Compiled by Umar Dalha. 👩🏻‍💻typing.......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* _Sadaukarwa_ *_miss Xoxo na_* *_Zarah bukar_* *_Ayusha muh'd_* *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._* _Bismillahirrahmanirrahim_ _ya ALLAH kabani ikon fad'ar abinda zai amfani al'ummarka, ka tsare harshena daga fad'an abinda zai cutar da al'ummarka, ameen_ _ina farin cikin sake had'uwa daku a sabon littafina mai suna *KARAYAR ARZEEK'I*, ina fata zaku bani had'in kai, ngd da k'aunarku gareni, nima ina k'aunarku lodi Lodi._😘😄 *_duk Wanda ya canja wani Abu a buk d'innan ALLAH ya isa ban yafeba.🙄_* *_page→1_* ..........6urum aka turo k'ofar tamkar za'a cireta. Zaune yake a bakin gado yana harhad'a wasu takardu, hankad'o k'ofar basashi ko gezauba barema ya d'ago Dan yasan bai wuce matarsace lubna ba, da wanan d'anyen aikin. Ta huro hanci had'eda rik'e k'ugunta da hannu biyu, wata uwar harara ta watsa masa, wadda baimasan tanayiba. *_Umar fharuq!!._* takira sunansa cikeda masifa. Bai amsataba baikuma d'agoba, harkar gabansa kawai yakeyi. Lubna dake tsaye tana karkad'a jiki takuma k'ufla, Dan haka tacigaba da magana cikeda tsiwa....... Gsky nikam nagaji, kasan yadda zakayi dani wlhy, shekaranjiya kacire yara daga makaranta bance maka komaiba, yaukuma shine zakazo da mutane suna zazzagaye gida?, shin mikake nufu?, ko shima gidan saidashi zakayine?, to wlhy idanma tunanin haka kakeyi ka canja, Dan bazan rayu banida tsuntsu baniga tarkoba. Aidama nasan tunda aka aura maka waccan 'Yar k'auyen, saimun shiga bala'i, gashinan tun ba'aje ko inaba komai yak'are, mayya mai farar k'afa tashigo rayuwarmu, saura kuma kurwarmu ake bibiya alashe yanzun... d'an tsaki yaja idonsa akan takardun dayake zubawa acikin wata 'Yar jaka, saida yagama tsaf sannan yad'ago fararen idanunsa yana kallonta, yanunata da d'an yatsa lubna kishiga hankalinki, kinsan banason shirme ko?, gidakam zan saidashi idankuma nakine saiki hana, inama yimiki albishir daki fara shiri Dan nanda kwana biyu zamu barmusu gidansu............. Jar ubannan kai, wlhy Umar baka isaba, ainima inada hak'k'i da gidan, tunda 'ya'yana sunada gado. Kansa ya girgiza yana rataya jakar akafad'a, ya ce, "mahaukaciya kawai, saiki bari saina mutu kafin yazama gadon nasu mtsoww. Umar nikake kira mahaukaciya?!. Bai tanka mataba yatako cikin nutsuwa yanufi hanyar fita...... Da Sauri tasha gabansa tana huci, wlhy babu Inda zakaje saika sanar dani wacece mahaukaciyar?. Kallon sama da k'asa yay mata, batareda yayi maganaba yaja tsaki tareda ra6awa ta gefenta zai wuce. Da Sauri takuma shan gabansa. Afusace ya ce, " wlhy koki tashimin a hanya, kokuma na kashe fuskaeki da mari...... Toka marenin mana, nagadai Nima ALLAH yabani hannun dazan rama. Ya ce, "ko?. "eh, kozaka gwadane?." Wani k'asaitaccen murmushi yasaki, yara6a tad'ayan gefenta yafice yana cije le6ensa. Binsa tayi da kallo tana girgiza jikinta alamar tsumuwar bala'i, saikuma ta rushe da kuka. Na ce, "tofa, anayinta." Shikam koda yafito d'ayan 6angaren ya Shiga, babu kowa a falon, sai sassanyan k'amshi dana AC dake tashi, TV ma a kashe take, hanyar wani d'aki yanufa. Tana zaune abakin gadonta dayasha gyara, ananma k'amshine mai dad'i dasaka zuciya nutsuwa ke tashi, ta rabga tagumi, daga ganinta Kasan tana duniyar tunani. Gyaran murya yayi had'eda sallama. Firgigit tad'ago tana kallonsa, sai kuma tazamo daga gadon Baki narawa ta ce, "yaya ina yini. Atak'aice ya amsa da lfy, yacigaba da fad'in kifara shirya kayanki nanda kwana biyu zamubar gidannan...... Baijira cewartaba yafito abinsa. Wasu siraran hawaye suka zubo daga kumatunta, Afili ta ce, "na Shiga uku ni Asma'u, shima gidan ka saida ya Fharuq?!, nikam naga ta kaina, karfa maganar aunty Lubna yazama gsky, ta rushe da kuka maiban tausayi........ _nakalli zarah, Zarah takalli Xoxo, mukayi tsuru tsuru tamkar munafukai, Xoxo ta ce, " tawan ta'ina zamu fara?, na ce, "umm tawan tambayi Zarah kotanada idea nikam banida fus._ _Zarah ta gyara tsayuwarta, hannunta rik'eda Biro da 'Yar takardar d'aukar rahoto, ta ce, " bily nimafa na toshe Dan naga gidan kowa a rikice yake bansan wazamu tunkara yabamu labariba?, Xoxo kozakije wajen lubna?._ _Kam bala'i babu inda zani daga rakkiya?, agabankufa mijinta yakirata mahaukaciya, sannan kucemin naje tasaukemin na jaki._ _Dariya muka gumtse nida Zarah danjin zancen Xoxo, Zarah ta ce, "bily fa?._ _Na ce, " um um kodai ke ki gwada, nisainayima wannan magana?._ _Shiru Zarah tayi, Dan itama batason komawa wajen lubna........_ _Zuwacan Xoxo taja numfashi idonta akan Zarah, ta ce, "Zarah nibamfa gane mi tawan take nufiba?, catayifa murakota d'aukar rahoto, amma sai wani shirin lik'a mana aiki takeyi?._ _Harar Xoxo nayi, amma tawan idan kuntayani na buga labarinnan naga ba fad'uwa kukayiba ko?._ _Hakane, amma gsky nikam bazan iya da wannan iya bala'in matar tasaba, kumafa ni sonsama nakeyi, Dan guy d'in yahad'ufa._ _Dariya muka shek'e da ita nida Zarah, Zarah ta ce, " haba 'Yar uwa kice kishi bazai barkiba kawai, ammafa Nima bily bawai zan tayaki bane, namiki rakkiyane kawai, saidai mukoma gidan zan tayaki da shawarar yanda zaki d'auki wannan rahoto._ _To shikenen ngd Zarah muje, kekuma tawan dazanmiki hanya ki aureshi ammafa yanzu nafasa._ _Kai tawan nidakefa ba'a jin kammu?._ _Aikodai yau za'aji...........🤥😏._ *_tab masu karatu akwai aiki Dan bansan yanda zaku sami cikakken labarinba, tunda masu d'aukar Rahoton duk matsoratane._* *_Daga miss xoxon Zarah Bukar, harni bilyn Abdul duk fararen kurayene򓰽򗀮_* _amma ni bilyn Abdul zan kawo muku cikakken labarin, tunda su o e anji tsoro😏._ Kikasance dani danjin yadda zata kaya😻😘. Bilyn AbDul ce👌🏼 *_luv you oll_* *_(((S))).....2017_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻typing.......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* _Sadaukarwa_ *_miss Xoxo na_* *_Zarah bukar_* *_Ayusha muh'd_* *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._* *_page→2_* ...........Tundaga k'ofar gida nafaracin karo da wasu manyan motoci akorikura har uku, duk an loda musu kaya, ra6awa nayi tagefensu nashiga cikin gidan, lallai tashi ya tabbata nafad'a azuciyata ina bin ko'ina nagidan da kallo. Asma'u naga tafito da akwatuna biyu ahannu tanaja, Umar dake jingine da motarsa yana latsa waya yad'ago yana kallonta, d'an ta6e bakinsa yayi yana kauda kai daga kallonta, aransa ya ce, "yarinya tamkar mara laka ajiki?, komai nata salaf-salaf...... Maganartace ta katse masa tunaninsa ta ce, " yaya gasu. Baiyi maganaba ya ajiye wayarsa saman motar, but yabud'e mata tasaka akwatunan, yarufe sannan yad'auki wayarsa yabud'e motar yashiga. Asma'u tana tsaye sai faman bin gidan da kallo takeyi, kwata-kwata zuciyarta babu dad'i takeji, tasan yaya umar ma yana dakewane kawai kasancewarsa mutum jarumi mai dakiya da kawaici, duk 6acinran da Umar zai shiga mawuyacine kagansa shinfid'e afuskarsa, mutumne daya iya 6oye sirrin zuciya........ Ganin bata shigoba yay mata horn. Da sauri tabud'e motar amma bata shigaba, tad'an sunkuyo ta ce, "ya Fharuk Anty Lubna fa?. K'aramin tsaki yaja, yace batana canba tund'azu, kinafa 6atamin lokaci. Jiki a sanyaye tashiga motar yaja yafice daga gidan zuciyarsa namasa zafi, amma sai ambatar innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yakeyi. Tuk'i yakeyi ahankali tamkar bayaso, dagashi har ita babu mai iya magana, lokaci-lokaci ita takan share hawaye, yana kallonta ta gefen ido. Ak'ofar wani matsakaicin gida yay farking, koba'a fad'aba nanne gidan dazasu dawo, domin annan muka tadda motocin akoru kurarnan sunata aikin sauke kaya dashigar dasu cikin gidan. Kad'an ya kalleta, kishiga ciki su Hasiya da Rafi'a da fatee duk sunanan sune zasu tayaki gyara kayanki, ni bara naje wani waje. To ALLAH yatsare, saika dawo. Ameen, yafad'a akan la66ansa. Bud'e motar tayi tafita, harta d'an fara tafiya saikuma tajuyo, ya Fharuk kayanfa?. Baitanka ba saida yatada motar, kije idan nadawo zan shigo dasu yanzu Sauri nakeyi, magana yakeyi amma ko Inda take baya kallo. Itama kanta ta jinjina tajuya tashiga cikin gidan, abakin matsakaicin bak'in gate d'in sukai karo da matasan samarin dasuka gama Shiga da kayan nata. Sannu tayi musu sannan tashige ciki. Bin ko'ina takeyi da kallo, gidan k'aramine irin ginin talaka mai k'aramin k'arfi, ko'ina shage yake da siminti lumus, haka tak'arasa cikin gidan tana raba hanya. Abakin fanfo taga Afrah da Amrah yaran Anty Lubna sunata wasa da ruwa, bata musu maganaba gudun kar cibi yazama k'ari Dan Anty lubna batason abinda zai ta6a 'ya'yanta ko kad'an. K'ofar falon tatura tashiga, Rafi'a da fatee Hasiya sukazo da gudu suka rungumeta, itama rungumesu tayi sunamai murnar ganin juna. Hasiya ta ce, "kai Anty Asma'u kinganki kuwa, wlhy kinyi bala'in k'yau, gidan ya Fharuk ya kar6eki. Hararar hasiya tayi cikin sigar wasa, Hasiya kina nandai baki canja haliba wlhy. Dariya sukayi suduka, Asma'u tabi falon da kallo, babbane sosai, sai kowace kusurwa da akwai k'ofa. Ganin kallon da takema falon yasa Rafi'a fad'in wlhy Anty tsarin gidan yayi sosai, kinga nan family falone, wancan k'ofar shine naki, akwai falonki da bedroom sai bathroom, wancan kuma na Anty lubna ne, itama iri d'ayane da naki, wancan na tsakkiyar kuma na ya Umar ne. Murmushi Asma'u tayi, tace ALLAH ya tabbatar da alkairi to. Ameen suka fad'a suduka. Kama hannunta fatee tayi, tana fad'in zomuje kigani harmun fara had'a miki bedroom d'inki. d'akin daya kasance NATA suka nufa, tuk'uru suka Dage suna aiki, kafin k'arfe biyu sungama komai har babban falon sun saka kujerun dasuka kasance ada na 6angaren bak'i agidan dasu dasuka taso, d'akin Ya Umar suka shiga, shima tsaf suka gyara masashi ko'ina yad'auki haske. Duk bidirinnan dasukeyi basuji motsin Lubna ba sai yanzu, duk sunzube a family falo suna maida numfashin Hajiya lubna tashigo itada Suhaima k'anwarta. Suhaima tabi falon da kallo tana wani yatsine fuska, Anty lubna wai kina nufin anan ya Umar zai ajiyeki?, aiko 'yan aikin gidanmu sunfi k'arfin zama acikin wannan kangon?. Baki lubna ta ta6e kibarsa kawai Suhaima Nima INA rakashine naga iya gudun ruwansa, amma wlhy bazan zauna awanan k'onannan gidanba saikace wata fak'ira, shima yasan bamu gaji tsiyaba wlhy. A to yakamadai kid'auki mataki, wannan gidan saidai su o e wad'anda dama atsiya aka taso, shigarta wannan gidan ai ita k'arin cigabane. Rafi'a tamik'e danufin maida murtani dantasan sarai da Asma'u suke. Da Sauri Asma'u tarik'e hannunta tana girgiza mata kai alamar a'a kartacr komai. Lubna ta gallama Rafi'a harara, to tabbatacciya da dakika tashi dukanmu zakiyi?. Shiru Rafi'a Tamata Dan Asma'u tahanata magana. Suhaima ta tuntsure da dariya Anty lubna kinga muje nifa kinganni bakowace bola bace abin kallo agareni. Fatee ma tabud'e baki Zata maida murtani Asma'u ta harareta. Daga k'arshema tashi tayi takad'a Kansu suka shige cikin falonta. Daga Lubna har suhaima Bahaka sukasoba, sunso su Hasiya su kulasu ayi badad'i, dama Neman dalili sukeyi da dangin Umar d'in. Suna Shiga Asma'u tarufesu da fad'a akan itafa batason tashin hankali, danhaka komi sukaimata karsuce zasu sake kulasu. Shiru sukai mata kowa tana turo Baki, dansu hak'urin Asma'u haushi yake basu. Sai magriba ya Umar yadawo gidan, suna zaune bayan sun idar da sallah yashigo. Suduka rissinawa sukai suna gaisheshi, ya amsa babu yabo babu fallasa. Ya ce, ''kutashi namaidaku gida. To, suna fad'a kowa tana mik'ewa daneman mayafinta, kowa yashirya sukaima Asma'u sallama, hawaye tafara da rok'onsu Dan ALLAH su ringa zuwa mata akai-akai. Hak'uri sukabata sukace zasuringa zuwa, dama makarantace take hanasu. Ya Umar duk yana jinsu, ganin sunk'i tahowa yadoka musu tsawa, kai banason rainifa........ Bama su bari yak'arasaba suka fita dad'an gudunsu. Asma'u tacusa kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka saboda kewar 'yan uwan nata, koba komai yau taji dad'in ganinsu, sunyi hira taji farinciki aranta. Bata kuma saka ya Umar a idontaba har wayewar gari, dama bazuwa kwana d'akinta yakeyiba, itakuma bata zuwa d'akinsa Dan duk hak'urinta tanada matuk'ar zuciya, dukda tasan basonta yakeyiba hasalima taimakonta yayi, amma ai baidace yarik'a mata hakaba kodan darajar zumincin dake tsakaninsu...... Share hawayenta tayi tamik'e zuwa kichin domin had'a breakfast. Ruwan shayi kawai tadafa da Lipton da kayan k'amshi Dan bataga wani abuba a stor d'in gidan. A tsakkiyar falon tazo ta ajiye kofuna da filas d'in shayin Dan ya Umar bayacin abinci akan dinning. Tana cikin d'an gyara kayan yafito daga d'akinsa sanye cikin farar jallabiya. Rissinawa tayi ta gaisheshi, saud'aya ya amsa yafice. Mintuna kad'an yadawo d'aukeda bak'ar Leda ahannnusa, Asma'u na zaune a babban falon tana jiran dawowarsa danta tambayesa yanda za'ayi. Ledar yamik'a mata, hannu biyu tasa takar6a tana masa sannu. Kujera yasamu daga d'an nesa da ita yazauna, itakuma tabud'e ledar, biredine aciki sai madara irin 'Yar sacet d'innan guda uku, sai sukari da bota ta Leda............. *_luv you oll_* *_(((S))).......2017_* [11/29, 11:03 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻typing.......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* _Sadaukarwa_ *_miss Xoxo na_* *_Zarah bukar_* *_Ayusha muh'd_* *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._* *_page→3_* ....... Ganin yanda kayan shayin yake yasata rarrabama kowa akofi ta ajiye, gamawarta babu dad'ewa saiga su Amrah sun fito da gudu. Jikin babasu suka fad'a suna fad'in daddy?. Ya ce, "na'am twin's d'ina kuntashi lfy?. Lfy lau, daddy yaushe zamu koma gidanmu?, nan gidan babu dad'i sai zafi babu AC. Murmushi kawai yamusu, yakama hannunsu suka sakko k'asa inda Asma'u tahad'ama kowa shayi. Dai-dai nan Lubna tafito, taci kwalliyarta cikin pink d'in shadda sai zabga k'amshi takeyi. Afrah data kur6i shayi tayi saurin zuboshi ak'asa tareda cillama Asma'u bread d'in data bata bayan tashafeshi da bota, nidai bazan sha tea d'innanba momy babu dad'ifa, ni dankali da kwai nakeso. Galala Asma'u tayi tana kallonta, ganin haka itama Amrah tayi cilli da nata gefe. Ya Umar duk yana jinsu amma yay kunnen uwar shegu dasu sai danna shayinsa da bread yakeyi hankali kwance. Lubna ta harareshi, tokaji sufa bazasu iya shan wannan tea d'inba maikamada ruwan wankin kai, koni wlhy bangoyi bayan sushaba tundasu ba dabbobi bane. d'ago idanunsa dasukayi d'anja yayi yana kallonta, baice komaiba yamaida kamsa yacigaba dayin break d'insa. Asma'u ma tea d'inta taja tahausha batareda tasake kallon inda Lubna da yaranta sukeba. Aiko ganin haka yasa Lubna fara zubar da ruwan masifa da tijara, sai zabgama Ya Umar gori takeyi. Wai aii babantane dama silar arzik'in nasa, wlhy tayi nadamar aurensa Dan aurensa bai amfaneta da komaiba sai fad'awa tarkon wahala, dan haka dolene yasaketa ita bazata zauna dashiba taringa shan ruwan wankin kai amatsayin shayi......... Haka taita zabga ruwan masifa babu Wanda ya kulata barema ya tanka mata, Asma'u tana gamawa ta tattara komai takoma d'akinta. Shima mik'ewa yayi yashige nasa d'akin. Itama ganin babu sarki sai ALLAH taja hannun Afrah da Amrah suka bar gidan. Bayan wasu 'yan mintina Umar Fharuk yafito tsaf sanye cikin k'ananun kaya sai zabga k'amshi yakeyi. Araina nace bawan ALLAHnnan ya iya d'aukar wanka wlhy. d'akin Lubna yashiga, amma saiyaga wayam, baice komaiba yafito yashiga na Asma'u. Tana falo kwance a doguwar kujera, chart takeyi abinta sai faman murmushi take zubawa. Sallama yay mata sannan yazauna kujerar dake fuskantarta. Itama tashi tayi zaune ta ce, "sannu. Bai amsaba amma idonsa na kanta, Ita saima duk kunya takamata, ganin haka yasashi d'auke kai daga gareta, ya ce, " zanje shagunana Dan inaso afara gyaransa muga kuma abinda ALLAH zaiyi, idan kud'in sunkai angama gyaran to ko haya saina bada, idan kuma basu kaiba saimuga kuma abinda yadace ayi. Jin yayi shiru tagane cewa yagama maganarsa, cikin sanyinta ta ce, "ALLAH ya tabbatar da alkairi aciki, Yakuma mayar da alkairi fiye da abinda aka rasa. Yaji dad'in addu'arta danhaka ya amsa da ameen yana mik'ewa. Saina dawo, yay maganar yana fita. Itama tace ALLAH yatsare takoma ta kwanta. %%%%%%%%%%%% Umar nafita daga nan gidansu yanufa, gidan babu laifi mai k'yaune Dan tuni Umar yagyarashi tsaf, komai na more rayuwa saida yazubama iyayensa shi, horn yayi maigadi yabud'e masa gate, saida suka gaisa sannan ya ida shiga ciki, yasamu guri yay fakin. Da sallama yashigo falon, Rafi'a ce kawai ta amsa cikeda farinciki, amma mama da Mufida da Harris sun amsane babu yabo babu fallasa. Waje yasamu yazauna ak'asa yana gaida mama. Dak'yar ta amsa masa, bai damuba yajuya yana amsa gaisuwar Rafi'a, harara ya gallama Harris da mufida Ku baku iya gaisuwa bane?, wai yaushe kuka rainanine?....... Kafin suyi magana mama ta cafe, a'a yabazasu rainakaba? Tunda kagaza yimusu maganin abinda yadamesu. Ajiyar zuciya yasauke, idanunsa harsun canja kala, ya ce, ''kiyi hak'uri mama abubuwane sai ahankali, kinsan dai halin Dana tsinci kaina aciki, inda Dane kobasu tambayaba zan basu, amma wlhy yanzu banida sh...... Kai dakatamin!!!, mama takatsesa cikeda tsawa, harni zaka bud'e baki kacema bakadashi, koma kunyar yin k'arya bakaji?, shekaranjiyafa kasiyar da gidanka miliyoyin kud'i amma har bakinka yafurta bakadashi, duk dai Wanda yagaza godema ALLAH to zai godema azabarsa. Wani yawun 6acinrai ya had'iye, muryarsa cikeda girmamawa agareta ya ce, "kiyi hak'uri mama, wlhy kud'in gidannan acikinsu aka cire aka sayi gidan damuka koma, sauranne kuma zanje nayi gyaran shaguna nana, bammayi zaton kud'in zasu kaini ko inaba. Hummm tonaji baban tsari tashi kabani guri, kama gyara duniya dasu ba shagunaba, itadai rayuwa duk Wanda yakedashi yagaza taimakon d'an uwansa aiyayi asara.... Da sauri Umar yad'ago yana kallon mahaifiyar tasu, idonsa yayi jajur, Rafi'a ma kuka takeyi, tana mamakin hali irinnan mahaifiyar tasu, kwatakwata mutumce dabata godiyar ALLAH, atunaninta ya Umar yafi k'arfin cin fuskarta kodan k'ok'arinsa nason k'yautata mata, duk cikinsu babu mai hak'urinsa dakuma kula da iyayensu, amma tunda iftila'in nan yasamesa 'yan gidan suka fara canja masa........ Maganar ya Umar ce takatse mata tunaninta, rissainawa yayi ya ce, " sai anjima, ALLAH ya huci zuciyarki, yakalli su Harris ya ce, "zantura muku insha ALLAH. baki suka washe suduka harda mama, ko kaifa d'an nan to ALLAH yayi albarka kaji, ameen yafad'a ala6ansa. Suma su mufida sai zabga godiya sukeyi, shidai ficewarsa yayi. Koda yashiga mota saiya fice daga gidna, tafiya yakeyi amma zuciyarsa namasa zafi, gefen titi yasamu yay fakin, yakifa kansa jikin sitiyari yana duk addu'ar datazo bakinsa, wlhy yana mamakin hali irinna mahaifiyarsu, alokacin da yakedashi tafi kowa sonsa da tattalinsa, kullum addu'a take masa dafatan alkairi dagamawa da duniya lfy, amma abin mamaki tunda komai yak'are masa saita fara canjawa, yanzu babu Wanda tatsana samadashi, batada magana saita ya Abubakar da Anty Sa'a da Harris da mufida, suma Kansu 'yan uwansa sun canja masa gaba d'aya, anty sa'a ce kawai da Rafi'a suke sonsa, yasa handky yana share hawayen dake kwarara a kumatunsa. Yakai tsawon lokaci awajen sannan yabirka motar yanufi kasuwa. Alhmdllh aiki yayi nisa Dan anata kwashe tokar gobarar data k'ona shagunan, ganin komai natafiya dai-dai saiya shiga mota yanufi majalissar abokansu. %%%%%%%%%%%% Zazzaune suke sunata kwasar hira da dariya, motar Umar tatsaya. Motsowwww ga k'aban nan cewar Hafiz. Waye k'aba?, Salman yatambaya idonsa akan hafiz?. Umar mana, kokai bakada ganewane, cewar Tasi'u. Al'kasim yata6e baki kaini wlhy fa banason yana ra6armu karya goga mana talauci. Ashe kagane d'an uwa, yanzufa d'angidan dayake mana tak'ama dashifa ya saidashi. Kai Dan ALLAH kabeer dagaske kakeyi?. Wlhy kuwa Hafiz da gsk, nima jafar take bani labari jiya, kunsan shi kunya bazata bari yafad'a manaba. Tofa, yanzu to ina Yakoma?. Wani kangon gida yasiya... Dariya suka shek'e da ita, Al'kasim ya ce, "su k'aba anji yaji........ Umar dake tsaye duk yana jinsu yagirgiza kansa tareda musu sallama............ Afurgice suke kallonsa, duksun tsargu kardai yaji firar tasu?, dansu basusan yama iso inda sukeba. Kowa yakama 'yan kame-kame. Hannu yamik'a musu suka gaggaisa fuskarsa d'aukeda murmushi, suna gama gaisawa ko zama baiyiba ya ce, " bara nawuce, Dama nabiyo gaishekune....... *_(((S)))....2017_* *_luv you all my fan's_*😻 [11/29, 11:03 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻typing.......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* _Sadaukarwa_ *_miss Xoxo na_* *_Zarah bukar_* *_Ayusha muh'd_* *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._* *_page→4_* ..........ah mungode angon Asma'u da uwargida Lubna. Baice komaiba sai murmushin takaici dayayi yajuya yashiga motarsa, suduka binsa sukayi da kallo, kai jama'a Kodai yaji mimuke fad'a?. Kai baiwani jimuba, idanma yaji saime kune kukejin tsoronsa. Mtsowwww miye abin tsoro a can?, mutumin da duk talauci ya gwaguyeshi, ni gwarama dabai zaunaba...... Umar da takaici yacika yana shiga motarsa yabar wajen zuciyarsa namasa k'una, waishi kowa ke gudu tamkar wani mai mugun hali, babu komai yagodema ALLAH, komai na duniya fararrrene kuma k'ararrene, zaiyi hak'uri insha ALLAHU, hak'uri irinna bayin ALLAH, hakadai yayta tunani harya isa gidansa, tun ak'ofar gida yaga motar mahaifin Lubna, cikeda mamaki yake kallon motar, tokodai Lubnace tazo da ita?, yatambayi zuciyarsa. Ajiyar zuciya yasauke tareda fitowa daga motarsa yashiga cikin gida, ganin takalma reras ak'ofar falon yatabbatar masa da babu lafiya. K'uru yayi yashiga da sallama, abin mamaki mahaifin Lubna ne da Mahaifiyarta, sai yayunta biyu da suhaima k'anwarta, Asma'u na tsigunne agefe da'alama kuka takeyima. Dukda babu Wanda ya amsa gaisuwarsa haka yak'arasa cikin falon, yarisina yana gaida iyayen nata, fuska babu yabo babu fallasa suka amsa, yad'ora dafad'in Abba lfy kuwa?. Lfy lau sai alkairi, Ameer yayan Lubna yafad'a amasife. Yawu Umar ya had'iye na 6acin rai, amma baice komaiba. gyaran murya mahaifin Lubna yayi, ya ce, "Umar nasan zakayi mamakin ganina agidanka?, toba abin mamaki baneba, baby ce takai k'ara akan bazata iya zama awannan kangon gidan nakaba, shiyyasa nazo ni dakaina na shaida maka nima banyarda d'iyata ta zauna anan ba, alfarma d'aya zan maka shine nabaka d'aya daga cikin gidajena kakoma kaida baby amma banda waccan sai farar k'afar, yanuna Asma'u. Sai yanzu Umar yad'ago yana kallonsa, yayi wani d'an murmushi sannan yamaida kansa k'asa. Duk azatonsu yaji dad'in k'yautarne shiyyasa ya murmusa, amma sai furucinsa ya tabbatar musu da sa6anin haka. Ya ce, " ngd sosai Abba da wannan k'yauta, saidai inamai baka hak'uri dabazan kar6aba, wannan shine gidan daya kasance dai-adai k'arfina, idan Lubna tana sona tayi hak'uri muzauna anan, danni gsky babu inda zan koma..... To aiko wlhy Umar saidai kasakeni........ Maganar Lubna takatseshi. Shiru yayi baice komaiba, Safwan ya ce, "tokaji fa, saika za6a sakinta kokuwa bin abinda takeso?. Kuyi hak'uri ya Safwan bazan iya sakintaba, kuma bazan koma ko inaba. To aikuwa zakaga sammaci, Dan yarinyata bazata zauna awannan kangonba tanacin gabza. Mom Dan ALLAH kuyi hak'uri, kufa iyayenmune baikamata irin wad'an nan zantukan suna fitowa bakinkuba. Mtsoww to ubana gayamin yanda zanyi?. Shiru Umar yayi Dan yasan wacece Mahaifiyar Lubna, masifaffiyace dama tafad'a aji. Mik'ewa sukayi suduka har Lubna d'in, kawai saiyajin anci kwalarsa. Cikeda mamaki yake kallon Lubna daketa girgiza jiki, ta ce, " wlhy saika sakeni. Tsawa yadaka mata ke banason iskanci sakemin Riga. Bazan sakiba wlhy saika bani takardata, kuma saki uku nakeso. Zuciyar 'yan mazan tazo kusa, aiko ya sharara mata mari..... Baisauke hannunsaba Mahaifinta shima yamareshi. Umar kana haukane?, agabana zama mari yarinyata, wlhy saikayi nadamar hakan, baby sakesa idan bai bayar da arzik'iba, aizaibada datsiya akotu. Sakinsa Lubna tayi suka fice suduka. Binsu kawai da kallo Umar yayi. Asma'u kuwa dama tun d'azu kuka takeyi, suna fita tashige d'akinta da gudu tana kuka. Itama binta kawai yayi dakallo. Zubewa yayi ak'asa yana sauke numfashi da hawaye, shikenan Dan *_KARAYAR ARZEEK'I_* tasamesa sai kowa yatsanesa?, shin shiya d'orama kansa?, miyasa mutane basa ganewa?, ya ALLAH kabani ikon cinye jarabawarka, ALLAH ka k'aramin hak'uri da Wuyan d'auka, yadad'e awajen zaune abin tausayi, dak'yar ya rarrafa yabar falon Yakoma d'akinsa. %%%%%%%%%%%% Bayan kwana biyu da faruwar hakan, ya Umar dukya k'ara ramewa yafita hayyacinsa, abincima sai Asma'u tasaka masa kuka yakeci, baya fita ko ina, yama tsaida aikin shagunan nasa, kud'in da k'annansa suka buk'ata yabasu. Yauma haka yatashi yanajin jikinsa duk babu dad'i, yasan tabbas da likita zai gwadasa saiyaga jininsa yayi hauhawar farashi zuwa dubu k'arewa 180+, yanzuma zaune yake afalo Asma'u ta ajiye masa abinci amma yakasa ci. Sallamar dasukajice tasakasu kallon k'ofar suduka, har Asma'u tamik'e ya ce, "tazauna yaje. Hannu yabama bak'on nasa suka gaisa, Umar ya ce, " kayi hak'uri ban wayekaba. Eh bazaka sannuba, sunana Ahmad ilyasu daga kotu aka aikoni nabaka wannan, yamik'a masa zungureriyar farar takarda. Jiki asanyaye Umar yakar6a, sallama yamasa yatafi, shikuma yajuya cikin gidan. Asma'u tabishi da kallo, tasan ko tambayarsa tayi dawuya ya amsa mata Dan haka taja bakinta tayi shiru. Zama yayi ya warware takardar ya karanta, girgiza Kansa yayi yana cije le6ensa, waishi Lubna takai kotu akan ya saketa?, tamanta da alk'awarin dasukaima juna?, tamanta da soyayyar dasuka Gina atsakaninsu?, tamanta hidima da k'aunar daya Nuna mata?, tamanta?, tamanta?, dayawa. Ninke takardar yayi yasaka aljihun jallabiyarsa. Yasakko yazauna ak'asa yaci abincin sannan yatashi yakoma d'akinsa yakwanta. Asma'u kam shiru tayi tana mamakin komi takardar ta k'unsa oho. %%%%%%%%%%%% Bayan kwana hud'u ya amsa kiran kotu. Bayan kammala wata shari'a aka fara tasu. Tashin farko lauyan Lubna yanemi takardar saki dabin kadin hak'in Marin da Umar yayma Lubna ranar. Umar ya ce, "shifa bazai saketaba, mari kuma it's tajama kanta. Alk'ali yaci kud'i, Dan haka yace tilas Umar yayi saki Dan Lubna tace yana barinta da yunwa, babu sittirar kirki, sharridai sosai suka shirya masa wad'anda dole suka tirsasashi yamata saki d'aya. Tayi tsalle tadire ta ce, ''uku takeso, Alk'ali ya ce, " yacika biyun. Ran Umar yakai k'ololuwar 6aci musamman da Lubna taci kwalarsa acikin kotu gaban d'unbin mutane, cikin 6acin rai yacikashe uku amma yace tabasa 'ya'yansa, nanma ta ce, "bai isaba tabada 'ya'yanta mayya tarainesu. Indai tak'aice muku tilas Umar yahak'ura, alk'ali yasashi biyan Tatar Marin dayayma Lubna, dakuma kud'i milyoyi akan rainon yaransa. Kukane kawai Umar baiba amma tuni duniyar tafara juya masa, a take anan yamata transpar d'in kaf kud'insa na Account zuwa Account d'inta, bai barma kansa ko nera d'yaba. Suna fitowa daga kotu yashiga mota yay gida ransa a6ace. Sukuwa su Lubna da 'yan uwanta sai farin cikin samun nasara sukeyi. Umar natsaida motarsa yafito, dak'yar ya iya shiga cikin gidan yana dafeda k'irjinsa, dak'yar ya iya sallama yashiga falon, aiko yana shiga ya yanke jiki yafad'i............... 