasuwancin family ɗin nasu. Wannan kenan. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________________ Free page Page 6⃣ Washe gari bamu da lectures ɗin safe sai na ƙarfe goma. Ina zaune a hostel inna duba hand out,waya ta ta fara ringing, sunan yaya Bashir ne ya bayyana cikin screen ɗin wayar. Naɗaga wayar tare da sallama ya amsa,sannan na gaishe shi ya amsa min. "kizo office ɗina akwai sakon da fawas ya aiko miki sai kizo ki karɓa,Dan fita nake son nayi". " To"kawai na amsa dashi sannan na kashe wayar. Gyalena na ɗauka milk color na bulluɓa a kafaɗa ta,Shigar atamfa ce a jikina simple ɗinki aka mata bamai taƙurawa ba. Yaya Fawas da kansa ya ɗinka min ita, an mata adon black stone a jikin ta. Wayata na ɗauka na fito izuwa office ɗin yaya Bashir,lokacin Dana kusa office ɗin shi kuma yana fito wa da sauri. "Sorry Hibba ki shiga ki jirani ina zuwa,akwai wani aboki na dazan taro shi yanzu".Dr Bashir ya faɗa lokaci dayake wucewa. Office ɗin nashiga na zauna ina latsa waya ta.Ta bangaren Habib kuwa Daren jiya dakyar ya samu ya runtsa. Washe gari kuwa sa wajajen 9:00 na safe ya samu ya farka. Yana tashi ya faɗa bathroom wanka yayi,as usual ya fito ɗaure da towel a waits ɗinsa da kuma wani ƙarami yana goge sumar kansa dashi yana dumping ruwan jikinsa. Gaban dressing mirror ya nufa ya fara shafe laulausar fatar sa, da mayuka gyara sumar sa yayi tare da shafa musu mai ai kuwa tunin suka hau sheƙi. Wata dakakkiyar shada baƙa ya fito da ita wacce aka yiwa aikin surfani,da Golding ɗin zare ɗinkin ya ƙawatu sosai. Ya saka sannan ya saka hular sa ma baƙa ce da rantsin Golding ajiki sannan ya saka a tsintsiyar hannunsa . Sannan ya feshe jikinsa da daddaɗan turare,kallon kansa yayi a cikin madubin Wanda kayan daya sa suka ƙara fallasar da sirrin tsan-tsan kyan halittarsa shi kanka yasan yayi kyau ba ƙarya. Phone ɗinsa ya ɗauka da key ɗin motar sa,ya fito ya nufa part ɗin Granny bai iske ta a falon ba. House maid ɗinta ne kawai suke ta gyare-gyare. Suna ganinsa Duk suka zube suna gaishe shi cike da girmamawa,kanshi kawai yake gyaɗa musu. Ɗaya daga cikinsu wacce tafisu manyan ta ya zubawa ido.A hankali yake motsa Dan ƙarami bakinsa yake cewa "Haba! Iya Bana hanaki Duk wani aikin wahala ba a cikin gidan nan ki bari sauran ma'aikatan suyi mana,saboda haka fa na ƙaru wasu ma'aikatan". Murmushi tayi wacce ya kira da Iya tana ƙara jaddada nutsuwa da sanin ya kamata irin ta Habib ɗin. "Babban mutum banason zaman haka ne,shiyasa nace gwara ina Dan motsa jikina".cewar Iya Langwabar da kai yayi yace,"To iya nidai banason kina wahalar da kanki,ina Granny?" Ta amsa masa datana ɗaki.Direct upstairs ya nufa inda ɗakin Granny yake. Tana kan sallaya ta iddar da sallan walaha kenan,ya shigo kusa da ita ya zauna cikin sanyayyiyar voice ɗinsa ya gaishe ta ta amsa. Kallo ta tsare shi dashi yayin da taga fuskar mahaifinsa ya bayyana akan fuskar tashi. Turo baki yayi ganin irin kallon datake masa yana cewa,"Tsohuwa wannan kallon fa?to nifa kar ki lashe ni". Murmushi tayi kafin tace,"ina zuwa haka?" "Zanje cikin YSU ne wajen Bashir,jiya naje ban same shi ba". Yana gama faɗar haka ya miƙe zai fita Muryar Granny ne ya dakatar dashi daga fitan. " Breakfast ɗin ka fa?" Yana shirin murda handle ɗin kofar ɗakin yace,"A kaimin part ɗin,sai na dawo zanci". Har zai fita sai kuma ya juyo da faɗin, "Yauwa Granny Dan Allah banason iya ta sake wani aiki a cikin gidan nan,Bana jin daɗi inna zo naganta tana wasu aiyukan buda da irin shekarunta". "Nima ba yanda banyi da ita ba amma ta ƙi dainawa amma karka damu zan ƙara mata magana".cewar Granny "To"Yace yayin da yake fita daga ɗakin. Fitowa yayi ya nufi parking lot,wata sabuwar mota dal ƙiran range rover ash color ya shiga,yayin da gate man ya kwangale masa gate ɗin ya fita. Yana shiga cikin YSU yayi parking mota sa,sannan ya buɗe ƙofar motar ya saƙalo ƙafafunsa wajen,ba tare da ya fito ba. Wayar sa ya ɗauka ya shiga dialing numbern bashir,ringing ɗaya ya ɗauka yana tambayar yana inane? yace "gani a parking space". Kashe wayar yayi dai-dai lokacin daya hangi bashir,ya nufo shi sannan ya fito daga cikin motar. Da fara'a Dr bashir ya iso,suka rumgume juna suna farin ciki Office ɗin Dr bashir suka nufa. Yayin da Duk inda suka wuce mutane ke bin habib da kallo,yan mata kuwa kowacce da rawan kanta suka fara tasowa suna gaishe da Dr bashir da kuma habib,Dr bashir ne kawai Mai amsawa. Har suka isa office ɗin,turo kofar suka yi tare da sallama a bakinsu,nan take naji zuciya ta ta fara bugawa da ƙarfi sallamar na amsa, Sannan suka ƙarisa shigowa cikin office ɗin. Dr bashir ya zauna a kujerarsa shi kuwa habib ya zauna a kujerar da take facing ɗina. Tunda ya shigo office ɗin zuciyar sa take bugawa,muna haɗa ido kuwa bugawar zuciyar tashi ta tsananta. Kallo na yake yi da sexy eyes ɗinsa masu kashewa mutum jiki. Dr bashir yace,"Sorry hibba na barki kinata jira". Sunkuyar da kaina nayi saboda izuwa yanzu na fara tsorita da irin kallon da yakemin nace,"La ba komai yaya bashir". "Bari na ɗauko miki saƙon na bari a mota".Dr bashir ya faɗa yayin dayake ficewa daga office ɗin. Kamar na ƙwala ihu naji da yaya bashir ya fita,ya barni dashi. Na daure nace"To yaya bashir"Sannan ya fita yana cewa. "Abokina sorry fa bari na ɗauko mata saƙo".Yana kawowa nan ya fita. Kamar jira yake yi yaya bashir ya fita yayi magana,cikin sanyayyiyar voice ɗinsa da na ji ta,tun daga toe ɗin na har cikin head ɗina Yace ,"Sannunki". Ba tare Dana dago na kalle shi nace,"Yauwa sannu". Kallona ya cigaba dayi hakan, ya ƙara tsorita ne.cike da tuhuma na ɗago kaina nace,"malam lafiya irin wannan kallon?". Murmushi yayi Wanda sai da fararen haƙwaransa suka bayyana. "HIBBA ko? Shine jiya gaisawa ma muyi a wayar shahida kika ƙi ko?". Cike da faɗa na ke cewa"Meye haɗina da kai da har zamu gaisa". " Amma ai ke musulmacce addinmu ne ya haɗa mu". Harara na watsa mishi na cigaba da kallon wayata. Shigowar yaya bashir,ya dakatar dashi daga maganar daya yi niyya. Ledodi yaya bashir ya shigo dashi ya ajiye a gaba yana cewa,"Yauwa hibba ga saƙon naki". Godiya nashi sannan na ɗauki ledar zan fita.Ina ɗaga ledar ta tsinke nan kuwa kayan ciki suka zubo ƙasa,kayan tea ne da abubuwan da dan makaranta kan iya buƙata na yau da kullum. Kamar na fasa ihu haka na fara tattare kayan,A hankali ya miƙe daga inda yake zaune ya fara tattrare kayan shima. Wata Leda yaya bashir ya miɗomin na zuba kayan aciki na fita. Hostel na wuce raina Duk baya min daɗi,Ina isa na ƙira yaya fawas ina mishi godiya har umma yabawa wayar muka gaisa da ita sama-sama.duk da bawani magana mukayi da ita sosai amma naji daɗi rabo na dajin muryan ta tun bayan zuwa na school. Hira mukayi sosai da yaya fawas nan yake faɗamin shima zai jona FCE potiskum dan yanzu alhamdulilla yana samu sosai a sana'ar sa na ɗinki,fatan alkhairi na mishi sannan mukayi sallama. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Free page Page 7⃣ kallo yabi bayana dashi har na fice daga cikin office ɗin,kallon shi Dr bashir yayi tare da sakin murmushi,sannan ya kawar da kansa gefe. Dan hararan shi habib yayi yace, "Wai meye ne haka malam?". "To ai kai zan tambaya habib".Ajiyan zuciya habib yasaka kana yace"kaga malam ka tashi mu tafi inda zamuje,tun kafin na canja ra'ayi kuma". Cikin sauri Dr bashir ya mik'e suka fita.Ina zaune a hostel shahida,ta shigo Dan harararta nayi tare da gyara kwanciya ta, sannan nace,"ɗazu naga mutuminki a office d'in yaya bashir". Washe baki tayi tace "Ayya my Prince,kin tinamin ma bari na kira shi". Tima dake zaune tana cin abinci,tace "wai ke shahida wanene wannan habib d'in?". Juya idanunta shahida tayi Wanda izuwa yanzu,na tabbatar haka tana yin shine a Duk lokacin da take cikin farin ciki. "ina ruwanki yar sa ido". Cewar shahida Taƙaitaccen murmushi Tima ya saka kafin tace,"To Allah ya ki hakuri bani na kar zomon ba rataya aka bani". Nidai dariya nake ta musu.cikin kwanacin nan muka fara exams sosai na maida hankali ga karatu. Ana haka habib ya koma katsina gidan ƙanin mahaifinsa suraj,Dan anan katsina ta dikko ɗakin kara manyan companies ɗinsu suke. Tun daya tafi ya kasa sukuni,kullum sai ya kira wayar hibba yayin da ita kuma bakin ta a baya fasa fadɗa masa,baƙaƙen maganganu. Nayi tinanin ina tura mishi numbern shahida, zai daina kira na Dan a zato na ya ɗauka wannan layin tane,Dan da shi ta kira at a first time dasukayi waya.sauran mu exams biy malamai suka tafi yajin aiki. Sosai nayi takaicin haka ma students da dama,duk haka muka fara tattare kayayyakin mu. ____________KATSINA__________ Zaune habeeb yake a office ɗinsa, yana duba wani file dake gabansa. Ajiyan zuciya ya saka mai ƙarfi tare da dafe ƙirjinsa saboda matsanancin bugun da take masa. Numfashi ya furzar tare da dafe kansa,tabbas ko shi kansa ba zai iya fasalta irin yanayin da shiga ba saboda wannan yariyar ba. Wayar sa ce ta fara ringing, ba tare daya duba Wanda ya kira ba ya kara wayar a kunnensa. Shiru yayi baiyi magana ba,gada dayan gefen Dr bashir ne ke ce"Mutumi na yane?". Kamar ba zai iya buɗe bakinsa yayi magana ba yace,"normal bashir ya school ɗin naku?". "Normal abokina mun shiga strike ai gobe ma,students za su watse wallahi". Cewar bashir Kamar an zabure shi ya miƙe da cewa"Okay nima zan zo damaturun kafin goben". Bai jira amsar da bashir zai bashi ba ya kashe wayar,key ɗinsa ya ɗauka ya fito daga office ɗin da sauri. Parking lot ya nufa yayin da drivern sa ya taso da wuri ɗaga masa hannu yayi yana cewa,"No ni kadai zan fita". A guje ya figi mortar yanufi gida gida,yana isa direct side ɗinsa ya nufa ya faɗa bathroom,a gurguje yayi Wanda ya fito dumping ruwan jikinsa yayi. Yasaka kayansa brown ɗin shadda sannan ya fito,side ɗin matar uncle suraj(ummi)ya shiga. Tana zaune a falo da sauri-sauri yake cewa,"Ummi zanje damaturu yanzu". Juyowa tayi tana fuskantar sa tace," Habib lafiya da yamman nan?". Cikin ƙoasawa dasan ya tafi ɗin yace,"lafiya kalau ummi akwai wannan company na groundnuts oil ɗin nan, da zamu buɗe,nake son naje naga yanda abubuwan suke tafiya". Fɗaɗa fara'ar ta ummi tayi kafin ta shiga faɗin"To habib Allah ya kiyaye hanya,ka gaishe min da grannyn inka je". "To"Kawai yace lokacin da yake, ficewa daga falon yana jin yasira nacewa,"Hamma habib zan rakaka".Amma ko ta kanta baiyi ba ya fice. A guje yake driving motar,ƙarfe sha ɗaya da wasu mintina ya iso cikin garin damaturu duk da gudun dayake zugawa,bura-bura estate ya nufa inda gidan granny yake. Yana isowa ya nufi part ɗnsa wanka yayi ya fito yayi sallolin da ake binsa,sannan ya jawo wayarsa jawo dialing numbern da yayi saving da HIBBA ya shiga yi. Ina zaune a hostel ina harhaɗa kaya na,wayata ta fara ringing na ɗaga,shiru yayi baiyi magana ba. Nace" hello".Sai a sannan yayi magana yace, "Yakike?"."Lafiya" na amsa dashi. Daga nan bai sake cewa komai ba,komai bai kashe wayar ba. Tsaki nasaka nace,"Dan Allah malam in baka da abin fad'a to ni ina da abunyi". Zaffafar Ajiyan zuciya ya saka sannan yace,"Okay sorry gobe zaku tafi ko?". Sanyaye na amsa da e, "Ayya Dan Allah goben before Ku tafi inason magana dake".Ya faɗa yana ƙara sau-sauta muryar sa. "okay"kawai nace tare da kashe wayata,na cigaba da haɗa kayana. Ajiye wayar yayi kan bed,sannan shima ya kwanta nan kuwa bacci yayi gaba dashi ko part ɗin granny bai samu ya leka ba. Washe gari da wuri ya tashi,wanka yayi ya shirya cikin nevy blue ɗin shadda wacce tasha aikin surfani da light blue ɗin zare,hular kansa ma da rantsin blue ajikin sa. Gyara sumar sa yayi tare da shafa musu mai sannan ya feshe jikinsa da turaren sa na lalatul sahara. Wayar sa ya ɗauka da key ɗinsa ya fito ta shiga part granny.tare da iya ya same ta ya shigo da sallama a bakinsa, Suka amsa suna Washe baki granny tace,"A'a Babban mutum yaushe a garin?". "Sauƙan jiya da dare"ya faɗa yayin dayake zama kusa da ita.Nan ya gaishe su suka amsa da fara'ar su,sannan ya dubi iya yana cewa, " Ƴar tsohuwa me kuka jagwalgwala ne yau a gidan?Dan nasan ba wani iya girki kuka yiba". Dariya suka saka kana iya tace"sinasir ne da miyar kubewa sa kuma kunnun gyaɗa".Yatsina fuska yayi yace,"A kawo min kunnun gyaɗan". Iya ce ta tashi zata kawo masa yayi saurin cewa,"A'a tsohuwa yi zaman ki bari na ɗauko da kaina". Ya miƙe ya nufi kitchen ɗin.(iya amintacciyar ma'aikaciyar gidan ce tun yana yaro granny tace masa ita take renon sa kuma tana masa wani irin so mai tarin yawa,kasancewar bata taɓa haihuwa ba.shiyasa shima yake jinta ta daban acikin ransa). Daga kitchen ɗin ya fito dauke da cup a hannunsa yana shan kunnun,yasha sosai Dan ba ƙarami daɗin kunun yaji ba. Miƙewa yayi yace"Granny zanje wajen bashir,yanzu zan dawo kiyi min addu'a allah ya bani sa'a". Bai jira amsar da zasu bashi ba ya fice daga falon.Tun wajen 9:00 na gama shiryawa,ina jiran habib amma har yanzu ana neman 11:00 bai zo ba,har su tima da zubaida sun tafi Shahida kuwa tare zamu tafi da ita. Lokaci zuwa lokacin nake duba agogon dake ɗaure a hannu na,tare da sakin tsaki da shahida ma ta shanya ni tun ɗazu wai taje sallama da wasu class mate ɗinmu yan Zaria. Shigowar motarsa na hango yayi parking dai-dai inda nake tsaye tare da kayan mu,Ya fito ya iso inda nake tsaye langwabe kai yayi yace"Afuwan na barki kina jira". Ban kula shi ba illa ƙara ɗaure fuska danayi."Sai murna ake za'a tafi gida ko?". Bansan sanda nasaki, dariya mai sauti ba nace, "e mana".Shima sai daya murmusa kafin yace, "may Almighty Allah tackle us this unnecessary strike". Da amin na amsa mishi dashi,sannan yaɗan fara Jana da hira duk na lura akwai abinda yakeson faɗa amma bansan meyake dakatar dashi ba. Ƙiran sallan da aka farayi yasa mukayi sallama ya tafi.ƙarisowar shahida ne yasa na dawo da kaina daga kallon motar sa danakeyi har tabar cikin school ɗin. Hararar ta nayi ina cewa"wai me kika tsaya yine?". "Wallahi hira muka tsaya yi dasu rukayya sunusi".Shahida ta faɗa tana ɗaukar akwatin ta. Motor park muka je muka shiga motar potiskum.Dai-dai kiran sallan la'asar muka shigo garin potiskum,ni na biya mana kuɗin motar. Godiya tayimin sosai sannan kowa ya ɗauki hanyar unguwansu,kasancewar shahida a old army barrack take. Ina sauƙa daga nafef na hango,yaya fawas yana fito wa daga cikin gida,da Sauri na sallame mai nafef ɗin na sauƙo da akwati na. A guje naje na isa ga yaya fawas ina cewa,"nayi kewar ka yaya na" riƙo hannu na yace, "Nima haka my cute angle". Sannan ya ɗauka min akwatina muka shiga cikin gidan. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam Book one free Book 2 paid @N300 _______________________________ Page 8⃣ Umma na zaune a tsakar gida tana sauraran radio,cike da farin ciki naje na faɗa kan cinyar ta. Itama fuskar ta ba yabo ba fallasa tace,"Wai ke ummul-khair yaushe zakiyi hankali ne?". Cikin yanayin zolaya yaya Fawas yace"Umma sai ranan darayi aure zatayi hankali". Cike dajin kunyar maganan yaya fawas,na miƙe ina cewa bari naje nayi wanka. Ɗakina na shiga nayi wanka, dama yaya Fawas inna sanar dashi zuwa na ya gyara min ɗakin. Ina fitowa Tima ta kirani na ɗauka kafin nayi magana tace"mutanan potiskum harkun isa?" "wallahi mun isa". Mun Dan taɓa hira kafin muyi sallama Na fito naci abinci sannan muka zauna,da yaya Fawas ina bashi labarin jami'a da yanayin mutanan cikinta,shima yana bani labarin gida bayan tafiya ta. _________________Habib__________________ Yana isa yayi parking motar sa ya fito ya shiga part ɗinsa. Direct bathroom ya nufa, ya sakewa kansa ruwa sannan ya ɗauro alwala ya fito. Doguwar jallabiyar sa fara Sol ya saka ya fito ya tafi masallaci. Yana dawowa ya koma part ɗinsa,canja shiga yayi izuwa shigar wani maroon ɗin yadi,tsayin rigar dai-dai gwiwarsa key ɗin sa da wayarsa ya ɗauka ya fito ya shiga part ɗin granny. Tana zaune a falo ta iddar da salla kenan,tana ninke sallayar ya shigo. Karɓan sallayar yayi ya ninke,sannan ya ajiye shi a muhallinsa Duban sa tayi tace"To har dawo?" "E granny katsina zan koma",Da mamakin ta take tambayar sa lafiya yaushe ma kazo?. Langwabar da kai yayi yace,"Granny zan tafi ne akwai akin Dana baro a can ɗin". "To ka gaishe min da sauran yan uwan naka".Har parking lot ta mishi rakiya sai jero masa addu'o'i takeyi. Shikuwa ya figii motar sa ya fita,duk ransa babu daɗi,dukan sitiyarin motar yayi tare da furzar da iska daga bakinsa,gefen hanya ya samu yayi parking tare da ɗaura kansa akan sitiyarin motar. Ransa duk a jagule,a hankali ya furta "ya rabb wani irin al'amari ne yake shirin faruwa da zuciyata?". Yafi 30min a haka wayarsa da tafa ringing ne ya sashi ya ɗago kansa.a hankali ya kara wayar a kunnensa yace "bashir yane?". Daga ɗayan bangaren bashir yace,"normal fa mutumina,yanzu Nazo gida granny take cemin kazo har ka koma tace min jiya ka shiga cikin YSU shine ko ka nemeni sannan ma wajen wa kaje a cikin school ɗin?". Ajiyan zuciya yasaka yace,"bashir I am on my way now if I reach home I Will call you," Yana gama faɗin haka ya kashe wayar, sannan ya zaburi motar ya hau titi. Yana isa cikin katsina direct office ya wuce,yayi locking kansa a office ɗin. Ƙiran sallan magriba da aka farayi ne,ya tilasta masa fitowa ya tafi masallacin da yake cikin companyn,sai da akayi isha'i sannan ya tafi gida. Yana isa ya shiga part ɗin Ummi,gefen ta ya zauna yana sauƙe numfashi ƙasa-ƙasa ya ɗaura kansa akan kafaɗarta. Dubanshi tayi tace,"A'a Habib har ka dawo baka min waya, ka sanar dani ba?". " Ummi tafiyar ce tazo ba tsammani".ya faɗa yana gyara kwanciyar sa akan kafaɗata. "To ya ka baro su Granny ɗin?"."Lafiya kalau tana gaishe ku, musamman this parrot". Ya ƙarishe maganan yana nuna Yasira da take zaune a falon. Cuno baki Yasira tayi tana cewa"Hamma Habib bana ce zan bika ba ka ƙi kulani".Yace "to school ɗinfa kiyi yaya dashi?". "Ayya Hamma naga ba daɗewa zamuyiba".Miƙewa yayi tare da faɗin"Ummi akawomin abinci na part ɗin"yana kawowa nan yafita daga falon. Bazan taɓa manta wata ranan alhamis ba,lokacin kwana na biyu da dawowa daga makaranta tun daga wannan ranan ƘADDARAR RAYUWA TA ta sauya. Da yamma muna zaune a kofar gida ni da yaya Fawas Muna shan iska,wata farar mota ƙiran Mercedes tayi parking dai-dai kofar gidan mu. Drivern dake jan motar ne ya fito ya buɗe bayan motar wani mutum ne ya fito,naso ace wannan ranan ta zama mafarki wannan ranan shine sanadin rubuta labari na tamkar a mafarki idanu na suka sauƙa akan fuskar Abba dake fitowa daga cikin motar. A zabure na miƙe domin tabbatar da abinda idona ya nunamin domin na saba irin wannan mafarkin,Bansan sanda hawaye suka zubo daga idanuna ba. A guje na nufi inda Abba yake tsaye na rumgume shi ina kuka,yaya Fawas ma zuwa yayi tare da rumgume shi. Riƙo hannuna Abba yayi muka ƙarisa cikin gidan,Umma tana fitowa daga wanka sukayi ido huɗu da Abba. Sake bukatin ɗin dake hannunta tayi cike da mamaki gami da jimami da son tabbatar da abinda ta gani tace,"Sule!sule Kaine wannan?". Abba yace"kwarai kuwa Juwahir nine". Tabarma na shimfiɗa mana muka zauna yayin da driven Abba ya shigo da wani akwati ya ajiye a gaban Abba sanna ya fita. Ruwa Umma ta kawowa Abba ta ajiye masa tana cewa tana tafe tana faɗin,"Sule kai kuwa meyayi zafi haka?zaka tafi abinka ko waiwayen mu bakayi ba". Abba yace"juwa kenan bagashi yanzu na zoba".yaya Fawas ya gyara zaman sa yana ƙara fuskanto Abba yace,"Amma Abba Duk tsawon lokacin nan ina kaje?". Murmushi Abba yayi tare da buɗe akwatin dake gabansa,ya Ciro waya guda biyu ƙiran iPhone 12pro max ya miƙawa yaya fawas ɗaya sannan nima ya miƙomin ɗayan yana faɗin"Mama na kema ga naki". A hankali nasa hannu na karɓa ina masa godiya,zannuwa ya Ciro ya mikƙawa Umma har ƙasa Umma ta zube tana masa godiya. Dubu ɗari ya miƙawa yaya Fawas yace ya riƙe koda wata buƙata Zara tazo Umma ce tayi saurin cewa"Sule kodai arzikin Kane ya dawo?". "Juwahir kinsa ikon Allah yafi gaban komai,shike azirta duk Wanda yaso a lokacin daya so kuma a sanda yaso".yana gama faɗin haka ya miƙe,Cikin sauri nace" Abba ina kuma zakaje?". "Ummul-khair inason na shiga cikin unguwane mu gaisa da mutane kinsa an Daɗe ba'a haɗu ba". Har ƙofar gida muka raka shi sannan muka dawo,kowa acikin mu jiran zaman dawowan Abba yake domin amsa mana tambayoyin da suke bakin mu akan dukiyar daya zo da ita. Muna zaune har aka kira sallan magrib yaya fawas ya fita masallaci,ina iddar da sallah waya ta ta fara ruri na ɗaga. Mun Dan yi hira da Habib sama-sama Dan ba kowani magana nake bashi amsar,bata sai dai nace masa uhmm da haka mukayi sallama. Mu na nan zaune har ƙarfe 9:00 na dare Abba bai dawo ba,har bacci ya fara ɗauka na Washe gari duk muka tashi da mamakin,rashin dawowar Abba har makwabtan muka tambaya ko yaje wajen su kamar yanda ya faɗa amma kowa yace bai ganshi ba. Kullum da sa ran dawowar Abba muke kwana acikin ranm ,har izuwa wata Daren ranan juma'a,yaya Fawas da Umma suna zaune a tsakar gida. Yaya Fawas kayan mutane yake ta yankawa ita kuwa umma sana'arta takeyi wato dama giya. Ni kuwa ina ɗaki ina waya da habib, kullum sai ya kirani a kalla sau biyar a yini,yana tambayar lafiya ta tun bana biye masa har na fara sakin jiki dashi. Sosai mukayi wani shaƙuwa mai ƙarfi da habib,har nakan iya sanya shi a cikin,jerin mutane mafi muhimmanci a gare ni acikin kwanakin nan har yaya Fawas ya fara fahimtar wani Abu. Sallama mukayi da Habib akan cewa zai shiga wanka inya fito zai kirani.Fitowa nayi waje na zauna kusa da yaya Fawas inna kallon yanda yake yankar kayan. Ina zama Abba ya faɗo cikin gidan a firgice,cike da tsoro halin da muka ganshi duk muka miƙe muna faɗin lafiya?. Bai kai ga bamu amsa ba motocin yan sanda suka zagaye gidanmu sannan wasu suka shigo ciki,wani jami'i ne ya ƙarisa kusa da Abba ya daka masa tsawa yana cewa"Be on ur kneel." Tunin Abba ya durkushe a wajenSannan jami'in yasa masa handcuff a hannun sa,suka ɗauke shi suka fice dashi duk cikin mu babu Wanda Allah ya bashi damar tambayarsu dalilin tafiya da Abba domin mamaki ya gama cikamu. Wasu hawaye masu zafi naji suna zubowa daga idanuna,wani ƙara na saka mai ƙarfi tare da zubewa a ƙasa ina wani irin kuka mai ban tausayi,durƙusawa yaya fawas yayi a gefena cikin kuka yace,Hibba kanwata ki daina kuka wallahi kukan ki yana ɗaga min hankali". Muryata can ƙasa nace "Haba!yaya Fawas taya bazan yi kuka ba kana ganin abinda ya faru fa Abba suka kama". Na ƙara fashewa da wani kukan rumgumo ni yaya Fawas yayi ya riƙe ni gam muka cigaba da kukan mu Umma kuwa sai safa da marwa takeyi. UWATACE SILA Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 9⃣ Haka muka kwana yanda mukaga rana haka muka ga dare,cikin mu ba Wanda ya runtsa. Washe gari kuwa tun da sanyi safiya muka tafi police station,abinda ke tafe damu muka bayyana musu suka ce mana ba,nan aka kawo shi ba saboda laifinsa babba ne,damaturu aka wuce dashi tun Daren jiyan. Umma tace"wa meya aikata ne haka shi kuwa?". Sai da police ɗin ya zabga mata harara kafin yace"Kinason kice baki San sana'ar mijinki ba,na haɗa kai ga masu GARKUWA DA MUTANE?". Dam-dam ƙirji na ya bada wani jiri naji yana ɗebata nan take na faɗi awajen sumammiya. Cike da tashin hankali yaya Fawas ya riƙoni,yana kiran sunana Umma tace,"To Dan Allah bawan Allah inmukaje damaturun zamu zama ganisa". Yace mata bashi da tabbacin zamu sama ganinsu Dan daga damaturun abuja za'a wuce dasu. Salati umma ta saka,tana faɗin"Sule ka cucemu ka cuci kanka sule mai ya kaika wannan aikin?. Wani police ne Wanda babu tsausayawa acikin ƙwallar idonsa ya dakawa yaya fawas tsawa,Yana cewa"Ku fice mana daga nan mutanan banza kawai". Ɗauka na yaya Fawas yayi nuka fito,muka nema nafef mukayi gida.tunin labari ya baza unguwarmu masu zagi nayi masu tsausaya mana suma nayi. Buɗe idona nayi a hankali,ina ƙarewa wajen kallo a zabure na tashi ina faɗin Abba!Abba!!Abba!!!.yaya Fawas ne ya kamoni ganin bana cikin hayyacina kuka yake matsananci yace, "Hibba kiyi hakuri abba zai dawo". A hankali na kwantar da kaina a ƙirjinsa ina kuka,haka muka yini muka kwana Abu ɗaya. Tabbas naga tashin hankali Umma matuƙar awannan lokacin tabbas tsakanin miji da mata sai Allah. Nikam ba abinda yake sake sani kukan zuci,kamar ina tuna umma ce ta kori Abba daga gida har, shaiɗan ya rinjaye shi ya aikata wanna aika-aikan. Tabbas UWATACE SANADIn duk wani ƙuncin rayuwa dana shiga,itace silar zubar hawaye na. Washe gari muka ƙara komawa police station ɗin,cikin rawar murya Umma tace,"Dan Allah bawan Allah ka sanar damu shin zamu iya ganinsa inmukaje damaturun?". Cikin zallar masifa yace,"wai Ku wasu irin mutane ne? nan fa aka sanar daku laifin wannan mutumin, to wallahi laifin,da mutumin nan ya aikata kuma cire rai da dawowarsa baza ku gani ba Dan wallahikashe su za'ayi". Salati Umma ta saka tana faɗin"Na shiga uku ni juwahir naga abun da ya isheni. Ni kuwa wani jiri ne naji yana ɗebata,da ƙyar na iya tsayawa akan ƙafafuna,riƙoni yaya fawas yayi idanunsa taf da ƙwalla yace,"Umma muje gida". Muna isa gida na wuce ɗakina na kwanta,wani nauyi naji zuciya tamin da sauri-sauru take bugawa tamkar zata fito daga cikin ƙirjina. Inajin wayata tana ringing nasan habib ne,sai dai bana cikin yanayin da zan iya ɗaukar waya a yanzu.Haka muka shafe kwanaki biyar cikin wannan tashin hankalin. A cikin rana ta shida, wani makwabcin mu ya shaida mana,da yankewa su Abba hukuncin kisa ta hanyar harbewa da bingida,kuma har an zartar musu da hukuncin. Har video yanuna mana a wayarsa, gasu nan kafin a kashe su suna fitowa daga kotu yan jaridu sai tambayoyi suke musu. Su goma sha ɗaya ne dukkaninsu matasa ne da bazasu ɗara shekaru ashirin da biyar ba a duniya,Abba ne kawai dattijo a cikinsu. Yana gama sanar da mu umma tace yaya fawas yaje police station,Dan tabbatar da gaskiyar wannan videon. Can ɗin ma da yaje suka bayyana masa da kotu ta yanke musu da hukuncin kisa kuma,har anzarta da hukuncin akansu. Dan acikin Wanda suke da plan ɗin yin garkuwa dashi har da ƙwararran engineer ɗin nan masu kamfanin kayan masarufi GALADIMA'S NIG LIMITED wato ENGINEER SURAJ GALADIMA. Duk abin da suke faɗa yaya fawas baya fahimtarsu yace. "To gawarsa fa ko zamu samu mu mishi sutura kamar yanda addini ya tanada?". Suka ce masa basa bada gawar irin waɗannan mutanan,birne su akeyi tare da sauran yan garkuwar a rami ɗaya. Lokacin danaji yaya fawas yana sanar da umma wannan labarin,ji nayi tamkar babu rai a cikin jikina. Tsayawa nayi cak!ba abinda yake motsi a jikina sai ido. Yayin da numfashi na ya fara barazanan barin gangar jikina,faɗuwa nayi a wajen ba wani gaɓa a jikina Wanda yake motsi. Cikin wani irin kuka mai bayyanar da tsan-tsan tashin hankali,yaya fawas ya iso inda na faɗi yana jijjigani umma ma sosai take kuka fuskar nan duk ta kumbura. Tunin gidan mu ya cika da taron mata, har yan daudun umma sunzo,sai kuma maza dasuke waje. Har yan-uwan Abba sunzo ƙaninsa(baffa) tare da matarsa hajara,sai kuma mahaifiyarsu inna dama suke nan suka ragewa Abba a duniya a matsayin dangi. Kowa yazo sai ya tambayi gawar Abba, umma takan ce musu a can aka masa jana'iza ba'a kawo gawar gida ba. Ina kwance da kan cinyar yaya fawas,a ɗakin umma.Dan tunda na faɗi yake riƙe dani ko gaisuwar dasu baffa ke karɓa a ƙofar gida ba jeba shi. Hannuna yana saƙale a cikin nasa yana murzawa a hankali.Inna na tofin addu'a a cikin ruwa tana shafa min a fuska. A Hankali na fara buɗe idona dana jisu sumin wani irin nauyi.Ina ƙarewa mutanan wajen kallo,wasu hawaye ne masu matuƙar zafi suka shigo rige-rigen tsiyayowa daga idona.magana ma ya gagare ni. Tashi nayi daga jikin yaya fawas,na matso kusa da inna na kifa kaina akan cinyarta ina kuka,bubbuga bayana takeyi a hankali da hannayen ta ita ma tana kukan. Har cikin ranta umma take ɗaurawa alhakin abinda Abba ya aikata,Lokaci daya naji kaina yamin wani irin nauyi,ko idona bana iya buɗewa ga wani azababben zazzabi daya sauƙa a jikina haka na yini cikin wannan halin ina maƙale ajikin inna. Da dare mutane sun safara watsewa,ina kwance har yanzu a jikin inna. Izuwa yanzu kam hawayen ma sun kafe sai dai kukan zuci,wayata ce ta hau ringing inaji har kiran ya tsinke aka sake kira a karo na biyu.shima banbi ta kansa ba sai da aka kira a karo na uku. Sannan inna tace,"wayar wayene wannan aketa kira?". Muryata har bata fitowa sosai nace"Tawace". "To ki ɗaga mana". nace"ki barshi inna ai kiran ma ya katsa". Ina rufe bakina aka wani Kiran yasake shigowa,ɗauka nayi tare dayin sallama bai amsa sallamar ba Duk dayasan muhimmancinta a addinance. Illa ajiyan zuciya da ya saka kafin yace,"Hibba for how many days nake kiranki bakya ɗauka?". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _________________________________ Page 1⃣0⃣ Kuka ne ya kubce min,a razane Habib yace,"Hibba lafiya?meya saki kuka?". Ajiye wayar nayi yayin da na kifa kaina akan gwiwata ina kuka. "Hello kina jina?" Shine abinda yake ta maimaitawa a cikin wayar,ganin haka yasa inna ta ɗauki wayar. Sallama tayi habib ya amsa tare da gaishe ta cike da ladabi da girmamawa,sannan inna tace,"Bawan Allah kayi haƙuri hibba yanzu bata cikin hayyacinta,bazata iya magana da kaiba". "Dan Allah meye faru da ita". Nan fa inna(baki ba sakata)ta shiga bayyana mishi duk abinda ya faru, sai dai bata sanar dashi irin mutuwar da Abba yayi tadai ce masa abba na ne ya rasu yau. Wani irin tausayi ne da kuwa abinda shi kansa baisan menene shi ba,suka ƙara shigewa zuciyar habib a lokaci guda,yasan zafi da kuma raɗaɗin maraici domin nasa iyayen bai taso a cikin su ba. Hawaye yaji suna gudana a fuskarsa,a hankali ya share su yace,"Dan Allah ko zakimin kwatancen gidan?". Nan inna ta shiga kwatanta mishi gidan,duk da ita ma ba wani sanin potiskum ɗin tayi ba ta'aziya ya mata sannan sukayi sallama. Washe gari bayan sallan zuhr,ina zaune a tsakar gidanmu yayin da mutane keta zuwa gaisuwa,yaya fawas ya shigo ya kirani gefe muka tsaya sannan yace. "Hibba kinyi baƙo a waje tare suke da bashir yayan abokina Faisal". "Ni yaya Fawas ba Wanda mukayi dashi zai zo". "Kije ki sanarwa inna da Umma zasu shigo su gaisa"cewar yaya Fawas. GefenUumma na tsuguna ina faɗa mata,ina rufe baki na kuwa sallamar habib ya sauƙa a cikin dodon kunnena,tare yake da yaya bashir da kuma ƙanin yaya bashir ɗin Faisal. Ɗaya bayan ɗaya suka gaida mutanen wajen, tare dayin ta'aziya wa umma da inna miƙewa sukayi yayin dana bin bayan su muka tsaya daga jikin motar yaya bashir Dan na lura da ita suka zo duk sunmin ya haƙuri. "Mun gode Allah "sannan suka tafi na amsa dashi. Wani abin takaici ranar da Abba yacika kwanaki uku da rasuwa a ranan Umma ta cigaba da sana'arta. Ranan bani ba hatta Inna da Baffa sun sha kuka mai isarsu. Wasa-wasa Abba ya cika wata biyu cur! da rasuwa, a ranan inna dasu baffa sukace zasu koma umma tace"Ita ta sama miji aurenta zatayi tana gama idda dan haka dani da yaya Fawas kowa zai koma wajen dangin mahaifinsa,saboda mijin da zai aure tan yace bazai riƙe mata ƴaƴanta ba". Yaya fawas yayi kuka tamkar ransa zai fita a ranan. Ya roƙi umma data barni na zauna,a wajenta kodan karatu na,amma umma tace"Ai daman,ba ita takeda hakkin kula damu ba dukkanin mu wajen dangin mu zamu koma ni zanbi su inna mukuma kano shikuwa yaya Fawas daman dangin mahaifinsa a azare suke Dan haka shima zai koma can da zama". Rabuwa da yaya Fawas,jinsa nayi tamkar ƙarshen numfashi na kenan a cikin duniya. Abba ya tafi tafiyar da ba waiwaye balle dawowa,yanzu kuma ga rabuwa da yaya fawas. Jinayi komai na rayuwar duniya ya fita a raina,meyasa mu kuma tamu ƙaddarar take zuwa mana a haka?meyasa umma bata tausayin halin da rayuwar mu zai shiga?meyasa Umma bata mana kallon ƴaƴa?. Tambayoyin dana kasa samawa kaina amsoshin su kenan. Duk mungama shirya kayanmu nida yaya Fawas muka fito dasu kofar gida, kuka muke tamkar bazamu sake ganin juna ba,riƙo hannuna yaya fawas yayi yace"Hibba ki daina kuka,kukanki na ɗaga min hankali my cute angle ko ina kika tsinci kanki,ki riƙe mutuncinki sannan ki riƙe addininki kinji ƙanwata?". "Yaya Fawas ajikin nakejin kamar bazamu sake haɗuwa ba".Hannu yasa yana share min hawayen fuskana. Kafin ya shiga faɗin"Hibba ki daina faɗin haka in sha Allah zanzo har inda kike my cute angle kinji ki daina kuka". Muryata har ya dushashe nace" yaya Fawas yanzu karatuna shikenan ya tsaya kenan?". "Hibba zaki cigaba da karatu domin shine burin Abba, ga kuɗin da Abba ya bani dashi akayi amfani wajen saya abinci da wasu abubuwa dubu talatin ne ya rage gashi yanzu zan baki ki riƙe a wajenki koda zaki buƙaci wani Abu". "Yaya Fawas ba abin dazan buƙata a yanzu sama da kasancewa tare da kai,amma Umma ta hana hakan yiyuwa" Muna cikin haka Umma tafito tare dasu Inna,Hajara da kuma Baffa Umma tace"Hibba Fawas sai dai kuyi haƙuri domin ba kuka ba komai zakiyi bazai sa na canza ra'ayi na ba". Cikin sauri Inna tace"Ashsha ashsha haba Juwa,ki barsu da baƙin cikin da kika sanya su aciki ma ya ishesu basai kin faɗa musu wadannan kalaman ba". Baffa da duk haushin Umma ya gama cika shi yace"Inna mu tafi". Ƙarisuwa Inna tayi tare da Ciro hannuna daga cikin na yaya Fawas ta riƙe muka fara tafiya. Tafiya nake amma bansan inda nake saka ƙafafuna ba,numfashi na sama-sama yake fita har muka isa tasha muka hau motar kano. Yaya Fawas kuwa inda nabarshi,nan ya tsaya yana wani irin kuka mai tsuma zuciyar Mai sauraro,sai da yayi Mai isharsa sannan shima ya nufi azare. Ƙauyen gano dake cikin karamar hukumar kano,muka nufa inda su inna suke da zama. Gidan ƙarami ne Mai ɗauke da ɗakuna biyu,ɗaya na Baffa da matarsa ɗaya kuma na Inna. A ɗakin Inna na ajiye kaya na saboda anan zan zauna muna isa na kira yaya fawas amma wayarsa a kashe. Kwana na biyu a gidan na fahimce irin rayuwar gidan nasu.Inna bata isa ta faɗawa Baffa,magana yaji ba yayin da matarsa Hajara take tsula tsiyarta son ranta wa Inna. Ranan ina shara Habib ya kira wayata,na ɗauka tare dayin sallama ya amsa sallamar tare faɗin"Hibba yanzu Bashir yake gayamin school ɗinku,sunyi resuming daga strike ɗin dasuka tafi.amma yace min ke baki komaba ko lafiya?". Hawaye suka ciko idona a hankali nace"Banida lafiya ne,amma in sha Allah innaji sauƙi nima zan koma". A kiɗime yace "Subhanallahi! tun yaushe?". Bansan sanda bakina ya furta"Tun last week"ba Cike da nuna damuwar sa yace"To Allah yaƙara lafiya " "Amin" Mun Dan taɓa hira har yake sanar dani tsautsayin dayaso ya faɗa ga uncle ɗinsa,na yan garkuwa dasu ka so kamashi. Na jajanta masa tare da addu'ar Allah ya kiyaye gaba Mun Dan tab'a hira kafin mukayi sallama. Na cigaba da sharan danakeyi,ina gamawa na nufi ɗakin Hajara sallama nayi aka amsa sannan na shiga. Baffa na zaune na shigo na zauna can gefe cikin nutsuwa nace,"Baffa sannu da hutawa" Ba tare daya ɗago ya kalli ni ba yace"Yauwa Mamana". "Baffa daman mun koma makaranta ne daga hutun da malaman makarantar sukaje shine nima nake son wani sati na koma". Sai a sannan Baffa ya ɗago ya kalle ni yana faɗin"Hibba kya bari dai abubuwa su dai-dai kafin kizomin da maganar komawa makaranta". Nace" Baffa makarantar nan shine burin Abba Dan Allah kar ka han......." Tsawa ya daka min cikin faɗa yake cewa"Wai ke Hibba wace iriyar mara hankali ne?,a halin damuke cikin inna mukaga ƙarfin ɗaukar nauyin karatunki. bayan ba abin da Sulen ya bari sai ɓata mana suna da yayi a gari to karatu dai wanda kikayi a baya Allah ya albarkace shi". Hawaye tunin sun fara wanke min fuska,na tashi ina fita daga ɗakin ina kuka na shiga ɗakin Inna. Yaya Fawas da Abba kawai nake tunawa Allah sarki mutuwa Mai tunan asiri. Wayata na ɗauka na shiga dialing numbern yaya Fawas yana ɗauka kuka nasa Mai ƙarfi nace "Yaya Fawas karatuna Baffa yace banzan cigaba ba". Da mamaki yaya Fawas yace"Meyasa yace haka?Baki gaya mishi burin Abba bane kiyi karatu?" " Na faɗa mishi yaya Fawas". Ajiyan zuciya yaya Fawas ya saka kafin yace"To shikenan my cute angle ki daina kuka na faɗa miki kukanki yana daga min hankali ko,ƙarshen watan nan zanzo sai muyi magana da Baffan ko?". Cikin sheshshekar kuka nace "to yaya Fawas". Haka muka cigaba da hirar mu kafin daga bisani mukayi sallama. Sati na biyu tare da su InnaBrannan baffa ya shigo yace a kirani.Hajara tazo tace min Baffa yana kirana naje na durƙusa a gaban shi nace" Baffa gani". Gyaran murya yayi kafin ya shiga faɗin"Mama na zamanki a haka bazai yiyuba sabida haka nasamo miki MIJiN AURE aure zan miki". Wani ras!naji gaba na yana faɗuwa,a kiɗime nace "Baffa aure kuma?"na faɗa maka fa ni karatu zanyi domin shine burin Abba Baffa inna gama sai ayi maganan auren". "Na dai gaya miki kenan,matuƙar kina ƙaunar ki cigaba da zama a gidan nan to sai kin auri NAZIFI". Idona fal da hawaye nace, "To ni wallahi bazan auri kowa ba". Mari baffa ya sauƙe min hagu da dama Yana faɗin "Shashasha to ki kasa kunne ki saurare ni, wallahi ko ubanki ne Sule ya dawo duniya bai isa ya hana aurenki da nazifi ba". Inna ce ta fito daga ɗakin ta,tana cewa "Adamu dan Allah kabar yarinyar nan haka,ka hana ta cigaba da karatun ma ai ya isa". "Haba!Inna wai ke ba daman anyiwa yarinyar nan,faɗa sai kita mita to wallahi aure zan mata koda son ranta ko babu". Hajara ce ta karɓe zancen tana faɗin"Haba!Inna meyasa kike ɗaurewa yarinyar nan gindi ne,in batayi aure ba to mezatayi?". Ajiyan zuciya Inna ta saka kafin tace"Hibba kiyi haƙuri taso ki shiga ɗaki". Na tashi na shiga ɗakin Inna na faɗa kan katifa ina kuka Bayan kwana biyu Baffa yace in shirya nazifi zaizo kaina na kallon ƙasa nace"Baffa bana jin daɗi bazan iya fita ba". Cikin zafin rai yace "Hibba ko mutuwa zakiyi wallahi sai kin auri nazifi". Da kukana na miƙe na shiga ɗaki naci kukana har na gaji na tausayawa kaina na daina. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Katsinawa wannan page din nakune bazan manta da karamcinku ba a rayuwata. Book 1 free Book 2 paid @300 ______________________________ Page 1⃣1⃣ Gashi wayata ta mutu,balle na kira yaya fawas domin babu wutan nefa a gidan baffa kuma ya hana ni fita ko'ina balle na sama waya nayi kira. Inna da hajara kuwa basu da waya baffa ne kad'ai mai ita,Ina zaune akan sallaya ina roƙo mahaliccina,daya sassauta min tsananin danake ciki. Bazan zargi umma da laifin jefa rayuwa ta cikin ƙunci ba,amma tabbas UWATACE SANADIn sanadiyar kuka na. Hajara ta shigo tana cewa,"kizo baffa yana kiranki"Miƙewa nayi nabi bayanta.A hankali kamar mai ciwon baki nace"Baffa gani" "Kije ki shirya nazifi na jiranki a waje". Miƙewa nayi jikina a sanyaye na fita wajen sallama kawai,nayi masa naja gefe na tsaya ina masa wani irin kallo mai cike da tsana. "Ina fatan an sanar dake dalilin zuwana?".Cewar nazifi Hararan na watsa masa ne ya sanya shi saurin ɗauke idonsa daga kallon daya kemin yacigaba da cewa"Maganar aure ne yakawoni amma bari na fara da gabatar miki da kaina.Sunana nazifi Sana'a ta noma ina noman dankali dawa Masada da kuma barkono sannan ina kiwon tattabaru ina aure k.........". Tsawa na daka masa ina cewa "Kaga malam kama daina mafarkin aurena Dan bazan taɓa aure mutum irin kaba, gwara ma tun kafin lokaci ya ƙure maka ka janye wannan maganar." Ban jira amsan dazai bani ba na koma ciki Baffa na tarar zaune a tsakar gida,ko kallonshi ban yiba nasakai zan shige ɗaki naji muryan baffa yana cewa. "Ya kukayi da nazifin?." Ya dakatar dani daga shiga ɗakin a dake nace"Baffa ni baimin ba kuma bazan taɓa aurensa". Mari naji baffa ya sauƙe min ta gefen fuska na sai dana jijiri na ɗebata. "Billahillazi koda gawarki ne,sai na ɗaurawa nazifi aure da ita kinsa alkhairin da yaron nan kemin kuwa?". A raina nace ina kuwa zan sani karo na biyu da baffa ya sake maimaita min. "MATUƘAR KINA ƘAUNAR KI CIGABA DA ZAMA ACIKIN GIDAN NAN SAI KIN AURE NAZIFI, "Yanzu ke kina tinanin har kina da wani ƴancin akan kanki ne ai hibba ko mai ya faru dake a rayuwarki to babu wanda zakiyi,kuka dashi face MAHAIFIYARKI domin ita ta zaga yi miki abinda uwa take yiwa ƴaƴanta". A guje na shiga ɗaki ina kuka,kuka nayi na fita hankali naci kuka mai isa ta bamai bani haƙuri saboda inna batanan daman ita ce mai kwantar min hankali.Tashi nayi na zauna tare da share hawaye na,ina kara tino furcin baffa. "MATUƘAR KINA ƘAUNAR KICIGABA DA ZAMA A CIKIN GIDANNAN SAI KIN AURE NAZIFI AURE ZAN MIKI NA HUTU". A hankali nace "Baffa zan bar maka gidanka na gwammace nabi dunyia akan na auri nazifi,matuƙar ina numfashi a cikin duniya sai na cika burin Abba sai na cimma ƙudurin yaya fawas na zama yar jarida". Ina cikin haka inna ta dawo,fara'a na ƙirƙiro na tashi na tarbeta. Kallo ta tsareni dashi tace "Hibba idonki kamar kuka kikayi ko?". Wani maraniyar murmushi nasaka tare da karɓan ledan dake hannunta nace,"A 'a inna kaina ne kemin ciwo kawai" "To Allah ya sauwake" nace "amin". Kwana nayi ina tufka da warwara a cikin raina,ko yaya fawas bazan Sanar mishi zan bar gidan baffa ba domin nasan shakka babu ba zai goyi bayana ba akan hakan ba. To ma ina zan nufa inna bar gidan baffa?,wanake dashi dazan nufe shi da matsalolina a halin yanzu?umma ce ta fara faɗu min a raina. Amma nasan ko hauka nakeyi basan nufi wajen umma ba domin baza ta karɓe ni ba.Wata zuciyar tace min to ki shiga duniya mana. Haka na kwana ban runtsaba,washe gari kuwa na shiga tinanin hanyar dazan bi na fita koda Ƙofar gida ne domin baffa ya hana ni fita ko'ina. Muna zaune da inna ina tsince mata wake,hajara ta fito daga ɗaki tana ta jaraba.Cewar wai gidan ba ruwa ga shi baffa ya fice abinsa ba tare daya nemo yaron dazai ɗeboba. Cikin hanzari nace"Bari naje na ɗebo ruwan". Inna tace "A'a hibba kar kijawa kanki abin magana,adamu yazo yata miki faɗa ki bari ya dawo ya nemo Wanda zai ɗebo ruwan da kansa". "To inna ki barta ta ɗebo mana daman,aikin metakeyi a cikin gidan".hajara ta faɗa tana wurgo min wata uwar harara. Cikin sanyin murya inna tace "To hibba kije amma Dan Allah karki daɗe" "To" Kawai nace, hijab ɗinna na ɗauka da waya ta sannan na ɗauki bokatin ɗebon ruwan na fita. Ina fita na ajiye bokatin a kofar gida,na nufi tashi duk daba wani sanin garin nayi ba. A ƙafa na ƙarisa tashan wani shagon saida wayoyi na hango a gefen tashar Na shiga na saida waya tavsannan na dawo cikin tasha. Ajiyan zuciya nasaka yayin da hawaye ke zubowa daga idona,ina zan nufa yanzu?wanake dashi dazan je wajen sa?inama-inama ace innaje wajen umma zata fahimci irin raɗaɗin danake ji a cikin raina ta karɓe ni?. Share hawaye na nayi dai-dai lokacin da wani mutum ya ƙariso Inda nake tsaye yana cewa "Hajiya KATSINA ne?". Lokacin ɗaya naji bakina yace "E",ba tare da yayi shawara da zuciya ta ba. "To bismilla ga can motar a can" Na shiga motar daman mutum ɗaya ya rage motar ta cika ina shiga kuwa direban ya ja motar. Tinda muka hau titi nake kuka har muka isa cikin katsina ta dikko ɗakin kara kunya gare Ku badai tsoro ba. Tabbas mutanen katsina sunmin karan da bazan taɓa mantawa dashi ba a tarihin rayuwa ta. Yaron Motan ne ya shiga tattaran kuɗin motan,yana isowa na zara daga cikin kuɗin waya ta dana sayar na bashi. Sannan na fita daga cikin motar,ina ƙarewa wajen kallo a duk cikin rayuwa ta ban taɓa ko mafarki zuwa katsina ba,sai gashi yau a dalilin maraici nazo. Mahaifiyata ta kasa janmu a jikinta ta riƙe mu duk daɗi Duk wahala,yayin da dangin uba suka Gaza Samar min da kwanciyar hankali. Haƙiƙa maraici cuta ne musamman na uba.Furcin baffa na tino"MATUƘAR KINA ƘAUNAR KI CIGABA DA ZAMA A CIKIN GIDAN NAN TO SAI KIN AURE NAZIFI". A hankali nace yayin da hawaye kebin fuskana "Baffa nabar maka gidan ka". Sannan wani kuka Mai ƙarfi ya kubce min nan na zauna cikin tashar naci kuka mai isa ta. ________________________________________ Inna tana zaune har tagama tsintar waken bani ba alamata tace"Hajara ko zakije ki dubo hibba ne kar,adamu ya dawo bai sameta a gida ba kinsan faɗansa". Harara Hajara ta cilla mata kafin tace"Kiji min inna da wata iriyar magana,hibban ƙaramar yarinya ce da inta fita sai annemota?Allah yasa ya dawo bai same ta ba komai ya mata ita ta jawa kanta". Tana rufe bakinta Baffa ya shigo riƙe da bokatin dana fita ɗebo ruwa dashi. Hamdala inna tayi tana faɗin"Adamu yana ganka da bokatin ita kuma hibban ina ka baro ta?". "Inna a kofar gida fa,naga bokatin na shigo dashi ita hibban ina taje?". Cewar Baffa Cike da jimami Inna tace"Tun safe ta fita ɗebo ruwa har yanzu ba ita ba labarinta". A harsale Baffa yace "uban wa yabata iznin fita?". " Inna ce sai danayi nayi,a bari sai ka dawo ka nema mai ɗebo ruwan amma ta dage akan zataje".Hajara ta faɗa tana cillawa Inna wata hararan. Tsaki Baffa ya sake tare da ficewa daga gidan.Bai Daɗe ba ya dawo inna da duk ta gama rikicewa tace"Adamu aganta?". Ajiyan zuciya ya saka kafin yace "inna Hibba butulu ce,Hibba ba ƴar mutumci bane a yau nayi mamakin kasancewar ta ƴar yaya Sule domin ko kaɗan bata gado halinsa ba". "Adamu meya faru yimin yanda zangane meye Hibban tayi?". Sai da Baffa ya numfasa sannan yace,"Inna Hibba guduwa tayi yanzu dana fita wani yake shaida,min ya ganta a tasha kuma yaga shigarta mota". Salati inna ta saka tana kuka tana faɗin"Adamu kagani ko sai dana gaya maka ka haƙura da maganar auren da yarinyar nan amma kaƙi,to yanzu ga abinda kajawo mana marainiyar Allah ta'ala". Cike dajin haushin maganar inna hajara tace"Haba!inna ya zaki daura masa laifin daba nasaba taje ai duniya ce tafi gabaruwa iya jima". ********************************* Tunda na sauƙa a tasha dana gama kuka na,na tashi na hau tafiya. Har aka ƙira sallan la'asar mai tallan pure water na tsayar na saya domin nayi alwala nayi salla,gefen zani na na since zan bata kuɗin ruwanta. Naga babu kuɗi salati nasaka tare da sake dubawa amma babu kuɗin ba alamar sa. Miƙa mata ruwan nayi ina cewa,"Kiyi haƙuri banga kuɗin nawa ba". "La ki riƙe kawai ba komai ki bar kuɗin",nace "nagode". Tafiya na cigaba dayi ina tinanin a ina na jefar da kuɗin nan,ga wata masifaffiyar yunwa dake nuƙurƙusa na. Hawaye ne suka fara tsiyayowa daga idona saura kiris wani Mai keke ya bugeni,sai daya rurrugamin ashar kafin ya wuce. Hawayen danake yi ne,suka tsananta gefen wani shago saloon na zauna nayi alwala sannan na shimfiɗa ɗan kwalina nayi salla akai. Na kuma cigaba da tafiya bansan inda zan nufa ba.Yunwa nakeji tamkar zan mutu ga wani masifaffen ciwon kai daya dameni ina tafiya ina haɗa hanya kamar bugaggiya,ina zuwa dai-dai wani gidan cin abinci na faɗi na suma. Nan jama'a suka cika a kaina aka shiga dani cikin gidan abincin,aka bani abinci naci sannan na soma dawowa cikin hayyacina. Wata matace Mai gidan abincin tace"Baiwar Allah ya kikejin jikin yanzu?" "Alhamdulillahi nagode da taimakon ki amma naso ace kin barni na mutu". Cikin sauri tace,"Subhanallahi! baiwar Allah meya miki zafi cikin dunyia har kike wannan fatan akanki?". Hakanan kawai naji zuciya ta bata nutsu da in samar da ita labarin rayuwa ta ba. Shiru nayi tare Sunkuyar da kaina ƙasa,ta dafa kafaɗa tare da faɗin"Ƙanwata ki sanar dani abinda ke damunki ƴar-uwar ki ce ni mace". Idona fal da hawaye nace,"Ki taimaka min domin Allah badan nasanar dake labarin rayuwa ba ta". "Wani irin taimako kike so?". "Wajen dazan zauna shine damuwata a yanzu."na faɗa inajin wasu sabbin hawayen nabiyo kunci na. Sai datayi Jim kafin tace,"Zan taimaka miki zamuje dake gidana in mijina ya amince ki zauna shikenan". "Nagode Allah yasaka da alkhari". "Amin ya sunanki?" Nace" HIBBA" ita kuma tace "sunan ta Amina". Haka muka zauna a shagon har yamma sannan muka tafi gidan ta dake unguwan fayamasa. Tun kafin mu isa ta shaida min tanada abokiyar zama balaraba da ɗanta ɗaya kabir tamin kashedi sosai,akan na kiyayi shiga harkan Balaraba da kuma ɗanta Kabir. Muna isa gidan muka tarar da mijin anty Amina yana tsakar gida yana alwala saboda ƙiraye-ƙirayen sallan magrib da aka fara. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 1⃣2⃣ Da sallama muka shigo ko sallamar bai amsa ba,yace"amina wannan kuma wacece?". Nan anty amina ta shiga bashi labarin yanda muka haɗu.Miƙewa tsaye yayi tare da ƙwalawa baralaba ƙira yana cewa"fito ki tayani ganin ikon allah". "Malam meye faru?",ta faɗa tana fitowa daga ɗakin. " Amina ce ta kwaso mana wata gayyar tsiya dubeta".ya ƙarishe maganar yana mata nuni da inda nake tsaye. kallona balaraba ta farayi from toes to head.Kafin tace"baiwar allah ina iyayenki?". A hankali nace"suna nan", "To maza-maza ki fice daga gidan nan kinada iyaye ki,barosu ki zauna damu.malam wannan yarinyar nan ba mamaki cikin shege tayi iyayen suka koro ta", Wani zafi naji a raina furcin balaraba sun soki zuciya ta,bansan sanda hawaye suka fara gosilo a fuska na ba. Roƙon sa anty amina ta shiga yi daya barni na zauna,sai daya kafa mata sharuɗa kan zata ɗauki nauyin ci da Sha na. Ta yadda itama balaraba kashedi tamin akan,kar nasake na shiga harkan ɗanta KABIR, ɗakin anty Amina muka shiga. Kallo ni tayi tana cewa" Hibba na roƙe ki dan girman allah ki dubi darajan taimakon dana miki ki kiyaye kanki daga shiga harkan balaraba da ɗanta,har ki zamo silar tarwatsewar aure na". "In sha allah Anty zan kiyaye haka". "Yauwa ki tashi kiyi alwala kiyi salla". Ta nunamin banɗakin dake cikin ɗakin na shiga nayi alwala nafito nayi salla. Ina zaune a inda nayi sallan nace"Anty Dan allah zanyi ƙira da wayanki inbazaki damu ba?". Cikin sakin fuska ta miƙomin wayar sannan ta fice daga ɗakin. Numbern yaya Fawas na saka daman na haddace ta akaina,na shiga dialing numbern. Inna ƙira caraf!yaɗaga inajin muryansa na fara hawaye to ma mezan faɗa mishi?nace masa na baro gida kenan saboda baffa zai aurar dani?ko kuma ince mishi na shiga duniya?saboda za'amin auren dole ko kuma saboda baffa ya dakatar min da karatuna?. Kashe wayar nayi ba tare dana mishi magana ba,muryarsa ma kaɗai danaji yasamar min da kwanciyar hankali. Kaina na kifa akan gwiwowina ina rusar kuka,tare da tinanin rayuwar dazan tsinci kaina anan gaba. __________________HABIB__________________ Ta bangaren habib kuwa rashin samuna a waya,da kuma rashin dawowata makaranta da bashir ya sanar dashi ban yi ba yasashi cikin tashin hankali. Kwance yake akan bed ɗinsa a part ɗinsa a gidan uncle suraj,yana dialing numberta kamar kullum yauma switch off aka ce masa,cigaba yayi da dialing numbern har izuwa lokacin da yasira ta shigo ɗakin.ko ƙaran shigowarta baiji balle sallamar data shigo dashi. Gefenshi ta zauna tana bubbuga pillow daya ɗaura kansa a kai tana cewa"hamma!hamma!!hamma!!!". Figigi ya tashi ya zauna ya haɗe rai yana cewa" wai ke ban hanaki shigo min ɗakin ba sallama ba". "Ayya hamma wallahi nayi sallama sai dai inbaka ji dan na shigo na tardaka tanata tinani". Yasira ta faɗa tana ƙoƙarin zaman gefen shi. Dafe kansa yayi tare da furzar da iska daga bakinsa. Sosai yasira ta fuskan ta akwai abinda ke damunsa tace" hamma kana cikin damuwa meyake damunka hamma na?". "Ba komai ƙanwata gajiyace kawai" A nitse tace" hamma zanfi yadda inkace min bankai inji damuwarka ba akan kace min ba komai". Cike da ƙosawa da sauraron surutunta yace" yasira nace miki ba komai ko", Miƙewa tayi tana cewa"okay tinda bazaka faɗa min ba hamma bari naje na faɗawa ummi watakil ita ka iya sanar da ita". Riƙo hannunta yayi yana cewa" zauna". Ba musu ta zauna tare da cewa" to inajinka hamma meye damuwarka?". A hankali ya dogo idanunsa dasu ka rikeɗe suka koma jajir ya zuba mata tare da cewa da ita ba komai. Ajiyan zuciya ta sauƙe kafin tace "hamma nasan ni bazan iya maka maganin damuwarka ba amma ban iya tayaka da addu'a,please hamma na meke damunka?". Nan fa ya sanar da ita komai har da yanda ya daina samun na a waya,gashi Dr bashir yace masa ban dawo school ba sannan sun sa Faisal ya ƙira.yaya fawas amma wayarsa shima kullum a rufe. Ya ƙarishe maganar tare da sassauta muryarsa sannan ya cigaba da cewa. "Yasira bazan boye miki ba,Innason hibba kuma zuciya bazata iya jure tashin taba duk ban furta mata ba,ina tsoron duk abinda zai sanyan ku tashin hankali mussamman ace nine sanadinsa,ina tsoron na rasa hibba domin muddin hakan ya faru zaku iya rasani". Tun daya fara maganar ba abinda yasira,take yi illa hawaye tabbas ta tausayawa ɗan-uwan nata matuƙa. Cikin kulawa tace" hamma kaje gidansu mana". " Yasira naje sau babu iyaka amma aka ce min sun tashi tun bayan rasuwar babanta". Riƙo hannunsa tayi tace"hamma bi'izininlahi ta'ala zata bayyana sannan zata amshi soyayyarka". Ajiyan zuciya sannan yace"allah yasa hakan ƙanwata,Dan ina fargaban saku iya rasani matuƙar na rasa hibba". Haka tayita kwantar masa da hankali har tasamu ya fito yaci abinci. Haka abubuwa suka yita tafiya duk weekend habib sai yaje damaturu yayin dashi da Dr bashir zasu garzayo potiskum,amma kullum bacigaba. Harsu shahida suka tambaya ko muna waya dasu,suka ce tun gaishewar rasuwar Abba dasu min basu sake samuna ko a waya ba. Ranan habib yana office ya dafe kansa ga tulin files ɗin dasuke gabansa,amma ya kasa dubasu,shigowar PC ɗin sane ya sashi ɗago kansa. "Sir waɗannan turawan masu company sarrafa alkama a chine ɗinnan sun iso har na shirya meeting ɗin". PC ɗin ya faɗa yana kallon shi. Miƙewa habib yayi ya nufi ɗakin taron nasu koda yaja ma yakasa tsinana wani abin kirki,a haka suka tashi gida ya nufa. Yana isowa ya nufa direct part ɗinsa ya shiga ya wuce bedroom kan bed ɗinsa ya faɗa yana sauƙe numfasha a hankali. Yakai kusan 30min a haka sannan ya tashi ya shiga bathroom yayi wanka, sannan ya fito ko mai bai shafa ba ya zara doguwar rigar jallabiyarsa fara tas! sannan ya fito ya shiga part ɗin ummi. Tare da uncle suraj yasame su sai yasira data zubawa makeken tv ƙiran plasma dake manne a cikin wall ɗin parlon, ido tana kallon wani series(hawas Maya)da ake haskawa a mbc Bollywood. Yana shigo da sallama ɗauke a bakinsa,ummi ta amsa sallamar gefen yasira ya zauna yana yiwa uncle suraj sannu da hutawa. Sai daya tambaye shi ya companies ɗin?yace" alhamdulillah daddy komai yana tafiya yanda akeso". "Masha Allah I hope kana shan magungunan ka". Daddy ya tambaya cike da kulawa Sai da yayi ƙasa da kansa sannan yace" E daddy Ina sha". Kallon yasira yayi yanda ta zubawa tvn ido ko kiftawa babu,da alama tana enjoying kallon series ɗin. "Wai ke yanzu kinajin abinda suke faɗa ne kika wani zuba ido haka?". Dariya tayi sosai sannan tace" hamma ina ganewa mana,kaima inkana kalla yau da gobe zakana fahimtar me suke faɗa".ta ƙarishe maganar tana mai da kallonta ga tvn. Murmushi yayi kafin yace"Gobe sayyid zai dawo ai munyi waya dashi ɗazu yake faɗamin sun sama hutu zaiyi maganinki inya dawo ai kinsan halinsa sarai". Sayyid lecturer ne a freedom college of nursing and midwifery kano,ita kuwa yasira tana shekaran ƙarshe a alƙalam university dake cikin katsina nan.inda take karantan biological science. Zaro idanu yasira tayi tana faɗin "na shiga uku hamma kawai kace mugun zai dawo". Nan ta miƙe ta nufi upstairs tana ta faman gunaguni. Dariya habib yayi sosai irin shirmen yasira wasu lokatan sukan mantar dashi damuwar dayake ciki,suma su ummi da daddy dariyar suke kafin ummi tace. "Zai dawo zaki maimaita a gabansa". Miƙewa daddy da habib sukayi,saboda ƙiran sallan magriba da'aka farayi,habib na Miƙewa yaji kamar wani Abu ya tukare masa zuciyarsa. Nan da nan yaji ƙirginsa ya masa nauyi da wani jiri dayake ɗibarsa,tangal-tangal yayi kamar zai faɗi daddy ya riƙi shi da sauri yana faɗin"habib lafiya?". Wani tari Mai ƙarfine ya sarƙe sa cikin ƙanƙani lokaci Duk yafita hayyacin sa. Ummi ta kawo masa ruwa,daddy ya basa sannan tarin yaɗan lafa daddy yace. "Tashi mu tafi asibiti habib". Ya faɗa yana ɗago habib ɗin "A'a daddy ai naji sauƙi ma". Badan sun so ba haka suka barshi dan basa son takura masa. Haka suka tafi masallaci suna dawowa ya wuce part ɗinsa,wanda ya sama rakiyar daddy. Sam bacci yaki ɗaukar sa har aka kira assalatun asuba,yanda yakejin jikinsa bai jin zai iya tashi balle har ya fita. A bedroom ɗinsa yayi,salla a zaune ma ya yita sannan ya koma ya kwanta kan bed ɗinsa. ƙarfe 9:00am dai-dai na safe Sayyid ya dawo cike son ɗan nasu Daddy da Ummi suke amsa gaisuwar dayake musu,ita kuwa Yasira tana maƙale jikin Ummi kamo kunnenta Sayyid yayi yana cewa. "Wato kin gani shine ko gaisuwa babu?". Tunin Yasira ta saki ihu tana yarfa hannu,tana faɗin "A'a Hamma Sayyid kayi haƙuri,wayyo Ummi zai tsinkemin kunne". Saketa yayi yana dariya tare da faɗin" ina hamma fa?". "Yana part ɗin sa" cewar ulUmmi Part ɗin Sayyid ya nufa yana tura kofan bedroom ɗin,ya hango shi kwance a ƙasa cikin jini da duk alamu aman jinin yayi. A kiɗime ya nufoshi yana kiran sunansa,da ƙarfi"Hamma!Hamma!! Hamma!!!". Wayarsa ya ɗauka ya kira wayar Daddy yana faɗa masa halin dayazo yasama Hamma Habib ɗin a ciki. Dukkaninsu suka shigo bedroom ɗin, ɗaukar shi Daddy da Sayyid sukayi suka wuce asibiti dashi. Emergency aka shiga dashi yayin da Yasira keta shirga kuka hakama uUmmi,sun kai kusan 1 hour suna jira,kafin likitan ya fito yace. "Daddy da Sayyid su same shi a office". Ummi da Yasira kuwa ɗakin da'aka shiga dashi suka shiga,yana kwance yana bacci ansa masa robar ruwa.Fuskarsa tayi fayau da ita sai ɗan raman dayayi. Kallon likitan Daddy yayi yace" doctor meyake damunsa?". Sai da likitan yayi Jim kafin yace,"Damuwa ce ta masa yawa kuma matuƙar ya cigaba da zama a haka zuciyar sa tana cikin barazana,dan zata iya bugawa ako yaushe". Sai da likitan ya numfasa sannan ya cigaba" Akwai abinda yake so Wanda bai same shi ba". Mamaki ne ya cika daddy fal! yana maimata,furcin likitan "wai damuwace ta masa yawa". Miƙewa yayi ya fice, ba tare daya ƙarisa jin sauran maganan da likitan ya cigaba dayi ba. Sayyid ma fitowa yayi daya gamajin sauran maganan da likitan ya faɗa musu yabi bayan daddy. Ɗakin da'aka kwantar da habib suka shiga,har yanzu bai farka ba. Gefenshi Daddy ya zauna,ya riƙo hannun sa sannan ya shiga faɗin. "Habib meyeke damunka a cikin wannan duniyan?mena gaza maka Wanda uba yake yiwa ɗansa?Habib ban barka kayi maraicin iyayenka ba domin na maye maka gurbin su?". "Wai meyake damunsa ne?,meye likitan yace?".uUmmi ta shiga jero tambayoyin a lokaci guda. Nan Sayyid ya faɗa mata komai.Kuka ta saka mai sauti tana cewa" innalillahi!da wani ido zan kalli Granny na gaza samarwa Habib farin-ciki" Da ƙarfi ta furta "Habib meke damun zuciyarka?". Dukkansu kuka sukeyi bamai bawa wani haƙuri.Fita Daddy da Sayyid sukayi masallacin dake cikin asibitin,nan kuwa yasira ta sama damar faɗawa mmi komai game da damuwar Habib ɗin. Ta tausaya mishi matuƙar,su Daddy suna dawowa kuwa suma ta faɗa musu. Tunda Sayyid ya sanarwa Granny ta ɗaga hankalin ta sai datazo, Nan fa Daddy ya dage sai an fitar dashi waje domin sama masa ingantaccen lafiya acewar sa zuciya ba wasa bace. Likitotin sukace masa ba sai an fitar dashi ba suma zasu bashi kyakykyawan kulawa. Amma Daddy ya dage sai ya fitar dashi,dan tunda sukazo asibitin yau kwana uku kenan sau ɗaya yayi magana. Nan ya shirya musu tafiya malesia domin kula da lafiyarsa,tare da Daddy da sayyid aka tafi. Yasama kyakykyawan kulawa daga likitotin kasar,amma sun shaidawa Daddy cewa zuciyarsa ta taɓo.Dan haka a kiyaye ɓata masa rai. Kwanan su goma sha shida aka sallame su,tare da kafa musu sharaɗin duk bayan wata uku Habib ɗin zai dinga zuwa ana duba lafiyar zuciyar tashi. Yasama kulawar ahlin nasa sosai har ya fara dawowa hayyacinsa,ƙoƙarin sa shine ya manta da hibba kodan farin-cikin iyayen nasa. Daddy kuwa tunda yasira ta faɗa musu nice sanadiyar damuwar Habib ɗin.Ya kira Bashir suka tattauna akan zance,nan Bashir yasake sanar dashi wasu abubuwan daya sani dame dani. Nan fa Daddy ya zubawa gidan TV da radio kuɗi anata cikiyata.dan a nasu zaton tare da Umma da kuma yaya Fawas muka tashi daga gidan. ___________________________________ Ina zaune a tsakar gida ina wanke-wanke,anty Amina kuwa ta tafi shago. Kabir ya shigo tare da wasu abokansa uku."Ke ki kawomin abincina ɗaki". Ya faɗa da tsan-tsan izza. Ko kulashi ban yi ba na cigaba da aukina,ya ƙaracewa "bakya jinane?,nace kikawomin abinci ko". Sai a lokacin na ɗago tare da faɗin,"Amma ai kasan niba yar aikinku bace dazaka sani aiki ko?". A harsale Kabir yayo kaina "ke ni kike faɗawa haka?", "An faɗa maka ɗin".na faɗa ina ajiye soson wanke-wanken dake hannu na. Mari ya shiga sauƙe min hagu da dama yana faɗin" shashasha to ko ita wacce ta kawoki gidan bata isa ina faɗa tana faɗa ba balle ke wawuya kawai,wacce zaman gidan iyayentaya gagare ta". Yana gama faɗin haka ya shiga ɗakin sa yayin da zugan abokan nasu suka rufa masa baya. Dafe kuncina nayi ina hawaye, a hankali na maimaita furcin kabir"WACCE ZAMAN GIDAN IYAYENTA YA GAGARE TA". Share hawaye na nayi cikin sanyin jiki na ƙarisa wanke-wanken sannan na dawo ɗaki nacigaba da sana'ata wato kuka,sai daf da magriba sannan anty amina ta dawo ko kaɗan ban bari ta fahimce wani Abu ba. Washe gari da wuri anty Amina ta tafi shago,sannan nima na fito na kama aikin dana san ko sharafar mutuwa nakeyi sai nayi wannan aikin. Share gidan sannan nayi wanke-wanke na wanke banɗaki. Na koma ɗaki na kwanta,a hankali naji ɗumin hawaye nabin fuskana.Ajiyan zuciya na saka tare da kwantar da kaina akan pillown. Haƙiƙa kowa da irin tasa ƙaddarar a rayuwa,mutuwa ta rabani da Abba ƙaddara kuma ta rabani da yaya Fawas. "Ya rabb ka nufeni da cimma abinda na fito nema wato karatu,na cika burin Abba sannan na cimma ƙudurin yaya Fawas". Na faɗa ina share hawayen dake bin fuska ta. Kamar daga sama naji balaraba na kwaɗa min kira,cikin sauri na miƙe na fito nace" gani". Ba tare ta kalle inda na keba tace"ke hibba saboda tsabar rashin mutunci shine baki sharewa Kabir ɗakinsa ba?,bayan nasanar miki kullum kina tashi kizo ki share masa ɗaki". Sanyayyan ajiyan zuciya na saka sannan nace"naga bai tashi daga bacci bane shiyasa ban shiga ba". Muryan Kabir naji yana cewa yayin dayake fitowa daga ɗakin nasa yana faɗin" munafuka ni tun yaushe na tashi,zaki wani ce wai ban tashi ba". "Yi shirunka basai ka ɓata bakinka ba ni nasan halinta tsabar munafurcine". Cikin sanyin murya nace"kabir kaji tsoron Allah yanzu fa ka tash........." Ban ƙarisa maganar ba Balaraba ta rufe ni da duka tana faɗin"shegiya munafuka acikin mu yawake miki ƙarya?". Duka na takeyi tamkar tsohuwa ta sama shantu,tun ina bata haƙuri har maganar ma ta gagareni. Anty Amina ce ta shigo tare da sakin salati,ta dakatar da balaraba daga dukan datake min ta hanyar cewa. "Haba! Balaraba meye baiwar Allahn nan ta miki a dunyia?,karki manta fa itama ƴace ga wasu sannan ƘADDARA CE(littafina mai zuwa in sha Allah) ta rabota da iyayenta". Cikin matuƙar ɗaga murya Balaraba take cewa,"To ni ina ruwa nace ina ruwa na.dakike cewa wai ƙaddara ce ta rabota da iyayenta, wayasan abinda ya rabota da iyayen nata".ta ƙarishe maganar tana wani huci. Ɗagoni anty Amina tayi ta riƙo hannuna tana faɗin"sannu hibba", A hankali na miƙe idona cike da hawaye nace"anty Balaraba Allah shine shaida na ban taɓa aikata,abinda kike zargina dashi ba sannan bashi ne silar barowata gida ba". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 1⃣3⃣ Taɓe baki Balaraba tayi tare da cewa, "ke akwai abinda zaki faɗa Wanda zan yarda shine, kuma wallahi yau ko sharafar mutuwa kikeyi a cikin gidan nan,sai kin sharewa kabir ɗakinsa." Cikin zafin rai anty amina ta shiga faɗin" ya isheki haka balaraba ina so kisani daga ke har ɗanki HIBBA ba baiwa na kawo muku ba". Tana gama faɗin haka taja hannuna muka shiga ɗaki. Zaunar dani tayi akan kujera tare da riƙo hannuna,dukka biyu tasa cikin nata tace. "Hibba ina mai baki haƙuri akan irin abubuwan da abokiyar zama take miki ita ɗanta ki cigaba,da haƙuri wataran sai labari". Cikin kuka daya ci ƙarfi na nace"anty Amina zamana a gidan nan,inaga kamar ina ja miki magana nagode da taimakon da kikamin Allah ya saka miki da alkhairi,amma ni inaga kamar inna tafi rayuwar gidan aurenki zaifi samun kwanciyar hanaki". Dakatar dani tayi da cewa"hibba ki daina faɗan haka,tun kafin kizo haka nake zaman haƙuri a gidan nan nidai ina mai baki haƙuri" ta ƙarishe maganar tare da sharemin hawayen dake bin fuskana. Buɗe baki nayi da niyyar yin magana amma anty Amina ta hanani wannan damar. "Tashi kije kiyi wanka,bari na haɗa miki ruwan zafi ko"anty Amina ta faɗa tana ƙoƙarin tashin daga kan kujerar damuke zaune. Toilet ta shiga ta haɗamin ruwan zafi sannan ta fito,tana cewa "kije kiyi wankan ko sai kiyi salla kici abinci". A hankali na tashi duk wata gaɓa a jikina ciwo yakemin na shiga banɗakin,rufe ƙofar nayi na jingina kaina ajikin ƙofar ina wani irin kuka mai raunana zuciyar mai sauraro. Shin haka daman rayuwar kowacce mace,yake cike da ƙalubale?ko kuma tawace kawai haka?.Allah sarki mutuwa ta tona min asiri,ta rabani da Abba.umma tagaza janmu a jikinta. A lokuta da yawa ina tinanin,anya umma tun da muka bar gidanta ta taba tinaninmu kuwa?.Dalilin maraici yau gani a inda bansan kowa ba. Ashe duk macen da bata gaban iyayenta, kallon ƴar iska ake mata kamar dai yanda balaraba take min?. Nayi kuka sosai sai dana,tausayawa kaina na daina fuskata duk ta kunbura saboda dukan danasha da kuma kukan danayi. Wankan nayi sannan nayi alwala nafito,anty Amina natarar tazabga tagumi hannu bibiyu. Cikin nutsuwa nace"Anty lafiya?" A hankali ta ɗago kanta tare da faɗin"hibba lafiya wani tinani nayi nace ko zamu fara fita shago tare". "To anty" na faɗa ina barin wajen Cike da farin cikin amsar Dana bata tace" yauwa hibba kinga duk zaki rage wannan tinane-tinanen da kikeyi". Wucewa nayi ba tare dana amsa mata ba nayi salla,sannan ta kawomin abinci tunda nasa abincin a gabana na kasaci.akan sallayan na kwanta nan take wani baccin wahala ya ɗaukeni. Tamkar a mafarki najiyo muryan mijin anty amina,sai zazzaga masifa yake yi,a firgice na tashi na nufi wajen na tsaya daga bayan labulen ɗakin ina jiyo abinda yake faɗa. Cikin matuƙar bala'i yake cewa"Amina na faɗa miki,tun ranar da yarinyar nan tazo gidan nan kar ta shiga harkan kabiru amma bataji bako?". "Malam baka fahimce abinda ya faru bane yarinyar nan ba f.....". Dakatar da ita yayi da cewa" to mezan fahimta ko ita balaraban data gayamin,zata miki ƙarya ne?nidai na faɗa miki ta fita harkan kabiru,dan wallahi in irin haka ya cigaba da faruwa to billahillazi a bakin aurenki". A firgice anty Amina tace"saki kuma malam meyayi zafi?". "Komai ma yayi zafi kabiru shi kaɗai nake dashi bazai yiyu ba yarinya tazo har gidan ubansa,tana cin arziki sannan ta nema ta takura mishiba,Ke baki haifamin ba kuma a nema kashe min Wanda nake dashi". Kukan anty Amina ke dannewa ne ya sama nasarar fitowa"malam,amma kasan ai haihuwa ta Allah ce ko?kuma nima bai manta dani ba". Tsaki ya sake yayi shigewarsa ɗaki,cikin sauri nima na koma na kwanta,inajin shigowar anty Amina ɗakin na rufe idona kamar mai bacci. Zama anty Amina tayi tana kuka,inajinta amma na kasa tashi inbata haƙuri. A hankali nima hawaye suka fara bin kuncina,Matar data taimake ni a lokacin danake matuƙar buƙatar hakan,ta ɗauke nauyin ci da Sha na lokacin da uwata ta gaza yin hakan a gareni,ta zauna dani zama na domin Allah duk da kasancewar bata san labarina. Yau a ta dalilina,take zubda Ƙwalla,a hankali nace"ya Allah ka bani abinda zan sakawa wannan baiwar taka dashi. ___________ GANO________ Zaune baffa yake,a kofar gida wani Mai mashin yazo ya faka dai-dai kofar gidan. Yaya fawas ya sauƙo daga mashin ɗin,ya nufo inda baffa ke kishingiɗe.bakinsa ɗauke da sallama. Durƙusawa yayi ya gaishe da baffa cikin sakin fuska baffa ya amsa tare da cewa"mutan bauchin yakubu yaka baro gidan naku?". Washe baki yaya fawas yayi kafin yace "baffa duk lafiya suna gaisheku". "Madallah ka tashi ka shiga ciki kasha ruwa inna ma tana ciki".baffa ya faɗa yana ɓantarar guntun goron sa Cike da rashin fahimta yaya fawas yace"baffa hibba fa?". Gyaran zamansa baffa yayi kafin ya shiga faɗin " fawasu yau kusan wata biyu hibba bata cikin gidan nan". Cike da rashin fahimta yaya fawas ya kuma tambayar sa"Baffa ko ta koma makarantar ne?Dan kullum ina ƙira wayarta,bana samu shiyasa ma nace bari nazo naga ko lafiya?". Gyaran muryan baffa yayi,tare da bayyanawa yaya fawas duk abinda ya faru. Wasu hawaye ne suka shiga zubowa daga idanun yaya fawas nan take ya suma a wajen,miƙewa baffa yayi yanata doka salati ya shiga gida ya ɗauko buta ya zuba mishi ruwa. Dogon ajiyan zuciya yaya fawas yasaka baffa ya riƙeshi yanata jera mishi sannun har suka isa cikin gidan,hajara ta shimfiɗa musu tabarma suka zauna. Cikin wani irin yanayi Mai matuƙar ban tausayi da wahalar fassarawa,yaya fawas yace. "Kuma baffa duk an bincika wajen sauran dangi bataje wajensu ba?". Caraf inna ta amshe zancen da cewa" gashi nan ba yanda banyi dashi akan ya haƙura da maganar nan ba amma yayi burus da maganata ai yanzu kaga abin daka ja mana". "To inna to karatun nata fa?"furcin yaya fawas Sai da inna ta gyara ɗaurin zaninta kafin tace" Adamu shine silar duk abinda hibba ta aikata sannan ka shirya fuskantar ubangijinka da laifin kasa sauƙe hakkin marainiyar da aka barma". Sai data numfasa sannan ta ɗaura da cewa"Adamu sanin kan Kane ka ƙuntatawa,rayuwar hibba dakai da matarka". Ajiyan numfashi baffa yayi cike da nadaman abinda ya aikata yace. "Inna ban taɓa tinanin hukuncin dana zartar akan hibba,zata iya barinmu saboda wannan ba". Cikin zubda ƙwalla murya can kasa,yaya fawas ke cewa" baffa baka kyauta min ba,shin baka tinanin halin da hibba zata shigane?,ko baka tausayin tane?,jinin kace fa ita ƴar ɗan-uwanka ce fa". Dafa kafaɗunsa baffa yayi yana cewa "fawasu ka kwantar da hankalinka in sha Allah duk inda,hibba take tana hannu mai aminci.Daga nan ka wuce wajen mahaifiyar ku ka tambaya ko can hibban taje". "Baza taje ba baffa kuma ko taje ma umma baza karɓe ta ba".cewar yaya fawas. Ɗaga hannanyen sa sama yayi,ya shiga faɗin" ya Allah ka tsare min ƴar-uwata aduk inda take acikin duniya,ka amintar da ita cikin amincewar ka dawo mana da ita cikin aminci". Yana gama faɗin haka,ya kifa kansa akan gwiwowinsa yana wani irin kuka Mai cike da tausayawa. Miƙewa hajara tayi tana cilla musu harara tayi shigewar ta ɗaki.. ______________HABIB_______________ Zaune yake akan kujera a cikin bedroom ɗinsa,na gidan granny sunzo gaishe ta tare dasu ummi,riƙe da wayarsa yana dialing numberna. Kamar kullum wayar a kashe yajita,dan uncle suraj har a companyn mtn ya bada numbern da zaran ansa layin akan waya zasu sanar dashi. Cilla wayar yayi kan bed ɗin sannan ya kwantar da kansa,akan hannun kujerar. Dafe ƙirjinsa yayi saboda bugun da zuciyar sa take masa,da sauri-sauri. Lokaci guda yaji numfashinsa yana ɗaukewa,tari ne ya sarke shi sosai ƙirjinsa yaƙara dafewa da ƙarfi. Tari yake yi sosai,har da jini ga numfashin sa daya ke barazanar barin gangar jikinsa,faɗowa yayi daga kan kujerar. Dai-dai lokacin da ummi ta shigo ɗakin salati,ta saka tana nufo inda yake a ruɗe ɗaura kansa tayi akan cinyarta sannan ta riƙo hannunsa tana murzawa. ƙwalla nabin fuskarta,ta fara kiran sunansa "Habib!Habib!!Habib!!!". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________ Page 1⃣4⃣ Lumshe idanu sa yayi a hankali muryansa can ƙasa-ƙasa yace"Ummi zan mutu zuciya na ciwo yake min". Ummi da duk ta rasa nutsuwar ta tace "A'a Habib bazaka mutu ba,ciwo bashine mutuwa ba". Wani razanan ne ihu tasaka ganin Habib ɗin ya daina motsi,hakan yasa su Granny,Sayyid,Yasira da kuwa iya shigowa. Dan dama sunzo gidan Granny ne dukkan sunzo gaisheta,Daddy kuwa yayi tafiya Japan. Asibiti suka wuce dashi GENERAL HOSPITAL dake cikin garin damaturun emergency aka shiga dashi. Wayarsa dake hannun sayyid ne, ta fara ringing ganin sunan bashir ya bayyana cikin screen ɗin wayar. Yasashi ɗaga kiran,nan yake sanar dashi halin da habib ɗin yake ciki,tambayarsa yayi"wani asibitine?"sayyid ya gaya masa. Granny keta safa da marwa kofan ɗakin da'aka shiga da Habib,Yasira da Ummi kuwa sai kuka suke iya nata lallashinsu. Within 15min Bashir ya iso cikin asibitin,Sayyid ya ƙira ya fito ya shigo dashi bangaren da aka kwantar da habib ɗin. Zama Granny tayi,tana sauƙe ajiyan zuciya kafin ta shiga faɗin"Ban shirya nasaka ba Habib da farko na rasa halima,nasara mijina sannan na rasa dukkanin iyayen ka Habib a lokaci guda.ya Allah ka ɗauki rayuwa domin na tabbatar bazan iya jure rashin Habib ba". Dafa ta Sayyid yayi yana cewa"haba! Granny inkina faɗin haka mu kuma ai sai ki karyar mana da zuciya, In sha Allah Hamma bazai mutu ba ki daina kuka".ya ƙarishe maganar yana zama kusa da ita Yana rufe bakinsa likitan dake duba Habib ya fito,cikin sauri suka ƙariso gare shi suna tambayar ya jikin Habib ɗin?. "Ku kwantar da hankalinku,Gajiya Ku biyo ni office".iya abinda likitan ya faɗa kafin ya wuce office ɗinsa Binsa sukayi a baya har izuwa cikin office ɗin nasan. Zama yayi tare dayin gyaran murya sannan ya fara faɗin"Hajiya Habib yana da wata damuwa a cikin ransa ko kuma ince akwai wani abu dayake so wanda bai samu ba,advice ɗin dazan baku a matsayinku na makusantan sa,Ku zauna dashi Ku tattauna ya faɗa muku damuwarsa inba haka ba hajiya I'm sorry to say za'a iya rasa sa gaba ɗaya". Ajiyan zuciya Mai nauyi Granny ta sauƙe tare da cewa "to doctor ko zamu iya ganinsa?". "E you can see him amma please kar ayi hayaniya dan hakan zai iya sa jinin sa ya hau". Fita sukayi suka nufa ɗakin, da aka kwantar da habib ɗin. Yana kwance yana bacci zama sukayi duk suna kallonsa, fuskar sa kaɗai ta isa mutun ya iya fahimtar girman damunwan dake cikin zuciyarsa. "Yanzu yakuke ganin za'ayi?" Cewar granny. Ummi tace " hajiya nidai gaskiya a tinani na,yabar ƙasan nan gaba ɗaya, dan inyaga ya nisanta da ita koyaga ya dena samun wasu labaru akanta hakan zai taimaka wajen rage tinaninta dayakeyi". Tana rufe bakinta habib yafara buɗe idanunsa a hankali. Dafe kansa yayi saboda wani irin nauyi daya yi masa,yana faɗin "wash!". Cike da nuna kulawa Granny tace "sannun babban mutum,inane yake maka ciwo?". Cikin ƙarfi hali yace"Granny kaina kaina ciwo yakemin". Ƙara riƙo hannunsa tayi tana murzawa tace "sannu". Bashir yace" Granny bari naje,na sanarwa doctor ya tashi daman yace inya tashi a sanar dashi".ya na gama faɗin haka ya fice. Sannan suka dawo tare da doctor ɗin duba shi yayi sannan ya bashi maganinsa ya sha,cikin ƙanƙanin lokacin ya sama bacci. Sai da dare sayyid ke sanar da daddy halin da habib ɗin yake ciki, faɗa daddy yayi sosai akan me za'a ajiye shi a asibitin 9ja?. Bayan yanada likitansa na mussamman dayake duba lafiyarsa a malesia. Tun kafin ya dawo ya gama shirya fitar da habib izuwa malesia. Haka kuwa akayi yana dawowa,ya ɗauke sa suka tafi malesian tare da sayyid wannan karan hadda granny kwanan su biyar suka dawo. Amma shi habib ɗin acan suka bari shi daman sugama magana da granny akan zai zauna acan.Na wasu lokaci kafin likitotin sun ƙara tabbatar da samuwar lafiyar zuciyarsa. Watansa uku acan bikin bashir ya taso da ƙyar granny ta amimce masa yazo. ________________________________________ Ina kwance a ɗaki anty Amina ta fita,unguwa naji balaraba na ƙwala min kira. Na fito nace"gani". Wasu tulin kayan wanki ta nunamin,tana cewa. "Ga kayan kabir nan yanzu ki wanke masa sannan inki gama kizo,zan aikeki kasuwa kimin cefa ne". "Anty balaraba waɗannan kayan,ai bazan iya wanke su ayau ba Sai dai na raba su yau nayi,gobe ma nayi". na faɗa ina ƙarewa yawan kayan kallo. Harara ta ɓalla min tana faɗin"ke zan sharara miki mari fa,ki kiyaye ni fa,a yau zaki wanke kayan nan gabaɗaya". Nauyayyen ajiyan zuciya na sauƙe, kayan na ɗauka na fara wankin. Tun safe har bayan la'asar ban gama ba gashi saboda anty Amina bata nan,ko abinci banci ba dama itace mai bani kuma yau bata nan. Haka na wanke kayan tas!ko sannu balaraba batamin ba balle tace min madalla. Ina shara anty Amina ta dawo,nabar sharan naje na karɓi ledan dake hannun ta ina mata sannu da zuwa. Cikin fara'a take amsa min,sannan muka nufa ɗaki. Tsawa balaraba ta daka min tana cewa "munafuka inazakije?baki gama min aikin dana saki ba?". Jikina na rawa nace"anty balaraba innayi salla zan fito na ƙarisa". "Yimin shuru wato kinga ta dawo ko shine zaku shige ɗaki kuyi sana'ar taku ta gulma ko?".cewar balaraba Ajiyan zuciya anty Amina ta sauƙe kafin tace"hibba shigo ɗaki kiyi salla,sannan kici abinci dan nasa tun safe baki ciba". Cikin ɗaga murya anty balaraba tace,"Yo daman wa kika ajiye acikin gidan dazai bata abinci?". Ba mu kulata ba,muka shige ɗaki anty Amina ta bani abincin data sayo min a hanya. Naci sannan nayi salla,na fito na ƙarisa aikin.na zaune kan sallaya bacci ya ɗauke ni. Washe gari anty Amina ta tashi da ciwon kai,don haka ko shago bata fita ba. Kamar kullum ina tashi na fara wanke-wanke nayi shara sannan na wanke banɗaki. Ina gamawa zan shiga ɗaki kabir yana fitowa daga ɗakinsa,wani harara ya cilla min mai cike da tsana lokacin da muka haɗa ido dashi. Ƙofar ɗakin balaraba ya nufa,yana faɗin"mama!mama!!mama!!!". Fitowa tayi tare da malam habu tace"lafiya kabir?". Marairaice murya yayi kana yace" mama dan Allah kiga wani irin wankin da yarinyar nan tamin duk basu fita ba salon kawai ta dafarmin da kaya". Kamar jira malam habu yakeyi ai kuwa ya rufeni da faɗa tare da cewa" ki ɗauki kayan nan yanzu ki kara wanke su. Wasu hawaye masu zafi suka shiga rige-rigen fitowa daga idanuna,kayan na kwatsa na fara wankesu, inayi ina hawaye har kiran sallan azahar ban gama ba. Fitowa anty Amina tayi tace "hibba kibar wankin nan ki tashi kije kiyi salla sannan kici abinci". Miƙewa nayi naje nayi alwala sannan nayi salla,Anty amina ta ɗebo min abinci inasa abincin a gabana naji muryar balaraba sai ashariya takeyi. Tana cewa "malam fito,kagane min ikon Mai sama yanzu na sauƙe abinci wani yazo ya ɗeba". Malam habu yana fitowa yafara kiran anty Amina, tana fitowa ya hau ta da masifa. Ta inda ya shiga bata nan yake fita ba,cikin sanyin murya anty amina tace "ayya malam a hibba fa na ɗebawa,naga tun safe take aiki acikin gidan nan kuma ban fita ba balle insayo mata shiyasa na ɗeba mata". Zabga mata mari malam habu yayi hagu da dama,sannan ya ɗaura da jaddada mata cewa. "Shin Amina ban faɗa miki nauyin ci da shan yarinyar nan yana kanki ba tun lokacin dakika kawo ta?,maza-maza ki wuce ki dawo da abincin nan". Ina zaune a inda anty Amina tabarni ta shigo ta ɗauki abincin, daman ko hannu na ban saba. Sannan ta dawo tace"hibba kiyi haƙuri,bari na baki ɗari biyu kije ki sayo wani abincin". "A'a anty kibar shi ma banajin yunwar". Bata kulani ba ta ɗauko kuɗin ta miƙomin ban mata musu ba na karɓa na fita. Ina tafe ina hawaye wannan wani irin rayuwa ce?,komai ya faru dani UWATACE SANADIn zubar hawaye na. Ina cikin tafiya wani Mai mota yayo kaina,kafin na kauce masa har ya iso gareni. Fitowa yayi daga cikin motar yayo kaina cike da faɗa ya fara zagina. Wata macece zaune agaban motar wacce bazan iya faɗin matarsa ce ko ƙanwarsa ba,ta fito tana ƙoƙarin hana shi zagi na.Ni kuwa ina tsaye na kasa ko motsi sai hawaye danakeyi. Wani mummunan kallo ya jefomin yace "dallah dube ta fa ko haƙuri bata iya badawa ba".hannu ya ɗaga niyyar sauƙe min mari. Cikin sauri na runtse idona,jin banji sauƙar Marin ba yasa na buɗe idona. Wani mutum ne ya kama masa hannun daya ɗaga da niyyar mari na. Ɗago kaina nayi da niyyar, gani ko wanene caf" idanuna suka sauƙa akan fuskan HABIB. Zaro idanu nayi bakina narawa nake furta" habib". Kallo ya tsareni da shi a hankali lips ɗinsa suka motsa tare da furta"HIBBA kece". Juyawa yayi yana bawa Mai motan haƙuri, ni kuwa cikin sauri na tsara ta cikin mutanan dasuka fara tarowa a wajen na bar wajen. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _________________________ Page 1⃣5⃣ Bayan wani shagon aski,na tsaya ina hangen habib sai bawa Mai motan haƙuri yakeyi. Yana gama bashi haƙurin ya juyo inda yabarni tsaye sai dai,bai ganin awajen ba waige-waige ya farayi. Tambayar mutanen wajen ya shiga yi ko akwai wanda yaga fita ta daga wajen?. wani yace masa "ai ta daɗe da barin nan dama tare kuke ne?". Da sauri-sauri zuciyarsa ke bugawa,tamkar zata fito daga cikin ƙirjinsa jingina bayansa yayi a jikin motarsa. Sannan ya fara zamewa a hankali har yakai ƙasa ya zauna. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!". Ya furtawa a hankali badan mutumin daya shaida masa yaga wucewa ta ba,tabbas da zaice gizo idanunsa ke masa. Wayarsa ya ciro daga cikin aljihunsa ya ƙira drivern sa,ya faɗa masa inda yake yace yazo ya ɗauke sa,dan a yanda yake jin kansa yanzu bazai iya driving ba. Ina tsaye bayan shagon naga tafiyar habib, wasu hawaye masu zafi suka fara bin kuncina. Tabbas bayan Abba da yaya fawas,banida wani masoyi kuma jigo kamar habib,amma bazan iya bayyana masa kaina a halin danake ciki yanzu ba. Da kyar nake ɗaga kafata har na isa gida kabir na iske a ƙofar gidan sai daya dallo min harara sannan yace. "Ke kuma lafiya zaki dawowa mutane gida kina kuka?". Ban kulashi ba nayi wuceta cikin gidan,anty Amina tana tsakar gida tana haɗa murhu na wuceta zan shiga ɗaki. Muryar tace ta dakatar dani tana faɗin "hibba lafiya meya faru?". Ban kulata ba dan ji nayi bakina ya kasa furta komai na shige ɗakin. Ina shiga na ƙara sakin wani Sabon kuka,anty Amina ta biyo ni ɗakin. Dafa ni tayi tare da faɗin" hibba lafiya ko kabir ne ya miki wani abun?". Kai na girgiza mata alamar a'a,tace "to menene?",faɗawa jikinta nayi nacigaba da kuka na itama tana tayani. Mucin kuka Mai iskar mu, Kafin anty Amina ta ɗagoni daga kwanciya danayi ajikinta.Hawaye fuskana ta fara share min tace "ya isa haka hibba meya saki kuka?". "Babu komai"na faɗa cikin kukan dayake shirin sarƙe ni. Miƙewa tayi tana cewa"shikenan hibba tinda bakai naji matsalarki ba,sai ki cigaba da kukan".cikin sauri na riƙo hannun ta. Nace"anty kiyi hakuri ki zauna". Zama tayi tana fuskanta na tace "inajinki menene?". Ajiyan zuciya nasaka yayin da hawayen danake ya tsananta. "Anty tabbas ki riƙe ni amana zan sanar dake labarin rayuwata,inkiga zaki iya zama dani a haka zanso hakan in kuma bazaki iya ba nagode da taimakon dakika min a rayuwa". Nan na sanar da ita,komai game dani ita kuka ni kuka ba mai bawa wani haƙuri.Har nagama hawaye bai bar zuba daga idanuna ba. Anty Amina tayi ƙarfin halin faɗin" tabbas rayuwa cike take da jarabawa kala-kala,ban taɓa jin labarin irin naki ba hibba.Ban taɓajin inda uwa ta aikata irin abinda ummanki ta miki keda ɗan-uwanki ba Allah yajiƙan abbanki". A zuciya na amsa da amin saboda kukan danakeyi yaci ƙarfina jin abubuwan nakeyi kamar yanzu suke faru,mussamman ranan da Abba ya rasu da kuma ranan damuka rabu da yaya fawas. Kamo hannuna tayi,tasa cikin nata sannan tace. "Hibba zan tsaya miki ki cigaba da karatunki,duk dama nima bawani ƙarfi ne dani ba gidan abincin na watace nake tsaye mata akai, amma gobe zanje gidanmu zan sanarwa mahaifiya ta inada dabbobi acan sai na tsayar nabaki kuɗin kiyi amfani dasu ki koma makarantar". Kuka na saka Mai sauti,nace"anty nagode Allah yasaka da alkhairi". "Ba komai hibba ai mun zama ɗaya yanzu".cewar anty Amina Ranan kwana nayi ina kuka washe gari anty Amina ta shirya,zata tafi gidansu dake karamar hukumar daura. Tare tace zamu je amma sai na tashi da matsanancin ciwon kai,hakan yasa ta tafi ita kaɗai. Ina kwance a ɗaki ina rawar ɗari balaraba ta banko labulen ɗakin sannan ta shigo tana cewa. "Nizan fita ki ɗaura min girki sannan kabir yana gida,duk abinda yace kimishiki tabbatar kin mishi". Ban damu na sanar da ita halin danake ciki ba dan nasan,hakan bazai sa ta basa aikin da tace nayi ba.Dan nasan ko sharafar mutuwa nakeyi sai nayi aikin nan kamar yanda ta saba faɗa min hakan. A hankali nace" to adawo lafiya".Bata kulani ba illa ficewa datayi daga ɗakin tare dajan wani tsaki mai dogon zango. Ina kwance naji kabir na ƙwala min ƙira da kyar na tashi na fito ina cewa" kabir lafiya?". Harara ya watsa min tare da cewa" ki wuce ki ɗaura min ruwan wanka".yana gama faɗin haka ya koma ɗakinsa. Wuta na haɗa na ɗaura masa ruwan sai daya tafasa sannan,na juye a bukati na nufi ɗakin kabir Kasancewar banɗakin sa acikin ɗakinsa yake. A ƙofar ɗakin na tsaya ina cewa" ga ruwan wankan". Daga ciki naji yana cewa "ki shigo ki kaimin banɗaki". Ban kawo komai a raina ba na shiga ɗakin, kasancewar irin jan kunnen da balaraba tamin kafin tafita,koma yanzu banason na ƙara jawa anty Amina magana awajen malam habu. Har kofar banɗakin na ajiye masa bukatin ɗin.Na juya zan fita naji kabir ya riƙo hannuna, firgice duk jikina ya ɗauki rawa na juyo. Bakina na rawa na furta" kabir meye haka?".na fara ƙoƙarin ture shi daga jikina. Manna bayana yayi jikin bango ɗakin tare da riƙe dukkanin hanneyana biyu cikin hannunsa ɗaya,yayin dayasa ɗayan hannun nasa ya cire min hijabin dake kaina. Zani ne ajikina kaɗai ɗaurin ƙirji kaina ko kwali babu,muryata na rawa nake faɗin. "Dan Allah kabir kayi haƙuri ka barni da mutumcina". Bai kulani ba illa wani irin kallon daya tsareni dashi da idanunsa da suka rikiɗe suka zama jajir. Bakina narawa na ƙara cewa"kabir kayi wa girma Allah kayi haƙuri,na haɗa ka da girman allah karka ketamin haddina". Duk magiyan danake mishi hakan baisa ya barni ba,cillani yayi kan gado yafara nufoni. Kuka nake ina masa magiya ina ja da baya har na iso ƙarshen gadon,ina waige-waige na hango kwaskon turaren wuta cikin azama na ɗauko kwasko. Kabir yana yiyowa kaina na buga masa kwaskon a goshinsa,cikin jin azaba yadafe goshin nasa da hannunsa. Nan take kuwa jini yace salama alaikum ya fara zuba kamar da bakin ƙwarya. Ɗago kansa yayi yana kalloni da idanusa dasukayi jajir,gashin kaina ya damƙo da ƙarfi ya cillani ƙasa daga kan gadon. Ɗago ni yayi yafara wankeni da mari hagu da dama,sannan ya hankaɗe ni kaina ya bugu da window glass ɗin windown ya sari hannuna. Wani ihu nasaka mai ƙarfi saboda azabar danaji.Dai-dai lokacin balaraba ta turo ƙofar ɗakin,daman kabir a buɗe yabarta. Salati tasaka tare da jefawa kabir,wani irin kallo Mai cike da tuhuma ganin jinin dake ta zubowa daga goshinsa. Cikin sauri kabir yace"wallahi mama ban mata komai ita ta shigo har cikin ɗakina". Cikin zafin rai da wani irin hucin ɓacin rai balaraba ta nufo inda nake durƙushe. Ɗago ni tayi tare da rufeni da duka ta ko'ina dukana takeyi tana faɗin. "Hibba Allah ya isa tsakani na dake ɗan nawa ƙwalli ɗaya shi kikeson ki lalata min?". Tana juyawa ta hangi bukatin ruwan zafin dake ajiyen ƙofar banɗakin kabir. Tureni gefe tayi na faɗi yayin da ita kuma taje ta ɗauko bukatin ruwan zafin. Ina kwance a ƙasa ina fitar da numfashi sama-sama naji sauƙar ruwan zafin a jikina,wani irin azababben ihu na saka lokacin dana kejin ruwan zafin na ratsa duk ilahirin sasan naman jikina. "Munafuka daman ki shigo gidan da nufin lalatamin yarone?to Allah yafi ƙarfin ki,ki tashi kibarmin cikin gida kafin na illata ki". Ƙafafuna na karkarwa na fara ƙoƙarin tashi,hijabina na saka sannan na tashi ina tafiya ina faɗuwa har na fita daga cikin gidan. Wani irin azaba nakeji acikin jikina ƙafata ko takalmi babu haka nake tafiya. Ga raɗaɗin da hannuna yake min inda glass ɗin ya yanke ni,idanuna basa ganu min komai sai baƙin duhu.duk gaɓoɓin jikina jinsu nake kamar ana sassara minsu. Faɗuwa nayi daga nan bansake sanin inda kaina yake ba sai buɗe ido nayi na ganni a gadon asibiti. Wani masallaci ne a cikin unguwan suka haɗa kuɗi suka ɗauki nauyin jinya ta. Ina fita daga gidan su kabir balaraba ta kira malam habu yana isowa,ta fara cewa"malam Amina ta cucemu ta kawo mana annoba cikin gida". "Balaraba meya faru?" Ya tambaya cikin zaƙuwa dason jin abinda zata faɗa masa. Nan ta faɗa masa ƙarya da gaskiya wai inason na lalata musu yaro,har neman kashe shi naso nayi na fasa masa goshi. A take a wajen malam habu,ya kira anty Amina a waya ya mata saki uku sannan suka wuce da kabir asibiti. ____________________HABIB______________ Tun lokacin da drivernsa ya ja motar suka nufi gida, tun acikin motar yaji zuciyarsa ta masa wani nauyi. Suna isa ya wuce part ɗin ummi, tana zaune tare da yasira wacce yanzu dawowarta daga makaranta. Driver ya shigo dashi,cikin Sauri ummi ta miƙe tana tambayar ko lafiya?. Zaunar dashi driven yayi sannan yace "hajiya kirana yayi nazo na ɗauke shi saboda bazai iya driving ba, amma sai naga kamar bashi da lafiya shine na taimaka masa na shigo dashi". Ummi tace " mun gode". Sannan ya fita kusa dashi ummi ta zauna tana cewa "sannu habib ina ka ajiye maganinka yasira ta ɗauko ma kasha?". A galabaice yace"yana bedroom ɗina cikin fridge". Cikin sauri yasira taje ta ɗauko maganin sannan ta ɗauko masa ruwa yasha. Yana sha ya sama bacci kallonsa ummi takeyi sosai tabbas yana matuƙar azabtuwa. Wayar tace ta fara ringing ganin sunana Granny ya bayyana cikin,screen ɗin wayar yasa ta ɗauka tare da kara wayar a kunnenta. Cike da girmamawa ta gaishe ta amsa tare da cewa" ya jikonki nawa?". Ajiyan zuciya ummi ta saka kafin tace"Hajiya duk lafiya habib ne dai yanzu ciwon sa ya tashi amma yanzu alhamdulillahi harma ya sama bacci". Ummi ta faɗa tana kallon fuskar habib ɗin. Salati Granny tasaka kafin tace,"ni daman tun farko banso wannan zuwan nasa da yayi ba,shine dai ya dage sai yazo auren bashir ɗinnan nafiso.Yayi zaman sa acan malesian a cigaba da duba lafiyarsa, yanzu ga irinta nima gobe zan taho katsinan". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________ Page 1⃣6⃣ Tun da Ummi ta sanarwa Daddy, ya taho Sayyid kuwa tunda Yasira ta faɗa masa halin da Hamman nasu yake ciki. Yace shima zaizo amma Daddy yace "masa yayi zamansa,jikin nasa da sauƙi daman ciwo ne na lokaci guda kuma yanzu da sauƙi". Nan yadage har sai da Daddy ya barshi nazo. Granny kam fafur taƙi yadda da maganar da Daddy yake ce mata,na jikin nasa yayi sauƙi. Sai datazo jikin Habib yayi sauƙi alhamdulillah,suna zaune akan dining sunayin break fast. Daddy yayi gyaran murya sannan yace" Habib duk ganinka cikin jinya yasa mun mance bamu tambayeka abun daya tayar maka da ciwonka,wai meya faru ne?". Ajiye spoon ɗin dake hannun sa habib yayi kana a sanyaye yace"Daddy ranan dana fitane naga hibba,da farko na zata gizo tamin kamar yanda kullum hakan take faruwa dani amma dana tambaye mutanen wajen,sai Ku shaida min dasuga lokacin datake barin wajen". Ummi tace"hakan yana nufin tana cikin nan katsina kenan?". "To ya kamata naje na sanar da ƴan sandan dana bawa aikin binciko ta,su binciko ko'ina domin tana cikin nan katsina"cewar Daddy. "Amma Daddy ko photon ta fa bamu dashi taya kenan insun ganta zasu ganeta?". Kurɓan tea ɗin dake gabansa Daddy yayi kafin yace"mama na munje wajensu da Habib, an ƙira Mai zane yana siffantar mishi ita shi kuma yana zana photon ta,to izuwa yanzu dai munada photon ta". Ajiyan zuciya Granny ta sauƙe wacce daman tun zuwanta bata koma ba tare da faɗin" to Allah ya bayyana ta",dukkanin su suka amsa da amin. Suna gama cin abincin Daddy ya biya ta station ya sanar dasu sannan ya wuce office. Saura kwana uku auren Bashir Habib ya shirya tafiya damaturu,Tare da granny da kuma Yasira suka tafi. Anyi wasu event kafin ɗaurin auren,ana ɗaura auren kuwa Granny tace Habib ya koma malesia. Hakan nan ya koma sosai Daddy,Granny da Ummi suka masa faɗa akan yawan tinanin dayakeyi,har rubutu Granny tasa a dunga masa yana sha. Daga can ya cigaba da kula da companies ɗinsu. _____________________________ Nasha jinya sosai a asibiti tamkar bazanyi rai ba. Wannan kuɗin da'aka haɗa mina masallaci dashi limamin masallacin ya cigaba da kulawa dani,dan nace musu "ni marainiya ce bansan kowa ba a garin". A haka aka sallame ni daga asibitin sosai nayiwa liman godiya tare da matar dasuke ta dawainiya dani. Sun tambaye daga nan ina zanje?,nace "musu zanje wajen dangina". Fatan alkhairi suka min sannan na tafi,matarsa har da bani dubu biyu wai nasha ruwa a hanya. Ina tafe ina tinani bansan inda zan nufa ba,bansan sanda hawaye yafara bin fuska naba. Izuwa yanzu kam nasan na jazawa Anty Amina, bala'i da masifa a rayuwar aurenta watakil ma izuwa yanzu malam Habu ya sake ta. Wani kuka mai ƙarfi ne ya kubce min WAYYO ALLAH.wai shin tunda muka rabu da Umma ta sake tinanin mu kuwa?. Ban ankara ba naji mota ta kwashe ni,Wasu maza biyu ne,suka fito daga cikin suna min sannu. Tare da tambayata"ko naji ciwo?"banji ciwo sosai ba kurjewa ne kawai,a hannuna da kuma ƙafata. Asibiti muka wuce, akamin dressing wajen dana ɗan ji ciwon. Ɗayan magidanci ne wanda nake kyautata zaton mahaifin saurayin,dasuke tare ne. Sukaje zasu kaini gidansu na huta tukun sai sukaini gidanmu,a gate ɗin wani tankamemen gida motar ta tsaya. Ya dannan horn gateman ya fito ya wangale musu gate motar tashiga. Cikin parking lot tayi parking fitowa sukayi,nima nafito a hankali ina ƙarewa girman gidan kallo. Wasu mata biyu na hango sun nufo inda muke tsaye. Tace"alhaji wannan itace yarinyar da sayyid ke gaya min a waya,kun bige da mota?". "Itace wallahi". Ta kalloni cike da tausayawa tare da faɗin "Ayya sannun ko". A hankali nace"yauwa sannu ina wuni".ta amsa tana cigaba da cewa "YASIRA Ki kaita tayi wanka,tayi salla sannan kikawo ta taci abinci". Wacce aka kira da Yasira ta amsa da" to Ummi",sannan ta riƙo hannuna muka shiga cikin gidan. Wani ɗaki muka shiga ta nunamin banɗaki nashiga nayi wanka,Sannan ta bani doguwar rigar material na saka nayi salla. Sannan muka fito falo ta kawomin abinci naci. Cikin jimami yYsira tace"yaya Sayyid a ina abin yafaru".Nan ya faɗa mata komai. Mahaifinsu yace"baiwar Allah a wani unguwa kike mu kaiki gida?". Kaina na sunkuyar ƙasa nace"ni ba ƴar garin nan bace". "To inane garinku?".Ummi ta tambaya Har yanzu kaina na kallon ƙasa nace"ni ƴar potiskum ce na jahar yobe". Ummi ta kuma cewa" To a ina iyayenki suke?". "Mahaifina ya rasu mahaifiyata kuma bama tare da ita".na faɗa ina danne ruwan hawayen dake shirin zubo min. Cike da tausayawa Ummi ke faɗin" Allah sarki baiwar Allah ko sanar damu labarin ki bamu da niyyar cutar dake". Haka kawai naji zuciyata ta gamsu dana sanar dasu labarin rayuwa ta a karo na farko,anan na sanar dasukomai akaina. Tun Dana fara sanar dasu Ummi ke hawaye,Yasira kuwa kuka take sosai har da shashsheƙa. "Innalil lahi wa'inna ilaihir raji'un", mahaifin nasu ya faɗa. Sannan ya cigaba da cewa"baiwar Allah haƙiƙa labarin rayuwarki yana cike da darrusa masu yawa,amma kinyi kuskure dakika gujewa danginki domin ita mace a gurare uku ya kamata a sane ta gaban iyayenta,ko gidan mijinta inko ba'a same ta a ɗaya daga cikin waɗannan biyun ba to a same ta a kabari.zamu zauna dake tsakani da Allah bamu da nufin cutar dake ni sunana ALH.SURAJ,ga mata HAJ.AISHA.Sannan ƴaƴanmu Sayyid da Yasira sai kuma yayansu yana malesia". Ummi ta ɗaura da cewa"meye sunanki". "Sunana Hibba". Share hawayen fuskar ta Yasira tayi kafin tace "Ummi nima yanzu na sama ƴar-uwa,daman yaya Sayyid da Hamma sai suyi ta haɗemin kai". Dariya sukayi kafin alh.suraj wanda naji suna ƙira da Daddy ya ɗora da cewa. "Zamu zauna dake har izuwa lokacin da kike tinanin danginki,zasu haƙura akan maganar wannan auren da zasu miki sai mu maidaki garesu,ke kuma ki nema yafiyarsu na bujirewa umarninsu dakikayi,kuma in sha Allah za kicigaba da karatun ki". Cikin zubda ƙwalla na matso na durƙusa a gabansa ina masa godiya. Ummi tace"yasira ki kaita ki nuna mata ɗakin dazata zauna". A hankali na Miƙe nabi bayan Yasira,ɗakin dake gefen nata muka shiga tace" Anty ga ɗakin ki sai ki duba inda abin da bai miki ba,sai ki faɗawa Daddy". Murmushi na saka nace"ɗakin yamin". "To masha Allah bari na barki ki huta".tana gama faɗin haka ta fice daga ɗakin. Yasira ta girmeni sosai amma koda wasa bata taɓa kiran suna na kai tsaye ba,sai dai tace min Anty haka nan nima nake Kiran ta da anty. Haka na cigaba da rayuwa,ƙarsashin kulawar alh.Suraj da iyalansa,babu tsangwama balle kyara. Sosai na maida hankali na ga karatuna domin shine burin yaya Fawas ne a rayuwa zamantowa ɗan jarida,dan haka na jajurce naga na zamto ƴar jarida. Nacigaba da karatuna a Alƙalam university lokacin kuwa Yasira ta gama. Kullum cikin maganar Hamman su sukeyi amma nikam ko a photo ban taɓa ganinsa,sai dai naji lokuta da yawa suna cewa suna matuƙar kama da Yasira. Sau da yawa insuna waya da Yasira takance min nazo mu gaisa,nace "kibarshi kawa Yasira wataran zamu haɗu". Bazan taɓa manta wani safiyar ranar litinin ba. Tun safe muka tashi da shirye-shiryen dawowar Hamman nasun, girki kuwa munyisa babu iyaka. Ƙarfe biyu Daddy da Sayyid, sukaje airport domin ɗauko sa. are da Yasira mukayi arranging dinning table ɗin sannan muka wuce ɗakina mukayi wanka. Ina fitowa daga wankar nawuce gaban dressing mirror, nafara shafe jikina da Mai,sannan na Zara doguwar rigar atamfar da daddy ya mana anko nida Yasira. Ina ɗaura ɗan kwalina Sayyid ya shigo ɗakin yana cewa"hey ladies Hamma has arrived." Da gudu Yasira ta fice tabi bayan Sayyid.Ina gama ɗaura ɗan kwalina feshe jikina da turare,sannan na wuce kitchen na ɗauko fruit salad ɗin damuka haɗa. Na ɗaura akan tray sannan na nufi falo bakina ɗauke da sallama,Ummi ce ta amsa sallamar sannan cikin farin,-cikin daya kasa buyiwa a saman fuskan ta tace"To Hibba yau dai ga ɗan nawa kingan shi nan". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 1⃣7⃣ Ɗauko kaina nayi ina satar kallonsa yana zaune agefen yasira ya lumshe idanunsa,yayin da yasira keta gabza masa surutu. A firgice na saki trayn dake hannuna ya faɗi ƙasa nan take ya tarwatse. Sayyid yace" Hibba lafiya?".A hankali Habib ya buɗe idanunsa dan ganin meyake faruwa. Lokaci daya muka haɗa ido a razane shima ya miƙe tsaye baki na rawa ya shiga faɗin "HIBBA". Hawaye nabin fuskata yana wanke hodar dana shafa nace "Habib". Miƙewa Ummi tayi daga inda take zaune tana cewa" Habib daman kasan Hibba ne?". Wasu hawayen farin-ciki,ne suka fara zubowa daga idon habib yace"Ummi itace fa". Sayyid cikin zaƙuwa yace"hamma itace Wa?". "Hibbata Sayyid itace". Cike da al'ajabi dukkaninsu suka kallo ni ummi kuwa da murna da mamaki ya gama,cika fuskar ta tace"Habib kana nufin Hibba itace yarinyar dakake so?,wacce kayi jinya a sanadin soyayyarta?". " Ummi itace". Rungumoni Ummi tayi tana jero godiya ga Allah"Alhamdulillah Allah yakawo mana,sauƙin jinyar Habib har gida".shi kawai take mai-maitawa. Runguma Habib ɗin sayyid yayi,yana faɗin na tayaka murna hamma. Kallo ya tsareni dashi yana sakin ajiyan zuciya,dafe ƙirjinsa yayi da sauri tare da runtse idonsa da ƙarfi. Ummi ta ke duban sa tace" habib lafiya?". Ƙara dafe ƙirjinsa yayi da ƙarfi yana cewa"Ummi zuciya na yamin nauyi". Cike da nuna kulawa dukkaninsu suke,masa sannu zaunar dashi Sayyid yayi ya kwanta akan kujeran tare da ɗaura Kansa akan cinyar Ummi. Yasira na zaune akasa kusa da kujerar dayake kwance akai ta riƙe hannunsa. Sayyid kuwa yana zaune a gefen Ummi sai sannu suke jera masa,cike da kulawa Ummi take kallon sa tare da faɗin" Habib anya kana shan maganinka kuwa?". Cikin sanyin voice ɗinsa,marar hayaniya yace"Ummi ina sha". "To yanzu ina maganin?". "Yana cikin akwatina".yabata amsa Akwatin na gefena inda nake tsaye Ummi tace"na buɗe na ɗauko masa maganin".Na buɗe na ɗauko sannan na ɗauko masa ruwa.Na miƙawa Ummi dakanta ta bashi maganin yasha.Tashi yayi ya zauna tare da ɗaura Kansa akan,kafaɗun Ummi yana kallona yana sakin murmushi ƙasa-ƙasa. Dai-dai lokacin da Daddy ya saƙo daga upstairs sanye da farar jallabiya,Dan tunda suka dauko Habib daga airport ya shige bedroom ɗinsa sai yanzu ya fito. Tun kafin ya zauna,Yasira tace"Daddy I have a gist for you". "To inajinki auta ta". "Daddy Anty itace wacce Hamma yakeso ɗinnan".cewar Yasira wacce bakin ta ya kasa rufuwa tsabar farin-ciki. Zaro idanu Daddy yayi yana cewa"hajiya wai maganan Dasira haka yake?". "Kwarai kuwa", Ummi ta faɗa tana shafo kan habib ɗin dake kwance akan kafaɗar ta.Godiya Daddy ya farayiwa Allah, kafin ya shiga bayyanawa Habib yanda suka haɗu dani. "Tabbas tun ranar dana fara ganin hibba,nayi zargin itace domin a yanda habib ya siffanta ta,aka zana hoton ta kama ce sosai". Take a wajen Daddy ya kira Granny yasanar mata tayi farin-ciki matuƙa. Dining area muka wuce muka fara cin abinci spoon ɗin kawai naketa,juyawa a cikin abincin nakasa ci Ummi dake ankare dani tace" Hibba lafiya?". Murmushi nasaka kafin nace"mmi lafiya kalau".Ina ankare da Habib sai satar kallona yakeyi,amma naƙi yadda mu haɗa ido dashi. Muna gama cin abincin muka dawo falo yasira tace"Hamma ina tsaraba ta?". Murmushi ya mata yace,"Ƙanwata tsarabarki nanan ɗauko min akwatin can". Ya mata nuni da wani pink ɗin akwati taje ta ɗauko ta ajiye a gabansa. Zungurin kanta Sayyid yayi tare da faɗin"kekam naga ranar dazakiyi hankali,mutumin dayaje jinya ina batun wani tsaraba kuma". Tuno bakin tayi tana matsowa kusa da Hamma Habib ɗin.Buɗe akwatin yayi ya fara Ciro dogayen rigunan abaya yace"Ƙanwata ga tsarabar ake kaɗai na sayo amma yanzu na fasa baki a wat.........". Sai kuma yayi shuru tare da sunkuyar dakansa ƙasa yana ɗan Sosa ƙeya. Cuno baki Yasira ta marairaice fuska kamar mai shirin, yin kuka tana cewa"Ayya Hamma na kayi haƙuri ka bani ". Murmushi ya saka yayin dayake cigaba da ciro kayan yace"sai kiyi kuma nidai na riga na faɗa miki". Wasu turarurruka ma'abota tsada Habib ya ciro tare da matsowa kusa da Daddy, ya ladabtar da murya ya shiga faɗin" Daddy ga naka tsaraban".Cike da happy karɓa yana sanya masa albarka. Ummi kuwa mayafai Habib ya sayo mata ta karɓa cike da farin-ciki,shi kuwa Sayyid wani danƙareren agogo Hamman nasa ya sayo masa. Sannan ya tura akwatin gaban Yasira wacce tun ɗazu take ta rarraba idanu ganin, Hamma ya kusa gama rabon kayan ita baice ga nata ba. Wani murmushi mai sauti,ta saka tare da ƙara jawo akwatin gaban ta tana kara duba kayan.Kallo ni tayi tare da faɗin"Anty zoki ga kayan mana". "A'a basai na ganiba kaya sunyi kyau masha Allah".na faɗa ina sadda kaina ƙasa Kafeni Habib yayi da ido,ko kiftawa bayayi da sauri-sauri ƙirjinsa ke bugawa.Na ɗauke idona daga cikin nasa,yana ɗago kansa suka haɗa ido da Ummi. Wata iriyar kunya ce ta lulluɓeshi cikin sauri ya tashi ya nufi upstair yana murmushi.Haka na wuni ranan duk banida kuzari maganar Ummi ce ketamin yawo cikin kwakwalwata"yarinyar dakeso,wacce kayi jinya domin soyayyar ta". Washe gari ina kitchen ina haɗa breakfast.Habib ya shigo yana sanye da farar jallabiya har ƙasa,a ƙofar kitchen ɗin ya tsaya yana kallona. Nikuwa sai aikina nakeyi,don bansan akwai mutum awajen ba.Ajikina kawai naji ana kallona,ina juyo wa kuwa muka haɗa ido da sauri na sunkuyar dakaina ƙasa nace"ina kwana". "Lafiya". Ya amsa yayin dayake shigowa cikin kitchen ɗin,yana cigaba da cewa" bari na tayaki aikin". Ban kulashi ba nacigaba da aikin danakeyi.Wuƙa ya dauƙa yafara yanka albasa yana cewa" Hibba I see like kamar bakiji daɗin ganina ba?". Ajiyan zuciya na saka kafin nace"na isa nace haka kai da gidanku,ince banji daɗin dawowanka ba." Fuskanto ni yayi sannan a hankali ya shiga faɗin"Nasan jiya kinyi mamakin furcin Ummi ko?". Kaina na ɗaga masa alamar e,Sannan ya cigaba da faɗin "Hibba" cikin kakkausar murya ya kiran sunan wanda hakan,ya sanyani ɗago kaina na kalle shi sannan na maida idona ƙasa. "Basan ina sonki ba sai,lokacin dana dena samunki a waya na cigaba da ɓoye hakan a raina har izuwa wani lokaci,yayin da hakan yamin babban lahani a cikin zuciya dalilin hakan iyaye na suka turani malesia.Dawowa ta kenan nazo auren Bashir shine ranan muka haɗu dake duk lokacin dana tinaki sonki ƙara dawowa sabo yake a cikin zuciyana,dan Allah ko sau ɗaya ne ki furtamin kina sona". Tsare shi nayi da ido hawaye nabin fuskana kamar yanda zuciya ta tasha faɗa min,tabbas yau na ƙara gaskatawa banida wani masoyi a cikin duniyan nan da ya wuce Abbana da yaya Fawas sai kuma Habib. A hankali nace" Habib wataran zan furta hakan a gareka." "Meyasa sa wataran?,sai bayan cutar sonki dake addabar zuciyana ta kasheni sannan ki furta, min Hibba meyasa bakya tausayi nane?" Yaƙarishe maganar tare marairaice fuska. Ɗauke kaina nayi kamar yanda,shima naga ya ɗauke kansa daga gare ni,sannan ya maida hankalinsa kan yankan albasan dayakeyi. Ajiyan zuciya na sauƙe tare da goge hawayen dake bin fuskana nacigaba da aikina. Yana cikin yanka albasan wuƙan ya yanki hannunsa,sakin wuƙar yayi ta faɗi ƙasa. Cikin sauri na iso inda yake sai yarfa hannun yakeyi first aid box na ɗauko masa yayi dressing wajen. Ɗago kaina nayi ina kallonsa nace" sannu". Cikin halin ko inkula yace"riƙe sannunki ai daman ba tausayina kikeji ba".yana gama faɗin haka ya fice daga kitchen ɗin. Da kallo nabi bayansa yayin dayake ficewa daga kitchen ɗin,A haka na gama girkin na jeresu akan dining sannan na koma,ɗakina nayi wanka doguwar rigar material nasaka maroon color sannan na fito falon. Sayyid na tarar zaune na gaishe shi ya amsa cikin sakin fuska,sannan na zauna tare da ƙurawa tv kallo. Muna zaune Yasira ta shigo tace "ayya Anty harkin gama break fast ɗin shine baki tasheni na tayakiba?". " Ba komai Anty Yasira ai naga kina baccine". Sauƙowar Habib daga upstair,shi ya dakatar da yasira daga maganar dazatayi. Sanye yake cikin shigar shadda Navy blue, hular Kansa ma da rantsin blue ajikintaSajen fuskarsa ya ƙara kwanciya luf asamar haɓarsa.A hankali yake sauƙowa daga upstair ɗin yana ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa. Gaishe shi Yasira da Sayyid sukayi a tsare yake amsa gaisuwar tasu nikam daman mun gaisa a kitchen. A tare Ummi da Daddy suka fito,dukkaninmu muka gaishe su suka amsa sannan muka wuce dining muka fara break fast. Tun da muka fara cin abincin babu Wanda yayi magana,sai Habib da yace "Sayyid ka shirya zamuje wajen Granny". " To Hamma"cewar Sayyid ɗin. Da haka muka gama cin abincin har compound muka musu rakiya,sai wani cin magani yakeyi ko kallon inda nake baiyiba suka tafi. Suna isa cikin garin Damaturu direct new bura-bura estate suka nufa gidan Granny. Wangale musu gate,gateman yayi suka shiga sukayi parking sannan suka fito suka nufi cikin gidan bakinsu dauƙe da sallama. Ba kowa a falon sai house maid ɗin,Granny tana goge-goge ta rusuna ta gaishe su. Sayyid yace "Granny fa?"tace "tana ɗaki tana salla". "To in ta fito,kice mata mun tafi masallaaci". Da to ta amsa sannan suka juya suka fita. Masallaci muka nufa saboda ƙiraye ƙirayen sallan la'asar da aka farayi.suna dawowa suka wuco part ɗin Granny tana zaune a falon suka tarda ita. Cikin farin-ciki ta tarbe su tana faɗin"lale da mutan malesia zance ko katsina". "Granny yanzu kam sai dai mutan damataru" Gaishe ta sukayi ta amsa tare da tambayar su mutan gidan,suka amsa mata da duk lafiya. Dinnig suka wuce ta zuba musu dambu wanda yasha kayan lambu da mai,ga lafiyayyan yaji.sosai sukaci abinci dan ba ƙaramin daɗi ya musu ba. Suna gama ci suka dawo falo kwanciya sayyid yayi akan ɗaya,daga cikin kujuren falon ai kuwan nan baccin gajiya ya ɗauƙa shi. Kusa da Granny habib ya zauna tana mata tausa a ƙafarta,kallon shi tayi kafin tace"Babban mutum Suraj ya sanar da ni yanzu haka,kuna tare da wannan yarinyar cikin gidansa sannan ya sanar dani labarin rayuwarta ko wannen mu shaida ne akan irin son dake mata,amma ba musan manufar ka akan hakan ba.Babban mutum nasan halin kane kyautatawa dan girman Allah ka riƙe yarinyar nan da amana sannan kuma ka daraja ta". Sosai maganganun Granny suka ratsa ƙalbinsa a hankali yake furta. "In sha Allah Granny zaki same ni mai biyayya da dukkanin umarnin ki". "Za muyi magana da Suraj ɗin,yanzu kam tunda mun samo maslaha ga matsalar sai a maida ta ga dangin ta mu nema maka auren ta,a yi abun nan hankali kowa ya kwanta"cewar Granny. Sosai Granny ta masa nasiha sannan ya fita yaje gidan Bashir nan,yake sanar dashi maganar dasu tattauna da Granny ɗin.Sosai Bashir ya masa murna tare da masa fatan alkhairi sai da yayi sallan magrib a can sannan ya dawo. Part Granny ya wuce nan ya tarda ta,zaune ita da Sayyid zama yayi yana cewa Sayyid."Ka tashi kenan malalaci kawai daga katsina,zuwa damaturu shine duk ka wani gaji haka". Murmushi Sayyid ya saka kafin yace"Hamma kawai kwantawa nayi na huta shine fa,baccin ya sace ni". Shima Habib ɗin murmushi ya saka haka nan ma Granny,sosai suka yi hirar su sannan suka ci abincin suka kwanta da gobe da wuri zasu koma zai ajiye Sayyid a kano sannan shi ya wuce katsina. Washe gari da wuri suka shirya sukaci ɗan waken da Granny tayi musu,nan Habib yake tambayar Iya dan tun jiya dasuka zo bai ganta ba. Granny tace"tayi wata tafiya ce zuwa ƙauye,ƙanin ta yana aurar da ƴarsa". Sun sama rakiyan Granny tare da kyawawan addu'o'i ta musu,a kano Habib ya sauƙe Sayyid domin aikin sa daya bari a can ɗin sannan ya wuce katsina. Koda ya iso office ya fara wucewa sai da tashi sannan ya wuco gida,part ɗin sa ya wuce direct ya nufi bathroom tare da sakewa kansa,ruwa sannan ya yasa kaya mara nauyi sannan ya kwanta nan kuwa baccin gajiya tayi awon gaba dashi. Sai dab da magrib ya tashi alwala ya ɗauro ya fita izuwa masallaci,nan ya zaune har akayo isha'i sannan ya dawo ya wuce part ɗin Ummi. Ina zaune ina karatun exam wanda muke dab da farawa cikin kwanakin nan,ya shigo falon ya zauna gaishe nayi ya amsa cikin sakin fuska yana faɗin"karatu akeyi ne?". nace "e".Yayin dana fara harhaɗa littattafaina zan koma ɗaki,na cigaba da karatuna muryar sa ce ta dakatar dani yana cewa"Fatima tsaya inason magana dake". Wani iri naji duk nasan Fatima suna na ne,amma ba kowa ke ƙirana dashi ba.ba tare dana juyo ba nace"inajinka". UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 1⃣8⃣ Tashi yayi ya iso inda nake tsaye,yana fuskanta ta sannan ya naɗe hannayen sa a bayan sa. "Munyi magana da Granny yau sannan izuwa yanzun na tabbatar da sunyi maganar da Daddy,akan maganar zuwa gidan ku nema min auren ki.Banason na tirsasawa zuciyar ki domin nafi son ta amshe ni cikin daɗin rai shin kina isona?zaki iya aure na?". Baki nane ya soma rawa na shiga faɗin"Habib idan nace banason ka to nima nasan ƙarya ne,amma yanzu karatuna shine mafi muhimmanci a gare ni ,mu jingine wannan maganar sai zuwa wani lokaci"ina faɗin haka na wuce ɗaki na barshi tsaye a wajen. Koda na koma ɗakin gagara na karatun yayi,hakan yasa na rufe littafin na lula izuwa duniyar danafi samun nutsuwa a cikin ta wato tinani.Ina zaune a haka Yasira ta shigo tana cewa"Anty kina nan ashe ke muke jira ki fito mu ci abinci. Tashi nayi nabi bayan ta muka fito tare,muna gama cin abinci muka tattare wajen tare da Yasira,zan shige ɗaki Daddy yace"na zauna ya nason magana dani".dawowa nayi na zauna. Ajiye jaridar dake hannunsa yayi sannan ya shiga faɗin"Munyi magana da hajiya kuma gobe in sha allah muke son muje gidan ƙanin mahaifinki da kika labarta mana yana zaune a kano,domin nemawa ɗan mu Habib auren ki.Dan haka muke son kimana kwantance duk dacewa ke zamu je". Wani zazzafar ajiyan zuciya na sauƙe kafin nace"Daddy ina neman alfarma a ɗan jinkirta zuwan har izuwan lokacin da zan kammala karatuna". "A'a Hibba aure baya hana karatuna,kamar yanda karatun baya hana aure.Na miki wannan alƙawarin zaki cigaba da karatun ki koda bayan auren ki da Habib ne,sannan ni zan kashe miki ko nawa ne har sai kin cimma burin ki"cewar Daddy. Ummi ce ta ɗaura da cewa"Hibba muna neman alfarmar ki ki taikama mana wajen cero rayuwar Habib amincewar ki muke nema domin baza mu miki dole ba". Da mai zan sakawa waɗannan bayin allahn,wanda suka bada gudumawa wajen cikar buri na?zuciyata tace kawai ki amshi buƙatar su ki auri Habib hakan zai zamto silar samuwar farin-ciki a zuƙatan su,domin na lura farin-ciki sa shine nasu. A hankali nace"na amince Ummi,nagode Allah ya saka muku da mafifin sakayyar sa". Habib da tun ɗazu yake jiran amsar dazan bawa tambayar Ummi,ya sauƙe ajiyan zuciya yana hamdala. Sosai Daddy da Ummi suke samin albarka,sannan suka shiga tattaunar maganar tafiyar da zamuyi goben.Nidai tashi nayi na koma ɗaki a hankali nake sauƙe numfashi sama-sama yayin da wani kukan da bansan na menene ba ya kufce min. Ɗan kwalli na na jawo na toshe baki na dashi,ina ƙoƙarin hana sautin kukan nawa fitowa tashi nayi na rufe ƙofar ɗakin sannan na dawo na kwanta na cigaba da kukan. Da wasu idanun zan kalli Inna?,mezan cewa Baffa?,banida ƙwarin gwiwan zan iya haɗa ido da yaya Fawas.watakil ma su zarge ni akan rayuwar dana yi a ba gida ba. Naso sai na kammala karatuna na zamto cikakkiyar ma'aikaciyar aikin jarida,sannan zan koma musu shiyasa ma ban taɓa yiwa su Ummi maganar son zuwa wajen su Baffa ba. Kuka nayi sosai har ina ƙoƙarin shiɗewa ganin haka ya sanya ni tashi nayi alwala sannna nazo na fara gabatar da nafila,ina iddarwa na shiga neman sau-saucin ƙuncin da zuciya take ciki a wajen mahaliccina,anan kan sallayar bacci ya kwashe ni. Washe gari duk muka shirya dan hadda su Ummi da Yasira zamuje Sayyid kuwa zamuje mu ɗauke shi a kanon,tunda muka hau titi nakejin faɗuwar gaba ban san abinda zanje na tarar ba a gano. Muna isa cikin kano muka wuce,freedom college inda Sayyid ke koyarwa muka ɗauke shi dan daman Daddy ya sanar dashi game da tafiyar. Muna isa cikin garin gano nafara kwantatawa Daddy gidan Baffa har muka,ƙofar gidan bansan sanda hawaye suka fa bin fuska na ba sai da naji Ummi ta dafa kafaɗata tana cewa"Hibba yanzu ba lokacin daya dace kiyi kuka ba ki share hawayen ki mu shiga". Share hawaye na nayi sannan muka fito muka shiga cikin gidan dukkanmu har dasu Daddy,Inna muka tarar tana shiƙar wake,sallamar damuka shigo da itane ya sanya ta ɗago kanta tare da sauƙe idonta kan ƙofar shigawa cikin gidan. Sake kwaryar dake riƙe a hannunta tayi,tana waro idanunta wajen tare son gaskaka abinda ta gani bakinta na rawa ta shiga faɗin"Hibba ce koko mafarkin dana saba neyi ne?". Nima tunin hawaye suka fara kai kawo a fuskata nace"Inna nice"na ƙarisa wajenta muka rungume juna. "Hajara fito fito kiga abin al'ajabi"Inna ta faɗa tana ƙara rungumo ni jikinta. "Haba!Inna wai meye ne kike ta wani kwaɗa min kira haka".Hajara ta faɗa tana fitowa daga ɗaki tare da gyara ɗaurin ɗan kwalin kanta. "Wa idona ke nuna min kamar Hibba?wato kin gama yawan duniyar nakin shine yau kuma,kika tino inda muke ko bayan kinsa ƙafa kin fice babu wanda ya ƙara saki a kwayar idon sa".Hajara ta faɗa tana tsaida idanunta akaina. Cikin mu ba wanda ya kula ta,tabarma Innaa ta ɗauko ta shimfiɗa mana muka zauna sannan suka shiga gaisawa dasu ummi. Inna tace"Hibba waɗannan fa ban shaida su ba". Kafin na bata amsa Daddy yace"Inna alkhairine ke tafi damu,amma kafin mukai ga sanar dake zanso ganawa da shi ƙanin mahaifin natan". "Adamu tun farar safiya ya tafi gona,amma yanzu duk inda yake nasan yana hanyar dawowa"cewar Inna. Tsaki Hajara ta saka sannan ta tashi tayi shigewarta ɗakin bayan ta gama cillo mana harara. Muna zaune a wajen Naffa ya dawo muna haɗa ido ya saki fartanyan dake saƙale a kafaɗarsa yana cewa"Mamana ke ce koko gizo idanuna kemin?". Tashi nayi naje na durƙusa a gaban sa hawayen nabin fuska na nace"Baffa nice Baffa na dawo gare ka,ka yafe min na rashin bin umarnin ka nayi". Nuni yamin da hannunsa kan na tashi daga durƙushewar danayi sannan yace"Hibba na yafe miki nima ki yafe min ƙuntatawa zuciyar danayi nasan nine silar komai daya faru dake,kaico! na dana gaza fahimta ƙuncin dana jefa zuciyar marainiya a ciki". "Baffa na yafe maka",riƙo hannuna yayi kuka zauna akan tabarman sannan suka gaida dasu Daddy. Nan Daddy ya shiga labarta masa yanda haɗuwar mu dasu ta kasance,har kuma da irin alaƙar dasuke son ƙullawa da dangin su.Sosai Baffa da Inna suka tausayawa irin rayuwar danayi a gidan Anty Amina. Nan wajen suka tsaida magana akan yanda aure zai kasance suka sanya watanni biyu,Inna ce ke sanar da ni bayan bari na gida yaya Fawas yazo.Nayi kuka sosai lokacin da Inna ke faɗa min irin mawuyacin hali daya shiga. Baffa na roƙa nace ya kira shi yace masa yana neman sa,amma kar yace masa na dawo hakan kuwa akayi a wajen Baffa ya kira yana sanar dashi yanason ganinsa gobe. Sosai Inna da Baffa suka yaba da kamalar Habib da kuma halin dattaku irin na iyayen sa.Sai yamma sosai su Daddy sukayi shirin komawa amma nida Tasira zamu zauna muyi kwana biyu a wajen su Inna. Muna zaune a ɗakin Inna nida Yasira munacin kwaɗon zogalen da Inna ta mana,Sayyid ya shigo ɗakin tare da faɗin"Hibba kije Hamma Habib yana kiran ki yana ƙofar gida". Hijab ɗin na saka na fito shi kuwa Sayyid ya zauna ya faracin kwaɗon shima,a tsakar gidan na tarar da Inna da Ummi sunata firar su kamar dama can sun sa juna. Yana zaune akan benci na hango shi na ƙarisa na zauna nisa dashi,wata leda dake kusa dashi ya miƙo min yana cewa"gashi waya ce ki riƙe a hannun ki dan kwana biyun daza kuyi a wajen su Baffa indinga samunki". Kaina na kallon ƙasa ina wasa da yatsun hannuna waɗanda suka sha jan lalle wanda Ummi tasa aka mana kafin tahowar mu,nace"A'a nagode ka bashi bana buƙatar sa". Tun farko zuwa na gidan su Habib Ummi ta saya min waya,amma na ajiye ta bana amfani da ita dan banda ma wanda zan ƙira da ita. Ajiye min ledar yayi kusa dani sannan yace"gashi nan dai na ajiye miki,kuma nasa miki sim aciki na kuma samiki lambobin su Ummi da Sayyid a cik.....". Saurin ɗago kaina nayi ina kallon shi wanda hakan ya sanya shi kasa ƙarisa maganar daya ɗauko. Yaya Fawas na tino lokacin da ya sayo min waya ranar dazan tafi jami'a,irin kalmaman Habib ya furta min yana cewa"ya samin sim a cikin wayar kuma yasa lambarsa". Saurin mayar da hawayen dasuka ciko idona nayi nace"nagode allah yasaka da alkhairi". Sai daya saki taƙaitaccen murmushi kafin yace"amin ". Wayarsa ce ta fara ruri ya ɗaga da sauri ganin sunan Granny ya bayyana cikin screen ɗin wayar. Sai suka gaisa sannan take tambayar sa sun "iso lafiya?"don ta kira Daddy bai ɗaga ba"lafiya kalau Granny"ya amsa mata dashi. Nidai maida hankalina nayi akan wayar da Habib ɗin ya sayo min,suka cigaba da hirarsu ban ankara ba naji ya miƙo min wayar yace "ga Granny zaku gaisa". A hankali na karɓi wayar na kara a kunne na duk kunya ta rufe ni,sallama nayi ta amsa sannan na gaishe ta shima ta amsa sannan ta shiga faɗin"Mun gode sosai kan irin halaccin da kika gwada mana,na amincewa ki auri Habib haƙiƙa kin ceto rayuwarsa a lokacin data dace Allah ya miki albarka". A sanyaye nace"amin"sannan ta cigaba da cewa"Kuma duk sanda ya ɓata miki kizo gidan kiyi zaman ki abinki". Dariya Habib yayi sosai kafin yace"Granny tun yanzu zaku fara haɗe min kai?".A hankali nace"nagode nima hajiya sosai allah yasaka muku da mafificin sakayyarku". Da "amin",ta amsa dashi sannan mukayi sallama na miƙawa Habib wayar shima ɗin sallamar yayi mata sannan muka cigaba da hirar mu. Har izuwa lokacin da Daddy da baffa suka fito,inna kuwa tanata ƙara jero wa Ummi godiya sai Yasira da Sayyid dasuke bayansu sosai Yasira ta yaba da yanayin garin.Tasowa nayi daga wajen Habib cike da kunya,naso wajen Ummi ina musu addu'ar Allah ya kiyaye hanya hakan nan ma Inna da Baffa ke musu bendir ɗin kuɗi Daddy ya ciro daga aljihun sa ya miƙawa Baffa duk yanda yaso Baffa ga karɓi kuɗin ƙi yayi.Haka suka tafi akan bayan kwana biyu Sayyid zaizo mu koma katsinan tare dashi inna kuwa ta haɗawa Ummi tarkacenta,irin na tsofaffi su bushshen kuɓewa da kalwa Ummi ta karɓa tare dayi mata godiya. Sai da muka daina ganin motar tasu sannan muka koma cikin gidan,ɗakin Inna nida Yasira muka shiga yayi da Innar ta shiga banɗaki,Baffa ma ɗakin Hajara ya shiga tana tsaye jikin ƙofar ya same ta sai huci takeyi. "A'a Hajara na zata ai bacci kikeyi,shiyasa ban ganinki ba a waje ashe idonki biyu?"Baffa ya faɗa yana zame babbar rigarsa. A wulaƙance ta kallo shi tare da faɗin"To mezan zo na muku?,Malam yanzu da hankalin ka ka ɗauki auren Hibba bakawa waɗannan mutanen?,wayasani ma ko dashi wanda aka fake da cewar anzo nema masa auren nata dashi suke yawon taziba.......". Bata ƙarisa ba sakamaton marin da Baffan ya sauƙe mata a gefen fuskarta,ba zato ba tsammani. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 1⃣9⃣ "Hajara izuwa yanzu kam,bazan jure ba sannan bazan ɗauki duk wani ɓatancin da zaki gandanta hibba dashi ba.A da na kuskuren jefa ta cikin ƙunci amma bazan ƙarayin mai-maita wannan ba"cewar baffa. Dafe kuncin ta hajara tayi tana faɗin"malam ni ka mara? ". "E sannan ba ma keba duk wani mahalukin dazai tsaya a gaba na,yana jefar hibba da mummanan kalami to irin hukuncin daya cancance shi kenan". Yana gama faɗin haka ya fice daga ɗaki,alwala yayi kafin ya leƙo ɗakin inna yana cewa"ku tashi kuyi salla an kira". Sannan ya wuce masallaci domin ƙiran sallan la'asar da aka farayi. A tare muka fito da yasira muna cikin alwalan,hajara ta fito sai data tsaya ta dallo mana wata uwar harara sannan ta fice tare da sakar mana tsaki.ba wanda yace da ita daga uffan muka kammala alwalar muka shige ɗakin inna. Hajara na fita gidan wata yayar taje wacce itama take aure a cikin ƙauyen ganon,tana zaune a tsakar gida tana tsintar yakuwa haraja ta shigo. "Ƴan-uwa rabin jiki,hajara kece tafe da yammacin nan?". Ƙarisowa hajara tayi ta zauna kafin tace"Adda barira wallahi nike tafe kuma matsalace ta kawo ni". Ajiye yakuwar dake hannunta adda barira tayi gefen guda kafin tace"to hajara kekuwa wace matsala ce ta ɗago ki cikin wannan sakaliyar yammacin?". "Wallahi adda kinga yau kawai muka wayi gari inna wannan yariyar da take ƴar wan malam ta dawo,bayan tsawon watannin data shafe bata gidan kuma wai harda wanda zata aura tazo tare da iyayen sa,shine fa daga nacewa malam ni ban yadda da dawowar wannan yariyar ba ya bincike ta shine ya wanke ni da mari nan a kunci na". Hajara ta faɗa tana gyara zaman akan tabarmar kaban salati adda barira ta shiga yi tare da faɗin. "Oh ni barira ƴan iska basa ƙarewa a duniya,yanzu shi adamun ne ya mare ki akan wannan maganar?". "Wallahi kuwa adda ni yanzu ma zuwa nayi ki haɗani da ɗaya daga cikin malaman da kuke hulɗa su,a mallake min shi ta yanda ko kara na ajiye zaiyi shakkar tsallake ta,tunda gashi yanzu tun ba'aje ko'ina ba ya fara mari na".cewar hajara. Dafa kafaɗarta adda barira tayi sannan ta shiga faɗin"haba!ke kuwa ƴar-uwa sai kace ba jini taba ai ita wacce ya miki abun a dalillin ta,ita za ayiwa bashi ba sawa zamuyi asa mata tsanar shi yaron data kawo zata auren,taji duk duniya babu wanda ta tsana sama dashi sannan daga baya zai mu dawo kan adamun.Yanzu ki tashi kije gida zanzo nima". Murmushi hajara ta saka kafin tace"yauwa adda ta". Nan suka cigaba da hirar su,sai da akayi sallar magrib sannan hajara ta komo gida. Muna zaune a tsakar gida hajara ta shigo kamar bataga mutane ne a wajen ba tasa kai tayi shigewarta ɗakin ta.ranar sosai mukayi hira da inna da kuma baffa. Washe gari tare da yasira muka gyara gidan tsaf!sannan muka ɗaura girkin shinkafar da baffa ya sayosai da muka gama komai sannan mukayi wanka,muna zaune a ɗakin inna ina karatun jarabawa wanda da zaran mun koma zamu fara. Inna ta ɗago labulen ɗakin sai data washe baki sannan ta shiga faɗin"ku fito munyi baƙo". Sai dana rufe littafin sannan muka fito tare da yasira. Turus nayi ganin yaya fawas zaune a tsakar gidan shida baffa,sai a sannan na tina da cewa daman yau zaizo a hankali naji ɗumin wasu hawaye masu zafi suna bin kunci na.Shima ni ɗin yake ganin bakin sa na rawa ya furta"hibba". "Yaya fawas". Yunƙura yayi zai tashi sai kuma ya koma ya zauna,da ƙarfi ya runtse idanun sa hawaye na zubowa kusa dashi na tsuguna ina kamo hannun shi ya fusge. "Yaya fawas dan Allah ka yafe min kar ka azababtar da zuciya ta ta hanyar yin fushi dani". Numfashi ya saka mai ƙarfi wanda ya tafiyar da kukan daya ke kafin yace. "Ummul-khair kin sani cikin wani hali,a ko yaushe zuciya ta kan nuna min kamar na gaza riƙe ki a matsayin amanar da abba ya barni,karki manta ranan da wannan iftila'in ya faɗawa abba abinda yace dani shine "ka kula da ƙanwar ka".wanda hakan ya zamto furcin sa na ƙarshe a gare mu". Sai daya numfasa sannan ya ɗaura cewa"Ina kika shiga?". Ɗaura kaina nayi kan ƙafarsa ina cewa"yaya fawas zaɓi ne ya ƙare min,a lokacin banda zaɓin daya wuce hakanamma haƙƙin ka danasu baffa bai barni nayi rayuwa cikin farin-cikin ba yaya na ka yafe min". Sunkuyar dakansa yayi wanda hakan yabawa hawayen dasuka ƙara ciko idonsa damar tsiyayowa sannan yace. "Na yafe miki my cute angel ki daina kuka kinji,kukan ki na ɗaga min hankali". "Na daina yayana,na daina ka gani"na faɗa ina share hawayen dake bin fuskar yana sauƙar har izuwa wuya ta. Sai a sannan yasira ta gaishe shi,ya amsa mata yayin dayake ƙoƙarin tsayar da hawayen sa,inna ce ta mishi bayani wacece ita. Sannan baffa ya sanar dashi komai daya sani game da habib da kuma ahlinsa,sosai yaya fawas yayi murna sai fatan alkhairi yake min amma baffa yace"ba za'a sanar da mahaifiyar kuba sai tukunnan abubuwan sun ƙara kamkama,dan kar tace wani abun kuma". Sosai inna tayi na'am da zance baffa haka nan ma yaya fawas,wuni mukayi muna hira da yaya fawas tare mukaci abinci wanda rabon mu dayin hakan tun kafin bayan rabuwa. Anan yaya fawas ya kwana dan dama tare dashi zamu koma katsina a cewar inna yaje ya gano wajen.kwana nan mu huɗu a gano sannan muka fara shirin komawa domin jarabawar da zamu fara. Tunda mukazo ba kallon arziki tsakanin mu da hajara,hakan nan zaman lafiya yaƙare tsakanin ta da baffa. Ranan ana gobe zamu koma katsina muna zaune a tsakar gida muna taya inna tsintar wake,baffa da yaya fawas kuwa sun tafi goma Adda barira ta shigo. Washe baki inna tayi kafin ta shiga faɗin"lale maraba da zuwa barira kece tafe?". "E wallahi inna nice tafe hajarar tana nan kuwa?"ta faɗa tana daga tsaye. "E ki shiga tana daga ciki". Gaishe ta mukayi a tare nida yasira ta amsa tanabin mu da wani irin kallon dana kasa fassara meyake nufi,mamaki ko al'ajabi. "Inna wannan ce yarinyar da ake tayi da ita a cikin garin nan ko?,ta sa ƙafa tabar gida tsawon lokaci ba wani makalukin daya sata a idon sa.Oh ni bariratu naga ikon mai mana ruwa da iska,abin mamaki baya ƙarewa a duniya inda ranka kuwa kasha kallo". Sai data bina da wani irin kallo mai cike da tuhuma,tana jawo kujerar da inna ta miƙo mata ta zauna sannan ta ɗaura da cewa. "Ke kuwa yarinya duk tsawon wannan lokacin ina kika shiga?,inna kika je?,wajen wa kike zaune?". A dunƙule ta jefo min tambayoyin tana ƙara kafe idon ta akaina. Hawayen danake ƙoƙarin hana fitowar sune suka biyo kunci na,yasira da ta lura da hakan ta kamo hannun na tana jijjiga min kanta tare dayi min alamar nabaryin kukan. Inna ce tayi saurin cewa"Ashsha haba!barira da girman kike biyewa maganar mutan garin nan haba". Fitowar hajara ne ya katse adda barira daga maganar da tayi niyyar amayar da ita. "Adda ki shigo mana kika tsaya daga waje"hajara ta faɗa tana daga tsaye ƙofar ɗakin. "To ai shikenan allah ya kyauta"cewar adda barira yayin datake miƙewa tayi ɗakin hajara. Sosai na sakin kukan danake dannewa duk mutane irin kallon dasuke min kenan?,meyasa zasu yanke min wannan hukuncin ba tare da bincike ba?,watakil inna jewa umma ma ita ma kallon hakan zata min wacce taje yawon duniya. "Anty kiyi haƙuri ki daina wannan kukan bashi da amfani,kuma kisan komai kikayi sai mutane sun sama abin suka acikin sa"yasira ta faɗa cikin sigar lallashi. Sannan inna ta ɗaura da nata"gaskiya ne maganar yasira domin yanzu kisan an daina kiyon dabba sai dai ta mutum". Share hawaye na nayi sannan nacigaba da gyaran wanken ba tare danace dasu uffan ba. Domin raɗaɗin da zuciya take ciki kalmomin baki sunyi kaɗan wajen furta shi. Adda barira na shigowa ɗakin hajara ta mayar da ƙofar langalanga ɗakin ta rufe. Ƙaran da ƙofar tayi ta sanyani juyo na ganni ƙofar sannan na maida kaina ga aikin danake yi. "Oh ni bariratu yau idona sun gane min abin mamaki,hajara ki dubi irin suturun da ke jikin wannan yarinyar sannan babu alamar wahala ko yunwa a tattare da ita.Sannan ace ba yawon karuwanci taje ba?".adda barira ta faɗa tana zare hijab ɗin dake kanta. Sai da hajara ta saki ajiyan zuciyawanda hakan,ke nuni da irin ƙuncin da zuciyar take cikin akan maganar sannan tace. "Ai adda baki gama komai ba,sai ma kinga yanda malam yake ririta kamar jariri ɗan wata uku". "Ai kuwa yau komai zaizo ƙarshe"adda barira ta faɗa tana since gefen zanin ta. Ƙullin magani ta ciro tare da riƙon hannun hajarar tana damƙa mata kullin tana faɗin. "Kinga wannan kullin shi zaki barbaɗa mata a cikin duk wani,abu nau'in ababen sha kamar kunu da dai sauran su.Bi'izinillahi indai tasha to sai dai a yi wani labarin amma ba wannnan ba domin ita da wannan yaron har abada zuciyar ta zatayi dakon tsanar shi,da duk wani abu daya dangance shi ki fara aiwatar da wannan kafin mu juyo kan shi adamun". Karɓa hajara tana ƙara damƙe ƙullin cikin hannunta tana faɗin"nagode adda ni daman nasan ba wani matsala tawa dazan kai miki ki kasa magance min ita". "Haba!ke kuwa ƴar-uwa nayiwa wasu ma balle ke". Haka suka cigaba da ƙulla mumanan manufofin su,muna zaune inda ta barmu suka fito ni kuwa ina zaune kan dakalin ƙofar ɗakin inna ina waya da habib. "To inna ni na wuce allah ya bamu alkhairin sa"cewar adda barira. "To a gaida mutan gidan"inna ta faɗa tana ɗaukar buta zata shiga banɗaki. Rakata hajara tayi sannan ta dawo "Ana ta abun kenan". Ta jefo min maganar yayin datake wucewa kusa da inda nake zaune tayi ɗakin ta,tana sakin wani yalwataccen murmushi. Da kallo nabita ina ƙoƙarin fassara manufofin dake dunƙule cikin wannan dariyar tata,jin Habib yana ƙiran suna na a cikin wayar yasa ni sakin wannan tinanin. Ko dasu Baffa suka dawo,nan muka zauna muna ta shan hira Yasira sai faɗi takeyi"zarayi missing ɗin kwaɗon zolayan inna". Da mamaki na naga Hajara ta fito ta zauna cikin mu,abinda da tun zuwan mu banga tayi shibada ita ake ta hirar. Baffa kuwa sosai ransa ya masa daɗi ganin hajara ta watsar,da komai daga ranta har ta fito ta zauna cikin mu,ana wasa da dariya. Washe gari da wuri muka shirya kayan mu muna jiran zuwar Sayyid,muna tsakar gida Yasira sai hoto take ɗauka mana da yaya Fawas da kuma su Inna da Baffa tana faɗin inmun Koma zata bayar a wanke mata su muryar Hajara dana tsinkaya ne ya katseni,daga sheƙa dariyar danake yiwa Yasira. "Hibba har kun fito kenan?,daman fura ce kingan ta mai kyau na dama miki ita". Ta ƙarishe maganar tana miƙomin kwaryar furan. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ___________________________ Page 2⃣0⃣ Karɓa nayi sannan nace"Ayya Anty Hajara da baki wahalar dakan ki hakan ba nagode". Sai data marairaice murya kafin ta shiga faɗin"Haba!Hibba kedai ki sha ko kaɗan ne ai zanji daɗi nima,tunda kuka zo fa ban samu na muku wani abu ba sai wannan". Inna ce ta amshe zancen tana faɗin"haba!Hajara suda zasuyi tafiya kyabasu fura salon ta kashe mata jiki". "Haba!ilnna furace fa kawai,kuma kingan ta ba mai yawa bace". " To ai shikenan"shine iya abinda Inna ta furta. A hankalin na kurɓa furan sosai tamin daɗi dan haka nake shan ta sosai,kaɗan na rage a cikin kwaryan ina tanɗe baki. Nan Yasira tace zata sha guntun da wani mungun hanzari Hajara ta karɓa ƙwarya daga hannun Yasira tace"Bari na zubo miki naki ta mussamman". Sannan ta karɓa ƙwarya taje ta zubo mata tas!Yasira ta shanye. Sallamar Sayyid ta sa dukkan mu kallo shi yaya Fawas ne ya amsa sallamar,sannan ya sukayi musabaha sayyid ya gaida Baffa da Inna suka amsa tare da yalwata fara'ar dake ɗauke a saman fuskokinsu. Kayan mu muka fito dasu muka sasu a motar sayyid sannan muka shiga yin ban kwana gasu Baffa.sosai yake mana addu'ar Allah ya tsare mu ya kuma kaimu lafiya haka nan ma Inna da hajara yaya Fawas kam daman dashi zamu tafi Sannan muka tafi. Muna shiga cikin katsina muka wuce gida a compound muka same su suna jiran isowar mu,cike murna Ummi take mana sannu da zuwa sam bakinta ya kasa rufewa. Yaya Fawas gaisawa sukayi da Daddy sannan ya gaida Ummi ma musabaha sukayi Habib sannan muka shiga,ko da muka shiga ƙara gaisawa muke tayi mussamman yaya Fawas da Daddy yake ta masa bayanin akan Habib ɗin. Ɗaki muka shiga da Yasira bayan Ummi tamin umarnin dana kaiwa yaya Fawas kayansa cikin part ɗin Sayyid,wanka mukayi sannan mukayi salla muka fito mukaci abinci,Habib kam tunda muka dawo yakejin kansa cikin wani farin-ciki na mussamman. Haka muka gama cin abinci muka dawo falo muka cigaba da hirar mu,haka nan kawai naji zuciya ta ta kasa nutsuwa da irin kallon da Habib kemin,miƙewa nayi ina cewa"Ummi ina zuwa"sannan ya wuce ɗaki cikin sauri. Sai a sannan Daddy yake sanar musu da sunsa bikin nanda wata biyu shi da Baffa sosai Ummi take bayyanar da farin-cikin game da haka.Haka nan ma Sayyid da yaya Fawas, Yasira kam miƙewa tayi da gudu tana nufo ɗakina. Ina kwance rufda ciki na rungume matashi na,Yasira ta shigo ɗakin kaina ta faɗo tana cewa"Anty nataya ki murna ansa auren ki da Hamma nanda wata biyu". Ras!naji gabana ya faɗi tureta nayi daga jikin na sannan na juya mata baya"Anty Yasira ki barni na gaji inason na huta". Nan ta fara lissafin kalolin event ɗin da za'ayi,ni dai kam bance da ita komai ba dan ji nayi duk raina ya jagule na rasa gane kaina haka na wuni. Da yamma ina kitchen ina haɗawa Ummi fruit sallad waya ta ta hau ringing,ko ba a faɗa min ba nasa Habib ne ɗagawa nayi na kara a kunne na ba tare da nace komai ba. "Please inba abinda kikeyi kizo inna jiran cikin garden".Bance mishi komai ba na kashe wayar tare da ajiye ta gefe guda. Sai da gama abinda nakeyi na kaiwa Ummi fruit sallad ɗin sannan na wuce ɗaki nayi kwanciya ta,wayar tace ta fara ringing tsaki na saka sannan na miƙe na saka hijab ɗin na har ƙasa sannan na fito. A cikin garden ɗin na hange shi yana zaune kan kujerun plastic da aka shirya su a wajen,da sallama na isa gare shi ya amsa sannan na zauna.Shuru ne ya ratsa wajen ina ɗago kai muka haɗa ido dashi saurin ɗauke nawa idon nayi daga cikin nasa yayin na naji,wata iriyar tsanar ganin fuskar sa ya shige ni tun daga yatsun ƙafata har tsakiyar kaina. "Amaryan Habib da yaddan allah"ya faɗa yana ƙare kafeni idanu. Sai dana haɗiye wani yawu mai ɗaci,wanda naji ɗacin sa ya wanzu cikin ko'ina a baki na kafin nace"Angon Hibba",Ba ƙaramin jarumta nayi ba wajen wannan haɗa waɗannan kalaman. Sosai ya saki murmushi sannan yace"Munyi magana da Granny tace inkun gama jarabawa nakai mata ke ku gaisa". "To Allah ya nuna mana nima zanso haka".na faɗa ina ƙara takurewa cikin hijabi ta. "Amin".ya amsa dashi sannan ya cigaba daja na da hira,dauriya kawai nakeyi nake amsa masa amma duk sa'in da sautin muryarsa ta bugi dodon kunne na tsanar shi ne take ninkuwa cikin zuciya. "Zan shiga ciki kaina yafara min ciwo"na faɗa ina ƙara takurewa. "Suhbanallahi!Allah ya sauwaƙe muje na baki magani"ya faɗa yana miƙewa. Tashi nayi muka jera dashi muka shiga cikin gidan maganin ya ɗauko mini nasha sannan ya taraka ni har ƙofar ɗaki,sai daya ga shiga ta sannan ya koma. Koda na shiga kwanciya nayi yayin da ƙaryan ciwon kan danayi ya zama gaske,domin ji nake tamkar an ajiye min wani abu mai nauyi a tsakiyar kaina.Bansan ta yadda zan fara tunkarar Daddy ba nace masa a fasa wannnan auren domin jinake da a ɗaura wannan auren gwara akai ni kabari. Kuka na saka mai ƙarfi ta yaya zan butulcewa mutanen dasuka zame mini gata a lokacin dana rasa hakan daga kowa,suka dawo min da farin-cikin dana yanke tsammani dashi,sannan suka bada gudumawa wajen cimma buri na. Ana cikin haka muka fara jarabawa kullum Habib shike kaini kuma ya dawo dani,a cikin haka yaya Fawas ya koma tare da Sayyid suka tafi wanda shima ya koma makaratan.kamar na bishi haka nakeji amma saboda jarabawar damukeyi nayi shuru. Cikin haka muka gama jarabawar Ummi na roƙa akan inason naje daura gidan su Anty Amina dan cikin,kwanakin nan sosai nakeyi mungaye mafarkai akan ta. Tare da Daddy Ummi suka tattauna maganar ya amince min,naje tare da Yasira da Habib haka washe gari muka shirya muka ɗauki hanyar daura muna isa muka tambaye gidan malam Mahiru mai ɗan kara anan kuwa aka nuna mana.Domin Anty Amina ta taɓa cemin mahaifinta babban malamin addini ne a cikin daura kowa yasan shi. Muna isa ƙofar gidan Habib yayi parking sannan muka fito nan naji kamar an sauƙe min wani abu mai nauyi,a cikin ƙirji na da sallama muka shiga cikin gidan akan anty Amina idona suka fara sauƙa wacce take zaune a tsakar madaidaicin gidan nasun tana wanke-wanke. Sallamar damuka shigo da ita yasanya anty Amina ɗagowa tare da amsa salllamar,sakin kwanon siban dake hannun ta tayi yayi da idonunta sukayi tozali da fuska ta. Miƙewa tayi tana faɗin"Hibba kece". "Nice anty Amina "na faɗa ina isowa gare ta. Rungume juna mukayi muna sakin kuka,wanda hakan ya sanya mahaifiyar anty Amina fitowa daga ɗaki ganin mu datayi haka yasata faɗin"Amina lafiya?,Waye waɗannan ɗin?. "Umma itace Hibba wacce nake baki labarin ta"Anty Amina ta faɗa tana zuƙar majinan kukan daya zo mata. Salati Umma ta saka tana ƙara jaddada iko irin na illahi,sarkin da ikonsa yake akan komai sannan tace"Baiwar Allah kullum Amina cikin zancen ki take safe da yamma,ko yaushe tinanin ta wani irin hali rayuwarki zaka faɗa?,duk sa'in data ɗaura goshinta a ƙasa da sunan salla kafin tayiwa kanta addu'a to sai ta nema miki tsari daga dukkan abin ƙi". Tabbas Anty Amina ta zame min tamkar garkuwa a rayuwata ta baya,sannan itace ta fara bani taimako a lokacin danake matuƙar buƙatan hakan,wannan dalilin yasa nima a ko yaushe take cikin addu'ata. Duƙusawa nayi ƙasa inacewa"Anty Amina nasan nayi miki silar lalacewar auren ki,ban saka miki da irin alkhairin da kika min ba sai dai ma igiyoyin auren ki da a sanadiyata tsinkewar su,ki yafe min anty Aminaa"na ƙarishe maganar take da jan furcin ƙarshen. Ɗago anty Amina tayi kafin ta shiga faɗin"Hibba ban taɓa sanyawa a raina wai kece kika kashe min auren ba daga ni har iyayena,abinda nasa a raina kuma nake tina shi a ko yaushe shine ƙaddarar bawa ba taɓa tsalle shi,dukkan mu a wannan duniyar kuna rayuwa ne tare da ƙaddararmu.Sannan ba zamu taɓa guje mata ba kamar yanda bazamu iya gujewa inuwar mu ba". "Anty Amina nagode,ga wanda zan aure wannna kuma ƴar-uwar sace"na ƙarishe maganar tare dayi mata nuni da su Habib da Yasira. Tabarma ta shimfiɗa mana muka zauna sannan suka shiga gaisawa da Habib. Muna zaune a wajen mahaifinta anty Amina malam Mahiru ya shigo,sai daya zauna sannna Umma ta shiga masa bayanin komai,jinjina kansa yayi kana yace"Tsarki ya tabbata ga sarkin daya ƙaddara saduwa tsakanin mu dake ". Sosai malam Mahiru ya mana bayanin yanda malam Habu yayiwa Anty Amina sakin wulakanci a waya tare da jifan ta da zargi kawoni domin na lalata musu rayuwar ɗa. Nayi kuka sosai da har sai dana rasa hawayen tsiyarwan sannan na shiga kukan zuci,abubuwan dasuka faru tsakani na da Kabir a ranan da Balaraba ta kore ni daga gidan ne,ya fara min yawo cikin ƙwaƙwalwata tamkar yanzu suke faruwa. Nan na sanar dasu ainihin abinda ya faru tsakanin mu da Kabir a ranar,inayi ina ƙwalla haka ma anty Amina,Yasira Umma da kuma Habib daya sunkuyar da kansa yana tare hawayen dasuke shirin zubowa daga idonsa. A duk cikin rayuwar sa ba halittan dayake girmamawa gamin da darajawa irin mace,wannan dalilin yasa aduk lokacin ya ga wata mace cikin matsala yake mata kallon ƴar-uwa ta jini,kuma yaken shiga lamarin ta mussaman irin waɗannan aka ketawa haddi har sai anmusu adalci. "Ba komai akwai Allah,kuma akwai ranar tsayuwa a gabansa domin yiwa kowani bawa hukunci dai-dai da abinda ya aikata".cewar malam Mahiru wanda hakan ya dawo da mu daga duniyar tinanin da mukayi nitso a cikin sa. UWATACE SANADI _Tsarawa/rubutawa_ ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________ Page 2⃣1⃣ Ƙiran sallan zuhr da aka farane ya sanya malam Mahiru da Habib fita masallaci yayin da mu kuma mukayi alwala sannan Anty Amina ta shigar damu ɗakin mukayi salla. Tunda na iddar da sallan nake zaune kan sallayar,ni kaina bazan iya fasaltar irin tsanar danayiwa Habib ba cikin kwanakin wanda shikuwa kullum burin shi ya kyautata min tare da neman hanyar da zai dawo min da farin-cikin dana daɗe da rasa shi. Shigowa anty Amina tayi ta dire mana kwanon ɗan-wake a gaban mu,maganar da Yasira tayi ne ya katse anty Amina daga tata maganar datayi niyya fiddawa. "Anty inso nayi waya da Ummi,naga missed call ɗinta amma ba services". "Wallahi muna fama da matsalar service a gidan amma da zaran kin fita ƙofar gidan kikayi tafiya kaɗan zaki samo sai kiyi wayarki"cewar anty Amina. Gyalenta dake kafaɗarta Yasira ta gyara sannan ta fita tana cewa"Anty Hibba bari naje wajen". Kaina kawai na ɗaga mata sannan ta ƙarasa ficewa.Zama anty Amina tayi kusa dani tana fuskanta na kafin tace"Hibba na kula da fuskan ki tabbas akwai abinda yake damunki menene?". Nauyayyan ajiyan zuciya na sauƙe sannan nace"Anty Amina wallahi ina cikin matsala babba,bazan ɓoye miki ba wallahi banason wannan auren na Habib domin na gwammace akai mishi gawata ko ganinsa banason yi zaman gidan gabaɗaya ya fice min a rai.Shiyasa na roƙi Ummi ta barni naso nan". Duk abinda yake raina na fitar daman ba wanda na sama damar yin maganar dashi sai yanzu danake gayawa anty Amina,ko yaya Fawas bamuyi maganar dashi ba. "Hibba tabbas a yanda kika bani labarin zaman ki da mutanan nan,basu cancancin suzo miki da buƙata ki kasayi musu ba maƙutar kinada damar yin hakan,ni wallahi ma tausayin Habib ɗin nake saboda ciwon dayake ɗauke dashi.Ki dage da addu'a ba abinda ya gagare Allah kita sanar dashi damuwar ki bi'izinillahi komai zai wuce amma kar ki sake koda wasa kiyi wannan maganar da kowa kinji?". Kaina kawai na gyaɗa mata domin naga Anty Amina bazata fahimci irin saurin da zuciya take iya ba wajen zana min tsanar habib da manyan harrufa a ko'ina a ciki taba. Shawarwari Anty Amina ta bani sosai tare da wasu addu'o'i,muna haka Yasira ta shigo sannan mukaci abincin. Mukayi sallan Asr kuwa muka yi shirin bari daura sosai Habib yayiwa malam Mahiru sha tara ta arziki,sai dana karɓa lambar wayar Anty Amina sannan muka tafi. Tunda muka fara tafiyar zuciya ta take min zafi ɗan wuni da nayi a wajen Anty Amina jina nayi saƙayau kamar ɗaurarran daya masa ƴanci. A hankali na lumshe idanuna sannan na kwantar da kaina kan seat ɗin motar ina maimaita "Hasbunallahu wa ni'imal wakil". Habib daya lura da yanayi na yace"Fatima lafiya?".Cikin kwanan kin nan kuma sunan daya tsiri kira dashi kenan. Kamar ya watsa min wuta haka naji lokacin da na tsinkaye muryar shin ya sauƙa cikin kunne na,sai dana harhaɗo jarumta kafin nace"Lafiya kalau kawai gajiyace". "Daga cikin katsina zuwa daura shine har kin gaji?,To next tomorow da zamuje damaturu fa sannan mu biya ta wajen su baffa"ya faɗa yana sakar min murmushi. Shagwabe fuska nayi ina ƙara lumshe idona nace"nidai ba inda zanje sai na huta". Murmushi ya ƙara sakar min a karo na biyu kafin yace"Haka ne kam tawan ba wanda zai ta kura miki"ya faɗa yana maida ga kallonshi ga titin. "Allah dai ya nuna mana lokacin bikin nan"Yasira ta faɗa sai a sannan na tino da ita dan tunda muka,shigo motar sai yanzun tayi magana da amin ya amsa mata. Muna isa gida nida Yasira muka wuce part ɗin Ummi yayin da shi kuma ya wuce part ɗinsa sosai hakan ya min daɗi.Zaune da Daddy muka tardasu muka gaishe su suka amsa mana tare da tambayar mu ya hanya."Alhamdulillah!na amsa musu dashi sannan na tashi zan shiga ɗaki. Inajin Ummi nacewa"To Hibba hankali ya kwanta yanzu dai ko,kije kin gano ta"murmushi kawai nayi na shige ɗaki. Anty Amina na ƙira na sanar da ita mun iso lafiya sannan na kira yaya Fawas sosai mukayi hira dashi wanda shikam zancen sa duk akan bikin ne,wanda yanzu saura sati huɗu. Washe gari kuwa da yamma ina kwance a ɗaki ummi ta aiko ƙirana,a falo na iske ta tare da yasira. "Hibba zo kiga kayan lefenki ne kafin gobe a wuce dashi gidan granny"ta ƙarishe maganar tana min nuni da akwatinan dake jere jeras a gabanta. Set uku ne masu launukan maroon,ash da kuma golding,ko wani set guda huɗu ne sai ƙaramar jaka a cikin sa. Sunkuyar dakaina ƙasa kawai nayi ina cewa"Ummi basai naga ni ba,sunyi Allah ya saka da alkhairi". Dafa kafaɗata tayi tare da faɗin"Amin hibba Allah ya miki albarka". A sanyaye nace"amin"sannan na koma ɗaki koda Habib ya dawo ya aiko ƙira na ƙin zuwa nayi,daya matsa kuwa Ummi ce tace ya barni kunya nakeji kar ya matsa min. Washe gari kuwa Ummi tajeta damaturu tare da kayan lefen a gidan Granny aka ajiye su,sannan suka wuce gano ita da ummi da kuma iya suka kaiwa su Inna lefen kamar yanda al'adar hausawa take dangin ango suke kaiwa lefe gidansu amarya. Ranan rasa inda zatasa kanta Inna tayi dan tsabar murna,sosai Baffa ya musu tarban azirki. Koda suka tafi Hajara rasa inda zata sanya kanta tayi dan baƙin-ciki,sam ta kasa zaune ta kasa tsaye.fargaban ta shine kar dai aikin nan baici ba. Gidan Adda Barira taje ta shaida mata,kwantar mata da hankali Adda Barirar tayi tare da cewa su bari dai suga nanda wani lokaci in ancigaba,dayin batun auren sai su san matakin da zasu ɗauka. Ummi kuwa kwananta uku a damaturu sannan ta dawo.Haka nan cikin kwanakin nan,da bikin keta matsowa kullum nake cikin kuka duk lallashin da Habib zai min bana kula shi,haka ko kalaman bakin Yasira zasu ƙare wajen tambaya ta abinda ke damun na bana tanka mata.Domin nima kaina zanso sanin abinda ke damun nawan. Ummi ce wasu lokutan kance dasu daman ko wacce,mace in lokacin bikin ta ya ƙarato takan tsinci kanta cikin fargaba. Tun ana saura sati biyu bikin Ummi ta sa akemin gyaran jiki sosai fatata ta murjewa ta ƙarayin,haske da kuma kyau.Cikin kwanakin nan kuwa wasan ɓoya mukeyi da Habib dan koda wasa bana yadda mu haɗu dashi. Ana saura kwana biyar bikin na koma gano tare da Yasira,dan acan za'a ɗaura.Ana ɗaurawa kuwa tare da waɗanda sukazo ɗaurin auren zamu juyo katsina. Guɗa Inna ta shiga rangaɗawa yayin da muka iso,ƴan-uwa da abokan arziki tunin sun fara cika gidan.Sosai Baffa da Inna sukayi farin-cikin zuwana. Washe gari kuwa yaya Fawas shima yazo,ranar wuni mukayi Baffa da Inna suna min nasiha haka nan ma Yaya Fawas. Da kanta Inna tasa aka zanzara min ƙunshi tare da Yasira,ana gobe ɗaurin auren da daddare ina tsakar gida ina waya da Habib Inna da yasira kuwa suna ɗaki. Hajara ta fito daga banɗaki taɓe baki tayi yayin datake ajiye butar dake hannun ta kafin tace."Oh ni Hajara duniya sam babu tsoron Allah a zuƙatan bayi,daga mutane sun taimaka miki shine kuma bari a aure ɗan gida,yo wayasan irin abinda aka bashi ya sha a kunu da shayi aka mallake shi". Ajiye wayar nayi ba tare danayiwa Habib sallama ba nace "Anty Hajara wai dani kike wannan maganar?". Sai ta dallo min harara kafin tace"A akwai wani dazanyi dashi bayan ke". Lokaci ɗaya naji raina yana mungun tafasa a harzuƙe nake faɗin"To ki buɗe kunnuwanki kiji abinda zan faɗa miki ni Habib baya cikin raina sannan da kike maganar wai na mallake shi,ni ko yanzu banƙi a fasa wannan auren ba baya gaba na balle kuma abin daya mallaka". Ina gama faɗin haka wuf na juya na wuce ɗaki,na barta tsaye a wajen. Kodana shigo ɗaki Inna na tarar zaune akan gadon ƙarfenta irin Nada mai rumfa,ta zabga tagumi hannu bibiyu.Yasira kuwa na kwance gefen ta tana bacci. Kallo ɗaya nayiwa Inna yanayin ta,ya tabbatar min data saurarin maganganun da mukayi da Hajara. Ɗauke kaina nayi na fara gyara inda zan kwanta muryartace ta katse ni. "Hibba inason ki tabbatar min da abinda kika faɗawa,Hajara shin da gaske bakya son Habib?". Gefen ta nazo na ɗauki pillow,ina cewa"Inna karka ki damu kanki fa,amsa ce kawai na bata dai-dai da tambayar data min kuma ai daman hakan takeson ji daga gare ni".na faɗa ina ɗaura kaina akan pillow na. "To kul Hibba kar na ƙarajin kinyi irin furcin nan,yanzu yanda gidan yake cike da jama'a da wani ya jiki fa ki daina irin haka banaso". Sai dana murmusa kafin nace"Inna kenan basai a fasa ba". Cikin sauri tace"A fasa meye ɗin". "Auren mana". "Allah ya shiryeki Hibbatu,ki kwanta kar gobe ki kasa tashi da wuri". Hmm Tabbas farin-cikin dangina shine abin daya zama abin tattali da riritawa a gare ni.Basan iya tunkarar ɗaya daga cikinsu in sanar dasu zuciya batason Habib ba,na gwammace in rayu cikin baƙin-ciki matuƙar nasu farin-cikin zai cigaba da wanzowa. Hajara kuwa nan inda na barta nan daɗi ya ishe ta,ɗaki ta koma fuskarta na bayyanar da tsan-tsan farin-cikin da zuciyarta ke ciki. "Alhamdulillahi madalla da Adda Bariri,wannan farin-cikin danake ciki haka Allah yakaimu gobe in fiddoshi waje".ta faɗa tana rufo ƙofar ɗakin. "Amin Hajara da alama dai akwai babban abun dakika shirya goben nan?". Tambayar da baffa ya wurgo mata wanda yasa hanjin cikin ta kaɗawa. Ya faɗa yana ƙara duban kayan dasuke gaban shi,wanda yaya Fawas ya ɗinka mishi,wanda zai sa ranar ɗaurin auren. "Ah Ah Malam daman kana ciki ne?,wallahi kasan duk wani masoyin mu yana farin-cikin ganin rana irin ta gobe.Ranar dazaka aurar da Hibba izuwa gidan mutumci,na tabbatar yaya sule zaiyi farin-cikin da hakan". Sai daya murmusa kafin yace"Haka ne maganar ki Hajara"A takaice ya faɗi maganar. Washe gari kuwa data kasance ranar juma'a ranar dake mafi daraja da falala daga cikin jerin kwanaki,dai-dai sauƙowa daga sallan juma'a aka ɗaura auren. Tun ƙiran assalatun farko Hajara ta tafi gidan Adda Barira,duk abinda ya wakana tsakani na da ita ta kwashe ta faɗa mata. "Adda ni yanzu so nake koda an ɗaura auren ya zamana ta kasa zaman gidan,hankalin ta ya kasa nutsuwa waje ɗaya.Ta yanda da ƙafarta zata baro gidan" Hajara ta faɗa fuskarta na bayyanar da tsatsan ƙiyayyarta gareni. Shewa Adda Barira ta saka kafin tace"Sha kuruminki ƴar uwa yanda kikeso haka nan za'ayi,kinga yanzu ma tashi zamuyi daga nan mu wuce wajen Malamin nan mu sanar dashi buƙatar mu". "Yauwa Addata tashi mu tafi,kafin Inna ta farka ta ga bana nan ta tsareni da tambayar ina naje". Hajara ta faɗa yayin dasuke miƙewa, fitowar kishiyar Adda Barira daga ɗakin tane yasa su tsayawa. Ɗaga labulen ɗakin tayi ba tare da ta fito gaba ɗaya ba,tana tsaye daga bakin ƙofar tace"Haba!Yaya ita kuwa yariyar nan meta tare muku a doron duniya?,meta aikata muku dahar kuke bibiyar ta da waɗannan munanan sharrukan?,Meye ribar ku indan kuka hana ta zaman gidan auren ta?.Shin bakwa tsoron ranar da Allah zai kamaku da laifin zaluntar wannnan baiwar tasa?. Tsawa Adda Barira ta daka mata,yasa ta shuru ba tare data ƙarisa maganar data ɗauko ba. "Laure ki kiyaye ni wallahi wato laɓe kike mana kenan ko?Ina ruwan ki da maganar mu meya shafe ki,muzaki nunawa kin fimu jin tsoron Allah". "A'a Yaya Allah ya baki haƙuri"cewar laure tare da sakin labulen ta koma ɗaki. Tsaki Hajara ta saka tare da faɗin"wallahi Adda ke kikayi sake har wannan matar take gaya miki magana son ranta haba!". "Kyale ta ƴar-uwa zanyi maganinta"cewar Adda ta faɗa tana gyara zaman mayafin ta a kafadarta sannan suka fita. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 2⃣2⃣ Gidan malamin suka wuce suka zayyana musu buƙatarsu bayan Adda Barira ta aje masa kuɗin aikin dana yankan daya ce za'ayi. Sosai ya basu tabbacin cewa ita da zaman gidan aure lafiya sai dai da wani,ɗa namijin amma ba Habib ba sai taji ta gwammace ta shiga duniya akan ta zauna a gidan sa. Sosai suka masa godiya sannansuka tafi gidan ta,Adda Barira ta wuce akan cewa zatazo anjima sannan Hajara ta wuco gida. Hakan nan ji zuciya ta,ta kasa sukuni tun da Habib ya ƙira ni yake shaida min nazama mallakinsa. Cikin wani tsadadden atamfa na shirya mai launin shuɗi,ɗinkin doguwar riga ne daya sauƙa min har ƙasa yayin da aka ƙawata ɗinkin da adon stones masu ɗaukar hankali. Tare dasu Sayyid da sukazo ɗaurin auren Ummi ta haɗo su da mai make-up. Sosai kwalliyar ta zauna a fuska na,sannan ta ɗaura min ɗan-kwali sannan na yafa gyale na daya kasance fari marar nauyi da kuma kauri haka nan kuma bashi da duhu. Yasira kuwa anko ta saka wanda harsu Inna ma sunyi shi,ko dana fito nan gidan ya ɗauki guɗa ta ko'ina. Yasira ce tashiga yiwa Inna magana a kunne,bansan meta faɗa mata ba sai gani nayi Habib ya shigo Sayyid na biye dashi a baya.Tare da tarin zugar abokansu. Wata guɗar aka sake rangaɗawa,wata tsohuwa na faɗin"Ga angon ga angon". Gaishe su sukayi sannan suka miƙe zasu fita bayan Sayyid ya sanar da Inna cewa yanzu za'a wuce da amarya. Dam!zuciya ta ta bada,duk da Ummi ta sanar dani daman da zarar an ɗaura zamu taho,amma ban zata abin zaizo min a haka ba. Bansan sanda hawaye suka fara bin fuska na ba,sai jin Habib nayi dab da inda nake tsaye yana share min hawayen. Kamar ana watsa min tafashashshen ruwan dalma,haka nakeji a duk inda hannun Habib ya sauƙa a fuska na. "Ki daina wannnan kukan fati na banaso kinji ko?"ya faɗa cikin raɗa,kaina kawai na ɗaga masa alamar naji. Nan kuwa abokansa suka fara hasko mu,da kemarurin wayoyinsu suna mana hoto. Sai a sannan na tino a inda nake,saurin matsawa gefe nayi ina sunkuyar da kaina ƙasa cike da kunya. Shi kam ko a jikinsa fita yayi yana ɗan sosa ƙeya. Yayin dasu Sayyid suka rufa masa baya ɗaki na koma na faɗa kan gadon ƙarfen Inna ina kuka,shigowa Inna tayi tare da zama dab dani tana faɗin"Hibba ba yanzu ne lokacin daya dace kiyi kuka ba,ki share hawayen ki inna da kyakykyawan zato akan Habib zai riƙe ki bisa amana". "Inna nima banida tantanma akan Habib Inna,kukan danake Inna wai yau ake ɗaurin aurena amma mahaifiyata bata damu da tazo ba balle sanin yanda za'a gudanar da bikin".Na ƙarishe maganar ina cusa kaina a cikin pillow. Ajiyan zuciya Inna ta sauƙe kafin tace"Hibba Fawas yaje sanar da mahaifiyar ku,amma ya samo ta tashi daga gidan kuma ba wanda yasan inda ta koma, ba wanda za'a tambaya cikin unguwan domin daman ba zaman mutunci sukayi ba". Cak!kukan danake yi ya tsaya yayin da zuciya ta min nauyi sosai. Numfashi na dayake sarkewa yasa ni tashi na zauna Inna ce ta fara ƙoƙarin yi magana,Amma na katse ta ta hanyar faɗin"Inna shikenan basai kinci komai ". Ina rufe baki na Baffa da yaya Fawas suka shigo ɗaki sai da suka zauna kafin baffa ya shiga faɗin. "Hibba dan girman Allah da manzonsa in an kaiki ɗakin ki kiyiwa mijin ki biyayya sau da ƙafa,ki riƙe dangin mijinki tamkar ƴan-uwa". Sosai Baffa kemin nasiha kafin yaya fawas ma ya ɗaura da nashi. Saida suka kammala sannan baffa ya ɗauko wata alkebba,ya lulluɓa min wanda ta sauƙa min har ƙasa. Ta da ce alkebba dan hatta ɗinkin ta na hannu ne da mata keyi a wancan lokacin,gyara min zaman alkebban inna tayi.Tana rufe min fuska na dashi sannan ta riƙo hannu na muka fito waje. Tunin motocin ɗaukar amarya sun hallara,sallama mukayi da irarun ƴan-uwan inna da sukazo sannan muka fito waje hannu na damƙe cikin na yaya fawas. Da Inna da hajara da kuma wata ƴar ƙanwar inna(shatu),dasu zamu tafi sai kuma yasira.Motar dake tsakiya yaya fawas yasaka ni ƙara damƙe hannunsa nayi yayin da ranar da umma ta rabamu ya dawo min cikin ƙwaƙwalwa ta. A hankali ya zame hannun shi daga cikin nawa,sai daya sakar min taƙaitaccen murmushi sannan yace"Allah ya bada zaman lafiya ƙanwata". A Zuciya na amsa sannan ya rufo mufin ƙofar,ta ɗayar ƙofar yasira ta shigo yayin da su inna suka shiga sauran motar. Muna shiga cikin katsina gidan ummi muka fara zuwa har yanzu kaina na lulluɓe da alkebba,Inna na riƙe dani muka shigo falon ummi wanda yake cike da mutane maƙil. A ƙasa na zauna yayin da ƴan-uwan mahaifiyar habib mutan ƙasar niger suka shiga feshe ni da turare. Ummi kuwa tsabar murna ma ta kasa zaune ta kasa tsaye,da an tambaya amaryar habin zatace"gata nan ƴar albarka". Muna cikin haka habib ya shigo ya sauya shiga izuwa wata farar yadi,Wacce aka iyawa aikin surfani izuwa yanzu kam na lura da cewa yana matuƙar son aikin surfanin. Ƴan-uwan mahaifiyar sane suka fara tasowa,yayin da wata tsohuwa daga cikin su ta ta kamo hannun sa har izuwa inda nake zaune. Tafukan hannunsa ta buɗe ta fesa masa turaren sannan ta umarce shi daya haɗa hannunsa da nawa,hakan yayi kafin ya miƙe ya fara min karin ƴan dubu-dubu ina daga zaune. Tunin gidan ya ɗauki shewa sai fatan zaman lafiya kowa ke mana,sannan aka wuce dani part ɗin habin ɗin su kuwa su inna nan part ɗin ummi sukayi zaman su. Tun ina sa tsammanin zuwarsu inna part ɗin har na daina,dan a zato na a nan zamu kwana tare dasu. Wata munguwar gajiya ce ta sauƙar min,da azababben ciwon kan daya sauƙa min lokaci guda sakamakon kukan danayi. Tashi nayi na faɗa bathroom nayo alwala sannan na fito kayan,akwatin na buɗe na ɗauka hijab nayi salla sannan na koma kan gadon na zauna. Ina zama suka turo ƙofar,a firgice ta gyara zaman danayi ina ƙara lulluɓe fuska ta da alkebban dake jiki na. Tare da sayyi da kuma Dr bashir suke sai kuma wani abokinsu ɗaya,zama sukayi kafin Dr bashir yace. "Amarsu ta ango to a buɗe mana fuskan mana". Ƙara sunkuyar da kaina ƙasa nayi ina sakin murmushi muryar habib datayi wa kunnuwa na dirar mikiya ne ya sanya murmushin,danakeyi gushewa yayin danaji zuciya ta tamin wani irin zafi. "A'a malamai ban fa gane wai ta buɗe muku fuskaba,kuyi abun zakuyi ku tafi"Habib ya faɗa yana ware idonsa akan Dr Bashir. Dariya dukkaninsu suka yi kafin sayyid yace"Shikenan Hamma zamu tafi tunda daman kowa a gidansa sarki mu kaga tafiyarmu,bazaka ƙara ganin mu ba sai ka neme mu". "Kyale shi sayyid Yau ai ranar sace"cewar ɗayan abokin nasu ya faɗa yana ajiye ledar dake hannunsa akan site drawer. Murmushi Habib ya saka sannan ya shiga faɗin"E dai kuyi tafiyar ku,mun gode". Miƙewa sukayi kusan a tare suna faɗin"To amarya mun bari ki lafiya". Tashi habib ɗin yayi ya rakasu tamkar na fasa ihu kozan sama rangwamen irin raɗaɗin da zuciya takemin,haka naji hawaye suka fara gosilo a saman kunci wanda nima bansan dalilinsu ba. A hankali naji ana yaye alkebban dana rufe fuska ta da ita. Ƙara sunkuyar da kaina ƙasa nayi yayin da yashi kuma ya zauna a bakin gadon,da ido ya tsare ni har sai na fara tsarguwa da kaina. "Ya isa haka kukan nan fatima ki daina kinji,yanzu ki tashi ki wanke fuskar ki kizo muyi salla mu nunawa Allah godiyar mu a gare shi,daya nuna mana wannan rana a cikin rayuwar mu". Maimakon na taƙaita kukan saima tsanan tashi danayi. "Hibba Ya isa nace miki,ki daina kukan nan kodan lafiyar ki"ya faɗa cike da kulawa. Sai daya tsazaita sannan ya cigaba da cewa"Baki da lafiya ne?,Meyake damun ki?". Ya faɗa yana ɗaura hannun sa a saman goshi na,sosai jiki na ya ɗau zafi rau. Sosai yake jera min tambayoyi ɗaya nabin ɗaya na cewa Meyake damu na?. Ganin irin yanayin daya shiga,sosai naji tausayin sa mussamman da na tino irin cutar da yake ɗauke da ita ta raunin zuciya. A hankali nake furta"Habib mahaifiya ta na tino yau har anyi bikina amma babu ita cikin mahalalta wajen aure na,Ina kewa ta inason na ganta koda daga nisa ne inason jin muryar ta inason mu zauna da ita muyi magana da ita irin ta ƴa da uwa". Duk da a wannan lokacin tinanin umma ba shi yafi sanya ni cikin damuwa ba,domin tsanar habib dayake girmama a cikin zuciya ce a wannan lokacin shine babban damuwa ta. Amma na ɗaukarwa kaina alƙawarin cewa zan bar abin a raina ba tare dana sanar da kowa ba,koda kuwa hakan zai zamto silar salwantar rayuwa ta. Sai daya sauƙe ajiyan zuciya sannan ya matso kusa da inda nake zaune,hannu na ya riƙo ya sa cikin nasa. Wasu hawaye masu zafi naji suna rige-rigen fitowa daga ido na,hannu na daya riƙe jinayi tamkar ya watsa min garwashin wuta. "Fatima ki miƙa dukkan lamuran ki izuwa ga Allah domin kuwa shine sarkin da baya kuskure a cikin lamuran sa,Ki godewa Allah ke kin taso kinsan wacece mahaifiyar ki,kin rayu da ita na tsawon lokaci domin baiwa ce ga duk wanda ya rayu tare da iyayensa biyu uwa da uba". Sai da yayi shuru na wasu daƙiƙu,Hawayen dasuka ciko masa idanu ya tare su da hannayen saSannan ya ɗaura da faɗin. "Ni ban taso tare da iyaye naba,na rasa su tun inada ƙarancin shekaru na rasa su a lokacin danake da tsananin buƙatar su,rashin iyaye ciwo ne da raɗaɗinsa baya misaltuwa haka nan kalaman baki sunyi kaɗan wajen furta su.Kiyiwa Umma kyakykyawan zato sannan ki dage da Addu'a komai zai dai-daita da izinin Allah yanzu ki tashi kiyi Alwala muyi sallah". UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam Page 2⃣3⃣ Duk da yanda zuciya ta take min soya,ɗaurewa nayi na tashi yayin daya riƙoni har izuwa ƙofar bathroom ɗin dake cikin ɗaki. Tare muka shiga mukayi alwala,sannan muka fito Salla muka gabatar raka'a biyu sannan muka shiga kirari ga mahaliccin mu kafin muka fara Addu'a. Nikam ta bangare na addu'a nakeyi Allah ya kawo min ɗauki da sauƙi a cikin damuwar dake damun zuciya ta,Ina tsoron ranan da Allah zai kamani da haƙƙin habib na aure dana tauye,Domin izuwa yanzu tsanar shi na rinjayar soyayyar da zuciya ke masa. Shikam ta bangare sa sosai yake mai ƙasƙantar dakai ga mahaliccin sa, yana roƙon ubangiji daya bashi damar zamantowa alkhairi ga rayuwar hibba sannan ya dawo mata da farin-cikin data rasa a cikin rayuwar ta. Muna iddar da sallan ya jiyo inda nake,kaina ya dafa sannan ya shiga min addu'a. Abincin da ummi ta sa a kawo mana da kyar naci abincin cokali uku nayi, shima kasa ci yayi sai tambayar da na lura baya gajiya dayin ta. Na tambaya ta lafiya ta nace kaina ke min ciwo,kasa cin abincin yayi yasani gaba yana min sannu. Alama yamin da hannunsa akan na matso kusa dashi,ba musu na matso jawo ni jikinsa yayi. Runtse idona nayi da ƙarfi sannan na jawo ɗan kwali na na toshe bakina dashi,saboda kukan danaji yana ƙoƙarin kubce min. Duk cikin naman jiki na ji nake tamkar yana watsa min tafashashshen ruwan zafi,Haka na ɗaure tare da ƙara runtse idanu na. Ina sakin ajiyan zuciya akai-akai ganin haka ya sa habib tinanin cewa nayi bacci,zame jikinsa yayi sannan ya gyara min kwanciya ta,ya ɗauko blanket ya lulluɓa min anan wajen. Baiyi niyyar tashi na na hau gado ba,dan yanda jikina ya ɗau zafi sosai ya zata zazzaɓi ke damu na kuma da kyar na samu bacci. Sai daya min Addu'a ya shafa min,kafin ya tashi ya shiga bathroom alwala ya ɗauro sannan ya fara gabatar da nafilfili. Washe gari da matuƙar ciwon kai da kuma zazzaɓin daya sauƙa a jikina tun dare jiya na tashi,magani nasha kodan damuwar da habib ya shiga a dalilin hakan ya sani daurewa na nuna mishi naji sauƙi Duk da inajin kwana ɗaya danayi a cijin gidan habib matsayin matar sa,duk na nema nutsuwa ta na rasa amma zan zamto masa mace ta kwarai. Da taimakon sa na shirya cikin shigar laffaya,sannan muka shiga part ɗin ummi. Ƴan-uwan mahaifiyar dasukazo muka fara gaishewa wata daga cikinsu ne ta shiga faɗin. "Oh duniya!Allah ya jiƙan zainaba yau ake bikin ɗanta amma bata duniyar rayuwa kenan". Da Amin dukkaninsu suka amsa dashi,lokaci guda na lura da yanayin habib daya sauya. Ɗakin da aka bawa su inna muka wuce muka gaishe su sosai inna ta ƙarayi masa nasiha. Sannan muka wuce part ɗin ummi ita nasihar ta ke mana sosai masu ratsa jiki da ƙwaƙwalwa. Ɗakin granny muka wuce sosai fuskar ta ke bayyanar da farin-cikin dake ƙasan zuciyar ta na ganin mu tare da tayi,Anan mukaci abinci sannan muka zauna tare da ita dakuma yasira data shigo yanzu. Da kuma matar Dr bashir maryam daman tare suka zo da ita,sosai muke shan hirar mu kamar dama can munsan juna Nan granny take sanar dani cewa ta faɗawa su Inna ma,da yamma za'a wuce dani gidan habib bazamu zauna anan ba dan dama ya gama gininsa. Da yamma kuwa da kanta ummi ta shirya ni cikin,shigar laffaya mai tsantsi da granny ta bani. Falon Daddy muka taro dukkanmu nasiha shima yayi mana,sosai tare da sanya mana albarka da fatan Allah ya bamu zaman lafiya. Granny da Inna dasu muka tafi gidan dake cikin unguwar Dutsen safa low-cost behind M&M pharmacy a nan cikin katsina ta dikko. Gidan babba ne sosai dan har yaso yakai na su ummi girma,part biyu ne dasuke kallon juna sai kuma wani ɗaya daga gefe wanda bai kai sauran girma ba. Ciki muka shiga har cikin ɗaki su granny,suka kaini sosai ɗakin ya ƙawatu da furniture masu launin ruwan toka. Muna zama habib ya shigo sanye yake cikin shigar manyan kaya kamar kullum,shadda ce fara sol wacce aka ƙawata ɗinkin da ado na zaren golding. A wuya da kuma hannun rigar,Inna ce ta amsa sallamar daya shigo da ita sannan ya ƙariso ya zauna akan ɗaya daga cikin sofan dake ɗakin. "Ga matar ka nan babban mutum amana ce da iyayenta suka duba kamala da kuma cancantar ka,suka ɗauke ta suka baka Idan kaci wannan amanar kasani kai da Allah kuma yana kallon ka ko mu ka ɓoye mana". Sai daya gyara zaman sa kafin ya shiga faɗin. "In sha Allah baza kuji wani abu marar daɗi ba tsakanin mu da yardan Allah". "Haka muke fata"cewar inna. Miƙewa sukayi dasu tafi nan inna take sanar dani gobe suma zasu koma gano. Sallama mukayi dasu sannan na musu fatan sauƙa lafiya habib ya raka su. Suna fita na sauƙe kuka mai ƙarfisosai zuciya ta take min suya,kamar na tashi nabi su haka nakeji dan bazan iya zaman gidan ba. Banji shigowar saba sai jin sauƙar numfashin sa nayi dab dani. "Ya isa haka Fatima tabbas nasan rabuwa da ƴan-uwa sai dole,amma duk wata ƴa mace da kika gani a cikin gidan aure ta fuskanci rana irin wannan ki daina kukan nan banaso kinji?". Kaina kawai na gyaɗa masa alamar naji,sosai yake amfani da duk wata kalamar dayasan zai kwantar min da hankali cikin furcinsa. Ƙiran sallan magrib ya tilasta mishi fita masallaci,nima tashi nayi nayo alwala sannan nayi salla. Sosai nake tausayin kaina da kuma irin rayuwar da zanyi cikin gidan habib. Ina zaune akan sallayar aka ƙira isha'i sai danayi sannan na ɗauko qur'ani na fara karantawa ko zanji sanyi cikin raina. Ina zaune wajen habib ya dawo zama yayi kusa dani,sannan ya jawoni jikinsa muka cigaba da karatun tare. Sai wajajen ƙarfe goma sannan muka ajiye qur'anin abincin da su granny suka taho mana dashi mukaci sannan muka fara shirin kwanciya. Ina zaune akan gado na lulluɓe ƙafata da blanket ya fito daga toilet shiryawa yayi cikin kayan bacci,3quarter ce tsayinta dai-dai gwiwarsa da t-shirt marar nauyi. Yaune karo na farko dana fara ganinsa,da ƙananan kaya sosai kuwa kayan suka amshe shi. Akan site drawer ya zauna yana fuskanto ni yace. "Ki kwanta ki huta nasan kin gaji ko gimbiya ta?". Murmushi nasaka tare da gyaɗa kaina,addu'a yamin ya shafa min sannan na lulluɓa min blanket ɗin. "Sai da safe fatan nishaɗantaccen bacci".ya faɗa yana kashe wutar ɗakin. "Allah ya kaimu" "Amin"ya faɗa yana ficewa daga ɗakin. Da kallo nabi bayan shi dashi yayin dayake ficewa sannan na sauƙe ajiyan zuciya. Sosai raina yamin daɗi danaga zai kwana a ɗakin sa,dama tun ɗazu fargaban danakeyi kenan dan bazan iya haɗa shimfiɗa dashi ba. Washe gari da wuri na tashi na haɗa breakfast sannan nayi wanka,ina tsaye a gaban mirro ina ɗaura ɗan kwalli ya shigo. Ta cikin madubin da hango shi yana tsaye bakin ƙofar ɗakin ya naɗe hannayen sa a ƙirjinsa. Juyowa nayi tare da gaishe shi ya amsa yana ƙarisowa inda nake tsaye,riƙo hannu na yayi muka wuce dinning. Da mamaki shimfiɗe kan fuskarsa yake tambaya na yaushe na tashi na haɗa wannan breakfast ɗin?. Murmushi kawai nasaka na cigaba da zuba mana abincin,wani lokacin inyana magana na tankamasa ma yakan zama min mayuwacin abu. Jallof ɗin taliya ne sai dai bansa vegetable sosai ba,kasancewar nasan habib ɗin baya ta'ammalin da duk wani abu green kamar alayyahu da dai-dai makamantarsu saboda lafiyar zuciyar sa. Sosai mukaci abincin suna ci muna hira cikin nishaɗi. Ummi ce ta ƙirashi ya ɗauka ladabtar da murya yayi ya gaida ta, ta amsa sannan tace ya bani wayar. Sai dana gaishe ta ta amsa tare da tambaya ta ya kwanan baƙunta nace. "Alhamdulilla" Na faɗa ina ɗagawa habib ido ɗaya irin abun nan dake nuna dako lafiya? Sakamakon kallon danaga ya tsare ni dashi. Wanda izuwa yanzu na fara karantar hakan na daga cikin ɗabi'arsa,muryar ummi ce ta katse min hanzari. "Anjima yasira zata kawo min kayan da dangin mahaifiyar habib suka miki". "To Allah ya kawo ta daman inada faɗa da ita". Sallama mukayi sannan na miƙawa masa wayar shima ɗin sallamar sukayi. Muna gamacin abinci ya miƙe tare da faɗin"Akwai wasu abokaina dasukazo a hotel suka sauƙa so innaso naje wajen su kafin su wuce". Kamar banji saba nayi na miƙe ina tattare kwanonka,izuwa yanzu kam na fara tsorita da irin tsanar da zuciya ta kewa habib ko muryarsa banason ji balle kuma na ganshi kusa da ni. Riƙo hannu na nayi tare da tsaida idanunsa cikin nawa. "I'm sorry Tawan wallahi daga nisa sukazo ne shiyasa zanje muyi sallama kafin su tafi,badan haka ba inna tabbatar miki babu abinda zaisa in fita a irin wannan ranar". "La!ba komai hamma habib na fahimta"na faɗa ina kashi masa ido ɗaya cikin sigar zolaya nayi maganar sannan na raba hannu na dan nasa. Gwalo idanu waje yayi kafin yace"waye hamman nakin?". "Kai mana" Sai daya murmusa kafin yace"zan dawo ai zamu gamu". Sosai na saki dariya sannan ya fita key ɗin motar dake ajiye akan dinning ɗin na ɗauka nabi bayan sa. Har jikin motar na rakashi tare dayi masa kyawawan,addu'ar sauƙa lafiya sannan yaja motar ya tafi. Sai da naga ficewar motarsa daga gidan sannan na sauƙe wata zaffafar ajiyar zuciya,yayin da wani nishaɗi ya sauƙa min lokaci guda ciki na dawo. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 2⃣4⃣ A falo na tsaya ina ƙarewa falon kallon,furnitures set biyu ne a ciki da masu launin shuɗi da kuma golding. Sai makeken Tv plasma dake manne cikin wall ɗin falon. Lokaci guda idanu na suka sauƙa akan hotunan mu na bikin dake ajiye gefen Tvn sai kuma wasu da aka kafesu a cikin wall. Matsowa nayi ina bin hotuna da kallo wasun ma bansan lokacin da aka ɗauke su ba. Waya ta data fara ringing ne,tasani barin cikin falon na wuce dinning. A hankali na ɗaga kiran tare da kara wayar a kunne na daga ɗayan bangaren habib yace. "I forget to tell you i love you,shine na ƙira na faɗa miki". Wasu zuffa ne suka keto min lokacin guda bakina na mungun rawa nace"me too"na faɗa ina dai-dai nutsuwa ta. Sosai nakejin sautin dariyarsa kafin yace"ki kula min da kanki kinji". "Uhmm kaima haka". Ban jira amsar dazai bani ba na kashe wayar,dawowa falon nayi na kwanta akan ɗaya daya cikin kujerun ina lumshe ido na. Bansan sanda na fara hawaye ba sai jin ɗuminsu nayi sunabin kunci na,Arazane na tashi jin ana bubuga hannun kujerar danake kwance akai. Ganin Yasira yasa na watsa mata harara ina ƙoƙoarin tashi na zauna tare da share hawayen dake fuskana. "Anty lafiya kike hawaye,ina shi hamma Habib ɗin?". Yasira ta faɗa tana bina da wani kallon tuhuma.Ban kulata na fara gaishe da mata biyu da sukazo tare wanda suke ƴan-uwan mahaifiyar Habib,amsawa sukayi suma suna ƙara tambaya ta dalilin hawaye dasu gani a fuska na. "Ba komai wallahi,wani abu ne ya shigar min cikin ido"na faɗa ina miƙewa domin ɗauko musu abin sha. Yasira kam nomban Habib ɗin,tashiga dialing ringing biyu kuwa ya ɗauko. Nan ta sanar dashi halin dasuka zo suka same ni,da mamakin ta sai taji ya saki dariya sannan yace. "Wai ba dan na fita ne wajen wasu abokaina da sukazo daga malesia yau zasu koma shine nakega dalilin wannan kukan". Murmushi ta saka kafin tace"Au hamma kace kukan daɗi take?". Shima murmushin ya maido mata dashi sannan sukayi sallama,ina shigowa falon hannu na ɗauke da tray. Kallo ni tayi yayin da take maida wayar cikin jakar ta tace. "Anty lalle hamma na shagwaɓa ki da yawa dan ya fita shine kike kuka". Sai da na galla mata harara sannan nace"Anyi ɗin"na faɗa ina juya idanu na. Anan suka wuni yasira take sanar dani su inna tun asubar fari suka tafi. Sai yamma sosai sannan suka tafi,bayan na musu rakiya sannan na dawo falon ina duba kayan dasu zo min dashi. Zannuwa ne da kwaraye wanda aka ƙawatasu da launuka,da zane masu ɗaukar hankali irin dai na ƴan mutan niger. Sai kuma kwaskon turaren wuta,suma sun ƙawatu da zanuka da kuma turaren wutan. Sosai kayan suka burgeni duk da ba wani yawa gare su ba,amma naji daɗin wannan kyautar tasu gare ni. Ƙaran shigowar motar habib danaji ne ya kawar da annurin dake fuska na,nan take naji raina yayi baƙi ƙirin,kamar na fita da guda haka nakeji. Ina zaune ya shigo miƙewa nayi na iso gareshi tare da karɓan ledan dake hannunsa,Inajin yanda zuciya ta take tsananta bugu. Rungumo ni yayi muka ƙariso cikin falon,saurin raba jiki na nayi da nashi. "Bari na kai maka ruwan wanka sannan ka huta"na faɗa murya ta na rawa haka nan ma jiki na. Ban jira amsa dazai bani ba na juya cikin sauri na wuce bedroom ɗinsa,Bathroom na nufa na haɗa masa ruwan wankan sannan na fito. Ina fitowa yana shigowa ɗakin kayan jikin sa na fara rage masa. "Jinki nake a ko'ina a cikin raina shiyasa bazan daina yiwa Abba addu'a ba,Allah yakai haske kabarin sa daya haifo min ke". "Amin ya Allah"na faɗa ina cire masa safan dake ƙafansa. Miƙewa yayi ya shiga toilet ɗin,kaya na ciro masa na ajiye masa akan bed ɗinsa sannan na fita. Sannan na fito na buɗe ledar daya shigo da ita,kaza ce da kuma rufaida yogurt ɗayan ledar kuwa fruit ne. Kitchen na wuce na zuzzuba komai a mazubin sa sannan na jere su akan dinning. Waya tace ta fara ringing na ɗaga da sauri ganin sunan yaya fawas,daya bayyana cikin screen ɗin wayar ina murmushi. Sai da muka gaisa nake tambayar sa yaushe zai zo gida na?. Sosai yake sakin dariya kafin yace"Haba!ai sai kin shekara tukunna" "Kai!yaya fawas ai kuwa ni zanzo". "Kul ban yadda ba kiyi zaman ki a ɗakin ki daga yin auren har zaki fara zuwa gida"ya faɗa yana ɗan ƙara sautin muryarsa. Fitowar habib ya sani haɗiye maganar,da ke maƙoshi na fuskar shi ɗauke da murmushi ya nufo inda nake zaune. "Ina habib ɗin fa". Tambaya da yaya fawas ya jefo min wanda ya sanya ni dawowa daga duniyar tinanin danayi nutso cikin sa. Miƙewa habib ɗin wayar nayi,ya karɓa tare da karawa a kunnensa ba tare daya tambayan waye ba. Sosai sukayi hira kafin daga bisani sukayi sallama,dinning area muka nufa mukaci abincin. Fruit ɗin kawai habib yake sha ni kuwa sosai nake yagar kazar ina bin bayanta sanyanyan rufaida yoguth. Sai danaji ni nayi ƙatti sannan muka tattare wajen,wata hamma na saka ina lumshe idanu na. "Bacci ko?". Gyaɗa kaina nayi yace"to ki tashi muyi salla sai ki kwanta ko?". Ya faɗa yana riƙo hannu na sai da muka gyara dinning ɗin sannan muka ɗauro alwala muka gabatar da sallan magrib. Muna zaune akan sallayar aka ƙira isha'i mukayi . Miƙewa yayi ya kamo hannu na muka nufi ɗaki,wanka na shiga na fito nayi shirin kwanciya. Sanda mafito yana zaune akan sofa yana aiki a lapton,ɗinsa kayan dasu yasira suka taho min dashi na ɗebo su na nuna masa. "Masha Allah kaya sunyi kyau"ya faɗa yana guban lapton ɗinsa. Rufe lapton ɗin nayi na cuno baki ina faɗin. "Hamma magana fa nake maka kana kallon lapton". Naɗe hannayen sa yayi a ƙirjin sa yana sakin murmushi yace. "To shikenan inajin ki ". Kayan na turo mishi gaban sa inna ce "kaga kayan sunyi kyau ko?"na faɗa ina tsaida idona akan sa. "To yanzu ke mezakiyi da wannan kwaryan haka da yawa". Ɗan hararar sa nayi ina cewa"ba ruwanka nidai inason abina".na faɗa ina tattare kayan. Saurin kamo ni yayi ya manna da jikinsa na fisge,kayan naje na ajiye a store tura ƙofar nayi sannan na jingina a jikin ƙofar. Da sauri-sauri hawaye dake ambaliya akan kunci na,zuciya ta na bugawa da tsananin ƙarfi. Dafe goshi na nayi ina karantu duk wata addu'a darazo baki na. "Ya Allah ka fini sanin kaina ya Allah ka sausauta min wannan tsananin danake ciki,ka nuna min ƙarshen shi ina tsoron ranar da zaka kamani akan laifin kasa bawa habib, hakkinsa na aure dana take a gaban dukkan halittunka Allah ka kawo min sauƙi ". Na ƙarishe maganar ina sulalewa ƙasa daga jikin ƙofar. Duk yanda naso kyautatawa habib,tsananin tsanar da zuciya ta ke masa wanda inada tabbacin ko a mizani,aka sashi sai ya rinjaye soyayyar danake masa. Shike hanani kyautata masa duk da yanda shi yake buri da kuma ƙoƙarin sauya rayuwata izuwa cikin dauwamemman farin-ciki. Kamar an tsigara min wani abu haka na zabura na tashi wanke,fuskata nayi a kitchen sannan na koma ɗakin. Yana zaune inda na barshi yana waya da granny,gefensa na zauna ina ƙurawa fuskar shi kallo sosai fuskar tamin baƙi ƙirin a idanu na. Saurin kawar da kaina gefe nayi,ina ƙoƙarin maida idona ga TVn dake aiki a cikin bedroom ɗin. Sai daya bani wayar muka gaisa da granny tare da ƙara,roƙo na dana kula da lokutan shan maganin habib ɗin Sannan sukayi sallama ya ajiye wayar. Sosai yake jana da hira duk yanda zuciya ta take min soya,haka na danne na ke bashi amsa cikin walwala. Saukar ajiyar zuciyan danakeyi neya tabbatar masa da nayi bacci kan bed, yakaini sai daya min addu'a kamar yanda ya saba sannan ya rufa min blanket. Shafa goshi na yayi a hankali yake furta"Hibba inason ki so mai tarin yawa". "Nima haka hamma habib".na faɗa ba tare dana buɗe ido na ba. Murmushi ya saka sannan ya kashe wutar ɗakin ya fita. Washe gari da wuri na haɗa mana breakfast,a gurguje habib yaci kasancewar yanada baƙi a office. Sanda zai fita har da ƴar hawaye ta,sosai ya shiga aikin lallashi na yana cewa"ba daɗewa zaiyi ba zai dawo". Sai dana mishi rakiya tare da masa addu'o'i sannan ya tafi. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa _Maimunah Tijjani Iyam_ _________________________ Page 2⃣5⃣ Ranar wuni nayi na rasa abinda dake damuna,kamar na fita a guje daga cikin gidan domin zaman gidan ya gundure ni. Alwala na ɗauro na fara jera salloli,sai dana iddar sannan na ɗauki Al-qur'ani na fara karantawa. Sosai na farajin sanyi a cikin raina na daɗe ina karatun sai danayi sallan zuhr sannan na tashi na fara haɗa abincin rana. Simple girki nayi dan na lura Habib ɗin,yafi son abinci marasa nauyi da kuma sauƙin sarrafawa. Ina gamawa na jere su akan dinning,dai-dai lokacin da waya ta fara ringing. Sai dana faɗaɗa fara'a ta sannan na ɗaga ƙiran ganin sunan Anty Amina ya bayyana. Sosai mukayi hira da ita take tambaya ta yanayin zaman namun. Sai dana sauƙe ajiyan zuciya kafin nace"Anty Amina gashi nan dai wallahi ba abunda ya sauya,sai ma ƙara tsanani dayake yi". Na ƙarishe maganar ina sharar ƙwallan dasuka ciko min idanu.Itama ajiyar zuciyar ta sauƙe sannan tace"Hibba ki cigaba da addu'a akwai wasu ma zan kawo miki,in sha Allah komai zai wuce tamkar mai komai bai taɓa faru ba.Meye ne bai faru ba a zamanki a gidan malam habu tsohon miji na?,amma ba gashi ba yanzu kamar ba ayi ba". "Haka ne Anty Amina amma nikam har na fara tinanin ko,inace masa ya sauwaƙe mi....". Saurin katse ni Anty Amina tayi ta hanyar faɗin"Kul Hibba wannan shine kuskuren daza kiyi mafi muni a rayuwarki,ki dubi irin karamci na iyayen Habib sune sanadiyar cigaba da karatunki,su suka maida ki ga dangin ki sannan suka miki babbar sutura ta hanyar yarjewa ki auri ɗansu." Sai data numfasa na wasu daƙiƙu kamar mai nazarin wani abu, kafin ta ɗaura da faɗin"Hibba aure shine rufin asirin ko wace ɗiya mace,idan kikace ya saki ki yanzu wani hujja kike dashi dazai zame miki madogara?,Da wani idon zaki fuskanci iyayen ki da kuma Fawas?". "In sha Allah Anty Amina zanyi yanda kika ce zan koyar da zuciya ta haƙurin zama inuwa ɗaya da Habib".na faɗa yayin danake bawa ƙwallan dasuka ciko min idanu damar zubowa. Ba kaɗan ba Anty Amina take kwanta min da hankali gami da bani wasu addu'o'in. Ƙiran sallan Asr da aka farayi yasa mukayi sallama bayan tamin alƙawarin kawo min ziyara,dan lokacin da akayi aure tayi tafiya shiyasa bata sama damar halalta ba. Sai dana gabatar da sallan,bayan nayi addu'o'in da Anty Amina ta bani na dawo falo. Wayata na ɗauka na shiga dialing nombar Habib katse ƙiran yayi sannan ya ƙira ni. "Ranki ya daɗe "ya faɗa cikin muryar da take bayyanar da tsananin gajiyar dake tattare dashi. Sai dana jefa masa tambaya na ya office ɗin?ya amsa da Alhamdulillah sannan na ɗaura da faɗin"Hamma yaushe zaka dawo?,wallahi nidai tsoro nakeji "na faɗa ina ƙara sausauta murya ta. "Kinga wallahi yanzu muka fito daga meeting,so innayin sallan magrib zan dawo". Ɗaukewar da wutar bob ɗin dasuke haska ko'ina na cikin falon sukayi,sakamakon ɗauke wutar nepa da akayi.Kafin kuma sola ta fara nata aikin yasanya ni ɗago kaina ina sauƙe idanu akan bob ɗin kafin nace"To shikenan tunda kace salla zakayi,amma dazaran ka iddar ban yadda a tsaya a ko'ina ba sai gida". Sai daya murmusa kafin yace"Consider is done ranki ya daɗe". Nima darawa na yi kafin daga bisani mukayi sallama,Ina zaune akam sallaya na iddar da sallan isha'i kenan naji ƙara shigowar motarsa,saurin shafa addu'ar dana keyi nayi sannan na miƙe tare da cire hijab ɗin dake kaina na cillashi akan bed na fito. Sanda na fito yana dai-daita parking cikin harabar gidan da ƙwayayen wutar lantarki suke hasko ko'ina kamar ba dare ba. Ƙarisowa gare shi nayi ya riƙo ni muka shigo cikin gidan,sai na rakashi bathroom ɗinsa yayi wanka sannan muka fito abinco mukaci,sannan muka cigaba da hirar mu. Ranar duk yanda zuciya ta take ƙara ayyanano min tsanar Habib kawarwa nayi na zage mukayi hirar mu. Haka rayuwa ta cigaba da juyawa,lokaci na tafiya yayin da duk wani bugun ko wani daƙiƙa na agogo tsanar Habib dake sake hayayyafa a cikin zuciya ta. Ana haka muka koma makaranta,idan na fita ji nake kamar kar na dawo cikin gidan. Mota Habib ya saya min sannan ya ɗauko min drivern da zai dinga kaini kafin nima na koya. Tun ranar da aka kawo ni gidan Habib,bamu taɓa haɗa ɗaki dashi ba har izuwa wannan lokacin. Sau ɗaya yayi ƙoƙarin aikata hakan bayan mu kwanta sosai nake,sakin kukan duk yanda naso dannesu kasa yin hakan nayi sai da suka fito. Tashi yayi tare da kunna wutar dake kan site drawer a gefan shi yana cewa"Hibba lafiya?,meya same ki?". Rasa abin faɗi nayi sai tsananta kukan danake yi danayi,matsuwa yayi tare da kamo hannuna. "Meya ke damunki,ki sanar dani "ya ƙara tambaya a karo na biyu. Sauke ajiyan zuciya nake a hankali cikin kuka nake faɗin"Kayi haƙuri Habib wallahi ban iya kwana tare da mutum ba ɗaki ɗaya ba,balle kuma ace gado ɗaya".banida da abunda zan faɗa a wannan lokacin daya wuce haka.Ƙara matse hannuwa na dake riƙe cikin nasa yayi da ƙarfi,sai da hannu na yayi wani ɗan ƙara. Manyan idanunsa daya ƙara waresu ya kafe ni dasu, sai a sannan naga wauta na ƙarara bai dace a matsayinsa a gare ni ba faɗa masa wannan maganar ba. Saurin sunkuyar da kaina ƙasa nayi ɗago haɓata yayi da hannunsa. "Duk wani abunda zai zamto silar wanzar da farin-ciki a fuskar ki,ki sani ina sonsa koda kuwa hakan na nufi nizan cutu"ya faɗa yana ƙara kafe ni da ido. Wasu hawaye ne suka biyo gefen kunci na,nan baki na ya ɗauki rawa haƙware na har ƙara sukeyi kamar mai rawar ɗari nace"Habib dan Allah ka tayani addu'a Allah ya kawo min sauƙi cikin gaugauwa". "Ko yaushe kina cikin addu'a na hibba matuƙar ina cigaba da numfashi a goron duniya bazan daina miki addu'a ba". Ya faɗa yana lumshe idanunsa sa ya buɗe su yayin da yake miƙewa,Magana na fara ƙoƙarin yi amma yayi saurin dakatar dani da faɗin"Ya isa haka bana buƙatar kice komai,kuma wallahi har ga Allah banji haushin ki maganar ki nasan daman dole kiji abun wani irin,saboda rashin sabo". Kaina kawai na ɗaga masa alamar ina sauraron sa"Ki kwanta yanzu kar gobe ki makara zuwa school ko?". Ya faɗa yana rufa min blanket ɗin,sai daya min addu'a ya shafa min sannan ya fita. "Hamma inasonka"na faɗa ina bishin da kallo. "Nima haka Hibbatuu" Ya faɗa tare dajan harafin ƙarshen,hakan ya sa na tino da Inna a lokuta da yawa haka take ƙira nada hHibbatu. Duk yanda naso nayi bacci kasa zuwar min yayi tashi nayi,naci kuka har na godewa rabbana. Sosai kaina yake sarawa,tashi nayi na ɗauro alwala nazo na fara salla ina iddarwa na fara karatun qur'ani. Sai wajen ƙarfe uku sannan na samo bacci asuba ma a makare nayi sa. Sannan na haɗa breakfast nayi wanka,nayi shirin tafiya makaranta na fito. Har ana neman ƙarfe takwas,Habib bai fito ba ɗakinsa na nufa na tura ƙofar a hankali. Tare da rangaɗa sallama yana kwance akan sofa daga yanayin,sa na tabbatar da dakyar yasamu baccin. Matsowa nayi na tsaya kusa da kujeran dayake kwance kallo ɗaya nayiwa fuskarshi na ɗauke kaina tare da runtse idanuna da ƙarfi. Sosai fuskar shi ta ƙara baƙancewa a idanuna ƙwayar idonsa,da haƙwaransa sune kawai nake ganinsu da haske. A jikinsa yaji ana kallon sa a hankali ya fara ware idanunsa saurin maida hawayen dasuke shirin zubo min nayi. "Hamma ka tashi lokaci fa ya ƙure"na ɗaure na faɗa yayin da wani miyau mai ɗaci ya taro min a baki na. "Subhanallahi!" Yana faɗa yana ƙoƙarin tashi,tare da sauƙe idanunsa akan agogon dake maƙale cikin wall ɗin bedroom ɗin. Toilet na shiga na haɗa masa ruwan wanka sannan na fito,towel na basa sannan ya shiga wankan. Sai danaga shigar sa sannan na saki kukan dayake nuƙurƙusa na cusa kaina nayi cikin gwiwoyi na. Tabbas nasan ina cutar da Habib amma bayin kaina bane nima.Na kasa tabbatar da yaƙinin da iyayen habib suke dashi akaina,na zan samarwa ɗannasu ɗan gaban goshi farin-ciki. Jin kamar za'a buɗe ƙofar banɗakin,ya sanyani sauri goge fuska ta.Na fara ciro masa kaya shadda ce nevy blue. Wacce taji aiki sannan na ciro masa hula da agogo,taimaka masa nayi na shirya sannan muka fito falon. A gurguje mukayi breakfast ɗin kasancewar inada lectures ƙarfe tara,sai dana bashi maganin sa yasha sannan muka fito. "Yau fa nizan kaiki school"ya faɗa yayin da muke nufar cikin parking lot ɗin,yana karkaɗa key ɗin dake hannun sa. Kallo shi nayi tare da sakar masa murmushi sannan nace"A'a Hamma na yafe kar kayi lattin zuwa office". Sai daya ɗan hararo ni sannan ya shiga faɗin"Aikin me nakeyi dahar zai hanani kaiki school na yau kawai?,to drivern ma tsallamar sa za'a yi,daga yau nizan na kaiki kuma ina ɗauko ki " "To ranka ya daɗe yanda kake so hakan za'ayi". "Yauwa dan abin ya fara motsawa"ya faɗa yana buɗe min ƙofar motar. "Meye kenan?"na jefa masa tambayar tare da tsaida idona akan sa ina jiran amsa ta. Sai daya juya idanunsa kafin yace"kishi mana".Sosai ya bani dariya yanda ya juya idanun nasan,kamar wata mace. UWATACE SANADI Narh _Maimunah Tijjani Iyam_ ______________________ Page 2⃣6⃣ Har muka isa cikin makaranta bamu daina hira ba,ba tare da san rayukan muba mukayi sallama. A wajen na tsaya ina bin bayan motar da kallo,yayin da yake ficewa daga cikin harabar makarantar. Nauyayyen ajiyan zuciya na sauƙe ina ma-inama ace farin-ciki zai ɗaure a zaman mu,ina ma ace zamu rayu kamar ko wasu ma'aurata,zanso na zamewa habib abokiyar rayuwa ta ƙwarai incike duk wani giɓin dake cikin zuciyarsa. Ta yanda bazai nema komai,daga gareni ya rasa ba ko badan soyayyar dake nuna min a aikace ba.Dan ya cancancin hakan daga gare ni.Nasha jin ana faɗar cewa "zuciya nason wanda yake kyautata mata". Amma narasa gane tawa zuciyar wata iriyar zuciya ce,marar godiyar Allah da duk yanda habib ke kyautata mata hakan ya kasa tasiri wajen canzuwar ta.Bansan sanda na fara hawaye ba sai ji danayi wata ƴar department ɗinmu Limat Auwal ,ta faɗa kafaɗuna tare da faɗin"Fatima suleiman lafiya kike tsaye ana ke ɗaya kina hawaye?,gashi har an kusa shiga lectures". Saurin ƙirƙiro murmushi nayi na yaɓa a fuskata kafin nace"Lafiya kalau wallahi kawai,yau na tashi banajin daɗin jiki nane".Na ƙarishe maganar ina share ƙwallar da bakin hijabi na. Kallon da take bina dashi,ya tabbatar damin da bata yadda da abin dana faɗa mata ba.Gaba nayi na ɗauki hanyar dazai sadani,da department ɗinmu ina cewa"Kinga kizo mu tafi,kinsa halin lecturer ɗin nan inya rigamu shiga ba barin mu zaiyi mu shiga ba". Biyo baya na tayi da ɗan saurin ta kasancewar duk makarantar ba wanda baisan halin prof A.S karumi ba,matuƙar ya rigaka shiga class to saidai kayi zaman ka a gindin bishiya dan bazaka shiga ba. Ƙarfe sha biyu muka fito,masallaci mukaje mukayi sallama sannan muka saya abinci mukaci.Sannan muka koma lectures wanda muke dashi ƙarfe biyu,sai ƙarfe huɗu sannan muka fito. Habib na ƙira na sanar dashi baifi mintuna goma sha biyar ba yazo.Gidan Ummi muka nufa ya sauƙe ni kan zai dawo anjima ya ɗauke ni,A falon ummi na tarar da duk mutanen gidan hadda daddy. Cike da farin-ciki suke amsa gaisuwar tawa,yasira kam kamar ranar ta fara gani na tana maƙale gefe na tana faɗa min yanda tayi missing ɗina.Nan muka zauna muka sha hirar mu,hadda sayyid dan shima yazo gida lokacin. Sai bayan magrib sannan habib yazo,muna zaune nan a falon ya shigo da sallamarsa ummi ta amsa. "Ango mijin amarya sai yau aka tino damu"Sayyid ya faɗa yana duban wayarsa. Ɗauke kansa yayi kamar baiji abinda ya faɗa ba,ya ƙariso ya zauna ya gaida Daddy da Ummi,sannan yasira da Sayyid ma suka shiga gaishe shi. Amsawa yayi tare da yiwa Yasira ishara da hannunsa akan tazo nan kuwa ta dawo kusa dashi ta zauna."Kai kuma meka dawo yi?,Sayyid kana wasa da aikin nakan nan fa"cewar Habib. Ajiye wayarsa da yake latsawa tun ɗazu Sayyid yayi sannan yace"Haba!Hamma ni shikenan kuma bazan so gida ba,haba satina nawa acan Hamma ka dubi fa duk yanda na rame". "Kai dai kam,Sayyid sai shiriyar Allah yanzu ne lokacin dayafi dacewa ace ka ƙire aikinka da muhimmanci". Daddy ne yayi saurin amshe zancen ta hanyar faɗin"Gaskiya ne abinda Habib ya faɗa,ni na rasa me kake zuwayi gidan nan yanzu yaushe ka tafi har ka dawo,suma makarantar dasuke barinka kakeyin son ranka". "Yanzu dani ne da ya fara cewa ni malalaciya ce kullum sai zaman gida"Yasira ta fada tana watsa masa idanunta. Miƙewa Sayyid yayi tare da shurin Yasira da ƙafa,sannan ya zauna kusa da Ummi tare da kwantar da kansa akan cinyar ta. "Ummi kinajin su ko wai hadda wannan parrot mouth ɗin ma duk sun saku ni gaba,Dan Allah inbanzo na ganku ba ina zanje".ya ƙarishe maganar tare da shagwaɓe fuska. Ummi tace"Haka ne Sayyid duk ka kyale su ko yaushe kazo zan buɗe maka ƙofa". Dariya muka saka sosai,nikam hadda riƙe ciki sai da mukayi sallan isha'i anan mukaci abinci sannan mukayi azamar tafiya.Kamar nace masa ni ana zan kwana,sai kuma naga kamar hakan dazanyi zan cutar dashi da yawa kuma zaisa su ummi suyi zargin wani abun. Haka muka tafi bayan Yasira ta mana alƙawarin zuwa tunda muka fara tafiyar bance uffan ba shi kaɗai yake ta surutunsa. Muna isa kowa na wuce ɗaki wanka nayi sannan na fara shirin kwanciya,ta cikin madubi na hango shi yana tsaye bakin ƙofar ɗakin,kamar ko yaushe ya naɗe hannayensa a ƙirjinsa. Tashi nayi na ƙariso gare shi sai dana ɗaga kaina sama kafin nake kallon fuskar shi nace"Hamma inason naje wajen su Inna,wallahi ina kewarsu daga nan sai ka kaini na gaida Granny". Murmushi yayi tare da riƙo hannu na muka dawo cikin ɗakin,sai da muka zauna bakin gado sannan yace"To in sha Allah gobe zan kaiki matuƙar hakan zai saki farin-ciki". "Na gode hamma". Na faɗa ina ƴar tsalle ta,sannan na tashi naje na ɗauko masa maganinsa da ruwana bashi ya sha. Mun ɗan taɓa hira kafin kowa yaje ya kwanta.Nikam tsabar zumuɗin da son ganin su baffa na da Inna kasa baccin arziki nayi.Assalatun farko kuwa na tashi,tsaf na gama shiryawa na nufi ɗakin Habib. Yana zaune dawowarsa daga masallaci kenan."Yanzu nake shirin zuwa na tadaki kiyi salla ashe ma har kin tashi". Sai da ɗan rusuna sannan na gaishe shi ya amsa,tare da cigaba da faɗin"Ya naganki haka da shirin ki?". "E na shirya ne". "Kin shirya zuwa inna kenan?"ya sake jefo min tambaya. Cikin ƙosawa da mu tafi ɗin nace"Hamma zuwa gano mana". Dariya ya saka mai sauti sai dayayi mai isharsa sannan yace"Kin duba agogo kuwa ƙarfe bakwai ma fa batayi ba". "Nidai mu tafi da wuri tunda daga can har gidan granny zamu wuce".Na faɗa ina ninke sallayar daya dawo daga masallacin da ita. Ganin zai fara wata maganar ya sanya nayi,sauri na faɗa toilet na haɗa masa ruwan wanka na fito sannan na fara ciro masa kayan da zaisa. Ganin da gaske nake yasa ya shiga wankan bai ɗau lokaci ba ya fito,dumping ruwan jikinsa na masa sannan ya shirya muka fito.Sosai driven yake sheƙa gudu da motar,kafin ƙarfe goma kuwa muka iso cikin gano. Wani farin-ciki,nishaɗi ko murnar dana kasa bambamce,a cikin ukun nan wane nakeyi naji suka mamaye birnin zuciyata.Tun kafin drivern ya gama dai-dai parking,a ƙofar gidan baffa na fito daga motar da gudu na,na shiga cikin gidan ina ƙwalawa Inna ƙira. Itama da murnar ta ta fito daga ɗaki nan kuwa na rungume ta,tare da Adda Barira wacce tunda Habib ya ƙira Baffa yake sanar dashi da zuwan namun. Hajara ta faɗa mata nan gidan tazo dan aiwatar da umarnin malam dan dole sai da taimakon ta,abin zai tafi ba tare da amsama mishkila ba. Sallamar Habib yasanya Inna raba jikin ta da nawa,sannan ta ɗauko sabuwar tabarmar kaban ta ta shimfiɗa mana. Sai da muka zazzauna kafin,muka shiga gaida Inna ta amsa tana mai sanya mana albarka.A hankali nakai dubana ga ƙofar ɗakin,Anty hajara wanda tun fitowarsu sukayi cirko-cirko suna tsaye a wajen nace musu. "Ina kwana nan ku". Sai a sannan suka dawo daga kallon mu nida Habib,da suka shagala dayi mussamman Adda Barira dan wannan ne karo na farko data fara ganinsa. "Lafiya kalau mutan katsina"Cewar Adda Barira sannan ta ƙariso,bakin tabarmar ta zauna cikin salo na gwanancewa a munafirci. Itama Anty hajarar kujera ta,ɗauko ta zauna tana ta faman washe baki.Ladabtar da murya Habib yayi kafin ya shiga gaishe su suka amsa ba yabo ba fallasa. "Lafiya kalau yaro,kuna nan dai lafiya ko ina fatan ba wata matsala?"cewar Adda barira. Ko ni da har yanzu ƙuruciya bai gama bari na ba sai dana sha jinin jiki na,ga duk mai hankali wannan tambayar tana cike da manufofi balle kuma Inna.Dan yanda tayi maganar sai nake tinanin kamar ko ta ganu irin zaman da mukeyi da Habib ɗin ne. Shigowar Baffa shiya katse Habib daga,maganar da zaiyi.Washe baki Baffa yayi kana yace"Lalle da mutan katsina ta dikko har kun iso?". "E wallahi Baffa dayake tun a lokacin danake sanar dakai ma zuwan namu a waya har mu taso". Habib ya faɗa yana miƙewa tare da Ƙarɓan fartanyan dake hannun baffan,ya ajiye gefe guda.Zaman Baffa yayi nan kuwa muka shiga gaishe shi yama amsawa. Kwaɗon zogala da Inna tayi ta kawo mana,sosai mukaci har muna rige-rigen kai loma nida Habib.Ganin haka yasanya Baffa faɗin"ko a ƙaro muku ne?". "A'a Baffa sai dai anjima,yanzu kam mun ƙoshi"na faɗa ina suɗar yatsa. Tashi Habib da Baffa sukayi suka koma ƙofar gida,yayin da muka kafa hirar mu nida Inna lokaci bayan lokaci Hajara take jefa baki a cikin hirar tamu. Adda barira kam izuwa yanzu na gama fahimtar so take ta kaini ga bango,domin duk tambayar da zata min sai ta sako. "Yaya zaman ku da Habib ɗin ina fatan kuna zaune kalau ko?". Murmushi kawai nake sakar mata,ko kaɗan ban yadda nayi maganar zaman dake da Habib da ita ba. Ƙiran sallan zuhr da aka fara,ya sanya Inna tashi tayi alwala sai data iddar da alwala tata sannna tace"Hibba ki tashi ki ajiye wayar nan,kiyi salla ".ta faɗa tana gyara ɗaurin zanin ta mai launin ruwan ɗaurawa. "To Inna ta yanzu nima zan tashi nayi ". Na ƙarishe maganar tare da sakin dariya,dan chart muke da Yasira ta what's app ina gaya mata munzo Inna ta mana wannan shegen kwaɗon zogalan nan natan mai daɗin tsiya. Ajiye wayar nayi sannan na tashi,na ɗauki butar da inna tayi alwala dashi na zubo ruwa na farayi. Ina cikin shafar kai Adda barira ta fito daga banɗaki. "Haba!Hibba dubi kanki,sai kace bana amarya ba duk kitso nan ya tsufa". Nidai nasan kitsona bai tsufa ba,duk da cewa kuwa tun na biki nane da aka min.Amma ina gyara shi sannan bana wasa da kula da gashi na duk da ba wani gashin kirki gare ni ba,amma ina tattalin abina. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________ Page 2⃣7⃣ Nikam ma dariya taso ta bani,bance da ita uffan ba na cigaba da alwala ta ina gamawa nayi ɗakin Inna. "Inna wallahi wannan matar ta cika iyayi da yawa,to ni yanzu ina ruwanta da kitson kaina?". Na faɗa ina shimfiɗa sallaya Inna tace "Ai Hibbatu da gaskiyar ta har yaushe zaki bar kanki haka ki tsefe shi kafin ku koma sai a miki wani". Sai dana fuskanto inda take zaune a bakin gado taya saƙar hula nace"Inna muda yanzu zamu tafi,kuma ma to inna tsefe wa zaimin?". "Hajara mana ai ta iya kitso,duk yawancin makwabtan mu nan suke zuwa ta musu". Ta faɗa tana tattara zaren a ɗan yatsar ta.Nidai bance uffan ba ko lokacin danake gidan Baffa ko kaina zai dudduge Hajara ba ta taɓa cewa in tsaife zata min ba. Kawar da tinanin komai nayi a raina,na tada kabbara na farayin salla ta.Inna iddarwa ƙiran Habib yana shigowa waya ta,katse ƙiran nayi sannan na ɗauko maganin sa dake cikin jaka ta,na fita ina cewa"Inna bari yanzu zan dawo sai nayi tsifar". Ƙofar gida na fito nan kuwa na hango shi zaune cikin mota Baffa kuwa na zaune bisa tabarmar dake shimfiɗe ƙofar gidan tare da wani baƙo. Sai dana gaishe su sannan na wuce wajen Habib ƙofar motar na buɗe na shiga,ina shiga kuwa drivern ya fita.Magananin na shiga balla masa,sannan na ɗauko goran faro dana hango cikin motar na miƙa masa. Runtse idanunsa yayi sannan ya saka maganin cikin bakinsa,kafin yabi bayansu da ruwa. "Nadai lura yanzu kin maida hankalin ki wajen ganin inasha kwayoyin nan,ba tare da miss up ba ko?". Sai dana murmusa kafin nace"E mana alƙawari fa na ɗaukar wa Granny,so kake inmuje taga ɗan jikallen nata ya rame tace bana kula dashi". Sai daya ƙara kora ruwar sannan yace"to ai waɗannan maganin basu zasu hanani mutuwa ba in lokaci na yayi". Sosai gabana ya faɗi kamar faɗuwar aradu,cikin mintunan da basu gaza ɗaya ba idanu na ya kawo ruwar ƙwalla. "Baza ka mutu ba Habib ka barni da tarin zunubin kasa sauƙe haƙƙin ka dana tauye,inna maka addu'ar tsawon rai ina fatan zuwar ranar dazan sauƙe haƙƙin ka da suka rataya a wuya.Bana son naje gaban Allah da wannan laifi mai girma". Ina gama faɗin haka na fice daga motar,ko Baffa dayake tambaya ta lafiya ban saurara ba na wuce cikin gidan. A soro na tsaya na goge hawayen fuska na,sannan na ƙarisa shiga ciki. A tsakar gidan na iske Inna,Hajara da kuma Adda Barira.Kan tabarmar dana gani shimfiɗe a wajen nakai,mazaunaina na zauna tare da zare hijab ɗin dake kaina. Nan Inna ta fara min tsifar tana gamawa Hajara ta miƙo min mataji na taje sannan ta fara min kitson. Runtse idanuna nayi da ƙarfi ina faɗin"wash!kiyi min guda goma". Saboda zafin kitson dayake ratsa ilahirin kaina,har sai da jijiyoyin kaina suka fito raɗa-raɗa. Kamar yanda na faɗa guda goman tamin dukka baya.Godiya na mata sannan ta miƙe tayi ɗakinta yayin da Adda Barira ta rufa mata baya. Nikam a wajen nayi kwanciya ta,riƙe da waya ta ina ƙiran yaya Fawas. Sai da Hajara ta rufo ƙofar ɗakin,tare da sake labulen sannan taja hannun Adda Barira suka zauna akan ledar data rufe ko'ina acikin ɗakin. "Adda kinga rabo ko?,ƙarshe dai gashi mun samo gashin kanta". Hajara ta faɗa tana ɗaga matajin dake riƙe a hannun ta,wanda yake ɗauke da gashin kaina a cikinsa. Taƙaitaccen murmushin gefen baki Adda Barira ta saka kafin tace"Yo ai daman keki tsaya sanya har kike ganin bazaki iya samowa ba.Ai ƴar-uwa ina tabbatar miki tunda wannan yarinyar ta zamto silar da Adamu ya ɗaura hannunsa akan ki da sunnan duka,abin dabai taɓa faru a cikin tarihin aurenku ba wallahi sai tayi kuka da idonta kai wataran ma sai ta nemi hawayen tsiyayarwan ta rasa,Ke kaɗai kika rage min a duniya babu iyayen mu,babu dangi tsayayyu akan mu,muba ƴaƴa ba ba jikoki ba bazan taɓa iya zuba ido wani ya zamto sanadiyar shigarki damuwa ya kwana lafiya ba". Ta ƙarishe maganar tana tino irin faɗi tashin dasukayi a rayuwa,da yanda dangi suka wofartar dasu bayan rasuwar iyayensu. Karɓan matajin dake hannun Hajara tayi,sannan ta cire gashin dayake cikin tare da ɓallo bakin matajin tasa cikin wani ƙyalle ta ƙulle su. Miƙewa tayi suka fito waje,muna tsaye muna sallama da Inna da kuma Baffa. Har jikin motar suka mana rakiya hajara da Adda Barira ma ba'a basu a baya ba. Muna tafiya Adda barira itama sallama tayiwa Inna sannan ta miƙe izuwa gidan malamin. Yana zaune akan kilisa ta iske shi,zama tayi dan daman ba'a masa sallama inza'a shigo wajen sa. "Allah gafarta malam ga abubuwan daka buƙata,mun samo su".cewar Adda Barira tana miƙa masa ƙullin. Ƙullin ya karɓa sannan ya ware gashin ya ɗeba kaɗan a hannunsa ya watsa cikin kwaryan dake gabansa,wanda yake cike da ruwa sannan ya shafa saman ruwan yana faɗin"Matso ki gani wannan itace?". Matsowa Adda barira tayi ai kuwa hoto nane ya bayyana cikin ruwan,gani nan cikin mota muna tafiya har mun kusa barin cikin ƙauyen gano. "Kwarai kuwa malam itace". Sai daya bushe da wata iriyar dariya marar daɗin,sauraro sannan ya shiga ƙulunboton sa da sauran gashin. Sai daya gama sannan ya buɗe idanunsa,dasuka rikiɗe suka juya kamar garwashin wuta. Ciki wata iriyar murna mai tsananin, sanyawa duk wani wanda aka yiwa magana da ita firgici da tsoro yace"Daga yau ba ita ba kwanciyar hankali sun raba hanya dashi zata tsane shi fiye da komai a cikin duniya,sannan zamu aika mata da aljani ɗan mama ya hanata samun nutsuwa a cikin gidan". Sai daya numfasa sannan ya ɗaure fuskarsa,kamar bashi yayi wannan dariya ɗazun nan ba. Sannan ya ɗauko wasu layu guda biyu ya miƙa mata tare da faɗin. "Ki sama tsohuwar rijiyar da ruwan cikin ta ya kafe,aka daina amfani da ita ki binne waɗannan layu a bakin rijiyar". Kamar an sauƙe mata wani abu mai nauyi daga ƙirjin ta,haka Adda Barira taji ranta ya mata fes zuciyar ta ƙal. Miƙewa tayi tare da ajiye masa kuɗin daya buƙata ta fice sai da ta binne layu sannan ta wuce gidanta. Yamma sosai muka iso cikin damaturu rabona da garin tun ranar da muka bar YSU.Direct gidan granny muka wuce sosai bakinta ya kasa rufuwa saboda murna,mussamman dataga Habib ɗin kamar hankalinsa yanzu a kwance yake. Iya kusa ransa inda zata sani tayi saboda tarairayar da take min.Anan muka kwana washe gari kuwa sai da mukayi sallan zuhr kafin muka fara shirin tafiya. Granny kam cewa tayi ya barni a wajen ta nayi kwana biyu,ya nuna mata bazai yiyuba saboda ina zuwa makaranta. Haka muka tafi bayan muje gidan Dr bashir matar shi nada tsohon,ciki haihuwa ko yau ko gobe.Sai wajajen ƙarfe goma da wasu mintinu muka isa cikin katsina,a gajiya muka isa gida. Ina shigowa na wuce ɗakina kayan jikina na rage nayi wanka na kwanta,ko jiran shigowar Habib banyi ba. Washe gari kuwa bamu da lectures sanin hakan yasa nasha bacci na,sai wajen ƙarfe takwas na farka.A gurguje nayi wanka na fito ban shafa komai a fuskana ba na fito na nufi kitchen. Ganin Habib danayi yana fere dankali yasa na tsaya,sannan nayi saurin cewa"Hamma kaika kanka kake wannan aikin?". Na faɗa ina ƙarisowa gareshi tare da karɓan wuƙar hannunsa na fara fere dankalin. Sai daya kama waist ɗinsa,yana sharar zuffar data taru a saman goshin sa sannan ya ce"Yau dai kawai nace bari na mana girkin na hutar dake,sai kuma naga abin na neman gagara nafi 20min ina fere dankalin nan". Murmushi na sakar masa ina cewa"to ai daman ba aikin ka bane,yanzu dai na hutar dakai bari naje na haɗa maka ruwan wanka,har kayi lattin tafiya office". Shima murmushin ya maido min dashi tare da faɗin"A'a nima na hutar dake zan haɗa ruwan wankan dakaina".ya faɗa yana ficewa daga kitchen ɗin. Cikin sauri nagama suya dankalin sannan na haɗa tea,na jeresu a dinning ina tsaye a wajen ya fito. "100 percent hamma kayi kyau kamar a sace a gudu". Nafaɗa ina ƙarisowa cikin falo domin ɗauko masa maganinsa,sai dana ɗauko sannan na dawo dinning area ɗin. "To ai ni bazan satu ba"ya faɗa yana jawo min kujera sai dana zauna na ɓalla masa maganin na miƙa masa da ruwa yasha. Muna gama yin breakfast ɗin muka tattare wajen tare,sannan na masa rakiya har wajen motarsa. Da mugun sauri drivern ya taso ganin fitowar habib ɗin,sai daya gaida mu sannan ya karɓa jakar habib ɗin dake hannu na. "Jiya dana dawo malam Idi mai gadi yake sanar dani matar ka ta haihu har yau suna shine baka sanar dani ba". Cewar Habib yana nuna kansa da key ɗin motar dake riƙe a hannunsa. Ƙoƙarin magana driven ya fara ya katse shi,ta hanyar zara hannunsa a aljihu ya miƙa masa wasu kuɗaɗe da bazasu gaza dubu ɗari ba. "Ga wannan kayi hidimar suna dasu, sannan ka koma gida sai jibi sannan ka dawo aikin,iyalanka suna buƙatar kularwa a halin yanzu". Sosai drivern yake godiya yana ƙara ɗurƙushewa a wajen,ɗaga masa hannu habib yayi alamar ya tafi. Addu'o'i na shiga masa sannan ya tafi,na juya na koma a falo na tsaya na kunna kallo. A hankali kunnuwa na suka fara jiyomin kamar ana ƙiran suna na a cikin bedroom ɗin Habib,wanda kuma na riga nasan cewa ni kaɗai ce a cikin gidan sai su malam idi dasuke waje. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ____________________________ Page 2⃣8⃣ Rage volume ɗin kallon danakeyi,nayi sannan na kasa kunne kozan ƙaraji amma banji komai ba.Miƙewa nayi na ajiye remote ɗin dake hannuna,na nufi kitchen zan ɗauko ruwa. Sosai gaba na ya faɗi ji danayi a wannan karan an ƙiran sunan nawan da ƙarfi kuma muryar yarace. Tunin jikina ya ɗauki rawa duk da yanda zuciya ta take bugu hakan,bai hanani dakatawa daga hanyar ɗakin Habib dana nufa ba. Sai dana runtse ido na da ƙarfi,baki na na rawa na shiga karantu bismillah sannan na buɗe ƙofar ɗakin. Wayam babu kowa kuma babu alamun ma wani ya shiga ɗakin,Sai dana lalleƙa har cikin bathroom amma babu kowa. Dawowa falon nayi na wuce na ɗauko ruwar na dawo hannunane,ya shiga karkarwa tunin na sake kofin tangaran ɗin dake hannun na ya faɗi ƙasa ya tarwatse. Wani ƙaton ƙadangare na gani akan kujerar falon inda na tashi ,irin masu jajayan kai ɗin nan. A guje na fice daga falon na nufi bangaren malam Idi mai gadi ina ƙwala masa ƙira. Tare da matarsa Hajja suka fito,kusan a tare suke tambaya na lafiya?. "Malam Idi dan Allah ƙadangare ne ya shigo min falo,ka fitar min shi".na faɗa ina waigen falon. "To". Kawai yace sannan ya nufi hanyar falon bai daɗe ba ya dawo yana faɗin"Hajiya nifa banga komai ba wallahi,na duba ko'ina a cikin falo". Sai dana dai-daita numfashi na dayake fizga tsabar kaɗuwar danayi sannan nace"Yana nan akan kujerar farko kana shiga zaka ganshi". "Wallahi Hajiya babu komai sai dai muje dake ki nuna min". Gaba yayi muka bishi a baya nida hajja muka nufi falon.Rarraba idanu na shiga ina duba inda naga ƙandagaren tabbas anan na barshi amma kuma yanzu babu ko alamarsa. "Hajiya to kindai gani,gaskiya nan kam babu wani abun".cewar Hajja Muryarta ne ya tsinkayo ni daga duniyar tinanin dana lula,figigi nayi ina cewa"to shikenan amma nidai tabbas na ganshi". Fita sukayi sannan na rufe ƙofar na koma bathroom ɗina sai dana ɗauro alwala sannan na kwanta bayan na kunna karatun alqur'ani a wayata. Sai wajen ƙarfe biyu sannan na tashi,salla nayi sannan na wuce kitchen na haɗa tea kawai nakeda sha'awar sha. Dan ba girki zanyi ba kasancewar Habib sai yamma sai dawo,ina buɗe ƙofar kitchen ɗin idanu na suka sauƙa akan wannan ƙadangaren,yana gefen gas yayin dayake fuskanto ƙofar kitchen ɗin. Saurin maida ƙofar nayi na rufe inajin yanda ƙirjina yake dukan tara-tara. "Innalillahi wa'inna alaihirraji'un". Kawai bakina yake iya furtawa,shi na cigaba da nanatawa har na tsawon wasu minti na. Nayi jihadi na buɗe ƙofar a hankali na shiga ware idanuna,ina sauƙesu dai-dai inda na ganshi yanzu wayam babu shi. Da wani mungun hazari na fice daga kitchen ɗin,ɗan madaidaicin part ɗin malam Idi mai gadi na kuma nufa. Nan na iske matar shi Hajja tana wanke-wanke,gani na datayi cikin wannan yanayin yasata miƙewa tare da faɗin. "Hajiya lafiya". Ta ƙarishe maganar tare da nauraye hannuwan ta,da ruwar ɗaurayar wanke-wanken natan. "Wallahi tallahi na ƙara ganinsa wai hajja bakwa ganin sa ne ni kaɗai nake ganinsa kenan?". Na faɗa ina sakin wani kuka mai matuƙar ƙarfi,ƙarisowa gareni tayi tasa hannu tana goge min hawayen dake sintiri a samar fuskana kafin tace"Kidaina wannan kukan Hibba,bari Malam ya dawo sai yaje ya ƙara dubawa kozai gansa". Kaina kawai na gyaɗa mata ina wucewa naje na fara mata wanke-wanken hawayen dake gudana a idona basu daina ba,kamar yanda nima banyi wani ƙoƙarin hanasu zubowa ba. Dan a wannan lokacin,ina tinanin su kaɗai ne zasu sani naji sauƙi daga irin raɗaɗin da zuciya take ciki. A nan part ɗin su Hajja na wuni koda malam Idi ya dawo Hajja,ta sanar dashi dayaje ya duba baiga komai ba.Sai gabda magrib Habib ya dawo,malam Idi dayaje buɗe masa gate nan yake sanar dashi ina bangaren su. Sannan ya ɗaura da sanar dashi abinda ya faru,ina takure akan tabarma na tisa kwanon dambum tsakin masaran da Hajja ta kawo min. Malam Idi suka shigo tare da Habib ina ganinsa naji wasu hawaye masu zafi sun shiga kwaranyo min.Gefen tabarmar yazo ya tsuguna tare da faɗin"Meyake faruwa ne duk na ganki haka,nata ƙiran wayanki bakya ɗagawa shiyasa ma na dawo yanzu dan ba kaɗan ba hankali na ya tashi,sai kuma malam idi yake sanar dani cewar wai ƙadangare ne ya shigar miki falo". "Wallahi Hamma duk inda na duba shinake gani,kuma su Hajja sunce basu ganshi ba". Na ƙarishe maganar ina tsaida ƙwayar idona dayake cike fal! da sabbin ƙwalla,akansa cikin son tabbatar masa da maganar tawan. Handkerchief ya ciro daga aljihunsa ya miƙo min,na karɓa na share hawaye na sannan ya riƙo hannun na na miƙe tsaye. "Malam Idi bari muje na gani da kaina" Ya faɗa yayin da muke ficewa daga part ɗin nasun,koda muka shiga ba inda habib mai duba ba amma babu wannan ƙadangaren. Hakan ya ƙara tabbatar min dacewa ni kaɗai kenan nake ganinsa,ranar kota kan abinci bamu biba muka kwanta. Sosai muka raya mafi yawa daga cikin,dare da nafilfili sannan muka fara karatun alqur'ani. Ranar Habib a ɗakina ya kwana yana gadina,amma duk da haka na kasa runtsawa. Haka muka waye gari na kafe kan Habib bazai fita ko'ina ba,Sosai ya shiga lallashi na tare da bani haƙuri akan cewa akwai baƙin da zaiyi daga Morocco,da zaran ya gama dasu zai dawo. Haka ya tafi sannan na dawo ciki nikam daman ranar bazanje makaranta ba. Saboda ana training na censors a department ɗin,tun ƙarfe takwas ɗin safe suke farawa zuwa shidan yamma,ko munje ba lectures za'a mana ba. Ɗakin Habib na shiga na sama wani babban MP nasa memory card ɗin a ciki na kunna karatun qur'ani,na ƙure volume. Da wuri Habib ya dawo inayin sallan isha'i na kwanta saidai,na kasa baccin haushin karnuka nakeji ta ko'ina a cikin kunnuwana. Kamar karnukan a cikin ɗakin suke,tashi nayi na zauna ina karatu duk addu'ar datazo bakina. Habib yana kwance kan sofa,yana bacci har nayi niyyar tashinsa sai kuma na fasa. Daga jiya zuwa yau baya samun ishashshen bacci,dan sai da asuba yake kwantawa indan na tashi. Ga kuma wuni dakeyi a office cikin kwanakin nan,alwala na ɗauro nazo na tada salla. A hankali na farajin na dainajin haushin,ana kan sallayar na kwanta ina fitar da hawaye. Wai sai yaushe zan sama farin-ciki ne a cikin rayuwa ta?,sai yaushe zan rabu da tarin damuwa da ƙunci?,sai yaushe nima zanyi rayuwa kamar yanda sauran,mutane sukeyi cikin farin-ciki da walwala?. Da waɗannan tarin tambaboyin dana gaza samun,amsarsu bacci yayi gaba dani.Haka rayuwa taita juyawa yayin da ko yaushe gane-ganen danakeyi suke ƙaruwa,ko Habib inna faɗa masa cemin yake baya ganin komai. Wai kawai nasa abun a raina nane nima shiyasa nake yawan gani.Cikin kwanakin dabasu gaza bakwai ba,nayi wata mungun rama duk wanda yasanni sai yace na rame. Ko makaranta daina zuwa nayi,indai ba fita mukayi da Habib ba bana samun nutsuwa,muna dawowa kuwa komai zai cigaba. Koda Habib ya faɗawa Ummi rubutu tasa aka amso min ina sha sannan tace in daina sauraron kiɗe-kiɗe. Daddy yace"Yasira tazo ta tayani zama kafin suga abunda Allah zaiyi". Haka Yasira ta dawo gidan da zama,daga zuwanta da kuma rubutun da Ummi take karɓo min na rage gane-ganen. Saidai hankali na yakasa kwanciya da Yasira a gidan sosai tasa mana ido.Inna tsoron ranar da zata ganu cewar,ba ɗaki ɗaya muke kwana da Gabib ba. Haka kullum muna rigata kwanciya duk juyin duniyan nan dazan mata nacewa taje ta kwanta.Murmushi kawai take sakar min tare da faɗin"Anty kuje kuyi kwanciyar ku,niba yanzu zan kwanta ba". Haka nan zamu tashi mubarta a falon,har sai taje ta kwanta sannan Habib zai koma ɗakinsa. Ranar na dawo daga makaranta Habib ya ɗauko ni,muna tafe muna hirar mu.Yasira muka iske a falo tana kallo,sannu da zuwa ta mana sannan muka zauna. Ruwan rubutun da Ummi ta aiko dashi ta ɗauko min nasha sannan na wuce ɗaki na. Wanka nayi sannan na canza shiga,izuwa wata doguwar rigar material marar nauyu na fito. Hakan yayi dai-dai da fitowar Habib daga ɗakinsa,dinning area muka nufa wanda Yasira da jere shi abincin data grika mana. Sosai naci abinci rabona da abinci tun safe,muna gamaci Habib ya tafi masallaci. Muma tashi mukayi mukaje mukayi sallan,sai da akayi isha'i sannan Habib ya dawo.Tashi mukayi mukaje muka kwanta,sai dai koda muka shiga ɗaki zama mukayi.Muna jiran Yasira takoma ɗakinta shima ya tafi nashi ɗakin. Sai wajen sha ɗayan dare sannan ta kashe kallon,tayi ɗakinta sannan Habib ɗin ma yafita bayan yamin sai da safe. A hankali ya fito daga ɗakin ya shiga nasa dayake ɗan nisa kaɗan da nawa.Yasira wacce tazo ɗaukar wayarta data barsa yana caji a falon taga fitowarsa. Wayarta ta cire tana ƙarabin ƙofar ɗakin da kallo,tafi minti talatin a wajen tana jiran taga fitowarsa amma bai fito ba. Komawa ɗakinta tayi tana tinanin to ko wani saɓani muka samu ne?. Da safe da niyyar yi mana maganar ta tashi,amma ganin mu datayi babu wani sauyi daga yanda muke,ya tabbatar mata da ba wani matsalar da muka samu. Tare da Habib muka fita ya sauƙe ni a makaranta sannan ya wuce office,sai ƙarfe huɗu muka fito na ƙira Habib na faɗa masa bai ɗau lokaci ba yazo,ya ɗauke ni muka dawo gida. Muna zazzaune a falon bayan munyi salla munci abinci sosai nakejin bacci amma Yasira ta kasa ta tsare a falon nan. Ɗan satin datayi a gidan sai naji dukna matso ta tafi.Miƙewa Habib yayi bayan ya amsa ƙiran da aka masa a waya. "Bari nakai matar malam Idi asibiti bata da lafiya". Ya faɗa sannan ya fice cikin sauri,fatan samun lafiya muka mata.Sannan nima na tashi zanyi ɗakina,"Anty bari nabiki nima"cewar Yasira. Ban kulata nayi wucewata tabiyo ni,hira mukeyi sosai muna kallon hotunan bikin mu da Habib. Sai ƙarfe gowa da wasu mintina,mukaji ƙaran shigowar motar Habib. "Anty ga mijin ki ya dawo bari na tafi".cewar Yasira ta faɗa tana tattare hotunan. Murmushi nabita dashi dai-dai lokacin ta Habib ɗin yake shigowa ɗakin,matsa masa tayi sai daya shigo sannan ta fita. Sai nada tambaye shi jikin Hajjan?,yace da sauƙi hawan jini ke damunta,harma an basu gado. "Allah ya sauwaƙe". Da amin ya masa sannna muka ɗan taɓa hira kafin yamin addu'a yafita.Yasira dake tsaye a cikin falo ta naɗe hannayenta,a ƙirjinta yau kam ta ƙudurce a ranta sai ta tabbatar da zargin ta. "Hamma". Ta ƙira sunnan shi a hankali ya juyo sai daya bita da wani irin kallo kafin yace"Me kikeyi har yanzu baki kwanta ba?". Sai data iso dab dashi sannan ta shiga faɗin"Hamma wani irin zama kukeyi da Hibba?,waɗannan abubuwa duk meya kawo su bakwa kwana ɗaki ɗaya,sannan kuma ba wai saɓani kuka samu tsakanin ku ba?". Dam-dam ƙirjinsa ya bada hannunta ya kamo suka nufi ɗakinta. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _________________________ Page 2⃣9⃣ Zama tayi akan ɗaya daga cikin kujerun dasuke ɗakin sannan shima ya zauna yana fuskanto ta. Shuru ne ya tsara ɗakin na wasu mintuna,katse shurun yasira tayi ta hanyar faɗin. "Hamma inajinka". Sai daya sauƙe wani nauyayyen ajiyan zuciya sannan ya shiga faɗin"Yasira inason wannan abun yaza mana sirri a tsakanin mu,ko ummi banaso ki sanar da ita balle kuma Sayyid". "In shaa Allah zan tayaka riƙe wannan sirrin,matuƙar naji dalilanta masu ƙarfi ne".Sai daya gyara zamansa yana mai lanƙweshe ƙafafunsa kafin yace"Tun ranar da aka kawo Hibba cikin gida na,a matsayin mata ta sunna bamu taɓa haɗa gado da ita ba,hasalima kowa a ɗakinsa yake kwana.Ta sanar dani cewa bata saba kwana ɗaki ɗaya da wani ba,hakan yasa na mata uzuri a tinanin abun na ɗan wani lokaci ne sai kuma naga saɓanin tinanina domin tun daga ranar bata sake min maganar ba". Sai daya numfasa sannan ya ɗaura da cewa"Abun yana damuna sannan ya hanina samun nutsuwa a cikin raina,har na fara tinanin ko batada lafiya ne?,A duk lokacin danayi ƙudirin tattauna maganar da wani makusanci na sai naji kamar an ɗinke min bakina Bashir ne kawai yasan da wannan maganar.Kuma bazan iya tilasta mata ba shiyasa na duƙufa da addu'a kema kuma inason ki tayani". Hawayen dasuke sintiri akan kunci ta Yasira ta share da bayan hannunta tare da faɗin"Hamma bata saba kwana ɗaki ɗaya da mutum bafa kace?,wannan abun har yakai dalilin daza a amshe shi tabbas ta cutar dakai meyasa bata tinanin zaka iya faɗawa ga halaka?". Miƙewa tayi da sauri tana cigaba da cewa"Hamma zanje na mata magana domin wannan dalilin nata,bai isa hujja ba". Saurin riƙo hannun ta Habib yayi yana mata ishara da idonsa,akan ta zauna babu musu ta zauna ɗin. "Yasira karki ɗauka cewar duk wanda yayi shuru kurma ne,wani yin shurun sa yana jiran lokacin daya dace ne,wani kuma shurun sa domin nazari ne,wanin kuma kawaicinsa shine maganar sa.Na tabbatar in maganar nan ta isa gasu Daddyn soyayyarsu gareni kan iya sawa idanusu su rufe,har su kasa yiwa Hibba adalci cikin hukuncin dazasu yanke". Kallonshi Yasira take yayin da wasu hawayen ke biyo gefen kuncinta tace. "Hamma wani adalci kake magana?,ita adalcin ta maka auren wata uku amma k...". Da wani hanzari ta miƙe"hamma ka barni yanzu naje na mata magana". Fisge hannunta daya riƙe tayi ,shan gabanta yayi cikin saurin tare da faɗin. "Nace ki bari ko a hakan ma muna rayuwa cikin farin-ciki da matata sannan inna jiran lokacin daya dace ne muyi maganar da ita". "Farin-ciki?farin -ciki fa hamma kace meyasa ka zaɓi raya nata farin-cikin,ta hanyar salwantar da naka?". Sai daya juya mata baya sannan yace"saboda ganinta cikin farin-ciki hakan yakan mantar dani raunin dake cikin zuciya ta ,banason koda da wasa ne naji kin mata wannan maganar sai da safe ki kwanta".Yana gama faɗar haka ya juya zai fita daga ɗakin. Jida nayi kamar za'a buɗe ƙofar ɗakin ya sanya ni saurin barin wajen na koma ɗakina.Akan gado na faɗa ina sakin wani kuka mai ƙarfi,tun lokacin dasuka fara maganar nake tsaye a ƙofar ɗakin Yasiran inajinsu. Wayar ta data manta naje kai mata,sai kuma kunne ne suka tsinkayo min wannan maganar. Tabbas ko nima na yadda da maganar,Yasira nasan ina cutar dashi a zaman mu. Kukan danakeyi yasa na fara jin zuciya ta tamin,wani irin nauyi idanuna baza ganumin komai.Runtse su nayi inna karanta sunaye mahaliccina,kafin daga bisani na tashi nayo alwala na fara karatun qur'ani. A hankali nake sauƙe ajiyan zuciya yayin dana farajin sauƙin a cikin raina. A nan kan sallayan baccin wahala ya ɗauke ni,washe gari kuwa banyi niyyar zuwa makaranta ba hakan ya sa nayi kwanciya nan inda nayi sallan asubahi.Jin zaman mutum danayi dab dani ya sanya ni dawowa daga tinanin,danayi zurfi a cikin sa. "Lafiya kuwa,tinanin me kikeyi haka?"ya faɗa yana kafe ni da ido. Sai dana tattaro nutsuwa ta kafin nace"Lafiya kalau kawai banajin daɗin jiki nane". Ƙara kafe ni da ido yayi kamar mai nazarin wani abun,yanayi na ya nuna masa kamar Yasira tamin maganar. "Ina kwana an tashi lafiya"na katse shurun daya karaɗe ɗakin. "Lafiya kalau Hibbatu"ya faɗa yana sakar mini murmushi. Tare muka fito falo hannun mu sarƙale cikin na juna,Yasira muka iske tana arranging dinning table na iso muka farayi tare. Kicthen naje ɗauko flask ɗin tea,ganin haka ya sanya Habib saurin faɗin."Kiyiwa Hibba wannan maganar ne?". "Mezaisa nayi haka tunda ka nunamin bakaso nayi kar ka manta fa hamma sirri ne dayake tsakanin mu". Ta faɗa tana ajiye plate ɗin dake hannun ta,wanda hakan yayi dai-dai da fitowa ta daga cikin kitchen ɗin. Cikin nishaɗi mukayi breakfast ɗin muka gama shiryawa nayi muka fita tare da Habib ya ajiye ni a asibiti wajen Hajja. Yasira kam a gida muka barta dan tace zataje wajen Ummi,a nan asibitin na wuni sannan na wuce gidan Ummi. Sai bayan isha'i sannan Habib yazo ya ɗauke mu,muka koma. Haka muka cigaba da zama,koda wasa ban bari Habib ya gane cewa naji tattaunawar sa da Yasira ba. Cikin kwanakin nan na rasa gane kaina,a lokuta mabambamta nakan shiga banɗaki nayi kuka har na godewa rabbi.Kamar ana huraa min wuta a duk ilahirin jikina,yayin da tsanar kallan fuskan Habib ke ƙara mamaye zuciya ta.In fita makaranta ne kawai nakejin sanyi a raina,haka nan ko na dawo a bangaren Hajja nakeyin zama na. Haka muka shirya zamuje duba Granny bata da lafiya,tunda muka hau titi nakejin bugun zuciya ta,na tsanar ta gaba sai faɗuwa yakeyi.Koda muka isa sai da Yasira ta taɓa ni tare da faɗin"Anty mun iso fa". Sannan na dawo izuwa duniyar zahiri daga tinanin dana faɗa. A falo muka iske Granny da iya suna zaune,da sallama muka shigo ɗauke a bakin mu. Nan take annuri ya bayyana akan fuskokin su,kusa da granny yasira ta zauna tana faɗawa jikin ta. Shi kuwa habib gefen iya ya zauna,daga can gefe kaɗan na zauna ina gaishe su. Suka amsa sannan muka yiwa granny ya jiki,dukkan mu sosai yanayin jikin naka da sauƙi. Sannan granny tamin ishara da hannun ta akan na matso kusan ta,ba musu na matso ina mai sunkuyar da kaina ƙas. "Babban mutum ya naga duk rame ko baka da lafiya ne? "cewar granny. Sosa ƙeya ya farayi yana ƙara sadda kansa ƙasa kafin yace"granny lafiya ta kalau akwai kwana nan aiki ne sukamin yawa" . "Hibba yana shan magungunan sa kuwa,dan nasan halin babban mutum business ɗinsa shine akan komai harma da lafiyar sa". Sai dana ƙarƙayo murmushin dole na yaɓa a fuskata,da fargaba da tsoro ya gama bayyana nace."Hajiya yana sha kuma ciwon nasan ma ya daɗe bai tashi ba". Hamdala tayi sannan iya ta kawo mana abinci,mukaci sosai ranar na wuni cikin nishaɗi.Part ɗin Habib anan muka sauƙa sai da muka sha hira da su iya kafin kowa yayi shirin kwanciya. Sai da safe muka yiwa Granny da iya sannan na wuce part ɗin Habib,shi kuwa Granny ya raka ɗakin ta,daman lokacin dayake inba tada lafiya haka yake mata. Nikam ina shiga nayi wanka sannan na kwanta inajin shigowar Habib na rufe ido na kamar mai bacci. Shima shirin kwanciyar yayi na zata a ɗayan bedroom ɗin zai kwana sai kuma naga tsaɓanin hakan. Ƙara rufe idona nayi da ƙarfi,inajin yanda hawaye suke gosilo a saman kunci na,sai dai ban bari ya gane kuka nake ba. Haka nan na kwana ban runtsa ba,jiki na gaba ɗaya ya ɗau kerma ko yaya na rufe idona wannan ƙadangaren nan nake gani yau kuma Washe gari da wuri na tashi na shirya,sannan na tada Habib tare muka fito muka nufa sashin Granny.Tana zaune a ɗakin ta muka iske ta,tana sauraron labaran safe dake haskawa a tashar NTA. Kusa da ita muka zauna a tare muka gaishe ta ta amsa,sannan muka ɗaura da tambayar ta ya jikin ta amsa mana,da da sauƙi.Tashi nayi ina cewa"Granny bari naje wajen iya". "To nima yanzu zanje wajen natan"cewar Granny.Fita nayi na nufi ɗakin iya na basu waje dan su tattauna,dan na fuskanta granny nason ta gana dashi na sirri. Dan duk wanda yaga habib ɗin dole ya tambaye shi,lafiyar sa dan ba kaɗan ba yayi wata rama a cikin kwanakin nan. "Granny kinsha magani kuwa?". "A'a yanzu nakeson na tashi nasha". Cewar granny tana gyara zaman ɗan siririn farin,gilashin dake zaune saman karan hancin ta.Tashi yayi ya ɗauko mata maganin sannan ya ɗauko goran ruwa,ɓalla mata maganin yayi sannan ya miƙa mata. A tare ta watsa su a bakin ta,sannan yasa mata goran ruwan a bakin ta."Babban mutum inason kuwa muyi wata magana dakai"ta faɗa tana cire goran ruwan daga bakin ta. Sai daya gyara zaman sa yana ƙara fuskan inda take zaune sannan yace"To granny inajinki".Murmushi ta saka yayin datake miƙewa tace"to jirani in shiga bathroom na fito". Kansa kawai ya ɗaga mata sannan ta wuce bathroom ɗin.Wayar sa data fara ringing ya ɗaga"Angon Hibba yane?"cewar Bashir. Sai daya shafa sumar sa kafin yace"normal na shigo damaturu fa". "Ya maka kyau ai shine koka leƙo inda nake,ya Hibban ina fatan dai yanzu komai ya dai-daita ?". Sai daya furzar da wani zazzafan iska daga bakinsa shuru yayi ba tare daya ce komai ba. Ganin shurun yayi yawa ya sanya bashir faɗin"Mutumi na yadai". Sai a sannan yace"bashir wallahi har yanzu ba abunda ya sauya,babban tashin hankali na ma yanzu yasira ta fahimce komai ina gudun ta sanarwa su daddy". Ya ƙarishe maganar yana miƙewa tsaye windown ɗakin ya nufa ya fara yaye labulen.Shima bashir ɗin sai daya numfasa kafin yace"Habib sanarwa su daddy fa shine mafita,domin ta nan ne za'aji dalilin ta na aikata haka tunda har yanzu bata baka wani gamsheshshen hujja ba". "Bashir zan cigaba da roƙon Allah ya bani ikon jurewa har,izuwa lokacin da komai zai zamto dai-dai.Cikin kwanakin nan na lura kamar zaman gidan ma ba daɗinsa takeji ba a cikin ni da ita na kasa bambamce waye marar lafiy........". Cak ya tsaye juyowan dazaiyi idanun sa suka sauƙa akan Granny,dake tsaye bakin bathroom ta naɗe dukka hannayen ta a ƙirjin ta da dukkan alamu ta daɗe a wajen. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 3⃣0⃣ Saurin katse ƙiran yayi yana maida wayar aljihunsa sai daya dai-daita nutsuwar sa kafin yace"Granny kin fito".Bata kula shi ba illa ƙarisowada tayi bakin gadon ta zauna tana aika masa da wani irin kallo mai cike da tuhuma. "Habib wai meyake faruwa ne tsakanin ka da Hibba?". "Granny ba komai fa muna zaune lafiya da Hibba me kika gani?"yafaɗa yana zama kusa da ita.Sosai ta kafe shi da idanu tana cewa"Habib duk tattaunawar ku da Bashir ba wanda banji ba,ka faɗa min gaskiya meyake faruwa?". Ƙara matsowa yayi kusa da ita tare da riƙo hannun ta kafin yace"Granny ki yarda dani babu wata matsala tsakani na da mata ta"ya ƙarishe maganar yana sakar mata murmushi. Kallonshi kawai takeyi cikin son tabbatar da maganar sa nacewa babu wata matsalan"tashi kaje".Ta faɗa tana ɗauke idonta daga kansa. Tashi yayi jiki a matuƙar sanyaye ya fice,a falo ya zauna akan ɗaya daga cikin kujerun yana lumshe idanunsa da ba komai a cikinsu face bacci da kuma tsan-tsan gajiya.Daren jiya yanda yaga rana haka nan yaga dare ji yayi kamar bazai iya jurewa ba dalilin haka yau yasanya shi tashi da azumi domin kare kansa daga faɗawa izuwa halaka. Tare da Iya muka gama haɗa abincin karin kumallon sannan muka fara kaisu dinnnig,ciki-ciki nayi sallama ganinsa danayi akan kujera ya lumshe idanunsa saurin mayar da hawayen daya taro min a ido nayi,yayin danaji wani kibiyar tausayin kaina ya karbi ƙalbina. Ko tantama banida shi wani maganar sukayi da Granny wanda ya jefashi cikin wannan yanayin,ajiye flask ɗin tea ɗin dake hannu na nayi akan dinning ɗin.Sannan na wuce part ɗinmu na ɗauko masa maganinsa sannan na dawo,nan inda na barshi na same shi sai dai izuwa yanzun ya buɗe idanunsa yana kallon rufin falon da yazamto shamaki tsakanin sa da sararin samaniya. Kusa dashi na zauna na ɓalla masa maganin sannan na miƙa masa,idanunsa dasukayi jajir ya zuba mini sosai abin ya bani tsoro dan gani nayi kamar baya numfashi.Hannu nasa a ƙirjinsa na tabbatar da zuciyar sa na bugawa sannan na sauƙe wata zazzafar ajiyan numfashi. Ganin baida niyyar amsar maganin yasa nasa masa a bakinsa saurin riƙe hannu yayi tana faɗin"Nasha maganin tunda asuba yau azumi nakeyi". Da mamaki na nace"Azumin meye?". "Azumin kare kaina daga faɗawa izuwa ga halaka".Wani abu ne wanda bazan iya fasalta shi ba naji ya ratsa dukkan jikina baiɗaya.Miƙewa nayi yayi sauri kamo hannu na tare da faɗin"zauna inason muyi wata magana". Ba musu na komo na zauna ƙara kareni da rikiɗaɗɗon idanusa yayi har izuwa lokacin da Iya da Yasira suka fito,saurin tashi daga kusa dashi nayi na miƙe na nufi part ɗinmu domin ajiye maganin. Koda na dawo duk sun gama hallara akan dinning table ɗin,banda Habib dayake har yanzu zaune cikin falon duk yanda naso sakar jiki na kamar ba abinda ke damuna kasa hakan nayi,banci abincin sosai ba na tashi na koma part ɗin mu.Akan bed na zube ina sakin wani kuka dayake fitowa kai tsaye daga ƙasan zuciya ta. Koda suka gamayin breakfast ɗin ɗakinta Granny ta wuce bayan tacewa Yasira ta same ta a ɗaki,Tana zaune bakin gado tana kaɗa ƙafafunta data saƙale su wuri guda Yasira ta same takusa da ita ta zauna. "Yasira wata tambaya zan miki kuma inason kiyi mini alƙawarin,cewa zaki sanar dani gaskiyar abinda kika sani dangane da lamarin". "In sha Allah Granny zan sanar dake komai game da tambayar dazaki min gwargwadon masaniyar danake shi akan abun". Cike dajin daɗin furcin Yasira Granny ta ɗaura da faɗin"inason ki sanar dani abun dakika sani game da irin zaman da babban mutum sukeyi da matar sa Hibba,nasan dole zakisan wani abu dan kice kike zaune dasu". Wannan tambayar ta sanya canjin cikin Yasira kaɗawa sai data basar kana tace"Granny wani abun kika ji ko kika gani daya sa kike zargi wani abu a tsakaninsu?". Sanar da ita duk tattaunar Habib ɗin dataji sunayi da Bashir tayi sannan ta ɗaura da faɗin"Tabbas akwai wani abun dasuke ɓoye mana wanda nakeson ki sanar dani yanzu". Jin wannan maganar ta Granny yasanya Yasira ganin ba amfanin ta ɓoye mata,komai tunda ta riga da taji rabin bayanin gwara kawai ta sanar da ita ko zata nemawa Hamma Habib ɗin masifa. Sai data gama wannan tinanin kafin tace"Granny tabbas abinda kikaji haka ne,Basu taɓa haɗa gado da Hibba ba hasalima a mabambamtan ɗakuna suke kwana,Hamma ya ɓoye muku hakan ne a tinanin sa zai iya yiwa tufkan hanci sai dai kuma abin na neman yaci tura.Dan bana raba ɗayan biyu azumi da yakeyi yau bana Allah da annabi bane sai dai ganin da yayi lamarin na neman fin ƙarfinsa". Tabbas abinda Granny ke hasashe ne ya tabbata tace"Tashi kije zamuyi maganar da suraj".riƙo hannunta Yasira tare da marairaice murya ta shiga faɗin"Granny dan Allah duk hukuncin dazaku ɗauka kar ku raba Hamma da matar wallahi yana sonta dukkanmu shaidane". Kanta kawai Granny ta ɗaga mata alamar taji,sannan Yasira ta tashi ta fice daga ɗakin kamar yanda Grannyn ta umarce ta da hakan. Wayar ta Granny ta ɗaga ta ƙira Suraj bugu ɗaya ya ɗauka,ko gaisuwa kirki bata bari sunyi ba ta wuce kai tsaye ga maganar dake bakinta.Ajiyan zuciya Suraj ya sauƙe bayan ya gama sauraron Granny sannan yace"Hajiya yanzu meye abunyi,dan bazamu zuba ido mu cigaba da ganin Habib a cikin wannan halin ba gudun kar hakan ya haifar maba da ɗa marar ido". Itama ajiyar zuciyar ta sauƙe kana tace"Zan tarasu na musu magana idan har bata gyara ba,sai mu aura masa ƴar-uwarsa YASIRA na tabbatar ita zata bashi kulawa yanda ya dace tunda ƴan uwa suke". Sosai Suraj yayi na'am da batun Granny sannan sukayi sallama,Ina kici cikin part ɗin mu ina haɗawa Habib abin ɓuda baki Yaya Fawas ya ƙirani bayan mun gaisa yake sanar dani yazo gano wajensu Baffa.Nan ya basu muka gaisa hadda Inna mun daɗe muna hira kafin mukayi sallama. Ina gama haɗawa na jeresu akan dinning dai-dai lokacin da Habib ɗin ya fito daga ɗaki domin zuwa masallaci,gabatar masa da dabino nayi yaci ina masa sannu da sha ruwa sannan ya fita. Sai danaga fitarsa sannan na koma ɗakin nayi nawa sallan.Kamar yanda ya saba sai da akayi isha'i sannan ya dawo,Shagwaɓe fuska nayi hadda hawaye na sannan na samu yaci abincin kaɗan jawo ni jikinsa yayi ya rungume,yana sauƙe ajiyan zuciya akai-akai kamar wanda ya shari mungun gudu. Ranar maƙale a jikinsa muka kwanta,washe gari kuwa da wurwuri muka tashi muka shirya kasancewar a ranar mukeson zuwa gidan Dr Bashir,Afalo muka iske su Granny hadda Iya. Kusan a tare muka gaida Granny da kuma Iya suka amsa ciikin sakin fuska,sannan muka wuce dinning mukayi breakfast. "Babban mutum yau baka azumin kenan"cewar Granny wanda hakan yasanya Habib ɗagowa ya kalleni kana yace"E Granny banayi sai ranan alhamis ai". Kanta kawai ta jinjina muka cigaba da cin abincin,koda muka gama dawowa falo mukayi muka zauna bayan mun zauna ne Granny tace"Babban mutum naji duk abinda ke faruwa tsakanin ka Hibba shiyasa na taraku anan,domin ji daga bakinku shin Hibba menene matsalar ki da kika bar mijin ki cikin wannan ukubar tsawon watanni uku?". Da dawani irin ƙarfi zuciya ta ke bugawa tamkar zata faso ƙirjina ta fito waje,sadda kaina ƙasa nayi inajin hawayen dake bin gefen kuncina yana sauƙa har izuwa saman wuya na. "Hibba ke muke sauraro"Granny ta ƙara faɗa a karo na biyu sai a wannan lokacin na ɗago kaina ina kallon Habib,wanda shima ɗin ni yake kallo baki nane ya shiga rawa nace"Hajiya idan nace akwai wani abunda Habib kemin na rashin kyautatawa wanda yasa nake masa haka to nayi ƙarya,ban taɓajin wani abun mai suna sha'awa ba,nima bansan dalili ba zuciya bata nutsuwa aduk lokacin dana ganshi kusa dani ". Na gwammaci yau in sanarwa Granny komai koda hakan kuwa na nufin za tace Habib ya sake ni,"shi kenan dalilin?"furcin Granny. Habib ne yayi saurin faɗin"Granny ina zaune lafiya da mata ta,bayan wannan abun bata rageni da komai ba dan Allah mubar maganar nan anan". Kallon da Granny ta watsa masa ya sashi yin shuru tare da sunkuyar da kansa ƙasa tace"Bada kai nake magana taba kabar ita wacce nayiwa,tambayar ta amsa". Ahankali nace"Wannan su kenan dalili na amma wallahi band.....".Saurin katse ni tayi ta hanyar faɗin"Kuje keda mijin ki ku nema magani na baku wata biyu,idan har na ƙara fahimtar irin haka na cigaba da faruwa tsakanin ku.To daman munyi magana da Suraj ga nan ƴar-uwar ka Yasira sai mu aura maka ita,ta kula dakai tunda dai ita ta kasa". Cikin wani irin hanzari Yasira tace"Granny dan Allah kubar Hamma da matar sa"tana kawo wa nan ta fice daga falon. Habib yace"In sha Allah zamu nemawa kanmu mafita".sai da ta ɗauke kanta kafin tace"Da kuwa kun kyautawa kanku,ni ban taɓajin irin wanga batun ba ". Iya da tunda ɗazu batace komai ba tace"Amma Hajiya sai na kega kamar yanda Hibban ta bayyana akwai alamu sihiri acikin lamarin". "Koma dai menene na basu nan da wata biyu in basu nemawa kansu mafita ba,zan zartar da nawa hukuncin"furcin Granny. Share hawayen dake kai kawo a fuska na nayi kafin nace"Iya bana tinanin sihiri ne domin bayan yaya Fawas da kuma Habib,duk duniya babu wanda ya damu dani balle kuma rayuwa ta domin hatta mahaifiyar da ta ɗauki cikina a jikinta na tsawon watanni tara na rayu cikin mahaifar ta,tayi naƙudata bata damu da ni ba. Balle kuma har ace wani ya damu da rayuwa ta har yamin sihiri".Na ƙarishe maganar ina ƙara fashewa dawani sabon babin kukan. "Wohoho!ƴarnan yanzu rayuwar nan an daina kiwon dabba na mutum akeyi,wanda baka damu dashiba shikuma komai naka tsule masa ido yake yi". Sai a sannan Habib yace"Iya ba wani sihiri kamar yanda ta faɗa zuciyar tace bata son gani na kusa da ita shine kawai".Saurin ɗago kaina nayi ina kallon shi meyasa Habib zaimin irin wannan fahimtar?,shi kaɗai nakeda yaƙinin zai fahimce ni?.Ashe shima fahimtar irin tasu Granny yamin na ganni cewa kamar faruwar hakan son raina ne. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 3⃣1⃣ Yana gama faɗin ya tashi yabar falon da kallo nabi bayansa yayin dayake ficewa daga falo,wasu hawayene suka shiga ambaliya saman kunci na Granny ma tashi tayi ta fita ya rage dagani sai Iya a falon. Ita keta aikin lallashina nima ɗin daga bisani tashi nayi na wuce part ɗinmu,a falo na tarar da Habib yana zaune kusa dashi na tsuguna sai dana tsagaita kukan nawan sannan na shiga faɗin"Habib nasan na cutar dakai amma nima bayin kaina bane wallahi nima ako yaushe,burina na fatarta maka kamar yanda kaima kake ƙoƙarin kwatanta hakan a kaina". Sai daya sauƙe wani ajiyan zuciya kana yace"Hibba bansan meyasa kike amfani da soyayyar danake miki ba wajen azabtar da zuciyata ba,amma na tabbata kinji abinda Granny ta faɗa zasu rabani dake"ya ƙarishe maganar cikin rauni. Magana na somayi amma ya dakatar dani ta hanyar faɗin"Kiyi haƙuri komai zaki faɗa yanzu bazan saurare kiba tashi kishiga ciki". Da gudu na miƙe nayi bedroom ina shiga na zube kan gado,ina sakin wani kukan mai matuƙar ƙarfi wanda nakejinsa yana fitowa kai tsaye daga ƙasan zuciyana. Sosai nakejin raina yana min zafi yayin da wani tarin mai ƙarfi ya sarƙe ni,tashi nayi zan shiga banɗaki jiri ya ɗebeni ya dawo dani kan gadon dafe kaina nayi inajin yanda yake sarawa. Ƙara yunƙurawa nayi na tashi hannuna na riƙe da kaina,na nufi banɗaki ina shiga nafara kwara amai sosai nake amayarwa jingina nayi da ƙofar banɗakin saboda jirin danajin yana ƙoƙarin yasar dani ƙasa.wanke fuskana nayi sai a sannan na lura da aman danayi wanda mafi yawansa jini ne. Kukane ya kubce min nayi saurin toshe bakina ina silalewa ƙasa,sunayen Allah na shiga karantowa wannan wace iriyar rayuwace?,menene yake shirin faruwa dani?. A hankali naja jikina na fito daga banɗakin bayan na ɗauro alwala hijabina na saka na tada salla,duk jikina ya ɗauki rawa ko sallan ma banyi ta da cikakken nutsuwa ba haka na sallame nan kan sallayan na zibe ina fitar da numfashi ɗaya-ɗaya. Baccin ma ya gagareni sai ciwon kan daya tsananta gareni har aka kiran zuhr ina kwance a wajen,na tashi nayi sallan sai danayi sallan la'asar sannan na ɗauko maganin Habib na fito falo. Ban tarar dashi a falon ba hakan yasa na fito na nufi part ɗin Granny acan cikin garden na hange shi,yana zaune kan kujerun cement irin waɗanda ake ginawa ɗina a cikin jami'o'i da suke zube a wajen. Da sallama na isa gareshi amma tinanin da yayi nisan ciwo a cikinsa yasa baiji zuwata wajensa,sai dana zauna dab dashi ina karkaɗa ledar maganin dake hannuna sannan ya farga da zuwana. Murmushi na sakar masa a lokaci guda na ɓalla masa maganin na miƙa masa,ya karɓa tare da afasu a bakinsa na miƙa masa ruwan yabi bayansu dashi. Tashi nayi zan tafi ya tsayar dani ta hanyar cafko hannuna cak!na tsaya ba tare dana waigo ba,tasowa yayi yana ƙara damƙe hannuwana cikin nasa sannan yamin ishara da idonsa hakana mu tafi tare muka jero dashi muka nufa part ɗin Granny. Afalo muka sameta tana zaune tare da Yasira sallamar da muka shigo dashi shiya sanya Yasira tashi tabar falon cikin sauri tayi ɗakinta. Zama mukayi muna yiwa Granny barka da hutawa,ta amsa ba tare data dube muba tashi Habib yayi yabi bayan Yasira wanda dalilin hakan naji wani baƙin-ciki ya ziyarci zuciyata. Furcin Granny ne ya faɗo min arai nacewa datayi wai zasu haɗa Habib da Yasira ƴar-uwarsa aure tunda ni nakasa samar mai da farin-ciki. Tashi nayi ina maiyiwa Granny sallama na nufi part ɗinmu inajin yanda ƙirjina yamin wani mungun nauyi,ina isa na wuce bedroom bayan na lock ɗin ɗakin na saki kukana. Sosai nakeyinsa numfashina har yana ƙoƙarin sarƙewa,lokaci ɗaya sai naji duk zaman gidan Grannyn ya gundure ni.tabbas nasan ina yiwa Habib wani irin son dako nima bansan adadinsa ba,haka nan kuma banji zan iya jure ganinsa dawace ƴa mace koda kowa Yasira ce. Habib kuwa gefen gado ya hango Yasira ta takure tana hawaye,kusa da ita ya zaune yana cusa hannayensa cikin tarin sumar kansa a lokaci guda yana furzar da iska daga bakinsa. "Kayi haƙuri ka yafemin na kasa riƙe maka sirrinka bada wani nufi na sanarwa Granny ba saidan ina tinanin kamar hakan zai kawo muku mafita a gareku". Sai daya fuskanto ta kana yace"Ƙanwata bakimin wani laifi ba hasalima taimaka min kikayi na gano abunda ban saniba,ashe ganina ne kusa da ita baso kinga yanzu sai indinga jaye jikina kodan farin-cikinta". Cikin wani kukan Yasira take faɗin"Hamma kanaji fa cewa sukayi zasu haɗamu aure wallahi Hamma bazan iya zaman kishi da matarka ba". Taƙaitaccen murmushin gefen baki yasaka kana yace"Bakya sona ne daman ban sani ba?"saurin jijjiga masa kai tayi alamar a'a.Sannan ya ɗaura da faɗin"to kukan nan na menene?". "Hamma banso ace nazamto silar dazaka sama saɓani tsakaninka da matarka".riƙo hannunta yayi yasa su cikin nasa kafin ya shiga share mata hawayen yana cewa"ki daina wannan kukan banso kinji,ki kwantar da hankalinki in sha Allah babu abinda zai faru kedai ki tayani da addu'a Allah ya ƙarfafa min zuciyata ta iya jure duk abunda zai faru nan gaba". Sosai tausayinsa ya ɗarsu a ranta ta share hawayenta ta nuna masa komai ya wuce,sannan suka fito tare basu iske Granny a falon ba dan haka suka fito suka nufa part ɗin mu. A falo ya zaune yace mata taje ta tasoni muje gidan Bashir ɗin,ina kwance naji ana knocking ƙofar nace"wayene". A ɗayan bangaren muryar Yasira na tsinkayo tana cewa"Anty daman Hamma ne yace inkin gama shiryawan ki fito ku taje gidan Bashir ɗin". Runtse ido nayi da ƙarfi ba tare dana buɗesu ba nace"kice masa banjin daɗi bazan iya zuwa ba". Juyawa tayi taje ta sanar dashi kamar yanda na faɗa masa,bai nuna wata damuwa ko kuma son yayi magana dani ba,ya miƙe ya fice yayin da Yasira ta rufa masa baya. Tare suka jera har jikin motarsa,ina tsaye cikin window ina hangesu sai danaga ficewar motarsa kafin na dawo na kwanta lamau akan gadon. Kuka nakeson nayi amma hawayen sunƙi zuwa,cikin haka har aka ƙira sallan magrib na tashi nayi ko bari kan sallayan banyi ba aka ƙira isha'i kasancewar nayi magrib ɗin a makare nayita. Ina iddar da sallan isha'in naji ƙaran shigowar motar Habib,na zata part ɗinmu zai shigo sai kuma naga akasin haka domin Part ɗin Granny ya nufa. Ganin haka ya sanyani komawa saman gadon na kwanta,figigi ta farka daga baccin daya fara fizgana sakamakon ji danayi kamar ana ƙoƙarin buɗe ƙofar. Yana gama kiciniyar buɗe ƙofar ya shigo yayin dayake zara sifiya key ɗin daya buɗe ƙofar dashi a aljihunsa. Gefen gadon ya zaune nisa dani kaɗan yace"tashi inason magana dake".tashi nayi jikina duk ba ƙwari kamar sabuwar haihuwar kazar da ruwan sama ya lakaɗa mata duka. "Hibba su Granny nason aiwatar da ƙudurinsu nason haɗani aure da Yasira,banga laifinsu ba domin nasan ƙaunarsu gareni shiya jawo hakan.Tun kafin aurenmu yaje ko'ina kinason wargaza farin-cikin dake cikinsa meyasa?,nasan kinsan cewa hakan yana iyasa a kashe aure ko?meyasa kika aikata hakan ga raunanniyar zuciyar da batasan komai ba face soyayyar ki?". Ya ƙarishe maganar yana ɗan sausauta muryarsa,sai dana haɗiye kukan dake shirin fito min cikin muryar datake bayyanar da raunin da zuciyata take ciki nace"Habib tabbas nasan na cancanci kowani irin hukunci daga gareka harma daga danginka,amma inaso kasani banyi kaina bane kamar yanda na faɗa maka jiya wallahi na rasa abinda kemin daɗi acikin duniyar nan,babu ranar danake fargaba irin ranar da Allah zai kamani da wannan laifin a gaban dukkan halittunsa.Bazan hanaka yin aurenka domin tabbas inayi hakan na tabbata azzaluma,kuma na tauye maka hakki.....". Saurin kai hannunsa yayi ya toshe min bakina kana yace"ki daina faɗi haka in sha Allah inama fatan komai ya dai-daita basai ankai ga ƙarin auren ba,munyi magana da Bashir akwai wani malamin daya sani yana bada magani game da irin lalurarmu in sha Allah zai taimaka mana". Hannunsa yakai saman wuyana zafi gau,magani ya ɗauko yabani nasha sannan muka kwanta ranar na ƙudurce zan bawa Habib dukkanin hakkinsa dana daɗe ina tauye su koda kuwa hakan na nufin ƙarshen numfashin dazanyi a rayuwata. Ranar farin-ciki wurin Habib baya misaltuwa dan abinda bai taɓa tsammani bane ya faru,dan a hirar dasuka da Bashir har suna tinanin wai ko aljani ne ya aure ni. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _________________________________ Page ɗin jiya ansama mistake wajen rubutun shine page 31 wannan kuma 32. __________________________________ Page 3⃣2⃣ Haka nan washe gari na tashi da matuƙar ciwon kai ga kuma wata iriyar kunyar Habib ɗin da yayi dabaibayiwa zuciyata. A ranar kuma shirya komawa katsina tare da Yasira har ƙasan zuciyata nake murnan komawar dazamuyi,muna gama kalaci mukayi shirin tafiya muna tsaye cikin harabar gidan Granny da Iya suka fito fatan sauƙa lafiya suka mana,Iya ta bani wasu addu'o'in. Bayan ta jani gefe ta faɗamin wasu abubuwan dazan nayi domin ɗauke hankalin Habib ɗin,domin nasan har yanzu yana fushi dani dannewa kawai yakeyi. Tunda muka baro cikin damaturu na lumshe idanuna ban boɗesu sai lokacin danaji Habib yana bubbuga kujerar motar dana jingina kaina aciki.Ware idanuna nayi wanda najisu har wani zafi-zafi sukemin sakamakon ciwon kan daya tsananta a gareni. Na tsaida idona akan fuskarsa jidanayi ya ambaci sunan Baffa yasa ƙirjina dukan tara-tara,inajin Baffa yana cewa"Kabawa Hibban wayan".tunin nafara ruwan ƙwalla ina jijjiga masa kaina alamar yace bana kusa. Shima hakan yaso ya faɗa masa amma ganin yanda Baffa yake surfa masifa yace"ki karɓa kawai"ya faɗa yana ɗan sausauta muryasa ta yadda Baffa bazai jiyo shiba. Ganin banida niyyar karɓa yasa shi sanya wayar a handsfree,sannan yace"Baffa gatanan tana jinka". "Wato duk abinda nake faɗa miki Hibba bakyajinsa ko?,ashe irin zaman dakukeyi da Habib kenan?,yanzu badan Hajiya jiya taƙirani ta sanar dani ba da haka zaki cigaba da cutar da wannan bawan Allahn ko?.Nace dashi yanzu ya kawo min ke kinaji ko?".Cikin muryana da fara dushashewa nace"naji Baffa ". Sannan yace inbawa Habib ɗin wayar,Habib ɗinne yayi saurin faɗin"Baffa inajinka". "Yanzu inaso ka kawo min ita,inkuma kana wani irin ka haɗota da driver suzo". "Ba koma Baffa yanzu zan kawota in sha Allah"Habib ya faɗa yana kashe wayar. Nikam runtse idanuna dani yayin danaji kaina ya sara mini da matuƙar ƙarfi,tunda naji yace Hajiya ce ta ƙirashi jiya ta sanar dashi nagane Granny yake nufi.Duk yanda naso haɗiye kukan dake zuwar mini kasa hakan nayi. Yasira ce keta aikin lallashina tana bani haƙuri,lokacin muna dab da shiga cikin kano muna wudil Habib ya faka motar a gefen titi. Lokaci guda ya feso iska daga bakinsa wanda har sai danaji titirin iskan a fuskana.Sai daya riƙo hannu na yana gyara zamansa yana fusko ni sosai har inajin bugun zuciyar sa yace"Hibba wannan kukan bashine mafita ba,inason ki matata kuma ina tabbatar miki zan tsaya miki a wani irin yanayi.Zan faɗawa Baffa wannan matsalar mun riga damun shawo kanta".ya ƙarishe maganar cikin son tabbatar mini da abinda ya faɗa ɗin. Banda na yadda da maganganun Habib ba nayi shuru ina haɗiye kukan danake yi,sai daya miƙo min tissue na goge hawayen daya ɓatamin fuskana sannan ya tada motar muka fara tafiya. Muna isa cikin gano muka wuce gidan Baffa sai daya dai-daita parking kusa da rumfar almajiran dake kusa da gidan sannan muka fito,Yasira ce gaba sannan Habib ni kuwa ina maƙale jikinsa muka nufa cikin gidan. Duk suna tsakar gidan hadda Baffa,Inna ce ta amsa sallamar da muka shigo da ita,sannan muka zauna kan yalwataccen tabarman damuka gani shimfiɗe a wajen. Inna muka gaisher ta amsa sannan muka gaida Baffa,fuskarsa kaɗai na kalla na fahimce yana cikin ƙololuwar ɓacin rai. Shuru ne ya karaɗe wajen na wasu daƙiƙun da bazasu gaza goma ba kafin Baffa ya shiga faɗin"Hibba watau bakya ganin girman kowa ke ko?".saurin jijjiga kaina nayi alamar a'a sannan ya ɗaura da cewa"Naji duk abinda kike aikatawa kuma wai abun takaici baki da wani dalili,kuma kin tabbatar dacewa lafiya kalau kike wallahi inaso kisani bazan ɗauki rashin mutumci ba Hibba kibi mijinki ki sana aljannar ki sannan ki gyara mu'alamarki tsakaninki dashi". Daga can ƙasan maƙoshina nace"in sha Allah Baffa " Sannan Inna ta ɗaura da cewa"Hibbatu menene matsalarki?,mekika nema kika rasa daga wajen mijinki?,bakya tsoron ki shiga fushin ubangijinki?nidai nasihar dazan miki shine kiji tsoron Allah kisani akwai ranar da zaki tsaya a gabansa domin hukunci.In kuma wata matsalarce dake ki fito ki bayyana sai a nema miki magani". Sai dana jawo gefen mayafina na goge hawayena kana nace"Inna banida matsala sannan banajin alamunta". Hamdala Inna tashiga yi kafin ta cigaba damin nasiha tana gamawa Baffa ya farayiwa Habib godiya akan irin halin dattakun daya nuna bai yanke ɗanynen hukunci ba. Anan zamu kwana domin Baffa yanema alfarmar haka daga Habib,shagon dake ƙofar gidan Baffa yasa almajirai suka sharewa Habib.Nikam tashi nayi na shige ɗakin Inna Yasira nabiye dani a baya tare da Inna. Hajara kam datun shigowar mu batace ko hazal ba ta bimu da kallo yayin damuke shigewa ɗakin Inna ɗaya nabin ɗaya. Wata dariya mai sauti ta saka yayin datake ƙoƙarin miƙe daga wajen ta fara haɗa wuta,tunda muka shiga ɗaki Inna ta tisani gaba tana ƙaramin wata nasihar tana ƙara nunamin halaccin kan. Sai da aka ƙira sallan Asr sannan muka fito mukayi alwala mukayi sallah,ina zaune kan sallayar Inna ta shigo da kwaskon turaren wuta a hannunta agabana ta direshi tana cewa"Ɗauki turaren nan kikai ɗakin Habibun". Miƙewa nayi na ɗauki kwaskon sannan na ɗauko maganinsa a cikin jakata na fito na nufi ɗakin nasa,daga waje na tsaya ina jera sallama ɗaya nabin ɗaya ganin ba a amsa ba yasa na tura ƙofar a hankali na zira ƙafafuna. Rarraba idanu na shigayi ina nema ta ina zan ganoshi,ba kowa a ɗakin sai dana ƙarisa shigowa na ajiye kwaskon hannuna,sannan na fara bin ɗakin da kallo. Ƴar katifa ce a ɗakin wanda Baffa yake sauƙan baƙi a cikin sa,sai kuma jakar kayan Habib ɗin wacce muka taho dashi daga gidan Granny. Ina tsaye naji kamar za a buɗe ƙofar ɗakin nayi sauri gyara tsayiwa tana fuskar ƙofar domin ganin mai shigowar.murmushi ya sakar min yayin dayake baida ƙofar yana rufewa,nima murmushin na maida masa dashi. Sannan ya ƙarisa shigowa ya riƙo hannuna muka zauna bakin katifar,maganinsa na ɓalla masa na miƙa masa ya karɓa sannan na ɗauko masa jakar ledar pure watern dana gani kusa da kwanon abincin da Inna taba Yasira ta kawo masa. Sai dayasha maganin sannan nace"yanaga kamar bakaci abincin ba"na faɗa ina jawo kwanon samiran gabana buɗewa nayi naga ko taɓa shi baiyi ba. "Kinsan banacin green ɗin abubuwa shiyasa banci ba,anjima zan shiga cikin gari wajen Sayyid zanci acan"ya faɗa fuskarsa ɗauke da murmushin daya kasa ɓoyiwa. Tuwo ne miyar ayyahu abincin sai yanzu ma ninasan me aka dafa dan banci ba,tabbas nasan baya ta'ammali da ire-iren wanga kalolin abincin. Sai dana maraice fuska kana nace"shine baka sanar dani na maka wani abincin ba". "Bakomai karki damu banajin yunwar nema shiyasa kikaga hakan"ya faɗa yana lakuto kumatuna. Daga nan ya fara wuce goma da iri,banyi ƙoƙarin hana shiba saboda alƙawarin dana ɗaukarwa kaina jiya.Haka nan shi kaɗai yake kiɗansa yake rawarsa.Da wani irin kunya na fito daga ɗakin na nufi cikin gidan wani kunyar ne ta ƙara zuwar min lokacin dana shigo naga Inna da Yasira zaune a tsakar gidan suna waya da Ummi. Cikin sauri nakejan ƙafata na wuce cikin ɗakin Inna,Sannan na fito na ɗibi ruwa a bokatin ƙarfen dake yashe kusa da randa. Na shiga wanka ina shiga na ajiye bokatin ina durƙushewa a wajen,toshe bakina nayi ina hana sautin kukana fitowa,duk cikin namana jinake kamar ana watsa mini tafashashshen narkarken ruwan dalma,yayin da fatana dukka ya ɗauki zogi. Jinayi duk na tsani kaina yayin da haushin kaina ya ziyarce ni,amma sai dai ko kaɗan banyi nadamar hukuncin dana yanke ba. Duk banida kuzari nayi wankan na fito na shige ɗaki,cikin tafiya ta dabata gama dai-daita ba. Koda wasa ban leko ƙofar ɗakin ba koda Inna ta bani abinci inkawa Habib a Yasira nabawa ta kai masa,da wuri na kwanta yayin da baccin wahala ya fara fisgana figiga na tashi ji danayi wayata tahau ruri. Jawo ta nayi ganin sunan Habib ne yasani ajiye ta gefe guda,ta cigaba da rurinta har ƙiran ya tsinke aka sake ƙira a karo na biyu. Tisa wayar gaba nayi na haɗe dukka hannayena biyu saman ƙirjina ina kuka kamar wata ƙaramar yarinya. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________________ Page 3⃣3⃣ Sai danayi mai ishata kafin na kwanta inajin yadda raina kemin zafi,washe gari haka na yini duk jikin babu kuzari hakanan kuwa tun dana tashi banda wulgawar Anty Hajara ba,Inna naji tana faɗawa Baffa cewa taje gidan Barira ne. Muna zaune a tsakar gidan munayin karin kumallo Habib ya shigo tare da Sayyid,tashi Yasira tayi ta karɓo ledar dake hannun Sayyid ɗin sannan suka ƙariso suka zauna. Sai dasuka gaida Baffa da Inna sannan nidabYasira muka gaishe su,tashi Habib yayi yana saka takalminsa sau ciki yana cewa"Hibba ki sameni awaje". Saurin dawowa nayi daga tinanin da kwakwalwata ta antaya,nabi bayansa da kallo har ya fice daga cikin gidan.Miƙewa Inna tayi ta zubowa Sayyid ɗanwaken ai kuwa kamar jira yakeyi ya naɗe hannun rigarsa yahau ci yana faɗin"Inna kamar kinsa kuwa na daɗe rabona dacin ɗanwake". Washe baki Inna tayi sannan ta fara cewa"Ai kuwa duk lokacin dakake sha'awar ci,ka garzayo zan maka har sai kaci ka ture". Sosai Sayyid ya saki dariya mai sauti yace"shiyasa nake ƙaunarki tsohuwar nan duk da kuwa kinƙi kabari". Wata ƴar gajerar dariya ce ta suɓɓuce min wanda hakan yasa Inna ankara dani tace"A'a Hibbatu har yanzu baki tafi ƙiran da Habib yamiki ba?". Yatsina fuskana nayi tare dacewa"Inna yanzu zan tashi".Ina kawowa nan na miƙe naje na ɗauka maganinsa sannan na fito na nufi ɗakin nasan. Can ƙasan maƙoshina nayi sallama sai dana jira aka amsa sannan nasa kai na shiga,yana zaune saman sallaya na ganoshi yana waya da Ummi. Nesa dashi kaɗan na zauna ina sauraron hiransu da Ummi,duk da ba komai dasuke faɗa nake tantancewa ba. "Ummi ki kwantar da hankalinki wallahi komai ya wuce ba wata matsala yanzu,ko ita Hibban ma yanzu ta canja".Cewar Habib hakan danaji ya faɗa ya jefani cikin kokwanto akan wani magana sukeyi haka?. Jin wayar danayi a kunnena yasa naɗan ɗago idanuna na kalleshi sannan nakuma maida dasu ƙasa,ina ƙara manna wayar a kunnena.Sallama nayi tun kafin ta amsa na ɗaura da gaishe ta ta amsa sai datayi jim kafin tace"Naji duk yanda kukayi da Granny kamar yanda in Yasira ce a matsayin dakike bazanji daɗi ace hakan ya faru a zaman aurenta ba,Haka nan ma ke Hibba ki gyara zaman aurenki duk wani mai ƙaunarki bazaiso ace daga auren wata uku har za'a kawo min kishiya ba.Saboda gazawarki.Ki dogara da Allah sannan ki dage da addu'a dakuma tsayiwar dare,zan kuma cigaba da sawa ana amso miki". Cikin karayar murya nace"In sha Allah Ummi zanyi yanda kikace,nagode Allah ya ƙara ingantaccen lafiya da nisan kwana mai albarka".na ƙarishe maganar inakai dubana ga Habib wanda na lura hankalinsa nakan laptop ɗin dake gabansa. Sallama mukayi da Ummi sannan na kashe wayar,na ɓalla masa maganin na miƙa masa. Ba tare daya juyoba yace"yau dai kam kiyi haƙuri mana ki barni na huta,da shan kwayoyin nan"ya faɗa yana shagwabe fuska. "Cab!kasan Allah kawai ka karɓa kasha ko kuma yanzu in fita waje na nemo mutane,su shigo su danneka na ɗure maka"na faɗa ina ɗan tsuke fuskata. Dariya yakeyi sosai har yana riƙe ciki sai ya gaji dan kansa kana yace"Ashe kuwa akwai yaƙi,ɗure sai kace wani sabon yaro ɗan yaye". Nace"ai kuwa kasha kawai shine samun zaman lafiya". Karɓa yayi yasa abakinsa sannan na miƙa masa ruwa yabi bayansu dashi,tashi nayi zanfi yayi saurin riƙo hannuna yana cewa na zauna tunin idanuna suka kawo ruwar ƙwalla nayi saurin taresu kar ya gani. Cikin muryata data soma rawa nace"Inna ce tace inzo da wuri zan rakata wani unguwa"ina kawowa nan nayi nasarar raba hannuna danawa na ɗauki hanyar fita daga ɗaki da ƴar sauri na,sai danazo dab da ƙofar ɗakin naji yana faɗin"inkin shiga ki sanar dasu yau zamu wuce". "Uhmm"nace sannan na fice na nufi cikin gidan,Hajara na hango tana dawowa,muna haɗa ido da ita ta jefomini wani murmushi dana kasa gano manufar yinsa. Sakeke na tsaya a wajen kamar wawiya,har ta raɓa ta gefena ta shiga cikin gidan.sannan nima na shiga nan inda na barsu Inna na dawo na tardasu. Yasira tana yanka lemo da abarban dasu Sayyid suka kawo. Sai dana zauna ina ɗaukar lemon dake dake kan fatanti a gaban Yasira nace"Hamma yace ki shirya anjima zamu wuce". Tace"To". Sannan muka cigaba da hirarmu ko lokacin dana shiga banga Hajara awajen ba,wanda nafi kyautata zaton ɗakinta tayi.yaya Fawas na ƙira mukasha hirar mu bayan shima yaƙara ja mini kunne akan na gyara zaman aurena. Sai damukayi sallan zuhr sannan muka fara shirin tafiya bayan mun sama kyawawan addu'ar sauƙa lafiya,nace"Inna yaushe zaki zo min?". Sai ta murmusa kan tace"Hibbatu sai kin haihu zanzo". Dariya nasaka sosai nace"Innata kenan".sannan mukayi sallama muka tafi,har muka shiga mota Baffa bai daina gargaɗina akan kar na sake yaji na ƙarayi wani abu makamanci haka,inkuwa na kuma shida kansa zaisa Habib ɗin ya sakeni,nazo gidan naci uwar abinda zanci. Da haka dai muka tafi bayan na gama ɗaukar huɗubar Inna da Baffa,sai da muka sauƙe Sayyid a makarantarsu sannan muka wuce. Muna isa cikin katsina muka wuce gidan Ummi,Habib kam ko shigowa baiyi ba ya wuce office a cewarsa wai yayi baƙi suna jiransa. Ummi muka samu zaune a falo tana sauraron tafsirin da malam Jabir sani mai hula yakeyi a tashar Albani TV.da sallama muka shigo Yasira najan akwatin kayan mu,da farin-cikin daya kasa ɓoyiwa a saman fuskarta ta miƙe tana amsa sallamar damuka shigo da ita. Sai da muka zauna sannan muka gaisheta ta amsa tana tambayar mu Granny da kuma su Baffa,muka amsa da lafiya duk suna gaisheki.Nan muka cigaba da hirarmu bayan ta tambaye mu ina Habib. Yasira ce tabata amsa dacewa"Ya wuce office wai ana jiransa". Hira mukayi sosai Ummi tana ƙara kwantar min da hankali akan maganar auren Yasira da Habib da Granny da Daddy suka ƙudurce yin hakan. "Wallahi Ummi nifa har yanzu ban ɗauki maganar da gaske ba,gaskiya bazan iya zuwa gidan Hamma a matsayin kishiyar Anty Hibba"cewar Yasira ta faɗa tana ɗan tsuke fuskarta. Daga ni har Ummi dariya muka ɓarke sai damukayi mai isharmu kafin nace"Haba!ke kuwa Hamman nakine zakice bakyason sa komeye?".na ƙarishe maganar cikin yanayin zolaya ina haɗa mata gira ɗaya. Pillown kujerar dake kusa da ita ta jefo min tana faɗin"wallahi Anty bazan iya ba".tashi nayi ina dariya ina cigaba da cewa"Amaryar Hamma Amaryar Hamma". Nan muka fara zagaye falon tana bina da pillow a hannunta. Ummi da dariyar datake yaƙi barinta ta sarara,sai data tsagaita dariyar kana tace"Allah ya shiryamini ku"tana kawowa nan ta miƙe ta shige ɗakinta. Haka muka yita zagaye falon muna cikin haka mukaji ƙaran shigowar motar Habib,fitowa mukayi dai-dai lokacin da Habib ɗin yake fitowa daga cikin motar a guje muka nufe shi saurin ɓoyewa a bayansa nayi ina maida numfashi. Sai daya dawo dani ta gabansa kana yashiga tambayarmu meke faruwa?Yasira ce tayi saurin bashi amsa tana cewa"Hamma cemin take fa wai Amaryarka".ta ƙarishe maganar tana jefo mini pillown hannunta. Shima dariyar ya saka tare da faɗin"Lalle dole ta fuskanci hukunci tunda tasamini ƙanwa hawaye". Ya faɗa yana ƙara haɗani da jikinsa muka ƙarisa shiga cikin gidan,sai gwalo nake yiwa Yasira wacce take sharar ƙwalla. Nida Yasira kitchen muka wuce shikuwa Hamma ya wuce ɗakin Ummi,abincin dare muka haɗa sannan muka jeresu hakan yayi dai-dai da ƙiran sallan magriba da aka farayi. Sai damukayi sallan isha'i sannan muka dawo falo muka zauna,har izuwa lokacin da Habib da Daddy suka dawo abinci mukaci sannan muka fara shirin tafiya,bayan Daddy yaƙara mana nasiha sosai. Yasira kam anan muka barta muka dawo,tun daga wannan rana nasakewa Habib jikina duk da yanda nakejin raina yana tafasa kamar rumon farfesu. Ranan na tashi da matuƙar ciwon kai dana jiki,ta yadda naji bana ƙaunar fito rana ko makaranta banje ba haka nan girki ma banyi ba dan Habib bazai dawo cin abincin rana ba. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________________ Page 3⃣4⃣ Dakƴar nake ɗaga hannuna saboda kasalar data sauka min,a dukkan jikina jan jikina nayi zan tashi jirin dake ɗibata ta dawo dani ta warɓa akan gadon.Ƙara yunƙuruwa nayi na tashi ina riƙe da gefen ƙuduna nayi toilet haka nan naji bazan iya alwalar da ruwan sanyi ba,hakan yasa na fito na jona heater sai daya tafasa sannan nacire na koma banɗakin. Alwalar nayi na fito inajin zazzaɓin dayake saɗɗata,na shimfiɗa sallaya na tada salla koda na iddar tashi nayi na nufi sashin Hajja. Tana shara na sameta ganina datayi yasata sakin tsintsiyar tana cewa"Hajiya kece a sashin namu bari to na ɗauko miki shimfiɗa". Ƙarisa shigowa nayi dai-dai lokacin data ɗauko mini tabamar ta shimfiɗa,na haye kai na zauna ina haɗe ƙafafuna wuri guda nace"Hajja aiki kita yine?"na faɗa ina kai kallona da tulin wanke-wanke take jibge a tsakar gidan. "E wallahi yau ma tashi sam banajin daɗin jikinane kisan jiki da jini". Na kuma cewa"Wallahi Hajja nima nagaji da zaman kaɗaicin ne nace bari na fito kinsan Yasira ta tafi". Tashi Hajja tayi ta zubo mini kunnu a babban kofin jug ta direshi gabana,yanda nakejin yanayin jikina yau banaji sha'awar cin komai kai hannuna nayi na taɓa jikin kofin naji shi zafi gau. Hakan ya tabbatar mini da bata daɗe da sauke shi daga kan wuta ba,ita ta zuba mini kunnun nakai bakina a hankali sanda naji daɗin kunnun ya mamaye ilahirin duk wani kusurwa na bakina. Yasa na lumshe idona sannan na ware su ina tanɗe leɓena na ƙasa nace"Hajja wannan wani irin kunnu ne?". Sai data murmusa kafin tace "Kunun aduwa ne". Kaina na ɗaga inajin daɗin kunun na tsiga mini duk dabasa sugari a cikinsa amma ba kaɗan ba yamini daɗi. Tashi tayi ta cigaba da shararta yayin da nikuma na zuƙe kununnan tas!sannan na tashi na haɗa wanke-wanken na fara mata. Nan wajen Hajja na wuni har sai danaji ƙarar shigowar motar Habib sannan na tafi,yana ƙoƙarin fitowa daga cikin motar sanda na iso cikin parking alot ɗin rungumoni jikinsa yayi muka ƙarisa cikin gidan. Adaddafe na haɗa mana dinner muna gama ci nabi lafiyar gado dan duk wata gaɓa a jikina jinta nake ta sake tsabar gajiyan danayi. Haka kullum ya shigaba da faruwa dani kasala da rashin son cin abinci dan komai naji sai na amayar dashi,kunnun aduwan da Hajja kemini ne kawai yake iya shiga cikina ya zauna ba tare dana amar dashi ba. Duk yanda Habib yaso muje asibiti ƙi nayi nace masa ciwo ne na lokaci guda kuma zai daina,yace ko yayiwa Ummi magana Yasira tazo?nace masa A'a. Ranar tun da Habib ya fita sallan asuba naketa kwara amai a cikin toilet sosai na galabaita,haka ya dawo ya iskeni bayan ya taimaka mini na wanke fuskana muka dawo ɗakin lamau na kwanta a jikinsa ina fidda numfashi ɗai-ɗaiya. "Hibba ki tashi mu tafi asibiti "bance dashi komai ba na tashi na fara shirya jikina muka fito muna nufa asibiti,koda mukaje bayan nagama zayyanawa likitan ababen dake damuna scanning ya tora ni. Muna zaune a ofishinsa muna jiran a kawo result ɗin,wata nurse ce ta turo ƙofar ta shigo bayan ta ɗan rusuna ta gaida likitan ta miƙa masa takardan dake hannunta sannan ta fice. Lalumar gilashinsa likitan yayi ya maƙala a idonasa,sannan ya shiga duba result ɗin zare gilashin ya shigayi a lokaci guda koma yana ƙara yalwata fara'ar dake shimfiɗe akan faffaɗan fuskarsa wacce girma ya fara bayyana akanta,sai daya miƙowa Habib hannu sukayi musabaha sannan yace"congratulation abokina madam tana da juna biyu na tsawon satikai shidda". A hankali na zare hannuna daga toshe hancina danayi saboda ƙarfin turaren dake ofishin na nema uzura mini,Habib miƙewa yayi nan yayi sujudul shukur yana mai jaddada godiya da ubangijin talikai. Nikam kunyace taso rufeni dana lura irin kallon da Habib ɗin ke aiko min dashi,tsam!na miƙe na fice daga ofishin ina ta mai-maita kalmar "Alhamdulillah"a cikin zuciyana. Inajin Habib yana tambayar likitan shawarwa akan yanda za'a kula da cikin,sanda nake ficewa daga cikin ofishin inda mukayi parking na nufa na shiga cikin motar iska mai matuƙar zafi na furzar daga bakina ina jingina kaina ajikin kujerar motar. Lumshe idona nayi ina hango fuskar Habib lokacin da likitan ke faɗamasa ina ɗauke da juna biyu,irin farin-cikin daya taso masa lokaci ɗaya. Banji shigowar saba saijin ƙarar rufe murfin ƙofar motar danaji saurin cusa kaina nayi cikin tafukan hannuna ina ɓoye fuskana,murmushi ya saka mai sauti kana yace"Hibba nagode wannan farin-cikin dakika sani a cikinsa yau Allah yamiki tukwuici da aljannarsa maɗaukakiya,Allah yasa wannan cikin ya zamto sanyin idaniya agaremu". A zuciyata amsa sannan ya tada motar tunda muka fara tafiyar idanuna suke runtse,ban buɗesu ba sai lokacin danajin motar ta tsaya ganin inda muke yasa na kallo shi da sauri. Ɗaga min gira ɗaya yayi yayin dayake ƙoƙarin since bal ɗin motar dake jikinsa sannan ya fita,wata zuciyar tace min"Mutumin nan yau kawai so yake kirasa inda zakisa kanki saboda kunya,inba hakaba meyasa daga barinmu asibiti zai kawoni gidan Ummi?". Jidanayi har ya zagayo ya buɗe min ƙofar motar yasa ya dawo daga tinanin dana lula,a hankali na sauƙo da ƙafata na fito muka nufa cikin gidan.A falo muka tarar dasu hadda Daddy Sayyid ma lokacin yazo gida. Sai da muka zauna sannan muka gaishe da Ummi da Daddy suka amsa,kafin Ummi ta ɗaura ta tambayata ya jikin nawan dan Habib ya faɗa mata kwana biyun nan banajin daɗin. Tun kafin nakai ga bata amsa Habib yayi saurin cewa"Ai Ummi kedai kam kin kusa samun jika"ya ƙarishe maganar yana miƙo mata takardan da likitan ya basa. Nidai kam da kunyar Daddy da Ummi yana nasara inda zan sakaye kaina,na tashi da sauri na nayi ɗakin Yasira na kwanta abini.koda Ummi ta karanta takardan godiyawa Allah ta shiga rabzawa ɗaya nabin ɗaya sannan tamikawa Daddy takardan dubawa yayi jikin tsanaki kana ya tsaki guntun murmushi tare da faɗin"Allah ta raba lafiya"duk suka amsa da amin. Nikam tun dana shiga ɗaki ban fitoba sai da zamu tafi,kaina a ƙasa hakana fito muka tafi Yasira sai dariya takemin,muna isa gida na wuce toilet na sakewa kaina ruwa sannan na ɗauro alwala na fito doguwar rigata marar nauyi na zira na tada sallan Asr daka fara ƙira ina iddarwana fito falo na zauna na tunna TV tashar Manara Tv nakai naci sa'a kuwa sun saka karatun al-qur'ani hakan yasa na ƙure volume kamar yanda Ummi ta umurce ni kafin tahowar mu akan cewa inyawaita sauraron karatu saboda neman tsari daga dukkan abin cutarwa. Ina zaune Habib ya shigo ya dawo daga masallaci yana tafe yana waya da Granny yana labarta mata zancen cikin ko zama baiyi ba ya katse wayar ya ƙira Baffa shima ya faɗa masa inajiyo guɗar da Inna tarangaɗawa,sallama sukayi sannan yazo ya zaune. Harara na cilla masa ina cewa"kowa kaikam sai ka ƙirashi ka sanar dashi nifa nafiso kawai sai dai aji na haihu".dariya maganar yaso ya bashi ya mazge yace"Kinsan aka cewa wai abokin kuka ba'a ɓoyewa mutuwa duk waɗanda kikaji na ƙiransu Granny nece,Baffa sai kuma Bashir sukuma masu farin-cikin ne akan wannan abun bakiji yanda Inna tayi murnan jin wannan abunba,shiyasa gobe zamuje asibiti mu taimkawa masu buƙata don mununawa Rabbi godiya akan wannan arzikin daya bamu". "Allah ya kaimu Hamma"na faɗa ina akai masa da murmushin yaƙe,yace "Amin". Hajara kam tun lokacin da kunnuwanta suka jiyo mata lokacin da Baffa ke faɗawa Inna maganar nasama ciki,ta kasa tsaye ta kasa zaune duk ranta ya jagule mata hijabinta ta saɓa a ƙafaɗarta ta fita ta nufi gidan Adda barira. Ganinta da Adda barira tayi haka ya tabbatar mata daba lafiya,miƙewa tayi tana tsame hannunta daga cikin ruwan wankin datakeyi ta nufeta tace"Ƴar-uwa lafiya kuwa?". "Ina kuwa lafiya Adda wallahi ni nafara tinanin malamin nan kawai cin kuɗinmu yakeyi"ta faɗa hawayen takaicin nabin gefen kuncinta. Jan hannuta Adda Barira tayi suka shiga ɗaki"Ki nutsu kimin bayani yanda kwakwalwata taza fahimta Hajara meya faru?". Share ƙwallar dake kai kawo a fuskarta Hajara tayi da bakin hijabinta kafin ta shiga labartawa Adda labarin cikin dake jikina,salati Adda ta saka tana tafa hannu kafin ta riƙe haɓarta tana cewa"kai!gaskiya wannan abun da mamaki yake,amma kinsan abunda zamuyi bari muje wajensa kawai muji ba'asi dan zama bai ganmuba".ta faɗa tana jawo hijabinta dake maƙale samar ƙofar ɗakin sannan suka fito UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam Page 3⃣5⃣ __________________________________ Suna tafe suna surutai kamar sabbin zararru haka har suka isa gidan boka Iro kamar yanda tsarin shiga gidan yake,ba sallama haka suka shiga suka zauna akan buzun dake yashe a ɗakin nasan. Ɗan muzgutawa Adda Barira tayi kana ta shiga faɗa masa komai,kamar yanda Hajara ta faɗa mata sannan ta ɗaura da cewa"Allah gafarta malam mudai yanzu burin mu shine a ɓarar da cikin dake jikinta sannan a ɗaure bakin mahaifar ta yanda bazama ta ƙara samun wani cikinba,sannan koma buƙata ta biyu munason shi mijin ƴar-uwar tawan daga shi har mahaifiyarsa a mallakesu sai yanda Hajara ta juyasu kamar raƙumi da akala" Wani dariya mai sauti boka Iro ya saka wanda ya karaɗe ilahirin ɗakinnasan kafin ya shiga faɗin"Sai yanzu na ganu matsalar da aka samu tun farko,watau ita yarinyar babu wani haƙƙinku tada tauye zaluncine kawai irin na mutum mai ƙafa biyu,sannan dazaku raɓeta to zata zamto muku katangar sugari zata zamo alkhairi gareku". Kallo-kallo Hajara da Adda Barira suka shiga aikawa junansu kafin Hajara tace"Malam dan Allah ba wannan ne ya kawo muba mudai ayi yanda mukace inkuma kanaga bazaka iya bane saika faɗa mana munema wani".ta faɗa cikin sakewa da aikin Boka Iro. Wani kallon daya watso mata da rikiɗaɗɗun idanunsa yasa hanjin cikinta haɗawa"Ta gama ƙona aljanin damuka tura mata da ayoyin Allah,kuma ta kasance tana yawaita zama da alwala zaiyi wuya aikin dazamuyi ya cita domin mijinnatan ma ba haka kawai ya zauna akan cikinba yana addu'o'i". "Allah gafarta malam yanzu meye abunyi?"tambayar da Adda ta jefa masa tana tsaida ƙwayar idonta akansa domin jin amsarta. Ƙasar dake gabansa ya shiga bugawa yaɗau lokaci ahaka kana yace"babu abunda zai gagara kunkawo kukanku inda za'a share muku hawaye,cikin zai zube kamar yanda kuka buƙata kuma ita da haihuwa saidai ta gani awani wajen anayi,amma kuma ana buƙatar azubda jini ga aljanu domin aga biyan buƙata". "To malam godiya mukeyi zakaga aike in sha Allah"cewar Adda. Tsawar daya daka mata yasata rikicewa yace"ki kiyaye bakinki ba'a ƙira mana Allah anan". "Zan kiyaye". Tashi sukayi muka tafi suna ayyana inda zasu samo kuɗin abin yankan da Boka Iro ya faɗa,kowa tayi gidanta. Tun dana sama cikinnan nake samun kulawar Granny da duk wani masoyin Habib yayi farin-ciki da hakan,Sosai na dage da addu'a gami da sallan dare har wani makarantar almajirai dake kusa da makarantarmu naba wasu sadaka nace suna tayani da addu'a. Ranan nadawo daga makaranta a gajiye ga wani azababben yunwar dana kwaso,ina shiga nayi wanka nayi salla sannan na fito zan shiga kitchen,hakan yayi dai-dai da turo ƙofar falon da Hajja tayi ganin wacce ke biye da ita yasa na ruga aguje na rungumeta tsam a jikina inacewa"Anty Amina yaushe kikazo ya akayi kika gane gidan?". Sai data rabani da jikinta kafin tace"kin mantane kin taɓa min kwatance gidansu Habib nan naje aka haɗoni da driver yakawoni,danazo bakyanan shine na zauna awajen Hajja". Riƙo hannunta nayi muka zauna sannan naje na ɗauko mata ruwa da abun taɓawa gaisheta nayi ta amsa,sannan nashiga yiwa Hajja bayanin wacece Anty Amina a gareni. Nan mukayi hirarmu sosai sosai hadda Hajja sai yamma lilis sannan Anty Amina tafara shirin komawa daura,Habib na ƙira awaya na sanar dashi zuwarta inzai sama dama yazo su gaisa kafin ta tafi ya shaida mini dazai zo ɗin. Muna zaune a falon nida Anty Amina izuwa lokacin Hajja ta tashi takoma sashinta,Anty Amina tace"Hibba yanzu dai ina fatan babu wata matsalar ko?". Sai dana numfasa kafin nace"Anty Amina yanzu nema nake cikin babbar matsala dan samun cikin nan danayi ji nake kamar shi zai zamto dalilin yankewa farin-cikin rayuwata gabaɗaya". Saurin katse ni Anty Amina tayi ta hanyar faɗin"Subhananlahi!mekike faɗi haka Hibba?ki zamto mai kyautata zato akan komai sannan ki dogara da Allah kinji?"Kaina kawai na gyaɗa mata ina mai sunkuyar da kaina ƙasa zuciyata cike take da fargaba acikin kwanakin nan danji nake ina dab da rasa duk wani farin-cikina. Ƙara shigowar motar Habib danaji ya sanyani ɗago kaina bai ɗau lokaci ba ya turo ƙofar falon ya shigo yayin Anty Amina ke gyara mayafin dake jikinta tana ƙara lulluɓe jikinta dashi. A ƙasa ya zauna irin zaman kan yatsun ƙafa yana gaida Anty Amina ta amsa tana ƙara tayashi murnar ƙaruwar damuka samu tare da addu'ar Allah yakawu masu albarka,da Amin ya amsa mata dashi.Sannan ta miƙe muna ƙarayin sallama da ita har harabar gidan muka rakota na rakata ta shiga sashin Hajja ta mata sallama. Goma sha tara ta arziki Habib yayiwa Anty Amina sannan yasa Driver yakita har gida tare da mata alƙawarin shima zai kawoni cikin kwanakin nan kafin nayi nauyi. Sai mukaga ficewarsu daga cikin gidan sannan muka koma ciki,ƙirar sallan magrib da aka farayi yasa Habib fita masallaci kamar kullum sai da akayi sallan isha'i sannan ya dawo. Bayan munci abincin daya sayo mana dan bana iya yin girki muka kwanta,ciki baccin dayaci ƙarfina na farajiyo Muryar Habib a hankali na fara ware idanuna da ba komai acikinsu face bacci,Akan sallaya na hangoshi ya ɗaga hannayensa dukka sama bayan ikirarin danaji yana zubowa Ubangijin talikai ya ɗaura da faɗin"Ya Allah kaine ka bani farin-ciki a lokacin daban tsammata ba,Ya Allah ka ɗaurar dashi acikin sauran kwanakin dasuka ragemini a cikin duniya,ka azurta mu da samu ƴaƴa na gari wanda addinin musulumci zaiyi alfahari dasu dan girman zatikan ka tsawaita rayuwata a duniya nima naga jinina". Yana kawowa nan addu'ar yashafa komawa nayi na kwanta lamau yayin danaji wani kibiyar tausayinsa ta harɓi zuciyata har ta sama damar tarwatsata. Ban rutsa ba sai wajajen ƙarfe uku Habib dazai fita masallaci ya tadani nayi salla. Sannan na shiga kitchen na harɗa mana breakfast tea ne kawai sai irish potatoe dana soya mana,ina jeresu akan dinning Habib ya shigo lokacin har gari ya fara haske da hanzari ya iso gareni tare da karɓan flask ɗin tea ɗin take hannuna ya ajiye yana cewa"Haba!bana hanaki wannan aikin ba meyasa baki bari na dawo nayi ba?". Shagwaɓe fuskana nayi kana nace"Kawai nagaji da zaman ne shine nayi". "To banaso kina wahalar mini da Baby,wai yaushe zaki fara zuba awo ne?"yafaɗa yana ɗaura hannunsa a ƙasan marata dan lokacin cikin ya fara fitowa. Sai dana ɗaga kaina kamar wacce ke tinanin wani abun kafin nace"jiya dai Anty Amina tacemin wani sati ya kamata na fara zuwa tunda yayi sati ashirin da uku yanzu". "Allah yanuna mana"ya faɗa na amsa da Amin sannan muka zauna cin abinci nace"Hamma sunan wa zakasa in aka haifa cikin nan?". Murmusawa yayi yana sipping tea ɗin dake hannunsa yace"In macece zansa sunan mahaifiyata Zainab kenan,inkuma namijine zansa masa sunan Abbanki". Dariya nasa mai sauti nace"Allah ya kawosu lafiya"yace"Amin". Da haka muka gamacin abincin muka kimtsa wajen,sannan kowa yayi ɗakinsa yafaɗa bathroom shiryawa nayi cikin ɗanye les mai launin ruwar hoda ɗinki rigar bubace mai faɗi wanda najini nasake sosai acikinta,haka nan nabar fuskata daga lip gloss sai ɗan hodan dana murza na lulluɓa mayafita na ɗauki wayata na fito bayan naɗan murza ƴar humrata dan bana saka turare inzan fita,tun nadaji malamai nacewa haramune sanya turare ga ƴa mace yayin fita. Ganin Habib bai fitoba yana nazauna a falon ina jiran fitowarsa,ban jima da zama ba ya fito cikin shigar manyan kaya kamar yanda ya saba farar shaddace sol!tsayin rigar ya tsaya dai-dai gwiwarsa gajeren hannun gareta sai kuma hular kansa mai launin ruwan ƙasa tunin falon ya cika da ƙanshin turarensa na Laylatul sahara. Hannuna na ɗaga masa alamar yayi kyau ina kashe masa ido ɗaya,da murmushi ɗauke fal!akan yalwataccen fuskarsa ya nufo ni ya riko ni yayi muka fita domin zuwa asibitin bada taimako. Sai dana shiga sashin Hajja na mata sallama sannan muka tafi,Asibitin farko damuka fara zuwa asibitin gwanatine dake cikin garin funtua sosai Habib ya ware bakin aljihunsa yana bada taimaki ga marasa lafiyan dake kwance a asibiti,wata mata data kuka akancewa kwanan ta biyar a asibitin tare da ƴarta dake naƙuta har ɗan yamutu acikin cikinta amma a waje suke kwana saboda ƙarancin ishashshun gadaje a asibitin.Da taimakon Habib likitan ya rubata mata resing zuwa wani asitibin na kuɗi yayin da Habib ya ɗauki nauyinsu. Tunda muka baro asibitin nake ƙara godewa Allah akan ni'imar lafiya daya bamu,har muka isa gida ranar Habib zaije office ba tare muka wuni dashi cikin unguwa kawai suka fita tare da Malam Idi suka ƙara raba kayan abinci ga gajiyayyun cikin unguwa saboda watan azumin ramadana da yake gabatowa a wannan lokacin. Tunda muka dawo daga asibitin gabana yake faɗuwa narasa dalili yayin da zuciya take rayamini cewar wannan farin-cikin danakeyi ayau kamar shine ƙarshe a rayuwata saurin kawar da wannan mummunar hasashe na zuciyata nayi. har Habib yadawo ya same ni a haka komai a suƙure nake aikata shi inajin yanda gabana yake tsinkewa kamar wani mummunar abu na dab da faru dani. Koda Habib ya tambaye ni cemasa nayi gajiyace kawai,haka mukayi dinner na wuce ɗaki nabar Habib a falo yana aiki a laptop ɗinsa tsananin fargabar da zuciyata take ciki ranar yasa na kwanta ba tare danayi alwala kamar yanda nasaba kullum ba. Cikin baccin daya fara saɗɗata nayi mafarkin wai cikin dake jikina ya zube,firgigi na farka ina toshe bakina saboda ihun danaji na shirin kubce mini ba shiri sannan na shiga karanto addu'o'in neman tsari. Yunƙurowa nayi zan tashi najini cikin jini tsamo-tsamo bedsheet ɗin gadon yajiƙe jaƙaf yazama jajir nan fa naji wani azababben ciwon mara da ciki da kuma baya ya karyo mini,dam!na faɗu daga kan gadon nahau juye-juye a ƙasan wanda har izuwa yanzu jini bai bar zuba daga jikina ba. Numfashina na fuzga da ƙarfi da nufin kwalawa Habib ƙira sai kuma naji kamar an ɗaure min maƙoshina,irin azaban danakeji a jikina na gama saddaƙarwa ajalinane ya riske ni,kofin dake ajiye akan site drawer na jawo na dugashi da kan tile's dake malale ko'ina a ɗakin. Jiyo ƙarar fashewar kofin yasa Habib shigowa ɗakin da hanzari yana ƙiran sunana ganina dayayi cikin halin danake ciki yasa ya nufo a matuƙar gigice. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam __________________________________ Page 3⃣6⃣ Ɗago kaina yayi lokacin har nafita hayyacina ya ɗaukeni ya fito muka nufi mota zaburar motar yayi da ƙarfi yayin da Malam Idi ya fito buɗe masa gate ɗin yana tambayar lafiya?ya faɗa masa abunda ya faru. "Subhananlahi!ai kuwa dai bari na taso Hajja ku tafi tare da ita"cewar Malam Idi yana nufar sashin nasu har daɗan gudunsa,sannan suka dawo tare da Hajja tashiga motar muka tafi. Koda muka isa asibitin Emergency aka shiga dani ɗakin ƴan ɓari,wankin ciki akami sannan aka ƙara mini jini leda uku sakamakon jinin danayi asararsa kafin zuwarmu. Lokacin da likitan yake shaidawa Habib batun zubewar cikin ba ƙaramin tashin hankali ya faɗa ba,ganin kamar shima ɗin yana buƙatar kulawar likitocin yasanya Hajja ƙiran Malam Idi ta sanar dashi,ta gidan su Ummi ya biya ya sanar dasu sannan suka garzayo asibitin dukkansu. Ganin su Ummi yasa Habib saurin miƙewa ya nufesu yana faɗawa jikin Ummi kamar jira yakeyi ai kuwa nan yasaki kukan dake ƙasan maƙoshinsa. "Habib kasama kanka nutsuwa kasani ba wayonku ko kuma dabararku ne A'a Allahn daya baku shi zai ƙara baku".Daddy ya faɗa yana ɗago Habib ɗin daga jikin Ummi,sannan suka ƙarisa suka zauna. Tunda mukaje bansan waye akaina ba haka nan na daɗe dabarin cikin hayyacina tun lokacin da akamin wankin ciki,sanyin asubar da'ake busawa shiya sanyani wangale idanuna dasuka kumbura tsimtim. Robar jinin dake saƙale a hannuna na fara kai kallona gareshi,kafin nafara ƙarewa mutanen dake cikin ɗakin kallo.Yasira ce ta fara lura dana tashi ta matso kusa dani tanamini sannu,sannan Ummi ma dake kan sallaya tataso ta fara jero nata sannun sai kuma Hajja itama ta ɗaura danata. Dai-dai lokacin da Habib da Daddy suka dawo daga masallacin dasuje domin gabatar da sallan asuba,da sauri suka iso gareni Daddy yana cewa"Hajiya ta farka kenan"Ummi tace"E yanzu ta tashi". Tsuguwana Habib yayi ya zuba gwiwoyinsa a ƙasa sannan ya riƙo ɗayan hannuna saboda ɗayan har yanzu jinin bai ƙareba balle acire mini shi. "Hibba kinga wani ikon Allahn ko?munata farin-ciki sai kuma Allah ya zartar da hukuncinsa,dole mu karɓa ƙaddararmu hannu bibiyu Allah yabamu wasu masu albarka"duk ƴan ɗakin suka amsa da Amin. Nikam kallo na tsuramasa cikin mamaki meyake nufi kenan babu ciki kome?daga nan kuma ban ƙara tantance abinda yake faɗaba sai dai ganin bakinsa yana cigaba da motsawa hakan ya tabbatar maganar yacigaba dayi. Bana tausayin kaina a wannan lokacin kamar yanda nake tausayin Habib yanda ya ɗaura buri akan cikin nan daga shi har danginsa mussamman Granny. Hawaye kawai nake fiddawa yana sauƙa har izuwa saman wuyata,Ummi da Hajja keta mini nasiha zuwa ƙarfe ɗayan rana su Inna da yaya Fawas sukazo daman tun daren jiya Daddy ya sanar da Baffa tare da Sayyid sukazo danshi ya taho dasu. Ina ganin yaya Fawas hawayen dana keyi ya tsananta yunƙuruwa nayi na tashi yayin daya iso gareni shi kuka ni kuka haka nan ma Inna sai faɗin"Ya Allah ka dubi rayuwar wannan marainiyar ka haskaka matashi dan soyayyarka ga annabinka Muhammadu (S A W)"take su Ummi na amsawa da Amin. Duk yanda naso nayi magana jinayi bakina yamin nauyi nakasa furta koda kalma ɗayace kuka kawai nakeyi kozanji sanyi a sashin ruhina danakejin kamar ana watsamini garwashin wuta. Ganin irin kukan danakeyi yasanya Daddy yiwa likitan magana akamin allurar bacci,tare muka yini dasu a asibitin har Hajja bata koma gidaba malam Idi ne dai yakoma amma har Daddy nan ya wuni. Zuwa yamma kuwa Granny da Iya suka iso ganinta yasanya Habib sakin wani kukan tamkar ƙaramin yaro lallashinsa ta shigayi saidai itama kanta kasa kashe wutar tausayin jikan natan mafi soyuwa agareta acikin zuciyarta,wanda hakan ya sabbabar da fitar hawaye daga idanunta. Sai bayan isha'i sannan na farka da wani masifaffan ciwon jiki,Granny ta matso tana min sannu kaina kaɗai nake gyaɗa mata,sannan ta gabatar mini da abinci a wannan lokacin banacin koda ƙwayar shinkaface zata iya wuce daga maƙoƙaruna har ta iya zaman acikin cikina. Ganin duk sunyo kaina yasa na ɗaure daɗan zuƙa tea mai kaurin da Ummi ta haɗa mini,ina gama sha zuffa ta karyo min Ummi da daman tasa ƴan aiki su kawo ruwan zafi ta haɗa min ruwan wanka Inna tamini wankan jego kamar yanda akewa ko wacce mai jego. Sai wajajen ƙarfe goma sannan Daddy,Sayyid,Yaya Fawas,Ummi,Iya,Hajja da kuma Habib da Yasira suka tafi sai dasuka sauƙe Hajja a gida sannan suka wuce gidan Daddy hadda Habib ɗin. Granny da Inna su suka kwana a wajena,washe gari kuwa tun dana tashi naga nayi wani masifan kumburi kowa yazo sai yayi mamakin irin kumburin danayi. Likitan yace ba matsala bane kawai rashin jinina ne yayi ƙasa aka ɗaura ni akan magungunar ƙarin jini,bayan an ƙara sakamin roba biyu na jinin wanda Habib yabada ɗaya yaya Fawas ya bada ɗaya dansune jininmu yayi dai-dai danasu. Kwanana bakwai a asibitin aka sallame ni,kwananmu ɗaya a gidan Daddy muka koma gano tare da Inna da kuma yaya Fawas. Habib da Sayyid su suka kaimu nan naga ansauya fasalin gidan Baffa an zamanatar dashi Inna ke fesamin ai Habib ne ya ƙara musu gidan ya saye gidaje biyu na makwabtansu ya haɗe ya ƙara musu a nasu. Ɗakuna manya-manya guda huɗu ne akayi acikin gidan dukka suna kallon juna,sai kuwa wasu biyu da akayisu a waje kamar shaguna,dana shiga ɗakin Inna kuwa ko ɗakin wata amaryan iyakaci dan ya zuba mata sabbin gado da kujeru hadda da labulaye. Ga simintin dake malale ko'ina a tsakar gidan,duban Inna nayi cike da mamaki nace"Inna duk wannan aikin yaushe akayishi bansani ba?". "Lokacin dakika sama ciki daya ƙira Adamu ya sanar dashi,bayan kwana biyu kuwa ya turo Sayyid da masu aikin ginin aka fara ya kama mana wani gidan haya anan kusa muka koma kafin a gama"Inna ta faɗa fuskarta cike da alhinin zubewar cikin. Nima shuru nayi ban ƙara cewa komai ba,ji danayi Baffa na ƙwalamin ƙiran na fito muyi sallama dasu Habib zasu wuce,yasa na fito bayan na zige akwatin kayana da Yasira ta haɗamin na ciro maganin Habib na fito. A zaure mukayi kiciɓus da Baffa da yaya Fawas suna shigowa na matsa musu suka wuce sannan na fita,da sallama na ƙarisa inda na hangosu suna tsaye da Sayyid. "Muzamu tafi saikin ƙara warwarewa sannan nadawo na ɗaukeki dan Allah matata ki kula da kanki"cewar Habib. Ƙasa nayi da idona kana nace"In sha Allah,Allah yakiyaye hanya ga magungunanka kana sha akan lokaci"na ƙare maganar ina miƙa masa ledar maganin ya karɓa sai faman faɗin yake zaiyi missing ɗina. Na katseshi da cewa "naga yanda ka sauyawa su Inna gida,mun gode Allah ya ƙara buɗi"yace"Amin aduk yiwa kaina Baffa kamar uba yake agaremu". Nace"Hakane shine ko ka sanar dani sai yanzu nakeji a bakin Inna". Haɗe hannayensa yayi guri duga alamar neman afuwa har sai sayyid yafara yimana dariya,kafin na rakasu suka shiga motar. Wasu kuɗi ya miƙo min wanda bazan iya ƙidaye yawansu ba yace na ƙire a hannuna kafin ya ƙara zuwa,na masa godiya sannan suka tada motar har sai da suka ɓacemin daga gani kafin na koma gida ɗakin Inna na wuce nayi kwanciyata dan har izuwa wannan lokacin ban sama tsarki ba. Sai yamma lilis na farka na fito waje ganin missed call ɗin Habib yasa na shiga dialing nombarsa,katse ƙirar yayi sannan ya ƙira. Na amsa na gaisheshi tare da tambayarsa sun sauƙa lafiya,ya amsa min da E sosai mukayi hira kafin yabawa Granny wayar mukayi sallama da ita dan itama yau zata koma Damaturu. Bayan munyi sallama da Habib na fito waje nan na tarar da Inna da Yaya Fawas na jonasu muka cigaba da hirarmu,kwanana uku da dawowa gidan Baffa yaya Fawas ya koma Azare. Innace tun zuwata gidan Baffa banga koda wulgawar Hajara ba to banyi ƙarya ba,balle kuma tamin jajen abunda ya faru.Inna na tambaya ko bata nan ne?tace min tana nan kawai dai wani baƙin halin yanzu ta dasawa kanta na zama a ɗaki,yayin da Adamu shima yanzu komai za'a faɗa akanta baya gani. Dariya maganar Inna taso tabani watau Inna mafa irin uwayen miji masu tsaurin nan ne,abinda yaragewa ƙaya zaƙi shine Hajararma ba daga baya ba. Tun ranar danayi ɓari jini bai bar zuba daga jikina ba tun ina ɗaukar abin kamar wasa har ya fara bani tsoro,satina uku da kwana biyu cur a gano hakan kenan yana nuna nayi wata ɗaya da kwana uku dayin ɓarin. Inna nasamu da maganar tace min itama abin ya bata mamaki danko haihuwa nayi ya kamata ace jinin ya tsaya zuwa yanzu,dan wasu basayin arba'in ma jinin yake tsaya musu.abin dayafi sanya mini tsoro acikin raina shine yanda jinin yake zuba sosai innace sosai ina nufi sosai bana wasa ba,dan daga safe zba uwa yamma ina ƙarar da pant goma sha uku zuwa sama. Wasu jiƙe-jiƙen gargajiya Inna ta haɗamin inasha amma babu abunda ya sauya,ganin haka yasa nafara sallolina sannan na ƙira Habib na sanar dashi yace na shirya zaizo yakaini asibiti sannan indaina shan jiƙe-jiƙen itacen gargajiya. Nasanarwa Inna haka na shirya kayana na fito dasu tsakar gidan ina jiran zuwan Habib,sai ranar na ɗaura idanuna akan Hajara tana zaune ƙofar ɗakinta tana ɓarar gyaɗa wata shewa tasaka hadda da tafa hannu kamin ta aiko min da wani mummunan kallo Inna ta kalleta tace"Allah ya shirya". Kamar jira takeyi ai kuwa ta miƙa tare da faɗin"Amin Inna ai masu neman shiriyar sunada yawa cikin hadda jikartaki dakike rawar ƙafa akanta,yo waya sanima ko maganin zubda ciki tasha shiyasa jinin ya ɓalle mata za'ayi wata rufa-rufa". Inna data gama zuwa har wuya tsabar haushi ta ɗaga hannu da niyyar zagawa Hajara mari,Baffa da shigowarsa gidan kenan yayi saurin riƙe hannun Inna data ɗaga. "Inna dan Allah kiyi haƙuri ki ringa sanyawa zuciyarki salama".cewar Baffa "Ai daka barta ta maren wallahi dasai naga abunda ya turewa buzu naɗi,dan kuwa zan nuna miki nima inada gata acikin garin nan". Martanin Hajara kenan tana karkaɗa ƙudu "Hajara nagodewa Allahn dayayi ni kuma yayi Hibba,gwara ita ai tunda har tasama cikin ya zube keda tun kafin a haifo ta duniya akayi naki auren ai har rana mai kamar tayau ko ɓatan wata acikin gidan nan baki taɓayi ba,in fitsari ya zama abun banza yo kaza tayi mana"cewar Inna tana hucin ɓacin rai. Kukan mafirci Hajara tasaka tana cewa"Malama kanajinta tana min gorin haihuwa?"tana kawowa nan ta juya fuu tayi ɗakinta yayin da Baffa fa rufa mata baya yana ƙiran sunanta. Nidai sakeke na tsaya ina kallonsu sannan na shiga laushin zuciyar Inna,muna cikin haka Habib ya ƙira wayata yana cemin yafito ya iso.Inna kam cewa tayi na tafi Allah ya kiyaye danko fitowa batayi sun gaisa da Habib ɗinba haka nan har natafi Baffa bai fitoba. Nace Habib Inna da Baffa sunje gaisuwar ta'aziya awani ƙauye,sannan muka tafi inata juyayin maganar Hajara acikin raina wani bangare na zuciyata kuwa cike yake da mamakin sauyawar da Baffa yayi. Tun kafin mubar kano mukaje asibitin Malam Aminu kano bayan munyiwa likitan bayanin matsalar dake tafe damu yace mana babu wani damuwa sannan ya rubuta min wasu magunguna mukaje pharmacy muka saya muka wuce. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________________ Page 3⃣7⃣ Nan yake sanar dani cewa Maryam matar Bashir ta haihu,da haka muka isa koda mukaje ɗaki na wuce nayi kwanciyata nan kuwa baccin gajiya ya kwasheni,Habib daman yana ajiyeni ya wuce office. Sai yamma na tashi na shiga bathroom na gyara jikina sannan na ɗauro alwala na fito zuhr da Asr na haɗa nayi atare dan banyi zuhr ba. Ina iddarwa na ƙira Maryam bugu biyu ta ɗauka,muka gaisa sannan na shiga yi mata murnar ansama ƙaruwa. Inata zolayarta Maman baby boy ina gimtse ƙirar ta turo min ankon dasuka cike na sunar har photon baby boy ɗinmu sak!Dr Bashir kamar kara aka tsaga. Fitowa nayi naje sasshin Hajja inajin ƙaunar yaron har cikin raina, tana gani na ta washe baki gami da faɗin"Hajiya na leƙa ɗazu ai naga bakya kusa". Sai dana zauna kan kujerar dana gani yashe a tsakar gidan,sannan na gaisheta ta amsa da fara'arta tana tambayata ya nabaro mutan gano,nace mata lafiya kalau duk suna gaishe ku. Nan muka cigaba da hirarmu har nake sanarda ita har yanzu jini bai tsaya mini,sai data ƙire haɓa kafin tace"wohoho hajiya ai kuwa dai ki nema magani,dan irin haka ya taɓa faruwa ga ƴar yayata wacce muke uba ɗayada ita,haka itama daga yin ɓari sai datayi wata shidda cur!a cikin jini.Da aka dage da neman magani aka gano ashe mayune sukayi ajiya a mahaifarta" Gwalo idanu waje nayi ina cewa"Kai lalle tasha wahala,Allah ya shiga tsakaninmu dasu". "Amin amma kema dai ki dage da neman magani,dan irin haka ba'a zama"cewar Hajja. Sai dana numfasa kana nace"Nima abin ya soma damuna amma muje asibiti anbani wasu magunguna kuma bazaiyi a haɗa maganin asitibi dana gargajiya a lokaci guda ba". Taɓa baki Hajja tayi tace "Amin amma magunguna asibitin nan kune dai yaran zamani kuka yarda dasu,amma mukam munfi gane mu sassaƙo itace da kanmu mu haɗa abun mu". Dariya maganarta taso bani ai kuwa nasaki dariyar har da riƙe ciki,ta miƙe tana cewa cikin harshen fulatanci"Allah ya shiryeki da abun dariya bayamiki kaɗan". A wajen Hajja na wuni sai da Habib ya dawo sannan na mata sallama na tafi,bayan mungama cin abinci na nuna masa ankon.ranar duk yanda Habib yake cikin matsuwa haka muka sawa ranmu dangana dagani har shi,saboda jinin dayake zuba daga jikina har izuwa yanzu. Washe gari na leƙa makaranta course mate ɗinmu sukayita min gaje abun ya faru,dan inada jama'a sosai a makaranta duk ba banfiye sakin fuska ba,tare da addu'ar Allah ya kawo wasu masu abarka. Banɗeba na dawo dan,a ranar zamu je damaturu gobe sunar Maryam ina dawowa na shirya kayana set biyu a cikin ƴar ƙaramar jakata,na fito nayiwa Hajja sallama ta takoni har harabar gidan tana min addu'ar Allah ya kiyaye. Dai-dai wannan lokacin motar Habib ta shigo,nasa kayana sannan muka ƙarayin sallama da Hajja muka tafi,bayan mun biya ta gidan Ummi. Gab da ƙiran isha'i muka isa cikin damaturu gidan Granny muka nufa,part ɗinta muka shiga nan kuwa muka sameta tana kishingiɗe tana sauraron tafsirin karatun da akeyi a Africa TV2. Amsa sallamar damuka shigo da ita tayi tana ƙara ƙawata fuskarta da kyakykyawar murmushin gefen baki,ƙarisowa mukayi muka zauna sannan muka gaishe ta ta amsa tana cewa "kunzo sunan kenan?".Habib yace"E wallahi". "Hmm ikon Allah kenan kema wataƙil yanzu da cikinki,ya kusa wata bakwai"cewar Granny tana tashi daga kishingiɗewar datayi.Sunkuyar da kaina ƙasa nayi ba tare danace da ita komai ba.tashi tayi tasa aka kawo mana abinci mukaci sannan muka wuce part ɗinmu. Kamar dai ko yaushe yau ma babu abunda ya shiga tsakani na da Habib,washe gari kuwa muka shirya tafiya suna hadda Granny,a ƙofar gida wajen ƴan raɗin sunan dasuka fara taruwa,Habib ya zauna sai faman yiwa Bashir tsiya yakeyi. A falo muka iske Maryam ana mata kawlliya,nan na lura da shaddar dake jikinta irin wanda ke jikin Bashir ne anko sukayi,gefenta na zauna bayan na gaida taron matan dana samu a falon. Rusunawa Maryam tayi tana gaida Granny ta amsa sannan wata dattijuwar mata ta miƙowa Grannyn yaron,ankona Maryam ta tashi ta ɗauko mini wanda nace mata daman ta bayar a ɗinka min. Ɗinkin doguwar rigace sosai aka ƙawata ɗinki da stone sai sheɗi sukeyi,na shiga ɗaki na saka sannan nima mai kwalliyar taɗan shafa min hoda. Dai-dai lokacin dana fito naji maroƙa nacewa"Alhamdulillahi yaro yaci suna Abubakar,Allah ya raya sadiqu". Taɓo maryam dake kusa dani nayi nace"Sunan Abbanki aka saka kona Abban Bashir?"murmusawa tayi kana tace"sunan Abban Habib dai surikinki". Shaf na manta dasunan mahaifin Habib,Abubakar ne sai danaji ta faɗa na tina. Granny kam tun dataji bakinta ya kasa rufuwa,sai sawa Bashir Albarka takeyi ba adadi,a waje kuwa koda Bashir ya sanar da Habib cewar Sunan Abbanshi yasaka rungumeshi kawai yayi dan daɗin yaji ya tsirka masa ba kaɗan bane,a ranshi kuwa yana girmama halacci irin na Bashir tabbas duk ɗan halak baya manta alkhairi kome ƙanƙantarsa. Da yammaci kuwa aka gabatar da ƙwarya-ƙwaryar walima da akayi acikin harabar gidan,Granny kam har izuwa yanzu bakinta yaƙi rufuwa jitakeyi kamar wannan ne farkon takwaran da aka fara sanyawa mijin natan. Haka taron suna ya watse lafiya aka sanyawa yaron laƙabi ABBUL-KHAIR sunan da za'a ƙiranshi dashi. A Falon Granny muka yada zango damuka dawo,nan nake tambayar Granny alaƙarsu da Bashir dan izuwa yanzu zuciyata ta fara rayamin suna da wata alaƙa tsakaninsu mai ƙarfi bayan abokatan su da Habib Sai data saki murmushi wanda yaƙara cika fuskarta da kwarjini kana tace"Babu wata alaƙa tsakaninmu ta nisa kota kusa,Shi Bashir ɗan asalin jahar maiduguri ne almajiranta ya kawoshi cikin damaturu,lokacin tun iyayen Habib sunada rai yake zuwa bara a gidan nan da haka har mukayi sabo dashi a lokacin shekarunsa basu ɗara na Habib ba.haka dai shaƙuwa ya shiga tsakaninsa da Habib har marigayi ya sashi a makaranta bayan ya nema iznin daga malaminsu ya amince,Tun daga lokacin cinsa da shansa,makarantarsa hatta suturansa a gidan nan yakeyinsu tare sukayi sauƙar alqur'ani da Habib kuma sukacigaba da karatunsu har izuwa matakin jami'a har ya sama aikin a YSU,kuma muka cigaba da zumuncinmu dashi harma da danginsa dan auren Habib ma duk sunzo". Tunda Granny tafara warware mini wannan kundin tarihin tanamin dalla-dalla na sake baki ina binta da kallo,Iya tace"Ai Bashiru kam ba daga nan ba indai kirkine". Anan mukaci abinci sannan muka wuce part ɗinmu bayan munyi sallah,shirin kwanciya mukayi na lura da Habib dayake cikin matuƙar buƙatuwa amma babu damar yin hakan,haka muka kwanta bayan na tabbatar da yayi bacci na tashi na shiga toilet naci kuka matuƙar kuka har saida numfashina ya fara ƙoƙarin sarƙewa,alwala na ɗauro na fito na iske shi zaune akan gadon ya jingina bayansa a jikin pillow idanunsa har wani ƙanƙancewa sukayi,ya zubosu saitin ƙofar banɗakin. Saurin kai hannu nayi na share hawayen dake sauƙar har saman tudun wuyana,na wuce zan ɗauka sallaya batare dana ƙara kallon inda yake ba.Har na shimfiɗa sallayan ina faman saka hijab yamin ishara da hannunsa akan nazo. Sai dana gama saka hijabin na tako a hankali na zaune a gefensa,riƙo hannuna yayi ya gyara zamansa ta yanda yake fuskanta sosai har munajin bugun zuciyar juna. Mun ɗau tsawon wasu daƙiƙun da basasu gaza gomaba kafin yace"Meyasa kike ɗaurawa kanki damuwa akan abinda,daga ni har ke bamu da iko ko kuma damar sauya shi,KADDARA CE(Littafina mai zuwa in sha Allahu).sai muyi ƙoƙarin karɓarta aduk yanda tazo mana". Sai daya sau-sauta muryarsa tare ƙara karfin riƙon da yayiwa hannayena dasuke saƙale cikin nasa kana ya ɗaura da faɗin"Matata ban aureki dan ki kasance a cikin kukaba,ban raboki da danginki dan haka ba". Cikin kukan dayake fizgata nace"Ba yarda da ƙaddarar data same mune banyi ba illa iyaka ina tsoron karna jefaka cikin wani hali". Muzgutawa yayi yana shafo kaina kafin yace"babu abinda zai faru da yarda illahu,kedai ki tabbatar kina shan magungunanki akan ƙaƙida,sannan ai ni yanzu ba abin tausayi bane domin zuciyata tayi ƙarkon da zata iya jure koma menene shi farinciki ko akasin sa". Kwantar da kaina nayi ajikinsa lokaci guda naji duk damuwata sun kau,inajin wani farin-ciki na ratsa jini da jijiyoyin jikina. Tashi mukayi tare yashiga bathroom yayi alwala sannan,ya fito mukayi sallan tare kana muka kwanta. Washe gari muje kasuwa da Granny da Iya muka haɗu kayan takwara sosai,sannan muka wuce gidan Bashir muka kai danginsa mutan maiduguri sai sanya albarka sukeyi. Sannan muka dawo gida muka fara shirin komawa katsina saboda jarabawar da zamu fara cikin satin nan,muka tafi tare da addu'ar Granny da Iya agaremu,sai dai koda wasa ban bari Granny ta fahimce inada matsala ba,dan ina sallata tunda nayi tambaya a wajen wani malami yace mini ya halalta nayi salla,dan jinin ya zama jinin ciwo sai dai na nema magani ba haka kawai zan zauna ba, ko Ummi bata sani ba kuma banajin Habib ɗinma ya sanar musu. Sha ɗayan dare ta gota muka shigo cikin katsina,a gajiye na shigo gida na watsa ruwa sannan nabi lafiyar gado. Washe gari Habib ya sauƙe ni a makarantan,wuni nayi cur!a cikin makarantar saboda akwai test ɗin da akayi bana nan sai dana tsaya nayi clearing ɗinsu kafi na dawo gida,sai dana leƙa sashin Hajja na tarar ma batanan sannan na shiga ciki. Haka Abubuwa suka cigaba da tafiya wasa-wasa har na shanye magungunar da aka ɗorani akai,tashin hankalina yafi na baya dana zaune na lissafa nayi wata uku da ƴan kwanakin dayin wannan ɓarin amma har yanzu jini bai tsayaba. Muka ƙara komawa asibitin likitan ya shawarce mu damu gwada na gargajiya,dan yafi zaton aljanune suka haddasa mini faruwar hakan,ba'ason raina ba Habib ya sanar da Ummi dan anema min magani,sosai ta dage wajen ganin tayi hakan nasha magunguna jiƙe-jiƙe bazasu irgu ba amma babu abunda ya sauya.hatta Inna ma bata fasa aiko min dasu maganinba haka nan ma Hajja tanayi nata ƙoƙarin da kuma Anty Amina. Ko da maƙiyin mune yaga Habib sai ya zubar masa da ƙwalla saboda halin daya shiga,ga wani uban ramar dayayi har kwanciya yayi a asibiti saboda cikin mara.ganin hakan Granny tace a ɗaura aurensu da Yasira kafin ni kuma Allah ya kawo min sauƙi. Ranar nayi kuka na fitar hankali domin inason Habib so matuƙa,na ƙira Yaya Fawas na faɗa masa lallashina yayi sosai tare sa shawartata akan na cigaba da addu'a in wannan auren alkairine Allah ya tabbatar da alkhairin dake cikinsa. Satikai biyu aka sanya biki duk wani labarin bikin a wajen Sayyid nakejinsa,dan har yanzu Habib ɗin bai faɗa min komai ba,wanda zuciyata take hashasho min nauyi maganar ta masa wajen furtawa,haka nan ma Yasira konaje gidan bata yarda mu haɗu. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ___________________________________________ Page 3⃣8⃣ Ranar ina makaranta munfito daga lecture na zauna akan kujerun dake cikin makarantar,abin duniya ya isheni narasa abunda kemin daɗi acikin raina amsar dazan bawa Habib zuciyata ke shiryamin inya sameni da batun aurensa ai ko zamar dadiru mukeyi dashi sai sanar dani. Sayyid da Ummi ne kawai kemin maganar,Ummi kuwa tana taushar zuciyata ko Granny bata taɓa furtamin ba. Naji wayata na fara ruri nayi saurin tsaida hawayena,na ɗaga wayar sannan na gaida Ummi ta amsa sannan tace nazo gida tana nema na. To kawai nace mata sannan na gimtse wayar naja jakata,na tara adaidaita nahau muna isa na biyashi dai-dai lokacin da motar Habib ta iso gidan. Ko kallon inda yake banyi ba danji nayi zuciyata tana tasafa,meya ɗauke ni daga shi har danginsa?dazai kasa sanar dani batun ƙarin aurensa,da sauri nawuce cikin gidan ina maida hawayen daya ciko min idanu. Hadda gudunsa ya biyo bayana sannan yasha gabana da sauri yake maganar numfashinsa na fita da sauri-sauri hakan kuwa alamu ne dake nuni da ciwonsa zai motsa. "Hibba dan Allah ki saurare ni kafin ki shiga inason magana dake". "Kayi haƙuri Ummi na jirana aciki"ina gama faɗin haka na fara wayar ƙarya inacewa"Ummi gani nan shigowa na iso". Na raɓa ta gefensa na wuce, duk yanda zuciyata ke girmama tausayinsa matsewa nayi nayi wucewata,hakan da yayi ya ƙara tabbatar min da bai san cewa nasan maganar ƙara auren dazaiyi ba. Koda dana shiga falo Yasira kawai na iske tare da Sayyid dan shikam har ya riga da yazo domin biki,sallamata dataji yasa tayi saurin miƙewa zatabar falo. Sallamar daban ƙarisaba kuwa na haɗiye sauran a cikina saboda son furta sunan Yasira da bakina keson yi. Ai kuwa cak!ta tsayi jin muryata ta daki dodon kunneta,takuwa nayi har gabanta tayi saurin runtse idanunta tana hawaye,riƙo hannunta nayi ina faɗin"Yasira meyasa yanzu kike guduna?duk inda kikasan samu haɗu bakya zama awajen?wannan abun dagani harke harshi Hamma Habib ɗin bayin kanmu bane,haɗin Allah ne ba mai iya canza shi.Sayyid ya sanar dani tun da Granny ta yanke wannan hukunci walwalanki ta gushe kika daina kula kowa kullum cikin kuka kike koshi Habib ɗin bakyaa saurara duk wannan saboda meye Yasira?". Kamar jira take namata tambayar tayi saurin cewa"Anty wallahi duk yanda naso hana zuciyata ayyana min cewa wannan auren kamar naci amanar kine kasa hakan nakeyi,na tabbata koshi Hamman basona yakeyi ba kawai dai bayanda ya iya ne". Zaunar da ita nayi nace"Yasira hukuncin Allah ne sai mu karɓe shi hannu bibiyu,bani da shakkar furta cewa Habib yana sonki domin duk cikin ƴan-uwansa ke kikafi kusa dashi,ki kwantar da hankalinki sannan ki saki ranki har ki faɗa fushi ubangiji kiyi biyayya ga umarnin magabatanki". Kwanciya kawai tayi jikina tana kuka na ɗagota,na share mata hawayenta nace taje tayi wanka taci abinci ta kwanta ta huta ta tashi ta tafi. Da kallo nabita nan take tausayi halin datake ciki ya dira cikin birnin ƙalbina,maganar da Sayyid ya farayi shiya dawo dani daga tunanin danayi nisan ciwo acikinsa. "Lalle Hibba kin cika mace mai dattaku madalla da mace saliha mai ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya da nutsuwa". Sadda kaina ƙasa kawai nayi kafin nayi wata magana,Habib ya turo ƙofar ya shigo kallo ɗaya nayiwa fuskarsa na tabbatar dacewa yayi kuka dan yanda idanunsa su ƙanƙance fatar fuskar tayi jajir. Yanda ya shigo falon kai tsaye ya wuce ya zauna,hakan ya tabbatar min dacewa bai lura da akwai mutane a wajen ba yanda numfashinsa yake fita har wani guguu yakeyi. Sayyid yayi saurin isa gareshi yana tambayarsa lafiya,kansa kawai ya jijjiga masa alamar Babu,na ɗauko maganinsa acikin jakata na tashi na ɗauko masa ruwa dai-dai nan Ummi ta fito daga ɗakinta. A Sayyid na miƙawa maganin yabashi yasha sannan Ummi ta zauna agefensa tana masa sannu,ya daɗe idanunsa a lumshe kafin ya waresu. Tare da Sayyid suka je masallaci saboda sallan Asr da aka farayi,muma tashi mukayi mukayi sallan sannan na leƙa ɗakin Yasira naganta tana bacci,tashinta nayi nace tayi sallah tace tana hutun sallah lokacin. Na fito falo nan na tarar da Ummi a falon na zauna domin maganar da zamuyi maganar data farayi yasamin nutsuwa. "Hibba mu bamu isa mu dakatar da abinda yake rubutacce acikin littafin rayuwarmu ba,Kiyi haƙuri domin nasan raɗaɗin da kikeji a cikin ranki saboda nima ƴa macece nasan zafin kishi kiyi haƙuri ki tausa zuciyarki". Murmushi na saka takaitacce nace"Ummi wallahi bakomai bantaɓa riƙonku acikin raina akan wannan aure ba dan nima inzan yiwa kaina adalci,nasan acikin halin da Habib yake ciki yana buƙatar ƙarin aure". Sosai Ummi taji daɗin maganata sai sanbaɗo min albarka takeyi,muna haka Habbi suka shigo Ummi ta tashi Sayyid yabi bayanta nima barin falon na fara ƙoƙarinyi muryar Habib ta katseni. "Zauna inason magana dake". Na dawo na zauna a hankali nake ɗago kaina ina satar kallon fuskarsa."Nasan Ummi ta sanar dake komai har cikin raina bawai na ɓoye miki dawata manufa bane sai dai illa iyaka kawai saboda yanda nake tinanin zaki ɗauki abun,bansan meyasa suka kasa karɓan uzurina a wannan lokacinba?bansan meyasa suka kasa haƙuri harki sama lafiya ba? wasu lokutan zuciyata takance dani ƙaunar dasukemin da tausayin halin dazan iya faɗawa shiyasa su haɗa wannan auren amm...". Saurin dakatar dashi nayi ta hanyar faɗin"Habib na riga danasan komai tun kafin Ummi ta ƙirani ta sanar dani,ina muka fatan alkhairi dakai da sabuwar Amaryarka". Cikin wani irin zafin nama ya tashi ya dawo kusa dani yana cewa"Wallahi Hibba babu yanda na iyane amma dazance a dakatar da auren nan,dan ina gudun azabar dazan tarawa kaina domin bazan iya gwatanta adalci a tsakaninku ba". Da murmushi fal!akan fuskata na ɗago idanuna cikin nasa nace"Habib na fahimce komai kuma ga duk mai hangen nisa zai yabawa namijin ƙoƙarin da iyayenka,sukayi dan ganin sun cetoka daga faɗawa izuwa haram inason na roƙi wata alfarma guda ɗaya tal!a wajenka mijina". "Inajinki menene?". "Inason ka cire duk wani damuwar dake ranka,ka miƙawa Allahn daya tsara wannan auren dukkan lamuranka saboda lafiyarka tanada muhimmamci agare mu gaba ɗaya idan bakason kanka to muna sonka". Wani ajiyar zuciya ya sauƙe mai ƙarfi yana cewa"Tsarki ya tabbata ga ubangijin daya sanya mace ta gari ta zama silar samun nutsuwa,madalla dake Allah ya miki albarka". Nace"Amin bari yanzu na tashi na turo maka Yasirar?"na faɗa ina miƙewa. Da kallo ya tsareni yace"Hibba ke bakii da damuwa akan ƙarin auren dazanyi ko?". Cikin sauri nace"meka gani"saboda tambayar tasa nasha jinin jikina lokaci ɗaya yanayina ya sauya naji babu abunda nafi buƙata illa nabar falon naje nayi kuka kozanji sau-sauci acikin raina. "Naga ko irin kishin nan ke bakya nunawa". Dawowa nayi zauna nace"Kishi wani halittane dake jiki kowani mutum mace kona miji,sai dai akwai waɗanda suke jahiltan abun,Ina matuƙar kishinka sai dai hakan bazaisa na haramta maka abunda ubangiji daya halicceni nida kai ya halalta maka ba amma da inada ikon fayyace maka damuwar dake cikin raina danayi hakan kodan ka sama amsar tambayarka". Ina kawowa nan a zance na miƙe na nufi ɗakin Yasira,da mamakina na hagota saman gado sai faman rusar kuka takeyi,saurin isa gareta nayi tare da dafa kafaɗunta ina tambayarta lafiya?. "Hibba daman na gaya miki Hamma baya sona gashi yanzu da bakinsa ya furta miki kawai babu yanda zaiyi ne amma daya dakatar da auren nan". Tun data fara maganar na gano inda ta dosa kuma hakan yasa na gaskaka hashashen zuciya nacewa taji tattaunawarmu da Habib. "Yasira bafa sonkine bayayi ba kawai dai abun ne yazo masa ba tare da zato ba.Amma na tabbata babu namijin dazai kalle kyakykyawa kamarki yace wai baya sonki sai dai inbai samu ba". Murmushi ne ya kuɓuce mata ba tare da zato ba tace"kedai Anty bakya rabo da zolaya".nace"Ai gaskiya ce ba zolaya ba,bakiga duk acikin danginku da Habib kawai kike kama ba?yanzu dai ki tashi kije falo yana jiranki kar kibarmin miji ya jira". Da farko taso tamin gardama akan cewa ita babu inda zataje,da kyar ta yanda ta saka hijab ɗinta tazaje nace"A haka zakije fuskarki ko ƴar hoda babu". Kafin tayi wata maganar har na isa gaban mirror na ɗauko hoda na shafa mata,nasa maka lidgloss a leɓɓanta sannan na fesheta da turare bayan na ƙara mata da humra tasaka,sannan ta fito. Sai danaga fitarta na sauke ajiyan zuciya nan take kuma naji zuciyata tamin wani irin nauyi dana tina wajen Habib zataje zance a matsayin waɗanda suka kusa zama miji da mata. Kukan dakecin raina na saka yayin danaji jiri na nema ya kadani,kwalban turaren dake hannune ya suɓɓe ya faɗi nan kuwa ya tarwatse ya barbazu akan tiles ɗin dake malele a ɗakin. Figigi na dawo hayyacina nayi sauri saka key a ƙofar dan kar wani ma yashiga ya sameni cikin halin danake ciki,naja jikina na wuce bathroom ina riƙe da ƙirji dayake min soya. Ina shiga nafara aman jini hadda gudaji gashi baƙiƙirin dashi sosai nake aman tamkar zan amayar da hanjin cikina,ina gamawa kuwa jikina yahau karkarwa idanuna suka daina gano min komai. Guri na nema cikin bathroom ɗin na zauna,ina kukan tausayin kaina da kuma irin rayuwar ƙuncin danakeyi. Da kyar na iya miƙe akan ƙafafuna na wanke fuskata nayi alwala,na fito na share kwalbar data fashen nayi mopping ɗin wajen sannan na tada sallan magrib dake faman ƙira yanzu. Koda na iddar Addu'ar neman sausaucin halin ƙuncin danake shiga nashiga yi,ina shafa addu'ar na ɗauka wayata na ƙira Baffa bayan mun gaisa shima nasanar dashi batun ƙarin auren Habib ɗin,ya nunamin ma Hajiya Granny ta sanar shi,nace yabawa Inna wayar ai kuwa ya miƙa mata muka gaisa itama na sanar da ita. Har taso tafini firgice tace"Hibba in wani laifin kika masa ki sanar min".nace"wallahi Inna ki kwantar da hankali muna zamanmu lafiya kawai dai,Allah ne yakawo lokacin ƙarin auren kisan kana naka ne Allah na nashi". Tace "Haka ne"nan dai tata bani shawarwari wanda mafi yawansu akan yanda zan ramawa dangin Habib irin halaccin dasuka min ne,dan dana sanar da ita cewa Yasira ce matar dazai aura ɗin sai naji hankalinta yaɗan lafa. Munayin sallama na buɗe ƙofar ɗakin na fito ina duba hannuna da kwalban ya yankeni da ina tattarewa,da mamakina na tarar da Habib a falo nace"Bakaje sallah bane". Na lura dukkansu sai a wannan lokacin suka ankara da shigowata falon,ya ɗago kai ya kalleni sannan kuma ya miƙe tare da faɗin"E wallahi yanzu nakeson naje mun tsaya tattaunawa ne hankalina baikai ga lokaci har ya ƙure haka ba". Kaina kawai na jinjina na wuce kitchen na fara haɗa abincin dare,nan Yasira tazo ta sameni muka farayi tare da ita,duk yanda naso sakin fuskata kasa hakan nayi saida damuwar dake cikin raina ya bayyana akanta. "Anty gaskiya kinyi dace kekam Hamma yana sonki da yawa"cewar Yasira. Kaina yana ga yanda albasar danakeyi nace"meyasa kikace haka?".ta rufe tukunyar miyar dake gabanta kana tace"Duk maganarsa sai yasako sunanki a cikin haka ya nuna ako wani lokaci kina cikin tianinsa". Murmusawa nayi nace"kema ina miki fatan yasoki haka". Riƙe haɓa tayi tace"Anty kenan wane ni ai sai dai kawai ayi sha'ani amma batun wai Hamma yasoni ai zance ne kawai". UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _________________________________ Page 3⃣9⃣ Murmushi kawai nasaka muka cigaba da girkin,har muka gama muka jeresu a dinnig dan Ummi batason ƴan aiki akwai wacce take wanke-wanke da mopping amma girki kam Yasira ce keyinsa. Muna gamawa na wuce ɗakin Yasira tana biye dani a baya,bathroom na faɗa nayo wanka sannan na fito nace Yasira ta bani wata rigar na sauya ta ɗauko min doguwar rigar atamfa nasaka sannan nayi sallan isha'i. Tare muka fito da Yasira nan muka iske Ummi dasu Sayyid zaune a falon,kai tsaye muka wuce dinning area Ummi tace mu sauƙo da abincin ƙasa tafijin dadin ci anan.sauƙo dasu Yasira tayi na shimfiɗa mana garduma sannan mukayi serving ɗinsu. Habib dana lura dashi ba wani jin daɗin abincin yakeyiba kawai turawa yakeyi,dan fuskarsa har yanzu tana bayyanar da girman damuwar dake danƙare ƙasan ransa. Haka muka gama cin abincin muka kimtsa wajen Daddy kam daman naji Ummi nacewa yaje Maiduguri ɗaurin auren ƴar abokinsa,Habib na roƙa akan yabarni na zauna anan har izuwa lokacin da za'ayi bikin tunda yanzu saura kwana tara. Ya amince a falo suka zauna suna hirarsu banda Habib daya lumshe idanunsa yana zaune kusa da Ummi,tashi nayi nakoma ɗaki na fara karatun jarabawar dazamu fara gobe in Allah yasa muna cikin rayayyu,duk yanda na maida hankali ga karatun kasa fahimtar komai nayi kawai nasa kuka dan a yanzu duk faɗin duniya babu abunda yakeda muhimmamci agareni kuma ya kwashe kaso mafi yawa daga cikin zuciyata,kamar gidan aurena mijina sai kuma karatuna ina basu muhimmanci sosai. Share ƙwallar dake kai kawo a fuskata nayi tare da kore duk wani tinani daga cikin raina,na fuskanci abinda nake karanta,wayata dana ajiyeta a saman mirro lokacin dazan shiga wanka ta fara ruri,na miƙe na ɗaukota ganin sunan Habib yasanya na dawo na zauna sannan na ɗaga ƙiran tare yin sallama. Sallamar kawai ya amsa daga nan yayi shuru ba tare daya sake furta ko kalma ɗayaba,sai fitar numfashin juna damuke irgawa. A hankali ya furta sunana na amsa sannan ya ɗaura da cewa"Bacci nakeji amma na kasa zuciyata tamin nauyi inaji kamar bazan iyaba". Nayi saurin cewa"Karka saka komai a ranka mijina Allah yana nan kuma babu abunda ya gagari ƙarfin ikonsa a wajensa muke nema". Ajiyan numfashi ya sauƙe yace"Bacci nakeson nayi ko zanji sauƙi acikin raina amma na kasa hakan". "Ka tashi kayi alwala,sannan kazo ka kwanta"tun kafin na ƙarisa maganar naji ƙarar buɗe ƙofar bathroom dayayi,ko bai faɗa ba nasan cewa ya tashi domin yin alwalan. Sai daya kammala alwalar sannan ya kara wayar a kunnesa yace"Nayi alwalar"nace"yanzu kazo ka kwanta a gefenka na dama kayi addu'a,sannan ka kawar da tinanin komai daga cikin ranka ka kama ambaton sunan ubangijinka" Ƴar siririyar dariya yasaka lokacin dayake jan blanket yana lulluɓe rabin jikinsa dashi yace"Sai kace wani ƙaramin yaro irin wannan bayani dalla-dalla haka". Nima sai dana murmusa kana nace"Ai bakada bambamci da ƙaramin yaro a wajena". "Meyasa mata dayawa suke faɗi haka?"yayi saurin jefo min tambayar. "Mace nayiwa mijinta kallon ƙaramin yaro badan ta raina saba sai dai dan shiɗin abin riritawa kamar dai ƙaramin yaro,miji abun a nunawa sone kamar dai yaron dayake buƙatar soyayya da kulawa.yaro idan yaso abu to mafi yawan lokuta ayi masa sai a kuɓuta daga fitinarsa,to hakama miji idan yaso abu in an masa sai a zauna lafiya"nakai ƙarshen maganar ina duba fuskata cikin mirron. Wani sanyin daɗi ne yaji ya tsirka masa shuru ya biyo bayan zancena sannan yace"Kin iya shirya zance mai kama zuciyar mai sauraronki,kuma zance irin na hankali wanda akayi amfani da hankali wajen samar dashi". Godiya na masa saboda irin wannan yaɓon dana samu kana nace"yanzu dai ka kwanta sai nabaka wani labari mai,daɗi har bacci ya ɗauke ka"yace "ya kwanta". Na gyara zama na shiga bashi tatsuniyar gizo da ƙoƙi,wanda Abba ke mana da daddare ni da Yaya Fawas,a duk lokacin da Umma tafita wajen sana'arta ta barmu a gida mu kaɗai. Tun dana fara mishi tatsuniyar idanu ke fitar da ruwan hawaye,kewar Abba na ziyartar rai da ruhi na.Jin shurun da Habib yayi ya daina amsawa hakan ya tabbatar min daya sama bacci na kashe wayar ina sauƙe wata ƙatuwar ajiyan zuciya wanda ya tafiyar da kukan danakeyi. Jidanayi kamar Yasira zata shigo yasa nayi saurin tashi har ina tuntuɓe da dustbin nashiga toilet na wanke fuskata,ina fitowa na same tana saka kayan bacci tamin sai da safe sannan ta kwanta. Na jawo takarduna na cigaba da karatuna sai wajen ƙarfe sha biyu na kwanta.washe gari na tashi da wuri kasancewar muna jarabawar dazamu ƙarfe takwas,kafin na fito har Yasira ta shirya breakfast tea kawai nasha nayiwa Ummi sallama na fito Habib yakaini a mota na bashi maganinsa ya sha sannan ya sauƙe ni a school ya wuce office. Sai ƙarfe goma muka fito nahau adai-daita na dawo gida ko jiran Habib ban tsaya yiba dan Ummi ta ƙirani Granny har ta iso,haka nan naji na nema nutsuwata da walwalata na rasa,zip ɗin jakata na zuge nacirowa mai adai-daitar kuɗinsa sannan na shiga cikin gidan. Gidana na fara zuwa na ɗebo kayana sannan nayiwa Hajja bayanin ƙarin auren Habib ɗin,ta cika da mamaki nidai haka naja akwatina na taho na barta na wuce gidan Ummi. Falon Ummi na shiga na tarar da Granny ta tisa Yasira a gaba,sai faɗa take mata akan tabi mijinta sau da ƙafa da zarar an ɗaura auren,kar ta tsaya ganina a matsayin wani abun har hakan ya hanata nunawa mijinta soyayyarta gareshi,hannuna yana kan handle ɗin ƙofar amma maganganun Granny dasuke tashi daga cikin falon ya hanashi tura ƙofar nashiga. Jida nayi an dafa allon kafaɗuna yasani nayi saurin juyowa ganin Ummi,yasa nafara saurin share hawayen fuskata da gefen mayafina. "Mun shiga"ta faɗa tana jan hannuna ta gaban Granny muka ratsa zamu shige ɗaki bayan na gaisheta ta amsa fuskarta ba yabo ba fallasa. Ɗakin Ummi muka wuce tace min anan zan zauna ba'a ɗakin Yasira ba,sannan ta shiga bani haƙurin akan maganganun Granny na nuna mata ni banma ji abunda suke tattaunawa ba. Rage kayan jikin nayi na shiga toilet na haɗa ruwa nayi wanka na fito,kukan dayake shirin fito mini naketa ƙoƙoarin dannewa,domin yanzu na farga na gane kuka bazai min maganin ciwon dake cikin ƙalbina ba.sai dai zai sausauta min wani daga cikin bangaren ƙuncin danake ciki. Domin kuka ba rauni bane wani yare ne na zuciya wanda baki,yayi kaɗan wajen furtashi ko kuma fasalta shi. Kaɗan-kaɗan na shafa mai a jikina nasa kayana nayi sallah,Ummi da tun fitowa take zaune saman gadonta tace nazo na tashi na zaune gefen ƙafarta a ƙasa. Sai data numfasa kana tace"Allah yasani har cikin ƙololuwar raina banason,wannan haɗin auren kawai dai Hajiya ce ta kafe akan hakan amma bazan jure ana miki cin mutumci akan idona saboda wannan ƙaddarar ta faɗa miki ba,wallahi bazan iya ba domin ko ba komai nima uwace kuma na haifa inke ƴatace bazanso ba". Tabbas inhar za'a bani alƙalami da tawada na rubutu jerin masoyana a rayuwar duniya,Ummi na daga cikin mutane mafi soyuwa a rayuwata.ƙarayin ƙasa nayi da kaina nace"Ummi idan Allah ya ƙaddatar akwai zama,a tsakaninsu babu yanda zamu iya nidai addu'ata Allah yasa wannan auren ya zamto silar samuwar farin- cikin Habib". "Hakane amma kema ya zama dole in dage da gyaraki har Allah ya kawo mana sauƙi,dan bazaki zauna ba haka ba". Kukan danake hana fitowarsu sune suka fito da matuƙar sauti har sai da Ummi ta razana nace"Ummi munyi maganin nan ba sau ɗaya ba,ba sau biyu ba munyi na asibiti munyi na gargajiya amma har yanzu bamu dace ba,wataƙil wannan shine ƙaddarata a rayuwa saimu zubawa sarautar Allah ido munga yanda zaiyi dani kuma". Kamo hannuna tayi sannan ta nunamin kusa da ita tace nadawo na zauna,na tashi na zauna akan gadon tana lallashina tare damin alƙawari bazata zura ido a wulaƙantani ba. Maganganun Granny suka dawo kunnuwa tamkar dirar mikiyi,na rutse idanuna kukan danakeyi yana tsananta a lokaci guda. Ummi tace nashiga toilet na wanke fuskata na tashi na shiga,nayi kamar yanda ta umarceni dana fito na tarar da ita tare da Yasira. "Naji duk tattaunawarku da Granny,bazan hanaki nunawa mijinki soyayya ba kamar yanda ta faɗa miki sai dai bazan laminci wulaƙanci ko kuma cin fuska ga Hibba ba,wallahi duk randa naji to kiyi kuka da kanki dan in ranki yayi dubu sai nabi su,one by one na ɓata su kuma gyaran jikin ma tare za'a muku". Tana kawowa nan a maganarta ta miƙe ta fice daga ɗakin,nima ƙafata danajisu sun min nauyi na jasu na wuce kan gadon Ummi zan kwanta,muryar Yasira dana tsinkayo ya dakatar dani daga hakan. "Hibba Wallahi duk maganganun Granny kawai na amsa mata ne amma babu wanda nakeda ƙudurin aikata shi a aikace,na mata uzuri domin tsabar son farin-cikin Hamma shiyake sata makancewa a wasu lokutan dan Allah ki fahimtar da Ummi". Ta kai ƙarshen maganar tare da takuwa ta riƙo hannuna,a sanyaye nace"Naji zan mata"na zare hannuna daga cikin nata sannan na kwanta. Koda Habib ya dawo Ummi tace masa yayi magana dani akan lefen daza'aje haɗawa gobe,inda abunda nake buƙata nima sai na faɗa ya amsa mata da to. Sai yamma lilis na farka a gurguje na faɗa toilet naje canza audugar matan dake jikina sannan nayo alwala,na fita nayi sallan Asr naɗan taɓa karatu kafin Sayyid ya shigo yace Hamma na ƙira na a falo. Ko cire hijabin danayi sallan banyi ba nabi bayansa muka fito falon,zama nayi yayin da shikuma ya fita.Habib ya sanar dani lefen daza'aje haɗawa gobe. "Gaskiya lefe zamu haɗa na bugawa a jarida,sake mana bakin aljihu zakayi"na faɗa ina ƙirƙiro murmushin ina yaɓawa a fuskata. Murmushi yasaka sai da hakwaransa suka bayyana da kuwa kyawawan wushiryar dake tsakanin hakwaran,kana yace"koma menene dai bazai kai naki ba"nayi saurin cewa"A'a kam harma zaifi dan ai yanzu samunka dana da ba ɗaya bane komai za'ayi shi a wadace". "To shikenan kema ki rubuta naki" Nace"nikam nahutar dakai aƙarawa amarya". Tsura min ido yayi har sai dana zargi kaina kona faɗa wani abunda,bai kamata na faɗa bane cikin kalamai na?maganar daya farayi tasa nadawo daga tinanin"Kije dai ki rubuta min duk abinda kike buƙata,daga naira ɗaya har abunda yake naira millayan goma zan miki shi".magana na fara ƙoƙarin yin ya ɗaga min hannun sa alamar bayason jin komai. Sai dana tashi daga kan kujerar danake na matso gabansa na durƙushe kan gwiyoyina ina cewa"Mun gode Allah yasaka da alkhairi Allah ya ƙara buɗi,Allah yabaka ikon yi mana adalci,Allah yasa mu zame maka mataye na gari sanyi idaniya agareka". Tunda na fara maganar yake amsawa da Amin har nakai Aya,ya taso ya rungumeni yana samin albarka,nayi saurin raba jikina danashi har wani ya ganmu na fice a falo da sauri na inacewa"Bari na ɗauko maka maganin ka".tun kafin yace wani abu har nakai ga barin falon. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam __________________________________ Page 4⃣0⃣ Ji nayi an jawoni da ƙarfi har ina neman faɗuwa,na juyo da sauri zan saki ihu Ummi ta toshe min bakina sannan taja hannu na mukayi ɗakinta,kan gado ta cillani sannan ta maida ƙofar ɗakin ta rufeta. Sai data zauna gefen kafin tace"Karki sake kice bazaki karɓa kayan nan ba,ki zauna ki rubuta duk abunda kike buƙata ki kaisama kinji ko?". Na gyaɗa mata kaina alamar naji sannan tace inje inkai masa maganin,na ɗauka nafita na bashi yasha tare mu kaci abinci dan ɗazu ba wani cin na ƙirki yayi ba sannan na dawo ɗaki nacigaba da karatuna. Daren Ranar Daddy ya dawo duk muna falo muna masa sannu da zuwa,suna ƙara tattauna maganar biki shida Granny,Ummi kam yatsina fuska tayi kamar batajin abunda suke faɗin. Washe gari kuwa ina gama zana jarabawata na dawo gida,Ummi ta tsareni da tambayar cewa ina takardar abubuwan danake buƙata datace na rubutosu tun a daren jiya?nace mata ban rubutaba. Na miƙo min wani farar takarda tace in Habib ya tambaye na basa,bata jira mezance ba tayi wucewar kitchen domin haɗawa Daddy tea. Buɗe takardan nayi ina karato abubuwan dasuke rubuce da manyan harrufa,ajikin takardan ɗaya bayan ɗaya.wannan list ɗin zai haura milliyan Biyar da ɗoriya,na maida takardar na rufe ina girmama irin ƙaunar da Ummi kemin a cikin raina. Da yamma kuwa Habib ya ƙirani yace nabawa Sayyid list ɗin abubuwan danake buƙata,na ɗaukar takardar nabawa Sayyid yakai masa. Bayan isha'i kuwa Ummi ta kaiwo Yasira tace tayi ƙirana an kawo kayan,na fito tun kafin na ƙariso wasu akwatun masu launin ruwan zuma suka ɗauki hankalina. Muna fara bubbuɗe kayan Ummi tace mai ruwan zuman shine nawa,mai launin ruwan hoda kuwa shine na Yasira.yawan akwatunan mu ɗaya da ita kuwa nashi bakwai-bakwai sai dai kayan ciki nata yaso yafi nawa yawa amma tsadarsu ma ɗaya. Nayi godiya na koma ɗaki Yasira kam daman tana ƙirana ta wuce ɗakinta,dan bai kyautu ta tsaya a wajen ba. Haka abubuwa suka cigaba da gudana gyaran jikina tare Ummi tasa ake mana da Yasira,duk yanda aka tsumata nima haka haka sha'anin biki ya kankama lokacin sauran mu kwana biyar mu gama jarabawa,kwana uku kuwa suka rage ɗaurin auren duk waɗanda muke shiri dasu a makaranta na bawa Lima IV ta raba musu. Ummi ta saya anko tace nasu Inna ne insun zo,ai kuwa nabada aka ɗinku mata duk da bawani taro za'ayi abikin ba dangine kawai amma gidan ya cika maƙil!ta ko'ina ka wulga mutane ne,ana gobe ɗaurin auren na dawo daga makaranta nasamo Inna tazo Baffa da Yaya Fawas kuwa ɗaurin aure zasuzo. Ƴan-uwan mahaifiyar Habib ma sunzo kodana nunawa Inna kayan faɗan kishiyar da akamin,ta yaba kyan kayan sosai. Ranar ɗaurin aure kuwa da asuba Daddy ya taramu ya mana nasiha sosai,ƙarfe goman safe za'a ɗaura auren har ƙarfe tara da wasu mintina ina kwance a uwar ɗakar Ummi. Zazzaɓi na neman rufeni jikina sai karkawa yakeyi daren jiya sam!na kasa runtsawa sai dana keɓe kaina a cikin banɗaki naci kuka sosai inna tari har da jini.bayan nasihar da Daddy ya mana na wuco ɗakin Ummi nayi kwanciyata. A haka Ummi tasamoni ta bani magani nasha,sannan ta haɗa min ruwan wanka nayi na shirya tace inje in dubo Habib dan har yanzu shima bai fitoba.mayafina kalan atamfar danasaka na ɗaura a kafaɗata na fito na nufi part ɗin Habib. Tun daga falo nake rabka sallama,jin shuru yasa na kutsa kai izuwa bedroom ɗin na sameshi yana kwance abunsa. Da mamakina na ƙarisa gareshi ina yaye bargon daya lulluɓa dashi nace"Haba!Ango ya haka anacan mutane duk sun haɗu kai kuma kana nan,ko shiryawa bakayi ba". Siririn tsaki ya saka yana dafe goshinsa yace"wallahi banajin daɗine,na rasa meka damuna". Har nakai ƙofar bathroom na haɗa masa ruwan wanka,sannan na ɗauko masa towel na basa ya shiga wankan,na gyare ɗakin tsaf!sannan na buɗe waduruf na ciro masa wasu sabbin kayan dana gansu a sama-sama nake kyautata zaton sune wanda zaisa. Ina ajiye kayan akan gado ƙira yana shigowa wayarsa lokaci guda yana fitowa daga toilet ɗin,ganin Bashir ne ke ƙirar wayarsa yasa nayi saurin isa gareshi na fara dumping ɗin ruwan jikinsa,na murza masa mai sannan ya zara kayansa. Na fereshi da turare sannan na riƙo hannunsa muka fito,part ɗin Ummi muka wuce,anan falon muka iske Granny muka rusuna muka gaisheta ta amsa tare da cigaba da cewa"Su Hibba uwar gida,watau shine tun dana sako ƙafata cikin gidanan,ko zuwa gaisheni bakyayi balle kuma kizo muyi hira,saboda kin ƙullace a ranki akan na dage sai mijinki ya ƙara aure ko". Habib yayi saurin cewa"Haba!Granny dan Allah ki daina wannan maganganun a gaban mutane". "To ubana"tana faɗa tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.dai-dai nan aka fito da Amarya Yasira ta shiryo tsaf cikin wani haɗanɗen leshi sai walƙi yakeyi,ƙannen Ummi suke riƙe da ita. Tashi nayi na kamo hannunta muka ƙariso cikin falon,nan kuwa mai carema ya fara ɗaukar mu bayan mun jera da Habib ɗin. Ana gamawa Habib ya fita wajen ɗaurin auren,zama nayi ina tinano maganar Granny,dangin miji kenan komai son dasuke maka wataran sai sun nuna maka kai ba kowa bane,bansan sanda na fara hawaye ba sai jinayi Maryam Matar Bashir dako lura da cewa tana cikin falon,ban yi ba ta riƙo hannuna,saurin kawar da hawayen nayi tamin raɗa a kunnena akan bai kamata nayi kuka cikin taro ba. Sai wasu su ɗauka baƙin-ciki nakeyi da auren,jan hannunta nayi nahau janta da ƙarfi har Abbul-khair yana neman faɗuwa daga hannunta muka nufa ɗakin Ummi. Muna shiga maryam ta maida ƙofar ta rufe har sai tayi ƙara,gauuu kakeji na zube akan gadon Ummi ina sakin kuka kusa ni Maryam ta zauna bayan ta kwantar da Abbul-khair tafara lallashina. "Hibba kiyi haƙuri Granny girma yanzu yafara zuwar mata,dole ana mata uzuri domin wasu tsuffin kamar yara sukan koma insukazo irin shekarunta,ki daina wannan kukan karma wani ya shigo ya ganki haka dan Allah"takai ƙarshen magana tana tallafo fuskana na tashi na zauna. Tashi nayi batare danace ko kanzil ba,danji nayi bakina gabaɗaya yamin wani irin nauyi,ajiyen zuciya kawai nake sauƙewa ɗaya nabin ɗaya,ganin haka yasa Maryam ta miƙe ta ɗauko min ruwa a fridge nasha ai kuwa na ƙara sakin kukan dayake fitowa kai tsaye daga ƙasan zuciyata ina cewa. "Maryam wani laifi na aikatawa ubangiji daya hanani farin-ciki a cikin rayuwa,tun daga yarintata har izuwa yanzu nayi tinanin aurena da Habib zai zamto makullin dazanyi amfani dashi wajen buɗe ƙofar farin-ciki a rayuwata ashe ba haka bane.ƙalubale cikinsa yafi komai yawa dai-dai da rana ɗaya ban taɓa samun nutsuwa acikin raina ba,kullum cikin tashin hankali da fargaba abun dazai faru nake, jarabawa kala-kala daga wannan sai wancan tun da aka tsaida maganar auren nan Granny ta canza min komai zan mata bana mata gwaninta.Ummi ce kawai ke fahimtata wallahi akwai damuwa sosai acikin wannan ƙirjin nawa amma banida wanda zan iya zama dashi na buɗe masa sirrikana,sai dai na shiga banɗaki nayi kuka yanzu har aman jini nakeyi,na tabbatar da za'a gwada ni to za'a gano ina ɗauke da ciwon zuciya,wani irin baƙin ƙaddara ne ke bibiyar rayuwata wallahi ina cikin matsala" Damƙe hannuna cikin nata Maryam tayi tace"Hibba kowani rayuwar aure akwai nasa ƙalubalen,sannan kowacce mace haƙuri takeyi a gidan aurenta ki godiyawa Allah daya miki ni'imar aure yasanyaki cikin bayinsa dasuka rayu ƙarƙashin inuwar aure mata nawa suka rasu ba tare dasunyi aure ba?mata nawa suka rasa ci da sha a gidan aurensu kuma suka cigaba da zaman auren?,Mata nawa suka rayu har suka koma ga mahaliccinsu basuyi aurenba?,Mata nawa suka rasa rayukansu saboda rashin lafiya?.Ke Allah ya azurta ki da lafiya,imani,kuma yayo ki musulma mai imani ya azurtaki da mijin dayake ganin darajarki gami da girmama alaƙar dake tsakaninku ki godewa Allah akan wannan ni'imar". Kukan danakeyi kawai na tsagaita sosai maganganun Maryam suka ratsani inajin wani sabon imani yana bin zuciya da ruhina,ruwan data kawomin naƙara sha sannan na tashi na shiga toilet na wanke fuskana sannan na Maryam ta gyara min kwalliyan fuskana. Muka fito sosai na saki raina duk abunda yake raina na damuwa dannesa nayi,nayita walwalata mukaita ɗaukar photo da Habib da Amaryarsa da kuma sauran dangi,sannan na fito wajen su Yaya Fawas da Baffa suka ƙarayi yimin nasiha sosai. Da yamma kusa jama'a sun fara raguwa,ina zaune a ɗakin da aka sauƙesu Inna ina cire kayana zan shiga wanka Yasira ta shigo Inna tace"Amarya "ƴar dariya Yasira tayi kana ta zauna kusa da Inna kafin tace"Amarya a ina kuwa Inna ai sai dai ayi sha'ani kawai". Ta dafa kafaɗarta nidai towel na zara na shiga wanka ta,har na fito na iske Inna tana tayiwa Yasira nasiha,Abbul-khair dake wance akan cinyar Inna na ɗauka na fara jijjigashi ya tashi kuma Maryam ta fita. A cinyata na ajiyeshi nashafa mai,sannan nasaka rigar atamfa ta nafito daga ɗakin na barsu ɗakin Ummi na zauna na tarar dasu tare da dangin mahaifiyar Habib. Ina zama Habib ya shigo suka gaisa da mutanen wajen,idona yakai kan wata matashiyar budurwa danaji an ambace sunanta da Batul naga sai wani shishshigewa Habib takeyi. "Hamma bakason zumunci wallahi yaushe rabon daka taku ƙasarmu" Ƴar dariya kawai yayi dan bai cika son shiga cikin taron mataba,kuma baya sakewa a cikinsu.koda ya gaji da suturunta hannuna yaja muka fita daga ɗakin muka wuce part ɗinsa,muna shiga falo ya zara babban rigarsa tare da sakin wata siririyar tsaki na dube shi lokacin danake gyara kwanciyar Abbul-khair a kafaɗata nace"Mijina wacece wannan batul ɗin ban wayeta ba?". "Ƴar goggo Suwaiba ce ƙanwar mahaifiyata,wai ahakan su kuke suka hada mu aure tun kafin na aureki ". Murmusawa nayi ina ƴar harararsa nace"Ai kuwa mun rufe ƙofa makullin ma muje fashi rijiya". Dariya mukayi dukkaninmu sannan mukayi ƴar hira,sai wajen ƙarfe tara sannan mukayi sallama ya taroni har ƙofar part ɗin Ummi. Washe gari akayi ƴar ƙwarya-ƙwayar walima wanda nina haɗa shi,ƙarfe biyu aka tashi da yamma kuwa Inna dasu Yaya Fawas suka koma na ɗeba mata zannuwa kala biyar acikin kayan da aka min,sannan Ummi ta basu savouiners ɗin bikin. Nida Sayyid mukayi sickers da kuma memo wanda yake ɗauke da hutonan mu,mu dukka uku Habib na tsakiyar mu,kallo ɗaya zakayiwa photon ka ganu irin kamar dake tsakanin Habib da Yasira,dan ko Sayyid dasuke uwa ɗaya uba ɗaya dashi basuyi kama haka ba. Dukkansu fararene nice baƙar fata a tsakaninsu,Maryam keta tsokala na wai duk nafisu kyau. Da daddare kuwa Daddy da Granny suka ƙara yimana nasiha,sannan na riƙo hannun Yasira wacce tayi shigar laffaya muka shiga mota,daga ni sai ita sai Habib dukka muna baya driver najan motar. Part ɗin dake kallon nawa aciki aka yiwa Yasira jere,ina riƙe da hannunta muka shiga part ɗin nace ta shiga da ƙafan dama tayi yanda na umarce ta kuwa nakaita har cikin bedroom na damƙata a hannun angonta. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 4⃣1⃣ Shurune ya karaɗe ɗaki nakawar dashi ta hanyar fara faɗin"Allah mun gode maka daka nuna mana wannnan ranar acikin rayuwarmu,bazan daina gode maka ba Allah daka bawa mijina matace ta gari tazama mallaki a gareshi,kuma mafi kusa dashi daga cikin ƴan-uwansa.Allah ka haɗa kanmu muzamo masa mataye nagari wanda zaiyi alfahari damu". Habib yace"Amin"a sanyaye kana Yasira ma ta faɗa. Ganin duk annurin fuskar Habib ta gushe lokaci guda yasa nace"To ango mijin amarya saura kuɗin sayan baki". "Baza'a yafe min ba?" Nasaki dariya nace"ina ka taɓa ganin an yafe kuɗin sayan bakin amarya,kawai ka biya don amaryarmu mai tsadace" "To nawane?"furcin Habib sai dana ɗaga kaina kamar mai tinanin wani abun kafin nace"duk kuɗin dake jikinka ayanzu shi zaka bayar shine farashi,ba a ƙidaye ba balle kace anmaka tsada". Yayi murmushi sannan ya ciro ɗaurin ƴan dubu ɗai-ɗai daga aljihunsa,guda uku ya miƙo min na karɓa ina miƙe tare da musu sai da safe. Habib ya kallo Yasira wacce fuskarta ke lulluɓe yace"bari na rakata".kafin tace wani abun har kai ƙofar ɗakin ya biyoni a baya. A falo muka tsaya inacewa nidai ya koma zan tafi abuna ni ɗaya,yaƙi haka ya rakoni part ɗina har cikin bedroom hannuna yaja muka shiga banɗaki nayo alwala sannan na kwanta ya rufa mini blanket,yamin addu'a ya toni dashi. Sai da safe mukayiwa juna sannan ya miƙe zai kashe min wutar ɗakin,har kai ƙofar ya jiyo tare da faɗin"ki rufe idanunki dan banason kiga fitana". Na ɗaga masa kaina alamar naji,sannan na rufe idanuna kamar yandaya umarce ni ya fita daga ɗakin wani kuka mara control ne suka suɓɓuce min tun inayi daga kwance har na miƙe na zauna na jingina bayana ajikin gadon. Jinayi wani ƙululun baƙinciki ya ziyarce dana tina wai yau Habib ne zai kwana da wata maccen a shimfiɗa ɗaya,abun danafi so da ƙauna acikin rayuwata na sadaukar danawa farin-cikin saboda ɗaurewar nasa.na rasa nutsuwar zuci na duk dan na raya murmushin dake saman fuskarsa. Sautin kukan dana keyi ne ya ƙaru sosai duk ɗakin ya ɗauka,nasoma ajiyan zuciya ɗaya nabin ɗaya. Ban iya runtsawa ba tsawon daren wannan ranar,wanda a tarihin rayuwata wannan daren yana ɗaya daga cikin darare huɗu dabazan mance dasu ba,na ɗaya dare aurin aurena da Habib na biyu daren da ya kwana da fushina acikin ransa lokacin da Granny ta ganu irin zaman damukeyi,na uku daren ranar danayi ɓari,sai kuma wannan daren danajin tamkar ƙarshen farin-cikin dazanyi kenan a iya sauran kwanakin dasuka ragemin a duniya. Ƙiran assalatun farko kuwa kamar acikin kunnuwana limamin ya ƙira,dan idona kar!lokacin na miƙe nayi alwala sannan nayi sallatul fajr nakuma sallan asubahin.na daɗe akan sallayan ina karatu duk wasu addu'o'in neman sauƙi dana iya. Sai wajen ƙarfe shida nabar ɗaki na wuce kitchen nafara haɗa breakfast,na soya irish potatoe da egg sannan na haɗa tea najeresu akan dinning,sanda na gama har bakwai ta wuce na shiga bathroom da sauri nayi wanka sannan na shirya saboda jarabawar da zamuyi ƙarfe tara na dawo falon. Ganin su Habib basu fitoba yasa nafara karatun exam ɗin danake dashi,har takwas tayi da wasu mintuna kafin na rufe handout ɗin danake karantawan. Na sauƙe wata ƙatuwar ajiyen zuciya ina tsaida kallon akan agogon bangon dake maƙale jikin wall ɗin falon,har na ɗaga wayata zan ƙira Habib sai kuma na fasa na wuce nayi nawa breakfast ɗin sannan na saka hijab ɗina na fito. A cikin harabar gidan na hango Habib da Yasira suna nufo nawa part ɗin,suna tafe suna nishaɗi fuskokinsu ɗauke da annashuwa,take zuciyata ta tayo min cewa sun more daren amarcin su,nayi saurin kawar da wannan tinanin na isa garesu kafin su iso na gaishe da Habib ɗin ya amsa,sannan Yasira ta gaidani a taƙaice na amsa datare da ƙarawa da "an tashi lafiya abincinku nakan dinning nizan tafi school". "Subhanallahi!na manta gaba ɗaya da jarabawar da zaki zana yau,dana fito tun ɗazu na kaiki ai"cewar Habib fuska cike da damuna nace"ba komai malam Habu zai kaini". Ban jira amsar dazai maido min da itaba,nayo saurin barin wajen ina amsawa Yasira Allah ya bada sa'a datamin da Amin. Habib ya ƙira malam Habu yace ya kaini makaranta ya amsa a ladabce,duk dana kusa makara sai dana leƙa sashin Hajja sannan muka wuce,har muka isa ina karatuna. Ƙarfe sha biyu muka fito lokacin sosai rana ta kwalle,mai buso zafinta ina tsaye ina ƙoƙarin dannawa Malam Habu ƙira na hango shigowar motar Habib,hakan yasani gimtse ƙirar. Ya faka motar na shiga sannan muka wuce,tun muka fara tafiyar bance ko kanzil ba har muka isa gida part ɗina na wuce na sakewa kaina ruwa sannan nayi sallah,na fito na shiga part ɗin Yasira saboda naga alama masu ganin ɗakin amarya sunzo. Muka gaigaisa dasu wanda mafi yawansu dangin Ummi ne,Batul na lura wacce tun shigowana falon take bina da kallo tana tseduntawa wasu ƴan mata biyu dasuke zaune kusanta cewa nice matar Hamman.Ɗayar tace"kai!Gaskiya masha Allah gata kyakykyawa da ita ga kuma kyawun hali dan naji anacewa komai na bikin da ita akeyi,bata nuna wani kishi ba".Ɗayar ta kuma cewa"Ai wallahi nikam ma burgeni tayi,kuma fa ba babba bace dan ance Adda Yasiran ma ta girmeta".Batul kam taɓe baki kawai tayi tana sauraronsu daga bisa naga ta ciro wayarsa daga cikin jakar tana latsawa. Wani sanyin daɗi ya sauƙa min dai-dai ƙalbina,saboda maganganun ƴanmatan sunmin daɗi dai-dai shigowar Maryam falo na sakar maka lausasar murmushi tare da miƙewa na isa gare na karɓa Abbul-khair. Sannan naja hannunta muka zauna muna gaisawa,Ina tambayarta yaushe zasu tafi tace min gobe. Har yamma Maryam ta wuni tare dani kafin muka wuce part ɗina,zatayi sallah. "Kai!ƙawata gaskiya kin burge mutane da yawa a auren nan,jiya bayan tafiyarku bakiji ba yanda aketa yabonki ba.Gaskiya kinyi namijin ƙoƙari yo nikam ai randa akace Bashir zai ƙara aure ai sai dai a tarar da gawarta wallahi dan zuciyata bazata jureba". Maganganun Maryam kenan danajisu a tsakiyar kaina,lokacin danake buɗe wardrope domin ɗauko mata hijabin dazatayi sallah.takuwa nayi na iso gareta ina ƙara ƙawata fuskana da murmushin danakejin ciwonsa a zuciyata ba tare danasan dalili ba sai dana miƙa mata hijab ɗin nace"Maryam ai zaman aure sai da siyasa da kuma dabara,koni kaina inace banajin kishi acikin raina to nayi ƙarya amma farin-cikin Habib ya fiyemin duniya da abunda ke cikinta.domin shine mutum na farko daya fara nunamin cewa nima mutumce mai ƴanci,shine mutum na farko daya ƙawata min rayuwata da babu abun dana saba dashi face baƙin-ciki,ƙunci da wahalar rayuwa ya sadaukar danashi farin-cikin akan nawa.ya zauna dani ina da lafiya har yanzu danake cikin halin jinya bai canza min ba balle ya jugeni". "Hmm to Allah yasa ya ɗaure ahaka,dan kinsa wasu mazan da zarar sunyi amarya duk wulaƙancin duniya sai su nema juyeshi akanki". Sai dana gyarawa Abbul-khair kwanciyarsa kafin nace"Maryam ai amarya kona buzuzune sai anyi mararinta,kuma komai lokaci ne wataran zai wuce matuƙar akayi haƙuri". "Hakane kuma"ta faɗa tana ƙoƙarin tada kabbara,nima na tashi nayo alwala sannan na tada tawa sallan,ina iddarwa sallamar Batul yana sauƙa a dodon kunne na kulolin abinci suka ajiye wanda aka aiko daga gidan Ummi zasu tafi nace"wannan abincin ai yayi yawa ku maida sauran kula ɗaya ma ta isa". Batul ta juya tare da faɗin"aw ai daman mun zata akwai ƴan-uwanki ne shiyasa aka aka kawo muku har haka".tana kawowa nan a maganarta ta kwashe kulolin biyun ta juya ta fita. Da kallo nabita har ta fice daga ɗakin,yayin data buga ƙofar harsai datayi wata ƴar ƙara wanda hakan yasa Abbul-khair firgita daga baccin dayakeyi yana tsala ihu,Maryam ta ɗauke shi tana jijjigashi har ya koma ta kwanta dashi. Maganganun Batul sai najisu kamar ba'a take min,ƴan-uwa kam nima kaina nasan bandasu wanda har zasu damu da lamaruna balle kuma sha'anin rayuwata,Inna ce kawai sai rabin ɓarin jikina Yaya Fawas.wata ƙatuwar ajiyan zuciya nasauƙe zuciyata na rayamin cewa yanzu kowa a danginsu yasan Labarin rayuwata kenan?,wataƙil har yanda na baro gida saboda auren Nazifi duk sun sani,wata zuciyar tace min tayaya ma bazasu sani ba tunda har ƙaramar yarinyar nan Batul tasani ai kuwa ma yasani. Nayi saurin kawar da hawayen daya taru acikin ƙuryan idona nacewa Maryam ta sauƙo muci abincin,na zuba mana mukaci tare muna gama ƴan makarantar su Lima Auwal dasu ƴan department ɗimu sukazo suna mim Allah sanya alkhairi dasuka tashi tafiya nabasu savouirners ɗin nayi. Maryam kam sai datayi sallan magrib sannan Habib sukazo tare da Bashir ya ɗauketa suka tafi.part ɗin Yasira ma babu kowa duk sun watse dan Granny taja musu kunne akan karda wanda ya kwana abar Amarya ta sake da Angonta. Part ɗina na koma nayi sallah nayi wanka sannan na fara katarun jabarawar dazamu ƙarƙare gobe da yarda mai duka.na daɗe inayi kafin nayi shirin kwanciya naso zuwa part ɗin Yasira amma dana duba lokaci naga har sha ɗaya tayi yasa nayi kwanciyata. Naje zan rufe ƙofar ɗakin, jiri na ɗibata yana nema dokani da ƙasa tabbas banida lafiya kuma na ƙudurce ziyarta likita gobe,na farajin ana turo ƙofar nayi saurin matsawa ina ƙara ware idona akan ƙofar dan bana tsammanin kowa yanzu. Habib ne tsaye a ƙofar ya shigo ciki,nakai hannu na nasha hawayen fuskata wanda suka fara zuba ba tare da sanina ba nace"Lafiya naganka anan?". Ya raɓa tagefe na ya shigo ya riƙo hannuna yace"meyasaki hawaye?"na ƙirƙiro murmushi nace"Abune ya faɗa min a ido,sai kuma baccin danaji wanda shiya haifar min da hawayen,duk amma ba wannan ba kai daya kamata ka kasance da Amaryar ka meya fito dakai?". Ƙara riƙon dayayiwa hannuna yayi yace"zuciyata ta kasa samun nutsuwa jinake inhar ban ganki ba bazan kwana lafiyaba"nayi saurin katseshi nace"Habib banason ka kasance cikin irin mazajen suke karayin adalci a tsakanin matayensu,Yasirama matarkace kuma tana buƙatarka a halin yanzu kaje ka sauƙe hakkinta dake wuyanka".nakai ƙarshen maganar ina zare hannuna daga cikin nasa. Magana ya somayi na hanashi wannan damar nace"koma menene gobe zamuyi maganar,gobe zamugama exams kuma inson naje asibiti naga likita dan banajin daɗi". Ƴar siririyar dariyar wacce ta tsaya iya kan leɓɓansa yayi yana riƙo hannuna na kwanta ya lulluɓamin blanket yace"meyake damuki?". "Kawai banajin daɗin jikinane sai kuma ciwon kan daya sakoni gaba". "Ba matsala goben sai nazo na kaiki ko MY JOURNALIST".na saki dariya mai sauti nace"A'a zanje dakina". Yamin saida safe sannan yafice daga ɗakin,har cikin raina banajin daɗin abunda Habib yakeyi na kasance a ɗakina ako wani dare cikin kwanakin kwanan Yasira,ya zama dole nayiwa tufkar hanci tun kafin kwarɓar tamu tayi ruwa. UWATACE SANADI Tsarawa/rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ____________________________________ Page 4⃣2⃣ Washe gari na tashi cikin matuƙar annushuwa raina fari tas!,zuciyata tamin ƙal!wanda haka yanada nasaba da tsayiwar daren danayi jiya ina nemawa kaina zaɓin Allah arayuwata. Bayan na gama haɗa mana breakfast naci nawa,sannan na shirya tafiya school zana exams ɗina a ƙarshe,wanda daga shi zamu shiga ajin ƙarshe a jami'in babu abunda yake damun raina dan inajin na kusa cikawa Yaya Fawas burinsa duk dashima ɗin ya gama NCE ɗin daya jona har ya fara aiki a wata makarantar kuɗi dake azaren,dakuma ƙudurin Abba nason muyi karatu. Kulolin Abincin nasa cikin basket na nufi part ɗin Yasira,tsit!kamar babu wasu halittun dake zauna cikin part ɗin shurun danayi haka ya tabbatar min dabasu tashi daga bacci ba,na jere musu abincin akan dinning sannan na ciro maganin Habib daga jakata na ajiye akan dinning ɗin da nufin inya fito yagani yasha. A Tsaitsaye na shiga sashin Hajja muka gaisa sannan,na karɓa key awajen malam Habu yau ni nakeson tuƙa kaina. Yau duk wanda ya kalleni acikin makarantar yasan nakai ƙololuwa acikin farin-ciki,dan ya kasa ɓoyiwa sai daya shimfiɗa ƙarara akan fuskata. Muna fitowa daga exams hall ɗin kowa murna yakeyi nagama jarabawar damukayi,sauran mu ganin result daganan kuma mun tafi ajin ƙarshe,naja motar na nufi asibiti. Na zayyanawa likitan abubuwan dake damuna tace naje amin gwaji tukunnna,nabi nurse ɗin aka min gwajin sannan na dawo ofishin na zauna,bai ɗau lokaci ba nurse ɗin ta shigo ta miƙa mata sakamakon ta fita,likitan ta fara dubawa sannan na ajiye takardan gefe guda ta zuba min na mujiya kana tace"Baiwar Allah abinda sakamako ya nuna shine kina ɗauke da hawan jini kuma jininki ya sauƙa sosai,akwai buƙatar ki maida hankali wajen kula da lafiyarki kuma ki cire damuwar dake ranki dan yana ɗaya daga cikin manyan abubuwan dake haddasa wannan ciwon,zan ɗauraki akan magani dan Allah sai ki kula ".ta kai ƙarshen maganar tare da fara rubutu ajikin wata takarda. Tunda ta fara maganar na nema annurin fuskata na rasa,duk farin-cikin danake ciki ya kau yayin da baƙin-ciki ya maye gurbinsa,take naji zuciyata ta karaya na fara hawaye.Likitan ta ɗago kanta tana dubana tace"Subhanallahi!haba ƙanwata ai wannan ba wani abun damuwa bane,matuƙar zaki daina saka damuwa acikin ranki kuma ki kula dashan maganinki zaki rabu da wannan ciwon ki daina kukan ya isa haka".ta faɗa tana miƙo min handkerchief ɗinta nakai hannu na karɓa ina goge hawayena. "Ya Allah wata irinyar ƙaddarace wannan wanda take bibiyar rayuwata tamkar inuwa,duk inda na shiga saina tarda ita Allah mena aikata arayuwata daka hanani jindaɗi a duniya?duk inda na raɓa babu sauƙi sai ƙunci Allah ka jarabce ni da jarabawa iri-iri daga wannan sai wancan ko yanzu ma acikin jarabawar nake,Ya rabbi samawati ka kawo min sauƙi cikin al'amurana kabani ikon cinye wannan jarabawar". Jidanayi likitan ta fara bani haƙuri tare da nunamin na ƙarfafa kaina,hakan ya tabbatar min da cewa a fili nayi maganar ba'a zuci ba kamar yanda na zata. Takardar result ɗin kawai na ɗauka na gyara zaman jakata saman kafaɗata,nace"Nagode"sannan na fita daga office ɗin ta tsaidani ta miƙo min takardar maganin data rubuta min tana ƙara bani wasu shawarwari sannan nafito daga office ɗin,pharmacy na wuce nasayi maganin sannan na dawo mota. Na jingina kaina ajikin kujerar ina fidda hawaye,na daɗe acikin wannan halin kafin na figi motar nayi gida,ina isa na wuce part ɗina kai tsaye bedroom na wuce na ɓoye maganin acikin kayana sannan nayi alwala nayi sallan zuhr ina iddarwa na ɗaga hannayena saman ina nema sauƙi agun sarkin da babu kamarsa. Sai dana shafa addu'ar sannan na zare hijabin na fito na shiga part ɗin Yasira tana zaune tana kallo na isketa,tamin sannu da zuwa na amsa ina tambayarta Habib yaga maganinsa kuwa akan dinning dana ajiye?tace yagani harma yasha kafin ya fita,nayi hamdala sannan na zauna muka cigaba da kallon tare. Sai damukayi sallan Asr sannan muka shiga kitchen domin ɗaura girki,an zuba kayan abinci sosai a store ɗinta anan mukayi girkin sannan muka jeresu a dinning na wuce part ɗina domin nayi wanka,wankan nayi sannan nasaka doguwar rigata anko sunnan Abbul-khair na wuce wajen kayana na ɓalla maganin nasha. Sannan na mayar dasu gurbinsu na ajiye,dan banason kowa yagansu koda Habib ne kuwa balle Yasira shiyasa banyi niyyar sanar dasu ina ɗauke da wannan ciwon ba. Shigowar Habib naji yasa nafito da saurina na tarbe shi ina masa sannu da zuwa,bai daɗe da shigowa ba Yasira ma ta shigo muka zauna zaman hira,Habib na tambayata jarabawar ƙarshe inata basu labarin irn murnan dasu ƴan department ɗinmu sukayi,wasu har tsere mashin sukayi. "Ya asibitin kinje?"ras!naji mummunar faɗuwar gaba na harhaɗo jarumta nace"E naje daman ulcer ce keson kamani kuma an bani magani".cike da kulawa yake faɗin"Allah ya sauwaƙe gaskiya ya kamata kina bawa kanki kulawa,kamar yanda kike kulawa damu acikin gidan nan". Yasira da ɗaura danata zancen"Anty gaskiya Hamma ya faɗa".nace"in sha Allah zan kiyaye kodan farin-cikinku dakuka kasance abu mafi soyiwa a gareni".suka saki dariya Habib yana ƙarasama mana albarka.kafin muje part ɗinta mukaci abinci na musu sai da safe,sannan Habib ya rakoni kamar kullum. Sosai na raya daren da salllolin dare da kuma karatun alqur'ani,washe gari ina iddar da sallan asuba kuwa na danna nomban yaya Fawas sai da kiran ya kusa tsinkewa sannan na ɗaga tun kafin mu gaisa ya dara jefo min tambayar "Lafiya naga kiranki a wannan lokacin?". "Lafiya kalau Yaya Fawas inaso nasanar dake wani abune"yayi saurin yace"Inajinki my cute angle menene"ya kai ƙarshen maganar cike da zaƙuwa. Sai dana tare ruwan hawayen dasuka ciko kurmin idanuna sannan nace"Yaya Fawas jiya naje asibiti bayan amin gwaji aka tabbatar min da ina ɗauke da Hawan jini,wallahi zuciya takusa tarwatsewa Yayana wannan wata iriyar rayuwace na gaji da ita wallahi na tsani duniyar gabaɗaya da abunda yake cikinta,ga wannan ƙaddarar data sameni tun lokacin danayi ɓari har izuwa yanzu da muke wannan maganar kullum cikin jini nake,wannan shine dalilin dayasa iyayen Habib suka haɗa aurensa da ƴar-uwarsa,wallahi ina cikin damuwa zuciyata tana min nauyi yanzu tinanin Umma ya uzura min sosai Yaya Fawas ka kusa rasani inajin hakan a jikina".na ƙarishe maganar ina kifa kaina akan pillow. Kusan mintuna biyu a tsakani kafin Yaya Fawas yace"Hibba ƙanwata kowa da irin ƙaddararsa a rayuwa mukuma haka Allah ya ƙaddara mana ya bamu Umma uwar dabata damu damu ba,balle taji damuwarmu acikin ranta.Sai dai a hakan mafa mufin dubun mutane gata domin wasu ko fuskar iyayensu basu sani ba,basu taɓa rayuwa dasu ba.Akwai wani abokina Imam shi kuwa ƙaddararsu mahaifiyarsu mahaukaciya ce,hauka takeyi tuburar har tsirara tana yawo akan titi kinga gwara mu ki kwantar da hankalinki ki daina kukan sai muyi magana ko?". Nace"To"sannan na ɗago kaina daga kan pillow nafara share hawayena. "Tabbas wannan babban lamarine amma kin sanar da Habib kina ɗauke da wannan ciwon?"a sanyaye nace"ban sanar dashi ba kuma na ƙudurce bazan faɗawa kowa ba face kai,ko Inna ban sanarwa ba". "My cute angle ba'a ɓoye ciwo domin dole wataran zai bayyana kansa,amma meye dalilinki na ɓoye hakan?". "Bazan iya sanar da Habib ba domin yanzu farin-ciki yafara wanzuwa acikin rayuwarsa,sanar dashi wannan lamarin zai ɗaga masa hankali fiye da tunani dan yana da sa abu aransa".sai daya numfasa kana yace"Ki sanar da Ummi na tabbatar zata nemo mana mafita,sannan maganar jinin nan gaskiya ya kamata mu tuntuɓi malamai don yafi kama da sihiri". Sai dana zuƙe majinan kukan dayazo mini kana nace"in sha Allah zanyi hakan zan sanar da ita". Sosai Yaya Fawas ya cigaba da kwantar min da hankali,har sai danaji raina yafara samun nutsuwa sannan mukayi sallama kan zan ƙira na sanar dashi yanda mukayi da Ummi. Tashi nayi na zare hijab ɗin danayi sallan dashi,na fito kitchen na wuce na haɗa mana breakfast sannan na dawo nayi wanka nafito falon ina zama Habib da Yasira suna turo ƙofar falon suka shigo,na miƙe tare da gaida Habib ya amsa sannan muka gaisa da Yasira. Ganin akwatinsa a hannun Yasira yasani faɗin"tafiya zakayi ne naganka da kaya"na ƙarishe ina tsaida idona akan akwatin. "Wallahi zanje Adamawa ne akwai mutane dasuke samar mana da gyaɗa acan,zamu gana dasu zan iya kaiwa kwana biyu zuwa uku haka".Tsuke fuska nayi nace"yaushe aka shirya tafiya ni ko sani banyi ba,to Allah yakaika lafiya yakuma tsare ka".ina kawowa nan na nufi dinning. Banyi zatoba kawai naji ya rungumoni ta baya nafara kiciniyar raba jikinsa danawa,amma na kasa muryarsa ta bugi dodon kunnena yana cewa"Haba wifey wallahi jiya da daddare ne suka ƙirani,kuma tafiyar tanada muhimmanci shiyasa zanje dakaina". Nasarar zare jikina nayi daga riƙo dayayi min nace"To Allah ya kiyaye dan Allah inkaje ka kula dashan maganinka akan lokaci".ya gyaɗa min kai alamar zaiyi hakan. Ina juyowa idanuna suka sauƙa akan Yasira wacce ta ɗauke kanta daga garemu,ta maida shi ga kallom TVn dake aiki acikin falon.kunya ta lulluɓe ni na cillawa Habib wata uwar harara watau yasan tana wajen yamin haka,da watace ai da mun kwashi ƴan kallo danma Yasira duk halayan Ummi ta ɗebo na haƙuri da kawaici. Jawo hannunta nayi muka wuce dinning ɗin,na fara zuba mana abinci kota kansa banbi ba sai dana gama na jayo nawa gabana nace"ki zubawa mijinki abinci"ta gwalo idanu waje tace"Anty ki cika ladanki kawai ki zuba masa". "Ai kema inason ki sama ladanne shiyasa nace ki zuba masa da kanki"ta cuno baki sannan ta tashi ta zuba masa yace"ba komai nasan zaman dazan nayi daku yanzu,tunda haɗe min kai zakuyi".nida Yasira a tare muka bushe da dariya mai sauti. Da haka muka gamacin abinci mukayiwa Habib takiya har harabar gidan,sai daya bi kan dukka ma'aikatan gidan ya sanar dasu zaiyi tafiya ya basu amanar iyalinsa suka masa tare da masa addu'o'i. Nan nake sanar dashi zamuje gidan Ummi yau tun kafin na ƙarisa Yasira ta saki shewa haɗi da tsalle tana cewa"Yau zanga Ummina zanga Ummina". Farin-cikin danagani akan fuskarta haka nan naji zuciyata karaya,tinanin Umma yafara dawo min cikin kwakwkwalwa ta,idan kaga mun cikin farin-ciki da walwala to ranar Umma bata gidan kodai tayi tafiya ko kuma tana wajen sana'ar ta,da zaran ta dawo duk walwalar mu take gushewa. Acikin zuciyata nake ayyano irin farin-cikin Yasira take ciki dan taji zamuje ganin Ummi,sai dai nakasa samun mizanin dazan kwatanta shi,daman haka ake kasancewa cikin irin wannan farin-cikin idan ɗa yaji an ambaci sunar mahaifiyarsa?na jefawa kaina tambayar inama zan iya dawo da hannun agogo baya inama zan iya dawo da rayuwar damukayi abaya duk dacewa babu komai acikinta illa ƙunci da baƙin-ciki amma inason kasancewa da Umma koda na daƙiƙa ɗaya ne. Dafa kafaɗata da Habib yayi yasa nadawo daga cikin tinanin danayi nisan kiwo acikinsa,yafara tambayata lafiya nace masa lafiya kalau kawai dai ni yamin alƙwarin zaina shan maganinsa akan lokaci dan shine babban matsalata,dan intashine zai iya kwana uku bai shaba. Shafo kaina yayi yace"in sha Allah zansha koda na kawar da damuwar dake kan fuskarki".na saki murmushi tare da godiya sannan nashiga yi masa addu'o'in neman tsari da kariya. Yasira taso sukayi bankwana sannan Malam Habu ya wuce kaishi airport ina tsaye a harabar gidan har sai danaga ficewar motar sannan na koma part ɗina,Yasira ma tayi nata domin shiryawa sai dana sha magani na sannan na fara shiri. Cikin mintuna dabasu haura arba'in na na shirya na fiti part ɗin Yasira na wuce ganin har yanzu bata fitoba na sameta ta baza kaya akan bed ɗinta tanacan gefen ta buga tagumin.na tambaye ta lafiya?wai ta rasa kayan dazata sa. Murmushi kawai nayi araina nace ƴaƴan masu kuɗine kena akwai sakalci,sannan na zaɓo mata wata doguwar riga ɗinki buba iya gwiwa da strength siket ta saka yamata ɗas!kuwa dayake datana da jiki. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani iyam _______________________________ page 4⃣3⃣ ni nayi driving ɗinmu har gidan ummi ina gama dai-daita parking muka fito yasira har kusa tuntuɓe tayi tsabar sauri datakeyi wajen shiga gidan. a falo muka iske ummi da sayyid,yasira ta faɗa kan ummi tana faɗin"nayi kewarki ummi wallahi sosai faɗanki da kuma abubuwa da yawa". na ƙariso na zauna ina guntse dariyar dake shirin suɓɓuce min,dan maganar yasira ba ƙaramar dariya ta baniba.ummi ta ɗagota tare da faɗin"kinci gidanku watau faɗa na ma kikayi kewa bani bako?"tayi saurim girgiza mata kaina sai a sannan muka gaishe da ummi ta amsa sannan sayyidd ma mutumina nake masa tsiyar meya kawoshi gida. ya ɗan gallo min hararar wasa kana yace"kema kin koya sa ido irin na mijin nakin ko,todai sa ido babu kyau ehe". na saki wata ƙatuwar dariya nace"kaji dashi dai aurar dakai zamuyi mu huta". yasira tayi caraf ta karɓe zancen tana cewa"wallahi ko budurwa bana tinanin yaya sayyid yana ita". "ummi ki basu labari an kusa nima a shafa min fatiha"sayyid ya faɗa yana jijjiga ƙafarsa wanda ɗaya ke kan ɗaya. sai da ummi ta ɗan dara itama sannan tace"todai sayyid ya samo matar aure yanzu ma jiran daddynku akeyi ya dawo asanar dashi". nan muka shiga zolayarsa a ina ya samota yace babu ruwanmu haka mukata yi,ummi na tambayar mu ina habib mukace mata yayi tafiya. sai da muka tashi domin yin sallan zuhr sannan nasama damar yin magana da ummi,har ɗakinta na bita tana zaune kan sallayarta tana addu'a sai dana jirata muka shafa addu'ar tare. sannan nace"ummi daman wata magana nakeson sanar dake"tace"inna jinki hibba"ta faɗa tana naɗe ƙafafunta waje guda. "ummi cikin kwanakin nan bani da lafiya ina yawan ciwon kai da kuma saka baccin danakeyi,har aman jini inayi shine naje asibiti jiya bayan amin gwaji aka tabbatar min da ina ɗauke da ciwon zuciya,bansanar da kowa ba koda habib bai sani ba domin ina gudun kar yaji ya faɗa wani hali".ina faɗa ina hawaye.salati ummi tasaka sannan ta ɗaura da faɗin"hibba aman jini fa kikace?innalillahi wa inna ilaihirraji'un!gaskiya ya zama dole kisanarwa habib wannan maganar domin ba'a ɓoye ciwo.mussaman ciwon zuciya domin shi yayi sanadiyar rasuwar uwata naga hatsarin dake tattare da ciwon.bawai shan magungunan bane a'a kiyi ƙoƙarin kiga kin cire damuwar dake ranki dan allah hibba". na sadda kaina ƙasa nace"in sha allah zan sanar dashi amma ba yanzu ba dayake tsaka da samun farin-ciki a rayuwarsa".haɓata ta ɗago tare da faɗin"hibba babu wanda ya cancanci yaji damuwar matarsa sama da mijinta,koda kisan kai kikayi zai nema rufa miki asiri ki ƙarƙafa zuciyarki inya dawo kinema lokacin daya dace ki sanar dashi kinji ƴata?".a sanyaye nace"to ummi zan sanar dashi,sai kuma ɗayar maganar munyi magana da yaya fawas akan jinin dake zuba min yace mu tuntunɓi malamai domin abun yafi kama da sihiri,amma nidai hankali bai kwanta da hakan ba domin a duniya ba tinanin akwai wanda ya damu dani balle rayuwata dahar zaimini sihiri". "hibba yanzu rayuwa ta sauya ta wuce duk yanda kike tsammani,na jikinka dashi ake haɗa kai wajen cutar dakai kuma zansa a nemo min malamin sai muje ki kwantar da hankalinki kinji,domin hawan jini ba'a fiye son mutum yana daɗa hankalinsa ba". "to"kawai nace nan tacigaba da kwantar min da hankali na ƙira yaya fawas nasanar dashi yanda mukayi har nabawa ummi wayar suka ƙara tattauna agame da matsalar tawan. na fito nabarsu suna maganar sayyid na iske yana shirya dinning table,da mamaki fal!a fuskana nace"mezan gani haka ɗan ɗakina kai ne da shirya dinnig ya kuma". ya saki murmushi haɗi da farfara idanunsa kana yace"to ai girkin ma ninayi inbaki sani ba,tunda na dawo inake girki a gidan nan" "lalle kam kace ka fara ɗaukan darasi ne tun kafin ayi auren,ashe amarya ta huta dayin girki"na faɗa ina ƙarisowa dinning ɗin sannan na fara buɗe kulolin na farko dana buɗe fried rice wanda yaji vegetable,na biyu kuwa fried chicken ne sai kuma sallad daya haɗa. na lumshe idon sakamakon ƙamshin daya ziyarci ƙofofin hanci na.na ɗago na masa thurum up ina cewa"weldone ɗan ɗakina". kusan a tare da juna ummi da yasira suka fito,kai tsaye dinning ɗin suka wuce yasira tace"meka dafa mana naji ƙamshi haka". "ɗan ɗaki nane ya mana girki"na faɗa ina buɗe musu kulolin."wannan ɗin wai shi yayi wannan girkin? tab!"ta faɗa tana nuno sayyid da hannu. ya galla mata harara kana yace"to mekika ɗauke ni,ga ummi ki tambaye ta wayake girki a gidan?". "sayyid shiyake mana girki yanzu,safe da rana harma dinner yarona yanzu sai dai son barka"furcin ummi kenan wanda ya kawo ƙarshen cece-cucen daya ɓarke tsakanin yasira da sayyid. muka zauna muka faracin abincin sanin damukayi daddy baya ƙasar,sai da mukacinye tas!munata santi sayyid kuwa sai dariyarmu yakeyi yanajin muna ƙara fasa masa kai. tare da yasira muka tattare wajen muka dawo falo muka zauna,nan umma ke tambaya karatuna nace mata mun gama exams saura muga result. na tashi zanyi sallan asr ɗakin yasira na shiga nayi alwala sannan na tada sallan,ina iddarwa wayata ta fara ruri na yalwata murmushin fuskana ganin sunan danayi saving nomban habib dashi ya bayyana ɓaro-ɓaro cikin screen ɗin wayar jigona sunan danayi saving dashi kenan. na ɗaga ƙiran tare yin sallama ya amsa sannan nace"kamar ka shiga raina yanzu nake tinanin na ƙiraka sai kuma natada sallah,ya hanya an isa lafiya?".ya sakar min murmushi yana cewa"lalle muɗin na dabanne tunda har tinanin dake zuciyoyinmu yakanzo ɗaya".murmushin nima na maida masa kana cewa"an isa lafiya ya gajiya?". "mun iso lafiya gajiya kam akwai shi sosai". "todai yanzu kaci abinci,kasha magani sannan ka kwanta ka huta da daddare sai muyi magana".ya amsa min har zai gimtse ƙiran nayi saurin faɗin"ka ƙira yasira kuwa?".inajin yanda ya furzar da iska daga bakinsa yace"a'a ban ƙira taba,ki gaishe ta ". "a'a bari dai na kai mata"kafin yayi wata kalmar na katse ƙiran na fito falo nan kuwa na tarda yasiran tana kallo,na danna mishi ƙira ya katse ya ƙara ƙira na miƙa mata tare mata bayyanin habib ne sannan nayi wucewata ɗaki dan banason sauraran abunda zasu faɗa. sai da mukayi sallan isha'i sannan muka fara shirin tafiya ummi tace dare yayi bazanyi driving ba sai dai sayyid yakaimu sai ya dawo a taxi.haka kuwa shiɗin yakai mu sannan ya dawo. ranar a part ɗina muka kwana tare da yasira,tun daga lokacin muke kwana tare da izuwa ranar da habib ya dawo. muna tsaye a harabar gidan muna jiran dawowar tun lokacin daya sanar damu jirginsu ya ɗaga,malam habu ya tafi ɗauko sa. tun ƙarar motar da mukaji ta tsaya a ƙofar gidan gate man ya wangale masa ya shigo bakunan mu suka kasa rufuwa.tun kan yagama parking muka isa gareshi dukkanmu muka rungume shi cike da murna da farin-cikin ganinsa cikin ƙoshin lafiya,muna laɓe ajikinsa muka shiga cikin gidan. a falo muka yaɗa zango muna gaishe yana amsawa daki-daki,sannan na miƙe naje na haɗa masa ruwan wanka yaje yayi a kuma ciro masa doguwar jallabiya fara sol!marar nauyi na ajiye masa na fito. nan na sama yasira tana ƙara arranging dinner na jonata muka cigaba dayi.muka zauna zaman jiranshi bai ɗau lokaci ba yafito. muka miƙe muka tarboshi sannan yasira ta zuba mishi abincin nikuma nafara bashi sai dana tabbatar dana cika masa ciki sannan na ƙyale shi,na ɗauko masa maganinsa nabashi yasha. sannan muna muka zuba namu abincin a plate ɗaya muka zuba mukaci tare da yasira. haka ranar muka wuni cikin walwala har dare muna hira,sai wajajen ƙarfe goma kana habib ya raka yasira part ɗinta ya dawo,dan a lokacin a ɗakina yake. ina gaban mirro ina shafe jikina da mai yashigo ɗaki,ta cikin madubin na hange shi. na miƙe na fara gyara mana shimfiɗa har nagama yana tsaye aƙofar ɗakin duk motsin danayi sai ya bini da kallo da haka na gama gyaran. sannan na ɗaga masa ido ɗaya alamar ko lafiya?baice dani uffan ba ya ƙariso cikin ɗakin ya zauna akan sofa,na takuwa na zauna kusa dashi ina fuskantarsa nace"hamma inason muyi wata magana dakai amma dan allah kamin alƙawarin bazaka sa abun aranka har ya haifar maka wani ciwon ba".sai daya musguta yace"in sha allah faɗi ko menene inajinki"ya faɗa cike da zaƙuwa dason jin menene. "ranar danaje asibiti ne daman gaskiyar magana ba ulcer ce ke damuna ba,kamar yanda na faɗa maka hawan jini ne ke damuna domin likitan ta tabbatar mini da hakan"nakai ƙarshen maganar ina sakin kuka mai sauti. a matuƙar razane ya kamo hannuna lokaci guda ya fara share min hawaye ne,kana yace"ki daina wannan kukan banaso"sai dana tsagaita kukan kafin yajefomin tambayar data ƙara karyar mini da zuciya"meyasa kika ɓoye min wannan lamarin shin bakai naji damuwarki bane ?". "habib na ɓoye maka haka ne domin banason ganinka cikin wani hali,zuciyata bazata jure ba idan nayi la'akarin dacewa yanzu farin-cikinka yafara dawowa domin kana samun komai awajen yasira ba kamar ni ba dana kasa sauƙe hakkinka.ummi tace nasanar dakai domin kai kafi cancanta daka sani akan kowa,kuma munyi magana da yaya fawas dama ummi akan cewa jinin dayake zuba min mu tuntuɓi malamai dan jinnu ma sunasa irin haka".na faɗa cikin kukan daya soma cin ƙarfina. rungumo ni yayi jikinsa yana bubbuga bayana yace"ya isa haka ki daina kuka in sha allah zaki rabu da wannan ciwon,sannan zamuje wajen malamai ɗin kamar yanda ummi tace". ajiyan zuciya kawai nake sauƙewa ɗaya nabin ɗaya har bacci yayi nasarar ɗaukata,ganin haka yasanyi kwantar dakai akan ƙafarsa sannan ya lula duniyar tinani. hawan jini to meya jawowa hibba irin wannan ciwon?meta nema ta rasa daga gare ni?idan ma akan ɓatan mahaifiyarta take damuwa ai ummi ta zame mata tamkar uwa bada mama ba.tabbas yasan hibba nada matuƙar haƙuri gami da zurfi ciki,aduk lokacin dazata aikata abu takanyi tinanin farin-cikin mutanen dake zagaye da ita.ako ina kuma aban kowani mahaluki zai iya bugun ƙirji yace yayi sa'ar samun nagartacciyar mace abar alfahari ako yaushe. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________ Page 4⃣4⃣ Washe gari koda na tashi na sama Yasira da Habib sun gama shirya komai na karin kumallo har sun kimtsa ko'ina sai sanyayyan ƙashin turaren dake tashi daga ko wacce kusurwa. "Anty kin tashi"Maganar Yasira wanda a safiyar wannan ranar shiya fara sauƙa cikin kunnuwana. "E wallahi yau na makara kadda dai har kin gama girkin?".Sai da taɗan murmusa tace"Hamma ne yayi komai nima kawai ƙarisawa nayi". Na kai dubana ga Habib yadake tsaye yana jera plate a dinning ɗin kamar baya sauraron abunda muke faɗi. Na gaishe shi sai a sannna ya ɗago ya amsa sannan na ƙariso muka gama tare mukaci abinci. A falo muka zauna domin Habib ya buƙaci tattaunawa da dukkanmu bayan gama cin abincin damu kayi.sai da yayi gyaran murya yana mai ƙara fuskanto mu kana yace"Yasira munaso mu sanar dake wani jarabawar da Allah ya ƙara jarabtar mu dashi na ɗaurawa Hibba cutar hawan jini ga kuma matsalar datake ciki na jinya tun daga ranar da tayi ɓari,mun yanke shawara kamar yanda Ummi ta shawarce mu akan mu tuntuɓi malamai akan matsalar jinin kuma yau zamuje mu sameta domin nemawa kanmu mafita". Yasira da tunda ya fara maganar tagama ruɗewa tace"Anty muna gida ɗaya dake amma ki kasa sanar dani meyasa".na riƙo hannunta inacewa"Banason na ɗaga miki hankali ne shiyasa ban sanar dake ba amma yanzu ba gashi kinsani ba". "Allah yabaki lafiya,Allah yasa kaffarane ga zunubanki"ta faɗa cikin kukan dake saɗɗanta.duk muka amsa da Amin kafin muka tafi kowa yaje ya shirya muka fito na ɗauko maganin Habib nabashi yasha tare da tambayata nasha nawa maganin na ammsa masa da e nasha,sannan muka tafi. Tunda muka hau titin zuciyata ke bugun tara-tara sau tara har muka isa,yana gama parking muka fito sanna muka wuce cikin gidan. Anan muka tarar da Iya da Granny sunzo,muka gaishesu Yasira na tambayar Iya yaushe sukazo?tace jiya da daddare kuma a ya zasu koma daman sunzo gaisuwar ta'aziyane na wata ƴar-uwan Iya data rasu anan katsinan. Habib ya sanar da Granny dalilin zuwarmu itama ta amince akan muje wajen malamin,Iya tace"akwai wani maganin gargajiya inhar sihiri ne to cikin kwana bakwai da yardan Allah zai karye ko za'a gwada shi?". Ummi tace"to Iya sai a gwada mugani ko Allah zaisa mu dace".Habib yace"Mungode iya" Jikina duk yagama yin sanyi na ƙara da cewa"mungode Allah yasaka da mafifin alkhairi"duk sula amsa da Amin kafin Iya ta shiga lissafo abubuwan da za'a buƙata.ganyen tunfafiya ne guda uku sai kuma nonon shanu mai kyau Ummi tace Sayyid yaje ya sayo nonon shanun ganyen tunfafiyar kuwar almajirai aka bawa naira Dari suka tsinko mana da yawa. Iya ta wanke ganyen tunfafiyar tasa a tukunya tare da nonon shanun yayita tafasfasa,sannan ta sauƙar daya huce aka juye shi acikin wani tsaftataccen bokati tace da safe kafin naci komai nafara shansa. Granny tace Habib yabarni nayi kwana biyu a gidan saboda maganin danake sha,haka kuwa ya barni suka tafi da Yasira duk safiyar Allah wannan ruwan maganin shike fara sauƙa a maƙoshi ne.Na ƙira Yaya Fawas nagaya masa halin da ake ciki yace incigaba da shan maganin har muga abunda Allah zaiyi. A rana na uku danayi ina shan maganin da safe Habib da Yasira sukazo,duk muna zaune a falo ana gaisawa Iya ta kawomin ruwan maganin na karɓa nasha inajin yanda yake sauƙa yanabin maƙoƙarona izuwa cikin ciki.naji jikina yaɗauki rawa zuffa ta shiga karyo mini daga kowace kusuurwa jikina take nafara kwara mai a wajen.Duk sukayo kaina suna min sannu sosai nake aman tamkar zan amaryar da hanjin ciki ga aman kore shar!dashi tun inayi daga zaune Iya da Ummi suna riƙe dani har na durƙushe inayi daga kwance. Suka ɗauke ni suka kaini ɗaki banɗaki suka shiga dani dana na galabaita sosai,ƙafafuna ma jansu kawai nakeyi dan jinsu nayi kamar a jikina sukeba.suka gyara min jikina sannan suka kwantar dani a gado ai kuwa banfi minti uku ba bacci ya tafi dani.dai-dai anan Habib ya shiga ɗaki gani na a kwance yasashi tambayar Iya ko lafiya?. Cikin tsantsan murna daya saka ɓoyiwa akan fuskarta da tsofa suka fara bayyana tace"Ai babban mutum sai dai mu godewa Rabbi domin sauƙi yasamu,tana tashi daga wannan baccin daman cikin biyune dole tayi ɗaya kode amai ko kuma zawo". Yasira da mamakin furcin Iya ya gama cikata tace"Hakan yana nufin kenan sihiri aka mata?to waye yayi mata hakan alhalin ita kowa nufinshi takeyi da alkhairi babu abunda ke zuciyarta face imani da tausayi". "Ai Yasira yanzu rayuwar duniya ta lalace lamarin sai dai muce innalillahi wa inna alaihir raji'un,kufito mu barta har zuwa lokacin dazata farka"furcin bakin Granny kenan,kamar jikinsu babu laka duk haka suka fara ficewa daga ɗakin Habib yace zai zauna tare dani har na farka. Zazzafar ajiyar numfashi yayi lokacin da duk suka gama fice daga ɗakin,maganganun Yasira na dawo masa cikin kunnensa tabbas abun yakai ayi mamakinsa sihiri wa yayiwa Hibba hakan?kuma meye dalilinsa na aikata hakan a gareta?. A iya zaman dasuka yasan bata da abokin faɗa balle ace har sunyi gaba da wani.da wannan tinanin ya iso gaban gadon ya zauna akan kafet ɗin dake yashe kusa da gadon akan gwiwoyinsa ya zube ya kamo hannuna yana ƙarewa fuskata kallo.ya zama dole ya gano wanda ya aikata hakan domin inbaiyi hakan ba zuciyarsa bazata rayu cikin salama ba. Bazan iya ƙidaye awannin danayi ina bacci ba,sai lokacin dana buɗe ƙiran sallan magrib shine abunda yafara sauƙar mini cikin kunne.na fara ƙoƙarin tashi a hankali duk jikina ciwo yake min akan sallaya na hango Habib ya idar da sallah yana addu'a ganin na fara tashi yasashi fasha addu'ar da sauri ya nufoni. Tare da tallafar kafaɗata ya jingina ni acikin pillow lumshe idanuna nayi wasu sirarun hawaye nabiyo gefen kuncina. "Ba kuka zakiyaba Hibba kamata yayi ki godewa Allah daya kawo mana sauƙi kuma mafita ga lalurarki". Muryan Habib kenan dana tsinkayo su a tsakar kaina,nayi saurin ware idanuna ina tsaidasu akan fuskarshi ko ranar dana fara ganinsa a office ɗin Yaya Bashir ban masa irin kallon nan ba. "Ki tashi kiyi sallolin dake kanki"ya kuma faɗa yana riƙe da hannuna,namiƙe na shiga bathroom.wasu tinanin nika suketa ziyartar kwakwalwata marasa kan gado,da haka nafara wanke fuskana sannan na zare kayana domin ina buƙatar na watsa ruwa ajikina. Pant ɗin dake jikina kodana cireshi naga jinin ya tsaya cak!na shiga hamdala ina ƙara godiya ga ubangiji tsabar murna har ƙwalla sai danayi. A gurguje nayi wanka tsarki sannan na ƙarayin wani wankan nayi na fito,ban iske Habib a ɗakinba wanda nake zaton ko yafita masallacine dan sallan magrib ma a ɗakin naga yayi. Ko mai ban tsaya murzawaba na saka kayana na ɗaura long hijab ɗina asaman sa na tada kabbara,sai da nayi duk sallolin dake kaina sannan nayi isha'i sosai nayi addu'o'i acikin sujjadata ta ƙarshe.sannan nayi sallama ina gamawa na shafa addu'ar na jawo wayata na danna ƙiran Yaya Fawas yana ɗauko ko gaisuwa ba muyiba na fara sanar dashi Allah ya kawo min sauƙi ina labarta masa ina hawayen farin-ciki. Shima haka nan murna ta gama cikasa ba abunda yake faɗi illah kalmar ALHAMDULILLAH,har mukayi sallama akan zai ƙira su Baffa ya sanar dasu dan Inna ba ƙaramin damuwa ta shiga ba. Ko zare hijabin kaina banyi ba na fito falo,nan na tarar da kowa hadda Daddy wanda ko dawowarsa banji ba,na ƙariso cikin falon ina gaida da Daddy ya amsa fuskarsa cike da ni'ima.Ummi ce ta fara faɗin"Hibba yanzu yaya kike jin yanayin jikin nakin?"na sadda kaina ƙasa nace"Ummi Alhamdulillah banajin komai hatta jinin ma ya tsaya". Duk suka haɗa baki wajen furta Alhamdulillah haƙiƙa Allah shine abun godiya. Yasira ta nufo ni tare da faɗawa jikina na rungumeta ina kukan murnan daya zomin,Ummi ta ɗagota daga jikina tare da cewa"Meye na kuka kuma ku kuwa?ai godiya zaku yiwa Allah daya kawo mana ƙarshen wannan masifa data samemu gabaɗaya".Granny ta ɗaura da faɗin"Haka ne kam sai dai mu godewa Rabbi,haƙiƙa Allah gwamin hikima ne". Na kai hannu na sharce hawayen fuskana,Habib tun ɗazu dayayi sujjada har yanzun bai ɗago ba. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 4⃣5⃣ Dukda kunnuwa na basa jiyo mini abunda yake faɗi cikin sujjadar amma na tabbatar godiya kawai yakeyi wa ubangiji daya nuna mana wannan ranar muna masu rayayyu. Ummi dake nake zaune ɗan nesa da ita,ta dafa kafaɗata nayi figigi na ɗauke idona dasuka ƙara kawo ruwar hawaye daga kan Habib. Na sunkuyar da kaina ƙasa sai a sannan Habib ya ɗago yana ƙara jere godiyarsa ga Allah sarkin da ikonsa yake akan komai da kowa tare dukkaninmu muka shafa addu'ar sannan ya taso ya zauna a mazauninsa nada. Daddy yayi gyaran murya"Haƙiƙa rayuwa cike take da jarabawa,sannan dukkanin mu munyi imanin cewa ƙaddarar bawa bata wuce kan mai ita.mu kasa jure jarabawar da Allah ya jarabci Hibba dashi na lalura tsawon watanni har sai da Haƙurinmu ya gaza muka haɗasa aure da ƴar-uwarsa.Tabbas haƙuri nasara ce babba kuma duk wanda ya rungumeta baya taɓewa wannan alƙawarine na Allah,Hibba ta kasance daga cikin mutanen dasuka karɓa ƙaddararsu hannu bibiyu,har gashi yau taci ribar wannan haƙurin datayi ba kowacce mace bace tazayi halalcin da kikayi kin danne duk wani kishi yayin auren Habib da Yasira kuma bayan auren baki canza su daga matsayin dasuke a da ba hatta mu muma kina bamu girman mu madalla dake Hibba Allah yayi muku albarka". Da Amin duk muka amsa dashi sannan Ummi ma ta ɗaura da nata nasiha haka nan ma Granny da Iya. "Kar wannan jarabawar tasa kiyi fatali da tauhidin ki na kaɗaita Allah duk abunda ya sama bawa daga gareshi ne sannan kuma rubutacce ne daman tun fil-azal acikin ƙaddarar rayuwarsa,karki bari zuciyarki ta zargi kowa akan faruwar wannan alamarin kisani babu wanda ya isa ya miki abunda Allah bai miki ba"furcin Granny kenan wanda naji sun ƙara sanyaya mini sashin ruhina kuma ya wanke duk hashashen da zuciyata kemin akan sihirin da Iya tayi magana akai na ƙara kawar da tinanina akan cewa wani ne yamin hakan amma zamu ƙara tattaunawa da yaya Fawas. Daddy dasu Habib suka fita masallaci domin sallan isha'i muma muka miƙe mukayi namu,ina zaune akan sallayata a ɗakin Ummi Yasira ta shigo kusa da inda na miƙe ƙafafuna ta zauna,tace"Anty kinga lamarin Allah ko?"kaina kawai na jinjina tacigaba dacewa"Wataƙil dasu Granny sunyi haƙuri har izuwa yanzu da Allah ya baki lafiya basu haɗa wannan aurenba". Ƙwayar idona na tsayar akanta"Yasira meyasa kike irin wannan tinanin kamar bamai ilmin addini ba?,kinsan fa ƙaddara bata wuce lokacinta koda wannan lalurar data faɗa mini ko babu ita idan Allah ya ƙaddara zaman aure a tsakaninki da Habib babu makawa sai hakan ya faru". Leɓɓanta ta fara motsawa alamar bakinta nason furta wani abun,nayi azamar kamo hannunta na riƙe gam!cikin nawa nace"Muci muci abinci duk mu suke jira".sannan muka jera muka fito Ummi da Sayyid suka tarar suna sauƙar da abinci suna ajiyewa akan babbar gardumar da aka shimfiɗa a wajen.muka ƙarisa muka tayasu sauƙarwa. Nida Yasira mukayi serving ɗin kowa sannan muma muka zuba namu a plate ɗaya muka faraci,Sayyid ya kallomu ya saki murmushi ƙasa-ƙasa yana maida kansa da plate ɗin abincin dake gabansa. Yasira ta ɗan harare sa tace"Faɗi karta kashe ka". "Naga kun ware min ɗan-uwa a gefe kun zuba abincinku ku biyu,shi kuma shi ɗaya gaskiya wannan ba adalci bane". Lokaci ɗaya muka bushe da dariya Habib kam murmushi kawai yasaka ya ɗauke kansa kamar yabajin abunda mukeyi. Granny ta gyara zaman tanakai lomar wainar masan farar shinkafar daka ɗebo cikin bakinta tace"Nima dai haka nagani ana nuna masa wariyar launin fata ƙiri-ƙiri,mijina ai ba gata ka rasa ba bari nazo muci tare ina baka a baki".ta miƙe ta dawo kusa da Habib dariya mai sauti muka saka nida Yasira hadda Sayyid wannan lokacin har Ummi da Daddy da Iya sai da suka murmusa,ganin Granny ta zage tsakaninta da Allah ta ɗebo lomar tana bawa Habib a baki shi kuwa ya wani sha kunu yana taunar abincin kamar an masa dole. "Lalle Hajiya kice yau ƙaunace ta motsa keda mijin nakin"furcin Ummi wanda yasa muka ɗan tsagaita da dariyar muka baza kunne don jin amsar Granny. "Ke dai Habiba bari yo banda yaran zamani ma dame suka fimu soyayyar ko kuma kula da mijin?".Muka ƙara tuntsirewa da wata dariyar. Da haka muka gama cin abincin cikin nishaɗi da tsantsar ƙaunar juna a matsayinmu na ahli guda,nida Yasira muka tattare wajen sannan muka dawo falo. Granny kam da Iya ɗakunan su suka wuce,Daddy da Ummi ma basu daɗe ba suka tafi ɗaki bayan mun musu sai da safe. Daga ni sai Yasira da Habib muke zaune a falon muna kallo wani series film ɗin da'ake haskawa a tashar Tauraruwa TV,Sayyid kuwa tunda aka ƙira wayarsa ya fice. Sai danaga ƙarshen film ɗin sannan na tashi na kashe kayan kallon nayiwa Habib sai da safe na wuce ɗakin Yasira. Koda daban juyoba jikina yabani irin kallon da Habib kebina dashi har kusan tuntuɓe da matattakala nayi. Na wuce ɗaki wanka nayi koda na fito na iske Yasira ta shigo har ta kwanta,dan daman a gidan zamu kwana.na wuce gaban mirro ina murza mai sama-sama a jikina wayata ta hau ruri gabana ya faɗi ras!ina juyayin abunda zaisa Habib ƙirana cikin daren nan dan bamu fiye yin waya da daddare ba ko lokacin dayake neman aure na. Na ɗauka tare da manna wayar a kunne na"Me kikeyi har Yanzu bakiyi bacci ba?". "Wanka nayi yanzu nake shirin kwanciyar"nakai ƙarshen maganar ina ɗan zame wayar daga kunnena na duba agogo wanda yake nuni da ƙarfe shaɗaya da mintuna arba'in,lalle na daɗe a banɗakin maganar daya somayi yasa na maida wayar kunnena. "Inason ganin ki yanzu please". Na gyara ɗaurin towel ɗin dake jikina kana nace"Yanzu dare yayi fa sosai sannan ga Ummi dasu Granny ina kunyar suka fitana na shiga part ɗinka".ya katse ni dacewa"To ni bari nazo"kafin nace wani abun ya kashe wayar. Zuciyata ta harba da ƙarfi na miƙe na ciro doguwar rigar bacci na nasaka,dan nasan tunda ya furta to babu makawa zai aikata inagama gamawa na ɗaura hijabi na akai sannan na ɗauka wayata na fito daga ɗakin. Saɗaf-saɗaf nake tafiya ina duba inda zan jefa ƙafata dugun kar nayi wani ƙwaƙwƙwaran motsin da zai tashi wani. Nazo dai-dai ƙofar fita daga falon naci an dafo kafaɗata ta baya,na juyo a firgice na zage iya ƙarfina zan ƙwala ihu naji an toshe mini baki na fara cikiniyar ƙwacewa. "Matsoraciya kawai tsoro kamar farar kura"ya faɗa yana janye hannunsa daga kan bakina. Na ɗan jefa masa harara ya tsareni da ido yace"Dakika fito ɗin ina zakije hmm watau anason abu ana kaiwa kasuwa". Na ware idanuna akansa inajin haushin kaina dana fito lokaci guda kuwa kunya ta mamaye ni,narasa yaushe Habib ya zama haka. "Muje mu zauna sai muyi maganar"ya faɗa yanayin gaba nabi bayansa izuwa cikin falon muka zauna akan kujerun dake fuskantar juna,haske farin wata d kuma walƙiyar da akayi wanda ke nuni da ruwan sama kan iya ɓarkewa a kowani lokaci yake hasko cikin falon,hakan ya bani damar kallon fuskarsa. "Shine duk kukayi zamanku anan kuka bari ni ɗaya ko?".nayi ƙasa da kaina ina wasa da yatsun hannuna nace"Nazata Yasira zata kwana acan ɗinne shiyasa". "To tashi mu tafi"nayi saurin cewa"mu tafi ina". "Ɗakin mijinki mana". "Baka kunyar Ummi ko wani gobe ya ganni ina fitowa daga part ɗinka,uwa uba ma Yasira". Ya aiko min da wani irin kallo dana kasa gane manufarsa kafin yace"Shiyasa ai nazo da kaina dan nasan ke bazaki iya zuwa ba tashi mu tafi kawai malama".duk na daburce nafara waige-waigen ina duban hanya kar wani ya fito. Naji ya rungumo ni yanacewa"Nima wasa nake miki kawai nazone naganki rabin raina domin nayi bacci mai daɗi,ku shirya cikin satin nan zamuje Nijar in sha Allah". "Baka sha maganinka ba bari na ɗauko maka,sai na taso maka Yasira itama ku gana".na faɗa ina rabashi da jikina har nakai ƙofa naji ya kuma riƙo hannuna najuyo ya marairaice fuska yace"Inasonki matata sonki yaabi dukkan sassan jikina Allah ya muku albarka".Sosai naji daɗin kalamansa nace"Amin rajlun amin"sannan nawuce ɗauko masa maganin inata juyayin canzarwa Habib lokaci guda dan ko mace bata fishi kunya ba rashin kunyarsa sai mun shiga ɗaki mun rufe ƙofa. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 4⃣6⃣ Maganinsa na ɗauko sannan na fara tashin Yasira,duk yanda nake bubbuga pillown da ƙiran sunan ta kasa tashi tayi,dan bacci yaci ƙarfinta sosai haka na fito na sanar dashi sannan na bashi maganinsa yasha muka yiwa juna sai da safe. Ranar har kusan sha ɗayan dare muna chart dashi,sosai na sake ina maida masa da kalaman soyayyar dake mini,haka kuwa na kwana raina fes da soyayyar JIGONA. Washe gari da wuri muka tashi muka haɗa breakfast kasancewar Daddy zaiyi tafiya,muka gama muka jeresu a dinnig. Munacin abincin Habib ke sanar da Daddy tafiyar dazamuyi zuwa ƙasar nijar. "Lalle ka kyauta dan kuwa daman suna ƙorafin cewa baka kai musu ziyara,kaga kuwa yanzu sai ka ɗeba matanka kuje dasu". Granny ta ɗaura da nata"Ka gaishe su sosai inkunje don Allah".yace"In sha Allah Hajiyata yau baza abani abincin bane?". Ta ɗan harare shi kana tace"yau kuma banyi niyya ba ai ga matanka nan suka baka". Muka sa dariya Sayyid yace"Yau kuma keda mai gidan nakin". Muka tashi muka raka Daddy compound ya tafi su Granny ma ayau ɗin zasu koma damaturu,muma haka nan yau naji Daddy dazai tafi yana cewa Ummi ta tabbatar mun koma ɗakunan mu. Tun taran safe su Granny suka tafi muma maka fara namu shirin Ummi ta haɗa min tsumi masu kyau da wasu turarurruka ma'abota kamshi.nayi godiya sannan muka tafi,duk muka watse muka barta daga ita sai Sayyid dan sunyi hutu a makaranta. Muna isana wuce part ɗin Hajja nasanar da ita komai,tsabar murna har sujudul shukr sai datayi. Da dare kuwa muna zaune duk a falo Habib ke sanar damu jibi ne tafiyarmu,bakina ya kasa rufuwa dan murna a dangin mahaifiyarsa Goggo Suwaiba mahaifiyar Batul ita kaɗai na sani sai kuma wasu siraru.Yace gobe zamuje gano muyiwa su Baffa sallama. Washe gari kuwa tun ƙarfe bakwai muna Hanyar Kano sosai muke tsala gudu muka isa kuwa da wuri. Tun a ƙofa na hango Baffa yana tsaye ya tare ƙofar da hannunsa yana bawa Hajara baki gami da haƙuri. "Malam kasan Allah yau a gidanmu zan kwana,ko ce mata akayi banda gata ne?"furcin Hajara kenan danajisu a kunnuwana yayin danake fitowa daga cikin motar na maida murfin ƙofar na rufe. Zuciyata ta buga da wani mungun ƙarfi a sanyaye na iso garesu,sai a sannan Baffa ya lura da zuwanmu ya washe baki"A'a Mamana kune tafe?"sannan ya maida idanunsa ga Hajara"Ke kuma ki wuce ciki inna shigo zamu ƙarishe maganar".ta saki wani tsaki mai dogon zango kama tayi ciki. Nida Yasira muka tsuguna muka gaishe shi ya amsa sannan Habib ma ya rusuna ya gaida shi sunayin musabaha,idanuna suka garwaya cikin na Habib nana take naji hawaye sun zomin da kuma kunyar yanayin damukazo muka iske Baffa da Hajara suna jayayya har a bakin titi. Nayi wuf na shige cikin gidan Yasira ta rufa min baya,Inna muka tarar tana zaune a tsakar gidan tanacin ɗumamen tuwo,tamiƙe ta tarbemu da fara'arta.idanuna suka sauƙa akan Hajara data garƙame ƙofar ɗakinta tana tsaye da gana must go ɗin kayanta tana ta faman huci da kaɗa ƙudu. Na sauƙe ajiyan zuciya dai-dai nan Baffa da Habib suka shigo muka tashi muba basu tabarman suka zauna yayin da muka ɗauko kujerun zaman tsakar gida irin na katako muka zaune,nan aka shiga sabon gaisuwa. Habib ya sanar dasu dalilin zuwar mu,Inna tayi tamana fatan sauƙa lafiya Baffa kam na lura duk hankalinsa ba'a jikinsa yakeba yanaga Hajara da izuwa yanzu take sakin ƙwafa. Habib ya fita saboda ƙiran zuhr da aka farayi yana fita yara suka fara shigowa da kayan abincin daya siyowa su Inna,aka fakesu a tsakar gidan Inna ta shiga sa masa albarka. Sannan muma muka tashi domin yin sallan,Yasira ta ɗauki buta ta shiga bayi hakan ya bani damar faɗin abindake raina ga Inna"Inna nikam meyake faruwa ne acikin gidan nan?". Ta gyara ɗaurin zaninta tace"kedai bari Hibbatu yo mezai faru kuwa banda abunda wannan baƙar makirar nan Hajara keson kitsawa a gidan nan,tun asuba ta hanamu bacci wai sai ya saketa dayake bata ganin mutuncin kowa shima kuma ban isa in faɗa masa yaji ba in sha Allah duk mungun nufinki akanki zai juye". "Idan kin isa da ɗan naki a yau ba sai gobe ba kisa shi ya sauwaƙe min,domin nima ina son naga jinina a duniya na gaji da zama da juya" Martanin Hajara kenan dasuka sanya Inna ƙara harzuƙa ta miƙe "Daɗin abun ma dai kafin ke ya auri wata matar kuma har ta haihu Allah ne yayi ikonsa ɗan baizo da rai ba,idan ba ƙaddara ba mai zaisa Adamu zama dake ƙarƙashi inuwar aure wallahi kinacin sa'ar mahaifiyarkine Laminde daba wannan batun yanzu akeyi ba". Nan suka fara maidawa junan su magana da nasan haka ne zaifaru dan ban fara tarar Inna da maganar ba daman nasanta da gajen haƙuri. Hayaniyarsu yasa Yasira fitowa daga banɗaki muka fara basu baki,sannan muka ja Inna muka shigar ɗaki. "Inna dan girman Allah ki daina biye mata,ai ko ba komai gaba kike da ita haka nan ma zurfin tinanin da shekarunki ya ɗara nata". Yasira ta amsa da"Haka ne Inna sai ana kai zuciya nisa".na ɗaura da faɗin"bari naje na haɗa miki ruwan wanka sai kiyi sallan". Har na kawo nan Inna bata tanka mana ba illa fucin datakeyi kamar saniya zatakai bugu,ga kuma wani uban zuffan datake haɗawa. Na fice na haɗa mata ruwan wanka sannan tafi izuwa banɗakin,fitanta daga ɗakin yabani damar sakin kukan dake nuƙurƙusan raina danaji zuciyata na mini soya sosai yayin danaji maganganun da Hajara ta yaɓa min lokacin danake ɗibarwa Inna ruwan wanka suna dawowa kunnuwana "Bi'izinillahi ta'ala haka zaki ƙare raguwar rayuwarki cikin ƙunci da baƙin-ciki.mijin dakike taƙama dashi ɗinma sai ya juya miki baya sai kin ƙwanmace kiɗi da karatu". Maganganunta sun taɓa mini rai sosai sannan sunsa na zubda hawaye idaniya,tabbas na daɗe da sanin Hajara bata daga cikin jerin masu ƙaunar ta a duniyar nan amma banyi zaton ƙiyayyar takai har ta fito min da ita a fili haka ba. Yasira ta fada kafaɗata tana bani baki duk da batasan dalilin kukan nawan ba. Jin fitowar Inna daga banɗaki yasani share fuskana,nafito na ɗauki buta nayi alwala na dawo nayi sallah. Naji duk na ƙagu mu tafi dan zaman gidan ya ishe ni,bamu sama zama da Inna ba amma a tsaitsaye na sanar da ita jinin dake zuba min nasama sauƙin shi,tace Yaya Fawas ya sanar da ita tashin Hankalin danazo na samesu aciki shi yasa ta sha'afa da batun tamin murna sosai. Ta jikin labule na hango inuwar Hajara ta nama laɓe tana sauraron abunda muke zantawa,maganar danake sanar da Inna yasa Hajara kusan faɗuwa a ƙas. Har sai datayi bol da kwanukan silbobin dake ƙofar ɗakin,batare data saniba tsabar kaɗuwa. Inna ma data lura da hakan ta ɗaga murna tana faɗin"Allah mun gode maka da kawowa marainiya sauƙi daga ƙunci dake ciki,ƴan baƙin ciki kuma sai a mutu". "Allah ya kyauta"na faɗa cikin raina. Munayi Asr kuwa muka fito zamu tafi bamuga Hajara a inda muka barta ba ,Inna ta rakomu ƙofar gida muka tafi. Koda muka hau titi Habib ya tambaye ni dalilin sauyawa nace masa gajiyace kawai. Muna isa namusu sai da safe nawuce part ɗin wanka kawai nayi nayi salla na kwanta raina a cunkushe. Washe gari Ranar dazamu tafi kuwa tun safe muka gama shirinmu mukayiwa Hajja sallama sannan muka biya wajen Ummi itama muka mata sallama. *ƘASAR NIJER*cikin jahar maraɗi muka dosa tun sauƙarmu a airport aka turo mana driver ya kwashe mu,tun kafin mukai ga shiga cikin gidan manya hatimin sarauta da kuma zane irin na gidan masauta da aka ƙawata ginin dashi ya fara ɗaukar idona. Aka buɗe mana makeken gate baƙi wuluƙ muka shiga hadimai ne keta safa da marwa a harabar gidan. Babbane gidan dan duk yanda na baza idanuna ban gano ƙarshen saba.ginin gidan irin na daɗe da ake yinsu da jar ƙasa gefe guda kuwa wasu bukkukine guda huɗu dake fuskantar juna an kewayesu da korayen flower gwanin ban sha'awa. Girman gidan ya tabbatar min da family house ne,saboda yawan part-part dake gidan. Wanda ya ɗauko mu daga airpot ya ɗeba akwatinmu yayi gaba dashi muna biye dashi. Sai da muka ƙetare faloli manya-manya guda uka sannan a na huɗun muke iske jama'ar gidan. Wata farar mata da shekarunta zaizo kusan dai-dai dana Inna sai dai hutu da kwanciyar hankalin datake ciki sun hana,shekarunta bayyana a fuskarta,ita ta fara miƙewa.tanada jiki da kuma tsayi a haɗe sannan launin fatarta fari sosai mai irin ja haka. Ta washe baki ta shiga zubo kirari ga Habib"Lalle maraba da Babban mutum dattijon arziki ubanmu maganin kukanmu,Habibu ɗa ga Abubakar da Zainaba Allah ya jiƙan rai,mai farar aniya yakuwar kan kabari baƙin cikin masu taushi matsu kusa daji ɗuminka". Ya tako a hankali ya isa gabanta tare da rusunawa ta zame hularsa daga kansa ta dafa kansa. Muma muka ƙarisa cikin dandamalin falon muka fara ɗibar gaisuwa ga baffanisa da sauran ƴan -uwa.tabbas Habib ɗan dangine dan duk girman falon mutane ne keta wulgawa tako ko'ina. Wannan dattijuwar matar danaji Yasira ta raɗa min cewa sunan ta Goggo Hanne sannan itace babba a zuriiyartasu,ta kalloni kallo ɗaƴa dana mata nagano izza da kuma ƙasaita da mulkin dake bin jinin jikinta dan ko magana zatayi sai sun bayyana. "Kece Hibbar ko?"na ɗaga mata kaina sannan ta ɗaura"Tabbas na samu labarin gwagwarmayar da Ubana yasha kafin yasama aurenki,ban hallata bikin ba sakamakon lokacin ina ƙasa mai tsarki ina gudanar da aikin hajji". Falon yayi tsif ita kaɗai ake saurara"Wannan gidan namu yanada tarihi babba a duk ƙasar nijer dan babu gidan sarautar daya ɗara namu a wancan lokacin,kakanmu nawajen uba shi yayi mulki da yayi murabus aka ɗaura wan mahaifinmu wanda har izuwa yanzu zuriyarmu ce ke mulki.Mu goma iyayen mu suka haifa nice babba sai mai bimin Isma'il sai Salamatu,Hadiza,Suwaila,Hayatuddeeni,Suwaiba,Lawisa,Jamila sai kuma autarmu Zainaba.Allah ya azurta mu da yawa dan duk cikin mu inkika cire Suwaiba da Zainaba sune kawai masu ƴaƴa ɗaɗɗaya amma dukkamu babu mai ƴaƴa ƙasa da goma,Sannan a tsarin gidanmu bama auren bare Zainaba ce kawai ta auri wanda ba ɗan zuriyarmu ba ɗan wata ƙabila can daban sannan ta buɗewa ƴan baya ƙofar yin hakan."ta kai ƙarshen maganar tana ɗan tsuke fuskarta. Adda Suwaila ta umarci ƴan matan dasu kaimu ɗaki mu huta kafin lokacin cin abinci yayi muka miƙe muna biye dasu a baya,ban sani ba ko ni kaɗai na lura da irin kallon da Adda Suwaiba mahaifiyar Batul kemin koko sauran jama'ar dake falon suma sun lura da hakan?. Irin kallon nan mai cike da ƙasƙanci dakuma son tabbatar min dacewa ni ba kowa bace,na kawar da kaina muka fice daga falon. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ___________________________ Page 4⃣7⃣ Farida ƴar Goggo Hanne da kuma ƴan biyun kawu Isma'il Nabiha da Nabila su suka kawo mu ɗakin,sannan suka juyo nidai wanka na faɗa nabar Yasira tana latsa waya. Acan falo kuwa Habib da babban ɗan Adda Salamatu Aliyu haidar suka fita sashinsa,Goggo Suwaiba ta rakasu da harara kawu Hayatuddeeni data lura da ita yace"lafiya Hajiya?". Ta taɓe baki"kai dai bari Ɗan-uwa wallahi inna tina wannan abun yana min ciwo fiye da zato". Goggo Hanne ta kallo ta"meye yake miki ciwon Suwaiba?" "Hajiya dangin mahaifin Habib sun cuce mu sun ɓoye mana babba al'amari akan auren Habib da wannan matar tasa Hibba take ko Habi,kunsan dai sanin kowa daga cikinku ne irin yanda aka kai ruwa rana kafin auren Zainaba da Abubakar ya yiyu,dan tazo mana da baƙon al'amari na auren bare bayan auren duk cikinmu babu wanda yake zumunci da ita kamar ni nasan dukkan rayuwar datayi a gidan mijinta sannan bayan rasuwarsu babu yanda bamuyi da dangin Abubakar akan su bamu riƙon Habib kodan lalurar dashike ɗauke da ita ba amma suka nuna mana kasawarmu.Munso haɗa shi aure da Batul nan ma suka nuna mana iko akanshi wai ya samu wacce yakeso hakan ya ƙara tuzura da yawa daga cikinmu". Shuru ya ratsa falon kowa yana jinjina kai alamar gamsuwa da maganganun Goggo Suwaiba. Adda Hadiza tace"to Suwaiba ai wannan abubuwan cikinmu babu wanda ba akan idonsa ya afku ba tabbas dangin Abubakar sun nuna mana iyakar mu akan ɗan ƴar-uwarmu matuƙa". Goggo Suwaiba ta ɗaura da faɗin"Duk ba wannan ne matsalar ba a matsayi irin na wannan gidan da mutane suke mana kallon daraja da kima ace jikan wannan gidan yana auren yarinyar datayi zaman kanta,ta guje iyaye da dangina ta zaɓa zaman bariki wanda babu mafaɗi balle mai kwaɓarka". A hanzarce Goggo Hanne ta tashi daga kishingiɗewar datayi ta ƙurawa Goggo Suwaiba na mujiya kamar yanda duk sauran ƴan uwan nasun sukayi cike dason ƙarin bayani daga bakin Goggo Suwaiba. "Hajiya bakije auren Habib na farko bane shiyasa baza kusan da wannan al'amarin ba nima ɗin danaje sai ranar auren Hajiya kulu take sanar dani kuma banason aga laifi na ace zan kashewa yaro aurensa akan abunda bai taka kara ya karya ba". Adda Salamatu ta gwalo idanu"Yo Suwaiba wannan ai sun nuna mana cewa basu ɗauke mu a bakin komi ba,ace auren Uban mu amma su ɓoye mana wannan abun".ta fashe da kukan takaicin dake cinta kawu Isma'il yace"Ai Hajiya ni bana ganin laifin kowa kamar na Zainaba ita ta dage akan sai ta auri Abubakar duk dangi ita ta fara nakasa mana al'adar auren zumuncin da mukeyi a tsakaninmu daya samu asali tun kaka da kakanni,dan haka duk abunda suka mana ita taja mana". Goggo Hanne data gama sauraron maganganun ƙannen natan ta sauƙe wata ƙatuwar ajiyan zuciya kafin ta sauƙe idanunta akan manyan ƴaƴansu dasuke zaune a falon,tayi gyaran murya kana ta umarce su dasu fice zasu tattauna a tsakaninsu,dan wannan ba lamarin daya shafesu bane dan tun kafin a haifosu suke gwagwarmaya akan auren Zainaba da Abubakar. "Inko hakane tabbas dangin Abubakar sun mana zagon ƙasa,ace yarinya tayi rayuwa ba a gaban iyaye ba ai wannan abun dubawa ne ƙwarai da gaske,zan zauna da Habib ɗin naji ta bakinsa inya tabbatar mana da abunda kika faɗa sai munsan matakin dazamu ɗauka"tana kawowa nan a zanceta ta miƙe tare da naɗe dukkan hannayensa a bayanta ta nufi ɗakinta,suma ɗaya nabin ɗaya suka fara fice daga falon suna tafe suna ƙara tattauna maganar. Ina zauna kan sallaya ina lazimi naji wayata ta fara ruri,na ɗan firgita saboda baccin gajiyan daya fara ɗaukata na ɗaga ina kallon Yasira datake kwance tana bacci hankali kwance sallama nayi ya amsa sannan ya ɗaura da"Ya gajiya dan nasan akwai ta saboda ke daga cikin Katsina zuwa daura ma gajiya kikeyi balle kinyi wannan tafiyar". Na ɗan tsuke fuska kamar ina gabashi kana nace"kuma gani a zaune ba garau kamar ba wani tafiyar da nayi gajiya ai yanzu tabi jiki". Ya saki murmushi yace"ko kuma tabi lafiyar gado ba"har na soma magana ya katseni"uhmm ni a wani part kuka sauƙa ne?". "Tab!ni kuwa ina zan sani ina baƙura wani part ne dai yana kallon na Goggo Hanne"na faɗa ina mimmiƙe ƙafafuna dasuka sanƙare tsabar zama guri ɗaya. "Part ɗin ƴan matan gidan kenan,ni kuwa gani a ɗakin wannan tuzurun Aliyu Haidar ai wallah......."bai ƙarisa ba naji sauƙar dukan wasan da Aliyun yakai masa,hakan yasani tinanin suna tare kenan. "Wifey kina ganin zai illatani ko daga faɗin gaskiya?"na ɗan murmusa nace"ai kuwa dayaga taron kanawa da katsinawa dan taron dangi zamu masa".shima ya maido mini da murmushin yana cewa"to dai kaji da kunnenka ko?in kayi zuciya kaima kayi auren". ya saki murmushi yana ɗaura agogonsa yafita cikin uniform ɗinsa na sojojin ƙasar nijar. Muka cigaba da hirarmu,ƙiran sallan isha'in da'aka farayi ya tilasta mana yin sallama bayan yabawa Aliyun wayan mun gaisa. Gefena na ajiye wayar na tada sallah,ina iddarwa kuwa nafara jeri addu'o'ina ban damu na tada Yasira ba dan tace min tun kafin zuwarmu tana fashin salla. Ƙiran Ummi ya shigo wayar Yasira da farko banyi niyyar duba waye ba balle har na ɗaga ƙiran,danaga an cigaba da ƙira ya sani tashi na ɗauka wayar zan tashe ta dana Ummi ce mai ƙira sai kawai na ɗauka muka gaisa tana tambayata ya mun iso lafiya na amsa mata da lafiya kalau sannan na tada Yasira na miƙa mata wayar. Ina zama Farida dasu Mima suka shigo na ƙara yalwata fuskata da murmushi muka ƙara gaisawa dasu Farida wacce na lura duk tafisu sakin fuska da kuma saurin saɓo haka nan kuma tafi sauran sakin jiki dani tace"Anty duk gajiyarce tasaku zaman ɗaki tun ɗazu muke jiran fitowar ku Hajiya sai aikowa takeyi wai mu fito cin abinci".na murmusa nace"wallahi yanzu nake cewa ina iddar da sallah zan tashe ta mu fito". Yasira na gamayin wayar muka fito na ɗaura hijabin danayi sallan dashi wanda ya sauƙa min har ƙasa dan ko takalmina ba'a hangowa na saka,suka ta min dariya muka fito falon farko damuka fara zuwa shi muka shiga nan kuwa muka tarar da kusan kowa ya hallata a wajen,muka zauna akan babban gardumar daka shimfiɗa. Bamu ɗau lokaci ba su Habib da wasu samari huɗu suma suka shigo wanda yake a gaba kuma duk yafi sauran jiki na raya a raina ko shine Haidar ɗin,mussaman danaji Adda Suwaila na tsokalar shi dacewa "to ga shugaban gauraye ma ya fito"ƴan matan ƙannen nasan suka saki dariya kallo ɗaya ya watsa musu duk suka shiga taitayinsu. Addu'ar cin abinci muka gabatar sanna kowa ya maida hankalinsa ga abunda yakeci,babu abunda kakeji sai ƙara cokula. Muna gamawa nima na shiga sahun masu tattare wajen sannan muka tsabtace shi muka dawo muka zauna na lura da Goggo Hanne da duk motsina take ankare dashi da kuma alamar damuwar dake fuskarta. Kawu Hayatuddeeni yace"Yanzu kai Aliyu duk ƙanneka sunyi aure ga Habib nan har da mata biyu,amma kai har yanzu kama kasa cire wacce kake son cikin ƙannen nakan" "kasan yanayin aikin mufa kawu bamu da lokacin kanmu balle kuma na wata,adai ƙaramin lokaci in lokaci yayi zanyi"cewar Aliyu Wannan karan Adda Hadiza mahaifiyarsa ce ta karɓe zance"Ai su kuma sojojin ce maka akayi basa aure koko meye?kai dai kawai kace baka da niyya ne". Sadda kansa ƙasa yayi"kuyi haƙuri in sha Allah zanyi in lokaci yayi"yana kawowa nan ya tattari wayoyinsa ya fice. "Hande min boni ni kuwa anya yaron nan ba aljanu gareshi ba,ace mutum da lafiyarka amma sam bakason zance aure"furcin da Adda Jamila ta rakashi dashi kenan. Muka tashi muka musu sai da safe sannan muka tafi izuwa makwancinmu,washe gari muka yini da Farida Yasira kam tana can wajen su Nabiha da Mima.bayan mu gamacin abincin dare a ranar kamar jiya kowa ya hallara. Goggo Hanne ta ɗan musguta kana ta umarce su Farida dasu tashi zasuyi wata maganar da ƴan uwanta tace Habib ya zauna wanda da farko ya miƙe zaibi ayarin su Khalifa ɗan Adda Lawisa ya komo ya zauna. Damƙo hannuna Farida tayi zamu tafi Goggo Hanne tace nina zauna,na komo na zauna ƙirjina namin dukan tara-tara sau tara. Kawu Hayatuddeni ne ya fara magana"Habib gaskiyar wani lamari mukeson mu sani shin da gaske ne matarka Hibba tayi zaman kanta kafin ka aureta sannan mahaifiyar ta uwar karuwai ne mahaifinta kuma ƙasurgumin ɗan fashi da makami?". Innalillahi wa inna ilaihirraji'un zuciyana ya buga tamkar zai fito daga cikin ƙirjina,na soma sakin hawaye Adda Lawisa ta dafoni haɗi dacewa"Ai ba abun kuka bane,kawai munason mun cewa hakan ne ko kuwa maganarce bamu fahimta ba". Goggo Hanne ta tsurawa Habib ido tace"Ubana kai muke sauraro". Na ɗago idanunmu suka gwaraye cikin na juna kansa ya soma jijjiga min wanda na kasa fahimta meyake nufi da hakan, ganin bashi da niyyar buɗe baki yayi magana ya sani cewa"Hajiya hakane kafin aure na da Habib nayi zaman kaina,nayi wata rayuwar da babu iyaye balle ƴan-uwa a kusa dani sannan gaskiya ne mahaifiyata ta kasance magajiyar karuwai amma mahaifina tsautsayi ya faɗa masa ko kuma ince ƙaddara.Tabbas na ƙudurce a raina cewa ko ba daɗe ko ba jima rana irin ta yau za tazo a rayuwata sannan za'a zargeni akan irin rayuwar dana gudanar a baya".na kai ƙarshen zancena tare da sakin kukan dayake fitowa kai tsaye daga ƙoƙon raina. Goggo Suwaiba ta rafza salati"kun gani ko ashe dai abunda naji babu kuskure acikin sa". "Ina mahaifiyarki take a halin yanzu"tambayar Goggo Hanne kenan na yarshe hawayena nace"bama tare da ita domin nakai shekaru tara rabon dana sata a idona,ina zaune ne a wajen dangin mahaifina a cikin kano a ƙauyen gano "na gwammaci na sanar dasu komai dan nasan tabbas tambayarta ta gaba shine a ina Habib ya ƙarbo aurena gwara na faɗa mata tun kafin ta tambaya. "Habib lamari irin wannan yanada sarƙarƙiya kabi ruɗin soyayya kayi zaɓen tumun dare,yarinyar da batayi rayuwa a cikin gidan iyayenta ba kamar yanda duk wata ƴar kirki takeyi, ta zaɓa rayuwar bariki ta gama yawon ta zibar ɗinta akan titi Allah kaɗai yasan adadin mazan datayi tarayya dasu wacce ta siyar da jikinta kai kuma dayake kaine dayyus marar kishin kansa marar hankali da hange nisa ai ko Allah ma yace ka zaɓawa ƴaƴanka uwa ta gari wacce zasuyi alfahari da ita kuma daga tsatso mafi kyawu.ita kuwa wannan menene abun burgewa da sanya shauƙi har ayi marmarin aurenta a kaf!cikin tarihin rayuwarta har wani tarbiyace gareta ita da ta taso acikin karuwai tanbaɗaɗɗo marasa mutumci kuma basa ganin kowa da mutumci hatta iyayen da sukayi silar kawosu duniya.wani tabbaci kake dashi akan cewa itama irin wannan rayuwar data taso taga mahaifiyar tanayi bazai burge taba?shawaran dazan baka ka nutsu ka sake tinani tunda su dangin uban nakan nagan kamar tsoronka sukejine koko meye ni ban sani ba,dasuka kasa nushance dakai wannan babban haɗarin daka tafka sannan kuma abu na ƙarshe kaje asibiti a bincika lafiyarka kar ta goga maka cutarsu ta karuwai cuta mai karya garkuwar jiki".furcin bakin Adda Hadiza kenan takai ƙarshe tana huci. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ________________________________ Page 4⃣8⃣ Kaina yana cikin gwiwoyina tunda ta fara maganar idaniyana suke fidda ruwan hawaye har takai aya,duk maganganunta akan dai-dai suke UWATACE SANADI a yau badan irin rayuwar da Umma ta zaɓawa kanta ba da ban fuskanci wannan ƙalubalen ba a rayuwar aurena. Habib kam hannayensa kawai yasa yana tare hawayen dayake yi zuciyarsa na masa nauyi sosai yana fizgar numfashinsa.idanuna dasukayi jajir kuma lokaci guda duk suka kumburu kamar zasu faɗo ƙasa na ɗago na sauƙe su kan Adda Hadiza na soma faɗin"Tabbas ban kasance daga cikin mataye da har zasuyi tinanin samun mazajen ƙwarai a rayuwarsu ba,domin duk wanda zaiso neman aurena sai an bashi labarin waye mahaifiyata da kuma abunda yayi silar rasuwar mahaifina UWATACE SANADI bazan zargi kowa ba sannan duk abunda zai faru soyayyarta bazai ragu a cikin wanna ƙirjin nawan ba.ban cancata zama da Habib ba ko ayau ya sakeni bazan daina yi masa fatan alkhairi ba domin shiya tsamo ni daga cikin ƙazantacciyar rayuwata.na kasance ako yaushe zuciyata dana cike da fargabar rana irin ta yau ranar da za'a goran tamin dan Allah mijina dan soyayyarka da annabi muhammadu S W A ka sauwaƙe min hankalin kowa ya huta kaima kasama salam..." Adda Lawisa tayi saurin kai hannunta ta makemin bakina"kul!waya gaya miki mace tanacewa mijinta ya sake ta haka siddan ba tare da wani dalili ba ai sai ki shiga fushin Allah". Adda Salamatu tace"ai dakin barta gaskiyan littafin arziki dayace ƴan gidan gadon rama da ƙulu idan suka sama aure a gida farfesu sunfi kowa iya fetsere".Adda Lawisa ta jinjina kai kawai. "Hajiya hakane tayi rayuwa ba a gaban iyayentaba amma wannan ɗinma da dalili,sannan kuma a cikin gidan Uncle Suraj ta zauna duk tsawon wannan lokacin,idan tanada wani mungun hali ai za'a gani a zaman dasukayi dasu Ummi".Cewar JIGONA mai kareni a ko yaushe. Goggo Hanne tace mu tashi mu tafi zata ƙara neman mu tare da tambayar Habib yaushe zamu tafi?.yace daman sati ɗaya zamuyi saboda hutun makarantana ya kusa ƙarewa zamu koma. Da kyar nake jan ƙafafuna na wuce ɗakinmu nayi sa'a kuwa ban tarar da kowa a ciki ba Yasira tana can tare dasu Nabiha.kamar jaka haka na faɗa kan gado ina sakin kukan da hawaye basa fitowa dan sun ƙafe,tabbas duk wata macen datayi rayuwa irin tawa ya zama dole a jefeta da zargi harma fiye da wanda Adda Hadiza kemin a halin yanzu.karo na farko a rayuwata danayi dana sanin auren Habib naji na tsani kaina gabaɗaya badan sanin danayi akan duk wanda ya kashe kansa makomarsa wuta ce ba to wallahi dana rataye kaina na huta da wannan rayuwar. Habib ne kawai zai iya wankeni daga wannan zargi domin yasan cewa a budurwa ya same ni,ban taɓa riƙe koda farce wani ɗa namiji balle yakaimu ga aikata alfasha,nasan hadda ƙiyayyar dasuke gwada su dangin mahaifin Habib itama ta shafe ni. Ina jin wayata data soma ringing har ƙiran ya katse aka ƙara kira a karo na biyu shima banbi ta kansa ba,sai ana ukun na yunƙura najawo wayar nakara fashewa da kuka ganin sunan mai ƙiran JIGONA na cilla wayar akan gado na koma na kwanta ina matso ruwan hawayena Naji ƙaran shigowar messega na duba. "Nasan bakya cikin nutsuwa a yanzu amma dan Allah ki ɗaga ƙirana inason muyi magana ne please wifey dan Allah ki sauyawa halin dazan shiga". Ina gama karantawa na sauƙe ajiyan zuciya na zubawa emojis ɗin dayasa a ƙarshen message ɗin masu alamar kuka,idanu har na fara maida masa da reply ƙiran Ummi ya shigo wayar na ɗaga tare da mannawa a kunnena na kasa furta koda kalmace. "Hibba dan Allah kimin magana na ƙira Habib naji shi cikin wani yanayi yamin bayanin komai ki kwantar da hankalinki,karkisa wannan a ranki zan turo miki kuɗi gobe ki shirya kayanki kiyi tahowarki dan bazan juri cin mutumci haka ba daga zuwarku kamar daman jira sukeyi".furcin Ummi kenan dasuka ƙara sanyani tsananta kukana nace"Ummi ni banga laifin kowa daga cikinsu ba domin duk maganansu akan dai-dai take,kowa zaiyi burin samawa ƴaƴansa uwa ta gari kuma mai usuli mafi kyawu da nagarta ,kun nuna min dukkan gata dakuka yarjewa Habib ya aureni sannan baku taɓa min gori ko kuwa nuna tsangwama ba nagode Allah yasaka muku da mafifin sakayyarku amma na fara tinanin na roƙo Habib ya bani takardata". "Hibba karda wahalar gidan miji yasaki ki gujewa bautar Allah ki sani shi aure ibadane kuma bauta kikeyi.duk abu mai muhimmanci ba'a samunsa cikin sauƙi ko jindaɗi sai ansha wahala duk duniya babu wanda ya kamata kibi sau da ƙafa kamar mijinki idan aka cire Allah da manzonsa,zaman aure sai an daure kuma sai an haɗa da haƙuri.yanzu kidan kikace ya sake ki shin kinsan waye zaiki kuma aura ne?,shin kinsa wani irin zama zakuyi dashi?,shin kina da tabbacin zaki dawwama cikin jindaɗi ba tare da jarabawa ba?.Hibba babu komai a cikin wannan rayuwar face ƙalubalen da zakita haɗuwa dashi,shifa ɗan-Adam ba zai taɓa zama cikin farin-ciki da jindaɗi ba". Tabbas banyi kuskuren bawa Ummi wani bangare mai girma acikin raina ba,domin ta cancanci hakan daga gareni kalamanta suka sanyaya mini ruhina nafara sauƙe numfashi a hankali kana nace"Nagode sosai Ummi Allah yaƙara lafiya da nisan kwana dan Allah ki tayani da addu'a Allah ya kawo min haske cikin rayuwata". Inajin yanda ta sauƙe numfashi tace"in sha Allah Habib zai zamto duk wani haske a rayuwar ki". "Ina fatan haka Ummina".sosai tayita kawo min misalai da ƙissan matan annabawa hadda ƙissan ƴar ma'aiki Nana Faɗima alaihissalam a gidan aurenta tasha wahala sai naji to waye mani ɗin dabazan sha wahala agidan aure ba tunda mai matsayi irin nata yasha balle ni. Mun daɗe muna waya da Ummi kafin mukayi sallama nayi niyyar ƙiran Yaya Fawas amma nafasa dan banason naɗaga masa hankali acikin wannan daren. Na tashi na nufi banɗaki na ɗauko alawa nafito na sama wayata tana ruri na duba naga Habib ke ƙira bakin gadon na zauna na zuwa wayar idano ina rafzar kuka kamar wacce aka aikowa da saƙon mutuwar uwa da ubanta. Har ƙiran ya tsinke na kasa ɗagawa mussamman dana tinu cewa zaman aurenmu dashi yakusa zuwa ƙarshe. Furcin Adda Hadiza suka soma dawo min cikin ƙwayar kaina"Shawaran dazan baka shine kaje asibiti a duba lafiyarka kar tasa maka cutarsu ta karuwai,cuta mai karya garkuwar jiki".kaina ya sara mini da matuƙar ƙarfi na durƙushe a wajen ina kuka na daɗe cikin wannan yanayin kafin nayi ƙarfin halin miƙewa ina riƙe da kaina da nakejinsa tamkar an ajiye min wani abu mai nauyin gaske saboda azabar ciwon dayake min. Na rarimo hijabina nasaka na tada sallar ina iddarwa Yasira dasu Farida suka shigo ɗakin nabisu da ido har suka ƙariso suka zauna,Yasira tace"Anty nazo na miki sai da safe ne zan kwana a ɗakin su Mima". Na sunkuyar da kaina nace"to atashi lafiya Allah ya bamu alkhairin sa". Ta amsa da Amin yayin datake jan hannun Nabiha suka fice,saura Farida ita kaɗai. "Anty kamar bakida lafiya duk jikin ki babu kuzari ko gajiyar ce har yanzu?"na ƙirƙoro murmushin daya tsaya iyakan leɓɓana nace"Babu komai Farida kawai yanayin ƙasar takuce kamar bata karɓe ni zazzaɓi nakeji". Ta taso ta dawo kusa na tare da ɗaura hannunta saman wuyana"bari na ɗauko miki magani"tana kawowa nan ta fice. Na maida kaina cikin gwiwoyina ina lazimi da gaɓoɓin hannuna,naji a rufo ƙofar ɗakin an shigo ban damu na ɗago naga ko waye ba dan nayi zaton Farida ce. Naji an rungumoni nayi saurin ware idanuna dasuke lumshe,cike da zaƙuwar ganin waye ya shigo min ɗakin. Idanuna suka tozali da Habib banyi ƙoƙarin rabashi da jikina ba dan kallon cikin idonsa danayi na hangi tsabar tashin hankalin dake cikinta. "Meyasa zakimin horo mai tsanani irin haka na yarda na amince ki hukuntani ta kowace hanya amma banda wannan". Nayi maza na haɗiye kukan dake shirin zuwar min nace"hakan shine mafita a garemu dani dakai gabaɗaya domin inaji a jikina an kusa a rabamu rabuwa ta har abada,daman duk wani abunda zai kawo haske a cikin rayuwata sai na fara murnar mallakarsa sai ya suɓɓuce min". Ya ƙara ƙarfin riƙon daya min yace"babu abunda zai rabamu sai mutuwa na miki wannan alƙawarin,zan zame miki haske acikin rayuwarki zan zame miki ɗan jagora ta yanda zakiyi tafiya ba tare da lalume ba". Hawayen dasuka fara bin gefen kuncina ya fara share min na tsanya ƙwayar idona cikin nasa"Habib ina gudun ranar da zatazo kaima ka zargini irin wanda ƴan-uwan mahaifiyar kemin a halin yanzu,na gwammaci muyi haƙuri da juna tun kafin zargi ya shiga tsakanin igoyoyin aur..."yayi saurin rufe min baki da tafukan hannyaensa"babu wata ranar makamanciyar irin wannan acikin rayuwarmu,na shaida cewa a budurwa a aure ki sannan ki kawo budurciki izuwa inda yafi cancanta watau gidan mijinki babu abunda zai faru komai zai wuce kinji haba cute Angle ɗin Yaya Fawas kimin murmushi mana". Bansan sanda taƙaitaccen murmushi ya kubce min na rungumoshi naji numfashinsa dake fuzga da ƙarfi na ɗago inabinsa da kallon tuhuma"Anya kasha maganinka kuwa?". "Har kina tinanin cewa kina cikin wannan halin zan sama nutsuwar shan magani?"na cizo leɓɓana na ƙasa nace "to bari na ɗauko maka kasha"na wuce cikin akwatin kayana na ɗauko masa daman raba maganin mukeyi wasu a wajensa wasu suna wajena. Na ɓalla masa yasha sannan muka zauna ya kwantar da kansa akan kafaɗa ta,Farida dataje ɗauko min magani ta turo ƙofar haɗe da sallama na zata zai tashi sai naga ya dake abunsa har ta shigo. "A'a Hamma daman kana nan ne,kuyi haƙuri na shigo muku a lokacin dabai dace ba"wuf ta fice daga ɗaki ta barni raina cike fal!dakunya shikam ko a jikinsa.na ture kansa daga jikina tare da aika masa siririyar harara"wai kai bakaji kunya bane?". "Kunyar meye kenan,to me kuma akayi yanzu?". "Nidai wallahi ka tashi ka tafi kar wani ya ƙara shigowa ya ganka".ya jefomin harara kana yace"sai nagama abunda ya kawo ni tukunna".ya kashe min ido ɗaya daga nan kuma na rasa bakin magana. Mun dan daɗe dashi kafin ya tafi na kwanta dan banason Farida ta shigo ta tardani idona biyu har yanzun kunyarta nakeji,inajin shigowarta na ƙara rufe idona ta kwanta a gadon tare da kashe wutar ɗakin. Juye-juye kawai nakeyi ina haɗa zuffa sai numfashin danake fitarwa da ƙarfi duk na yaye bargon dana lulluɓa dashi,firgigi na farka ina haɗa duk wata addu'ar data fara zuwa bakina a wannan lokacin.na juyo na kalli Farida datake baccinta cikin kwanciyar hankali mummunar mafarkin danayi akan Umma ya fara dawo min cikin ƙoƙon kaina na fashe da kuka. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 4⃣9⃣ Najawo ɗan kwalina na toshe bakina tare da runtse idanuna ina tinano mafarkin danayi,Umma nagani acikin wani mayiwacin hali na jinya duk ta ƙanjame ta bushe kamar ba itaba wacce duk wanda yasanta zai shaideta dason gayu da ƙyale-ƙyale shekarunta kuwa daman ajiye su takeyi a gefe. Faffaɗan dajine mai cikowar bishiyoyi da manya da ƙananan halittu tana yashe a ƙasa kiyashi da tururuwa suna shiga ta hancinta suna fitowa ta baki da kunnenta,cikin muryarta dabata fitowa sosai tace cemin nida Yaya Fawas mu yafe mata. Ta maimaita kalmar a gareni yafi sau yanda tela yake taka keken ɗinkinsa,ko ince yafi sau shurin masaƙi yanayin dana hangata shiyafi komai ɗaga min hankali da sanyani fargaba mai tarin yawa yayin dason ganinta ya mamaye ni sai dai ta ina zan fara nemanta?ina zan nufa?waye zan tunkara?. Tambayoyin dasuka tokare min rai kenan ciwon kan ya dawo min sabo idanuna suka min nauyi sosai duk da banida haske fata amma sai da fuskana tayi jajir. Na zaro ƙafafuna ƙasa zan sauƙa daga kan gadon,jirin ya maidani na koma na sake yunƙuruwa naji muryar Farida sun sauƙa a kunnuwana"Anty lafiya kuwa?". Maimakon nabata amsar tambayarta sai na fashe da kuka mai tsuma zuciya da sanya rauni.ta ƙara matsoni tare da faɗin"Suhbanallahi!lafiya kike kuka ko bakida lafiya ne kona ƙira Hamma Habib ne?". "Babu komai basai kin ƙira kowa ba kawai mafarkine nayi ya tsora tani"na faɗi maganar filla-filla kamar mai koyar magana. Ta riƙo hannuna tasa cikin nata tare da gyara zaman datayi a bakin katakon gadon ƙiran italian bed"Anty nasan kina cikin wani hali na rashin kwanciyar hankali domin na saurari dukkanin tattaunarwa ku dasu Hajiya tun ba yau Goggo Suwaiba take yawa da wannan maganar acikin dangi tun bayan lokacin dataje bikinku itada Batul da kuma matan kawu Isma'il.babu wanda ya ɗauki abunda muhimmanci sai yanzu dasuka ganki amma kisa a ranki cewa komai muƙaddari ne jarabawa bata ƙarewa a rayuwar mumini mai imani idan kikayi haƙuri zaki ribanto dashi in sha Allah,Hamma yanasonki danko ɗazu na ganewa idona ai wannan ma kaɗai ya isheki godiya wa Allah". Na sauƙe numfashi"Farida nagode da shawararki amma ke bazaki fahimci irin raɗaɗin da zuciyata take ciki ba,banama ko wacce ɗiya mace fatan tayi irin rayuwata koda kowa maƙiyiyatace domin babu komai a cikinta face ƙunci,baƙin-ciki,rashin hankali da kuma tarin ababen dasuke hana zuciya sukuni su sanya ruwar idaniya zuba ako yaushe". "Jarabawar mutum takanzo masa ta ko wacce siga kiyi tawakkali,komai lokaci ne dan Allah ki daina wannan kukan kar ya haddasa miki wani ciwon tun ɗazu kike yinsa"ta ƙarishe zance tana share min hawayen dake gudana tsakanin kuncina da kan haɓata. Banajin kona gwada zan iya tsayiwa akan ƙafafuna nace Farida ta riƙe ni na tashi tayi riƙo da kafaɗata na miƙe na nufi banɗaki. Raina cike maƙil da mamakin irin zufin tinani irin na Farida na tabbatar na girme ta a shekaru balle kuma na haɗata da Yasira,sai dai tanada girman jiki dan inmuka jera da ita ka iya rantsewa kace yayatace. Nan nagane cewa shi tinani da sanin ya kamata ba daga shekaru yake ba kwance fuskana na somayi bayan na kawar da tinanin Farida daga raina. Na tabbatar da inada ciki a wannan lokacin sai ya zube saboda tashin hankalin dana tsinci kaina aciki,na jawo ƙafafuna dasuka min nauyi inaji tamkar basa jikin gangar jikina. Nan inda na barta na fito na iske Farida ta taso ta kamo hannuna ta zaunar dani,na lumshe idanuna a hankali sannan na waresu akan Farida wacce taketa jera min sannu ɗaya nabin ɗaya nace ta ɗauko min maganin hawan jinina acikin akwatin kayana ta ɗaukomin sannan ta haɗu min da goran ruwa nasha. "Anty bari naje na sanar da Hajiya ko Hamma Jabir zai dubaki tunda shi likitane koma yana gida yau". Na buɗe idanuna datunda nasha maganin na maida su na lumshe"A'a Farida ai ciwo ne kawai na lokaci ɗaya daman yana min irin haka lokaci zuwa lokaci har na saba,kar ki ƙira kowa in sha Allah zuwa safe zanji sauƙi". "Allah yasa" tafaɗa cikin harshen fulanci sannan muka kwanta ina duba agogon wayata daya nuna ƙarfe uku saura mintuna biyar. Kodana kwanta bacci ya gagari idona yanayin danaga Umma aciki sai dawo min yakeyi har zuciyata inason nayi tozali da Umma inhar na sanyata cikin idona wallahi ko ranar na koma ga mahaliccina na cika burina. Sanyin da aka fara bushawa na asubahi shiya tashe ni nayi sallah sannan na tada Farida tayi,inta jiwo hayaniyar samarin gidan daga bayan window ɗinmu na tambaya Farida tace min ai a akwai masallaci a cikin gidan sun fito salla ne. Da safiya nafito daga wanka kenan Yasira ta shigo muka gaisa tana gaya min sunyi waya da Granny tana gaishe ni nace ina amsawa nima zan ƙirata dan mun daɗe bamuyi magana ba. Tare da Farida muka fito muka bar Yasira a ɗakin,part ɗin Adda Lawisa muka fara shiga dan shi yafi kusa da namu kamar yanda na lura dacewa al'adar gidanne kullum da safe ake shiga kowani part a ɗebi gaisuwa. Tana zaune da mijinta muka iskesu muka shigo bayan sun mana izini sannan muka bisu da gaisuwa duk suka amsa cikin sakin fuska,mussaman mijinta datun zuwanmu nikam ban gashi cikin gidan ba. "Alhaji ga matar uban namun fa"Adda Lawisa ta faɗa tana masa nuni dani ya ɗago ya sake kallona "Ayya kice matar tsoho ke yanzu kina yariyarki kika yarda kika auri tsoho"ya faɗa cikin barkonci Adda Lawisa ta galla masa harara"ai ba auren dole bane ita ta ga tsohon tace tana so".nayi ƙasa da kaina ina murmushi. Ya miƙe yana cewa Adda Lawisa zai fita,ta kamo hannunsa suka fita tare domin yi masa rakiya amma tace mu jirata. Na taɓo Farida data toshe kunnuwanta da earpiece "mijin Adda Lawisa akwai shi da zolaya" "Ai indai Uncle zaid ne kaɗan ma kika gani,daga shi har ita ɗin haka suke soyayya kuwa ko a gaban waye yinta sukeyi shiyasa kullum Hajiya kecewa basuda kunyar fulani". Nan muka jira dawowar Adda muka ɗan taɓa hira da ita sannan muka wuce part ɗin Adda Hadiza,ciki-ciki ta amsa sallamar damuka shigo da ita tana daga kishingiɗe ƴar aikinta na mata tausa sai ƴar autarta Arfat dake wasa a waya. Muka zauna tare da gaisheta ta amsa fuskar nan babu yabo babu fallasa. "Ke kuma Farida daman su Mima sun faɗa min kin wani manne mata sai kace chewgum duk inda zata kina biye da ita".Farida tayi rau-rau da ido"Adda shi Hamma Habib ɗinne yace naje ina ɗebe mata kewa kinga wannan ne farkon zuwanta batasan kowa ba ba kaman Adda Yasira bace ita ai mun ɗan saba da ita". Tsuke fuska tayi tana haɗe girar sama data ƙasa tace"kewa ko?wannan ce za'a nema sai ɗebe mata kewa ɗiyar data tsallake iyayenta tayi rayuwar ita kaɗai,saboda tana ganin cewa ta isa ta kai.to a wancan lokacin ɗin uban waye yake ɗeba mata kewar?ai ita tasan hanyar da sukebi ire-irenta marasa kamun kai wajen ɗebewa kansu kewa". Zuciyar datake cikin ƙirjina ta duba da mungun ƙarfi yayin da hakan yabama hawayen danake matsewa damar fitowa,meye Adda Hadiza take nufi dani?akan abunda bata da masaniya akansa take jifana da waɗannan munanan zargin?. Farida ce ta soma magana itama tana matso nata ruwan hawayen"Haba Adda dan Allah kuyi haƙuri mana ai abunda ya wuce ƙoƙari ake wajen mantawa dashi sai a gyara gaba".harara ta cilla mata kana ta ɗauke kanta daga garemu. Na miƙe idanuna taf!da ƙwaya nace"Adda a huta lafiya"ina kawowa nan na ɗauki hanyar barin falon Farida data taso zata biyo baya na Adda Hadiza ta dakawa tsawa tare da faɗin"ke kuma ina zakije shashasha dawo ki zauna min anan".ba musu Farida ta koma ta zauna. Kaina ya saramin hawayen danakeyi suka tsananta nazo dai-dai ƙofar fita daga falon naji na bangaje mutum nayi saurin ɗago kaina muka haɗa ido da Aliyu haidar ɗin Adda Hadiza,na ɗauke nawa idon daga cikin nasa Habib ne ke biye dashi shima ya rufo ƙofar ya shigo. Nayi saurin maida kaina ƙasa sannan na fara ƙoƙarin raɓawa ta gefensu zan fita,amon muryarsa danaji sun sauƙa cikin dodon kunnuwana yasani tsayawa cak ba tare dana waigo ba. "Lafiya Hibba wani abunne ya faru?"kaina kawai na jijjiga masa alamar A'a na cigaba da tafiyata. ya kallo Aliyu yana faɗin"bari na bita naji ko menene".har yakai ƙofa Adda Hadiza ta buɗe dukkan muryarta tans faɗin"kar kasake kasa ƙafarka kabar cikin falon nan da sunan binta". Aliyu ne ya fara magana cikin harshen fullaci wanda yafi zaunawa a bakinsa fiye da hausa"Adda kuka fa takeyi ai a kyautu ya bita yaji dalili ko". "To ubana zai kaso ka dukan nace bazai jeba ko"tana kawowa nan a zancenta ta koma mazauninta ta zauna. "Allah yabaki haƙuri"cewar Aliyu suka dawowa sukayi suka zauna cikin falon kawuna a ƙasa. Ɗaki na wuce naci kukana na godewa rabbana,Mimi tazo ƙirana na fito cin abinci.sai da kowa ya hallara kana muka somacin abincin bayan mun kammala Habib yacewa Goggo Hanne yau zamu tafi zamubi jirgin ƙarfe huɗun yamma. "Ubana kace sati ɗaya zakuyi yanzu kuma maiya canza maka ra'ayi?". Yana ɗan sosa ƙeya yana sunkuyar dakai"Goggo wani aiki ne ya tasomin acan ɗin na gaggawa". "To saika barsu matan nakan ai"cewar Adda Salamatu. "Adda ai itama Hibbar tana makaranta kuma hutunsu ya kusa ƙarewa"ya faɗa yana kallon Aliyu wanda shiya kitsa masa hakan.Goggo Hanne tace "Allah ya kaiko lafiya yabada ladan zumunci"tsiraru daga ciki suka amsa da Amin. Muna barin falon muka wuce ɗaki muka fara tattara kayanmu nida Yasira,zuwa ƙarfe biyu kuwa duk muka fito da shirinmu munayi musu bankwana Goggo Hanne tamin ishara da hannunta akan na zo na taho na iso gabanta ta shiga"kowasu iyaye na gari zasu sowa ƴaƴansu samun mataye na gari duk abunda kikaji ko kika gani inason ki barsu anan kar ki tafi dasu a zuciyarki kinji ko?"na ɗaga mata kaina"Madalla"ta furta sannan ta ɗebo wasu liffayu masu kyau da ɗauƙar ido batamu nida Yasira mukayi godiya muka karɓa. Kowa hankalinsa yana ga Yasira mussamman ƴan matan,Adda Lawisa ce kawai tamin fatan sauƙa lafiya sannan ta karɓi lambar wayarta ita da Farida. Khalifa ne ya kaimu airpot tare da Farida dasu Nabiha,dai-dai ƙarfe huɗu kuwa jirginmu ya ɗaga daga nijer zuwa najeria. Muna sauƙa a najeria naji kamar an zaga ƙirjina ana kwashe mini kaso mafi yawa daga cikin damuyoyina,kwana biyu damukayi a nijer har wata ƴar rama nayi ga tinanin Umma daya addabi ruhina,ban samu nutsuwar ƙiran Yaya Fawas mu tattaunaba. Muna sauƙa Malam habu yazo ɗaukar mu muka tafi gida,da Hajja idauna suka farayin tozali ai kuwa nafito na isa gareta muna musayen gaisuwa a tsakaninmu sannan Habib ma ya fito suka gaisa. Yasira dana lura kamar bata da lafiya dan duk jikinta babu kuzari ga ƙafafunta dasuka kumbura tsimtim. Malam Habu ya sauƙo mana da akwatunan mu sannan muka nufi part ɗina gabaɗaya,Yasira ta zauna tana sauƙar da numfashi. Page 5⃣0⃣ Na zauna kusa da ita"Lafiya kuwa ƴar-uwa kodai gajiyace?"ta dafe goshinta idanunta suna lumshe tace"wallahi Anty duk banajin daɗin jiki nane". "Ki tashi kiyi wanka sai ki samu ki kwanta" Ta miƙe muka shiga bedroom ɗina Habib kam daman yana shigowa ya fita zuwa masallaci domin gabatar da sallan magrib.sai dana iddar da sallan isha'i na fito falo naɗan tarkaɗe kujerun da ƙura ya fara sauƙa a jikinsu sannan na wuce kitchen domin ɗaura girki indomie na tafasa mana yana gamowa na juye mana shi a babban plate,sannan na haɗa tea na jeresu a falo na tashi zan koma kitchen na ɗauko cups Habib ya turo ƙofar falon ya shigo sallamar daya shigo da ita ɗauke a bakinsa na amsa ina nufar hanyar kitchen ɗin. Koda na dawo zaune a saman kujera na sameshi yana latsa wayar salularsa"ina Yasiran naga ke kaɗai kike aikin?". "Tana ɗaki batajin daɗin jikintane"ma faɗa yayin danake zama ina rufe bakina kuwa tana fitowa nayi saurin miƙewa na isa gareta saboda tangal-tangal ɗin datakeyi har yanzu tana dafe da kanta. Sai da muka zauna Habib ke tambayarta lafiya?tace kanta ke mata ciwo sai kuma ciwon jiki da kumburin da ƙafafunta sukayi,sannu yayi mata akan cewa gobe in Allah ya kaimu zasuje asibiti. Sosai duk muka maida da hankalinmu ga Yasira muna bata kulawa abincin dataci ma kasa zama yayi a cikinta sai data amar dashi,lokaci ɗaya duk ta galabaita ina riƙe da ita mukayi ɗaki ta kwanta inata jera mata sannu har bacci ya ɗauke ta sauƙar numfashinta kawai nakeji,na gyara mata blanket sannan na fito falo wajen Habib. "Tasama bacci ne?".nace"E ta kwanta"na kai ƙarshen zancena ina nufar gefen TV na ciro wayata daga cajin danasata lokacin dazan shiga kitchen,sannan na zauna ina danna ƙiran Ummi bugun farko ta ɗaga muka gaisa sannan na shaida mata mun dawo,ta cika da murna kuwa dan daman na lura bason zaman mu acan takeyiba. Ina datse ƙiran naji hawaye sun ciko idanuna kewar Umma ya ziyarceni,wayar da mukayi da Ummi sai naji inama ace da UWATA nakeyinsa take bani shawarwari kamar yanda Ummi ke bani,take ƙoƙarin yayemin damuwata kamar Ummi,take ɗaukar duk wani lamari nawa da muhimmamci. "Wifey lafiya kuwa kuka kuma nameye?"Tambayar da Habib ya watsa min wanda hakan ya fargar dani cewa hawayen ya fara zuba min cikin sanyi nace"Umma na tina wallahi zuciyata tana kewarta irin yanda kalaman baki bazasu iya faɗinsa ba,yau da Umma na kusa damu babu wanda zaimun kallon karuwa balle har a zargini akan wata rayuwata"na fashe da kuka har da shiɗewa Habib ya jawoni ƙirjinsa"Hibba dan Allah alfarma ɗaya zan nema a wajenki ki daina saka abu a ranki kinsan fa lalurar dakike tattare da ita,na miki alƙawarin matuƙar Umma na raye a bayan ƙasa kuma acikin wannan duniyar damuke rayu sai na nemo miki ita sai na dawo da ita gareki". Ajiyan zuciya kawai nake sauƙewa kukan na nema cin ƙarfina nace"nagode Allah yasaka maka da mafifin alkhairinka yanda kake ƙoƙarin faranta min Allah ya faranta maka". "Amin debbo am"ya faɗa yana shafo gefen ɓarin fuskana. Mafarkin danayi akan Umma na sanar dashi ya min alƙawarin zai kaini gano dan mu tattauna maganar da Inna da Yaya Fawas.tare dashi muka shiga bedroom dubo Yasira yanayin jikinta yasani cewa ko zata kwana a part ɗina kawai. Ya amince muka kwana tare da ita shima sai wajen ƙarfe biyu kafin ya tafi ɗayan bedroom ɗin ya kwanta,dan bata sama bacci mai tsawo ba sai a wannan lokacin data fara take farkawa. Washe gari kuwa da wuri nagawa duk wani aikin gida nasawa Yasira ruwa tayi wanka sannan mukafi asibiti.muna zuwa muka wuce ofishin wani abokin Habib bayan mun gaisa ya sanar dashi lalurar data kawo mu bayan yayiwa Yasiran wasu tambayoyi tana bashi amsa ya ƙira wata nurse yace amata gwajin fitsari aka masa,suka fita tare sun kai mintuna ashirin kafin Yasira ta dawo office ɗin bayan wasu mintuna nurse ɗin ta kawo result ɗin. Da cikekken nutsuwa yakebin result ɗin daki-daki da kallo yana karantawa ya ƙara fara'ar fuskarsa ya miƙawa Habib hannu sukayi musabaha kana yace"Abokina wannan labarin dazan baka na cancanci tukwuici gaskiya"Habib ya gyara zama"inajinka menene faɗi". "Abunda result ɗinna ya nuna Madam na ɗauki da ƙaramin ciki na tsawo sati huɗu ina kyautata zaton tafiyar da kukayine ya wahalar da ita kasan wasu masu cikin tafiya kaɗan ke wahalar dasu da abun dake cikin cikinsu,sannan cikin inka lura tun daga yanzu ya fara zuwa mata da laulayi sai a kiy....."bai ƙarisa ba sakamakon ƙarƙarfar rungumar da Habib yakai masa. Yana jero godiya ga rabbul samawati,Yasira dake zaune kusana ta ɗaura kanta saman kafaɗata nima na rungume tsam!a jikina hawaye nabin fuska wanda na kasa bambamcewa na farin-cikine kona akasinsa. "Habib kabari dai na ƙarisa ko"cewar likitan Habib ya dawo matsuguninsa ya zauna yana aikin jerawa Yasira sannu wacce tayi ƙasa da kanta sabili da kunya. "A kula da ita sosai sannan kar abarta tanayi aikin ƙarfi kamar ɗaga abu mai nauyi da dai makamantarsu,sannan a kula kar ana ɓata mata rai a lura sosai sannan zan rubuta muku magungunar ƙarin jini sai ku nemesu tana sha dan sunada matuƙar amfani a gareta".ya kawona yana jawo wata farar takarda yafara rubuto magungunan,yana gamawa ya miƙawa Habib ya karɓa tare da ƙarayi masa godiya nima na ɗaura da tawa sannan na riƙo hannun Yasira muka fice. Cikin pharmacy Habib ya wuce yayin damu kuma muka wue idan yayi parking na buɗe mata ta shiga sannan nima na shiga yana dawowa muka tafi gida,tun a mota na ɗaga waya zan sanar da Ummi Habib ya gargaɗeni akan cewa mu bari sai gobe inmuje gidan sai kowa ya sani. Muna isa gida muka wuce part ɗin Yasira har cikin bedroom nakaita tare da tambayarta kotanada buƙatar wani abun tace a'a,Habib neya ɓalla mata magungunan tasha. "Na tayaka murna Habib da Allah ya amshi du'a'ina,na daɗe da sanin kanason ƴaƴa sannan kaima kanason ganin jininka a duniya tun danayi ɓari har yanzu babu labari.sai kuma gashi Allah ya azurtamu dashi Allah ya sauƙeki lafiya".na faɗa ina kai kallona gareta. "Amin Anty kema ina miki addu'ar samun naki".na riƙo hannunta"bari na barki ki huta ko dan Allah inkina buƙatar wani abun ki sanar dani".kanta ya ɗaga min na miƙe nabar ɗakin ina maida ƙofar ɗakin zan rufe Habib ya riƙe na sakar masa na ɗauki hanyar barin falon. "Tsaya muyi magana"ya faɗa yana isowa gareni"Naso dake zan fara samun iyali Hibba naso ace kece wacce zaki fara haifa min ƴaƴa amma hakan ma nagodewa Allah kuma kema ina miki fatan samun naki twins zan baki"ya kai ƙarshe yana kashe min ido ɗaya. Na ciro leɓɓena na ƙasa nace"Hmm Habib wani lokacin abunda muke tsarawa kanmu ba shine alkhairi garemu ba,sanna kuma kaine ma mai bayarwa kenan?". "kinfa gane abunda nake nufi fa wifey". Na ɗan saki murmushi taƙaitacce wanda ya tsaya kan leɓɓana nace"kaje matarka tanada buƙatarka a halin yanzu kadaiji abunda likita ya faɗa".ban bashi damar faɗin komai ba na fice daga falo ƙafafuna har suna harɗewa cikin zanina tsabar saurin dana ɗebo. Ina shiga na wuce bedroom na kwanta hawaye ne suka ciko min idona na kawar dasu,tare da tambayar kaina meke damuna nidai nasan ba hassada nakeyiwa Yasira da Habib akan samun cikin nan ba. Na miƙe nayi alwala na gabatar da sallan zuhr sosai nayiwa Umma addu'a sannan na shafa,na jawo wayata na shiga danna nombar Yaya Fawas bugun farko ya ɗauka muka gaisa cikin hawaye na sanar dashi mafarkin danayi da Umma da kuma irin yanayin dana ganta a ciki. Ba kaɗan ba hankalinsa ya tashi shima sai dai ya danne wajen ganin ya kwantar mini danawa,na sanar dashi zuwa gano dazamuyi shima yace zaizo da haka mukayi sallama. Na shiga kitchen na haɗa mana abincin rana kodana kammala har ƙarfe uku tayi nayi sallan Asr,inata jiran ko Habib zai shigo amma har izuwa wannan lokacin babu shi babu labarinsa. Na fito na shiga sashin Hajja tana zaune tana talgen tuwo na isketa muka gaisa sannan najawo kureja na zauna,na kalleta nayi dariya haɗi da cewa"Hajja inada labari mai daɗi amma sai kin biya fa tukunna". "Faɗi indai baifi ƙarfina ba ai sai nabaki". Na ƙara sakin wata murmushin kana nace"Yasira ce ke ɗauke da ciki ɗazu munje asibiti likita ya tabbatar mana". Sai data rufe tukunyar ta juyo yana fuskanta na kafin tace"Amma wallahi na taya Habib murna ƙwarai Allah ya sauƙeta lafiya"ta numfasa kafin nace wani abun a tsakani ta ɗaura"wohoho amma Hibba kinada wata irinyar farar zuciyar daba kowa yakeda ita ba mussamman a wannan zamanin,ace da bakinki koma da murnarki kike sanar da samun cikin kishiyarki". Na saki wani murmushi mai ciwo"Hajja ban ɗauki Yasira a matsayin kishiya ba hasalima kallon ƴar-uwa ta jini nake mata,Duk wani abunda dazaiyi silar wanzar da farin-ciki a rayuwar Habib inasonshi Hajja bakiga yanda ya ruɗe da murna ba lokacin da likita ke sanar damu tanada juna biyu".na ƙarishe maganar ina sharce ruwan ƙwallen daya taro cikin ƙwayar idona da hannuna. Ta taso tare da tada kafaɗata"Inada kyakykyawar zuciya na tabbatar Allah bazai barki haka ba kema Allah yabaki naki ita kuma Allah ya sauƙeta lafiya"na amsa da Amin ina miƙewa nace"bari naje na dubota kota tashi daman cewanayi bari nazo na faɗa miki wanna kyakykyawan labarin na karɓa tukwuicina". "Ai kuwa kin cancanci tukwuici"na fice ina dariya part ɗin Yasira na nufa muka haɗe da Habib a ƙofar bedroom ya fito daga kitchen hannunsa riƙe da kofin tea na tambaye shi tata tashine yace e nashiga ina mata sannu. Nace abinci ya kammala su fito muci amsar da Habib yabani yaso gigitani dan banyi tsammanin basa. "Ki kawo mana namu anan kawai dan yanda ƙafafunta ya kumbura banajin zata iya takasu". Ban ƙara furta komai ba na miƙe nabaro ɗakin naje na haɗa musu abincin nasa cikin basket na aje musu akan dinning nakoma part ɗina. Abincin na isa a gaba nasa kayin koda spoon ɗaya tun aurena da Habib bamu saba raba kwanon abincin ba,har zuwan Yasira ma tare mukeci yau ce rana ta farko ciki tarihin zaman aurenmu da mukaci abinci daban daban kuma muna cikin gida ɗaya na tashi na kwashe kwanukan nakai kitchen na ajesu raina duk narasa meke min daɗi. Page 5⃣1⃣ Ina dawowa falon na isa ga wayata wacce keta ruri na ɗaga tare da mannata a kunnuwana nayi sallama daga ɗayan bangaren Maryam ta amsa na tambayeta Abbul-khair tace yana lafiya ta bashi wayar yayita min kwaɓar maganarsa da bana gane komai a cikinsa. Muɗan taɓa hira da ita sosai kafin mukayi sallama na ajiyewa wayar nayi alwala domin sallan magrib ban tashi daga kan sallayar ba sai danayi Isha'i.ganin abincin rana ma bamu cinyeshi ba yasa ban ɗaura girki ba na fito na nufi part ɗin Yasira ko yanzu ma Habib na nan yau dai na lura ko office baije ba ko masallaci bai fitaba. Ina zama na sauƙe idanuna akan kulolin abincin rana dana ajiye ko gusar dasu daga inda na aje ba'ayi ba balle nasa rai ko anci na kallo Yasira nace"baku ci abincin bane?"Habib ne ya amsa"wallahi wai bazata iya ciba shigowarki ɗazu tea na haɗa mata shima bata shaba". "Haba!Yasira ta yaya zaki zauna babu ci bayan kinsa yanzu bake ɗaya bace ki daure kici ko kaɗan ne bari na tashi na zubo miki"ko amsar dazata bani ban jiraba na miƙe na zubo mata abincin sannan na tsiyaya mata zoɓon daaa haɗo abincin dashi na dire mata plate ɗin a gabanta.ganin batada niyya yasa na fara bata da kaina a hankali take taunar abincin kamar ranta bayason tana haɗiye spoon na uku dana bata kuwa ta fara kakagin amai. Ta miƙe a harzance tayi bathroom yayin da nida Habib muka rufa mata baya sosai take kwara aman duk ta jigata nayi riƙo da kafaɗarta Habib ya wanke mata fuskarta muka fito kwanciya tayi nan take kuwa baccin wahala yayi gaba da ita nacewa Habib bari na gyara banɗakin tsaf!na tsaftace ko'ina na bulbula turare na fito. Tare muka zauna wajen Yasira raina cike fam!da tausayinsa dan naji ana cewa ciki mai laulayi bashi da daɗin sha'ani balle ita kuma daya fara mata tun da wuri. Har sha ɗayan muna nan ganin bata farka ba yasa nacewa Habib kawai zan kwana tare da ita. Washe gari tun danayi sallan asalatu ban zauna ba,tare da Habib muka haɗa breakfast ya shiga wanka ni danayi nawa wankan na tada Yasira ta shiga tayi ina shirin tafiya gano da zamuyi yau ta fito itama ta shirya dan zamu biya ta wajen Ummi. Ko yanzu ma basa cin komai tayi na lura ko ƙamshin abincin ba wani so takeyi ba dan tunda ta zauna a dinning ɗin hannunta ke rufe da hancinta,da kyar ta iya zuƙar ruwan tea shidai bata amar dashi ba. Mukayiwa Hajja sallama muka tafi muna isa muka isa Ummi tayiwa Daddy rakiya zai fita muka fito muka kwashi gaisuwa nida Yasira mukayi ciki Habib ya tsaya dasu bansan meyake ce masa ba. Tare da Ummi suka shigo kalmar Alhamdulillah yaƙi barin bakinta tun kafin su zauna naji Habib nace"Ummi zamu barta anan zamuje gano tun jiya babu abunda tasa a cikinta dan Allah a matsa mata taci".Ummi ta aika masa da hararar daya sanyashi jin kunya ya sunkuyar dakai yana ɗan sosa ƙeya"tashi mu tafi". Na kamo hannun Yasira nasa cikin nawa kana nace"To ƴar-uwa zamu tafi a kula mana da babyn mu sosai sannan kar a mana huron yunwa dan Allah"na ɗan marairaice murya a ƙarshen zancena. Har jikin mota tayi mana rakiya sai da muka fice daga cikin gidan sannan ta koma ina hangenta ta cikin madubin motar. "Gorko am idan Allah ya sauƙi Yasira lafiya tunda ta kammala karatunta mezai hana a nema mata aiki tunda kaga nima inna gama ba zama zanyi ba aikin zan nema"lokacin mun iso dai-dai hanyar da zata rabomu da cikin katsina nayi maganar ya kalloni fuskar nan fal annushi a shimfiɗe yace"To yanda kika tsara haka za'ayi Matar Aljannah". Na saki murmushin jindaɗi har muka isa cikin gano muna hirarmu gwanin burgewa dai-dai sanda muka nufa unguwar Baffa na ciro wayata daga cikin jakata nace"bari na ƙira naji lafiyar babynmu"yasa dariya"lalle wannan babyn dan gata ne"nayi fari da idanuna nace"sosai ma kuwa ai Allah dai ya kawoshi lafiya".shigowar ƙiran Yaya Fawas cikin wayata yasani katse ƙiran dazan soma na daɗa yace min ya iso nace muna gamu a kusa.A A ƙofar gida na hangi Yaya Fawas na fito da saurina na isa gareshi na ware manyan idanuna nace"Yaya Fawas kaha yanda kayi wani ƙiɓa kuwa ga wani hasken daka ƙarayi". "Haba my cute sai dai in idonkine ba ni bawani ƙiban danayi"Habib ya iso haɗi da cewa"ai dai kuwa kayi ƙiba kodai nima idon nawan ne"muka saki dariya sannan sukayi musabaha suka gaisa nidai na barosu a wajen na shigo cikin gidan tun daga zaure nake jiyo banbamin Inna ina sako kaina ciki kuwa najita na faɗin"Aikin banzan aikin wofi an fake da jinyar da bata taka kara ta karyaba duk an ɓata mana gida da ƙazanta".ina zaro ƙafata na kusayin tuntunɓe da marfin tukunya wanda yasa Inna waigowa"Ah Hibba kuke tafe".na ƙara ware idanuna inabin tsakar gidan da kallo kwanukan wanke-wanke ne jimgim a watse ta ko'ina kai kace sunyi wata baronsu da wanke-wanke ga wasu kayan wankin da aka gibjesu gefe guda wasu an farayi wasu kuwa ko jiƙasu ba aiba.na tattare ƙasan zanina na shigo saboda ruwan dake kwance maƙil a tsakar gidan kamar ayi ƙiyo wanda nake alaƙanta hakan ga fanfon danaga yaketa tsuba shi ɗaya. "Inna lafiya kamar ba mutane acikin gidan?"na faɗa ina ƙarƙaɗe ƙasan zanina.ta taɓe baki tana gyara ɗaurin ɗankwalinta dake neman sulewa daga kanta tace"Wallahi tafiyar kwana uku rak!nayi shine Hajara ta maida gidan nan haka nima ɗazu dawowata Adamu yake sanar dani zuwanmu nace bari na ɗan tattare tsakar gidan". "Bata da lafiya ne?"na kuma jefa mata wani tambayar ta kuma taɓe baki kana tace"wai ba gatacan kwance a ɗaki". Na jinjina kaina