********************* TAKAICIN UBA……📝📝📝 ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Na Nazeefah Sabo Nashe.. Daga k’ungiyar Elegant Online ✍🏽 Arewa books @nazeefah. Wattpad @Nazeefah381. 08033748387. (Alhamdulillah cikin hukuncin ubangiji na sake zuwa muku da wani sabon littafi masoyana, da nake fatan ya faranta muku fiye da na baya a kullum da ku nake alfahari. Ina sake mik’a godiya ta gareku dafatan Allah ya karb’i ibadunmu.) Daga alk’alamin marubuciyar Me Zan yi da ita? Da Ya abin yake? Mafari…………….. ****************************** Page 1 A zafafe ta fito daga office d’in Cikin sauri tamkar zata tashi sama. Da sassarfa sosai ta isa wajen tarin jerin motocin da suke fake a parking lot d’in da yake ma’aikatar. Ba tare da damuwa ba suke ta darewa suna bata hanya don ba sabon abu bane a wajensu a tarin lokuta suna yawan ganinta a haka, cikin wannan yanayin mai firgitarwa. Sai da ta tattare zumbulelen bak’in hijab d’inta da ya zame mata tamkar uniform saboda duk wanda ya san AYRA GAYA da wannan shigar ta dogon black hijab mai jan k’asa ya santa, da kuma black nik’ab. Da wuya a samu mutumin da ya san zallar kamannin na AYRA GAYA in dai ba makusancinta ba shak’ik’i ko kuma daga cikin y’an uwanta sai kuwa abokanta na makarantun primary da secondary da wanda ya santa shekaru goman baya da suka wuce, don na jami’a ma d’aid’aikune suka san zallar kamannin na AYRA GAYA. Da zafin nama sosai ta finciki kan motor, haka yanayinta yake komai a zafafe take yinsa tamkar namiji so take lallai sai ta maye wa mahaifiyarta haushin rashin haihuwar d’a namijin da ake cewa ba ta yi ba. A gareta duk abinda wani d’a namiji zai aikata za ta aikata irinsa koma kai tsaye ta bugi k’irji ta ce zata aikata wanda ya fi shi. Ta fi yarda da cewa What Man can do woman can do better, fiye da what Man can do woman can do. Duk wanda yake cikin ma’aikatar bin ta suka yi da kallo suna tabbatarwa da kan su cewa yau ciwon AYRA ya motsa don sun fi danganta ta da mai cutar jinnu ko tab’in hankali saboda yanayin yarda take mu’amalantar mutane halayenta gaba d’aya ya farrak’a da na mutane sai dai masu shafar jinnu. Yanzu zaka ganta da sanyin hali anjima kaga ta murd’e ta zama wata iriyar mace mai bak’ar zuciya mai zafi da saurin fushi. Ta ko ina take jefa motar har zuwa sanda Allah ya kawota unguwar Rail way inda anan ne suka tanfatsawa mahaifiyarsu gida ita da y’an uwanta su hud’u har ita cikon ta biyar d’in kafataninsu zallar mata. Horn d’in da ta dinga dannawa Mai gadin a zafafe ne ya tabbatar masa da cewa yau Uwar d’akin nasa ba lafiya ba, don da lafiya take idan ta yi sau biyu bai zo ya bud’e ba da kanta take zuwa ta tura gate d’in ta kan ce masa “Yi zamanka Baba na san hutawa kake bana son katsewa mutum hutunsa musamman idan barci ya d’aukeshi balle kai da shekaru sun ja.” Yau kam ya san tunda take wannan gigitaccen horn d’in ya tabbata aljannun uwar d’akin nasa sun motsa. Sai da ya ja Innahu min sulaimanu sannan ya bud’e gate d’in abinda ya ke zargi ya tabbata domin dai ko glass d’in motar bata sauke ba balle ya saka ran samun gaisuwa kamar yarda duk ta saba idan tana cikin sukunin zuciya da walwala. Madadin haka ambaleshi da iska ta yi a zafafe ta kai kanta ma’ajiyar motocin gidan. Da k’arfi ta tura k’ofar da zata shigar da kai ainahin harabar tsakargidan kafin shiga main parlour na gidan. Tun a waje dama ta shaida zuwan y’an uwanta ganin motocinsu duka a wajen. Ta sani sun zo don su d’aga mata hankali kamar yarda suka saba su saka mahaifiyarta ta kwana tana mata mita akan rashin aurenta kamar a kansu take zaune. Kafin ta shiga sai da ta tuge nik’ab d’in da yake fuskarta sannan ta tura k’ofar. Ga hasashenta kuwa suna zaune zagaye da mahaifiyarsu, yaransu a gefe suma. Hutun makaranta ake ta san shi yasa suka zo da su. Tsam ta d’inke sauran annurin da yake fuskarta ta tattare ta waje d’aya kamar ba a tab’a halittar dariya a fuskarta ba. Cikin wani irin taku mai nuna a shirye take da tunkararsu da duk wacce suka zo ta isa wajen su. Kafin ta zauna tana cin magani tana kuma amsa gaisuwar da y’ay’ansu suke mata tamkar bata so, don gaba d’aya idonta ma Akan screen d’in waya yake. Sai da ta runtse ido ta bud’e Kafin ta zare bak’in shade d’in da yake idonta. Su Kansu ba yaran ba Sai da suka razana da ganin yarda k’wayar idanunta suka jirkice zuwa launin ja. Murya a cunkushe ta zube idanunta cikin na Babbar yayarsu kafin ta ce “Ina yininku?” Tana nufin gaba d’ayansu don bai Zama lallai ta bi su d’aya Bayan d’aya ba. Jikinsu a sanyaye cike da kulawa suka fara amsa gaisuwarta. Suna sonta sosai fiye da duk tunanin mai karatu, wani irin so suke nuna mata da gata da yasa ko kad’an ba sa son ganin b’acin ranta, burinsu gaba d’aya a kanta yake suna burin kyautata rayuwarta da samar mata da farin ciki fiye da nasu farin ciki ba su sani ba ko don kasancewar ta taso da wani tabo a zuciya mai wuyar gogewa. So suke su d’auke mata wancan bak’in fentin na mahaifinsu da ya yi naso a zuciyarta har ya haifar da rud’ani da k’iyayyar jimillar maza a zuciyarta, har hakan yasa ta yiwa maza kud’in goro ta kuma k’addara ba zata tab’a aure ba a rayuwarta, duk da tarin baiwa da Allah ya bata na wani irin kyau cikar haiba da zati hakan yasa take b’oyewa maza jikinta da fuskarta don kada ma su kwad’aitu da son aurenta, ba ta son ko kad’an a mata zancen aure duk da kasancewar a shekarunta ya kamata ace tana da auren shekara ashirin da shidda cif. Ta sha alwashi a zuciyarta duk sanda y’an uwanta suka mata aure ba tare da amincewarta ba tabbas za su d’au gawarta a washegari a gidan mijin, don tabbas sai ta kashe kanta. Sab’anin nata burin, y’an uwanta burinsu ta yi aure burinsu yau ace ga mijin AYRA, su duk tunaninsu jinnu ne ya aureta duk da suna tunanin wancan bak’in fentin da mahaifinta ya shafa a zuciyarta ne yake biyayyar ta sai dai hakan ba zai saka ya zama gamsashshiyar hujjar k’iyayyar maza a zuciyarta ba. Duka-duka shekarunta nawa a duniya sanda lamarin ya faru? Bai kamata ya zame mata hujja ba da zata tattare duka maza ta saka su a mizani d’aya ba. Sakin ajiyar zuciyar da mahaifiyarsu ta yi shi ya dawo da dukkansu daga tunanin da suka afka. Yaya Dija da tafi kusa da ita da sauri ta dafata “Please Ammaty kada ki saka damuwar da zata zame miki lalurar da zamu rasa ki mu shiga uku kin dai san ke kad’ai muke gani ki zame mana farin ciki a rayuwa AYRA bata da asara tunda tana sani take saka ki b’acin rai,ki godewa Allah tunda dukkanmu muna d’akin mazajenmu ita kad’ai ce mai kafaffiyar zuciyar da ta kasa gusar miki da b’acin rai itama kuma da ikon Allah lokacin ta yazo k’arshe za mu sadata da d’akin miji ko sadakarta za mu bayar.” Wani kallo AYRAn ta kafe Dija da shi don dama duk ciki tafi raina ta musamman kasancewarta sak’uwarta ta mik’e a zafafe tana wurga mata kallo kafin ta ce “Idan kun tashi sada ni da d’akin miji Ku tabbata kun tanadi likkafani da duk wani abu da kuka san mamaci zai buk’ata don ina tabbatar muku tabbas suna na gawa a gidan duk uban da ya yi tsautsayin aurena, haba ku k’yaleni mana rayuwarku ko tawa shin ban tsare kaina bane? Ko rashin aure ya saka ni aikata zina? Ba zan aure ba na sake jaddada muku tunda auren ba wajibi bane a musulunci balle ace ya zama farilla.” Yarda take maganar sosai zuk’atan su suka sake samun rauni don zahirin abinda yake k’ark’ashin zuciyarta take fad’a da kuma duk wani tarin confidence d’inta a yarda take tabbas idan aka mata auren zata iya aikata kashe kan nata kamar yarda take fad’a ba wai iya kan harshenta abin nata ya tsaya ba a’a har k’asan ranta iya zallar gaskiyar kenan. Kafin su yi wani yunk’uri tuni ta burma kanta cikin d’akin da ya zama mallakinta ne a gidan ta kuma rufo k’ofa da k’arfin gaske wanda ya yi daidai da kece wa da kukanta. Amma tabbas yau ta yarda bata tantama AYRA jinnu ya aureta. Kuka take tana fad’in Ya Allah ka taimaki ne akan yarinyar nan ni ba wani namiji tsayayye da zai tsaya min akan lamarinta ba, Ubanta kuwa da shi da babu a wajena duka d’aya Ya Allah kada ka d’au raina ban ga auren AYRA ba.” Eesha ta ja ajiyar zuciya kafin ta kama tafin hannun Amman tasu ita kanta kukan ne yake son k’wace mata ga shi nan dai yanzu auren yaransu za’a fara amma ita AYRA ta k’i ta bud’e fuskartata ma maza su ganta balle su sota kullum fuska a dunk’une cikin nik’abi, jiki a na’de cikin burgujejen Hijabi, bata hoto ma balle ka nunawa wani ko zai so ta, duk da su kansu sun san gangancin gaske ne su aurar da ita ba da son ranta ba, yarda Ayran take da zafin zuciya kamar siya mata tikitin tafiya lahira ne, ko bata rantse ba sun yarda da tace ko an yi auren ma kashe kanta zata yi wa ya aikesu wannan ganganci gwara su zuba mata ido har zuwa sanda Allah zai yi ikonsa a kan ta. Kaf d’in su hawayen suke har da y’an matan y’ay’ansu da ake zancen aurar da su nan da watanni kad’an masu zuwa lamarin AYRA kowa da shi yake kwana yake tashi. An sha yi mata ruk’ya amma babu alamun jinnu tare da ita, kawai ta d’arsa wa kanta tsanar maza ne a zuciyarta tun tashinta. To fa! Ko mai Uban AYRA ya aikata mata da ya d’orata a tubalin k’in maza da aure ma gaba d’aya. Za mu ji anan gaba kad’an Ku dai Ku biyo JIkar Nashe. Ku shiga link ‘din nan don samun labarin a sauk’ak’e a can kawai zan dinga posting. Daga yau nagode. https://chat.whatsapp.com/EZyeAwHEGGhJz1pRBmmale Takaicin Uba….. Na Nazeefah Sabo Nashe.. 08033748387. ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 2.. Zainab da tun shigowarsu bata ce komai ba, don tana da zafi idan ta ce zata biye ta Ayra fes zata mata mugun duka, sau tari Ayran ta fi shakkarta fiye da kowa a cikin y’an uwanta, don da wuya ta kulata amma duk ranar da ta bari ta kaita bango ranar Zainab d’in marinta take. Itace Yarsu ta biyu amma ta fi shakkarta fiye da Majeeda Babbar Yayarsu. Huci kawai take tana jin takaicin Ayra na sake katantawa da zuciyarta. Bak’in cikinta d’aya yarda za su fara aurar da d’iyoyin cikinsu Ayran na zaune a gida kuma ba wai rasa mazajen auren ta yi ba, tun bayan da ta fuskanci kyanta da jikinta ya na janyo hankalin maza gareta tun kafin ta gama Secondary school sai ta k’irk’irarwa kanta sanya dogon zumbula zumbulan hijabs kuma bak’ak’e wuluk da su. Ta bi kuma fuskarta da nik’ab ta k’unshe harta da hannunta sai ta sanya masa hand gloves da k’afafunta idan ka ganta sai ka zata d’aya daga cikin y’an k’ungiyar Shi’a ce. Ajiyar zuciyar da ta ja mai k’arfin gaske ya dawo da hankalinsu kanta. Ta d’ago fuskarta a had’e sosai kafin ta ce “Ammaty da laifinki kema, ya kamata ki nunawa Ayra ke kike iko da ita kuma kin isa ki zartar da hukuncin da ya wajaba ta bi shi da son ranta ko babu umarni ne Allah ya bata, kina da damar da zaki aurar da ita ga duk wanda kika so.” “A aurar da ita ba da amincewarta ba ta kashe kanta kenan ko?” Babbar yarsu Majeeda da ta fi su sanyin hali kusan duk ita ta d’auko halayen Amma ta fad’a idanunta cikin na zainab k’anwarta mai bi mata. Cikin takaici Zainab ta saki murmushi kafin ta ce “K’aryar banza ce ba zata kashe kanta ba wallahi kawai don ta saka mu k’i mata auren ne take wannan furucin, kuma raina mu ta yi don taga Amman bata da wani tsayayyen namiji da zai jajirce a kanta, ina ma Kawu Saddi zai dawo da naga uban da zai hana shi aura mata duk wanda ya yi niyya.” Amma kallon Zainab kawai take kafin ta girgiza kai “Tsaf zata aikata kisan kanta, kamar ba ki san kafiya da taurin zuciya irin na Ayra ba, da wannan tunanin fa ta tashi a zuciyarta, K’iyayyar maza a ranta take tun bayan da mahaifinku ya d’arsa mata hakan a ranta, ku cigaba da yi mata addu’a dai Allah ya kawar da wancan lamarin a zuciyarta ya sanya mata nutsuwa da tunanin cewa mazan ba duka suka taru suka zama d’aya ba, Allah ya mata jagora ya sa naga auran Ayra kafin kushewata.” Ayra kuwa tana shiga d’akin cikin b’acin rai ta tub’e suturun jikinta daga ita sai underwear ta shige toilet ta saba a yanayi irin wannan sai ta sakar wa kanta ruwa take samun sukuni. Gaba d’aya ta ware shower d’in a kanta tana burin zuciyarta ta sassauta daga yanayin b’acin ran da take ciki, amma ina kamar ana sake angizo mata b’acin ran, hotunan lamarin suna sake mama ye ganinta tamkar yanzu abubuwan suke faruwa ta runtse idanunta ta shiga dukan bango da dukkan k’arfinta kai kace zata ruguza duka tiles d’in toilet d’in ko zafin hannunta bata ji, hawaye kuwa zuba yake sosai a idonta. Ta tsaneshi ta tsani mahaifinta tsana mafi muni, bata jin har ya koma ga ubangiji zata yafe masa tarin laifukansa, bata ji ko mutuwa ya yi zata d’aga hannu ta rok’a masa gafarar Ubangiji. Tsawon lokaci tana cikin wannan yanayin kafin ta fito daga cikin tub d’in sanye da rigar wanka bata damu da tsiyayar ruwa da gashinta yake yi ba, ga wani irin kakkarwa da jikinta yake saboda ruwan sanyi ta sakarwa kanta duk da kuwa muku mukun sanyin da ake. Ba abinda ta yiwa jikinta illa towel da ta saka ta nad’e gashin kanta haka ta shige cikin blanket ta k’udundune kanta tana rawar d’ari sosai zazzafan zazzab’i ya rufeta ban da Amma ta hanata da tuni ta maka wancan Uban nasu a kotu.. tunanin da take kenan tana cizon leb’en bakinta da har suke fitar da jini Saboda datsesu da take yi. Kamar Amma ta san za’a yi haka ta biyo bayanta ita da Dijah da Majeedah. Suka ci sa’a k’ofar d’akin a bud’e take bata rufeta ba hakan yasa suka shiga kansu tsaye, da sauri Amma ta k’arasa gadon don daga inda suke suna juyo sautin had’uwar hak’oranta da suke bayyana alamar halin da take ciki. Amma na k’ok’arin yaye bargon Ayra na ja tana sake k’udundune jikinta murya a shak’e alamar kukanta ya tsananta take cewa “Barni na mutu Ammaty, tunda ba kwa son rayuwata, wallahi da na yi aure na zauna k’ark’ashin wani namijin gwara na mutu tun yanzu zuciyata suya take da zafi daga zancen auren ma ina ga an yi auren na tabbata idan ban kashe kaina ba zuciyata kuwa zata buga da kanta na mutu ku huta.” Cikin azama Amma ta jata jikinta ta rungume ta tausayi sosai take bata kuma laifinta ne da bata wayar mata da kai tun tana k’arama ba ta bari abin ya girmama a zuciyarta bata sanar mata Mazan ba halinsu d’aya ba kowa da halinsa, yanzu y’an uwanta ba gashi suna zaune da mazajensu lafiya ba cikin so da k’aunar juna, tun a lokaci bukukuwansu Ayran ta sha fad’ar ba zata tab’a aure ba, kuma ko mazajen nasu bata wa magana a zaton Amma duk wasa take bata san lamarin ya yi tasiri a zuciyar Ayra ba ta yarda ta dunk’ule maza waje d’aya ta lak’kaba musu halaye guda. “Kunna room heater Dija jikinta da zazzab’i sosai. Ki kuma kira min y’an uwanki na sake kafa musu sharad’in da duk wanda ya k’etare sai dai ya nemi wata uwar ba ni ba, ba zaku hallaka min yarinya ba tunda ba a kanku take zaune ba, ba kuma ta tab’a jawo min abin magana ba.” Amma ta fad’a cikin b’acin rai zuciyarta cike da tausayin Ayran. Da sauri ta ja Hand dryer tana busar mata da gashin kanta kafin ta shafa mata mai a sassan jikinta ta zura mata doguwar Riga mai nauyi sannan ta saka mata rigar sanyi shayi mai zafi ta saka Dija da suke tsaye jigum jigum ta had’o mata haka ta tilasta mata ta sha duk da tana turjewa sai da ta gama Amman ta hau murza mata k’afa sannan ta kalli sauran yaranta da suke tsaye musamman Zainab da ta fisu uzzira wa Ayran akan aure “Kada wanda ya sake mata maganar aure bana so, tunda ba a kanku take zaune ba, duk cikinku ba wanda ya fuskanci irin matsalolin mahaifinku fiye da ita a rayuwa ta taso da abin a ranta don haka tilastawarku ba zai sa ta mance da wancan k’addarar ba har ta yi aure ku barta haka nan idan Allah ya nufa zata yi aure zata yi idan bai nufa ba ku k’addara hakan Allah ya rubuta mata ba kuma wanda ya isa ya canja k’addarar bawa. Ba y’ay’a za ku aurar ba ko Jikoki ku aurar shi Aure lokaci ne ko bayan raina kuma ban amince muku ku tialsta mata ba doka ce na saka musamman ke Zainab na fad’a na sake fad’a.” Tsit d’akin su kayi, ita kuwa Ayra farin ciki ne ya kamata duk Wani nauyi da zuciyarta ta yi tuni ta yi k’asa a yau Kam ta tabbata Ammaty ta tace tana kuma gudun b’acin ranta. Ji ta yi kamar ta tashi ta taka rawa ta dinga kallon Zainab tana dariya k’asa-k’asa kafin ta ja bargo ta kwanta bayan ta sha maganin saukar da zazzab’i ta lumshe idonta barci mai dad’i yana d’aukarta. Amma ta tisa k’eyarsu a gaba suka fice. Ko a falo jajanta lamarin suka dinga yi Amma ta sake zabga uban tagumi tana duban yaran nata ‘daya a zuciyarta tana godewa Allah da ya raya mata har suka zama wani abu a duniya kamar ba su bane a lokutan baya ta dinga wahala da su, abubuwa da dama suka dinga rincab’e mata. Da sauri ta runtse idanunta ba ta son tuna wancan bak’ar rayuwar don muninta ya girgimama. Dijah ce ta fara kawar da tunanin ta hanyar cewa “Mu mata addu’a Amma, ina tunanin lamarin Ayra sai addu’a Khairan In sha Allah ubangiji zai kawo wani da duk k’iyayyarta da aure sai ta aureshi in dai mijinta ne.” Gaba ‘d’aya suka jinjina kai Amman ta fara korarsu ta hanyar cewa sai su tashi su tafi gidajensu tunda sun birkita mata y’a “Don sanda kuka sake zuwa kuma harzik’a min auta wallahi zaku sani.” Murmushi suke kawai suna mik’ewa ‘daya bayan ‘daya don dama yammaci ya kawo kai. Takaicin Uba….. Na Nazeefah Sabo Nashe 08033748387. 3… Littafin Takaicin Uba.. paid book ne, 500 ne kacal ga masu buk’atar karanta shi za su iya biyan ku’din su ta wannan account ‘din a saka su a paid group..2118666253 U B A. Akwai kuma special people masu son a bisu har gida a tura musu privately ba ruwansu da hanyaniyar group, ko turo min inda aka wuce ni a kullum aka yi posting zan tura musu privately. Ku biya 1k kacal. Sai masu turawa groups ‘din su ku kuma ku biyo ni gida mu yi ciniki. Kada ku manta littafin mai zafi ne fiye da ME ZAN YI DA ITA? Da YA ABIN YAKE? Sai na jiku pages 12 ne kacal free pages. ————————— Ko a wajen rakiyar da Amman ta musu, kashedin da Amman ta sake musu mai tsauri ne, don yau kam Ayra ta gigita tunaninta gani take a condition d’in da ta tarar da ita tsaf zata kashe kan nata. Ta sake jaddada kashedinta ga Zainab musamman kasancewar ta fi su tsaurara lamarin. Zainab ajiyar zuciya kawai take saki don dai ita da za’a bi ta tata da Tuni Ayra ta dad’e a d’akin miji gani take duka zancen kisan da take rainin hankaline don ta ga suna biye mata ne. A tunaninta wancan kuskuren mahaifin nasu bai zama dalilin da zai rinjayi zuciyarta ta gicciyar da lamarin aure lokaci guda ba. Ta d’auke kanta bayan ta tabbatar wa da mahaifiyarsu ba zata sake tsoma baki game da lamarin Ayran ba sai dai tana rok’on Ubangiji ya ganar da su abinda ita tuni ta dad’e da ganewa. Bata wani jima a wajen ba ta ja tawagar yaranta ta bar gidan ranta a matuk’ar b’ace don idan ta zauna tabbas duk wanda ya takaleta zata iya sauke takaicinta a kansa. Ko a mota mitar da take kenan sai da Babbar y’arta ta dinga tausar zuciyarta kafin ta samu ta lafa daga b’acin ran da take ciki. ___________ Da wani irin farin ciki ta tashi da safiyar kashegarin ranar da abin ya faru. Zuciyarta wasai ta tabbata a yanzu ko da ganganci babu mai sake mata maganar aure tunda Amma ta Riga ta gindaya sharad’i mai zafi game da lamarin auren. Ta sani sarai suna shakkar mahaifiyarsu ba sa son bijirowar b’acin ranta ko misk’ala zarratin. A tsaye take a gaban mudubi tana sake cancad’awa fuskarta kyakykyawan make up. Da ya sake bayyana wani irin sihirtaccen kyanta ko ba ta yi kwalliya ba dama mai kyau ce balle ita ma’abociyar son kwalliya ce da duk wani k’yalek’yale. Eyelashes d’inta ta sake bi da mascara ta tusa musamman kasancewar su zara-zara kamar na kanti sai dai nata ne daga Indallahi (naturally). Kyakykyawan lips d’inta ta gogawa pink lipstick sai ya sake bayyana tsananin kyanta ta d’aura d’ankwalin black material da yake jikinta sai dai bai b’oye zara-Zaran gashin da suke kwance luf-luf a gaban goshinta ba. Ta d’an fesa turarenta mai matuk’ar k’amshi da tsada na kamfanin lulu. Sannan ta d’au gogaggen hijabinta bak’i sid’ik wanda ya zame mata gado ta ratayashi da nik’ab da hand bag d’inta ta fice Falon gidan. Kamar kowace safiya gidan an gyarashi tsaf da taimakonta da na mai aikinsu sai baza k’amshin turaren sandal wood yake mai asalin k’amshi. Saman Dinning ta zauna tana had’a coffee ga al’adarta duk safiya sai ta sha coffee kafin ta ci komai, musamman kasancewrta ma’abociyar k’in abinci tsakaninta da abinci akwai gaba mai girman gaske. Ta zari salted biscuit guda biyu ta fara sha da coffee d’in. Amma ta bi hannunta da kallo “Yau ba zaki ci ko chips d’in ba, sarkin k’in cin abinci.” Girgiza kai ta yi tana cuno bakinta “Wallahi Ammaty yau Abincin nan ba zai samu shiga ba, wannan ma is okey idan na ci abincin ba zan iya hassala komai a office ba, kuma ina da aiki mai tarin yawa.” Amma ta girgiza kai “Madalla da Agogo sarkin aiki shi yasa ga ki nan kullum jiya I yau.” Mik’ewa ta yi tana tuntsira dariya cikin farin ciki ta rungumi Amman kafin ta zura hijab d’inta da nik’ab ta kuma zurmuk’a hannayenta a aljihu ta sake rungumar Amman murya k’asa ta ce “Amma yau may be zan iya kaiwa past 4:00 saboda muna da meeting.” Amma ta matsa hannayenta tana murzasu kad’an-kad’an cikin kulawa ta ce “Allah ya yiwa nemanki albarka Auta. Ya tabbatar min da ke kan tafarkin sirad’il mustak’eema.” Feck ta bata a kumatu ta fice da d’an hanzari ganin 7;30 tuni ta wuce Amma ta sake Binta da wasu addu’oin a zuciyarta “Ubangiji ya yaye miki wancan tunanin a zuciyarki, ya kawo miki mijin aure na gari da zaki goge tabon k’iyayyar maza a zuciyarki, har ki furta da kanki wata rana MAZAN SUNA SUKA TARA.” Irin Addu’oin da Amman take Bin ta da su kullum kenan a cikin sallolinta guda biyar. Ta tabbatar kuma Allah yana jinta abubuwan duka za su wuce da ikon Rabbi sai dai jinkiri. Kowanene Mijin Ayra? Shine tambayar da kullum takewa kanta take kuma burin ganin Mijin Ayran kafin a kaita kushewa. ________________________ A zaune akan dakalin k’ofar gidan nasa ya zuba hannayensa a k’unci cikin zuzzurfan tunani. Kana ganinsa ka ga wanda talauci ya yiwa dabaibayi. Ba shi da sukuni ko kad’an kullum kuma a cikin halin da yake kasancewa kenan. Amininsa na kullum ya iso wajen hannunsa rik’e da ledar da take d’auke da k’osai da kunu. Kamar kowace safiya nan yake biyo wa su ci da abokin nasa. Ya zauna daf da shi yana kai hannu kan kafad’arsa kasancewar duk sallamar da ya masa bai ji ba dalilin zuzzurfan tunanin da ya afka. A razane ya d’an jiyo duk da ya san shine don shi kad’ai ne mutumin da yake mu’amalantarsa dalilin rashi da ya fad’a kowa ya daina kula shi, sab’anin sanda ya ke da ku’di kuwa shine na kowa har fadanci ake masa. Malam Hadi ya ja tsaki yana kallo cikin idanun abokin nasa kafin ya ce “Wallahi idan ba kayi wasa ba Tunani zai bugar maka da zuciya. Kullum fa a yanayin da kake kenan, kana da hanyar yayewa kanka duk matsalolinka amma ka zauna talauci ya maka dabaibayi bayan a y’ay’anka har da matar Minister matar d’an majalisa matar gwamanan banki ka zauna talauci zai kasheka.” Alh. Kabiru ya girgiza kai kafin ya ja wata nauyayyiyar ajiyar zuciya ya cire hularsa furfurar kansa gaba d’aya ta bayyana alamar yana cikin wahala “Wallahi Hadi ba zan iya ba, ba zan iya ido hud’u da talatu ba shin da wani ido kake son na kalli su kansu yaran nawa balle Talatu na tabbata a duniya a yanzu ba wanda suka tsana sama da ni.” Mai. Hadi ya ja tsaki kafin ya bud’e takardar k’osan da za su ci shima ba don komai yake wannan hak’ilon da Amininsa ba yake ciyar da shi kullum sai don ya san tabbas nan gaba kad’an zai fanshe wahalarsa a duk lokacin da Amininsa ya daidaita da y’ay’annasa duk da ya san abin da kamar wuya, don tab’argazar da Amininnasa ya aikata girmanta ya yi shaharar da ba za su yafe masa nan kwana kusa ba, idan ma za su yafe masa ‘din kenan, bai k’i ba ko idan suka gan shi a gadon sharafa yana shirin tafiya kushewa amma ai bai bari sun gwada ko sau d’aya su ga ko za’a dace ba.Don haka yana cilla k’osai a bakinsa ya ce “Ka bari mu gwada ni zan je da wani a cikin danginka a gaya musu halin da kake ciki ai ba kai zaka je ba.” Alh. Kabiru ya ja ajiyar zuciya kafin ya ce “Ina jiye muku tsoron sauke muku kwandon wulak’ancin da suka yi niyyar sauke min.” “Sai me? Daga wulak’ancin in dai za su amince su dinga baka Naira waye bai san arzikin da suka yi ba? Amma su ko tunaninka ba sa yi kamar ba kai ka haifesu ba.” Ya girgiza kai “Na yi musu abinda ban cancanci afuwa ba, a haka ma gode musu nake da lamarin bai kai mu ga kotu ba, tunda ka nace sai ka je shikkenan na baka dama ka gwada zuwa amma fa duk abinda ya biyo baya kada ka yi kuka da ni ka yi kuka da kanka.” Mal. Hadi ya girgiza kai cikin farin ciki ya ce “Ko kai fa ba mamaki ma kai kake abinka su tuni sun manta wallahi.” Alh. Kabiru ya zaro ido cike da tabbatarwa ya ce “Wallahi ba su manta ba ai abin ba abin a manta ba ne.” Malam Hadi ya girgiza kai “Ai shikkenan kada su manta d’in ka bar ni da su, idan an bi da su ta ruwan sanyi suka k’i ba da had’in kai dole a bi da su ta yarda shari’a ta ce, yara dai naka ne ko jikinku a ka tsaga tilas a ga jininku d’aya da su don haka tilas ba’a canjawa tuwo suna a cikin satin nan zan je har gidan ayi wacce za’a yi.” Alh. Kabiru shiru ya yi idanunsa a k’asa tunani ya rinjayar da hasken annurin da yake fuskarsa, fuskar tuni ta bak’unci wani irin yanayi da tarin dana sani da nadama gami da kaico su suka wanzu a fuskarsa. Hawayen da ya saba zubar wa suka shiga ambaliya a fuskarsa. Da gaske lamarin yana masa ciwo yana ji da yana da iko da ya dawo da rayuwar baya ya gyara tarin kuskurensa, shi da kansa ya Riga ya san ya dasa tsanarsa a zuciyar yaransa da ma duk wani da yake kusa da shi. Ashe da gaske lokacin zai zo da zai yi bak’in cikin wancan fentin da ya goga wa kansa tamkar yarda mahaifinsa ya gaya masa tun yana raye. Cikin wata karyayyiyar murya da take rawa ya ce “KAICONA NI KABIRU ni da kaina na yi Allah wadarai da halayena da suka gabata Astagfirullah Ya Allah.” Ya saka hannu ya d’auke k’wallar da take idanunsa yana dafa hannayen amininsa murya cike da sanyi ya ce “Ka taimaka min Hadi don girman Allah ka shawo min kan su, ko da ba za su dinga min komai ba ni ba wannan bane burina, burina su yafe min su kuma amince su karb’eni a matsayin mahaifi ina tabbatar maka yarda nake jin yarda zuciyata ke ciwo tabbas ta kusa bugawa na mutu. Dukiyarsu bata gabana amincinsu kawai nake nema.” Wani kallo Hadi yake masa a zuciyarsa yana tunanin rashin hankalin abokin nasa, bai San wace irin dukiya ce da yaran nasa ba shi yasa yake fad’in haka. Kamfani ne da su Guda na kayan gine-gine da duk Nigeria da mak’waftanta ba wanda bai san kamfanin ba saboda bunk’asar sa (Talatu furnitures and construction company) Amma ji zancen da yake wai shi ba don arzikin su zai shirya su ba, ai kuwa shi ba za’a yi wannan k’aryar da shi ba shi don arzikinsu zai daidaita su don ya san tabbas shima zai dandali arzikin. Amma don kada ya nuna zalamarsa sai kawai ya girgiza kai yana tabbatar masa zai yi iya bakin k’ok’arin sa. ______ Tunda Ayran ta tafi aiki. Amma Talatu ta mik’e alwalarta tayi don gabatar da sallolinta na walaha kamar yarda ta saba. Tana idar wa ta kishingi’da tunani ta fara yi game da Ayran da yarda take so ta yakice aure daga rayuwar ta, tabbas ba taga laifinta ba don idan ka ji tarihinsu na baya hakan da Ayran ta yi shine daidai dole ta tsani maza ta kuma jinginasu ga ma’auni ‘daya ba kowa kuma ya janyo hakan ba sai mahaifinta, da ya cusa mata k’iyayyar maza tun tana y’ar ficilarta da hakan ta tashi a ranta. Talatu ta runtse idanunta sai ga wasu irin tarin hawaye suna kwaranya daga idanunta masu k’una da zafin gaske.. Ta dinga cizar lab’banta tana fa’din Namiji ! Namiji!! Allah dai ya kyauta amma tun farkon rayuwarta ita kanta uwar Ayran da Takaicin ‘da namiji ta tashi Ya ilahi take ta furtawa a ranta saboda yarda zuciyarta take zuba luguden daka… TAKAICIN UBA… Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. https://arewabooks.com/book?id=6455383e1c910f5cf9785c27 (Kada fa ki bari a yi tafiyar nan ba ke! Takaicin Uba yanzu aka fara wani irin mur’dadden labari ne mai sanya tausayi takaici ga uwa ba tsantsar k’iyayyar da take juyewa ta koma makauniyar soyayya. Kun sani sarai bana kawo muku labaran banza. Za’a sha dariya, Za’a goge hawaye duka a cikin labarin. Zai zo muku Akan 500 kacal. Sai special people manyan matan nan masu aji da ba sa son hayaniyar group, suna kan kujerar su za’a tura musu har cikin wayarsu ba ruwansu da an tsere min turo min. Za su biya 1k kacal duk da Naga Akwai Hajiyoyin gimbiyoyin mazajensu da suke tura min yafi haka. Tabbas gaisuwar ku daban ce.. samba’do ku’dinki ta wannan account ‘din 2118666253 U BA.. Y’ar mutan makwarari ke cewa Marhababikum Lale Lale ana uhibbukum billah 😊😊😊❤️ 4_____________ Da walwala sosai a fuskarta take duban sakatariyar tata duk da bata ganin fuskarta amma a muryar shugabar tata ta fahimci tarin farin cikin labarin da ta zo mata da shi, na zuwan bak’uwar da ta dad’e tana tsimayin zuwanta. Aminiyartace sosai da karatu ya farrak’a su shekarun da suka wuce ita ta koma rayuwar egypt saboda admission da ta samu a can, yanzu ma hutu ta zo don ta samu aikin koyarwa a can egypt d’in. Tunda ta mata waya zata zo take cikin murna da zakwad’i da son ganin aminyar tata Saboda tsawon lokacin da ta d’auka bata ganta ba. Saleemah Sa’ad ta shigo cikin wata irin k’Saitacciyar shiga, fuskarta d’auke da matsanancin murmushi tana bin office d’in AYRA GAYA da kallo. Shigar da take jikin Ayran ce ta sa ta ware ido tana kallonta so take ta ga fuskar Ayran da nik’abi ya mata shamaki. Da hanzari Ayran ta tuje nik’abin fuskarta ganin sakatariyar ta ta ta fita cikin farin ciki da murna ta isa wajen Saleema ta kai mata kyakykyawar runguma. Salima ma murmushi take tana sake duban Ayran da ta k’ara wani irin fitinannen kyau fatarta sai kace glass don taushi da sulb’i. Sai dai yanayin shigarta ya bawa Salima mamaki. Ayra dai Ayra da ta sani y’ar gayu mai yawan saka English wears sanda suna secondary school ita ce sanye da wannan shigar me ya faru? Me ya mayar mata da Ayra haka? Bata yarda ta zauna ba har sai da ta cillawa Ayran tambaya “Malama yaushe kika yi aure ban sani ba? Kuma wani rik’akken Malamin kika aura da ya mayar da ke haka?” Ayra ta saki murmushi tana jan hannun Salima,suka zauna a kan katafariyar kujerar mai taushin gaske da take can gefen office d’in. “Questioneer Allah ya dawo min da ke, ban yi aure ba Allah Kuma Kada ya k’addara min aure a rayuwata, ba na fatansa ko misk’ala zarratin daga yau kuma bana son naji kin sake danganta ni da kalmar matar aure please and please.” Ta fad’a tana had’e hannayenta waje d’aya alamar rok’o. Wani irin kallo galala Saliman take mata na tsananin mamaki da takaicin Ayran, ashe har yanzu wancan bahagon tunanin yana nan a zuciyarta babu abinda ya canja sai ma dad’a bun k’asa da lamarin ya yi. Tun suna yara ta sha fad’ar haka sai dai sam suna d’aukan abin shirme a Kullum kuma suka tambayeta dalili sai dai ta yi murmushi ta runtse ido tana rawar murya zata ce “Dalilina mai k’arfi ne kuma gamsashshe amma babu buk’atar ku ji shi.” Daga haka zata goge k’wallar idanunta a kuma tsayin ranar ba zaka sake Ganin walwala tattare da ita ba, wannan dalili ya saka Saliman sam bata cika damunta da tambayar son sanin mak’asudin k’iyayyarta da aure ba. Yanzun ma jan ajiyar zuciya ta yi kafin ta ce “Allah ya kyauta, ni kuwa yanzu shirin auren ne ya dawo da ni Nigeria na ga kuma ba wacce ya kamata ta shige min hidimar bikina idan ba ke ba. Tunda duk k’awayen namu sun yi aure daga ni sai ke ne dama mu ka yi jinkiri.” Tuni duk wata walwala da take fuskar Ayra ta Kau, murya a shak’e ta hau girgiza kai had’e da fad’in “Idan kin amince mai zumbulelen hijabi da nik’abi ta ja ragamar bikin ki sai na ce you are welcome.” Kallon cikin ido Salima take mata kafin ta ce “As how Malama? Kada dai ki ce min duk in da za ki da wannan shigar ki ke zuwa?” Ta girgiza kai cike da tabbatar mata “Bayan ku na kusa da ni da muka yi secondary tare ba wanda ya san kamannin Ayra Gaya ko mutanen da muka yi jami’a tare tsirari ne suka sanni, bari na sanar miki k’arshe mutanen companyn nan ba su san zahirin kamanni na ba, da wannan shigar suka sanni na ci sa’a companyn na mu ne ba wanda zai takura min akan shigata. Ko yanzu ba ki ga sai da ta fita sannan na bud’e miki fuskata ba?” Saliman ta sake dubanta tana mamaki da al’ajabi da wani ne da kyan Ayra cike da fariya zai dinga nuna shi amma ita kyan ne ma bata son a dinga gani ta ‘dan jijjiga kai kafin ta ce “Kada dai ki ce min duk don kada ki samu miji ki ke aikata haka?” Ayra ta d’aga kai tana sakin murmushi “Ko Shakka babu, tunda na taso na lura maza suna son d’aga min hankali Saboda fuska da kyawun jikina na gwammace na zama haka, ba su ganni ba ma balle su kwad’aitu da so na.” Saliman tana sakin wani irin bahagon murmushi ta ce “Sai dai idan ubangiji bai nufa ba, da ikon rabbissamawati sai alkadarinki ya karye soonest za ki aure.” Wani irin kallo Ayra take mata da idanunta da suke bayyana tsagwaron b’acin ranta ta janye hannunta daga kafad’arta cikin b’acin rai ta nuna ta da yatsa “Matuk’ar kin San irin alkaba’in da za ki dinga janyo min kenan, na rok’eki kada ki sake bayyana fuskarki a a idanuna sabida komai ma zai iya faruwa siblings d’ina ma ina samun mummunan sab’ani da su a duk lokacin da suka min irin wannan.” Hawaye ne fal idanunta ta mik’e ta shige toilet d’in da yake office d’in. Jikin Salima Sa’ad ya yi sanyi sosai har ta ji tana nadamar furucinta ita kanta hawayen ne yake son zubo mata. Fitowar Ayran daga toilet ya saka hankalin Saliman ya sake ta shi ganin yarda idanunta suka jirkita saboda tsananin tashin hankali. Sai dai da murmushi ta ke kallon Saliman da alamun son kawar da waccan damuwar daga ranta. Ko bakomai Saliman bak’uwace shekara nawa ba su had’u ba bai kamata ta bak’unceta da wannan yanayin ba. Ta dafa kafad’arta tana sake wawuro murmushin duk da k’ok’arin kufce mata da yake son yi ta saki ajiyar zuciya. Idanunta cikin na Saliman ta ce “Kada ki damu K’awata komai ya wuce raina ne ya b’aci, bana Iya controlling temper d’ina a duk lokacin da aka bijiro min da waccan maganar dafatan za ki kiyaye please.” Da sauri Saliman ta d’aga mata kai tana sakin tata ajiyar zuciyar had’e da fad’in “Alhamdulillah, wallahi na zata kina fitowa shak’eni za ki yi.” Murmushi Ayra ta saka had’e da sake mayar da nik’ab d’inta ta sakeshi ya rufe mata fuska ruf jin ana mata knocking sannan murya a kaurare kamar yarda ta saba kaurarata don bata son ko dad’in muryarta ya ja hankalin maza, balle su so sanin fuskar mamallakiyarta, ta bada izinin shigowa. sakatariya ce take sanar da ita zuwan wani bak’on costomern su da ya saba zuwa siyan kayan k’awata toilet. Tana ba shi izinin shigowa Saliman ta mik’e tana fad’in “Ayra bari na wuce Zan shigo Gida In sha Allah don ina son ki taya ni zab’an outfits da zan amfani da su lokacin biki, may be jibi tunda week end ne ki ganni ki turo min address d’in gidan.” Ayra ta zura hannu a jaka ta ciro mata compliment card da address d’in gidansu yake jiki ta mik’a mata. Saliman ta sa hannu ta amsa tana nazarin yarda take jin sunan unguwar ta railway, jin shigowar mutumin yasa cikin azama Saliman ta mata sallama ta fice. Tsawon mintuna suna k’ulla harkar kasuwanci da mutumin ba tare da ya san yarda fuskarta take ba, har mamakin yarda take k’udundune fuskarta yake don ko k’wayar idanunta baya gani, ya sha tunanin wani irin miji take aure mai matuk’ar tsanani da takura har haka da ko yatsun matarsa bai amince a gani ba. Sau tari ya kan ja ajiyar zuciya ya kuma jinjinawa mijin nata a zuciyarsa don ko bakomai ya yi maganin masu zalamar kallon mata irinsa, duk ga tunaninsa Ayran matar aure ce. Yau d’in ma siyayya mai yawa ya musu sannan ya mata sallama bayan ya tura mata takardar da take nuna shaidar ya biya kud’in. Ayra ta bi bayansa da kallo tana mamakin yarda yake kafeta da ido ta tabbata da zata bari ya ga fuskarta ba abinda zai hana shi nuna mata zalamarsa a fili, ta ja dogon tsaki had’e da jin tsanarsa a ranta ta tsani kallo ta kuma tsani duk namiji mai kallon mata irin kallon da ake kira kallon k’urilla. Daga wannan takaicin ta ji aikin ma ya gundureta gaba d’aya ta yi switching system d’inta had’e da mik’ewa ta fara tattara komatsanta da niyyar tafiya gida. _____________ A harabar gidan nasu da yake railway tsaye kusa da maigadi Mal. Hadi ne yake masa magiyar a bar shi ya shiga. Mai gadin ya kafa ya tsare a kan dokar gidan da Ayra ta kafa masa na rashin amincewa duk wani namiji shiga gidan sai da sanin ta matuk’ar ba d’aya daga cikin surikan gidan ba, shima ta jaddadawa mai gadi idan da wasu suke tare ya tbbata ya sanar da ita zuwansu kafin su shiga cikin gidan, duk wannan tana yi ne a k’ok’arin killace kanta daga idanuwan duk wani namiji. Dannowar kan motar Ayran ya bawa Baba mai gadi damar fad’in “Alhamdulillah ga Hajiyata nan ma ta zo idan ta amince ka shiga sai ka shiga.” Malam Hadi ya hau gyara babbar rigarsa da ta sha guga daga shekara sai shekara yake sakata, ranar idi Amma yau ganin gidan da zai zo yasa ya cancad’e kwalliya cikinta shine har da nad’a rawani. Gyaran murya kawai yake yana shaidawa Maigadi “Yanzu zaka ga ko wanene ni? Zaka san Ka wulak’anta ni saboda ni da mahaifin yaran nan ba mu da wani banbanci.” Hankalin Maigadi ya d’an tashi ga zatonsa duka abinda Hadin ya fad’a da gaske ya ke. Tun da ta yi parking bata fito daga cikin motar ba illa k’urawa mutumin da yake tsaye kusa da mai gadi ido da ta yi. Ba zata mance da shi ba, ba zata manta wannan fuskar ba, fuskar makusancin aminin mutumin da ya kira kansa da sunan mahaifinsu. Ta runtse idanunta ta bud’e tana sake sauke magananta a kan mutumin, wani b’acin rai da tashin hankali yana sake ziyartarta ta tsani duk wani mutum da yake da alak’a da wancan mutumin mai amsa sunan mahaifi a wajensu. A hankali ta cigaba da dukan sitiyarin motar cikin mabayyanin b’acin rai. Ji take tamkar ta fisgi motar da gudu ta je ta take shi ta huta da ganin fuskarsa da take tuna mata da fuskar wancan mutumin. Tsawon lokaci tana cikin motar ba tare da ta san me ya kamata ta aikata ba. Tabbas ta san idan ta bari ya shiga gidansu yau mahaifiyarta Ammaty ba zata kwana lafiya ba, sai ya tayar mata da tsohon mikin da yake zuciyarta. Dabara ce ta fad’o mata, hakan ya sa ta daddage ta sakarwa Baba Mai gadi wani irin gigitaccen horn, da ba shiri ya saka shi tahowa wajenta a sukane. Da kyar ta sauke glass d’in motar idanunta a rufe ta watsowa Baba mai gadi tambayar “Me wancan mutumin ya ke yi a gidan nan?” Baba Mai gadi da bai san dawar garin ba, cikin in ina ya ce “Wai wajen Hajiya yazo.” Ta ciji leb’enta na k’asa da k’arfin gaske kafin ta murza yatsun hannunta suka bada k’ara k’as-k’as “Ka sanar da shi kafin na irga Biyar ya bar cikin gidan nan idan ba haka ba, ko ma me ya faru da shi ba ruwana.” Da sauri kuwa Baba Mai gadi ya koma wajensa ya sanar da shi sak’on, sai dai madadin ya tafi wata dariya ya tuntsire da ita cike da tabbatarwa ya ce “Ka koma ka sanar da ita ba inda zan je sai na ga Hajiya.” Tana daga cikin mota tana kallon yarda yake da hannunsa alamar da gaske yake abinda yake nufi ba ta yi magana ba illa ficewa da ta yi ta isa inda suke cikin tsukakkiyar fuska duk da ba ‘a ganinta kafin ta isa wajen ji take tamkar ta waska masa mari sai dai bayyanarta wajen ya canja mata tunaninta ganin yarda mutumin yake kallonta shek’ek’e kamar ya ga kashi. Ba tare da ta gaisheshi ba ta nuna masa gate cikin dakiyar murya ta ce “Cikin lumana Alhaji ka fita daga gidan nan.” Cikin izgili ya ce “Idan na k’i fa tabbatacciya wad’anda suka d’ebe kayansu daga gaban ma’aiki, kuna nan cikin daula kun bar ubanku cikin bak’in talauci wallahi ku kiyayi ranar had’uwarku da Allah.” Cikin matuk’ar b’acin rai ta zare nik’ab d’in idanunta fuskarta ta bayyana sosai kamanninta suna nan ba su b’ace masa ba Auta ce. Ya dinga mamakin girmanta da murd’ewar halinta yarinyar da da ko hannu ba zaka saka mata a baki ta ciza ba. Ta sake nuna masa gate “Na had’a ka da Allah ka fita,ko kuma na saka fita ta dole.” Wata dariya ya saki yana sake gyara zamansa kan kujerar robar da yake zaune a kai. “Fitar da ni ta dole” a zafafe ta juya ta nufi can baya inda Ke jin karnukansu suke na police dogs guda uku manyan gaske, da sauri ta sake su ta nuna musu gate. TAkAICIN UBA… Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. Biya ‘dari biyar kacal don a yi tafiyar Ayra Gaya da ke… Ko ki biya special people (Mutane na musamman da ake tura musu kai tsaye cikin wayoyinsu. Akan Naira dubu kacal. Ta wannan account ‘din 2118666253 U B A) Page 5___ Da wani irin wawan haushi suka nufi kansa, in da hakan ya saka shi wani irin rawar d’ari da firgici k’afafunsa suka shiga rawa. Ya nufi bakin gate da sauri da niyyar fita, sai dai tuni suka cim masa, bai san sanda ya saki fitsari a wandonsa yana ihu da tumami. Sai da Ayra taga suna nufin yagalgalarsa sannan ta dakatar da su ta hanyar kad’a musu harshe irin yaren da take musu kenan idan tana so su bar abu. Cak suka tsaya sai dai suna zazzalo harshensu idanunsu a Kansa da yake mutsu-mutsu ya kasa nutsuwa sam ga ni yake kamar kwanansa ya k’are. Rok’on Mai gadi yake da ya bud’e masa gate d’in ya samu ya fece amma Ayra ta k’i bada damar hakan. Cikin takun isa ta k’araso wajen idanunta cikin nasa ta tsaya a gabansa tare da nuna shi da yatsa. “Ina baka shawarar kada ka sake tunkarar gidan nan, idan ba haka ba Wallahi ka sake zuwa sai na basu damar da za su yagalgalaka. Idan ma Shine ya turoka ka d’agawa uwata hankali ka gaya masa ya shirya tafiya kotu ne? Don wallahi sai na makashi a kotu bisa tarin laififfukansa na baya don ba zan bari wani abu ya samar min mahaifiya ba matuk’ar ina raye.” Jikinsa sake b’ari yake yana tattare rigarsa ganin suna son sake nufarsa Ayra ta dakatar da su sannan ta saka Baba Maigadi ya bud’e masa gate d’in kafin kace me Hadi ya arce da gudu kamar mai gudun tsere da gaske karnukan sun firgita shi. Dariya Sosai Ayra ta yi kafin ta mayar da gate d’in ta rufe ta mayar da kallonta kan Baba Mai gadi. “Kada a sake bud’ewa Mutumin nan gate doka ce na saka.” Gyad’a kai Baban ya yi don bai hango wasa a lamarinta ba illa tsananin b’acin rai da ya hango a kan fuskarta. Ya bi bayanta da kallo tana shigewa cikin gidan. Mamaki Baba Mai gadin yake jin cewa wai mahaifinsu yana da rai har ma yana cikin wahala amma sun kasa taimaka masa, ya shiga tunanin wani irin girman laifi mahaifin nasu ya musu da har suka shafe labarinsa a duniyar su. Ya saki nauyayyiyar ajiyar zuciya yana tunanin koma menene Lamarin Mai girma ne. ________________________ Ko da ta shiga Amman tasu tana d’aki hakan ya sa bata damu sosai ba don ta san bata ji duk abinda ke faruwa ba barcin k’ailula take na bayan azahar zuwa la’asar. Zubewa ta yi kan kujera barcin take son yi amma bata son shiga d’aki tunanin da ta saba ya mata rufdugu musamman mutumin nan da yazo ya sake dawo mata da abinda ya wuce take ganin kamar a lokacin abubuwan suke faruwa. Ta runtse ido wani irin zafi take ji k’irjinta yake yi bata san Waye ya nuna masa gidan ba….. Da sauri ta rarumi wayarta a hasalance ta shiga kiran Dijah Yayarta da take bi, tana zaune a unguwar shara’da. Sai da ta yi ringing sosai kafin Dijahn ta ‘daga. Ayra ta sauke ajiyar zuciya kafin ta gyara zamanta ta ce “Mutumin can da Yake amsa sunan mahaifinmu kin san yau ya turo Mak’ocinsa Hadi Gidan nan?” Da sauri Dijah ta zaro ido kafin ta ce “kan Uban can again? Har yanzu bai hak’ura da nacin mu yafe masa ba kenan tsawon shekara uku idan ban mance ba rabon da ya sake aikowa.” Ayra ta ja ajiyar zuciya kafin ta ce “To yau ya aiko ni kuma na rakaka Hadi da kare a yarda ya tsorata na san kuma ba zai sake waiwayo gidan nan ba.” Dijah ta yi dariya sosai kafin Ta ce “Amma Ayra kin kyauta min, sai dai Kada ki sake ki gayawa Yaya Zainab don kin san har gobe ita burinta mu manta abinda ya wuce mu yafewa Baba..” Ayra ta ja tsaki ta ce “Abinda ba zai tab’a faruwa a rayuwa ba kenan ba yafiya tsakanina da Baba wallahi.” Dijah ta ja ajiyar numfashi ita kanta zuciyarta ta fara cunkushewa da b’acin rai balle Ayra da lamarin Uban nasu ya fi shafarta murya a sanyaye ta ce “Relax Ayra ba wanda zai ce ki yafe masa ba ke ba ko ni babu yafiya tsakanina da wannan mutumin da yake kiran kansa da sunan mahaifinmu.” Ayra tana sakin wata irin ajiyar zuciya ta kashe wayar ha’de da kishingi’da ta runtse idanunta da k’arfi Ko sunan mahaifinta bata son tunawa balle ta jingina shi da sunanta shi yasa a makaranta ma kowa da AYRA GAYA ya santa kai da dama zata iya mayar da sunanta AYRA TALATU. Don shine Sunan ka’dai da ya kamata ta jingina sunanta da shi.. cikin tsananin zuzzurfan tunani wani irin barci mai nauyi ya ‘dauketa. (Cikin barcin ta yi mafarkin da y’a gigita tunaninta, mafarkin da shine ya zamo somin tab’i na rugujewar duk wani shirinta, mafarkin da kai tsaye zata iya danganta shi da abubuwa da dama a rayuwarta…. Bata son tabbatuwar mafarkin Amma ta San abu ne me wuya bai tabbata ba, dalili ta Saba mafarki su zama zahiri a rayuwa.) ______________ Sai da ya isa bakin titi sannan ya dakata daga gudun fanfalak’in da yake. Bakin wata bishiya ya tsaya yana haki gaba d’aya ya gama tsorata, tsinuwa kuwa Ayra ta sha ta ta fi cikin kwando. Sai da ya samu nutsuwa sosai sannan ya lura da cewa ko takalma babu a k’afarsa ya ja tsakin takaici yana da tabbacin a can gidan ya bar takalman nasa. Ya shafa kansa hular ma babu sai babbar rigarsa da take rik’e a hannunsa bai ma san sanda ya cireta ba. Ya shiga laluban aljihunsa ya ci sa’a yana da Naira d’ari biyu kacal da ta rage masa hakan ya sa ya shiga neman abin hawa. Sai dai abin takaici duk wanda ya gan shi k’in tsayawa yake ganin k’afafunsa ko takalmi babu ga wando a yage haka yasa suke masa kallon mahaukaci sabon kamu. Haka ya dinga jan k’afafunsa ya san tabbas sai ya kusan kai magriba kafin ya isa gida. Ba Ayra ba a ranar har aminin nasa sai da ya tsinewa. ________ Ko gidansa bai isa ba ya zarce wajen da suke zama da Alhaji Kabirun duk yammacin duniya. Ya ci sa’a ya tarar abokan zaman nasu ba wanda ya dawo da kasuwa balle su zauna dama su ne ko da rana ka zo zaka same su a wajen dalilin rashin aikin yi. Alh.Kabirun ma a zaune yake yana tsimayin jiran aminin nasa yana addu’ar Allah yasa a dace a wannan karan idan ya je. Duk abin duniya ya isheshi nadama yake sosai da sosai a cikin ransa. Yana ganin Mal. Hadi gabansa ya fad’i don ko bakomai ya tabbata ba’a yi nasara ba musamman yarda ya ganshi kamar an Jefo shi ba nutsuwa sam a tattare da shi. Zuciyarsa ce ta buga da k’arfin gaske, baya fatan jin mummunan sak’on da Hadi zai ba shi don ya tabbatar ba abin alheri ba ne, ba sai ya fad’a ba ya san hak’ansa bai cimma ruwa ba, ya sani ba su yafe masa ba kamar yarda dama yake hasashen hakan, kafiya da nacin Hadi ne yasa ya ce ya je. Sosai zuciyarsa ta yi nauyi ya sake jingina sosai da jikin bango yana lumshe idanunsa da suka jirkata suka bayyana tsananin tashin hankalin da yake ciki. Hadi ya Galla masa hararar gefen ido da takaicin rashin tamabayarsa duk da ya san baya buk’atar ji ne amma dole ya gaya masa tilas su raba b’acin ran da zuri’arsa ta k’unso masa da shi. Ya gyara zamansa Fuskarsa a d’aure ya ce “Kabiru ka haifi bala’i, ka haifi yaran da suka d’ebe kayansu daga gaban Annabi. Auta ce fa ta so ganin bayana ba ma yayyanta ba, yarinyar nan har ta yi girman da zata kasa ganin martabata ina ce sanda abin nan ya faru bata da wayon da zata gane komai amma idan ka ga abinda yarinyar nan ta min zaka yi mamaki.” Wani irin duka k’irjinsa yake musamman da ya ji ya ambaci sunan Auta hankalinsa ya matuk’ar tashi ya fi jin shakkar ta fiye da y’an uwanta ya fi jin shakkar had’uwa da ita fiye da ta mahaifiyarta ya san girman laifin da ya aikata mata ya fi na sauran. Cikin takaici Hadi ya ce “Ina tabbatar maka idan ba gidan radio ka shiga ka tabbatar musu da zaka tsine musu ba ba za su yafe maka ba, matsiyata kawai kai yanzu ma baka da amfani a wajensu tunda ko aurensu za’a yi basa nemanka. Da kyar fa na sha ina gaya maka kare suka sakar min, jikina duka fitsari ne.” Duk da abin ya kai a yi dariya hakan bai sa ko murmusawa Alh. Kabiru ya yi ba don shi kad’ai ya san halin da zuciyarsa take ciki, ta masa nauyi sosai sai k’ok’ari yake da numfashinsa amma ya gagara samuwa, tuni idanunsa suka fara k’akkafewa Malam.Hadi bai yi auneba sai ganinsa ya yi ya zube a wajen. Da sauri ya d’aga shi ya hau jijjiga shi sai dai ba alamar numfashi a tare da shi. Mal. Hadi hankalinsa a tashe ya shiga neman taimako kasancewar gidan Alh.Kabirun da y’ar tazara daga inda suke zama. Mutane suka afu a kansa ana neman yarda za’a samu a masa taimakon gaggawa….. ___________________ Ta cigaba da barci mai nauyin gaske, barcin da zata iya kiransa mara dad’i kuma mai wahala a wajenta don dai babu sukunin zuciya barcin ya d’auketa hakan yasa ta cigaba da wasu irin birkitattun mafarkai. Bugun k’ofar da ake ne ya sata farka wa ba shiri da kyar ta lalubo addu’ar tashi daga barci ta karanta, idanunta sun mata nauyi sosai kuma har a lokacin ba ‘a daina bugun ba. Ta saki tsaki kad’an sannan ta ja hijab d’inta ta saka ta nufi k’ofar don bud’ewa don dai ta san ba namiji ba ne, sanin cewa Baba Maigadi ya rik’e zancenta gam kamar karatun sallah na rashin barin maza su shigo musu gida ba tare da sanin su ba. Tsayawa ta yi kad’an a bakin k’ofar cike da muryar barci take fad’in wanene?” Daga can aka ce mata “Mune” ta saki ajiyar zuciya kafin ta murd’a handle d’in ta bud’e jin cewa mata ne. Idanunta ya sauka a kan Dattijuwar matar fara k’al mai zubin larabawa kana ganinta ka ga sadakar yalla. Murmushi ta d’an saki kad’an had’e da fad’in Sannunku da zuwa Ku shigo mana.” Ta ja gefe ta basu hanya suka shigo wani sihirtaccen k'amshin turare yana fitowa daga jikinsu da alama Gabbasa suka wa kayan. Ta cigaba da jan zumbulelen hijabinta kafin ta russuna ta gaida matar, duk da bata shaidata ba kallon sani kawai take mata. Da fara'a sosai itama take amsawa shekarun da yawa ba zata banbance wannan y'ar aminiyar tata bace ko kuma jikarta. "Talatun tana nan?" Da sauri Ayra ta d'ago tana kallonta, jin sunan da ta kira mahaifiyar ta da shi, Allah yasa dai ba daga dangin mutumin can take ba da na ji takaicin gaisuwar da na mata. Ta ayyana hakan a ranta don ba wanda yake kiran Amman da wannan sunan sai wanda ya yi mata sanin da can. kamar ta ce bata nan sai dai ta ja bakinta ta tsuke amma tuni duk wata walwala ta fuskarta ta d'auke tamkar d'aukewar ruwan sama. Ta mik'e tsaye had'e da cewa "Bari na duba." Daga haka ta hau matattakalar benen inda zata sadaka da d'akunan barcinsu. Allah ya so bata saka Mai aiki kawo musu kayan motsa baki ba da ta yi takaicin hakan. A kan dadduma ta samu Amman tana karanta Azkar na bayan Sallahr la'asar. Murya can k'asa ta yi sallama ta zauna a gefen Amman had'e da saka kanta kan kafad'ar Amman wata kasala take ji tana dabaibayeta da wata irin fad'uwar gaba. sosai k'irjinta yake bugawa har Amman ta d'ago a tsorace tana kallonta da sauri tana fad'in "Ke lafiya?" Da sauri ta kama hannun Amman ta saka a k'irjinta tana lumshe ido hawaye sai kwarara yake ta ce "Amma ba ni da lafiya, k'irjina ne yake bugawa daga yin ido biyu da bak'uwarki." Amma ta zaro ido tana fad'in "Wacece kuma bak'uwata?" Ayra ta saki wata ajiyar zuciya haeshenta ya yi nauyi sosai kafin ta ce "Tana k'asa Amma, Allah yasa ba da mugun abu ta zo miki ba don ni ban tab'a ganinta ba sai yau." Jikin Amma ya yi sanyi sai dai bata nunawa Ayra ba, amma tun Ayra tana yarinya in dai ta yi irin wannan abun to tabbas abin farin ciki ko akasinsa ne yake faruwa.. muryar Amma a sark'e tana shafa kan Ayran a hankali ta ce "Khairan In sha Allah. ta shi muje na ga wacece." Daga Taskar Jikar Nashe.❤️🙏 TAKAICIN UBA…. Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Page ____6 Da sauri Ayra ta girgiza kai tana dafe da k’irjinta ta ce “Je ki kawai Amma bana son sake ganinta gabana sake tsananta bugu yake wani irin kwarjini ne da ita da kaifin idanu, masu sanya mutum rusunar da nasa idanun ko bai shirya ba.” Amma ta mik’e ita ma nata jikin a sanyaye ta nufi hanyar da zata sadaka da step d’in da zai saukar da kai parlourn k’asan. Jin saukowa daga bene yasa bak’uwar ta yi saurin juyowa ta zubawa step d’in idanu bayan ta mik’e tsaye cike da zak’uwa da son zuwan Talatun, ta zare glass d’in idanunta tana sakin kyakykyawan murmushin da Ya sake k’awata kyan fuskarta. Ita kanta Amman ba k’aramar juriya ta yi ba da Allah ya kiyaye bata kifa ba da ta yi ido biyu da bak’uwarta ta. Tafiyar ta gaba d’aya a harhad’e ta isa wajenta da sauri da niyyar ta tabbatar da zahirin abinda take gani a idanunta shin da gaske ita d’in ce ko kuma gizon da ta saba mata ne a shekarun baya da suka wuce? Ta bud’e baki da k’yar ta na nunata da d’an yatsanta manuniya ta ce “Hameedah? Shin da gaske kece ko kuwa mafarkin da na saba yi ne?” Ko kafin ta Ankara Hameedah ta kai mata runguma hakan kuma shi ya cire mata kokwantonta ta tabbatr dai Hameedah ce a gabanta, Hameeda dai aminiyarta ta k’uruciya da k’addara ta rabasu, tun bayan rasuwar mahaifin Hameedahn suka tattara suka koma k’asarsu ta Labanon bata sake ganinta ba sai yanzu. Babu abinda zai saka ta manta da fuskar Hameedan don babu abinda ta canja sai alamun girma da ya bayyana k’arara a tare da ita. Sun dad’e rungume da juna suna sakin hawayen farin ciki, kafin Hameedan ta saketa tana kauda hawayen idanunta wanda yake nuni da zallar farin cikin da take ciki. Ta dad’e bata ga abinda ya faranta mata rai kamar had’uwarta da aminiyartata da take d’aukan ta kamar jininta. Amma ta Saka hannu tana share mata hawayen kafin ta ja hannunta su zauna akan kujerar mai cin mutum hud’u. Sai da ta zaunar da ita sannan ta koma bakin matattakalar benen tana k’walawa Ayra kira. Sosai Ayra ta ji Kiran har tsakiyar kanta, abinka da wanda yake a rud’e tuni rud’ewar tata ta ninka ta da. Ta manta da hijabinta ta sauko a guje tunani take wani abin ne ya samu Ammanta. Turus ta yi tana dubansu ganinsu a zaune cikin matsananciyar walwala da farin ciki. Yara mata guda biyun kuwa suka zubawa Ayra ido suna mamakin tsananin kyan da Allah ya bata da dirarren jiki ko su da suke ruwa biyu ba zasu nuna mata komai ba. Ashe a Nigeria ma akwai kyawawa da Kyansu ya kere na su. Sai sannan Ayra ta ankare da cewa ta manta hijabinta da yake mata kariya daga kallon k’urilla. Gabanta ya cigaba da matsanancin bugu idanunta a k’asa ta kasa jurewa kallon cikin k’wayar idon bak’uwar Amma. Dattijuwa Hameeda kuwa cikin ranta ta dinga yabon kyawun Ayra har ta ji wani lamari ya fad’o mata ta dinga Binta da kallo tana hasashen abinda zata had’a d’in shine abinda ya dace. Murmushi sosai ya dinga bayyana a fuskarta ta kalli Amma kafin ta ce “Fatabarakallahu Ahasanul khaleek’in ita ma wannan ta muce?” Amma ta d’aga kai tana murmushi kafin ta ce “Itace Autar sauran duk na musu aure.” Gaisuwa sosai suka sake yi da Amma da Ayran Amman ta kalli Ayran ta ce “Wannan itace Hameeda babbar Aminiyata da nake baku labari, nake sanar da ku tun bayan rasuwar mahaifinta Mamansu ta wuce da su k’asar su Labanon.” Ayra a d’an rud’e ta d’aga kai tana jin takaicin kallon k’urillar da suke Binta da shi. “Maza ki had’o musu drinks da abinci, amma ban ji dad’i ba da baki sanar min zuwanku ba, yaushe kuka shigo k’asar?” Dattijuwar ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Tun bayan rabuwata da k’asar nan sai jiya nazo shima d’in Baban yaran nan ne ya damu a kawosu su ga y’an uwa saboda halin rayuwa ina zuwa kuma na je ainahin main house na ku anan ake bani address d’in nan d’in.” Ta fad’a cikin juyayyiyar hausarta. Amma ta d’aga kai kafin ta ce “Amma kuwa ba ki kyauta ba, ace yara ba su san dangin ubansu ba sai yanzu.” Hamida ta saki murmushi ta ce “Yayansu yana zuwa ai, the moment ya samu hutu yana yawan zuwa don first and second wife d’insa har third ma anan ya auresu, sune dai basa zuwa.” Amma ta ce “Ma sha Allah suma sun girma su nawa ne?” Hannayenta ta d’aga tana counting shida cif But biyu maza hud’u mata.” Amma ta girgiza kanta kafin ta ce “Allah musu albarka, yanzu Yayan nasu matansa har uku?” Ta fad’a tana k’ok’arin serving nasu abincin da Ayra ta kawo ta jere musu ta wuce sama. Hameedah girgiza kai ta yi tana d’an sakin murmushi kafin ta kalli y’an matan ta ce “Ku bi k’awarku sama mana kafin mu gama ganawa kun san bana son ina magana ana zaune.” Da murmushi suka mik’e bayan sun d’au plate cike da snacks, Hameeda ta kalli Amma ta ce “Autannina kenan su twins ne.” “Da gani babu tambaya.” Amma ta fad’a tana murmushi. “Zallar kamanninsu ya isa ya bayyana kansu a matsayin twins, ya sunan su?” “Tayseer da Tasleem.” Hameedah ta fad’a idanunta akan Amman da take cewa “Allahumma barik.” “Su kuma naki yaran su nawa ne?” Amma tana murmushi ta ce “Hameedah kenan, kina nan da halinki abin babu kara? Madadin ki ce na ki yaran sai kice nawa yaran, su bakwai ne Shu’ayra da suke kira Ayra ce auta, sauran duk suna d’akin mijinsu itama Ayran dalili ta cunkushe a ranta da ya nuk’urk’usar da son tarayya da kowane d’a namiji a zuciyarta, idan banda haka da tuni tana d’akin mijinta.” Ji ta yi kawai Hameedah na fad’in “Alhamdulillah Ma sha Allah, ki ce kaya ya tsinke a gindin kaba tabbas abinda Allah ya jefoni yi kenan.” Cike da mamaki Amman take bin ta kallo, kallon da k’arara yake nuna son k’arin bayani. Gaba d’aya fuskar Dattijuwa Hameeda ya canja idanunta suka d’an canja launi daga kalar fari k’al da suke a da kafin wanzuwar b’acin ran zuwa kala mai sirki da ja kad’an a ciki. Kamar ba zata ce komai ba ta d’au cup mai cike da kunun aya mai mugun sanyi ta kai bakinta sai da ta sha sosai don gard’in kunun ayar ya ratsa har tsakiyar kwanyarta ba d’an kad’an ba ya yi dad’i. Ta dire cup d’in tana sake sakin murmushin da kai tsaye za’a iya kiransa na k’arfin hali sannan ta ce “Alfarma d’aya za ki min Salamatu, ki bawa d’anki Amin auren Shu’ayra ko dukkan matsalolinsa za su zama labari.” Sosai Amman ta razana da jin abinda ta ce mata sai dai bata bayyana hakan ba illa shiru da ta yi tana nazari a zuciyarta ya zama dole ta gayawa Hameeda wacece Ayra? Ta hakane kawai zata san cewa Ayran ba ta dace da zama maganin matsalolin d’anta ba, bisa dalilin tarin nata matsalolin da suke zube a kwanyarta. Jin shirun Amman ya yi yawa yasa Hameeda ta matsa kusa da ita sosai ta kama hannayenta gaba d’aya ta matse su cikin nata murya a sark’e kamar mai don yin kuka ta ce “Ki taimake ni Salamatu, wannan ne hope d’ina kad’ai akan rayuwar Al’amin.. Bayan aurensa da matarsa ta farko da suka so juna kamar za su mutu, anan Abuja suka had’u ya aureta ya tare anan Abujan, cikin hukuncin buwayi gagara misali ranar da tazo haihuwar d’ansa na biyu ta mutu. Lamarin da ya gigita Al’amin da kyar na shawo kan matsalarsa duk da har yanzu ba zance ya dawo normal ba ana dai gurgura rayuwar yarda ta samu. Al’amin mai son jama’a mai wasa da dariya sakin fuska da walwala gaba d’aya lokaci guda aka musanya halayensa zuwa wani irin baud’ad’d’en mutum mai saurin fushi da yawan hassala. Ya d’au tsawon lokaci yana katantawa da rayuwarsa ya kasa nutsuwa ma ya yi abinda ya dace sai da na saka aka dinga masa rok’on Allah sannan na samu ya d’an rage wasu abubuwan. Mutane da dama suka dinga ba ni shawarar na aura masa aure da son sa ko ba son sa, na dinga bin shawarar mutane ina aura masa auren sai dai abin haushi duk matar da na aura masa bata iya shawo kansa, don bata shekara suke rabuwa, yanzu zancen da nake miki tsawon shekararsa biyar rabon da ya yi aure. Yaron da matarsa Halim ta bar masa har ya shiga secondary school shekararsa sha d’aya. To yanzu na ga Ayra kuma ta dace da irin matar da duk k’in sa da aure idan ya ganta sai ta masa, tana da structure d’in da zata janye hankalin namiji ko bai shirya ba, duk da wa’dancan ‘din ma kyawawa ne amma a haka ya rabu da su. ki taimaka min ki ba shi aurenta mu yi tuwo na Maina.” Tsit Amma ta yi tana murzar goshinta. Wannan fa shine ga bikin zuwa babu zanin d’aurawa, don dai Hameeda bata san wacece Ayra ba shi yasa ta bijiro da wannan zancen. Ta d’au mintuna tana aikin tunani tana Tufka tana warware wa ta kasa bawa Hameeda gamsashshiyar amsar da ta dace. Da kyar ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Ayra ba matarsa bace, saboda sam bata dace da shi ba, idan aka yi auren komai k’ara damalmalewa zai yi madadin abubuwa su gyaru. Dukkanninsu akwai wani ciwo da dafi a zuciyarsu wanda zai tarwartsa duk wani farin ciki da zai tunkarosu a rayuwar aurensu. Ayra ta k’udirce ba zata tab’a aure ba a rayuwarta haka zata zauna, yayin da Amin ya zama mijin matacciya. Ta yaya kike tunanin Ayra zata yi abinda har zai gusar masa da tunanin waccen matar tasa alhali itama ba ta son auren? Don haka ki yi hak’uri ki bar maganar kada ayi abinda zai zo Ya lalata mana zumunci. Akwai bak’in fentin y’ay’a maza a zuciyar Ayra wanda yasa ta tattara duka maza ta saka su a ma’auni d’aya. Allah ya ba shi matar da zata dace da shi.” Hameedah ta dinga girgiza kai ba don ta gamsu ba sai dai ta’ajibin lamarin. Me zai janyowa Ayra tsanar aure da y’aya maza haka? Ko ma menene tabbas lamarin mai girmane sai dai sam ba zata janye k’udirinta ba, ta san Ayra da zarar taga Amin zata ji tana sonsa don yana da duk wasu tarin qualities da zai saka mace ta so namiji ga nata hasashen fa kenan? Bata san Ayra ta yi nisa bata jin kira ba, ko da gold aka k’irk’ireshi bai zama lallai ta so shi ba. “Ki bari na gwada da kaina zan mata magana In sha Allah za’a dace.” Amma ta saki murmushin takaici kafin ta ce “Shikkenan tunda ba ki yarda ba, bari na kira miki ita.” Daga haka ta haye matattakala don kiran Ayran da take can tana kallon twins sun baje sai hira suke kamar da can sun santa. Ba su san haushi suke bata ba, don ita bata son mutum mai yawan surutu. Shigowar Amma da kiranta ne yasa duk suka sauka k’asan a tare. Hameeda na ganinsu ta nuna musu hanyar sama alamar su koma ba da su zata yi magana ba. Gaban Ayra na fad’uwa ta zauna daga gefen kujerar da take kusa da dattijuwa Hameedan, tana jin k’irjinta kamar zai tsage zuciyarta ta fito. Da murmushi sosai dattijuwar take kallonta kafin ta gyara zamanta ta ce “Haba daughter na matso nan kusa da ni, magana za mu yi mai mahimmanci bana son kowa ya ji.” Zuwa lokacin ba k’irji ba kad’ai hatta gangar jikin Ayra kad’a wa take da mugun k’arfi, bata son mafarkinta ya tabbata bata son mugun mafarkin da ta yi a barcin ranar ta ya tabbata, ta dinga jin kamar ana kad’a mata gangi. Kasa matsawar ta yi illa baya da ta yi ta rab’e jikin kujerar cikin rawar murya ta ce “Nan d’in ma is okey Hajiya.” Murmushi Hameeda ta yi ta ce “Kada na sake jin kin kira ni da Hajiya ki kirani da sunan da yara suke kirana da shi Ummi tunda kema y’ata ce.” Ayra gyad’a kai ta yi tana wasa da zobban da suke hannunta idanunta a k’asa Ummi ta d’an matsa kad’an kusa da ita ta ce “Ki yi hak’uri da abinda za ki ji daga bakina, ki sani komai muk’addarine daga Allah, sannan ina son shaida miki a shekarunki ba abinda ya dace da ke irin a gan ki a d’akin auren sunnah, me zai saka d’an Sunna ya ce baya son Sunnar Manzon Allah ai aure ibada ne…..don haka nazo ki taimaka ki auri Yayanki Al’amin….” Cak maganar ta tsaya ganin yarda Ayran ta mik’e da sauri idanunta a waje tana mata wani irin duba nunata kawai take kafin ta durk’ushe a wajen tana fad’in “Ya ubangiji ka d’auki raina kafin tabbatuwar mafarkina, bana son aure kuma ba zan aureba da na yi aure gwara na ganni a cikin kabarina, Hajiya ina ganin girmanki please kada ki bari girmanki……” ta cije leb’enta tana tauna leb’enta cikin jirkicewar launin idanu ta fara kwararar da zafafan hawaye. Ummi Hameeda tsoro ne sosai ya kamata bata san lamarin ya kai girman haka ba……… Jikar Nashe.❤️❤️✍🏽 TAKAICIN UBA… Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. Page 7….. Da tsananin takaici Amma ta dinga bin Ayra da kallo, tana mamakin irin fetsarewar idanunta da har take fad’awa Hameeda hakan. Idanunta su suka rusunar da nata idanun da suka yi tsaitsaye kan Ummin. Hankalinta ya tashi matuk’a don ta dad’e bata ga Amma a cikin wannan yanayin ba na matsanancin b’acin rai. “Durk’usa ki bata hak’uri ki kuma b’ace min da gani, wani irin abu ki ka aikata haka? Ce miki aka yi tilas za ‘a yi a miki auren?” Idanunta ne kawai suke zubar da k’wallar ta zube a gaban Ummin harshenta na rawa ta ce “Ki yi hak’uri, I don’t meant to hurt you.” Ummin ta saki ajiyar zuciya tana d’aga mata kai, sam abinda Ayran ta yi bai girgiza ta ba, Amin yana yin wanda yafi wannan idan aka bijiro masa da maganar aure, abinda take so ta gane mai ya janyowa Ayran wannan matsanancin k’iyayyar auren, daga maganar tun ba a aiwatar ba ta shiga cikin irin wannan yanayin to ina ga ance an d’aura mata auren ba bisa ra’ayinta ba, tabbas akwai k’ura. Murya a sanyaye ta ce “Ta shi ki je Ayra, Allah ya shige mana gaba.” Ta mik’e tamkar wacce k’wai ya fashewa a ciki, gaba d’aya haushin Ummeey ya gama dabaibaye zuciyarta gani take kamar tana shirin rusa mata farin cikinta ne. Ko da ta hau sama bata koma d’akinta ba don bata buk’atar hayaniyar twins direct d’akin Amma ta shige ta kullo har da murza key. Tana buk’atar kad’aicewa don samun sauk’i daga rad’ad’in da k’irjinta yake mata. Hameeda na ganin ta gama hawa Stair case d’in ta mayar da kallonta a kan Amma da kanta yake a sunkuye. Tsam ta mik’e ta dawo kusa da ita ta sake kama hannayenta a karo na biyu ta ce “nuna b’acin ranki ba shi zai kawo warwarar matsalar yarinyar nan ba, anya kuwa babu jinnu a cikin lamarinta?” Amma ta k’ura mata ido kafin ta girgiza kai murya a sanyaye ta ce “Babu wani jinnu a cikin lamarinta, illa TAKAICIN UBA da ya gigita tunaninta ya kuma saka mata tsanar maza had’e da jingina musu suna d’aya..” Amman ta fad’a wannan karan muryarta sosai ta karye ta shiga zubar da hawaye “Mahaifinta shi ya kambama tsanar maza a zuciyarta tun tana da k’uruciyarta har ta tashi da abin a ranta, ni kuma na yi sake da na barta har yanzu ban aurar da ita ba, na bar zuciyarta a kan wancan tunanin da zaton wata rana zata fuskanci ba haka bane. Na yi nadamar hakan da na sani tunda k’ank’antar shekaru na aurar da ita, ni kuma tausayinta ne ya rinjaye ni, na fi tausayinta k’warai da gaske fiye da y’an uwanta ko don k’addarar tafi girma a kanta fiye da su.” Shiru Hameedah ta yi tana son tambayarta wacce k’addara ce amma bata fiye son k’ure mutum ba, da ta so da kanta zata fad’a mata ba sai ta tambayeta ba. Madadin yi mata kutse cikin sirrinta sai ta kawar da wancan zancen ta sako wani “Da zaki amince da na ce miki matsalar Ayra koma wace iri ce ta zo k’arshe, ki amince a wannan karan kuma ki jajirce ki bani had’in kai mu had’a aurennan da sonta ko ba son ranta na san In sha Allah babu abinda zai faru sai alheri.” Shiru Amma ta yi tana son ta bada goyon baya, tana tsoron tashin hankalin Ayran wanda bata san mai zata aikata ba, kada ta je zancen da take ya tabbata na kisan kanta a duk yayin da ta bud’i ido ta ganta a gidan aure, don haka ta kasa amincewa Ummeey illa jinginar da kanta da ta yi jikin kujera ta lumshe idanunta a hankali ta ce “Ki bani lokaci na yi shawara, koma me kenan In sha Allah za ki ji.” Ummeey ta saki hannayenta had’e da cewa “Allah yasa mu ji alheri ki yi addu’a sosai nima zan yi.” Ta d’aga mata kai. Ummeeyn ta mik’e tana cewa “Bari mu tafi mun ja lokaci da yawa dafatan kema zaki kawo min ziyara kuma don Allah shawarar taki kada ta d’au lokaci.” Amman tana kallonta ta ce “Yanzu kina nufin har mun gama hirar yaushe gamo? Haba Hameedah? Tun muna y’an mata fa rabon da mu had’u, baki tambayeni wa na aura ba wanene uban yara na? Baki tambayeni ya rayuwata ta cigaba da tafiya ba bayan kin tafi kin bar ni cikin matsaloli ba?” Hameeda ta sake zama had’e da dafata ta ce “Ni kaina ina son jin labarin bayan rabuwa, amma kada ki manta na sanar dake jiya na shigo k’asar nan ina da gidajen zuwa da yawa baya ga haka kuma naga alama akwai damuwa sosai a tare da ke bana son tuno miki da waccan bak’ar rayuwar, abu d’aya da zan tambayeki an ga dangin Innah bayan tafiyata? Don na san har ta rasu ba ki san kowa nata ba.” Amma ta runtse ido sosai kafin ta ce “Ba’a gansu ba, har yau ko b’urb’ushinsu ban gani ba, na yarda tawa k’addarar kenan dafatan Allah ya had’amu a darussalam.” Hameeda tausayi k’arara ya sake bayyana a fuskarta ta ce “Allah ya gafartawa Innah, ki yi hak’uri zan dawo In sha Allah ko kuma na ce sai kin zo. Ki gaida Kabiru tunda na samu labarin shi kika aura na yi bak’in ciki sosai amma da na tuna shine k’addararki sai na yi miki fatan nasara a rayuwa ki sanar masa Hameedah Daru ta zo.” Amma ta saki wata ajiyar zuciya kafin ta ce “Rabona da Kabiru da Auren Kabiru shekara Sha biyar kenan cif, ke dai labari sai mun had’u.” Daga haka ta hau sama don kiran twins. Ta bar Ummeey da sakakken baki da ta’ajibin abinda kunnuwanta suke jiye mata, shin wace irin k’addarace ta raba Talatu da Kabirunta duk da dama ta san ba soyayyar sa a zuciyatta? Me ya faru haka? Bata dawo daga tunanin ba taga sun dawo da y’an biyu gaba d’aya hannayensu d’auke da manyan ledodi shak’e da sutturu na alfarma. Jikinta a sanyaye ta dinga bin Amma da ido ji take kamar ta zauna ta fasa tafiyar Amman ta bata labarin bayan rabuwa. Sai dai kuma bata son k’ure mutum akwai lokaci…… Koda ta dawo daga rakasu bata bi ta kan Ayra ba, ta shige kitchen ta cigaba da ayyukanta da Dane damun kanta zata yi har sai Ayran ta bud’e d’akin ta lallasheta, yanzu kuwa tana murd’a d’akin ta ji shi a rufe ta juya abinta ya zama dole ta nunawa Ayra lokaci yazo da ya kamata ta zubar da makaman yak’inta ta yi aure, sai dai tana tsoro k’warai da gaske ta ke tsoron barazanar da Ayran ta yi akan rasa rayuwarta idan aka mata auren dole. Sai dare can bayan Isha sannan Ayran ta fito jikinta a sanyaye ganin yarda Amma ta banzatar da lamarinta. A falo ta samu Amman tana kallon wani sabon shiri da ake a Arewa ta zauna kusa da ita, amma Amman ko kallonta ba ta yi ba illa ma sake mayar da hankalinta kan television d’in, duk da rabin tunaninta dama yana kan Ayran ta kuma ji dad’i da ta ga ta fito sumul k’alau ba abinda ya sameta. Jikin Ayra a sanyaye ta ce “Sannu Amma.” “Yauwa” kawai Amman ta ce ta cigaba da jan carbinta ba tare da ta sake bi ta kan Ayran ba. Take hawaye ya yankewa Ayran a idanu ta sake jin tsanar Ummeey a ranta da duk ita ta janyo mata wannan matsalar. “Kada ki saka ni gaba da kukan jin da’di ban hanaki Kukanki ba amma ki koma cikin ‘dakinki, don ban ga abinda aka miki ba, aure ne ba kya so to falillahil Hamdu, sai ki tanadi amsar da za ki bawa ubangiji sakamakon b’ata min rai da kika yi.” Hankalin Ayra ya sake k’ololuwar tashi ta tabbata yau ta kai Amma tik’ewa, ina ma zata iya da ta yi shahada ta amince da auren ko da na wuncin gadi ne, ba zata iya ba tana jin zuciyarta zata fashe a duk ranar da ta had’a makwanci d’aya da ‘da namiji balle ta kai g ya kusanceta. Ta runtse idanunta tana ganin abin kamar ma ya faru, zuciyarta ta dinga bugu kuka sosai ya kece mata, da sauri ta ‘dora kanta a saman cinyar Amman tana kuka na gigitar hankali. Duk dan ta yi nasarar ‘daga hankalin Amman sai dai bata nuna mata ba, ta dai cigaba da kallonta tana jin tausayinta yana tsirga mata sosai, a hankali ta cigaba da jan addu’oi a bakinta da niyyar Allah ya sauk’ak’awa Ayran ta samu sauk’in zuciya. So take ta rarrasheta amma tana gudun aikata hakan, gani take kamar wannan hanyar data b’ullo shi zai saka Ayra ta amince ta yi auren ko bata so. Kukan sosai ta yi kafin ta share hawayenta ta mik’e a sanyaye karo na farko a rayuwarta da take kuka a gaban Amma bata rarrasheta ba abinda ya ki’dimata kenan a sanyaye ta koma kan kujera ta lafe, ba zata iya cin abinci ba duk da yunwar da take sasik’ar hanjinta. Amman ta bita da kallo kafin cikin k’arfin hali ta sake d’auke kanta ta cigaba da jan Addu’oin da suke bakinta. ******************************** A bakin faffad’an windown mai d’auke da glass mai girman gaske yake tsaye hannayensa sanye cikin aljihun jibgegiyar rigar sanyinsa, don garin canada akwai muku-mukun sanyin da har dusar k’ank’ara yake zubarwa (Snow). Sanyin yake ji sosai sai dai ya kasa barin wajen windown duk da windown ba’a bud’e yake ba. Yana tsaye yana hango yarda ko ina ya lullub’e da dusar k’ank’ara kamar ma ba’a halicci k’asa a wajen ba. Ya saki ajiyar zuciya tunawa da ya yi marigayiyar matarsa ta fi k’aunar yanayin fiye da komai, saboda yarda take kanainaye jikinta a nasa kamar mage. Ya lumshe ido a hankali ya ambaci sunanta a saman lab’bansa “Hibbah!” yana jin tamkar ta amsa cikin duhun idanunsa yake hango fuskarta tana sakar masa kyakykyawan murmushin da yafi so daga gareta. Ya da’de idanun a lumshe yana tuno memories d’in su masu da’di da suka kasa barin kwanyar kansa. A hankali ya bu’de idanunsa da ya ji sun masa nauyi kamar ‘dan maye wani feeling na muguwar sha’awa na taso masa. Yanayin da ya da’de bai riski kansa a cikinsa ba tun bayan aurensa na uku da Lubna ta ribace shi ta saka masa desired tablet a cikin coffee ‘din da ya saba sha duk dare. Tabbas ranar ta samu kansa domin kuwa kasa mallakar kansa ya yi sai da ya kusanceta sai dai abin haushin ya tarar da ita fanko ma’ana bata kawo budurcinta ba, kamar dai wancan Auren da yayi na Sa’eeda itama fankon ya tarar da ita shikkenan ya saka wa kansa cewa duka y’an matan yanzu hakan suke, ai kuwa ta jawowa kanta daga ranar ya saketa yana takaicin ha’da jikinsa da nata da ya yi. Da sauri ya fa’da toilet baya son yanayin ya cigaba da zagaye jikinsa yazo yana rasa inda zai saka tsananin buk’atarsa. Ruwa sosai ya sakarwa kansa kafin ya fito ya zari car key ‘dinsa ya fice daga gidan bayan ya gama k’arewa hotonsu da Hibba kallo. TAKAICIN UBA……. Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. 8…. Driving yake yana sauraron Karatun Alkur’ani daga k’ira’ar sudais. Shi ka’dai ne abinda yake saurare ya rage masa zugi da ra’da’din rashin Hibbarsa. Ko da ya yi parking a makeken wajen shak’atawar kasa shiga ya yi ya shiga cusa hannayensa cikin tarin sumar gashin kansa da ya gadota daga gurin Ummeeynsa. Ya dinga cukuikuye gashin yana jin kansa na sara masa kafin ya mayar da seat ‘din kujerar ta sa ya koma ya kwanta tunanin rayuwarsu da Hibba na sake bujiro masa…. K’arar da wayarsa ta yi ne ya farkar da shi daga wancan tunanin, ba sai ya kalli screen ‘din wayar ba ring tone ‘din ya sanar da shi wacece ‘Ummeey’ ya fa’da yana sakin murmushin gefen kumatu kafin ya jawo wayar ya kanga a kunnensa. Cikin muryar shagwab’a kamar yarda ya saba mata magana ya ce “Hayateey!” Ummeey daga ‘daya gefen ta saki murmushi tana jin da’din sunan da yake kiranta da shi. “Amin ya gida hope dai kana lafiya, muma kwanan mu uku a Nigeria.” Ya ‘dan yi dum da waya a kunne kafin ya ce “Nigeria kuma how comes? Ya aka yi Abeey ya barku kuka je?” Dariya ta yi sosai kafin ta ce “Da kansa ya sauko ya ce mu je. Yauwa ba wannan yasa na kira ka ba, Amin bu’de kunne da kyau ka ji lokaci ya yi da ya kamata ka yi aure.” Wani irin dum ya ji k’irjinsa ya buga, Ummeey zata sake janyo masa wani jidalin kenan shi tun yaushe ya cire maganar aure a rayuwarsa, ya Riga ya gama da wannan babin an gama samun mata na gari tun bayan da Hibba ta rasu. “Ba ka ji ni ba ne?” Ummeey ‘din ta fa’da with a serious tone. Sakin ajiyar zuciya ya yi kafin ya ce “Na ji Ummeey, amma ina neman alfarma, not now please, wallahi ban shirya aure ba, ko kuma na ce na gama buk’atarsa a rayuwata tunda dai Hibba ta haifa min mai yi min addu’a.” Cikin b’acin rai Ummeey ta ce “Ko da nice nake so?” Muryarsa a cunkushe ya ce “Don Allah Ummeey a bar maganar, please!” “Ka yi k’arya kuwa in bar maganar aure, haka kawai da ranka da lafiyarka in dai ba mu’amala kake da matan banza ba ai ya kamata ace zuwa yanzu ka ajiye iyali, don haka magana ‘Daya da zan maka na samar maka mata y’ar aminiyata ta yarinta da nake yawan baku labarinta wato TALATU, don haka umarni na baka ba shawara ba..” kafin ya ce komai ta katse wayar don ta san idan ba haka ta yi masa ba, Ba zai ‘d’au zancen serious ba. Gaba ‘daya ji ya yi zuciyarsa ta karye, ya tabbatar tunda ta fa’da ‘din sai ta cika alk’awarinta. Ya runtse idonsa yana tunanin menene mafita? Wannan karan kam ya zama dole ya bijirewa umarninta, shi kam da zata bar shi haka ma tsaf zai iya rayuwarsa har ya koma ga lillahi babu aure. Wajen shak’atarwa da bai shiga ba kenan, ya da’de a zaune a motar kafin ya ja motar da sauri ya fice daga garden ‘din. ____________ Tun Asuba da ta mik’e bata farka ba, ta shiga gyaran gidan da abincin da ta san Amma ta fiso, gurasar larabawa da alkubus sai kunu da k’osai. May be idan Amman ta ga wannan hidimar da ta mata ta sassautawa zuciyarta daga fushin da ta tsiri yi da ita tun jiya da bak’uwarta da ta kira bak’ar bak’uwa ta zo gidan. Sai da ta jera kayan akan dinning table da taimakon mai aiki. Sannan ta kunna sunnah t.v tashar da ta san Amman ta fi muradin kallo a koda yaushe. Tsaf ta fito cikin shigar alfarma. Ta dinga bin falon gidan da kallo ganin yarda aka canja masa tsari. Ga dadda’dan k’amshi da aka baje falon da shi, na abinci da na k’amsashshen turaren wuta mai sanyaya ruhi na mutanen chad. Murmushi ne ya so sub’uce mata sanin cewa Ayra ce duk ta shirya hakan sarai ta san neman sulhu take tun jiyan tana lura da ita fushin da take da ita yana damun zuciyarta, sai dai ba zata bari ta fuskanta ba. Ta zauna tana sake addu’ar fatan alheri ga Ayran kamar yarda ta kwana tana yi a cikin sujuda, ji take kamar warwarar matsalar Ayran ce ta zo. Ita kanta ta ji tana son Ayran ta yi wannan auren ko da sonta ko ba son ranta. Tana jin takun tafiyar Ayran, ta kawar da waccan fuskar tata mai yalwar fara’a ta saka wacce ta aro tun yammacin jiya, mai wuyar kallo a wajen Ayran mai fa’dar mata da gaba da sakata ‘dimuwa. Zuciyar Ayra ta buga sosai ganin har a lokacin waccan caku’da’ddiyar fuskar tana nan tare da ita. Ta yi k’asa da kanta tana jin yarda zuciyarta take bugu a hankali take furta ‘Wannan bak’uwa ta cuceni na shiga uku, ban tab’a ganin fuskar mahaifiyata a haka ba kamar yau.’ Jiki a sanyaye ta isa gefen Amman kamar yarda ta saba ta rab’a jikinta da nata a hankali ta bata sumbata a kumatu “Ammaty Ina kwana?” “Lafiya” ta fa’da tana sake ‘d’aure fuskarta sosai, Ayran gabanta ya fa’di sosai ganin ba sassauci da da ne sai ta janyota itama ta ha’da goshinta da nata kafin ta ce “Lafiya lau Auta ta, kin tashi lafiya.” Ta dinga wasa da hannunta kafin murya a raunane ta ce “Amma I cooked your favourite dish.” Ta ‘dau tsawon lokaci kafin ta yi jarumta ta kawar da tausayin Ayran daga ranta ta ce “Ana sa’im.” Ayran ta dinga kallonta wani iri kafin ta ce “Sa’im kuma Amma? Yau fa laraba idan ban manta ba.” Zuciya a dake ta ce “Na sani. Kuma ki k’yaleni haka bana son magana.” Tuni idanun Ayra ya fara tsiyayar da hawaye ta dinga bin ta da kallo kafin ta fashe da kuka ta fa’da kanta. Amman bata hanata ba amma fa bata saka hannu ta rarrasheta kamar yarda ta saba ba. Duk da zuciyarta tana bugu haka ta mayar da idanunta kan T.V a zahirance kallon take amma a ba’dinance kukan Ayra ne yake tsaya mata a zuciya. Ta da’de tana kukan kafin Amman ta saki ajiyar zuciya ta ‘dago kanta. Idanunta cikin nata ta ce “Saurareni Ayra, idan kina son ganin walwalata ya zama dole wannan karan ki yi ya’ki da zuciyarka ki amincewa auren nan, idan ba haka ba kin bar ganin walwala ta. A kullu yau min ina gaya miki ba duka maza ba ne halinsu ‘daya akwai wa’danda halinsu ya Sha banban da na mahaifinki yanzu yayyenki ba duk sun yi auren ba, duk da ta ki k’addarar ta fi ta su girma, kada ki manta ni kaina idan na tuna lamarinki abin yana min ciwo wani lokacin kwana nake ban yi barci ba saboda tsananin b’acin rai kuma ma ba wannan ba, ki tuna wani abu ‘daya mana yau ace na mutu na barki ina za ki kama? D’an uwana ‘daya tak da nake da shi kina ganin dai shekaru ashirin ba mu ji labarinsa ba, aurenki fa shine abinda ya fi cancanta..” Hawaye take idanunta ba k’akkautawa ita Kanta Amman danne zuciyarta take bata bayyana nata kukan ba, amma wanda take yi a zuciyarta ya fi na Ayran yawa ya fi shi kuma ciwo. Ayran da sauri ta mik’e ta shige wani k’aramin falo da yake k’asa. Kuka take sosai tana tunanin ina ma zata iya da ta amincewa aurennan tunda yanzu ta lura burin Amma gaba ‘daya ya tattara ga son aurar da ita, sai dai ina har a lokaci zuciyarta bata karkata da neman rushewar wancan adawar da takewa aure ba, ba zata iya ba ba zata iya ha’da makwanci da namiji ba…. Ba zata iya bawa namiji lokacinta ba balle ta masa girki ko ta nuna masa wata kulawa Menene Mafita? Shine kawai abinda take tunani ta runtse idanunta kawai tana hango wata mafita da take tunanin ita ce zata tserar da ita daga wannan auren ba tare da kowa ya zargeta ko ya k’alubalanceta ba…. Ta dinga sakin ajiyar zuciya tana jin cunkoson b’acin ran da zuciyarta ta yi tana warwarewa hankalinta ya kwanta ta mik’e tana ka’de jikinta…. ________________ Magriba sakaliya ya shiga gidan nasa. Alh.Sulaiman turaki ya yi parking a bakin harabar gidansa. Kana ganinsa ka ga usulin fulani kuma ingarman namiji mai tsayi da fa’di fari tas da shi, farin nasa har wani ratsawa yake yellow. Ba walwala a fuskarsa ko ka’dan don bai kasance daga cikin mutane masu walwala ba. Ya dinga amsawa masu gadinsa sannu da zuwan da suke masa fuska a ha’de. Ta k’ofar baya ya shiga gidan nasa, k’ofar da direct zata sada shi da stair case ‘din da zai hau zuwa part ‘dinsa. Ta ga shigowar tasa ta ji kuma takunsa don haka ta mik’e tsam ta sake bulbulawa kanta turare sannan ta bi bayansa, ta cikin sashen da take da zai sadata itama da stair case ‘din nasa. Ta yi kyau sosai cikin shadda light brown da ta sha ‘dinkin y’an senegal, jelar gashinta sai reto take a gadon bayanta. Farin ciki fal fuskarta da zata yi arba da shi a yau bayan shafewar wasu watanni tunda ya dawo wajen amaryarsa bai sake waiwayarsu ba don haka ta shirya taran sa tana son kuma ta nuna masa tana nan a Hameedarta mai tsananin kishi wanda dama dalilin hakan ya sa ya barta a can k’asarsu ya kuma hanata zuwa Nigeria. Sai yanzu da ya tabbatar girma yazo mata hankali ya samu ya san da wuya ta zo ta aiwatar da haukan kishi zata ji kunyar hakan. Tsawon shekaru sha biyar da aurensa da amaryarsa tun a lokacin ta so dawowa mahaifarta cikin dangin babanta amma S.Turaki ya kafe sam bai amince da hakan ba kuma ko hutu bai amince ta zo ta yi ba. Yanzun ma an kai ruwa rana kafin ya amince da zuwan nata, kuma zuciyarsa tana d’ar-d’ar sai dai ko a waya bai nuna mata ba, dalilin yayan Babanta ne ya sanar da shi ya kamata ta zo ta ga dangi yaranta kuma su san dangin kakansu tunda Amin da y’ar uwarsa ne kawai suka tab’a zuwa. A can ya ha’du da ita wajen business ‘d’insa soyayya mai k’arfin gaske ta shiga tsakaninsu, duk da ra’ayinsu ya sha banban shi mai kafaffiyar zuciya ne yayin da ita kuma ta kasance mai sassauk’an hali. Ko a wajen tarbiyyar yara sai da suka sha artabu don sosai ya nuna mata ya fi son yaransa su tashi da harshen hausa a bakinsu ba harshen su na labanawa ba, don dole ta amince take musu magana da duka harsunan biyu shi yasa suka iya hausa kamar me? Tunda itama bahaushiyar ce mahaifinta haifaffen cikin garin kano ne kuma asalin bahaushe, mahaifiyarta ce kawai ta kasance daga jinsin larabawan labanon. Tun lokaci da ta rigime da son zuwa Nigeria shi kuma ya tattara ya mata yaji tsawon wata bakwai sai da ya ga abin nata ba na k’are bane sannan ya ce su tattara su taho ya gama musu gini. A hankali ta tura k’ofar idanunsu suka gamayya da juna. Fuskarsa ta ‘dan saki ka’dan yayin da tata ta washe da fara’a gaba ‘daya ta dinga jifansa da k’awataccen murmushi. Hannu kawai ya mik’a ya janyota kusa da shi ba tare da ya yi magana ba. Ta shige jikinsa sosai tana k’ok’arin kawar da kishin da yake k’asan ranta. Sosai ta shiga nuna masa yarda ta yi kewarsa tana gaya masa yayinda shi kuma ya shiga sarrafata ba bakin magana a tunaninsa hakan ne kawai Zai nuna mata ya yi kewarta ba ‘dan ka’dan ba….. Zazzafan coffee ‘din ta shiga jujjuya masa tana k’ok’arin mik’a masa murya a sauk’ak’e ta ce “Na samarwa Turaki mata…” gaba ‘daya cup ‘din ya sub’uce a hannunsa yana dubanta ya ce “Ba dani ba, na gama yiwa Turaki aure yana zubar min da mutunci ta hanyar sakin yaran mutane..” Takaicin Uba…. Na Nazeefah Sabo Nashe.. 08033748387. 9_________ Da k’imata da mutuncina kika saka ya dinga zubar min da mutunci a idanun jama’ar da nake jin kunyarsu matuk’a dattijan mutane masu fa’da aji a K’asar nan haka kawai yake sako musu yaran ba laifin tsaye ba na zaune, wannan karan kam ba dani ba ki bari ya nemawa kansa da kansa matar da ya ji yana so kuma zai iya zama da ita kamar matarsa ta farko.” Shiru Hameeda ta yi ta zuba hannayenta a k’unci don sarai ta san mijin nata kaifi ‘daya ne Baya magana biyu ta san kafin ta shawo kansa aiki ne ja. Murya can k’asa ta yi magana tana goge masa jiki da handkerchief in da ya b’aci da coffee “Ka yi hak’uri Yallab’ai hannunka fa baya rub’ewa ka yar idan ba mu nema masa aure ba ba ta yarda za’a yi Turaki ya nemawa kansa mata, kuma ba k’ima da mutuncin mu bane a ce Turaki yana zaune ba matar aure…” Da sauri ya ‘d’aga mata hannu “Sau nawa na siya masa mutuncin ni ya zubar min da nawa mutuncin? Sau nawa na bashi k’imar ni ya kawar min da tawa k’imar? Ba ruwana kema kuma ki fita daga sabgar rashin aurensa idan ya gaji da zama ba auren da kansa zai nemawa kansa aure..” Fuskarta ta ‘daure sosai don ta san idan ba hakan ta masa ba ba zai yarda da abinda zata ce ba “Ka gwada wannan karan ina tabbatar maka za’a dace In sha Allah don matar da na zab’ar masa ina tabbatar maka itace matar da ta dace da irinsu Turaki wanda duk taurin kansa ba zai iya ‘dauke idanunsa daga kanta ba, na yarda da Talatu na san ba zata bar yaranta kara zube ba dole zata samar da nagartacciyar tarbiyya ga yaranta wacce za su yi zarra a cikin mutane.. In sha Allah wannan karan ba zai samu mafakar rabuwa da wannan matar ba, tunda waccan dai ya ce saboda rashin budurcinsu yake rabuwa da su, to wannan karan kam an yi dace In sha Allah an samu gidan mutunci..” Tsawon mintuna ya ‘dauka idanunsa cikin nata kafin ya jijjiga kai ya ce “Saboda nacinki na amince zan nema masa aure a karo na hu’du bayan rasuwar matarsa, sai dai on a Condition Wallahi idan ya sake ya rabu da wannan matar sai dai ya nemi uban da zai masa walittarka aure next time.” Cikin murna Hameeda ta dinga jijjiga kai alamar ta amince ta kama hannunsa tana godiya, a tunaninta matsalar Ameen Turaki tazo k’arshe don ta amince da nagarta da tarbiyyar yarinyar… Shima yana murmushin ya ce “Wanene Uban yarinyar? A ina za’a same shi a yi maganar auren?” Ya fa’da yana kallon k’asan k’uncinta da yake lob’awa saboda dariyar farin ciki da take ya sani Amin shine mafi soyuwa a cikin zuciyarsu fiye da duk wani ‘da da suke da shi dole farin cikinsa suke nema ta ko ina. Hameeda ta fara bashi labarin Kabiru da Talatu na lokutan baya sannan ta tabbatar masa zata tambayi Talatun sanda za’a samu Kabirun a je masa da maganar auren duk da ta b’oye bata sanar da shi basa tare ba. Ya ‘daga kai ya ce “Sai ki gaya min gobe don ina son in yi kyakykyawan bincike a kansu kafin maganar aure ta kankama don yanzu ba kowane b’aragurbi kake so ya shigo maka cikin zuri’a ba.” Cike da gamsuwa Hameeda ta hau ‘daga kai, don ita sam bata hango aibu game da Amma Talatu da zuri’arta ba. ___________________________ Da zazzafan zazzab’i ta tashi mai ha’de da sarawar kai da mutuwar jiki gaba ‘daya. Ta da’de a kwance a saman gadon ta kasa katab’us sai juyi take tana jin yarda gab’obinta suke ciwo matuk’a da gaske. Hawayen idanunta tuni suka k’afe k’af bak’in cikin da take ciki ya fi gaban ta zubar da hawaye sai dai gum da baki kawai. Ta dinga murza goshinta tana jin yarda jijiyar kan take sake d’aure mata. Tabbas a Lokacin ji take rabuwarta da numfashinta shine abu mafi soyuwa a wajenta fiye da fushin da Amma take yi da ita akan sai ta amince da maganar aurennan. Har sha biyun rana bata fito ba, balle ta yi aiyukan da ta saba yi a duk safiyar ranar, Amma kuma bata nemeta ba duk da hankalinta kacokam yana kanta sai dai bata son ta nuna mata karaya da sauri. Sallamar Dijah ne yasa Amma ta saki ajiyar zuciya don ta San dole Dijan zata tambayi Ayran ko don kasancewar lahadi ce ta san bata gari. Dija da yaranta gaba ‘d’aya suka zo gidan maza biyu mata biyu. Yanayin da taga Amman ya tsorata don haka a ki’dime ta dinga tambayar Amman ko lafiya? Amma tana murmushi da son kawar da cunkushashshiyar damuwar da take ranta ta ce “Lafiya lau Dijah kune tafe da tsakar ranar nan, wannan satin nan aka yi yo kenan.” Ba don Dijah ta yarda ba ta ‘dagawa Amman kai ha’de da cewa “Allah Amma baki da lafiya ko baki fa’da ba idanunki sun nuna, don Allah me ya sameki?” Amma ta saki ajiyar zuciya tana amsa gaisuwar jikokin nata kafin ta ce “Maza ku tafi sashenku ku yi wasa” suka mik’e kuwa suka yi hanyar sashensu don musamman Amma ta Ware wajen saboda jikokinta. Suna tafiya ta mayar da kallonta kan Dijah ta fara bata labarin halin da suke ciki da Ayra tun maganar auren da aka zo da ita. Wani farin ciki ya ziyarci Dijah ta saki murmushi tana fa’din “Alhamdulillah Allah Alhakamu nesa ta zo kusa, Allah Amma wannan karan ki cire tausayin Ayra a ranki ki sadata da ‘dakin mijinta ganin kina nuna kina tausaya mata ne yasa take sake tab’arewa ki zubar da tausayinta a gefe a mata auren shi angon ya ladabtar da ita ta hanyar da dole zata yi zaman auren.” Amma tana jijjiga kai shawarar Dijah ta zauna daram a ranta ta ce “Haka za’a yi Dijah, amma ba anan matsalar take ba, shima fa mijin ba son auren yake ba, don kuwa mijin matacciya ne ance bayan mutuwar matarsa sau uku ana masa aure yana sakin matan, to tsoron da nake ji kada ya mayar da Ayra bazawara itama ya saketa..” Dijah dariya ta saki ta ce “K’arya yake Amma, ai ba irin su Ayra maza ke saki da wuri ba, sannan kuma irin wannan auren Ai yafi da’dewa zaki sha mamaki nan gaba yarda za su zo suna son juna, balle Ayra tana da duk wata sura da zata tafi da hankalin namiji….” Karaf zancen nan ya shiga kunnen Ayra da take shirin fitowa falo. Cikin b’acin rai ta juya jikin mudubin console ‘din da yake falon ta dinga k’arewa kanta kallo tana jin takaicin zamowarta a jinsin kyawawa, ai kuwa in dai don kyan zai sota tabbas zata je ta siyo muni da ku’dinta zata jirkita halittarta da artificial ta hanyar da ba zai tab’a ganin kyanta ba sai zallar muninta ta yarda zai saketa da sauri, ta ma ji da’di data samu wannan labarin na ba ya iya rik’e aure sabida matacciyar matarsa, ashe ma aure ne zata yi na wuncin gadi ta dinga sakin murmushi farin ciki ya cika zuciyarta ta zubar da wancan tarin bak’in cikin ciwon kan ma nemansa ta yi ta rasa da sauri ta k’arasa falon cikin karsashi ta fa’da jikin Dijah tana fa’din “Oyoyo da Yayar Amarya.” Ba Dijah ba Harta Amma sai da ta dinga kallonta da mamaki ita kuwa sai dariya take ta kama hannun Amma tana murzawa cikin dakiya ta ce “Amma ki yafe min na amince zan yi auren tunda shine farin cikin ki..” wata irin runguma Amma ta kai mata tana shafa bayanta farin ciki yasa fa’di take “Alhamdulillah, Allah nagode maka daka bani yara masu biyayya Ubangiji yasa ya zame miki farin ciki a rayuwa yasa mutuwa ce zata raba ku..” yarda k’irjinta ya buga da Amma ta saurara da kyau zata fahimci zallar yaudara ce cikin zuciya ta dinga furta ba Ameen ba Ya Allah, Allah kasa kada na yi ko sati a gidansa Ubangiji ka sanya masa tsanata kasa abinda na nufi yi ya yi aiki.” Dijah tuni ta ‘dai waya ta dinga kiran sauran Yayyansu tana sanar musu kyakykyawan albishir ‘din. Kowa ya ji sai ya ce “Dijah bana son zancen banza da wasan banza.” Sai Dijan ta musu rantsuwa sai su saki ihu tare da fa’din “Alhamdulillah! Ma sha Allah” wa’danda suke gari tuni suke cewa yanzu za su zo wa’danda suke Abuja kuwa sai ki ji suna muna nan zuwa ranar Friday. Tausayinsu ya kama Ayra ganin yarda suke ‘daukan lamarin da girma basu San auren jeka na yika za ta yi ba. Sai dai ba zata nuna musu ba, ta fi son a jingina duka laifin a kansa tunda an masa tambarin auri saki. Da wannan tunanin Ayra ta saki zuciyarta ta daina damuwa da zancen auren sai ma shiri da ta fara yi da zuciyarta na yarda zata samu artificial abubuwa ta sauya halittun fuskarta ta yarda ba zai tab’a son ta ba. _____________________ Cikin asibitin murtala specialist hospital b’angaren emergency nan aka kwantar da Alh.Kabiru. Tun bayan fa’duwarsa da mutane suka taimaka suka kawo shi asibitin yake kwance a wajen, da kyar aka samu k’aninsa yake jinyarsa. Yaransa maza kuwa babu wanda ya sake zuwa tun bayan da suka yi zuwa bibbiyu. Matarsa ce dai kullum tana zuwa ta yi zaman awa guda ta tafi, tunda likitan ya sanar cutar mutuwar b’arin jiki ce ta kama shi don haka zai samu tsawon lokaci kafin ya warke. In dai ba waje za’a fita da shi ba. Yau ma bata zo da wuri ba sai kusan azahar tuni likita ya basu sallama ita dama ake jira, don k’aninsa ba shi da ku’din motar da zai kinkimeshi zuwa gida. Ranta a b’ace da jin cewa ku’din daga wajenta za su fito ba ta dinga hararar k’aninsa tana tsaki “Allah wadaran dai zumunci irin naka Kamilu ace baka da ku’din motar da zaka kai ‘dan uwanka gida.” Kamilu shima a harzuk’e ya dubeta “Kada dai ki ce zaki zageni, lokacin da yake da shi kin bar shi ya taimaka mana ne ina ce ke kika gurji arzikinsa yanzu ma sai ki fito da ku’di ki kinkimeshi ki kai shi gida, ai ni na yi na Allah don girman Allah ma na duba na zo na zauna da shi daga nan kuwa gida zan yi Allah ya bada lafiya ya sauwak’a.” Kabiru dai bin su yake da kallo idanunsa cike da rauni hawaye yana bin fuskarsa ka’dan-ka’dan shi Kabiru shine ya zama haka tun a duniya ma kenan? Mutanen da ya kyautatawa lokacin da yake da shi su suke gudunsa a halin da yake tsananin neman taimakonsu. Ganin da gaske Kamilun zai tafi yasa hannunsa mai ‘dan ragowar lafiyar ya kamo shi hannun yana rawa ya dinga nuna masa alamar ya taimakeshi. Tausayinsa ka’dan ya kama Kamilun ya fasa niyyarsa ta tafiya ya juya a hankali ya kinkimeshi tunda Kabirun yanzu ba wani nauyi gareshi ba don ma dai ‘daya b’arin jikin nasa ya nauyaya. Sai da ya saka mata shi a A daidaita ta samu ta rik’eshi da k’yar sannan ya juya ha’de da cewa “Allah ya k’ara lafiya Yaya, In sha Allah zan gaya mutanen k’auye halin da kake ciki nima kuma zan dawo duba ka idan an kwana biyu.” Daga haka ya juya ya wuce Kabiru ya bi shi da kallo gani yake kamar sallamar kenan kamar ya rabu da ‘dan uwansa kenan. Hawaye ya ‘dan zubo masa wanda yasa Larai sakin tsaki ta ce “Ko na kira shi ya tafi da kai ne? Nima an rage min wahala Haba ka bi shi da kallo kamar me?” Da sauri ya ‘dan kawar da kansa da k’yar daga kallon Kamilun shi kuma ‘dan adaidaitansu ya ja yana mamakin halin wasu matan irin na Larai mijinki ba lafiya Amma kina masa irin wannan ‘dabi’a? _________________ Idanu Turaki ya sake zubawa wayar tasa, yayin da kiran Hayateey wato Ummeey bai fasa shigowa cikin wayar ba. Ya dinga murza goshinsa yana jin tsoron ‘dagawa don ya san zancen da zata masa kenan zancen Aure! Bata San shi mata gaba ‘daya haushi suke ba shi ba gani yake duk halinsu ‘daya Sun zubar da k’ima da mutuncinsu a titi. Da k’yar ya ‘d’aga wayar cikin rashin da’din murya ya ce “Hayateey! Barka da yamma.” Hamida ta ja tsaki kafin ta ce “Yanzu Turaki kana ganin kira na sai da kaga dama sannan zaka ‘daga? To ya yi kyau hakan da ka yi ba shine zai saka na fasa waccan maganar ba, idan kaga ban ‘daura maka aure nan da wata guda ba kace an kai ni kushewata…” K’irjinsa ya dinga duka sosai kamar zuciyarsa zata b’alla k’irjin ta fito murya a dashe ya ce “Please! Ummeey ki janye wancan zancen, wallahi tunda kika sanar da ni hankalina ya kasa kwanciya..” “Ai kuwa sai dai kada ya kwanta don aure babu Fashi, har na gayawa Abbanku, kuma ya amince akan cewa za’a yi nan da sati biyar kafin azimi da sati biyu kenan, sai ka fara mata processing visa, ka kuma fara shirin zuwa biki ka tafi da matarka ka ji na gaya maka.” Turaki kasa amsa mata ya yi illa jan huci da ya dinga yi, gaba ‘daya tun kafin ya ga yarinyar ya ji ya tsaneta a zuciyarsa don bai tab’a ganin auren da Ummeey ta so kamar na tan ba, ya kasa kashe wayar yayinda Ummeey ta dinga jin hucinsa Har cikin ranta ta kashe wayar ba tare da ta tausaya masa ba, don ita tabbas ta San gata ta yi masa ta yarda ta gwangwajeshi da zuk’ekiyar mata wanke hannu ka tab’a. Ya dinga bin wayar da kallo bayan jin Ummeey ta katse wayar, wato ma ta daina tausaya masa da da ne idan ta ji a wannan yanayin lallashinsa zata dinga yi tana lallab’ashi akan ya amince Amma wannan karan Sam ba ma amincewarsa take nema ba dole za’a masa ya ciji leb’ensa a hankali kafin ya mik’e yana zagaye ‘dakin AUREN DOLE kenan Ya furta a nutse yana murmushi kafin ya ce “Koma wacece ina baki shawara kada ki yi ganganci shigowa cikin rayuwar Turaki tabbas zaki nadama don zaki zaman aure ne kamar zaman kurkuku!” Haka ya dinga fa’da yana murzar hannnayensa yana tunano irin zaman y’an Marina da za suyi da Future wife ‘din tasa. Takaicin Uba….. Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387 Page 10.. _____________________ Da safiyar lahadi Hameeda ta isa gidan aminiyarta don ta isar mata da kyakykyawan albishir, sannan ta tambayeta in da za’a samu Kabiru mahaifin Ayra a Je masa da zancen neman auren. Tsaye Ayran take a parlour sanda ta dinga jin knocking ‘din da ake daga babbar k’ofar parlourn na su, da sauri ta ‘dau Hijabinta ta zura shi tana mamakin Wanda zai zo musu gida a irin wannan time ‘din musamman ranar da ta kasance ta hutu ce ga duk ma’aikatan gwamnati wato hutun Ester Monday. Fuskarta ba walwala sosai ta dire burner ‘din da take hannunta tana aikin turare gidan. Ta k’arasa cike da takaicin koma waye bak’on ba tayi maraba lale da zuwan sa ba. “Wanene?” Ta fa’da cikin sanyin murya sab’anin waccan muryar da take ara ta yafa mai kauri da rashin da’din amo. Ummeey tana murmushi ta ce “Bu’de Ayra bak’i ne.” Tuni cikin Ayra Ya yamutsa don tabbas ko da magagin barci ta tashi ba zata mance muryar matar da tazo ta Dagula mata lissafi ba fargabarta ‘daya kada ace tare take da ‘dan nata, don haka da sauri ta mayar da kallonta kan CCTV camera ‘din da take parlourn don tabbatar da hasashenta. Ba taga kowa ba sai Ummeeyn da y’an matanta da suka zo rannan ta ja tsaki bayan ta jawo nik’ab ‘dinta ta k’unshe fuskarta. Sannan ta Zare lock ‘din murya a cunkushe ta ce “Barka da zuwa.” Ummeey ta shafa kanta ha’de da fa’din “Barakillah! Ma sha Allah” ta fa’da duk da ba ta ganin fuskar Ayran. Ita dai bata yi magana ba ta juya da sauri don ta basu damar shiga cikin parlourn. Ba tarbiyyarsu bane k’in gaida bak’i musamman babban mutum don haka bisa tilas ta durk’usa ta gaida Ummeeyn ba tare da ta cire nik’ab ‘din ba. Sam Ummeey bata damu da hakan ba ta amsa mata cike da kulawa sannan ta mik’e ta hau don kiran Amma. Da sauri Tayseer ta ce “Wait Ayra tsaya mu gaisa.” Takaicin yarinyar yasa kamar ta juya ta mata duka sai dai ta mik’a mata hannu sannan ta sake mik’awa Tasleem hannu itama suka mik’e suka rungumeta don haka kawai suke son Ayran suna kuma fatan maganar da Ummeey ta gaya musu ta tabbata tabbas da Yaya Turaki ya gwangwaje da mata. A saman sallaya ta tarar da Amma da casbaha a hannunta, da alama sallar walaha ta idar. Babu damuwa sosai a fuskarta don ta yi alk’awarin ta daina nuna damuwar ta ce “Amma, kin yi bak’i a k’asa.” Amma ta ‘d’ago tana kallonta da son k’arin bayani ba tare da ta yi magana ba, Ayra ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Bak’uwar aminiyarki ta yarinya ita ce ta zo.” Daga haka ta juya ta shige wani k’aramin falon da yake saman don bata son ma komawa k’asan balle ta sake ha’duwa da yaran can masu shegen magana kamar ana saka musu batir. Amma ta bita da kallo tana ‘dan sakin murmushi kafin ta mik’e ta nufi parlourn k’asan. Da murna da farin ciki ta tari bak’uwarta ta ta zauna a gefenta bayan ta k’wala wa mai aikinta Inna Habi kira, tana zuwa ta saka ta kawo musu ‘dan abin motsa baki. Sai da suka gama ‘dan ciye ciyensu sannan Amma ta ce su Tayseer su hau sama wajen Ayra. Suna tafiya Ummeey ta dubeta ta ce “sai ki ka ganni da sassafe, Yallab’ai ne Ya ce na zo na tambayeki inda za’a samu Kabiru aje masa da maganar auren tunda na ji kin ce min yanzu ba kwa tare.” Gaba ‘daya annurin dake fuskar Amma ya ‘dauke tsaf, ta ha’de ranta sosai bayan ta zube idanunta a k’asan carpet ‘din da yake shimfid’e a wajen. Tsawon lokaci tana jin yarda zuciyarta take tuk’uk’in b’acin rai, an zo gab’ar da bata so a duk lamarin auren yaranta, gab’ar da za’a ce sai an ga ubansu sannan za’a yi maganar aure da su, ina ma zata iya da wallahi ta Mayewa Ayra gurbin Kabiru don bai cancanta ya zame mata uba ba idan su wa’dancan ta amince Ya yi wakilcin auren su Ayra fa? Shin ya cancanta ya zama waliyyinta a wurin aurenta? Ya cancanta ya amsa sunan mahaifinta? Zuciyarta ta dinga bugu tana jin kamar ta fito ta gayawa Hameeda duk abinda ake ciki, sai dai tana tsoro tana tsoron kada maganar auren ta rushe da tabbas sai ta fito ta ce da Hameeda Ayra bata da uban da Ya wuce ita kanta, itace Uwar Ayra sannan kuma ita ce ubanta.. ajiyar zuciyar da take yawan saukewa ne yasa gaban Hameeda Ya dinga fa’duwa ta fara hasasho tabbas akwai matsala shin mai aminiyarta take b’oye mata ne game da rayuwarta ta baya? Jiki a salub’e ta kama hannayen Amman ta matsa su sosai cikin sigar son kwantar mata da hankali ta ce “Me ke faruwa ne Talatu? Menene abinda kike son b’oye min ki sanar da ni komai muninsa ni mai rufa miki asiri ce.” Amma ta zuba idanunta cikin na Ummeey tana jin kamar ta gaya mata wata zuciyar na kwab’arta don haka ta yi saurin sakin yak’en dole kafin ta ce “Rabuwar mu da Kabiru ba ‘a yi rabuwar da’di ba, mun rabu ne tsiya-tsiya kuma tsahon lokacin nan gaskiya ba zan ce ga inda za’a same shi ba, don haka ina ga kawai ba sai an kai maganar wajensa ba kin san ni, na sanki kuma kin san asalina kuma da aure na haifi Shu’aira ba da zina ba na amince Shu’aira ta auri Turaki na bashi auren ta halak malak.” Ummeey ta saki ajiyar zuciya jin ba wata matsala bace gagaruma sai dai ta San ko giyar wake ta sha bata isa ta je ta ce da Abban Turaki a cire maganar uban Ayra a ‘d’aura aure kawai ta San lamari ne da ba zai yiwu ba musamman sanin sa a mutum mai kafaffen ra’ayi Wanda ba ya jin bari dole ne a nemo Kabiru ko kuma a samo wani mutum daga cikin danginsa ya maye gurbinsa, don haka ta mayar da kallonta kan Amma kafin ta ce “Samun Kabiru ba zai yi wuya ba, kamar yarda neman inda kike bai min wuya ba Talatu don haka zan koma can unguwarmu inda a can aka min kwatancen nan na tambayesu ko Sun San inda Kabiru yake..” Da sauri Amma ta girgiza Kai “Kada ki fara Hameeda, don har Abada ba zan amince Kabiru ya yi waliccin Ayra ba balle ya amsa sunansa a matsayin mahaifi da na yi haka gwara na hak’ura da aurar da Ayra na sakata a gaba na yi ta kallo, Abu ‘daya zan iya amincewa da shi, shima ba bisa son raina ba sai don bin dokar shari’a a je a samu wani daga dangin Kabiru ya ‘daura mata aure kamar yarda na yiwa sauran y’an Uwanta a can k’auyensu akwai Kamilu k’anin ubansu shi ya aurar da sauran y’an uwanta to itama Ayran bisa dole na amince ya zama waliyyinta.” Shiru Ummeey ta yi bayan gama Jin Amman, tana da abin cewa sai dai bata son ta tilastawa Amman wajen bata labarin da ta tabbata Jin sa ba mai da’di bane. Gaba ‘daya walwalar da ta tarar da aminiyarta ta a cikinta tuni ta yi k’aura daga fuskarta don haka ta fara k’ok’arin gajarta musu zaman. “Shikkenan, ba damuwa zan samu Mai gidan da wannan maganar na gaya masa suje can k’auyen Gayan a nemi Kamilun, Amma idan Sun je ta yaya za su gane kwatancen gidan da za su je?” Amma ta yi tsam da ranta don bata da numberr kowa daga dangin mijinta da sai ta ba su don haka ta saki ajiyar zuciya “Idan Sun je Garin Gaya a k’auyen Shagogo su tambayi gidan Sarkin K’ira Kamilu ba za su sha wahala ba za’a kai su.” Ta fa’da tana kawar da kai da jin takaicin ambata sunan garin da ta yi, don shi kansa garin bata buk’atar tuna shi balle ahalin cikinsa. Ummeey ta rubuta a waya ta yi saving don gudun mantuwa sannan ta mik’e tana k’walawa su Tayseer kira. Amma da bata son su cigaba da zama bata hana su tafiya ba, saboda yarda zuciyarta take a tunzire duk wasu abubuwa da suka shu’de suna k’ok’arin sabunta a zuciyarta. Har bakin k’ofa ta raka su kafin ta dawo ta zauna ta shiga zuzzurfan tunani, tsoronta ‘d’aya kada aje garin neman aure a binciko wancan abin takaicin da take dakon b’oyansa shekara da shekaru.. ta hau jijjiga kai cikin muryar kuka a hankali yarda ba za’a jita ba, duk da dama a cikin ‘daki take ta ce “Kaiconka Kabiru Allah Ya isa ba zan tab’a yafe maka ba, Har gaban abada kuwa..” zuwa lokacin bugun zuciyarta ya k’ara tsananta tana jin zuciyar na mata wani irin ciwo da nauyi sosai. ______________________ Tunda ya dawo daga Office Ya zube a kujerar da take balcony ‘din gidan. A hankali yake jin b’acin ran nasa na yawaita tun bayan da Abbansa Ya kira shi ya sanar da shi za’a nema masa auren da bai San da zamansa ba. Wato dai da gaske suke sai sun masa auren dole haka mana zai kira shi? Gaba ‘d’aya jijiyoyin kansa suka ‘d’aure ya dinga jin tunanin matarsa yana dawo masa cikin zuciya. Ita ka’dai ce macen da ya samu a budurwa duka sauran da ya aura fanko suke It means duka matan yanzu sai sun yi watsewarsu a titi suke aure a Nasa tunanin fa kenan. “Ba abinda zai ha’dani da ita idan ta shigo ‘din ma, haka zata tattara kayanta ta tafi don ba ni na ce ta amince da auren mutumin da bata San shi ba bata San ya nake ba.Mace ‘d’aya nake ganin bayan mutuwar Matata zan sota na aureta tunda dama ita na fara so kafin k’addara ta ha’dani da Hibba… sai dai a ina zan lalubota ban san sunantaba kamanninta ne kawai suke zane a zuciyata. Ya lumshe ido yana jin yanayinsa yana canjawa a duk sanda ya tuno da kamanni da suffa ta waccan yarinyar. Shigowar abokinsa da suke zama a gida ‘daya ne ya ankarar da shi tsawon lokacin da ya ‘d’auka a wajen, ko kafin ya yi saurin shigewa gida Mukhtar ya tarar da shi. “Tsaya mana Turaki, na san fa ka ganni ka ke k’ok’arin shigewa. Me ya faru ne two days bana ganinka. Ranar ma ina ta knocking ka rufe k’ofa.” Turaki a dole ya tsaya fuskarsa ba walwala sosai ya zuba masa ido don Mukhtar Akwai surutu yayinda Turaki magana bata cika damunsa ba. “Am too busy kwana biyun nan shi yasa.” Mukhtar ya jijjiga kai “Ai kuwa sarkin nacin naka ta zo nemanka Ya fi sau nawa, wai Turaki me yasa ba zaka hak’ura ka auri yarinyar nan ba.” Turaki Ya ‘dan matsa kansa a hankali ya furta “Shaheedah why? Ban san me zan wa yarinyar nan ta fita sabgata ba.” Mukhtar ya ja hannunsa “Let’s talk, ka San ba zan baka shawarar banza ba wallahi Shaheeda na Sanka sosai ka amince da aurenta ni ban ga aibunta ba.” “Ni na gani.” Turaki Ya fa’da cikin tafasar zuciya “Ragowar wanin zan aura? Sau nawa ina kamata da samari suna rungume da Juna a hakan kake son na aureta ta zama uwar yara na? Ajiye maganarta a side a yanzu ma ni ba bu maganar aure a wajena ban sani ba ko idan na tsufa.” Mukhtar ya dinga dubansa yana mamakin furucinsa kafin ya jijjiga kai “To Allah ya kyauta, zan bawa Shaheedah hak’uri Allah Ya bata mafiyinka ta yi aurenta ta huta.” Ya ‘dan tab’e baki “Da ya fi mata sauk’i.” Mukhtar ya kawar da wancan zancen ta hanyar cewa “Hope kana shirin zuwa Nigeria na ga Christmas ta kusa. Gwara mu tattara mu je hutu k’asar mu ta gado.” Turaki ya sake runtse idanunsa zai so zuwa Nigeria Amma yana tsoron zuwa Ya ga y’ar da za’a mak’ala masa ya aura “Not now. Ka gaida mutanen Nigeria.” Daga haka ya shige gida. Ya bar Mukhtar yana binsa da kallo yana nazari anya abokin nasa ba aljannah bace ta aureshi? Sun da’de tare kuma zai iya shaidarsa ya yi rantsuwa akan cewa baya neman mata? To ko dai bai da lafiya? Sai ya tuna matarsa ya tuna tsananin soyayyar da suka sha kamar ba za’a Mutu ba, sai ga shi tashi guda mutuwa ta yi musu yankan k’auna, Amma shekarun ai da yawa Ya ci ace ya manta da ita? Ina Turaki bai manta da matarsa ba, ko da yaushe hotonta ne mak’ale kan screen ‘din wayarsa, System da komai ma kai har a zuciyarsa soyayyarta ke ‘dawainiya da Shi, shi yasa duk macen da ya kalla sai ya ga bata burgeshi kamar uwar yaransa. Ita take dishashe masa y’an mata.. idan ya tuna yarda ya sameta a Daren farko matsayin cikakkiyar mace sauran kuma matan nasa Ya same su fanko sai ya ji kimarta da darajarta suna sake hauhawa. ____________ Da nutsuwa Hameeda ta fara bawa mijinta cikakken address ‘din inda za’a samu Kamilu. “Ta yaya Babanta ya koma Kamilu bayan kin ce sunansa Kabiru?” Tambayar da ya yi mata a bazata ita ta ka’da y’an hanjinta ta shiga In da In da. S. Turaki Ya zuba mata ido kamar yana son gano rashin gaskiya a tare da ita murya Babu wasa ya ce “Ina mahaifinta ko ya rasu ne?” Ta girgiza kai “Alkunya ce dai kawai ta fulani ya barwa k’aninsa a nemi auren a wajensa.” S. Turaki Ya girgiza kai “Shikkenan, za mu isa wajensu a cikin satin nan.” Ta gyara zamanta tana jin da’din da bai gano akwai wani abu da take b’oye masa ba “Amma na ce Abban Turaki za dai kasa Turaki yazo auren nan ko?” Ya ‘dan dubeta ka’dan sai kuma ya ce “In sha Allah, idan yana da buk’atar hakan.” TAKAICIN UBA……. Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387 Page 11 Haka aka yi kuwa Mahaifin Turaki da wasu daga cikin danginsa suka je Har k’auyen nemawa Turaki aure. Sun yi mamaki k’warai ganin mutumin da Ya zo amsar ku’din auren. Da mutunci da kamala ya tarbesu, Ya kuma amshi ku’din ba tare da Ya sanar da su mahaifin Ayran yana nan da rai ba. A tunaninsa Mahaifin Ayran ne Ya turo su nan wajensa kasantuwar shi ba shi da lafiya. Haka nan aka tsayar da maganar biki sati biyar masu zuwa. Don haka kashegari ya shirya takanas Ya taho Kano, don ya kawowa Kabiru ku’din auren y’ar tasa. Sanda Ya isa Gidan Kabirun yana kwance shi ka’dai ba matar gidan, balle Yaran gidan da kowa Ya kama gaban sa. A wannan karon tausayinsa Ya kama Kamilu sosai ya dinga tsinewa Matar tasa da yaran nasa. Kabirun yana hawaye daga gefen idonsa Kamilu Ya mik’ar da shi sosai ya zauna akan yagulalliyar katifarsa da ta sha jiki, Tabbas duniya a wannan karan ta juya masa baya…. Kamilu Ya dinga jinjina lamarin girman Ubangiji ko shi da yake k’auye dai ya fi Kabiru wadata da jin da’din rayuwa. Bayan Sun gaisa a tausashe Kamilu Ya tambayi jikin nasa? Kabiru jinjina kai kawai ya yi don ba zai iya cewa da sauk’i ba, domin Har ga Allah babu sauk’in. Ya dai ja bakinsa da ya ‘dan karkace ya yi shiru don maganar ma wahala take masa. Kamilu Ya zaro uwar ku’din da yake aljihunsa Ya zube a gabansa. Da mamaki Kabirun yake kallonsa kafin cikin karyayyan harshensa ya ce “Na Menene?” Shima Kamilun da mamaki yake kallonsa “Ban gane ba? Ba kai ka tura a kai min ku’din Autarka ba na aure?” Kabiru yana hawaye Ya girgiza kai Ina yaga wannan darajar da Talatu zata saka a kawo masa ku’din auren y’ay’ansa balle wannan da lamari mafi nuni da ko tunawa ba ya son yi ya afku kanta…… Ya ja hannunsa da k’yar ya goge zufar da take goshinsa ga k’walla da ta cika masa kwarmin ido. Ya kalli Kamilun cikin takaicin abin ya ce “Yaute aka kai maka Allah ya tanya alheri, Ban tani ba.” Tausayinsa ya kama Kamilu sosai a karo na farko tun bayan faruwar lamarin ya dafa shi cike da kulawa ya ce “Ka daina saka damuwa a ranka, In sha Allah wannan karan zan daidaitaka da y’ay’anka zan gaya musu ibtala’in cuta da ya sameka, na kuma sanar da su tarin nadamarka, idan an dace shikkenan. Lamarin ne da ciwo kuma na tabbata Har yanzu wannan tabon bai bar zuciyarsu ba. Sai ka toshe kunnuwanka daga duk abinda Talatu zata fa’da maka, ta cancanci ta gaya maka duk maganar da ta zo bakinta tabbas k cucesu ka zalincesu ka bar musu bak’in tabo mai wuyar gogewa musamman Na Auta.” Kabiru wannan karan kasa hak’urcewa zuciyar sa ya yi sai da ya saki kuka sosai Kamilu yana rarrashinsa. Shigowar matar gidan ce ta farkar da su daga zaman jigum jigum da suka yi kowa zuciyarsa ba da’di. Ta zube magananta a kansu kafin ta ja dogon tsaki tana kallon Kamilu da yake mayar da ku’di aljihu ya so ya yafitarwa Kabirun wani abu daga cikin ku’din amma ya san yana ba shi muguwar matarsa ce zata amfana don haka ta tura su aljihunsa yana muzurai don sam shima baya raga mata duk da ya san babu laifinta a rabuwar Kabiru da Iyalinsa. Daga haka Ya mik’e ya yiwa Kabirun Sallama akan ya je ya samu Malam Hadi shi ya san gidan ya raka shi su kaiwa Talatu ku’din auren. A bakin layi Ya tarar da Malam Hadin suka gaisa, sannan ya sanar da shi buk’atarsa ta son ya raka shi gidan Talatu. Malam Hadi cikin fa’duwar gaba ya dubeshi “Wa? Ni da zuwa wanann gidan ai sai dai idan gawata aka kai…..” nan ya dinga ba shi labarin abinda ya faru a ranar Kamilu ya dinga dariya har da rik’e ciki “Sun yi maganinka kenan, ai shikkenan mu je na tsari Adaidaita sahu ka masa kwatance yarda zai gane sai ya kai ni.” “Wannan kuwa” Malam Hadi ya fa’da yana murza gemu. Shi kansa Kamilu sanda aka nuna masa gidan aka ce nan ne gidan Talatu sai da mamaki ya kusan kashe shi, don sanda aka yi auren y’ay’anta ba anan ‘din suke ba suna tsohon gidansu na rijiyar zaki Wanda ko kusa bai kai wannan ba, ya dinga jinina lamarin girman Ubangiji tabbas ya yarda shine Azza wa jalla. Mai gadin hana shi shiga ya yi har sai da ya yiwa Ayra waya ya sanar da ita wanene. Cikin takaici Ayra ta ja baki ta tsuke tana huci haushi da takaici ne suke nuk’urk’usar zuciyarta ta dinga fisgar leb’enta Har mai gadi ya gaji da shirun ya zata ba ta ji don haka ya ce “Hello Hajiyata kina ji?” Ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Ina jinka, ka ce ya shigo..” ta furta murya a sanyaye tana ‘dauke k’wallar idonta. Wato auren nan dai da gaske sai an yi shi? Akwai gwara ma kenan a gidan auren nan don na sha alwashi sai ya sake ni ba tare da ya rik’e ko hannuna ba.” Ta furta cike da confidence. Gaba ‘d’aya yaranta suna nan sun zagayeta murna ce kawai fal ransu. Su ka ji bugun k’ofar Amma ta ce “Dijah maza bu’de.” Dijah na bu’dewa suka yi ido hu’du da Babansu Kamilu. Tuni ta ‘d’an ha’de ranta tana ba shi hanya ya shige. Bayan da k’yar ta ce “Sannu da zuwa.” Duka gurin ma sanda ya shiga sai da suka tsuke fuskarsu tsam hatta da Amma. Akan dole suka rusuna ka’dan suka gaisheshi kafin su yi yunk’urin mik’ewa. Da sauri Kamilu ya dakatar da su “Ku yiwa Allah ku zauna akwai maganar da zan yi da ku.” Sai da suka kalli Amma suna son su ji umarninta. Amman ta ‘daga musu kai alamar ta amince su zauna. Zaman suka yi sai dai kowa fuska cunkushe. Kamilu ya gyara zamansa.. “Ina son tuna muku ayar da Allah yace ku bi iyaye ku yi musu biyayya da hadisai da dama da suka yi bayanin girman iyaye…. Alhamdulillah na San kun san su Amma me yasa kuka take? Na San Kabiru tabbas bai kyauta muku ba, Amma a halin da ake ciki Kabiru agajinku yake nema da tallafinku Saboda ya kusa barin duniya duk da ba a san gawar fari ba, Amma ina tabbatar muku Kabiru yana daf da kushewa, ku yiwa girman Allah ku yafe masa laifinsa, ya yi nadama wallahi ba k’arama ba, Kabiru yana can kwance da shanyayyen b’arin jiki ba shi da mai kula da shi. Me yasa ba zaku tausaya masa ba ku aikata masa alheri ko da sau ‘d’aya ne a rayuwarku kada daga baya ku zo kuna da na sani. Hajiya Talatu ke zaki taimaka ki yi wannan aikin alherin ki sanya su su sanya tausayi da rahmar iyaye a ransu su kula da Kabiru, wallahi yau sai da na zubda masa da hawaye kada kuje garin ramuwar abinda ya yi muku ku jefa kan ku a wuta, tunda shi dai ya yi nadama kuma hak’kinku ne ku masa biyayya ku kyautata masa ko da shi bai kyautta muku ba…” “Ba zamu masa biyayya ba, don bai cancanci biyayya a wajenmu ba, bai kuma cancanci mu kira shi da sunan mahaifin mu ba, wani irin abu ne bai mana a rayuwa ba? Yanzu ne da duniya ta juya masa baya kake son mu taimaka masa, idan har su za su taimaka masa ni dai ka cire ni a ciki sunansa ma bana buk’atar ji balle na tausaya masa…… shi a loakcin da komai ma ya faru ya tausaya min? Ya ji tausayi na na ce maka?” Ta fa’da cikin wata irin murya mai cike da rauni hawaye yana bin k’uncinta ta runtse idanunta tana hasko wancan lokacin a idanunta kamar abin yanzu ya faru jikinta ya fara shaking.. da sauri ta zube anan. Talatu da yaranta suka mik’e da sauri suka isa wajen Ayran da take wata irin kakkarwa kamar ta kifa. Amma ta juya cikin takaici ta ce “Kamilu zaka kashe min y’a nagode tashi ka tafi kawai ka zari dubu ashirin a ku’din da ka kawo mun gode sosai.” Ta fa’da tana ‘daga Ayra da take kamar a sume. Tana salati don ta da’de rabonta da suman akan lamarin sai yau. Kamilun jikinsa a sanyaye ya mik’e da sauri yana dana sanin lamarin da ya zo musu da shi. A Haka Ya fice daga gidan yana tausayin yaran da ubansu don suma abin a tausayawa ne musamman ita Auta. Haka suka dinga Shafa mata ruwa kafin ta kawo ajiyar zuciya tana fa’din “Ba zan yafe masa ba, bana son sa Ya Allah ka San abinda ya min ka San irin tozarcin da ya mana…” da sauri Amma ta rufe mata baki tana girgiza kai “Akul na sake ji Ayra, na haneki da sake furta mummunan kalma ga Kabiru ki yi hak’uri ya isa idan ba so kike ki sakawa kanki ciwon zuciya ba.” Ayra ta ja ajiyar numfashi ta rik’e bakinta tana sake sakin kuka … ———————————- Tunda ta tafi gida Zainab Yayar Ayra ta kasa sukuni, Har sai da ta ‘d’auko wayarta ta danna kiran Kamilu da ta ‘dau numberrsa a wayar Amma. Bugu biyu ya ‘dauka ta yi masa bayanin kanta sannan ta ce “Don Allah da safe ka shigo gida na mu je mu duba Baban.” Kamilun ya ja ajiyar zuciya dama ya san Zainab ita ce mai sauk’in hali a kaf yaran Kabiru ya mata alk’awarin da safen zai zo ya kaita In sha Allah. Sanda ta je ta ga mahaifinta da halin da yake ciki zuciyarta ta raunana sosai tsawon shekaru ashirin rabon da su saka shi a idonsu. Cikin mamaki yake duban Zainab yana sakin hawaye. Duk da bata saki fuskarta ba ta gaisheshi cike da kulawa sannan ta saka Kamilu ya kaishi mota su kai shi wani private hospital da suke da family file a can. Haka ta yi ta hidima da shi ba tare da sanin su Amma ba. Duk da dai itama tana yi ne ba bisa da’din rai ba. Shirye-shiryen aure sosai Ya kankama a wajen Yayyan Ayra. Burinsu Ya cika za su kawar da ita su huta. Shiri suke sosai suna ta zuwa kasuwa fitar da anko da sauran kayayyakin da za’a buk’ata a lokacin bikin. Har Events sun je sun kama tun bayan da Kamilun yazo har gida ya sanar da su an saka ranar bikin sati biyar cif. Ayra kallonsu kawai take tana mamakin budirin da suke kamar ta gaya musu ta shirya zaman gidan auren ne, auren da ta tabbatar idan zai ‘dau lokaci ma ba zai zarce sati biyu ko uku ba. A yanda ta k’ayyade masa lokaci kenan. Angon da bata san shi ba, kuma bata buk’atar saninsa kamar yarda itama ta tabbatar bai santa ba. Ranta a b’ace yake musamman idan ta tuna nan gaba Ka’dan dole a kirata a matsayin matar aure ko da ta bar gidansa kuwa sai an danganta sunanta da nasa. Bak’in cikinta kenan abinda kuma yake hanata sukuni kenan. Farin cikin Amma ne kawai yake kawar da bak’in cikinta, kuma tabbas zata yarda da wannan auren na wuncin gadi saboda Amma, amma ita ka’dai ta San k’udirin da ta rik’e a zuciyarta na yarda zata tafiyar da rayuwar auren, ba mamaki daga kanta ko kallon mace ba zai sake sha’awar yi ba balle aurenta. Ta saki murmushin mugunta bayan da ta tabbatar ta kusa cimma k’udirinta Takaicin Uba… Na Nazeefah Sabo Nashe Elegant Online Writers 12. Hameeda ganin S.Turaki har a lokacin bai yi niyyar tursasa ‘dan nasa ya dawo ba, da kanta ta kira shi a waya murya ba alamun wasa ta ce “Turaki wannan ce magana ta ta k’arshe da Kai a kan maganar auren nan, na gaya maka dole ne ka dawo a yi auren nan da Kai sannan kuma ka turo da sadaki da ku’din Kayan lefe kafin isowar taka.” Turaki cikin b’acin ran takaici da gajiya da Jin maganar auren nan ya ce “Toh Ummeey, Amma me yasa dole sai nazo? Ku yi abinda ya dace kawai?” “Ba zamu yi abinda ya dace ba Turaki saboda aurenka ne Kai zaka zauna da matarka ya zama dole ka zo ku fahimci juna, in banda haka wane irin aure ne wannan ko ce maka aka yi sadaka suka Baka y’ar?” Turaki kamar ya amsa ta da “Eeh mana ai kamar sadakar ne yarinyar da ban Santa ba ban tab’a ganin ta ba ace an bani ita ai sadaka kawai aka bani.” A fili kuwa sai ya ja ajiyar zuciya kafin ya ce “Shikkenan Ummeey zan turo duk abinda ya dace, then I will try my best naga na zo don kawai farin cikinki.” “Yauwa ko kai fa? ‘D’an Albarka, da har kasa na fara tunanin ko an canja min Turaki ne a can k’asashen masu jajayen kunnuwa.” “Mhnn” kawai ya ce murya a shak’e alamu k’arara Sun nuna Ummeey ta gama tik’e shi, don dai ba yarda zai yi ne a matsayinta na mahaifiyarsa, Amma da ya ce ta jira ta ga Uwar da ya zab’a y’ay’ansa shekara da shekaru yake dakon soyayyarta, kamanninta kaf ba su ‘dauke daga idanunsa ba, duk sau ‘d’aya tak ya tab’a ganinta tun bayan mutuwar matarsa Har yau bai sake ganinta ba, sai soyayyarta da yake ta dako. “Yauwa sai na jika.” Hameeda ta fa’da tana katse wayar cikin murmushin samun nasara. Gidan Talatu take son zuwa ta ji menene abinda Ayran ta fi buk’ata ta tambayo colours da sizes ‘din takalmin Ayran da ubder wears ‘din ta. Burinta a yi auren nan duk a zatonta Matsalar Turaki ta zo k’arshe gani take Turakin ya sake dacewa da mata kamar matarsa ta farko. Bata San abinda Ayra take shukawa ‘d’an nata ba da ta sani tabbas da farin cikinta ya tak’aita. Gaba ‘daya ahalin Amma suna baje a parlourn Ma sha Allah y’ay’a da jikoki birjik a zube Ayra ce kawai take bedroom ‘dinta saboda hayaniyarsu da ta fara damunta. Ummeey ta yi sallama ta shiga falon da fara’arta take fa’din “Aa A’a, yau bataliyace a gidan namu haka.” Kasancewar sun je har gida Sun gaisheta hakan yasa suka ganeta da sauri suka baje suna gaisheta. Ummeey ta dinga amsa musu tana rarraba idanun yarda zata ga surikarta ta so take yau ko a fakaice ta yi mata hoto ta turawa Turaki ya ga canca’de’diyar matar da ta samo masa. “Na ga kowa ban ga daughter ta ta ba.” Amma tana murmushi ta ce “Ai Allah ya ha’daki da misklar yarinya sai kun yi hak’uri da halinta. Dijah kirata tana sama ‘dakinta.” Dijah ta tafi da sauri ta bar Ummeey tana fa’din “Ai gwara haka sau tari yawan surutun ba shi da amfani.” Amma ta ce “Kamar yarda rashin maganar ma ba shi da amfani ba. Yauwa ni kuwa mu je daga can falon akwai maganar da za mu yi da ke…” Ummeey ta mik’e ta bi bayanta suka bar su Zainab suna maganar kirkin Ummeey “Wallahi Ayra banda shak’iya ce ai ta dace da Surika ta k’warai” Zainab ta fa’da tana jinjina girman rashin kirkin Ayran Wanda idan ya tashi rufe idonta take ta mata da duk wata alak’a da take tsakaninku. A falo Amma ta ‘d’an dubi Hameeda kafin ta ce “Dama tambaya zan miki anya shi Turakin ya amince da auren nan?” Ummeey ta na murmushi ta ce “Me kika gani?” “Gani na yi har yanzu ko waya ban ce Sun tab’a yi ba.” Ummeey ta ja ajiyar zuciya “Turaki Talatu yana da taurin Kai da kafiya idan na biyewa ta son ransa ba zai yi aure ba shi yasa sam ban damu da amincewarsa ba kamar yarda na tabbatar itama Ayran ba wai ta amince ba ne don haka ki k’yalesu idan suka je su ci kansu sa daidaita kansu a can.” Amma ta ja ajiyar zuciya Sam ba amsar da ta so ji ba kenan, amma ya ta iya burinta sada Ayra da ‘dakin mijinta. “Amma Hameeda mai yake raba shi da wa’dancan matan?” Hameeda ta ja ajiyar zuciya kafin ta ce “K’addara duk da dai yanzu ya gaya min wai ba masu kamun Kai ake Kai masa ba sai Sun gama gantalewa a titi. Kin ga amsar tambayar dai shine ba sa Kai budurcinsu……….” Zuciyar Ayra da take niyyar shigowa ‘dakin ta wani irin bugawa tamkar zata tarwatse daga jikinta, ta rasa me zata yi murna ko farin ciki? kafin ta saki wani zazzafan murmushi ta jingina da bango “Idan kuwa haka ne Turaki wannan karan…..” “Waye nan?” Maganar Amma ta katse mata tunaninta hakan yasa da sauri ta fa’da falon tana furta “Ni ce fa Amma!” Amma ta saki tsaki tana jinjina maganar Hameeda ta kalli Ayra ta ce “Lab’e kuma kika koma yi?” Ayra ta girgiza Kai nik’abin da yake fuskarta ne ya sa Amman bata ga dariyar da fara’arta ba. Da k’yar ta durk’usa a gefen Ummeey tana gaisheta Ummeey ta dafa bayanta ta ce “Yau ‘din ma rowar fuskar za’a min? Ai shikkenan idan da Hotonki turo zan nunawa angonki..” da sauri ta girgiza Kai cikin takaici ta ce “Ummeey bana hoto ko a waya.” Amma ma ta sake tabbatar mata, “Ai ina ji Ayra rabonta da hoto tun na graduation na Primary, ita ko irin hotonnan na Zamani na y’an mata ba yin sa take ba, wai duk don wani ya ganta ya d’orawa kansa son ta.” Ummeey cike da mamaki ta gyara zama “To saboda me? Ko da yake duk ba matsala bace ki je yanzu waje wata daga y’an uwan ki ta d’aukeki sai a turo min, sannan ki bani sizes na ki.” Ayra ta dinga ha’diyar wani yawu mai ‘daci a zuciyarta tana Jin haushin Ummeey da ta bi ta shigo rayuwarta ta yamutsata. Dabara ta fa’do mata ta ce “Ummeey na rok’i alfarma please!” Ummeeyn kallonta take sosai kafin ta dafata cikin kulawa ta ce “Ba wannan tsakani na da ke Daughter just go straight to the point, ki fa’di ko me kike so zan miki.” Ayra ta ji da’din jin hakan sosai don haka murya a sanyaye ta ce “Kada ku bari mutumin da zan aura ya san zahirin kamanni na don Allah.” Ta fa’da tana ha’da hannayenta alamar rok’o. Amma da sauri ta ce “Saboda me kenan?” Ummeey ta yi saurin dakatar da Amman tana murmushi “Ba ruwanki, ba mu sako ki cikin zancenmu ba, na amince Ayra na ‘daukar Miki wannan alk’awarin na San kina da babbar hujjar da tasa za ki aikata haka.” Ta sunkuyar da kanta sosai ta ji da’din samun Ummeey a yarda take so ta yi godiya sosai kafin ta ce “Sannan please ba zan bi shi ko ina ba zan zauna anan garin, saboda ni nake kula da companyn mu.” Ummeey ta yi jum tana tunanin yarda zata amincewa Ayran da hakan, sai dai bata son Ayran ta ‘dauketa a matsayin mace mai son kanta don haka ta ce “Shikkenan, zan duba wannan In sha Allah tunda anan ‘din ma yana da gida ai ya tab’a zama da matarsa ta farko Amma da Abbansu Abuja Ya ce za’a kai ki.” “Abujan zata je ita zata zab’a wa kanta abinda take so.” Amma ta fa’da cikin hassala da jin haushin Ayra na wannan titsiye da ta yiwa surukarta. Ummeey ta girgiza kai “Ko ‘daya, yarda take so haka za’a yi tunda ba mu zamu yi mata zaman auren ba, yanzu ki tashi ki je ki rubuto min abubuwan da ki ke buk’ata a lefenki da sizes na komai na ki.” Da sauri ta mik’e ta cikin hijab take kallon hararar da Amma take watso mata. Ta ‘d’an saki murmushi a karo na farko shirinta ya fara tafiya yarda take so. A bakin gado ta zauna hannayenta zube a fuskarta, takarda da biron a hannunta idanunta na zubar da k’walla takaici take ji wai ita ce zata yi aure duk da alwashin da ta sha a kan ‘da namiji, wai yau da kanta zata rubuta abinda take so na aurenta ashe kuwa ba zasu kawo mata lefen ba. Ko sunan lefen bata son ji, angon ma bata San sunansa ba kuma bata buk’atar ji, buk’atar ta shine samun hanyar da zata gujewa auren nan… Ina ma zata iya tafiya ta bar Amma tabbas da ta tserewa auren nan ko da kuwa ta hanyar barin k’asar ne, duk da dai ta San burinta zai cika musamman sanin cewa ance shima angon baya maraba da auren? Shigowar Dijah da dariyar da ta shigo tana yi ne ya dawo da ita cikin hayyacinta. Ta zubawa Dijahn ido da ta shigo ‘dauke da wasu kaya a hannunta tana fa’din “Bikin autarmu ai dole mu kece raini, wajen event mafi tsada za mu kama mu dagargaji Dinner, sati guda za mu yi muna cashewa abinda muka da’de muna fata Allah dai ya nuna mana, ga ankonki ma a hannuna ki turo Drivernki ya karb’a” ta fa’da tana kashe wayar idanunta cikin na Ayra da itama ta ke kallonta cikin mabayyanin b’acin rai, Da gaske ji take kamar ta tashi ta rufe Dijah da duka su tuna lokutan baya. “Idan da Wanda ya isa ya jani ya kai ni gurin bikin ai sai mu gan shi. Dijah ki fita daga harka ta abubuwanki Sun fara isata.” “Kamar yarda na ki suka fara isata ba, biki kam ai dole ki je shi Allah ya nuna mana lokaci. Yanzu ma Amma ce ta ce na gaya miki mai miki gyaran jiki ta zo zata ga yanayin fatar taki.” “Kan bala’i, au Har wani gyaran jiki kuka shirya yi min? To wallahi kada ma a fara idan ba so kuke na fasa auren ba..” Dijah ta bita da kallo tana nazarinta ‘Tabbas akwai abinda Ayra take b’oye musu bata shirya zaman auren nan ba, ta amsa ne kawai gudun b’acin ran Amma don haka jikinta a salub’e ta fice ya zama dole ta tattauna da y’an uwanta kada a zo matsala ta faru….” ____________ A kitchen suke shi da yaron sa Aman, da ya samu hutu a ranar, yaron yana da rashin ji ga shi sosai ya sangarta shi ganin shi ka’dai Hibba ta bar masa yarinyar da ta Haifa wajen haihuwa ita ma ta bita. Turo baki yaron kawai yake cike da sangarta yake furta “Ni Ummeey zan je Abbu.” Tsaki ya ja yana k’ok’arin tsiyaya masa fresh milk a cup. Aman duk da shekarun da yake da su shekara goma cur har a lokacin baya iya yiwa kansa komai saboda shagwab’a shi da suka yi. Cup ‘din ya karb’a ya sha sosai kafin ya ce “Abbu, Please Ummeey.” Ya zuba masa ido kafin cikin b’acin rai ya ce “Aman zan zaneka fa, nace maka Ummeey na Nigeria ni kuma ban shirya zuwa Nigeria yanzu ba…” Yaron cikin takaci ya fice da sauri yana kuka sosai. Jikin Turaki ya yi sanyi saboda Sam baya son b’acin ran Aman ‘din don haka don dole ya fara nema musu ticket na tahowa Nigeria, da shirin idan ya zo dole ya ruguza auren da ake son masa, sabida har a lokacin zuciyarsa bata gama amincewa da auren ba. Zai bi duk hanyar da zai bi yaga ba’a yi auren ba. TAKAICIN UBA….. Last free page In sha Allah. Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. Ku biya ku’din ku ‘dari biyar kacal ta wannan account ‘din 2118666253 U B A. (Labarin Ayra Gaya dai yanzu aka fara, tafiyar mai tsaho ce, wannan kamar masomi ne abubuwa da dama suna gaba) ArewaBooks @Nazeefah Nashe Wattpad @Nazeefah381 _______________________ Ana saura sati biki aka kai lefe, lefen da Ya amsa sunansa na lefe don kaya ne a ciki ba na wasa ba. Sai dai duk zuzuta kayan da jama’a suke bai saka Ayra koda da sau ‘daya ta dubi kayan ba, wani irin ciwo take ji zuciyarta na mata, Wanda bata raba ‘daya biyu ciwon zuciya ne yake son kamata, ji take da Allah zai ‘dauki ranta da ta huta da bak’in ciki akan a wayi gari ana fa’din Ayra matar wani k’ato. Suna nufin Alwashin da ta sha ya bi iska kenan? Har a lokacin k’iyayyar jinsin maza na nan ‘danfare cikin ranta, ta kuma k’udirce abubuwa da yawa cikin ranta akan mutumin da aka ce zata aura.. Kuka ta yi sosai kafin ta mik’e tsam ta fara zagaye cikin ‘dakin hannayenta sak’ale a baya ta isa walk-in closet’s ‘din da yake ‘dakin, cikin wani k’aramin akwati ta janyo sak’on da aka kawo mata ranar a office ta tsaya tana duban kayan tana sakin murmushi “Gwara na k’are rayuwata a prison da na amince na ha’da jiki da wani gardin da sunan aure duk da na San a duk sanda ya kusanceni sai ya yi nadamar kusantata…. Ta runtse idanunta tana girgiza kai “Oh No! God forbid na tabbata duk randa na ji namiji a jikina ranar zan tafi lahira bak’in ciki ka’dai ya isa ya tarwatsa zuciyata. A ranar ma tun safe aka dinga fama da ita akan ta bari a yi mata gyaran jiki amma ta k’i. Ganin yarda ta hassala har tana neman zube musu ne yasa Majeederh ta ce su k’yaleta ai fatarta mai kyau ce bata buk’atar gyara tunda ko gashi babu a fatarta luwai take kwance kamar bayan k’wai, kada su suka ta shi’de musu kamar yarda take aikatawa a duk sanda ta kai k’ololuwar b’acin rai. Babu k’awarta ko ‘d’aya da suka San da labarin bikin, ta ja bakinta ta tsuke duk da dama ta San wasu da dama idan ta gayyacesu bikin ba zuwa za su yi ba, tunda itama bata halartar na su bikin. Barcin safen da Ya ‘dauketa ne yasa ta wani mafarki da ta Saba yi shekarun baya, mafarki ne mai firgitar wa akan rayuwarta ta baya da ta gabata, tunda ganin abubuwan da suka farun kamar a lokacin suka farun take ta dinga wani irin ihu. Ihun da ta kara’de kafatanin gidan nasu. Kowa da yake gidan ya ji ihun. Hakan yasa Amma da y’an uwanta suka bazama ‘dakin nata. Sai suka tarar da ita cikin mafarkin take wannan ihun tana kiran Amma zai raba ni da mutuncina Amma ya cuceni…… Amma ki taimaka shikkenan sun….. Zufa ko ta ina yanko mata ya ke. Tuni Amma ta k’arasa wajenta cikin tashin hankali ta kamata tana karanta mata duk Addu’oin da suka zo bakinta. Ta da’de bata ga y’ar tata cikin wannan halin ba, ta ma da’de ba tayi wannan mafarkin ba. Sai yanzu? Aka kunna mata a.c saboda gumin da take zubarwa ga wani irin ja da fatarta ta yi, jijiyoyin kanta suka bayyana ra’da-ra’da. Jikin Amma a sanyaye ta dinga Shafa mata ruwa a sassan jikinta kafin ta kawo ajiyar numfashi alamar ta farka daga suman nata wuncin gadi…. Ta dinga bin ‘dakin da kallo, kafin ta kafawa Majeederh ido tana sakin hawaye ta mik’awa Majeedarn hannu da itama take bulbular da nata hawayen kamar yanzu abubuwan suka wakana Sun dawo musu sabbi gar a cikin zuk’atansu. Sauran y’an uwan nata ma kukan suke. Amma bata hanasu ba don itama a b’oye take share nata hawayen. Ko da yaushe Ayra ta yi irin wannan mafarkin a halin da suke kasancewa kenan. Hatta jikokin Amma da basu San tushen abin ba sai da jikinsu ya yi sanyi suka kafawa iyayensu ido suna nazartar su, so suke su gano me iyayen nasu suke b’oye musu da har yau ba su sani ba. Sai dai ina? Yanayin fuskar tasu yasa suka kasa bu’de baki su yi musu tambayar da take cin ran su. Ayra ta yi lamo akan cinyar Amman tamkar dai wancan lokacin sanda lamarin mai gigita tunani ya wakana. Tausayi Amman take bata tafi tausayawa Amman akan ita kanta. Ta kama hannun Amman tana matsawa, tana so ta ‘dauke mata damuwar da ta gani a idanunta, ta sani duk abinda Amman take dauriya kawai take duk da tarin walwalar da take ciki, ta San zuciyar Amman a wahala take, kamar yarda ta tashi tun farkon rayuwarta Har yanzu wannan arzikin nasu bai isa ya saka zuciyar Amma ta manta da wancan bak’in al’amarin ba da sam bata son tuno shi. “Ki yi hak’uri Amma, mafarki na yi, mafarkin da kullum bana son yin sa, har murna nake da na ‘dau lokaci bai dawo min ba, sai yau har gaban abada Amma ba zan yafewa wancan mutumin ba, shi ya dasa min wannan bak’in cikin a rayuwata da sau tari wani lokacin nake jina kamar na rasa nutsuwata da hankalina har tambaya nake wa kaina me yasa tun a lokacin Allah bai ‘dauki raina na huta ba, ga wani bak’in cikin zan sake shigarsa Amma bana son auren nan wallahi zuciyata ciwo take min, Amma idan har kun dage sai an yi na amince sai dai ina rok’onku kada ku yi wani sha’ani da zai bayyanawa duniya ina murna, wallahi bana murna Amma bak’in ciki nake yi! Bak’in cikin da nake ji da dama in dai ba laifi a kaina da na kashe kaina na huta da na amsa sunan matar namiji. Na tsani Maza Amma! Na tsanesu duk duniya ba abinda bana so irin Jinsin maza, har godiya nakewa Allah da Ubangiji yasa ba ki haifi namiji ba, na tabbata da ba zan so shi ba, ba zan masa kallon tausayi da jin k’ai ba… Yaya kuke ji idan na yi aure Allah ya k’addara min na haifi namiji Am sure ba zan so shi ba… ta fa’da tana k’unshe bakinta saboda wani irin kuka da ya k’wace mata. Amma bayanta kawai take duka alamar rarrashi itama ji take kamar ta fasa yiwa Ayran aure kada ta je ta haukata y’arta a banza da wofi, sai dai gatan da zata mata shine auren, musamman sanin cewa ba dawwama zata yi a duniya ba, idan ta mutu Ayra ina zata kama? Don haka dole ta jajirce ta ga ta aurar da Ayran tana fatan nan gaba ka’dan abinda take ji ya zama labari. Ta kalli sauran yaranta musamman Majeederh da take wani irin kuka kamar ranta zai fita. “Majeederh kukan nan ya isa haka, kowane bawa ba shi da ikon canja k’addarar da take bin sa, mu godewa Allah duk halin da muka tsinci kan mu. Abu ‘d’aya da zan sanar da ku duk wata hidima da kuka shiryawa bikin nan a janyeta, a ‘daura aure kawai a yi saukar Alkur’ani a kaita ‘dakinta tunda ta ce bata so, kada zafin ya mata yawa.” Kowa ya yi na’am da haka illa Dijah da ta ji abin sam bai yi mata ba, duk k’uzun da ta sha na gwangwajewa a bikin Ayran ya bi iska kenan.. ta dinga cizar baki takaici fal fuskarta Har sai da Amman ta balbaleta da fa’da sannan ta russuna “Idan hidima kike so idan ki ka yi hak’uri ai ga ku nan da bikin y’ay’a bayan sallah sai ki je can ki k’arata, wannan dai na soketa haba ina dalili? Ta ji d abu ‘d’aya mana.” Ganin Amma ta saka fa’da yasa Dijah ta ja bakinta ta tsuke tana hararar Ayran da take sake kanainaye jiki a cinyar Amman. Fateema ‘daya daga cikin y’an matan jikokinta ta gyara zama tana kallon Amman, tambayoyi ne fal a cikinta Amma bata San ta yarda zata b’ullo musu ba, amma a yau kam ya kamata su san menene ya wakana a rayuwar iyayen nasu da suke b’oye musu ba kuma su tab’a basu fuskar da za su fuskanta ba. Ta cire duk wani tsoro da fargaba ta dubi Amman “Amma, ya kamata yau ku bamu labarin rayuwarku da abubuwan da kuke b’oye mana, ni dai gaskiya akwai abinda nake son sani Har yau bamu tab’a ganin wani daga cikin y’an uwanki ya tako nan ba? Haka nan mun ji labarin Babansu Ammeey yana raye Amma shima bamu tab’a ganinsa ba… me kuke b’oye mana ne? Me yake faruwa ne?” “Ubanki ne yake faruwa!” Fateema ta ji maganar Mamanta Zainab a kanta cikin zafin rai ta cigaba da cewa na ce “Fatima ubanki ne yake faruwa? Ke har kin yi girman da zaki titsiye Amma haka? Me kike so ki ce? Kina so ki ce ba ki yarda da nagartar asalinmu bane ko me? Me ye gaminki da Uban mu? Ko Ubanki ne?” Da sauri Fateema ta girgiza kai ta runtse idanunta cikin dana sanin tambayoyinta da ya hassalo mata uwa lokaci ‘daya. “Ku tashi Ku fice ban san ma rainin da ya kawo ku cikin mu ba, kuma ko da wasa kada ku sake maimaita hakan kuna ji na?” Da sauri suka hau ‘daga kai bayan saurarar Umma sunan da suke kiran Eesha da shi kenan, jikinsu a salub’e suka tattara suka bar ‘dakin ganin fuskokin iyayensu kamar an aiko musu da mala’ikan mutuwa. Jikin Ayran ya ‘d’auki ‘dimi da kakkarwa tilas Amman ta saka ta a gaba suka tafi asibiti ta ga likitan da ta Saba gani. Ya sake bata magunguna ya kuma ba su shawarwari akan ta rage tunanin abin da yake damunta shine yake hassala mata tashin ciwon nata. Amma ta gamsu da bayanin likitan sai dai ta San ita kanta ta yi k’arya ta ce zata kawar wa da Ayran da wannan tunanin Wanda ta girma da shi ta tashi da shi cikin ranta, sai dai Addu’a kawai zata dage da yi mata addu’a Allah ya la’d’dafa mata. Haka suka koma gida kowa zuciya ba da’di musamman Majeeda da take jin tsohon bak’in dafin yana son taso mata, don dai ita ta fi su hak’uri ne tana da hak’uri matuk’a da gaske, don haka da wuya ka gane abinda yake damunta. Haka dai a ka dinga shirin gudanar biki, kowane b’angaren bikin ba karkasashi har gwara b’angaren dangin ango Hameeda kam ji take kamar yanzu Turakin zai fara aure, ta zage shiri take sosai ita da autannin y’an matanta, Tasleem da Tayseer da suke ji da gayu da iyayi kamar me.. yau suke saka rai da dawowar Turakin, sai dai har dare Turakin bai dawo ba, ga shi a kashegarin ranar za’a ‘d’aura auren. Ran Hameeda kam ya b’aci don Turakin bai tab’a b’ata mata rai kamar irin ranar ba. Shiga ‘dari fita ‘dari ta danna kiransa a waya sai dai still ana sanar mata layin wayarsa na Nigeria ba’a kunne yake ba, alamar bai iso k’asar ba, takaici Ya hana Ummeey magana illa zugum da tayi hannaye a k’unci tana tunanin me zata cewa aminiyar tata? A kan rashin zuwan Turakin? Duk wata damuwarta kawar da ita ta yi ta jingine a gefe, a sanda mijinta ya dawo fuskarsa tamkar bai tab’a dariya ba. Duk da ta San bai cika fara’a ba amma wannna karan ta san ransa a b’ace yake matuk’a. Jikinta a sanyaye ta mik’e ta shiga kitchen ta ‘dauko masa juice mai sanyi da ta ha’da masa da kanta na zallar apple da strawberry. Ta tsiyaya masa a cup tana nufar bakinsa da shi. Sai dai ga tarin mamakinta a karo na farko da ya k’i shan abin hannunta ya ture hannun nata Har lemon ya zube… kafin kace me? Gaba ‘d’aya idanunsa Sun rine saboda tsananin b’acin ran da yake ciki….. “Waye uban yarinyar nan da Turaki zai aura? Yana raye ko ya mutu?” Jikinta na rawa ta kalleshi gabanta yana fa’duwa ta ce “Me ya faru? Ubanta yana da rai mana bai mutu ba.” Sai ta ga ya saki murmushi yana cizon leb’en bakinsa “Tabbas Turaki bai yi sa’ar uwa ba, da kika rasa matar da zaki aura masa sai b’aragurbi, yaran da suka mayar da ubansu bakomai ba, suka wulak’anta rayuwarsa alhali yana cikin tsananin neman taimakonsu, bayan su suna cikin daular duniya… abin da zan tambayeki shin kin san wacece yarinyar da zaki ha’da a aure tsakanin ‘dan ki da ita? Ba ki yi bincike ba ba kiyi komai ba…. Ina tabbatar miki ba zan bari Turaki ya auri yarinyar nan ba don ban ga ta inda suka ha’da hanya ba, yarda suka banzagatar da ubansu banga ta inda mu za su dubemu da idon rahma ba idan wani abu ya same mu…… Ki je ki ga muhallin da ubansu yake rayuwa a cikin tsananin ciwo.. sannan me suke yi da suka samu wannan d’aukakar lokaci guda.. matane fa.” Ya fa’da yana dallareta da idanunsa da suke bayyana b’acin ransa “Karuwa zaki aurawa Turaki… Turakin da ya saki mata har hu’du saboda ba su kai mutuncinsu gidansa ba… ta Yaya kike zaton zai zauna da Karuwa mai b’oye kamanninta don kada a shaida ita wacece kullum cikin shigar blacks Hijabs da nik’abs ita zaki aurawa Turaki?” Turaki da yake tsaye a bayan k’ofa rik’e da hannun Aman duk ya ji zantukan Mahaifinsa.. ya damk’i hannun Aman da yake k’ok’arin fisge wa ya shige cikin gidan….. Ina shi za’a aurawa Karuwa? Ta yaya idanun Ummmeey suka rufe? Ya ja hannun Aman da k’arfin gaske nufinsa su fice daga gidan don ko me za’a yi ba zai auri Karuwa ba…….. K’arshen free pages idan kana son cigaban labarin ka hanzarta biyan ku’dinka a tsunduma ka cikin paid group a kan Naira ‘Dari Biyar Kacal.. labarin Ayra dai yanzu aka soma.. shin ko kun san me Uban Ayra ya mata? Me ya haddasa mata k’iyayyar maza a zuciyarta? Shin Auren Ayra da Turaki zai yi yu? Idan ma ya yiyu ya kuke ganin zaman nasu zai kasance yarda Turaki ya tsani matansa na baya har ya sake su saboda ba su kai budurcinsu ba… ta Yaya zai so Ayra da ake mata kallon Karuwa wacce ubanta……… Ku dai biyo tafiyar y’ar mutan makwarari cikin labarin Takaicin Uba…… tafiyar mai nisan zango ce… wacece Amma? Wace irin gwagwarmayar rayuwa ta sha? Duka yana nan tafe. Y’an gayun nan y’an k’walisa wa’danda ba sa son hayaniyar group ku biya dubu ‘d’aya kacal. Labarin zai sameki direct cikin wayarki ba ruwanki da an tsere min an wuceki abin ki yana killace kan wayarki sai sanda kika ga damar karantawa. Ku taho mu tafi garin su Ayra Gaya tare da ku. Ki saka ku’din ku a wannan account ‘din. 2118666253 U B A. Da ku nake alfahari.. Nazeefah Nashe… Takaicin Uba… Na Jikar *_Nashe*_ Paid pages. 13 Hameeda ganin S.Turaki har a lokacin bai yi niyyar tursasa ‘dan nasa ya dawo ba, da kanta ta kira shi a waya murya ba alamun wasa ta ce “Turaki wannan ce magana ta ta k’arshe da Kai a kan maganar auren nan, na gaya maka dole ne ka dawo a yi auren nan da Kai sannan kuma ka turo da sadaki da ku’din Kayan lefe kafin isowar taka.” Turaki cikin hukuncin takaici da gajiya da Jin maganar auren nan ya ce “Toh Ummeey, Amma me yasa dole sai nazo? Ku yi abinda ya dace kawai?” “Ba zamu yi abinda ya dace ba Turaki saboda aurenka ne Kai zaka zauna da matarka ya zama dole ka zo ku fahimci juna, in banda haka wane irin aure ne wannan ko ce maka aka yi sadaka suka Baka y’ar?” Turaki kamar ya amsa ta da “Eeh mana ai kamar sadakar ne yarinyar da ban Santa ba ban tab’a ganin ta ba ace an bani ita ai sadaka kawai aka bani.” A fili kuwa sai ya ja ajiyar zuciya kafin ya ce “Shikkenan Ummeey zan turo duk abinda ya dace, then I will try my best naga na zo don kawai farin cikinki.” “Yauwa ko kai fa? ‘D’an Albarka, da har kasa na fara tunanin ko an canja min Turaki ne a can k’asashen masu jajayen kunnuwa.” “Mhnn” kawai ya ce murya a shak’e alamu k’arara Sun nuna Ummeey ta gama tik’e shi. “Yauwa sai na jika.” Hameeda ta fa’da tana katsewa wayar cikin murmushin samun nasara. Gidan Talatu take son zuwa ta ji menene abinda Ayran ta fi buk’ata ta tambayo colours da sizes ‘din takalmin Ayran da ubder wears ‘din ta. Burinta a yi auren nan duk a zatonta Matsalar Turaki ta zo k’arshe gani take Turakin ya sake dacewa da mata kamar matarsa ta farko. Bata San abinda Ayra take shukawa ‘d’an nata ba da ta sani tabbas da farin cikinta ta tak’aita. Gaba ‘daya ahalin Amma suna baje a parlourn Ma sha Allah y’ay’a da jikoki birjik a zube Ayra ce kawai take bedroom ‘dinta saboda hayaniyarsu da ta fara damunta. Ummeey ta yi sallama ta shiga falon da fara’arta take fa’din “Aa A’a, yau bataliyace a gidan namu haka.” Kasancewar sun je har gida Sun gaisheta hakan yasa suka ganeta da sauri suka baje suna gaisheta. Ummeey ta dinga amsa musu tana rarraba idanun yarda zata ga surikarta ta so take yau ko a fakaice ta yi mata hoto ta turawa Turaki y’a ga canca’de’diyar matar da ta samo masa. “Na ga kowa ban ga daughter ta ta ba.” Amma tana murmushi ta ce “Ai Allah ya ha’daki da misklar yarinya sai kun yi hak’uri da halinta. Dijah kirata tana sama ‘dakinta.” Dijah ta tafi da sauri ta bar Ummeey tana fa’din “Ai gwara haka sau tari yawan surutun ba shi da amfani.” Amma ta ce “Kamar yarda rashin maganar ma ba shi da amfani ba. Yauwa ni kuwa mu je daga can falon akwai maganar da za mu yi da ke…” Ummeey ta mik’e ta bi bayanta suka bar su Zainab suna maganar kirkin Ummeey “Wallahi Ayra banda shak’iya ce ai ta dace da Surika ta k’warai” A falo Amma ta ‘d’an dubi Hameeda kafin ta ce “Dama tambaya zan miki anya shi Turakin ya amince da auren nan?” Ummeey ta na murmushi ta ce “Me kika gani?” “Gani na yi har yanzu ko wata ban ce Sun tab’a yi ba.” Ummeey ta ja ajiyar zuciya “Turaki Talatu yana da taurin Kai da kafiya idan na biyewa ta son ransa ba zai yi aure ba shi yasa sam ban damu da amincewarsa ba kamar yarda na tabbatar itama Ayran ba wai ta amince ba ne don haka ki k’yalesu idan suka je su ci kansu sa daidaita kansu a can.” Amma ta ja ajiyar zuciya Sam ba amsar da ta so ji ba kenan, amma ya ta iya burinta sada Ayra da ‘dakin mijinta. “Amma Hameeda mai yake raba shi da wa’dancan matan?” Hameeda ta ja ajiyar zuciya kafin ta ce “K’addara duk da dai yanzu ya gaya min wai ba masu kamun Kai ake Kai masa ba sai Sun gama gantalewa a titi. Kin ga amsar tambayar dai shine ba sa Kai budurcinsu……….” Zuciyar Ayra da take niyyar shigowa ‘dakin ta wani irin bugawa kafin ta saki wani zazzafan murmushi ta jingina da bango “Idan kuwa haka ne Turaki wannan karan…..” “Waye nan?” Maganar Amma ta katse mata tunaninta hakan yasa da sauri ta fa’da falon tana furta “Ni ce fa Amma!” Amma ta saki tsaki tana jinjina maganar Hameeda ta kalli Ayra ta ce “Lab’e kuma kika koma yi?” Ayra ta girgiza Kai nik’abin da yake fuskarta ne ya sa Amman bata ga dariyar da fara’arta ba. Da k’yar ta durk’usa a gefen Ummeey tana gaisheta Ummeey ta dafa bayanta ta ce “Yau ‘din ma rowar fuskar za’a min? Ai shikkenan idan da Hotonki turo zan nunawa angonki..” da sauri ta girgiza Kai cikin takaici ta ce “Ummeey bana hoto ko a waya.” Amma ma ta sake tabbatar mata, Ummeey cike da mamaki ta gyara zama “To saboda me? Ko da yake duk ba matsala bace ki je yanzu waje wata daga y’an uwan ki ta d’aukeki sai a turo min, sannan ki bani sizes na ki.” Ayra ta dinga ha’diyar wani yawu mai ‘daci a zuciyarta tana Jin haushin Ummeey da ta bi ta shigo rayuwarta ta yamutsata. Dabara ta fa’do mata ta ce “Ummeey na rok’i alfarma please!” Ummeeyn kallonta take sosai kafin ta dafata cikin kulawa ta ce “Ba wannan tsakani na da ke Daughter just go straight to the point, ki fa’di ko me kike so zan miki.” Ayra ta ji da’din jin hakan sosai don haka murya a sanyaye ta ce “Kada ku bari mutumin da zan aura ya san zahirin kamanni na don Allah.” Ta fa’da tana ha’da hannayenta alamar rok’o. Amma da sauri ta ce “Saboda me kenan?” Ummeey ta yi saurin dakatar da Amman tana murmushi “Ba ruwanki, ba mu sako ki cikin zancenmu ba, na amince Ayra na ‘daukar Miki wannan alk’awarin na San kina da babbar hujjar da tasa za ki aikata haka.” Ta sunkuyar da kanta sosai ta ji da’din samun Ummeey a yarda take so ta yi godiya sosai kafin ta ce “Sannan please ba zan bi shi ko ina ba zan zauna anan garin, saboda ni nake kula da companyn mu.” Ummeey ta yi jum tana tunanin yarda zata amincewa Ayran da hakan, sai dai bata son Ayran ta ‘dauketa a matsayin mace mai son kanta don haka ta ce “Shikkenan, zan duba wannan In sha Allah tunda anan ‘din ma yana da gida ai y’a tab’a zama da matarsa ta farko Amma da Abbansu Abuja Ya ce za’a kai ki.” “Abujan zata je ita zata zab’a wa kanta abinda take so.” Amma ta fa’da cikin hassala da jin haushin Ayra na wannan titsiye da ta yiwa surukarta. Ummeey ta girgiza kai “Ko ‘daya, yarda take so haka za’a yi tunda ba mu zamu yi mata zaman auren ba, yanzu ki tashi ki je ki rubuto min abubuwan da ki ke buk’ata a lefenki da sizes na komai na ki.” Da sauri ta mik’e ta cikin hijab take kallon hararar da Amma take watso mata. Ta ‘d’an saki murmushi a karo na farko shirinta ya fara tafiya yarda take so. A bakin gado ta zauna hannayenta zube a fuskarta, takarda da biron a hannunta idanunta na zubar da k’walla takaici take ji wai ita ce zata yi aure duk da alwashin da ta sha a kan ‘da namiji, wai yau da kanta zata rubuta abinda take so na aurenta ashe kuwa ba zasu kawo mata lefen ba. Ko sunan lefen bata son ji, angon ma bata San sunansa ba kuma bata buk’atar ji, buk’atar ta shine samun hanyar da zata gujewa auren nan… Ina ma zata iya tafiya ta bar Amma tabbas da ta tserewa auren nan ko da kuwa ta hanyar barin k’asar ne, duk da dai ta San burinta zai cika musamman sanin cewa ance shima angon baya maraba da auren? Shigowar Dijah da dariyar da ta shigo tana yi ne ya dawo da ita cikin hayyacinta. Ta zubawa Dijahn ido da ta shigo ‘dauke da wasu kaya a hannunta tana fa’din “Bikin autarmu ai dole mu kece raini, wajen event mafi tsada za mu kama mu dagargaji Dinner, sati guda za mu yi muna cashewa abinda muka da’de muna fata Allah dai ya nuna mana, ga ankonki ma a hannuna ki turo Drivernki ya karb’a” ta fa’da tana kashe wayar idanunta cikin na Ayra da itama ta ke kallonta cikin mabayyanin b’acin rai, Da gaske ji take kamar ta tashi ta rufe Dijah da duka su tuna lokutan baya. “Idan da Wanda ya isa ya jani ya kai ni gurin bikin ai sai mu gan shi. Dijah ki fita daga harka ta abubuwanki Sun fara isata.” “Kamar yarda na ki suka fara isata ba, biki kam ai dole ki je shi Allah ya nuna mana lokaci. Yanzu ma Amma ce ta ce na gaya miki mai miki gyaran jiki ta zo zata ga yanayin fatar taki.” “Kan bala’i, au Har wani gyaran jiki kuka shirya yi min? To wallahi kada ma idan ba so kuke na fasa auren ba..” Dijah ta bita da kallo tana nazarinta ‘Tabbas akwai abinda Ayra take b’oye musu bata shirya zaman auren nan ba, ta amsa ne kawai gudun b’acin ran Amma don haka jikinta a salub’e ta fice ya zama dole ta tattauna da y’an uwanta kada a zo matsala ta faru….” ____________ A kitchen suke shi da yaron sa Aman, da ya samu hutu a ranar, yaron yana da rashin ji ga shi sosai y’a sangarta shi ganin shi ka’dai Hibba ta bar masa yarinyar da ta Haifa wajen haihuwa ita ma ta bita. Turo baki yaron kawai yake cike da sangarta yake furta “Ni Ummeey zan je Abbu.” Tsaki ya ja yana k’ok’arin tsiyaya masa fresh milk a cup. Aman duk da shekarun da yake da su shekara goma cur har a lokacin baya iya yiwa kansa komai saboda shagwab’a shi da suka yi. Cup ‘din ya karb’a ya sha sosai kafin ya ce “Abbu, Please Ummeey.” Ya zuba masa ido kafin cikin b’acin rai ya ce “Aman zan zaneka fa, nace maka Ummeey na Nigeria ni kuma ban shirya zuwa Nigeria yanzu ba…” Yaron cikin takaci ya fice da sauri yana kuka sosai. Jikin Turaki ya yi sanyi saboda Sam baya son b’acin ran Aman ‘din don haka don dole ya fara nema musu ticket na tahowa Nigeria, da shirin idan ya zo dole ya ruguza auren da ake son masa, sabida har a lokacin zuciyarsa bata gama amincewa da auren ba. Zai bi duk hanyar da zai bi yaga ba’a yi auren ba. Takaicin Uba.. Alk’alamin ——-Jikar Nashe 08033748387. Motsin yarda Aman ke turjewa ne ya ankarar da Ummeey da S.Turaki cewa tabbas akwai alamun mutum a wajen. Da sauri S.Turaki Ya mik’e don ganin wanene. Turaki ya gani a tsaye yana k’ok’arin ciccib’ar Aman da ya zama mai k’iba irin ta yara ka’dan, Aman ‘din yana turjewa alamar rashin son tafiya. Cikin tsawa S.Turaki ya ce “Turaki me ye haka? Yaushe ma kazo ban sani ba?” Turaki da takaicin Aman ya gama k’ullewa ya dire shi yana k’ok’arin shiga cikin gidan don ta window Abban ya masa magana. Ransa a b’ace ya danna kai cikin falon idanunsa a kan Ummeey da ta yi zugum hannayenta a kan k’unci ta zabga uban tagumi. Tausayin Amma ne a ranta da kallon da mutane suke mata ba tare da ita ta sani ba. Ba ta zuwan Turaki take ba yanzu yarda zata tursasa mijinta ya amince da auren shine abinda da take buri a yanzu. Ta sauke ganinta a kan Turaki da yake zaune idanunsa a lumshe zuciyarsa yake Jin tana shirin tarwatsewa, Jin takaicin wai Ummeey ce zata ha’da shi aure da karuwa? Yanayinsa Babansa ka’dai ya kalla ya tabbatar ya ji duk zancen da suke, shi yasa tun shigowarsa ya kasa furta musu komai sai matsa yatsunsa yake yi. Idanunsa a lumshe. “Ka daina gaisuwa ne?” S. Turaki ya watso masa tambayar yana k’ok’arin jan Aman da ya yi tsaye silently yana bin su da kallo da alama bai saba ganinsu a hakan ba. Da k’yar Turaki ya ‘dago yana kallon Uban nasa “Am Sorry Abba, ina cikin wani yanayi ne, na zo shigowa ne na ji kamar ana zancen yarinyar da za ku aura min karuwa ce.” Da sauri Ummeey ta ‘d’ago tana zuba masa kallo cikin idanunta masu rauni shikkenan kuma magana ta rushe tunda har Turaki ya ji wannan maganar ta San ko me za’a yi ba zai amince da auren ba. Ta fara Jin k’walla na son zubo mata Me zata cewa Talatu? Me zata ce mata ta fahimci ba laifin ta bane rashin auren Turaki da Ayran? Babu! Zuciyarta direct ta bata amsa Tabbas Talatu zata ‘dauke ki mayaudariya tana murna zata aurar da y’ar ta da take jiran lokacin tsawon lokaci, sai katsam ana shirin ‘daura aure taje mata da bak’in labarin an fasa anya zata iya kuwa? Abin da ciwo fa… “Tabbas abinda kunnuwanka ya jiye maka, haka abin yake Turaki, yara ne mata da suka tashi a hannun uwarsu mace suka tara mata dukiyar da ba a San musabbabinta ba, bayan rabuwar auren su da Baban yaran, a matsayinka na mai cikakken hankali me zaka kawo yarinyar tana yi da suka tara uban ku’di haka? Sannan yarinyar shekarunta ashirin da bakwai cur babu maganar aure a tsarin rayuwarta saboda tana samun inda ake ‘debe mata kewa, Babban abin takaicin ma yarda suka banzagatar da uban su, don Baka ga muhallin da yake ba, ga shi a kwance ciwon paralysed ya kama shi saboda bak’in cikin su, ta ko ina bai kamata ka auri yarinyar nan ba, ka bari zan nema maka yarinya y’ar gidan mutunci ka aura.” Turaki ya saki ajiyar zuciya ya kuma yarda da duk abinda Abban ya ce masa, aure ne dai ake so ya yi to su bari da Kansa zai nemo matar aure ba sai Sun masa wannan auren na walagigi ba. “Ka bar shi Abba da kaina zan nemi mata na aura.” Abba ya girgiza Kai “Shikkenan sai ka k’ok’arin samowa kafin ka koma tunda uwar ka ta dage sai ka yi auren.” Turaki ya ‘daga Kai yana mayar da kallonsa kan mahaifiyarsa da ta fara yiwa Abban magana cikin raunin murya “Amma kafin ta Kai ga haka ka bari na je wajen Talatu na ji gaskiyar zance mana.. ni dai gani nake kamar sharri ake musu wallahi Talatu ba zata yi irin wannan rayuwar ba, akwai dai wani Abu a k’asa, akwai kuma dalilin da yasa suka banzagatar da uban nasu idan ma haka ‘din ne, ba zai yiyu haka kawai ‘da ya wulak’anta uban sa ba.” “Ke kin ga ko me ma za ki je ki jiyo ni ‘dana ba zai auri wannan yarinyar ba, don haka Kai Turaki idan yarinya mai tarbiyya kake so maza ka je gidan Alaramma akwai y’ay’a mata masu tarbiyya kuma kyawawa da su, a mayar da auren kanta.” “Ai kuwa sai dai ta ha’da mata biyu wallahi, don kamar yarda ka ke da hak’ki a kansa nima ina da hak’ki, kuma ban tab’a kawo masa kowacce mace ya aura ba sai wannan don haka ko karuwar ce haka zai aureta ai jihadi zai yi, ba ku san irin shak’uwar da muka yi da Talatu bane muna yara jin Talatu nake kamar y’ar uwata don haka ko karuwar ce wallahi in dai ni na haifeka sai ka aureta…” Hameeda ta fa’da cikin matsanancin b’acin rai. Da gaske ta tunzira sosai don tana ji ko sama da k’asa zata ha’de Babu mai canja mata ra’ayi. Turaki da mahaifinsa kallonta kawai suke. Kafin S.Turakin ya yi k’wafa ya ce “Ni kike gayawa haka? To za mu gani idan mace tana walicciin auren d’anta shashasha da baki san ciwon kan ki ba, kawai ki janyo mana jangwam cikin gida.” B’ata masa magana ba illa mik’ewa da ta yi a zafafe ta shige sashenta ta sha alwashin sai Turaki ya auri yarinyar nan ko da nata auren zai yi girgi’di da soyayyar Talatu Allah ya halicceta. Gobe asubanci zata yi ta je ta samu Talatu ta ji ainahin labarinta da dalilin da yasa suka rabu da Kabiru ka dama labarin bayan rabuwarsu.. Turaki kuwa bin mahaifiyarsa Ya yi da kallo yana mamakin yarda ta kafe a kan sai ya auri y’ar nan, sai kace wacce aka sammace, ta ina zai iya aurar yarinyar da aka ce k’iri-k’iri karuwa ce? ______________ Da sassafe Hameedah ta yi parking a harabar gidan Talatu. Ta fito jikinta a sanyaye idanunta Sun kumbura ainun kana ganinta ka San bata Samu isashshen barci ba, sam bata da kwanciyar hankali har sai ta dangana ga Talatu ta ji zahirin magana akan wancan zancen da mai gidanta yazo mata da shi. Gobe ne ‘d’aurin auren ya zama dole ta samu mafita a yau kafin duk wani shirinsu y’a ruguje. Da mamaki Ayra da take tsaye a falo tana k’ok’arin fifita ruwan sha don zata sha ta fice aiki take kallonta. Da sauri ta dire cup ‘din a kan console ‘din da yake bayan k’ofar da ta bud’ewa Ummeey. Ta matsa gefe tana ce mata “Barka da zuwa.” A sanyaye Ummeeyn ta amsa tana bin falon da kallo kafin ta mayar da kallonta kan Ayra da take kallonta tana nazarin yarda Ummeeyn ta canja gaba ‘d’aya bata da walwala kamar yarda ta Saba shigowa da fara’a a lokutan baya. “Talatu ta tashi?” Ayra ta ‘daga kai “Bari na kira ta.” Ummeey ta girgiza kai tana ‘d’an sakin murmushi a hankali “Kyaleta bari na k’arasa ‘dakin.” Ta haye saman ta bar Ayran tana ‘d’an tab’e baki addu’a take a ranta Allah yasa auren aka fasa da don zallar murna sai ta zuba ruwa a k’asa ta sha ta kuma jero azimi na wata guda cur. Amma da ta idar da Sallahr walaha tana ganin Hameeda ta mik’e da sauri tana k’arasawa wajenta ha’de da Zare hijab ‘din da yake jikinta. Idanunwanta sun bawa Amma tsoro don daga ganin su basa cikin kwanciyar hankali. Ta saka hannu ta ja hannunta suka zauna bakin gado. “Ko baki fa’da ba na san akwai abinda ya tayar miki da hankali..” Amma ta ce murya a sanyaye don yarda zuciyarta take bugu ta tabbatar maganar auren ce suka fasa, ba mamaki Sun juyo mummunan abu akan Ayran, shi yasa ta dinga fargabar auren. Hameeda ta ja ajiyar zuciya “Ki kwantar da hankalinki Talatu, ko da na ji mugun abu babu abinda zai hana na ha’da Aure Turaki da Ayra ki k’addara Sun auri juna Sun gama..” Ta dafa kafa’dar Talatun “Akwai wani abu Talatu, akwai wani abu da kike b’oye min ko kuma ba kya son tuna shi, shine dalilin da yasa ba ki gaya min ba, Ina son ji Talatu, Ina son jin tarihin ki da bayan rabuwarmu, me ya faru a rayuwar aurenki da Kabiru duk da ina ji lamari ne mai girma, amma ki k’addara ni y’ar uwarki ce ta jini da zan iya b’oye Miki sirrinki kada ki ji shayin gaya min…” Ko kafin ta gama idanun Talatu Sun fara tsiyayar da hawaye, kuka take sosai tana tuno waccen rayuwar da ko mak’iyi ta bata fatan ta shiga irinta… Ta runtse idanunta tana ganin hotunan abin kamar yanzu lokacin abubuwan suka faru…… majigin abubuwan ta dinga gani a idanunta. Murya a shak’e idanunta a kulle ta ce A wani lokaci a can zamanin baya…. Amma ta dinga cizar bakinta tana k’ok’arin fa’da da zuciyar da take son hana ta bawa Hameeda labari, duk da wasu abubuwan ta sani amma wasu fa? Anya idan Hameeda ta ji gaskiyar zance zata yarda ‘danta ya auri Ayra? Kanta a k’asa cikin raunanniyar murya ta cigaba da k’ok’arin bada labarin nata… Takaicin Uba…. Na Jikar Nashe 08033748387 Paid pages (Ki kiyaye hak’kin wani kada ki karanta abinda baki biya ku’dinsa ba, 500 ne kacal ga mai buk’ata.) Cikin wani irin Yanayi Amman ta fara Shekaru ne bila adadin da suka gabata, Iyayen mahaifiyarta irin fulanin nan ne na tashi, ba sa wannan daji basa wancan. A wannan karan ma suka yada zango a dajin Mambila da take jihar TARABA STATE. Ba su ‘dau kwanaki da kafa bukkokinsu ba ayarin y’an fashi masu tafiya da mutane su siyar a matsayin bayi suka shigo rigar suka dinga sara da suka don kawai su yi gaba da dukiyoyin Iyayensu da shanunsu da kuma iyayen nasu kan su,ashe sun da’de suna bibibyarsu ba tare da saninsu ba, sai a wannan lokacin da suka far musu cikin dare. Ayarine na fulani masu yawan gaske sai dai Sam basu da Makamin kare kai, dalilin a wancan lokacin k’asa lafiya k’alau take ba’a fiya samun irin wa’dannan matsalolin ba. Matsala ‘d’aya ce da take addabar mutane inda ake zuwa a mamaye gari mutanen ciki wa’danda suka yi saura kuma a kame su a matsayin bayi, a je a siyar a masarautu ko a siyarwa manyan y’an kasuwa, wasu kuma su kan kaiwa iyalinsu su dinga musu bauta ko kuma su yi k’wark’wara da su. Ganin yarda suka tunkari ayarin su Mahaifiyarta sai suma Mutanensu na Fulani suka taso don kare kan su sai dai ba su da k’arfin wa’dannan jama’un. A wannan lokacin Innar Talatu ba zata wuce shekaru goma ba tana ji tana gani aka kashe iyayenta Yayyenta maza guda hu’du suka gudu. Ita da yake mace ce tana da rauni ganin mutuwar iyayenta sai ya sanyayar mata da gwiwa ta kasa tafiya ta durk’ushe wajen gawarwakinsu tana kuka mai tsima zuciya. A wannan lokacin ne mutanen suka Ankara da ita suka kuwa kamata suka na’deta da igiya kamar yarda ake wa bayin wancan lokacin suka ha’data da sauran mutanen da suka kama a wajen suka saka a wani Babban abu kamar amalanke suka tafi da su, bayan Sun kwashe tulin dukiyoyin iyayensu da shanunsu. Ba mai magana har suka kawo kasuwar da ake cinikin bayi. A ranar da suka iso shi kuma Malamijo kakana ya shigo kasuwar don sarar bayi ya kai gidajen masarautu kamar yarda suka Saba. Su biyar ya siya ciki kuwa har da Mahaifyar Talatu. Haka ya ‘d’unguma da su wani k’auye a kano tun kafin Gaya ta zama gari tana daji a sannan anan yake zama shi da almajiransa koyarwa yake yi sai kuma cinikin bayi. Yana zaune a garin shagogo tun kafin kafuwar wannan garin tun mutanen cikinsa ba su fi a k’irga ba. Tunda ‘dansa ya k’yalla Ya ga Innarta da ake kira Danejo ya kafewa mahaifinsa a kan shi yana son Innarta ta kada a siyar da ita. Malamijo ya san shi da son mata don haka ya zabga masa harara ya na fa’din “Ina zaka kai mata uku Moddi?” Ya fa’da masa da yarensu na fulde. Amma Ya ce shi ya ji ya gani yana son Inna ta. Haka Malamijo Ya hak’ura ya bar Mahaifiyarta Danejo a gidan sa da zummar idan damuna ta fa’di za’a yi aurensu da Moddi.” Wannan shine mafarin shigarsu duk wata masifa a rayuwa saboda halin da suka shiga sun gwammace ace can gidan sarautar aka kai Mahaifiyarta. Duk da a lokacin su ayarin da aka ha’do da Danejo murna suke mata suna cewa ta rabauta daga bauta. Ashe da rayuwar da zata shiga gwara mata rayuwar bauta. Tana ji tana gani ranar Malamijo ya saka sauran y’an uwanta a gaba da zummar zai kai su masarautar Kano a siyar idan an siyesu shikkenan idan kuma ba’a siyesu ba sai ya k’ara gaba da su. Mahaifiyarta sam bata samu soyayyar surukartaba ba don k’iri-k’iri ta dinga nuna rashin son auren, Amma da yake Malamijo mutum ne tsayayye mai kafewa a kan ra’ayinsa sai ya dage da cewa sai an yi auren. Haka aka ‘daura auren bayan fa’duwar damuna ta kuma tare a gidan Moddi b’angare ‘d’aya da sauran matansa da suke ji tamkar su saka wuk’a su kasheta saboda tsana. Innar ta ta ce ta sha matuk’ar wahalar zaman aure gidan don duk wasu aiki na su sai da ta zama ita take yi, wahalar da take sha ta tabbata ko bayin da aka tafi da su bai zama lallai su sha ta ba. Ita ce surfe nik’a daka a turmi sannan ita zata yi yo musu itace ta ‘dora Sanwa bayan ta ‘debo ruwa a can wani rafi mai nisan gaske. Duk ta k’are ta koma’de dama ita ba jikin arziki ba. Duk tsananin kyanta mai fisgar hankali sai ya fara dishewa dalilin bata samun kula da kanta kullum a cikin aikin wahala take. Kamanninta sak da Ayra don gaba ‘d’aya Ayra ita ta ‘dauko idan ta kalli Ayra sai ta ga kamar ita take kallo. Sau biyar tana samun ciki cikin yana b’arewa duk da soyayyarta da samun ‘da haka ta zubawa sarautar Allah ido tana tunanin ba mamaki bata da rabon ganin k’wanta a duniya. Burinta ya ta’allak’a da ta samu haihuwa don bata da mai ‘debe mata kewa sai maigidanta shi