😕wayyo ya Umar Fharuk😥. *_(((S)))....2017_* *_luv you all my fan's_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻typing.......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* _Sadaukarwa_ *_miss Xoxo na_* *_Zarah bukar_* *_Ayusha muh'd_* *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._* *_page→5_* ........da sauri Asma'u da Rafi'a sukayo Kansa, jikinsu sai rawa yakeyi, summa rasa taimakon dazasu bashi, Rafi'a ce tai k'ok'arin fita waje da gudu, cikin sa'a tayi gamo da mak'ocin ya Umar d'in zai fita. Kuka tasaka masa tana nuna masa cikin gidan, amma takasa magana. Ya ce, "yammata lfy kuwa?, fad'amin mike faruwa ne?. Dan ALLAH ka tai makemu ya Fharuk karya mutu....katai makem..... Ai baima bari tak'arasaba ya afka cikin gidan. ALLAH yasa ya iya mota, Dan danan suka taimaka masa suka d'akko ya Umar dayayi jagaf tamkar gawa. Rafi'a tafad'a musu asibitin datasan ya Umar d'in yana zuwa shida iyalansa harma dasu yakansa akaisu idan basuda lfy. Suna zuwa asibitin Rafi'a ta ce, " sukaishi office d'in Dr jafar. Babu marasa lfy ak'ofar office d'in Dan haka suka sami damar Shiga kai tsaye, Dr Jafar nazaune yana rubuce-rubuce jin anshigo ko sallama babu yasakashi d'agowa yaga wanene. Kafin yayi magana,... Rafi'a ta ce, "Ya Umar muka kawo Doctor pls ka taimakemu karya mut...... Kafin takai k'arshe anshigo da ya Umar, doctor yatashi ya taimaka musu aka d'orashi ad'an gadon da'ake d'ora marasa lfy. 'Dan duddubashi yayi sannan yadawo ya zauna yana kallonsu Rafi'a. Ya ce, " miya sameshi?. Fad'uwa yayi. Numfashi doctor yasauke tareda fad'in ALLAH ya sawak'e. Ameen, Asma'u da Rafi'a suka fad'a. Doctor yacigaba da fad'in, gsky bazan 6oye mukuba Umar yana cikin matsala, yanzu haka sai mun kwantar dashi sannan musan taimakon dazamu basa, zakuje kubiya kud'in gado dasauran Mayan aiki. Da sauri Asma'u ta ce, "doctor nawa ake buk'ata?. Uhmm kamar 100k insha ALLAH zasu isheku komai harma da canji. Idanu suka zaro waje harda had'a baki wajen fad'in 100k fa doctor?. Eh, haka nafad'a, aikunsan asibitin kud'ine wannan. Rafi'a ta ce, " to doctor tunda ya Umar abokinka ne kumasa duk abinda yadace idan yadawo hayyacinsa saiya Baku. Kai yagirgiza mata, bazai yuwuba aii, shima yasan dokar asibitinmu aii, kuma ma idan nace zanyi k'uri namasa komai idan yatashi yanada abin biyanane?, kuma kunsan Umar bashida ko sisi yanzu saidai yazamemin kaya, so kuke kawai kunemo kud'i kunga yana cikin danja. Wash hawayene masu zafi sukrbin kumatunsu Asma'u, sudai sunsan doctor Jafar aboki ya Umar ne nakusa, Wanda sunada tabbacin yana cikin jerin wad'anda sukaci gajiyarsa da dukiyarsa fiye da kowa, amma yau danyaga bayidashi shine yake furta wad'an nan kalamin akansa. Asma'u tadurkushr masa yana kuka da rok'on doctor jafar, amma yay kunnen uwar shegu da ita, saga k'arshema masifa yahauyimusu, kai nifa kuna cikamin kunne da 6atamin lokaci, idan kunada kud'in daza'a lura da Mara lafiyarku kubada, idan bakudashi kud'aukeshi kukaisa asibitin gwamnati. Ran Asma'u ya6aci sosai, dama ita akwai zuciyar tsiya, mik'ewa tayi fusace taja hannun Rafi'a suka fita. Saida sukaje harabar asibitin Rafi'a ta tirje tana ad'in Anty Asma'u wai ina zamujene?. Hawaye Asma'u tashare, ta ce, "Rafi'a kirakani inda ake sqida wayoyi, zansaida wayata, nasan insha ALLAH ko 25k zatayi. Ajiyar zuciya Rafi'a tayi ta ce, "to kije shagon su labaran na anguwarku, nikuma sainaje nafad'ama su mama king a yakamata su sank ko?. Eh hakanma yayi, saimun had'u to. Saga nan kowa yanufi inda zashi, sukabar makwafcin nan nasu tareda ya Umar. Shagonsu labaran Asma'u take, babban shagone da'ake saida wayoyi daduk abinda yashafi hakan, had gyara sunayi, matasane sunkai Bihar masu tsaron shagon, kowa da abinda take kula dashi. Asma'u tashiga da sallama, wani matashin saurayi ya ce, ''yammata kina buk'atar wani abune?. Fuskarta takuma tamkewa damage Asma'u babu damace wajen rashin walwala. Ta ce, " inaso na said a wayane. OK to naga wayar. Wayarta taciro tamik'a masa. Yakar6i wayar yana jujjuyawa tareda d'agowa yana kallonta. Ganin kallon mamakin dayake binta dashi yasata fad'in malam lfy kuwa?. Eh to Hajiya dadai sauk'i, amma tsakaninki da ALLAH wayarnan takice?. Cikeda mamaki take kallonsa, tagyara tsayuwarta sannan ak'ufule ta ce, "namaka kama da a6rauniyane?. A'a wlhy Hajiya ko d'aya, kinsandai rayuwarce sai'a hankali kawai, amma idan ranking ya6aci kiyi hak'uri. Idanma ban hak'uraba dukanka zanyi, kashiga cikin wayar sosai insha ALLAHU zakagane idanma tawace ko akasin haka. Shawararta yabi yashiga bincike awayar, tabbas tatace Dan hotunantama dake kai sun Isa shaida, yad'ago yana kallonta to Hajiya nawa zaki sayar?. Kasiya yanda yadace, nidai ina rok'onka kamin adalci kawai, nima dolece tasakani saida wayar badan nasoba. Jinjina kai yayi, ya ce, "nasiya 150k. Idanunta tazaro waje, kai malam kallifa da k'yau kaga wayar dake hannunka. Murmushi yayi Hajiya nagani sosai, wlhy nama saya da daraja aii....... Kafin tayi magana wani dake kusadasu yana sayen waya ya ce, " gsky kacuceta Dan wayarnan bata sha wahalaba. Asma'u da mamaki yakashe ta ce, nifa duk bamma fahimci inda kukadosaba, wayar dabata wuce 25k ba kuke kira mata 150k?, ahankama har ana fad'in an cuceni?. Wanda yasaka musu bakin ya ce, "Hajiya amma dai bake kika sayi wayarnanba?. Eh bani nasayaba, yayanane yasiyamin. Haba shiyyasa bakisan kud'intaba, wannan wayar dakike gani, ana saidata 400k wlhy. Idanu sosai Asma'u ta kwalalo waje, sai maimaita yawan kud'in take azuciyarta, dubu d'ari hud'ufa?, tabd'ijan, lallai ya Umar yayi k'ok'ari...... Tunaninta yakatse yayinda taji maganar labaran abayanta. A'a Asma'u lfy kuwa?. Lfy lau wlhy Labaran, nazo nasaida wayane. Tofa ina wayar?. Kaganta nan, tayi maganar tana nunama masa wayarta dake hannun saurayin. Hannu yamik'ama saurayin yabashi wayar, saida ya rissina sannan yabashi alamar girmamawa. Labaran yakar6i wayar ya jujjuya sannan ya ce, " nawa kasiya?. In ina saurayin yafarayi alamar rashin gsky, labaran ya girgiza kai kawai danyasan halin yaran shagon dason zuciya. Baice komaiba yak'irgo kud'i masu yawa yabata, Asma'u ga 330k kiyi hak'uri datayin farko dayayi mini. Babu komai tafad'a tana murmushi, ngd sosai labaran, amma Dan ALLAH kozan samu memory nakwashe abin kan wayar?. Babu damuwa, idan nakwashe zanbama Rafi'a takawo miki. To ngd sosai labaran. A babu damuwa Asma'u. Agurguje tafice tasamu adaidaita cikeda kwarin guywa suka nufi asibitin.......... *_(((S))).......2017_* *_luv you all my fan's_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR AZEEK'I!!_*💎 *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO......😜_* *_page→6_* .......Anshigar da ya Umar babu dad'ewa su mama suka iso, suduka sukai kan Asma'u suna tambayar jikin ya Umar d'in?. Jikin Anty sa'a tafad'a tana kuka, wannan yasa suka k'ara rud'ewa. Makwafcinsune yamatso, cikin hikima yamusu bayani. Godiya sukai masa sosai, daganan aka koma zaman jigum-jigum. *_3h...ago_* Dr yafito shida Nurse's dasuka taimaka masa. Shimadai rufuwa akansa sukayi suna tambayarsa jikin ya Umar. Yabuk'aci ganin wasunsu a office d'insa, amma babu Wanda zaya iya hak'uri abarsa abaya, Dan haka suka tafi suduka. Dr bai hanasuba saima gurin zama daya nuna musu. Kowa yasamu waje yazauna yanajiran bayani, bayan Dr yagama 'yan rubuce- rucensa yad'ago yana kallonsu, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce, "Alhmdllh, gsky Ku k'ara godema ALLAH akan taimakon daya bama Alhaji Umar danba kowane yake irin fad'uwarnan yatashi dai-daiba, amma shi Alhmdllh babu wata Marsala, saidai yana cikin matsannanciyar damuwa wadda saida taimakonku aikinmu zaikai ga nasara, yanzudai yasamu barci kuma bazai farkaba harsai nanda 24h Dan munaso zuciyarsa tasami Hutu sosai. Yanzu ga wannan zakuje kubiya kud'ad'en sannan kuma asayi wad'annan magungunan kafin ya farka. Atare sukace to Dr mungode sosaifa. Karku damu aikinane. Godiya suka masa sannan suka fita. Suna fita Mama ta kalli ya Abubakar, ta ce, " Abubakar saika amshi takardun kaje kabiya kakuma sayo magungunan ko?. Fuska ya murtike tamkar zai fasa kuka ya ce, "to kuzama shaida idan yatashi zai bani kud'ina Dan na kasuwane. Asma'u da Anty sa'a, mufida, Rafi'a duk kallon mamaki suke masa, shikansa ya fahimci haka amma saiya basar yamik'ama Asma'u hannu alamar tabashi takardun. Kanta ta girgiza ta ce, ''ya Abubakar kabarsa akwaima kud'i awajena kuma insha ALLAH zasu ishemu komai. Babu kunya ya washe bani yana fad'i a to kinyi k'yankai Asma'u. Babu Wanda yatanka masa acikinsu, Asma'u da Anty sa'a suka tafi wajen da Dr yafad'a musu. Sunbiya kud'in komai sannan sun sayo duk magungunan da ake buk'ata, dawowarsu babu dad'ewa ya Abubakar yawuce kasuwa akabarsu mama anan. Sumadai zuwa dare duk suka tafi akabar Asma'u kawai awajensa, da mamace zata tsaya Asma'u tace taje tahuta ita zata zauna dashi, dak'yar tayarda saida su Anty sa'a suka saka bakima. Bayan tafiyarsu Asma'u tayo alwala tashimfid'a sallaya, sallar isha'i tagabatar tayi addu'a sosai darok'on ubangijin al'arshi akan yakawoma mijinta d'auki da sassaucin halin daya tsinci kansa aciki, tashafa addu'ar tanamai zubar da hawaye, bayan kammalawarta saman kujerar dake d'akin tadawo ta zauna ta talsurama k'yak'yk'yawar fuskar ya Umar idanu, duniyar tunani tafad'a wa rayuwarsu tabaya maicikeda abubuwa na ban mamaki, ban haushi, al'ajabi, tausayi, farinciki, da jarabawoyi kala-kala........... *_SHEKARUN BAYA DASUKA SHU'DE_*🤔 Malam Tsalha baduku tsohon kirki mai mata d'aya da 'ya'ya uku aduniya. Hajara tsohuwa mairan k'arfe uwargida kuma amarya agidan malam Tsalha baduku, ta haifamasa yara uku 2maza 1mace. Usman, Kabiru, Binta. Sun rasu suduka tun shekarun baya dasuka shud'e. Usman yanada mata d'aya da yara Uku shima, Mero itace matarsa suna kiranta da mama, malam Usman mutumne mai hak'uri da kawaici, yanada son 'yan uwansa sosai dakuma iyayensa, bawani mai k'arfi banebashi amma mutumne mai Neman nakansa cikin tsaftatacciyar hanya, akwaishi da wadatar zuci dakuma Nuna godiyar ALLAH kan abinda yabashi walau kad'an kokuma mai yawa. Saidai Bahaka bane ga matarsa Dan itakam akwai hange-hange da son kud'i damai kud'i, Indai Kanada naira tokuwa kai abokin tafiyane, idankuwa babu to kana gefene awajenta. Yaransu uku Sa'adatu, Abubakar, Umar Fharuk. Sai kuma Kabiru matarsa d'aya wasila amma basu ta6a haihuwaba. Halin Kabiru shima yasha banban Dana malam Usman dankuwa shimadai akwai son 'yan canji, toshikam babu laifi yanada d'an hali danyafi malam Usman arzik'i. Sai Binta itamadai tayi aure harda yaranta, halintakam irinna malam Usman ne dantanada hak'uri sosai da kuma zafi idan ka k'ureta. Yaranta hud'u duk mata, Saratu, Asma'u, Fateema, Hasiya. ALLAH yayima malam Usman rasuwa tunsu Umar suna k'anana danshi bama sosai yasanshiba, bashida wayo sanda yarasu. Bayan Rasuwar malam Usman rik'on yaran yacigaba gudana hannun mahaifiyarsu mama, ta taka rawar gani sosai wajen kula dasu har bayan shekara uku da rasuwar malam Usman sai kawu Kabiru yazo da buk'atar auren mama abisa shawarar da inna binta k'anwarsu tabashi. Dagudu kuwa mama ta yarda Dan tasan Kawu Kabiru yanada d'an abin hannunsa gashi kuma baita6a haihuwaba, ba'a wani 6ata lokaciba aka d'aura auren, anan gidan tacigaba da zama, cikin ikon ALLAH kuwa saiga ciki, wayyo zokaga murna wajen kawu kabiru da family gaba d'aya, tattali sosai yakema mama, ciki yanakai wata Tara da wasu kwanaki ta sunkuto d'anta Namiji Wanda yaci suna Usman suna cemasa Harris, shekarar Harris biyu mama takuma haihuwar mace Mufida, daganan sai Auta Rafi'a. Rafi'a nada shekara biyar aduniya Anty sa'a tayi aure bayan ta kammala karatunta na Secondary, taso cigaba da karatu amma hakan bai samuba, shima Ya Abubakar a daddafe da buga-buga yakammala Diploma d'insa, daganan yay aure yanad'an sana'ar saida kayan provision awani shago dake k'ofar gidansu. Bata sake zaniba akan Umar Fharuk dan shimadai duk ajirgi d'aya suka sauka, bayan kammala secondary yafara karatun nasa a B,U,K saboda k'yawun result d'insa kai tsaye degree suka basa, dahad'a gabas had'a yamma aka kammala, ALLAH yabashi nasarar fita da result mai k'yau, yayi farinciki sosai hakama 'yan uwansa musamman ma mama Dan aganinta itamafa karan 'ya'yanta yakai tsaiko yanzu. Umar yadawo zaman gida babu aikinyi, tun zaman yana masa dad'i harya fara gundurarsa, tuna maganarnan ta hausawa dasukance babu maraya sai rago tamasa allurar tashi domin Neman abinyi, duk abinda yasan zai rufa asirinsa yinsa yakeyi babu sanya ko girmankai irinna 'yan bokon nan, ana haka wani abokinsa yay masa hanyar Babur na adaidaita sahu, sosai Umar yaji dad'in wannan taimako, cikin farin ciki yazoma mama da kawu Hamidan wannan labari. Hummm, amma saisuka gwaleshi da nuna masa wannan k'ask'ancine, yaza'ayi kamarsa dayakeda kwalin degree yak'are da tuk'a babu, gsky yacanja shawara amma ba wannanba. Wannan lamari ya6ata ran Umar sosai, Dan haka ransa a6ace yanifi gidan inna binta. Tarba sosai yasamu agurinta Dan d'an gatantane. Inna tasaka Fatee takawo masa abinci da ruwa, saida yaci yak'oshi sannan yakwashe komai yafad'a mata. Itama ranta ya6aci sosai Dan haka taita fad'a kamarsu mama na gabanta, takuma kwantar masa da hankali akan zata samesu, shikuma yaje yakar6i adaidaita sahud'in yafara aikinsa. Yaji dad'i sosai Dan haka yayta mata godiya, daganan hira maidad'i suka cigaba dayi Dan akwai shak'uwa tsakaninsu sosai. Sallamar Asma'u da Hasiya ne yasakasu katse hirar suka amsa. Asma'u tazube littatafanta na islamiyya tana fad'in wash inna wlhy nagaji yau. Binna ta ce, "to sannu ragguwa, amma bakiga yayankiba. Idanunta tad'ago ta kallesa, saikuma ta kauda kai tace ina yini. Bai amsataba saima hararta dayakeyi, takuma fad'in inayini, Dan ita azatonta baijibane, d'an yatsine fuskarsa yayi sannan ya amsa, yamaida kallonsu ga Hasiya da itama take gaidashi, ya ce, " Autar inna ya islamiyyar?, kinadai yin k'ok'ari ko?. Hasiya ta jinjina kai ta ce, "eh yaya munayi, yanzu hakama ina ajin sauka nida yaya fatee, yaya Asma'u kuwa sune manya Dan sune 'yan ajin hadda. d'an satar kallon Asma'u yayi, suna had'a ido ya kauda kai. Asma'u tad'an ta6e baki tareda mik'ewa tashige d'akinsu tana k'unk'unai Dan haushin ya Umar takeji saboda abinda yay mata shekaran jiya, tana hira da saurayinta ya koreshi, abin bak'aramin haushi yabataba. Bata k'ara fitowa falonba saida taji yatafi sannan tafito. Inna tabita da kallo, kekuwa Asma'u mikikeyi ad'aki tun d'azun?. Kanta tad'an sosai ta ce, "inna ina wayane da Anty saratu fa. Inna batace komaiba ta mik'e, saida takusa zuwa k'ofa sannan tajuyo tana kallon Asma'u, ta ce, "idanma laifi kikaima Umar to wlhy kiyi gaggawar bashi hak'uri Dan kinsan Sam banason raina nagaba. Asma'u ta kwa6e fuska kamar zatayi kuka, nifa inma ban masa komaiba. Ohodai nidai nafad'a miki, inna tafad'a tana ficewa daga falon........ *_(((S)))......2017_* *_Luv you all_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→7-8_* ......Umar kam tun aranar yaje yakar6i Babur d'in Adaidaita sahu, kuma aranar yafara aiki, ganin alkairin daya samu yasakashi farinciki sosai tareda samun kwarin guywa. Bai sanarma kowa yafara aikiba agidansu saida inna tazo washe gari sukai magana dasu mama, badan mama tasoba ta amince, amma babu yanda zatayi Dan tanason inna binta sosai kodan k'aunar datake nunama 'yayanta, ta taka rawar gani sosai akan karatun Umar Dan d'an gidantane. Tundaga ranar Umar yacigaba da hayar adaidaita sahunsa, dukda mama bata nuna farincikinta aikai hakan bai hanashi yimusu hidaimaba da d'an abinda yasamu, babu yabo babu fallasa suke kar6a, shikam Umar ko kad'an hakan baya damunsa harkokinsa kawai yakeyi. Ana haka sai wani al'amari yafaru a wani daren Juma'a ranar alhamis kenan da daddare. Bayan Umar yagama aikinsa misalin k'arfe 11 saiyayi harama tafiya gida. Yana cikin tafiya saiyaga ana d'aga masa hannu tundaga nesa, lamarin yabashi tsoro Dan azatonsa 'yan fashine ko 6arayin Babur, haka yak'arasa wajen guywarsa asage yanata ambatar duk addu'ar datazo bakinsa. Yataka birki agaban dattijo da wani matashi daketa k'ok'arin tsaidashi, matashin saurayinne yayma Umar magana. Abokina Dan ALLAH kozaka kai alhaji gyad'i-gyad'i?. Shiru Umar yayi na 'yan sakwanni zuwacan yasauke ajiyar zuciya tareda kallon agogon hannunsa, ya ce, "abokina darefa yayi duba kagani, gashi kasan akwai tazara daganan zuwa gyad'i-gyad'i. Nasani abokina amma Dan ALLAH ka taimaka, wlhy daga airport na d'akko mai gidana saikuma mota tamana tsiya, tun d'azun muke tsumayen abin hawa amma bamu samuba. Kafin Umar ya ce, " wani Abu dattijon Alhaji yalek'o yanafad'in yaro kadauro Dan ALLAH, wlhy nagaji sosai burina kawai nahuta. Ajiyar zuciya Umar yasauke tareda gyad'a kai ya ce, "shikenan shigo mutafi baba. Alhaji yaji dad'i sosai, Dan haka yashiga sakama Umar albarka, kayansa direban yakwaso zuwa adai-daitar sukaiyi sallama Umar yaja suka tafi. Tunda suka tafi babu maima wani magana, Umar yana tuk'i yana tunanin rayuwa da yanda take tafiya, Alhaji kam yayi shiru abaya saboda gajiyar zaman jirgi dake nuk'urk'usarsa, saida suka isa gyad'i-gyad'i sannan Alhaji yanuma Umar layin dazasu shiga. Ak'ofar wani katafaren gida suka tsaya, Umar yajinjina kai azuciyarsa yana fad'in wani kaya sai amale..... Alhaji yakatse masa tunani da mik'a masa kud'i masu yawa Wanda shima baisan adadinsuba. Umar ya yakalli kud'in ya kalli alhaji sannan ya ce, " baba 350 ne kud'inka aii. Murmushi alhaji yayi ya ce, "d'ana karka damu kaidai kar6i. A'a baba ngd kabani iya hak'k'ina kawai, girgiza kai Alhaji yayi dakuma ajiyema Umar kud'in akan cinyarsa, babu yanda Umar ya iya dole yakar6a yay godiya sannan yatafi gida da addu'ar ALLAH yakaisa lfy. Inda yake kai adai-daitarsa yanufa, yasamu guri yay fakin, abinda yake lilli6eta yajawo zai rufe sai idanunsa suka sauka akan wani d'an k'aramin akwati, shiru yayi yana nazarin kowaye ya manta?. Wata zuciya ta ce, " masa Alhajin Daka sauke yanzu. Afili ya ce, "hakane kuma, ya kalli agogonsa saiyaga har 12:36, gsky yanzu yana tsoron sake hawa titin nan, kuma idanma ya iya komawa yanada tabbacin za'a barsa yashiga wannan gidan a irin wannan lokaci?, d'an tsaki yaja tareda d'aukar akwatin yana fad'in insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu da sassafe saina kai masa. Da wannan shawarar yanufi gida, dama kullum shine k'arshen dawowa gida shiyyasa yake rik'eda key d'in gidan guda d'aya, bud'ewa yayi yashiga sannan yamaida yarufe tareda addu'ar rufe gida, d'akinsa yashiga yay wanka da shirin barci sannan yay nafilfilinsa kamar yanda yasaba ya kwanta. _washe gari_ Tunda yatashi yay sallar asuba bai koma barciba dama shi haka yake bai iya barcin safeba kullum yana dawowa daga masallaci zai d'auki alkur'ani yahau karatu, saida gari yay sha sannan yay addu'oi yatashi, wanka yashiga. Shigarsa babu dad'ewa mama ta shigo d'akin, idontane yasauka akan bak'uwar jakar mai k'yau, jikinta har rawa yakeyi tabud'e jakar, idanu tazaro amatuk'ar razane Dan ganin mak'udan kud'in dake cikeda d'an akwatin duk daloline sababbi k'ar. Razanuwa da ganin kud'in yasa takasa aikata komai har Umar yafito daga wanka, shimadai bak'aramar razana yayi dagani kud'inba, Dan yauce rana ta farko daya fara ganin zunzurutun kud'i tsirara agabansa masu yawan haka. Jikin mama amace ta ce, " Umaru INA kasamo wad'annan kud'in haka?. Zama yayi abakin katifarsa, yajanyo jakar yana rufewa mama ba nawabeneba, wanine nad'auka jiya da daddare shine yamanta da jakar. Mama ta washe baki tana fad'in Umaru aii yamzun sunzama naka tunda tsuntuwa kayi, lallai kagodema ALLAH da wannan arzik'i daya yimaka, dama masu iya magana necewa dare d'aya ALLAH kanyi bature. Kallonta kawai yakeyi damamakin ganin rikicewar datayi Dan kawai taga kud'i, shi rabonma dayaga fara'ar mama agareshi harya manta wlhy, amma duba daga ganin kud'i dukta rikice, ya kauda Kansa saboda 6acin rai, amma kasancewarsa jarumin 6oye sirrin zuciya sai fuskarsa bata nunaba ko kad'an, cikeda ladabi ya ce, "mama zan maida MASA kud'insa ne, Dan zan gane gidan Dana saukesa insha ALLAHU. 6ata rai mama tayi, ta gallama Umar harara to Uban masana basaikaita maidawarba, idan banda ga6anci ALLAH yabaka irin wannan dukiyar har kayi tunanin maidama mai ita?, shi Kasan ta hanyar daya samu?, k'ilama 6arawon gwamnatine. Kiyi hak'uri mama ALLAH ya huci zuciyarki, abinda zaki duba wannan kud'i ba hakkina bane, koma tayaya maisu yasamesu wannan shiyya d'aukarma Kansa kaya, inada damar maida masa kud'insa, to aii gara na maida domin ubangijinafa da barci ko gyangyad'i baya d'aukarsa yana kallona, kuma baya yafe hak'k'in wani akan wani face kanemi gafarar Wanda ka zalunta, tonikuwa mizaisani butulcema ni'imar da mahalliccina yay mini? na tsarkakakkiyar zuciya. Mik'ewa mama tayi a fusace tafice tanata masifa. Umar ya girgiza Kansa tareda sauke zazzafan huci, afili ya ce, " mama ALLAH ya shiryeki. Niko bilyn Abdul sai na ce, "ameen ya Umar🤷🏽‍♀. Koda Umar yagama shirinsa yanufi d'akin mama Dan mata sallama kamar yanda ya saba. Da sallama yashiga falon, babu kowa sai Mufida da Rafi'a dake break fast kowanne sanye cikin kayan makaranta na gwamnati. Gaisheshi sukayi, ya amsa yana tambayar ina mama?. Mufida ta ce, "tafita makwafta yaya. Makwafta kuma?, yanzu da sanyin safiyarnan?. Shiru sukayi basuce komaiba, ya ce, " to kutashi mutafi idan kun gama?. Rafi'a ta ce, "yaya bazakayi kari ba yau?. A'a Rafi'a yau ina saurine, kudai kutashi muwuce, to suka fad'a suna mik'ewa, kowa yad'auki jakarsa ta makaranta suka fice. Atsakar gida suka gamuda kawu, Umar yadurk'usa har k'asa yana gaida shi, Abba ina kwana. Lfy lau Umaru anfito?, eh Abba mun fito, to wannan akwatinfa haka?, Abba wlhy wanine ya mantashi jiya dana d'akkoshi shine zanje na mayar masa, tofa yo kai Umaru banda abinka aii wannan tsintuwace, karik'e abinka kawai mana, nasandai bai wuce kaya bane aciki?, murmushi Umar yayi yanamai jinjina halin iyayen nasu aransa, ya ce, " karka damu abba nasan gidansa zankai masa dan takardune aciku, aikin 6ur inji tusa, a'a jeka kakaimasa abinsa, mizakayi dawasu tarkacen takardu dadai kud'ine ko kaya saika rik'e, nanma murmushi kawai Umar yayi harsu Mufida na tayashi. Rafi'a da Mufida ma suka gaidashi, suma amsawa yayi cikeda fara'a. Sallama sukai masa sannan suka fice, wajen adaidaitarsa sukaje, saida ya goge sannan suka shiga, makaranta yafara saukesu daganan yanufi gyad'i-gyad'i. Da gyar ya iya gane layin, yatsaya adaidai inda yasauke dattijon Alhaji, gidan dayaga alhajin yashiga yake kallo, shi saima yanzu yaga gidan sosai, katafaren gidane na mai jida 'yan canji, komakaho yashafa katangar gidan yasan mai gidan ya shahara kuma yagama jik'ewa da data. Yad'an dad'e atsaye yana tunanin yanda zai shiga gidan, baigama tunaniba yaga an wangale k'aton gate d'in gidan, wata dalleliyar motace tafito bak'a wulik sai d'aukar ido takeyi, k'arfin hali Umar yayi yamatsa kusada motar yana d'aga masa hannu. Ahankali aka sauke bak'in Gila's d'in motar, wani matashin saurayi dabaifi sa'an Umarba ya bayyana. Umar ya ce, "sorry Dan ALLAH inada tambayane?. Inajinka saurayin yafad'a cikeda isa. Umar ya ce, " jiya nakawo wani dattijo gidannan, to bayan mun rabu sainaga yayi mantuwa Dan haka nakawo masa abinda ya manta d'in. Saurayi ya kashe motarsa sannan yacema Umar ya kamannin dattijon yake?, danshi ko kad'an baikawo dad d'insu bane. Lissafa masa Umar yashigayi, cikeda mamaki Saurayin ya ce, "my dad, tomiya kaishi hawa adaidaita sahu?, bud'e motarsa yayi yafito, ya ce, " to muje cikidai. Umar yad'auki d'an akwatin suka shiga cikin gidan, saurayi na baya Umar nabinsa abaya............ *_(((S)).....2017_* *_Luv you all_*😻🤝. [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→9-10_* .........Wata had'ad'diyar k'ofar Gila's suka nufa, saurayin ya danna wani abu k'ofar tabud'e da kanta, Umar dai yanadaga baya yana kallon ikon ALLAH. Bayan k'ofar tabud'e suka shiga k'aton falon dayagama k'awatuwa da kayan alatu, gurin zama saurayin ya nunama Umar sannan yashiga cikin gidan domin Neman iso. Umar na zaune yanata Rarraba idanu tsakanin falon da kayan dasuke ciki saurayin yadawo. Bismillah yafad'a yana nunama Umar hanya, mik'ewa yayi yad'auki jakar suka tafi, gaba da gabanta Umar yafad'a aransa yayinda suka shiga falo na biyu, saiyagama falon farko Ashe bai had'uba, yayinda suka shiga na Uku sai kan Umar yakusa kwancewa Dan maganama ta gagaresa, benen dake tsakkiyar falon suka hau anankam Umar yakasa daurewa saida ya ce, "masha ALLAH, falone nafad'a aji Wanda koda saga binnin sin kazo dolene ka yaba, nanma gurin zama ya nunama Umar. Umar yazauna kad'an akujerar tamkar bayaso, sai 'yan kalle-kalle yakeyi. Woow!!...... Yaji wata zazzak'ar murya yafad'a. d'ago fararen idanunsa yayi ya sauke akan k'yak'yk'yawar fuskar mamallakiyar muryar, ya sauke numfashi ahankali tareda kauda idonsa akanta Dan itama nata icon nakansa kam ko k'yaftawa batayi. Batasamu damar yin maganaba dad da Safwan suka fito. Umar yamike domin nuna girmamawa ga dattijon, dattijo yay dariya tareda fad'in a'a saurayi kaine?. Nine Alhaji, Umar yafad'a cikeda girmamawa. Bismillah zauna mana, zama Umar yayi ak'asa, Alhaji ya ce, " a'a tashi ka koma saman kijera mana, nanma yayi wlhy Alhaji ngd. Daganan Umar ya gaida Alhaji, cikin fara'a ya amsa masa, Umar yad'ora da fad'in Alhaji dama mantuwar sannan kayi, to jiyan naso dawowa na maida maka saikuma naga dare yayi shiyyasa nabari sai yau. Tunda Alhaji yay tozali da akwatin kud'insa sai mamaki da al'ajabi ya lullu6esa, damage akwai sauran mutane nagari aduniya irin Umar?, Alhaji yajawo akwatinsa gabansa yabud'e, kud'insa na nan yanda ya shiryasu, yad'ago yana kallon Umar cikeda mamaki, Safwan ma dai kallon Umar yakeyi, hakama budurwarnan tad'azun. Ajiyar zuciya Alhaji yasauke tareda fad'in yaron kirki kenan, nunama rasa abin fad'a saboda lunbin mamaki daya cikani, yaro yaya sunankane?. Umar Fharuk!. Masha ALLAH Umar Fharuk mai gaskiya da rik'on amana, lallai kadace da k'yak'yk'yawar zuciya maicikeda alkairi, ALLAH yasa kad'ore haka har karshen rayuwarka, wlhy bammasan namanta jakarnan awajenka ba, amma saboda adalcinka ka kawomini, kila dasai natashi amfani dakud'in naita bulayin Neman, kaidai ALLAH yayi maka albarka. Gaba d'aya suka amsa da ameen har mom da Suhaima dake fitowa yanzun, Safwan yamik'ama Umar hannu sukayi musabaha sannan ya ce, "d'an uwa munfa gode sosai, nizan wuce abujane lokaci NATA tafiya, To ALLAH yatsare Nina ngd sosai. Safwan yayma iyayrnsa da k'annensa sallama harya kama k'arfen bene zai sauka budurwar d'azu ta ce, " ya Safwan Dan ALLAH karma manta da sak'ona wajen Fidoo. Karki damu baby zan fad'a mata insha ALLAH. hannu tad'aga masa tana murmushi harya sauna. Umar ya ce, "zaitafi wajen aiki, harya mik'e Alhaji ya ce, " Hana Umar Fharuk koma ka zauna aii alkairi dank'one baya fad'uwa k'asa banza, baby kusa kuku yashirya mana break fast. To dad, Budurwar d'azu wadda suke kira baby ta amsa. Babu yanda zaiyi dole yahak'ura ya zauna har aka gama shirya had'ad'd'en break fast a dinning. d'unguma sukayi gaba d'aya zuwa dinning, Umar dukaya takura, musamman akan kallon k'urullah da baby ketamasa tun d'azun, dasun had'a ido saita sakar masa k'ayataccen murmushi, adaddafedai yakammala break d'in yamik'e, Alhaji yakama hannunsa har falonsa dashima ya amsa sunansa dankuwa komai yaji tamkar baza'a mutuba, zaunar dashi Alhaji yayi akan luntsumemiyar kujerar ta alfarma sannan shima ya zauna, idonsa akan Umar ya ce, "Umar Faharuk kayi karatu?. Eh Alhaji nayi. Wane mataki ka taka?. Nahad'a degree d'ina Alhaji harda bautar k'asa. Masha ALLAHU, ammafa kabirgeni wlhy, awannan zamanin bokowane matashine kamarka zai kammala karatun Degree ba yadawo tuk'a adaidaita sahu, Dan aganinsu hakan zubar da girmane, kuma bahaka baneba. Umar dai kansa na k'asa yana murmushin jin dad'i. Alhaji ya ce, " to yanzu insha ALLAHU zan taimakeka domin nima ka taimakeni taimakon dabazan ta6a mantawa dakaiba atarihin rayuwata, idan kanason aiki kakawo takardunka zan nema maka, idan kuma kasuwanci kakeso wannan mai sauk'ine daga gobe ma zaka fara insha ALLAHU?. Wani dad'ine yatsarga zuciyar Umar, yad'ago yana kallon Alhaji, zamowa yayi k'asa ya tsigunna yana masa godiya, Alhaji yakamashi yamaida saman kujera yana fad'in karma damu Umar kaima kazama d'ana aii, yanzu wanne kaza6a?. Alhaji naza6i kasuwanci Dan dama shine burina, nayi karatune Dan kare mutuncin kaina amma badan aikiba. To Alhamdllh naji fad'in za6inka nima sosai, Alhaji yamik'e yana fad'in jirani ina zuwa. Babu dad'ewa yafito, yazauna kusada Umar tareda mik'a masa makullin mota, Umar ga wannan tukuycin alkairinka gareni. Idanu Umar yazaro bakinsa na rawa ya ce, "baba motacrfa?. Dariya Alhaji yayi ya ce, " nasani Umar motace tana nan aharabar gidannan, zansa direba yakaimaka har gida, idankuma zaka d'auka da kankane babu laifi. Hawayen farinciki Umar yakeyi, ya ce, "baba dakabarsa, wlhy ban kawo maka jakarnan danka sakamin dawani abuba, namaido maka da itane saboda tsoron ALLAH da cin hak'in saba nawaba. Alhaji yakamo hannun Umar yasaka masa key d'in Hana fad'in nasani Umar, nima namakane badan na biyakaba aii. Godiya sosai Umar yayma alhaji sannan yafito. Afalo yatarar da baby da Suhaima, suna ganinsa baby tamik'e tsaye cikin fara'a ta ce, "ya Umar kafito?. d'an murmushi yamata tareda jinjina Kansas. Takashe masa ido d'aya tana wani far da idanu, tobara namaka rakkiya ko. Baice komaiba Dan tafara gundurarsa, kusan at are suka sauka, ganin haka yasaka Suhaima bin bayansu da sauri danson ganin abinda zai faru. Har wajen gate suka rakoshi, yashiga a adaidaitarsa yatada, baki Suhaima ta ta6e afili tace kambu tak'ashinnan, yanzunan duk had'uwar bawan ALLAHn Nan a adaidaita sahu yazo?. Hararta Baby tayi sannan tak'arasa kusada Umar dake k'ok'arin tafiya, ta ce, " ya Umar mungodefa sosai, inafata zaka cigaba da ziyartarmu Dan sada zuminci?. Kallonta kawai yayi baice komaiba ya kauda kai. Murmushi tayi azuciyarta ta ce, "ka cancanta my guy, afili kuma ta ce, " I Love you so much.💋 Da sauri Umar yad'ago yakalleta amma tuni harta bar wajen ta isa inda Suhaima ke tsaye tana kallonsu. Kasa tafiya yayi yatsaya binsu da kallo, harsaida suka isa gate sannan Baby tajuyo ta kanne masa ido d'aya tashige cikin. Wata sassanyar ajiyar zuciya yasauke sannan yakuma tada baburd'in yafice daga anguwar cikeda farin ciki. Tunanima yake wayakamata yafara fad'ama albishir d'innan, su mama ko inna ko Anty Sa'a?, baisan dawa zai faraba. Daga k'arshedai ya yanke shawarar fara zuwa gidan inna, dankoba komai itace ta k'arfafa masa hayar adaidaita sahun, togashi tasilar hakan yayi gamon katar da tarin alkairi, kunga kuwa aii ita yafi cancanta tafara sani ko?.🤷🏽‍♀ Kai tsaye gidan inna yanufa kuwa........ *_(((S)))........2017_* *_Luv you all_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO......😜_* *_page→11-12_* ........Tun'a k'ofar gida yaci karo da abinda yasaka farincikinsa rauni, wato ganin Asma'u da wani saurayin ranar, Asma'u na ganinsa ta 6ata fuska Dan gudun karya k'ara bata kunya kamar ranar, abisa tsautsayi suka had'a ido, yamaka mata wata uwar harara. Kauda kanta tayi daga kallonsa, saurayin na gaisheshi amma ko kallon bai isheshiba yashige cikin gidan. Asma'u tarakashi da harara. Saurayin ya ce, "Asmy wanene wancan kuma?, nagafa sai hararmu yakeyi?. Baki Asma'u ta ta6e ta ce, " yayanmune. Kai Asmy shine baki fad'aminba na gaisheshi da k'yau?. Uhmm kaga Zayyan share batunsa kawai, yanzu yaushene zaka dawo a tafiyar?. Uhmm insha ALLAHU bazan wuce 2year's ba zan dawo. Kai kana nufin bayan mun kammala s,s,c,e fa kenan?. Eh hakane my Asmy, amma kiyi hak'uri nima Bahaka nasoba wlhy, kinsan karatunane yakawo haka, kuma umarnin Abba ne babu yanda na iya. Shikenan ALLAH yatsaremin kai, yasa kaje a sa'a kadawo a sa'a. To ameen my Asmy, shiyyasa nake k'ara sonki da k'yaunarki akowacce dak'ik'a ta rayuwata. Murmushi Asma'u tayi, tareda fad'in nima ina sonka sosai zayyan, tayi maganar tana rufe fuskarta da hijjabi. Dariya zayyan yayi yace Asmy sarkin kunya kenan...... A6angaren ya Umar kuwa ransa a6ace yashiga gidan, inna data fito daga d'akin baba mahaifinsu Asma'u ta ce, "a'a Umaru kaine agidan?. Murya acinkushe ya ce, " nine Inna, sannu. Yauwa Umaru, amma yanaga kamar Ranka a6ace yake?. Da sauri ya saisaita nutsuwarsa, shikansa yana mamakin yanda baya iya 6oye Bacin ransa idan yaga Asma'u da saurayi, kuma aii hakan bata faruwa akan Mufida kosu fatee, wata zuciya ta ce, "aigara Mufida tayi girma tunda tana 100L a jami'a, amma Asma'u fa SS 1 take a secondary........ Innace ta ta6ashi, firgigit yadawo daga duniyar tunani, ta ce, " tunaninmi kuma kakeyi Umaru?. Cikin inda-inda ya ce, "babu komai Inna wani albishir Nazo miki dashi, amma mi Asma'u yakeyi awaje da safennan?, mima yahanata zuwa makaranta. Dariyace taso kufcema Inna saboda hango kishi k'uru-k'uru a idanun Umar, amma saita dake tace kasan suna Exam, toyau basuda ita shiyyasa, wancan kuma Zayyanne wai zaiyi tafiyane shine yazo suyi sallama. Kansa kawai yagyad'a amma bai iya cewa komaiba yamik'e yana fad'in bara nagaida baba. To kashiga yana ciki. Ak'ofar d'aki yayi sallama, saida aka bashi izinin Shiga sannan yashiga. Baba na zaune yana karin kumallo Umar yashiga, cikeda fara'a yataresa, Fharuku kaine agidan namu?. Nine baba ina kwana?. Lfy lau Umar ya hidimomin duniya?. Alhmdllh baba. To masha ALLAHU, kaga matso muci abinci ko?. A'a wlhy baba nakarya nikam. Kai Umaru karfa filako kakeyi?, a'a baba yazanyi filako agidanmu, nak'oshine kawai, to shikenan, yawajensu Maman taku?, lfy lau suke baba sunama gaisheku, a muna amsawa wlhy. Umar yamik'e to baba bara naje mugaisa da Inna natafi wajen nema. To Umaru ALLAH yabada sa'a kaji, ayitadai hak'uri da yanayin rayuwa, duk Wanda kaga yayi hak'uri baici ribaba to d'an kad'an yayi, duk abinda ALLAH ya albarkaci mutum dashi karya raina yace Alhmdllh, to insha ALLAHU ALLAH zaibasa mafiyinsa agaba kajiko?. To baba ngd sosai, ALLAH yak'ara yawancin kwana. Ameen Umaru ALLAH yayi albarka kuma. Amen summa ameen baba, naira 500 ya ajiyema baba, baba ga wannan asha fura. Kai a'a Umaru zoka d'auki kud'inka kaji, nikam bazan kar6aba, airik'e kankuma dakukeyi abin alfahirinmune basai kumbamu ko sisiba. Hhh baba Dan ALLAH ka kar6a kasamusu albarka, nima banisu akayi. To shikenan Umaru ALLAH yak'ara bud'i na alkairi ngd sosai. Babu komai baba Umar yafad'a yana ficewa daga d'akin. d'akin Inna yashiga, azaune yatadda ita tana jiransa, yasamu waje yazauna suka k'ara gaisawa da tambayar lfyar juna. Alhmdllh Inna sai godiyar ALLAH. To aii haka akesonji Umaru, wanekuma albishir aka kawo mini?. Murmushi yayi tareda gyara zama yazayyane mata komai tundaga jiya har safiyar yau. Farinciki sosai Inna ta Nuna harda kukan dad'i, tashi tayi tagad'oma baba shima yayi farinciki sosai, har d'akin inna yashigo yataya Umar murna da wanan k'yauta. Suna cikin farincikinsu saiga Asma'u tadawo hannunta d'auke da Leda. Itadai kallonsu kawai takeyi, data kasa jurewa saita ce inna wai miya farune kuketa murna haka?. Inna ta zayyane mata komai, itama sosai tanuna farincikinta akai, ya Umar kam sai antaya mata haarar yakeyi, ko a jikinta wai antsikari kakkausa. Bayan sun gama murnar yatashi yatafi akan zaidawo gobe yanuna musu motar. To d'an Albarka, ALLAH yayi albarka kaji. Ameen inna saina dawo......... Daganan sai gidan Anty sa'a, ita kad'ai yatarrar agidan Dan yara suntafi makaranta, tamik'e da k'yar saboda tsohon cikin dake jikinta, oh ni Umar dama kana duniya?. Dariya yayi ya ce, "Anty Sa'a ina zanje?, hidimomine kawai sukaimin yawa. Haka kuka iya kullum kaida Abubakar da Harris bakwa rasa uzuri aii. Tab Anty aii garani da wad'annan, kema kinsan ina k'ok'arin zuwa wajenki fiye dakowa agidanmu. Eh to hakane kuma, amma aii kaima wani lokacin saika 6ace 6at. 'Yar dariya yayi ya ce, " hakadai kikace Anty sa'a. Oh hakama zakace?, Anty sa'a tafad'a tana fita daga falon. Babu dad'ewa tadawo d'aukeda tire shak'e da kayan ciye-ciye. Da sauri Ya Umar yamik'e yatarota, kai Anty yakamata ki saukema kanji irin wad'annan aiyukan, ai kinyi nauyi dayawa. Zama tayi da dabara, shima ya ajiye tiren sannan ya zauna. Ta ce, "k'anina yazanyi, aii dole natashi nayima kaina, 'Yar mai aikin dake taimakamin kakarta tarasu taje gida tun shekaranjiya, jabeer da Laila kuma mizasu iyamin inbanda su 6ata. To da wannan Dan wannan kuma, amma gsky mata kuna bani tausayi matuk'a, koda rainon cikinnan kad'ai akabarku aiba k'aramin k'ok'ari kukayiba, balle ga haihuwa, raino, tarbiyya dukfa suna kanku, kai ALLAH yasaka muku da aljannadai. Amin d'an k'anina, Anty sa'a tafad'a tana dariya. Shima dariyar yayi yana kai kofin zo6o bakinsa, saida yasha sosai saboda k'aunarsa da zo6o sanan ya ce, "big aunty dawani daddad'an albishirfa nazo miki. Tofa k'anina ko ansami matar aurene?. d'an tsaki yayi ya ce, " Anty wane matar aurefa, aii aurena banan kusaba kuma dainamin zancensa. Umar kanka d'aya kuwa?, wai sokake saika tsofe agidane?, shekararka fa 28 yanzu, amma ace babu aure agabanka?. Hummm Anty sa'a kenan, Ku kawai auren kuke ambata, amma bakwa tunanin inda mutum zai ajiye matar, abinda zataci, Wanda zai mata sittira dakuma matsalolin yauda kullum musamman na rashin lafiya dakanzo tamkar ha6o. Hakane Umar amma aii duk ALLAH ne mai komai da kowa ko?. Hakane Anty ALLAH yasa mudace to, dama albishird'in nawa shine..................tas ya zayyane mata komai. Saboda farinciki jitake kamar tatashi taita tsalle, ta ce, "ALLAH sarki Umar kaga ribar hak'uri ko?, lallai yau nayi farinciki sosai, ALLAH yasa iyakar wahalar kenan. Amen Anty sa'a ngd. Sund'an dad'e suna hira sanan yatashi yaymata sallama yatafi. Daga nan aikinsa yatafi, yau cikin d'unbin farinciki yakeyin komansa har zuwa dare daya koma gida. Yaukam dawuri yakoma gidan Dan ana isha'i yakoma. Afalo ya iske mutanen gidan suduka, har yaya Abubakar yazo, suka gaisa Harris da su mufidama suka gaisheshi, mamadai ta had'e masa gabas da gamma, amma wanan bai hanashi gaishetaba. Kamar yafad'a musu saikuma yayi shiru da bakinsa, and'anyi hira ya Abubakar yatashi yatafi, shima Umar mik'ewa yayi yamusu sallama yatafi d'akinsa, ganin haka Harris ma yamik'e akabar mama da 'yan matanta.......... *_(((S)))........2017_* *_luv you all_*🤝😻. [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_Gaisuwa da fatan alkairi agareku, Action baby & Maman Khaleed, alkairin ALLAH yakai muku aduk Inda kuke, ALLAH yabar zuminci, INA alfahari daku😻😍❤👌🏼._* *_page→13-14_* ........washe gari Umar yay shirinsa, kamar yanda yasaba yalek'a ya gaida mama, dukda bata wani amsa masa yanda yakamataba amma hakan bai damesaba yamik'e yashiga d'akin Abba shima ya gaisheshi, baisake bin takan kowaba yafice abinsa sai gidan Alhaji. Yau har ciki mai gadi yabarsa yashiga da Babur d'insa, yananan tsaye saiga baby tafito yaudai tayi kwalliyarta sa6anin jiya dayasameta cikin kayan barci. Cikeda rangwad'a tak'araso garesa, Umar yajanye idonsa daga kallonta, Hii my guy, tafad'a tana dafa adaidaita sahun. d'aure fuska Umar yayi, ko kallonta baiyiba barema tasamu amsa. Abin ya6ata mata rai, amma saita dake, ta ce, "sorry Assalamu alaika. Sai yanzu Umar yajuyo fuskarsa babu yabo babu fallasa ya ce, " wa'alaikissalam. Murmuahi tamasa tareda fad'in dama haka kake babu sauk'i?. No bahaka bane, yadace duk inda d'iyan musulmi yashiga farko yafara sallama kafin yasamu damar aiwatar da Abu nagaba, ina fata daga yau zaki gane kuskurenki ki gyara. Tayi far da idanunta, cikin sanyin murya ta ce, "kayi hak'uri zan gyara insha ALLAH. Wani murmushin daya kasheta yamata, talumshe idanunta domin jin wani dad'i ya ratsa zuciyarta, bata dawo daga magagin shauk'in so ba muryarsa tadaki kunnenta......... Wai miye cikakken sunankine?, nasandai baby ba suna baneba...... Da sauri taware idanunta akansa, cikeda salo ta ce, "sunan Lubna." Shima maimaita sunan yayi a la66ansa, ya ce, "lubna!, nice name. Cikeda jin dad'i ta ce, "da gsk?. Kansa ya jinjina mata yana murmushi. Wani uban tsalle tayi Wanda yasakashi tsayawa kallonta, ngd ya Umar I love you wlhy. Umar kam yadaskare atsaye, mamakinta yakeyifa, tun jiya take ambatar kalmarnan akansa, amma yagaza gane inata dosa......... Muryar alhajice takatse masa tunaninsa, Umar kayi hak'urifa baby tacikaka da magana. Murmushi Umar yayi ya ce, "babu komai Alhaji aii muna gaisawane. Duk'awa yayi yana gaida Alhajin, Alhaji ya amsa yanamai kamasa ya tadashi tsaye, Lubna tazo saitin kunnen Dad d'inta tagaya masa wani Abu danima banjiba. Dariya dad ya ce, " baby da gsk koda wasa?. Dad serious wlhy, tarufe idonta. Masha ALLAH babyna ALLAH yatabbatar mana da alkairi, kisa aranki kinsameshi kinji, kanta tagyad'a tanamai farinciki, shidai Umar dabaisan miye zancen nasuba kallonsu kawai yakeyi. Tundaga Ranar Alhaji yad'ora Umar akan dukiyarsa, Umar ya ajiye daidaita sahu, yafara hawa motar da Alhaji yabasa, lokacin dayakaima su mama wannan zance mama tamkar zata goyashi Dan farinciki, tundaga ranar yazama d'an lelenta, komai Umar, duk wani motsinta Umar, abinci saiya za6a, idan yadawo daga kasuwa tayita nannan dashi tamkar wani jariri. Shi Umar ma wani Abu dariya take bashi damamaki. A6angaren kasuwa kuwa komai yaaa tafiya masa daidai saboda kasancewarsa mai ilimi, kullum cikin dabarar kasuwanci yakeyi Dan haka dukiyar Alhaji tak'ara bink'asa, ga Umar mutumne mai gsky da rik'on amana Dan haka Alhaji yake matuk'ar son Umar Fharuk. Umar yazama d'an gida sosai, bashida wani shamaki agidan Alhaji, ko ina shiga yakeyi, ahaka kuma soyayaya mai k'arfi tak'ullu tsakaninsa da Lubna, soyayya mai tsafta suke nunama juna. Umar kam komai yacanja masa yanzu, yafara zama babban mutum, ga d'inkuna na alfarma Alhaji namasa, duk motar dayaso hawa yake agidan Alhaji, gashi kowa sonsa yakeyi agidan. Ganin yanda abubuwa suke tafiya daidai Alhaji yabama Umar jarin kansa ya ce, "shima yajuya, amma duk da haka yana kula masa datasa dukiyar. Ubangiji mai hikima cikin k'ank'anin lokaci Umar yabunk'asa yazama babban d'ankasuwa abin kwatance, ga abokai masu kud'i daji da Kansu, kowa sonshi yakeyi, agidansu kam yazama shine babba, sai abinda yace, yamaida k'annensa makarantar kud'i, yagyara gidan tsaf tamkar bashiba, hakama inna binta bai mantataba, dakansa yacanjama Asma'u wata makaranta tafara zuwa, suma su Hasiya ya canja musu makaranta, dangi kowa yanacin amfanin Umar, mamako sai d'agawa da Nuna isa itama d'anta yazama wani Abu, zannuwa take sakawa masu tsadar gsk, harta canja k'awaye, komaidai zamzam. Ana cikin haka Alhaji yabashi damar turo iyayensa domin Neman auren Lubna. Sosai Umar yay murna da wanan batu Dan yana tsananin k'yaunar Lubna sosai, babu Wanda bai Santaba a family nasa, taje gidansu sau babu adadi domin gaida mama, har inna da Anty sa'a saida aka kaita ta gaida. Manya sun shiga ansaka ranar auren Ya Umar da Lubna watanni kusa. \\\\\\\\\\\\\\\\\\\\\\ Asma'u takalli 'yan uwannanta dasuka baje kayan alawa da biskit sunata rabo, baki ta ta6e tareda kauda kanta daga Kansu tacigaba dacin abincinta. Antu Saratu ta harareta, kekuma miye kike wani ta6ema mutane bakine?. Nifa yaya Saratu bance komaiba. Fatee dake 6are cingam ta ce, "yaya Asma'u kodai kina kishine?, Dan sainaga kamar kinason ya Umar. Kutttt, Asma'u tafad'a tareda jifan fatee da murfin kwano. Kaucewa fatee tayi tana dariya, suma 'yan d'akin dariya sukeyi duka, Asma'u tayo kan Fatee tana masifa, da gudu Fatee tafito Asma'u ta biyota. Gaf tayi karo da Abu, baya taja da sauri tareda dafe goshinta tana fad'in wash ALLAHna, abisa tsautsayi ta taka 6awon ayaba, aiko tazame suuuuu zata fad'i. Da sauri yaruk'o hannunta ta fad'o jikinsa, daddad'an kamshin turarensa ta shak'a ta lumshe idonta, saikuma tabud'e da sauri danjin antureta gefe. Ya harareta kewai bakida Kaine?. Idanunta ta kwalalo waje, saikuma tahau kakka6e jikinta tana wani had'e fuska, yakatseta da fad'in ina hankalinki yatafi?. Saida tad'an murgud'a bakinta amma bai ganiba sannan ta ce, " yana jikin...... Bata k'arasa fad'aba ta hango fatee, dagudu tawucesa tabi Fateen suka afka d'akin inna. Girgiza kai Ya Umar yayi shima yanufi d'akin. Afalon yatarar dasu suna zagaye kujeru, hasiya da Anty Saratu sunata tuntsura dariya, cikin dariya Anty Saratu ta ce, "wlhy Ma'u kifad'i gsky, Dan nima nadad'e ina zargin soyayya kukeyi da ya Umar, kumafa wlhy kun dace, kardai ki cuci kanki, kifad'a sai'a had'a masa biyu kawai. Dan ALLAH Anty Saratu kibari, ALLAH zakusa nakuma TSA....... Bata k'arasaba ta hangi ya Umar tsaye abakin k'ofa, mak'alewa maganarta tayi amak'oshi. Suma duk kallonsu Yakoma kansa, yak'araso d'akin shima, guri yasamu ya zauna suka gaisa, ya ce, " innafa?. Inna tana gidanku aii tunda safe. Ayya aiban saniba, dayake badaga gidan nakeba. Ruwa Hasiya takawo masa da zo6o, zo6on yasha Dan yanaso sosai, domin shima Inna takeyin zo6o ta ajiye . Asma'u kam d'aki tashige, tana shiga hawaye suka fara bin kumatunta, tabbas son Yaya Umar na neman illata mata zuciya, tadad'e da d'umbin sonsa azuciyarta tun tana karama, haka taketa dakonsa, saboda alkunya irinta 'ya'ya mata Hausa Fulani dakuma tsoronsa Dan tuni ta lura ya Umar kam haushintama yakeji, wannan yasa take dannewa da k'ok'arin ciresa aranta, amma hakan na Neman gagara. Ashe duk k'ok'arin danne zuciyarta da takeyi akan ya Umar 'yan uwanta harsun fara fahimtarta?, ya ALLAH ka kawomin agaji akan wannan lamari, idan ya Umar mijinane ALLAH ya karkato da hankalinsa kaina, idan kuma ba mijina bane ya ALLAH kaciremin sonsa azuciyata na hak'ura da zayyan d'ina, daya dawo muyi aurenmu..... Share hawayen fuskarta tayi da sauri danjin muryar ya Umar na kwala mata kira. "Husna!." "Husna!!." Lumshe idanunta tayi sannan ta amsa, shikad'aine yake kiranta da Husna, shiyyasa takanji sunan daban kamar ba nataba. Asanyaye tafito, yana tsaye a bakin k'ofa da alama fitama zaiyi, kallo d'aya tamasa ta kauda kanta, tad'anje nesa dashi tashaya kamshin turarensa na bugun hancinta, shima idonsa akanta yamik'a mata kud'i yana fad'in da safe kije gidan matar Yousif kikaimata ta ajiye masa, saura kuma idan kinje ki kai dare. Saida ta tura baki gaba sannan ta kar6a, yamik'a mata d'ari biyar na mashin, nanma kar6a tayi, baijira cewartaba yafice. Da harara tarakashi, tajuyo cikin falon tana k'unk'uni. Anty Saratu dasu Fatee suka shek'e da dariya harda tafawa suna fad'in soyayya ruwan Zuma. Asma'u bata kulasuba tashige d'akin inna domin ajiye kud'in............ *_(((S))).......2017_* *_Luv you all😻🤝 ._* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_masha ALLAH, ALLAH yasauki k'awata Ayusher Muh'd lfy, ya azurtata da samun haihuwar baby gal, Ubangiji ALLAH yaraya mana ita akan turbar musulinci, ALLAH yasa Bad'i mudawo sunan twin's kuma_*😻😜 *_page→15-16_* ............Shirye shiryen biki ya kankama sosai, ya Umar yagama gyaran gidansa tsaf, gidane na garari Wanda za'a iya kira namai kud'i, kowa yagani dolene ya yaba Dan gidan yaginu babu k'arya. Agidansu amaryama shirin biki akeyi na 'Yar gata Dan wannan shine karo na farko dazasu aurar, komai na 'yan gata aka shirya, damma mahaifiyarta batason auren, Dan taso ace lubna ta auri d'an shahararren mai kud'i irinsu amma ba Umar ba, to amma babu yanda zatayi tunda takafe shitake so. Mama kam wannan aure yamata dad'i d'anta zai auri d'iyar masu kud'i, sai d'agawa da fariyya takema 'yan anguwa. Asma'u tunda aka fara shagalin bikinnan tashiga matsanan ciyar damuwa, amma haka tadage da addu'oi harda azumi tana addu'ar ALLAH ya danne zuciyarta tazama mai hak'uri, inna tana kula da duk halin da Asma'u tashiga amma babu yanda zatayi saidai ta taya d'iyar tata da addu'a tunda haka ALLAH yatsara lamarinsa. *_biki buduri_* Ansha biki na nunawa a duniya Dan taron d'aurin aurene daya halarci manya-manyan masu fad'a aji ak'asarnan, sarakuna, 'yan siyasa, 'yan kasuwa, harda shugaban k'asa, lamarin bak'aramin girgiza Ya Umar yayiba, Dan baita6a zaton ko kansilan anguwarsu zaizo d'aurin aurensaba bare shugaban k'asa gaba d'aya. Biki kam saidai Sam barka Dan nera tayi kuka sosai. Bayan biki amarya da ango ansha amarci babu k'arya, sosai suke zuba soyayya kamar babu gobe, saida ya Umar yay sati biyu baya fita kasuwa, koda yaushe yana gida manne da lubna, abinci saidai suje su sayo. Tsawon wata d'aya ana kashe kan amarci, amarya babu abinda takeyi dagaci sai barci, komai saidai 'yan aiki, wani lokacinma ya Umar keyimata wankan, abinda yafara 6ata masa rai da ita shine son jiki, komai saidai ayi mata tana a kwance, daidai da ruwan dazaisha saidai tasaka 'yan aiki sukai masa, gyaran d'akinsama haka, wani abin k'arin haushinma shine duk sanda zaidawo gidan saidai ya Tatar da ita shame-shame kwance 'yan aiki namata tausa, wannan lamari na 6ata masa rai matuk'a. Daya kasa daurewa yafad'ama mama saitace yacika k'orafi shikam, ya yarinya tatashi cikin Hutu yanzu zai k'ok'arin tsinke mata, itafa bata yarda ko fad'a yaringa yima Lubna ba, abin ya6ata masa rai, yarasa wane irin haline da mahaifiyarsu?, haka yabar gidan ransa a6ace. ////////////////+//////////// A6angaren Asma'u kuwa abubuwa sun mata sauk'i, tanata k'ok'arin cire ya Umar azuciyarta, tamaida hankalinta sosai akan karatu babu wasa, burinta bai wuce Zayyan d'inta yadawo suyi aureba. Ana haka Lubna ta fara laulayin ciki, zazza6i da yawan amai sun addabeta Dan haka ya Umar yakaita asibiti, gwaji farko akace cikine. Cikin tashin hankali lubna ta ce, "doctor jafar cikifa kace?". Dariya Doctor jafar yayi, ya ce, " hakane lubna kina d'aukeda babynmu. Afusace takalli ya Umar da farinciki yacika zuciyarsa shima zai zama baba, ta ce, "Umar kanajindai abinda doctor yafad'a aii?. Murmushi ya Umar yayi yarungumota zuwa jikinsa yana fad'in naji sweet d'ina, kuma inacikin farinciki...... Bai k'arasaba ta fisge jikinta daga nasa, ta6d'i jan Umar wlhy bazata sa6uba, yaza'ayo kamarni 24year's ace inad'aukeda ciki, lallai akwai lale awannan batun. Cikin mamaki ya Umar ya ce, " Lubna akwai lale kamar yaya?, wannan ba abin farinciki bane?. Abin farincikine agareka Umar, ammani abin kunyane da bak'inciki agareni, ace kamarni beby wata hud'u da aurena aganni da ciki, haba saikace dai wata akuya, asaima k'awayena sumin dariya wlhy. Daga ya Umar har doctor jafar kallonta sukeyi cikeda mamaki, ya Umar ya kwantar da murya cikin Nuna damuwa ya ce, "haba Lubna miye abin kunya ga samun k'yautar ALLAH?, kitunafa akwai dubunmu dasuke nema amma ALLAHA bai basuba muyabamu, bakuma dan munfisu agurinsa bane, a'a ikonsane yasa yabamu sukuma baibasuba, amm....... Hannu tad'aga MASA cikin masifa ta ce, " kaga Umar Dan ALLAH sauraramin da wannan wa'azin naka mana, nifa nace banason ciki yanzu, danhaka saikasan yanda zakayi dani, ban shirya rainon cikiba ayanzu kuma babu mai tursasani nayi. Ran ya Umar yafara 6aci, Dan haka afusace shima ya ce, "to wlhy Lubna babu mai zubarmin da ciki, dukma abinda zakiyi saidai kiyi, yamik'ama doctor jafar hannu sukayi musabaha, abokina ngd, yadaka mata tsawa dallah malama tashi muwuce. Mik'ewa Lubna tayi Dan tsawar Umar d'in ta razanata sosai Tundaga wannan ranar zamansu yafara rawa, kullum cikin fad'a da tashin hankali, abin kamar wasa har yakaisu ga zuwa wajen iyaye, mahaifiyar Lubna ta goyi bayan lubna ta zubda ciki, amma mahaifinta ya hana, sosai lamarin ya6ata ran Lubna, tundaga wannan lokacin komai ya canja musu, shidai yana nuna mata kulawa sosai da tattali, duk abinda ta ce, "tanaso zai saya matashi, ga cikin NATA da saka shagwa6a, tattalin dayake nuna mata yasakata sakin jiki itama ta manta da komai suka koma zuba soyayyarsu, mama bata had'a sati d'aya batazo gidanba ganin Lubna. Ahaka cikin lubna yashiga watan haihuwa, kuma Yakama lokacin hutunsu Asma'u suna gida. Ya Umar yaje ga inna tabashi Asma'u danta taya Lubna zama tunda tace bataso akawo mata kowa, dayace to yad'akko Asma'u?, saitace ta amince zata zauna da Asma'u Dan mutuniyarta ce. %-%-%-%-%-% Tunda Asma'u tazo saita raina tsaftar matar gidan Dan bawani zuwa sukeyi sosaiba, batayi k'asa agwiwa ba tace duk 'yan aikin su huta tazage sosai tagyara gidan har d'akin ya Umar ko INA yad'au k'amshi, takuma shiga kichin tamusu abinci mairai da lafiya. Lubna dakebin Asma'u da kallo ta ce, "lallai sunnunki da k'ok'ari, wai bak'yajin ciwon jikine?. Dariya Asma'u tayi tareda fad'in wlhy aunty Lubna banajin komai, aiini ban d'auki aikin gidannan aikiba, idan dawani bayan wannan tom zanyi kuma natashi garau. Baki luban ta ta6e tace lallai wahala da rai. Asma'u batace komaiba saidai dariya. Da ya Umar yadawo tun a harabar gidan yaga canji, yashigo falon shima cikeda mamaki yakebin ko ina da kallo, Asma'u dake zaune tana kallo tamik'e tana fad'in sannu da zuwa ya Fharuk. Kallonta yayi ya ce, " yauwa Husna sannunki, Lubna kam ko kallo bai ishetaba tana zaune turus ak'asa, ya Umar yak'arasa gareta yana murmushi, rungumota yayi had'eda manna mata kiss akumatunta, Uwar biyu ykk?. Fuska ta yatsine masa tana wani kumbura Baki, kacefa yanake tunda kahad'ani da aiki, murmushi yayi acikin kunnenta ya ce, "aitare mukayi bani kad'aiba ko?, bare amin d'agwaiy, dukan wasa tamasa ak'irji, yatashi yana dariya, daidainan Asma'u tafito daga kichin d'aukeda k'aramin tire tad'ora ruwa da lemo da cup, ganin yamik'e ta ce, ''ya Fharuk ga ruwa. Kallonta yayi acikin wani yanayi, tunda yay aure ba'a ta6a akawo masa ruwaba ayayin daya dawo gida, wani lokacinma saizaici abinci za'a bashi kokuma ya rok'a, kansa ya jinjina mata yakoma ya zauna, Asma'u ta tsiyaya ruwa ta mik'a masa, kar6a yayi tareda bismillah yasha, Lubna ta ce, " Asma'u kedai bakya gajiya, yanzunan k'ato dashi saikin kawo masa ruwansha?. Kallonta kawai Asma'u tayi amma bata iya furta komaiba, shimadai ya Umar zuciyarsa ta sosu da maganar ta Lubna amma saiya share yamik'e bayan yagama sha, d'akinsa yashiga danya rage gajiya, Kallon ko ina yakeyi cikeda sha'awa, yasan wannan aikin Asma'u ne Dan matarsadai bata iya komaiba sai addabama 'yan aiki, dawad'annan tunane-tunanen yay wanka yashirya sannan yadawo falon, inda yabar Luban nan yasameta da wahalallun 'yan aikinta suna faman mata tausa, harya zauna Asma'u ta ce, "ya Fharuk ga abincifa. Kallonta yayi saikuma ya kauda idonsa, ya ce, " yaushe kika iya abinci?, idanu Asma'u ta kwalalo danjin rainin hankalin mutuminnan, saikace yau yafara cin abincinta, tad'an murgud'a baki sannan ta ce, "aibani nayiba Anty Lubna CE. Da sauri ya kalleta, saita kauda idonta, ya jinjina kansa Dan yagane bak'ar magana tamasa, itako Lubna saita washe baki tana fad'in a'a kedai kikayi abinki, ni inani ina aikin wahalarnan, my Honey kaje kaci wlhy akwai dad'i sosai dantafi kuku iyawa, nidama zata dawo nan gidan danaso haka.. Kallonta kawai yakeyi cikeda al'ajabi amma yagaza furta mata komai, saida ya mula Dan kansa harma Asma'u tayi fushi sannan yasakko k'asa Dan bayacin abinci a dinning, Asma'u tajere masa komai tazuba masa, aii mutuminku dayayi cokali d'aya saida ya lumshe idanu, sosai yakejin dad'in abincin, wannan yana d'aya daga cikin abinda yasa ya d'akko Asma'u ta zauna dasu. Tundaga ranar komai Asma'u takeyi agidan, tazama tamkar itace matar gidan, kwananta takwas dazuwa Lubna ta haihu 'yan biyu duk mata, wayyo zokaga murna wajen ya Umar da sauran dangi harma da family d'in Lubna, ranar suna yara sunci sunan mama da momyn Lubna, wato Maryam da Haleematu, za'a ring a kiransu Amrah da Afrah. Bayan suna dakamar sati biyu su Asma'u suka koma makaranta, Dan haka ta tattara ta koma gidan d'aukeda shatara ta arzik'i daga Lubna da Ya Umar............... *_(((S))).....2017_* *_Luv you all_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* _masu karatu karfa Ku rikice, har yanzu muna cikin tunanin Asma'u ne_. *_page→17-18_* .........Shekaru sun shud'a sosai Dan su Asma'u harsun kammala s,s,c,e d'insu, amma haryau Zayyan bai dawoba, abin yana damunta, hakama iyayenta, gashi bata kula kowa Dama saishi, iyayenta sunso Sumata aure tunda ta kammala secondary amma hakan ya gagara, suna zaman jiran dawowar Zayyan, a haka Asma'u takusan cinye shekara agida. Ranar ya Umar saiyazoma Inna da shawarar mizai hana Asma'u takoma makaranta da wannan zaman?, idan saurayin nata yadawo koda tana karatunne sai ayi auren tacigaba agidan mijinta. Da farko inna da baba sunk'i, amma ya Umar yadage da nuna musu fa'idar karatun sai suka amince. Babu 6ata lokaci yafara nema mata makaranta, dandanan kuwa aka samu Dan yanzu su Yaya Umar sunzama manya, komai shine yayi mata, tafara zuwa makaranta nan FCE kano. ___________________ Agidan ya Umar kam abubuwa na tafiya daidai, yaranshi sunyi girma ko ina zuwa sukeyi, ga surutun tsiya abakinsu, soyayakam shida matarsa sai abinda yay gaba, hakama danginsa kowa sonsa yakeyi tamkar ya goyasa musamman mama da kawu kabiru, ga abokaimadai hakane, abokai gareshi tamkar tsiya, shikansa yana mamakin wasuma a ina ya sansu?, 6angaren kasuwarsa saidai godiyar ALLAH, kullum k'ara cigaba yakeyi, yabud'e babban super market akasuwa, komai kashiga zaka samu awajen, tundaga suturu akwai 6angarensu, kayan kwalliya, kayan mak'ulashe, kayan abinci, kayan d'inki, kayan wuta, kai harsu wayoyi dukzaka samu, ya bunk'asa sosai, gashi yabuga musu wani k'aton gida na garari mai 6angare buyu, tuni Lubna tarud'e da tambayar d'ayan 6angaren nawaye?. Ya ce, "mata na yarane, idan sunyi girma can zasu koma, hankalinta yad'an kwanta amma ba sosaiba Dan bata yarda dashiba ko kad'an. Rayuwadai ta shud'a sosai, hargasu Asma'u sun kammala karatu na tsawon shekara uku, tafito da result mai k'yau, masha ALLAHU Asma'u tazama cikakkiyar budurwa mai kimanin shekaru 22 Aduniya, har yanzu bata kula kowa wai tana jiran Zayyan, amma k'ark'ashin ranta tana mak'ale da son ya Umar har yanzu dan dai babu yanda zatayine, ayanzuma ganin take yamata nisa fintin kau danya zama babban mai kud'i matashin maiji da kansa, tako ina ya Umar yagama had'ewa gashi da d'abi'u irin na manya wad'anda suke matuk'ar k'ara masa kwarjini a idon jama'a. Ayanzukam bak'aramin bud'ema Asma'u wuta su inna sukayiba akan ta fidda miji, hankalinta yakai k'ololuwar tashi, idan tana kuka saidai su Fatee suyita lallashinta da bata baki. Ana cikin haka saiga Zayyan tamkar an jehoshi, Asma'u tayi farinciki mai yawa, amma daga baya tayi kuka harya kaita ga kwanciya asibiti saka makon maganar da Zayyan yazo mata dashi mai ratsa zuciya. Lokacin da Zayyan yazo Asma'u tafito bayan ya aika kiranta, batayi zaton shibane Dan haka tafito cikin fushi, yayinda tayi tozali da Zayyan yaci wani uban wanka yana jingine da motarsa saita rikice Dan farinciki, cikeda zumud'i tak'araso garesa tana fad'in zayyan da gsk Kaine?, kokuwa mafarkin Dana saba yine?. Zayyan yad'ago yana kallonta babu yabo babu fallasa, tun anan jikin Asma'u yayi sanyi Dan ganin halin ko in kula da Zayyan ya nuna agareta, jiki a sanyaye tace sannu da zuwa, bai amsaba amma yamik'a mata IV. Cikeda mamaki ta amsa tanamai Kallonsa, tayi k'arfin halin fad'in zayyan wannanfa?. Yatsine fuska yayi ya ce, "IV d'in aurenane nanda kwana 30 kacal, kiyi hak'uri tunda natafi ban sake nemankiba, wlhy nayi gamon katarne da tsaleliyar budurwa a can yayin karatuna, gata 'Yar masu kud'i, ke idai tak'aice miki ta kereki a komai na rayuwa, tun shekara uku dasuka wuce nadawo k'asarnan ALLAH bai bani ikon zuwaba saiyau, naga kuma bai daceba ace ansha bikina baki saniba shiyasa nakawo miki katin gayyata, nabarki lfy... Yana gama fad'a yashige motarsa yabar anguwar tareda bud'a mata k'asa. Ai Asma'u saikawai tayanke jiki tafad'i, ya Umar ne dayazo gaida inna yaganta kwance ak'ofar gida, da farko masifa yafara mata amma dayaga bata koda motsi sai tsoro yakamasa, yagirgizata amma shiru kakeji, anahaka saiga baba dasu hasiya, arikice suma suke tambayar lfy kuwa?. Nima wlhy baba ban saniba, a haka na Tatar da ita, dasukaga magana bazata musuba suka kwasheta sai asibitinsu Dr jafar. Natak'aita muku zance saida Asma'u tayi kwanta biyu assume sannan ta farfad'o, tashin hankali kuwa ba'a maganarsa wajen family d'inta. Bayan kamar sati d'aya Asma'u tadawo daidai aka tambayeta sanadi?, tafad'i yanda sukayi da Zayyan. Ransu inna ya6aci matuk'a harya kai ga inna tasamu ciwon hawan jini itama, ga Asma'u jikinta yak'i dad'i yauda lfy gobe babu. Wannan 6acin ran yasa ya Umar cewa ad'aura masa aure da Asma'u kafin ranar d'aurin Auren Zayyan. Kowa yayi na'am da wannan batu a family, Dan haka bayan kwanta uku da faruwar haka aka d'aura auren Asma'u da ya Umar batareda tasaniba, saidaga bayan shima ba'a fad'a mata mijinba. ____________________ Hummm randa wannan lamari yafaru ya Umar yaga tsantsar tashin hankali agidansa, Dan Lubna tamkar zata kunna musu wuta su k'one, zage-zage da tsine-tsine dangin ya Umar sunshashi, tundaga ranar zaman lfy ya k'aura agidan, bayan kwana Uku Asma'u ta tatare agidan Dan ba'ayi wani shagalin bikiba, amma dukda haka saida abokansa suka shirya musu denner, bayan kawo Asma'u aka halarci wannan denner wadda ta tata hankalin Asma'u dataga waye aka aura mata amatsayin miji na har abada, shin murna zatayi kokuwa bak'inciki?, batada za6in ko d'aya sai aikin kuka a 6oye har aka tashi denner, daganan kowa yakama gabansa, ya Umar Yad'auki Asma'u suka tafi gida, har 6angarenta yarakata, suna shiga yajuyo batareda yace da ita uffanba. 6angaren Lubna yadawo Inda yatarar da shika-shikan bala'i Dan ranar kwana sukayi babu barci harya shashshek'a mata mari biyu, taci kuka sosai tamkar ranta zai fita. A6angaren Asma'u ma bawai barcin tasamuba, kwana tayi kuka ita kad'ai. ____________________ Tsawon kwana uku Sam babu zaman lafiya agidan Yaya Umar, Lubna ta tada hankalin kowa agidan, adaren kwana na hud'u kuma wani tashin hankalin yazoga ya Umar customs suka rik'e masa kaya babu gaira babu dalili, ya Umar yarasa inda zai saka kansa, yabi duk wata hanyar daya dace kayansa su k'u6ta abin ya gagara, haka ya hak'ura, ba'a k'ulla wataba ranar aka wayi gari kuma wai shagonsa yayi gobara komai ya k'one ba a mori komaiba, wannan tashin hankalin ne yahad'u yayma ya Umar yawa, komai yazo yak'are, har aka koro masa yara daga makaranta, yazo ya saida gidansa, ga kowa ya gujesa ciki harda matarsa Lubna, ammasa k'arfa-k'arfa akan 'ya'yansa, hargashi da tsintar kansa agadon asibiti batareda ya shiryama kansa hakanba. _______ _______ _____ *_Mun dawo labari_* Firgigit Asma'u tadawo daga tafiya dogon tunaninta na tsawon shekaru dasuka shud'e abaya, takai dubanta ga agogon dake d'akin karfe 2:47am, idanunta tazaro tana mai mamakin doguwar tafiya datayi atunani batareda tasan dare yayi nisa hakaba, ahankali tasauke idonta akan ya Umar dake barci, fuskarsa tayi fayau, ya k'ara haske dukda kasancewarsa bak'i sosai, yarame sosai sai dogon hanci, tashare hawayen dasuka cika mata fuska sannan tamik'e, bayin dake d'akin tashiga kasancewar ya Umar kad'ai aka kwantar aciki Dan baya buk'atar hayaniya, alwala tayo tazo ta shimfid'a sallaya tayi nafilfilinta tareda karatun alkur'ani mai girma, tayi addu'oin samun lafiya ga mijinta sosai sanan tashafa ta kwanta awajen saman sallayar barci yay awon gaba da ita........... *_(((S)))......2017_* *_Luv you all my sweet Fan's_* [11/29, 11:04 AM] ‪+234 809 466 2407‬: 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→19-20_* _Washe gari_ Amakare Asma'u ta tashi kasancewar bata kwanta da wuriba,, ta tashi da addu'a abakinta, ganin yanda haske ya gauraye d'akin yasata zaro idanu waje, ta kalli agogo k'arfe 7:06am, zummbur tatshi Dan gabatar da sallah, agaggauce tayi sallar, tana idarwa saiga doctor Al-Ameen ya shigo, suka gaisa ya tambayeta mai jiki?. Da sauk'i doctor, Asma'u tafad'a tana d'an murmushi. Shima murmushin yayi ya ce, "Alhmdllh, yad'an duddubashi sannan Yakuma kallon Asma'u, Hajiya insha ALLAHU nanda awa d'aya zuwa biyu zai iya farkawa. Alhmdllh doctor, mungode sosai. Karki damu hajiya, mugodema ALLAH kawai, fita yayi. Ita kuma ta tsurama ya Umar daketa barcinsa idanu cikeda shauk'in so. _ya Umar bak'ine kuma k'yak'yk'yawa masha ALLAH, bazamu kirasa dogoba haka kuma ba gajere bane yana dai tsaka tsaki, yanada cikar hallita mai k'yawun haiba dan bai kasance siririba, yanada d'an jikinsa dai-dai misali, mutumne mai yawan hak'uri da kawaici, bakomaine abin magana awajensaba, bashida yawan hayaniya amma akwai yawan fara'a ga wanda yasani, bayason raini arayuwarsa, yanadason 'yan uwansa da mahaifiyarsa, so ya Umar dai yakai akirasa cikakke kuma nutsatstsen namiji abinson kowace mace._ Asma'u tasaki wani k'asaitaccen murmushi Wanda batasan tanayiba, gsky tana bala'in son ya Umar, harma tana ganin tafi kowa sonsa aduniya..... Da sauri tad'ago danjin an dafa kafad'arta, Rafi'a tagani, sukaima juna dariya, Rafi'a ta ce, " haba Anty Asma'u irin wannan tafiya haka?, ya Umarfa nakine. Murmushi Asma'u tayi, ta ce, "wai yaushe kikazone?. Nakai Minti biyar akanki wlhy, amma ko kad'an bakisan da shigowataba, kina cikin shauk'in so. Kai wai Rafi'a yaushe kika koyi rashin kunya ne?. Hhhhh daga fad'ar gsky auntynmu, wai ni inama Anty Lubna ne, kobatasan bashida lfya bane?. Wlhy Rafi'a ban saniba nima, rabonta da gidan tun washegarin randa kukaje datazo itada iyayenta. Tofa ALLAH ya k'yauta, kardai ace itama butulcin zata masa?. Asma'u ta ce, "Hmmm Rafi'a kenan, aii mutanen duniya sun wuce yanda kike tsammaninsu wlhy, yanzu jiya kinsan kuwa mina Tatar a asibitinnan bayan dawowata daga saida waya?, bakiga mun canja likitaba?. Nagani, kuma tunjiya naso tambaya amma tashin hankalin halinda ya Umar yake ciki ya hanani tambaya, miya farune?. Asma'u tashare hawayen fuskarta sannan ta ce, " lokacin Dana dawo a waje na tadda su ya Umar, makwafcinmu ya tallafesa yana kwance ak'asa, da hanzari nak'arasa garesu Dan azatonama ya Umar ya rasune, cikin kid'ima na tambayi koya mutu?." Makwafcinmu ya CE, "a'a da ransa, wai Doctor jafarne yafito dasu waje saboda mun dad'e bamu dawoba. Kaina kawai na jinjina Dan bak'incikinsa bashine agabanaba, lfyar ya Fharuk nake dubawa, na ce, " babu damuwa mu maidashi nasamo kud'in. Dak'yar ya Fharuk yad'agamana hannu alamar a'a karmu maidashi, na marairaice murya INA fad'i haba ya Umar daka dai daure mun maidaka tunda lfyarka Muke nema..... Makwafcinmu ne yakatseni da fad'in gaskiya Hajiya koni ban goyi bayan hakaba, Dan bakiga wulak'anci da cin zarafin da likitancan yamanaba, mutane sukaita kallonmu, dazaki amince akwai wani d'an uwana shima likitane anan dasai na kirashi. Da Saudi nace kirashi kawai. Bayan yakirashi babu dad'ewa saiga Doctor Al-ameen, cikin mamaki ya ce, "wannan ba Alhaji Umar bane?. Mukace shine, agaggauce makwafcinmu yabashi labari, ran doctor Al-ameen ya 6aci matuk'a, babu 6ata lokaci yasa aka kawo gadon d'aukar Mara lafiya aka d'auki ya Umar, namatsa kusadashi INA MASA godiya, na ce, " ammafa bamu biya kud'in komaiba. Harya fara tafiya yajuyo gareni ya ce, "haba Hajiya aiba kud'i yakamata mufara damuwa dasuba lfyarsa, kije ki ajiye mufara fuskantar matsalarsa, wlhy Rafi'a har kukan dad'i nayi danjin furicin likatannan. Rafi'a ta share hawayen fuskarta itama ta ce, " ALLAH sarki ya Umar kana ganin rayuwa, bakomai ALLAH yana tareda masu hak'uri aii, ALLAH yabaka ikon jurewa. Asma'u ta ce, "Ameen dai Rafi'a. Rafi'a ta ce, "ga abinci nan inji mama. Wayyo mama munsata aiki. Baki Rafi'a ta ta6e ta ce, " kebar Maman nan itama haushi take bani, inaji inama ace ba ita ta haifemub...... Da sauri Asma'u ta rufe bakin Rafi'a, a'a karki fad'i haka Rafi'a, duk lalacewar mahaifi mahaifine, mubita da k'yak'yk'yawar addu'a kawai kinji. Rafi'a batace komaiba saima hawaye dasuka cika mata idanu. _Bayan 3h..._ Zuwa sannan asibitin yacika da dangi,harsu inna sunzo, amma duk doctor ya tsaidasu awaje Dan yana saran farkawar Ya Umar. Cikin ikon ALLAH kuwa agogo na nuna k'arfe 10:00am sai ya Umar yafarka, dagashi sai Harri's a d'akin Dan Asma'u taje gida tayi wanka, cikin gaggawa Harris yafita zuwaga likita, yana sanar masa suka iso tare, bak'aramin farinciki Dr Al-ameen yayiba Dan ganin Ya Umar ya farka cikin hankalinsa, Dr al-ameen yad'an k'ara duddubashi sannan yafito yasanarma su mama. Gaba d'ayansu suka shiga d'akin ya Umar na zaune jingine jikin gado, mama tazauna akusadashi tareda kamo hannunsa ta ce, "Umarina sannu kaji?. Murmushi yamata, Dan bayason yin magana, suma su Rafi'a, Anty sa'a, Anty Saratu, inna, mufida, hasiya, Fatee dadai sauran 'yan uwa suka shiga yimasa sannu, kansa kawai yake iya d'aga musu, aransa ya ce, "ko ina wannan yarinyar?.'" Bayan kamar minti talatin doctor yashigo ya ce, "suyi hak'uri sukuma bashi waje ya huta, duk fita suka kumayi akabar Harris kad'ai, doctor ya ce, " kataimaka masa yaje bayi danyayi wanka sannan yaci abinci yasha magani. To doctor mungode sosai. Doctor nafita Harris yataimakama Ya Umar yarakashi har cikin bayi, saida yaji yafara wankan sannan yafito waje indasu inna suke. Babu dad'ewa Asma'u tadawo, abinda tafara tambaya shine ya Fharuk yatashi?. Mufida tayi dariya, ta ce, "Asma'u amaryar ya Umar, yatashi yana nan zaune kekad'ai yakeson gani. Fuska Asma'u tarufe tana dariya, ALLAH yasoma mama da inna sunacan zaune agefe su kad'ai, Anty sa'a ta ce, " jeki kigansa kinji ma'u, k'yale Mufida. Ba musu Asma'u tashiga d'akin, babu kowa Dan haka ta kakka6e gadon tagyara sannan tazauna jiransa. Tana nan zaune aka bud'e k'ofar bathroom d'in, d'ago idanunta tayi sai suka had'a ido da ya Umar, tai saurin kauda kanta Dan ganinsa dagashi sai tawul, cikin tafiyar mara lfy dabayajin k'arfi yak'araso kan gadon, saida ya zauna sannan ya kalleta, kanta ak'asa ta ce, "ya jikin?. Kallonta yakumayi tareda fad'in da sauk'i, yayd'an tsaki wai ina Harris d'in?. Asma'u ta ce, " yaje gida yadawo." Shiru yayi, zuwacan kuma ya CE, "sakama k'ofarnan key zan shirya kar wani yashigo, jikin Asma'u a sanyaye tamik'e amma saita fara k'ok'arin fita, ya ce, " ina zakije kuma?. Uhmm dama zanjiraka awaje, idan ka kammala saina dawo, yad'an d'aure fuska sannan ya ce, "dawo. Babu musu Asma'u tadawo tazauna inda take ada. Man shafawa yamik'a mata, kar6a tayi tana mai satar kallonsa, duk yayi wani cid'in-cid'in da fuska, ya ce, " d'an shafamin mannan hannuna duksunyi sanyi saboda k'arin ruwa.. Yanda yake magana a cikunshe babu alamar wasa yasa Asma'u mik'ewa da mai ahannnunta, ta lakata amma saitata murzashi Dan takasa ta6a jikinsa, ganin yanda taketa mulmula man takasa ta6ashi saiya mik'a mata hannunsa, cikeda kunya tafara shafa masa, jitake tamkar k'asa tatsage tashiga ciki Dan kunya, shikam gogan naku ko a jikinsa shi dad'inma shafa man yakeji, jiyake tamkar tana masa tafiyar tsutsa, idonsa a lumshe harta gama. Tashi yayi yana shiryawa, Asma'u kam tazauna kanta ak'asa. Saida yagama shiryawa sannan tajawo kulolin abinci tazuba masa, yana zaume yana kallonta harta gama, tad'ora masa filet d'in abincin a bak'in gado, shiru yayi bai d'aukaba baikuma yi maganaba, ganin haka yasa ta ce, "ga abinci. Fuska ya yatsine dawane hannun zanci?, nacemiki hannuna yanamin ciwo. Cikeda mamaki take kallonsa, wannan wane irin sabon salone daga ya Umar kuma?, yana nufin itace zata bashi abincinma?....... Yakatsemata tunani da fad'in jeki kiramin mama ko inna subani tunda ke bazaki iyab..... Bata bari yak'arasaba ta d'auki abincin tamatso tana bashi, yanda take basa abincin takasa kallonsa saita bashi dariya, amma baiyiba yadaure ya gimtse, tana cikin bashi abincin aka kwankwasa k'ofa, tashi tayi taje ta bud'e, su mamane da matan anguwarsu sunzo dubashi. Babu kunya yamik'ama Asma'u filet d'in abinci wai tacigaba da bashi, wayyo ALLAH Asma'u tamkar zata fasa ihu, babu yanda zatayi tacigaba da bashi harya k'oshi, tazuba ruwa a cup tamik'a masa, yanzudai kar6a yayi yasha da Kansa........... *_Luv you all_* *_(((S)))......2017_* .👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *Amma saga yau na sakad'a Xoxo da hajja ce & zeety, 🤔kona had'a da Rano?, umm baradai nabarta kawai.*🤥 _muhud'u writer's Asso..... Kenan._😜😂 *_page→20-22_* ..........Alhmdllh jikin ya Umar yana yin k'yau, yaji sauk'i sosai, saidai abinda ba'a rasaba. Dangi kam balaifi suna d'an zuwa ganinsa, musamman wad'anda zuciyarsu bata manta da d'umbin alkairinsaba sanda yakeda kud'i. 