sannan na rusuna na gaida Inna ta amsa na kai Mayafi da jakana ɗaki na fito muka hau tattare gidan muka saka komai a matsuguninsa na kama kwankwosona ina faɗin"wash bayana"Inna ta kalloni haɗi da cewa"Sannu sai kizo kiyi sallah ki huta kafin su shigo"na zari buta nayi banɗaki sannan na fito na fara alwalar na kammala saura wanke ƙafar hagu data ragemin Hajara ta fito daga ɗaki tsabar firgicin dana shiga lokaci guda yasani tsakin butan ina ƙara binta da kallo. Dama can ba fara bace amma ta ƙarayin baƙi sosai ga fatan jikinta dayake daddarewa kamar bayan kunkuru duk ta bushe ta ƙare sai idanu da haƙwara. Ko kulani batayi ba tayi abunda yafito da ita ta koma ɗaki,na ƙarisa alwalar na shiga ɗaki jikina har rawar mazari yakeyi. "Inna meyasa ba'a kaita asibiti ta sama kulawar jami'an lafiya ba gaskiya nikam ban taɓa ganin mai irin wannan cutar ba"na faɗa cike da jimami. Cikin halin ko in kula Inna tace"ai daman shi alhaki kwuikuyone kuma ai hausawa sunce sharri ɗan aike ne idan ka aikeshi to sai ya dawo maka ai daman duk wanda yace zai wulaƙanta sunnar ma'aiki ya taɓe wallahi"duk da ban fahimci inda maganganun Inna suka dosaba amma ban sake cewa komai game da maganar ba na tada sallana ita kuma tafita dubo abincin damuka ɗaura. Ina iddarwa najiyo sallamar su Baffa sun shigo Yaya Fawas ya shimfiɗa musu tabarma Inna ta zubo musu abinci tana tambayar Habib cewa ina Sayyid yace yana cikin makaranta. Sannan muna ta zubo mana namu abincin tashigo mana dashi ɗaki,munaci nake sanar da ita ƙaruwar damuka samu na cikin dake jikin Yasira tayi murna sosai muna gamawa kuwa Baffa yayi ƙirana na fito sannan muka fara tattauna abunda ya taramu.sosai Baffa yayi farin-ciki yana ƙarawa da cewa"Daman nima inada ƙudurin zama daku akan hakan lokaci yayi da zaku nemi uwarku domin bahaushe yace ba'a canzawa tuwo suna kai kuma Habib Allah ya maka albarka Allah ya tsare bayanka".duk muka amsa da amin sannan Yaya Fawas ya bashi wasu bayanai akan Umma garinsu da sauran abubuwa. Nidai abunda nasani shine bayan rasuwar Abba,Umma ta ɗaura wani auren bamu taɓa kallon wanda ta aurenba daga ni har yaya Fawas.yace bazai riƙe mata ƴaƴanta ba duk da wanna kalmar ta malam bahaushe dayake cewa maso uwa yaso ɗanta amma Umma ta zaɓeshi sama damu damuka tsaga jikinta muka fito. Wasu hawaye masu matuƙar ƙona suka shiga gangarowa daga idanuwa har izuwa saman tudun kuncina suna sauƙe zuwa wuyana. "Ashsha Hibbatu wannan ai ba abun kuka bane banda abunki ai mafita ake nema"furcin Inna kenanna sauƙe ajiyan numfashi ina cigaba da sauraron Baffa dayake yiwa Habib bayani tiryan-tiryan. "Nidai nawa shawarar itace a fara duba gidajen karuwai da ƴan daudu tukunna ko Allah zaisa a dace a ganota acan"furcin Inna kenan daya tokare mini rai na sanƙare awajen ina ɗago ido muka haɗa da Yaya Fawas na lura shima kukan yakeson yayi na matso gabansa ai kuwa muka saki kukanmu muna tausayin rayuwar da muka taso acikinta. "Ya isa haka my cute angle"ya faɗa yana kawar da hawayen fuskana. Sai dana tsagaita kukan sannan muka fito zamu tafi Habi ke tambayar Yaya Fawas a wacce makaranta yake koyarwa ya sanar dashi. "Sai mu buɗe maka wata ƙaramar makaranta kana kula da ita kaga idan Allah ya kawo mana ƴan dagwai-dagwai sai mukawo makasu kana koyar mana dasu ko?"su biyun suka saki dariya Yaya Fawas yace"Ai kuwa kaga bayan koyar dasu dazanyi hadda toyar masa zan koya musu"suka ƙara tuntsirewa da wata dariyar nidai jinsu kawai nakeyi nayiwa Habib godiya akan makarantar dayace zai ginawa yaya Fawas. Sannan muka tafi sai da muka tsaya a gefen titi Habib ya lallashi ne sannnn muka ɗau hanya muna isa cikin Katsina magariba ta goso kai ya ajiyeni a gidan Ummi sannan ya wuce masallaci.na shiga Ummi na tambayata ya hanya na amsa data da Alhamdulillah sannan na shiga nayi sallah hadda isha'i na haɗa sannan na fito na same Ummi a kitchen na tayata muka gama girkin ban tambayeta ina Yasira ba saboda dana shiga ɗaki nakanga tana bacci. Habib yana dawowa ya fara da tambayar Yasira Ummi tace tana ɗaki tana bacci da kyar tasha tea sannan ta sama wannnn baccin,mukaci abincin Daddy kuwa yayi tafiya damaturu wajen Granny muna gamawa muka fara shirin tafiya na taso Yasira Ummi tamana rakiya muka tafi. A hanya Yasira taga mai saida rake tace tanaso muka tsaya ya sayo mata,ɗaya tasha tace ya isheta tans riƙe da sauran har muka isa gida. Part ɗin Yasira dukkaninmu muka nufa tayi kwanta tayi shirin kwanciya,na haɗa mata fruit sallad takasaci sai da Habib ya karɓa yabashi da kansa sannan tasamo taɗan taɓa kafin ta kwanta. "Tazama bacci muje mu kwanta ko"na faɗa ina miƙewa da mamakina naji yace"kije matar Aljanna zanzo na sameki"tunda naji yace haka ban ƙara gigin cewa komai ba nayi gaba. Bathroom ɗina na wuce na shiga toilet na watsa ruwa na fito narasa abunda kemini rai acikin wannan duniyar ina zaune kar na gama karatun al-qur'anin danakeyi Habib bai shigo ba har ƙarfe sha ɗaya ta gota. Page 5⃣2⃣ Cire rai nayi da dawowarsa duk danasan cewa yau a ɗakina yake yau nayi kwanciyata ina ƙarewa rufin ɗakin kallo naji hawaye fal!a idona. Cikin bacci daya fara zuwar min naji shigowar Habib na ƙara ƙamƙame idanuwa wutar ɗakin ya fara kunnawa haske ya gauraye ɗaki gabaɗaya wanka yafara shiga sannan yayi shirin kwanciya,ya kwanta"nasan idonki biyu ki tashi"nayi burus nacigaba da kwanciyata. "Bata samu bacci bane shiyasa na daɗe"sai a sannan na iya buɗe bakina na furta"Uhmm".zai riƙoni na zame "tun dawowar mu nakeson musama lokaci naƙara baki haƙuri akan abunda ya faru a nijer". Na musguta har yanzu na bashi baya nace"ba komai ya wuce kuma ai tun lokacin da hakan ya faru ka bani haƙuri kuma har raina ban riƙesu ba". Ya shafo goshina"Allah ya miki albarka Matar aljanna". "Gobe Zamu koma makaranta in Allah ya kaimu". "Allah ya kaimu innaga result mai kyau akwai kyauta"na murmusa irin murmushin gefen baki ɗinnan kana nace"Nagode". Haka tsawon wannan daren nakasa sakar jikina hasalima shi yayi kiɗansa kuma ya taka rawarsa,Washe gari na tashi da wuri na gama aikina na cikin gida na tsaftace ko'ina na haɗa mana breakfast sannan nayi shirin tafiya makaranta fitowata daga wanka yayi dai-dai da shigowar Habib ɗakin yana ɗaura maɓallin hannun rigarsa. Mukasa sakarwa juna murmushi na shirya cikin ɗinkin riga da zani na atamfa mai ruwan goro,breakfast ɗin muka sanya cikin basket muka nufa part ɗin Yasira. Basket ɗin dake riƙe a hannunsa yakai kan dinnnig ya ajiye sautin kukan Yasira kunnuwana suka fara jiyomin ƙasa-ƙasa na ƙara ware idanuwa a falo don ganin inda sautin ke fitowa kusan a tare dukkanmu muka nufi ɗakin da ɗan sautinmu har ina ƙoƙarin rigashi shiga. Bathroom na wuce kai tsaye inda kukan ke fitowa tana nan zaune daɓas!a ƙasa tana rero kukanta na saki salati da sallallami na ɗagota ta wanke fuskarta muka fito falo Habib keta jera mata sannu sannan ya wuce ya ɗauko mata magungunanta. Kanta yana kan kafaɗata nace"bari na zubo miki abinci inkinci sai kisha maganin"ta girgiza min kai alamar A'a muka haɗa ido da Habib yada kasa zaune balle tsaye yaje ya zubo mata fanke da miyan danayi a plate. Yana ajiyewa ta miƙe hadda guduta tayi bathroom ta hau kwara amai sai data gama ta fito naje na gyara ɗakin ma gabaɗaya dan komai yayi kaca-kaca,kodana fito suna zaune da Habib yana bata abincin a baki cikin sigar lallami nazo na zaune,har ta cinye sannan na ɓalla mata maganin tasha ta tsura mata ido ta gallo min harara tace"meye kuma?". "Babynmu nake saurara Allah sarki bawan Allah an barshi da yunwa"tasa dariya Habib yace"nima dai abunda nagani kenan".sannan nida mukaci namo abincin muka fito tare muka shiga sashin Hajja sannan muka fita da Habib ya sauƙe ni a makaranta. Tun kafin na ƙarisa cikin department ɗinmu Leema Auwal take fesa min result nawa yayi matuƙar kyau nako cika fam!da murna banƙiba a lokacin na tiƙi rawa abuna sai wajajen ƙarfe uku da rabi na baro cikin makarantar inta tararradin Yasira gashi banyi mana girkin rana ba kuma nasan a halin datake ciki bazata iya taɓuka komai ba,adai-daita na tara na koma gida ina isa na sakarwa kaina shower sannan na ɗauro alwala na fito na cazan shiga zuwa wasu marasa nauyi sannan na tada sallah ko addu'ar kirki banyi ba na fito na shiga part ɗin Yasira. Tana bacci a falon na tattare kwanukan safe nakai kitchen sannan na ɗaura mana na rana yana gamuwa na juyeshi a plate dan sanin danayi Habib bazai dawo da ranaba shiyasa ban sashi cikin girkina ba. Duk yanda nayi ta kafe akan bazataci ba rakenta na jiya ta ɗauko daga cikin fridge tasha,nan na wuni muna hirarmu ƙiran Habib kuwa sau biyar yan shigowa wayata babu abunda yake tambaya face baby da Uwar baby. Nan na haɗa mana dinner sai bayan sallan isha'i Habib ya dawo muka fito muka tarboshi munacin abincin nake sanar dashi sakamakon result ɗinna yayi kuwa matuƙar murna har yana cewa shi zai fara sanar da yaya Fawas wannan labarin. Ranar hira mukayi as one family sai wajen ƙarfe sha biyu sannan na musu sai da safe kasancewar ranar Habib a ɗakinta yake ya rokoni part ɗinna tare damin addu'a kamar yanda ya saba har zai fita na riƙo hannunsa na sakar masa lallaushar murmushi nace"Baban unborn Baby a kwana lafiya"ya maido min da murmushin haɗi da cewa"To matar aljanna abun kuma hadda tsokala"na turo baki nace"babu wani tsokala ai gaskiya ce". "To shikenan my journalist"ya faɗa tare da shafa saman goshina na rakashi da murmushi yayin dayake ficewa daga ɗakin. Kashe gari ina gaban mirrio ina ɗaura ɗan kwalina wayarta dake kan gado kusa da jaka da mayafina ta hau ruri nazo na ɗaga muka gaisa da Maryam ina tambayarta Abbul-khair tace min Bashir ya fita dashi sunje gidan Granny. "Jiya da daddare Habib ya ƙira Bashir yake sanar dashi wai Yasira tana ɗauke da ciki?"na ɗan sunkuyar dakai ina wasa da pattern ɗin daka yiwa ɗinkin doguwar rigar jikina kwalliya dashi nace"E wallahi abubuwa nema suka sha kaina na manta ban sanar dake ba". Inajin yanda ta tsikar da wani siririn tsaki sannan ta cigaba da faɗin"Hibba wallahi ina tausaya miki halin mazan wannnan zamani sao dai addu'a karfa Habib ya canza miki mussamman ma Granny akan wannan cikin dake jikin Yasira".wani zazzafar iska na furzar daga bakina kana nace"Maryam bazan hana Habib da danginsa ruɓaiya soyayyarsu ga Yasira ba mussamman a wannan lokaci domin ku....."ban kai aya ba ta katseni"kedai kawai Allah ya kyauta shine fatan dazamuyi"na murmushi dan nasan cewa ba haka taso ji daga gareni ba sallama mukayi na ajiye wayar na gama shiryawa zan fito daga ɗaki ƙiran Yaya Fawas ya shigo wayata na maƙala wayar a kunnena ina fitowa falo murna ya fara tayani akan result ɗina sannan ya sanar dani cewa sunyi magana da Habib jibi zamuje potiskum akan maganar Umma. Da haka mukayi sallama na fito zani part ɗin Yasira ina tafe inajin gabana namin matsanancin bugu na dafe dai-dai ƙirjina sanda na iso ƙofar part ɗin tare da sauƙe ƙatuwar ajiyan zuciya sannan na murɗa handle ɗin na shiga. Habib ne tsaye yana arranging dinning na ƙarisa gareshi gaishe shi na farayi ya amsa sannan na tsaida idona akan dinning ɗin ina ɗagowa ya kashe mini ido ɗaya sannan ya riƙoni muka dawo falo muka zauna. Naɗan waiga nace"Yasira bata tashi bane?"yace"ta tashi tana wanka ne shine na fito nace yau dai barina haɗa mana breakfast na hutar dake"nayi ƙasa da kaina nace"Ai kuwa nagode daman yanzu Yaya Fawas ya ƙirani yake sanar dani kunyi magana dashi har jibi zamuje potiskum,mungode sosai mijina yanda kake ƙoƙarin dawo min da farin-cikin da nayi nisa dashi Allah ya kyautata maka,Allah ya shiga cikin lamurank.."sauran maganar suka maƙale a maƙoshina saboda kukan daya zomin ba shiri. Sai dayaka ƙara matsoni kana yace"Dukkan abunda na miki acikin wannan duniyar ban biyaki irin halallacin dakika min ba Hibba kinsoni sannan kiso duk wani abunda zai sanyani farin-ciki bazaki taɓa gogewa acikin tarihina ba"ya kai ƙarshe yana share min hawayen dake kai koma bisa tudun kuncina. Yasira ta fito muka gaisha sannan Habib ya zuba mata abinci yabata kamar na jiya taci sosai sannan muma mukaci na mata sallama Habib ya sauƙe ni a makaranta.har ƙarfe biyar sannan na dawo nayi wanka sannan nayi sallan magrib dan an ƙira sai danayi isha'i sannan na shiga part ɗin Yasira tana bacci na isketa na haɗa mana dinner sannan na tada ita tayi wanka na ƙira Habib ya katse ƙiran ya ƙara ƙira na ɗaga haɗi da faɗin"kana inane babynmu fa yunwa yakeji kuma kasan inba kai ka basa ba akwai matsala". "Gani kusa da gida yanzu zaku ganni". "Allah ya dawo mana da daddyn unborn baby cikin aminci"yayi dariya sannan na ajiye wayar baifi mintuna goma sha biyarba ya dawo muka tarboshi kamar kullum sannan mukaci abinci nan yake sanar da Yasira tafiyar da zamuyi jibi zai kaita wajen Ummi kafin mu dawo. Sosai mukayi hira kafin Habib ya rakoni na kwanta,washe gari banje makaranta ba sai ranar da zamu tafi tafiyar safe zamuyi dan zamu tsaya a gano sannan mu wuce azare mu ɗauki yaya Fawas. Wajen Ummi muka ajiye Yasira,Ummi ta ƙarƙafa mini gwiwa sosai kukan danake dakonsa tun daren jiya na ska da ƙarfi nace"Ni wallahi Ummi yanzu ko gawarta ne inaso nagani wallahi".Ta rungumo ni ta haɗa da jikinta tana bubbuga bayana tace"In sha Allahu ma zaku sameta tana raye da yardan Allah"ta ɗagoni ta mana rakiya ita da Sayyid dan mun sameshi a gidan sannan muka ɗauki hanya ƙarfe goma ta gota muka isa cikin kano muka nufa gano. Inna ce a tsakar gidan tana tatan kamo muka shiga ta tarbo mu da fara'arta sannan ta shimfiɗa mana tabarma muka zauna muka fara gaisuwa,Baffa ya fito daga banɗaki shima ya zauna muka gaigaisa. "Allah ya dubi niyyarku kyakykyawa ya baku sa'a ya datar daku ya sada saduwa tsakaninku da wannan baiwar tasa"cewar Baffa a sanyaye na amsa da amin can ƙasan maƙoshina sannan Inna ma ta ɗaura danata sai naji duk jikina yayi sanyi Baffa da Habib suka fita masallaci saboda ƙiran sallan zuhr da'aka farayi kafin su fita Habib yake cewa Inna suna dawowa zamu tafi. Na tashi nayi alwala nayi salla a ɗakin Inna ina daga kan sallayan nace"Inna ni kuwa banda Anty Hajara ba tun shigowar mu".hular sanyin yaran da take saƙawa ta ajiye gefe guda sannan tace"Hajara ai jiki yaƙi daɗi ya rikice sosai ba irin maganin da bamuyi ba amma abu yaci tura,malaman asibiti ma cewa suka mu dawo da ita gida acigaba da mata na gargajiya,ki tashi ma kafin ku tafi kije ki dubata tana ɗakinta". Na miƙe na fito tun kafin nasa kaina cikin ɗaki wani uban wari ya ziyarci ƙofofin hancina,na tura ƙofar tare da zara ƙafafuna ciki tana kwance saman tabarma numfashinta yana fita da ƙarfi sosai duk fatarta ya daddare yayi jajir dashi na tsuguna kusa da shimfiɗar tatan nace"Anty sannu ya jikin?". Runtse idanuta tayi hawaye na gangarowa tayi azamar ɗamƙo hannuna ta riƙe gam!ta fara ƙoƙarin yin magana harshenta ya cika mata baki babu damar yin wata magana duk tinanina zafin ciwo ke sata haka dan duk jikinta ya ɗau mazari ga maganar da takeson furta min babu damar fitarda. Na zame daga tsugunan danaji na zauna nace"Anty kiji shuru basai kinci komai ba Allah ya baki lafiya yasa ya zama kaffara ga zunubanki".idanu ta kafeni dashi har yanzu tana hawaye na zare hannuwa daga nata nace"zamu tafi Allah ya ƙara sauƙi"ina kawowa nan na miƙe tsam nima jikina duk ya ɗau rawa ko me takeson faɗa min ni kuwa Allah masani.na fito dai-dai shigowar Baffa da Habib,Inna ta fito mukayi sallama har zaure ta takomu sannan ta koma muka ɗauki hanyar Azare. Page 5⃣3⃣ Tunda muka hau titi zuciyata da tinanina yake ga Hajara wallahi tausayin halin da idona suka ganta a cikin ya zama babban gurbi cikin ruhina Allah kaɗai yasan azabar datakeji a cikin jikinta gashi bakima ya rufo sai ido kawai. "Lafiya kuwa kike?"Habib ya jefomin tambaya wanda yasani dawowa cikin hayyacina daga tinanin dana faɗa na ɗan musguta nace"lafiya ƙalau kawai yanayin jikin Anty Hajara ne ya tsaya min arai wallahi tanajin jiki". "Allah ya bata lafiya nima inzamu dawo zan tsaya in dubata"na jingina kaina jikin kujerar motar ina fidda numfashi ɗaɗɗaya. Ana ƙiran sallan magrib muka isa cikin garin bauchin yakubu muka ƙira yaya Fawas muka sanar dashi muka masa kwantacen inda muke yazo ya zamemu muna shiga layin gidan dayake farko muka tsaya a ƙofar gidan wasu yaran da bazasu haura shekaru biyar ba suka fito su biyu daga cikin gidan wani matsanancin kaman da na gano a fuskarsu da yaya Fawas yasani tinanin cewa ƙannensa ne wanda suke uba ɗaya dasu. Muka fito daga cikin motar yaran danaji ya ƙira sunansu da Mahmud da Sadiq suka gaishe mu tare da faɗawa jikin yaya Fawas suna masa oyoyo,jagoranci ya mana har izuwa cikin gidan muka zauna a falo yace bari ya ƙira mana mutanan gidan yabi wata ƙofar dake cikin falo ya fito ai kuwa suka dawo da jama'ar gidan a bayansa. Daga ni har Habib suka zame daga kan kujerar damuke zaune muka gaida matar babansa da suka fito tare ta ama fuskarta cike da yalwan fara'a sannan tarin ƙannansa suka shiga gaidani da Habib. "Tsarki ya tabbata ga ubangiji talikai"na faɗa cikin raina tabbas Allah yayiwa dangin yaya Fawas ilhamar kyau gasu farare tas wanke hannu ka taɓa,rabona dasu tun Abba na raye da mukazo ta'aziyyar rasuwar mahaifinsu. Wasu ƙannensa mata suka jani ɗaki nayi sallolin dasuke kaina Wacce tafi ɗayar surutu tace"Anty ko yaushe in yaya Fawas zashi gano sai munje masa zamuje sai yaƙi"na kallota nayi murmushi ina dan jan carbin dake maƙale a yatsata nace"gaskiya Yaya Fawas bai kyauta ba amma kuma ba gashi yanzu nazo ba".natayi saurin cewa"Ai ko lokacin da kikayi ɓarima munso zuwa sai kuma lokacin muna makaranta". "Ke daikam Anisa bazaki barta ta huta ba kincika da surutai"wacce aka ƙira da Anisa ta tsuke fuska tace"Kai Fadila akwai ki da ƙarawa abu gishiri yanzu har wani surutu nayi". Mahaifiyarsu ta shigo ta samemu tace mu fito muci abinci muka fito su Habib ma sun dawo tare mukaci abinci ana raha ana hira. Raba dare mukayi muna hira da ƙannen Yaya Fawas haka nan kawai naji yaran sun shige mini rai sosai bansani ba kodan matuƙar kaman dasukeyi da yaya Fawas ne oho. Washe gari kuwa tun ƙarfe takwas muka gama shirin wucewa Potiskum mukayi sallama da ƙannen yaya Fawas da mahaifiyarsu sannan muka wuce tare da yaya Fawas. Bamu sama isowa potiskum da wuri ba saboda lalacewar da motar tana mana a hanya.Yaya Fawas naga yayi waya da wani sannan kuma muka nufi wata unguwan da ake ƙira da ƘODAWA. Muka faka muka fito muna jiran isowar wannan mutumin dasukayi waya da yaya Fawas wanda bansan wanene ba, zafin ranan da ake bushawa ya dakeni bugun zuciyata ya tsananta sai naga duk garin ya sauya min rabona da garin potiskum tun ranar da Abba ya rasu nabi su Inna izuwa gano. Sallamar da mutumin yazo da ita ta dawo dani hayyacina sukayi musbaha da Habib da kuma Yaya Fawas sannan na gaishe shi ya amsa yayi gaba muna binsa a baya na lura a buge ma yake yana tafiya tana tangaɗi. Wani gida muka shiga mai yalwan jama'a sai da muka shiga na gane inda muzo gidan KARUWAI ne kowa yana sabgar gabansa duk babu mai suturar mutumci a jikinsa.ya nuna mana wani ɗaki yace mu shiga muka shiga wata dattijuwar macece zaune a ɗakin tana daga kishingiɗe tana sauraron radio muka gaishe ta ta amsa a daƙile sannan na zubawa wanda ya shigo damu na mujina. "Allah ya taimake uwarmu maganin kukanmu,ai waɗannan sune baƙin danake gaya miki cewa zasuzo neman magajiya uwar tantirai haj.Juwahir"ta tashi daga kishingiɗewar datayi tace"ina ƴaƴan natan suke a cikinku?".duk mukayi shuru kamar ruwa ya cinye mu Habib ne yayi ƙarfin halin cewa"dukkan mu ƴaƴanta ne dan Allah idan kinada labarin inda ta koma da zama shi muke buƙata". Tun shigowarmu ɗakin na gane matar a kallo ɗaya danayiwa fuskarta,Umma tasha aikena wajenta sai dai a wancan lokacin ba'a wannan gidan take ba nayi mamaki ma dabata shaida muba. "To nidai banace da takamenmen inda ta koma da zama ba dan tunda ta ɗaura aure tabi mijinta suka koma can garin arnan nan a kudu shekara ɗaya daya wuce nasama labarin cewa shi mijin data auren ɗan shan jinine ya rufeta a ɗaki yanata gallaza masa ita kuwa ko wayarta ka ƙira bata shiga.sai haj.Luba mai babban harka tace ta ganota a Lagos tana bara bakin danger wannan shine abunda nadanasi ko nace labarin danaji akanta". Kusan suma nayi a inda nake zaune a cikin ɗakin da wari tabar sigari ya gauraye ko'ina Yaya Fawas ya shaƙo kwalarta idanunsa sun firfito yace"Wallahi ƙarya kikeyi wallahi ƙaryane ba Umma bace aka baki wannan labarin akanta". Habib da wannan matashin daya shigo damune sukayi nasarar ɓamɓare hannun yaya Fawas daga jikinta. Da rarrafe na matso kusa dashi na ɗaura kaina dayake sarawa akan cinyarsa ina kuka haka nan ma shima kukan yakeyi. "A'a nifa bazaku maida min da gida kamar na mutuwa ba tunda na sanar daku abunda nasani ma ban siraba to ku fice min daga gida banda ikon jalla ma ta yaya za'ace wai Juwahir ne ta haifa waɗannan ƴaƴan masu nutsuwa da kamewa Allah ne kaɗai yasan adadin yawan ƴaƴa matan da Juwahir tayi silar rabo su da gidan iyayensu ta jefasu a rayuwar bariki Mahaifiyarku tun a nan gidan duniya sai ta fuskanta abunda ta shuka sai tayi mutuwar da ko uwar data haifeta ne bazata shaida ta ba".Furcin Ladi ƴar caras zuciyata ta buga da matuƙar ƙarfi naji ƙirjina kamar an ajiye min wani abu mai nauyin gaske. Yaya Fawas ne ya riƙo hannuna muka fice daga ɗaki ina laɓe lamau a jikinsa duk jikina ya sake,Habib yana biye damu a baya. "Bari naje na karɓi kuɗin sallama na ai ba aikin banzan na muku ba"cewar wannan matashin ya kai ƙarshe yana ficewa daga ɗakin ya biyo mu a baya. Bayan motan na shiga na kwanta akan kujerar ina sauraran yanda bugun zuciyata ke tashi.A jikin motar suka tsaya Habib yace"Bawan Allah yaya sunanka".yaja da baya yana binsa da wani kallo da riƙiɗaɗɗun idanunsa da ƙwaya tasa suka canza launi yace"Sunana Lawan bani kuɗina kawai na wuce". "Bazan baka ba domin kona baka nasan ƙwayoyi zaka saya dasu,meyasa kana matashi mai jini a jika wanda yanzu ne lokacin daya kamata ka nutsu wajen gina rayuwarka ta inganta sai kuma ka bige da shaye-shaye kanada iyaye shin bakason suyi alfahari da kai koda na rana ɗaya ne a matsayin ɗa na gari a garesu?". Tabar sigarin dayake zuƙa ya cire daga bakinsa yana tsaida idanunsa akan Habib kana yace"Iyaye?iyaye fa kace,iyayen da tun ina cikin zanin goyo suka yar dani akan titi babu tausayi balle tinanin rayuwa ko mutuwata,tun lokacin dana buɗi ido naganni acikin wannan gidan kuma wannan matar ta zame mini uwa wallahi tun lokacin da naji mutane na faɗar ta yanda aka sameni an jefar dani a wulaƙance ina kuka naji ban ƙaunar ganin iyayena ko kaɗan"Hawayen dasuka fara taruwa a idonsa ya kawar"bani kuɗina kawai malam na wuce". Buɗe motar Habib yayi ya cire masa kuɗin ya basa tare da complementary card ɗinsa yace duk sanda ya shiga katsina ya nemesa sannan muka tafi. Tunda na ɗaura haƙarƙarina na kwanta ban sake sanin inda kaina yake ba,dan jinayi bana fahimtar duk zance dasukeyi haka nan idanunsa basa ganu min komai sai duhu bakina yayi nauyi bana iya furta koda kalma ce. Sai buɗe ido nayi na ganni a gadon asibiti Habib na zaune gefen gadon ya dafe goshinsa da alama dai tinani yakeyi,Yaya Fawas kuwa yana tsaye jikin window yana jeƙan wajen.kaina ya sara da ƙarfi nayi ƙoƙari haɗa kalmomin bakina nace"Ummaa". Hakan yasa duk suka nufo ni suna min sannu gani Yaya Fawas ya sani sakin kuka"Wallahi Yaya Fawas nikam na yafewa Umma in tana raye a duniya zan cigaba da addu'ar Allah ya sada fuskokinmu da alheri inkuma bata raye zan cigaba da nema mata gafara wajen Allah". "Kiyi shuru ya isa haka my cute angle kinga ba isheshshen lafiyace dake ba" Na kuwa yi shurun ina zuƙar majinar kukan daya zo min,suka fita zuwa masallaci domin gabatar da sallan zuhr nurse ta shigo ta cire min robar ruwan da aka samin domin ya ƙare na shiga cikin banɗaki dake cikin ɗakin nayi alwala na fito nayi sallah. Zuwa yamma aka sallame mu Habib yace zamu kwana sai gobe mu wuce dan har ya kama mana ɗaki a GOLLAKA HOTEL ,na dade akan sai mun koma bauchi a ranar dan bana ƙaunar na ƙara koda minti talatine a cikin garin potiskum. Haka muka ɗauki hanya zuwa ƙarfe tara muka isa cikin bauchi daman Yaya Fawas ya ƙira ya sanar dasu dawowarmu,suna zazzaune a falo muka shigo fuskata duk ta kumbura mahaifiyarsu kawai na gaida na miƙe zan shige ɗaki ko takan Anisa wacce take min tayin abinci banbi ba nayi shigewata zasu biyoni Habib yace suyi haƙuri su barni sai zuwa anjima. Wanka kawai nayi nazo nayi sallah ina iddarwa na ɗaga hannayena sama" ya Allah kaine mai karɓan addu'a to ya Allah ga baiwarka can bamusan halin da take cikiba wataƙil tana raye ko tana cikin matattu duk bamu sani ba,ya Allah aduk inda take kasa tana cikin aminci ka kareta da kariyarta ka rabata da dukkanin abin ƙi"na shafe addu'ar yayin da wani kukan ya suɓɓuce min har na kwanta wayata tahau ruri banida buƙatar yin magana da kowa a halin yanzu dan haka nama kasheta gabaɗaya. Washe gari tun asuba su Anisa dasu Mahmud suka shigomin ina haɗa kayana Mahmud yace zai bimu yanata rikice har muka fito tafiya bayan munyi karin kumallo mahaifiyarsu tamin nasiha sosai mai ratsa jikin dan daren jiya Yaya Fawas ya sanar daita abunda da muka riska acikin potiskum. Habib ya bata kuɗin da ban tsaya ganin yawansu ba tayita zubo masa godiya haɗin da shi mana albarka sannan mukayi sallama dasu muka tafi sundai min alƙwarin kawo min ziyara da zaran sunyi hutun makaranta. Har muka iso cikin katsina banida wani kuzari a jikina gidan Ummi muka fara nufa muka ɗauko Yasira a nan ma Ummi itama tamin nasiha sosai hadda Daddy dan shima mun sameshi ya dawo a lokacin. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 5⃣4⃣ Muna isa gida na wuce part ɗina nayi wanka na fito falo don neman abunda zansa acikin cikina su Habib da Yasira ma suka shigo lokacin danake wanka inajiyo tattaunawar dasuka tsaya yi da Yasira akan Umma shawarar dasuka yanke tamin dai-dai nacewa zasuna zuwa da yaya Fawas da Sayyid kawai potiskum ɗin duk sanda suka ƙara samun wani labarin akan Umma. Kallo ɗaya na musu na ɗauke kaina nayi kitchen nafara ƙoƙarin kunna gas,har na kusa sauƙar da tean dana ɗaura Yasira ta shigo da tulelen cikinta a gaba sosai cikin ya bayyana duk da cewa watanni uku ne amma ga wanda bai sani ba sai yace yakai wata bakwai. "Anty yanzu Hamma yake sanar dani har kin kwanta a asibiti dan Allah ki cire komai daga cikin ranki ki miƙa dukkan lamuranki zuwa ga Allah"Furcin Yasira kenan danaji sun ƙara karyar min da zuciya na daɗe inajin irin wannan maganar daba bakin mutane da yawa kowa haka yake faɗa min"haƙuri-haƙuri"ita na runguma badan itaba da yanzu banzo inda nake ba. "Yasira na daɗe da yakice komi daga raina amma Umma kam banajin zan iya hana zuciyata tinaninta a kowani daƙiƙa"na kai ƙarshen zancena ina sauƙar da tukunyar shayin dana ɗaura domin ta daɗe tana tafasa. Sai data kalloni da idanunta waɗanda suke bayyanar da zallar tausayina a shimfiɗe acikinsu kana tace"in sha Allah,Allah zai bayyana mana ita cikin aminci".nakai hannu na kawar da ruwan hawayen dasuka ciko mini kwaryan ido nace"Amin". Tacs ruwan shayin nayi sannan na tambaye Yasira abunda zataci domin na samar mata dashi tace taci a gidan Ummi tea ɗin kawai ya ishe ta. A jere muka dawo falo muka zauna bayan na kunna mana kayan kallo,muka fara shan tea ɗin.wani lumshe idano Yasira tayi tana sakin hamma kafin tace"wallahi Anty bacci nakeji cikin nan yana sani bacci sosai". Nakai dubana gareta tabbas cikin nan na wahalar da ita matuƙar ga duk ƙafafunta sun kumbura kamar lale-kabo nace"to ai kuwa ya kamata kije ki kwanta kafin a ƙira sallah"ta fara ƙoƙarin miƙewa ta ɗauki hanyar bathroom ɗina har ta kusa shiga Habib ya fito daga ɗakinsa suka sakarwa juna murmushi sannan ta shige shi kuma ya iso ya zauna. Banji isowarsa cikin falonba balle zama gab dani da yayi sai jin muryarsa danaji kamar a tsakiyar kaina yana faɗin"Hibba damuwa bashine mafita akan wannan lamarin daya same muba addu'a da miƙa wuya ga Allahn daya ƙaddarta mana hakan shine mafita".na sauƙe nauyayyen ajiyan zuciya hawaye suka ciko idanuwa ya fara share mini su"Hibba ki ƙara haƙuri in sha Allah komai ya kusa zuwa ƙarshe da iznin Allah"jijjida kaina kawai nayi alamar naji haka yayita bani baki da aikin lallashina yaya Fawas ya ƙirani sosai ya ringa kwantar min da hankali harsu Anisa ya bawa muka gaisa kafin mukayi sallama. Ranan Habib a ɗakina yake Yasira ta kwana a part ɗinmu a ɗayan ɗakin. Washe gari tun dana tashi asuba ban zauna ba sai dana gama haɗa mana breakfast nayi shirin tafiya makaranta,har muka fito falo da Habib banga koda kulgawar Yasira ba hakan yasa duk muka ɗunguma izuwa ɗakin,tana ta sharar baccinta hankali kwance muka isketa na wuce toilet na haɗa mata ruwan wanka nasamo Habib har ya tasheta maganganun danaji yana mata yasa naji ba daɗi faɗa yake mata akan tabarni inata aiki ni kaɗai tana nan tana bacci. Ta tashi ta shiga wanka sannan muka dawo falo jiran fitowarta cikin mintunan da basu gaza ashirin ba ta fito mukayi breakfast sannan nayiwa Yasira sallama muka fita da Habib zai sauƙeni a makaranta. "Hamma wai ni meye amfanin tawa motar indai kullum kai zakana kaini kuma ka ɗaukoni gashi kuma har koya min kasa anyi"na faɗa yayin dana ke tsaida da ƙwayar idona akan fuskarsa datake cike da yalwar annuri shimfiɗe ta ko'ina. "Zaiyi amfani ranar da bana kusa amma yanzu danake tare dake nizan kaiki kuma na ɗauko abata"yakai ƙarshen maganar yana buɗe min ƙofar motar nasa kai na shiga ina dariyar maganarsa.shima ya zagayo ya shiga sannan ya data motar muka fita. A hanya yake sanar dani sunyi magana da Ummi za'a samo min mai aiki dan aikin yafara mim yawa tunda Yasira tayi nauyi bata iya yin komai ga kuma fita makarantar danakeyi. "Allah sarki Ummina ako yaushe mai tausayinace,Allah ya saka miki da alkhairi". "Amin"na amsa dashi nayi saurin juyowa ina kallonsa dan ni a tinanina a zuci nayi maganar ya ɗan murmusa yana maida kallonsa kam titi yace"gobe za'a kawota ki ganta".nace "Allah ya kaimu". Haka muka isa cikin makarantar muna hirarmu gwanin burgewa har department ɗinmu ya rakoni duk wanda ya gannu zai tabbatar da babu abunda yake damun ranmu illar gangariyar soyayyar da muke gwadawa junanmu.sai da suka gaisa da Limat Auwal sannan mukayi sallama ya tafi. Ƙarfe biyar saura muka gama lectures,yazo ya ɗaukeni a hanya muka sayi kaza da youthgut muka tafi gida.shi mukaci muka kwanta. Washe gari ranar banida lectures sai ƙarfe biyu dan haka ina gama aikina nayi kwanciyata tun munayin breakfast Ummi ta ƙira Habib take sanar dashi an kawo ƴar aikin Sayyid zai kawota,dalilin hakan yasa shima ya zauna a gida bai fita office ba. Cikin baccin danakeyi naji Yasira na tashi na tana ƙiran sunana a hankali,nayi wata shegiyar miƙa na tashi zaune. "Anty kifito Yaya Sayyid sun zo da ƴar aikin".kaina na ɗaga mata ta fice daga ɗakin ina biye da ita a baya ina faman mirtsike idanuna da bacci yaci ƙarfinsu. Turus naja na tsaya ƙafafuna suka shiga karkarwa jin zan iya sulalewa a kowani lokaci yasa na jingina bayana da jikin wall ɗin falon ina ware idanuwa akan ƴar aikin da Ummi ta turo cikin son tabbatar da hashashen zuciyana. Tan durƙushe a ƙasa kusa da kujaran da Yasira takw zaune akai kanta na kallon ƙasa amma hakan bai hana ni kallon fuskarta ba,rabul ɗin idanunta sunyi baƙin dasu alamar taci kuka mai isharsa kafin zuwa yanzu,ta ƙara baƙancewa ta bushe sosai daga sanin danayi mata ada. Bakina yana mungun karkarwa har ana iya jiyo yanda haƙwarana suke gogan juna,kar-kar sautin dasuke badawa kenan"Balabara"kalmar da nayi nasarar furtawa kenan ina sulale ƙasa na zauna daɓas!ina hawaye. Sai a sannan ta ɗago idanunta ta miƙe zumbul lokacin da ƙwayar idanunmu suka gwauraye cikinna juna,ta shiga nunoni da yatsa"Hibba"ta faɗa tana fashewa da wani matsanancin kuka. Yasirace tayo kaina tare da tambayata lafiya,ban iya bata amsa ba sai sautin kukana daya karaɗe ilahirin falon dan da iya ƙarfina nake fidda shi. "Na gaskata wannan magana ta masu iya magana dasukace alhaki kwoikwoyone kanan sharri ɗan aikene duk yanda yayi nisan kiwo sai ya dawo ga mai shi,Hibba yau kece a cikin wannan daular wacce naso ƙasƙantawa na wulaƙanta na bita da sharri har illataki nayi ta hanyar kwara miki ruwan zafi akan laifin da bakiji ba baki gani ba.tabbas hakkinki keda Amina bazai barmu mu rayu cikin sa'a ba,Kabir ya lalata rayuwarsa da baƙin cikinsa malam ya rasu yanda na ganshi turmi da tabarya da ƴar maƙwantanmu mai shekara sha biyu Allah ya nuna min annabi.son raina yasa na ɓoye faruwar hakan har sai lokacin daya fara nemana yanzu yana can ya haukace sakamakon shaye-shaye banida komai banida kowa sai Allah naga taskon rayuwa abincin bakina ma yana gagarana wani lokacin Kabir ya lakaɗa min ɗan banzan duka sai dai maƙota su shigo su kwaceni". Takai ƙarshe tana ƙara fashewa da wani sabon kukan,bani ba hatta Yasira da Sayyid sai da suka koka mata inganin sandan Habib ma yake yarshe nashi hawayen.miƙewa nayi jiri na ɗibata na isa gareta muka rungume juna"Hibba ki yafe min,ki yafe min ko Allah zai sausauta min halin rayuwar danake ciki". Sai dana haɗiye kukan dayake shirin suɓɓuce min kana nace"na yafe miki Anty Balaraba ban taɓa riƙeki a raina ba". "Nagode Allah ya saka miki da allahairi"ta faɗa tana ƙara riƙon datamin a jikinta,na ɗago kaina tare da riƙon hannunta muka ƙariso tsakiyar falon inda su Sayyid ke tsaye nace"Habib wannan itace kishiyar Anty Amina mahaifiyar Kabir,su suka fara bani taimakon farkon shigowata katsina suka bani matsuguni acikin gidansu bazan taɓa mantawa dasuba a tarihin rayuwata"na fashe da wani kukan zuciyata na tino mini irin rayuwar danayi tare dasu na ƙunci da wahala. "Tsarki ya tabbata ga ubangijin talikai,wanda ya tsara faruwa komai tabbas Allah baya bari hakkin wani mussamman wanda aka zalunta". Muryar Sayyid kenan dana tsinkayo sun bugi dodon kunnuwana,muka zazzauna sannnn Habib ya fara nashi jawabin"Duk abunda ya faru ya wuce sai dai muyi fatan Allah ya tsare na gaba ya kuma rabamu da mummunan ƙaddara.yanzu Kabir ɗin yana ina?". Cikin kukan daya gama cin ƙarfinta tace"yana nan acikin unguwa yanabin bola". Nan wajen Sayyid ya ƙira Ummi ya sanar da ita ta kuwa cika da al'ajabi,Yasira ta kawo mata abinci taci sai da nutsuwarta ya dai-daita sannan Habib yace muje unguwartasu ganin Kabir da farko na nuna bazani ba amma daga baya na shirya mukaje hadda Yasira. Unguwarsu tada tun can baya itace basu canza ba,muna isa ƙofar gidan naji wani kuka ya zomin ranar farko da Anty Amina ta kawoni gidan ya dawo min cikin kwakwalwata da kuma tarin abubuwan dana riska cikin gidan. Wasu samari akasa suka kamo Kabir suka kawoshi inda muke sai fizge-fizge yakeyi,hauka tuburan babu kama hannun yaro.aka sashi cikin motar da Sayyid yazo da ita. "In sha Allah zanyi duk mai yiyuwa wajen ganin ya sama lafiya,ga wannan ki riƙe a hannunki sannan duk lokacin da kikeda buƙatar wani abun zaiki iya zuwa gida ki sanar dani"ya ƙarsihe yann miƙa mata bendir ɗin kuɗi ƴan dubu-dubun daya ciro daga aljihunsa. Hannunta na rawa ta karɓa tana ƙara fashewa da wani kukan har shiɗewa takeyi,yau Hibbace a gabanta wacce taso ƙasƙantarwa ta tozartata yau ita ta zame mana gata kuma majingina,wacce ta ɗaurawa tsana da ƙiyayya babu laifin tsaye balle na zaune yau itace ta zamto mata mai share hawaye a gareta. "Allah kenan me yanda yaso". Kalmar data furta kenan tana ƙara neman yafiyata a karo ba adadi,na ƙara jaddada mata na yafe mata sannan muka tafi akan Sayyid zai kawo mata saƙo. Dukkanmu gidan Ummi muka nufa muka ƙara sanar da ita abun daya faru da kuma Kabir da za'akai asibit domin duba lafiyar ƙwaƙwalwarsa. "Hibba kinga lamarin Allah ko,tabbas alƙawarin Allah tabbatacceni duk wanda ya rungumi haƙuri haƙiƙa ya rungumi babban nasara a rayuwa yau dalilin haƙurinki ya jawo miki ɗaukaka". Furcin Ummi kenan sannan ta ɗaura da nasiha a garemu tare da buga misali da rayuwata,anan muka wuni Habib da Sayyid kuwa tun zuwarmu suka fita wani asibitin kuɗi aka kai Kabir domin duba lafiyarsa.komai Habib ne ya ɗauki nauyinsa likitan ya musu hanya aka fita dashi Cairo. Har gida Balaraba tazo ta ƙarayiwa Ummi da Habib godiya,ranan dana ƙira Anty Amina nake sanar da ita ba ƙaramin kuka tayiba domin komai rashin imanin mutum yaga rayuwar da Balaraba takeyi sai ya zubar mata da kwalla. Bazan taɓa manta wannan ranar ba a kaf!cikin rayuwata muna zaune da Yasira a part ɗin mum gama lissafin watannin cikinta kenan wata bakwai da sati biyu,ta tashi ta shiga bedroom ɗinma zatayi sallah.ganin ta daɗe bata fito ba yasa nabi bayanta tana zaune a cikin toilet ɗin tun shigowata nakejiyo nishinta. Na saki salati ganin jinin dayake bin ƙafafunta na rarumota jikina muka fito ɗaki,ɗamƙo hannuna tayi tasa cikin nata zuffa na tsatstsafo daga kowani sassan jikinta"Anty cikin nan bazan haife shi ba mutuwa zanyi, ki yafe min inna taɓa ɓata miki acikin zamanmu ki roƙa min Ummi itama ta yafe min Hamm......"bata ƙarisa ba sakamakon numshinta data jawo da ƙarfi sai kuma ta sake dukkan jikinta. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 5⃣5⃣ Kuka nasaka mai matuƙar sauti na gama ruɗewa na fara jijjita ina faɗin"Yasira ki tashi dan Allah kar kimin haka ki buɗe idanunki ki kalle ni".shine abunda naketa maimaitawa kafin na miƙe kamar an tsira mini wani abun na koma falo na ciro wayata dake caji nashiga dannawa Habib ƙira,ƙiran farko bai ɗagaba sai a ta biyu ya ɗaga. "Hamma dan Allah kazo gida Yasirace ke naƙuda ka hanzanta"ban jira abunda zai ceba na zame wayar daga kunnewa na ruga ɗakin da duguna na rungumota jikina jini duk ya malale ɗakin,kuka nakeyi sosai naji an buɗo ƙofar ɗakin an shigo na miƙe kuwa da saurina a zatona Habib ne. Hajja ce ta shigo shaf!na manta da zamanta acikin gidan,na isa gareta da saurina"Hajja ki duba min Yasira ta daina motsi". "Yanzu Habib ya ƙira Malam yake sanar dashi wai nazo na dubata shima yana hanya yaƙiraki bakya ɗagawa"ta faɗa muna ƙarisowa cikin ɗakin. Ɗaukarta mukayi muka kwantar akan gado Hajja ta fara danna cikin a hankali,ina zaune gefe babu abunda nakeyi sai ƙwalla, jikina ya ɗauki rawa kamar ana jona mini wutar lantarki. Ƙaran shigowar motar Habib yasa Hajja cewa mu fito da ita kawai akaita asibiti,muka fito da ita a ƙofar shigowa falo mukayi kicibus da Habib duk muka mufa inda yayi parking muka saka a motar muka nufa asibit hadda Hajja. Har muka isa asibitin bata motsa ko ƴar yatsanta ba balle musa rai da zata buɗe idanunta,muna isa nurses suka ɗauko gado suka ɗaurata akai aka shiga da ita emergency. Innalillahi wa'inna alaihirraji'un"na furta can ƙasan maƙoshina haka daman ake haihuwa?kowacce mace sai data ɗanɗana wannna azabar ta naƙuda?,koki sauƙa lafiya koki sauƙa a lahira.wallahi sai naji wani sabon ƙaunar Umma ya ƙara dasuwa cikin rai da ruhina.indai sai data ɗanɗana wannan azabar ta haihomu ta cancanci komai daga garemu.nishin naƙudarma kaɗai wani abune haka muka tsaga jikinta muka fito kowa na mata san barka bayan mum rayu tsawon wata tara acikin mahaifanta ta jure nauyin ciki ajikinta ta cigaba da ɗauniya damu batare da nuna gazawa ba tabbas uwa ta cancanci dukkan sadaukarwa. Fitowar likitan daga emergency room ɗin yasani kawar da wannan tinanin na bada hankalina ga abunda yake faɗin. "Ta zubar da jini sosai tana buƙatar jini sannan kuma bazata iya haihuwa da kanta ba dole sai an mata CS dan abunda yake cikinta baya motsi zaka bini office domin kasa hannun akan takardun". "A ɗauki nawa jinin asa mata"abunda bakina yayi gaggawan faɗa kenan. Likitan ya kalloni"bamu fiye ɗaukar jinin mace ba amma kije lab a gwara inyayi dai-dai danata tukunna". Nabi bayan nurse ɗin muka nufa lap Habib kuma suka wuce office da likitan,jininmu yayi dai-dai aka ɗauki leda ɗaya daga jinina sauran ukun kuwa aka saya dan,Habib a jininsu baizo ɗaya ba. Har ancike takardan cs ɗin daza amata za'a shiga da ita Habib yace zaije ya sanar da su Ummi,Hajja tace ya bari sai ta haihu lafiya tukunna kar ya tada musu da hankali. Muna zaune aka fito da ita an sanya mata kayan tiyata a jikinta,hadda hula jikin da ledar jinin aka shiga da ita.na saki kuka mai ƙarfi sai da duk mutanen wajen hankulansu ya dawo gareni. "Hibba ba kuka take buƙata a yanzu ba addu'armu tafi buƙata shi zamu mata".kwantar da kaina kawai nayi a ƙirjinsa ina fidda hawaye shima ɗin ƙarfin haline kawai. Mintuna goma a tsakani nurse ɗin ta fito da sarsarfa ta iso garemu tana faɗin"Ta sauƙa tun kafin ayi cs ɗin ta sama baby girl".bansan sanda na miƙe na rungumota jikinaba ina hamdala.Habib kuwa hadda sujudul shukr Hajja tace"kaga yanzu sai ka sanar dasu ƴarsu ta haihu lafiya". Ya dannawa Sayyid ƙira ya sanar dashi sannan ya ƙira Granny itama ya faɗa mata,murna gurin Ummi da Granny ba'a magana,ta shirya Sayyid zai kawota asibitin. Muna Zaune aka fito da Yasira aka wuce da ita ɗakin hutu,ita kuwa babyn suka shiryata suka miƙo min ita,tsam!na rungumeta a jikina ina sakin ajiyan zuciya.nurse ɗin ta koma fitowa tace"Hibba da Habib su shiga tanason ganinku". Har rige-rigen shiga mukeyi tana kwance tana ƙarewa ceiling ɗin ɗakin kallo,har yanzu ledar jinin na jikinta. Kusa da ita na zauna Habib kuwa yaja kujera ya zauna kusan gadon,babyn na miƙa mata ta karɓa tana ƙarewa fuskarta kallo. "Anty ga amanar wannan yarinya zan baki,ki tarbiyartar da ita tamkar ƴar dakika haifa a cikinki nima muka fatan zaman lafiya mai ɗaurewa keda Hamma.Hamma ga ƴata nan kazama shaida na mallakawa Hibba ita ko Ummi ban yarda abata ita ba". "Haba ƴar-uwa wannan wani irin magana ne in sha Allah babu abunda zai faru"na faɗa ina karɓan babyn daga hannunta. Riƙo hannunta Habib yayi yana murzawa a hankali yana faɗin"Babu abunda zai faru Allah ya baki lafiya ita kuma Allah ya raya mana ita". Jijjina kanta kawai tayi tace"Ruwa Hamma"ya miƙe domin ɗauko mata ruwan wayarsa da tafa ringing ya ɗaga,na ɗauki goran ruwan na ɓalle murfinsa na fara bata a baki.a hankali take sha ni kuwa duk hankalina yana kan babyn da tun ɗazu take baccinta. Gani naji ta fara dawo da ruwan baya wucewa idanunta sun kafe wajen guda ta tsaya cak!. "Yasira!Yasira!!"na faɗa ina ɗan taɓo kafaɗarta ai kuwa sakake ta zame daga kishingiɗewar da tayi.na ɗago hannunta ya sake lamau,nayi jarumtar kai hannuna dai-dai ƙirjinta naji baya bugawa. Ihu na kurma salati yana biye dashi Habib ya ƙariso ciki da hanzari ,babyn danake ƙoƙarin saketa ya fara karɓa.hannuna na rawa na masa nuni da Yasira"Hamma bata motsi ta tafi ta barmu". Shima bugun zuciyarta ya fara taɓawa yaji shuru"Hamma ta mutu ko dan Allah karkace min ta mutu".na faɗa ina ƙara ƙarfin kukan danakeyi wanda yasa Hajja da nurse ɗin shigowa.Hajja ta riƙeni dan a lokacin ƙafafuna suna barazanar kasa ɗaukata. Nurse ɗin tace mu fito mukafito muka zauna a waje,sannan taje ta sanar da likitan suka dawo tare mintuna biyu a tsakani likitan ya fito duk muka isa gareshi. Dafa ƙafadun Habib yayi"Abokina sai haƙuri Allah ya mata rasuwa ta koma ga mahaliccinta"yana kawowa nan yabar wajen yayin da nurse ɗin ta rufa masa baya. "Waye ya rasu?"sautin muryan Ummi kenan daya sa dukkaninmu juyowa muka zubawa hanyar shigowa wall ɗin idanu,nan take naji zuciyata ta karaya nakasa gaskata maganar likitan wai ƴar-uwace ta rasu?. Saurin isa gare Ummi nayi na faɗa jikinta ina sakin wani razanannen kuka a cunkushe,ta ɗago ni"Ke Hibba menene na kuka kuma bayan ta sauƙa lafiya,muje na ganta".har tayi gaba na riƙo hannunta ta fizge taje ta karɓa yarinyar dake hannun Hajja tana jijjigata. Habib ya iso gareta tare da ɗaura kansa kan ƙafadarta"Ummi Allahn dayafimu son Yasira ya karɓa abunsa". Hawaye kawai idanunta yake fitarwa tunda ya faɗa mata bata ƙara wani ƙwaƙwaran,motsi ba haka nan ta rungume yarinyar tsam!a jikinta.a duk sanda naji sautin kukan yarinya sai anji kamar ana sukan raina da mashi amanar Yasira ce a gareni wannan yarinyar. Sayyid kam nan inda yake tsaye ya durƙushe ya haɗa kai da gwiwa,yana nashi kukan na rashin ƴar-uwarsa ɗaya tal!a duniya.Hajja ce ta fara lura da yanayin Ummi akayi saurin sanar da doctor ya dubata yace jininta ne ya hau aka bata gado. Habib yake sanar da Granny lokacin daya ƙirata inaji,tana faɗa masa gobe zasu ɗauko hanyar katsina ganin jaririya da uwarta,sanda ya sanar da ita kuwa Allah kaɗai yasan irin tashin hankali da kaɗuwar data shiga.Haka nan ma Daddy shikam tunin ya biyo jirgin ƙarfe huɗu ya taho. Tun zuwarshi Sayyid yake faɗa mishi halin da Ummi take ciki ya shiga ɗakin."Hajiya ita mutuwa halittace ta ubangiji dukam mairai bazai tsallake ba,sannan ita da tafi ba gaggauwa tayi ba mukuma damuke nan ba jinkiri mukayi.kowa lokaci yake jira in tayi kuwa babu tsimi babu dabara sai an tafi,Yasira addu'ar mu take buƙata fiye dakomai ahalin yanzu Allah yajiƙanta ya karɓi shahadar ta". Amin-amin shine abunda yata fitowa daga bakunan mutanen ɗakin,sannan suka wuce wajen likitan suka karɓawa Ummi sallama.jaririyar datake tsala ihu iya ƙarfin da ubangiji ya bata,datake riƙe a hannun Sayyid sai faman jijjiga yakeyi. Haka muka fito ina riƙe da Ummi zuciyata tamin nauyi sosai dan jinayi kamar an ajiye min dutsi acikin ƙirjina. Motar Sayyid muka shiga nida Ummi da kuma Hajja,sai Sayyid ɗin yake driving ɗin motar.Habib da Daddy kuwa sun tsaya tahowa da gawar. "Hajiya dan Allah kiyi haƙuri,ai haƙuri akeyi kowa yasan mutuwa tanada zafi da raɗaɗi amma dangana ake sawa zuci"furcin Hajja kenan ga Ummi. Muna isa na ɓalle murfin motar muka fito,muka shiga cikin gidan Sayyid kam lock ya dannawa motar ya ɗaura kansa kan siriyari yana nashi kukan mai tsuma zuciya.har sai dasu Habib suka iso tare da motar asibitin data ɗauko gawar Yasira sannan ya fito. Part ɗin Habib aka shiga da gawar aka ajiye sannan Daddy yasa aka rufe gabaɗaya part ɗin.tun shigowarmu cikin gidan na wuce ɗakin Yasira yayin da Hajja ta ƙara wanke jaririyar ta saka mata kayan sanyi ta goyeta. Furcin Yasira na ƙarshe a gareni su suke tamin sowa a kunnuwana,wallahi har yanzu zuciyata ta kasa yarda cewa wai ta rasu bata cikin wannan duniyar.akan gado na zibe ina sakin wani kuka dakai tsaye yake fitowa daga can cikin ƙoƙon raina. Zuciyana tana min zafi sosai tamkar zata fito daga cikin ƙirjina,ta tada rawar banjo jikina duk ya ɗauro mazari na miƙe jiri na ɗibata na nufi toilet nayi alwala na fito. Na tada salla ina iddarwa na shiga addu'ar neman gafara ga Yasira,na daɗe kafin na shafa addu'ar tsawon ranan wannan ranar yanda mukaga rana haka mukaga dare.kaina kan cinyar Ummi har akayi ƙiran assalatu.babu abunda jaririnyar tasha har yanzu bayan ruwan zamzam ɗin da Hajja ta bata,sai yanzu da aka kaɗa mata madara tasha sannan aka mata wanka ta koma bacci. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 5⃣6⃣ Ƙarfe taran safe aka gudanar da jana'izan,har an tafi kaita Granny da Iya suka iso ganinta yasa gidan ƙara ruɗewa.nikam tun daren jiya bana iya buɗe koda ƙwayar idona ne sakamakon nauyin dasukamin da kuma azababben ciwon kai daya sauƙa min. Tabbas duk wanda ya halalci sallan jana'izan ya tafi mamakin irin mutana nan da Yasira tasamo,da kuma yabo daga bakunan mutane,kowa yazo sai ya tambaye abunda ta haifa ta bari Hajja ke gabatar da ita.jaririya kamar ta amma taƙi yarda da kowa daga ni sai Hajja ko Ummi bata yarda da ita. Suna dawowa daga maƙarbarta Habib,Sayyid da kuma Yaya Fawas daya sama halaltar jana'izan suka shiga.falon yaƙara ruɗewa sosai gaban Ummi ya ƙariso ya tsuguna ya ɗaura kansa jikin ƙafafunta tana sakin kukan daya tukare masa zuciya da sai yanzu ya sama damar fitar dashi. Sayyid kuwa jikin Granny ya kwanta yayin da Yaya Fawas ya zauna kusa dani,wallahi duk mai ɗauke da ɗigon imani sai ya tausayawa wannan ahalin. Nima hawayen nake fitarwa da sauri-sauri numfashina na fizga da ƙarfin tsiya Yaya Fawas ya kwanto da kansa dai-dai fuskana"My cute angle ba'a fiye son wannan kukan ga mamaci ba addu'a zakiyi mata Allah ya jiƙanta halinta na ƙwarai ya fita,ya kuma raya abunda ta bari". Kaina kawai na ɗaga masa amma kuka kam bansan lokacin dazan daina basa,Habib yamin ishara da hannunsa akan nazo na kuwa miƙe na isa gareshi Babyn tana hannuna ya haɗamu dukka ya manna da jikinsa kamar kuwa an kunna mu duk muka fashe da wani kukan. "Haba Habib kai dazaka lallashe ta kuma kai kake haka,addu'arku take buƙata domin yanzu shi kaɗai ne gatan dazaku mata ba wannan kukan ba". Furcin Daddy kenan yana ƙarisowa cikin falon,yayin da matan dake zazzaune suka fara mishi ta'aziyya yana amsawa.riƙo Habib yayi ya ɗamƙashi a Sayyid yace su fita suyi sannan ya kaishi part ɗinsa ya kwanta,tare da Yaya Fawas suka fita. Kusa da Ummi ya zauna yana lallashinta duk da ba komai dayake faɗa nake iya tantancewa ba,na miƙe jiri na ɗibata nayi ɗaki sai dana kwantar da Babyn sannan na tashi zan shiga bathroom naji hannunta ya kama jikin hijab ɗina.na juyo na zare a hankali hawaye duk wanke gaban hijab ɗin nashiga toilet na ɗauko alwala na fito na tada sallah. Ban tashi daga kan sallayanba har aka ƙira Asr nayi ina zaune na shafa addu'a kenan,wata ƙanwar Ummi ta shigo na gaisata ta amsa sannan ta ɗauki Babyn ta fita da ita.ba jimawa Hajja ta shigo da kulolin abinci,ta diresu a gabana ko kallonsu ban yi ba. "Ga abinci ki daure kici rabonki da abinci tun jiya ai yunwarma sai ta miki illa". Na sauƙe ajiyan zuciya"Hajja banajin sha'awar komai bazan iya ci ba". "Hibba daurewa zakiyi ko tea kisa a cikinki".kafin nakai ga bata amsa wayata dake kan gado ta fara ruri,ta miƙo mini nayi saurin ɗaga ganin sunan mai ƙiran. "Sayyid yaya akayi?"na fara ina kara wayar a kunnena.daga ɗayan bangaren yace "Hibba dan Allah kizo kiga Hamma na kawoshi part ɗinsa amma baya cikin nutsuwa,ke kaɗai zaki iya kwantar masa da hankali a halin dayake ciki yanzu". Sauƙe wayar nayi daga kunnena ba tare dana furta masa komai ba,na fara ƙoƙarin miƙewa maganar da Hajja ta farayi ya dakatar dani. "Ina koma zakije?". "Zanga Habib ne"na faɗa ina ficewa daga ɗakin na ratsa mutanen dake falon na fita,babu haske ko kaɗan a falon duk bub ɗin a kashe suke dan jiya da aka kawa gawar Daddy yace akashe su,a hankali na tura ƙofar bedroom ɗin na shiga haɗe da sallama.na fara ware kumburarrun idanuwa a ɗakin can kan bed na hangoshi tana kwance ruf!da ciki. Na saki ƙofar na isa gareshi na fara jijjiga ƙafarsa a hankali ina ƙiran sunansa"Hamma!Hamma!!Hamma!!!?".shuru mai amsa ba wanda hakan ya haifar mini da bugawar zuciya da ƙarfi.na jawoshi yana dafe da ƙirjinsa numfashi na fida da wani ƙara gu-gu-gu haka kakeji. "Subhannallahi na shigaa uka ya Allah"na furta a riɗime na wuce kan mirro ma ɗauko masa maganinsa sannnn na ɗauko goran ruwan dana gani akan site drawer na bashi maganin yasha.na isashi gaba ina kuka,murmushin ƙarfin hali ya mini yana shafo gefen fuskana. "Hamma kar ka tabi kabarmu dan Allah kaima,wallahi zuciyata tana dab da tarwatsewa".a hankali yaja jikinsa yazauna ya jingina jikinsa da nawa kallon fuskana yakeyi da hawaye yakets gudana yace"Bazamu rayu tare matata,zamu rayu mu riƙe amanar Yasira". Kaina na jijjina masa ina mai ƙara tausayinsa tabbas dole yafi kowa jin mutuwar Yasira,a yanda naji Granny na faɗawa wasu mata sanda zan fito tana cewa "tun haihuwar Yasira,Habib ne ya fara ɗaukarta ya kuma hana kowa ita shi yake rainonta har ta girma intana rashin lafiya baya iya matsawa daga kusanta.ranar da aka sata a makaranta shiya kaifa idan yaji kukanta to babu kwanciyar hankali a tattare dashi duk dangi dashi kaɗai take kama,sunyi shaƙuwa sosai duk rashin son maganarsa amma in Yasirace zagewa yake suyi hira,itacs mutum na farko da duk wani abun farin-ciki ko akasinsa ya sameshi yake fara sanarwa.ko Sayyid dayake namiji kuma kusan sa'anni suke basuyi shaƙuwar dasukayi da Yasira ba". Na sauƙe kyakykyyawar ajiyan zuciya ya ɗago kansa"Muje kuyi sallama da Fawas zai wuce Baffa kam tun ɗazu ma ya wuce". Nayi riƙo da hannunsa ya sauƙo daga kan bed ɗinmu muka fito,cire harabr gidan yake da maza dan haka muka tsaya daga wajen parking lot ya ƙira Yaya Fawas a waya suka taho tare da Sayyid. "To my cute angle nizan wuce sai kuma sadakan uku,zamuzo dasu Anisa da Hajiya ". " Allah ya kiyaye hanya mungode"nayi jarumtar faɗa,duk suka amsa da Amin. Ranar ma haka ban iya rutsawa ba tare da Babyn muka kwana duk juyin dazanyi sai na kalle fuskarta,da tsan-tsan kama da mahaifiyarta yale malale akai. Washe gari ina shirya Babyn naji sallaman Maryam ta falo suna gaisawa dasu Ummi da Granny,suna gamawa ta shigo ta kalloni cike da tausayi tana faɗin"Ashe kuma Yasira sa'i yayi,wallahi muna maiduguri Habib yake sanar da Bashir shiyasa bamu sama jana'izan ba yanzu ma ko gida bamuje ba.Allah ya jiƙanta ya kyautata makwancinta". A sanyaye nace"Amin ya Allah".sannan ta karɓa Babyn tanata faɗan kamanninta da Yasira. "Kuma gata tufarkalla kamar ba cikin wata bakwai ba". Nace"uhmm". Ina zaune akan sallaya na iddar da sallan Zuhr kenan Hajja tashigo take cemin"Inna ta iso"ina ganinta naji zuciyata ta karaya na tina lokutan damuke zuwa wajenta tare da Yasira muci musha ayi raha ayi dariya,ai kuwa na saki kukana na fara binsa wiwi muka rungume juna.sai da mukayi mai ishermu kafin ta rabani da jikinta suka fara gaiswa dasu Granny. Na neɓa waje na zauna ina zama Anty Amina ta shigo ta'aziyya ta farayiwa Ummi da Granny sannan ta zauna kusa nida Maryam muka gaisheta tana ƙarayi mana gaisuwa,Maryam ta miƙa mata Babyn. Balaraba da tun da akayi rasuwar take gidan ta taso ta kusan Anty Amina tann mai fashewa dakuka"Amina ki yafe ni kiyafe min alhakinki bazai barni nayi rayuwa cikin farin-ciki ba".itama Anty Aminan kuka takeyi"Balaraba na yafe miki Allah ya yafe maan gabaɗaya ya jiƙan malam". Amin muka ama dashi yayin da waɗanda basu bansuba suka fara binsu da kallo.sai yamma Anty Amina ta tafi tare da Balaraba suka fita tanuna mata gidan da Habib ya kam mata haya. Inna kuwa da Maryam ana suka kwana,da asuba bayan munyi salla Inna ke gaya min yanayin jikin Hajara ya tsananta shiya hanata zuwama lokacin da akayi rasuwa dan suna wajen magani,fatan samun lafiya muka mata nida Maryam. Ranar za'ayi sadakan uku kuma naji Granny nacewa hadda bakwai zaka haɗa,bayan sallan zuhr mutan Nijar su Aliyu haidar,Farida,Kawu Isma'il da kawu Hayatuddeni sai kuma Nabiha da khalifan Adda Lawisa suka zo. Aka musu tarba suka yiwa Granny da Ummi ta'aziyya.ina zaune a ɗaki dawowa na kenan daga part ɗin Habib nakai masa abinci su Farida suka shigo hadda Kalifa duk suka gaisheni tare da min gaisuwa na amsa sannan na sako hijabina na ɗauka Babyn na fito muka gaisa dasu Kawu Isma'li ya karɓa Babyn ya mata addu'a sannan suka fita wajen maza a waje. Basu daɗe da fita ba Sayyid ya shigo dasu Anisa,Fadila hadda su Sadiq da Mahmu da kuma Hajiya mahaifiyarsu,aka gaigaisa sannan nayiwa Ummi bayanin ƙanne yaya Fawas ne da mahaifiyarsu. Hajiya dasu Mahmud da kuma Yaya Fawas a ranar suka koma azare,su Anisa da Fadila kuwa sai anyi suna,Kawu isma'il da Kawu Hayatuddeni ma da kalifa Lagos suka wuce zasuyi sati acan kafin suzo su wuce. Ranar da Yasira ta cika kwanaki bakwai da rasuwa ranar akayi suna,babu wata gayyata ba iya yamu yamune dangi.muna zazzaune dasu Anisa da Farida a falo Sayyid ya shigo bakinsa har kunne rabon da naga dariyarsa tun Yasira nada rai.Iya ta katse masa hanzari ta hanyar faɗin"Wa aka samu?". Ya ƙara yalwata fuskarsa yace"FATIMA aka samu sunan HIBBA". Nayi gaggawan ɗago kaina ina tsaida ƙwayar idona akan Sayyid,ya ɗaga min kansa alamar tabbatar mini da zancensa. "Kai!Masha Allah amma kuwa Habib ya kyauta wallahi Allah ya raya FATIMA".furcin Iya kenan a karo na biyu. Su Farida da Maryam sukata murna nikam sakeke na tsaya duk tinanina sunan Ummi ko Granny za'asa. Ummi ta fito daga ɗaki itama yanzu takejin sunan da aka sa a bakin Daddy ta rungumeni,na saki kukan dana kasa tantancewa na farin-cikine kona akasinsa. "Ai ba kuka zakiyi ba Hibba,Allah ya rayata ta ɗauko halinki ita kuma Allah ya jiƙanta da rahma". Furcin Ummi kenan danaji kamar ta karanto abunda ke cikin zuciyana,yau gani ga ƴar Yasira amma babu Yasira.na karɓa Babyn dake hannun Farida suna mata hoto na rungume a jikina a zuci nake faɗin"Allah ya bani ikon riƙe amanar Yasira". Har Yamma ban sama ganin Habib ba dan yana cikin mutane ga kuma ƴan office,dasuka zo masa gaisuwa.da yammacin Inna ta shirya komawa Gano saboda rashin lafiya Hajara tare da Sayyid suka tafi dan naji yana cewa Ummi zai shiga cikin makaranta za'ayi exams ɗinsa amma a ranar zai dawo. Sai da dare Habib yashigo Ummi sai sa masa albarka takeyi haka nan ma Granny da Iya,bama kaman Daddy.Dazai fita yace nakai masa Babyn,na karɓeta daga hannun Granny nabi bayansa. Part ɗinsa muka shiga muka yada zango a falo ya karɓa Babyn yana ƙarewa fuskanta kallo. "Hamma nagode nagode kamin abunda bazan iya biyan ka da komai ba a rayuwa,sai dai na dawwama cikin addu'ar nema maka dacewa dakuma gamawa lafiya". Murmushi ya wurgo mini kana yace"bakiga farin-ciki ba wajen Daddy danace sunanki za'a sa,MU'AFSA nakeson a ɗinga ƙiranta dashi". "Allah ya raya MU'AFSA"na faɗa ya amsa da Amin. Muɗan taɓa hira kafin na dawo na barshi da Mu'afsa mukayi kicibus da Anisa tana fitowa nabita da kallo"ina zakije?". Ƙasa tayi da kanta tana wasa da yatsunta tace"Yaya Aliyu Haidar ne ya aiko Farida ta ƙira ni".sarai na ganewa take nufi amma na basar na kuma cewa"Waye haka?"ta ɗago tace"Yayan su Farida wanda naji kina cewa soja ne".murmushi kawai nayi wanda rabona dashi tun kafin rasuwar Yasira na shige. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _______________________________ Page 5⃣7⃣ Washe garin sunan tun safe Maryam da Dr Bashir suka koma damaturu,ƙannen Ummi ma duk sun tafi jiya da aka ƙare sunan.ranan Yaya Fawas yazo ɗaukar su Anida da Fadila tun zuwar Yaya Fawas na lura da yanda yake satar kallon Farida dasun haɗa ido sai su sakarwa juna murmushi.haka nan Anisa da Aliyu Haidar,Sayyid ma na lura sai wani shan ƙamshi yakeyiwa Fadila. Ni kaɗai na saki dariya mai sauti bayan na gama wannan lissafin cikin kwakwalwata,dai-dai lokacin dana gama shirya Mu'afsa na saɓata a ƙafada zan fito.makeken hotonmu nida Yasira da kuma Habib wanda muka ɗauka ranar aurensu dayake maƙale a ɗakin ya dakatar dani daga fitan. Na ƙurawa hoton idanu rayuwa fa kenan gatanan kamar ka mata magana ta amsa,amma babu daman hakan koma nayi da baya bayan na ciro hoton na zauna ina ƙara binshi da kallo. "Allah ya jiƙanki Yasira,Allah ya karɓi shahadar ki". "Amin". Naji an amsa naji saurin waigowa dan tinanina a zuci nayi maganar,yana tsaye bakin ƙofar ya naɗe hannayensa a bayansa ya rako ya iso gareni,durƙusawa yayi dai-dai fuskana"Banason wannan kukan domin da kinsa yanda zuciyata take raɗaɗi idan naga hawayenki,to dakin tausaya min kin daina"ya ƙarishe yana goge mini hawayen. "Taso muje ga can su Fawas zasu koma ke suke jira".ya ƙare zancen yana karɓan hoton dake hannuna ya maƙala shi a gurbi shi sannan ya riƙo hannuna muka fito ina riƙe da Mu"afsa. A harabar gidan muka iskesu suna tsatstsaye ya lanƙwaso da kansa"kinga mutumin ko Aliyu Haidar,kin kusa zama suruka".na saki murmushi ashe bani kaɗai nake zargin soyayya sukeyi da Anisa ba. Muna isa Yaya Fawas ya karɓa Mu'afsa yana mata wasa sai kwalalo masa dariya takeyi. "My cute angle ki tayani godiya Habib ya cika alƙawari yadai dage sai na tabbata a Malunta,domin har an saya fili yanzu har anfara gini ".na rausaya kaina nace"Mungode Allah yaƙaraa buɗi". "Ai naga ka fara neman aurene shiyasa nace nima gwara na zage,kaga sai anyi ga sabuwar makaranta ga sabuwar Amarya ko Farida?".saurin tufe fuskarta tayi da tafukanta tayi ciki da guju muka bita da dariya. Mukayi sallama dasu Anisa,Ummi ma ta fito sukayi sallama hadda su Granny sannan suka tafi tare da sallahon gaisuwan dana bayarwa akaiwa Mahmud da Sadiq. Nan nabar Habib sunatayi da Aliyu Haidar,Mu'afsa na hannunsa muka dawo falo tare dasu Ummi anan muka zauna Granny ta shiga faɗin tanason a bata Mu'afsa ta riƙeta a wajenta ƙirjina ya shiga bugun lugudai jikina yayi sanyi ƙalau ina tino furcin Yasira na ƙarshe a gare ni"Amana ce a gare ni Mu'afsa duk yanda zanyi bazan yarda tayi nisa da niba"amsar da zuciyata ta bani kenan na miƙe na koma ɗaki. Sara da Marwa kawai nakeyi nakai mari nakai bango ƙiran sallan zuhr yasa na faɗa banɗaki ya ɗauro alwala na fito ina shirin tada sallan Nabiha ta shigo da Mu'afsa ta kwantar da ita tayi bacci sautin tashin muryan Habib danaji a falo yasa nazo bakin ƙofar na tsaya ina bada hankalina ga inda zance ke tashi a cikin falon. "Granny da anyi haƙuri dai domin kafin Allah ya karɓa rayuwar Yasira sai datace ta mallalawa Hibba wannan ƴa data haifa,sannan kuma amana ce ta bar mata da anyi haƙuri an bar mata ta riƙe tunda ma mai sunan ta ce"furcin Habib kenan daya sanya ni saurin gyara tsayiwata ina jiran amsar da Granny data bashi. "To shikenan daman wai naga tana zuwa makaranta ne shiyasa nace ko za'a bani ita na riƙe". "Ai Granny tama kusa ƙare makarantar dan yanzu tana ajin ƙarshe"Cewar Ummi daya sani sauƙe wata kyakykyawar ajiyan numfashi ba shiri na ɗaura da Hamdala sannan na dawo na data sallan na daɗe ina yiwa Yasira Addu'a kafin na shafa addu'ar na damo wa Mu'afsa madararta nazo na tada ita na soma bata sai data daina karɓa dan kanta kafin na toɓeta na mata wanka na shiryata cikin wasu kayan marasa nauyi nan kuwa ta koa baccinta na kwantar.Sallamar Anty Amina yasani saurin ɗago kaina daga wayar da muka soma da Yaya Fawas yanzun nan na tashi na tarbo ta kusa da Mu'afsa ta zauna kafin na ƙare wayar muka fara gaisawa tana ta mamakin girman Mu'afsa kamar ba bakwaini ba rurin da wayata ta soma ya sani karata a kunnena daga ɗayan bangaren yace"Matar aljanna ki fito compound ina jiranki". "To ga Anty Amina ma kuwa tazo"kamar jira yake yii ya koma cewa"yauwa ku fito tare".cike da mamaki na sauƙe wayar daga kunnena ina binta da kallo kafin nace"Anty Amina Habib na miki magana yana compound" "To"kawai tace muka miƙe duk muka fito bamu iske Ummi da Granny a falo ba haka nan muka fito compound ɗin,cikin garden muka hangosu an sanya kujeru duk suna zazzaune hadda da Daddy muka isa bakina ɗauke da sallama,sallamar daban iya ƙarisawa ba kenan sauran suka maƙe ƙasan maƙoshina jikina ya ɗauki mazari hannuna dayake rawa na ɗaga na fara nuna shi dashi"KA-KA KABIR".ya miƙe a hanzarce yana kallona sanya yake cikin farar jallabiya da ƙaramar hularta kallo ɗaya zaka sama kaga cikakken ɗan ƙwaya koma ince mashayi gaba ɗaya ko ranar da muke gidan Balaraba aka taho dashi ban ganshi ba domin motar Sayyid sula shiga daga nan kuma suka zarce asibiti dashi. Anty Amina tayi nasarar riƙo hannuna da har yanzu ban ɗauke shi daga nunin dana keyi da Kabir ba Daddy yace mu iso mu zauna kusa da Ummi na zauna Mu'afsa kuwa Sayyid ya karɓe ta. "Hibba dan Allah ki dubi girman Allah da manzonsa ki yafe min nida Mahaifiyata tabbas mun zalunce ku daga ke har Anty Amina kuma munga sakayya tun anan duniya alƙwarin Allah ne baya barin haƙƙin wanda aka zalunta,a irin sharrin da bamu miki ba har keta miki haddi naso nayi Allah bai bani dama ba amma yau ke kika zama mana gata a duniya kika saka mana da alkhairi wajen ceto rayuwarta dana Mahaifiyata.dan Allah ki yafe min ko hakan zaisa na sadu da ubangijina lafiya"furcin Kabir kenan yana durƙushe kan gwiwoyinsa. Kuka nakeyi sosai har ina neman shiɗewa abubuwa da yawa suke dawo mini kamar yanzu suke faruwa mussamman ranar da Kabir yaso mini fyaɗe Balaraba ta kwara mini ruwan zafi tafashashshe a jiki wanda har yanzu tabon bai bar fatar jikina ba yana nan.Granny ta dafo ni"Hibba yayi nadama kuma ya shiryo ki yafe masa domin Allah yana son masu yafiya. Idanuna suka sauƙa kan Balaraba dake gefe guda tana nata kukan cikin hijabi na zuƙe kukan dana nakeyi ganin Habib ya doso inda nake sunkuya yayi yana min magana wanda ko Ummi dake kusa na bana tinanin data iya jiyo abunda yake furtawa saboda yanda ya sausauta muryarsa"Debbo am tabbas sunyi nadama yafiyarki gare su kan iya zamowa sausauci daga rayuwar ƙunci da sukeyi". Na yarce ƙwallan dake shimfiɗe saman tudun fuskana"Na yafe mata Kabir daga kai har Mahaifiyarka Allah ya yafe mana gaba ɗaya".Cikin wani kukan ya koma cewa"Anty Amina kema ki yafe mana". "Na yafe maka Kabir Allah ya jiƙan Malam"Duk aka amsa da Amin Daddy yace nazo alama yamin da hannunsa na kuwa tashi na isa gabansa"Allah ya miki ɗiyata Allah ya albarkace rayuwarki data ƴaƴan da zaki haifa Allah ya shiga cikin lamuranki ya wanzar miki da haske alfarma annabi da alqur'ani"tunda ya fara maganar nake amsa da amin haka ma su Ummi har yake aya. Sayyid ya miƙawa Kabir Mu'afsa yana faɗa mishi ƴatace,yakarɓe ta yana kallonta da idanunsa dasuke taf!da ƙwalla.ba kunya na miƙe daga gaban Daddy nacewa Kabir"bani ƴata zan shiga ciki"na lura da yanda jikinsa ya ƙara sanyaya ya miƙo min ita yana cewa"Allah ya rayata". "Amin"na karɓa abata nayi cikin gida nan suka zauna kafin Kabir da Balabara suka tafi Anty Amina ma ko sallama bamuyi ba ta tafi tsawon sauran wunin ranar ban leƙo ko falo ba a ɗaki na ƙarar dashi ina godiya da mahaliccina washe gari su Kawu Isma'il suka zo a ranar zasu koma nijar Daddy yayi ta musu godiya haka suka tafi bayan munyi sallama dasu Farida da Nabiha. Mu'afsa na hannun Hajja data zo yanzu na barta na wuce ciki lokacin dazan shige ɗaki naji Daddy da Habib da kuma su Ummi da Granny na tattaunawa akan Kabir yanda zasu inganta rayuwarsa tunda ya shiryo ko sana'a ne a sama masa ɗauke kaina nayi nayi shigewata ɗaki ina shiga Yaya Fawas ya ƙirani muka gaisa sannan na sanar dashi abunda ya faru yayita min nasiha sosai akan haƙuri nikam ko yaushe cikinsa nake rayuwa mun daɗe kafin mukayi sallama bayan yabawa su Mahmud mun gaisa. Ranar da Yasira ta cika kwanaki ashirin da rasuwa ranar da safe Granny da Iya suka koma damaturu da misalin ƙarfe Tara na safe muna zazzaune a falo tare da Sayyid da Ummi,Daddy kuwa tare suka tafi dasu Granny damaturu.Habib ya shigo yanayin daya shiga cikinsa ya sanya dukkanimun jefa masa tambayar lafiya?guri ya nema ya zauna kafin yace"Hibba ki shirya zamuje Gano yanzu" Cike dason ƙarin bayani muka haɗa baki nida Ummi wajen cewa"lafiya kuwa ko wani abunne ya faru?" "Ana maka magana kayi shuru wani abunne ya faru?"Ummi ta ƙara faɗa a karo na biyu ya ɗago ya kalleta yace"Baffa ne yace na kaita jikin Anty Hajara ne ya tasha".Ummi ta shiga rafza salati tace na tashi na shiryo yanzu mu tafi na kuwa miƙe ƙirjina na bugun lugudai na saka mayafina sannan na shirya kayan Mu'afsa a jaka tare da madararta na fito na amsheta daga Hannun Sayyid muka tafi Ummi nata mana addu'ar sauƙa lafiya anan ta ƙira Daddy take sanar dashi yace in mun sauƙa Habib ya ƙira shi. Tunda muka hau titi fargabata ta tsananan ta haka nan cikin mu babu wanda yayi magana lokaci zuwa lokaci na lura da yanda Habib yake yarshe gumi duk da air condition ɗin dake aiki a cikin motar,wata zuciyar ta raya min koma Inna ce ta mutu yake ɓoye min yace wai jikin Anty Hajara ne?.tunin hawaye ya fara wanke mini fuska nace"Dan Allah Habib inma Inna ce ta mutu kake ɓoye min ka sanar dani wallahi zan karɓa ƙaddara aduk yanda ta zomin". "Debbo am kamar dai yanda na gaya miki haka Baffa ya sanar dani".na sauƙe ajiyan zuciya badan na yarda da kalamansa ba. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ______________________________ Page 5⃣8⃣ Har muka isa cikin Gano banida kuzari sai tufka da warwara nakeyi a cikin raina zuciyata tana mini sarƙa yana gama daidaita parking na saɓa Mu'afsa a kafaɗata na nufa ƙofar gidan cikin sauri shima ya kashe motar ya biyo bayana buɗe dukkan muryata nayi na kwaɗa sallama tun a zaure Habib yayi nasarar cinmu mini"Hibba ki nutsu mana ki kwantar da hankalinki". Ban iya bashi amsa ba nasa kai nayi shigewata cikin gidan ganin Inna danayi suna tsaye a ƙofar ɗakin Hajara ita da Baffa ya sani sakin hamdala ina godewa Allah sannan nayi saurin isa gare ta"Inna lafiya kuwa menene yake faruwa?". "Jikin Hajara ce ya tashi yau dai jikin yafi na kullum tsanani sai dai Allah ya bata damar buɗe baki tayi magana wanda rabonta da magana har lissafin kwanakin ya ɓace min tun ɗazu take ambaton sunan ki tana cewa a ƙira mata ke tana son ganinki". Duk na gama ratsa nutsuwa ta nace"tana ina yanzu?"dai-dai nan Habib ya shigo su kayi musabaha da Baffa gaisuwar da ya jefawa Inna ta hanata amsa mini tambayar dana mata a farko."Tana ɗakinta"ta faɗa tana min nuni da ɗakin Mu'afsa na miƙa mata saboda naji tana ƙoƙarin sulalewa ƙasa daga riƙon dana mata na shiga ɗakin duk suka rufa min baya.kusa da ita na tsuguna ina kamo hannunta sannan na furta sunan ta duk halittun jikinta ya sauya ina iya jiyo yanda duk gaɓoɓin jikinta suke karkaryewa abunda yafi sanya mini tsoro a zuciyata kenan ta ɗago idanunta da har sun rufe tace"Hibban ce?"nayi saurin amsawa da"e nice Anty Hajara ya jikin". "Malam a ƙira min Adda Barira a ƙira min Adda tazo". Da hanzari yafita ya aika yaro yaje ƙiranta bata ɗau wani lokaci mai tsawo ba ta iso a ɗimauce ta faɗa kan Hajara tana sakin kukan daya sanya mana tausayinsu a zuƙatan mu"Adda ba kuka zakiyi ba tabbas yau ne ranar ƙin dillanci Adda ranar da zamu dibi abunda muka daɗe muna shukawa kuma muka ƙarar da rayuwarmu wajen masa ban ruwa,nidai tawa ta ƙare wannan jinyar ta ajali ce Hibba inaso in sanar dake wani ƙulli".Inna ce tayi saurin faɗin"Ashsha haba Barira keda zaki lallasheta kuma kema kike kukan,Hajara ai zafin jinya ba ita take nuni da mutuwa ba ki daina wannan surutan dan Allah". "Inna na aikata babban laifi a rayuwata wanda innaje dashi gaban Allah bazan sama rahamarsa ba".Shuru ne ya ratsa ɗakin baka jiyo sautin komai dana munsharin da Mu'afsa take yi akan cinyar Inna. "Hibba na cuce ki na zalunceki naci amanarki duk saboda son zuciyata na azabtar dake akan laifin da bakiji ba baki gani ba,abun ya faru ne tun daga ranar da kika dawo gidan nan tare da iyayen Habib nayiwa Malam magana akan ban yarda dake ba karuwanci kije kikayi hatta shi Habib ɗin ma wataƙil daruron kine wannan maganar ta fusata shi har ya mare ni abunda bai taɓa haɗa ni dashi ba kenan duka.najewa Adda Barira da maganar ta kuma ɗaura ni akan hanyar data kawo ni izuwa ga nadamar danake ciki yanzu mu muka sa aka cire miki son Habib a cikin ranki kuma aka hanaki jin daɗin zaman gidansa aka haddasa miki ƙiyayyar sa acikin zuciyarki lokacin danajin labarin samun cikin da kikayi sai da mukaga bayansa sannan hankalinmu ya kwanta kuma muka sa aka ɗaure miki mahaifa aka kuma sanya miki zubar jini ako yaushe burin mu rayuwarki ta dawwama cikin ƙunci da baƙin-ciki muka sa aka mallake mana Malam ta yanda duk ko kara na ajiye zaiyi shakkan tsallakewa,hakan ya bani damar tsula tsiya ta son raina sai dai Allah yafimu ƙarfinmu ya bamu nasara akan abubuwa da yawa da muka ƙulla miki bamu sani ba ashe ranar irin ta yau tana nan zuwa Adda Barira kin cuce ni kin cuci rayuwata duk ke kika ɗaura ni akan wannan layin".takai ƙarshe tana matsanancin kuka. Kasa wani ƙwakwƙwaran motsi nayi tun sanda Hajara ta fara magana nake hawaye har ta ƙarishe ban fasa ba haka nan ma Inna da Adda Barira,Habib da Baffa kuwa kawai dauriya ce da ƙarfin hali irin ta maza amma suma basu ƙi su saki kukan ba.Inna ce tayi ƙarfin halin faɗin"Lalle duniya abar tsoro ce aihun kaji tsoron Allah kaji tsoron mutum mai ƙafa biyu,Hajara ki cuci kanki kin cuci rayuwarki kinci amanar zaman aurenki meye Hibba ta tsare miki a rayuwar duniya?ashe duk wannan abunda dayake samun ta daga wannan sai wancan ashe duk kece sila?". "Inna sharrin shaiɗan ne da kuma sharrin Adda Barira". Baffa daya kai ƙololuwar ɓacin rai yace"Hajara kin cuce ni kin haddasa na ɓatawa uwata nayi jayayya da ita a lokuta masu yawa nayi sanadin zubar hawaye daga idaniyar ta wallahi ki cuce ni badan duk wanda ya kashe hukuncinsa shima shine kisa ba,wallahi dasai na kashe ki a cikin ɗakin nan.amma ba komai kije keda Allah zaki ga sakayya gashi nan ma tun kafin ayi nisa kin fara gani na sake ki saki uku ki tattara kibar min gida na".dukkan jikinta ne ya hau jijjiga yayin da wani tari mai ƙarfi ya sarƙeta hawaye sharɓe-sharɓe kwance a saman fuskanta. "Baffa haƙuri zakayi ba a yanke hukunci ciki fushi mussaman in akayi la'akari da halin da take ciki a yanzu"furci Habib kenan daya sa Baffa saurin faɗin"wannan zan yafewa?ba dai wannan Hajarar ba bakasan irin abubuwan da ta dinga kitsawa bane a cikin gidan nan babu irin abun daba tayi wa Inna a gaban ido na ba amma banida ikon magana". Rarrafowa Adda Barira tayi ta matso kusa na tare da kamo dukkan hannuna ta ciƙe"Hibba ki gubi girman Allah da ma'aikinsa ki yafe mana ki yafe mana haƙiƙa mun cutar dake aihun".Inna ta miƙe cikin hanzari ta fincike hannuna daga cikin na Adda Barira"Wallahi babu yafiya tsakaninmu daku har abada wannan shari'ar sai muje gaban Allah zamuyi ta domin cuta kam kun cutar damu matuƙa Allah ne kaɗai zai iya mana sakayya"yana kawowa nan ya ɗago ni taja ni muka fice daga ɗakin tana jijjiga Mu'afsa data tashi yanzu,dirsham ta zaunar dani akan gadonta kamar mafarki haka nake ganin duk abubuwan dasuke wakana a halin yanzu kuka nakeso nayi amma ruwan hawayen sun gagara samuwa. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"bakina yayi nasarar furtawa ina jawo numfashi na dayake sarƙewa da ƙarfi mena tsarewa Anty Hajara a duniya mena aikata mata dana cancanci wannan ɓakin ƙiyayyar daga gare ta?a iya sani na ko kallon banzan bai taɓa shiga tsakanina da Adda Barira ba balle har na aikata mata wani mummunan laifin da zatayi ƙudurin ganin bayana ta ko wani hali.yau na ƙara gaskawa cewa bana daga cikin bayin da suke da ƙaddaran jin daɗin rayuwar duniya,figigi na dawo hayyacina sakamakon dafa ni da Inna tayi"ki tashi kiyi sallah".banajin zan iya tsayiwa akan kafafuna a halin danake ciki hakan yasan nace Inna ta ɗagani tayi riƙo da hannuna naje nayi alwalan na dawo a zaune nayi sallan zuhr da Asr dan duk banyi su ba ina zaune kan sallayar aka ƙira magrib nayi sannnn na jawo Mu'afsa jikina wayata ta hau ruri na tsura mata ido har ƙiran ya tsike aka sake ƙira a karo na bakwai kenan dan naga adadin missed ɗin Ummi cikin wayata biyar nata biyu kuma daga Sayyid.kuka na saka mai ƙarfi danake jin ciwonsa sosai acikin ƙalbina mezan cewa Ummi wannna tashin hankalin da muka tarar na tabbatar a wannan lokacin da inada ciki zai iya zubewa saboda matsanancin tashin hankalin danake a ciki. Tun daga cikin ɗakin nake jiyo yanda Adda Barira keyiwa Inna magiya da ban haƙuri amma Inna ta kafe akan babu yafiya tsakaninmu dasu har gaban abada tana ƙara jaddada kafin asuba su kwashe kayan Hajara su bar gidan tun kafin ta tara musu mutane,sautin kukan da Hajara take yi daga cikin ɗakinta ya sanya ni rutse kumburarrun idananu,kamar rago za'a yanka shi irin kakakin da yake yi babu bambamci koda ɗan taƙi da irin sautin dayake fita na kukan Hajara."Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wayyo ni Allah na,Allah mun tuba Allah mun tuba Inna ku tausaya mana Hajara zata mutu".furcin Adda Barira kenan tana zubewa akan gwiwonyinta tana riƙo ƙafar Inna,saurin tureta gefe tayi tana faɗin"Ai bakuga komai ba ma badai haƙƙin marainiya kuka ɗaukarwa kanku wallahi sai kunga sakayya".tana kawowa nan wuf!ta banko labulen ɗakin ta shigo tana hushin ɓacin rai madarar Mu'afsa ta haɗa ta soma bata.tashi Adda Barira tayi tana mai cigaba da kukan da takeyi ta fice daga gidan,gidan limamin unguwar ta nufa kai tsaye ta shaida masa abunda yake faruwa bata ɓoye masa komai ba dan a yanzu mafita ɗaya ce garesu YAFIYAR HIBBA.Furcin Hajara suka fara dawo mata cikin kunnuwanta"Adda kije ki roƙar mana yafiyar su wallahi ana min azaba acikin jikina ki roƙesu su yafe mana koda za'a sausauta min azabar danake ji acikin naman jikina Adda inna koma ga Allah da wannan laifin ina tausayin makomata".kuka mai tsanani ta fashe dashi"na cuce ki Hajara na cuce ki na ɗaura ki akan hanya marar ɓullewa da sanda kikazo min da wannan maganar na miki nasiha da haka bata kasance gare mu kaico na ni Barira". "Lalle duniya abar tsoro ce babu shagallalle face wanda ya biyewa ruɗun ta har ta ruɗe shi,kun aikata babban zunubin da Allah maɗaukakin sarki ya haramta su na haɗa shi da wani abin halitta muje gidan na meke faru". Miƙe tayi tana gaba yana biye da ita har suka iso gidan Habib da Baffa suka iske suna ƙoƙarin shiga gidan wanda dawowar daga masallaci kenan,ganin Liman ɗin ya sa Baffa isa gareshi yana bashi hannu sukayi musabaha sannan Habib.wani mummunar kallo da Baffa ya aika mata yasa saurin rusunar da ƙwayar idonta ƙasa a yanda yakejin tsanar ta ko wuƙa zai iya caka mata ba tare da nadama ba.maganar da Liman ɗin ya soma yi yasa shi ɗauke idonsa daga gare ta"Wannan baiwar Allah ta taso ƙafa da ƙafa tazo ta same ni akan matsalar dak faruwa yanzu a cikin gidanka,shiyasa nazo domin gyara lamarin". "Mu shiga daga ciki amma wallahi kamar yanda na faɗa a abaya zaman aure ya ƙare tsakani na da Hajara kuma sai munyi shari'a a kotun Allah kotun da babu alkali kuma ba'a karɓan rashawa ko cin hanci".furcin Baffa kenan yanayin gaba sannan suka biyo shi. Habib ne ya shimfiɗa musu tabarmar dake yashe a wajen suka zauna kafin yayi ƙiran Inna,tare muka fito bayan na kwantar da Mu'afsa da Inna ta gama bawa madara tayi bacci.waje muka nema muka zauna kafin muka gaishe da Liman ɗin ya amsa yana gyara zaman babbar rigarsa a jikinsa.Adda Barira ta rarumo Hajara ta fito da ita yayin da warin dake fita daga jikinta ya ɗumame wajen jinginata tayi da jikinta ta zauna domin bata iya zama ita kaɗai. Tsaf!Liman ɗin ya ƙarewa Hajara kallo kafin yayi gyaran murya ya soma faɗin"naji duk abunda yake faruwa shi lamari irin wannan dole sai ankai zuciya nisa kuma ansa mata haƙuri,dangana da yarda da ƙaddara tabbas na daɗe banji labarin daya rauna zuciyata ba kamar wannan duniya ta zama abun gudu wasun in suna aikata laifi sai kaga kamar basa tunawa da mutuwa alhalin ita ma halitta ce na ubangiji kuma tana kan duk wani mai rai laifin shirka babban laifine a wajen Allah mai girma amma idan aka yi tuba nagartacciya tare da ɗaura niyyar baza'a sake komawa gare ta ba Allah yakan iya yafewa mai aikata ta,sai kuma haƙƙin cutar da wannan baiwar Allahn da kukayi na hana mata nutsuwa a cikin gidan aurenta kuka hanata samun haihu wanda hakan ya jefata cikin tararradin rayuwa kun ɗauki haƙƙinta har sai ta furta da bakinta cewa ta yafe muku domin Allah baya yafe laifin dake tsakanin bawa da bawa har sai shi wanda aka zaluntar ya yafe". "Wallahi Malam waɗannan mutanen sun cutar damu sun shiga tsakanina da ɗana daya daya rage min a duniya tsakaninmu dasu babu yafiya har duniya ta naɗe"Inna ta faɗa tana fashewa da Kuka har Marinta Hajara tasha sa niyyar yi a gaban Baffa amma baya iya taɓuka komai ashe ba banza an shanye shine. Habib ne ya soma magana cikin taushin murya"Inna dan Allah kiyi haƙuri kowa yasan sun aikata ba dai-dai ba amma ita afuwa tanada daɗi kuma tana da kyau ko Allah muna masa laifi ya yafe mana". Sautin kukan Hajara da Adda Barira ya karaɗe dukkan wajen,cikin azaba Hajara ta soma faɗin"Malam ka dubi girman Allah ka yafe min ko zan tarar da mahaliccina cikin salama"tsuke fuskarsa yayi gum!kamar hadirin daya ke gab!da zubar da ruwa tare da cifanta da wani guntun tsaki yana kawar da kansa gefe. "Malam Adamu cikin gurare da yawa acikin littafin alqur'ani mai tsarki Allah yayi bayani akan irin tagammashin bayin masu haƙuri,a wata ayar har yana cewa babu wanda zai iya biyan masu haƙuri sai shi a wata ayar kuma yace lalle yana tare da masu haƙuri.wata rana an tambaye Manzon(S A W)cewa menene haƙuri?,sai yace haƙuri shine juriya akan baƙin-ciki,yin raha ga maƙiyi,barin mummunar zato,cire girman kai,karɓan uzuri a inda kasan ba gaskiya,haƙuri a inda kake da ƙarfin ramuwa,yafiya ga wanda ya cecu ka sannan kuma kyautatawa ga wanda ya munana maka wallahi haƙuri babban rabo ce". Wannan bayanin na Liman ya sanya jikinmu yi sanyi ƙalau kaina dayake tsakakkanin gwiwana ina fidda hawaye masu ɗumi na ɗago"Na yafe miki Anty Hajara,na yafe miki duniya da lahira Allah ya baki lafiya ya tashi kafaɗunki"abinda da yake a cikin zuciya nane bakina ya shiga karantowa ba tare dana shirya ba.Sosai Liman ya saki hamdala na lura Inna sam bataji daɗin furci na ba dan nan da nan ta kuma haɗe rai tana aiko mini da wani irin kallo daya sanya jikina ƙara yin laushi na motso gareta hannuwanta na riƙo cikin muryata da bata fita sosai na fara faɗin"Inna ki yafe musu muma fa muna aikawata Allah laifi kuma da zaran mun roƙi yafiyarsa yake gafarta mana mu a wani dalilin zai sa muƙi karɓan tubansu,haƙiƙa sun cutar damu cuta mafi munin kwatantawa amma haƙurin shi yafi Inna dan Allah ki yafe musu suje da halinsu". Zazzafar ajiyan zuciya ta sauƙe yayin da idanunta suka fara kawo ruwar ƙwalla ta ƙara matse hannuna cikin nata"Hibba kinga rayuwa iri-iri masifo daga wannan sai wancan babu ɗaga ƙafa kuma duk Hajara ce silar faruwar komai,inada yaƙinin da ta sama dama zata iya kawar dake daga doton duniya gabaɗaya.amma kamar yanda kikace suje da halinsu na yafe musu amma su tattara su bar gidan nan tunda yanzu babu igiyar auren Adamu akanta.dan matuƙar zan cigaba da ganinta zuciya zata iya ɗebata na lahanta ta wataran". "Alhamdulillah in sha Allahu zakuga sakamakon wannan haƙurin da kukayi,yanzu saura kai Malam Adamu". Mintuna biyu a tsakani muna sauraron abunda Baffa zai ce kafin yace"Ba komai Malam taje na yafe maka".sosai su Hajara suka ƙara satin wani kukan suna nufo ni Inna tayi saurin dakatar dasu,sannan taja hannuna mukayi ɗakin,nasiha Liman ya ƙara gabatarwa su Hajara kafin ya tafi.yana ƙara tausan zuciyar Baffa dan ya kare akan cewa baza su kwana masa a gida ba sai dai sun fita da daddaren nan sai da Habib da Liman suka roƙe shi sannann ya amince akan asubar fari su tafi. A gefen Mu'afsa na zauna ina wani irin kuka daya tunkushe mini numfashi waje guda wayata na kallo har yanzu ƙiran Ummi ne ke shigowa. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam _____________________________ Page 5⃣9⃣ Inna ce ta ɗaga ƙiran ko gaisawa ba suyi ba Ummi ta fara zubo mata tambayoyi wani nabin wani"Ina Hibba da Habib ɗin ina fatan dai lafiya ya tafi ya barmu cikin jimami gashi su dukkan basa amsa waya inmun ƙira su". "Lafiya amma dai ba ƙalau ba"Furcin Inna kenan kafin ta hau warwarewa Ummi sare da abawa akan abunda ya faru zaman ƴan bori Ummi tayi tana sulalewa ƙasa dirsham!kalmar innalillahi wa inna ilaihir raji'un kawai take furtawa wanda hakan yasa Sayyid da Daddy nufo ta karɓan wayan Sayyid yayi yana duba wanda tayi wayan tashi kafin ya kara wayar a kunnunsa"Meyake faruwa ne kun barmu cikin duhu?"Inna ta feɗe masa komai cikin wani irin hucin ɓacin ran ya daya taso masa lokaci guda yake faɗin"Yanzu ina ita Hajarar,ina fatan dai tana hannun hukuma ko?". Taɓe baki Inna tayi kafin ta shiga labar ta masa Baffa ya riga daya sake ta kuma duk mun yafe mata. "Wallahi Inna babu wani yafiya bata cancanci hakan ba dan Allah ki riƙe min su zuwa goben zanzo cikin Kanon wallahi sai na musu dukan da ku uwar data haife su inta gansu ba zata shaida su ba".cikin Sauri Daddy ya fizge wayar yana gimtse ƙira bayan yace wa Inna gobe suma zasu ɗauko hanyar kanon,duk abinda Inna take faɗi babu wanda baiji ba domin wayar a handsfree take,wajen Ummi ya fara isa yana lallashinta. Ina kwance har yanzu kamar matacciya zuciyana na mini soya da raɗaɗi Inna ta shigo ɗakin wayata ta miƙo min haɗi da cewa"Ga Fawas za kuyi magana".da ƙyar na iya wangale ƙwayar idona na tashi daga kwanciyar dana yi na amsa wayar ina manna ta kunnuwa shuru nayi sai kukan danake wanda ya tsananta ba tare dana san dalili ba. "My cute angle tabbas rayuwar duniya tana cike da ƙalubale kala-kala da kuma jarawaban da baza mu iya kaucewa faruwarsu ba,amma haƙuri da dangana yake sawa rayuwa ta cigaba da gunada tamkar babu abunda ya taɓa wakana.yanda kika yafewa Anty Hajara kinyi matuƙar kyautata ƙanwata Allah ya gubi wannan haƙurin da kikayi ya saka miki da mafificin sakayyarsa".a wahalce na amsa da amin sannan ya ɗaura da faɗin"in sha Allah nima gobe zan zo cikin Kanon,sannan banason kisa wannan damuwar a cikin ranki har ya ɗaga miki ciwon ki kinji my cute angle".sai dana tare hawayen dake shirin gangaro mini kana nace"Yaya Fawas duniya ta fara bani tsoro matuƙa cin amana na babba da yaro kamar baza'a koma ga Allah ba,na daina tsoro ko kuma fargaban komai yanzu a rayuwa domin duk abunda nake tsoron da fargaban rasa su sun faru dani,mun rasa Abba ga matsalar Umma har yanzu bamu san inda take ba ga rasuwar Yasira wallahi Yaya Fawas ji nakeyi kamar na fita nayi hauka ko zanji sanyi a raina".nakai ƙarshe ina toshe bakina saboda ƙarfin kukan danaji yazo mini Inna da tun data kawo min wayar take tsaye ta zauna tana dafa kafaɗarta na ɗaura hannuna saman nata maganar da yaya Fawas ta fara ta sani bashi hankalina"Ba zamu dawwama cikin kukan dan wasu sun cin amanar mu ko kuma dasun baƙan mana ba,Hibba inaji a jikina wahalar mu ta kusa zuba ƙarshe,inaji a jikina mun kusa daina kuka mu rayu cikin walwala da dariya kamar kowa.an tambayi FARIN-CIKI cewa a ina kake rayuwa?amsar daya bayar cike da tabbaci yace"a zuciyar wanda ya yarda da ƙaddarar Allah(SWT) gare shi muyi haƙuri in sha Allah zamu cinye wannan jarabawar. Daga ni har Inna muka amsa da amin sai daya tambayi Mu'afsa na amsa masa da tana lafiya sannan muka yi sallama,naje na ɗauro alwala na fara jera nafilfili na daɗe a haka kafin na shiga roƙan Allah ya min zaɓi a cikin rayuwarta har na kwanta naji ƙaran shigowar saƙo a wayata ko dana duba Habib ne babu komai a cikin saƙon face kalmomin kwantar da hankali da ɗarsar da nutsuwar zuci ga wanda yake karantawa,wani murumushi mai ciwo nayi sanda na ƙare karanta saƙon ina ƙara kawo Mu'afsa jiki ina rufa mana bargo. Ban taɓa ganin daren da ya mini tsawo ba kamar wannan baƙin daren a gare ni,juyi kawai nakeyi bacci sam yaƙi ziyarta ta zuciyata banda tufka da warwara babu abunda take saƙa mini,banda bacci ya cika cikakken barawo da bazaiyi nasarar ɗauka ta ba a wannan daren saboda yanda nakai matakin ƙarshe a tashin hankali da rashin nutsuwa a tattare dani.cikin gyangyaɗin daya fara ɗauka ta babu daɗewa nayi jiyo an kurma ihu nayi saurin buɗe idona ƙar!ina ƙara saka kunne tare da sauƙe idona akan Inna da take gefen take munsharin ta,har na koma na kwanta na kuma jin an kurma wani ihu a wannnn ƙaron hadda faɗin"wayyo ni na shiga uku"naji an faɗa. Tsoro ya dira a birnin zuciyata ƙiran sallan assalatun farko da aka farayi ya sanya ni dawowa hayyaci na,cikin saurin na fara data Inna sai data tashi ta zauna nace"Inna bakiji ana ihu ba ?"ta hau mirtsika ido kafin ta kai ga furta wani abun muka ƙara jiyo wani ihun haɗe da salati da sallallami. "Wannan ai Barira ce".Inna ta faɗa duk muka zabura muka fito muka nufa ɗakin Anty Hajara.gefe guda muka hango Adda Barira ta kafe kai da gwiwa taan rusar kuka kamar ƙaramar yarinya wiwi sai rera shi take yi Inna ce ta fara isa gare ta" Barira wai me yake faruwa ne kodai jikin Hajaran ne Allah dai ya nuna mana wayewa gari lafiya ku tattara ku tafi". Cikin dusashewar muryarta da bata fitowa sosai Adda Barira ta shiga faɗin"Inna Hajara!Inna Hajara!!Inna yar-uwata dai bat........"tsawan da Inna ta daka mata yasa sauran maganganunta maƙalewa a maƙoshinta"wai menene ki fito ki faɗa abunda yake faruwa kita faɗin wai Hajara,to Hajarar me?". "Inna Hajara ta rasu Hajara ta rasu".ta faɗa tana ƙara sautin kukanta wanda hakan yayi dai-dai da fitowar Baffa da Habib zasu masallaci hayaniyar Inna ta sasu shigowa ɗaki.daga ni har Inna sai yanzu muka lura da Hajara dake wanke ta mimmiƙe ido har sun kakkafe fuskarta ta ƙara duhu da matuƙar muni babu kyawun gani balle in misalta muku yanayin sa.na riga kowa isa gareta na soma jijjiga ta sosai ina ƙiran sunanta da duk muryata amma bata motsa ba balle nasa rai da zan sama amsa,durƙushewa nayi a wajen wani kuka mai matuƙar ƙarfi da ciwo ya karyo mini na buɗe dukkan muryata na shiga fiti dashi wajen wanda duk ɗakin ya ɗauka.har yanzu da Habib yake ɗago ni daga jikinta banbar jijjigata ba ina faɗin"Dan Allah Anty Hajara ki tashi dan Allah ki buɗe idanunki wallahi ni na yafe miki na yafe miki duniya da lahira na yafe miki".kwantar da kaina nayi a kafaɗarsa ina cigaba da rero kukana. Baffa ya lulluɓa mata wani zanin dake kusa da shimfiɗar tata yana rufe mata idonta da suka ƙafe da hannayensa sannan yace mu fito zasuje masallaci dasu sanar da liman ƙarfe goma za'ayi jana'izan.ina maƙale jikin Habib muka fita wani sabon tashin hankali naji yana ziyartar rai da ruhina da ya kusa tarwatsa su babu shiri har ɗakin Inna ya kaini yanata min nasiha dan tun jiya bamu sama damar zama da shi ba,sai daya ga hankalina ya ɗan lafa sannan ya fita izuwa wajen,wajen Baffa suka nufa masallaci. Nima na tashi nayo alwala sannan nazo na gabatar da tawa sallan a zaune nayi ta dan jinayi jikina babu ƙarfi bazan iya tsayawa akan ƙafata ba,bayan dogon addu'ar dann shafa na ɗauko wayata nayiwa Yaya Fawas text akan rasuwar Anty Hajara da kuma lokacin da za'ayi jana'izan yana tafiya nayiwa Ummi ma sannan na kashe wayar gabaɗaya na ajiye ta gefe guda,ina zaune a wajen Inna da tun ɗazu ta fita nemo matan da za suyiwa Anty Hajara wanka ta dawo tun kafin ta shigo take faɗin"innalillahi wa inna ilaihir raji'un duniya ina zakije damu"har ta shigo ɗaki bata daina ba nace"Inna lafiya kuwa?".sai data zare zaman hijabin dake wuyanta kafin tace"Wallahi Hibba duniya abar tsoro ce aihun wai yanzu duk matan dake wankan gawa a unguwan nan sun basa su wanki mushiriki ba Hajara ta jazawa kanta bala'in".zuciyata ta shiga lugudan tara-tara inata juyayin yanda wannan maganar ta fita har kowa yaji ta wata zuciyar ta ce min hakan baya rasa nasaba da yanda Adda Bariria ta fita jiya ta ƙira malam Liman da kuma ihu da tayi ta sakewa da asubahin nan. "Inna yanzu yaya za'ayi kenan?"na jefa mata tambayar ina kafeta da ido"Yaya zamuyi kuwa ai duk wanda yaji abunda Hajara ta aikata dole yayi gudunta kuwa,ni zan wanken ta ai baza'a biyewa halinta ba".ban ƙara cewa komai ba Inna ta ɗauka Mu'afsa tayo mata wanka sanna ta shirya ta na miƙa mata madararta dana gama damawa yanzu ta fara bata. Su Baffa suka dawo da likkafani dasu turare da sauran abubuwan suka miƙawa Inna,ta karɓa bayan ta sanar dasu yanda suka wanye da masu wankan gawan,bangan Baffa ya nuna wata damuwa ba haka nan suka fice. Ƙarfe tara bata cika ba su Ummi suka iso ta shigo Sayyid da Daddy kuwa suka zauna wajen,wajen su Baffa duk da Baffa yace baza'a yi zaman makokin a gidan sa sai dai suje gidan Adda Barira suyi,itama Adda Bariran tun kafin su Baffa su dawo daga masallaci yazo ya aiko yaro ya kawo mata takardan sakinta uku cur. Kusan babu tazara mai yawa tsakanin zuwan su Ummi da zuwan Yaya Fawas tare dasu Sadiq da Mahmud suka zo,Ummi da Inna ne suka wanke Hajara tas!suka kuma shiryata sannan aka fito da ita akan mata salla tsirarun mutane ne suka sama damar halaltar sallan jana'izanta kaita makoncinta kuwa daga Baffa,Yaya Fawas sai Daddy da Sayyid sai wasu maƙwatanmu su biyu sai su Sadiq da Mahmud.haka nan cikin gidan babu taro mata da yawa iya yamu yamune sai Kishiyar Adda Barira Larai data zo ko jimawa babu itama tana mana gaisuwa ta tafi abinta. Sai yamma sannan su Baffa da Daddy suka shigo duk suka tara mu muna ƙara mana nasiha sosai,ana ƙarewa Baffa yace Adda Barira ta fito ta tafi,Daddy yayita bashi baki akan ya bari ayi ko sadakan uku ne sannan ta tafi ya yarda da hakan badan yaso ba sai dan nauyin Daddy dayake ji. Granny ta ƙirani ta min jaje sosai tare da nata salon nasiha,bayan kwana biyu su Anisa da Fadila da kuma mahaifiyarsu Haj.Jummai suka zo suka mana ta'aziya washe gari kuwa ana sadakan uku suka shirya komawa Azare hadda yaya Fawas muna zazzaune a tsakar gida Adda Barira ta fito a guje Ummi da Haj.Jummai suka riƙota sai fizge-fizge takeyi tana ƙoƙarin keta kayan dake jikinta ganin baza su iya ba yasa su ƙiran Daddy da Baffa suka shigo duk yanda suka so zaunar da ita hakan ya gagara duk ta keta suturar dake jikinta ta figi hanyar waje da gudu. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!Barira ke kuma haukacewa kikayi Allah ya kawo miki sauƙi"furcin Inna kenan dai-dai nan Sayyid da Fadila da suke zance a waje suka shigo suna tambayar lafiya.nan Baffa ya ƙira Liman ya ƙara manaa nasiha mai ratsa zuciya akan cin amana da haɗarurrukanta,wanda ya sanya ni jin komai na rayuwar duniya ya fice mini a rai. Ranar da Yamma su Yaya Fawas suka koma azare washe gari muma mukeda niyyar wuce katsina sosai na keta kukan daya riƙe mini ƙirji sanda zamu tafi muna sallama da Inna da ƙyar na raba jikina da nata sannan muka tafi,Motar Sayyid muka shiga nida Ummi,Habib kuwa sun rigamu wucewa shida Daddy.Muna isa cikin Katsina muka wuce gidan Daddy Ummi na riƙe da Mu'afsa muka fito daga cikin motar muka nufa cikin gidan kaina danaji yana sara mini da matuƙar ƙarfi na dafe har muka kai ga shiga falo kai na tsaye na wuce ɗakin Yasira na shiga bathroom na sakewa kaina ruwa lumshe idona nayi a hankali ina tinano abubuwa da yawa da suka faru a rayuwata.na daɗe a wannan yanayin kafin na ɗauro towel na fito doguwar rigarta na zata har ƙasa sannan na tada sallan zuhr,ina iddarwa na fito na wuce kitchen zan haɗa mana lunch Habib da Daddy suka shigo ledar dake hannun Habib nayi saurin karɓa ina yiwa Daddy sannu da zuwa ya amsa mini yana yalwata annurin dake saman fuskarsa. Basu daɗe da shigowa ba Ummi ta fito riƙe da Mu'afsa tana ganinta ta fara sakin dariya tana ƴar tsalle-tsalle na karɓe ta,Ummi na ta mata tsiyar taga uwarta dole ta ƙita.kitchen na wuce na jujjuye abinci da Habib yayi order sannan najesu akan dinner duk muka taso muka zauna zaman ci.juya cokalin kawai nakeyi amma na kasa ci Ummi data lura dani ta jawo plate ɗin gabanta ta fara bani da kanta wani abun dana kasa fasaltar ma'anar sa ya dirar mini a rai inama ace Ummi mahaifiyata yanda take bani kulawa haka.muna gama cin abincin Habib da Sayyid suka tattare wajen Ummi na musu tsiyar sun zaman yan daudu basu da aiki sai aikin mata.Falo muka dawo muka zauna muna hira wanda duk akan cin amana irin na ƙarin mutum ne da kuma yanda tsoro Allah yayi ƙaracin a zuƙatan al'umma jifa-jifa nake soma bakina acikin hirar tasu.Sayyid yaɗan musguta yana fuskanto Daddy sosai yace"Daddy daman Fadila ƙanwar Yaya Fawas ce mun dai-dai kanmu da kanmu nakeso manya su shiga cikin lamarin a tsaida magana tunda yanzu yana ajin ƙarshen a makarantar sakandiri"yakai ƙarshen zance yana sunkuyar da kansa ƙasa yana ƴar dariya. "Babu komai zamu tattauna maganar da Granny sannan mu tsaida ranar zuwan namu".cikin saurin Sayyid ya ɗago kansa yana faɗin"Nagode Allah ya ƙara girma da nisan kwana masu albarka".duk muka amsa da amin kafin nace"Ah to lalle yanzu ya kamata a ninka biyayyar da ake min dan na zama surika tun yanzu". "Ai daga yanzu kin zama babbar Anty,Allah yaja da kwanankin Antynmu"cewar Sayyid maganar sa ta samu dariya sosai Ummi tace"banda lalacewa zamani wai ace yaro dashi ake maganar aurensa mu lokacin mu mijinma bazaki sanshi ba sai bayan an ɗaura an kaiki ɗakinki kuma a hakan ake zaman lafiya".Habib yace"Haka ne kam Ummi ku ai lokacin ku ƴaƴan akwai haƙuri amma gaskiya mukam bazamu yarda da wannan tsarin ba yanzu"Ummi ta kai masa duka a kafaɗarsa yayi saurin gaucewa yana dariya haka nan ma muda Sayyid.Maganar da Daddy ya soma yi ya katse mana hanzarin mu gabaɗaya"Hajiya na manta ban sanar da kuba Habib kawunka Isma'il na nijar yamin magana akan Amina cewa yasano a bashi dama ya shiga cikin manemanta,gobe Hajiya zakuje ki sanar da ita duk yanda kukayi sai ki faɗa min na kuma sanar dashi". Washe baki har kunne Ummi tayi kana tace"Kai Alhamdulillah lamari yayi daɗi wallahi Allah ya haɗa kansu idan shine mafi alkhairi ga Amina"duk muka haɗa baki wajen furta kalmar amin,na tabbatar idan Anty Amina ta auri kawu Isma'il zata huce takaicin aurenta da Malam Habu gashi daman naji Farida nacewa matarshi mahaifiyar su Nabiha shekara ɗaya kenan da rasuwarta Adda Hanne ta sako shi gaba akan batun ƙarin wani auren Allah ya tabbatar da wannan auren ni kaɗai nayi maganata kuma na amsa abina.nan muka cigaba da hirar har aka ƙira sallan Asr sannan su Daddy suka fita masallaci nida Ummi duk muka wuce ɗaki,sai danayi sallan magrib sannan na fito na haɗa mana dinner na jeresu akan dinning sannan na koma ɗakin Ummi na tarda ita tana wanka a Mu'afsa tagama tana tsantsameta da towel na iso na zaune gefen gadon ina cewa"Ummi wanka kuke yine?"tace"Eh wallahi na bata madarar tane shine na mata wanka nasan babu jimawa zatayi bacci".sai data shirtaya muka fito zaman jiran dawowarsu sannan muka ci abinci mukayiwa juna sai da safe muka kwanta ranar mun taba dare muna waya da Habib sosai wanda hakan yasa naji dul damuwata ta hau. Sai da akayi sadakan arba'in ɗin Yasira sannan muka koma gida na sanar da Hajja komai ta cika da mamaki tana ƙara gaskata wannan kalmar ta malam bahaushe da yake cewa"Makashinta na tare dakai".zuwar Granny sadakan suka tattauna da Daddy akan maganar turawa nemawa Sayyid auren Fadila,ta kuwa amince domin ta yaba da tarbiyarta.ni nake sanar da Anty Amina magaanar Kawu Isma'il. "Hibba nifa yanzu wallahi lamarin aure ya fice mini a rai kwata-kwata gwara nayi zamata a gidanmu na iya bautar Allah har lokacina ya iske ni".nace"Anty Amina ai shima auren wani nau'in bautar Allahn nan,dan Allah ki bashi dama wallahi zakiji daɗin zama dashi".ta numfasa kafin tace"to babu komai zamuyi maganar da Abba duk yanda yace hakan za'ayi".naɗan murmusa nace"Yauwa Anty muzo daura musha biki ba"tayi saurin katse ƙiran cike da kunya. A cikin satin daya kama su Daddy sukaje nemawa Sayyid auren Fadila a azare,watannin uku aka sanyan da zaran da ƙare makaranta da wata ɗaya kenan,satin sama kusa mutan nijar suka dira a daura neman auren Anty Amina sosai Malam Mahira ya yaba da dattakunsu aka tsaida da lokaci nanda sati uku dan baso ake yaja lokaci ba.a san nan fa Aliyu Haidar ya bayyanar da soyayyarsa da Anisa da duk dangi. UWATACE SANADI Tsarawa/Rubutawa ©Maimunah Tijjani Iyam ___________________________ Page 6⃣0⃣ Cikin wannan satin muka fara jarabawar ƙarshe a makaranta,duk da har yanzu mutuwar Anty Hajara bata gama bari raina ba amma na maida hankalina kaf ga karatu zuciyata tana yawan hashasho mini ina gab!da cika burin Abba da Yaya Fawas na zama cikakkiyar ma'aikaciyar aikin jarida.ranar na dawo gida a gajiye dan sai jarabawar ranar ta caza mana kai sosai gashi yamma ta fara kawo kai,a hanyata ta dawowa gida traffif line ya tare ni lokaci zuwa lokaci nake saki siririn tsaki ina jijjija Mu'afsa da duk ta gama yin laushi tsabar gajiya tana kwance a gefena acikin motar. Kona da iso gida na iske motar Habib a cikin parking space hakan ya tabbatar mini har ya dawo na saɓe Mu'afsa a kafaɗata sannna nayi cikin gidan da sallama ɗauke akan leɓɓana na turo ƙofar falon na shiga yana tsaye a dinning ya amsa sallama kafin na isa gareshi har ya tako gabana ya karɓi Mu'afsa nace"Gorko am girki kayi haka kai daka dawo daga office nasan kuma ka gaji,ai daka bari na dawo na mana"nakai ƙarshe ina shagwaɓe fuska ya shafo kuncina haɗin da cewa"Debbo am ai naga na dawo da wuri ne kuma babu abunda nakeyi shiyasa nace yau dai kaɗai bari na hutar dake na mana girkin"na rusunar da ƙwayar idona ƙasa kana nace"shiyasa ako yaushe bana shakkar bugan ƙirji nace mijina na daban ne ko a cikin ƴan maza".ya riƙo hannuna muka ɗauki hanyar bedroom har mun kai ga ƙofa yace"shiyasa nima ako yaushe idan na rasa wani abu sai naji cewar Allah ya mini gata fiye da duk wani ɗa namiji a duniyar daya azurtani da samu nagartacciyar mata". na rausayar da kaina cike da kunya sannna na fara yiwa Mu'afsa wanka sannan na shiryata suka fito falo sannna nima na shiga wanka sai danayi sallan magrib sannan na fito na amshi Mu'afsa ya fita masallaci karatun jarabawar da muke dashi gobe na farayi yayin da na ajiye Mu'afsa akan kekenta na koyan zama. Sai bayan isha'i sannan Habib ya dawo mukaci abincin ina ta yaba daɗin da abincin yayi shi kuwa sai dariya yake mini haka muka kammala muka kimtsa wajen sannna muka dawo falo muka zauna. "Gaskiya ya kamata na yiwa Ummi magana a samo mana mai raino,ke ki huta ga makaranta ga kuma aikin gida".na gyara zaman Mu'afsa akan cinyoyina tana zuƙar madararta kana nace"Nagode Allah ya saka da alkhairi amma Mu'afsa amana ce a gareni tun ranar data zo duniya,zanzo ace ni nayi dawauniyar ta da kai dan na cika yaƙinin Yasira a gareni".ya riƙoni haɗi da cewa"haka ne Allah ya raya mana ita"na amsa da amin. Haka na washe gari kafin na tashi Habib ya gama haɗa komai na karin kumallo mukaci kafin na shiga nayiwa Hajja sallama ya sauƙe ni a makaranta.haka rayuwa ta cigaba da juyawa a gareni izuwa yanzu kam zan iya cewa Habib ya maye mini gurbin duk wani abunda na rasa a baya,baya barina nayi ƙunci balle ruwan hawaye ya zuba daga idaniyata.ana cikin haka bikin Anty Amina da kawu Isma'il ya taso,Daddy shi ya ɗauki nauyin yi maka kayan ɗaki gabaɗaya ni kuwa na haɗa mata kayan kitchen sosai da kuɗin da Habib ya bani nayi amfani dashi. Ban sama zuwa bikin da wuri ba dan har sai da su Ummi suka rigani zuwa saboda jarabawar da mukeyi sosai na maida hankali ga karatu saboda itace ta ƙarshe,sai ranar ɗaurin auren Habib yazo ya ɗauke ni a makaranta Mu'afsat kuwa tun safe damuje wajen Ummi suka tafi dauran da ita kafin na zana jarabawa muma muzo.sosai yake sharara gudu akan titin dan ya sama ɗaurin auren cikin ƙanƙanin lokaci kuwa muka iso a ƙofar gida ya tsaya da ƴan ɗaurin aure suka cika maƙil!ni kuwa na shige ciki bayan mun gaisa da Aliyu Haidar dasu Khalifa wanda suma suka zo ɗaurin auren. Ɗakin dasu Ummi suke na nufa a gurguje nayi wanka na sauya shiga muka zauna dasu Ummi da Anty Amina har Balaraba tazo dai-dai sauƙowa daga sallan juma'a aka ɗaura auren kuma a lokacin za'a wuce da Amarya maraɗi,iyaye suka fara mata nasiha hadda Ummi ina riƙe da hannunta muka fito waje wajen motocin dasuka zo ɗaura amarya sai da ta shiga motar kafin na ƙara yalwata fara'ar fuskana nace"Allah ya bada zaman lafiya,Allah ya kauda sharri ya kawo ƙazantan ɗaki".can ƙasa ta amsa da amin tana ƙarawa da cewa"saura kuma kar kizo min". "In sha Allah zaki ganni"nafaɗa ina maida marfin ƙofar ina rufewa.ƙanwar mahaifiyarta dana Malam Mahiru sai kuma Balaraba su kenan suka tafi kai amarya sai da motar ta ɓace mini daga gani kafin ya ɗauki hanyar shige cikin gidan maganan da Aliyu Haidar ya fara min ya sani waigo tare da Habib suka taku inda nake tsaye. "Kinji mutuminki ko wai ya matsu a aure nashi auren".na saki murmushi kafin nace"Ai kuwa dai zama mu fasa baki shida ko gaisuwa baya zuwar mini,kaga Sayyid ai daya iya allonsa zai kwance yasha".shima taƙaitaccen murmushi ya saka haɗi da cewa"With all respect Antynmu ina miƙo gaisuwa"kafin nayi magana Habib yayi saurin faɗin"Bamaso sai dama kuma ƙora". Haɗe rai yayi yana watsawa Habib idanunsa na mazan fama yace"Ai bakai a ciki,Antynmu nidai yanzu zan tafi a taya mu da addu'a. "Allah ya kiyaye hanya Allah ya tsare"duk suka amsa da amin sannnn ya miƙo min Mu'afsa dake hannunsa"Antymu wannan yariyar ta shiga raina fiye da zato wallahi,kodai zaki bani ita ne".na gwalo idanu waje nace"Lalala!wannan kyautar da wuya domin Mu'afsa wani bangare na jikina ne kai dai zan baka Anisa naga salon naka kiwon tukunna".Duk suka murmusa kafin ya ciro ɗaurin kuɗi ƴan dari bibiyu yace a sayawa Mu'afsa Sweet nayi godiya sannan mukayi sallama da Khalifa suka tafi na koma wajen su Ummi a cikin gida. Sai da mukayi sallan isha'i kafin muka baro daura Mahaifiyar Anty Amina tayi ta yiwa Ummi da Daddy godiya haka nan ma Malam Mahiru musha albarka daga bakinsa,Gidan Daddy duk muka sauƙa a part ɗinsa. Kwanaki biyu a tsakani da dawowar mu daga daura ranar ina makaranta nabar Mu'afsat wajen Ummi saboda ba daɗewa zanyi ba,mun fito daga exams Hall na ciro wayata daga jakana missed call ɗin Habib huɗu a wayata,Yaya Fawas kuwa shida Ummi biyu na ruɗe zuciya na raya mini ko wano abunne ya kuma faru.nayi saurin faɗawa cikin mota na tada ita na kuwa hau titi sosai nake sharara gudu har na iso ko parking ban gama dai-daitawa ba na fito a falo na iske dukkansu cike da mamaki nace"Yaya Fawas yaushe kazo?".Ummi ce ta amsa min da cewa"An sama labarin Mahaifiyarku ne a can jahar Zamfara shine yanzu zamuje".zuciyata tayi mumunan tsikewa saboda mafarkin danayi akan Umma daren jiya tana cikin mummunan yanayi. Ban kuma furta wata kalmar ba Daddy yace"Hibba ki kwantar da hankalinki in sha Allah zakuje ku sameta cikin aminci kuma ga Hajiya ma da ita zaku tafi da Sayyid nima gobe zanje Damaturu na sanar da Granny,a cigaba da addu'a.maganar jarabawar da kukeyi kuma zansa a zana miki har ku dawo". Kaina kawai na jinjina sannna muka fito daga falo nida Ummi muka shiga motar Sayyid.Habib da Yaya Fawas kuwa suna mota ɗaya sosai ya kwantar mini da hankali tare da mana fatan sauƙa lafiya bayan ya ƙara jaddarawa Sayyid cewa da zaran mun isa ya ƙira shi ya faɗa masa.haka muka ɗauki hanyar jahar ZAMFARA tunda muka fara tafiyar na nema nutsuwata na rasa ko abincin da Sayyid ya tsaya ya sayo mana kasa ci nayi rabunmu da Umma shekara goma kenan da ƴan kai yau gani hadda aure da ƴa. Kukan zuci nake yi mai matuƙar raɗaɗi da ƙuna sai yamma sosai muka isa cikin jahar zamfara gidan wani aminin Daddy muka sauƙa nan matar nada kirki aihun dan ta tausaya mana matuƙa muka kwana sannan da safe muka fara shirin nufar ƙaramar hukumar ƙauran Namoda nan akaji labarin Umma,tsakanin jiya da wayewar safiyar yau na fahimci akwai abunda Habib da Yaya Fawas suke ɓoye mini to menene shi?tambayar dana watsawa kai kenan kenan dana kasa karantar amsarsa a fuskokin Habib da Ummi.da wuri muka isa cikin ƙauran namoda muka zarce wata unguwa mai yawan cunkoso da yalwar halittu birjin da Sayyid yaja ya sani ɗauke kaina ƙarewa yanayin unguwar kallon dana keyi Ummi ta faɗa surfa masa faɗan yayi duƙi da ita a hankali duk muka fito ina goye da Mu'afsat.koda da kuskure Habib bai yarda muka haɗa ido ba haka nan suka wuce daga nida Ummi muna biye dasu.tsukakkene gida ne mara yalwan fili wata dattijuwa muka iske tana dama koko a ƙofar ɗaki sallamar da muka shigo da ita ya sanyata watso ƙwayoyin idonta akanmu sannan ta amsa dana binmu da kallon rashin sani muka ƙariso muka zauna akan tabarma dake yashe kusa da ita. "Bayin Allah ban shaida ku ba daya ke idon tsofa ba gani nake dasu sosai ba,Allah dai yasa ba wani masifar Bashari ya ɗauko min ba". Habib ya ɗan musguta kana yace"Baaba daman shi Basharin muke nema Allah yasa yana nan". Sai data zame daga zaman datayi kan dakalin ƙofar ɗaki izuwa bakin tabarmar sannna ta shiga faɗin"Bashari baya nan amma bana raba ɗayan biyu yana can wajen shaye-shayensa sai anjima kuma zai dawo ya ɗauki wannan matar dayazo ya jibge mana a gida ya tafi yawon bara da ita". Cike da wani irin hanzari Yaya Fawas yace"Ina matar yanzu zamu iya ganinta" sai datayi nisa kafin tace"ya gargaɗe ni akan ko ɓako nayi kar na sake na sanar dashi zaman matar nan a cikin gidan nan,amma inkun tabbata cewa cikinku.babu ɗan sanda zan nuna muku ita".sai a sannan Sayyis yace"Meyasa mu zaki nuna mana ita bayan kince ya hafa miki sharaɗi akan hakan?". "Ɗan nan saboda nagaji da ganin yanda yake yaudarar mutane da sunan cewa mahaifiyarshi ce suna buƙatar taimako,har yake yaudarar masu raunin zuciya akan hakan sau ɗaya ya lamince min na bata abinci kullum tana ɗaki,ranar daya shawo giyar har fyaɗe yana mata.Bashari maraya ne dukkan iyayensa suna ƙasa kakarsa ce ta bangaren Uwa amma baya ganina da kima dan Allah ku ceci rayuwar baiwar Allahn nan ku fitar da ita daga cikin gidan nan".sakake na tsaya ina bin bakin wannan matar da kallo muda mukazo neman Umma kuma mezai kawo mu nan,wacece wannan matar da suke magana akanta meye haɗin tafiyarmu zuwa Zamfara da ita?.maganar Ummi ta dawo dani daga wannan tinani na ƙwaƙwalwata"Dan Allah ko zaki fito mana da ita muganta". "Bazata iya fitowa ba domin ko tsayiwa akan ƙafafunta bata iyawa balle har ta taka su,sai dai ku taso mu shiga ɗakin tare". Ummi ta riƙo hannuna bayan ta amsh Mu'afsa ta damƙata ga Sayyid duk mukabi bayan wannan dattijuwar,a ƙofar ɗakin muka tsaya tashiga waiwaigen dutsin da zata ɓalle kwaɗon da aka garƙamawa ƙofar,Habib ya ɗauko wani dutsi ya shiga ɓalle kwaɗon sannan ya cire shi ya yar gefe guda duk muka ɗuru cikin ɗakin nikam fargaba da kuma tsoro sun kwashe kaso mafi girman yawan a zuciyata.yayin da bangare guda kuwa nake cike da tsagwaron mamaki. Sautin kukan da yaya Fawas ya fara fitarwa a hankali ya sani kai gubana ga matar dake shimfiɗe akan fasheshshen simitin ɗakin,gefenta ɗaya ya janye bata motsa shi gabaɗaya ga ƙanjame ko wani mai cutar sidan ya fita kyawub gani,fatar jikinta duk ta nannaɗe wuri guda halittun jikinta sun sauya matuƙa inka ganta zakace yariyace ƴar shekara tara saboda yanda ta kuma ƙanƙancewa jiri ya shiga ɗebata na fizgo numfashina da ƙarfin gaske nace"UMMA"na nufota a matuƙar gigice cak!na ɗage yaya Fawas daga kusanta ko nima bansan inada wannan ƙarfin ba sai yau,na ɗagota daga cikin wannan yashin ɗaki na rungume a ƙirjinaYaya Fawas ya zare babban rigarsa,ya rufa mata a jikinta da babu komai dangin sutura.ɗimin hawayen dake sauƙa ajikina yana ratsa ni duk ɗakin kuka mukeyi har kakar Bashari,na ɗago ta daga jikina ina share mata hawayen da take yi"Umma ki daina kuka ga munan munzo kinga Hibba ce ga kuma Yaya Fawas"na kai ƙarshe ina janyo hannun Yaya Fawas na haɗɗ da nata na riƙe na daɗe banga hawaye a fuskar Yaya Fawas ba ko sanda Abba ya rasu baiyi irin wannan kukan ba. Ganin yanda numshina ke fita da wani irin ƙarfi da kuma ƙara yasa Ummi isowa gareni ganinta kusa dani yasani tsananta kukana nace"Ummi kinga Umma ce a cikin wannan ƙaramin yanayin daman na daɗe ina mafarki da ita cikin mummunan yanayi"nakai ƙarshe ina kwanto da kaina jikin Ummi ta fara bubbuga bayana cikin sigar lallashi hawaye na zuba mata. "R-R-Ruwa-a-a"Umma ta faɗa dalla-dalla,kakar Bashari ta fita da saur i ta dawo da kofin ruwan a hannunta ta fara bata,na ɗago na karɓa ruwan na fara bata da kaina dan gani nayi kamar bata sanya mata a bakinta,"Mukai ta asibiti a duba ta"cewar Habib. "Yaro ku barni!ku barni!!,ko yanzu na mutu na mutu cikin farin-ciki naga ƴaƴana"wannan maganar ya ƙara sanya mu sakin wani kukan.ta mana alama nida Yaya Fawas akan muzo muka matso kusanta sosai ta shiga faɗin"Ban kasance irin uwar da ƴaƴanta zasuyi alfahari da ita ba,ban kasance cikin matan da mazajensu suke alfahari da samun su ba.ban ciba ci rayuwata tun lokacin ƙuruciya ba har girma ya zo min.na cece ku dana kasa baku tarbiya kamar kowacce uwa na kasa janku a jiki kamar ko wasu ƴaƴa.nayi nadamar yakice ku daga jiki danayi nayi nadama yanda na galzawa rayuwar Sule da abunda ya tafi na bari.sai danaga sakayya tun anan gidan duniya Allah ya nuna min iyakata,bayan aurena da Cindu sabon mijin dana aure duk da ba musulmi bane akan bai hanani aure sa ba muka tattata muka koma can garinsu Edo a nan na gane ɗan ƙungiyar shan jini ne na nemi ya bani takardata ya hanina daga ƙarshe ya kulle ni a ɗaki babu ci babu sha ko ranaa bana gani.wata rana nayi nasarar fice daga gidan cikin duhuwar dare nayi tafiya na tsawon lokaci da ƙafata.amma sai daya cin mini ya ɗaureni ya bamar gidan ranar ya duke ni kamar bazai barni da numfashina ba ya maida ni ɗakin ya kulle duk wayewar safiya sai y kawo wasu ƙattin maza uku dukkansu sun kwanta dani,bayan wani lokaci cikin dare ya fito ya yasar dani bakin titi wasu samarin mashaya mukayi zina dani a baina jama'a amma babu wanda ya kawo min ɗauki.wani mai mota ya ɗauki ya kaini Lagos ya yar dani a bakin gada anan na fara bara a bakin danger,inason dawowa potiskum amma kona mota bani dashi,ciwo yaci ƙarfina har yakai banayi fitowa barar wata rana mota ta kaɗe ni ya kuma tsere aka kaini asibiti aka tabbatar ina ɗauke da cutar mai karya garkuwar jiki sannan akwai ciki dake maƙale ƙasan marata.tun da aka sanar da wannan batun suma waɗanda suka kawo ni asibitin basu ƙara waiga taba,cikin dare na gudu daga asibitin saboda banda kuɗin dazan biya su,na zubar da cikin ta hanyar ɗirkawa kaina ruwan gishiri.na kuma haɗo ciwon shanyewa ɓarin jiki shine muka haɗo da jikan wannan baiwar Allah daga lagos ya ɗauko ni izuwa nan zamfara ya fara yawo bara dani da sunan mahaifiyarce ni muna buƙatar taimako domin lalurar danake ɗauke da ita,mutane da yawa sun tausaya mana su ɗauki kuɗi su bashi,ya dawo dani cikin wannan ɗaki ya kulle da dare kuwa ya min fyaɗe ta ƙarfi".ta ƙarishe wani tari mai ƙarfi yana sarƙeta kakar Bashari ta fara bata ruwa,a hankali na zame jiki daga na Umma zuciyata tana luguden tara-tara wai daman duk maganar dasu Habib sukayi a waje akan Umma ne?innalillahi wa inna ilaihir raji'un,a gaban mijina da kuma surikata Umma ke irgo mana adadin mazan da sukayi lalalata da ita.haɗuwar ta farko kenan da Umma amma da wannan baƙin labarin kunnuwansu suka fara saurara,na tausaya mana nida Yaya Fawas matuƙar tausayi domin mu ababen tausayi ne.ji danayi kamar ana shigowa cikin gida duk muka baza kunnuwan mu ɗauke da wakar RUSH na mawaƙiya AYRA STAR a bakinsa ta shigo a buge tatil"Jar uban can wani ɗan kutumar uban ne ya buɗe ƙofar ɗakin nan, bana ce kar wanda ya kuskura ko kusan ƙofan nan yazo ba ina Kakan ne Dija mai masa kina inane?". Duk jikinta baiɗaya ya ɗauki rawa ta fita waje ta same shi tana faɗin"Bashari ne ya dawo". Wani irin huci yaya Fawas yake fitarwa ya miƙe yabi bayan Kakar Bashari,yana daga tsaye yana yalinsa na wanda yake a shaye Yaya Fawas ya damƙo wuyarsa ya fara kakakin mutuwa ya shiga kai masa duka ta ko'ina yayin da Sayyid ma ya fito ya jona shi sosai suke dukansa.duk muka fito babu abunda Kakar takeyi sai kuka tana faɗin"Dan Allah kar ku kashe min shi,wallahi shi kaɗai nake dashi a duniya duk iyayensa sun rasu maraya ne.ku masa kowani irin hukunci amma dan Allah kar ku rabani dashi". Ummi ce ta riƙo Yaya Fawas yana janye shi Habib kuwa ya riƙe Sayyid duk da hakan basu daina kaiwa Bashari duka ba.Yaya Fawas da yayi nasaran ƙwace daga riƙon da Ummi ta masa ta zari bukacin ƙarfe dake gefe ya makawa Bashari a goshi,jini ya fara tsiyaya ya ɗaga da niyyar sauƙe masa a karo na biyu kakar tasi saurin shiga tsakaninsa da Bashari kula takeyi sosai tace"inba kashe shi zakayi ba ka barshi haka idan dukan da kuka masa bai ishe ku gani nima ku daka,nasan Bashari ya aikata kuskure babban kuma ya cancanci tsatstsauran hukunci". Sauƙe bokitin Yaya Fawas ƙasa ya faɗi yana hucin ɓacin rai,ban taɓa sanin Yaya Fawas yanada taurin rai irin yau ba koda yake bahaush yace "IDAN ANA DARA FIDDA UWA AKEYI". "Wallahi wallahi sai ka kwana a hannun ƴan sanda sai ka girbi abunda ka shuka dabba kawai dan ko dabba bazai aikata abunda ka aikata ba,in sha Allah sai kayi wulaƙantaccen ƙarshe".cewar Sayyid ya faɗa yana nashi hucin kwance a ƙasa cikin jini suka bar Bashari numfashinsa na fita ɗai-ɗai ga goshinsa dake fitar jini har yanzu ihun da Ummi ta saka ya sanya mu shigewa wajen Umma a guje as ones.duk jikinta ya ɗauki rawa Habib yace mu fito da ita mu tafi asibiti haka nida Ummi muka ɗauko ka izuwa wajen inda muka faka mota muka shiga da ita nida Ummi. Sayyid ya jawo Bashari kamar kayan wanki ya saka shi a booth ɗin mota kakar sa sai makiya take masa amma kota kanta bai biba,da mungun gudu muka isa asibitin aka shiga da Ummz yayin da likitoti suka rufu akanta domin jefo rayuwarta,nan ƙiran Daddy ya shigo wayar Ummi lokacin daya ƙira yana tare da Granny"Hajiya wai meyake faruwa,na ƙira wayoyinku dukkan bakwa amsa ƙira,ina fatan an dace?". Wani numfashi mai nauyi Umma ta fesar kafin ta shiga bayyanawa Daddy duk abubuwan da suka faru,daga shi har Granny babu wanda tausayin Umma bai dirar masa a rai ba.Daddy yace"Yanzu ina Sayyid ɗin yakai shi yaron". "Ina kyautata zaton afishin ƴan sanda ya wuce dashi tare da Fawas suka tafi".ya kuma cewa ta haɗa shi da likitan asibitin suyi magana,a Habib ta miƙawa wayar ta sanar dashi yanda sukayi da Daddy,ofishin likitan ya nufa bansan mai suka tattaunaba suka fito tare likitan yake sanar da Ummi cewa.sunyi magana da Daddy yace yanzu su mata abunda ya dace zuwa gobe mun taho katsina daga nan kuma zai shirya mana yanda zamuga doctor a ƙasar moscow. Haka akayi su kayi ƙoƙarin dai-daita numfashinta ta hanyar maƙala mata robar iska.Yaya Fawas da Sayyid kuwa ofinshin ƴan sanda suka miƙa Bashari ga hukuma DPO ɗin division ɗin ya tabbatar musu da doka zaiyi aiki.sai yamma sosai sannan suka dawo asibitin,bayan isha'i haj.Rashida matar aminin Daddy tazo ita da ƴaƴanta mata biyu,Ummi ce take kwatanta mata asibitin awaya har dare ta tsala basu barmu munga Umma ba sai dai mu leƙe ta ta window. Tsawon dare wannan ranar ban iya tsurawa ba har akayi ƙiran assalatu farkon na tashi sai danayi sallah kafin na tada Ummi ma tayi nayiwa Mu'afsa wanka zuwa ƙarfe bakwai duk mun shirya,nurses suka fito da Umma aka sanya ta cikin motar Habib robar ƙarin ruwan da aka mata yana nan a jikinta.nida Ummi kuwa motar Sayyid muka shiga sai da muka jira dawowarsu daga ofishin ƴan sandan da sukaje shida Yaya Fawas.daren jiya Habib ya ƙara mokawa wajen Kakar Bashari ya kwantar mata da hankali sosai tare da bata tallafin kuɗi. Motar Habib Yaya Fawas ya shiga yayin da Sayyid yake jan motar da muke a ciki nida Ummi,tana riƙe da Mu'afsa akan cinyarta nidai gabaɗaya hankali da nutsuwata sunyi ƙaura daga gangan jikina,har mubar cikin jahar Zamfara muna dab da shiga cikin Zaria Sayyid ya amsa wani ƙiran da daga ni har Ummi bamu da masaniyar da wanda yayi ƙiran. Salatin dayake jerawa ɗaya nabin wani ya sanya Ummi tambayar sa lafiya?,ya faka motar a gefen titi ya juyo ya kalle ni hawaye yana taro masa a ido nace"Sayyid lafiya wai meyake faruwa ne dan Allah ka sanar damu". Shuru yayi na tsawon mintuna biyar kafin yace"su Hamma ne sukayi accident". "Innalillahi wa inna ailaihir raji'un a ina sukayi accident?". "Bansani ba domin nima ƙirana akayi da wayar Yaya Fawas ake sanar dani yanzu".Motsi mai kyau na kasa yinsa bakina ya shiga karkarwa saboda tsananin sun furta abunda yake raina,nayi nasarar jawo numfashi na daya fara nisa da gangan jikina nace"ina fatan ba wanda ya rasa rai"ya ɗaga kansa alamar bai sani ba.aka ƙara ƙiran wayarsa babu jimawa ya katse ƙiran,ya ƙira Daddy ya gaya masa yace shima yanzu aka ƙirashi aka sanar dashi,yace ya airpot yanzu ya sama mana jirgin da zaizo katsina ya biya mana nida Ummi mu dawo shi kuma ya wuce inda akace sunyi accident ɗin. Haka muka wuce cikin Kaduna muka zarce airpot,Sayyid ya ƙira Daddy ya haɗa shi da Managern wajen sukayi magana.nan da nan aka sama mana jirgin katsina muka shiga sosai Ummi ta tsorita saboda yanda numfashina yake shiɗewa.Muna isa cikin katsina malam Habu yazo ya ɗauke mu a airpot muka wuce gida,Daddy kam daga can Damaturu ya wuce kadunan. Tunda muka shiga cikin gidan nakasa zama safa da marwa kawai nakeyi nakai mari nakai bango,Ummi ta kalloni da idonunta da suka bayyanar da zallan tausayina tace"Hibba ki kwantar da hankalinki in sha Allah babu wani mummunan abunda zai faru".nazo kusanta hawaye nabin kuncina nace"Ummi dan Allah inma sun mutu ne a sanar dani wallahi zan ɗauki ƙaddara aduk yanda tazo mini".nakai ƙarshe ina kwanto kaina saman ƙirjinta ta fara lallashina. Wunin ranar cur daga ni har Ummi bamuda kwanciyar hankali,mu ƙira wayar Sayyid da Daddy yafi sau shurin masaƙi amma basa ɗauka Ummi ta ƙira Granny tace itama tana hanyar zuwa katsinan,yamma sosai Granny ta isi muna zaune a falo kowa da abunda ke ransa mukaji ƙaran shigowar mota duk muka miƙe zumbur muka fito harabar gidan,motoci uku ne suka shigo ɗaga daga ciki motar asibiti ce duk suka faka.ganin Yaya Fawas ya fito daga cikin motar asibitin Habib na biye dashi duk hannayensu da bangeji Habib shikam har goshinsa ga ƙafarsa ɗaya da yake ɗingisata. Na ruga a guje na isa ga Yaya Fawas cikin kukan dana ɗau lokaci inayinsa nace"Yayana ance kunyi hatsari ina Umma fa?".ya ɗaura kansa a saman kafaɗata tana hawaye na ɗagoshi nace"Dan Allah Yaya Fawas ka taimakawa zuciyata wallahi tana dab!da faso ƙirjina ta fito,ka sanar dani ina Umma". "Hibba sai dai muyi haƙuri Allah ya fimu son Umma shiyasa ya karɓi abunsa".bazan iya tantance muryar waye naji yana faɗin haka ba,a tsakanin Yaya Fawas Habib ko Sayyid.ƙirjina ya buga da tsatsan ƙarfi daga nan ban kuma sanin inda kaina yake ba. Sai buɗe idona nayi naganni a gadon asibiti maganar rasuwar Umma ya fara mini sowa a kunnuwana,Inna dake zaune kusa dani suna magana da Ummi da Yaya Fawas ta lura da buɗe ido da nayi.ta fara jefo mini sannu babu ƙauƙautawa ganin Yaya Fawas ya sanyi ƙoƙarin tashi daga kwanciyar danayi nace"Yaya Fawas dan Allah ka nuna mini Umma ka kaini wajenta,wallahi inaso inayi mata kallon ƙarshe".ya zauna tare da riƙo hannnuna"My Cute angle haƙuri zamuyi Umma ta amsa ƙiran ubangiji abunda yatafi buƙata daga garemu shine addu'a shi yazamu cigaba da mata". "Hakane Hibbatu Allah ya jiƙan Juwahir ya yafe mata kurakuranta"cewar Inna cikin maganganun da suka cigaba dayi na fahimce cewar har anyi sadakan uku na rasuwar Umma.wallahi hawaye nakeso su zubo mini amma hakan ya gagara samuwa a gareni sai kukan zuci danakeyi mai tsananin ƙona da yamma aka sallame ni tare da haɗani da wasu magungunan ciwon zuciya muka taho gida,Daddy da Granny muka iske a falo suna zaune muka shigo Granny ta miƙe ta riƙo ni muka ƙariso cikin falon.Mu'afsa dake kwance jikin Daddy daga ganina ta taso cikin tafiyarta dabata daɗe da soma yinsa ta faɗo jikina,Habib ya ɗagota ya ɗauke Daddy yace na matso kusansa na tashi nayi kamar yanda yace. "Hibba haƙiƙa duk mun shaida cewa mutuwa wata halittace na ubangiji,da duk mai rai bazai tsallake ta ba.rashin uwa rashi ne mai matuƙar zafi da ba'a warkewa daga ciwonsa da wuri sai dai haƙuri da karɓan ƙaddara aduk yanda yazowa mutum babban raboce,Allah ya jiƙanta ya kuma bamu haƙurin rashinta".a sanyaye na amsa da amin hawayen idona ya kafe kaf!ko ɗigon ruwar ƙwalla ban fitar ba Daddy ya ɗaura da cewa"Ki cire komai a ranki mu godewa Allah tinda ya ƙaddara saduwa a tsakaninku har an nema yafiyar juna kafin rai yayi halinsa,yanzu kije kiyi wanka ki fito kici abinci".na miƙe da ƙyar jiri na ɗibata Granny tace"Allah sarki!Allah kaɗai yasan raɗaɗin da take a ciki,kukan zuci takeyi". Ina shiga ɗaki na mayar da ƙofar na rufe nan na zauna naci kuka na fitar hankali duk da hawayen basa zuwa,nafi awa ɗaya kafin na tashi na shiga bathroom na sakewa kaina ruwa na ɗauro alwala na fito na tara salla a zaune nayi sallan saboda ƙafafuna da suka matuƙar rawa. Ina iddarwa na shiga zabgawa Umma addu'ar neman rahma,na daɗe kafin nayi shirin kwanciya dan bana sha'awar fita balle zama cikin mutane na fiso na kaɗaita ni kaɗai a halin yanzu.inajin Habib yana knocking a ƙofar ɗaki nayi kamar bazan buɗe ba sannan na tashi na buɗe masa,a bakin gado muka zauna sai daya ƙare mini kallo tsaf!yace"Matar aljanna wannan damuwar ba shi bane mafita,ki miƙa dukkan lamuranki ga Allah shine sarkin da ikonsa ya game komai yanaji kuma yana ganin duk abunda yake faruwa,dan Allah ki tausaya min ki daina saka damuwa arankii kinji Debbo am".na ɗaga masa kaina alamar naji haka ya cigaba da kwantar min da hankali har nayi salama sannan yace na tashi mu tafi part ɗinsa banyi musu ba yaja hannuna muka tafi Mu'afsa na hannunsa. Sai da akayi sadakan Bakwai sannan Granny da Inna suka koma,ranar na fita makaranta na amshi jarabawata.lokacin saura kwana biyu mu gama,a wajen Ummi nake barin Mu'afsa dan yanzu watanta bakwai har tana ƙoƙarin tsayawa,ina dawo daga makaranta na biyo tanan da dare Habib yazo ya ɗauke mu.duk na fita hayyacina ga raman dana zuƙa kullum Habib cikin kwantar mini da hankali yakeyi haka ma Daddy da Ummi,cikin haka muka kammala jarabawa sai ranar na tsinci kaina cikin farin-ciki yau na cika burin Yaya Fawas na zamowa MA'AIKACIN JARIDA,na cika ƙudirin Abba nason muyi karatu ko bayan ba ransa.wani daɗin daya darso a birnin ƙalbina ya sani zama akan ɗaya daga cikin kujerun plastis dake cikin makarantar na tsura kaina cikin hijab ina sakin kukan daban dalilinsa ba.tun rasuwar Umma hawaye suka ƙaurace mini sai yau suka zubo mini nayi shi kuwa kamar ba gobe,ƴan department ɗin sai murna sukayi na kammala cikin yarda mai duka. Sallama nayiwa su Limat Auwal da wasu ƴan department ɗinmu da muke shiri dasu,na ja motata nayi gida dai-dai shigowar motar Daddy isana kenan na fito na jira fitowarsa sannan na isa gareshi na karɓa jakan hannunsa,muka isa falo Sayyid da Habib muka iske suna arranging ɗin dinning suka yiwa Daddy barka da zuwa sannnn Ummi ta fito na miƙa mata jakar na isa ga Mu'afsa dake bacci kan gadonta na yara ina kallon fuskarta"Ayya!ƴar amanata kinata bacci kenan"daga haka na saɓe ta mukayi ɗaki,wanka na farayi na fito nayi sannan Asr a makare sannan na fito falo na taya Ummi fito da kulolin abincin. Nayi serving ɗinsu sai da muka gama ci muka komo falo Daddy yace"Hibba kun ƙare jarabawa yau ko?"na ɗaga masa kaina"Masha Allah,Allah ya taimaka"duk muka amsa da amin. "Kyauta ta farko ga JOURNALIST"ya ƙare yana miƙo mini makullan motoci guda biyu na matso na miƙa hannu cikin nutsuwa na karɓa nace"Daddy nagode sosai Allah ya saka da alkhairi Allah ya ƙara girma da nisan"yace"Amin Ƴar albarkata". Ummi tace"Alhaji motar nan naga ai tanada ita tunda mijinta ya saya mata,ai da wani kaddarar ka sai mata da kuɗin motar dakayi niyyar batan".murmusawa Daddy yayi ya ɗaura da faɗin"Me kikeci na baka na zuwa Hajiya?".ya kai ƙarshe yana ƙara miƙo min wasu takardun daya ciro daga aljihunsa"wannan takardun gidade ne guda biyu da fili ɗaya na mallaka miki shi ko bayan raina". Na rasa bakin godiya tsabar murna kawai nasa kuka Habib ya rusunar da murya yace"Daddy mum gode Allah ya ƙara arziki"duk suka amshe da amin.Sayyid sai murna yake min yana faɗin ya masa motar da zaina aƙa inzashi azare wajen Fadila,Daddy yace kar na sake na bawa kowa motata don ni ya saya bayason ganin kowa a tare da ita.sai da aka fara ƙiran sallan magrib sannan suka fita masallaci,na shiga ɗaki na ƙira yay Fawas na sanar dashi shima ya cika da murna yana ƙara jinjina karamci irin na dangin Habib,sai ƙarfe tara muka bar gidan. Mun raya wannan dare da sunna nida Habib fiye da sauran dararen rayuwar aurenmu da suka shuɗe,washe gari da yamma Sayyid ya haɗa mini walimar murnar gama makaranta ana gidan Daddy har yaya Fawas da Inna haka nan ma Balaraba da Kabir,koda da wasa ban sakar masa fuskaba balle ya sama damar shige min dan har yanzu inajin zafin abunda Kabir yamin a rayuwa.aka taro ya watse kowa ya tafi da murna da sha'awar rayuwarmu nida Habib a raina nake cewa basu san gwagwarmayar da akayi ba kafin ak iso nan.a wajen taron Habib ya gabatar mini da ticket ɗin zuwa ƙasashe uku daya mana na farko saudiyya na biyu Moscow sai kuma spain da zaran an gama bikin su Sayyid zamu ɗaga. Bikin Sayyid da Aliyu haidar za'a farayi dan Yaya Fawas yace sai an farayin na ƙannen nasan tukunan Anisa da Fadila,Daddy shi ya ɗauki nauyi yiwa Anisa da Fadila harma da Farida kayan ɗaki kaf!nida Ummi da Inna da kuma Granny mukaje dubai muka sayo musu furnitures na kece raina dukka kayan iri ɗaya,Ummi kuwa ta lodo musu kayan kitchen sosai anan aka haɗa lefen Sayyid dana yaya Fawas.kwanan mu takwas sannan muka dawo,harkan biki ya kankama ganda-ganda. Inna da Hajiya Jummai da kuma Ummi suka kai kayan ledan Yaya Fawas ga Amaryarsa Farida a ƙasan nijar cikin Maraɗi.kwana huɗu tsakani aka kawo na Anisa lokacin su Granny da wasu ƙannen Ummi hadda Hajja sun tafi kai na Fadila duk suka haɗu a can azare ɗin.kowani shawara Daddy zaiyi sai yayi ta dani haka nanma Ummi da Granny,Tun ana sauran sati biyu Maryam tazo da tsohon cikinta nayita yi mata tsiya.ana saura kwana biyu muka shirya walima washe garin ɗaurin aure kuma in an kawo amarya ayi dinning Anisa ma anan za'a kawota kafin a wuce da ita Nijar ɗin. A cikin harabar gidan aka shirya waliman,ina zaune a ɗaki ina murza hoda a fuskata Mu'afsa na zaune gefena tana game acikin wayata,Habib ya shigo na ɗago na kalle tare da amsa sallamar daya shigo da ita wajen Mu'afsa ya fara isa cikin magananta da bai gama nuna ba tace"Abbi tun ɗazu Ammina take nemanka aka ce mata ba'a ganka ba"ta kai ƙarshe tana ware masa hannayenta muka saka dariya sosai yariyar zata jawo mini ruwa ɗazune nake tambayar Ummi saboda wasu ƴan office ɗinsu da sukazo har zasu tafi basu gaisa ba take cemin ita ma tun safe bata sanya shi a idonta,shine Mu'afsa ta riƙe zancen cikin kanta yariya sai shegen wayo kamar wata babba alhalin ko shekara biyu bata cika ba. An ankara ba nayi ya rungumo ni ta baya tana kallona ta cikin madubin yace"Menen tun ɗazu kike nemana kodai inkiyi missing mijinki a kusa dake ne?"na jaye jikina yace"To Mu'afsan ta fita na aiketa wajen Ummi". "Munje ko kaga yanzu za'a fara walimar"ya riƙo hannuna yana cewa "babu inda zaki".tunda ya furta nasan sai ya aikata nayi raurau da idanu nace"Hamma dan Allah ka fito mu tafi kar Ummi ta fara neman mu".ya saki dariya yana lakuce mini saman kunci na kai masa dukan wasa saboda lip gloss ɗin dake leɓɓana daya lakuce mini.sanda muka fito har an fara gabatar da walimar wanda ya sama halaltar manyan malaman sunna na cikin katsina da kewayenta.Mu'afsa na ganimu ta nufo mu da gudunta Abbinta ya ɗauke ta ya nufi wajen Bashir,ni kuwa na zama kujera kusa da Maryam nazauna.na lura sai murmushi take sakewa ƙasa-ƙasa na galla mata harara nace"faɗi karta kashe ki". "A'a babu komai tattabau uwayen soyayya".na taɓe baki na maida hankali ga jawabin da malaman suke yi.ƙarfe shida na yamma taro ya watse aka shiga gida ranar kwana mukayi babu runtsawa saboda shirye-shirye ɗaurin auren gobe,Habib sai duka mini ƙira yakeyi akan yana jirana a part ɗinsa har sai da Ummi ta gane ta karɓa wayan ta mishi magana ko kanzil ya kasa ce mata saboda kunyar data mamaye shi. Washe gari tun asalatun farko muke aiki saboda ɗaurin auren ƙarfe goma ne,da wuri muka kammala komai muka shiga shiryawa sai dana shirya Mu'afsa tsaf!sannan Anty Uwani ƙanwar Ummi tazo ta ɗauke ta nima na shirya cikin wani less ruwan sararain samaniya da mukayi ankonshi nida Ummi,Granny da Mu'afsa sanda na fito naji Ummi nacewa har sun tafi azare ɗaurin auren. Ana ɗaura kuwa zasu taho da amarya Fadila da kuma Anisa saboda gobe ƴan nijar zasu zo da anyi dinner su ɗauki amaryasu su wuce da ita,hakan ya tino mini da ranar ɗaurin aurena da Habib hakan wata al'adar ne nasu ana ɗaura aure ake ɗaukar amarya. Zuwa ƙarfe uku masu motocin ɗaukar Amarya suka iso,dukkansu sunyi shigar liffaya iri ɗaya sak sunyi mungun kyau aka fara feshe su da turare sannan aka shiga dasu can ƙuriyar falo,Kawu Isma'il dasu kawu Hayatuddeeni da mahaifin Aliyun haidar ɗin da wasu biyar daban shaidasu ba sukazo amsarwa ɗansu Aliyu haidar auren Amisa.tare da Anty Amina sukazo akan gobe insu Adda Salamatu sun su koma tare.ranar duk yanda Habib yaso mu haɗu gagara hakan yayi sai da Daddy ya shiga yayi ta mim faɗa wai ina gyara auren wasu ni kuma ina wasa da nawa haka na tafi part ɗin Habib na kwana acan. Washe gari gidan babu masaka tsinke tsabar yawan jama'a da cinkoson motocin,zuwa ƙarfe biyu su Adda Salamatu dukkansu suka iso dasu Nabiha,Nabila dasu Mima a cikin part ɗin Sayyid suka sauƙa dan ba'a nan akayiwa Fadila jere ba a kano zasu zauna wajen aikinsa. Ƙarfe huɗu aka fara shirya zuwa wajen dinner,ko ya saka ankonsa harsu Nabiha amare kuwa shigar farin less mai ɗigo-ɗigo ruwan golden sukayi aka tsantsaresu da make-up.sai lokaci ango Aliyu haidar ya sama damar isowa da zugan abokansa dukkan su suna cikin unfiorm ɗin sojoji. Nida Habib da Mu'afsa anko farin shadda mukayi aka min ɗingi doguwar riga da adon golden ɗin flower a wuya da hannun riga wanda yayi dai-dai da kalar hular da Habib yasa akanshi,Mu'afsa kuwa ita doguwar rigar aka mata iya gwiwa na raba mata ganshinta gida biyu na kame mata shi da ribbon pink colour,sosai muka ɗauki hankulan mutanan da suka halalta dinner ƴan mata sai shigewa Habib sukeyi na kuwa mannewa abuna.da haka dinner ya tashi bayan anci ansha yaya Fawas ya zubo addu'o'in neman zaman lafiya ga ƙannen nasan,washe gari tun ƙarfe tara aka wuce da Anisa Nijar tare dasu Adda Salamatu da sukazo suka tafi da ƙannen haj jummai da kuma na mahaifinsu sai kuma Anty Amina itama da jaririn cikinta maƙale jikinta. Da yamma kuwa aka wuce da Fadila gidanta take kano,ranar Sayyid da Ummi suka ƙarayin kukan rasuwar Yasira sosai sai da suka bawa kowa tausayi,yana daga cikin babban burin Yasira son ganin Sayyid yayi aure Allah bai ƙaddaraba har ta rigashi yi.nima sai dana koka mata sosai shiyasa na tsaya tsayin daka wajen ganin komai ya tafi kamar yanda Yasira ta daɗe tana tsarawa. Duk yanda naso zuwa kai Fadila,Habib hana ni zuwa yayi.Daddy ma ya goya masa baya cikin daren na kwana da zazzaɓi mai zafi ajikina sai kwara amai nakeyi duk jikina babu kuzari,muna gama breakfast Habib ya kaini asibiti aka tabbatar ina ɗauke da jaririn cikina a maƙale a ƙasan mara na,murna wajen Habib ba'a misaltawa muna dawowa sai daya bi kan kowa ya faɗa mishi ko sai faɗin yakeyi daga auren Yaya Fawas sai zuwa suna duk suka sanya ni cikin kunya. Gidan Daddy muka zauna saboda auren Yaya Fawas sati biyu ne tsakaninsa dana su Sayyid,kulawa ina samunsa bana wasa ba kamar kwai haka Habib yake riritani haka nan Ummi da Daddy,Granny ma ba a barta a baya ba.duk sati Baffa ke aiko min da ruwan rubutu ina sha da wasu ƙarin addu'o'in.lokacin da bikin yaya Fawas ya rage saura kwana biyar Ummi ta hanani ɗaga komai a cikin gidan hatta ruwan wanka haɗa mini takeyi da kanta,washe garin ranar muka wuce azare da Ummi,Granny,Iya hadda Hajja da maryam. Nan Inna take fesa mini Nazifi ma yazo ɗaurin auren naje mu gaisa,take kwakwalwata ta shiga dawo mini da abubuwan dasuka wakana a da Nazifi ne silar komai.Fadila tazo Anisa ce dai bata zoba,Daddy da Habib da kuma Sayyid da Yaya Fawas da wasu yayun mahaifinsa da kuma Baffa suka ɗunguma nijar karɓawa Yaya Fawas auren Farida.Ƴan ɗaurin aure na watsewa na leƙo zaure na hangi Nazifi tsaye daga waje na nufi da sallamata ya amsa sannan muka shiga maidawa juna gaisu. "Allah sarki!Hibba Inna ke cemini kinyi aure har inada ƴa kinsa ni tun lokacin da aka neme ki aka rasa,nima na tattara kayana nabar gano".na ƙara rusunar da ƙwayoyin idona nace"E wallahi Nazifi nayi aure har inada yarinyata ɗaya Mu'afsa,kai fa tare da matarka kuka zone?".yasaki murmushi kawai ina sadda kansa ƙasa yace"Har yanzu banyi aure ba wataƙil nan gaba nasone na roƙi yafiyarki domin nasan cewa na taka muhimmiyar rawa wajen jefa rayuwarki cikin ƙunci har shaiɗan yayi galaba akanki kika guji gida". "Babu komai Nazifi Allah yasani ban ƙullace ka a raina ba,Allah ya kawo maka mace ta gari".yace"Amin ki gaida min da mai gidan nakin".har na juya zan tafi Mu'afsa ta rugu wajena da gudu ta rumgume ƙafafuna na ɗagata sama tace"Ammina wannan waye ne shima yaron Hadiya Inna ne?".nace"A'a wannan yaya nane"ta gaishe shi ya amsa yana binta da kallo sosai soyayyar yarinya ya maƙale masa a ruhi.nidai na barshi tsaye nayi wucewa na ciki,ranar na ƙira wayar Habib yafi sau yanda tela yake taka keke amma bai ɗauka ba ƙarshe na haƙura nayi kwanciyata,washe gari aka kawo amaryar yaya Fawas da yamma akayi dinner koda Habib ya shigo gaida Ummi da Inna da safe ko kallon arziki bai mini ba ya fice,har yanzu danake shirin tafiya dinner raina bai sama sukuni ba,ɗinki buba nayi da zanita na lulluɓa mayafina ina riƙe da hannun Mu'afsa na fito a motata muka tafi wajen dinnern dasu Mahmud da Sadiq. Duk hankali na yana ga Habib a wajen dinnern ina juyowa muka haɗa ido da yaya Fawas yamin ishara da hannunsa akan nazo na tashi na isa gareshi bansan mena tina ba lokaci ɗaya idona suka kawo ruwar ƙwalla suka fara zuba Yaya Fawas ya riƙo hannuna shima hawayen yakeyi yau ranar ɗaurin auren yaya Fawas amma babu ran Umma babu na Abba cikin muryan kukan dayake ƙara zuwar mini nace"Yay Fawas mu kuma haka zamu rayu babu uwa balle uba Allah ya jinƙanku". "My cute angleb akwai Allah kike raya rayayye a cikin matacce har ya fito duniya tabbas shi zai jiɓanci lamuran mu".daga ni har shi kuka mukeyi sosai Mu'afsa ta tashi tazo wajenmu yaya Fawas ya ɗaukre ta ta fara share masa hawaye tana faɗin"Abbu ka daina kuka kaga ka samin Ammina kuka ko Hadiya Inna ce ta muku bulala". "Na daina yarinyanta"ya faɗa yana share hawayensa Ummi tazo ta riƙe hannuna muka koma mazauninmu na da Mu'afsa kuwa nan wajen Yaya Fawas da amaryar ta zauna.ƙarfe goma an gama komai nihar har nayi shirin kwanci naga saƙon Habib yana shaida mini gobe da safe zamu wuce katsina,ina gama karantawa na kashe wayar na kwanta raina fal!da tinani. Washe gari na sanar da Ummi tace na shirya ɗin kawai mu tafi,haka na shirya mukayi ban kwana da yaya Fawas muka tafi muka bar su Ummi anan sukam sai sunyi ƙara kwaba biyu.har muka isa cikin katsina bai tanka mini ba yana ajiye mu a gida ya wuce offics na shiga gyare-gyaren gidan sannan na ɗaura girki nayi wanka koda na fito ana ƙiran magrib nayi ban tashi ba sai danayi isha'i sannan na fito falo saboda ƙaran shigowar motar Habib danaji na tarbo shi tare da gabatar masa da abinci yace ya ƙoshi. Na tari gabansa ina kuka nace"Habib mena maka kake min wannan hukunci mai tsanani,dan Allah ka fito ka sanar dani". "Babu komai".nayi saurin cewa"zanfi yarda idan kace mini bazaka faɗa ba akan kace min babu,wallahi wannan hukuncin yayi min tsauri mijina zuciyata tana azabtuwa"ya rungumo ni jikinsa saboda kukan dana saka mai matuƙar sauti muka zauna akan sofa yace"Meye haɗinnki da Nazifi ranar na ganku kuna tsaye kunada wani dangantane dashi na nisa kona kusa,wanda ni ban sani b?". "Ba muda wani dangankata tsakaninum ko ranar ma Inna ce tace naje mu gaisa don tunda yaji auren Fawas yace zaizo ya nema yafiya ta shiyasa har na tsaya dashi amma kayi haƙuru Rajlun amin".ya ɗago kaina tare da tallafo kuncina yace"Babu komai ya wuce matar aljanna kinsan mijin nakine yanada tsananin kishi akanki,banajin akwai namijin daya ɗara ni kishi fa".naɗan murmusa babu shiri yace"taso muje muci abincin ko"na miƙe nabi bayansa shi yayi serving ɗinmu ya kalloni yace"Jibi ne tafiyarmu kuma sai lokacin haihuwarki yayi kusa sannan zamu dawo".Na tausayar da kai nace"Allah ya nuna mana"yace"amin". Ana gobe zamu tafi su Ummi suka dawo mukaje musu sallama Ummi tace mubar Mu'afsa,Abbunta ya nuna yafison mu tafi ta ita.Granny sai shimfiɗa masa kashedi takeyi da zaran na shiga watan haihuwa ya dawo ni gida.ko gano bamuje ba saboda tafiyar tazo a gaggauce sai waya nake sanar da Baffa ya mana fatan Allah ya tsare hanya,Maryam ma a waya nake sanar da ita.kafin mu tafi Yaya Fawas da Habib hadda Daddy sukaje zamfara domin shari'ar Bashari inda aka yanke masa hukuncin zaman gidan yari na shekaru talatin tare da taran naira dubu ɗari takwas a bisa laifin aikata fyaɗe da kuma zanba cikin aminci. Saudiya muka bara halalta muka sauƙe farali sannnn muka wuce ƙasar moscow,matuƙa na yaba da tsarin zubin moscow watan mu uku da kwana biyar a moscow muna more rayuwarmu,na murj na ƙarayin haske sosai fatana tana glowing fiye dana da ga wani ƙiban dana narka hak nan ma Mu'afsa har shi kasan Habib ɗin.watan mu biyar a spain muka dawo nijeria saboda naci irin na Granny,tun muna moscow Anty Amina ta haihu da zamu dawo kuwa muka tsaya ta nijar ta sama baby boy ɗinta mai sunan Malam Mahiru haka nan ma Anisa ya ƙarayi kyau sosai kwanan mu uku muka dawo nijeria. Sayyid da Yaya Fawas da matayensu sukazo ɗaukar mu a airpot muka wuce gidan Ummi ta tarbe mu cike da fara'a kai ya ilahi gaskiya nayi kewar Ummi babu mizanin dazan kwatanta adadinsa.bamu cika sati biyu da dawowa ba na haihu sai dai nasha baƙan wahala sai nada wuni ina naƙuda ban haihu ba ƙarshe ma sai da aka min Cs sannan aka ciro mini tsantalelen yarona na miji mai matuƙar kama da Ummi kamar kara aka tsaga. Murnan wajen Habib babu kama hannun yaro kasa zaune yayi balle tsaye,dan lokacin da aka shiga dani Cs ji yakeyi kamar nima rasani zaiyi kamar yanda Yasira ta tafi ta barmu ta irin wannan hanyar.tana riƙe da yaron ya hana kowa karɓansa har muka isa gida. Kullum yana naniƙe damu wataran har sai Granny ta koresa,har daina zuwa office yayi ranar suna kuwa baby yaci sunan Abban -SULEIMAN-.Inna har kuka tayi tsabar murna da farinciki su Fadila da Anisa har Anty Amina sunzo sunan Balabara da Hajja ma haka dasu Adda Suwaila.Maryam ma da ƴaƴanta biyu Diana ƙanwar Abbul-khair. Ranar sunan Habib ya mallaki min takardun gidade biyu da takardar sabon Companyn sarrafa alkama dayake ginawa dukka.duk muny shigar shadda ash nida Habib da Mu'afsa kowa ya tafi da sha'awar rayuwar aurenmu da Habib a ransa. Kwana biyu Anisa dasu Adda Suwaila suka koma,Daddy yace su Fadila da Farida ma su koma ɗakunansu.daren ranar Daddy ya ƙirani ya miƙa mini takardun sama min aikin da yayi a wani sabon gidan jarida -MANUNIYA-.na rasa bakin magana tsabar farin-ciki Habib ne kawai yake masa godiya Ummi na tayasa.ranar kasa bacci nayi tsabar murna yau dukkan damuwata ta kau na cika burin -ABBA- na cimma ƙudurin -YAYA FAWAS- yau nice ma'aikaciyar aikin jarida. -AKKAM-laƙabin da muke ƙiransa kenan sa wani lokacin har rigima mukeyi da Habib akan yanda yake nuna tsallar soyayyar ƙiri-ƙiri ga Akkam nikam nasan har na gama haihuwa bazan haihu wacce zata kai -MU'AFSAT-ba sonta bazai taɓa canzuwa a cikin ƙalbina ba.sai da Akkam ya cika wata uku cif sannan na fara fita aiki.lokacin Mu'afsa ta shiga makarantar Nursery.inna dawo daga aiki na fiyo wajen Ummi na ɗauketa mu tafi gida. -BAYAN SHEKARA- Zaune nake akan ɗaya daga cikin laushashshun kujerun falo masu launin kalar Maroon,haka nan ma kalan dogayen labulen ɗakin carpet mai launin milk dake malale a tsakiyar falon. Gefe guda kuwa wasu kujerun ne milk colour ga makeken tv plasmaa cikin wall ta can gefe kuwa hotonmu da Habib,Mu'afsa da Akkam ne duk fuskokinmu ɗauke da annuri a manne cikin wall ɗin an gine dashi,daga gefen shi hotona ne nida yasira.a hankali na miƙe ina ƙara damƙe takardan asibitin dake nuna ina ɗauke da ciki na tsawon sati biyu duk na burkice saboda har yanzu ban yaye Akkam ba,tun dawowata daga Office nake dukawa Habib ƙira yana cemin yanzu zai iso,ko ta wajen Ummi ban biya na ɗauko Mu'afsa da Akkam ba. Inajin ƙaran shigowar motarsa na sakin hawayen dake maƙale a ƙuyar idona,ya isoni cikin sauri"Ummul-kam lafiya kuwa meya faru a asibitin?".yakai ƙarshe yana riƙo hannun ya karɓa takardan sai daya karance tsaf!kafin yace "Alhamdulilah!Allah na gode maka zanga jinina a duniya sosai"na ɗan harare shi ina kai masa duka a kafaɗansa nace"ni wallahi a cire min shi kaga Akkam fa ko shekara baiyi da rabi ba ko yaye sa banyi yanzu kuma ga wani cikin".ya ƙara riƙo hannuna muka zauna"Haba Debbo am ma'aurata nawa suke neman haihuwa ido a rufe Allah bai basu ba,mu kuma Allah ya bamu maimakon mu gode masa sai kice acire miki gaskiya banji daɗi ba kuma ki gaggata tuba zuwaga ubangijinki"na rusunar da kaina ƙasa nace"Na daina!na daina rajlun amin Allah yabamu masu albarka amma Akkam fa yaya zamuyi dashi?". "Zan ƙira Ummi ya cigaba da zama kawai a wajenta sai ana bashi madara"na jinjina kaina alamar gamsuwa ya ruɗe min hanayensa na faɗa jikinsa.nana wajen ya ƙira Ummi ya sanar da ita Akkam ya zauna a wajenta saboda Hibba nada ciki tsabar kunya yasa Ummi kashe wayar ba tare data gaɓa sauraran sauran zancensa,yakuma ƙiran Inna ya faɗa mata dan tsaban son ƙara kunyata ni har tambayar ta wai meya kamata ina ci ko sha don inganta lafiyar abunda yake cikina nasu na gargajiya.bayan ta gama lissafo min sukayi sallama ya haɗa zai ƙira yaya Fawas ya kwance na turo baki haɗi da faɗin"ni wallahi babu wanda zaka kuma ƙira ya isa haka"yasa dariya yace"Ummul-kam kenan ai abun alkhairi ne ya same mu dole na sanar". "Ni Abbu Mu'afsa wannan haihuwa babu wanda zan sanar sai dai kawai kowa yazo ya ganni da babyna"ya kuma yin wani dariya muka miƙe muka shiga ɗaki. Ranar haihuwa naci wahala harma fiye dana haihuwar Akkam dan kasa nishi nayi gabaɗaya duk na gama galabaita har an shirya shiga dani tiyata na haihu ƴan biyuna ɗaya mace ɗaƴa namiji,dangi gabaɗaya ya ɗauka dan basu da ƴan biyu da yawa ranar suna yara sukaci sunan -DADDY- da -YASIRA- muna ƙiransu -IKRAM- da -AKRAM-.haka rayuwa ta cigaba da juyawa farin-ciki da zaman lafiya na ƙara wanzuwa a tsakaninmu ana cikin haka Fadila ta haihu ta haiho baby girl ɗinta yariya taci sunan Ummi suna ƙiranta da -AFRIN-sati uku tsakaninta da Farida itama baby girl ta samu aka sanya sunan Inna suka ɓoye mata suna suna ƙiranta da -AJMAL-.Anisa kuwa ciki haihu ko yau ko gobe. A cikin taƙaitaccen lokacin da Allah ya tsara mini rayuwa a cikinsa,na haɗu da jarabawa kala-kala daban-daban amma na godewa rabbi daya barni da imani na a cikin ko wani hali,har na kawo wannan matsayin a rayuwa Habib ya zama duk wani -HASKE- a rayuwata. -ALHAMDULILLAH- Anan na kawo ƙarshen wannan littafin nawan mai suna UWATACE SANADI,ina roƙon Allah duk abunda na rubuta dai-dai a cikinsa ya haɗa mu akan ladan,inda nayi kuskure kuwa ƙarancin ilmi ne,Ya Allah ka tsare mini hannayena wajen rubuta abunda zai zama cutarwa ga al'umman musulmai tare da tarbiyarsu. Ga me neman wannnn littafin ko wani ƙarin bayani zai iya tuntuɓata ta wannan lambar kamar haka -07038908713-. Maimunah Tijjani Iyam