kuma bai isa ya shigo wajen ta ba ko ta masa magana dole sai ranar girkinta, don haka sai ta kwana hu’du ba tayi magana da kowa ba don ko ta yi maganar ma Babu mai kulata tsana da tsangwama suke nuna mata muraran. A kan Talatu haihuwa ta fara tsaya mata, bayan ta burne yaranta biyar wasu sai ta fara saka rai da su sai su mutu, wasu kuma tun kafin su zo duniya suke mutuwa a ciki. Idan ta tashi haihuwa ita ka’dai take haihuwa a ‘daki Babu mai taimakonta ga shi ita ba dangi ba, ita zata yiwa Kanta wankan jego ta gyara y’ar sai an ci mugun sa’a ne za su shigo mata barka, dangin Mijinta ma ba sonta suke ba balle ta saka ran samun salama a wajensu. Sanda ta samu ciki ne uban mijinta ya dage da mata rubuta da addu’oi cikin ikon Allah sai cikin ya tsaya ta kuma haifi jaririyar ta lafiya mai cikakken lafiya. Bayan wata guda da haihuwar yarinyar da ta sakawa Bo’ddo Malamijo ya amsa kiran Ubangiji daga nan ta San cewa ta rasa duk wani gata, tunda Ubangiji ya amshi surikin nata mai tsaya mata tsayin daka, musamman ta fannin matarsa da ta zama Uwar mijinta. Bo’ddo ta taso da kazar-kazar ga farin jini wajen jama’a, sai dai zuwa lokaci k’ank’ani sai farin jinin nata ya kau, don duk inda ta shiga sai kyara da hantara kamar wacce aka yiwa asiri. Don dole ta koma ba inda nake zama ta ji da’di sai wajen Mahaifiyarta kullum tana jikinta a rakub’e itace abokiyar hirarta da ita ka’dai ta Saba don mahaifinta ma sai taga kamar baya sonta ko kallonta baya yi, sau tari idan ta matsa jikinsa sai ya hantareta har ta sakawa kanta cewa Mahaifiyartace ka’dai take k’aunarta a duniya. Sanda take shekara bakwai a lokacin aka fara ginin gidan su Hameeda, da aka tabbatar ‘dan hakimin garin ne da ya je k’asar Saudiya karatu shine zai dawo aka dinga zuwa kallo dalilin ginin bulon suminti ake ginawa ba na k’asa ba kamar yarda aka Saba a duk sassan garin, don haka gidan ya ‘dauki hankalin jama’a tun kafin ma mamallaka gidan su bayyana kansu. Sanda aka gama ginin aka zuba fitilu sai gida ya zama abin kallo, kullum k’ofar gidansu Hameeda a cike yake da jama’a, kowa burinsa na Shafa fentin da aka ranga’da wa gidan yake. Da fitilu da suke amfani da engine generator don ko gidan mai garin babu su, dalilin ba’a Kai wuta garin ba a wancan lokacin. Wata rana suna zaune kawai sai suka dinga juyo hayaniya a waje ana ‘dan hakimi ya dawo amma ya dawo da mata balarabiya Har da y’a. Jin haka yasa ta fita a guje don itama ta je ta ganewa idonta. Ai kuwa dai sai ga shi ta gano Hameeda fara sol da ita, Hameedar da ta zame mata tsanin farin cikinta kafin rabuwarsu ta hangota a jikin Babarta a shekaru zata iya bata shekara biyu don dai ita Hameeda tana da girman jiki ne, yara suka dinga kallonta ana janta ganin yarda aka Mata kwalliya da riga da wando Har da wata hula mai fa’di mai kare rana. Tana kuka babanta ya ‘dauketa ya sanyata a kafa’da Ya kaita gida, don da alama tsoron mutanen take ji. Ta bata sha’awa lokacin sosai ta koma gida tana bawa Inna labari, tana murmushi ta Shafa kanta ta ce “Ke ma Bo’d’do babanki ai yana son ki.” Girgiza Kai ta yi da sauri tana ‘d’an zubar da k’walla don a lokacin ta fara sanin ciwon kanta. Ta ce “Baya so na Innah, kowa ma na duniya baya so na ke ka’dai kike so na shi yasa nake burin na girma da ke na samu ku’di don ki huta, na kuma nemo Miki y’an uwan ki” Ta girgiza Kai “Kayya Bo’ddo na fitar da rai da ganin dangina, ta ina zan gan su bayan duk kowa tarwatsewa ya yi, ke dai ina son ki dage ki yi karatun muhammadiya ki kuma koyi sana’a saboda ko bayan Raina kada ki zama abin tausayi.” Ta saka kanta a jikinta tana kuka “Inna ba zaki Mutu ba, in sha Allah sai na tsufa.” Sai taga ta yi murmushi ta girgiza Kai “Mutuwa ai dole ce Bo’ddo, tana kan kowa, sannan kada ki sake cewa kowa na duniya baya son ki, yaushe kika zagaye duniyar balle ki sani? Nan dai na kusa da ke ba sa son ki, Allah zai kawo mai son ki kin ji ko bayan Raina…” kalma kenan mafi muni da ta tsani ta ji ta a bakin Inna, sai kawai ta kifa kanta a cinyarta ta rufe ido, so take ta bar maganar, sai ta jawo mataji ta shiga kunce mata kitso dama ita take mata kitso da komai da ya danganci mata Lalle da sauransu. Da daddare suna raku’be a cikin ‘dan akurkin da za’a Kira shi ‘dakinsu to akurki mana don na matan gidan duka ya yi ukun nasu. Moddibo da muke kira Baji ya shigo da sallama idanunsa a kanta, ya ‘dan yi tsaki “Ke kuwa Danejo baki da aikin yi sai ki saka y’a a gaba kina hira ko fulako babu.” Da sauri Inna jikinta na rawa ta tureta daga jikinta ta mik’e zaune “Ka yi hak’uri Moddi ban San da zuwanka ba.” Ta fa’da don har ga Allah bata San da zuwan nasa ba don ba ranar girkinta bace, to ko ranar girkin nata ne bai mayar da ita komai ba saboda an Zare masa son ta a zuciyarsa. Ya sake sakin tsaki “Ki shirya gobe ki je sabon gidan can na yaron Mai gari za ki fara musu aiki.” Da sauri Inna ta ‘daga kai kanta a k’asa don bata isa ko idanunsa ta kalla ba, ya sake rataya sandarsa ya fice da sauri. Sai taga Inna ta lumshe ido ta ‘dan rik’e k’irjinta da yake matsa mata da ciwo a lokacin. Ta saki kakkaurar ajiyar zuciya. Da sassafe haka ta tashi bayan gama aiyukan da yake gidansu ta tasa Bo’ddo a gaba ta tafi makarantar Allo, ita kuma ta tafi gidan yaron mai gari. Wannan zuwa gidan su Hameeda da take yi ba k’aramin bak’in jini ya sake jawo mata ba, dalilin mahaifiyar Hameeda mutuniyar kirki ce, kuma tana taimakawa Inna sosai, wani lokacin har Kayan Hameeda take bayarwa a bawa Bo’ddo tunda aka je Da ita gidan sau ‘d’aya ta k’yalla ido ta ganta sai jininsu ya ha’du idan ma Inna bata je da ita gidansu ba sai ta saka an zo har gida an tafi da Bo’ddo ko ta saka a rakota. Duk abinda Inna ta samo mutanen nan ta k’arfin tuwo suke k’waceshi su raba a tsakaninsu. Inna Sam bata damuwa kullum cewa take na rasa dangina ma balle abin duniya. Ana haka Wata rana Inna ta tafi gidansu Hameeda, Bo’ddo kuma ta sawo Kai kenan zauren gidan su sai ta ji kamar ana ambatar sunan Inna don haka sai ta rab’e ta ji zancen da ake tunda ta ji ana ambatar danejo maganar Kulu da ake kira Inna wuro ita taji tana cewa “Wallahi Malam ya tabbatar min idan na burne layar nan a cikin ‘dakinta to sai buzunta don ciwo zata kwanta sosai har kwananta ya k’are.” Sai ta ji Sun yi dariya Inna Habi ta ji ta ce “Yanzu kin bisne kenan?” Ta yi shewa ta ce “Ai ba a bori da Sanyin jiki..” jikin Bo’ddo na b’ari ta yi sallama ta shiga gidan, duk sai ta ga Sun zubo mata ido ba tare da Sun amsa sallamar ba. Gaba ‘daya a ru’de ta fa’da ‘dakinmu burinta ta gano inda ta binne abin kafin dawowar Inna, sai dai bulayin duniya ta rasa wajen ba inda bata tona ba, Amma babu labarin laya ba zancenta. Tana k’ok’arin tone waje ‘daya da ya rage mata Inna ta zabga sallama ta shigo.. cak ta tsaya a Bakin k’ofa tana k’are mata kallo “Bo’ddo! Me kike yi haka?) tana k’ok’arin tashi ta turata waje ta sako kai, Bo’ddo ta saka ihu ba ta San sanda ta ce “. “Kada ki shigo Inna za su kasheki” sai dai kafin ta rufe bakinta ta ga Inna ta dafe kanta sai kuma ta ga ta yi luuuu zata fa’di, da sauri ta k’arasa wajenta ta fa’do jikina tana wani irin mak’yark’yata…. Takaicin Uba. Paid pages 15 Na Nazeefah Sabo Nashe Ta dafe kan Innar tata da taga tana rik’e wa tana fa’din Bo’ddo…. Sai dai duk abinda take son fa’da ya tokare tsaf a mak’oshinta, harshenta ya karye ta kasa furta koda kalmar ‘a’ sai ido data zubawa ‘diyartata cikin wani irin matsanancin hali take fitar da nishi da wani irin yawu a bakinta. Ganin furucin ba zai yiwu ba sai ta koma yiwa y’arta nuni da hannu irin maganar bebaye, Bo’ddo ta gane mai take nufi so take a kirawo mata mijinta Moddi don haka da sauri ta ajiye kan Innarta Akan matashi, ta fita a guje, ba tare da ta kula da lab’ewar da matan gidan suka yi ba a bakin k’ofar ‘dakinsu, fuskarsu ‘dauke da matsananciyar fara’a da alama burinsu ya cika, burin da suka da’de suna Neman hanyar kammaluwarsa sai yau Allah ya yi, Sun tsani Danejo Sun tsani su bu’di ido su ganta a cikin gidan tun a farkon fari da Moddi ya nuna mata wani irin so, su suka jirkitar da soyayyarta a zuciyar Moddi zuwa matsananciyar k’iyayyar da shi Kansa ba zai iya fasalta ta ba, sau tari idan ya ganta a cikin wahala ya kan ji wani sashe na Zuciyarsa yana tausaya mata, sai dai a duk yayin da ya yi nufin taimaka mata sai ya ji zuciyarsa ta kasa, sai ya ji kamar an yiwa gangar jikinsa dabaibayi. Ganin hak’arsu ta kusa cimma ruwa sai kowacce ta shige bigirenta suna jiran su ji an fasa kukan Danejo ta Mutu. A can gona ta tarar da Moddin, tana hakin gudun da ta sha ta zube a gabansa, yanayinta ka’dai ya duba ya ji wata irin fa’duwar gaba ta sameshi da sauri ya ce “Ke Bo’ddo k’alau kuwa?” Hanyar gida ta nuna masa tana haki da k’yar kalmomin Inna…’ suka fito daga bakinta sai kawai ta sake juyawa a guje, shima bai yi k’asa a gwiba ya bi sahunta da sauri yana addu’ar kada Allah ya tabbatar da hasashensa na rasuwar Danejo, me zai ce da Allah? Akan irin wahalhalun da suka bata, baya so Danejo ta mutu bai nemi gafararta ba, ya San ya gallaza mata gallazawa mafi muni… da kwatantuwa. Ko kafin ya je gida tuni ya jik’e sharkaf da gumi, zuciyarsa tana wani irin duka da fisga kamar zata bar k’irjinsa. Isar sa k’ofar ‘d’akin Danejon ya yi daidai da lokacin da ta amsa kiran Ubangiji cikin ambatar sunan Allah, da Allah ya bata dama ta fisgo shi da k’yar a harshenta. Shikkenan ji kake ‘dif Danejo ta wuce kushewa inda ba a dawowa. Duk da yarintarta bai hanata gane ta rasa Innanta ba har abada, wani irin kuka zata yi babu! Gani take kuka ma rahma ne tunda ga shi tana son ta yi ta kasa, wani irin k’unci take ji a ranta tana kallon Gawar Innanta da Moddi ya zubawa ido, yana hawaye ji yake da yana da iko da ya dawo da ran Innajin ya gyara kuskuren da ya aikata sai dai ba dama… Shigowar Innawuro cikin ‘dakin ya tunatar da Bo’ddo waccen maganar da ta ji suna yi, da sauri ta mik’e idanunta a warwaje tana duban Innawuron tana fa’din ta kasheta… wallahi su suka kashe min Inna su suka bisne wani Abu a cikin ‘dakin nan.. Moddi ne ya jawota jikinsa a tunaninsa zafin mutuwa ne yake Neman zautar mata da k’wak’walwa “Ki yi shiru Bo’ddo..” ya fa’da yana kallon Inna wuro cikin tsananin firgita da kallon da take wa Bo’ddo sai Kuma kamar an tsikareta ta Mik’e ta fice daga ‘d’akin. Bo’ddo ta sake binta da Kallo tana tunani cikin ranta. Shigowar Hameeda da mahaifiyarta ne yasa kukan da bata shirya yinsa ba ya fito mata, Mahaifiyar Hameeda ta jata jikinta cikin tausayawa ta dinga buga bayanta tana mata nasiha mai ratsa zuciya. Haka tana ji tana gani aka fita da mahaifiyarta don kaita kushewa shikkenan Sun yi sallama da Inna ba zata sake ganin Inna ba.. hakan yasa kukan ya sake kece mata… ⭐️⭐️ Watannin da suka biyo baya, masu muni ne a wajenta, watannin da ba zata taba’ mantawa da su ba cikin tarihin rayuwarta, sai yanzu ta san menene maraici? A lokacin ta San kalmar da ake fa’da ga Wanda ya rasa iyaye wato sai hak’uri. Tabbas ta yarda sai hak’urin domin bata da sukunin zuciya ko ka’dan zuciyarta ta zama a k’untace sau tari ta kan ji wani abu ya tokare k’irjinta. Bata da kowa bata da komai Kowa ya juya mata baya, babu mai kallonta da idon rahma ta ji sanyi, ita take kula da kanta sannan aikin da mahaifiyar ta take yi kacokam ya dawo kanta, ba su duba k’ank’antar shekarunta ba, ba su duba rauninta ba duk aikin da suka ga dama shi suke bata. Mahaifiyar Hameeda jigo ce a rayuwarta, matar da ba zata tab’a mantawa da ita ba, ita ta Maye mata wani gurbi daga guraben da Innarta ta bari, sau tari tana bak’i in cikin yarda Bo’ddon ta lalace, har kaya take bata Amma a banza don ba zasu barta ta mora ba. Yaransu masu ido da kwalli suke bawa. Da kanta ta yi tattaki ta je Har gida da zummar ta karb’i bo’ddon ta dawo k’ark’ashin kulawarta, sai dai sam Moddibo Ya k’ek’ashe idonsa Ya hana tunda Innawuro ta masa wani kallo. Da ky’ar ya amince ta dinga zuwa tana yini ta dawo da yammanci. Lokacin ta samu d’an sassauci a gidan su Hameeda take cin abinci ta sha ta yi wanka Hameeda kuma ta koya mata karatun boko. Suka shak’u sosai da Hameeda duk inda za su je tare suke zuwa Hameeda ta zame mata garkuwa tunda ita macece mai zafi ba kuma ba ta ‘daukan raini. Bo’ddo hankalinta ya fara kwanciya duk gari suka fara rubibin neman aurenta a shekarunta goma kacal. Hakan ya sake tunzira su Inna wuro haushi kamar ya huda k’irjinsu. Suka canja mata suna daga Bo’ddo zuwa Talatu don suna bak’in cikin su kirata da sunan da kai tsaye yake nufin kyau a fillanci. Kabiru wani hatsabibin mutum ne da ya gagari jama’ar k’auyen, kowa kuma yake jin shakkarsa don idan ka bari ka shiga gonarsa mai rabaka da shi sai Allah. Tunda ya k’yallara ya ga Talatu ya saka ‘dambar samun aurenta ko ta wane hali. Ya uzzira wa Talatu da neman Soyayyarta ko da ta dole ne. Babu kuma wanda ya isa ya kulata idan kuwa ya ji labarin kana neman aurenta har gida yake zuwa Ya baka garga’di mai kyau. Talatu bata kulashi domin bata ma shirya soyayyar ba a k’ank’antar shekarunta balle ta karb’a, me ma ta sani? Shi yake ki’dansa yake rawar sa. Sau tari ya sha rutsata Amma sai Hameeda ta janye ta tana masa masifa. Mahaifiyar Hameeda ita taso tsaya mata akan maganar Kabiru sai dai kana taka Allah na tasa cikin dare ciwon ciki ya kama mahaifin Hameeda Ya rasu, hankalunsu suka tashi. Wannan shi ya jawo Su Hameeda barin k’asar don takanas iyayenta suka aiko aka tafi da ita da yaranta gaba ‘daya. Hameeda Kuka Talatu kuka don ba sa son rabuwa da juna Amma suna ji suna gani aka rabasu suka tafi don Moddi yace ba zai bada Talatu ba a barta aure zai mata. Wannan shine mafarin shiga duk wani hali da Talatun ta tsinci kanta, tabbas mummunar k’addararta tana ‘danfare ne da auren Kabiru. Kuka da ihu ba irin Wanda ba tayi wa mahaifinta ba, a lokacin da Ya k’udiri aniyar aura mata Kabiru. Su Inna wuro kuwa gefe suka koma suna shek’e mata dariya da tunanin hak’ansu ya Cimma ruwa, burinsu Ya cika Talatu zata yi k’ask’antacciyar rayuwa a gidan Auren Kabiru. Shekarunta sha uku cif sanda aka ‘daura mata aure da Kabiru aka kuma kai ta ‘dakinsa ba tare da shagalin bikin da aka sabawa duk wata budurwa a garin ba. Matar k’anin Babanta Innayo ita ce mai ‘dan kulawa da lamarinta tun bayan tafiyarsu Hameeda, sai dai su Inna wuro Sun fi k’arfinta komai za tayi sai dai a bayan fage. Ita ta bata buta da langa tuwo da miya da tray na langan sai cup, sauran tarkace kuwa wanda ya ga Allah ne ya bata mai kofi mai faranti mahaifinta kuma ya siya mata katifa shikkenan aka sadata da ‘dakin mijinta. Gidan mijin da kai tsaye zata iya kiransa kurkuku saboda bala’in da tarar a cikinsa. Gidan mijin da da aurensa gwara babu, gidan Mijin da Ya rusa mata farin cikinta da na y’ay’anta gaba ‘daya…. Gidan mijin da da da da ‘din da yawa ita kanta ba zata iya lissafo rashin alherin Auren Kabiru ba da bakinta, sai dai ta San duk wata jarrabawa da Mace take fuskanta a gidan aure ta tata ta zarce ta tata. Takaicin Uba…. 16 Nazeefah Nashe 💔💔💔 Daren farko a gidan mijinta, dare ne da ba zata iya mantawa da shi ba, dare ne da kai tsaye zata iya kiransa Rabin mutuwarta don a yarda Kabiru ya kusanceta cikin k’ask’anci da rashin tausayi shi ya fara firgitata da lamarin aure, gaba ‘d’aya duk wata buk’ata tasa ya jirkice ta akan k’aramar yarinya, ba tausayi ba tunanin k’ank’antar shekarunta, ta dinga jin wani irin ra’dadi da azaba, kai kace gabanta ne zai zazzago. Yana gamawa kuma ya tsallake gefenta Ya kwanta ya barta tana kuka mai tsima zuciya. Ji take da da hali da ta bi mahaifiyarta inda ta tafi da ta huta da wannan azabar duniyar. Kukan ma da take madadin rarrashi Kabiru tsaki ya yi ya hau mata masifa “Malama ki min shiru, bana son shashasha cin banza menene amfaninku dama ku mata? idan banda wannan ‘din ba don haka dama ai aka ce mu aureku, kuma sadaki na ne nake gurza son raina kin san da wahalar da na samo ku’din da na biya sadakin ki? yanzu ma hutawa zan yi na k’ara.” Wani irin kuka ta sake saki duk da tana k’ok’arin kawar da kukan, Amma ta razana k’warai da jin furucinsa. Haka nan tana ji tana gani ya sake haik’e mata cikin daren nan, wannan karan Talatu sai da ta shi’de ta rasa inda zata saka kanta, bai damu da suman nata ba ya ja filo Ya mayar da kansa yana sakin murmushin jin da’di. Sai da ya ga alamu Sun nuna kamar ta mutu sai ya mik’e ya samo ruwa Ya watsa mata sannan ta kawo gauron numfashi, ta dinga jin haushin da addu’ar da ta yi bata karb’u ba, ta shek’a barzahu kamar yarda Innanta ta tafi. Har rana ta ‘daga Talatu ta kasa tashi, don ba k’aramin illa Kabiru Ya mata ba a gabanta, ciwo take ji sosai ga jikinta ya mata tsami, kwanciya kawai ta yi kan katifa tana zubar da hawaye rashin sanin abinda zata yi, bata da kowa a garin da zai zo ya duba halin da take ciki kamar yarda ake wa Amare a duk darensu na farko a garin. Tana kallo Kabiru ya yi wanka Ya zira kayansa ya tsallake ya fice yana fa’din “Gwara ma ki k’warara jikinki da azahar zan dawo na sake…” Yana shirin fita ya wurgo mata ku’di “Idan kin gama rakin ki saka yaro ya siyo miki koko da k’osai, ko ba komai ai kin samu cigaba don na tabbata a gidan tsoho ‘dumame ake ci.” Wannan karan runtse ido ta yi tana fatan mutuwarta kafin azahar ‘din don ta tabbata idan Kabiru ya sake kusantarta a halin da take ciki mutuwa zata yi Har lahira, gabanta kamar ana zazzaga borkono saboda ra’dadin tashin hankali. Kamar daga sama ta juyo muryar matar k’anin Babanta Innayo tana sallama ita da ‘danta Jabiru da Ya rik’o mata roba da wata leda mai ‘dauke da langa da ta yiyo mata farfesun ganda. Farin ciki ya shiga zuciyarta ka’dan, musamman da ta ‘daga labilai ta shigo tana zabga salati “Me zan gani haka ni Tarasulu?” Ta fa’da tana kai idonta kan Talatu da jini ya b’ata jikinta. Ta k’arasa da sauri tana nunawa Jabiru waje “Maza Jabiru ta fi wasa, ba wajen zamanka bane nan.” ta kamata tana fa’din “Tashi Talatu mu gani Amma Kabiru an yi matsiyaci Allah yasa bai illata ki ba.” Da k’yar ta mik’e amma zama ya gagara sai kuka da ta saka ta rungume Innayo tana furucin mutuwa zata yi.” Salati kawai Innayo take ganin yarda Kabiru ya mata illa ba y’ar ka’dan ba.ta mayar da ita ta kwantar da ita ha’de da fita sararIn gidan da sauri ta ha’da wuta. Ruwa mai zafi ta zuba a roba ta kai cikin ‘dakin da ko dab’en siminti Babu k’asa jajir zube a k’asan ‘dakin. Ihu kawai Talatu take da ta shiga cikin ruwan nan da aka zuba gishiri da lalle da bagaruwa ka’dan, sai dai ta ‘d’an samu sauk’i. Sai yamma Innayo ta tafi ta bar Talatun tana tsinewa Kabiru a ranta. Bayan dawowarsa a yammacin ranar ma sai da ya sake kusantarta yana fa’din sadakin sa ya mora. 💔💔💔💔 Haka rayuwar ta cigaba da tafiya a wajen Talatu cikin wani irin mugun yanayi, tun farkon rayuwarta bata huta ba har zuwa sanda ta haifi y’arta ta farko. Lokacin ne ta fara samun abokiyar hira. Duk da Majeederh irin yaran nan ne miskilaye amma tana Jin da’din zama da ita. Kabiru Sam bai damu da yarinyar ba ba ruwansu da ita, sanda aka haifeta ma da k’yar ya yanka mata abin yanka shi ‘din ma sai da yaga idon y’an gari Sun masa caaa aka sannan ya yanka ‘dan bunsuru, riga kuwa guda ‘daya jal ya siya mata shikkenan sai ya matse bakin aljihunsa, a cewarsa shi bai shirya haihuwa ba, koma ya shirya ma ba mace yaso a Haifa masa a farko ba, shi da yake son Magaji da zai taya shi noma, me zai yi da mace da bata San komai ba sai dai a taimaka mata haka rayuwarta zata k’are kullum sai dai ya wahalta mata. Hakan yasa Talatu ta zage ta dinga aikatau itace wankau itace surfau duk don ta kula da rayuwarta da ta ‘yarta. Majeederh na da wata uku cur wani cikin ya sake bayyana a jikinta, wannan karan ma Kabiru bai so bayyanar cikin ba, ba don komai ba sai don cikin yana hanashi rawar gaban hantsi ya fi so a koda yaushe ya kusanceta ba safiya ba dare ba rana, ba kuma wata kulawa yana shigowa zai fara gyaran murya sai kuma ya ce “Gyara” daga gyara ‘din nan sai dai ta ji mutum ya shigeta. Hakan ya sanya mata rashin son auren ta dinga tunanin bakomai a cikin rayuwar aure sai wahala. Abinci kuwa tsaba yake ajiye mata ita zata nemi na mai da na Maggi, ba abinda ya dame shi, tunda shi zai fita ya samu mai kyau ya ci. Haka ya sata a gaba da fa’din sai ta zubar da cikin, ita kuwa ta kafe ba zata zubar ba. Ido a raunane ta kalleshi kafin ta ce “Haba Kabiru ka yi hak’uri mana, tunda cikin ya riga ya shiga kuma Baka San me za mu Haifa ba, wata k’ila nan gaba sune za su ji k’anmu.” Ya zuba mata harara “Ni dai na gaya Miki idan kuwa kika sake kika haife cikin nan sai dai ki nemi uban da zai Miki hidimar sa, haka kawai mace da zarar an tab’a ki sai ciki kamar ke Kika kawo haihuwa duniya.” Kuka take sosai kafin ta ‘daga Kai ta ce “Na yarda zan yi wahalar tasa, in dai zaka amince na haifeshi.” Bai sake magana ba ya zabga tsaki ya fice daga gidan. Yana ayyana idan kin san wata ba ki San wata ba. Daga wannan furucin sai ya samu dama, San da ta tashi haihuwa nak’udar ta zo mata da matuk’ar wahala ga Innayo ba lafiya dama ita ce mai taimaka mata, haka ta yi ta murk’ususu a ‘d’aki tana addu’a ga Majeedah ta yi yarinta balle ta aiketa mak’ota a samo mai taimaka mata, cikin hukuncin Ubangiji ta haife y’arta jajur da ita. Sanda Kabiru ya dawo daga yawon Daren sa idanu ya zuba mata ita da jaririyar, cikin b’acin rai ya ce “Me kika haifa?” Ta sunkuyar da Kai tana taraddadin amsar da zata ba shi. Murya a raunane ta ce “Macece.” Wani uban ashar ya k’unduma kafin ya ce “Ina fatan baki manta yanda mu kayi da ke ba, to har yanzu ina nan Akan Baka na, k’wandala ta ba zata yi ciwon Kai a kan lamarin yarinyar nan ba, tunda ke ba abinda kika iya sai haihuwar y’ay’a mata.” Ya zabga tsaki ya fice ba tare da ya ko kalli y’ar ba, balle ya mata hu’duba. Wa’danda suka dubi Allah ne suka dinga zuwa mata barka a k’auyen, Innayo tana fama da kanta ba dama ta zo gidanta sai aike ta mata da gaisuwarta saboda itama tsohon ciki ne da ita haihuwa ko yau ko gobe zata haifi k’anin ‘danta Jabiru. Haka ta yi jegonta ga Majeedah y’ar shekara ‘daya da Rabi ga Zainabu jaririya. Ta sha matuk’ar wahala don Zainabu kam ko bunsurun ma bata samu ya yanka mata ba, ita da kanta kuma ta ra’da mata suna Zainab. Bayan sati guda da haihuwar Zainabu Innayo ta amsa kiran mahallicinta bayan doguwar nak’udar da tasha bata haife abinda yake cikinta ba. Sanda Talatu ta je dubata ta ja hannun Talatu ta ‘dora Akan na Jabiru ‘danta da Talatun ta ba shi shekaru biyu. “Na baki amanarsa Talatu, na San idan na mutu babu Mai kula da shi tunda kinga ubansa ba mazauni bane ba, Ki kula da shi don Allah Talatu.” Wani irin kuka ne ya kecewa Talatu, kukan da ake kira kuka mai tsananin cin rai ta dinga Jin duniyar tana juyi da ita, sanda ta tabbatar Itama Innayo ta amsa kiran mahaliccinta. Bayan sadakar Uku kowa ya ce ba zai rik’e Jabiru ba tunda Akan idonsu Innayo ta bada amanarsa ga Talatu bata San da su ba, to Talatu ta je ta rik’e Jabiru sun bar mata. Haka Talatu ta ha’de Kayan Jabiru kaf ta tafi da shi gidanta. Tashin hankali ba Wanda ba su yi da Kabiru ba Akan Jabiru, ya ce sai ya bar masa gidansa. Ita kuwa bu’dar bakinta ta ce “In dai zaka kori Jabiru sai dai ka ha’da da ni.” Sak ya yi yana kallonta don duk bala’insa yana son Talatu don yana samun gamsuwa a wajenta fiye da kowace Mace da zai kusanta don haka ganin da gaske take sai ya ce “Shikkenan ki yi ta rik’e shi Amma ki tabbata kwabo na ba zai yi ciwon Kai a Kansa ba.” Talatu ta bi shi da kallo kamar ta ce masa dama mai kake tsinanawa yaranka ma balle Wanda ba naka ba? Sai dai ta ja bakinta ta yi shiru. Haka ta hak’ura ta ja Jabiru ta rik’e shi suke ta gwagwarmayar rayuwar tare. Bayan wata uku da haihuwar Zainabu Kabiru ya tattara ya tafi ci rani birni, don a cewarsa ya gaji da zaman noma ya tafi Neman arzikinsa. Sai bayan tafiyarsa sannan Talatu ta fahimci tana da ciki.. hankalinta ya tashi sosai don ita kanta a wannan gab’ar bata so haihuwar ba, saboda kula da su Zainabu ma aiki ne ja a wajenta balle ga Kabiru ya tsallake ya tafi ya barta da kula da yara. Cikin ya zo mata da wani irin laulayi mai wahalar gaske. A wannan tsukun kuma Mahaifinta ya fa’di ya mutu duk y’an uwanta suka juya mata baya. Ta rasa gata ta kowane fanni sai Gatan Allah. Ga yara ga ciki da k’yar suke samun su ci abinci sau ‘d’aya a rana sau tari tuwo ne take tuk’a musu shi su kwana biyu suna cin sa kafin ta sake musu wani, sai kuwa koko da suke sha da safe shima don Jabiru yana zuwa taya aikin noma ne to idan za’a sallameshi sai ya ce ya fison a ba shi tsabar masarar da geron sai ya kawowa Talatu su ‘d’an kwana biyu suna ci. Ta gefe guda rik’on Jabiru sai ya zame mata alheri don ko bakomai yana taimaka mata kuma yana tayata wasu daga aiyukan gidanta, musamman sanda cikinta ya tsufa har a lokacin Kabiru bai waiwayi gida ba tsawon wata shidda har ta haifi y’arta ta uku da ta sakawa Aishatu bai waiwayesu ba sai da ta kusan arba’in sai ga shi yazo, abinda ya bata mamaki yarda ya zama Alhaji Kabiru lokaci guda ba kamar yarda ya tafi ba. Sakar baki ta yi tana kallonsa da tsananin mamakin canjawar tasa lokaci guda. Ko ha’diyar yawu ya gagareta illa wani irin fa’duwar gaba da Ya risketa lokaci guda.. tunaninta ‘daya wace Sana’a Kabirun yake da ya samu wannan sauyi lokaci guda… Fashi..?Yankan kai..? Sune abubuwan da suka zo mata k’wak’walwa ta runtse idanunta tana fa’din Allah a’a Ubangiji kada ka k’addara masa Uban y’ay’ana ne ba zan so ya kasance daga cikin wa’dannan halayen ko ‘daya ba. Cikin takaici Kabiru ya dinga harararta ganin yarda duk ta yagune ga wata y’ar a cinyarta da alamar wata haihuwar ta sake yi, shikkenan haihuwa zata kassara masa Jikinta, jikin da yake samun Hutu a cikinsa, ji yarda Nonuwanta suka tamushe. Kasa b’oye furucin ya yi a cikin ransa ya fito da shi a fili yana yagune fuska ya ce “Wai yagwalgwal kenan haka kika dawo nonuwa a shafale kamar silifas.. ina ai lokacin k’ara aure na ya zo.” Idanunta kamar su zubar da hawaye ta ‘dago ta zubesu cikin nasa “Yanzu irin kallon da zaka min kenan Kabiru duk da da’dewar da muka yi bamu ha’duba?” “Wani kallo kike son na miki banda wannan ‘din? Kin saki jiki kina ta zuba haihuwa uwa tunkiya ‘dan kyan da kike da shi ma duk yara Sun tsotse ina ai mata suna birni Alaji ka gansu a cike fam suna juyi da k’yar ke kam ai kin tashi daga aiki kin dawo kamar tsohuwar mota rik’onki sai mai hak’uri.” Ya fa’da yana fa’dawa cikin ‘daki “Ki kawo min abinci kizo kuma ki gyara duk da sai na rufe ido na ina hango wa’dancan tsalatsalan y’an matan sannan zan iya biyan buk’ata ta dake.” Wani abu mai ‘daci ne yazo ya tokare mata wuya da mak’oshinta, jikinta a salub’e ta shiga kitchen ragowar ‘dumame ta zubo masa da ruwan sha a kwanon sha. Yana cikin ‘dakin ya baje kan katifa gefe guda ga ki’dan garaya ya ware a radio yana rausayar da kai, daga shi sai gajeran wando ya nuna mata katifa fuska a murtuke ya ce “Gyara, kuma ki ‘daure wa’dannnan abubuwan naki masu kama da silifas bana son ganinsu, na Saba ganin tula-tula.” Takaicin Uba…. Na Nazeefa Nashe Pg 17 💔💔💔💔 Runtse idanunta ta yi cikin Jin zafin furucinsa da take ganinsa kamar cin fuska ne a wajenta, cin fuska mana idan ma ragwab’ewar tayi waye y’a janyo mata? Aikin wahala take yi don ta Tsira da mutuncin ta da na y’ay’anta babu cima mai kyau da zai gyara mata jikinta da fatarta, ba dole ta yamushe ba.. ta ma godewa Allah da ta Kai har haka bata yak’une ba. Ta ha’diye wani Abu mai ‘daci tana shirin juyawa ta fice, ya fincikota ya afka mata kamar yarda ya Saba. Bayan ya gama gurzarta son ransa ya mik’e yana zabga tsaki har da tsartar da miyau ransa a b’ace ya ce “Aradu mata na birni, ya aka yi gabanki ya bu’de kamar k’ofar gari..” wannan karan hawayen idonta kasa ‘daukewa suka yi, ta sake su suna zuba kamar famfo, ita kanta ta San ta bu’de bayan haihuwar Aisha, rashin ku’di y’a hanata zuyartar babban asibitin birni duk kuma wani magani na gargajiya da tayi ya kasa karb’arta. Ya fice ya na ayyana tabbas rabuwarsu ta matso kusa don daman gaban nata yake yiwa to da alama gaban nata ya tashi daga aiki. Ya fice daga ‘dakin daga shi sai gajeran wando yana sake Jin tsanar Talatun a cikin zuciyarsa yaushe akayi auren? Yaushe ma har ya gama cin sadakinsa da za’a ce har ya gama ‘debe ni’imar Talatu? Har ya fito daga wanka tunanin sakinta kawai yake don ba zai iya cigaba da zama da ita babu mamora ba. Yana da ku’din da zai auri ko y’ar mai gari ce a garin don haka zai yi amfani da ku’dinsa ya auro duk matar da yake so, idan yaso ya jinginar da Talatu don kada ya saketa idanun duniya su dawo kansa a ce ya ci amanarta don ya ga ba inda zata je, duk da shi surutun mutane bai fiya damunsa ba. Sai da ya fita ya sake dawowa, sannan ya lura da y’ar jaririyar da Talatun take shayarwa Akan cinyarta. Tun daga bakin k’ofa ya fara k’unduma zagi. “Kan Uban can, wata haihuwar kika yi Talatu, ke dai wato kin zama kaza nan da nan kin saka k’wai. Ko da yake jiki magayi ai, wannan karan kuma me kika Haifa?” Jabiru da yake gefe ya dinga auna masa harara ta bayansa yana jin kamar ya shak’eshi ya Mutu. Talatu kuwa muk’ut ta ha’diye wani Abu a wuyanta tana kallonsa, ya birkito y’ar yana masifa “Na ce me kika haifa? Allah yasa dai namiji ne wannan karan kiga yarda zan Miki gata don burina na ga an haifa min namiji ba mata gayyar matsala, Allah yasa magaji….” Cak yawun bakinsa ya k’afe ya tura jaririyar jikinta “Ungo tsiyarki Talatu, Allah dai ya tsinewa haihuwa irin taki ace duk sanda zaki haihu mace zaki haifa don masifa..” Wannan karan ba Talatu ba Har Jabiru sai da ya saki hawayen bak’in ciki musamman jin yarda A’isha ta tsanyara kuka saboda bugeta da yayi da hannunsa garin turata. Suna kallo ya shige ‘daki yana fa’din “Komawa zan yi ba zan zauna bak’in ciki ya kashe ni ba, Amma kafin na koma sai na samu dalleliyar yarinya na aura na huce takaici, ke kuwa wallahil azeem sai dai ki yi wahala da y’ay’anki ina tsiya ina haihwuar yara mata.” Tana kallo Ya saka kai ya fice daga gidan bayan ya fallawa Majeeda yarinya y’ar shekara hu’du mari ya fice yana “Shegun ‘yay’annaki idanunsu kamar na mayu.” Ya fice ya bar Talatu da tafasar zuciya ta rasa wa zata rarrasa tsakanin Majeedah Aisha da Jabiru da shi ma yake kukan kamar mace. Kabiru gidan mahaifinsa kai tsaye ya wuce akan sabon machine ‘dinsa, sanye da shaddarsa da aka yiwa bugun k’yalli. Tun a tsakargida ya fara musu yayyafin Naira. Da’di kamar ya kashe Innarsa ‘danta Kabiru ya ku’dance bata damu da inda ya shiga ya fita ya samo ku’din ba. Sai da suka gaisa ta ce “Oh Kabiru shikkenan kuma sai muka nemeka b’at muka rasa.” Ya ‘dan shafa sajen da ya tara yana fa’din “Neman ku’di Inna, birni na wuce don na lura idan ka zauna a k’auyen nan ba zaka tab’a arziki ba.” “Tabbas kuwa Kabiru yanzu da ka tsallaka ga ka nan shar da kai.” Ya na dariya ya ce “Wallahi kuwa Inna ai bana Insha Allah zaki sauke farali.” Innan ta ‘d’an ja ajiyar zuciya “Wace ni da zuwa Makka bayan matarka tana ta haihuwar yara mata akai akai kamar wacce aka cewa jeki kya gani, ai tarin aurensu ya kamata ka fara.” Ta fa’da da gatsali don itama haihuwar Talatun tana ci mata tuwo a k’warya, kuma hakan da tayi so tayi ta bugu cikinsa ta ji ko ya damu da Talatun da yaran da take haifa masa. Sai ta ji Ya ce “Wa? ni? Allah ya kiyaye ai sai dai ta nemi uban da zai wa yaranta kayan ‘daki don masifa a ce shekara hu’du y’ay’an mace uku, kuma duk mata, ni wannan ta k’arshen ma ban san da cikin ba sai haihuwar na ji, ni fa Inna zama na da Talatu ya isheni tana can ta yamushe kamar tsohuwar mota, don haka sakinta zan yi..” “Kada ka fara, so kake mak’iya su saka ni a wak’a, ka barta da halinta ka samu wata kai kuma ka aura abinka ita kuma ta ci kanta ita da yaranta.” Kabiru ya ji da’din maganar mahaifiyarsa don haka ya gyara zama yana fa’din “Hakan ma za’a yi Inna, yanzu wace yarinya zaki samo min a garin nan y’ar manyan mutane.” Inna ta yi dariya sosai kafin ta ce “Haba dai Kabiru garin nan kuma? Ai birnin zaka koma ka samo y’ar manyan mutane ka aura tunda dai yanzu arziki ya zauna maka kamar yarda nake so.” Ya yi tsam da ransa yana tunanin anya matan birni za su so shi? Sai dai kamar yarda Innarsa ta ce arzikinsa shi zai siya masa aure don haka Ya ja ‘damarar auren matar birni. Tabbas Innarsa ta yi gaskiya da ta ce yafi k’arfin matan da Suke k’auyen Shagogo. Ya kissima kalar matar da yake so ya aura y’ar manyan mutane mai ilimi matar da zai shiga da ita duk inda yake so. Haka ya tashi Ya bar Innan bayan ta da’da kambamashi da sanar da shi ko y’ar sarkin kano ya ce yana so Babu mai hana shi in dai da uwar ku’dinsa. Yana fitowa ya yi kicib’us da Hadi abokinsa Hadi Har da tsallensa yana fa’din “A’a lallai Inye sai ga Kabiru. Ko da yake yanzu ka zama Alhaji Kabiru, wai don Allah menene sirrin ne? Ko nima dai birnin nan zan zo na bika.” Nan da nan fara’ar da take fuskar Kabiru ta ‘dauke ya girgizawa Hadi kai “Ba zaka iya harkar da nake ba Hadi, don haka kawai ka tsaya a inda kake.” Hadin ya kalleshi Galala kafin ya ce “Bak’in ciki kake min Kabiru?” Ya girgiza kai “Ba wani bak’in ciki ni gaskiya kawai na gaya maka Amma idan ka ga sai ka je sai ka bari na gane kan harkar sosai tukun na sai nazo na ja ka.” Hadi ya amince da haka suka k’arasa daga majalissar abokansu inda suke zama. Tsaf ta gyara gidan ta kuma yi masa tuwon masara mai kyau miyar kub’ewa har wake ta watsa saboda miyar ta sake ‘dan’dano. Ta wanke yaranta tas duk don kada ta sake laifi a wajensa. Sannan ita ma ta yi wankan ta saka Jabiru ya amso mata bashin turare mai sauk’in ku’di Wanda ake ‘durawa a K’walabe k’anana. Jabiru ba don ya so ba yaje siyan turaren nan yana tafe yana tsinewa Kabiru. Atamfarta da take sonta sosai duk da ta sha jiki sai dai itace sabuwa a cikin kayan ta ita ta saka ta ‘d’an yi kyau da ita Har da wanke kai da taje shi ya yi baya, sai ga kai yana k’yalli abinka da gashin fulani, kuma da yake mace ce mai tsafta tana kulawa da jikinta sosai. Tun da ya doso gidan ya ji zuciyarsa ta fara tsananta da b’acin rai, sam baya son tafiya gidan don ya san kwashi kwaraf zai tarar a gidan sunan da ya saka mata kenan. Gaba ‘d’aya yanzu gani yake ya fi k’arfin a kirashi da mijin Talatu saboda yarda yake ji da tashen naira, ku’din da ba a San inda ya samo su ba.. Kamar yarda ya saba haka ya danna kai cikin gidan ba sallama bakomai sai gyaran muryar da shi yake nuna musu ya dawo. Majeeda a tsorace ita da Zainab suka rungume Jabiru suna k’ikkifta ido, ba don komai ba sai don tsoron mahaifinsu da ya zame musu tamkar dodo jikinsu Har rawa yake, hakan ya ankarar da Kabiru Ya watsa musu wani kallo, mai nuni da zallar takaici shi suke gani su razana haka kamar wani Dodo ai kuwa yau zai yi maganinsu. Ya shige ‘daki Ya cire babbar rigarsa Ya wurgar don daman sabonsa ne duk abinda zai cire wurgar da shi zai yi sai dai Talatu ta ‘dauka ta adana na wankewa ta wanke. Wata igiya ya hango mai kauri igiyar da Jabiru yake k’ullo itace idan ya yiyo. Ya zaro igiyar ya fito tsakar gidan da sauri. Majeeda ya fara ja daga jikin Jabiru duk da k’ok’arin Jabirun na son cetonsa sai dai da yake Kabirun jibgege ne tuni ya wancakalar da Jabirun a gefe ya fara zabga musu igiyar. Zaniya sosai ya musu tun suna ihu har suka kasa ihun sai mayar da numfashi suke. Sai da hannayensa suka gaji sannan ya yar da bulalar yana zubawa Talatu ido “Ko zaku rama musu ne don na ga kuna hararata.” Talatu ta mayar da k’wallar bak’in cikin data gangaro kwarmin idonta tana girgiza masa kai cike da takaicin halayensa, ya shige ‘d’aki yana fa’din “Gobe ma don Uban yarinya ta sake gani na ta gudu. Y’an jakar Uba idanu kamar na mayu.” Ya ci karo da kwanukan tuwon da ta jera masa, ya ‘dan bu’de da sauri kafin ya saki tsaki ya mayar da kwanon ya rufe ji ta yi yana k’wala mata kira da wani sabon suna da ya ra’da mata “Ke Uwar y’ay’a Ballagaza zo nan..” Ta mik’e ta saka k’afa zata je Jabiru ya ce “Don Allah Yaya kada ki je.” Ta juyo tana masa alamar ya yi shiru ta shiga cikin ‘dakin. Durk’usa wa ta yi sosai murya a raunane ta ce “Ga ni.” “Na ganki Ai, uban wa kika ajiye da zai ci miki bak’in abin nan? Na miki kala da mutumin da zai ci irin wannan abincin?” Ta yi saurin girgiza kai “To maza ‘debe shirginki kafin na miki facali da su a fuskarki shashasha kawai. Takaicin Uba.. Na Nazeefah Nashe Pg 18 💔💔💔💔💔💔 Ta runtse idanunta tana Jin takaici da zafin zuciya yana k’ok’arin buga mata zuciya, Ya Ilahi ya Kabiru yake so ta yi ne? Wannan wulak’anci tabbas ya fara mata yawa sai dai rashin takamaimai inda zata je ne yake durk’usar da ita a gidan Kabiru, tabbas da ta San inda zata ga dangin mahaifiyarta da bata zauna gidan wannan bak’in azzalumin ba, da bak’in cikinsa yake shirin aikata lahira. Ta sauke idanunta kan abincin da ta sha wahalar girka masa shi, har sai da ta surfa Masarar ta wanke ta tas, sannan da daketa a turmi Amma duk da wannan wahalar Kabiru yake kiran tuwon ta da bak’in tuwo alhali ko Mara gani sosai ya dubi tuwon nan ya san fari ne tas da shi, tuwon da babu ficikarsa a ciki ta yi ne kawai don ta kyautata masa a matsayinsa na Wanda ya bar gida wata da watanni. “Ba zaki kwashe ba? Sai na kifa Miki mari?” Ta juyo muryarsa a sama cikin daka tsawa, a razane ta hau tattare kwanukan ta fice da su da sauri hawaye na bin fuskarta, ta zauna a tsakar gida hannayenta zube a k’unci tana kallon yaranta da Jabiru yake ta hidima da su, tunani ta zurfafa a cikin sa na yarda ta taso a rayuwarta cikin wahala ga shi har zuwa yanzu bata huta ba, ba mamaki ma yaranta su tashi suma a wahalar.. Kuka ne sosai a kufce mata ta shiga furta “Ya Allah kada ka k’addarawa yara na koda makamanciyar wannan wahalar balle irinta.” Tana zaune ta dinga jan Hasbunallah kafin ta ji zuciyarta ta yi sauk’i. Daga ‘dakin ya dinga k’wala mata kira hakan ya sa ta farka daga tunanin da take ciki a razane, da sauri ta amsa tana shiga k’uryar ‘dakin. Sai da ta bita da kallon sama da k’asa sannan ya saki tsaki “Mace duk a koma’de, ni dahalla samu mifici ki yi min fifita na kasa barci. Wallahi na tsani na bu’di ido na ganki wai a matsayin matata, na rantse da Allah da na San haka zaki koma’de ba ta yarda za’a yi na biya sadaki na aureki, ga shi yanzu kin zame min k’arfen k’afa na sake ki ace ban Miki adalci ba don na ga ba inda zaki idan banda haka wallahi sakinki zan yi ki tafi gidan Ubale.” Bata masa magana ba haka ta dinga masa fifitar yana antaya mata bak’ak’en maganganu ga Kukan A’isha tana ji Amma ya hanata zuwa ta ‘dauketa. ___________________ Haka rayuwar ta cigaba da gangara musu cikin matuk’ar wahala da rashin matallafi sai Allah, Kabiru idan yasa k’afa ya tafi birni bata sake Jin ‘duriyarsa sai ya yi wata shida, ga shi baya ajiye musu komai ita takewa kanta da y’ay’anta komai, a hakan har makarantar boko ta gwamnati ta cilla Majeeda da Zainabu, suke tafiya da Jabiru da yake secondary. Har fargabar zuwan Kabiru take saboda da yazo tijara iri-iri yake mata, kuma ba yarda ba tayi da shi ya bata ku’di a mata aikin bu’dewar da gabanta ya yi Amma Kabiru ya hana ya ce ba shi da shi, ita kuma ku’din Sun mata yawan da ba zata iya biya ba, don haka ta yi zamanta a haka tunda shi yake mora ai ba ita ba. Ta wani fannin ma ita hakan ya fiye mata, tunda ko bakomai ta samu hutun haihuwa da gurzar da yake mata ba dare ba rana tunda yana daga cikin irin Harijan mazan nan. Kwatsam wata tafiya da Kabirun ya yi da ya tashi zuwa gida sai suka gan shi ya dawo da dalleliyar mace babbar mace sosai kuma Wanda a haife ta haifi Talatu tare suka zo a cikin mota yana janta. Tunda zauren gidan suka fara jiyo k’amshin matar don haka Talatu ta hau zuba ido tana son ganin mai shigowa. Tsaye turus ta yi sanda ta ga Kabiru y’a shigo da matar suna tafe suna wasan banza a tsakaninsu yana dukan mazaunar matar da k’afafunsa alamar a cikin nisha’di yake. Talatu ta tsaya tana kallonsu yarda suke lamura ko kunyar k’ananan yaran ba sa ji. Ya wani kama matar ya rungumeta yana shafar jikinta, da sauri Talatu ta kalli Jabiru da yake tsaye yana anta yawa Kabirun mugun kallo ta ce “Jabiru maza ku tafi ka raka su makarantar allo kafin ka wuce gonar.” Jabiru ya janye yaran suka fice yana Jin kamar ya mangare Kabiru da yake shirin tub’ewa matar riga, to yarda ya zura kansa yana laluben matar kamar mayunwacin zaki, dama kuma shiryota ya yi, yazo ne don ya ba’kantawa Talatu ko ta gaji ta hak’ura da aurensa su gudu da yaranta idan ta ga matar da ya aura, ya sha alwashin sai ya koreta don a gabanta zai dinga saduwa da matar idan ma bata gudu ba, yafi so zuciyarta ta buga ta Mutu ya huta ta yarda babu mai zarginsa. Da sauri Talatu ta shige ‘daki tana Jin zuciyarta na shirin bugawa kamar wuta, ta jingina da bango hannayenta a k’irji sai mayar da numfashi take na zallar takaicin Kabiru da bak’in cikin rashin wajen zuwa da tabbas bata k’ara koda awa guda a gidansa ba zata tsere kafin Kabiru yasa bak’in cikin sa ya kasheta. Tana runtse da ido hawaye na malala ta ji Sun danno kai cikin ‘dakin suna sakin wata irin dariya. Yanayin da ta gansu ba kaya a jikinsu ya sata saurin saka k’afa zata bar ‘dakin sai dai me? Sai Jin muryar Kabirun ta yi yana fa’din “Kina fita daga ‘dakin nan, a bakacin aurenki ki tsaya ki ga yarda ake saduwar aure mai da’di da cikakkun mata masu cikakken Gaba ba naki fafaroma ba..” ta tsaya Cak bata jiyo ba, Amma Kabiru yana kan matar yana wani irin nishi ya ce rashin juyowarki da kallonmu kamar kin tsinke igiyar aurenki ne..” Jin haka ya sa ta juyo jikinta na rawa ganin wasu irin abubuwa da suke ta runtse idonta Kabiru ya sake daka mata tsawa ya ce “Bu’de ki ga yarda macen da ta San abinda take, take kula da mijinta…. Wayyo sahiba cigaba da’di da’di…….” Wani irin duhu Talatu ta dinga gani kafin su ji kif ta kifa da alama zuciyarta ta buga kamar yarda Kabiru yake so…. Kabiru bai bi ta kanta ba sai da suka samu gamsuwa sannan ya isa inda take yana fatan Allah yasa ta Mutu ya huta, sai dai burinsa bai cika ba domin da alama akwai sauran kwana tare da ita don jijiyar hannunta tana motsawa, ya saki tsaki ha’de da janta gefe ya fice daga ‘dakin. Wanka suka yi tare da karuwar matarsa da take jurewa Harijancinsa, don itama Harija ce mabu’kaciya ta masifa kuma ta da’de tana Neman miji kamar Kabirun bata samu ba dalili kenan da aurenta yake ta mutuwa sai dai gamuwarsu da Kabiru a gidan wata magajiyar Karuwai ta ji shi a jikinta a matsayin irin mijin da ta da’de tana nema shikkenan ta ce ta samu mijin aure don duk maitar sha’awarta tsaf Kabirun yake ‘dauke mata har ma ya buk’aci k’ari hakan dama take so shi ya sa zamansu ya zo ‘daya take lallab’a Kabirun kamar k’wai don bai k’i su kwana suna Abu ‘daya ba ba ya gajiya Sam, style kala-kala na kwanciya ba Wanda shi da matar ba su k’ware a kansa ba. Suka yi wanka suka saka k’afa suka fice daga gidan, yana fatan Allah yasa kafin su dawo daga gidan su Talatu ta k’arasa cikawa shikkenan ba shi da wata sauran matsala… Takaicin Uba… Pg 19 Nazeefah Nashe. 💔💔💔💔💔 Shigowar su Jabiru da yarda suka tarar da ita ne yasa hankalin Jabiru a tashe ya yi kanta da sauri yana girgiza ta, sai dai shiru babu alamun numfashi a tattare da ita, da sauri Jabiru ya kandamo ruwa ya zuba mata, sai sannan ta saki ajiyar zuciya tana kallon su Jabirun da k’yar ta mik’e zaune tana Jin yarda k’irjinta ya mata nauyi. Abubuwan da suka farun suka dinga dawo mata daki-daki ta runtse idonta tana fatan duk abinda ya wakanan ya zama mafarki… zata so hakan, zata so ace mafarki take don lamarin yafi kada da mafarki ba gaskiya ba… Maganar da Majeedah ta yi ne ya sata ta bu’de idonta da k’yar tana kallonsu ganin yarda suka zuba mata ido yasa ta yi k’arfin halin tartaro nutsuwa ta sakawa kanta. Tana murmushin k’arfin hali ta kalli Jabiru ta ce “Me yasa ka watsa min ruwa ina barci na mai da’di?” Jabiru ya ‘dauke k’wallar da take idonsa don baya son k’ara mata damuwa a kan wacce take ciki. “Na tashe ki kin k’i tashi, shi yasa na zuba miki ruwa.” Ta sauke kakkaurar ajiyar zuciyar tana kallon Majeedah da Zainabu da suka yi zugum, sai kuma ta mik’e tana fa’din “Kai mu je tsakar gida mu sha iska..” “Mama Baba Mugune, ba zai ga Annabi ba ko? Kema dukan ki ya yi? Dama ya mutu.” Cak ta tsaya daga shirin ficewa daga ‘dakin da ta yi ta juyo tana kallon Majeedah da take furucin kuma da alama iya gaskiyar abinda yake zuciyarta kenan. Ranta a b’ace ta dawo ta ‘daga Majeedah ta zuba mata mari “Kul na sake ji Majeedah mahaifin naki kike kira da wannan kalamin.” “Ba shi da sunan da ya zarce wannan Anty Talatu ki barta ta fa’di abinda yake ranta.” Jabiru ya fa’da fuskarsa kamar ya saka kuka. Talatu ta bi bango ta sulale ta zauna hankalinta a tashe, ta fara tunanin wace wauta Kabiru yake da har ya sanyawa y’ay’ansa tsanarsa ba tare da ya lura da cewa Kansa yake cuta ba.” Kuka ne ya kufce mata ta fara tunanin mai zai faru ranar da aka wayi gari y’ay’anta Sun k’i mahaifinsu saboda tarin laifukansa Ya subhanallah! Allah ka shiryi Kabiru ka ganar da shi gaskiya tun lokaci bai k’ure masa ba. Ta furta a hankali kafin murya a raunane ta dafa Jabiru da Majeedah ta ce “Ku yi hak’uri musamman ke Majeedah ba a tab’a canja mahaifi kuma ko me ya yi Miki har abada yana nan a sunan mahaifinki don haka ki ce Astagfirullah Akan sab’on da kika yi, idan ba so ki ke Allah ya k’ona ki ba.” Da sauri Majeedah ta ce Astagfirullah Allah na tuba sannan ta fa’da kan Cinyar Talatun tana kuka tana fa’din Mama ni bana son sa tunda kema ba ya son ki.” “Ba zaki daina ba kenan ko Majeedah?” Ta furta a tsawace kafin ta tureta daga jikinta ta mik’e ta yi tsakar gida tunawa da ta yi yaran ko abinci ba su ci ba. __________ ⭐️Haka rayuwar ta cigaba da gangarawa cikin wani irin yanayi mai wuyar fasaltuwa a wajen Talatu, Zamani ne da ba zata manta da shi ba kacokam zata iya kiran kanta Mara sa’a a rayuwa a wancan lokacin. Kabiru ya banzagatar da ita da y’ay’anta tun bayan da ya fahimci bata da mamora ya bi kuma duk wata hanya ta cusguna mata don ta gudu ta bar aurensa, Amma Talatu ta yi mursisi a gidan auren saboda ba ta da inda zata je, don haka tilas ta hak’ura da duk wani wulak’ancin Kabiru. Idan ya saka k’afa ya bar k’auyen ma sai ya shekara bai waiwayesu ba da ita da yaranta ita take kula da su gaba ‘daya Jabiru shi yake fita ya yi hak’ilo ya samo musu tsabar abinci ita kuma ta samo musu Kayan masarufin da zasu dafa abincin. A wannan yanayin katsaham Kabiru ya zo garin, ya kuma sanar mata za su koma cikin garin Kano kuma shawarar matarsa mai tsohon ciki ya bi, Akan ya zo ya tafi da Talatun ta dinga yi mata aikace-aikacen gidan, don Kabiru ya zo birni a sa’a duk da har a lokacin ba a San sana’arsa ba Amma fa yana da gidan Kansa da motarsa ta hawa, gida kuwa mai gate duk da dai ba tanfatsetse bane a Amma a wajen mutanen k’auye dole za su kira shi aljannar duniya. Talatu ta yi Jim tana kallonsa, Sam bata son binsa birni anan ma da yake ganin idon Wanda ya sani yana wulak’anta ta ina ga an je birni, cikin k’asa da murya ta ce “Ni dai da zaka bar mu anan ‘din da yafi bana son zaman maraya.” Ya watso mata harara kafin ya ce “Ai kuwa idan kika ce ba zaki bi ni ba, ki tabbata kin yiwa igiyar aurenki. Da kika samu ma zan Kai ki birnin aikin banza banda Sahiba ce ta takura ni ban ga dalilin da zan yayabeki zuwa birni ba.” Tana Jin haka ta ja bakinta ta yi shiru ta tashi ta fara ha’da musu tsummokaransu don dai su ne kawai da su ba wani abin ba. Don ko katifa ba su da ita ta lalace gaba ‘dayanta. Sai da za su tafi sannan ta ga Ashe har da Hadi da matarsa kuma suna ‘dan ‘dasawa da mAtar Hadin, Hadin ne dai Sam ba sa shiri. Wani k’aramin gida Kabirun ya kamawa Hadin anan unguwar da yake, ba don komai ba sai don Hadin ya iya masa banba’danci. Tunda suka sauka suka fara kalle-kalle abinka da ba sabanba kuma ba su tab’a shiga birnin ba. Sanda suka je gidan Kabirun suka shiga falon matar sa Sun yi mamakin ganin dukiyar da Kabirun ya tara Amma ya kasa tallafarta da yaranta. Ta ha’diye wani Abu mai ‘daci bayan da ya umarceta ta durk’usa ta gaida matar, dama ko bai ce ba ta yi niyya don ita dai bata ga Aibu ga hakan ba tunda dai matar ta girmeta, sai dai shi hakan da yayi ya yi ne don ya cusguna Mata. A yatsine take amsa gaisuwarsu kafin ta watsa wa Kabirun wani kallo ta ce “Mai da’din ai sai ka kaisu can ‘dakin bakin gate ko? Don ka San dai wannan k’azantar ba a gidana ba, ka kuma sanar da ita dalilin da yasa ka dawo da ita nan ko? Don ban amince kwanciyar aure ta shiga tsakaninku ba, ba zan iya wannan jagwal ‘din ba ina zaman zamana a harba min ciwon sanyi, kai ma bak’in nacinka ka saki matar nan ka k’i sakinta, ko da yake barta ma na huta Neman y’ar aiki Amma dai zan gaya Miki ba ke ba mijina, nawa ne ni ka’dai na fi son ko da yaushe na ji shi a jikina kina ji na ko? Idan kin kiyaye komai kike so za ki samu ke da yaranki Amma idan kin k’i zaki ga wulak’anci wallahi.” Ta fa’da tana wani k’as k’as da chewingum sai kuma ta watsawa su Majeedah harara “Ku don ubanku baku iya gaisuwa bane?” Kabiru ya ce “Ina za su iya? Ai bata koya musu ba, ban da abinki kema mai zak’in me zan yi da ita yanzu matar da ta wawake kamar k’ofar gari ai ta tashi daga aiki ina zaune da ita saboda har yanzu ta k’i yi min gagarumin laifin da zan saketa almura da tuni na aikata ta tafi duk inda zata je ma.” Wani k’ululu ne ya tokarewa Talatu k’irji sai dai ta danne kukan da take ji yana taso mata don bata San ta nunawa Kabiru karayarta da wuri, don ta fahimci don ya tuburata ya ‘daukota ya kawota nan, to zata jure zata jure duk wani k’alubale da zata fuskanta daga wajensa fatanta Allah yasa ta amsa jarrabawarta daidai. Kabiru ya mik’e yana harararta “Sai ki mik’e mu je na raka ki, kin kwaso sangamemen ‘da kin taho min da shi to kuwa sai dai ya zama Maigadi ya dinga kwana a bakin gate.” Bata ce masa komai ba, har zuwa sanda ya kaita wani ‘daki da yake bakin gate, wani ‘dan mitsitsi da shi, sai k’aramin Toilet da yake daga harabar gidan. Ta da’de a tsaye tana k’arewa ‘dakin kallo kafin ta saki ajiyar zuciya tana addu’ar Allah ya bt hak’uri da juriya a kan duk wani k’alubale da zata fuskanta a zaman gidan nan. Yana tsaye yana binta da kallo kafin ya saki tsaki “Ba za ma ki godewa Allah kin samu cigaba ba? Daga turb’aya kin koma ‘daki mai shimfi’de da leda?” Karo na farko ta Ware idanunta a kansa tana Jin kamar ta ce masa gwara turb’ayar akan nan inda ka kawo ni a wulak’anta ni, sai dai bakinta ya gaza furucin, bata Saba ba bata saba iya mayar masa da magana ba bata da wannan courage ‘din. Don haka ta mayar da idanunta k’asa tana ji ya zabga tsaki ya fice daga ‘dakin yana fa’din “Idan ba za ki iya ba, sai ki ja komatsan yaranki ku tafi duk gidan uwar da kika ga dama.” Zubewa kawai ta yi a k’asa sarai ta lura da take-taken Kabiru kora da hali kawai yake mata, ita kuma har yau ta kasa hak’ura ta tattara ta tafi ta bar shi, Ina ma zai bata gida ta yi zamanta da yaranta to da sai ta ce ta amince ya saketa. Su Majeedah suka matsa jikinta suka kanainayeta ga yunwa suna ji fuskarsu kamar su saka mata kuka, ta ja su ta rungume a jikinta a hankali ta ce ‘KHAIRAN IN SHA ALLAH’ Wunin ranar a tsaye cur ta yi shi saboda aikin da Karimatu ta yi ta saka ta, aiki take tuk’uru har sai da gab’banta suka dinga ciwo. Da daddare da kanta Kariman ta zuba musu wani abinci ‘dan mitsil a cikin k’aramar cooler, sanda ta bu’de abincin da suka hannu iya su uku yaran suka cinyeshi ban da ita da Jabiru, don hak’ura suka yi suka bar yaran da suke ta kukan yunwa tun yammacin ranar. Haka rayuwa ta dinga gurgura musu ba wani haske da suka samu a rayuwar kullum a cikin duhu suke, tsawon wannan lokacin daga shi har matarsa Sun mayar da ita kamar mai aikin gidan, idan ka shigo ma gidan ba zaka tab’a tsammanin matar gida ba ce saboda yarda kamanninta ba su dace da hakan ba, yaranta ba suturar arziki duk da ta samu Karimatu ta saka Mai da’dinta ya kai yaran makarantun gwamnati a cewarta suna hanata barci, da zarar Sun dawo kuma za su tafi makarantar allo sai ka ji gidan sak’at sai b’uruntun Talatu tana aiki. Duk da tsohon cikin kullum tana kitchen tana juyo iface-ifacensu wani lokacin sai suna tsaka da saduwa da ranar Allah Kabiru zai k’wala mata kira ya ce ta kawo musu ruwa idan ta kawo kuma ya ce sai ta tsaya ta kalla ko kuma a bakacin aurenta, haka zata tsaya tana kallonsu a ranar idan ba wani ikon Allah ba ba zata yi barci ba saboda yarda zata samu kanta a Jin zafaffiyar sha’awa har kuka take da hawayenta, wani lokacin idan ta yi niyyar Jawa Kabiru Allah ya isa sai ta ji ta kasa musamman kasancewarsa Uban y’ay’anta idan ya tsiyace ya lalace dole za’a kira shi uban y’ay’anta. A wannan mugun zaman da suke Cikin Karimatu ya isa haihuwa da ta tashi haihuwar sai Allah ya bata haihuwar ‘da namiji zo kaga murna wajen Kabiru ya dinga wage baki yana fa’din “Allah nagode maka, yanzu ne na san na haihu da na haifi ‘da namiji ba mace, Kabiru ya yi magaji.” Dole a lokacin Talatu ta sakawa kunnenta auduga ta rufe idanunta ruf, ta daina ji ta daina gani duk don kada ta ‘dorawa kanta ciwon zuciyar Rashin mutuncin da Kabirun yake mata. Sa aka yanka a haihuwar aka yi kuma gagarimin suna, abinda bai tab’a ha’da shi da sauran y’ay’ansa ba, ko Majeeda da take y’ar fari bai mata yanka ba. Su dai nasu idanu Talatu kuma ta kwab’esu da koda wasa kada su sake su yi abinda Ubansu zai harzuk’a da su, komai lokaci ne wata rana sai labari. Satin Karima biyu da haihuwa cikin dare matsuwa ta saka Kabiru ya nufi ‘d’akin Talatu ba tare da sanin matarsa ba. Talatu sai jinsa kawai ta yi a jikinsa tana shirin kwa’da ihu ya fella mata mari ha’de da cewa kina magana ta ji wallahi a bakin aurenki, haka ya gurji Talatu ba ruwansa da su Majeeda da suke kwance Wanda Talatu bata tantama Majeedah ta farka kuma ta gan su don bata da nauyin barci. Ba laifi ya ‘dan ji ta ha’de ka’dan sai dai ba kamar lokacin farkon aurensu ba. Haka ya mik’e yana gyara wandonsa “Saura kuma ki bari ta fuskanci wani abin ya shiga tsakaninmu wallahi a bakin aurenki.” Ya fice yana sakin tsaki bayan ya tsallake Jabiru da duk abinda yake yi a cikin kunnensa. Daga wannan kusantar da ya yi mata cikin ikon Allah sai cikin Deejah ya shiga, ba tare da ita kanta Talatun ta sani ba don tuni Karima ta gyare jikinta suka koma suna gurzar amarci ya manta da wata Talatu. Sai da ciki ya yi wata biyar sannan Karima ta ankare ranar Talatun na mata gyaran falo ta tsaya tana dubanta kafin ta ce “Zo nan Talatu? Me ye wannan nake gani a jikin ki kamar ciki?” Talatu a daburce ta dinga ja da baya tana shafa cikin da tun watan jiya da ya fara motsi ta San da shi. Karima ta k’unduma wani uban zagi kafin ta ce “Kan Uba? Wato haintata ku ke? Ke da wancan bak’in munafukin?” Da sauri Talatu ta zube a wajen don ta tabbatar yau zamanta a gidan Kabiru ya k’are….. Takaicin Uba… Pg 20 Nazeefah Nashe 💔💔💔💔 Jikin Talatu sosai ya fara rawa, gwuiwoyinta da take durk’ushe a kai suka gagara ‘daukarta bata San sanda ta zube turus akan mazaunanta ba. Gumi ko ta ina ya shiga zubo mata.. Kariman na shirin sake magana shigowar Kabiru ya katseta ta dallareshi da manyan idanunta, kallon da yake nuni da zallar tuhuma. Gabansa ne ya fa’di dalilin bai San me ya faru ba. Ya mayar da kallonsa kan Talatu da take zaune dab’as ya zabga tsaki don da alama mai zak’in ta tab’a “Kada ki damu kan ki da wannan gaya min me ta miki ba mamaki zamanta ne ya zo k’arshe a gidan nan…..” “Yi min shiru Kabiru.” Ta fa’da a tsawace “Yau k’aryar ka ta k’are me ye wannan nake gani a cikin Talatu?” Cikin mamaki ya kai dubansa kan cikin Talatun da ya fara tasawa ka’dan sai kuma ya girgiza kai yana jin fa’duwar gaba ya ce “Menene kuwa mai zak’in? Ai ni ban ga komai ba banda Tumbi da alama ta fara ci tana k’oshi zata ajiye zuguda…” Karima ta mik’e ranta a b’ace ta k’arasa wajen Talatun da ta yi k’asa da idonta tana ambaton sunan Allah a ranta, ta San dai tabbas yau aurenta da Kabiru yazo k’arshe dama abinda yake so kenan. Kallon sama da k’asa ta yi mata kafin ta ce “Ke me ye a cikin ki? Fa’da masa da bakinki saboda in ga k’arshen mak’aryaci yau.” Bakin Talatu na rawa ta ce “Ki yi hak’uri Hajiya komai ya faru ne bisa kuskure… shi… ma bai san da cikin ba?” Wani irin waro ido Kabiru ya yi ina zunduma uban ashar “Ciki? Ciki kuma? To uban wa ya miki cikin?” Karima ta fa’da idanunta cikin na Talatun. D’aga kai ta yi tana kallon Kabiru da yake k’ik’kifta ido ta nuna shi.. “Shine wallahi tun bayan haihuwarki da sati biyu ya je ya haik’e min, daga nan ne ciki ya shiga.” Karima ta saki salati tana kallon yanda Kabirun ya yi tsilli-tsilli kamar bawan da ya yiwa Uban gidansa laifi, sai zuba gumi yake yana jin kamar ya shak’o Talatun Ya mak’ureta Ya shek’ata barzahu. Cikin tsananin Kishi Kariman ta dinga zabga musu harara dukkanninsu kamar wa’danda suka aikata zina, sai kuma ta ciji leb’e ta shige ‘dakinta tana fa’din bari na tattara na bar muku gidan tunda ka samu wacce ta fini a wajenka wallahi ka bani mamaki yaushe zan iya wannan kwamacalar?” Da sauri Kabiru ya bi bayanta bayan Ya kaiwa Talatu hauri da k’afa yana fa’din “Wallahi ba abinda zai hana ni sakin ki a yau ‘din nan, mara mutunci kawai.” Koda ya bita ‘dakin tana tattara kayan k’arya da niyyar harzuk’a masa tunani bata yi aune ba ta ji mutum a jikinta, ya san yarda take mabuk’aciya ba zata iya tsallake abinda take masa ba, dama tarko ya ‘dana mata, tuni suka yi luf suka fara aikata abinda suke so, tun Talatun na jin iface-ifacensu har ta ji tsit. Jikinta a salub’e ta mik’e ta nufi ‘dakinta ta fara tattara musu kayansu kafin su dawo daga makaranta su yi gaba, don dai ta tabbata yau zamanta a gidan Kabiru ya k’are. Wani irin k’unci da zafi game da ra’dadin zuci da na gangar jiki take ji, hawayen ma ya k’i zuwa tana mamakin hali irin na Karima da Kabirun ma gaba ‘d’aya kamar ba su San tana da hak’kin aurensa a kanta ba? Komai ya lafa a tsakaninsu, Kabiru ya yi mata bajintar da kaso mafi yawa daga b’acin ranta ya zagwanye, illa zallar kishin da yake neman ya kassara mata zuciyarta. Yana matsa kumatunta ya ce “Dafatan dai kin hak’ura mai zak’i kamar zuma.” Ta lumshe idanunta tana fa’din “Dole na na hak’ura Amma iya laifinka ka’dai na hak’ura banda na waccen matar, a yau nake so ka saketa ka mayar da ita can k’auyen inda ka ‘daukota idan ya so ko gidan ka bar mata ni dai bana son tana shigarta yarda kake shigata kishi nake ji sosai.” Yana dariya ya ce “An gama yau nima ai ta kai ni bango, a dole fa naje na kusanceta…” da sauri ta ‘daga masa hannu “Bana son jin kalmar nan Mai da’din tana bak’anta min rai.” Ya kai mata sumba ha’de da fa’din “An gama my madara.” Ya fice yana y’ar wak’a jin sa yake a sama yarda Karima ta tarbeshi yau abin ya yi santi ne, kai Karima ta ko ina kin kai mace canca’di ni da k’orama.. Ya fa’da daidai lokacin da yake saka kai ‘dakin Talatu Ya San kuma ta ji shi sarai kuma daman don ta ji shin ya fa’da. Ta ha’de y’an suturunsu kaf a buhu tana zaune ta zuba uban tagumi. Ya ja tsaki “Maganinki ai, ba bakinki ya iya magana ba ai yanzu kya tattara ki koma k’auye ke da yaran ku cigaba da cin gabzar tuwo kuma ko haihuwa kika yi kada ki nemeni in dai ba namiji kika haifa ba ki ra’da sunanki da kanki Amma ni na sake ki saki ‘daya…..” Da sauri a kuma razane ta ‘d’ago tana kallonsa kafin ta zube a gabansa “Don Allah Ka yi hak’uri kada ka yi min haka ina kake so na je?” “Ki koma can gidan k’auyen na bar Miki zan sanar a garin da shaidu da komai.” Ta ‘d’an saki ajiyar zuciya jin abinda ya ce, In dai da muhalli ta amince ya saketan zata je ta kula da kanta da rayuwar yaranta da yanzu sune a gabanta, duk da k’ank’antar shekarunta ta gwammaci ta yi rayuwa ba aure a kan rayuwar auren Kabiru, da babu abinda zata k’arar sai tashin hankali gwara ta je ko k’asa su dinga ci in dai za su rayu. Ya fito tsakargida Ya k’walawa Karima kira, ta fito cikin kissa daga ita sai wani gajeran wando da riga vest Kabirun yana kallonta yana murmushi ya ce “Haba mai zak’in, kada kisa mu koma ruwa mana, kin san fa bana gajiya da nink’aya a k’oramarki ta zuma.” Ta ‘dan ka’da harshe “Kazo mana My da’din ai ka San bana gajiya da amsarka tunda kullum k’oramar a cike take ba k’andas ba…” A gaban Talatu suka fara tub’e surutun jikinsu kafin ya ‘dauketa cak su shige ‘daki. Talatu ta dinga kokawa da numfashinta kafin ta runtse idanunta tana kiran sunan Allah a zuciyarta. Da k’arfi ta dinga kiran Ya Allah ka agajeni kada bak’in cikin Kabiru ya zama ajalina. Bayan dawowarsu daga makaranta Kabiru ya zari dubu biyar ya bata a cewa su shiga mota su koma can Shagogo. Haka ta ‘debi yaranta zuwa tasha. Jabiru ne ya ‘dauki kayansu da yake cikin buhu suka tafi shi kam don ta shi zamansu a Shagogo ya fiye masa wannan zaman rashin y’ancin da suke yi, gwara can sai su da’de ma ba su ga matsiyacin ba, don tuni ya ba shi suna. Zuciyarta bak’i k’irin suka isa garin Shagogo ta bu’de musu gidan suka shiga, ragowar canjin hannunta da shi ta bawa Jabiru ya yi musu ‘dan siye siye na kayan abinci kafin a wayi gari ta aika a sanar da mutanen gari ta dawo za kuma ta cigaba da sana’arta ta surfe da nik’a dakan hannu. Haka ta jajirce wajen neman ku’di ita da Jabiru da Masha Allah yanzu ya zama saurayi ya kuma tabbatar da ba shi da kowa sai Talatu don mahaifinsa tun watannin baya da suka shige ba su sake jin ‘duriyarsa ba. Rayuwa suke ta wahala, mai cike da k’unci da ‘dacin zuciya Amma duk da haka bata fasa bawa yaranta ilimi ba ta tsaya ta jajirce a makarantar Gwamnatin da suke zuwa Jabiru ne yake taimaka musu a wasu fannin karatun da yake mutum ne mai kwanya yana da k’ok’ari sosai. 