'Yan uwansa dai suna mamakin rashin zuwan Lubna asibitin, kuma duk Wanda ya tambayesa saiyayi kicin-kicin da fuska alamar baya buk'atar maganar, ganin haka kowa ya daina tambayarsa Lubna. Yauma duk suna asibitin har kawu kabiru da babansu Asma'u, 'Yar hira akeyi da raha irinta family idan an had'u, ya Umar kam shiru baya cewa da kowa k'ala, Harris ya kalli ya Abubakar ya nuna masa ya Umar da baki (zind'e kenan, kuma babu k'yau😏.) Baki ya Abubakar yata6e shima suka had'a ido da matarsa Haleesat. Asma'u duk tana kula da abinda sukeyi, hakama Anty Sa'a, hawaye yacika idon Asma'u tamik'e ahankali tafice. Ya Umar dake kallon duk wani motsin kowa, har abindasu ya Abubakar sukeyi masa, yabi Asma'u data fita tana kuka da kallo, ahankali yalumshe idanunsa yanamai jin tausayinta, shima sakkowa yayi daga gadon yanufi hanyar fita....... Inna ta ce, "Umar ina zuwa kuma?. d'an shafa kansa yayi, idonsa ak'asa ya ce, " inna zand'an tattaka ne, na gaji da kwanciyarne". To aii dakayi magana sai ko Harris ya taimaka maka, kaida bakajin k'warin jikinka". A'a inna yayi zamansa zan iyama, nafison nayi dakaina. To shikenan, jeka, idan kagajidai kadawo kaji. Kansa ya jinjina mata tana murmushi, sannan yafice. Asma'u na zaune akujerun dake jere a tsakkiyar reception d'in asibitin, kanta a duk'e yake shiyyasa ya Umar baiga halin datake a cikiba, takawa yayi zuwa gareta. Da sauri tad'ago danjin mutum ya zauna a Kusada ita. Had'a ido sukayi da ya Umar, sai kawai tad'auke kanta, tamaida k'asa tana k'ara share hawayen dasuka silalo mata yanzun, girgiza kansa yayi tareda kamo hannunta ya rumtse anasa, yaarrrrr tsigar jikinta ta tatashi, yauce rana ta farko da ya Umar yata6a rik'e hannunta amatsayinta na matarsa, ta rumtse idanunta harda cije le6e....... Bata gama dawowa dai-daiba taji muryarsa na kuwwar fad'in Husna!. K'ara rintse idanunta tayi sosai takuma kasa amsashi. Shima baya buk'atar amsar tata Dan haka yacigaba da fad'in, Husna shin bazaki zama jaruma baneba?, kina ganin rayuwa zata cigaba da tafiya komai da kuka?, Husna bamusan randa rayuwa zata canja bafa, kenan hawayenki basuda ranar k'afewa?, kinga d'ago ki kalleni. Shiru Asma'u takasa d'agowa, amma tana sauraren dukkan maganganunsa. Ya kuma fad'in husna kalleni mana. d'agowa tayi cikeda kasala, suna had'a ido tayi azamar janye nata, yad'aga baki zaiyi magana Anty Sa'a tak'araso wajen..... A'a d'an k'anina mikuma kukeyi anan wajen?. Baice komaiba saidai nuna mata Asma'u da kanta ke k'asa yayi. Anty Sa'a tad'anyi murmushin takaice tareda zama Kusada Asma'un suka sakata tsakkiya itada ya Umar. Itama dafa kafad'arta tayi, cikin sigar lallashi ta ce, "Asma'u kik'ara zama mai hak'uri da jarumta dukda nasan kinadasu, kicigaba da yima mijinki kuma yayanki addu'oin fatan alkairi, kizama mai k'arfafa MASA gwiwa kinji?. Karki sake damuwa da abinda wasu suke masa barema harya sakaki kuka, ALLAH daya basa shiyya kar6i abinsa badan baya son Umar ba, sanda ya azurtasa baiyi shawara da kowaba, hakama yayin amshewa, suma basufi karfin ya kar6e daga garesuba. _antambayi Mazon ALLAH (s,a,w) waye talaka?._ _sai ya ce, "Wanda zaitashi ranar k'iyama babu komai na aikin alkairi a gidauniyar ayyukansa._ To Ashe talaucin duniya bashine talauciba, dukiyar duniya ba itace arzik'iba, Dan *_KARAYAR ARZEEK'I_* ta riski Umar ba hakan na nufin ALLAH baya sonsa baneba, ya jarbceshine Dan kawai yaga nauyin imaninsa, wannan itace *Kaddararsa* Dan haka bashida ikon tsallakewa, inhar d'an Adam bazai iya gujema kaddarar ranar mutuwarsaba, to tabbas bai Isa gujema duk wata k'addara a yayin rayuwarsaba, kibar kuka kinji. Jin jina kai Asma'u tayi, cikin raunin murya ta ce, " Anty sa'a ngd da tunatarwarki agareni, ALLAH yak'ara bamu jarumtar cinye jarabawarsa, Ameen ya rabbi Asma'u, ALLAH ya albarkaci rayuwar aurenku. Murmushi Asma'u tayi, azuciyarta ta ce, "Ameen Anty Sa'a". Ta juya tad'an kalli ya Umar, muryarta kasa-kasa ta ce, " ya Fharuk kayi hak'uri da d'aga hankalinka danayi harka taso kafito, insha ALLAH wannan shine na farko kuma na k'arshe. Mik'ewa yayi yana fad'in ni bakimin laifin komaiba dama. Daga Asma'u har Anty Sa'a da kallo suka bishi harya shige d'akin dayake jinya. Asma'u tajuyo tana kallon Anty Sa'a, kanta a langwa6e ta ce, "ya Umar yanada wuyar sha'ani anty". Murmushi Anty Sa'a tayi tareda fad'in duk taurinsa kece zakisakashi yayi sanyi k'anwata, nakumasan zaki iya saboda jarumtarki... Itama tana kaiwa k'arshe ta tatashi tabar wajen. Da kallo Asma'u tabita harta shige, ta sauke ajiyar zuciya tana wani murmushi da juya maganar Anty sa'a a zuciyarta, indai hakane to tabbas zata zama zaruma wajen maida ya Omar sanyi kamar yanda Anty Sa'a tafad'a, tabbas tanason ya Umar sosai kuma zata zauna dashi aduk halin dayake ciki, itama mik'ewa tayi tashiga d'akin Da sallama tashiga, wad'anda sukaji suka amsa, tanemi waje kusada Fatee ta zauna, data d'ago ido saita kama ya Umar na kallonta, Anty sa'a na kallonsu tana dariya ciki-ciki..... _____________________ Kwana biyu tsakani aka sallamai ya Umar suka tattara sai gida, duk dangi sun musu rakiyya zuwa gidan nasu. Wani abun mamaki tundaga babban falo suka fara gani, kaf abinda ke falon an kwasheshi babu komai sai agogon dake manne abango, kallon-kallo aka koma kowa yayi cirko-cirko kamar zakaru na shirin fad'a, Asma'u ce tayi k'arfin halin d'aga k'afafunta tashiga cikin falon sosai tana kalle-kalle. Babu Wanda ya iya cewa Uffan aduk taron, Dan Ya Umar baibama kowa damar hakanba, hasalima d'akinsa yashige yabarsu anan, a falon nasama abin mamakin ya tarar Dan nanma komai babu sai agogo dawata kujera guda d'aya dayakan zauna domin hutawa, sai tebiri agefenta Wanda yakan d'ora abubuwa, dak'yar yaja k'afarsa zuwa cikin bedroom d'in zuciyarsa cikeda tunani kala-kala, nanma dai bata canja zani ba Dan babu komi sai katifa da jibgin sutturunsa akai, saikuma tarkacen daba'a rasaba, jin hajijiya na neman d'ibarsa ya dafe bangon d'akin, cikin zuciyarsa yake tunanin wayayi masa wannan aikin?, badai za'a danganta ta'asarnan da 6arayiba Dan babu abinda 6arawo zaiyi da katakai, zuciyarsa tafara rawa akan ina Asma'u tasamu kud'in biya masa asibiti?, can wata zuciyar ta ce, "ita ta saida kayan gidan kenan?. Damm gabansa ya fad'i yay shiru batareda iya koda kwakwkwaran motsiba, yama rasa wane tunani zaiyi akan Lamarin........ A 6an garen Asma'u madai tunani take yaushe ya Umar yay cinikin kayan gidansu?, kanta bai ida kwancewaba saida tashiga nata d'akin, babu komai an kwashe sai katifa, hattada akwatinanta na lefe ankwashesu kaf, sai kayan datazo dasu daga gida aka zube a katifa, innalillahi wa'inna ialaihirraji'un kawai take iya amabata, yaraf tazube bisa katifar tana sauke numfashi, wai miya shiga kan ya Umar ne haka?, Dan kawai *KARAYAR ARZEEK'I* ta riskeka sai komai daka mallaka yazama hajar rabawa a kasuwa?, haba wannan wace iriyar rayuwace?....... 6angaren dangima dai kowa lamarin yagirmi tunaninsa, amma babu halin magana, dansu duk tunaninsu su ya Umar sun saida kayan gidanne dan nema masa lfy, wannan yasa tausayinsu ya d'arsu a zukatan wasunsu, Anty sa'a ma kasa zama tayi ta tattara 'ya'yanta suka tafi tana kuka da tausayin k'anin nata, ganin haka sauran sukaima Asma'u sallama suma suka tattafi. Daga Asma'u har ya Umar sun riski kansune a halin shiru da zargin juna, kuma har zuwa yammaci babu Wanda ya iya neman d'an uwansa balle tambaya agareshi, ganin agogo ya nuna 3:45pm yasaka Asma'u tashi tafito da k'yar saboda jin cikinta yafara kiran Ciroma tasan kuma ga ya Umar ma hakane. Kicin tanufa da nufin dafa musu komi yasamu su zirarama hanjinsu, mamaki al'ajabi da tsinkewar zuciya duk suka risketa alokaci guda, wayam babu komai akicind'in koda kuwa cokaline, hakama sitod'in babu alamar kwayar gero acikinsa, ta nisa tareda sauke numfashi, tama rasa abin fad'a Dan haka tafito zuwa d'akin ya Umar. Tofa. ta ambata yayinda tayi tozali danasa d'akin shima wayam, ta hard'e hannayenta ak'irji tana k'ara raba idanu akan komai, shin kuka zata fasa kokuwa kururuwa?, da sauri tafito zuwa d'akin Lubna, nanmadai an kwashe komai ko tsinke ba'a bariba, nasu d'akunan yafi dama-dama tunda anbar musu katifu da agogunan kallon lokaci. Ayanzun kam ba tsinkewar zuciyace kad'ai ta risketaba harda tsinkewar 'Yar hanji da daskarewar jini, da k'yar taja k'afafunta takoma d'akin ya Umar, masu iya magana kance ta inda aka hau aii tanan ake sauka. Bedroom d'insa takutsa kai batareda neman iziniba bare tsoron shiga, babu kowa ad'akin saidai k'arar ruwan wanka daga bathroom d'insa, wannan yasa tazauna abakin katifar tanabin tulun kayansa dake jibge bisa katifar da kallo............... *_luv you so much my sweet fan's, ALLAH yabar zuminci, inata godiya da k'aunarku gareni, wlhy nima ina matuk'ar k'aunarku aduk inda kuke alkairin ALLAH yakai muku😻😻😻😻❤❤❤❤❤❤🤝💋._* *_(((S))).......2017_* *_Luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* _Na gaisheku my Deexerh da Billy S Fari & Deejerh, alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke, ina alfahari daku._😻😻🤝💋 *_page→23-24_* .......Yana fitowa tamik'e zumbur tamkar wadda aka tsikara, da sauri tafice a d'akin, shikuma ya rakata da kallo, baice komaiba ya zauna yana shafa mai, duk jikinsa babu k'arfi yake jinsa, jallabiya kawai ya zura yafito domin tafiya masallaci sallar la'asar. Afalonsa ya tadda Asma'u, harzai wuce saikuma yajuyo ya kalleta, itama shi take kallo, amma suna had'a ido tajanye nata, ya ce, "lfy kuwa?". Tashi tayi tsaye tana tura baki gaba, muryarta na rawa ta ce, "ya Fharuk miyasa zakayi haka?". Kallonta yakeyi sama da k'asa Dan baisan inda maganar tata ta dosaba, hasalima shiyya dace yamata wannan maganar saboda saida kayan gidan datayi. Ganin kallon dayake mata yasaka jikinta yin sanyi. shima juyawa yayi yafice abinsa batareda yasake cewa komaiba. Dak'yar ta iya jan k'afarta takoma d'akinta, itama sallar ta gabatar, tana nan zaune akan sallayar cikinta na k'ugin yunwa taji alamar shigowar mutum, kafin tayi wani yunk'uri k'amshin turarensa ya sanar da ita shine, sosai yake bin d'akin da kallo, jiyayi wani haushi yakuma turnik'e zuciyarsa, to aii 6annar tayi yawa, kujerun babban falo kad'ai zata iya saidasu sama da dubu d'ari biyu, amma shine hardana d'akinsa Dana d'akinta?, afusace ya ce, "k! Waimike damunkine?. Asma'u tad'ago tana kallonsa, tuni tsoronsa ya tasirantu azuciyarta Dan ganin yanda idanunsa suka kad'a sukayi jajur. Muryarta na rawa ta ce, "yaya babu abinda ke damuna fa"...... Wata Uwar harara ya galla mata wadda tasakata saurin tsuke bakinta, Yakuma Daka mata tsawa ubanwaye yasakaki saida kayan gidannan!?. Cak jikin Asma'u yatsaya daga rawar dayakeyi, sosai take kallonsa dakuma mamaki, shi Kansa ya lura da hakan. Ta d'auke idonta daga kansa tana fad'in niban saida ko cokaliba agidannan, nima kuma d'azu maganar danaje yimaka kenan, dai-dai da kicin ba'a bar komaiba hakama d'akin Anty Lubna babu komai........ Shiru yayi yana kallonta, zuwa can kuma ya ce, " to idan bake bace wanene?, kinsandai 6arawo bazai saci katakai yabar kayan sakawaba?, shin inama kika samu kud'in biyamin asibiti?. Zuwa yanzun kam zuciyar Asma'u tafara tunzura, Dan haka tafara maganar dad'an karsashi, wayata nasayar nayi hidimar asibitinka, Dan alokacin banida abinda yawuce wayar saikuma kayan lefena Dan sukad'ai na mallaka agidannan, sukad'ai kuma zan bigi k'irji nace nawa, ko a shekaranjiya danazo gidannan komai yana nan, na tabbata duk Wanda yay wanan aikin ajiya yayishi.... Fuuuuu tashige bathroom batareda tajira cewarsaba. Cikeda mamaki yabita da kallo, dama yasan tuni Asma'u tanada tsiwa daga bayane tabari saboda tana shakkarsa, fita yayi zuwa d'akin lubna danya gaskata maganar Asma'u. Ilai kuwa babu komai acikinsa, kamarma ba'a ta6a ajiye wani Abu daya danganci mutumba, can jikin k'ofar window ya hango wata farar takarda, ahankali yataka ya zareta tareda bud'ewa, anutse yafara karanta takardar, baikai da zuwa k'araheba yasaketa awajen yana ambatar addu'ar da akeso musulmi yayi yayinda al'amura suka tsananta a gareshi. ↓ *_“Allahumma laa sahla illaa maa ja'aaltahu sahlan wa anta taj'alul hazna izaa shi'ita sahlan”._* _(ya ALLAH! babu wani Abu mai sauk'i, sai abinda kasanyashi yazama mai sauk'i, kuma kai kana Sanya tsanani idan kaso yazama sauk'i)._ Haka yayta maimaita wanan addu'a ahankali nutsuwa tafara zuwa agareshi, d'aukar takardar yayi yafice daga d'akin Yakoma nasa. Asma'u dake la6e tana kallon duk abinda ke faruwa takoma baya da sauri Dan ganin zai fito, koda yashiga d'akinsa saiyayi wurgi da takardar a katifar, shima yafad'a saman kayan ya kwanta domin samun sauk'in zafin da yakeji. Asma'u nanan zaune afalo shiru saiga Rafi'a da abinci, sosai tayi murna da hakan, bata 6oyema Rafi'a damuwarta tasanar da'ita komai. sosai lamarin ya girgiza Rafi'a. Asma'u tamik'e takaima ya Umar abincin, tadad'e akansa tana masa magana amma ko motsi baiyiba bare tayi tunanin zai amsata, hakan yasa tadire abincin tafitowarta. ++++++++++++++++ Haka rayuwar gidan tacigaba datafiya cikeda k'unci da damuwa, babu mai shiga harkar wani acikinsu, gaisuwa kawai take had'asu saikuma kaimasa abinci Wanda Rafi'a tajuri kawowa kullum bada sanin mamaba. Ranar yashirya fita, tsaf yafito yanata zabga k'amshi, idan baka saniba bazaka ta6a cewa yana cikin wata damuwaba, fuskarnan fayau sai Annurin hak'uri ketashi, saidai duk Wanda yasan ya Umar ya kalleshi a yanzu yasan ya rame sosai, sai dogon hancinnan dayay ziri-ziri, jin k'amshin turarensa ya yawaita awajen yasaka Asma'u dake kwance d'agowa tana kallonsa, tashi tayi zaune. Shima sai binta yakeyi da kallo, gani yake dukta canja masa, kamarma tayi bak'i, tausayinta ya d'arsu azuciyarsa, zama yayi abakin katifar kusada ita, cikin taushin murya ya ce, "Husna bakida lafiyane?. Kwalla suka cika mata idanu, kanta ak'asa ta ce, " a'a lfyta k'alau". Shiru yayi yana nazarinta, zuwa can yasauke numfashi, d'aya daga cikin wayoyinsa yazaro saga aljihu, yacire sim Cart d'insa sannan ya kalleta, ina cim cart d'inki?. Yana nan, tafad'a kanta ak'asa. "d'akkomin". Tashi tayi tamkar kazar da k'wai yafashema aciki, yabita dakkalo sanye take cikin sket da Riga na shadda ruwan ak'asa mai turuwa, ada kayan sunmata kad'an amma yanzu data rame sunmata yawa....... Katse masa tunani tayi da mik'a masa sim Cart d'in, baice komaiba ya kar6a ita kuma takoma inda takeda ta zauna. Saka sim Cart d'inta yayi a wayar ya sassaita mata abubuwa sannan yamik'a mata yana mik'ewa. Galala take kallonsa da waya a hannu, ganin haka ya d'ora mata bisa cinyarta, ya ce, " zanje wani waje yanzu Dan inaso nafara Neman aiki. Muryar Asma'u a sanyaye ta ce, "ALLAH yatsare yabada sa'a". Amin yafad'a yanamai jin dad'in addu'arta har cikin zuciyarsa. Tunda yafice taketa juya wayar a hannunta tana murmushi, aranta ta ce, " ko wayarnan takai nawa?, Dan tabbas daga ganinta an sayeta da kud'i masu nauyi. Ta sumbaci wayar tana murmushi tareda shak'ar daddad'an kamshinsa dake tashi a jikin wayar, ahankali tafurta ALLAH yabarmu har Abadan my Umar Fharuk!, abinsona, farincikina, Nusfulhayat d'ina, hawaye suka gangaro abisa fuskarta....... Kamar wadda akaima magana akunne tamik'e zummbur tanufi d'akinsa, takardar ranar tafara bulayin nema, amma duk inda take zatonta babu ita, tacije le6e tana yarfe hannun jin bak'in ciki, harta kama hanyar fita saikuma tadawo, bai k'yautu ace tacigaba da Barin d'akin da kayansa akan katifarnanba, komawa tayi tazauna ahankali tafara ware gogaggu da wankakku wad'anda babu guga, harma damasu daud'a aka had'a awajen, zagewa tayi sosai tagyara d'akin tsaf, tad'akko zanin gado ta shimd'a, kamar ance tad'an d'aga katifar saiga takardar ranar, wani murmushi jin dad'i tasaki, ta d'auki takardar ta ajiye gefe saida tagama gyara komai tsaf sannan tafice zuwa d'akinta cikeda son ganin abinda takardar ta k'unsa....... Ya Umar kam koda yafita ak'ofar gida sukaci karo da makwafcinsa, hannu yabasa suka gaisa, ya Umar yamasa godiya sosai akan taimakon daya masa ranar, babu komai d'an uwa aii anzama d'aya, amfanin makwaftakar kenan. Hakane gskyarka ngd sosai ALLAH yabar zuminci, saidai bansan sunankaba. Murmushi makwafcin nasa yayi ya ce, "hakane. Ni sunana Muktar". Masha ALLAH malam Muktar, nikuma sunana Umar Fharuk. Masha ALLAH Umar, daga yau ina fata zamu zama abokan juna, matanmmuma zasu zama k'awaye. Babu damuwa Muktar ALLAH yabarmu tare, suma saimuyi k'ok'arin had'asu. Sund'an dad'e suna hira, sannan Muktar yamasa sallama yakoma wajen aikinsa, dama yayi mantuwane yadawo d'auka. Ya Umar ma mashin ya tsaida yahau suka nufi inda zaije........ *_(((S))))......2017_* *_Luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→25-26_* ........Jikin Asma'u har rawa yakeyi wajen bud'e takardar, ta jingina da k'ofa bayan ta rufe tafara karantawa. *↓* *_hii Umar Fharuk_* _Hummm abin mamaki da al'ajabi._ _hhhhh Umar nasan abinda zaku fara ambata kenan kaida matsiyatan danginka da Mayyar matarka a yayin da kuka shigo kangon gidanka kuka tarar babu komai a cikinsa, hhhhhh to kasan wacece ta shirya wad'annan abubuwan mamakin da al'ajabi kuwa?. nice nan Lubna, nayi hakane saboda bazan ta6a barin kacigaba da morar wani Abu daga dukiyarmuba, bazan ta6a barin wannan shegiyar matar taka jin dad'in rayuwa da kaiba wlhy Umar, nice nan na kwashe komai nagidannan kuma nayi k'yauta dasu, Ku k'arata acikin talaucinku dama ahaka kuka taso kuma ahaka zaku k'are, Dan matiyaci ko'a tulun manshanu kasakashi haka zaifito bai dangwali komaiba, nasoka tamkar babu wani namiji aduniya, mahaifina yamaka gata tamkar shine ya haifeka, amma saboda butulci irin na talaka karasa dami zaka sakamin saida wata abar banza wai kishiya, tom ga fili gamai dokinan, saura kuma sukuwa ko?, ALLAH yabada sa'ar cin gabbaza mukan nagaba yayi gaba nabaya sai labari, abinda yasa zan barka katsira da gidan dakake cikima saboda yazama tukuyci wa tsaron dukiyar mahaifina dakayi abayane kawai, afrah da amrah kam kasaka aranka baka ta6a haihuwar wasu 'ya'yaba aduniya, nikam kamanta dani hakan zaifi yimaka sauk'i._ _wassalam matarka ada😜._ Ajiyar zuciya Asma'u tasauke, k'irjinta har wani d'agawa yakeyi sama saboda bugawar da zuciyarta takeyi da k'arfi, tadafe k'irjin tareda lumshe idanunta hawaye na zurara akumatunta, wani tausayin ya Umar ne yaketa walanked'uwa azuciyarta, ashe dama duk abubuwanan saboda ita yake faruwa dashi?, haba Anty Lubna miyasa zakiyi hakane?, gara'ace kin rabani da ya Fharuk da'ace kin cutar dashi da k'untata rayuwarsa sabodani, inason ya Fharuk banason wani Abu dazai ruguza duk wani cigabansa, ya ALLAH ka kawoma wanan bawa naka d'auki, tazame ta zauna k'asa da6ar tamkar wata mai shirin hawa bori. Tadad'e a wajen tana kuka kamar wadda akace inna ko baba sun mutu, ganin babu sarki sai ALLAH tamik'e tawanke fuskarta, hijjabinta ta d'auka tasaka tafito. Hartaje k'ofar fita saikuma ta fasa, komi ta tuna?, dawowa tayi tazauna a tsakar gidan tanabin k'adangaru daketa guje-guje da kallo......... Ya Umar kam yanacan yanata bulayin Neman aiki, duk inda yasan yanada wata alfarma ada saida yaje, amma k'alilannema acikinsu suke Nuna sun ganeshi, wasuma nunawa sukeyi basuta6a ganinsaba, murmushin takaici kawai yakeyi yatafi, har yamma lik'is babu wani cigaba saima wahalar kishirwa da yunwa data addabesa, ganin magriba takawo kai yahau mashin yanufo gidansu. Atsakar gida ya iske Mufida da Rafi'a suna hada-hadar girkin dare, Rafi'a dake wanke naman kaji tad'ago tana kallonsa da murmushi, yaya Sannu da zuwa. Yauwa Rafi'a, aiki kukeyi?. Eh yaya INA yini. Lfy lau ya makaranta?. Alhmdllh yaya. Mufida itama ta gaisheshi. Amsa mata yayi itama cikeda kulawa, Dan itama yanzu tausayinsa takeji tunda ya kwanta a asibiti. Ya ce, "mamafa?". Tanan ciki itada ya Abubakar. Okey shima yazo gidanne?. Eh yaya. Cikin falon yashiga da sallama, ya Abubakar da mama suka d'ago suna amsa MASA babu yabo babu fallasa, durk'usawa yayi yana gaida mama, ta amsa MASA kadaran kadahan, hannu yamik'ama ya Abubakar shima suka gaisa, suna gama gaisawa ya Abubakar yamik'e, to Mamana bara nawuce gida saikuma gobe, babudai abinda kike buk'ata ko?. A'a Sadiq d'ina bana buk'atar komai wlhy kawadatamu dakomai saidai nace ALLAH yayi maka albarka yak'ara arzik'i. Ameen Mamana saida safe. ALLAH yakaimu ka gaidamin 'yan jikokina da d'iyata. Zasuji insha ALLAH. saida yaje bakin k'ofa sanan ya ce, " o Umar sorry fa namanta kananan bamuyi sallamaba Ashe, saida safe konace saiwani jik'on danku kunyi wuyar gani yanzu. Ya Umar dakansa ke a duk'e tun d'uzun yana sauraren tad'in Nasu mama, ya d'ago idanunsa dasuka fara canja launi zuwaja saboda 6acin rai, yasan sarai habaici ya abubakar yamasa amma ko kad'an fuskar jarumin naku bata nunaba, fuskarsa shimfid'e da murmushi ya ce, "babu damuwa ya Abubakar saida safe agaida iyalin, ficewarsa yayi batareda ya amsaba. Ya Umar yadawo da kallonsa ga mama datake k'irga kud'in da ya Abubakar yakawo mata yanzu sai murmushi takeyi ana dangwalar yawu da k'ara Tisa k'irgar, baice komaiba yamaida Kansa k'asa yana jiran takammala. Saida tagama tsaf sanan yad'ago ta kalleta, gabad'aya fuskarta ta canja yanzu babu walwala, amma kuma idonta na kan ya Umar d'in. Muryarsa a raunane ya ce, " mama dama Nazi nasanar dake yanda mukayi da Lubna ne. Baki mama ta ta6e amasife ta ce, "Umaru kaini rabani dawata lubna tunda kud'in ubanta basu ammfaneka da komaiba, idanda su wasu mutanene arzik'ine Aida sun taimakeka kodan ganin halin masifar dakake ciki, amma mutanannan sunyi funfurun fus saboda bak'in ciki irinna mai arzik'i dabayaso talaka yasamu, wace irin wahalace bakaima ubantaba fisabilillahi amma yamzu suka watsar Sakai, kofa dubaka basuzoyi asibitiba harkayi kwanakinka kagama jinya.... Shidai Umar tunda mama tafara sababinta baice komaiba kansama na k'asa, saidai zuciyarsa tana mamakin halin *_MANTA ALKAIRI_* irinna mahaifiyarsa, koba komi iyayen Lubna sun taka rawar gani akansa, kuma har gobe yana ganinsu da mutunci bakuma zai manta da karamcin dasukai masaba a baya...... Jin mama tayi shiru yagane tagama NATA, muryarsa a tausashe ya ce, "tom mama kiyi hak'uri amma bawannan maganarce dama kawoniba. Tsaki mama tayi ta ce, " kaji zancen banza to miya kawoka!?". Saida ya had'iye wani yawu k'irjinsa yana dukan uku-uku ya ce, ''mama na saki Lubna tunkafin na kwanta a asibiti". Ba mamaba har Mufida da Rafi'a dake k'ok'arin shigowa saida suka daskare awajen, maganarsa ta razanasu. Cikin tsawa mama ta ce, "Umaru bakada hankaline!!?, kokuwa kafara shaye-shaye bansaniba!!?". d'ago jajayen idanunsa yayi yana kallonta, cikin girmamawa ya ce, " wlhy mama bana shan komai, amma idan kin bani dama zan fad'a miki dukkan abinda yafaru harna saketa. Wani huci mama tasauke harda hura hanci ta ce, "ina jinka. Ya Umar ya sauke ajiyar zuciya sanan cikin nutsuwa yafara zayyanama mama komai, Rafi'a da Mufida sai hawaye sukeyi, mama kanta jikinta yayi sanyi, wani k'auna da tausayin d'an nata suka ratsata, tabbas tana matuk'ar son 'yayanta mafisifar son kud'i da hange-hangene kawai suke dakusheta, ya Umar yayi shiru ayayinda yakai karshe, zuciyarsa sai zafi takeyi da rad'ad'i, jiyay k'irjinsa yafara nauyi, addu'arnan ta yaye bak'inciki da tafiyar da k'uncin zuciya yafara ambata..... *↓* *_“Allahumma inni abduka ibnu abdika ibnu amatika, naasiyatin bi yadika, maadhin fiyya hukmika adlun fiyya k'adha'uka as'aluka bi kullis min huwa laka sammaita bihi nafsaka au anzaltahu fiikitaabika au allamtahu Ahdan min khalk'ika awista' asarta bihi fii ilmil gaibi indaka an taja'ala k'ur'ana rabii'a k'albii, wa nuura sadrii, wa jalaa'a huznii wa zahaaba hammi”._* _(ya ALLAH ni bawankane kuma d'an bawanka, kuma d'an baiwarka, makwarkwad'ata a hannunka take, hukuncinka zartaccene akaina, kuma k'addararka gareni mai adalcice ina rok'onka dakowanne suna Naka, Wanda ka ambaci kanka dashi, koka saukar dashi acikin littafinka, koka sanar dashi ga wani daga halittarka, koka ke6ance kanka da saninsa acikin ilimin fake da ke wurinka daka Sanya alkur'ani ya zama kaka ga zuciyata, da haske ga k'irjina, da kwaranyewa ga bak'in cikina, dakuma mai tafiyar da damuwata)”._ *↓* *_“Allahumma inni a'uzu bika minal hammi wal huzni, wal ajzi wal kasali wal bukhli wal jubni, wadhal'id daini wa galabatir rijaali”._* _(ya ALLAH! ina neman tsarinka daga damuwa da bak'in ciki, da gajiyawa da lalaci, da rowa da ragwantaka da nauyin bashi, da rinjayen mazaje)._ Ahankali k'irjinnansa yafara rage nauyi, zuciyarsa yafara sanyi, wata nutsuwace tafara riskarsa babu abinda yakeyi sai sauke ajiyar zuciya, da sauri Rafi'a tabud'e firij ruwa tad'akko batareda ta nemi kofiba ta mik'a masa, shima bai tsaya tambayar kofinba ya 6alle murfin yana kwankwad'awa cikinsa, saida yashanye ruwannan tas sannan yadire gorar, dama k'aramar gorace, kansa yad'ora jikin kujera yana sauke numfashi ahankali, bayan wasu 'yan mintuna nutsuwarsa tadawo gaba d'aya, har bak'in cikin da mutane suka cusa masa d'azu wajen neman aiki dukya kwaranye, saima wani nishad'i da farinciki daya mamayesa....... Maganar mamace ta sauka a kunnensa, cikin tausayawa ta ce, "ALLAH ya k'yauta, saikadage yanzu kafara neman aiki da takaddunka, dama kaine kak'i aii tuni, yanzu da aikin kayarda ya samama maka alokacin daya baka za6i aikaga da haka bata faruba ko?........ Kallon mama yakeyi k'ur da mamaki wai ita har yanzu batayi laushi bane?, wai sai yaushene mahaifiyarsu zata daina wanan masifaffen son kud'in nata da hange-hange, (wata zuciyarsa ta ce, " addu'a kawai zakucigaba da mata"). Yananan zaune harta gama surutanta, jin ankira sallar isha'i yamik'e yamata sallama. Awaje yatadda k'annen nasa mata duksunyi tagumu, yata6a Mufida dake kusadashi, "k! Lfyarku kuwa?". Figigit suka dawo hayyacinsu, babu komai yaya. Okey tomni nawuce saida safe. Lah yaya munfa kusa gama abinci katsaya kaci mana. No ngd saida safe... Yafad'a yana fita. Rafi'a da Mufida suka bishi da kallo cikin tausayawa. Kai tsaye gidansa yanufa, baishigaba saida yayi sallar isha'i a masallacin anguwarsu sannan yashiga gida. Tun a tsakar gida yaga canji Dan yau gidan yasha gyara, yana shiga abban fallo wani k'amshi mai dad'i yabigi hancinsa, dukda babu komai afalon sai agogo amma yasharu tas sai k'amshi ke tashi, jin tafiyar abayansa yasakashi d'agowa da Sauri.............. *_(((S))).......2017_* *_I Love you all my sweet fan's_*💋 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→27-28_* ........Asma'u ce sanye cikin doguwar riga ta atanfa, kayan sunyi bala'in zama ajikinta d'as, taci kwalliya ta alfarma sai bulala k'amshi takeyi, cikeda yanga tak'araso gareshi, shikam tsaye yake gingiringin tamkar wani gunki, harta k'araso gareshi amma bai motsaba. Cikeda mamaki Asma'u take kallonsa, miya samesa haka?, kokuwa kwalliyar tatace batayibane?, shiga tayi bin jikinta da kallo tamkar mai Neman wani wani Abu, can tad'ago tana kallonsa itama, ya Fharuk lfy kuwa?. Firgigit yadawo hayyacinsa tareda sauke wata nannauyar ajiyar zuciya!, 'yan kame-kame yafara na basarwa, no. babu komai yafad'a yana nufar d'akinsa. Binsa da kallo tayi saikuma ta tab'e baki, kadaiji dashi tayi maganar tana masa gwalo😜. Ya Umar nashiga d'akinsa yazube bisa katifar datasha d'an karan gyara, lumshe idanu yayi yana murmushi, yadad'e baiji farinciki irinna yanzuba, a 'yan watannin nan yama manta shi macene kokuwa namiji?, kwata-kwata bayajin wata sha'awa ko son kasancewa da mace, damuwa ta mantar dashi farinciki da nishad'i, yaukam Asma'u ta tunatar dashi koshi waye, Dan kwalliyarta tasakasa begen wani Abu, babu k'arya yarinyar tanada jiki irinna mata masha ALLAH, hannu yakai yashafa sumar Kansa wadda ba gayubane yasakashi tarata, a'a damuwace kawai da rashin lokacin kai, tashi yayi zaune yanamai bin ko'ina na d'akinsa da kallo, komai tsaf kamar ba d'akin daya zama bolaba acikin kwana hud'u dasuka wuce. Ajiyar zuciya ya sauke tareda furta *_“Alhamdllh alaa kulli hallin”._* A gaggauce yatashi yacire kayansa, wanka yashiga sauri-sauri ya kammala Dan yana burin sake ganin Asma'u da k'yau, baiwani d'auki dogon lokaciba yagama shiryawa cikin wando iya gwiwa da k'aramar Riga mara hannu, turare yafesa sanan yasaka silifas yafito babban falon dayake tamkar zaure, babu kowa afalon Asma'u takoma d'akinta, shima d'akin nata yanufa, tana a falonta zaune kan tabarmar data shimfid'a waya taketa latsawa tana kallon hotunan ya Umar sannan yana Umar Fharuk d'insa, tana murmushi, Dan sanda akayi hitunan yana wasa da nairane, shikansa yana son hotunan sosai, yad'an dad'e tsaye yana k'are mata kallo, ganin batasanma yanayiba yay mata gyaran murya. Jikinta har rawa yakeyi wajen 6oye wayar. Baice da ita komaiba yazauna kan tabarmar, saida yazauna sanan yamik'a mata hannu alamar tabashi wayar yagani. Idanu ta kwalalo masa waje, ya Fharuk bafa wani Abu baneba. Uhm nasani, kibani dai. Marairaice fuska tayi tamkar zata FASA kuka Dan batason yaga mitake kallo, ALLAH ya bawani abun ashsha bane hotuna nake kallo. Hotunan waye?, yay maganar cikeda cin magani. Uhm uhm namunefa nidasu Hasiya da Fatee....... Batama bari ya tanka ba tamik'e tafita Dan kawo masa abinci. Binta yayi da kallo, dukda bai yarda da itaba. Yana nan zaune tashigo da tiren abinci, kallon tiren yayi dake d'aukeda komai sabo, kuloli Kofi cokula filet duk sababbi, kallonta yayi da k'yau yanzukam fuskarsa amatuk'ar d'aure take, ayatsine ya ce, "wad'annan abubuwanfa INA kika samu kud'in siyensu?. Ad'arare ta kallesa muryarta na rawa ta ce, " uhm ya Fharuk sauran kud'in wayarnanne dama nabama Fatee tasiyo mana saboda naga ko kofin shan ruwa babu agidannan, dama sonake ka kammala cin abincin namaka bayani amma kayi hak'uri nayi Abu batareda Neman shawararkaba. Ahankali ya furzo huci daga bakinsa yana kauda kai daga gareta. Jiki a sanyaye tahad'a MASA abincin agabansa, tuwon masarane daya tuk'u da k'yau saikuma miyar k'u6ewa d'anya dataji d'anyen kifi da daddawa sai k'amshi ke tashi, a jok d'in kam zo6one shima sai k'amshin kayan yaji yakeyi. Tunkafin yafara cin abincin k'amshin yawunsa keta tsinkewa, sosai ya k'agara yafara saka lauma, amma jinkai da k'asaita irinta mazaje yasakashi mazewa harda kauda kai gefe. Cikin sanyin Murya Asma'u ta ce, "ya please kaci abincin, Dan ALLAH kada kamin horo akan hakan." Tausayi tabashi Dan muryarta har rawa takeyi, amma baice komaiba, hannunsa takama tasaka acikin ruwan data aje arobar wanke hannu, Fes ta wanke hannun yana jinta, bai ankaraba yaji hannunsa acikin miyar, kallonta yayi da sauri, ta langa6e kai gefe tamkar zata FASA ihu, kona baka da kaina?, tayi maganar hawaye na zurara akumatunta. Kad'an yarage ya fashe da dariya amma saiya gimtse ya antaya mata hararama. Tashitayi tamkar Mara laka tashige bedroom, shikuma yaraka bayanta da murmushi, tana shigewa yafara saka lauma yana lumshe ido saboda dad'in da tuwon kemasa. Saida yaci yak'oshi sanan ya wanke hannunsa, tuwon yad'iba a filet yatafi d'akinta danyasan itama bataciba, kwance take akan katifa rubda ciki da alama ma kuka takeyi, aransa ya ce, "idon kuka kenan". Zama yayi abakin katifar yana ambatar sunanata, Husna tashi kici abincin. shiru tamasa batayi koda motsiba. Ganin haka yakamo hanninta yana murzawa ahankali, zumbur Asma'u ta tashi zaune tana muzurai, wani yarrrr! Taji yayinda yake Mirza tafin hannunta, batareda yace mata komaiba yad'ora filet d'in abincin saman cinyarta, maza kicinyeshi tas. Fuska ta shagwa6e tana turo baki nima na k'oshi tunda kaima bakaciba, ido d'ya yad'age yana kallon shagwa6a, saikuma yayi murmushin gefen baki yana fad'in waya gaya miki banciba?, saida nakusa cinyewama nakawo miki sauran. Ya Fharuk da gsk?. Kansa ya jinjina mata. Bismillah tayi tafara cin tuwonsa, shikuma cikin dabara ya d'auki wayarta yafara bincike, ganin hotunansa take kallo d'azu yasakashi sauke ajiyar zuciya, tayi sagare tana kallonsa Dan mamakin wannan ajiyar zuciya, saida tagama tsaf taje ta wanke hannu sannan tadawo ta zauna abakin katifar hannunta d'aukeda kud'i masu d'an yawa har kashi biyu. Naminene?, yafad'a batareda ya kar6aba. Zan maka bayani aii. Yau bayan fitarka Inna tazo gidannan, takawo mana kayan abinci, sannan tace nabaka wad'annan kud'in tanuna masa kashi d'aya acikin kud'in, wad'an nan kuma na sauran wayatane, saidai kayi hak'uri nata6a wasu aciki. Amma ya Fharuk nayi wani tunani. Mizai hana shagonnan na k'ofar gida kazuba kayan provisions acikinsa har muga abinda ALLAH zaiyi akan Neman aikin naka. K'yawawan idanunsa ya tsura mata yanamai kallonta cikeda so da tsananin k'auna, tun Asma'u tana yarinya yake sonta amma wasu abubuwa suka hanashi nunawa dakuma soyayyar Lubna data rud'eshi kasancewarsa mutum maison wayayyar mace. jiyake tamkar ya rungumeta. amma bazaiyi hakaba Dan gudun karta rainashi. Jin yayi shiru gashikuma ya tsura mata idanu ta ce, "ya Fharuk! Mike faruwane?. Ko shawarata batayi daidai baneba?. Ajiyar zuciya ya sauke, a'a Husna shawararki tayi, amma kibari zanyi tunani. Kud'in inna kuwa gsky bazan amsaba, za'a maida mata abinta, idanni har ban bataba, amatsayinta na uwa agareni, tom baik'yautu na kar6a daga garetaba. Humm yaya kasandai halin Inna sarai, wlhy na tabbata bazata amshi kud'innanba, tunda har tayi niyya. Amma kagwada kagani, Dan kunfi kusa. Hararta yayi, kokina kishine?. Asma'u tazaro idanu waje, ya Fharuk nikam kishinmi zanyi dakai? bayan inna tabamu labari tunkan tasamemu kaine d'anta, yanzukuwa danta samemu bazata ta6a had'a soyayyarka da tamuba. Tokaga idanma nayi kishin, ainayi abanza. Ammafa inad'anyi kad'an. ‘tayi maganar tana dariya damasa gwalo.’ Shima murmushin yayi, yamik'a hannu zai cafkota ta zulle. Filo yad'auka yajefeta dashi, wlhy nakula yarinyarnan kinrainanifa. Hannu tasa takare kanta daga filon, cikin dariya ta ce, "ALLAH niban rainakaba." ‘ashagwa6e take masa magana.’ Shikam yayi sagade yana kallon yanda takeyin dariya k'yawawan fararen hak'oranta suna burgeshi. Saida tamik'e tsaye sannan tad’auki filon itama ta jefa masa, ta antaya da gudu waje. Lalala nikika jefama fillo? Lallai yau jiki magayine. Yay maganar yana mik'ewa yabita abaya da filon. Tana ganinsa tafita babban falo da gudu tana dariya, zagaye falon sukaitayi yana tilla mata filo, itakuma tana gudu. Sunkai wasu mintina ahaka har Asma'u tagaji sosai tafara bin bango tana haki. Taku biyu ya damk'ota, zille zille tafara tana fad’in ya Fharuk natuba, ALLAH bazan sakeba. Zaki gayamin hakane idan kika horu, gaba d’aya yad'auketa yakoma d’akinta. Sai fad'in yayi hak'uri takeyi ALLAH bazata sakeba. Ahaf yarinya zancen kikeso kuma, aii daga yau idan ance kimin rashin kunya bazaki sakeba kuma. Wayyo na Inna plss, narantse bazan sakeba. Ko saurarrta baiyiba yajefata bisa katifarta. Zuwa yanzukam da gsk tsoronsa tafara shigar Asma'u, kardai mutumin nan yace mata wani Abu zai mata, nashiga uku ni Asma'u, wlhy tsoro nakeji, atsorace ta yunk'ura zata tashi ya damk'ota da sauri suka fad'a saman katifar atare.......... _“kuyi hak'uri da wanan wlhy murace taketa nuk'urkusata, ga ciwonkai🤧, da k’yar na iya wannanma.”_ *_(((S))).......2017_* *_Love you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* _Wayyo mura🤧🤧🤧🤧🤧🤧🤧🤧._ *_page→29-30_* ........Humm miye labarin Lubna ne? Su Lubna anagida hankali kwance, tak'ara k'yau da k'iba tamkar ba itaba, hakamasu Afrah sunyi 6ul-6ul dasu, an maidasu wata had'ad'd'iyar makaranta ta 'ya'yan manya. Lubna duk inda taso zuwa takeyi, gakud'i ga Hutu, babu ruwanta dawani maganar iddah sai kula samari takeyi yara k'anana. (Dan mamanta ta ce, "bazata auri mai mataba, saidai saurayi d'anyen jini). Tako hau kan wannan magana tayi d'ane-d'ane. dukda ta ce, ''ita yanzu aure baya gabanta. Karatuma zata koma." Gantalin zuwa biki kuwa itada Suhaila sunmaidashi tamkar cin gwaza, Lubna tabiye mata sosai tamkar wata budurwa, ko bak'i akayi a gidan ba'a cewa Afrah da Amrah 'ya'yan Lubna ne, Dan basaso ace tata6a aure barema harta haihu. Dad bazama yakeba sosai Dan haka baisan wainar da'ake toyawaba agida, Ameer da Safwan yayyensu suma dai samma kal, Dan duk taron kwara da ama ne, babu mai tada wani suma shaid'anun kansune, Neman mai gyarasu sukeyi barema su gyara wani. Ayanzu hakadai cikin hidimar shirye-shiryen bikin Ameer d'in sukeyi, zai auri d'iyar wani babban k'usa a gwamnati, shirin biki takeyi na garari na d'angata. Duk suna zaune afalo dad ne kawai babu Dan yaje k'asar Chaina, akwatinane guda 30, set biyar kenan, kowanne da kalarsa, dank'are suke da kayan alfarma na garari, kayan lefen Ameer ne dasukaje gabad'aya gidan har k'asar Dubai suka had'osu, jiya da daddare suka dawo, shine yau ake duba abunda babu, kayane na garari babu na k'asa da dubu d'ari biyu, kayan sakawa kawai na less, shadda, atanfa, material, dadai sauran yayi, kala d'ari hud'une, banda su jallabiya, k'ananun kaya..etc, kayan shafa kam da takalma jakunkuna aiba'a magana, barema azo kan yari, sark'ok'in zinari goma sha biyu, 'yar dubu d'ari biyar itace k'arama. Humm masu karatu! Mahaifinsu Lubna fa bak'aramar dukiya ya taraba, suma 'ya'yansa babu Wanda bashida hannayen jari a ciki da wajen k'asarnan, saidai kuma acikinsu babu mai aikinyi Dan bama su nutsu sunyi karatunba, kasuwancin kuma bazuwa sukeba bare su koya, to anrigada antara musu. _wlhy 'ya'yan many an k'asarnan basa karatu ko kad'an, 'ya'yan talakawa muke maida hankali muyi karatu komai wuya komai dad'i, amma da zaka karad'e madafun ikon k'asarnan zakaga duk 'ya'yan masu fad'a ajine awajen, akuma many an kujeru, mu 'ya'yan talakawa mune ak'asa k'alilanma kenan acikinmu da'aka d'auka aikin, shiyyasa kullum k'asarmu tana cikin masifu iri-iri, tomasu rik'eda k'asar duk basusan ciwon kansuba ballantana su taimaki na k'asa dasu, basusan ana talauciba bare su taimakawa talaka, basusan komaiba saibin k'asashen duniya suna shek'e ayarsu yanda suka gadama da karuwan kafirai._ ALLAH yasa mudace. Lubna tad'aga wata sark'ar zinari tana fad'i kai 'yan uwa sark'arnanfa tawuce dani wlhy, dolene nakoma Dubai kafin biki nima nasaka ayimin. Harararta Ameer yayi, ya ce, "kefa dad'ina dake kenan, babu yanda za'ayi mutum yayi Abu mai k'yau saikinyi copy copy, ai abin kunyane ma ace aga amarya da sark'ar k'anwar ango ma da ita." Safwan ya ce, "bar yarinyarnan kaji, aidama agidan wancan k'aban take har a yanzu dabata samu yanda takesoba." Cikin shek'ewa da dariya Suhaima ta ce, "bro's kubarta, wlhy badan ceton da momy taima baby ba dayanzun k'ila mun fara bata kwancen kaya." Duka Lubna takaima Suhaima, tana fad'in bakinki ya sari d'anyen kashi muguwa kawai. Kuma wlhy duk Wanda Yakuma had'ani da Umar zamu kwashi 'yan kallo agidannan, natsaneshi! Na tsaneshi wlhy!." ‘tayi maganar tana hawaye.’ Safwan dake Kusada ita yaruk'o hannunta, sorry babyn dad! Karki damu bazamu sake fad'aba kinji, sark'a kuwa dakud'inama zan saya miki. Murmushi tamasa tana mai share hawayen fuskarta. Daga nan Suhaima da Ameer ma suka bata hak'uri, murmushi mom tayi tana cigaba da birkita kayan Dan bincikawa......... ____________________ Koda ya Umar yajefa Asma'u kan katifa shima saiya fad'a Kusada ita. Idonta cikeda kwalla tadubeshi, pls ya Fharuk natuba, ALLAH bazan sakeba. Ido d'aya yad'age yana kallonta da d'ayan, yamatso daf da ita tamkar zai shige jikinta, k'amshin turarensa na matuk'ar dukan hancinta, gadad'in k'amshin da turarensa kemata ga fargabar abinda zai mata, tad'an runtse idanunta danjin bai tankaba. Jin hannumsa akan k'irjinta Yakuma firgitata, tawaro idanunta yayinda shikuma ya ida kai hannunsa kan kunnenta na dama, Wanda dama shiyakeso ya damk'o. Jin anmurd'a mata kunni da k'arfi yasakata sakin wata kasalalliyar k'ara tareda ruk'o hannunsa tana shiii da baki. Wayyo ya Fharuk wlhy akwai zafi, sheeeeeee! Plss natuba wlhy. Shikam murmushinsa kawai yake saki tana k'ara Murza kunnen saboda salon mugunta, saida ya tabbatar taji gargad'insa sanan yasaki kunnen yatashi yana wata dariyarsa wadda Asma'u batasanma ya iyaba. Ficewarsa yayi, itakuma tana rik'e da kunnenta dakemata rad'ad'i da zugi, jitake tamkar tarushe da kuka, afili ta ce, "mugu d'an masa, ALLAH yasakamin. Yana shiga d'akinsa yafad'a kan katifarsa fuskarsa shimfid’e da murmushi. Lumshe idanunsa yayi tamkar mai barci, tabbas abaya yayi soyyaya da Lubna, kuma har yana ganin bazai ta6a son wata 'ya maceba bayan ita, saboda yasameta wayayya yanda yake buk'ata. Ya burkita kwanciyarsa zuwa rubada ciki tareda k'ara k'an k'ame filo ak'irjinsa, shikad'ai yasan miyakeji. dannidai bilyn Abdul bazan saniba🤷🏽‍♀........ Washe gari dawuri Ya Umar yashirya cikin shadda milk color, d'inkin zamani, tamasa k'yau aynun, idan bakasan yana cikin wani haliba saika d'auka irin masu kud'innanne ko 'ya'yan masu kud'i da Hutu ya huda, duk wannan bitada k'ullin da ya Umar yashiga hakan bai canja kalar fatarsaba, tana nan lumi da ita, sai shek'i da Annuri ketashi, gakuma gashi daya kwanta luf luf afatar tasa. Fitowar Asma'u kenan daga wanka yashigo d'akin, dasauri taja hijjab tasaka. Shima kauda kansa yayi gefe, zanje nagaida Inna, kokinada sak'o?. Kallonsa tayi sosai da mamaki, yaukuma wani sabon salonne akazo dashi?. Ganin kallon datake masa yasashi juyawa yana fad'in tunda bakida sak'on saina dawo. ‘batareda yajira amsartaba yafice abinsa. Ta6e baki Asma'u tayi, afili ta CE, "hummm ya Fharuk kai zumane nalura saida wuta, indai banda Neman magana yau kafara zuwa gaida inna? Kata6a fad'amin zakaje? Bare sallamar saika dawo?.... Cigaba tayi da mitarta tana shafa mai, saida tagama tsaf tasaka kaya sannan tafara shirin gyaran gidan....... Agidan inna kam bayan ya Umar yashiga ya gaida baba sukad'an ta6a hira sannan yashiga d'akin inna, tana zaune tana karyawa, Fatee nagefenta tana yankan d'inki Dan bayan ta kammala secondary d'inta sai baba ya ce, " tashiga wani makaranta nan kusadasu na koyon d'inki tunda basuda k'arfin dazata cigaba da karatu kafin kuma ALLAH yakawo mata miji, sosai tadage a makarantar takoyi d'inki acikin wata shida, zuwa yanzukam takware harma kawomata mutane sukeyi. Inna ta washe hak'ora tana fad'in lale dakai yarona. Shima fuskarsa shimfid'e take da murmushin yaje Kusada inna yazauna yana fad'in yauwa innata, nasameki lfy?. Lfy lau Umaru ya iyalin naka?. Lfy lau suke inna, tamace agaidaku. To ina amsawa. Fatee ta ce, "ya Umar ina kwana?. Lfy lau Fateema tela, ya d'inkin? Kinadai k'ok'ari ko?. Eh wlhy Yaya inayi sosai, yanzuma kayan gidansu zaliha naketa d'inkawa na ankon bikin kareema nanda next week, kusan kala 20 kenan na d'inka na manya da yara. Masha ALLAHU, amma kinyi k'ok'ari, kuma naji dad'i, inason mitum mai k'ok'ari akan Sana'a komin k'an k'antarta, ALLAH yak'ara bada sa'a. Ameen Yaya ngd sosai, ina Anty Asma'u?. Tana gida nabarota tace agaisheku. Muna amsawa da k'yau. Inna Hasiya fa? Tana inane?. Hasiya tana islamiyya kasan malama za'ayi wanan waje Umaru. Da k'yau Inna, aii anason Haka, itama ALLAH yacika mata burinta. Ameen Umaru yacikamana gaba d'aya. Ya Umar yagyara zama yana fad'in inna dama akan kud'in jiyane dakika kaima Husn........ Hannu inna tad'aga masa batareda ya k'arasaba, kaga Umaru nidai banbaka kud'innan Dan wani abuba, nabaka amatsayina na uwa agareka, tsakanin uwa da d'akuwa aii babu jayayya ko?. Ya Umar yad'aga mata kai. Tacigaba dafad'in to Indai kasan hakane bana buk'atar jin komai daga bakinka, kaje kasamu sana'a koda k'aramace kafara ALLAH yasaka albarka acikinta. Kokad'an banaso kacigaba da wahalarmin da kanka awajen Neman aiki, ALLAH yabada nasara akan duk abinda aka saka hannu. Ameen inna, ngd sosai dakasancewarki uwa agareni, lallai nayi dace dasamu uwa tagari mai share hawayena, ngd sosai inna, ALLAH yak'ara tsawon kwana da lafiya, ng...... Kaga godiyar ta isa haka, ALLAH yayi muku albarka gabad'aya. Ameen suka amsa shida Fatee daketa zuba murmushin jin dad'i. Inna mikuka dafa yunwa nakeji?. Umaru kokone da Alala da Fatee tayi, Fatee maza tashi ki kawo masa. Amma ita lalatacciyarnan tana ina kafito baka karyaba tabarka?. A'a inna balaifinta baneba, nine, nayi sakkon fitowane da wuri saboda nabiya wajen wani abokinane kafin nazonan dayace zaimin hanyar aiki, amma koda najema saisukace yawuce Abuja tun ajiya, dama yamin k'aryane kawai irinna 'yan boko. Karka damu Umaru inna tafad'a tana kwafa, komai zaizama labari wataran, kama ture batun samun aiki karungumi 'Yar sana'ar da ALLAH yaza6a maka, inada yak'inin wataran sai sundawo suna nemanka da kud'i kagagara ganuwa agaresu. Shikenan inna nahak'ura, yanzudai munyanke shawara nida Husna............nan yazayyanema inna komai akan maganarsu tajiya da Asma'u tamasa. 100/100 inna tabada goyon baya tareda addu'ar alkairi. Yadad'e agidan, Dan har shabiyu sanan yatafi......... _____________________ Tundaga ranar suka shiga gyaran shagon dake k'ofar gidansu kamar na 'yan tireda, cikin kwana hud’u aka zuba komai, dukda kayan bawani yawane dasuba amma Alhmdllh sund'an k'ayatar. Tun aranar suka fara ciniki kasancewar dama babu wani shagon tireda a anguwar, sai idan anje can k'asan layinsu ko baya. Tunda safe ya Umar kezuwa yabud'e saboda masu sayyar safe, idan Asma'u ta kammala break taje takai masa shagon tunda da k'ofa tacikin gidan. Hakama da rana, da daddarema haka, zuwa 11:30 saiya rufe yashigo gida. Tsakaninsa da Asma'u kam babu komai sai gaisuwa da girmamawa, ita tsoronsama takeyi, aganinta tunda yafara mata gargad'in ranar to aii zuwa nangaba duk abinda yazo zuciyarsa zai iya mata. Yaukam antashi da muku-mukun sanyi, wanan yasaka Asma'u tashi da zazza6i mai zafi da mura......... *_(((S)))).....2017._* *_luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→31-32_* ........Tunda tayi sallar asuba takoma ta k'udundune a bargo. Shikam ya Umar tundaga masallaci baima dawo gidanba yana shago, agogo ya kalla dake cikin shagon har 9:37am amma Asma'u bata lek'oba, sallamar wani saurayi tak'atse masa tunani, ya amsa yana mik'a masa hannu suka gaisa, saurayin yace abashi Sabulun wanki, d'akkowa Ya Umar yayi yabashi, saikuma ga wasu yara, doledai ya hak'ura yacigaba dabama mutane abinda sukeso, haka shagon yake wuni cikin shige da fici namasu siyayya. Har 11 tayi baisamu damar shiga gidanba, gashi Asma'u ma bata lek'oba, yanaji azuciyarsa badai lafiyaba. Can zuwa 11:30 mutane sukad'an lafa saiya rufe shagon yashiga gida. Har yanzu Asma'u nak'udundune abargo, sai rawar sanyi take faman yi da sambatun zazza6i, dama ita haka take indai tana zazza6i tatayin sambatu kenan. Da sallama ya Umar yashigo, ganin Asma'u a kwance cikin bargo sai gabansa yafad'i, k'arasawa yayi cikin d'akin sosai yana fad'in lafiya kuwa?. Asma'u dabatasan yanayiba sai rawar sanyi takeyi tana sambatu dakiran baba, inna, Fatee, Rafi'a, hasiya, kuzo kutaimakeni, wayyo ya Fharuk zan mutu kazo plzz..... Ganin yanda take abirkice yak'arasa da sauri yazauna bakin katifar, husna lafiya kuwa? Yay maganar yana yaye k'aton bargon data lilli6a ajikinta, wani hucin zafin zazza6i yabigeshi, da sauri tarik'o hannunsa tana fad'in wayyo Yaya rufeni sanyi nakeji sheeeeee!!!!. Lilli6eta yayi tareda fad'in sannu, amma miyasa baki fad'aminba tun d'azun? Haba mutum yata zama da ciwone?. Mik'ewa yayi zai fita tarik'o hannunsa tana kuka, wayyo ya Fharuk kaina kamar zai fashe, k'irjinama haka, kataimakeni wayyo. Tausayi tabashi sosai, dawowa yayi yazauna akusada ita, tad'ago da dak'yar tad'ora kanta saman cinyarsa, kokad'an bataso yatashi data Kusada ita, (dama itakam wanan salon zazza6inta kenan, saitaji wani akusada ita). Ya Umar yad'an rintse ido danjin yanda zafin zazza6inta ya ratsamasa jiki, tausayinta yakuma kamashi, kanta yashafa ahankali, husna kikwanta zanje nama muktar maganane kozai samo mana doctor d'in dazai dubaki. Uhm uhm Yaya banason allura wlhy, kabarni kawai. Yaya zan barki husna! Kinta6a ganin anbar mutum cikin ciwone? Kiniji yanda jikinki yayzafi kuwa?........ Kafin tace wani abu sai sukaji sallaman Rafi'a. Ya Umar ne ya amsa, tatsaya ak'ofar d'aki danjin muryarsa, jin shiru nawani lokaci ya ce, "shigo mana." K'arasowa tayi cikin d'akin, ta gaida ya Umar sanan ta tambayi miya sami Asma'u?. Batada lfyne, yauwa shiga nan makwaftanmu kima muktar magana kozai samo mana doctor dazaizo gida?. To Yaya, ammafa masu sayen Abu suna jiranka a k'ofar shago. O!. kinga kar6a key d'in, idan kinmasa magana saiki bud'e ki zauna, kafin nagama. OK, tana kar6ar key d'in tafice da sauri. Mintina k'alilan saiga Muktar yazo, dak'yar ya Umar yasamu Asma'u tabarsa yatashi, fitowa yayi wajen Mukhtar, hannu yabasa suka gaisa sanan yamasa bayanin ga doctor Al-ameen nan zuwa. OK Abokina ngd sosaifa, ALLAH yabar zuminci. Abokina aii babu godiya tsakaninmu, munrigada munzama d'aya, ciwon madam kodai munsami baby ne?. Dariya ya Umar yayi yana fad'in abokina baby kuma? A INA?. Hhhh babu wani baby abokina, zazza6ine kawai wlhy. To shikenan ALLAH ya k'ara sauk'i, cikinma muna addu'ar zuwansa nan kusa. Murmushi kawai ya Umar yayi batareda yace komaiba. Babu dad'ewa saiga doctor Al-ameen ya iso, suna gaisawa ya Umar yamasa iso zuwa cikin d'akin Asma'u. Har yanzun kuka takeyi da surutanta, ya Umar yazauna Kusada ita, yayida doctor Al'ameen ke a zaune bisa wani tum-tum da lubna bata d'aukaba, Mukhtar kam na tsaye daga k'ofa. Tambayoyi yamata tana basa amsa, amma fad'i take pls doctor kada kamin allurafa. d'an dariya doctor Al-ameen yayi, ya ce, "madam kina tsoron allurane?." Kanta ta jinjina alamar a'a, cikin muryar Mara lafiya ta ce, "doctor banasone kawai." Gashi kuma dolene amiki ita, Dan teiport nadamunki sosai. K'an k'ame hannun ya Umar tayi sosai tana fad'in pls Yaya kace karyamin banaso. Harararta yayi danshi surutun yafara bashi haushi, yanada kishi sosai. Magun guna yabata sanan ya ce, "zai mata alluran dabata so d'in. Hawaye tafara zubarwa Rana k'ara k'ank'ame ya Umar tamkar zata koma cikin jikinshi. Kamo hannunta yayi yamik'ama doctor Al-ameen Wanda yake rik'e da igiya dansan d'aura mata yanemo jijiya. Igiyar ya d'aura mata, cikin sa'a aka samo jijiyar. Hawaye takeyi sosai Rana k'ara k'ank'ame ya Umar. Tana ganin yanufota da allurar yak'ara sautin kukanta, taso tabama Umar dariya amma saiya gimtse, doctor da Muktar kam saida suka murmusa. Wata uwar harara da ya Umar ya galla matace tasakata nutsuwa waje d'aya, amma hawayen basu daina zubaba. Tanaji tana gani akamata allurarnan, har aka gama tana k'ank'ame da ya Umar. Doctor ya kalli ya Umar ya ce, " Alhaji insha ALLAH zazza6in zai sauk'a, taci abinci tasha maganidai, ammafa idan har zuwa yamma akwai Matsala saika kirani. Okey doctor ngd sosai ya Umar yafad'a yana bashi hannu, saida suka rakashi har motarsa sanan ya Umar yadawo Muktar kuma yashiga gidansa. Babu dad'ewa saiga matan Muktar Sadiqqa tashigo gidan, lokacin ya Umar na k'ok'arin had'ama Asma'u shayi. Gaisuwa sukayi da ya Umar, ta tambayeshi mai jiki, sanan ta ajiye kular abinci data kawo. A'a Maman Faisal abokina yatadoki ko?. Lah babu komai wlhy, aii kawai kama koma shagon saina lura da ita, abincima nanan na ajiye a shop d'in. A'a aii hidimar tayi yawa Maman Faisal. Wlhy babu wani yawa Indai ba rainawa kayiba. Mik'ewa ya Umar yayi yana dariya, ni na' Isa?, aii sadai nace ALLAH yasaka da alkairi yabar zuminci kawai. To Ameen. Yana fita saddiqa tashiga hidimar bama Asma'u abinci, saiga Rafi'a da ya Umar ya kar6eta ya ce, "tashigo gida. Atare suka gyara gidan tsaf, bayan Asma'u taci abinci Saddiqa tasakata tayi wanka tasha magani, sanda tafito angyara d'akin tsaf, saikawai tasaka wasu kayan takuma kwanciya sai barci. Saida suka gama komai sannan Maman Faisal tawuce gida, Rafi'a kam saida tamusu abincin dare takuma gyara gidan tsaf sannan tawuce gida Dan tanaso taje islamiyya. Ya Umar yanata zagayata danyaga yajikin, amma har yamma bata farkaba. Sai bayan isha'i daya shigo yataradda ta tashi. Kintashi?. Kanta tad'aga masa, har yanzun tana cikin bargo. To yajikinnaki?, da sauk'i amma har yanzu inajin sanyi wlhy. Zai daina shima, tashi kiyi sallah ko?. Nanma kanta ta jinjina sannan ta yatsina fuska, yaya dama akwai ruwan zafi sainayi dashi, bazan iya da ruwan sanyiba. OK bara naduba ko Rafi'a tazuba a filas. Rafi'a tawucene?. Eh tun d'azun tawuce, tanason zuwa islamiyya tace. Batace komaiba, shima yafita yakawo mata ruwan zafin, dakansa ya taimaka mata zuwa bayi, tsayawa yayi kanta yak'i fita. Tajuyo tana kallonsa kamar zatayi kuka, kafita to. Gira yad'age sama tareda d'an langa6e kansa gefe, bazaki iyayi agabana baneba?. Gyad'a kanta tayi cikeda shagwa6a. Murmushi yayi, ya jingina da bango harda hard'e hannu ak'irjinsa yana kallonta. Ta marairaice murya tana k'ank'ame jikinta, yaya sanyi nakeji wlhy, kuma zanyi fitsarin atsaye... d'an zaro idonsa yayi waje, ya CE, "da gsk?." ALLAH kuwa. Murmushi yayi mata sannan yafice batareda yace komaiba. Tana idar da sallan takuma zuwa zata kwanta, rik'o hannunta yayi yana fad'in no zauna ki huta. Wayyo ya sanyi fa. Toni wannan sanyi namiyene? Dayak'i tafiya. Bara nakira doctor namasa bayani...... Kafin Asma'u ta ce, wani Abu saiga Faisal (babban yaron Muktar), rissinawa yayi ya gaidasu, yayma Asma'u sannu, sanan ya ce, "uncle Abba ya ce, "kakawo key d'in shop yazauna, kaikuma kazauna wajen aunty. To yarona ALLAH yayimaku albarka kaji, gashi kacemasa ngd. Rissinawa yayi yakar6a yafita. Shikuma yashiga kiran doctor. Bayan sun gaisa yaymasa bayanin harfa yanzu Asma'u tanajin sanyi. 