💔💔 Kabiru ya shiga wani irin yanayi na rashin sa’a a sana’arsa kullum baya samun sa’a ba kamar yarda Ya Saba ba, musamman sana’arta sa ta rashin sa’a ce tunda caca yake yi. Hankalinsa ya yi mugun tashi ganin yarda abokan hamayyarsa suke yin sama da fa’di da duk abinda ya tara, hakan yasa Ya tafi wajen bokansa samun mafita. Ya da’de yana zane a k’asa kafin ya ‘d’ago cikin murmushi ya ce “Ai kai ka kori sa’ar taka da hannunka Kabiru.” Kabirun ya waro idanunsa da son k’arin bayani, “Ban fahimceka ba?” Ya tuntsire da Dariya sosai ya ce “Ka yi nisa da taurarin da suke haska sana’artaka, waccen matar da ka saka itace sa’arka a rayuwa don kuwa taurarinka da nata sun daidaita don haka ka yi Gaggawar dawo da ita idan ba haka ba rigar sawa sai ta gagareka.” Jikinsa na rawa ya ce “Kada Allah ya nuna min hakan, Yanzu me ye abin yi?” “Abin yi yana hannunka nasarar ka tana cikin auren waccen matar da ka saka, kuskure mafi muni da ka aikata a rayuwarka. Ina tabbatar maka idan baka dawo da ita ba, abincin ci ma sai ya gagareka.” Kabiru Ya yi amanna ya yi amanna da furucin bokon saboda aikin jahilci, don haka daga nan ko gida bai koma ba, kai tsaye ya tafi Shagogo don take a wajen ya ce “Na janye sakin da na wa Talatu, na mayar da aure na da ita, tunda na San ciki ne da ita bata isa haihuwa ba balle ace ta gama idda.” ________ Tun kafin ya isa gidan karo na farko a rayuwarsa ya siya musu tsire da kayan abinci har da lemo da abaya da lemon kwalba k’waya biyar, duk ba don Allah ba sai don kad aTalatu ta yi masa bore. Karo na farko ya siyawa yaran silifas duk da bai San sizes ‘dinsuba haka ya jidesu zai ji ya goge laifinsa a wajen Talatu, duk da Har a yanzun tsanarta ce fal a zuciyarsa Amma zai yi hak’urin zama da ita Har ya yi nasarar tara abinda ya tara daga nan sai ya saketa ya tattara ya bar k’asar a lokacin Ya tabbatar Sun yi hannun riga da talauci… (Anya kuwa Kabiru? Zaka gama da duniya lafiya? 🤦🏿‍♀️) Takaicin Uba… 21 Nazeefah Nashe. 💔💔💔💔 Katsaham suka gan shi kamar a jefo shi a cikin gidan, sai yak’e baki yake duk a k’ok’arin sa na son samun fada a wajen Talatun. Tsananin mamaki ne yasa ta saki tsintsiyar hannunta da take tattare k’asar tsakar gidan, tana kallonsa a razane. Sai dai bakinta ya yi nauyi sosai wajen furta masa ko da kalmar ‘A’ ne. Haka su Jabiru suka zuba masa ido cikin jin takaicinsa ganinsa, Wanda daga idanuwansu zaka fuskanci ba su ji da’din ganinsa ba.. sosai Jabiru ya tsani arba da fuskar mutumin da kai tsaye zai kira shi bak’in mugu. Ya dinga jin tamakar ya shak’o mak’ogaronsa Ya mutu. Bai bi ta kan mugayen kallon da suke watso masa ba, ya isa inda Talatu take tsaye kamar mutum mutumi yana dashe mata hak’oransa masu kama da k’ofar gari, sosai yau Talatu ta gano muninsa Wanda da bata tab’a tsayawa ta tantance ba sai yau, sam ba zaka ganshi ka danganta shi da fulani ba, Hancinsa a baje ga fa’din fuska haka idanunsa fici-fici, abu ‘d’aya da yake b’oye muninsa shine a tsaye yake da cikakken zati da suffar jiki irinta maza ban da haka Babu wani abu mai kyau a jikin Kabiru, ta kai idanunsa kan k’afarsa faskareriya da ita kamar yarda kansa yake faskarere. Yarda yake zabga mata murmushi ne abin ya bata mamaki ta saki baki tana kallon ikon Allah, bata tab’a ganin Kabiru a yanayin farin ciki Har haka kamar yanzu ba. Ko farkon aurensu ba ta riski fuskarsa da mayalwaciyar fara’a haka ba. “Wani irin abu ne wannan Talatu? Kina gani na kin saki baki kina k’are min kallo kamar yau kika fara ganina, madadin ki taho a sukwane ki rungumeni ki nuna min kin yi kewata.” Ta dinga k’ok’ari yak’i da nunfashin da yake son kufce mata, kada Allah ya tabbatar da hasashenta, idan har aka ce Kabiru mayar da Aurenta ya yi tabbas ya cuceta, cutar da har ta koma ga rabbi ta San ba za ta daina mata k’una a zuciya ba, ba mamaki ma sanadin haka ciwon zuciya ya turnik’e ta ta mutu ko ta huta da ganin wannan kayan haushin, sai dai bata fatan mutuwarta yanzu idan ta mutu Ina yaranta za su je alhali ba su da gata… Ya k’araso kusa da ita sosai kamar mai niyyar shigewa jikinta. “Bar dogon tunani Talatu, ba inda tunani zai kai ki.. abinda kike so ki sani yanzu za ki ji shi, Ni Kabiru na mayar da aure na da yake kan ki, don haka Har yanzu a matsayin Matar Kabiru ki ke, Ya zan yi tunda kin zame min matar K’addara dole zan zauna da ke, Har zuwa sanda zan cika muradina..” Zuwa lokacin Talatu da k’yar take fusgar Numfashinta idanunta taf da hawaye ta sauke su Kan Kabiru karo na farko a rayuwarta cike da k’warin gwiwa ta ce “Ni kuma ban amince ba, ban amince da Komen ba Kabiru, ba na sonka bana son aurenka bana muradin sake zama da kai a matsayin miji na, kamar yarda ina jin Takaici kai tsaye na kiraka Uban Y’ay’ana, zama na babu aurenka Ya fiye min komai don haka ban amince ba, har abada bana son Kome gidanka…” “Ai kuwa kin sha k’arya, zama a gida na daram, tunda na gano mak’asudin arziki na yana ga aurenki da nayi, don haka dole Ki amince ki zauna da ni ko da hakan na nufin mutuwarki, Wanda bana fata sai lokacin da na gama ku’dancewa..” Ya fa’da yana mata kallon sama da k’asa, ya saki y’ar dariya “Wallahi Talatu ni kaina a dole na mayar da aurenki, don idan da macen da na tsani na bu’di ido na ganta tare da ni to ke ce! Amma Ya zan yi tunda Malamina ya gaya min ke ce sa’a ta, ke ce k’ashin arzikina..” “Ashe kuwa zaka dawwama a talauci don ba zan tab’a komawa aurenka ba, yanzu ma kuwa zan isa ga Mai gari na sanar da shi a mana iyaka da kai..” hannu yasa ya nuna mata hanya “Maza Talatu, Maza Bismillah zan ji zan kuma ga ni, idan Mai garin Ubana ne, duk duniya ba Wanda Ya isa ya b’anb’ari igiyar aurenki a hannuna sai sanda kika gama Tara min arziki a sannan zan baki lasisin tafiya don na gama buk’atarki..” Ba ta yi masa magana ba, Illa zarar mayafin da ta yi tana jin k’warin gwiwa da karsashi na isa wajen Mai gari a raba ta da Kabiru, da a yanzu take ganin ya zame mata k’arfen k’afa. ⭐️ kaf Mai gari ya gama jin buk’atun Talatun da irin abubuwan da ya dinga mata na cusguna wa tun aurensu har yanzu, duk da ta yi k’ok’ari sosai wajen b’oye masa wasu abubuwan ba don komai ba sai don gudun zubewar mutuncin y’ay’anta. Tausayinta sosai ya ratsa zuk’atan mazauna wajen, mutane da dama suka yi Allah wadai da hali irin na Kabiru. Take Mai gari ya aika a kira masa Kabiru. Fuskarsa a ‘d’aure sosai ya isa fadar Maigarin, Ya saki guntun tsaki ganin yarda idanun mutanen wajen ya dawo kansa. Aka zayyano masa kaf laifinsa, ransa a b’ace ya dinga girgiza kai yana jifan Talatu da kallon Ni kika tonawa asiri za mu ha’du anjima. Sosai ya raunana idanunsa akan maigarin, Ya yi k’asa da muryarsa cikin murya mai nuna alamar nadama ya ce “Ranka Ya da’de duk abubuwan da ta lissafa haka ne, Amma a yi min afuwa sharrin shaid’an ne, Ni kaina a yanzu na yi nadama na kuma yi Allah wadai da Halina da na kasa rik’e Talatu da kyautatawa duk da matsayinta na rashin gata da maraici, Amma In sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba, ina neman afuwar Talatu da duk jama’ar gari gaba ‘d’aya.” Jikin mutanen wajen ya yi sanyi ganin yarda Kabiru ya amsa laifinsa Wanda daga kallo ‘d’aya da zaka masa zaka hango tsananin nadamar sa tamkar dai abin ya kai zuci, sai dai k’ark’ashin zuciyarsa shi ka’dai ya san hukuncin da ya tanadarwa Talatu a daren yau sai ta gane kurenta k’arshenta ma sai ya farka mata mata cinta gaba ‘d’aya don sai ya nuna mata mazantakarsa irin wacce bata tab’a gani ba, ta hakan zai horata. Mai gari ya yi gyaran murya yana Kallon Talatu da takaici yake neman bugar mata da zuciya, sarai ta San Nadamar Kabiru iya cikin idanunsa ne kawai bai kai cikin zuciyarsa ba, Amma ta San tana yin magana mutane da dama za su ga gazawarta a fannin hak’uri, don haka ta ja baki ta tsuke tana ha’diyar wani yawu mai ‘dacin gaske, don dai ta San tabbas ne komawa aurenta gidan Kabiru, tunda ya yaudare Maigari da zantukansa na gaibu. Kamar hasashen ta kuwa ta juyo muryar Maigari a sama yana fa’din “A yi hak’uri Talatu, shi dama zaman aure ya gaji haka, komai sai ka yi hak’uri Alhamdlllah tunda ya gane kuskurensa na San hakan ba zata sake faruwa ba.” Kuka sosai Talatu ta saka murya a sark’e ta ce “Wallahi yallab’ai k’arya yake bai yi nadama ba, kuma ba don Allah zai mayar da aurena ba, zai mayar da ni ne don cikar burinsa haka yace da zarar burinsa ya cika zai sake ni…” Tsam Maigarin Ya yi da ransa yana k’arewa Kabiru kallo so yake ya gano gaskiyar Talatun a cikin k’wayar idanunsa, sai dai Kabirun ya k’i ba shi damar haka ta hanyar kawar da kansa yana fa’din “Allah ne shaidata, da zuciya ‘d’aya zan mayar da Talatu gida na.” Maigari ya saki ajiyar zuciya a ransa ya ce idan ka San wata ai baka san wata ba “Kabiru ka ka’ddara aurenku da Talatu Mutu ka raba ne Takalmin kaza, duk randa ka saketa zaka gamu da fushin jama’ar gari gaba ‘d’aya, sannan dole ne ka dinga sauke Duk wani nauyinta da yake kanta.” Kabiru yana murmushi ya ‘daga kai “In sha Allah Yallab’ai ba za’a samu kuskure ba, a dai rarrasar min ita komai ya wuce.” Mai gadi ya sake bawa Talatu hak’uri sannan ya ce “Ku mik’e ku tafi, Allah ya Miki albarka Talatu duk kuma abinda ya Miki kizo ki sameni ki gaya min.” D’aga kai kawai ta yi tana kokawa da numfashin da yake son sark’e mata hawaye mala mala ta bar wajen Maigari. Tun a hanya Kabirun Ya fara y’ar wak’arsa da alama komai ya tafi yarda yake so. Suna shiga cikin gida ya zuba mata masifaffun Idanunsa “Ni kika kai k’ara ko Talatu? Da yake ke matsiyaciya Har da zama ki bada labari kaf rashin arzikin da nake miki, ai kuwa kin yi da ‘d’an halak yau zaki gane banbancin Kabirun da da na yanzu, ba duka ba zagi Amma abinda zan Miki sai kin gwammaci duka da zagin bar ganin kina da tsohon ciki ba abinda Ya dameni sukuwata ka’dai yau ta isheshi ba mamaki ma ta marka’de a cikin don na San dai macen dai za ki sake haifa, ina baki shawara ki killace Yaranki cikin dare kafin su fara zatan wani abin cutarwa nake Miki musamman wannan yaron ya Jabiru, ko da yake ai shima ya balaga sarai ya san abinda muke,,, Yau za ki karb’i amarci Talatu Allah yasa dai kin tsuke, ko da yake ko baki tsuke ba yau daidai nake da ke.” Ya fa’da yana shek’a dariya “Yau Talatu zaki ji maza, baki san komai ba yau zaki san ainahin muguntar Kabiru a wancan Fannin, sai kin gwammaci baki kai k’arata ba wallahi, idan yaso gobe ma ki je ki kai k’arata in ji ko yana da damar da zai hana ni kusantarki a duk sigar da Naga dama…” Zuwa lokacin tuni zuciyar Talatu ta shiga lugude, da gaske kalaman Kabiru Sun gigita ta, ta dinga jin kamar ta durk’ushe a wajen ta ba shi hak’uri kafin afukuwar komai ba, duk wani karsashinta da jarumtarta suka zagwanye, ya suka k’are a daren farko ma da take da yarintarta balle yanzu da Take da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe.. hawaye ya fara bin k’uncinta tana tunanin shikkenan yau ba mamaki Kabiru sai ya sadata da kushewarta, gaba ‘d’aya jikinta ya jik’e Jagab da gumi, ta dinga jin dama ta haihu tun kafin Kabirun Ya mayar da aurenta da ko za’a tsireta ba zata komawa auren ba, amma ina? K’addara ta riga fata kuma kowane bawa tafe yake da k’addararsa ta ta bak’ar k’addarar shine Auren Kabiru da ya zame mata bak’in kumurci… Ta ina zata iya ‘daukar lalurar Harijancin Kabiru da wannna trutsetsen cikin nata, ta tabbata da ya ce turmushe shi bakomai bane zai iya aikata fiye da haka, ta dinga addu’a Allah ya kawo mata haihuwa a yanzu ko zai yi dalilin da zai saka Kabiru ba zai mata kusantar mugunta a wannan daren ba. Tana kallo ya fita ya dawo da wasu k’ullin magani a hannunsa ya ‘Debo ruwa a kwanan sha ya k’arasa wajenta yana mata kallon k’asa-k’asa. “Maganin k’arin k’arfin maza ne, ban tab’a sha ba saboda ni kaina na yarda da baiwar da Allah ya ba ni da ana ragewa ma rageta zan yi…. Ya saki Dariya sosai kafin ya cigaba da furta “Amma yau zan sha, zan sha kawai don in yi Miki muguntar da za ki ji a jikin ki Talatu ba mamaki sai na ha’de gabanki da bayanki Sun zama rami ‘daya saboda gurzar da zan Miki….. Hahhhha Maza bisa kan ki Talatu….” Rintse idanunta ta yi tana kiran sunan Allah….. (Kabiru? Anya kuwa zaka ga annabi? 🤦🏿‍♀️😭) Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe. 22 💔💔💔💔💔 Tana kiran sunan Allah tana cije lab’b’anta saboda tsabar razana da Jin Kalaman Kabiru, hankalinta a tashe ta dinga Jin kamar ta rok’eshi ya yi hak’uri kada ya ce zai mata kusantar da zata jawo mata illa, Amma wata zuciyar ta dinga ankarar da ita a kan kada ta rok’eshi, ta Kai kukanta wajen mai duka shi ka’dai ya san yarda zai yi da muguntar Kabiru, idan ya fi k’arfinta ai bai fi k’arfin Allah ba. Don haka ta ‘dauke hawayen idanunta wani irin sukuni ta ji a zuciyarta ta samu k’arfin gwiwa sosai, ta dinga jin duk wata shakka da tsoronsa suna zagwanyewa Suna bin iska sosai ta samu karsashi da k’warin gwiwar fuskantar duk wani k’alubalensa na yau da Wanda zai zo nan gaba ma ta shirya masa. Idanunta da suka yi jajur ta watsa a kansa daidai lokacin da yake sake sakin dariya bayan ya sake hambu’dar magungunansa yana fa’din saura na dare ma in da zan ji da’din keta mace son raina.” Talatu ta ‘dauke kanta ha’de da surar buta ta shige Bayan gida. Alwala ta yi cikakkiya ta fuskanci alk’ibla don kaiwa Allah kukanta, ta da’de sosai tana addu’ointa kafin barci ya ‘dauketa a wajen da ta yi Sallahr. Ana Sallahr Isha’i Kabiru Ya shigo gidan kamar an hanka’do shi cikin tashin hankali, don sosai maganin ya fara masa aiki kaf jijiyoyin jikinsa sun mik’e car agaji kawai suke nema, bai tab’a riskar kansa a masifaffiyar sha’awa irin ta yau ba. Ya dinga jin kamar zai Mutu idan har bai samu ya kusanci Talatu ba ya keta duk wani sauran mutuncinta. Da k’yar yake ‘daga k’afarsa yana aikin k’are jikinsa da hannu, don kada yara su ga halin da yake ciki.Talatu jin muryarsa ya sata saurin ‘dagowa gabanta yana fa’duwa “Kallo na za ki tsaya yi? Ba za ki kawar da yaran nan ba, na fa gaya Miki yau sam ba nutsuwar da zan iya killace muryata don kada wa’dannan banzan yaran naki su ji, ki yi maza ki shigo don a matse nake ko komai ma ya wakana a gabansu, ni ba abinda ya dameni tunda ba haramci nake aikatawa ba.” Da sauri Talatu ta dubi Jabiru da duk Ya gama fahimtar zantukan Kabiru gani ta yi kawai ya runtse ido kafin Ya kalli su Majeedah ya ce “Ta shi Mu je can ‘dakin mu k’arasa karatun..” Kabirun ya watsa masa wani kallo “Ya fiye maka, kafin kunnuwanka su jiye maka abinda kwanyarka ba zata iya ‘dauka ba, duk da kai ma ka balaga ai.” Jabiru ya watsa masa banzan kallo, Sai dai Kabirun bai bi ta tasa ba jin yarda gaba ‘d’aya jikinsa ya ‘d’aure agaji kawai yake nema ya afka ‘dakin yana fa’din “Maza maza Talatu yi sauri don Allah kafin na Mutu..” Da sunan Allah ta mik’e a bakinta sai dai me? Tana mik’ewa ta ji wani ruwa mai yawan gaske ya biyo cinyoyinta ga azabar ciwo da ya turnik’eta lokaci guda, ta durk’ushe a wajen tana kiran sunan Allah don ta tabbatar haihuwa ce ta zo mata, ba zato ba tsammani duk da a watan haihuwar take. Jin Shiru Kabiru ya k’unduma wani uban ashar ya fito da sauri daga shi sai gajeran wando yana mita “Wani irin iskanci ne wannan Talatu? So ki ke na Mutu ko?” Daidai lokacin Talatu ta saki wani nishi sai ga Deejah ta fa’do duniya, da kara’dinta na kukan jarirai mai sautin Inyaaaaa’ da alama da k’arfinta ta dira da lafiyar ta. A tsorace Kabiru ya ware ido cikin rawar baki ya ce “Kan Uba? Talatu ba dai haihuwa ki ka yi ba? Da kin cuceni ina zan kai wannan jarabar da take ci na yau?” Ya fa’da kamar ya saka kuka ga mararsa ta sake k’arfi ta ‘d’aure gaba ‘daya. Talatu ba ta bi ta kansa ba, ta k’walawa Majeedah kira. Yarinyar na zuwa ta saki baki da muryarta ta ce “La Yaya Jabiru Umma ya haihu fito ka ga.” Da sauri Talatu ta ce “Me ye haka? Jabiru yi zamanka kada ka fito, ke kuma Majeeda maza ki ‘dauko min y’ar jakar nan da nace miki y’an kayan haihuwa ne na tana da zan ‘dau rezar yanke Cibiya.” Majeeda ta juya ta koma ‘dakin da suke don ‘dauko ledar, Kabiru da yake tsaye sai matsa k’afa yake cikin wani azabar yanayi ya fa’da cikin ‘d’aki yana neman mafita, ga gari ba karuwai ba balle ya je ya kai buk’atarsa can. Ya dinga gurza jikinsa cikin tashin hankali Amma madadin abu ya lafa, Sai ma k’ara ta’azzara yake, gani yake a yarda yake jin kansa Mace ‘d’aya ma ta masa ka’dan da kuma zai iya jan mota da sauk’i sai ya yi sauri ya koma Kano wajen mai zak’in sa, tunda bata San nan ya taho ba, bata San ma ya mayar da auren Talatu ba. Shi ka’dai ya dinga wasu irin abubuwa a ‘daki Talatu na jiyo shi daga tsakargida tana sakin dariya k’asa-k’asa, shi yasa aka ce idan zaka hak’a Ramin mugunta ka Gina shi daidai kanka. Ga Kabiru dai ya jefa kansa cikin wahala ji yake kamar zai rasa ransa saboda masifaffiyar sha’awar da ta sako shi gaba, ga Talatu Allah ya tsallakar da ita daga muguntarsa. Kabiru Har haki yake ja da sunan Allah yana fa’din “Na cuci kaina da kaina ni Kabiru? Talatu Allah ya so ki da rahmar sa ni kuma na jefa kaina a wahala wayyo Allah yau ina zan kai Jarabata..” Wannan Talatu da Allah ya ba sauk’i ta gyara jikinta da y’arta tas sai da ta tuntsire da dariya son ranta, tana duban y’arta fara sol da ita mai kama da ita kwabo da kwabo Sam bata ji bak’in ciki da haihuwarta ba, bata kuma saka ranta a son haihuwar ‘da namiji ba duk Wanda Allah ya bata tana murna tana kuma farin ciki da ‘doki. Ta koma ‘dakin da yaranta ta mik’awa Jabiru y’ar tana murmushi “Ga y’a ka kuma samu Jabiru..” Da hanzari Ya amsheta yana murmushi ya kalli su Majeedah Ya ce “Kai duk ta fiku kyau wannan daga ganin bakinta zata yi tsiwa ta gaske.” Majeedah ta turo baki alamar fushi Zainab kuwa amsar y’ar ta yi tana fa’din “Eeh, bakomai don ta fi ni kyau ai k’anwata ce.” Jabiru ya mik’e y’an ragowar ku’dinsa da suke jikinsa ya je ya samo mata balangu mai zafi ya kawo mata. Ta karb’a tana saka masa albarka tana jin so da k’aunar Jabiru kafin k’aninta mai binta da suke uwa ‘d’aya uba ‘daya, hak’ika Jabiru wani jigo ne a rayuwarsu ita da yaranta, don sun fi masa kallon mahaifi fiye da Kabiru da bai San komai ba sai dai ya yi cikinsu a haife masa. Sai dare sosai ta ‘dauke y’arta ta shiga ‘dakin da Kabirun yake, Har lokacin bai yi barci ba, ya yi zigidir cikin wani irin mawuyacin hali na masifa abubuwa kala-kala yake yi marasa da’din kallo sai dai Har a lokacin bai samu sauk’i ba, saboda bai fitar da tarin abin da ya cunkushe masa a gaba ba. Talatu ta tab’e baki ha’de da yiwa y’arta da ita kanta shimfi’da daga can gefe, a zuciyarta tana fa’din Allah ya k’ara ninka maka azabar da kake ciki, ni ka so ka cuta sai ga shi cutarka ta ka’re a kanka. Har Uku na dare Kabiru ya kasa barci, ji yake kamar ya fita ya haura katangar wani gidan ya samu wata Ya mata fya’de amma ba hali, don yana fita ana dubansa za’a gane halin da yake ciki yarda komai na jikinsa yake mik’e a tsaye ba ta yarda zai iya b’oye hakan. Rashin samun madafa kawai sai ya tunkari Talatu dole ne Ya sauke mata duk abinda yake ji idan ba so yake ya Mutu ba ta rok’i Allah gafara daga baya. Cikin barci ta ji mutum ya birkitota, da sauri kuma a razane ta Ware ido tana kallonsa cikin mamaki ta ce “Kabiru haihuwa fa na yi?” Ya saki tsaki yana shirin danneta ya ce “Eeh na sani, a hakan zan kusanceki idan ba so ki ke na Mutu ba.” “Ta ya zaka kusanceni alhali bana cikin tsarki?” “Ki min shiru Talatu bana son magana zan rok’i Allah istigfari idan komai ya lafa.” Salati ta saka salati “Yanzu Kabiru ko da ace da kyau kashe ni zaka yi? Da zaka kusanceni ranar da na haihu gurin ko dakushewa bai yi ba ciwo ne fa a wajen..” “Ki min shiru Talatu idan kika k’i yarda wallahi cikin yaran can zan ‘dau wata ba sauke mata buk’atata idan ya so in gudu na bar garin kin ga ko bakomai na bar ki da abin kunya……” (Kai wannan takaici ba zai bar ni cigaba da rubutu ba mu tara gobe tabbas Kabiru baya cikin hankalinsa kamar Wanda ya sha k’waya?🤔🤦🏿‍♀️ Takaicin Uba…. Nazeefah Nashe. 23. 💔💔💔💔 Jikinsa har rawa yake wajen son ganin ya cika burinsa ta ma kowane hali. Cikin tashin hankali Talatu take rok’onsa tana k’ok’arin samawa kanta mafita tun kafin ya jefata a halaka ko ya sauke duk wata buk’atar sa Akan Majeedah da tafi shekara takwas ba. Ganin yana Neman cimma burinsa yasa ta hanka’dashi cikin wani k’arfi da rabbi ya k’imsa mata, ta mik’e a sukwane ha’de da ‘dauke y’ar jaririyar ta, yau kam idan ba’a yi da gaske ba zata iya zama ajalin Kabiru a gidan idan shi bai yi sanadin zuwanta lahira ba. Da sauri ya mik’e a niyyarsa na ya kamota ya haik’e mata wala ta gaba ko ta baya, ganin haka yasa ta yi saurin wawurar dogon sandan da yake yashe a k’asa “Wallahi ko ka saurara min Kabiru ko na yi ajalinka a daren nan.” Kabiru ya cizi baki cikin azabar yanayi ya ce “Ni kuma na gaya Miki ko ki tsaya ko na sauke duk wata buk’ata ta kan waccan y’ar taki.” “Ashe kuwa yau zaka isa lahira don tsaf zan ha’da maka taron jama’ar garin nan na sanar da su abinda ka aikata na tabbata jefeka za su yi.” Ganin yana gyara tazuge a niyyarsa ta ya fice ya kinkimo Majeedah ya sa ta daddage ta sake hanka’dashi ta gaba ya fa’da k’asa a ruf da ciki da k’arfi ya ce “Wayyo Talatu kin kashe ni, Talatu kin fasa min aba….” Talatu ta saka Kai a guje ta bar ‘dakin, wajen yaranta ta nufa Jabiru yana kwance daga gefe can a tsakar gidan inda yake kwana in dai Kabirun yana gidan ya barwa su Majeeda ‘dakinsa da sauri ya mik’e don kusan za’a iya cewa yana Jin abubuwan da suke wakana “Yaya Talatu ba abinda ya Miki ko?” Talatu ta shige ‘dakin tana fa’din “Jabiru Majeeda so yake sai ya lalata min Majeeda saboda jarabar da take cin sa, ka taimakeni Jabiru.” Cak Jabiru ya tsaya Kwanyarsa ma ta daina aiki, illa zallar hucin b’acin ran da yake fitarwa ya runtse idanunsa yana Jin tabbas lokaci yazo da zai nakasta Kabiru tabbas da alamu yana son ya rasa k’afafunsa ko hannayensa ko ma kacokam ya rasa Kayan jarabartasa a Daren nan. Ya tsaya tsaye kamar Soja a k’ofar ‘d’akin yana jiran ya ga ta inda Kabiru zai zo ‘dakin ‘daukan Majeeda ya ga nasa haukan da bai tab’a gani ba. Lokacin shi Kabiru yana ‘d’aki ma, cikin azabar ciwo ga shi madadin fa’duwar tasa da ya yi hakan ya yi silar samun sauk’insa sai Abu ya gagara zufa ce take yanko masa ko ta ina, haka Kabiru ya ga daren nan a idanunsa ba tare da ya runtsa ba, ya ci munanan alwashi a kan Talatu da zarar ya warke, banda ma itace arzikinsa da wallahi saki uku zai mata a Daren nan ya kuma sallameta da ita da yaranta wannan karan ko gidan zama ba zai ba su ba, don kafin ya bar garin sai ya siyar da gidan ko ya bada shi kyauta. _____________ A can birni kuwa wajen Karima mai zak’in Kabiru, hankalinta a tashe yake rashin ganin Kabirun ya dawo bata San dalili ba shi yasa ta nemi Hadi amininsa ta gaya masa rashin dawowar Kabirun. Hadi shima ya shiga ru’dani don bai San Kabirun ya mayar da auren Talatun ba don haka suka shiga juyayi har daga k’arshe Kariman ta bada shawarar Hadin ya tafi k’auye ya ga ko Kabirun can ya tafi wani abin ya rutsa da shi. Hadi ya amince da shawararta don haka ana idar da Assalatu ya sab’i hanya tunda abune ba na waya ba babu hanyar sadarwa a gari idan ma akwai a cikin birni babu a k’auyen Gaya ma balle Shagogo. Yana isa garin gidan Kabiru ya tafi Kansa tsaye don ta nan ‘din ya kamata ya fara bincikensa. Gidan tsit ya dinga zabga sallama daga waje, Talatu ce ka’dai a ‘d’aki tana gyara y’arta yara da Jabiru duk Sun tafi makaranta, sai Kabiru da yake ‘daya ‘dakin yana nemawa ka sa mafita idanunsa Sun ka’da Sun yi jajur kamar gauta. Haihuwar da Talatu ta yi kawai yake tsinewa don ita ta jaza Haka da tuni ya turmushi Talatun son ransa. Talatu ta sab’a jaririyarta a baya ta isa bakin katangar da ta raba gidan da waje. Ta amsa sallamar don ta gane muryar Hadi ce ras a bakin gidan. Yana dashe baki ya shigo idanunsa a kan jaririyar Talatun ya ce “A’a A’a ahe haihuwa kika yi ba labari? Ki ce shi yasa mutumin ya lalab’o nan, Kabiru na Talatu alherin Allah, me aka samu? Ko kuwa an kuma ne mace ta haifi mace?” Talatu cikin takaici ta harareshi ta ce “Eeh an kuma mace ta haifi mace har abada haka nake son na yi ta haihuwar yara mata Sun fiye mazan musamman idan mazan gayyar tsiya zan Haifa irin ku Kai da abokin ka.” Turus Hadi ya yi yana kallonta musamman ganin yarda ta bursine idanunta da toka lallai Talatu ta cika ta tumbatsa. “Allah ya baki hak’uri Kabirun yana ciki ne?” Ta nuna masa ‘dakin da yake da ‘dan yatsa sannan ta shigewarta ‘daya ‘dakin tana dariyar yarda Kabirun yake zuba nishi a ‘d’aki. Hadi yana shiga ‘dakin a yanayin da ya gan shi ya yi saurin juyowa yana fa’din “Ashsha lamari bai yi da’di ba, Me ya sameka haka Kabiru? Ko sutura babu a jikin ka?” Wani da’di Kabiru ya ji yana Jin kamar cutar sa ta warke duk da Hadin bai iya mota ba Amma ya San yarda zai yi ya masa maganin abin ko karuwa ya je can gidan magajiyar karuwai ya samo masa tunda dai shi ba zai iya fita haka ba sai a masa dariya. Ya ja mayafi ya rufe jikinsa da k’yar “Shigo Hadi shigo don Allah ko zaka fitar da ni a wannan masifar ban sani ba ko ajalina ne yazo.” Hadi ya shiga yana cewa “Wai me ya faru ne? Na ga al’amarin haka ba kyan gani?” Kabiru murya a dusashe Saboda wahala ya fara ba shi labari. Hadi ya guntse dariyarsa da k’yar ya ce “Yanzu Bari a gwada maka magani tukun na, kafin mataki na gaba idan maganin bai yi ba.” “Hadi ba wani magani da nake buk’ata mace kawai itace magani na wacce zan saukewa duk jarabata. Don Allah ka tabbata ka samo min mai juriya wacce zata shanye lalurata ni kuma zan naka ko nawa ne wallahi.” Hadi yana Jin ku’di ya mik’e yana fa’din yanzu zaka ga aiki da cikawa. Ba tare da shakkar komai ba Hadi ya kawo karuwar gidan, wacce kana ganinta ka ga tantiriyar iblishiya sai tauna cingam take tana kallon Talatu da take zaune sama da k’asa, Hadi ma Talatun ya kalla da Take kallonsu cike da mamakin k’arfin hali irin nasu, Hadi yana dariya ya ce “Mai gida ne yace a kawota ta kwashe masa lalurarsa tunda ke ba hali.” Talatu cike da takaici da bak’in ciki ta tab’e baki ta ce “Allah raka taki gona.” Ta shige Cikin ‘d’aki tana Jin wani irin zafi da tuk’uk’in bak’in ciki. Sai dai ita hakan ya fiye mata a kan ya b’ata mata rayuwar y’arta da take ji da su. Tana ji suka dinga shagulgulansu a ‘daki, b’acin ranta ‘daya yarda suke abinsu a kan shimfi’darta, ba Wanda zata gayawa sai rabbil izzati don yanzu lamarin Kabiru tsoro yake bata. A ranar dai tabbas karuwar nan ta San ta shigo hannun maza don ta galabaita iya galabaita har sai da ta gwammaci ki’da da karatu Talatu kuwa dariya kawai take zuba mata ganin yarda take tafiya kamar y’ar kaciya. _________ Bayan wasu shekaru, kamar almara arzikin Kabiru ya dinga hab’aka y’a zama matashin mai ku’di na gasken gaske, don haka ya dinga wata fankama yana taka duk uban da ya so a shagogo. A lokacin ya sake Gini a b’ari guda a gidan Talatu Gini ne yake na bulo da bulo har Talatu da yaranta suna murna za su koma sabon waje. Musamman ganin yarda na Sun ya kwarab’e. Sai dai burinsu bai cika ba saboda rana guda aka shigo da gu’da, Talatu tana tsohon b’angarenta sai ji ta yi ana Ku matsa ga Amaryar Kabiru shalele danda’deshiya y’ar mai arzikin Gaya..” cak Talatu ta yi da tsintsiya a hannunta ta zubawa yaranta ido da suma suka zuba mata na su idon musamman Majeeda da Zainab da lokacin sun ma fara wayo. Idanun Majeedah yana ruwa ta ce “Umma, Aure ya yi ko?” Talatu ta runtse idanunta tana tunanin yaushe rabon da ta ga Kabirun an doshi watanni bakwai idan ya zo kuma gurin ginin sa kawai yake zuwa ba ya bi ta kanta tunda wancan Lamarin ya afku ya tattarata ya watsar ga Deeja tana shirin shiga shekara biyu. Gurin da yaranta suke murna za su koma shine zai ‘dau amarya ya saka? Kawai sai ta ji tana hawaye idanu bibbiyu karon farko da ta kasa b’oyewa yara damuwar ta….. Takaicin Uba… Nazeefah Nashe 24 💔💔💔💔 *SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?* *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*. *NA GWADA NA GA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*. *ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.* *AKWAI FULL, AKWAI RABI TA, YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*. *SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.* *DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*. *TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU* *08032773332* *DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.. __________ Ta zube idanunta cikin na Jabiru da yake tsaye yana tsumayin amsarta, kamar yarda su Majeedah suka yi jigum suna son jin furucinta, bata da ikon da zata b’oye musu gaskiyar lamari bayan abinda idanunsu suka gano musu, don haka murya a sark’e ta ‘daga musu kai “Aure ya yi, ku musu fatan alheri..” Daga ta janye idanunta daga kansu ta runtse su tamau, tana sauraran bugun zuciyarta, da yake bugawa da k’arfin gaske. “Allah ya tsinewa auren, ba zan musu addu’a ba Umma.” Zainab ta fa’da idanunta na waiwayi cikin fuskar mahaifiyarsu da take hango tsagwaron b’acin rai. Murya a sanyaye Talatu ta ce “Kul Zainab kada na sake ji Allah ne Ya ba shi damar ya auri mace sama da ‘daya..” “Idan zai iya adalci ba.” Jabiru ya katseta da nasa b’acin rai “Ki hak’ura da auren mutumin nan, da ba don komai yake cigaba da zama da ke ba, sai don wata manufa tasa ta banza, da kunnena na ji yana gayawa Hadi ke ‘din ke ce k’ashin arzikinsa shi yasa ba zai rabu da ke ba, Har sai ya samu dukiya mai tarin yawa sanadiyyar aurenki, don haka Yaya Talatu wannan karan ki fito masa a mutum ki rabu da aurensa kafin ciwo ya bugar miki da zuciya ki cuci rayuwar Auren ki.” Da k’yar ta bu’de ido tana kallon Jabiru da idanunsa suka ka’da suka yi jajur ji take ina ma zata samu Kabiru ya sawwak’e mata wannan wahalallen auren da ta yi murna. Ta ja huci ta fesar da numfashin da ta tokare mata mak’oshi “Na fika son hakan ta faru Jabiru, a yanzu na fi k’aunar mutuwa ta da zaman aure da Kabiru.” Jabiru ma hucin Ya saki kafin ya ce “Ki bani dama, wannan karan ko ba ya so sai ya sake ki, yana daga cikin dalilin da yasa na k’i amsar scholarship na tafi malaysia saboda bana son na tafi na barku a wahala..” “Na sani Jabiru, ina rok’on Ubangiji Ya maka mafiyin abinda ka min ni da yara na, a yanzu na fi buk’atar ka tafi karatun ko bakomai ba ma zama masu haihuwar guzuma ba, Y’a kwance uwa kwance ka je ka yi karatunka kawai tunda Allah ya baka kwanyar yi.” Jabiru ya girgiza kansa “Ba zan iya ba Yaya Talatu, Har sai na kawar da wannan mutumin daga rayuwarku na kuma sama Miki gwagwgwab’ar sana’a.” Daga haka ya saka kai ya fice da sauri don hayaniyar y’an kawo amaryar ma sake bak’anta masa zuciya suke. Haka y’an kai amarya suka shige suka fice, Babu Wanda Ya bi ta kan Talatu balle a bata hak’kinta na uwargida a kai amaryar wajenta su gaisa, To ta ina za su girmamata? Bayan mijinta ya k’ask’antata duk Wanda Ya shigo gidan ma zata zai yi Talatun y’ar aiki ce ba matar gida ba. Yarda Ya dank’arawa amarya gini na bulo da sumunti ga fenti da babu mai irinsa a garin sai gidan ‘dan mai gari marigayi babansu Hameedah. Haka gidan ya ‘da’de tsit sai saurarar shigowar ango da tawagarsa. Da kirari aka rako shi gidan, Ya zubawa Talatu da yaranta harara ganin yarda suke zaune abin su suna cin tuwo miyar kuka, ya saki tsaki ganin yarda abokan nasa suke kallon Talatun da yaranta da kuma bak’in tuwon da suke ci.. shi Talatu zata tonawa asiri? Ai Kuwa zai yi maganinta. Da yake abokan y’an a bi Yarima a Sha ki’da ne, su ma halinsu ‘daya ba Wanda ya damu da cimar su Talatun balle sutturun da suke jikinsu Wanda tazararsu da almajirai ka’dan ne duk da wadata irin ta Kabirun. Yana dashe baki ya burma kai cikin ‘dakin amaryar abokansa suka raka sa Har cikin ‘dakin suna zolayarsa da Alaji ka yi babban kamu fa! Ya sosa k’eya yana fa’din “Kaya iya kaya ba, mhmn harkar ai ta manyan mata ce gaba bum bum baya tum tum.” Suka saka shewa gaba ‘d’aya kaf a kunnen Talatu, ta ‘dan mele baki jira take abokan su tafi a yi wacce za’a yi tsakaninta da Kabiru da duk wani rashin mutuncinsa, saki kam kamar Ya saketa ya gama a daren yau. Cikin daren ta dinga tsimayin fitowarsa daga ‘daki, saboda bata son ta je b’angaren amaryar inda za’a ga laifinta. Suna shirin kwanciya Allah ya taimaketa ta ji ya fito daga ‘dakin da sauri ta zame Dijah da take jikinta ta fita, Yana shirin saka kai a zaure ta cimmasa cikin dakakkiyar murya ta ce “Ina da magana Kabiru.” Mamaki k’arara a fuskarsa na ambatar sunansa kai tsaye da ta yi gatsal ba risunawa bakomai ya juyo yana dallareta da torch light ‘din da yake haske engine generator da ita “Lallai Talatu wuyanki ya isa yanka, ko ba sunana na ji kin ambata ba, gatsal ba alamar rusinawa.” Madadin ta shiga firgici da ganin b’acin ransa kamar yarda ta Saba a lokutan baya wani k’warin gwiwa ne ya sameta ta sake dallareshi da idanunta kafin ta ce “Ina zaton dai ainahin sunanka kenan Kabiru ba wani na canja maka ba.” Wannan karan fitilar sai da ta kusa zamewa daga hannunsa don al’ajabi. Bai farka daga wancan mafarkin ba ta sake kashe shi da wani. “Magana ta ba ta arziki bace, shi yasa babu dalilin sakaya sunanka, Sakina nake son ka yi kuma a yanzu ba sai anjima ba.” Kabiru ya saki dariya ha’de da fa’din idan na k’i fa? Zan ji duka ne? Rasa kunya.” “Dole ma za ka yi Kabiru, don kuwa na gama zama da kai, don babu amfani a cikin zaman aurenka gwara na yi zaman kaina na San zaman kaina nake, me auren naka yake tsinana min me kake ba ni da zan mararin son zaman gidanka, banda bak’ar izaya da cin mutunci, to komai Ya zo k’arshe na kai iya matsaya saki nake buk’ata.” “Ai kuwa ba za ki same shi ba, tunda har ke ki ke son sakin, ban gama buk’atar aurenki ba, idan lokaci ya yi ba sai kin buk’ata ba zan sake ki, Amma Wallahi yanzu babu mai saka ni na sake ki. Kaf garin Kano ba ma nan k’auyen Gaya ba.” Daga haka ya tada engine zuciyarsa tana jin b’acin ran titsiyen da Talatu ta yi masa, ai kuwa zai shayar da ita mamaki. Jabiru da kaf yake jin su daga ‘d’akin da yake kwance ya yi k’wafa kafin ya mik’e ya fito a zafafe kamar an Jeho shi, daga sama Kabirun ya ji Jabirun yana cewa “Kawai tunda dai yanzu sakin take so, ai sai ka saketa fisabilillah cuta iya cuta ai ka yi mata, wace izayar kuma kake son mata bayan wannan da take ciki…” Cak Kabirun ya yi yana dallare Jabirun da yake masa magana da tsananin mamaki ya ce “Au ko zuwa ka yi ka saka ni dole na saketa? Na ga alama akwai wani sirri a tsakaninku da ku ke b’oyewa, to ba zan saketa ba har sai na cimma manufata ta aurenta idan ya so idan na saketa sai ka ji da’din Maye gurbina don da alama kai ‘din dadironta ne yarda kake hak’ilo a kanta ba banza ba…” cak Jabiru da Talatun suka yi cikin tashin hankalin jin maganarsa Jabiru a zabure ya ce “Wal’iyazubillahi, an gaya maka kowa ma macece a gabansa kamar yarda kai ka saka lamarin mata a gabanka. Kai ne ba zaka iya rayuwa sai da mace ba, Amma ni ko na rasa matar aure ba zan auri Yaya Talatun da nake mata kallon uwa ba. Kai dai da ka Saba bin matanka ka ji da kanka kada ka sake sakawa da ni. Kuma saki dole ka saketa tunda bata son Auren.” Kabiru ya ciji leb’e ba tare da ya yi magana ba, kawai ya tada engine ya yi gaba amma ya yi alk’awarin maganin Jabiru ko mu da’de ko mu jima sai ya cusawa Jabirun irin bak’in cikin kalamansa da ya cusa masa. Jabiru ya bi shi da harara kafin Ya kalli Talatun da jikinta duk ya Mutu saboda takaicin Kabiru. Bil hak’ki maganar tasa ta girgizata. “Ki share hawayenki Yaya, kada wannan ya ‘daga Miki hankali Amma dai gobe ki je wajen mai gari ki rok’eshi yasa Kabiru ya sahhale Miki auensa kafin takaicinsa ya bugar Miki da zuciya.” Hawayen idon nata kasa ‘daukewa suka yi saboda ta firgita da jin kalaman Kabiru ta tabbata shirun da ya yi yana nufin abubuwa da yawa ta kuma San ya iya sharri ko wane iri ne, sai dai fatan Allah ya kiyaye Jabiru daga sharrinsa, da Jabirun ma zai gane ya tattara Ya bar garin kafin Kabirun Ya k’ulla musu k’ullaliyya. Kashegari ba ta yi k’asa a gwiwa ba ta nufi wajen Mai gari ta zayyane masa duk rashin mutuncin da Kabirun yake mata, Babu abinda ya canja tun daga zuwa wajen mai gari shekarun baya Har kawo lokacin da take bawa mai garin labari. Hankalin Mai gari ya tashi matuk’a da gaske ya kuma aika ‘dan aike Ya taho masa da Kabiru ko da a kaine. Kabiru yana jin sak’on Mai garin Ya saki murmushi a ransa Ya ce “Talatu kenan, idan kin san wata ai ba ki San wata ba mu je zuwa.” Ya bi bayan ‘d’an Aiken suka tafi wajen Maigarin. Ran Maigarin a b’ace Ya wankeshi tas ba tare da ya tsaya Ya ji ta bakinsa ba, Kabiru ransa ya b’aci da tijarar da Talatu ta janyo masa a wajen Mai garin, sai dai bai ce komai ba ya bada hak’uri ha’de da yin nadama kamar yarda ya aikata a wancan zaman nasu na farko. An kai ruwa rana kafin mai gari ya yarda ya amshi tayin hak’urinsa sai da ya saka shi Ya bawa Talatu hak’uri ha’de da tabbatar masa dole ne ya ‘d’auke duk wani nauyi na Talatu da yaranta, kuma wajensa zai dinga kawo komai duk k’arshen wata. Kabiru ya amsa ba tare da ja in ja ba. Tun a wajen Mai gari ya ciri ku’din da aka yanka masa ya dank’awa Talatu da yake zuba mata harara ta k’asan ido ba tare da kowa ya sani ba. Talatu ta amshi ku’din tana zubawa Mai gari godiya “Bakomai Talatu, ki je kuma duk abinda ya sake miki ki zo ki gaya min, ni ba azzalumin shugaba bane kuma ba zan yarda wani ya zalunci wani a yankinaba matuk’ar ni ne shugaba a wannan garin.” Kabiru dai hak’uri yake bayarwa kawai “Kuma ka tabbatar itama ka gyara mata mahallinta kamar na waccan matar da ka ajiye, da da wuri ma na samu labari ba zan bari ita matar taka ta tare ba sai dai Talatun ta tare ko baka so. Na gaya maka umarni ne na baka ba shawara ba.” Kabiru dai hak’uri ya sake bayarwa yana k’ok’arin danne fushinsa kada abinda ya b’oye Ya fallasu, Amma shi ka’dai ya san abinda yake zuciyarsa na daga tanadin rashin arzikin da zai yiwa Talatu da ma Jabirun da ya zugata. Ya ci alwashin sai Mai gari ya yi tur da su sai kuma yasa a koresu daga garin gaba ‘d’aya. Abin mamaki ko a fuska bai nunawa Talatu b’acin ransa ba, ya dai raya a zuciyarsa aurensa da Talatun ya zo k’arshe. A lokacin da yake hidimar shirin aikata tuggunsa a lokacin Allah ya k’addara shigar cikin Ayra. Tsawon shekaru biyu cur bai yi kwanciyar aure da Talatun ba, tun bayan wancan lamari da ya faru, kwatsam wani dare ya je ya Sha kalar maganin da ya tab’a sha a kwanaki saboda yana son koyawa yarinyar da ya aura hankali musamman rashin kunyar da take masa a kan yarda yake gallazawa Talatu, Sau tari tana bawa yaran Talatu abubuwa a b’oye su k’wai madara da bread, da suke karyawa da su, wani lokacin Har da ragowar nama, don haka kawai sai Allah ya kintsawa amarya son Talatun da jin tausayin halin da take ciki. Ya sha kamata idan ya ce ta daina sai ta yi masa rashin kunya ta ce ba zata daina ba. Yana gayawa Hadi sai Hadi ya zuga shi da cewa ba mamaki Amaryar ta raina k’ok’arin sa a gado ne shi yasa ba ta masa biyayya, duk da Kabiru ya ji shakkun hakan don ya san raki irin na Suwaiba sau tari guduwa take ta bar shi idan ta ji wahala, sai ya kasa k’aryata Hadin, Hadin ya kawo masa maganin maza mai k’arfin gaske. Cikin Dare Amarya da taga tashin hankali kwatankwacin Wanda Talatu ta gani a wancan daren, sai ta bawa wandonta iska ta fice a guje sai gidan iyayenta don ta lura sosai Kabiru ya fi k’arfinta ba zata iya da shi ba. Hankalin Kabiru a tashe ya zura jallabiya ya isa ‘dakin Talatun, cikin barci Talatu ta ji yana jan hannunta yana fa’din “Ke Talatu tashi ki bani hak’kina.” Talatu ta Ware idonta jin zancen banbarakwai “Ki tashi Malama, idan kuma kin k’i wallahi sakin ki zan yi, kuma ba za ki tafi min da yaro ko ‘d’aya ba.” Tilas Talatu ta bi shi ‘dakin amarya in da ta ga ya nufa, a tsorace take kallonsa “Ina matar gidan?” “Ba wannan na tambayekiba gyara kawai Malama.” Shikkenan ya afka mata. Sai da komai ya nutsa, Ya yi tsaki yana zuba mata ido. “Ke wai Talatu ba za ki je ki nemi maganin da zai mayar da ke mace ba ko? Kina zaune mace ba ‘dan’dano ba komai abu kamar k’ofar gari, wallahi dole ma na rabu da ke don ba zai yiwu na dinga ciyar da ke a banza ba, dole ma na San hanyar da zan bi na rabu da ke ba tare da kowa ya ga laifina ba.” Talatu ta saki nurmushin takaici kafin ta ce “Ka ba ni ku’din ka ga ban je bane?” Ya saki tsaki yana fa’din “Tashi don Allah ki tafi wajen yaranki, ai ke kin tashi daga aiki ba wani garanbawul da za ki yiwa kanki.” An kai ruwa rana kafin amarya ta dawo, da zummar a ja masa komai ya daina shan abubuwan da za su k’ara masa k’arfi don ba zata jura ba. Kabiru murmushi kawai ya yi don itama tabbas rabuwa zai yi da ita Karima ce mai iya ‘d’aukan lalurarsa to itama ta ‘d’an fara sanyi dalilin ciwon bayan da sakota a gaba. Wata ‘daya da faruwar wannan abin abubuwan marasa da’di suka faru, domin dai kamar yarda Kabirun ya ci alwashin ramuwar gayya hakan ce ta wakana da taimakon Hadi da ya sake ba shi gurguwar shawara “Wallahi hakan kawai za ka yi ka rabu da ita salin alin, kuma Har yaran ka ce baka so, tunda ba ka tabbatar da zamantowarsu naka ba.” Kabiru ya ji da’din ba shi k’warin gwiwa da Hadi ya yi don da gaske yana jin haushin ciyar da Talatun da yaranta da yake yi. Don haka suka shirya mai fishshesu. Ranar da abin ya faru sai da ya daidaici amarya ta tafi gidansu kwana sannan ya fakaici idon Jabiru da Ya dawo daga wajen abokansa zaman hira ya shigo da ‘y’ar wak’arsa a bakinsa kawai sai Kabiru da Hadin suka shak’eshi a zauren gidan suka saka masa yanki a hanci take ya sandare musu, Hadi ne ha rik’eshi shi kuma Kabiru ya je ya shak’awa Talatu a fuska dama barci take sai ta cigaba da nauyayyan barcinta, ya Zare yaranta Ya mayar da su ‘dakin da Jabiru yake kwana ita kuma ya zare mata Riga suka zo suka ‘dora Hadin a jikinta bayan Sun cire masa tasa rigar daga haka suka fice suna dariyar cimma burinsu Kabiru ya tafa da Hadin ha’de da cewa Shikkenan na huta da k’aya haba ka yi ta wahala da mace a iska sai a bi wani yariman a sha ki’da… Waje suka fita suna ihu ha’de da kiran mak’ota “Ku zo ku zama shaida Innalillahi kwarto a gidana a kan shimfi’dar mata ta suna nan haihuwar turmi da tab’arya……..” Kabiru ya fa’da a wata majalisa da ba su tashi ba, cikin kuka da gigitar tashin hankali kamar gaske……… (CAB, Kai Kabiru ta nan kuma ka b’ullo tashin hankali dole yaranka su k’i yafe maka, Anya Kabiru za ka gama da duniya lafiya, to ko wannan ne laifin da Ayra ta rik’e ko kuma akwai wani gagarumin laifin a gaba? Mhmnn Tabbas yara ko daga haka aka tsaya kun ga Takaicin Uba….. sai dai fa akwai wata a gaba ku dai ku cigaba da saurare don jin wata sabuwar k’addarar da ta afku tsakanin Ayra Gaya da Babanta…🤔 a yi hak’uri gobe ba na typing sai sunday In sha Allah, nagode da jumirin karatu. Love you all.” Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe. 25 💔💔💔💔 *SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?* *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*. *NA GWADA NA GA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*. *ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.* *AKWAI FULL, AKWAI RABI TA, YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*. *SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.