'Yar dariya doctor yayi, ya ce, "wanan aikinkane Alhaji, indai babu zazza6in to Alhmdllh, maganar sanyi kam tana buk'atar d'umin jikinkane kawai. Da sauri Asma'u da ya Umar suka kalli juna Dan yasaka wayarne a Hans Free. taja bargo ta kwanta, shikuma yad'auke idonsa daga kanta yamaida hankalinsa akan maganar doctor. Okey doctor babu damuwa ngd sosai, saida safe. ALLAH yakaimu Alhaji, agaidamin da madam. Okey zataji, agaida iyali. Koda ya Umar ya kammala wayan baikalli Asma'u ba yatashi yafice, itako tak'ara k'udundune kanta a bargo, tamkar wadda ake shirin sacewa. Waje yaje wajen Muktar, saida sukad'anyi magana ta mintuna sannan yadawo gidan. Kaitsaye d'akinsa yanufa, yay wanka tareda shirin barci tsaf sannan yakoma d'akin Asma'u. Harma tafara barci ita. Yad'an dad'e akanta yana k'are mata kallo cikeda tunani kala-kala tamkar bayason abinda yay niyyar yi agareta na bata taimakon da doctor yabashi shawarar. Tsawon mintuna sannan yazauna abakin katifar tareda d'aga bargon yashiga ahankali. Jawota yayi ya manna da jikinsa, wata sassanyar ajiyar zuciya ya sauke tareda rinmtse idanunsa. Itakam sai kawai tagyara kwanciyarta danjinta cikin wani lallausan jiki, gawani d'umin mai dad'i da k'amshi. Barcin yaci k'arfinta shiyyasa ko farkawama batayiba. Amma ga mutumin naku ba haka baneba, jinsa yakeyi tamkar bashiba, tuni yasan shi mutumne mai yawan buk'ata shiyyasa yake tausayin fara kusantar Asma'u, amma yazaiyi? Zuciyarsa takasa daurewa, akwana biyunnan hak'uri kawai yakeyi. Yanason kasancewa da matarsa amma yana gudun karkuma ta rainashi. Yakuma k'ank'ame ta sosai tamkar za'a kwaceta daga gareshi, jin anrik'eta tamau yasakata motsawa, shima saiya sassauta mata. Addu'a yamusu ta barci, tanata barcinta amma shi yagagara yin nasa saboda kwad'ayin kasancewa da ita................ *_"ngd duknaga sak'on gaisuwarku, harma damasu kirana, harma wad'anda basu sami damaba, dukna gode ALLAH yabar zuminci, nama warke, ammafa ina jiran kazar😋😋🤷🏽‍♀😄"_*. Luv you all💋💯 *_Luv you all_* *_(((S))).......2017_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→35-36_* .......Haka yayta zagaye d'akin yana surutai, saida yagaji Dan kansa sanan yashirya cikin wankan k'ananun kaya yafito sai baza k'amshi yakeyi. Idan kaga ya Umar saika d'auka irin matashin saurayinnan ne dabai wuce 26 ba, yanada tsafta Da son k'amshi sosai. Atsakar gidan Yakuma tarar da su Asma'u, wadda tun d'azun tadawo wajen Maman Faisal. Saina dawo yafad'a yana k'ok'arin ficewa. Adawo lafiya sukafad'a suduka, shikuma yafice. Yana fita Maman Faisal tashiga yima Asma'u fad'a (Dan ta girmeta gsky, zata iya zama sa'ar Anty saratu ma). Haba Asma'u yanzunan mijinki zai fita bazaki masa rakkiyaba? Idanfa kika saka wasa wata zatazo ta kwace miki miji. Nakula kinada sakaci sosai. Hakamafa d'azun abirkice kika fito, kamar wadda taje wajen dodo. Kodai akwai matsalane?. Girgiza kai Asma'u tayi, Dan aganinta baikamata tabama Anty Saddiqa labarin abinda yafaru itada ya Umar ba. Maman Faisal tacigaba da fad'in to gsky ki gyara kinjiko. maza sunason ana kula dasu tamkar kwai a cokali. Indai kinama namiji haka to tabbas zai koma miki tamkar jinjiri wlhy. Hakane anty amma wlhy ya Umar daban yake, yacika tauri dayawa. Wani lokacinma dolene kiji matuk'ar tsoronsa. Hummm Asma'u kenan, duk taurin namiji mace saita sakashi laushi. Shawarar dazan baki ki fara karatun Hausa Novels, insha ALLAH zaki k'aru matuk'a da ilimin zama da miji. (Musamman idan kin had'u da buk d'in marubutan dasuka san Kansu) akwai wasu buks dana karanta na bilyn Abdul, na tabbata zaki k'aru acikinsu. To a ina zan samu?. Bak'yayin charting?. Inayi da, amma yanzu banayi. Tom Indai ba mijinki ya hanakiba kikoma yi zan baki no. d'inta. To Anty ngd sosai. Maman Faisal tamik'e dak'yar saboda tsohon ciki datakedashi, haihuwa yau ko gobe, bara naje gida, nasan sunacan sunamin 6arna tunda sukak'i dawowa. To Anty ngd..... .................................. Su Lubna anata hidimar biki, shiri sukeyi na garari Dan bikin namasu akwaine babu k'arya. Komai awadace yake tafiya, party kam aii anshirya yafi kala 10, su Lubna sune amarori k'irjin biki. Yau kamu Dan haka sukaci uwar kwalliya nawani sky blue d'in less itada Suhaima, sai walk'iya sukeyi, idan kagansu kai kace sune amaren, bakowa zaiga Lubna ya ce, "ta ta6a aureba bareba harda yara biyu. Harabar gidan suka fito inda abokan Ameer suke birjik, duk sunci wankan bak'in wando da yellow d'in Riga, wanan shine kwalliyar kamu na maza. Matankuwa yellow d'in wando da bak'ar riga. Sudai su Lubna basu sakaba. Wani abokin Ameer ya ce, " kai yarinyar canfa tawuce dani wlhy, wai k'anwar Amee CE?. Inaganin k'anwarsace, ammafa in k'aramar tafimin k'yau, kasanni ko aure zanyi banason yar 20+ gsky. Nafison daga 16 zuwa k'asa. Dariya abokin yayi, ya ce, "humm aikai mugunta kakeji....... Wucewarsu Luban tagabansu tahanasu cigaba da hirar. Sukam basusan sunayiba, sun wuce sun barsu da k'amshinsu. Mota suka shiga, Lubna tajasu suka bar gidan. Kaitsaye hall d'in daza'ayi kamu suka nufa. Dangin amarya Suma sunyi shirinsu sosai, amarya tad'auki k'yau, naira tayi kuka agidannan. Su Lubna sai nan nan akeyi dasu, sukuma suna fankama da Nuna isa, su adole dangin miji. Babu dad'ewa su Ameer suka iso. Ba awani tsaya 6ata lokaciba aka fara gudanar da kamu Wanda yak'ayatar. Sai wajen 9pm aka tashi, ansha casu kam babu k'arya. Idan kuga yanda Lubna tadage tana rawa saikusha mamaki...... ____________________ Tunda Anty Saddiqa tafad'a mata idan tana sakaci wata zata kwace mata miji tashiga damuwa, tana matuk'ar son mijinta, tanajin ya Umar yafi sauran maza awajenta, idan akace wata zata iya kwaceshi agareta takanji tamkar an soki zuciyarta da mashi. Wasu zafafan hawaye suka gangaro bisa kumarunta. Bata sharesuba, saima cigaba da matso wasu datayi. Duvanta takai ga agogon d'akin, karfe 9:23pm amma har yanzu ya Umar bai dawo gidanba, tun fitar d'azu da yamma. Tana mamakin ina yajene har zuwa wannan time d'in?. (Zuciyarta ta ce, ''yaje tad'i.") Rushewa tayi dawani kuka mara dalili.... Ni dariyama tabani aradu😂. Tana nan tana kukanta saitaji motsin bud'e k'ofa, da sauri tad'ago tana kallonsa. Ya Umar ne sanye cikin kayan barci, da'alama ma yadad'e da dawowa gidan. Shima kallonta kawai yakeyi amma fuskarsa ko kad'an babu walwala. Cikin d'akin yak'araso, yaja tum-tum yazauna har yanzu idanunsa akanta. Itadai nata na k'asa, ga hawaye sha6e- sha6e a fuskarta. Ahankali ya firzo huci daga bakinsa yana mai kauda kansa daga gareta. Ko kad'an bayaso yaga mace na kuka. Shi mutumne mai tausayi sosai musamman akan mata. Yakuma dawo da kallonsa gareta, kukan mikikeyine? Ko har yanzu bakida lafiyar?. Shiru tamasa, bata d'agoba, bakumata tanka masaba. Dan zuciyarta wani irin zafi takeji, gani takeyi kamar da gsk daga tad'in yake. Cikin d'an fad'a-fad'a ya ce, "wai bakijinane!!?. Da sauri tad'ago takalleshi, ganin yanda yakuma tur6une fuska sai tsoronsa yakuma kamata. Bakinta na rawa ta ce, "bakaine kaje tad'iba." Tad'i!?. ‘ya Umar yafad'a cikin sigar tambaya da mamaki.’ Itama kanta tad'a tana wani kumbura baki. Siririn tsaki yayi, amma batajiba. Ya ce, "kewaye yagaya miki naje tad'i?. Gabantane yafad'i, dan kuwa dai zuciyartace ta sak'a mata, bawanine yafad'a mataba. Shima ganin haka sai kawai ya girgiza kai. Yakuma yin k'aramin tsaki tareda fad'in kinga ni bar wannan banzan shirmen naki gefe, magana nazo muyi. Tashi kije ki wanke fuskarki kidawo. Ahankali tamik'e kamar wadda kwai yafashema aciki tashiga bayi. Fes tawanke fuskarta sanan tadawo gareshi. Saida sukaja wasu 'yan mintuna sannan yay gyaran murya:- inaso kibani hankalinki nan muyi magana. Kanta ta jinjina masa alamar to. _d'azu fitar danayi naje office d'in su muktar ne, dama tun kwana hud'u daya wuce munyi magana, ya ce, " nabada takarduna zai kaima ogansu yanemamin aiki. Dafarko ban aminceba Dan narigada na fidda raina ga aikin. Amma saiya nace sosai da magiya da kawomin hujjoji akan fa'idar Neman aikin harna amince. Jiya yakai takardun, yaukuma ogan nasu saiya buk'aci ganina. Shine Muktar yakirani ina shago yasanarmin. Wanna dalilin yasa nashirya naje. Tom saidai kuma abinda yagirgizani shine ogan su muktar abokine ga dad (mahaifin Lubna) akwai dangantaka mai k'arfi a tsakaninsu ta kasuwanci gsky, Dan sanda ina k'arkashinsa yasha aikena awajensa. Abu na biyu kuma shine Alhaji Ahmad mai kano yad'aukeni aiki ak'ark'ashin kamfanin nasa, ya ce, "kuma yana buk'atar bayani daga gareni akan abinda yasa muka rabu da mahaifin Lubna. Yabani dama daga nan zuwa gobe, idan nafad'a masa yace zuwa Monday zan fara aiki. Yakika gani nafad'a masa gsky?, kokuwa na hak'ura da aikin kawai?. Ban fad'ama kowa maganarnanba saike, koshi Muktar baisan yanda mukayiba. Asma'u tasauke ajiyar zuciya sanan ta gyara zama. Yaya nidai abinda nake gani kafad'a masa kawai, Dan ALLAH yagani bacin amana ko cutarwace taravaku da mahaifin anty Lubnar ba, yanzu kuma aiki za'a d'aukeka idan kayi kuma za'a biyaka, kaga kuwa guminka zakaci bawai a k'ark'ashin wani zaka zaunaba. Kuma ina ganin koda kafara aiki tom nikuma saina cigaba da lura da shagon harmuga abinda ALLAH zaiyi. Sosai ya Umar yagamsu da bayaninta Dan haka ya jinjina mata kai alamar gamsuwa, gawata k'aunarta na ratsashi, wani lokacin idan tayi Abu tamkar wata babba. Idan shirmen yamotsa kuma sai an sauke masa cikin tirela😂. Asma'u tayi murmushi mai kwantar da zuciya, ya Fharuk natayaka Murna, ALLAH yabada nasara da sa'a. Ameen Husna ngd. Filo yajawo ya kwanta. Gaban Asma'u ne yafad'i, karfa asake irin ta ranar. Kamar yasan tunanun datakeyi saiya mik'e zaune yana fad'in yau baza'a bani abinci bane?. Da sauri Asma'u tamik'e, Dan danan tacika gabansa da kulolin abinci, tashi yayi zaune tazuba masa komai. Yanzukam babu laifi yad'an saki fuskarsa, Dan yanacin abinci yana satar kallonta. Sukan had'a ido lokaci-likaci, ganin haka ya Umar yad'auke idonsa gaba d'aya daga kanta yamaida ahankali kan cin abincinsa. Kamar daga sama yaji Asma'u ta ce, "ya Fharuk inada tambaya?." Idanunsa masu haske yad'ago yana kallonta, saida ya had'iye abincin bakinsa sannan ya ce, ''ina saurarenki?." Shiru nawani lokaci tanata juya maganar a zuciyarta, kamar tayi kamar kartayi, can wata zuciyarta na angizata akan ta tambayesa da ace tazauna cikin duhu. Jin tayi shiru yace yadai? Kokin fasane?. A'a. Dama inason tambayarka minene maganin mata?. Sosai ya ware idanunsa akanta. Aransa yace mike damun kan yarinyarnan?. (Inhar bai mantaba Lubna ta ta6a fad'a masa kayan k'arin ni'ima sune ake kira Maganin mata. Dan yata6a rutsata tana sha saiya tambayeta maganin minene wannan?. Dayake Lubna macece da batada kunyar Abu kai tsaye, musamman ga mijinta, sai takecemasa maganin k'arin ni'imane).......... Ganin yayi shiru yadaina cin abincin, kuma gashi ya tsura mata idan ko k'yaftawa bayayi saitasha jinin jikinta. ad'arare ta ce, "ya Fharuk akwai matsalane?. Girgiza mata kai kawai yayi yacigaba dacin abincinsa, Dan aganinsa dawata manufa daban tamasa tambayar, ashema k'aryar gudunsa takeyi, tasan komai, tana raina masa hankaline kawai. Wani d'an murmushin gefen baki yayi, shikad'ai yasan miya kitsa wa zuciyarsa. Asma'u kam tayi gum, Dan sosai tasha jinin jikinta akan tambayar. Harya kammala cin abincin babu maicewa da d'an uwansa k'ala. Bayan ta gyara wajen ta kwashe kwanikan tadawo d'akin. Inda tabarsa anan ta iskesa. Ya ce, " kinason amsar tambayarki?. Kanta ta jinjina da sauri. Yalumshe idanunsa yana wani murmushi na musamman Wanda Asma'u bata ta6a gani daga gareshiba. Zan baki amsar tambayarki amma nima zan tambayeki Abu biyune, idan kinsani bazan amsa mikiba. Idan baki saniba zan had'a duka nabaki amsa, amma bayauba, zan baki amsar Abu d'aya a daren yau, biyun kuma saida safe. Bata kawo komai arantaba ta ce, "to ina saurarenka. Mizakiyi da maganin mata?. Na biyu:- miyasa kika tambayeni. Gefen wuyanta ta Sosa Dan batasan amsar dazata bashiba. Ganin haka ya ce, "shikenan, tashi kiyo alwala zan baki amsar farko dakika tambayeni............... _kuyi hak'uri danifa, yanzu bakwajina yanda ya kamata, wlhy nayi matuk'ar busy ne kawai, kutayani da addu'ar samun nasara kawai._ *l Love you all*😍 *_((S)).....2017_* *_luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→37-38_* ..........Bata kawo komai arantaba tatashi zuwa Bathroom, babu dad'ewa tafito d'aureda alwala. Ya Umar baya d'akin, da alama shima yaje d'auro Alwalane. K'ok'arin canja zanin sallah tafara, saigashi yashigo. Babu Wanda yace da d'an uwansa k'ala. Ya Umar yad'auki sallaya ya shimfid'a musu guda biyu. Sallah suka gabatar raka'a biyu. Ya Umar yadafa kanta yay addu'a kamar yanda addinin islama ya koyar mana. Sai ayanzu wani tunani yazo zuciyar Asma'u. Gabanta yashiga fad'uwa da dukan tara-tara. Duk addu'oin dayaketa kwararawa bata fahimtar komai, kawaidai tad'aga hannunta samane. amma ko ameen tagagara furtawa. Nashiga uku ni Asma'u! Shin mi ya Fharuk yake nufine? Nidai nasan wannan sallace da MAZON ALLAH (SAW) yakoyar damu muyi aranar da aka kawo mace amatsayin amarya. To amma shi ya Fharuk miye tasa manufar?. ‘wani ras gabanta yafad'i yayinda zuciyarta tabata wata bahaguwar amsa.’ Bata dawo hayyacintaba taji ya Fharuk na girgizata. "K!. Tunanin mi kikeyine haka?. Firgigit tadawo hayyacinta, sai mazurai takeyi da idanu. Murya na rawa ta ce, " ya Fharuk mizai farune?." Kallonta yayi kamar zaiyi magana, saikuma yafasa ya mik'e, saida yazauna abakin katifar sannan ya ce, "mizai faru, kamarya?. Shiru tayi Dan gane kato6arar datasoyi. Baikamata ta nuna masa tama fahimci wani abuba, tunda yamaidata k'aramar yarinya. Itama bara zata nuna masa tanada wayo fa. Bai kuma cewa da ita komaiba taga yad'auki keys d'in shago yafita. Ta k'ofar cikin gida yabud'e, mintuna kad'an yadawo hannunsa d'aukeda yogot mai sanyi. Sau d'aya takalleshi ta kauda kanta. Shima zama yayi da yogot d'insa ahannu. Husna bani kofi biyu. Tashi tayi tamkar mara laka ajiki tafita batareda tayi koda tariba. Ya Umar yabita da kallo yana murmushin mugunta, 'Yar rainin wayo zaki fad'a musu yau da bakinki. Kigama wani langa6e-langa6en jikinki yau babu fashi saina mire sadakina. Haka Asma'u tadawo da kofuna jiki duk a sanyaye. Tanata tunanin abinda zatayi Dan ku6ta daga tarkon ya Fharuk. Kofunan yakar6a a hannunta, yazuba musu yogot mai dad'i, sai k'amshi yakeyi tamkar na kwakwa da abarba. Yacika Kofi d'aya sannan yamuk'o mata. Bismillah. Fuska ta yatsine sosai, kaikace batada lafiya. ya Fharuk nak'oshi, ni koma abincin dare banciba saboda cikina yanamin ciwo sosai. Dariyace taso kwacema ya Umar Dan ganin yanda Asma'u tawani narke fuska da narke jiki, amma dayake jarumin kamewane saiya dake, aransa ya ce, "zaki fad'a musu yarinya, ak'alla nabaki shekara 15 a duniya, duk wani shirinki a tafin hannuna yake. Amma afili saiyayi murmushi, ayya Husna sannu kinji, kar6a kisha kida kad'anne saina kawo miki magani. Ciwo bayason zama da yunwa aii. Shiru tayi tana satar kallonsa, kardai yagano shirinta shima?. Jin sanyi a hannunta ya katse mata tunani, kofin yogot d'inne yasaka mata ahannnu. Suka had'a ido, yad'age gira d'aya yana kallonta da ido d'aya, kona baki da kainane? Naga kamar kinajin jiki sosai. Ahankali ta kad'a kanta alamar a'a. Shima murmushi yayi yaja Kofi yazuba nasa. Hankali kwance yakeshan abinsa. Itakam Duk a d'arare take. Dukma zamansa a d'akin ya gundureta, tak'agara yagama yatafi. Amma amamakinta koda ya kammala saitaga yayi mik'a tareda zamewa ya kwanta akatifarta yana fad'in Alhmdllh. Tana nan tana cancana yogot d'in tamkar maiba yaron goye abinci har nawani adadin mintuna. Ganin shan yogot d'innata bana k'are bane yasa ya Umar mik'ewa yafita. Kamar yasan mitake shiryawa a zuciyarta yacire key d'in k'ofar yatafi dashi. Yana fita ta tashi da sauri danufin kulle k'ofa amma saitaga wayam babu key. Wani haushi da tsoro suka kamata lokaci d'aya, afili ta ce, "wayyo ya Fharuk dama mugunta ka shiryamin? Sai hawaye sharrrrr akumatu. Ganin kuka bazai mataba ta tuna dawani d'an kwalbar turare da Anty Saratu tabata ta ce, " tayi amfani dashi Daren farkonta bazata sha wahalaba. Cikin saurinta kuwa tafara lalubarsa, ALLAH kuwa yabata sa'ar ganinsa harma dawasu daban, bata ta6a amfani dako d'ayaba. Shid'in kawai ta d'auka sai wasu turare guda biyu masu fitinannen kamshi. Da hanzari tad'auka tashige bathroom. Duk yanda Anty Saratu ta koya mata haka tayi bayan tayi brush ta matsa ma bakinta wani Abu maid'an karan k'amshi. Sosai tagyara jikinta dukda tanata addu'ar ALLAH ma yasa karya dawo d'akin. Rigar barcin data d'akko maid'an kauri tasaka saboda yanayin sanyi da'ake ciki. Agurguje tagama tadawo d'akin, katifarta ta haye, yau babu zancen doguwar addu'ar barci. Dandanan ta kammala taja bargo ta k'udundune har kanta, ita adole barci takeyi. Shiru har minti kusan 20 suka shud'e kamar ya Fharuk bazai dawoba. Harta fara murnar rashin dawowarsa taji anturo k'ofa dawani fitinannen turare. Tasan ya Fharuk a 6angaren k'amshi babu sanya. Dukda k'irjinta na dukan uku-uku saida tayi murmushin jin dad'in k'amshin mai saka nutsuwa da farinciki........... Jin shigowarsa bargon gabanta yasake sabon salon lugude. Da Sauri tamatsa danjin ya mannata da jikinsa. Murya a raunane ta ce, ''ya Fharuk! Lafiya kuwa?." Lafiya k'alau, miya farune?. Um....um...dama naga kazo nanne, yau bakajin barcine?. Inaji mana Husna!, bagashi Nazo zanyiba. Idanu ta kwalalo waje, kasancewar akwai wuta, kuma baikai ga kashewaba yaganta sosai yanda take zare ido kaikace taga wani ojujune. Ya Fharuk kana nufun anan zaka kwana?. Umm. Kenifa kincikani da surutu. ranar dabakinki kikacemin kinajin sanyi, damma Nazo na taimakeki shine zakimin salo?. Baki Asma'u ta turo gaba, afili ta ce, "yo aii ranar kace, nikuma yau sumul nake, babu abinda ke damuna. Humyim dama d'azu k'arya kika zabgamin wai bak'yajin dad'i ko abinci bakiciba cikinki na miki ciwo?. Asmah arink'adaijin tsoron ALLAH. k'arya batada k'yau. K'ara turo baki tayi gaba. Shikuma yasaka d'anyatsa ya d'alli bakin. Da sauri tadafe bakinta hannu tana kukan ta6ara wai zafi. Baikuma bi takantaba harya mik'a hannu yakashe fitilar d'akin. Asma'u batason duhu, shima kuma sarai yasani amma yakashe Dan Neman magana. Tana ganin duhu tak'ank'amesa da sauri. Wayyo ya Fharuk kataimaka ka kunna, ALLAH bazan iya barci cikin duhuba. Kunnenta yalaluba, ahankali yake mata magana. Karki damu da duhu My Noor, kid'auka nine fitilarki, zakiga haske ya mamaye d'akin.. Yarrrrr tsigar jikin Asma'u yatashi saboda salon da ya Fharuk yake mata magana akunne. K'ok'arin barin jikinsa tafarayi. yakuma ruk'ita da k'yau yanda bazata guje masaba. Fitinannan k'amshin jikinta yake sunsuna. Wannan wane irin turarene kika saka Husna;?. ‘yay maganar murya asark'e, tamkar mai shirinsa yin kuka.’ Itama cikin Rawar murya data jiki ta ce, " turarene kawai yay.........." Batakai ga k'arasawaba ya manne bakinsu waje d'aya. Itakuma rawar jikintane yak'aru, dukda jikinta yana kar6ar sak'onninsa 100%, amma zuciyarta na razanar da ita wahalar dazata sha. Wannan yasa tafara kuka wuywuy da mutsu-mutsun kwace kanta. Gogan naku kam aii abin nema yasamu, aikin gabansa kawai yakeyi, yanda yake cikurkud'a Asma'un kaikace baita6a kusantar wata maceba a duniya. Nidai bilyn Ku sim sim nafito gudun aikata laifin kallon k'urulla🚶🏻‍♀.............. _kuyi hak'uri da wannan_.😻 *_Nagaisheku da k'yau 'yan group d'ina, ALLAH yabarmu tare.🙏🏻 irin tamau-tamau d'innan😉😻._* *_(((S)))........2017_* *_Luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→39-40_* ..........Idanun Asma'u biyu aka kira sallar Asuba. Amma koda motsin kirki takasayi daga inda take. Ciwon jiki da zafi a k'asanta duk sun addaba mata, sun taru sun zubar matama da zazza6i. Ga kukan datasha adaren jiya. Ya Umar kuwa barcinsa yakeyi sosai, shima barcin baiwani dad'e da d'aukarsaba saboda kukan da Asma'u takwana tanayi. Shikuma yana aikin lallashi. Sai wajen k'arfe 3 da 'yan mintuna barci ya saceta, shima yasamu yayi nasa. Ita dayake barcin wahala tayi, saita rigashi farkawa da wuri. Har aka fara kiran sallar farko ya Umar bai motsaba, itama Asma'u barcine yasake saceta.(kunsan dai aikin shaid'an). Wannan barcine yakaisu har 6:48 na Safiya. Ya Umar ne yafara farkawa ayanzunkam. Ganin haske ya yawaita, yasakashi mik'ewa zumbur, bakinsa d'aukeda addu'ar tashi barci. Innalillahi yashiga ambata Dan ganin agogo. Baima bi takan Asma'u ba yashige bayinta, wanka yayi agaggauce yad'auro alwala yafito. Jikinsa sai rawa yakeyi, arayuwa yana matuk'ar shiga damuwa idan lokacin sallah yawucesa. Hakan na 6ata masa rai. Anutse yagabatar da sallar Asubahi, yanamai cigaba daneman gafarrar ALLAH na jinkirta yinta akan kuskuren barci. Saida ya kammala hankalinsa ya kwanta yadawo kan Asma'u. Dubansa yakai gareta, anyi sa'a kuwa fuskarta tana fuskantarsa. Wani k'asaitaccen murmushi yasaki yana wani lumshe idanu, ahankali ya furta Husna daru kenan!, ALLAH yay miki albarka, ya dawwamar da ruhinki cikin farinciki, kamar yanda kika sakani adaren jiya. Nidake la6e agefe na ce, "ameen ya Umarin mu."🤸🏻‍♀😻 Tashi yayi daga kan sallayar yakoma kan katifar ya zauna saitin fuskar Asma'u. Sosai ya tsira mata idanu tamkar yau yafara ganinta, jiyake wata k'aunarta naratsa 6argonsa da jinin jikinsa. "ada yaso Lubna harma yake ganin bazai ta6a son wata mace bayan itaba, amma zuwa wannan ranar labarin yasha banban, dankuwa jiyake abayama baiyi wata soyayyaba, yanzune zaisan miye soyayyar, yanzune zai amayar da ita inda yadace, yanzune zaisan miye farinciki acikin soyayya. Ahankali yakai hannunsa saman d'an bakin Asma'u daketa barcinta. Zagaya d'an yatsansa yakeyi akai cikeda shauk'i. Sannu ahankali Asma'u tafara motsawa harta bud'e kumburarrun idanunta akansa. Suna had'a ido tamaida nata idanun tarumtse gam. Murmushi yayi tareda fad'in haba my Husna! bud'e idanun mana. bud'e ki kalleni da k'yau ni nakine ke kad'ai, zan kasance dake har Abadan Hayatee na. Wani sanyin dad'ine ya kwarara azuciyar Asma'u, itakam yau wace irin godiya zatama Ubangijin talikai mai sassauya al'amura. Yanzunan ya Umar ne dabakinsa yake furta mata kalmomin nan? Ya Umar d'innan mai tsada da aji mijin Anty Lubna? Ya Umar d'innan da sonsa yazama garkuwar farincikinta tun tana k'arama? Ya Umar d'innan da takema kallon Wanda yafi k'arfinta abaya? Ya Umar d'innan daya mallake zuciyarta da dukkanin komai nata batareda yasan tanayiba? Ya ALLAH kaine Sarki mafi Girman iko da Rahma, ALLAH Kaine kake bayarwa ka k'ara batareda ka k'osaba.........hawaye sosai keta kwarara a kumatunta. Ya Umar yakuma matsawa gareta zuciyarsa dukba dad'i, azatonsa har yanzu kukan abinda yay mata takeyi. Rungumeta yayi tsam ajikinsa, murya a raunane ya ce, "kiyi hak'uri my Husna! nasan ban k'yautaba amma ki gafarceni." ALLAH yay miki albarka, kisaka azuciyarki Umar Fharuk nataredake har Abadan. Yanda kika saka ruhina da zuciyata acikin farinci kema ALLAH ya dauwamar danaki Ruhin a farinciki. I love you so much my Husna. Aii Asma'u batasan sanda tak'ara k'ank'amesaba tana zubda hawayen farinciki. Shikuma yana aikin shafa kanta da lallashi. Saida tayi mai isarta sanna yad'auketa cak zuwa bathroom. Ananfa akeyinta Dan Asma'u bazata iya tsayawa ya Fharuk yamata wankaba. Tun yana had'a ruwan zafin daya d'akko daga kichin tagwada fita daga bathroom d'in, amma kamar yasan mitake nufi ya dinkare ko'ina na k'ofar. Da d'an zafi sosai yahad'a ruwan zafin sannan yadawo da kallonsa ga Asma'u. Suna had'a ido tayi k'asa da kanta tana hawaye. Murmushi yayi ahankali yamatso gareta, murya k'asa-k'asa ya ce, " my Husna kincika shagwa6a. Kodai nakira Inna ko mama?. Sosai tawaro idanu akansa. Saikuma wasu hawayen suka kuma gangarowa. Tunawa batayi sallar Asubaba yasakashi sungumarta yasaka arobar daya had'a ruwan zafin, dama daga Ita sai riga iya guywa. Wani zallo tayi tareda k'ank'amesa tana kuka. Wayyo ya Fharuk wlhy akwai zafi. Innata kice yabarni wayyo ALLAHNA. Sake dannata yayi da k'yau yana murmushin wannan kuka. Afili ya ce, "Husna karfa kisaka gaban inna yayta fad'uwa, tun jiya kiketa kiranta. Ya Isa haka kada ki k'aremin sunan Innata!. Zuwa yanzu tad'an daina mutsu-mutsun tashi, saidai hawayen dasuka kasa k'arewa. Saida ruwan yahuce yakuma zuba ruwan zafi, baibartaba saida ya tabbatar tagasu dak'yau sannan ya ce, "kin iya wankan tsarki?. Kanta tad'aga masa kawai, har yanzu hawaye takeyi. Baifitaba har saida yaga yanda tayi, ya tabbatar tayi dai-dai sannan yanad'ota a tawul ya d'akkota kamar wata jinjira. Akatifar yadireta, yagoge mata jikinta yasaka mata kayan data ware domin yin sallah. K'ara d'aukarta yayi yakai inda abin sallar yake. Baibar wajenba saida ta kabbara sallar. Dawowa yayi inda katifar take, yacire bargon. Ido yazaro waje Dan ganin yanda zanin gadon yad'an 6aci kad'an. Mamakine yakamashi, dama bakowace macece ake ganin jini a Daren farkontaba? Yasan Lubna tagirmi Asma'u amma ita jinin data zubarma har tsoro yabashi a lokacin. Saikuma gashi Asma'u ita babu sosai. Ubangiji mai iko, matanma akwai banbanci atsakaninsu kenan?. *_hattara samari, kudaina d'aukar cewa dolene sai kunga jini adaren farkon matanku zaku yarda takawo budurci cikakke gareku. Mata kala-kalane, bakowacce bace ake ganin jini adaren farkonta. Mutanen da, suna aurar dayara suna k'ananane, shekara 12-13-14 kaga kuwa wad'annan yarane d'anyu dolene a iya ganin jinin. Kuma alokacin matan basa yawan yin abubuwan dazai saka burcinsu yin rauni._* *_ayanzunkam bahaka bane, mafi yawanci ana aurar da mata 18-19-20-21-22+ ne, gakuma