* *DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*. *TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU* *08032773332* *DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.. ________ Mutanen Majalisar ba su gama yarda da abubuwan da Kabirun yake fa’di ba, saboda shiga ru’dani da tashin hankali, abu ne da za su kira shi sabon abu don hakan bata tab’a kasancewa a garin su ba, garin da suke girmamashi suke kuma ganinsa a gari mafi k’ololuwar daraja. Ganin ba su yarda ‘din ba, Ya sa Kabiru k’ara sakar musu kuka “Na san za ku yi mamaki, Amma ina son ku zo idanuwanku su nuna muku abinda na fa’da ‘din da gaske nake ba kuskure sharri ko k’age a cikinsa.” Firgitgit kamar an tsikaresu suka mik’e don zuwa su tabbatar da abinda ya fa’da musu, idan kuwa ta tabbata tabbas sai sun ‘dau hukunci irin na Shari’a akan Matar Kabiru da kwarton da aka kamata da shi, ba za su yarda ba, ba za su amince su bar yankinsu kara zube ba, a dinga aikata duk ba’dalar da aka so dole su ‘dau mataki irin Wanda addinin musulunci ya tanadar. Zuwansu tsakar gidan ya saka Kabiru saurin shammatarsu ya kamfato ruwa a bokiti don ba ya son su San ba sa hankalinsu balle a ‘d’ago shi. Yana shiga ‘dakin kafin su Farga ya shek’a musu ruwa a fuskarsu, tuni suka kawo doguwar ajiyar zuciya da yake maganin k’arfinsa bai kai har yarda za su ‘dau tsawon lokaci suna barci ba. Da sauri mutanen wajen suka fara jan salati da salallami suna ficewa daga ‘dakin cikin tashin hankali. Sai a lokacin Jabiru da Talatu suka farga da halin da suke ciki, Jabiru ya runtse idanunsa da yake jin sun masa nauyi, zuciyarsa kamar ta fito don tsananin harbawar da take, Shikkenan Kabiru yaci riba a kansa ya nuna masa ya fi shi sanin duniya kamar yarda ya sha jan kunnensa, Ya zai yi dole ya amsa laifinsa, laifin da baya tunanin ko giyar wake ya sha zai iya aikata shi da wanin Talatu ma da ta masa rik’on ‘da balle ita Talatun da kanta. Tabbas Kabiru ya cucesu musamman Talatun da abin sai ya fi tab’a mutunci da k’imarta ba mamaki ya shafi har zuri’arta. Hawaye ne Ya ji yana zubo masa, hawayen da Kabirun Ya da’de yana son ganinsu a idanunsa yau ga shi suna zuba kamar famfo. Talatu kuwa tsabar bak’in ciki tun bayan da ta Ankara da halin da take ciki ta ji zuciyarta kamar an danneta da bulo, numfashinta ma da k’yar yake fita sai ta fisge shi da k’arfi, Bata tab’a sanin Kabiru ya mata tsana Har irin haka ba, da za ta kai ya b’ata mata sunan ta ya b’ata mata sunan zuri’arta ya shafa mata bak’in fenti Mara gogewa. Me ta yiwa Kabiru ne? Me ta yi masa har haka da ta cancanci wannan bak’ar cutarwa daga garesa. Ashe bata cancanta Ya gode mata ba, bisa ‘dawainiya da take da y’ay’ansa shekara da shekaru madadin haka mummunar sakayyar da zata biyo baya kenan? Duk a dalilin rashin gata, a dalilin bata da inda zata je, shikkenan burinsa ya cika, burin da ya da’de yana mafarki za’a koreta daga Shagogo za kuma ta fita yawon duniya tunda ba ta da inda zata, ita kukan ma ta kasa ashe kuka ma guri yake samu, wani bak’in ciki ya zarta na hawaye sai tafasa da k’unar zuciya, ji take da ba haramun bane aikata kisan kai, tabbas da ta shek’a kanta barzahu a wannan daren kafin wayewar gari labari ya yi shela abinka da k’aramin gari, mutane su fara mata kallon mazinaciya, ta tabbata sunan yaranta ya gama b’aci har abada, abu na gaba bata yarda za’a yi mutanen Shagogo su yarda su cigaba da zama da ita garin. Kafin wanzuwar asubahi tuni Talatu ta zuge tas, ta yi wata irin rama kamar me, saboda tashin hankalin da take ciki, ita da kanta ta tabbatar ba abinda ya shiga tsakaninta da Jabiru don ko rantsuwa zata iya yi akan Jabiru ba zai iya rik’e ko da yatsanta ba da sunan alfasha balle ya keta mata haddi, zalunci ne kawai irin na Kabiru me son sai ya rabu da ita kamar yarda yake kiranta alak’ak’ai, da wannan tozarcin da ya mata gwara ai Ya tsaida wuk’a a mak’oshinta ya fille wuyanta ta iske kushewarta. Yarda ta ga rana haka ta ga dare ba tare da ta ji ko alamun barci a tare da ita ba. Jabiru kuwa tsaye ya yi a ‘dakinsa kamar Soja cikin mummunan tashin hankali, ba zai manta ba ya ji sanda Kabiru da Hadi suka mak’ureshi amma ba shi da hujja don haka ya zama dole ya amsa laifin da ba nasa ba a wajen mai gari, bai damu da kansa ba, ya san shi namiji ne kuma zai iya barin garin ya isa duk inda yake so cikin salama. Amma Talatu fa? Wani kallo zata samu daga wajen jama’ar gari? Yaya kuma yaranta za su zama a cikin mutane? Yaran da ya so su girma a gabansa su zama abin alfaharin da Kabirun zai yi da na sanin rashin kula da su da bai yi ba, sai ga shi cikin lokacin k’alilan Kabirun ya ruguje duk wani buri na su da suka jima da shi. Ya runtse idanunsa yana dukan kansa da bangon ‘dakin cikin mabayyanin b’acin rai, tuni idanunsa suka jirkita daga ainahin kalarsu zuwa jajaye kamar garwashi, ji yake idan aka ba shi dama zai iya hallaka Kabiru ya masa kisa mafi muni. Dole ne ya samu mafita, tilas ne ya samo musu mafitar da za su Tsira da mutuncinsu shi da Talatu kafin wayewar gari. (To fa! Ko ta yaya Kabiru zai samo musu mafitar?) Tun bayan idar da sallahr Asuba mai garin Shagogo ya tabbatar akwai magana a bakunan mutanen garin da suke zagaye shi a bakin fadar tasa inda yake amsar gaisuwa a wajen mutanen garin duk bayan Sallahr ta asuba. Wasu daga cikinsu tuni labari ya iskesu don haka suka yi dandazo a bakin fadar garin da son sanin ainahin gaskiyar abinda kunnuwansu suke jiye musu ana ra’de-ra’dinsa, hakan duk suka yi shi ya tabbatarwa Mai gari babu lafiya don haka Ya gyara zamansa yana gyaran muryar da ta ankarar da jama’ar da suka yi dogon kiwo cikin tunani. “Ko zan iya sanin me ya faru?” Mai garin ya fa’da cikin son kawar da y’ar hayaniyar da take ta shi a wajen. Tsit wajen ya yi ana sauraran ‘daya daga cikin mutanen nan na Majalisa da suka ga komai a kan idanunsu. Ya sake tashi ya tabbatar da zahirin abinda ya gani. Salati da Salallami aka ‘dauka a wajen, cikin tsananta mamaki da tsananin al’ajabi, mafi yawan mutanen wajen suna danganta hakan da al’mara, don abu ne da kai tsaye za su kira shi da farau a garin tunda hakan bata tab’a kasancewa ba kafin faruwar wannan ‘din don haka duk suka k’addara dole ne a zartar da mummunan hukuncin da zai ka’dar da y’an hanjin kowa ta yarda wani ma ba zai yi kuskuren sake aikata irin hakan ba. Mutane da dama suka dinga furta Allah wadai ga Talatu da Jabiru, don haka Mai garin ya yi tsit yana nazarin fuskokin jama’ar wajen da kai tsaye ya san idan ya furta abinda yake tasa zuciyar za su masa tawaye, don haka ya shanye nasa hasashen don ya san Kabirun zai iya aikata fin hakan ma, amma a yanzu ba shi da muryar da zai fa’dakar da mutane hakan kowa idonsa ya rufe so suke kawai a yiwa Talatu hukunci. “Hukunci ba ya yiwuwa, har sai na ji daga bakin Talatu da Jabiru don haka a je a taho min da su.” Furucin Mai garin kenan, da bai yiwa jama’a da’di ba, musamman an samu shaidun gani da ido da suka tabbatar da faruwar hakan to wace shaida kuma za’a nema bayan hakan? bayan abinda idanuwan mutane Har bakwai suka ga ni suka kuma shaida. Tausayin Talatu shine a zuciyar Mai gari shi yasa yake addu’ar Allah yasa Talatun tana da makamin da zata kare kanta, don ba ya raba ‘d’aya biyu tabbas wannan Sharrin Kabiru ne, muguntarsa ce da son lallai sai ya tozarta rayuwar Baiwar Allah. Tana can k’uryar ‘dakinta cikin ma’daukacin Tashin hankali, yaranta gaba ‘d’aya Sun tasa ta a gaba suna hawaye, ranar ba Wanda ya karya a cikinsu, don duk da yarintar Majeedah ta hankalce da sharrin da aka yi wa Mamanta ita da Zainabu. Majeedan ce ta yi k’ok’arin dama musu ruwan koko sai dai ko ka’dan ya k’i shiga cikinsu, Deejan ma ka’dan ta sha duk hankalinsu a tashe yake da yanayin da Ummansu da Abba Jabiru suke ciki. Wata irin tsanar Mahaifinsu ta k’ara rub’anya a kan wacce suke masa da, tsana mafi munin da za ka yiwa wani abin halitta. Yarda na ta hankalin yake a tashe haka na Jabiru yake, ban da yana tausayin halin da zata shiga idan ya arce ya bar garin da tun a daren jiyan ya yi b’atan dabo a Shagogo, to ya san yana tafiya zargin da ake musu za’a tabbatar da shi ba tare da jayayya ba don haka zai tsaya a kashe shari’ar kafin ya bar garin, don sam ba zai iya cigaba da zama a Shagogo ba bayan afkuwar wannan lamarin gwara ya yi nisa da Talatun duk da yana jin tsananin tausayin barin ta da yara, Amma gwara ya je ya dinga yi musu addu’a a duk halin da ya tsinci kansa. Don haka ya kammale kayansa wata y’ar jaka kaya kala biyu ya saka a ciki sai tarkacen litattafansa. Tunda suka fara jiyo Sallamar daga sama a zauren gidan, gaba ‘d’aya hantar cikin su ta ka’da don sun tabbatar sak’on Mai gari ne, hakan yana nufin labari ya gama kara’de Shagogo. Talatu da Jabiru kusan a tare suka runtse idanunsu suna jin amsa kuwwar Sallamar cikin kunnuwansu. Da k’yar Majeedah ta mik’e a hankali k’afafunta suna rawa ta isa bakin dangar gidan. Murya a raunane cike da k’unci ta amsa sallamar. “Yauwa maza ki ce da Uwarki Mai gari na kira yanzu-yanzu ya ce a same shi a fada da ita da abokin shai’danancinta.” Maganar ta zowa Majeeda a bazata, ta dinga Kallon mutumin tana zubar da hawayen takaicin furucinsa da ya yi a kan Ummanta da Abba Jabiru, a shekarunta Ya ci a ce ta gane abinda ake nufi. Jikinta a sanyaye ta juya tana jin da zata iya da ta canja k’addarar mahaifiyarta na Auren Kabiru da ta yi… da zata dawo da rayuwar baya da ta so ta ga mahaifiyarta cikin ahalin danginta na Uwa, don na Uban bata ga abinda suka tsinana mata ba, tunda Babanta ya Mutu ta zama tamkar ma bata dangi tsaf suka zareta daga cikinsu ko maganarta ma ba’a yi. Ta sauke idanunta a kan mahaifiyarta tana jin kamar ta ce mata Su gudu kafin jifa da tsinuwar mutane garin ta fa’da kan Mahaifiyarta. Amma idan Sun gudu ina za su je? Sai dai a wannan gab’ar barinsu Shagogo ya zama dole. Talatu kallonta take kamar mutum mutumi ta kasa magana sam sai sautin shiga da fitar numfashinta na iskar da take shak’a kawai ake ji. “An aiko ko?” Ta yi furucin kamar ana tilastata yawun bakinta ya k’afe k’af wani irin ‘daci take ji a bakin nata. Majeeda ta ‘daga kanta tana tattare hawayen da yake son zubo mata Wanda suka kasa tsayuwa tun daren jiyan don a kan idonta mutanen suka shigo. “Ki zauna da su Majeedah kada ku fita ko ina, bari na je na ji me ake ciki, idan kuma Sun kashe ni ne, na horeku da hak’uri a rayuwa a duk yanayin da zaku riski kan ku, don na tabbata ba za su bar wannan laifin ya tafi a banza ba. Allah ya isa Kabiru!” Ta furta tana jin wasu hawaye na rubdugun zubo mata, tausayin y’ay’anta take ji, don ta ita tuni ru’danin duniya yasa ta cireta a zuciyarta, zata iya cewa a lokacin ta fi mararin mutuwa fiye da rayuwa banda tana tausayin halin k’uncin da y’ay’anta za su shiga, sai dai ta bar su a hannun Allah y’a cigaba da kula da lamarinsu don ta tabbata anzo gab’ar da Jabiru zai farrak’a kansa da su. Ta saka Majeedah ta je ta gayawa Jabiru sak’on Mai gari. Kansa kawai ya ‘daga. Taf fadar take a cike mak’il, Kusan za’a iya cewa kaf mazan garin manyansu sa yaransu Sun hallara a k’ofar gidan Mai garin, don haka Talatu k’afarta ta dinga harhar’dewa kafin ta isa ainahin in da zata zauna, tana jin sunayen da mutane suke kiranta da shi kala-kala a kunnuwanta “Fasik’a Mazinaciya Ballagaza yau sai mun jefeki, Ishara ga duk wata Mace mai shirin kwaikwayonki……..” Talatu ta runtse idanunta tana jin sautin zuciyarta kamar zata bullok’o daga k’irjinta da gaske Kabiru ya gama cutarta.. Jikar Nashe…..✍🏽 Takaicin Uba… 26. Nazeefah Nashe.✍🏽 _______ Saura k’iris ta afka kan dandazon jama’ar, saboda jiri da yake kwasarta, da k’yar ta dake ta sakawa zuciyarta k’warin gwiwa ta zauna a inda Mai garin ya nuna mata da yi mata alamun ta zauna. Yarda zuciyarta ke rawa, haka duk gab’b’anta suke girgiza kamar mai cutar kakkarwa. Tausayinta sosai ya ratsa zuciyar Mai gari ya dinga tunanin hanyar da zai bi ya wanketa daga wannan mummunan zargin. Shi kuwa Jabiru fuskarsa a ‘d’aure tamau ya samu gefe can ya zauna yana k’ok’arin ‘dauke idanunsa daga Kan Kabiru da yake jin kamar ya mak’ureshi huta. Zuwa lokacin Fadar ta yi tsit ana sauraran Mai gari da dukkannin jawabinsa, da yake yin su a nutse kamar baya so, kalamai yake zubarwa cikin ilimi da Basirar da Allah ya ba shi ba don komai yake kwararo wa’azin ba sai don ya sanya tsoron Allah a zuk’atansu. Sai dai ga hasashensa ba Wanda ya damu da wa’azin nasa, don ba wannan suke son ji ba, burinsu su ji matsaya, su ji yarda aka kwana, ‘dai’daikunsu ne wa’azin Maigarin ya girgiza musu zuk’ata, har ya ‘darsa musu tausayin Talatun a ransu. Mai gari Ya sauke ganinsa a kan Kabiru da yake zaune gefe ‘daya cikin tunani, sosai ya yi zurfi a tunanin yana ganin kamar abinda ya yi bai kyauta ba, yana jin kamar ya wanke Talatu daga zargin nan, amma Ya san matuk’ar ya wanketa to dole ne Maigari ya mayar masa da aurenta, abinda ba ya so baya fata don ya gama shawarar rabuwa da Talatu rabuwa kuwa ta har abada. “Kabiru!” Kiran sunansa da Mai garin ya yi cikin kakkausar murya ya farkar da shi daga wancan tunanin da sauri ya ‘daga kai yana kallon Mai garin. “Ka fa’di tsakaninka da Allah, abinda ka fa’da a kan Talatu gaskiya ne? Ka tuna Allah yana kallonka idan ka yi mata sharri a kan abinda na ta ji ba bata gani ba, Allah yana kallonka kuma shi zai hukuntaka irin hukuncin da ake yiwa mai laifi irin naka.” Kabiru ya sunkuyar da kansa yana son k’aryata kansa, yana tunanin makomarsa a wajen mutane, bai San da wani ido za su kalleshi ba, k’arshenta ma duk wani hukunci da yake tunanin za su yiwa Talatun su jirgeshi a kansa. Don haka murya na rawa ya ‘daga kansa “Duk abinda na fa’da gaskiya ne, kuma ba ni ka’dai na gani ba sai da na kira shaidu suka tabbatar da abinda na fa’da ‘din.” “Rantsuwa zaka yi.” Maigari ya bashi Umarni cikin dakiyar murya da Takaicin Kabiru don a matsayinsa na Wanda ya fi Kabirun shekaru da mu’amala da mutane tuni ya gano tsagwaron rashin gaskiyarsa. Murya a dake Kabirun ya ce “To wace rantsuwa kuma zan yi, banda abinda mutane suka shaida, amma tunda rantsuwar ka ke so zan rantse maka, Na rantse da Allah duk abinda na fa’da a kan Talatu gaskiya ne…” maigari ya runtse idonsa, jin yarda jama’a suka kaure da hayaniya kowa yana fa’dar son zuciyarsa. Talatu dai tana zaune tsabar bak’in ciki ta zama kamar mutum mutumi, mutuwa kawai take rok’a a wajen Allah, tabbas Kabiru ta cuceta cutar da ba mai iya wanketa sai Allah… Jabiru kuwa ido Ya kafawa Kabiru cikin takaici a zafafe ya ce “Allah Ubangiji Ya tsinewa mai k’arya, tabbas ba mu da shaida sai Allah, don haka na barka da Allah akan abinda ka yi min In sha Allah kafin mutuwarka sai ka wulak’anta, dalilin wannan sharri Maigirma da ka yi min.” Tuni mutanen wajen suka yi yo ca a kan Jabiru, Har da masu k’ok’arin jifansa da duwatsu sai da Maigari ya tsawatar cikin tausayawa ya kalli Jabiru da ya yi k’asa da kansa yana zubar da hawaye idanunsa jajur, ji yake dama duk wannan abin da ake ya zama Mafarki, sai dai Ina? Ya san k’addara ta riga fata, Kabiru ya yi musu bak’in fentin da zai yi wahalar gogewa a idanun mutane. “Jabiru ka ji abinda Kabiru ya ce shin ka amsa laifinka?” Ha’diyar zuciya ya ragewa Jabiru kawai ya mutu ya huta, saboda yarda zuciyar tasa ta k’ulle ta daina aiki yarda ta kamata me zai ce? Ko ya ce ‘din ma babu mai yadda don haka gwara ya yi shiru kawai. “Baka ji na Jabiru? Kana da damar da zaka kare kanka.” Girgiza kai Jabiru kawai ya yi “Allah ne shaida ta ban aikata abinda yake zargina da shi ba, asalima ban san Wanda ya kai ni cikin ‘dakin ba, abu ‘d’aya na sani dama ya sha alwashi a kaina, ya ci burin sai ya b’ata min suna a gari, don haka ina masa murna, ina ta ya shi murna da ya samu dama a kaina tabbas wata shari’ar sai a lahira, ka gafarce ni Mai gari amma a kan hanyata nake ta barin Shagogo ina neman afuwar duk Wanda na b’atawa na yafewa kowa amma ban yafewa Kabiru ba kuma har abada Babu yafiya tsakani na da shi. Na bar ku lafiya.” Daga haka ya mik’e jikinsa a salub’e yana k’ok’arin kawar da kai daga kallon Talatu, don yana jin wani irin kuka da take na fitar hankali, Wanda ba ya raba ‘d’aya biyu kukan tafiyarsa ne, kukan rabuwa da shi ne, shima kukan ne ya taho masa, har ba ya iya ganin abinda ke gabansa, saka sawayensa kawai yake ta inda yaga dama kamar mai tafiya a kan iska, jakar hannunsa ce kawai damk’e a hannunsa haka ya saka kai ya mik’i hanya ba tare da ya san inda za shi ba. Wannan ce silar rabuwar Jabiru da Yaya Talatunsa. Wasu da dama daga cikin fadar Sun tausayawa Jabiru, har ma suna jin kamar su ruga da gudu su kira shi, yayin da wasu suka bi shi da kallon banza da tofin Allah tsine. Mai gari bai hana shi tafiya ba don ya hango tafiyar itace abinda ya fiye masa alheri fiye da zamansa a garin, tunda shi Namiji ne ba shi da Kaico a duk inda zai riski kansa sab’anin Mace da shigarta duniya yake nufin al’amura da dama. Fadar ta samu bak’uncin shiru, tun bayan da Maigari ya yi gyaran murya alamar yana son cigaba da magana daga inda ya tsaya. “Kabiru me ye matsayar magana? Abin nufi za ka cigaba da zama da Talatu ko kuwa ka samu hanyar rabuwa da ita kamar yarda ka ke fata?” Maganar Maigari ta masa dirar Mikiya ya ‘dago da sauri yana kallon idanun Maigarin sai dai da sauri ya ‘d’auke kansa don ba zai iya cigaba da kallon k’wayar idanun Mai garin da suke nufin abubuwa da dama ba. “Ka gafaceni ranka ya da’de, na sake zare igiya ‘d’aya a aurena da Talatu.” Mai gari ya kalleshi yana murmushi kafin murya k’asa k’asa ya ce “Burinka ya cika Kabiru, amma me yasa ba zaka kalmashe auren gaba ‘daya ba, ma’ana Ka sawwak’e mata duka igiyoyin auren, tunda dai ban ga amfanin barin ragowar igiyar ba.” Tsit ya yi yana kallon Maigari k’asa k’asa, abinda ya so yi kenan,wato sakinta gaba ‘d’aya sai dai Amininsa Hadi ya ankarar da shi abinda ya manta daga shara’din boka a kan kada ya sake ya saki Talatun gaba ‘d’aya don siririn arzikinsa yana cikin igiyar auren Talatun, don haka yake shakkar sakinta gaba ‘d’aya kada ya koma y’ar gidan jiya. Don haka ya ja bakinsa ya yi gum. Yana sauraran Mai garin da ya yi gyaran murya. “Abisa duk abubuwan da muka ji daga bakin duka b’angarori guda biyu, Wannan hukuma Mai adalci zata bawa Talatu mafaka a gidanta, sannan ina yiwa Kabiru Umarni ya tattare yaransa ya rik’e a hannunsa dukkan wata ‘dawainiya tasu ta koma kansa, wajibi ne ya basu cima mai kyau sutura da karatu mai inganci, ba kuma mu amince da yin tozarci ga Talatu ga zuri’arta ba, duk wanda aka samu da aikata haka akwai mummunan hukunci a kansa. Allah yasa mu dace. Tsit fadar ta yi saboda da yawa mazauna cikin ta wannan hukunci na Uban gari bai yi musu ba, har da wa’danda suka jefa ayar tambayar ga Mai garin shi kansa, akan wace hujja zai bawa Talatu wajen zama idan dai ba da wata a k’asa tsakaninsu da ita ba, ba su tab’a ganin shari’ar da Maigari Ya tausayawa irin wannan ba, don haka dole su masa tawaye. Kabiru kuwa hankali tashe yake duban Maigari jin abinda ya ce wai dole shi zai rik’e yaransa ya ciji leb’ensa yana sakin tsaki k’asa-k’asa shi da baya son wahala don me za’a jingina masa ta y’ay’a ya zama dole ya yi abinda zai girgiza zuk’atan kowa a daren yau, ko don gujewa rik’on yaran da baya farinciki da wanzuwarsu a duniya da sunan ahalinsa. Talatu kuwa zuciyarta ce take dukan tara-tara Sam wannan hukuncin na Uban gari bai mata ba, ya k’yaleta kawai su yi tafiyarta ita da yaranta don bata son cigaba da zama a Shagogo garin da kai tsaya ba zata k’arar da arzikin da ta samu a cikin sa ba, banda arzikin haihuwar yaranta, ta Yaya ma Mai gari zai ce zai rabata da yaranta? Bayan su ne farin cikinta, su ne danginta uwa uba don su ka’dai take zaune take dake zuciyarta take rayuwa banda haka da tuni wani labarin ake ba wannan ba, sai dai ya zama dole ta yiwa Maigari biyayya a k’ok’arin sa na kare mata mutunci da ya yi bai cancanci butulci a wajenta ba, don haka ta yi gum da bakinta tana sauraran bugun zuciyarta da take jin kamar zata wuntsilo. Mai gari ya bata umarnin ta je ta kwaso kayanta ta kawo gidansa ta kuma dank’awa Kabiru yaransa. Yana jiranta a safiyar gobe ta dawo gidansa. Tana wucewa ana binta da maganganu k’asa-k’asa maganganu masu ciwo masu suka nauyin zuk’ata. Ta dake ta share ta dinga amabatar Allah a zuciyarta. Har dare Kabiru yana ‘dakinsa na sashen amaryarsa yana k’ulla mai fishsheshi. Kafin ya amince da shawarar da zuciyarsa ta ba shi “Guduwa zan yi na bar garin, idan ya so sai naga uban da zai ‘dora min wahalar y’ay’a, itama wannan shak’iyiyar yarinyar sakinta zan yi in je in samu mai zak’in mu gudu Lagos abin mu, kafin na mana cuku-cuku mu haura k’asar Dubai.” Ya saki shewa shikkenan fak’at ba ni da wata matsala…… Jikar Nashe✍🏽 Takaicin Uba… Nazeefah Nashe✍🏽 27. 💔💔💔💔 *SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?* *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*. *NA GWADA NA GA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*. *ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.* *AKWAI FULL, AKWAI RABI TA, YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*. *SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.* *DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*. *TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU* *08032773332* *DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.. Hankalin Kabiru ya kwanta da shawarar da zuciyarsa ta ba shi. Don haka cikin daren ya saki amaryarsa ta hanyar rubuta mata takarda ya ajiye a kan gadon ‘d’akin inda idan ta dawo zata gani. Babu tausayi ba tsoron Allah, ya gama kammale kayansa tsaf. Asubar Fari ya shige cikin motarsa mai k’irar Carina Toyota tun samfurin ta mutanen da. Ya jata da sauri ya bar garin yana tunanin har abada ya rabu da alak’ak’ai Talatu da shirgin y’ay’anta mata. Ko da safe Talatu da ta game ha’de shirginta tsaf na tafiya gidan Maigari, hankalinta bai kwanta da barin yaranta ba, don haka sam zuciyarta ba sukuni ta dinga jawa Kabiru Allah ya isa a cikin ranta da ya zama silar rabuwar farin cikin su, ina yaranta za su tsoma kansu bayan babu Abba Jabiru babu ita kanta Uwarsu da ta tabbatar dai su biyun dai sune majinginar y’ay’anta a rayuwa. Su kansu yaran ba sukuni a cikin ransu, zuwa yanzu sun tabbatar da abinda suke zargi rabuwa da mahaifiyarsu bayan Abba Jabiru shima ya tafi. Majeeda da Zainab kuka kawai suke na tashin hankali, Talatu tana bin su da kallo rashin sanin abinda Zata ce musu ya sa ta ja bakinta ta tsuke tana jin tafasar da zuciyarta take mata. Suna zaune jugum a tsakargida Amaryar Kabiru ta yi sallama ta shigo gidan, dawowarta daga bikin da suka je a birnin kano kenan, ta riski wannan bak’in labarin da ta ji shi kamar saukar aradu, da gaske lamarin ya girgizata duk da ta san ko mafarki take ba za’a ce mata Talatu ta aikata hakan ba ta yarda, a ‘dan zaman da ta yi da Talatun ta tabbatar da nagartuwar halayenta da sahihancin sauk’in kanta ba zata tab’a amincewa Talatun zata aikata haka ba, ta san sharri ne irin Kabiru da ya riga ya kafawa Talatun karan tsana. Shi yasa tun daga wajen da aka gaya mata take sharar k’walla tana jin tausayin Talatun ya game zuciyarta da sassan jikinta. Yanzu ma ‘dora idanunta a kansu kenan ta ji zuciyatta ta tsinke murya a raunane da alamun kuka ta ce “Allah ya saka miki Talatu, tabbas Kabiru ya cika azzalimi nima kuma tabbas zama na da shi ya k’are don ance idan kaga gemun ‘dan uwanka ya kama da wuta ka shafawa naka ruwa, zai iya yi min abinda ya miki.” Talatu ta ‘dago da raunannun idanunta ta zube su akan Amarya. Kuka ne yake son zubo mata amma tana k’ok’arin danne su da k’arfin tsiya ta girgiza kai “Kada kice haka, ke dai nake murna zaki rik’e min y’ay’ana na san ba zaki tab’a cutar da su ba, kamar yarda zuciyata take gasgata min kina da jajurtacciyar zuciyar da zaki kula min da su.” Shiru amarya ta yi tana goge hawayenta tabbas zata iya cigaba da zama da Kabiru ko don ta rungumi y’ay’an Talatu da take jin su kamar nata y’ay’an, ba wai Zata zauna bane don Kabiru. Tsawon lokaci suna zaune Jugum, Talatu so take ta zare jiki ta fice ta bar yaran sai dai zuciyarta na mata wani irin nauyi idan ta tuna ko raba makwanci ba su tab’a yi da yaranta ba lokaci guda ace za’a raba su tabbas za su sha wahala. Jikin Amarya a salub’e ta mik’e ta shige ‘d’aki anan idanunta suka sauka kan takardar da Kabiru ya ajiye mata a kan gado, da sauri ta zura hannu ta ‘dauka da yake ta yi karatu har makarantar k’aramar secondary don haka bata sha wahalar karantawa ba. Tsaf ta gama karance takardar sakin nata da ya yi mata har uku, madadin b’acin rai murmushi ta saki tana furta “Hakan ya fiye min, ita kanta Talatu tafiyar taka na san ta fiye mata sau dubu ko bakomai dole a bar mata yaranta da gidan ma gaba ‘d’aya, mugu azzalimi In sha Allah sai Allah ya saka mata.” Daga haka ta fito rik’e da takardar a hannu tana murmushi ta ce “D’an akuyan Mijin naki nima ya sakeni saki uku, don haka ba mai rabaki da yaranki ki cigaba da zama a gidan nan kina kula da su. Allah ya tayaki Talatu.” Farin ciki ne sosai ya dirga a zuciyarta, tabbas ta ji da’din jin hakan ta dinga furta Alhamdulillah cikin tarin annashuwa da farin ciki. Ta godewa Allah da hakan ya faru ta tabbata Maigari zai ce ta yi zamanta gidan Kabirun. Ai kuwa Kamar ha’din baki Maigari yana jin labarin guduwar Kabirun ya saki murmushi kawai, ya tabbatar Kabirun ‘dan iska ne ajin farko a shai’danun mutane, ya san tabbas sai ya yi nadamar wannan abinda ya yi ko mu da’de ko mu jima. Da kansa ya yi umarnin Talatun ta cigaba da zama a gidan mijinta ta tarbiyyar da y’ay’anta wata rana zata yi alfahari da hakan. Maganganu iri-iri suka dinga yawo a gari, akan saboda me menene hujjar da Maigari ya zab’a kyautatawa Talatu fiye da musguna mata alhali bata cancanci irin wanann abubuwan da Maigarin yake yi ba, sai zance ya fara zagaya gari a Kan tabbas akwai abinda Maigari yake nufi da Talatun ko kuma shima kwarton tane shi yasa ya kasa ya tsare a cikin lamuranta. Bai kulasu ba duk da zantukan sun zo kunnuwansa ya ha’diye ya shanye duk wani b’acin rai da ya dinga hank’oro a zuciyarsa tunda dai shi ya san don Allah yake yi to zai cigaba da yi don Allahn yana kuma rok’on Allah ya ganar da jama’ar garinsa. Hankalin mahaifiyar Kabiru ya tashi sosai, ta dinga jin tsanar Talatu tana sake hauhawa a zuciyarta, ta kuma yi alk’awarin tilas sai tayi sanadin da Talatun zata bar Shagogo ko da zata yi yawo tsirara, ta Yaya Mai gari zai ‘dau gida guda ya damk’a mata gida mai ginin bulo da siminti, ita kuma shine bak’in cikinta har hakan yake neman ya kassara mata zuciya wani zubin har kasa runtsawa take. ___________ Watannin da Suka biyo baya wasu irin watanni ne da Talatu ba zata mance wanzuwarsu a rayuwarta ba, saboda bak’in cikin da ta ‘dan’dana mai zafin gaske, mutane Shagogo sun tsaneta tsana mafi muni, ko me ta kasa ba’a siya akan cewa ba za su siyi kayan fasik’a ba, hakan yasa rayuwa ta sake musu tsanani ta kai ta kawo wani zubin abincin da za su ci ma gagararsu yake, sau tari Maigari ne yake mata aike a b’oye na hatsin da za su ‘dan kwana biyu suna ci, ture ta maganar hatsi idan an sameshi masarrafinsa fa? Da me zata sarrafashi su ci abinci, tunda bata da ku’din mai da na kayan ‘dan d’ano, sau tari haka suke k’amusar abincin da zallar yaji ko mai babu. Tabbas Talatu ta ga tashin hankali a wannan lokacin tashin hankalin da ko mak’iyinta bata fata ya kasance a cikin sa, rayuwa ta juya musu baya suka zama kamar almajirai har Talatu ta gwammaci barin Shagogo fiye da zaman cikinsa, amma idan ta bar Shagogo Ina zata da yara mata har hu’du, ta runtse idanunta bata son ta zama silar da yaranta za su zama karuwai, dole ne ta zauna a Shagogo tunda bata da inda ya fi nan. ________Ana Wata Ga Wata___ Murnar Talatu da take yi na gama idda ba tare da Kabiru ya sake zuwa ya mayar da ita ba, sai ya koma ciki sakamakon wayar gari da aka yi ta fara jin motsi a cikinta, motsin da ta tabbatar ciki ne, musamman yarda motsin yake sake k’arfi kamar zai fasa cikin ya fito duniya. Sanda ta fara ji gabanta ne ya shiga fa’duwa take a wajen ta fara fa’din Innalillahi Ni Talatu Naga Ta kaina! Ciki Kuma? Tabbas ta ga ta kanta tunda dai ta tabbata a sharri da makirci irin na Kabiru ba zai amshi cikin nan ba, musamman idan ta haifi mace zai iya cewa ba cikinsa bane, tunda a sanda abin ya faru da kusantar da ya yi mata bai fi sati guda ba… ta runtse idanunta tana addu’a a ranta Ya Allah ka fitar da ni daga sharri da makircin har da Tuggun Kabiru…. Wasu hawaye masu zafi suka dinga kwararo mata, sam ba ta yi farin ciki da samuwar cikin ba, kuma ba ta jin zata iya zubar da shi. A hankali cikin ya fara girma har ya bayyana kowa ya fara ganinsa, a lokacin ne hankalin jama’ar gari ya fara dawowa kanta, aka fara yama’di’di da zancen tun ana yinsa a b’oye har aka samu tsagerun da Suka zo har gida suka tsare Talatu cikin gatsali suka ce mata “Amma Talatu kin san ba zaki haifa mana cikin shege a garin nan ba ko? Tunda ba’a tab’a yi ba ba kuma zamu fara ta kanki ba, ba zaki haifa mana abinda zai ‘debe mana albarkar gari ba, don haka mun baki kwana biyu ki tattara dake da yaranki Ki bar garin nan, kuma a wannan karan ba Maigari ba ko waye bai isa ya ce za mu cigaba da zama da ke ba, Fasik’a Mazinaciya…” Wani irin duhu Talatu ta fara gani a idanunta sauran maganganun da suka biyo baya duk bata fahimce me suke cewa ba, ta dafe kanta da hannu biyu saboda yarda yake sara mata kamar zai rabe biyu, YA ALLAH MAFITA…” ta furta a hankali cikin wata murya mai karya zuciya ji kake yif ta sume a wajen…… Jikar Nashe✍🏽 Takaicin Uba. Nazeefah Nashe✍🏽 28. 💔💔💔💔 Sai da suka ga ta suma sannan hankalinsu ya tashi, ba don komai ba sai don rashin sanin abinda za su cewa Maigari idan ya tambayesu yarda aka yi Talatun ta suma alhali ya garga’de su akan lamarin Talatun. Tunanin zuba mata ruwa ne ya kawo musu a kai, don haka ‘d’aya daga cikinsu ta kandamo ruwa a rijiya ta shek’awa Talatun, ai kuwa sun samu ta kawo wani dogon numfashi alamar ta farka daga suman, ta dinga bin su da ido tana jin k’ullin zuciyarta yana k’ara kananna’dewa Sharrin ya mata zafi ya kuma mata ciwo sosai fiye da nusgunawar Kabiru. Cikinta za’a sheganta mata? Cikin da ta tabbatar Kabiru ne ubansa amma mutane suna son su Sheganta mata shi? Wace irin Masifa ce wannan? Ina ma zata ga dangin Mahaifiyarta ta gudu can wajensu ta huta da wannan gararanbar da take yi a rayuwa. Kukan ma ya k’i zuwa, sai bin matan da suka cika mata gida da kallo take, tana nazarin fuskokinsu masu bayyana zahirin abinda yake zuk’atansu, da gaske Talatu ta hango tsagwaron tsanarta a idanunsu, ta lumshe ido bata ga laifinsu ba, Kabiru ne ya bada k’ofar da za su kafa mata zargi tunda shi ya mata sharrin Tarayya da Jabiru. Runtse idanunta ta yi tana sauraran furucin Matan mara da’din Ji da suke ta sakinsa a kanta. Tsawon lokaci suna abu ‘d’aya kafin su shige su tafi suna sake jaddada mata ta nemi Mafita ita da yaranta don ba za su tab’a amince mata ta zauna a garin su ba. Murmushi ta saki kawai Murmushin da yake bayyana tsananin wutar b’acin rai da take huruwa a zuciyarta, Dole na tattara na bar garin nan kafin bak’in cikin Kabiru da mazauna cikinsa ya kashe ni. Hakan ta bari a ranta, za ta yi nisa da Shagogo ta manta da labarinsa tsaf ko da hakan yana nufin komai ma a rayuwarta idan ta ce komai tana nufin komai ciki har da Mutuwa saboda wahala duk ta aminta a kan zamanta a Shagogo garin da ba zata k’arar da zaman jin da’di a cikin sa ba, sai bak’ar wahala da masifu iri-iri daga wannan sai wannan. Tsit gidan ya yi, bayan ficewar da mutane suka yi suka bar gidan. Ta mayar da Kallonta kan yaranta mata guda hu’du da suke zaune a can gefe cikin matuk’ar tashin hankali, zuciyarta a wannan karan kasa jurewa ta yi har sai da ta zubar da k’wallar da tun ‘d’azu take kokawa da su a kan zubowarsu. Ta bu’dewa yaran nata hannu alamar su iso gareta, ai kuwa kamar jira suke suka rugo gaba ‘d’aya suka shige jikinta suna sakin nasu kukan mai matuk’ar gigita hankali. Tsawon lokaci suna kukan kafin ta bi su ‘d’aya bayan ‘d’aya ta share musu hawaye tana fa’din “To ya isa, In sha Allah ba sauran kuka yau yau za mu bar wannan garin da kullum ba abinda mu ke fuskanta a cikinsa sai bak’ar wahala. Ku tashi Majeeda ku ha’de mana y’an sauran kayan mu da suka rage masu ‘dan kyau, gwara mu je birni ko aikatau na rarrabaku a gidan mutane ni ma na samu wani gidan na dinga musu aikatau idan ya so idan muka tara abinda muka tara sai mu samu jari mu kama ko gidan haya ne.” Sosai Majeeda da Zainab suka ji da’din wannan shawarar ta ta suka kuma amince gwara kam gwara su je su yi aikatau ‘din da wannan zaman rashin madafar da suke tunda nan ‘din ko kayan sana’a suka kafa ba mai siye sai ace wai Uwarsu mazinaciya ce. A daren ranar da suka gama kimtsa kayan su, da niyyar kashegari za su bar garin, a daren Kabiru ya sauka ya zo daga lagos afujajan da shi, kamar wanda aka cillo ya fa’da gidan Talatun. Wata irin fa’duwar gaba ce ta riski Talatun sanda ta yi arba da shi, ranta a b’ace ta dinga kallonsa, duk da wannan karan ta shirya masa ba wanda zai saka ta zauna da aurensa. Ya zauna dab’as a tsakar gida yana ‘dan kallon Talatun k’asa-k’asa ha’de da jin b’acin ran ganinta da ciki, sai kuma ya saki murmushi yana dubanta “Talatu kenan, kika wani zuba ido kina kallona ba aurenki na zo mayarwa ba, Wannan gidan nawa na zo siyarwa, saboda na je na fito da wasu kayana da Jami’ai suka rik’e min, Sai ga Shi Alhamdulillah na zo a kan gab’a don na ji labarin mutanen garin nan sun miki kashedi a kan bar musu gari sakamakon cikin shegen da kika yi.” Ya tuntsire da dariya “Kin ga cikin sauk’i sai ki wuce ki bar min gida na na siyar da shi na k’ara gaba, abin da’di har y’ay’an ma na bar miki su halak malak har duniya ta na’de bare wannan cikin da duniya ta shaida ba nawa bane, har abada ki barshi a sunan shege don ba zan amsheshi matsayin jinina ba, abu na gaba ki rik’e a ranki duk inda zaki je da igiyar aurena guda ‘daya a Kanki don Malamina ya tabbatar min idan na sake ki ni da arziki har abada don haka tun bayan tafiyata na isa wajensa ina jin abinda ya ce kuma a take a wajen na mayar da igiyar aurena dake kan ki don haka duk inda za ki shiga kina nan a matar Kabiru ba shegen da zai aure ki, yara dai na bar miki da wannan cikin da Duk garin Shagogo sun shaida Shegantakarsa….. ya tuntsire da dariya……………” Tsit Talatu ta yi da bada labarin sakamakon wata irin gigitarciyar k’ara da Ayra ta saki a daidai k’ofar ‘dakin. Daga ita har Hameeda suka k’arasa bakin k’ofar da sauri don sanin me ya faru. Cikin fa’duwar gaba Amma ta kai kallonta kan Ayra da ke zube kamar gawa idanunta a kakkafe ba alamar numfashi a tattare da ita. Talatu a gigice ta ratsa sauran jama’ar ta yi kan Ayra tana fa’din “Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna! Na shiga Uku Hameeda! Na kashe y’ata da kaina, sam Ayra bata san duk wannan labarin ba, ban tab’a bata ba, sabida yarda zuciyarta ta taso da tsanar mahaifinta sakamakon Tata k’addarar da ta faru tsakaninsu k’addarar da ta haddasa mata tsanar aure, na tabbata tunda ta yi wannan zubewar ta ji duk labarin da nake baki daga farko har k’arshe.” Hameeda ma jikinta rawa yake ta hau bubbuga Ayran sai dai kamar tana buga Dutse, don Ayran bata da alamar ta san me take yi, hankalinta tashe ta kalli Talatu tana fa’din “Dama ta tab’a irin haka?” Talatu tana hawaye sosai ta girgiza kai tana fa’din “Tana suma dai, amma bata tab’a sandarewa irin wannan ba.” “Kamata mu kaita asibiti.” Hameeda ta fa’da da sauri tana k’ok’arin ‘daga Ayran da su Dijah suka zagaye suna kuka gani suke shikkenan Ayran ta mutu ta bar su, tunda ta sha fa’da Insha Allah idan suka nufi yi mata aure kafin su sadata da gidan miji zata mutu kowa ya huta. A guje Hameeda take jan motar, cikin wani irin mugun speed, sam ta manta a Nigeria take ba a k’asar su Lebanon ba, burinta ceton rayuwar surukartata da take jin sake son aurensu da Turaki tun bayan da ta ji wani sashe na labarinsu duk da bata gama ji ba, amma yanzu ta ‘dora ‘danbar son aurensu, za kuma ta yi yak’i da duk wanda ya bayyana k’iyayyarsa ga auren cikin kuwa har da mijinta ko da hakan yana nufin abubuwa da dama.. Mintuna k’alilan ne suka sada su da asibitin Nasarawa in da anan Babban likitan da yake ganin Ayran yake. A tsorace yake kallon Ayran da take kamar gawa a shimfi’de a sandare, hankalinsa tashe ya shiga k’ok’arin ceto lafiyar ta sai dai hakan ya gagara dole ne sai ya gayyato wasu daga cikin manyan likitoci daga asibitin Aminu Kano saboda ya yi iya yinsa amma Ayran bata farka ba. Don haka ya ‘dan saka mata drip da wasu allurai ya fice da sauri ba tare da ya saurari su Amma da suka taso da saurin suma don son sanin ko Ayran ta farka. Sai dai ba su ci sa’ar cimma sa ba don a hanzarce yake tafiyar kamar zai tashi sama. Tsawon awoyi biyar likitocin biyar suka ‘dauka kafin su samu Ayra ta kawo wata doguwar ajiyar zuciya, ta sake runtse idonta tana fata ta bu’de idon ta ganta a cikin Kabari bata son a ce tana raye a wannan duniyar mai cike da ru’dani, tsawon mintuna biyar idanunta a runtse tana fatan y’an maganganun da take ji a cikin ‘d’akin k’asa k’asa na likitoci ya zama maganar Mala’iku ce, da ta yi murna da farin ciki ta kuma godewa Allah da ya ‘d’auke ranta a wannan duniyar da ba abinda ta tsinta sai ba’cin rai, ashe bayan wancan gagarumin laifin da Kabiru ya mata akwai wani laifin na Sheganta ta da yasa Mutanen Shagogo suka yi. Anya kuwa a duniya akwai yaran da ba su yi sa’ar mahaifi ba kamar ita da y’an uwanta har abada ba zata yafewa Kabiru ba, kuma tana jiransa ya zo lahira a yi shari’a a tunanin Ayra fa Duk wannan zantukan da take yi a cikin Kabari take, murna take ta mutu ta huta ba za’a mata auren da bata so ba. “Dagota.” Ta jiyo muryar Likitan da take zaton Mala’ika ne, don haka ta ‘dan kanne ido da son ganin Mala’iku da wata suffa suka zo mata, tunda ta san ance idan ka yi aiki Mai kyau suna zuwa maka a kyakykyawar suffa, idan ka yi Mummuna su zo maka a mummunar Kama. Tsaf murnarta ta koma ciki, ganin likitan da sirinji a hannunsa ya na shirin yi mata allura, bata tantama asibiti ne, abinda yake nuna a zahire har a lokacin tana raye kenan, me yasa bata mutu duk da burinta na son Mutuwa kawai sai ta samu bakinta yana furta “Ya Allah na fi buk’atar zuwa wajenka a kan zama cikin duniyar nan, don haka kada ku sake ku min allurar nan, da za ku burge nima da nace muku na fi son ku min allurar da zata zama ajalina…” Cak likitocin suka tsaya da aikinsu cikin tausayawa suka zuba mata ido.. Ya Ilahi me ya samu yarinyar nan ne? Jikar Nashe✍🏽 Takaicin Uba…. Nazeefah Nashe✍🏽 29. 💔💔💔💔 *SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?* *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*. *NA GWADA NA GA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*. *ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.* *AKWAI FULL, AKWAI RABI TA, YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*. *SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.* *DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*. *TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU* *08032773332* *DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.. —————- Likitocin suka cigaba da zuba mata idanu cikin tarin mamaki, ganin yarda take sakin surutai barkatai kamar wacce ta ci kai. Da k’yar d’aya daga cikin likitocin ya yi azamar dakatar da ita daga yunk’urin da take na fincike abin k’arin ruwan, ya yi Saurin danne hannunta yana kallon cikin idanunta da suke jirkicewa zuwa wani yanayi na daban, kamar mai shirin rasa hankalinta da tunaninta ma gaba ‘daya. Allurar barci ya yi mata don zuwa lokacin ya hango cewa allurar barcin itace taimakon gaggawa da ya kamata a samar mata, ta saki ajiyar zuciya daidai lokacin da take lumshe manyan idanunta cinkoson hawayen da ya yiwa idanunta dafifi suka shiga rige-rigen sakkowa kamar an kunna famfo. Likitocin suka saki ajiyar zuciya a tare ha’de da yarfe gumin da yake goshinsu don ba k’aramar jigata su ta yi ba. A zaune suka samu su Amma jigum-jigum, fuskarsu cike fal da alhini da ya bayyana a cikin idanunsu, burinsu kawai sanin Halin da Ayra take ciki zuwa lokacin Amma ta kai k’ololuwa a tashin hankali, sam bata san Ayran na nan lab’e ba da bata saki baki da jiki tana bawa Hameeda labari ba, labarin da take ta tattalinsa bata son Ayran ta sani balle ta rub’anya shi a kan wancan laifin ta sake ninka k’iyayyar maza a ranta, sai ga shi cikin sauk’i ta ji daga bakin da ta tabbata ba zai mata k’arya ba. Likitan da ya zama shine likitan Ayran tun tale-tale tun bayan afkuwar wancan lamarin da ta razana ta ‘dimauta har ya zame mata uwa zata samu matsala a kwanya, ya sauke idanunsa a kan Amma, ransa a ‘dan b’ace ya ce “Ku biyo ni Office akwai abinda zan fa’da.” Da sauri Amma da Hameeda suka mik’e suka bi bayansa, zuwa lokacin Amma bata jin akwai abinda zata b’oyewa Hameeda jin ta take kamar y’ar uwarta shak’ik’iya. Tsawon lokaci yana rubutu a file ‘din Ayra ya bar su Amma da suka k’agara su ji halin da Ayran take ciki zaune sun zuba uban tagumi idanunsu a kansa, suna hango tsagwaron b’acin ran da yake ciki. Sai da ya mula don kansa sannan ya ‘dago idanunsa cikin na Amma ya ce “Idan ba kya son lafiyar yarinyarki me zai hana ni ki bar min ita kafin ki haddasa mata ciwon hauka?” Amma gabanta ya buga, bugawar da in dai kai mai k’arfin ji ne kana zaune kusa da ita sai ka jiyo. “Ta shiga condition ‘din da k’iris take jira ta kai ga limit ‘din rasa tunani, inma saboda b’acin ran da kuke haddasa mata ko kuma kuna tuno mata wancan mugun abin da na yi garga’di a kan kada a dinga tuno mata, ban da Allah ya kiyaye a yau zuciyar yarinyarki daf take da bugawa don gaba ‘d’aya sai da komai na jikinta ya tafi hutun yajin aiki saboda wani abu da ya gigita mata tunani, mun sha wahala sosai kafin daidaituwar komai a jikinta, and for My last warning kada ku sake ‘d’aga mata hankali idan ba haka ba komai zai iya faruwa idan na ce komai ina nufin komai, dafatan za ku kiyaye Allah yasa mu dace. Yanzu za ku barta a nan zuwa gobe mu ga Abinda Allah zai yi, amma dai a kiyaye, kiyayewar shine abinda muka fi buk’ata.” Shiru ya bak’unci office ‘din, duk wani farin ciki da son auren Turaki da Ayra da Hameeda take yi sai murnarta ta koma ciki, bata son abinda zai haddasawa Ayra ciwon hauka don haka kafin aiwatar da Auren ya kyautu k’warai ta tambayi Likitan ba matsala idan aka aurar da ita? Don haka ta gyara zamanta cikin sakin nauyayyiyar ajiyar zuciya idanunta cikin na likitan da ya mayar da kallonsa kanta jin ajiyar zuciyar da take. “Ba matsala likita idan aka mata aure?” Jim ya ‘dan yi yana juya biron a hannunsa “Ba zai zama matsala ba, idan aka dace mijin na mata bahagon so wanda zai iya shanye duk wasu Matsalolin da zata zo masa da su, amma zai iya zama matsala idan aka samu miji mara kula ko kuma aka yi rashin dace ita bata son sa, amma tabbas Auren shi ya dace da ita, shine abinda zai ‘debeta mata kewa ya kuma kawar mata da wancan tunanin, duk hakan kuma zai faru ne idan aka samu dacen Mijin ya zama mai kulawa sab’anin haka kuma komai zai iya faruwa, kuma ina da yak’inin ba namijin da zai samu dalleliya kamar Ayra ya kasa kulawa da lamarinta ta kai mace duk yarda ake son Mace ta kai koma fiye da.” Likitan ya fa’da yana lumshe ido k’ok’ari yake sosai wajen danne abinda yake taso masa dangane da Ayran saboda ba tun yau ba yake jin masifar son ta sai dai ta k’i ba shi dama, ga shi Allah ya ha’da shi da wata iriyar mata mai masifaffen kishi da idan ba’a yi wasa ba haka zai k’are rayuwarsa da Mace ‘d’aya jal. Amma ta saki ajiyar zuciya idanunta cikin na Hameeda da itama ta saki ajiyar zuciyar suka mik’e duk a tare hankalinsu a tashe da tunanin ta yarda za su b’ullowa lamarin. Tsawon lokaci Hameeda tana tare da Amma, kafin tunanin zuwa gida ta taso Turaki a gaba ya duba Ayra yazo mata, dole ne kuma ta ja kunnensa a kan aikata duk wani kuskure da zai zamo sanadin b’acin ran Ayran, bata jin zata iya hak’ura da ha’da auren Ayra da Turaki, mafarkinta ne kuma shine burinta da take jin zata iya rasa nata auren matuk’ar Turaki zai auri Ayra, wannan karan zata bijirewa Mijinta har sai ya amince da auren ko da haka yana nufin komai ma.” Ta mik’e hannunta rik’e da jakarta ta isa inda Ayran take barcinta cike da alamar gajiya da wahalallen numfashi da take fitarwa a nauyaye kamar ana fisgosa. Ta saka hannu ta tattare gashin Kan Ayran ta mayar da shi baya ha’de da tofa mata adduo’i a kan fuskarta. Amma ta dinga jin da’din kulawar da take bata “Bari na je gida Talatu zan dawo zuwa da Yamma na san har na dawo ma bata farka ba tunda Doctor ya ce sai zuwa Magrib Zata iya farkawa, kada ki saka komai a ran ki, ki kuma k’addara aurensu alheri ne da za mu yi tutiya da shi nan gaba.” Amma ta ‘d’aga kai tana sakin murmushi “Allah yasa Hameeda, Allah yasa mu yi Alfahari da hakan.” Gaba ‘d’aya ’d’akin suka amsa da “Ameen” Hameeda ta saka kai ta fita da ‘dan azama. ❤️❤️❤️❤️ Daidai lokacin yana tsaye a ‘dakinsa, hannayensa saye cikin dogon wandon da yake jikinsa a bakin babban windown yake tsaye idanunsa a kan harabar gidan kamar mai nazarin wani abu, sai dai tunani ne cunkushe a zuciyarsa, tunanin macen da ta tsaya masa a rai bayan Mutuwar Hibba, da zai ganta ita ka’dai yake jin zai iya aura ya kuma zauna da ita cike da soyayyarta kamar yarda ya so Hibba. Sau ‘d’aya ya tab’a ganinta a kuma kallo ‘daya wanda ya sa shi azamar snapping ‘dinta a wayarsa ba tare da ta sani ba, kallon da ya mata yasa ta zabga masa harara ha’de da ‘d’auke kanta tana cije leb’e har yau abin ya k’i b’ace masa, kamar bita haka yake hango fuskarta da take nunawa Yayarta shi ta mata nuni su tashi su bar wajen. Turaki ya lumshe ido ya saki murmushi ha’de da ware idon ya sauke a kan wayarsa ma’adanar inda yake ajiye hoton ya shiga, kullum yana cikin wayarsa kuma ko ya canja waya hoton yana nan ba ya saka in rabuwa da shi. Murya a d’ashe cikin sautin da yake bayyana tsananin buk’atuwarsa da son ganin yarinyar ya furta “When? And Where? Ya fa’da yana ‘dan taune harshen sa, sai kuma direct ya shige ‘d’akin da yake zane-zanensa da yake shi mutum ne ma’abocin zane-zane, kaca-kaca ‘d’akin yake da shirgin hotunanta da na matarsa mai rasuwa, ya dinga bin hotunan da kallo tamkar su ne za su sada shi da inda yarinyar take. A hankali ya ja ajiyar zuciya jin wayarsa na k’ara yana dubawa ya ga sunan Ummeeey Hayateey’ d’an murmushin da bai shirya yinsa bane ya sub’uce masa a hankali ya ce “Dangerteey kuma ba, ke ka’dai ce a rayuwa zaki min auren dole na yarda, amma wannan karan am sorry to say idan yarinyar nan ta sake ta shigo hannuna Zata wahala.’ Shi ka’dai yake magana kafin ya kai wayar kunnensa “Turaki kana ji na?” Sai da ya lumshe ya bu’de a kan hoton yarinyar da ta k’ura masa ido sannan yace “Yes Ummeey.” Yauwa ka zo gida yanzu ina son ganinka.” Daga haka ta katse wayar ta bar Turaki da waya a hannu yana kallonta, kafin ya mayar da kallonsa kan aljannar sa ta airport da ta huda masa zuciya. Ya ‘dan shafi gefen k’uncinta kamar wani zararre ya hau zagaye kyakykyawan kissable lips d’inta. “Kin gani ko? Kin ga abinda ki ke shirin jawo mana kin k’i ki bayyana min kan ki ga Hayateey nan zata min auren dole, ba ruwana kin jawowa kan ki zama da kishiya It’s your fault Angel.” Ya fa’da yana lumshe ido kafin da azama ya fice yana tunanin ko hotunanta zai baza cigiya. Sai da ya sake wanka, sannan ya saka wata arniyar shaddarsa bak’a wuluk mai masifar k’yalli, sai ta sake fito da ainahin kalarsa da ta kasance fara mai fatsifatsi, don shi ba fari bane dau tsaka-tsaki yake kalarsa ta caku’da data larabawa da kuma ta Ubansa da ya kasance usulin bak’in bafulatani. Ba gwanin saka hula bane don haka ya yi combing kansa ya shafa masa mai da Hair spray. Ya fito yana baza k’amshin turaren Miyaki ‘dan usulin mai tsadar gaske. Ya da’de a falon gidan su yana ‘dan waige-waige da jiran ta inda Ummeey zata fito, kafin Tayseer ta fito tana niyyar shiga kitchen ta hangoshi a zaune ya jingina a kujera idanunsa a lumshe kamar mai barci. “Ya Turaki Barka da zuwa.” Idanun a lumshe ya amsa “kice ma Ummeey na zo.” Bata wani damu da rashin kallon ta da bai yi ba, don ba tun yanzu suka saba da yanayinsa da ya jirkice haka ba tun bayan mutuwar matarsa, da Kam Turaki mutum ne mai barkwanci da yake tasa su a gaba da wasa da dariya banda yanzu da ya rikid’e musu ya koma SINGHAM, sunan da suke kiransa kenan ita da Tasleem. Tana sanar da Ummeey ta ce “Ki ce masa ya shigo nan.” Tayseer ta juya da sauri don isar da sak’on Ummeeyn. Tana gaya masa ya mik’e, don ya san tunda Ummeey ta ce ya shiga ‘d’aki magana ce mai muhimmanci za su yi, Allah yasa dai ba a kan auren Karuwar nan bane. Hannayenta zube bisa k’uncinta ya same ta, da alamar yanayin damuwa da yake shimfi’de bisa fuskarta, ya gama karantar halayen mahaifiyarsa zai kuma iya rubuta littafi guda akan halayenta abu ‘d’aya ya kasa sabawa da shi, rigimarta da kafewa a kan ra’ayinta sama da na kowa ko da kuwa ba itace da gaskiya ba. Idanunta da suka taru da k’walla ta zuba masa, hakan ya sanya shi mutuwar jiki har bai san sanda ya isa gabanta ba ya durk’ushe sosai yana kamo tattausassun hannayenta cikin nasa yana matsawa a hankali cike da ladabi da alamar rarrashi. “Menene Hayateey?” Shiru ta masa tsawon lokaci tana nazartar k’wayar idanunsa kafin ta saka hannayenta cikin tarin sumar gashin kansa murya a k’asa ta fara magana “Ku biyar Allah ya ba ni, a cikinsu kuma kai ka’dai ne namiji, wanda nake jin ina da iko da shi fiye sa sauran matan tunda su da zarar sun yi aure sun koma k’ark’ashin ikon mijinsu, wanda suka yi auren kuma dama Suna can k’ark’ashin iko da umarnin Mijinsu, me yasa Turaki? Me yasa kake son karyan gwiwa ta hanyar bijirewa umarnina, yau ko yarinyar nan da gaske karuwa ce ashe ba zaka iya sacrificing farin cikin ka ba don samar da nawa, ka aureta?” Ta sake murza hannunta cikin nasa tana son ganin yanayinsa da sanin shin maganarta ta tana huda zuciya da kwanyarsa. “Burina samar da farin ciki a rayuwar Ahalin Talatu, ta sha wahala sosai a Rayuwa, wahalar da ko da karuwancin ta shiga ba za’a ga laifinta ba, ko y’ay’anta karuwancin suka yi sun yi a kan gab’ar da ta dace, balle bai zama lallai ace hakan ta faru da su ba, Ka min alfarma a wannan karan ko da hakan shine alfarmar da zaka min ta k’arshe a rayuwa ka auri yarinyar nan.” Ta fa’da tana sakin wasu irin hawaye, hawayen da take son su k’arya masa zuciya har ya amince da buk’atarta. Hak’anta kuwa ya cimma ruwa don yarda jikinsa ya dinga rayuwa zuciyarsa ta dinga bugawa sakamakon jin hawayen yana ‘diga masa ya dinga furzar da ajiyar zuciya har bai san sanda cikin tashin hankali da rawar murya ya damk’i hannunta ba yana furta “Na amince Na amince Ummeey ko da hakan yana nufin k’arshen rayuwata!” Murmushin da bata shirya yinsa bane ya sub’uce mata a kan kyakykyawar dattijuwar fuskarta, ta dinga murza hannunta tana fa’din “Thankyou Turaki, Shukran Al’amin Allah ya yi maka albarka Aminullahi.” Yayinda take farin ciki shi kuma bak’in ciki ne yake nuk’urk’usar zuciyarsa, ya dinga jin sautin bugunta da k’arfin gaske, ga wani ‘daci da ya yi masa dabaibayi a mak’ogaransa, tabbas ko wacece yarinyar nan ta zame masa bak’ar k’addara a rayuwarsa kuma zai wahalar da ita ta cikin ruwan sanyi ba tare da ya bar kowacce irin kafa da Ummeey ko mutane za su gane ba, shi da auren Karuwa? Ya dinga murza goshinsa yana kallon Ummeey da yarda take sakin dariyar farin ciki tana fa’din “Ina son ka gayawa Abbunku da bakinka ka amince da auren kuma ko me zai ce maka kada ka janye In sha Allah sai ka yi alfahari da auren nan.” Ya ha’diye kakkauran yawu kawai da k’yar kuma ya ‘d’aga mata kai alamar ya amsa. “Yanzu bari na shirya mu je asibiti tare da kai an kwantar da yarinyar bata da lafiya, jibi kamar yarda ka sani ‘daurin aurenku yana nan ba fashi In sha Allahu.” Ya sake lumshe ido kawai ha’de da mik’ewa ya fita falo yana jin tafasar k’una da zuciyarsa take yi. Burinsa ya yi ido biyu da yarinyar nan, tun yau ya fara nuna mata matsananciyar tsana ta hanyar kallo zalla. A mota ma idan banda zancen ba abinda Hameeda take masa burinta ya je ya ga Ayra ta tabbata daga kallo ‘d’aya zai fara mata mahaukacin so. Anya kuwa! To za dai mu gani. JikarNashe✍🏽 Takaicin Uba….. NazeefahNashe✍🏽 30. 💔💔💔💔 Cikin zafin nama ya yi parking a harabar asibitin, suka fito daga cikin ha’daddiyar motar tasa. Mai samfurin Benz bak’a wuluk da ita. Burinsa ya je ya ga wacce ta shanye masa Ummeey da zuciyarta tsaf ta hanata sakat har sai ta ha’da su auren su, don zuwa yanzu yafi amincewa da abinda zuciyarsa ke gaya masa na cewa asiri aka ma Ummeey ta rikice har haka da son aurensa da karuwa. Takunsa na kullum cike da izza yake yinsa kamar wane basarake duk da dai shi ‘din jinin sarautar ne sai dai ba don sarautar yake wannan takun ba sai don hakan ya zama tamkar a jininsa ne, naturally halittarsa ce daga Allah. Fuskarsa ba walwala ko kad’an, sab’anin fuskar Ummeey da ta kasance cikin ma’daukakin farin ciki, yau burinta zai cika Turaki zai ha’du da Ayra, ha’duwar da take nufin abubuwa da dama kamar yarda ta ‘darsa a zuciyarta, ta san da wuya Turaki ya tsallake tarkon da ta ‘dana masa, ba namijin da zai k’i amsar Ayra a matsayin mata idan har ya yi katari da kallonta ko da kuwa sau ‘d’aya ne jal, balle a ce ya mata na biyu, tana da wani sirrin kyau mai fisgar zuciya da gangar jiki zuwa gareta. Jikinta da fatarta wasu irin halittu ne da ba su gama game duniya ba halittu ne da Allah ya zab’i ka’dan daga cikin mutane ya basu. Fara ce amma ba fari irin na India larabawa ko turawa ba, fari ne mai caku’de da wani sirkin brown colour da ya ha’da tata colour ‘din ta musamman, gogaggiyar fata mai kama da ta jarirai, gewayayyiyar fuska mai ‘dauke da hab’a mai kyan gaske da ta bada wani beauty point a k’asanta, hancinta a duk sanda ta yi murmushi sai karan hancin ya lotsa ga kyakykyawan ido mai ‘d’auke da wasu ‘dogon tawardar Allah daga cikin ainahin farin idon a guda ‘daya, girarta a tank’ware take irin tank’warawar da masu kwalliya suke yi. Ta ko ina Ayra ta cika mace ko a cikin mutanen k’etare da wuya a zak’ulo mai kyanta, balle idan aka yi duba da dirin jikinta doguwa ce amma ba sosai ba don idan ta shiga sahun irin zaratan matan nan zata iya zama gajeriya. Haka Hameeda ta cigaba da wassafo surar Ayra Gaya a idanunta tana sakin murmushi kafin su kai ga isa ainahin ‘d’akin da aka kwantar da ita. Bata sani ba hausawa sun ce daidan wani karkataccen wani ga Turaki duk wa’dannan abubuwan ba sune abin buk’ata a wajensa ba ya fi son Macen da ta amsa sunanta na Mace wacce ta rik’e mutuncinta ta kai budurcinta gidan Miji itace Matar aure, kuma itace abin tutiya da tunk’aho har ma da bugar k’irjin nunawa a matsayin Matarsa, to fa! Ko zai samu haka ga Ayra Gaya? _________ Tuni ta farka daga dogon barcin da likitan ya saka ta, idanunta ne kawai a lumshe tana saurararn yarda Zuciyarta take bata shawarwari kala-kala game da Kabiru da kai tsaye zata iya kiransa matsayin Mak’iyi ba Mahaifi ba. Sallamarsa da wani zazzafan k’amshin turaren da ta jiyo ha’de da muryar Ummeey shine abinda ya fa’dar mata da zuciya sautin bugun zuciyarta ya sauya daga sassauk’a zuwa nauyayya, cikin abinda bai fi second biyu ba ta janyo mayafin da yake saman kanta ta rufe fuskarta da shi, idan akwai wani abin halitta da bata son gani a yanzu to Ummeey ce da a halinta ma gaba ‘d’aya, tana sahun farko a mutanen da take wa kallon wa’danda basa son farin cikinta idan har zata ce sai an mata auren da bata so. Turaki kuwa kallo ‘d’aya ya yiwa gadon sai kuma ya ji zuciyarsa ta ‘dan buga da sauri, kafin ya yi azamar durk’usawa gaban Amma da ta masa wani irin kwarjini ya shiga gaisheta. Amma na sakin murmushi da jin dad’in ganin santalelen Mijin bugawa a jarida da yake shirin zama na Ayranta, farin ciki ya lullub’eta daga yanayinsa ta hango kamar zai yi tausayi, kamar zai rik’e mata Ayra rik’on gaskiya kamar zai nunawa Ayran soyayyar gaskiya da zata narkar da tata zuciyar ta fara son sa ko da bata shirya ba. (Mhmn, Amma bata san waye Turaki ba, Mage kenan mai kwanciyar ‘d’aukar rai) ya yi k’asa da kansa sosai yana tambayar jikin Ayran, duk k’ok’arin Ayran na son kada ta ji sautin muryarsa sai da ta ji sautin muryar ya daki kunnenta ya sake ninka mata fa’duwar gaban da take ciki, wato da gaske dai ita Ayra itace zata yi aure har ma yau ga ta ga namijin da yake shirin amsa suna Mijinta, ashe kuwa akwai gwarama don yarda ta sake jin labarin Mahaifinta ta sake tsanar Maza a zuciyarta don haka duk Mijin da zai aureta sai ta sauke duk wani fushi na Mahaifinta a kansa, ba zata bijire ba a yanzu burinta ta farantawa Amma rai ko da hakan na nufin ita zata dawwama cikin bak’in ciki ne, Amma ta sha wuya bai kamata kuma ta k’ara mata wani b’acin ran a kan wanda take ciki ba, a hankali cikin zuciyarta ta ce “Zan yi Biyayya Ammaty.” Tana fa’da wasu hawayen bak’in ciki suna gangarowa a zuciyarta. “Barci take ne?” Maganar da Ummeey ta yi ya sata saurin sake runtse ido, sai kuma ta ji Amma ta ce “Ai tunda kika tafi ma bata tashi ba, sai dai ko a tasheta ko don su gaisa da Turaki.” Gaban Ayra ya fa’di sosai kafin ta ji Ummeey ta ce “A’a, ba sai kin tasheta ba, gudun me ake? Abinda Doctor ya ce a barta ta tashi da kanta, ki kyaleta ko gobe ya dawo.” Ayra ta saki ajiyar zuciya a hankali, Tsaf Turaki ya ganta ta cikin bargon da take lullub’e yarda k’irjinta ya ‘d’aga sosai suma da hankalinsu a kanta yake za su ganta, sai dai da yake shima ‘din ba a gabansa take ba sai ya tab’e baki yana mik’ewa ya kalli Ummeey “Zan je, saboda ina son zuwa gidan Alhaji daga nan zan turo Driver ya ‘d’auke ki.” Ummeey ta jinjina kai “Hakan ya yi, ka gaisheshi.” Alhaji shine wan Babansa da yake ba ya haihuwa to yawanci Turaki yake ‘d’auka a matsayin ‘dansa so yake masa sosai fiye da A.S da ya kawo shi duniya. Amma ta bi bayansa da kallo tana sakin ajiyar zuciya, hankalinta a yanzu ya kwanta ta san Turaki ta ko ina ba shi da makusar da Ayra da zata k’i amsar sa a matsayin Miji sai dai son zuciyarta. Ummeey ma kallon Amma take tana murmushi ta ce “Na so fa yau sun ha’du.” Amma murmushi kawai ta saki kafin ta mayar da kallonta kan Ayra da take mutsu-mutsu ta ce “Gobe ma rana ce, dole za su ha’du Ai.” ________ Rikici sosai Hameeda ta yi da S. Turaki a daren ranar, yarda ta burkice masa ya tabbatar da gaske take duk abinda ta fa’da ‘din har k’asan ranta. Duk da zuciyarsa na son bujire mata amma ya kasa k’ok’arin hakan sakamakon soyayyar da yake mata, ba zai iya rabuwa da Hameeda ba a kan wani dalili mara tushe don haka ya runtse idanunsa yana fa’din “Enough Malama!” Hameedah ta yi tsit da ‘dan bakinta tana sauke idanunta a kansa, farin ciki ya kusan kasheta ganin da burin nata ya kai inda take so, ta cigaba da haske shi da idanunta da suke mata garkuwa a duk sanda ta nufi tashin hankalinsa. Sosai kallon ya yi tasiri a kansa murya a cunkushe ya ce “Saboda maganar aurennan kika amincewa rabuwa da ni?” Ta ‘d’aga kai tana sake bawa kanta k’warin gwiwa duk da ta ji kunyar amsar da ta ba shi amma bata son ya ga lagonta. Ya saki murmushi kafin ya ce “Ina guje miki ranar da na sani Hameedah, saboda na ji a majiya mai tushe yarinyar nan Karuwa ce, ita kike son ki ha’da da Turaki, yaron da ya saka a ransa ba zai zauna da Matar da ba ta kai masa budurcinta ba, ashe kin shirya ruguza zumuncin naku ke da k’awarki, don ina tabbatar miki Turaki ba zai k’i sakin y’arta ba in dai ta gagara kai masa mutuncinta, a lokacin da wani ido za ki kalli Talatu? Don haka maganin kar a yi kada a fara, amma idan fa kin ji.” Hameeda ta yi shiru cike da nazari tana tsoron ranar da Turaki zai bata kunya, amma zuciyarta ta k’i amincewa da janye maganar auren, don haka murya cike da dauriya ta ce “In sha Allah hakan ma ba zata faru ba Abbu.” “Idan kuma ta faru kada ki sako Abbu a ciki.” S.Turaki ya fa’da yana tsatstsareta da ido, so yake ya karya lagonta yasa ta amince ta janye maganar auren da bakinta don shi sam har a zuciyarsa baya son auren, amma ya lura zuciyar matar tasa ta kai mak’ura bai hango zai iya samun nasara ba. Ta sake ‘d’aga kai cike da k’warin gwiwa ta ce “Na amince.” Ya ‘dan jijjiga kai “Shikkenan, Allah ya kai mu jibi a ‘daura aure, amma duk abinda ya biyo baya ki kuka da kan ki ba ni ba.” Da wani irin farin ciki ta kai masa kyakykyawar runguma tana jaddada masa godiyarta a kunnensa. ___________ Kashegari kam sosai jikinta ya yi sauk’i bayan ta sha Allurai da k’arin ruwan likita. Zuciyarta ta yi sauk’i sosai daga nauyin da ta yi, ta samu confidence sosai na tunkarar abinda take son aiwatarwa game da Mahaifinta, a yanzu ne zata shayar da shi mamaki zata nuna masa Talatu ta haifi mai share mata hawaye, sai ta sanarwa duniya waye shi? Sai ta sake k’ara masa wani ciwon fiye da wanda yake ciki ba mamaki ma abinda zata aiwatar ‘din ya zama ajalinsa sanadiyyar bugawar zuciyarsa. Da murna duk y’an uwanta suka tareta tun daga bakin gate, don ba su bar gidan ba, suna jiran a ‘daura aure a kaita gidanta, tunda duk wani budiri Amma ta sauke shi ta ce a bar shi tunda Ayran ta nuna bata ra’ayi. Ta dinga bin su da kallo tana sakar musu Murmushin da kai tsaye za su iya kiransa na dole. Majeedah ta jata jikinta suka isa har cikin Falo, inda anan aka zauna ana wasa da dariya duk don su sake ‘debe mata kewa. Ita dai da ido kawai take bin su ba tare da ta tofa tata ba, maganar auren da aka ce za’a ‘daura mata gobe shine abinda yake tada mata hankali, sai dai ta shanye ta daure duk don gudun b’acin ran Amma, da ta lura tana farin ciki idan ana maganar auren. _________ Sosai k’ofar gidan ya cika mak’il da y’an ‘daurin auren musamman kasancewar a yanzu su Ayran sun yi suna, ko don zamowar companynsu na T.Gaya da ya shahara a sassa daban-daban a k’asar nan, dama k’asar da take mak’oftaka da Nigeria. Taje sumar kansa yake yana sake mayar da kallonsa a kan hoton aljannarsa da ta kafa masa ido kamar kallonsa take a zahiri. Ya saki murmushi a karo na biyu yana sake ‘daukar hoton ya sanya a jikinsa murya a k’asa kamar mai magana da mutum ya ce “Ko ma me ya faru ke kika jawo Angel. Me yasa kika k’i tsayawa mu yi magana a airport da tuni haka bata faru ba, ga shi nan kin saka ina ta bulayin nemanki ban sameki ba, dalili ban san sunanki ba..” Sai kuma ya mayar da kallonsa kan hoton Matarsa Hibba da yake sakar masa murmushi ya kai hannu ya shafa fuskarta “For ever ke ce Sirri na Hibbateey.” Ya saki ajiyar zuciya yana tunanin aure a karo na biyar bayan rasuwar matarsa, wannan ‘din ma still ya tabbatar ba in da zai je. Ya yi saurin fesa turarensa ha’de da saka hula ganin lokacin ‘daurin auren har ya kusa shigewa, ga waya abokansa suna ta kiransa. ______________ Kicin-kicin ta yi da fuska tana kallon Dijah da Aysha da suke tsaye a kanta fuskokinsu kamar su yi kuka da alamun rok’o a kan fuskokinsu. Aysha ta zauna a gefenta tana dafa ta ka’dan cikin sanyin murya ta ce “Haba Ayra Please wace amarya kika tab’a gani ta zauna haka ranar ‘daurin aurenta, ki daure ki saka kayan nan ki fita cikin mutane a gaisa Amma zata yi farin ciki da haka.” Ta ‘dago idanunta tana kokawa da hawayen da suke son zubo mata don ta yi alk’awarin ta daina zubar da hawayenta a banza, murya a dashe ta ce “Dama don farin cikin Amma nake zaune har yanzu a gidan nan, ban da haka da tuni kun da’de da nemana kun rasa.” Aysha ta lumshe ido “Hakane, mun sani yanzu ma don Farin cikin Amma ki shirya kada angwaye su zo su gan ki haka ne kike so mu ce da jama’a.” Ta yi saurin ‘dago kanta “Kin fa’di abinda zai saka ni ba zan yi wankan ba balle na saka kayan in dai don wannan mutumin ne.” Tana fa’da ta mik’e ta isa bakin window zuciyarta na tafasa ta kafawa dandazon jama’ar da suka zo shaida ‘daurin auren ido ciki kuwa har da y’an jarida, tabbas a yanzu ne take da dama a yanzu ya kamata ta samu damar da take nema. Cikin zafin nama ta jiyo jin an dafata sai idanunta suka sauka cikin na Amma da ta kafa mata su, da sauri ta rusunar da nata idanun don ba zata jurewa kallon da Amman take mata ba. “Ki shiga ki yi wanka.” Amma ta fa’da mata da kakkausar murya mai nuni da ta fara gajiya da halin Ayran. Zuciyarta kamar ta buga haka ta shiga Toilet ‘din a daidai lokacin da ta ji wani marok’i ya fara sanarwar An ‘daura auren Shuayra Kabeer Gaya da angonga Al’amin S Turaki. Cak numfashinta ya tsaya na wuncin gadi ta dinga jin amsa kuwwar maganar a cikin kunnuwanta, da kyar ta watsa ruwa ta ‘daura ye jikinta ta fito tana jin kamar ta kifa don rashin k’warin jiki. Shikkenan yau ita Ayra ita ce zata amsa sunan Matar Wani…. Ashe ranar zata zo ranar da take gudunta ko da yaushe sai da ta rusketa, ana cewa ranar aure ranar farin ciki ita kam gareta tabbas wannan shine ranar bak’in cikinta….. __________ Ana gama ‘daurin auren kowa ya watse dai ‘dai’daikun abokan ango da suka tsaya ganin Amarya. Ayra tana zaune kan sallaya inda ta idar da sallah tana rok’on ubangiji ya bata nasara a kan abinda take shirin yi a zaman aurenta, Allah yasa ya amince ya yarda da k’udirinta na sakinta kamar yarda take so. Ta ji an turo k’ofa da sauri ta ja nik’ab ‘din fuskarta, tana jin yarda yanayin bugun zuciyarta yake k’ara k’arfi, ga wani turare da ya ki’dima mata hancinta, bata kai ga tambayar waye ba, ya k’araso d’akin cikin wata irin tafiya kamar ‘dawisu ya zuba mata idanu ganin yarda take sake k’udundune kanta a cikin Hijabi, murya a shak’e kamar wanda aka yiwa dole ya ce “Mik’e, ki kuma zare wannan bak’in abin na fuskarki kowa ya ga munafukar fuskar da ki ke b’oyewa…” Ras gabanta ya fa’di ganin tana shirin b’ata masa lokaci da kansa cikin zafin nama ya kai hannu ya fisge nik’ab ‘din…. JikarNashe✍🏽 Takaicin Uba…. NazeefahNashe✍🏽 31. 💔💔💔💔 Da zafin nama Ayra ta damk’i yankin hijab ‘din nata, bata son bayyana fuskarta a wajensa balle ta kalli fuskarsa da ta kira mummuna duk da bata ganta a zahiri ba. Furucinsa gareta shine abinda ya tsaya mata a mak’oshi. Ya bi kyawawan yatsun nata masu kama da na jarirai da kallo kafin ya sake azamar fincike Hijabin da k’arfin gaske, lokaci d’aya zuciyarsa ta tsaya cak daga bugun da take ya tafi suman wuncin gadi sanda ya yi arba da fuskarta, fuska ce da ba zai tab’a mantawa da ita ba, fuskar da ta tsaya masa a zuciya shekaru takwas da suka shige, sanda idanunsa suke a bu’de ita kuma na Ayra a runtse suke don bata son ganinsa mutumin da a karo na farko za’a kira shi da suna MIJIN AYRA… Tsawon lokaci yana aikin kallonta yayinda duk wata soyayyar da yake mata take zagwanyewa take zama k’iyayya da matsanancin jin haushi. ANGEL’ ya furta Sunan a saman harshensa, cikin sautin da shi kansa bai tabbatar na sa bane saboda a yarda ya yi furucin, Ayra ta sake rintse ido bayan jin saukar sautin sunan da ya kirata da shi cikin kunnuwanta, takaici ya k’umeta dama ta san da wuya idan ya ga fuskarta bai so ta ba, shi yasa take ta k’ok’arin b’adda kama kafin ya ganta ‘din, sai dai tana nata Allah na nasa sai ga shi karo na farko namiji ya tasa ta a gaba daf da daf yana k’are mata kallo, kallon da ta tabbatar na zallar sha’awa ne har yana wani kiranta da Angel. (Kash Ayra na ce Kash da za ki bu’de idanunki ki ga yarda Turaki yake miki kallon tsana da k’yama da kin k’arya ta kalaman ki.” “Kyan ‘dan Miciji..” Turaki ya furta a fisge cikin mabayyanin b’acin rai, idanunsa suka jirkita zuwa wani launi daban mai cike da nuna zallar jin haushin Ayran. Ya sakar mata Hijabin yana sake kallon fuskar hoton da yake kan wayarsa kafin ya saki mabayyanin tsaki ya ce “Na yi dana sanin ha’duwata da ke a yau, na yi kuma Takaicin da ya zamo ke ce Matar da aka aura min, ban da umarnin Mahaifiya a yau Zan sake ki saki uku.” Da sauri Ayra ta ware idanunta a kansa, idanun nasu suka gamu a lokaci guda ba tare da sun shirya ba, ji ta yi ba zata iya k’yale kalamansa ba ba tare da ita ma ta tofa nata ba, ita fa dama ta sani Maza duka halinsu ‘d’aya ga shi nan tun a ranar farko daga ‘daura aurensu zai bayyana mata halin y’an maza ai kuwa daidai take da shi. “Da igiyar a hannuna take da ko minti biyu aurenka bai cika a Kaina ba, kamar yarda Biyayya ka yi nima ina tabbatar maka biyayyar na yi, Biyayya Mai cike da taken ‘daukan fansa, ban shirya aure ba ban kuma ‘dau kowane namiji a bakin komai ba banda Karen farauta na, da ina da iko duk mazan duniya sai na mayar da su bayin Mata, tunda kun zubar da darajar da Allah ya baku, abu na k’arshe da zan gaya maka ba kowacce banzar magana Ayra Gaya take ‘d’auka ba….” Ta fa’da tana zabga masa kallo mai cike da tsana da Takaici iri-iri, da gaske ji take kamar ta tashi ta rufe shi da duka. Yarda ta ta zuciyar take haka shima ta sa take zafi da tafasa fiye ma da tata, takaicinsa na farko yarda yake fatan ganin Angel nitsatstsiyar mace ba haka ya sameta ba tunaninsa a yarda ya ganta da shigar kamala da hijabi har k’asa bai yi zaton zai samu tambarin karuwanci a kanta ba. Kullum addu’arsa Allah ya ha’da shi da Angel su yi aure ta haifa masa yara masu suffarta da kamalarta ku san duk wanda ya san shi da Aljanarsa har Aman da yake k’arami ya san burin Dadansa na ganin Angel har idan yana so ya masa abu yaron ya kance Allah ya baka Angel Dada, sai ga Angel ta zo masa a yanayin da yake k’yamatar duk wata Mace. B’acin ransa ya cigaba da hauhawa da ya gano itama ba son sa take ba sab’anin wa’dancan Matan da suke masa masifar So. Ya mik’e cike da izza yana sake bin ta da kallo kafin cikin cunkushewar murya ya furta “Barkanki, Allah ya taimakeke da ba kya son auren, dama duk wasu tamba’daddu Ai ba su fiye son a aurar da su a killacesu ba, dalili saboda ba za su samu damar huld’a da kowane karabitin namiji ba, ki k’addara gidan Turaki kamar Prison ne. Gwara ma tun farko ki san yarda kika yi kika bijirewa auren nan cikin sauk’i don ni ban shirya zama da Karuwar da mutane suka santa a kan Karuwanci ba…” Cak numfashin Ayra ya daina tafiya yarda take so, wani abu ya zo ya tokare mata zuciya Karuwa! Yau ita ake kira da Kalmar Karuwa ta bud’e baki zata yi magana sai dai kafin ta furta komai ta hango shi ya fice a zafafe har yana bugo mata k’ofa da k’arfin gaske. Da sauri ta mik’e tana shirin bin sa ta ci masa mutunci Majeeda ta shigo ‘d’akin nata tana ‘dan sakin murmushi. “Amarsu ta ango!” A zafafe Ayra ta ‘dago tana kallonta kafin wasu hawayen bak’in ciki su shiga suntiri a idanunta murya a k’untace ta ce “Yaya Majja bana so please!” Daga haka ta koma Kan gado ta kwanta tana tunanin a yanayin da zata shiga gidan wancan mutumin mai amsa sunan MIJINTA! Abu ‘daya da ta yi farin ciki da shi ta san ba zai wahalar sakinta ba tunda ta hango bahagowar tsanarta a idanunsa mai caku’de da jin matsanancin haushi ba tare da ta san laifinta garesa ba, illa son zuciya da ya bi wajen saka mata sunan Karuwa! Kalmar da take fita bisa gaskiyarsa har k’asan zuciyarsa, ya zama wa jibi ta nuna masa ita ‘din Karuwa ce kamar yarda aka fa’da ya ji ya kuma yarda. Sai a lokacin ta ji k’amshin turaren da ya bar mata a ‘d’akin ya addabi hancinta ta dinga jin rashin da’din turaren har k’asan ranta. A zafafe kamar kuma yana ‘dakin ta mik’e da azama tana hararar in da ya zauna, kafin ta ‘d’auko nata turaren ta fara feshe ‘d’akin da shi, da niyyar nata k’amshin ya rinjayi nasa ko hancinta ya huta da shak’ar k’amshin nasa mai saka ta dinga tuna mummunar fuskarsa. Ga mamakinta kamar turi ta yiwa na sa turaren don ba abinda ya ragu sai ma k’ara k’amshin da ya yi a ‘dakin. Majeedah dai na tsaye tana bin ta da murmushi k’asa-k’asa don sarai ta fahimci abinda take nufi. Wannan zarka’de’den mijin ta san lokaci ka’dan zai sace zuciyar Ayra, yanayinsa na kamun kai da nutsuwa Uwa uba kwalliya da fasali mai kyau irin na cikakkun maza ya isa ya fisgo hankalinta garesa. A zuciyarta ta ce “Dama kin daina wahalar da kan ki yarinya, k’arewar shak’ar k’amshin turarensa nan da sati guda za ku zama k’ark’ashin inuwa guda zan ga kuma ga uban da zai hana shi kusantarki. A zahiri kuwa murmushi ta saki ta ce “Sai ki tashi ki fita a gaisa da mutane tunda Dodon naki ya tafi.” Ayra ta yi burus da ita kamar bata fahimci mai take cewa ba. Tunda ya samu ya fice daga gidan ya saki jin yanayin zuciyarsa ya cigaba da zafafa, Ina ma duk abinda ya gani mafarki ne, ba Angel ‘dinsa bace, da k’yar ya samu ya isa inda motarsa take abokinsa Kamal yana jiransa. Bai bi ta kan kallon da Kamal ‘din yake masa ba, ya fa’da motarsa da sauri ya zauna a mazaunin Driver yana kallon Kamal a zafafe ya ce “Zaka shiga ko na yi gaba?” Kamal ya saki ‘dan murmushi kafin ya bu’de motar ya shiga yana fa’din “Su kuma sauran mutanen da ka bari a tsaye suna jiranka su maka Allah ya sanya alheri fa?” “Su nemi Uban da ya gayyato, look Kamal bana son magana please and please!” Kamal ya saki murmushi yana fa’din “Mhnm, ba ni na kar zomon ba…” a guje ya finciki motar bai tsaya ko ina ba sai a gidansa da yake Riba’do Road. Bai saurari Kamal da yake masa magana ba illa cilla masa key ‘din motar da ya yi ya fad’a cikin gida yana fa’din “See you later.” Kamal ya bi shi da kallo sam bai damu ba, saboda a karo da dama irin halin da abokinsa yake kasancewa kenan, a duk sanda aka ce an masa aure tun bayan mutuwar matarsa, sai dai na yau ya fi na kullum don daga ganinsa a harzik’e yake harzik’in da ya bayyana har a saman k’wayar idanunsa. Kasa kai kansa ‘d’aki ya yi, ya ci burki a falonsa. Kwanciya ya yi kan carpet idanunsa runtse yana tunano a sanda ya fara ganinta sanye da dogon Hijabin da ya mata kyau, ha’da idon da suka yi da saurin turo bakinta alamar k’unk’uni tana jan nik’ab ‘d’inta duk ba su b’ace daga kansa ba, suna nan zaune ra’dam a zuciyarsa kamar yanzu abubuwan suke faruwa. Ya sha mafarkinta a matsayin matar da yake so, ya sha mafarkin shine mijin da zai amshi budurcinta ashe wasu banza ye can sun amshe, bai san da maza nawa ta yi mu’amala ba abinda yake assasa bak’in cikin zuciyarsa kenan. Ya sake bu’de pic ‘d’inta a wayarsa samun kansa ya yi da zabga tsaki da cilli da wayar ya tura hannunsa cikin gashin kansa a hankali yana jin kamar ya saki kuka ko ya samu sauk’in zuciyarsa… 💔💔💔💔 Kabiru ya dinga bin Kamilu da kallo da goro da alawar hannunsa, muryarsa a raunane ya ce “Kamilu an ‘daura ko?” Kamilu ya ‘daga kai yana washe baki ya ce “Ai Auta ta yi goshi, manyan mutane ne suka aureta don baka ga cikar da aka yi ba, a idanuna dai na ga manyan gwamnati masu rik’e da manyan mak’amai duk sun halarta.” Kabiru ya sunkuyar da kansa yana jin k’wallar da take shirin zubo masa ta fara zuba ba k’akk’autawa, takaicin kansa da dana sanin abubuwan da suka faru a baya suka dinga bijiro masa, ji yake da yana da iko da ya mayar da bara bana, tabbas da ya dawo da rayuwarsu ta baya ya nunawa Talatu tsananin Soyayya ya kuma so abinda za ta haifa ko da za su kasance Mata ‘dari ne. Fitowar Karima daga ‘d’aki cikin zafin rai ne yasa Kamilu fasa fa’dar abinda ya yi niyya. Kabiru ya dinga dubanta cike da takaicin yarda take masa abubuwa kamar ba Mijint aurenta ba, yaranta mazan da yake tunk’ahon ta haifa masa sun zama sam ba su da amfani tunda ba sa tausaya masa sun kuma raina shi matuk’ar raini musamman suka bi turbar da nahaifiyarsu ta ‘dora su na shi ‘din ba Uba bane na gari kuma kaf ‘dawainiyar gidan ita take yi. Ya dinga tunanin irin gatan da ya dinga musu a lokutan baya ya mayar da y’ay’an Talatu ba komai ba don kasancewarsu Mata sai ga shi yanzu sune suka zama wani abu, sune suka zama y’ay’an da za’a kalla a yi alfahari da su ba wa’dannan da ba su da tarbiyyar arziki ba. “Auren wa aka ‘daura? na ji ana ta kambama Mijin a baki kamar wani shugaban k’asa.” Kamilu ya bita da kallon banza, kamar yarda ya saba a duk sanda za su ha’du, bai bata amsa ba illa mayar da kansa kan Kabiru da yayi ya ce “Kana ji ko Yaya? Idan an kwana biyu In sha Allah daga can Gayan za mu yi gangamin zuwa kaf ahalinmu mu bawa Talatu hak’uri, duk da mu ma mun yi kuskure mun cutar da ita da yawa a rayuwa haka za mu toshe kunnenmu daga dukkan abinda zata ce mana….” “Ahayye cas! Kace dai kawai shegen kwa’dayinku za ku je ku nunawa Talatu, saboda rashin zuciya In sha Allahu sai ta muku korar kare… arzikin nata na karuwanci da ba’a san asalin ungulu bane sai a ce daga masar take.” Kamilu ya tab’e baki yana kallonta “Don uban mutum ya ce Ungulun ba fara bace mana, kin ga Karima idan kina jin y’an rashin mutuncinki ki daina tsunduma Kamilu a ciki, don ni ba k’aramin aikina bane na b’atar da mace Wallahi shima Yayan shi ya ga zai iya kayan rashin mutuncinki. Kuma zuwa gurin Talatu kamar mun je idan ma Maular ne za mu je a hakan tana da abinda za mu Maulatan ne, gayyar tsiya arna a idi.” Ya mik’e a zafafe yana fa’din “Yaya Allah ya k’ara sauk’i na bar bak’i a waje suna jirana.” Kabiru ya ‘d’aga kai yana sakin murmushi mai bayyana k’uncin da yake ciki “Nagode Kamilu, kace musu nagode da ziyarar da suka kawo min.” Kamilu ya saka takalminsa yana fa’din “Sai mun zo In sha Allah.” ______________ Tsaf Yayyen Amarya suka shirya gidan Amaryar da yake Riba’do Road sun kashe ku’di har da na mamaki kaya ne y’an turkey masu tsanar gaske aka zuba mata, gida ya yi ras da shi sai jiran amaryar da zata tare a ranar da daddare. Ayra kallonsu kawai take, tana tausaya musu yarda suke rawar jikin auren nan, Auren da ya sakawa suna Jeka na yi ka. Magribar Fari Amma ta shiga ‘dakinta ita da mai gyaran jikin da zata mata na tafiya gidan miji, bata yi musu ba aka gyareta tsaf sai tashin k’amshi take tamkar wacce aka b’arar da kwalaban turare a jikinta, ita kanta k’amshin har tsaya mata yake a mak’ogaro, haka aka na’deta cikin tsumammiyar laffaya fara tas da ita. Cike da sanyin jiki Amma ta zauna a gefen gadon cikin rawar murya da son kawar da kukan da yake son kufce mata ta ce “Ayra! Alhamdulillah Nagode Allah da ya nuna min aurenki, ba zan ce miki komai ba game da zaman aure na san kin san komai tunda ke ba jahila bace, sai dai ina neman alfarma‘d’aya a wajenki wacce itace cikamakin duka buri na da farin cikina Ki yi Min alk’awarin za Ki yiwa mijinki biyayya, biyayya da ake da suna biyayya kwatankwacin wacce na yiwa Babanki, kada ki ba ni kunya Ayra please kada ki yi abinda Mijin zai dinga kiranki da sunan y’ar Mace ki min wannan alfarmar Ayra don Allah.” Ta fa’da kuka na kufce mata kukan da take yi ba don komai ba sai don ta saka Ayra rauni a zuciya ta saka ta ta amince da alk’awarin ko da bata shirya ba. “Wannan ce kawai sakayyar da nake so ki yi min a matsayina na mahaifiyar da ta raineki ita ka’dai ba tare da Uba ba, cin ki da shan ki iliminki suturarki duk ni ce, ki tina irin k’alubalen da na sha a kan ku a rayuwa wannan ne kawai abinda nake so ki yi min…” Kuka ne ya kufce wa Ayra fiye da kukan da take yi, ya zata yi ? Ya zata yi da Umarnin Mahaifiyarta da take jin kamar ta k’ullla mata dabaibayi ne, kamar Amman ta shiga zuciyarta ta ga mai take k’ulla wa waccen mutumin da aka kira da sunan Mijinta. Jin tsananta kukan Amman tana fa’din “Na san ba zaki min wannan alfarmar ba Ayra….” Da sauri ta fa’da jikinta tana furta “Na miki Amma, na miki alk’awari ko da hakan yana nufin rusawa nawa farin cikin ne ko da hakan ya na nufin ajalina ne, zan masa biyayya irin biyayyar da kike so Ammatyyyyy….” Ta fa’da cikin wani irin gunjin kuka mai nuni da zallar zafafar zuciya…. Jikarnashe✍🏽 Takaicin Uba…. *Nazeefahnashe* ✍🏽 32. 💔💔💔💔 *INGANTACCEN ZANCE*. *Ina da INGANTATUN SAIWOWI na gyaran mejego ko amare*. *Haka uwargida ma ban barta a baya ba da irin nata tagomashin* *Kaya ne masu kyua ba garabiti ba* *SAIWOWIN itatuwane da basu da illah* *Da sau'ki zaki same su, amma aikinsu yawa ne dasu.* *Akwai hadaddun turaren wuta, da zai kawar Miki da karni da bashin damina*. *Kawai ki tuntu'bi wannan lambar dan samun gamshasshen bayani* *Nation wide delivery* *08032773332.* ✍️. Zan masa biyayya irin biyayyar da kike so Ammaty, zan masa girki da duk wani abu da ya danganci matar aure na gari,amma please kada alk’awarin da zan miki ya shafi gangar jikina don Allah Amma ba zan iya ba, ba zan iya ba!!” Amma tana murmushi ha’de da matsa hannunta ta ce “Za ki iya In sha Allahu zaki iya Ayra, idan har ya kusantoki ki amince masa shine amfanin auren, ba ki da ikon haramta masa jikinki Alhali ubangiji ne ya halasta masa ki yi hak’uri ki kuma dinga karanta Hasbunallah a zuciyarki, komai zai wuce da izinin Allah, ki kuma saka a zuciyarki ba duka maza bane halinsu ‘daya da yawa daga cikin maza halayensu sun farrak’a da na mahaifinki, ina ji a jikina biyayyar da kika mana ba zata tafi a banza ba, In sha Allah kin dace da mijin k’warai Ayra, kamar yarda na dinga rok’on Ubangiji na san kuma ya amsa In sha Allah ba za kuyi Boranci a gidajenku ba, za ku zama ababan So a wajen Mazajenku ababan tattali da nuna kulawa a kowane hali, ina ji a jikina kuma addu’ata ta amsu ki saka a zuciyar ki biyayya kika je gidan Mijinki, biyayyar da zata kai ki dukkan Matakin nasara Allah ya miki albarka ya sadaki da dukkan alhaiiran da suke cikin gidan aure, ya nisanta ki da sharrin da yake cikinsa.” Zuwa lokacin fa’dar yanayin da Ayra take ciki abin ba zai kwatantu ba, ta dai san k’irjinta ya yi nauyi, nauyin da bai tab’a yi mata ba ta dinga kokawa da numfashinta da yake fitar da k’yar. Kukan ma ya ‘d’auke tsam daga idanunta ba mamaki tashin hankalin ya zarce na fitar hawaye sai dai a dinga furzar da shi ta hanyar numfashi mara da’di, Da gaske ba zata iya ba ba zata iya ha’da makonci da wancan mutumin da ya kirata kai tsaye da sunan Karuwa ba! Tana ji tana gani a karo na farko a ka b’anb’are jikinta daga na mahaifiyarta Majeeda ta maye mata gurbin Amma ta tabbata dai ita Ayra yau zata yi sallama da Amma zuwa gidan Aure, abinda hasashenta ko mafarkinta bai tab’a kwatanto mata ba. Amma ta damk’i hannunta ta rakata har mota tana tofa mata addu’oi masu mahimmanci daga bakin Uwa wacce ta amsa sunanta UWA TA GARI. Sai da ta saka a cikin mota sannan ta juyo karo na farko tana sakin nata murmushin mai tafe da ajiyar zuciya da hawaye masu ‘dimin gaske, tana murna da auren Ayra a wani b’angaren kuma tana takaicin rabuwa da Ayra mafi soyuwa a cikin y’ay’anta. Ta saka hannu tana share hawayen ha’de da fa’din “Khairan In sha Allah” Jikinta a salub’e ta koma cikin gidan zuciyarta cike fam da tunanin ko wane irin zama Ayra zata gudanar a gidan Mijinta duk da dai ta yiwa abin riga kafi ta hanyar saka ta yi mata alk’awarin da ta tabbatar ko da Ayran zata wahala sai ta cika mata shi saboda yarda ta san yake darajata fiye da kowa a duniya haka take girmama zancenta fiye da na kowa a duniya. *** Tas suka sake gyare gidan suka ba’deshi da turarukan wuta. Kafin Majeeda ta ciro kwalbar Humra tana murmushi ta ‘dorata a kan mudubinta, ita ka’dai ta san tarkon wannan Humran mai gigita maza kenan da zarar mace ta yi amfani da ita to fa namiji bai isa ya tsallake tarkonta a wannan daren ba, Sirrin mutanen Chadi kenan daga wajen Anty na Surayya dee marubuciyar Halin yau, gida ya ba’de da K’amshi musamman sun san Ayra ma’abociyar son k’amshi ce kada ma na bare bari ya ji labari da na turarukan OUD. Suka sake mata nasiha duk da sun san bai zama lallai ta amshi irin wannan nasihar ba sai dai nan gaba zata yi mata amfani lokacin da za su daidaita da Mijin. Gida fa ya yi tsit, an bar Ayra daga ita sai halinta. Ranta a b’ace ta janye lullub’in abayar da yake jikinta ta fara bin ‘d’akin da kallo da ya ji set ‘din fararen furnitures farare k’al da su, sai ratsin ash (ruwan toka ka’dan) ta mik’e a hankali tana zagaye ‘d’akin kamar mai son ganin wani abu, sab’anin haka zuciyar ce a cunkushe ta rasa kuma mai zata yi ta samu sauk’in nauyin da k’irjinta yake mata, Ta faru dai ta k’are ita Ayra Gaya yau aka yiwa aure, auren da ta taso da adawarsa a ranta. __ A daidai lokacin da take cikin wannan yanayin, shima ango yana can gaban Ummeey ransa a matuk’ar b’ace shi ka’dai ya san me yake ji a zuciyarsa Ga soyayyarta ga kuma k’iyayyarta ga Jin Haushinta duk sun taru sun caku’de masa a zuciya. Ji yake kamar ya fasa kuka. “Tashi ka tafi Turaki, ka bar y’ar mutane ita ka’dai a gida abu ‘d’aya zan sake jaddada maka Ka ji tsoron Allah! Ka kuma amshi matarka a duk yarda ka sameta budurwa ko akasin haka kada ka ja da ikon Allah, ba mamaki ka sameta a yanayin da baka so ba to ka saka a zuciyarka k’addara ce ba kuma da son zuciyarta komai ma ya faru ba, please kada ka fake da hakan ka sakar min y’a, duk da nima ban tabbatar ba amma labarinsu Akwai rikitarwa komai ma zai iya faruwa ba abin mamaki ba ne, a halin da suka taso please ka taimakeni Turaki kada ka ba ni kunya.” Kansa ne ya sara sosai ya ‘dago yana sauke jrikitattun idanunsa a kan na Ummeey da gaske kenan ta san Yarinyar Karuwa ce Amma ta amince da auren su, ya ‘dan cizi k’asan leb’ensa kafin ya mik’e a kasalance yana ha’da hanya ya nufi k’ofa, sama-sama ya jiyo muryar Ummeey tana fa’din “Tsaya Ga abincinku ka tafi muku da shi, sawa na yi aka girka muku don na san yau gaba ‘dayanku ba wanda ya Saka loma a bakinsa, kun kasa yarda gata muka yi muku nan gaba za ku ga amfanin hakan. Allah ya tashe mu lafiya.” Ta fa’da tana damk’a masa Kwandon abincin a hannunsa. Ya d’auki mintuna biyar a cikin motar ya kasa Driving ‘din, gaba ‘d’aya ransa dama a jagule yake ga Ummeey ta sake k’ara masa wani tashin hankalin ta tabbata dai da gaske ne disvirgin ce ya runtse idanunsa kafin ya tada motar cikin kasala ya nufi hanyar gida. Yana isa Gida wanka ya shiga ya da’de cikin ruwan da ya sakarwa kansa kafin ya fito jikinsa saye da bath robe yana tsane gashin kansa da towel. Tsaf ya shirya cikin wasu kayan barci na companyn Hilfiger ya feshe jikinsa da turaruka na musamman. Duk da yunwar da take na’de a cikinsa haka ya yi nufin kwanciya yana runtse idanunsa sai dai ina yunwa ta ce bata san wannan ba abinci kawai cikinsa yake buk’ata Ga shi bai fiye son abinci mai nauyi da daddare ba. Tsaki ya ja sosai kafin ya mik’e niyyarsa ya je kitchen ya samu abinda zai ci. Daidai lokacin Ayra tana tsaye a Kitchen sanye da Riga da wando na barci da suka tsaya mata iya cinya sai y’ar hula da ta saka a kanta, har ta saka hijabi don tsoron ha’duwa da shi sai ta tuna sunan da ya kirata da shi, don haka ta cire Hijabin ta wurgar gwara tun yau ta fara nuna masa ita Karuwance, a duk inda a ka san Karuwa kuwa an san bata da kunya. Cak ya tsaya daga bakin k’ofa yana k’arewa sassan jikinta kallo zuciyarsa tana wani irin bugawa da sauri kamar zata fisgo ta fito daga k’irjinsa, tunda yake bai tab’a katarin ganin Mace mai cikakkiyar sura irin tata ba, ya runtse idanunsa kafin ya bu’de ya sake saukesu a kanta, daidai lokacin ita kuma ta juyo jin kamar ana kallonta da sauri ta rik’e cup ‘din Lipton ‘din da yake hannunta da ya yi niyyar sub’uce wa saboda yarda idanunsa suka yi tasiri a kanta. Sai a lokacin ta ji haushin kanta na yarda ta bari wani banza na kalle mata jiki a banza, duk da dai dama bai cancanci ta ji kunyarsa ba wanda ake so Ai shi ake jin kunya. Da sauri ya ‘d’auke Kansa zuwa inda fridge yake Hakan ya bawa Ayran damar ‘daukar Mug ‘dinta ta fice da sauri. Ta gefen ido yake kallon fitarta da yarda duk wata sura ta take a bayyane, tuni duk ya bi ya rikice mazantak’ar ta motsa gefe ‘d’aya na zuciyarsa kuma yana tabbatar da karuwancinta ta yarda rana guda a daren farko ta iya fitowa da wa’dannan fitsararrun kayan, idan ba Karuwa na wace zata aikata haka? Ya saki dogon tsaki yana k’ok’arin jona kettle don tafasa na sa tea ‘din. Yarda yake zaune a bakin gado yana sipping hot tea ‘din a uzurce idanun sa a kan t.v d’in da take kafe a bangon d’akin sai ka zata kallon yake sai dai ina ba kallon bane a gabansa surarta ce kawai take amsa gizo kamar wani aikin asiri. Ya ja tsaki a zuciyarsa yana raya da gangan ta yi daman ta yi ne don hakan ta faru da shi ya zama dole ya je ‘d’akin ya nuna mata Shi jikinta baya gabansa, Jikin da maza da dama suka gama banbance sirrinsa da shi zata yaudareshi Ina ba dai shi jikar Turaki ba dole ya gaya mata bata gabansa ya mik’e a zafafe yana fa’din “In dai ni ne ko sha’awarki zata hallaka ni ba zan kusanceki ba, ina da Kishi, kuma shi zai ja na kasa kusantar ki tunda na Riga na san wasu can sun shiga k’ofar da ba ni na fara bu’de ta ba.” Ya bu’de k’ofar ‘dakinta da azama kamar an jefo shi, daidai lokacin da Ayra ta yi wani kyakykyawan juyin da ya kusan sumar da Turaki a tsaye, ta kafeshi da idanunta ha’de da fa’din “Malam Lafiya?” Sai da ya ha’diyi kakkauran yawu kafin ya ce…… *Jikarnashe✍🏽 Takaicin Uba…. Nazeefah Nashe✍🏽 33. 💔💔💔💔 “Lafiyar kenan.” Ya yi furucin cikin dakewar murya, yana sake ‘daure fuskarsa tamau alamar duk zancen da zai mata da gaske yake from the bottom of his heart. Ita ‘din ma fuskar ta ‘d’aure sosai tana jan tattausan blanket ‘din da yake gadon don son suturta jikinta da ta ga yana wa kallon k’urilla. “Bar wani k’udundune jiki… jikin da ban san iya wa’danda suka kalleshi ba, ban san iya wa’danda suka tab’a shi ba.” Ya fa’da yana wani furzar da hucin b’acin rai “Ba abinda zan kalla a jikinki, kamar yarda ba abinda zan yi da mai jikin, idan ma dalilin da yasa kike bayyana shi kenan, ki k’addara a ranki Ni Turaki na fi k’arfin kusantar wannan k’azamin jikin naki, Turaki mai tsarki kuma kamilalle don haka dole ne wacce zata zamo Matar Turaki ta kasance kamilalliya ba irin ki ba, ki saka a zuciyarki duk ranar da na kusanceki kamar na damk’a miki takardar sakin aure ne don haka bar yaudarar kan ki da nuna min wannan jikin…” zuwa lokacin ya gama hassala zuciyar Ayra k’iris take jira ta fashe, ta dinga ha’d’iyar wasu irin yawu masu ‘dacin gaske, tana furzar da numfashi mai tururi mai nuna zallar hassalar da zuciyarta take ciki. Me wannan mutumin yake nufi? Waye ya gaya masa ita Karuwa ce? Ita ‘din da wani ‘da namiji bai tab’a rik’e hannunta ba, sai dai sanda wancan mummunan abin ya afku. K’ok’ari take ta ha’diye maganar sai dai ziciyarta ta kasa bata dama, dole ne ta furta masa mai ‘dacin da shima zai ji b’acin ran da take ciki. “Jikin Ayra Gaya, yafi k’arfin kowane karabitin namiji, Jikin Ayra ba shi da arahar da zata bari ka kusance shi,Jikin Ayra na mazan da suka amsa sunansu maza ne, ba na irin ku da kuke sakin Mata barkatai ko kuma matan suke guduwa da k’afarsu sabida rashin biya musu buk’ata ba, ba mamaki a tsaye kake namiji a ba’dinance kuwa muna Maza ne, ka je ka tambayi wa’danda suka gaya maka ina karuwancin da wasu kalar Maza nake yi? Maza jajurtattu, Mazan da suka amsa sunansu maza a zahiri da ba’dini.” Zuwa lokacin duk wasu k’ofofin jikinsa sun bu’de saboda tsabar b’acin rai, idanunsa sun jirkice zuwa wani launi daban mai bayyana hassalar zuciyarsa, ji yake tamkar ya keta ta k’arfin tsiya ya nuna mata yafi k’arfin ta kira shi muna maza. Bai san sanda ya kai kansa bakin gadon ba yana tsatstsareta da ido cikin b’acin rai ya ce “Banda wani dalili daban da yau na tabbatar miki da cewa Turaki Ingarma ne ya fi k’arfin wulak’ancinki, sai dai kash ba zan iya kusantar k’azamin jiki irin naki ba,ina sake jaddada miki duk ranar da na kusanceki ki tabbatar kamar na katse igiyar aurena guda da take kan ki na fa’da miki haka ne saboda ki tabbatar ba abinda zai burgeni a jikin ki ko da zan ganki (naked) tsirara a gaba na. Daga haka cikin b’acin rai ya juya a sukwane ya bar ‘dakin, ita kuma Ayra ta saki murmushi tana danna save a recording ‘din da ta saka, shikkenan ta samu hanyar rabuwa da wannan mutumin, tunda shi ya yi furucin da bakinsa sai dai fatan Allah ya kai mu lokaci! Ta fa’da tana sakin murmushi a hankali kuma ta ce Mu je zuwa yanzu wasan ya fara.” Ta furta a hankali tana rungumar filo cikin tsananin farin ciki. Ya da’de yana zagaye faffa’dan falon nasa mai girman gaske da ya ji adon farin painting da ash chairs da dinning set complete set dai na latest chairs na k’asar Turkey. Hannayensa sark’afe a baya yana bitar kalaman Ayra da suka zame masa tamkar Hadda. Da gaske ba mutumin da ya tab’a ba’ta masa rai kwatankwacin yarda Ayran ta masa yau, wani kishi ne yake nuk’urk’usar zuciyarsa da b’acin ran kalamanta wai shi ta kalla take kira bai isa namiji ba, ji yake kamar yaje ya mata irin kusantar da zata san suna da tazarar banbanci tsakaninta da mazajen da suke hul’da da su ya dinga kai mari yana kai gauro cikin tsananin takaici da bak’in ciki. Kafin ya yi k’wafa ya zare kayansa ya kwanta a kan hannayensa. Sai dai fa barci ya ce bai san wannan ba surarta ce ta dinga masa gizo cikin yanayin da ya ganta ‘dazu. Ya dinga juyi yana sakin tsaki akai-kai. (To fa! Anya Turaki hanyar daka ‘dauko mai b’ullewa ce? Kada fa masu supporting Ayra su mana dariya. Tohm ni dai ba ruwana) Da k’yar Ayra ta mik’e a safiyar ranar ba don komai ba sai don rashin samun isashshen barci. Bayan sallahr asuba kuwa tunda ta sheme bata sake motsi ba sai yanzu da ta dinga jin bugun k’ofa kamar a tsakiyar kwanyar kanta. Ta ‘dan saki guntun tsaki tana mik’ewa. Tattare gashin kanta ta yi da ya barbazu ta saka band ta ‘daureshi sannan ta zura hijabi akan rigar barcinta. Ta d’an fice da azama jin bugun k’ofar yana sake tsananta. A bakin k’ofar da zata sadaka da babban falon ta tsaya murya cike da alamun tashi daga barci ta ce “Wanene?” Daga can waje su Tasleem suka amsa da “Mu ne bu’de Sis Ayra.” Ta mur’da key ‘don ha’de da sakin murmushin da kai tsaye zata kira na k’arfin hali ita da kanta ta san a iya kan leb’enta ya tsaya. Su kuwa gaba ‘daya suka rungumeta cikin farin ciki har Aman da suka zo da shi ba’a barshi a baya ba wajen kai mata kyakykyawar runguma. Ta ‘dan shafa kansu cike da kulawa tana janye jikinta ha’de da zubawa Aman ‘din ido ko ba’a fa’da mata ta san jinin wancan mutumin ne, ta ‘dan tab’e baki kawai tana juyawa suka bita cikin falon. Zama suka yi a kan kujeru suka gaisa sosai kafin Ayra ta kalli coolers ‘din da suka dire a saman dinning ta saki ajiyar zuciya don dama da wata mahaukaciyar yunwa ta tashi, tana jin kuma k’iwar shiga kitchen ta yi girki. Ta mayar da kallonta kansu kafin ta mik’e ta ce “Excuse me don Allah, tashi na kenan bari na yi wanka na zo mu gaisa sosai.” Har ta tafi ta ji Aman ya ce “Aunt Dada fa?” Cak ta tsaya ta juyo da k’yar ta kalli yaron kamar zata masa tsawa sai kuma ta ‘dan saki tsaki a hankali ta ce masa “Do you know his room?” Ta furta cikin k’asa da murya sosai don bata son su Tasleem su ji. Aman ya girgiza kai alamar bai sani ba, Ayra ta saki tsaki ka’dan kafin ta ce “Oya Go and Sit down zai fito yanzu.” Daga haka ta juya da azama ta shiga ‘dakinta tana tsaki k’asa-k’asa “Ina ruwana da wani Dada da zaka tambayeni shi, Dado ba Dada ba.” Tsaf ta shirya cikin ha’dadden Swiss brocade ‘dinta, light pink pink mai adon blue ta taje sumar kanta ta kama kafa ‘daurin ture ka ga tsiya sosai ta yi kyau ba k’arami ba, musamman ‘dan bakinta da ya sha pink lip stick da ya sake bayyana tudun lips ‘din ka’dan kamar an dasa mata su. Cak ta tsaya tana kallon yarda ita kanta ta hango kyan da ta yi, tsoronta ‘d’aya kada wancan mutumin ya ce saboda shi ta yi. Ta saki tsaki tana fa’din “Ba don kai na yi ba, dama tun filazal kwalliya a jikina take.” Cikin wani irin taku mai bayyana zallar izza ga wanda ya kalleta kai tsaye zai fassarata ta isa falon da ta bar su. Cak ta tsaya daga bayan kujera cikin takaicin ganinsa a falon zaune suna hira da y’an uwansa cikin farin ciki, ga Aman a gefe yana ta zuba surutu. Ta ‘dan cije leb’e tana tab’e bakinta kafin ta ‘d’auke kanta kamar bata gan shi ba ta nufi dinning area. Abinci ta zuba sosai ta zauna ta nutsu ta fara ci ba tare da ta sake bi ta kan su ba. Tun wucewarta har zuwanta idanunsa a kanta yake k’asa-k’asa, yana mamakin zallar kyan da Allah ya bata amma madadin ta gode masa ta hanyar killace kanta har zuwa gidan Mijinta sai ta zab’i ballagazar da kanta a titi kowane banza yana da damar da zai kusanceta idan dai zai bata ku’di, gaba ‘d’aya sai ya ji ransa ya b’aci ransa ya yi duhu yana jin haushin kasancewarta macen da ya ‘d’au tsawon shekaru yana dakon soyayyarta. Sai Bayan sun yi sallahr azahar sannan suka ce mata za su tafi Yaya Turaki zai kai su gida. Har ta ce su gaida gida sai kuma ta ga hakan kamar bai dace ba, don haka ta dakatar da Tasleem da sauri ta koma ‘dakinta ta ha’da musu cosmetics ta basu, yaronsa kuwa komai ma ba zan ba shi ba balle ya ce saboda shi zan yi.” Ta yi furucin a fili tana kinkimar ledar ta fita. A bakin k’ofar motar ta tsaya Kuma jikinta ko mayafi babu don a tuaninta amfanin Nik’ab ‘dinta ya k’are. Amin Turaki ya saki tsaki ganin yarda gardener da Gate Man suka kafa mata ido a zafafe yarda su Tasleem ba za su ji ba ya ce “Ai gwara ki nuna musu jikinki a araha dama da irin su kika dace.” Kalmar ta shigeta sosai ta bu’de baki a zafafe zata gaya masa magana ta ga ya finciki motar a mugun speed ya ba’deta da iska ya tafi. Tana daga tsayen ta dinga gartsawa lab’banta cizo wasu hawayen da bata shirya musu ba suka fara suntiri a fuskarta. “Na rantse da Allah sai na rama.” Ta furta tana jin wani ciwo a zuciyarta ta koma cikin gida da sauri. Ta da’de cikin yanayin b’acin rai da takaicin mutumin da ko sunansa bata rik’e ba…. Sai dare sannan ya dawo, tun daga compound ya fara jin k’amshin abincin da take dafawa. Ya dinga jin yawun bakinsa yana tsinkewa tabbacin komai ma ake dafawa ransa ya kai matuk’a wajen son ci. Daidai lokacin tana tsaye tana shafe jikinta da sihirtacciyar humrar da Majeeda ta ajiye mata ba tare da ta san menene sirrin humrar ba, ta dinga ambulata har kamar tana shirin hawa mata kai, haka kawai ta ji k’amshin humrar ya yi mata har inda take so. Ta zura rigar half boubou da dogon wando don garin ana ‘dan zafi sosai. Da y’ar wak’arta ta shiga kitchen ‘din sai dai cak ta tsaya ganin yarda ya cika plate da abincin da ta dafa arabian spaghetti da Patoosh salad sai Bake fish a gefe mai ha’de da sauce na dankali. K’amshin Humrar da ya dirar masa hanci ne ya sa shi juyowa da sauri idanunsa a kanta tana tsaye ta rik’e k’ugu. Ya ‘dan tab’e baki yana mata kallon sama da k’asa yana jin wani abu yana ziyartar gab’b’an jikinsa wanda yake da tabbacin tsumammiyar sha’awarsa ce take son bujiro masa ta kowane hali. Ya ‘d’aga mata gira “Ya aka yi?” Ta bi plate ‘din da kallo murya a shak’e ta ce “Dalili?” “Gidana ne, kuma dolenki ne ki girka ki ba ni, kin ji da’di da ta nan fannin ba a yi failing ba.” Ya fa’da yana nuna mata abincin, a gefe guda kuma yana k’ok’arin controlling kansa da zuciyar da take ce masa ya je ya rungumeta ko ya samu sauk’in abinda yake ji, kamar wanda magana’disu yake jan sa zuwa gareta ya sauke idanunsa kan k’irjinta da suke masa dangwalaliya ta saman Riga, lokaci guda ya ja hannayensa ya ‘dora a kan… cak numfashinta ya tsaya cak ta waro idanunta a kansa….. Jikarnashe ✍🏽 Takaicin Uba… Nazeefah Nashe✍🏽 34. 💬 Kina nan kina lak’e-lak’e abin haushi tuni free page ya k’are, ga tafiya ta fara nisan zango Ayra da Turaki har an yi aure ana zuba badak’ala a gidansu duk kin kasa biya ki kwashi romon labari ana jiran a samu na banza. In dai kin cika mace da ta amsa sunanta mai aji biya 1k dubu guda kacal a watsaki a tafiyar y’an special people idan kuma kin ga ba zaki iya ba har yau k’ofa a bu’de yake ki biya 500 kacal na watsa ki sashen normal group. Ga ‘dand’ano ku karanta ku ji yarda labarin ya fara ‘daukar harami. Samu numberr marubuciyar don biya kai tsaye. 08033748387. Yanzu aka fara tafiyar mai nisan zango ce! 💔💔💔💔 Janye hannun nasa ya yi da sauri yana zabga mata harara ha’de da nuna mata ‘dan k’waron da ya mak’ale a kan rigarta mai kama da butterfly. A razane ta daka tsalle don matsoraciyace ta gasken gaske, k’ok’ari take k’waron ya fita daga jikinta shi kuwa yana tsaye yana k’are mata kallo, cikin dauriya da dake dariyar da take son kufce masa. Yayi folding hannayensa a k’irji yana kallon yarda take ihu, sai da ya ga abin nata ba na k’are bane gudun kada ta tara masa mutane sai ya yi tsaki, ya damk’eta da sauri yana saka hannayensa kan dukiyar fulaninta don son zaro k’waron da shige mata riga. Cak ta ji numfashinta na neman ‘d’aukewa bayan jin saukar tattausan hannunta a dukiyar fulaninta, shi kansa sai da ya yi azamar runtse ido lokaci guda kuma ya rik’e numfashinsa da yake k’ok’arin kufce masa jin wani yanayi da ya ritso gangar jikinsa tun daga yatsun k’afarsa har zuwa kwanyar kansa. Da azama ya janye gangar jikinsa daga rik’on da ya yi mata wanda ya janyo gamayyar k’irjinsu. Ya zabga tsaki yana fa’din “Matsoraciya!” Ya ‘dau plate ‘din da ya shak’e da abincin ya zaga ta gefenta ya wuce yana kallon yarda gaba ‘d’aya ta takure waje ‘daya kamar wacce za’a ce kyat ta gudu. Bayansa ta bi da kallo tana lumshe ido ita ka’dai ta san yanayin da ta ruski kanta a sanda ta ji hannunsa a jikinta abu ne da bata tab’a jin sa ba, yanayi ne da ba zata iya fasalta shi ba ta dinga jan ajiyar zuciya kafin ta bu’de fridge ta ‘d’au robar ruwan swan mai sanyi ta kafa a bakinta cikin wawuyar kwankwa’da ta shanye shi tas, da burin abinda take jin ya k’aurace mata, sai dai ina kamar sake rura wutar abin ta yi, cikin wata irin murya ta furta ‘Ya salam!” Kafin ta ja k’afafunta ta fice daga kitchen ‘din da kasalar jiki. Tana fita idanunsu suka gauraya cikin na juna yana zaune a dinning ya tasa plate ‘din a gaba, duk da soyayyarsa da abincin sai ya ji abincin gaba ‘d’aya ya fice masa a rai, abinda yake so yake muradi ya fi gaban abincin, ya bi bayanta da kallo yana sake sakin ajiyar zuciya ganin yarda komai na jikinta yake shaking kamar da gayya ma take aikata komai. Ita ‘din ma kwanciya ta yi akan gado ta kifa cikinta kan filo duk wani yanayi da ta tabbatar na sha’awa ne yana amsa kuwwa a jikinta, abinda bata tab’a ji ba, tana da feeling ko a gida amma bata tab’a wannan mahaukacin feeling ‘din ba. Ta dinga damk’ar filon tana jin kamar ta je ta kai masa kanta. Sai dai ina! Ba yanzu ba bata shirya fuskantar wulak’ancinsaba. Da k’yar ya tura abincin, amma loma biyar ya yi ya ji abincin ya gundireshi, shima ta tatan ya yi ya b’alle murfin ruwan ya kafa a bakinsa, bai kuma dire ba sai da ya shanye shi tas, sannan ya mik’e a kasalance yana ture plate ‘din abincin kamar shi ya masa laifi. Ya haye saman gidan inda anan part ‘dinsa guda yake. Kai tsaye ya shige toilet ‘dinsa ya sakarwa kansa ruwan sanyi yana tunanin ya zama dole ya yi nisa da yarinyar nan idan ba so yake ya zubarwa da kansa mutunci ba, duk da cika bakin da ya yi. Har ya saka pyjamas ya kwanta barci duk da ba barcin yake ci ba, amma a halin da ake ciki gwara kwanciyar shi ya fi alheri, ya kuma zama dole a gobe ya fara shirin barin k’asar nan kafin ya kunyata kansa a gabanta. Don ya tabbatar duk ranar da ya kai kansa gareta ranar sai ya sha gori a wajenta. Barcin yake son yi ta k’arfin tsiya sai dai idanunsa suka ce ba su san wannan ba, surar Ayra kawai suke sake hasasho masa da tudun kayan fulaninta faffa’dan k’ugu da tsukakken cikinta kamar na y’ar tsanar roba, shi bai tab’a sanin akwai mata a zahiri masu irin suffar ta ba, sai yanzu da ya yi katari da ita, ya zata ko akwai su sai dai irin masu shiga gasar sarauniyar kyau wanda kai tsaye an san surgery ake wa wasu da yawa daga cikinsu, wasu kuma tsabar workout ne yayinda wasu kuma supplement suke sha. Ya dinga duba hannun nasa wanda ya yi aikin cire mata k’waro yana tunanin ina ma hannun ya dawwama yana jin lallausan kayan fulaninta. Ya da’de a yanayin da ya kira daren dare mai wahala a wajensa don bai tab’a shiga yanayi kwatankwacin wannan ba, bai yi aune ba yana duba agogo ya ga lokaci ya ja sosai ya saki tsaki ha’de da mik’ewa ya fara laluben maganin da yake sha ya samu barci. Ita ‘din ma hakan take a wajenta koma fiye da shi, don ita bata san yarda zata yi ta yi controlling kanta ba, abu ne Sabo a wajenta da ta rasa ya zata yi kuka ma kawai ta saka tana ja masa Allah ya isa, ga shi har a lokacin bata daina jin waiwayin hannunsa a kan dukiyar fulaninta ba abin dai kamar aikin sihiri. Sai da ta dinga addu’a ta kuma mik’e da k’yar ta shiga ta yi wanka ha’de da alwala ta zo ta fara sallah sannan ta samu komai ya lafa mata amma tabbas ta ji a jikinta. ____________ Da safe da k’yar ta bu’de nauyayyun idanunta tana sauke su a kan agogon da yake ‘dakin. Da sauri ta mik’e daga gadon da addu’ar farka wa daga barci a bakinta. Ta zuro k’afafunta da azama jin yarda cikinta yake karta da alamar ulcer tana son ta tashi ta kuma tabbata yunwar jiya ce. Brush kawai ta samu ta yi ta zura zumbulelen hijabinta don ba zata sake saken mutumin nan ya sake ganinta ba hijabi ba. Shiru falon ba kowa da alama shima bai tashi ba. Ta bi plate ‘din abincinsa da kallo wanda ya bari tun jiya a wajen ta d’an saki guntun tsaki dole nema kafin barinta gidan nan ta samo y’ar aiki don ita bata son k’azanta aikin gidan kuma ya mata yawa ita ka’dai. Fresh Milk ta samo ta sha cikin cup kafin ta yi wanka ta samu ta girka wani abin mai sauk’i ta ci. Sai da ta gyara falon tsaf da kitchen ‘din don su ka’dai ne suka yi k’ura sannan ta shiga wanka. Tsaf ta shirya cikin wata Moroccan wear mara nauyi sosai ta kawo gogaggen hijabinta da ya rufe mata jikinta ta saka sannan ta fita zuwa kitchen. Sanda ta fito falo ta tabbatar yana wajen, don yarda k’amshin turarensa ya mamaye falon. Shi ‘din ma nata turaren ya sanar da shi zuwanta sai dai bai ‘dago ya kalleta ba don ya lura kallon nata shi yake haddasa masa tashin hankali da rashin nutsuwa ya kuma ji kamar magana’disu yana jansa zuwa gareta. Ta gefensa ta wuce ta shige kitchen ‘din ba tare da ta masa magana ba. “Idan akwai abinda kike buk’ata wanda za’a siyo miki ki rubuta a takarda zan je shopping don jibi zan bar k’asar nan.” Cak ta tsaya hannayenta a kan handle ‘din k’ofar kitchen ‘din jin maganarsa kamar daga sama. Kamar wacce aka yiwa umarni kuma sai ta juyo ta sauke idanunta a kanta “Amma dai ba da aurena za ka bar k’asar nan ba ko?” Sai a lokacin ya ‘dago ya zuba mata idanunsa da suke tabbatar da yanayin da ya kwana, da ace ita mai ganewa ce tsaf zata hango tsumammiyar soyayyarta mai caku’de da sha’awarta a cikin idanuwansa, sai dai da yake ba sani ta yi ba, don ba soyayyar ta tab’a ba sam bata gane ba, ya da’de yana binta da kallo kafin ya saki dogon tsaki ya ce “Ki shirya anjima mu je ki maimaita wannan maganar a gaban Ummeey don ita ta auro min ke, ba mamaki idan ta ji furucinki ta tabbatar ba kya son auren ta saka na sake ki na fi kowa burin hakan.” Ya fa’da yana fighting da zuciyarsa mai k’ok’arin k’aryata kalamansa. A zafafe ta ce “Idan ka yi niyyar saki na Ai ba sai Ummeey ta sani ba, tunda ba ta da hurumin sakin aurena kai ne mai wannan hurumin.” “Kin kuma taki rashin sa’a bana k’etare Umarnin mahaifiyata. Kin gane ai na San muhimmancinta don haka duk munin abu Idan ta ce na yi nake aikata shi ko da hakan zai zame min illa a rayuwata, ko da zan dawwama da bak’in cikin hakan. Idan kin shirya sai mu je ki mata bayani nima kin hutassheni.” Ya fa’da yana ka’da key ‘din hannunsa ya fice ya barta a tsaye tana jin wani turnik’in b’acin ran kalamansa da gaske ya sake hura wutar bak’in cikin da yake zuciyarta. Ta rintse ido tana fa’din “Allah ya kai mu anjimar zan tabbatar maka ba ni da kunya zan bika wajen nata na kuma fa’da ba na son ka sai me?” _______ Kafin ya dawo tsaf ta shirya cikin wani zafafen Hkg lace da ya ji bu’da’dden ‘dinki Half boubou da siket, duka a cikin irin ‘d’inke-‘dinkenta na gida da aka mata don ta k’i yarda ko ka’dan ta tab’a masa kayan lefe. Tsaf ta fito lace ‘din ya sake haska fatarta duk da ba fara bace tas, ta kafa ‘daurin ta ture ka ga tsiya sannan ta baza gashinta a saman kafa’darta ta ajiye matching bag ‘d’inta kusa sa gyalenta red maha’din lace ‘din nata. K’amshi kawai take zubawa ta koma falo ta kame kan kujera tana jiran ta ga ta yarda zai shigo don da gaske ta yi shirin zuwa sanar da Ummeeyn a raba auren nasu don kuwa ba taga alamar duk wasu plans nata za su yi tasiri a kansa ba. Tsawon nawa guda cur ta zauna a falon kafin ya shigo falon yana ‘dora idanunsa a kanta, duk da yarda gabansa ya tsananta bugu bai nuna hakan a saman fuskarsa ba, ya shanye a ransa yana ha’de fuskarsa lokaci guda a zahirance ya kawar da kansa a bad’inance kuwa sake k’issamata matsanancin kyanta yake sai kace aljanna nema kike tilas sai kin tarwatsa min zuciya. Ya yi furucin a zuciyarsa yana harararta k’asa k’asa “Allah yasa ba ni kika yiwa wannan kwalliyar ba?” Da sauri ta ‘dago itama tana kallonsa kafin ta ‘d’auke kai cikin zafin rai ta ce “A wane dalilin zan maka kwalliya?” “A dalilin kina son siye zuciyata” ta sake tunzira da kalamansa sai ta hau furzar da huci kafin ta ce “Kada Allah ya nuna min ranar da zan yi wani abu don kai.” Ya ji zafin furucinta amma sai ya shanye ta hanyar yin k’wafa ya kama k’arfen staircase ‘din da zai kai shi sama yana fa’din “Sai dai kar a kuma.” Ta yi saroro tana kallonsa kafin ta ji takaicin kanta ya kamata me ya kaita ma yin kwalliyar. Hawaye ta ji yana son zubo mata saboda yarda ta ji ta muzanta da kalamansa sai dai ta shanye tana cizan leb’enta “Komai ma yau zai zo k’arshe ka yi da wata ba Ayra ba.” Ya da’de kafin ya sauko k’asan idanunsa a kanta ya fita ba tare da ya ce mata komai ba, duk da ya san jiransa take su fita. Da sauri ta mik’e ta bi bayansa don dama ba motarsa zata shiga ba a tata Motar zata bi bayansa don bata san gidan Ummeeeyn ba. Mamaki ne ya kusa kashe shi a tsaye ganin yarda ta shiga motarta ta tayar cikin zafin nama, wato ‘dan iska ta mayar da shi da ya zauna yana jiranta. Ya ja k’wafa yana gyara sit ‘dinsa ya kwanta abinsa cikin motar idan ta san wata Ai bata san wata ba, idan ta san hanya sai ta kai kanta. Ayra ganin abinda ya yi sai itama ta saki murmushin a cikin tata motar ta mayar da sit baya ta yi kwanciyarta tana fa’din “Daidai nake da kai zamaninka.” Tsawon mintuna talatin suna zaune a hakan ba wanda ya yi k’ok’arin yiwa ‘dan uwansa magana. Ganin hankalin masu hidimar gidan yana neman dawo kansu sai ya saki ajiyar zuciya ya yi tsaki kawai ya fita daga motar yana fa’din “Ba zaki jawo min raini ba shashashar yarinya.” Cikin takun isa da gadara ya isa wajen motarta a zafafe ya bu’de murfin motar b’arin driver ‘din ya jawota da k’arfin gaske har tana shirin samun makwanci a k’irjinsa sai ta yi saurin ja ta tsaya tana masa kallon hadarin kaji “Menene haka?” “Ke zan tambaya menene haka? Kina son jawo ma kan ki raini ne wajen mutanen can?” Ya fa’da yana nuna mata masu gadi da suke ‘dan kallonsu k’asa-k’asa “Idan ke kin shirya karb’ar raini ni ban shirya ba, so that ki nutsu ko don ki siyawa kan ki respect ba don Turaki ba.” Ya yi furucin k’asa-k’asa idanunsa cikin nata kuma har a lokacin hannayensu sark’afe da juna bai saki ba kamar wasu masu kallon soyayya duk wanda ya gansu a lokacin abinda zai kawo wa ransa kenan, ma’aikatan kuwa murmushi suke saki k’asa-k’asa saboda yarda abin ya musu kyan gani. Hannunsa rik’e da nata har ya isa wajen motarsa ya tura ta a mazaunin driver sai sannan ya saki tsaki yana harararta k’asa k’asa ganin yarda take k’ok’arin janye hannunta tun kafin ya saki “Sai kace wani abin arziki ne a hannun naki, hannun da ya gama shan ruk’o gurin kowane k’ato.” Ya fa’da yana k’ok’arin tayar da motar “Hannayen garadan sun fiye min naka masu kama da na mata.” Cak ya tsaya daga k’ok’arin tayar da motar da yake yi. “Ba za ki daina suffanta ni da mata ba ko? So kike sai na bayyana miki b’acin raina ta hanyar da zaki banbancin Turaki da duk namijin da ya tab’a kusantar ki ko?” Ya ciji leb’ensa “Banda bana son ratsa gonar da wasu suka tab’a shuka yau da kin banbance tazarar da ke tsakanin sama da k’asa ina tabbatar miki akwai banbanci mai nisan gaske ki kiyaye harshenki.” Ya yi furucin in a serious tone fuskarsa a ha’de da alama da gaske yana jin zafin ha’da shi da jinsinta da take. Har suka je bai sake magana ba driving ‘din da yake kansa ya san ransa a matuk’ar b’ace yake, suna tsayawa ya danna lock ba tare da ya kalleta ba ya ce “Ina tabbatar miki ki san hanyar da kika bi Ummeey ta amince na sake ki shine kwanciyar hankalinki idan ba haka ba…. Mhmm Wallahi zama gidan Turaki zai zame miki zaman kabari a matakin farko.” Ya fa’da yana lumshe tsumammun idanunsa “Ruwanki ne kina shiga ki k’unduma min zagi a gabanta idan ta yi magana ki bayyana rashin kunyarki k’iri k’iri ta hanyar zaginta itama ina tabbatar miki ko gware kuka yi da ita kuka zo duniya k’arewar soyayya sai ta saka na sake ki, shawara na baki kyauta.” Ya fa’da yana dukan sitiyari. (A min afuwa sakamakon wa’dannan kwanaki da suka riskemu In sha Allah daga wannnan posting ‘din zan k’ara posting ‘d’aya sai kuma Allah ya kai mu bayan sallah, kowa ya san girman wa’dannan gwala Gwalan kwanakin da suka rusko mu, bai kamata bawa ya shagala da duniya ba bai rub’anya aikin da zai samu dacewa ranar gobe k’iyama ba, karatun novel ba namu bane Karatun k’ur’ani shine abinda ya kamace mu a wa’dannan ranaku don haka y’ar uwa ina tunatar da ke da barin shagala da duniya mu ribaci kwanakin mu ta hanyar rub’anya nafilfili da karatun alk’ur’ani ya fiye mana karatun novel dafatan za ku fahimce ni nagode k’warai daga gobe sai bayan sallah In sha Allah. Tafiyar mai nisan Zango ce Kada ku damu In sha Allah za mu cimma ga ci. Jikar Nashe ta ku ce Ayra da Turaki suke cewa Allah ya bamu ladan aikin da zamu yi a wannan ranakun yasa muna daga cikin bayin da za’a y’anta daga wuta. Astagfirullah min kulli zanbun. Love you all.❤️❤️) Takaicin Uba… Nazeefah Nashe✍🏽 35. 