abubuwan 'yan matan kanyi dake saka buducinsu yin rauni batareda sun saniba. Yawan d'aukar Abu mai nauyi, horo da ake bama yara a makaranta, hawa mashin, tsallaka kwata, yawan tsalle-tsalle, musamman dayanzu 'yammata suka lalata kansu wajen rawa. Irin wad'annan abubuwan da dama dawad'andama ban lissafoba duk suna saka budurci yin rauni koda mace takasance ma'bociyar kamewa. Mata saimu kula. Kukuma maza Ku fahimcemu, bawai ganin jini face-face agado bane alamar mace takawo cikakken budurci gidan miji. ALLAH yasa mugane, ameen._* Yaye zanin gadon ya Umar yayi zuciyarsa fes babu wani wasiwasi akan Asma'u, domin kuwa shine sheda akan tsam yasameta, bama k'aramar wahala yashaba wajen fasata. Lallai yakamata sauran maza irinsa su fahimci haka suma. Asma'u kam tuni ta idar harta kwanta awajen. wani zanin gadon yasake, dukda wannand'in bai 6aci dayawaba, amma baidace abarsaba. Yana canjawa ya d'akkota yamaida saman katifar dan barci takeyi sosai. Zanin gadon yakai bayi yasaka a bokiti ya wanke tas yaje waje ya shanya. Yana gamawa yadawo d'akin yakwanta tareda rungume abarsa suka koma barci mai dad'i. *_1:4pm_* Sai k'arfe d'aya da minti hud'u ALLAH yabasu ikon farkawa kusan atare, amma Asma'u tariga ya Umar tashi, motsin tashintane ma yatadashi. Tanajin motsin tashinsa ta lafe ita adole barci takeyi. Murmushi ya Umar yayi tareda yimata cakulkuli. Dariya sosai tazo mata, dukda zafin datake d'anji idan tayi motsi babba hakan baisaka ta dainaba. Ganin yanda take dariya yasaka ya Umar dariyar shima. K'ank'amesa tayi sosai tana cigaba da dariyarta dafad'in ya Umar yi hak'uri Dan ALLAH, ALLAH kuwa abinnan babu dad'i. Daina yimata yayi, yajawota jikinsa ya rungumeta tsam zuciyarsa fal farinciki. Sunkai 30minutes ahaka yana gaya mata dad'ad'an kalamai wad'anda suka sakata k'ara ganin kimarsa a idonta. Dama can ita bataji haushinsaba, aganintama hakan zai iya zama sanadin dazaisa ya sota. Sa6anin da da ita keta fama da dakon sonsa a zuciyarta. Bayan wani lokaci yad'auketa cak sai bathroom. Zille-zille tafarayi ita adole bazatayi wanka dashiba. Shikuma yace bata isaba, aii daga yau tarema zasu ringa wanka, danshi hakan yana cikin tsarinsa. Ganin zata fita yad'ebo ruwa yazuba mata ajiki. Dole tatsaya awajen cak, shikuma yashiga yimata dariyar tsokana. Ta6ara tafara zuba masa shikuma yana lallashi har aka kammala wankan yad'akko kayarsa kamar d'azun. Da k'yar tasamu ya yarda yatafi d'akinsa yabarta ta shirya itama. Kowa shirinsa yayi mai k'yau. Asma'u tad'an daure tagyara d'akinta da babban falo sannan tashiga kicin Dan nema musu abinda zasu saka abakin salati. Ganin rana tayi sosai sai kawai tad'ora jalof d'in taliya da dankali. Tasaka busashshen kifin da ya Umar yasaya musu shekaran jiya. Cikin 'yan mintuna k'alilan gidan yacika da k'amshi ainun. Dama Asma'u gwanace a wajen abinci. Ya Umar daya tsaya had'a wasu takardu yay shirinsa tsaf cikin shadda fara tas, dakakkiyar shaddace 'Yar ubansu, yad'inkata tun yana shanawa da naira. Shaddar d'inkin zamanine fetet, tayi masa k'yau aynun, yad'akko bak'ar hula yasaka, yasaka safa da takalmi bak'i sau ciki. Wayyo masu karatu tamkar ba ya Umar dake cikin k'angin rayuwaba. Idan kagansa zaka d'auka har yanzu ajik'e yake da laimar kud'i. Fitowa yayi yanata bulbula k'amshi, tamkar Wanda yay wankan turare. Yalek'a d'akin Asma'u bata nan. Jin motsi akicin yasakashi nufar can. Asma'u dake jera abinci akan tire Dan ta kammala komai tajiyo k'amshin turaren ya Umar ya yawaita awajen. Lumshe idanu tayi ahankali tabud'e akansa, bak'aramin tafiya da ita wankansa yayiba. Shima tayi masa k'yau sosai. K'arasowa yayi cikin kichin d'in ya rungumeta, cikin kunnenta yarad'a mata, haba My Husna! Waya gaya miki amarya na aikin a irin wannan ranar?. Fuskarta tashiga sinnewa a k'irjinsa ita adole kunya. Yad'ago fuskar tata a acikin tafukan hannunsa, idanunsa suna yawo bisa k'yak'yk'yawar fuskarta. Kiss ya manna mata agishi da hanci, ahankali ya furta ALLAH yay miki albarka my Husna. Ina k'yaunarki sosai. Saida ta k'ara sinne kanta a k'irjinsa sannan ta ce, "nima haka yaya ina k'yaunarka." Rungumeta yayi tsam yana juyi da ita Dan murna. Sundad'e ahaka sannan yad'auki tiren abincin sukaje falo. Tare sukaci abincin dukda Asma'u akunyace take, ko ido batason suhad'a dashi. Bayan sun kammala yatayata suka gyara wajen sannan ya ce, " bara yaje wajen Alhaji mai kano, dama k'arfe biyu yace yadawo. Addu'ar fatan nasara da dawowa lafiya tamasa. Shikuma ya ce, "taje ta kwanta tasake hutawa Dan anjima za'a k'ara irin amsar jiya......... Aibata bari ya rufe bakinsaba takwasa dagudu zuwa ciki. Dariya yafita yanayi da jinjina shirme irinnna Asma'u............ *_(((S)))........2017_* *_Luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* *_page→41-42_* ..........Itama daida tashiga ciki gudun nata yabata dariya, Dan haka tayi dariya sosai harda rik'e ciki. ALLAH nagode maka daka nuna min wannan rana mai cikeda tarin farinciki. Wai yau nice da ya Fharuk manne da juna, yana gayamin kalamansa masu dad'i da tsada. Ya ALLAH ka d'orar mana da wanan farinciki har k'arshen rayuwarmu.... Ameen Asma'u. ____________________ Su Lubna ansha shagalin biki, kud'ikam sunyi kuka abikinnan, komai anyishi asarauce. Su Lubna kam ashiga wanan afita wanan. Dama d'inkuna sukayi na garari itada Suhaima. Zuwa yanzu kam amarya tazo gida. Taroma yatashi kowa yakama gabansa. Su Lubna suna d'aki anata zabga barcin gajiya, gidan tsit kamar babu bil'adam acikinsa. Sai can nad'an jiyo hayaniyar su twins ad'akinsu. Can na nufa danna ganema idanuna. Aiko sune suketa tsalle-tsalle agado, duksun hargitsa d'akin. Babu laifi yaran sunyi girma sosai, ga kamanninsu da ya Umar sunfito sasai. Saidai Hassana farace. Usainace dai komai na ya Umar bata bariba, har dariya idan tayi kamar tasa... Barisu nayi nafito Dan inada abunyi..... ____________________ Alhamdulillahi ya Umar yayima Alhaji Ahmad mai kano bayani gamsashshe akan rabuwarsa da mahaifin Lubna. Dayake mutumne mai fahimta, saiya gamsu da komai, yakuma bama ya Umar hak'uri. Kayi hak'uri Umar, da abinda suka aikata maka. Amma inada tabbacin babu laifin Alhaji awannan lamarin, saidai idan matarsace tazugashi. Nasan halinta batada kirki kokad'an, bataso kowa yara6i Alhajin Dan aganinta za'a k'are musu dukiya. Murmushi Ya Umar yayi ya ce, ''to ALLAH ya kiyaye." Ameen dai Umar. Yanzu zaka iya fara zuwa aiki daganan zuwa Monday. Alhamdulillah ngd sosai Alhaji, ALLAH yak'ara bud'i na alkairi. Ameen Umar.. Daga nan Ya Umar yatafi sai kuma gidan inna. Babu kowa a tsakar gidan, sai kaji da su Inna ke kiwo sunata kaida kawo. Yakuma yin sallama ak'ofar d'akin da takalma suke birjik har wajen k'afa shidda. Kusan atare suka amsa. Sannan yashiga. Sannu da zuwa suka shiga yimasa da gaisheshi, yayinda shikuma idonsa kebin Harris da kallon mamaki. Dama yana zuwa gidannan?. Shima kansa Harris d'in yalura da kallon da yayan nasa kemasa, Dan haka yay k'asa da Kansa alamun jin kunya. Inna duk tana kallonsu. Ya Umar yaje kusada inna ya durk'usa cikeda ladabi ya gaidata. Cikin fara'a ta amsa masa da tambayar lafiyar iyali?. Ya ce, komai Alhamdulillah. Asma'u ma na gaishesu. Muna amsawa. Kallonsa yamaida ga Anty Saratu, ya ce, "sarkin yawo kenan, kekam kina iya sati d'aya bakizo gidannanba?.. Kanta ak'asa ta ce, " ya Umar wlhy har sati uku inayifa." Harara ya balla mata, a'a har shekara kinayi, inna ba kwana hud'u dasuka wuce Nazo gidannan natarar da yarinyarnan ba agidannan?. Dariya inna tayi, wlhy hakane Umar, nima yanzu babu jimawa nagama mata fad'an yawo, dan ba abune mai k'yauba. Ya Umar yakuma harararta, mijin nakine sakarai dayake barinki, ke ko saboda yara yawon baya damunki?. To daga yau karna sake ganinki agidannan sainan da wata uku. Idan bahakaba kuma ranki zai 6aci matuk'a. Gyad'a kai tayi dukda hukuncin NASA bawai yamata dad'i baneba, Dan Anty Saratu akwai d'ambazan yawo kamar taci k'afar kare. (Shima mijin NATA bayaso, amma saboda yana matuk'ar sonta saiyake barinta).. Daga nan hira akad'an ta6a, wadda ya Umar bawani saka musu baki yakeyiba sosai, garama idan inna tayi magana. Zuwa can ya ce, "inna Nazo wajenkine." To yaron arzik'i, nima kuwa dama ina nemanka. Saratu da Hasiya, fatee kufita. Amma Harris yatsaya. d'agowa ya Umar yayi ya kalli Harris d'in da yay k'asa da Kansa, Dan bak'aramar kunyar ya Umar yakejiba. Bayan fitarsu Inna ta kalli ya Umar. Umaru! Inaso kabani Aron hankalinka nan, mufara maganar da Harris yazo da ita, dukda nasan bakazomin da sakaren maganaba kaima, amma na Harris ma yanada matuk'ar muhimmanci. To inna ina saurarenku. Inna ta kalli Harris daya marairaice fuska tamkar zaiyi kuka. Harisu taso kazo nan. Jiki a sanyaye Harris yataso, yazo kusada ya Umar yazauna. Inna ta nuna masa ya Umar da ido. Zamansa ya gyara muryarsa na rawa ya ce, "yaya Dan Girman ALLAH kayi hak'uri, ka yafemin duk abinda namaka. Wlhy na tabbata duk gidammu babu mai mana Abu tsakani da ALLAH kamarkai. Abunda yafaru abayama sharrin shaid'anne. Ka gafarceni, insha ALLAH bazan sakeba. Wlhy yanzu ina tareda kai 100%....... Ya Umar yakatseshi da fad'in wai Harris miya farune? Nifa bakamin komaiba wlhy. A'a yaya namaka wlhy, Dan ALLAH karkace ban maka komaiba, idan kace haka zan d'auka bazaka yafeminba. Hummm shikenan Harris nayafe maka, harma sauran, damani banrik'e kowa acikinkuba, saidai inason kuringa fahimtar miye rayuwa akowane yanayi tazo gareku. Wlhy ya Umar nagane kam yanzu. Jiya naje wajen ya Abubakar akan yabani naira dubu goma na kar6o result d'ina. Amma shine ya hauni da masifa wai bashidashi, shima somuke mu karyashi kamar yanda muka karyaka *_KARAYAR ARZEEK'I_* tasameka. Yanzufa nauyin kayan d'akin Mufida yana kansa. Shi wlhy bazai iya da fitinarmuba mudasu mama........ Ya Umar Yakuma katseshi da Sauri, Harris ban ganeba, ansakama mufida ranar aurene? Da har aka fara maganar kayan d'akinta?. Inna da Harris suka kalli juna cikin mamaki.... Har had'a baki sukeyi wajen fad'in kana nufin baka saniba?. Ahankali ya Umar yakad'a kansa tamkar k'aramin yaro. Sallallami inna tafara tana tafa hannu, oni binta wannan wace irin rayuwace haka?. su yaya Kabiru suka d'auki duniyane?. Ammafa ranar da'aka kawo kud'in danaje ban gankaba saida na tambayi Maman taku, shine ta ce, "anfad'a maka amma kace aiki yamaka yawa Abubakar ya wakilceku tunda shine babba. Shekaran jiya kuma daza'a saka ranama saida nayi magana, naga babukai babu iyalinka, nanma tace anfad'a maka harma kazo, anasaka rana wai katafi saboda Asma'u batajin fad'in jikinta. Wani huci mai zafi ya Umar yashiga furzowa daga bakinsa, idanunsa sun kad'a sunyi jajur, yay ka d'a kansa yana ambatar *_" innalillahi wa'inna ilaihirraji'u."_* Ganin haka mama takwalama Hasiya kira. Ta ce, "takawo ruwa mai sanyi. Saida ya Umar yasha sosai sannan hawaye suka fara gangarowa akumatunsa masu zafi kuwa. Babu Wanda yahanashi, Dan hawayen zasu saka zuciyarsa yin sanyi tarage nauyin datayi. Harris ma hawayen yakeyi, danshima yafara fuskantar matsala irinta ya Umar awajen mama da Abba. Kullum saita masa gori baita6a yimusu komaiba itada abba. Inna ta ce, " ya isa haka, kuyi hak'uri, kucigaba dama iyayenku addu'a kunji. Komai zaizama labari. Ya Umar yasauke ajiyar zuciya yana fad'in babu komai mama, yawuce, amma yanzu wane wata aka saka bikin Hamidan?. Nanda wata biyarne Umaru kaji. Murmushi yayi ya ce, "ALLAH yakaimu inna. Kuma insha ALLAH bazan nuna musu nasan komaiba, kaima Harris karka nunama kowa ka sanarmin. Harris ya jinjina masa kai kawai. Daga nan mama tamusu nasiha da nuna musu muhimmancin zuminci da kula dajuna, had'inkai suzama tsintsiya mad'aurinki d'aya. Suduka nasihar tashigesu dak'yau. Sukaitama mama godiya. Ya Umar kuma yafad'a musu shima alkairin daya samu ayaud'in daduk abinda yafaru. Farin ciki sosai suka shigayi, Harris harda rungume ya Umar, shima yarungume d'an uwansa suna farinciki. Bayan sun nutsu ya Umar yace to Dan ALLAH su binne maganar anan kar kowa yaji. Inna ta ce, " hakan yayi Umaru!, koni ban goyi bayan wani yaji zancennanba. Harrisu kakula kaji. Insha ALLAH inna babu maiji wlhy. Amma yaya tunda zaka fara aiki zandawo tsare shagon, basai Asma'u tazaunaba. Murmushi ya Umar yayi, dama bayason zaman Asma'u ashagon Dan yanada tsananin kishi sosai. Godiya sosai da farinciki ya Umar yanuna akan abinda Harris yamasa. Daga nan hira mai dad'i suka cigaba dayi har zuwa wani lokaci sukaima inna sallama suka tafi. Daga nan gidansu suka nufa. Duk afalo suka iskesu har ya Abubakar da matarsa, anbaje alawa da biskit anata rabo. Ya Umar yagaida mama cikeda fara'a, ko kad'an bai nuna musu komaiba, ya Abubakar ma suka gaisa, suma hamida da Rafi'a suka gaisheshi. Matar ya Abubakar sai wani cika da batsewa takeyi ita adole matar mai kud'i. Kota kanta baibiba yamuk'e yamusu sallama. Kowa yayi mamakin da yau bai zauna hiraba, tunda yaga duk suna nan, (kuma kowa yasan ya Umar dason ahad'u gaba d'aya ayi hira) amma yau sai sukaga sa6anin haka. Gashi ko alawa da biskit d'in gabansu bai tambayi kona miyeba, kuma fuskarsa asake babu wani alamar 6acin rai agareshi. Sallama yamusu yafice. Mamadai tasha jinin jikinta, hakama ya Abubakar, dama shine yazuga mama wai kar agayama ya Umar, idanma angaya masa mizai musu? Mutumin da bashida ko sisi. Kayan dake shagon nasa basu wuce na dubu 60 ba gabad'ayansu. Da ire-iren wannan musalan yabige hankalin mama da Abba, ya ce, ''kuma shine zaima Hamida kayan d'aki. Su su Rafi'a basusan ya Umar baisaniba, amma sunsha mamaki dabasuga Asma'u ba awajen saka rana. Daga nan gidansa yanufa hankali kwance. Yana tsaye abakin titi zai tare adaidaita sahu, harma ya tsayar dawata suna ciniki saiga wata ash d'in mota ta giftasu. Har mai motar yad'an wuce saikuma yadawo baya. Horn yayma ya Umar, ya Umar bai d'agoba, dan kokad'an baid'auka dashima akeba. Mai motar nan yasake yin Horn harsau uku. Ganin haka mai adaidaita yayma ya Umar dake k'ok'arin Shiga magana. Malam dakaifa mai motarcan yake. Dani kuma? Ya Umar yay maganar yana lek'o kansa Dan tabbatarwa. Hannu kuwa yaga and'ago masa. Tofa bara naga wanene ina zuwa. Babu damuwa mai adaidaita yafad'a. Ya Umar yafito zuwa motar. Maimota yabud'e yafito yana fad'in *_Umar bin Usman!_* dama rai kanga rai?. Soasai ya Umar yazaro ido waje, Yazeed! Dama Kaine?. Cikin farinciki suka rungume juna. Yazeed ya ce, "Umar ina kashige haka? Nayi nema harna gaji. Natambaya amajillisa su alkasim sunce min suma basusan inda kakeba yanzu, wai tunda mall naka yak'one ka gujesu gaba d'aya. Murmushi ya Umar yayi kawai, ya ce, " Yazeed wannan bamaganar titi bace, kabari next time Idan mun had'u zamuyita. Amma yaushe kadawo k'asarnan?. Wlhy tun sati biyu daya wucefa. Tunda nadawo kaina fara nema awashe gari, naje gidanka akace aii katashi, natambayi abokai sukace basu saniba. Naje gidansu Lubna natarar suna biki. Cikin ikon ALLAH yanzu har zan wuce saina hangoka. ALLAH Sarki Yazeed, yanzu dai ina zamu had'u mai Babur yana jirana. Wai inama motarka naganka zaka hau adaidaita?. Murmushi kawai ya Umar yayi ya ce, "Yazeed kaidai babu abin fad'a abakina sai Alhamdulillah. Yazeed ya jinjina kai, shikenan sallami mai adaidaitar kazo muwuce. A'a kaje uzurinka, baikamata na katse makaba. No. Babu Inda zanje wlhy, nakai Zuhrah gidane suna wani taro a family d'insu. Yazeed yaje dakansa yabama mai adaidaita d'ari biyar sannan ya sallamesa. Mai adaidaita sai zabga godiya yakeyi yatafi. Ya Umar kam yashiga motar Yazeed suka tafi suma.............. *_(((S)))........2017_* *_Luv you all_* 👩🏻‍💻......... 💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎 *_NA_* *_Bilyn Abdul_* *_Sadaukarwa_* _miss Xoxo na_ _Zarah Bukar_ _Ayusher Muh'd_ *_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_* _sak'onki ya iso gareni *Ummu sadeeq* alkairin ALLAH yakai gareki aduk inda kike._ Luv you zam zam😻 . *_page→43-44_* *........Wanene yazeed?.* Yazeed Mudansir kura. shine cikakken sunansa. d'ane ga Alhaji mudansir kura shahararren d'an siyasa kuma d'an kasuwa. Mutumne shi mai gaskya da tsayawa agidansa, wannan shine yabama 'ya'yansa damar tsayawa sukayi karatu, dakuma samun ingattacciyar tarbiyya. Yazeed sun had'une da ya Umar awajen bautar k'asa. Sosai suka shak'u awannan lokacin, dan abotace maicikeda k'auna da gskya acikinta. Bayan kammalawarsu kowa yakoma gida. Akuma wannan lokacinne rashin lafiya takama Alhaji mudansir, aka kaishi k'asar London domin yin jiyya. Yazeed ne yake zaune awajensa. Tundaga lokacinnan ya Umar yadaina samunsa awaya. Har ALLAH ya azurtashi alokacin. Kusan shekara biyu basu sake had'uwaba har akayi bikinsa da Lubna sannan su Yazeed suka dawo. Dawowarsu babu dad'ewa mahaifinnasu yarasu Alhaji Mudansir kura. Tunda ya Umar yaji Rasuwa hankalinsa yatashi, dayake lokacin Yakama k'asa yanada kud'i babu laifi shine yaja abokansa su Dr jafar, Alkasim etc....... Dadai sauransu sukaje gaisuwa. Murna sosai yazeed yayi daganinsu, yabama Ya Umar hak'urin rashin nemansa, sannan suna arikice ko wayar da Number sa ke aciki bai d'aukaba. Ya Umar ya ce, "babu komai yamasa uzuri. Tundaga nan yazeed yazama d'an cikinsu shima, idan yanada lokaci haka zai shiryo yazo majalissar matasan masu kud'in asha hira. Daga nan aka saba sosai. Gafda za'ayi aurensa da Asma'u yazeed yatafi k'asar Indonesia wani course, wanan yasa basu sake had'uwa da ya Umar sai yau.. Wannan kenan *mundawo labari.* Suna tafiya ya Umar yana bama Yazeed labarin abubuwan dasuka faru abaya. Idon Yazeed yayi jajur saboda azabar 6acin rai, yanason ya Umar sosai. Muryarsa cikeda damuwa ya ce, " amma miyasa bana samun no d'inka kusan shekara d'aya kenan?. Hum kabari kawai yazeed, wlhy cire sim cart d'in nayi gabad'ayama na ajiye, nabar na family na kawai, amma na kasuwa bana buk'atar kowa taredani, saboda abubuwan da mutane suka aikatamin. Hakane Umar, d'an Adam sai abarsa da halinsa, kaga yanzu yakamata kagane bakowane ke k'aunarka Dan ALLAH ba saidan kud'inka. Wlhy Umar haka rayuwar take tafiya ga kowa, idan kanadashi saikaga anata sonka, amma dasun k'are sai kowa yafara gudunka. Dan Adam kenan mai manta alkairi. Amma gsky Lubna da family d'inta da Dr Jafar sunfi kowa bani mamaki. Babu komai kayi hak'uri Umar, ALLAH yanason mutane masu hak'uri. Wlhy komai ya wuce yazeed. Yanzu kam bana tareda kowacce irin damuwa. Dariya sosai yazeed yayi, ainasan bazaka damuba tunda kana tareda amarya kanashan amarci. Harararsa ya Umar yayi, yana fad'in aikai dama matsalarka kenan bakada kirki kokad'an. Duk hanyar tsokanar magana kasani. Hhhhhhhh abokina aikaine kanada abubuwan mamaki Dana dariya. Ankawo maka yarinya kanata wani mata mazurai. Kuma babu kunya saika lalla6a daga baya hhhhhhhh. Kai waya gaya maka na lalla6a? Masheranci. Hhh nasanka Umar wlhy sosai. Inaga daga Family d'inka babu Wanda yaymaka irin sanin dana maka. Kaji dashidai masheranci. Saika tsaya munzo gidan. Yazeed yataka burki amatsakaicin k'ofar gidan na ya Umar, jiyayi tausayin ya Umar yakuma shigarsa. Dabadan karyayi kuka akirashi maceba da wlhy saiyayima ya Umar. Lokacin anak'ok'arin shiga sallar La'asar. Ya Umar ya ce, "sufara yin sallah sannan. Suna idar da sallah cikin gidan suka nufa. tun atsakar gida wani farinciki yaratsa zuciyar ya Umar. Dama Yasan Asma'u tuni mai tsaftace. Shiyyasa baita6a fargabar zuwa dawani gidansaba akowane yanayi. Tunda suka shigo yazeed ketabin ko'ina nagidan da kallo. Tabbas rayuwa nada abin tsoro. Idan yatuna yanda Umar yasamu kud'i abaya, ko'a mafarki wani baxaiyi tunanin ganinsa a irin wannan gidanba. Amma abin birgewa kokad'an babu wata k'asurgumar damuwa tartare da Umar d'in. Tab aii da wanine dayanzu yabi daji ciwon hauka yakamashi. Kai gsky Umar jarumin namijine abin kwatance awannan zamanin. Ya Umar yakamo hannun Yazeed Dan ganin yana tafiya ahankali. Ajiyar zuciya yazeed yayi tareda dawowa cikin hankalinsa. Ya Umar baice dashi komaiba sukai sallama ak'ofar falon. Asma'u ta amsa cikin nutsuwa. Jin kamar muryar ya Umar yasakata fitowa daga bedroom. Adaidai nan kuma su ya Umar suka shigo falon. Komawa tayi ciki da saurinta Dan d'aukar hijjab. Carpet d'in dake falon ya Umar ya nunama yazeed. Saida yaga ya zauna sannan yabi Asma'u. Abakin k'ofa sukayi karo tasako hijjab. rungumeta yayi, daddad'an k'amshinta na kuma sakashi a shauk'in k'aunarta. Kanta ak'asa ta ce, ''sannu dazuwa." Yauwa Sarauniyata, ykk? Ya jikin?. Lfy lau, kuma ni lfyta k'alaufa. Murmushi yayi yana kallon yanda take cuno baki. Ya sunkuyo kad'an yabata kisses guda uku, abakinta da goshinta. Kunyace takuma kama Asma'u, Dan haka tayi k'ok'arin kwace kanta ta gudu amma saiya ruk'ota da k'yau. Humm guduwa kikeson yine? To aiia tare Muke da babban bak'o. Da sauri tad'ago ta kallesa, yaya bak'ofa?. Kansa yad'aga mata, har yanzu idonsa akanta. To amma miyasa Baka kirani kafad'aminba? Da saina masa binci na Musamman, tunda kace abban bak'one. Hakane my Asmy yazeed babban bak'one agaremu. Amma kiyi hak'uri Nima a ahanya na tsintoshi. Ayya to babu damuwa. Amma yanacin garau-garau?. Gira yad'aga mata, tareda k'ara rungumeta ajikinsa ya ce, "aibakinkine garau-garau d'in. mizai hana yaci sarauniyata." Dad'ine yake ratsa zuciyar Asma'u aduk lokacin dataji ya Umar yasauya mata wani suna daban, musamman sarauniyata dayake cemata. Jin tayi luf ajikinsa yasakashi d'agota. Yadai Husanata? Ko kina buk'atar d'umin mijinkine?. Da Sauri ta d'an tureshi tafice daga d'akin. Shima bayanta yabi yana dariya k'asa-k'asa. Afalo ya isketa suna gaisawa da yazeed. Sosai yazeed yaba da tarbiyyar Asma'u. Ya Umar na fitowa Asma'u tana mik'ewa tafita. Akusadashi ya Umar ya zauna. Yazeed ya kalleshi daikuma ya bushe da dariya. Harararsa ya Umar yayi. Mikuma yabaka dariya kaikuma?. Yazeed bai iya maganaba sai dariya, daya kalli ya Umar saiya sake tuntsurewa da dariya. Ganin haka ya Umar Yakuma harararsa. Kai malam yafa isheka, wai miye matsalarkane?. Cikin dariya yazeed yakunna waya yayma ya Umar hoto. Da Sauri ya Umar ya warce wayar danson ganin miya faru?. Idanu yazaro waje, shima saiya fara dariyar. Bakinsa yagani duk jambaki. Da Alama kiss d'in dayayma Asma'u ne yakwaso jambakin. Sunacikin dariya Asma'u tashigo. Itama suna had'a ido da ya Umar tayi murmushi ta ajiye tiren hannunta. Tun d'azun tana ganin jambakin amma tak'i Sanar masa. Saving d'insu tayi. Had'd'd'iyar jallop d'in shinkaface wadda taji kayan lambu, dukda babu nama aciki bare kifi sai zabga k'amshi takeyi. Tunkan sufaraci yawunsu ya tsinke suduka. Ta tsiyaya zo6onta dayaji kayan k'amshi a kofuna guda biyu sannan tamik'e. Bismillanku, tafad'a tana mik'ewa. Tunda suka faracin abinci babu mai iya yima d'an uwansa magana. Ta kurma kawai akeyi, babu Baka sai kunne. Sosai sukaci abincinnan, Dan abincin yayima yazeed dad'i. Shi matsalar dayake fuskanta kenan agidansa, matarsa bata iya girkiba. Ko indome tadafa masa saidai yaci kawai da hak'uri. Amma badan dad'iba kam. Bayan sunci sunyi dam, suka kora da sassanyan zo6on. Ayanzu kam yazeed yakasa daurewa saida yayi magana. Kai abokina kana kwasar gara wlhy. Yoni Ina samun haka mizai dameni. Kallonsa ya Umar yayi yana murmushi jin dad'in an yabama Asma'unsa. Haba abokina Kanada matafa? Yakake fad'ar irin wannan maganar. Hummm abokina kenan aii kasan ko'a Matan wata tafi wata. Hakane. ALLAH yasa mudace. Ameen yazeed yafad'a yana k'ara tsiyaya zo6on akofi. Bayan sun kammala Asma'u tafito ta kwashe komai. Jok d'in zo6on kawai tabar musu. Daga nan suka cigaba da hira har zuwa magriba. Sun tattauna abubuwa da dama, ciki harda kud'i da yazeed yabama ya Umar har na 10millions yayi gyaran shagonsa. A take anan kuma yay masa transfer a Account d'insa. Yanda kasan gumaka haka ya Umar da Asma'u suka koma awajen. Ya Umar yarungume yazeed yana masa godiya. A'a Umar babu godiya a tsakaninmu, kayana nakane. Hakama kayanka nawane. ALLAH ne yahad'amu, to dan haka saimu gode masa. Hakane abokina amma kaid'in nadabanne acikin al'umma. ALLAH ya saukar da farinciki da alkairi arayuwarka da zuriyarka. Yanda ka k'yautata mana kaima ALLAH ya k'autata maka damafiyin haka. Ameen Umar ngd sosai da addu'arka. Yanzu abinda yakamata gobe idan ALLAH yakaimu kashirya zamuje wani waje akan kayanka da custom suka rik'e. Ajiyar zuciya ya Umar ya sauke. Yazeed wlhy dama mun hak'ura kawai. Duk hanyar danake tunanin kayannan zasu fita nabi, amma kowa saiyace babu yanda zaiyi. Murmushi yazeed yayi, yadafa kafad'ar ya Umar, karka damu Umar, awannan karon insha ALLAH zasu fito. Aii komai na k'asarmu hanyace. Kaidai karka fidda rai da rahamar ALLAH. Shikenan yazeed ALLAH yakaimu goben. Ngd ngd ngd......... Katseshi yazeed yayi da sauri..... Nifa banason godiyarnan. Idan kanayi sainaga tamkar baka d'aukeni d'an uwaba. Tom kayi hak'uri na daina. Daganan yazeed yamik'e, rafar 'yan d'ari biyar yabama Asma'u wai tukuycin ciyar dashi daddad'an girki datayi. Girgiza kanta tayi, idanunta ak'asa, a'a ya yazeed ngd basai kabani tukuyciba. Banmmasan zakuzo tareba da anmaka na musamman aii. Kai aii wlhy wanna danacima na musamman ne. Ke dai kawai ALLAH yak'ara dank'on k'auna keda abokina. Ngd sosai.. Asaman kafet d'in ya ajiye suka fita.. Godiya sosai tamasa, da sak'on gaisuwa ga iyalinsa sannan takoma ciki, tana mamakin yazeed. Dama akwai irin wad'annan mutanen har yanzu adoron k'asa?. A can kuwa ya Umar yarakashi har mota yana k'ara masa godiya da k'yak'yk'yawar addu'a shida zuriyar sa. Saida yaga yabar Layin sannan yashigo cikin gida. *_(((S))........2017_* *_Luv you all_*