💔💔💔💔 Tsam ta yi da ranta tana bin sassan falon Ummeeyn da kallo, da jiran ta inda zata fito. Shi kuwa yana zaune daga gefe fuskarsa ba yabo ba fallasa. Sai ta ga ya mik’e yana murmushi ya isa inda hotonsa da Marigayiyar matarsa Hibba yake, wanda aka ‘dauke su ranar biki. Ya zubawa hoton ido yana ‘dan sakin murmushi kamar kuma wanda aka ingiza sai ya ciro hoton duk da girmansa ya iso wajen Ayra da shi. A fuskarta ya nuna mata hoton “Dubi ki ga Matata. First love ‘dina salihar mata ta gari, mai nagartattun halaye da tarbiyya wacce ta kawo min budurcinta har gida ba irin ki ba da ta zubar a waje…..” cak Ummeey da take shirin shigowa ta tsaya jin munanan kalamansa a kan Ayra, ita kanta kalaman sun yi girma a wajenta bai kuma kamata ace ya gayawa Ayran ba. Ta ‘dan runtse idonta cike da takaici a tunaninta tuni suka daidaita kan su, ashe akwai sauran rina a kaba. Duk wani annurinta ya ‘d’auke tsaf ta fara tunanin ko da gaske Ayra bata kai budurcinta ‘dakin Miji ba. Shikkenan ta tabbata Turaki ba zai so Ayra ba amma dole ta yiwa tufkar hanci. Ayra kuwa lumshe ido ta yi daga zaunen duk da ta ji ‘dacin kalamansa sai dai bata sake ta nuna masa ba ko a kan fuskarta ta saki ‘dan murmushi kafin ta furta “Kowa da k’addararsa ina tayaka jimami na rashin managarciyar mace da kuma auren ballagazar Mace a karo na biyar.” Ummeey ce ta saki gyaran murya hakan yasa da Sauri Turaki ya matsar da hoton daga fuskar Ayra Yana kallon Ummeeyn fuskarsa a ‘dan daburce. Bata nuna masa ko a fuska ta ji kalamansu ba illa murmushi da ta yi tana duban Ayra da ta mata wani kalar azababben kyau. “Daughter ya gida? Zo mana taso maza.” Ayra duk sai ta ji gwiwarta ta yi sanyi a sanyaye ta isa wajen Ummeeyn ta ‘dan rungumeta ka’dan, Ummeeyn ta hau shafa bayanta “Hope kina lafiya mhmn?” Ayra ta ‘d’aga kai tana ‘dan zamewa k’asa sosai don gaishe ta, haka kawai yau sai ta ga girma da mutuncin Matar kamar ba zata iya fa’dar abinda ta zo da niyyar fa’da mata ba, kunya sosai ta rufeta. Ummeey ta ja hannunta ta zaunar da ita a gefenta tana duban Amin Turaki da yake tsaye ya zube hannayensa a aljihu yana kallonsu k’asa-k’asa. “Kai kuma fa ka tsaya kamar soja, ko kallon hoton Mar’atussalihar ne har yanzu?” Basarwa ya yi ka’dan ya je ya jingine hoton don ya san magana ce mai kama da harshen samo Ummeeyn ta gwa’ba masa “Duk wata mace ba burinta bane rasa Budurcinta kafin a kaita gidan miji, ba lallai bane a yawon banza Yarinya take rasa budurcinta wata k’addara ce wasu dole aka musu wasu kuma girman shekaru ne da aiyukan yau da kullum suke kawar musu da budurci, ka daina jam’u kana tattare mata gaba ‘d’aya kana musu ku’din goro, ka ji na gaya maka.” Ummeey ta fa’da cike da basarwar duk da ta hango matsananciyar kunya a fuskar Ayran da ta yi kamar ta zunduma ihu. Shi kuwa gogan ko a jikinsa sai ma waskewa da ya yi ya zauna daga gefe yana gaida Ummeeyn, ta amsa kadaran kadahan fuskar ba yabo fallasa. “Dama sallama na zo miki, gobe zan wuce Turkey.” “Ma sha Allah visar Ayran ta fito kenan?” Da sauri ya ‘dago yana kallonta kamar ya ‘dora hannu a kai ya yi ta zunduma ihu. “Ba da ita zan tafi ba, akwai maganar ma da ta zo gaya miki.” “Ashe kaima baka shirya tafiyar ba.” Idanunsa a raunace ya ‘dago yana kallonta sai dai bata ma nuna ta san me yake ba, ta ‘dauke kanta tana kallon Ayra “K’afarki k’afar Mijinki duk inda zai je ki zame masa kamar jaka, kuskurena babba barin mijinki lulawa wata k’asar ba tare da ke na in dai yana da halin tafiya da ke ‘din.” Sannan ta mayar da kallonta wajen Turaki fuska ba wasa ta ce “A tun tashinka ka san sarai ba na barin Abbunku ya yi tafiya ba dani ba, don haka idan kana don ganin b’acin raina ka tafi ba da Ayra ba, ba gama magana.” Daga haka ta k’walawa Mai aikinta kira don su Tayseer ba sa nan sun tafi Saloon “Maza ki kawowa Ayra abinci.” Mai aikin ta juya da sauri. Turaki ya tsume a kan kujera sai zabgawa Ayra hararar k’asan ido yake. Ummeey duk abinda yake tana kallonsa kafin ta tab’e baki a ranta ta furta sai dai ka mutu. Ganin bai samu goyon baya ba, don haka ana kawo abincin ya mik’e zumbur ya ce “Ke tashi tafiya za mu yi.” Ayra ta ajiye cup ‘din Kunun ayar da yake hannunta duk da taso cin abincin ta Kuma lura da gayya ya mata haka sai dai bata damu ba ta saki murmushi kawai Ummeey ma ta lura da mugunta ya shirya don haka ta k’walawa Salame kira tana zuwa ta ce “Juyewa Ayra abincin nan a coolers ki zuba mata kunun ayar, yau na hutar da ita girki.” Turaki cikin k’unk’uni ya ce “Wallahi sai ta yi don ni tuwo zan ci.” Ummeey dariya ce taso kufce mata sai dai ta gimtse ta ce “Bakomai zata yi Ai lada zata samu, aikin miji ba abinda ya fishi samun lada, duk abinda ya saka ki ki yi kin ji littafin ki na shiga aljanna kike cikawa.” Ayra ta ‘d’aga kai tana amsar ledar da Ummeeyn ta bata na ha’daddun turarukan Humras da designers. “Idan kun shirya tafiyar ka samar mata visar sai ka yi waya ka sanar min in mata shirin tafiya, ka kuma kaita gidansu, don na san kaima baka je ba, daga nan ku wuce can direct ka yi wa mahaifiyarta godiya.” “Mahaifinta fa?” Ya fa’da yana kallon Ummeey. Ba Ummeey ka’daiba har Ayra sai da ta razana da jin tambayarsa, tun da take bata tab’a jin haushin tambayar ina Mahaifinta ba kamar yanzu, kafin tayi wani yunk’uri na fa’dar abinda yake bakinta ta ji furucinsa cikin dakakkiyar murya yana fa’din “Ko da yake na ji labarin ba su ‘dauke shi da daraja ba, yana can yana walagigi da rashin lafiya, ba su damu da shi ba balle su agaza masa a yanayin ciwon da yake ciki, amma ba mamaki yana gudun cin dukiyar da ta tabbata hanyar da aka sameta ba ba ta halal ba ce….” Amin!” Ummeey ta ambaci sunansa cikin tsawa hakan yasa ya ha’diye sauran zantukan da suke ransa wanda tabbas ya yi su ne don ya hassala zuciyar Ayran. K’wallar bak’in ciki ce ta fara gangara a kumatun Ayra, a yau kam ta sake dank’arawa Maza suna ‘daya duka kuma halinsu ‘daya sam bata hango banbancin da ake cewa suna da shi ba. Cikin b’acin rai Ummeey tace “Wani irin shirme ne haka Turaki, me yasa kake son tabbatar da abinda bai zama lalle bane gaskiyarsa, shin ka zauna ka tuhumi Ayra labarin rayuwarta ne, ko kuma ka fi yarda da na yamad’idin da mutane suke zuwa suke gaya maka, ka kiyaye fa! Bana son rashin hankali kana ganin yarda ka sakata kuka ka b’ata mata raina banza, shi wanda yazo ya baka labarin me yasa bai baka labarin abinda shi mahaifin nasu ya yi musu ba? Kada ka sake bana so idan kuma ya sake ki bugo waya Ki gaya min.” Ta fa’da tana share mata hawayen da har a lokacin yake sintirin zuba daga idanunta. “Yi hak’uri kin ji daughter wata rana sai labari, kuje Allah ya yi miki albarka.” Kafin su yi aune tuni Amin ya yi gaba don haushin kukanta yake k’ara masa ji yake shima da da hali tabbas kukan zai saka. Driving kawai yake ba tare da ya sake kallon b’angaren da take ba, duk da yana jin shashshek’ar kukanta a kai a kai, ya maze ya basar yana yak’i da tasa zuciyar. Har suka je gidansu Ayran kafin su shiga ya yi parking yana juyowa gaba ‘d’aya ha’de da zuba mata ido. Ji yake kamar ya rungumota jikinsa ya lallasheta amma hassalalliyar zuciyar sa na kwab’arsa da aikata haka. “Ki yi min shiru, kuka dai kuka sai ka ce ke ka’dai ce me idon kuka.” Ya fa’da yana kafeta da narkakkun idanunsa, kamar sake tunzirata ya yi ta sake sakin kukan wannan karan da ‘dan k’arfin gaske. “Mtsw! Wallahi idan ba ki min shiru ba Zan miki abinda tilas na kashe miki bakin kukan, haba meye haka salon mu shiga a ce wani abu na yi miki, ni ya kamata na yi kuka ni da aka ha’dani da jangwam amma kece mai bakin kuka.” Ba tayi shirun ba duk da warning ‘din da ya yi mata, hassala zuciyarsa ta yi bai san sanda ya janyota jikinsa da k’arfin tsiya ba, ya saka bakinsa cikin nata kamar wanda ake sakawa shocking haka Ayra ta ji, ta fara k’ok’arin k’wacewa amma ta kasa sakamakon sake shigar da jikinsa cikin nata da ya yi sosai, tuni Ayra ta nemi kukan ta rasa sai tsoro da rawar jiki. “Sai da nace ki min shiru kika k’i shi yasa na biyo da ke ta hanyar da tilas ki yi shirun.” Ya fa’da yana sakinta ha’de da goge bakinsa da tissue yana harararta k’asa-k’asa “Haka kawai kin sani ha’da baki da bakin da ya ga mazan duniya.” Tsit ta yi cikin mutuwar jiki tana gyara gyalenta gaba ‘daya wani yanayi ne yake bak’untar jikinta, ga idanunsa da suke mata yawo a jiki da ta kasa samun nutsuwa da su. “Ka daina kallona bana so.” Ta yi furucin cikin matuk’ar kasala da zai lura k’warai zai gane bak’uwa ce a lamarin ya tab’e baki “Me zan kalla a Jikinki, ba fa na son fulako idan zaki saki jiki ki saka Kina acting just like you don’t know anything.” Ya fa’da yana cize bakinsa ha’de da son sake lalubo k’wayar idanunta amma ta kasa ba shi dama, madadin haka ma da sauri ta fice daga motar tana furta Allah ya isa k’asa-k’asa sosai da murya. Kawai sai ya samu kansa da zabga murmushi yana shafa lab’bansa da har a lokacin yake Jin taushin sussulb’an leb’enta a kansa “She has a kissable and sweetable lips.” Ya fa’da a hankali ha’de da lumshe ido yana sakin sassauk’ar ajiyar zuciya tabbas ya sake janyowa Kansa jangwam yau. Da k’yar ya samu komai ya lafa masa ya sarrafa kansa wajen fita da azama daga motar kamar komai ma bai faru ba. Sai dai idanunsa sai da ya maka musu bak’in glass don idan ba haka ba tsaf za a faro jirginsa yarda idanun suka canja kala suke nuna zallar jarabar da yake ciki. Duk inda ya motsa kuma k’amshin mayataccen turarenta na nan a jikinsa, kamar yarda nasa ya mak’ale a nata jikin. Amma tunda ta sauke idanunta a kan Ayra wani farin ciki ya ratsa zuciyarta, tabbas burinta ya cika yau ga Ayra ta zo gidanta a matsayin Matar wani, abinda zatonta bai tab’a bata ba. Sam bakinta ya kasa rufuwa ji take kamar sun shekara ba su ha’du duk da kwana biyu ne kacal. Rungumeta ta yi sosai a jikinta, itama Ayran ta cusa kanta jikin Amman tana sakin kuka mai tafe da shagwab’a “Amma na na yi kewarki.” “Nima na yi kewar Ayra ta.” Amman ta fa’da tana shafa bayan Ayran cike da tausayi da kulawa. Sun da’de a haka suna jin bugun zuciyoyin junansu kafin Amman ta janyeta suka zauna kan kujera tana fa’din “k’alau dai ko? Farin cikin ganinki ya makantar da ni na kasa ganin aibun fitarki a kwana biyu kacal.” Ayra ta ‘dan ‘d’aga kai da niyyar amsa mata sai suka tsinkayi muryarsa daga bakin k’ofa yana fa’din “K’arya zata miki Amma, ba wani k’alau takura ni ta yi sai na kawota da takardar sakinta…..” Ya fa’da yana zura hannu a aljihu da niyyar zaro takardar da yake nufi ba. Ba Amma ka’dai ba hatta Ayra sai da ta ji fa’duwar gaba ta dinga bin takardar da yake mik’a mata da kallo. Shi kuwa ya kafeta da ido lokaci guda kuma yana lumshe idon ha’de da sake mik’a mata takardar. Wannan karan saura k’iris zuciyar Amma ta daina aiki……. (A yi hak’uri cigaba zai biyo bayan sallah In sha Allah.) Kada ku manta Alk’alamin rubuta Labarin k’addarar Ayra mai tsawo ne. Ku dai ku cigaba da bibiyar Jikar Nashe in sha Allah ba za ku yi asarar ku’din ku ba. Ayi sallah lafiya Love you all. 😊😌) Takaicin Uba… Nazeefah Nashe 36. 💔💔💔💔 Dafatan an Yi sallah lafiya? Allah ya maimaita mana yasa mun yi karb’ab’biyar ibada. _________________ Ayran kanta gabanta ne ya dinga fa’duwa ta zuba masa idonta da suka fara jirkita zuwa wata colour daban, me hakan yake nufi da ya yi mata wannna sharrin? So yake ya b’ata tsakaninsu da mahaifiyarta ko me? Hannu na shaking ta karb’i takardar duk da ta so samuwar takardar sai dai sam bata so fitar ta a wannan gab’ar ba. Amma ma zuciyarta zuwa lokacin tuni ta yi rauni tana jin sautin fitar numfashinta ba bisa k’aida ba. Ta dinga ware ido tana son ganin abinda yake takardar duk da har a lokacin Ayra ta kasa bu’dewa idanunta a lumshe suke kawai, hakan take so amma tana tausayin Amma bata san a yanayin da zata riski kanta. “Sak’o ne daga mai gadi wata k’awarki ce ta ce a baki ya biyo Ki zai baki ya ga har kin shige cikin gida.” Cak numfashinsu ya tsaya na wuncin gadi a lokacin suka saki ajiyar zuciya a tare Ayra ta ware idonta tana kallonsa itama Amman kallonsu take sai da ta gyara zamanta kafin ta ce “Amin me ya faru ne na ji kana min maganar Ayra ce take son ka saketa?” Ya yi k’asa da kansa sosai kafin ya tank’washe K’afa yana gyara murya ya furta “Amma ina yini?” Sai a lokacin Amma ta tuna basu gaisa ba tana murmushin ta ce “Lafiya lau Turaki, ashe fa ba mu gaisa ba kaine duk ka ru’da min tunani tunda ba kowacce uwa bace zata so aurar da y’arta a ce an saketa a kwana biyu kacal.” Ya jinjina kai “Abinda nake ta son ta gane kenan Amma sai dai yarinyar nan taurin kai ne da ita kullum sai ta tuk’eni akan sai na saketa shi yasa na ce ta zo mu zo wajenki da kanta ta gaya miki don kada na saketa a ga laifina…” Da sauri Ayra ta ‘dago ta zuba masa ido jin sharrin da yake yi mata, suka ha’da idanun nata idon yana kawo ruwa shi kuwa da sauri ya ‘dauke kansa yana murza hannunsa. Amma kuwa tsabar takaici kasa magana ta yi illa k’asa da ta yi da kanta idanunta a runtse takaicin Ayra na neman kasheta me take son Turakin ya ‘d’auka bata da tarbiyya ko me? Jin Ayran ta fara kuka yasa Turakin da Amman suka yi saurin ‘dagowa Suna kallonta Amma tace “Wani irin iskanci ne wannan kin yi laifi tun ba’a yi miki fa’da ba ki b’are baki kina kuka, wallahi ko ki rufe min baki ko yanzu na ba shi umarni ya zane min ke, ki bar ni da bak’in cikin ma da yake cin zuciyata, Allah ya saka maka da alheri Amin da baka aikata abinda take son ka aikata ba ka yi aikin hankali ke kuma ki je don kan ki, Ina dai gaya miki ki kiyaye tsallake umarnin Allah don wallahi aure ba abin wasa bane, ka yi hak’uri don Allah Turaki sai ka yi hak’uri da halayenta ta riga ta saka tsanar maza da aure ma gaba ‘daya ne a ranta amma wata rana sai labari In sha Allah.” Turaki yana ‘dan murmushin gefen kumatu ya ce “Bakomai Amma In sha Allah Zan cigaba da hak’uri da ita a cigaba da mana addu’a.” “Kullum ita muke yi Turaki, Allah ya ha’da kanku. Ki durk’usa ki ba shi hak’uri na ce miki.” Ayra murya na rawa tace “Ka yi hak’uri idan na maka ba daidai ba idan kuma ban maka komai ba…” “Rufe min baki anan wajen a gaban nawa ma rashin kunya za ki masa? Anya kuwa Ayra?” Ta sake ha’diyar yawu mai ‘daci kafin ta ce “Ki yi hak’uri Amma.” “Hak’uri na ‘d’aya ki bi mijinki sau da k’afa ki aikata duk abinda ya umarceki kin ji Ayra?” Ta ‘d’aga kai tana share hawayen da suka kasa tsayawa daga zuba daga idanunta “Ku tashi ku je Allah ya yi muka albarka.” Turaki ya amsa da k’arfi ita kuwa Ayra a hankali cikin dasashshiyar muryarta ta amsa abubuwa kala kala ta k’udirta a ranta da zata ‘dauki fansa a wajen mutumin da ta ra’da masa sunan mugu tabbas sai ta rama wannan alwashi ta ci. Shi kuwa Turaki cikin farin cikinsa ya fita daga gidan ya shiga motarsa ya kuma ware ki’da cikin wak’ar da yake so ko yanzu burinsa ya cika kuma ko yanzu ya saketa ya tabbata babu wanda zai ce masa don me? Jikinta a sanyaye ta bu’de marufin k’ofar don shiga, daga cikin yake k’arewa idanunta kallo abinka da mai girman idanu tuni sun tashi sun yi luhu-luhu sabida kukan da ta fara. Maganar Baba Maigadi ce ta tsayar da ita daga shiga motar. “Hajiya kin ga sak’o ko?” Ta ‘dan mayar da mayafinta ya rufe mata fuska don bata son yaga alamun ta yi kuka kafin ta ‘d’aga kai murya a dashe ta ce “Na gani Baba, daga ina ne?” “K’awarki ce ta ce a baki, da nace ga numberrki ta kira ki sai ta ce ba zata kira ba itama tana da numberrki amma yanzu ta goge tunda kin nuna bata da muhimmanci an yi bikin ki bata sani ba.” Ayra ta ‘dan saki murmushi ka’dan don ta san Besty ce zata mata haka “Bakomai Baba zan nemeta nagode.” Ta zuge jaka ta ‘Debo ku’din da bata san adadinsu ba ta ba shi. Godiya sosai ya yi mata tare da jaddada addu’ar neman zaman lafiya a aurensu da zuri’a ‘dayyiba. Bata san me yasa ba kawai sai ta samu bakinta da amsa addu’ar tana shiga motar. Amin ya zube mata idanunsa kafin ya ‘dauke yana tab’e baki ka’dan ya ce “Kika amsa kuma? Kin manta sunan auren namu?” Bata amsa shi ba, don ba k’aramin haushi yake bata ba ji take kamar ta shak’o shi ta yi ta dukansa har sai ta gaji. Ya cigaba da jan motarsa yana bin wak’arsa cikin nisha’di. Tsawon kwana uku ya ‘d’auka yana nemar mata visa duk da bai so haka ba ya zama dole ya bi umarnin Ummeey idan yana son gamawa da duniya lafiya. Da k’yar aka gama mata visar don haka yau a gajiye lik’is ya dawo gidan da kuma neman fa’dansa kamar yarda ya saba. Sai dai bai sameta a falon ba, da alama tana ‘daki ba mamaki ta gaji da rigimar yau ta shige ‘dakinta da wuri. Shi kuma yana son janta da rigimar don sau tari ta haka ne ka’dai yake samu ya ha’da jikinsa da nata ya samu sauk’i a wasu lamarin, don shi ka’dai ya san a yanayin da yake kwana. Ya san kansa ya san shi ‘din ma buk’aci ne yana mamakin yarda ya ‘d’au tsawon shekaru har hu’du bai kusanci mace ba, duk da magunguna yake sha da y’an dabaru amma yana wahala, yanzu kuwa da yaga mace kusa da shi kuma macen da ya da’de yana mafarkin samuwarta a matsayin matarsa tazo masa a matsayin matarsa sai lamarin yake da’da k’amari yake kuma nema yafi k’arfinsa. Sau tari ji yake kamar yaje ya kusanceta ko da ta k’arfin tsiya ne, da ya tuna wasu banza sun Riga sun bu’de hanyar sai ya ji ransa ya b’aci. Sai da ya yi wanka ya saka pyjamas na barci ya feshe jikinsa da turaruka sannan ya nufi ‘dakinta don ya sanar da ita ta shirya goben flight ‘din 4:30 za su bi zuwa Moscow, don ya fasa turkey ‘din sai ya je Moscow tukun na zai dawo ya je Turkey. Don a Moscow ne yake da gida nasa na kansa kuma a can zai barta ya nufi Turkey ‘din. Daga ita sai b’ingilin towel take zaune gaban mudubi shima ta zameshi zuwa k’ugunta don ta ji da’din shafawa jikinta mai sosai. Bata san yana gidan ba bata san kuma zai shigo ba da bata zauna a haka ba. Kuma k’ofarta ma a bu’de ta barta don ta saba ko a gida haka take fitowa daga wanka ta zame kuma towel ‘din ta shafe jikinta da Oil ko moisturizer. Idanunsa ne suka masa kyakykyawan gani da dukiyar fulaninta da suke tsaye cokar cokar kamar torch light. Da sauri ya ware idonsa yana kallonsu ta mudubi ta ganshi don haka itama cikin tashin hankali ta ja towel tana rufe jikinta da shi, muryarta na rawa ta runtse idanunta tana fa’din “Out Malam! Ta ya zaka shigo min ‘d’aki without any notice.” Kamar mara motsi haka ya tsaya da yaji tsayuwar na neman gagararsa sai ya koma jikin bango ya jingina yana kokawa da magana’disun da ke k’ok’arin jansa zuwa gareta. Komai ma ya kunce masa a yanzu kawai ita yake buk’ata da duk wasu halittu na jikinta, da gaske yarda yake zaton samunta haka take koma ya ce ta wuce haka ta ko ina itace kalar macen da yake so ya runtse idanunsa madadin ya daina ganin abubuwan sai ya ga still su idanunsa suke hasko masa hannunsa ya tusa cikin sumar kansa da yake jin kamar ana fisgar gashin nasa. Ita kuwa Ayra tana can k’udundune da mitsitsin towel ‘din da idan ta yi sama da shi k’asanta ne zai fito idan ta barshi a k’asan kuma dukiyar fulaninta zai cigaba da gani, abinda wani mahaluk’i bai tab’a ganar mata ba. Murya na rawa tace “Please Turaki hakan bai dace ba, ba kyau ganin tsiraicin wani don Allah ka fita.” Maganartata da yarda muryarta take shaking sai ya zame masa kamar fami daga abinda yake ji har bai san sanda ya iso wajenta ba cikin wani irin taku, sai dai kawai jin k’amshin turarensa ta yi ya k’ara yawaita a hancinta. Murya a dashe ya sunkuya daidai wuyanta yana sauke hucin numfashi a dokin wuyanta ya furta “Menene bai dacen ba? Abubuwan da mutane bila adadin suka gani without dowry shine bai dace ni da na biya sadaki na kalla ba, halak ‘dina ne fa, kuma ya halatta na ga duk inda naga dama a jikinki don haka cire min wannan towel ‘din Sadakina zan mora…” da sauri Ayra ta damk’i towel ‘din ganin fuskarsa ba annuri da gaske yake son rabata da towel ‘din “Ki bari na cire ta limana, ko na fisge da k’arfin iko, tunda dai gaba ‘dayanki ni nake iko da ke.” Ya fincike towel da k’arfin gaske ya wulla shi can gefe, da sauri Ayra ta damk’i k’irjinta da tafukan hannayenta. Turaki kuwa numfashinsa ne yake neman ‘daukewa da kyar ya sake k’arfin halin watsa mata magana “Abin mamaki kika bar wasu banza ye ma suka gani sai nine marainin wayanki.” Shammatar sa Ayra ta yi ta shige toilet da mugun speed ta datso k’ofar. Ba shi da k’arfin binta don duk jikinsa a sanyaye yake da k’yar ya zame ya fice daga ‘dakin Yana jin yarda halittunsa suke ‘daurewa tamau agaji kawai suke nema. Ayra kuwa kuka ta saka a toilet tana tunanin k’arshen tozarci da wulak’anci yau Turaki ya yi mata shi. Ta dinga hango mayatattun idanunsa da suke bu’dewa Suna lumshewa a Kan halittunta. Da k’yar ta fito jin ya fita daga ‘d’akin ta datse k’ofarta ta zura Riga ha’de da kwanciya tana mayar da numfashi. __________ Da k’yar ya mik’e da safe don yana son zuwa karb’o musu boarding pass. A falo ya tarar da ita tana ta aikin babbaka turare jikinta sunk’ufe da hijabi kallo ‘d’aya ya mata ya ‘dauke kai ita kuwa mamakin yarda ya fito da wani bak’in glass ya maka take, har ya gifta ta ya juyo murya a shak’e ya ce “Ki zama ready Flight ‘din mu zai tashi 4:00 sharp. Ki buga waya ki sallami kowa.” Bai jirata ba ya fice da sauri ya barta tsaye tana jin wata razananjiyar fa’duwar gaba, da tunanin shikkenan tata ta k’are idan ta sake ta bi shi k’asar da ba tasu ba yanzu menene mafita? Ta fa’da tana cizon leb’enta na k’asa abinda ya zame mata jiki……. JikarNashe.✍🏽✍🏽 Takaicin uba…. Nazeefah Nashe 37. 💔💔💔💔 Saukar hawayen da ta ji a saman kuncinta ya tabbatar mata da ta kai k’ololuwar b’acin rai. Me Turaki yake son mayar da ita ne? Abar ikonsa da zai dinga juyawa kamar sitiyarin mota a duk sanda ya so, shi bai san sam ba sonsa take ba, ba kuma ya gabanta kamar yarda ta tabbatar ita ‘din ma ba a gabansa take ba. Ta ha’diye abinda ya tsaye mata a mak’oshi kafin ta raruma wayarta da sauri ta shiga danna kiran layin Amma gwara ta sanar mata ita ba zata bi Turaki ba, to idan ma ta bi shi wa zai cigaba da kula musu da dukiyarsu. Bugu biyu Amma ta ‘dauka don dama zancenta suke da Dijah tana bata sak’o zata kai mata na kazar ta da aka kawo daga zuru, da sauran tarkacen kayan matan da ya jaddadawa Dijah a kan ta shanyesu tas a gabanta. Ta ‘d’aga wayar tana murmushi kafin ta ce “Y’ar gidan Amma ya aka yi?” Madadin ta amsa mata sai ta saki kuka, kuka sosai take yi kukan da ya razanar da zuciyar Amma, da sauri ta hau fa’din “Ke tsaya, me yake faruwa Ayra?” “Amma na gaji da k’arfin ikon da mutumin nan yake nuna min, juya ni yake kamar wadda ya saka ku’di ya siya.” “Haka auren ya gada Ayra sai hak’uri. Yanzu me ya faru?” Ayra ta sake sakin sautin kukanta da take son lallai sai ta siye zuciyar Amma da shi ta amince da buk’atar da zata zo mata da shi. “Wai sai na bi shi, Ni kuma in yi yaya da nawa aikin idan na bi shi.” “Ki ajiyeshi ki bi umarnin aure shi ne abinda zai rabauce ki duniya da lahira, ina za ki bi shi?” “Can inda yake aiki.” Amma ta saki murmushi ta ce “Ma sha Allah haka ake so.” Da sauri Ayra ta zaro ido jin abinda Amman tace “Me kika ce Amma?” Da sauri Amman ta k’unshe baki don dariya ce take son kufce mata “Cewa nayi Allah sarki zan yi kewar autata, ki yi hak’uri kin ji ki bi shi Allah ya miki albarka.” Kuka ta saka sosai tana jan hanci ta ce “To Amma kuma ya hana nazo na muku sallama ke kizo don Allah.” Amma ta waro ido “In Zo ina? Rufa min asiri da zuwa gidan suriki, ga dai Deejah nan dama ina shirin aikota gidan naki kiranki ya shigo, ki tabbatar duk abinda ta kawo miki kuma kin yi amfani da shi tas kin ji y’ar albarka bana son ki min musu sai ‘dan gata ne yake samun irin wannan kayan kada ki min wasa da su in dai kina son farin ciki na.” Ta saki ajiyar zuciya murya na rawa ta ce “To Amma.” Amma ta zare wayar a kunnenta tana fa’din “Ayra Danger! To idan baki bi mijinki ba me zaki zauna ki yi anan ni nagode masa ma Ai daga ganinsa ba zai ‘d’au shirgin shiriritar ta ba.” Deejah na dariya ta ce “Yau da kanki Amma kike kiran Ayra mashiririyace.” Itama dariyar ta yi kafin ta ce “Ai sunan nata kenan, kullum madadin girma k’ara zama yarinya take, ta shi maza kije ki titsiyeta sai ta cinye komai na jikin kazarnan ta kuma shanye roman sannan ta shanye tsumin nan tas kada ta saka ni asarar mak’udan ku’di kazar nan ka’dai ta isheta komai ta b’arin aurattayya koda zata shekara bata sha komai ba dangane da magungunan mata.” Deejah ta mik’e ‘dauke da ledar a gabanta tana fa’din “Mu Amma wannan karan baki mana kazar ba.” Ta harareta kafin ta ce “Ta autata nake yi kowa ta fitar da ku’dinta ta siya.” Deejah ta ‘dan turo baki tana fa’din “Ai shikkenan zan samu Anty Surayya marubuciyar Halin yau na siya a wajenta don itama tana kawo su masu kyau.” “Ya dai fi miki.” Amma ta fa’da tana gyara kwanciyarta a saman 3 seater don da gaske sosai take gyara y’ay’anta bata son su yi rayuwar boranci a gidan aurensu kamar yarda ita ta yi a nata gidan auren saboda rashin gata. Da sallama Deejah ta shiga chalet ‘din gidan sai dai tsit da alama Ayran tana can ciki, don haka ta zaro wayarta ta fara kiranta tana ‘d’agawa ta ce “Malama ina k’ofa ki bu’de min.” Ayra da sauri ta yayimi gyale ta fito daga kitchen ‘din don bu’de mata k’ofar kana ganin yanayinta ka ga mara walwala sam zuciyarta bata mata da’di. Sosai ta rungume Deejah cike da tsananin farincikin ganinta Deejah tana murmushi ta ce “Malama kada ki yar da ni, yau ke ce kike murnar gani na?” Ayra bata yarda ta saketa ba sai da ta saki kukanta sosai a jikinta sannan suka shiga ciki Deejah tana fa’din “Kukan da’di kike Ayra, Allah ya kashe ya baki dandatsetsen Mijin kerewa sa’a madadin ki gode masa sai kike son butulce masa dubi fa ni’imar da ubangiji ya miki ta ko ina, kuma daga ganin Turaki irin mazan nan ne masu kashe Matansu da soyayya mai nutsar da zuk’ata, kulawa da riritawa har sai kin gaji da shi.” Ayra ta zaro ido tana fa’din “Mhnm! Yaya Deejah baki san halin wannna mutumin ba kenan, wallahi wahala kawai yake ba ni kin san kallon da yake min kuwa? Wai karuwa! Ko uban wa ya gaya masa na tab’a karuwanci?” Deejah ta waro ido a tsorace ta ce “Ban gane ba ya kusanceki ya ji akasin budurci a tare da ke ne?” Ayra ta ‘dauke k’wallar da take zuba k’asan idonta tana girgiza kai “Allah ya kiyaye wannan mutumin ya kusanceni, shima ya yiwa kansa togaciya ya ce duk ranar da ya kusanceni na k’addara kamar na karb’i takardar Sakina a hannuna ne, shi ba zai kusanci fasik’a ba da ta Riga ta gama rabawa maza jikinta a waje ba, Wannan maganar Ya Deejah tana min k’una a rai, kuma wallahi bana tunanin zan yafe masa wannan k’azafin, koma me ya faru Ai k’addarar bawa baya wuceta.” Deeejah kanta jikinta tsuma yake da b’acin ran abinda Ayran ta gaya mata take, sam sai ta ji ta fara jin haushin Ameen duk da ta tabbatar da wata a k’asa ba mamaki wani ne ya zo ya bashi labarin akasin labarin su. Jikinta a sanyaye ta dafa Ayran murya da laushi ta ce “Tabbas! Bawa baya shige k’addararsa, Auren Turaki shine ta ki k’addarar Amma kuwa zai yi nadama a duk sanda ya samu labarin ainahin abinda ya faru, kada ki kula shi a wannan gab’ar duk abinda zai miki ki zama tamkar doluwa ki k’ask’antar da kanki ina tabbatar miki wata rana da bakinsa zai furta Kaico na ni Turaki, yanzu ki cigaba da amfani da duk wasu magunguna da za’a baki, za su miki amfani wata rana, ga kaza nan Amma ta ce ki cinye tas a tattaro mata k’ashin na kai mata ki shanye tsumin nan, ita kuma wannan zumar da garin maganin ki tafi da su da fresh milk za ki dinga sha ko yoghurt k’arfe nawa ya ce za ku tafi?” Ta nuna mata yatsunta hu’du alamar k’arfe 4:00 za su tafi. Deejah ta duba agogo ta ce kin ga ba lokaci yanzu har 1:00 ki zauna ki ci kazar ni bari na shirya miki akwatin da za ki tafi da shi, shawarata ki jajirce wajen kwalliya da dadda’dan girki har sai kin janye hankalinsa tsaf sannan wasan zai fara. Sai yazo ya yi regretting kalamansa.” Ayra murmushi kawai ta saki tana tunanin idan ta samu ta b’alle daga gidan Turaki bata tunanin akwai wani mahaluk’in da zai mayar da ita. Tsaf ta gyara zama ta fara cin kazar nan, don dama bata ci wani abincin kirki ba, ga kazar ta yi mata da’di a bakinta tsumin ma kamar Lemo haka take kurb’arsa ba canjin taste sosai. Deejah wasu irin futinannun kaya ta dinga zubawa Ayran a babban akwatin da za ta tafi da shi, Nightwears masu masifar bayyana surar jiki da English wears sai kayan mu na gargajiya ka’dan. Ta saka mata wasu sexy turaruka masu masifar janye hankalin namiji duk a kayan da ta taho mata da su. Ta gama gyara wa ta kulle akwatin tana ‘dan sakin murmushi don ta tabbbata idan Ayran ta san tsiyar da ta k’ulla mata sai sun kwashi y’an kallo. Tana komawa falo bugun k’ofar su Ummeey yana ratsa falon Ayran na dubanta ta ce “Ya Deejah har kin yi me?” “Har na ha’da kwashe tarkacen Ki ki shiga ciki ga bak’i nan kin bararraje.” Ta fa’da tana sakin labulan windown ganin su Ummeey ne. Tsam Ayra ta mik’e da sauri ta shige ‘d’aki da shirginta. Ummeey tana murmushi tace “A’a Yaya Deejah ana nan kenan.” Deejah ta mata sannu da zuwa tana amsa gaisuwar su Tayseer da suke gaisheta ta ce “Ban da’de da zuwa ba na zo mata sallama.” Ummeey ta girgiza kai hakan Yayi kyau mu ma sallamar muka zo mata don shak’iyanci sai yau Turakin yake gaya min wai yau za su tafi.” Deeja ta yi dariya kawai ta basu hanya suka shiga ciki ita kuma ta shiga kitchen don kawo musu abin tarar bak’i. Hijabinta ta zumbula ta fita falon, fuskarta washe da murmushi ta isa kusa da Ummeeyn tana shirin Zubewa Ummeey ta jata gefenta “Zo ki zauna kusa da ni kin ji daughter, nifa bana son wannan y’ar kunyar ki saki jikinki ni Mamanki ce ba wani surika.” Ayran ta ‘dan shiga jikin ta ka’dan tana gaisheta. Ummeey ta amsa cike da kulawa “Ya shirin tafiya? Mijinki Ai bai kyauta min ba Da sai yau yake sanar da ni za ku tafi, Allah yaso na yi miki tanadin tafiyar.” Su Tayseer suka gaisheta ta amsa musu cike da kulawa tana tsokanarsu da “Shine ko ziyara? Ai shikkenan nagode.” Tayseer ta yi dariya “Wallahi mun so zuwa Ummeey ce ta hana mu wai ba a zuwa gidan amarya.” “K’warai ni na hana ina dalili kuzo ku dameta, Aman ma hana shi zuwa na yi yanzu ma ni na hana uban su tafi da shi na ce ya yi zamansa a nan, idan an kwana biyu suka zo hutu sa tafi da shi ko su barshi ma gaba ‘d’aya.” Ta bu’de jakarta ta mik’awa Ayra wata shopping bag mai kyau “Kada ki yi wasa da su turaruka ne masu kyau da nagarta ko Wanne da gab’ar da ake gogashi akwai bayanansu a jiki. Wannan Kuma yaji ne ki tabbata kina yawan cin sa a abinci shima akwai nasa sirrin daban sauran kayan kuma duk akwai yarda zaki yi amfani da su, ki min alk’awarin ba zaki yi wasa da su ba Mu daughter.” Ayra tana murmushi ta ‘d’aga mata kai tana mamakin hali irin na Uwar mijinta mai sauk’in hali ta Kuma ‘dauketa kamar y’arta ba surika ba. Ba su da’de a gidan ba, Turaki ya dawo da ‘dan hanzari don har 2:45 ta yi kuma kamata ya yi a ce 3:00 suna airpot. Turus ya yi ganinsu zube a falon sai kuma ya ‘dan zauna Kusa da Ummeey yana gaisheta ta amsa tana nuna masa Deejah jin bata ji gaisheta ba “Baka ga Yaya Deejah bane?” Ya mayar da kallonsa inda take nuna masa ba tare da ya ganeta ba ya ce “Ina yini?” Ta amsa masa da sakakkiyar murya Ummeey ta ce “Na san dai baka shaidata ba, to surikarka ce Yayar Ayra ce ita Ayran take bi.” Ya ‘dan saki fuska ha’de da sabunta gaisuwar sannan ya mik’e da sauri yana duban Ayra “Ki wuce ki shirya da sauri mun kusa makara kuma ba mamaki kina da kaya ke za ki yi delaying ‘dina.” Mamaki ya kusa kashe Ayran a zaune ganin yarda yake mata magana murya a nutse cike da kulawa. “Ai kuwa mace ba za’a rabata da shirgi ba, Maza Ayra ki je ki shirya sai mu sauke ku a airport ‘din mu wuce.” Ta mik’e ta shige ‘dakinta tana sake jaddada mamakin makircin Turakin. Tsaf ta shirya cikin wata doguwar Riga mara nauyi sosai light blue ta yane kanta da mayafin rigar ba k’aramin kyau ta yi ba duk da bata shafa komai a fuskar ba sai powder da lip balm. Tattausan k’amshi ne a jikinta wanda in dai ba ka matso kusa da ita ba bai zama lallai ka ji shi ba. Ta saka Blue shade ‘dinta a jaka sannan ta watsa chewingum da sweet a jakar. Takalmi rufaffe ta saka duk da yana da ‘dan tudu ka’dan. Tunda ya fito yake duban agogo yana tsaki k’asa-k’asa yarda ba za’a ji shi ba. Gaba ‘d’aya falon suka zuba mata ido ganin yarda ta fito kamar a saceta a gudu, shi ‘din ma ta k’asan ido yake kallonta yana fa’din ’Me Kyan ‘dan miciji.” Babban akwatin ya kalla sai ya ji Ummeey ta ce “Ke Tayseer za ki iya jan akwatin ne, ga mijin ta Ai da kin bari ya taimka mata ya yi koyi da sunnar Manzon Allah.” Da sauri ya ja Trolley ‘din don da gaske sun kusa makara. Su Ummeey suka bi bayansa bayan Deejah ta kashe duka switch ‘din gidan tana jin kamar ta saka kuka haka kawai take kewar rabuwa da Ayran. Har Airport suka rakasu suna tafe Ummeey tana sake jaddada musu muhimmancin aure da zaman lafiya a cikinsa. Turaki ji kawai yake don duk abinda ta fa’da ya san sa kawai dai akan wannan yarinyar ne ba zai gwada ba, haushi yake ji sosai idan ya tuna yarda ta sarayar da mutuncin ta a kan titi, shi kuma irin jararabawarsa kenan bai tab’a zina ba amma ayi ta aura masa mazinata. Suka yi sallama kowanne da guntun hawayensa a idonsa Deejah dai kasa daurewa ta yi sai da ta saki kukanta sosai. Sun shiga jirgi Ayra ta dinga duban jama’ar kowa zata gani sai ta ganshi a kan trolleyn sa da jibgegiyar rigar sanyi da hula a saman trolleyn, shima kuma Turakin haka ta gansa da su. Bata dai yi magana ba ta shige ta bi bayansa tana kallon yarda yake wani ha’de rai yana mazewa kamar wanda aka gayawa bak’ar magana. Suna zama yana sakin tsaki musamman ganin yarda wani ya zubo mata ido kamar zai lasheta murya k’asa-k’asa cike da Takaici ya ce “Matsalar ka auri yarinyar da ta tab’a yawon duniya kenan, duk inda ka je da ita sai ka samu wanda ya santa dubi dai yarda wancan yake kallon Ki da alama ya tab’a mu’amalantarki.” Da sauri Ayra ta ‘dago tana kallonsa ha’de da kallon mutumin da yace yana kallonta sai kuwa mutumin ya saki murmushi ha’de da ‘d’aga mata hannu ya ce “Ayra Gaya kwana biyu?” Wata hautsinawa cikin Ayra ya yi ganin Kallon da Turaki yake mata cikin wani irin razanannen kallo fuskar nan tasa kamar an masa albishir da mutuwar Ummeey, murya a sark’afe ya ce “Ta shi ki koma wajensa wa ya sani ma ko ke kika sanar da shi tafiyar da za mu yi ya biyoki idan yaso ku je can ku cigaba da abinda kuka saba…… Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe 38. 💔💔💔💔 A tsorace Ayra ta zuba masa manyan idanunta masu kama da an ‘diga zaiba a ciki, wani irin hucin b’acin rai yana fitowa tun daga zuciyarta har zuwa mak’ogaronta tana furzar da shi ta k’ofofin hancinta, shi ‘din ma idanun nasa wanda ake kira da sexy eyes ya zuba mata yana jin kamar ya shak’eta ya daina ganinta ya huta da takaicinta da yake cin ransa. “Bar tsareni da ido ko sharri na miki? Kina ji dai Ai ya ambaci sunanki, ki mik’e ki koma wajensa kafin na aiwatar da abinda raina yake gaya min.” Ya fa’da yana sake nutsar da idanunsa cikin nata. Ga mamakinsa sai ya ga Ayran ta saki ajiyar numfashi tana sakin murmushi lokaci guda ha’de da mik’ewa “Shi wancan ‘din da kake gani ya fiye min kai sau dubu, kuma yanzu zan k’arasa wajen nasa.” Ta ‘d’au jakarta tana shirin ficewa daga inda take a zaune. Ganin da gaske take bai san sanda ya saka k’afa ya kwarfo ta ta fa’do cinyarsa yasa hannu ya rik’e mata hab’a “Ni zaki rainawa hankali? Tafiyar da kike shirin yi?” Ya fa’da yana jefa mata wani irin kallo da yasa tsigar jikinta ta tashi, shi kansa zuciyarsa harbawa take da sauri dalilin kusancin da suka samu sosai a tsakaninsu. Bai ‘dauke idon ba ya dai san ya samu galaba a kanta ganin yarda ta lumshe ido zuciyarta na harbawa sosai “Tashi ki je, na ce ki tashi ki je gurin wanda ya fi ni muhimmanci.” Kasa mik’ewar ta yi illa zamewa da ta yi ta koma mazauninta tana mayar da numfashi a hankali, idanunta a lumshe Turaki kuwa ya sake tsare gira ganin yarda mutumin ya mik’e ya iso inda suke. A Karon farko ya mik’awa Turakin hannu, kamar ba zai ba shi ba kuma sai ya ba shi fuskarsa a ha’de, shi kuwa mutumin sai ya sake mayar da kallonsa kan Ayra Gaya yana sakin murmushi ya ce “Ba ki gane ni ba ko? Brother mijin Yayarki Majeeda ne, sau ‘daya nima na tab’a ganinki a gidanta a nan na shaidaki, so ya gida?” Ayra ta saki ajiyar zuciya tana kallon Turaki ta saki murmushi ha’de da cewa “Gida Alhamdulillah, nagode sosai.” “Bakomai nima tare da iyalina nake, yanzu za su shigo sai ku gaisa.” Ayra ta ‘d’aga kai shi kuma mutumin ya shige. Sai sannan Ayra ta sake mayar da kallonta kan Turaki ta saki murmushi ha’de da fa’din “Zato zunubi…. Allah ya yi mana sakayyar k’azafin da ka yi mana.” Daga haka ta mayar da kai tana lumshe ido da k’ok’arin mayar da k’wallar da take son zubo mata. Shiru cikin jirgin ya ‘dauka dalilin sanarwa fara tashi da jirgin zai yi kowa yana addu’a a cikin zuciyarsa. Shi kuwa Turaki turaren Ayra ne duk ya bi ya takura masa kamar a jikinsa aka saka. “Kada ki sake saka turare idan za ki fita ba na so.” Ya samu kansa da fa’da cikin isashshiyar murya ba tare da ya kalleta ba. Ayra ta gefen ido ta kallesa tana ‘dan turo baki kafin ta ce “Kafin ka san haramcin hakan na fika sani.” “A saboda kin girmeni kin kuma rigani shiga islamiyya ba, ki rufe min wannan bakin naki kafin na yi maganinsa ta tilas, Sai tsiwar tsiya kawai.” Ya fa’da yana jan tsinin hancinta. Ayra ta kautar da kai ha’de da jan bargon cikin jirgin ta k’udunduna saboda barcin da ya fara fisgarta. Turaki murya k’asa k’asa ya ce “Ai ba ki ma fara jin sanyi ba yarinya sai mun je Moscow zan ga uban da zai baki Aron rigar sanyi da kika taho haka wai ke y’ar gayu.” Gaban Ayra ya yi wani irin duka don sosai ta san kanta bata son sanyi ko ka’dan don tana da cutar pneumonia mai k’arfin gaske. Ta ware ido tana kallonsa “Amma baka fa’da min ba tun a gida.” “Ba zan fa’da ba, ke duk bincikenki ba ki tab’a binkito Moscow garin sanyi ba ne, ai dai kin san Rasha ba sauk’i a wajen sanyi to Moscow da ya zama babban birninta sai ki ke tunanin zai zama garin zafi… mhmn za ki gane baki da wayo.” Ayra ganin da biyu yake mata mugunta sai ta maze ta masa banza ta nuna masa ba damuwa. _____________________ *Moscow* Sheremetyevo Alexander S. Pushkin International Airport. Bayan wahalce wahalcen tafiya, da Transit Allah ya isar da su babban filin tashin jirgi na Moscow. Tun daga yanayin da Ayra ta gani ta window na dusar k’ank’ara da take zuba a garin Ayra ta tabbatar da maganar Turaki na zuga sanyin da ake a garin. Hankalinta ya tashi musamman ganin yarda kowa yake aikin saka rigar sanyinsa da hula har da safa, ta dubi yaloluwar rigar da take jikinta sai ta ji k’irjinta ya buga. Duk abinda take Turaki na kallonta yana sakin murmushi k’asa-k’asa kafin ya ja trolley ‘dinsa yana kallonta ya ce “Shall we?” Ayra ta ‘d’aga masa kai jikinta a mace ta bi bayansa tunda ita tata akwatin aunata aka yi sabida girmanta. Haka suka fice daga cikin jirgin suna zura k’afarsu a step ‘din jirgin Ayra ta ji wani huci mai kama da k’ank’ara ya buso fukskarta da sauri ta k’ank’ame hannayenta a k’irji ta fara jin hak’oranta na ka’dawa da gaske ake sanyi ba na wasa ba, ba kuma irin sanyin mu na Nigeria ba. Tana hango masu sanye da jibga jibgan rigunan sanyin ma suna aikin k’udundune jikinsu masu mata kuma suna shigar da su jikinsu. Sai ta zama abin kallo a wajen mutane ganin yarda take sanye da y’ar shafal ‘din After dress. Sosai jikinta yake rawa hak’oranta na ka’dawa da k’arfin gaske kamar za su datse harshenta. Turaki yana gaba bai san abinda ake ba, tun Ayra na k’ok’ari har ta gagara don nunfahshinta ya fara fita sama sama kamar Athmatic tuni ta samu waje ta zauna tana mayar da numfashi. Maganganun mutane ne suka ankarar da Turaki ya juya don ganin me ke faruwa yana janye wayar da yake yi daga kunnensa. Da sauri ya ware ido ganin Ayra zube a k’asa ta k’udundune ga mutane turawa sun yi cincirindo a kanta. Bai san sanda ya saki akwatin hannunsa ba da sauri a ‘dimauce ya k’arasa in da take, hankalinsa a tashe ya ‘dagata ya mannata da k’irjinsa sai dai tuni numfashinta ya fara season. Da azama ya janye rigar Sanyin da take jikinsa ya shiga kiciniyar saka mata yana jero duk addu’ar da tazo bakinsa don da gaske gani yake kamar zai rasa Ayra a gab’ar da yake jin sonta yana neman kassara masa rayuwa. Bata numfashi don numfashin ya tsaya cak hakan yasa mutane suka nemi kawo masa ‘dauki ta hanyar kiran ma’aiktan da ke cikin airport ‘din aka zo da ambulance aka ‘dauketa da gaggawa bayan an manna mata oxygen a hancinta. Tuni Turaki ya gigice ta lafiyar Ayra kawai yake don haka yana zaune gaban gadon akan idonsa ake komai duk da k’ok’arin doctors ‘din gani yake kamar ba sa aikata komai kamar ya amshe su yake ji, sun kuma rok’esa ya fita ya k’i don baya jin ko taku ‘d’aya zai iya k’arawa daga inda yake. Da k’yar suka samu nasarar janyo numfashin nata ta fara fisgar sa da sauri kafin a hankali ta bu’de idonta tana sauke su kan Turaki da ya kafeta da nasa idon hannayensa damk’e da nata hannayen yana murzasu cikin wani salo. A hankali ta sake janye idonta tana lumshe su kafin k’ak’karfan nunfashin ya biyo bayan barcin da ya ‘dauketa mai bayyana tsananin galabaitar da take ciki. Turaki ya saki ajiyar zuciya yana kaiwa lab’banta gamsashshiyar sunbata ba tare da jin kunyar likitocin ba duk da suma ba su da kunyar ya da’de yana tsotsar bakin nata abinda ya da’de yana mafarki kafin ya janye yana mayar da nasa nunfashin da yake fita da wata irin nauyayyiyar soyayyar Ayra mai shirin b’alla k’irjinsa cikin wata irin murya ya ce “Ya Rabb save my wife you know she is my everything.” Ya fa’da yana lunshe ido sai ga wata siririyar k’walla tana zuba daga idanun nasa. Da gaske ainun ya tsorata sosai gani yake kamar zai rasa Ayra a gab’ar da ya shirya mallaka mata rayuwarsa gaba ‘d’aya tunda ya kasa jumurin jurewa idan ba so yake ya samu matsala a gab’ban jikinsa ba da gaske wahalar da soyayyarta take ba shi ta kai mak’ura kullum barcinsa a wahale yake yinsa, shi yasa ya ji ya amince zai karb’eta a duk yarda ya sameta tunda ba budurcinta yake yiwa ba zallar so mara algus yake mata. Tafin da likitocin suka masa ne ya ankarar da shi abinda ya yi ‘din, sai kawai ya sakar musu murmushi yana murza hab’arsa mai cike da kwantaccen gashin da ya k’arawa kyansa kyawu mai ban k’aye. Har tsakiyar dare yana tare da ita sallah ce kawai take tashinsa daga wajen. Ta da’de tana barcin kafin ta samu ta farka sai sannan ta tuna a inda take ta dinga bin ‘d’akin da kallo kafin ta sauke kallonta a kan Turaki da ya zuba mata nasa Sexy Eyes ‘din ya kamo hannunta yana matsawa A hankali “Ya jikin?” Muryar da ya mata magana ce ta saka ta k’ara dubansa da kyau tana tantama idan daga bakinsa furucin ya fito. Ya ‘d’aga gira yana sake murza hannun a tausashe ya lumshe ido kafin ya ware su a kanta “Am sorry! Me kike so yanzu?” “Gida” ta fa’da cikin karyayyiyar murya Ha’de da k’ok’arin zare hannunta yana murmushi ya ce “Wane gidan?” “Gidan Amma.” Ta fa’da hawaye na zubo mata kamar an kunna famfo wannan karan hawayen ya kalla sosai kafin ya ‘dauke kai cikin kasalalliyar murya ya ce “Kukan mace shine abu mafi munin saurare a wajena Don Allah ki bari” kukan ta sake fashewa da shi sosai ya ware ido yana kallonta kafin ya kai bakinsa daidai kunnenta yana fa’din “Kina son na saka ki shirun dole ne?” Yanayin kallon da yake mata ne yasa ta runtse ido da k’arfin gaske, ta caku’de fuska kafin ta ce “Please ka min booking flight na koma gida sanyin garin nan zai hallakani.” “Zan miki maganin sanyin, za ki daina ji in dai kin bani dama bari mu isa masauki.” “Da me zaka min maganin sanyin?” “Da jikina.” Ya fa’da yana k’ank’antar da idanunsa cikin nata…. A razane ta dinga kallonsa tana son gano abinda furucinsa yake nufi…. A yi hak’uri uzuri ne yau ya tsareni shi yasa za ku ga typing ‘din ka’dan. Nagode…😊 Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe. 39. ❤️♥️❤️♥️ Kokawa ta fara yi da yawun bakinta da k’yar ta samu ta ha’diye Wanda ya tsaya mata a wuya. Ba ka’dan ba furucinsa ya razanata me take shirin ji? Me yasa yanzu yake son kusanta kansa gareta? Bayan a da ba shi da ra’ayin hakan asalima k’yama muraran yake nuna mata, me ya canja zuciyarsa shin ya daina mata kallon fasik’ar ne? Karuwa? Kamar yarda a lokuta da dama yake kiranta. Tabbas kuwa an zo gab’ar da zata ba shi mamaki zata nuna masa Jikin Ayra Gaya mai tsada ne ba kuma za’a same shi karabiti ba tana da ajin da zata ja zarensa har sai ya raina kansa, kuma bata fatan gamayya da wani ‘da namiji da sunan auratayya duka ta tattarasu ta jefa su a mahalli ‘daya, sunansu ‘daya halayensu ‘daya ba su da wani banbanci sai ta fuskar kamanni. Tunanin da take yi kenan a ba’dini yayin da shi kuma ya zuba mata masifaffun idanunsa masu nuni da zallar soyayyarsa da buk’atuwarsa zuwa gareta. “Kin yi shiru?” Ta jiyo sautin fitar furucin nasa kamar ba nasa ba kamar aro muryar ya yi yake mata magana da ita, ina waccan Kausashshiyar muryar mai fitar da sauti cikin isa da gadara wato yanzu sak’on yaudararsa yake son isar mata tunda ya kwa’daita da jikinta ashe kuwa za su kwashi y’an kallo. Ta ja siririn tsaki da ya fita ta iya tsakanin lab’banta “Na gaya maka ba abu mafi soyuwa gareni a yanzu irin na ganni a Nigeria….” Mhmnm ya saki ajiyar zuciya yana matsawa da jikinsa sosai kusa da ita fuskarsa tana neman gugar tata don har tsinin hancinsu yana gugar juna ga numfashinsu da yake sauka lokaci guda yana dukan junansu, numfashin da yake sake hargitso masa da kwantacciyar sha’awarsa ta shekara hu’du, ita ‘din ma hakan ce ya kasance a tare da ita kusancin nasu ya saka ta a wani yanayi da ya matuk’ar gigita tunaninta. Da sauri ta ja jikinta har tana ha’da k’irjinta da nasa abinda ya saka shi saurin runtse ido yana fitar da wani sauti na ‘Ahhhh’ a hankali ya runtse idonsa yana mayar da gangar jikinsa jikin kujera hannayensa cushe cikin gashin kansa yana fisgarsa a hankali cikin zuciyarsa yake furta yarinyar nan nema take ta k’ureni. Shiru ya bak’unci ‘d’akin kowa ya afka cikin wani yanayi da shirun shine yafi amfani a lokacin don dai magana ta furucin baki ba zata iya fita ba, idanunta a runtse suke yayinda shi kuma ya kafa mata ido yana kewaye jikinta da kallo ba inda bai yiwa kallon k’urilla ba a ranar fatansa kawai Allah ya kai damo ga harawa ya zubar da abinda yake cikin jikinsa yake wahalar da shi tsawon shekara hu’du. Bata bu’de idon ba shima kuma baya fatan ta bu’de yafi son ya morewa kallonta yana tunanin ta sigar da zai bi ya mallaki zuciya da gangar jikinta. Idanunta a runtse amma ta san idanunsa a kanta suke yawo. “Na gaya maka gida nake son zuwa.” “Na ‘daure ki ne?” Ya fa’da da yanayin fara gajiya da maganar gida da take masa. Ta ware ido tana kallonsa shima ‘din kallonta yake kafin ya furta “Ki k’addara ke da gida sai nan da shekara cif idan muna da yawon rai.” “Wasa kake amma?” Ta furta cike da mamakin kalamansa “Time will tell bari mu ba ko wasan nake.” Shima amsa ya bata yana ‘dauke kansa don ya lura kamar laushin da ya fara masa ne yake nema yasa ta rainashi bata son har yanzu daurewa yake ba idan ya tuna shashashun mazan da ta yi hul’da da su, don haka kafin komai ma ya shiga tsakaninsu sai sun je an musu gwajin HIV da STD don ba zai je ya samu cuta a banza ba. “Kin tab’a test ‘din HIV da STD?” Ya samu kansa da jefo mata tambayar da shi kansa bai shirya yinta ba illa sub’utar harshe. A gigice ta ‘dago tana masa kallo kafin ta ce “Whatttt???” Ya kafe ta da ido duk da kunyar ta na neman kama shi sai ya ga kamar tambayar bata dace ba, amma kafaffiyar zuciyarsa ta hana hakan yi masa tasiri fuska a ha’de shima yana ‘dan ware ido ya ce “Yess! Kin san duk wanda yake yawon banza ya kamata time to time ya dinga test ‘din nan.” Numfashinta ne ya fisga da k’arfi da b’acin rai ta sauke idanunta k’asa don yak’i da k’wallar da take son zubo mata sam bai dace ta yi masa kuka ba tunda shi bai san mutunci ba “Ina son rayuwar aure da ke, amma on One condition dole ki je asibiti a miki wannan gwajin.” “Idan kuma na k’i fa?” Ta fa’da tana tsareshi da idanu da yake hango matsanancin b’acin rai a cikinsu “Fine and good sai na bar ki da y’an iskan ki, ni kuma na auro Kamila.” “Shine abinda ya fi maka sauk’i don wallahi da na ha’da gangar jiki da kai gwara na mutu..” Da sauri ya ‘dago yana kallonta da gaske ya hango matsananciyar tsanarsa a idanunta cikin b’acin rai ya ce “Kin gwammaci ha’da jiki da y’an iska a kan ni Mijinki na sunnah.” Tana girgiza kai alamar tabbatarwa ta ce “Sun fiye min kai sau dubu, su cikakkun maza ne da suka amsa sunansu Maza idan nace cika ina nufin cika ta zahiri da ba’dini kai kuwa fa na tabbatar yarda kake da hasken fatar nan baka da k’warin da zaka iya gamsar da Mace rago ne kai tabbas!” Bata san sanda ya mik’e ba ita dai kawai ta gansa a gabanta yana huci kamar zakanya “Ni kike kira ragon namiji?” Ya ciji lab’bansa “Lokaci ya zo da ya kamata na ankarar da ke menene ma’anar ragon namiji tabbas a yau ba sai gobe ba zan nuna miki ragontaka ta…” “Me zai saka ka kusanci sauran wasu?” “Rashin kunyar da kika min ne zai saka na banbance miki tsakanin aya da tsakuwa wallahi sai kin raina kan ki ki tanadi duk wani magani da kika san zai samar miki da sukuni a irin gurzar da zan miki tunda ke ba ki da kunya duk dai na san hanyar a bu’de take warwar Amma yau zaki banbance tsakanina da sokwayen mutanen da kike kira sun fi ni.” Sosai ta tsorata da furucinsa sai dai ko ka’dan bata nuna masa a fuska ba, don k’arfin hali sai cewa ta yi “Sai mu zuba mu gani.” Ya runtse ido yana jin amsa kuwwar furucinta ba ka’dan ba ransa ya b’aci ji yake kamar tun a yanzu ya fara fatali da duk wata sutura ta jikinta ya je mata a Jaruminsa kamar yarda Hibba Uwargidansa ta sha Kambama shi da sarautar jarumtaka ya shafi sajensa yana futar da murmushin takaici. Sai da drip ‘din da aka saka mata ya k’are tsaf sannan suka tafi don samun motar da Zata kai su Five star Hotel da ke garin Moscown anan yake son ya kafa mata tarihi mai wuyar gogewa a kwanya. Ayra kam gaba ‘d’aya ta tsure da jin furucinsa kawai daurewa take kuma a yanayinsa bata hango zai janye daga alk’awarin da ya ‘d’auka ba, babu alamar haka don kallonta kawai yake yana sakin murmushin da kai tsaye ta kira na mugunta. D’aki ‘daya jal ya kama musu mai masifar kyan tsiya an gyara gadon da katifa mai wani irin laushin tsiya ga k’amshi da sanyi ko ta ina yana tashi daga ‘dakin. Ayra kamar ta yi kuka ta shiga kallonsa murya na rawa ta ce masa “Nan ‘din nawa ne ko naka?” “Namu ne.” Ya bata amsa yana tsalle a kan gadon cikin nisha’di kafin ya mik’e kansa a kan hannunta ya ce “Madam di Madam ya dai na ga bakin tsiwar ya mutu.” “Ba zan iya kwana ‘daki ‘daya da namiji ba.” Ta fa’da tana kallonsa narai narai da idanunta “Yau kika fara? Ai kin Riga kin haddace yarda ake kwana ‘daki ‘daya da namiji tunda har kina banbance rago da gwarzon namiji, don haka ki saki jikinki Malama bana son wani pretending just like you don’t know anything.” Ya fa’da yana tsareta da wani irin kallo da bai tab’a mata ba sai yanzun. Ayra ta saki ajiyar zuciya kafin ta kalli ‘dakin ta ga ko y’ar kujera babu alamar dama da gayya ya kama ‘dakin ko kuma don masu honey moon aka k’irk’iresa. “Duk ba wannan ba ni dai ka taimakeni ka kama apartment.” “Ban ga dama ba.” “Bari naje ni to na kama.” “Bismillah.” Ya fa’da yana kashe mata ido ha’de da nuna mata hanya da sauri ta ‘d’au hand bag ‘dinta ta zuge tana addu’ar Allah yasa ta taho da Dollar card ‘dinta sai dai wayam bata gansa ba, sai tarkacen Atm card da ba zasu mata amfani a k’asar ba, ta saki tsaki tana cillar da jakar, da mamakin yarda aka yi dollar card ‘din ya yi b’atan dabo bayan da kanta ta saka shi a ciki. Shi kuwa yana kwance yana sakin dariya k’asa k’asa don tuni ya sace Dollar card ‘din saboda irin wannan kada ta zo tana masa tak’ama da ku’di. D’an k’asan gadon ta samu ta raku’be ta zauna tana jin kamar ta saka hannu a kai ta kurma ihu wannan wace irin masifa ce? Wato shikkenan bata da mafita kenan sai ta zama k’ark’ashinsa ya juyata kamar yarda yake so, da ace da Dollar card ‘dinta da sauk’i zata iya booking flight ta wuce Nigeria idan taga dama, to yanzu ko tarkacen numbers ‘din da suke ciki bata haddace ba. Tana kallo ya ta shi ya zaro towel a trolley ‘dinsa fari tas da shi daga ganinsa Sabo ne. Ta runtse idonta ganin yana shirin cire kaya a gabanta duk abinda take yana kallonta ta mudubi ya tab’e baki a ransa ya ce ka ji y’a kamar bata tab’a ganin namiji a tub’e ba. Ya cire kayan daga shi sai boxer ya shige toilet yana jin wani nisha’di a ransa ko abinci a hotel ‘din za a basu ba inda zai je. Tana jin ya rufe k’ofar toilet ‘din ta mik’e da sauri ta hau binciken kayansa ko zata ga card ‘dinta sai dai ko alamarsa bata gani ba. Har ta gaji ta zauna tana haki yanzu kam ta amince bata da mafita, lamarin sai addu’a. Wanka ya yi sosai sai zabga k’amshin turaren wanka na companyn Makari yake harta da kansa sai da ya wankeshi ya fito sanye da rigar wanka yana tsane kansa da hand towel. Ita kuwa tana jingine da gado a takure barci ne yake fisgarta ga shi tana jin yunwa ga gajiya wanka take son yi amma ta Ina zata fara shiga toilet yana cikin ‘dakin. A kanta ya tsaya yana combing kansa hakan yasa take jin ‘d’igar ruwan kansa a fuskarta, ta bu’de idonta mai nuna alamar gajiya ya ce “Ki tashi ki yi wanka bana son k’azanta.” Murya a raunane ta ce “To don Allah ka fita ka bani 20 minutes na shirya sai ka shigo.” “Ashe kuwa ba za kiyi wankan ba, idan baki yi wasa ba da kaina zan shiga toilet ‘din na cu’deki, me kike b’oyewa ne jikin da wasu banza suka gama ganewa?” Ta ‘dan turo bakinta tana bu’de akwatinta gwara ta ‘dau kayan ta shiga toilet ta yi wankan ta shirya a can. Takaici ne ya kusa kasheta ganin kayan da suke cikin akwatin, sai lokacin ta san da tsiyar da Deejah ta shuka mata. Ganin yarda ta yi kasak’e tana kallon kayan ya saka shi matsawa shima yana dubansu “Ya dai? Ko ba kayanki bane?” Cikin takaici ta rufe akwatin tana fa’din “Nawa ne, amma ba ni na shirya kayan ba.” Da mamaki yake bu’de akwatin yana fa’din “Then so what? Kayan ne ba su miki ba.” Ya fa’da yana ‘d’aga kayan kafin ya saki murmushi “Godiya dubu ga wacce ta ha’da kayan kamar ta san irin wanda nake so kenan.” “Ni kuma ba zan saka su ba.” Ta fa’da kamar ta yi kuka tana hawa Deejah Allah ya isa a zuciyarta “Me ye sabo a cikin kayan da dama su kika saba sawa ki zumbula hijabi sai kin je wajen Mazan banza ki bu’de jiki, ko nine kike min bak’in cikin ganin halaliyata? To wallahi sai kin saka ko ki yi yawo tsirara.” Kife kanta ta yi a cinya tana sakin kuka don ta kasa danne kukanta, duk da kukan ya tab’a zuciyarsa haka ya danne ya maze yana fa’din “Ki tashi Malama ki je ki yi wanka, ko na ‘dauke cak na miki don wallahi a wannan daren sai na nuna miki asalin ragon namiji.” K’irjinta yana dukan uku uku ta ‘dago tana kallonsa. Ba ta yi aune ba ta ji ya ‘dagata cak ya nufi toilet da ita. Ta fara wutsil wutsil da k’afafu Amma ko gezau bai yi ba har sai da ya direta a ha’dadden toilet ‘din kafin ya ja k’ofa ya rufe yana fa’din “20 Minutes na baki ga abinci nan an kawo ki ci ki k’oshi don ba ‘daga k’afa..” ya zauna gefen gadon yana sakin murmushi shi ka’dai kafin ya fara fesa turaruka a kowane gab’a lungu da sak’o na jikinsa. To fa! Wannan dare akwai kallo Allah sarki Ayra za’a shiga hannun Maza zaki san kin kira Turaki Ragon Namiji… kafin ta fito daga wankan bari mu lek’a Nigeria mu ji wainar da ake toyawa. ______________ Tsaf Amma Talatu ta shirya cikin tsadaddiyar atamfarta super wax. Sai zabga k’amshin turaren gabbasa take wanda ta turara kayanta da shi. Gidan Hameeda take son zuwa, don ta gaji da k’orafin da Hameedah take mata a kan rashin zuwanta. Drivernta da suka ‘daukar mata shi yake janta a motarta suna tafe tana saurarar karatun alk’ur’ani cikin suratul mulk k’ira’ar Sudais. Sai da suka je bakin gate ‘din sannan ta kira Hameeda ta sanar mata zuwanta. Murna da farin ciki suka ziyarci fuskar Hameedan da sauri ta kalli Tayseer da take shirin shiga kitchen ta ce “Maza bu’dewa Amma k’ofa.” Ita kuma ta mik’e ta isa anthem ‘din gidan ta tsaya tana tsimayin zuwanta. Da farin ciki ta tareta suka isa cikin falon tana fa’din “Ai dama na saka a raina in dai baki zo ba ni da kaina zan je a satin nan, don na k’agu na ji k’arashen labarin Kabiru Wallahi da kuma irin k’addarar da ta afkawa Ayra da yasa mata tsanar Maza. Ina son jin wani laifi Kabiru ya mata har haka?” Amma da ta shigo da karsashinta tuni duk wata fara’a da walwalar fuskarta ta arce, idanunta suka ka’da suka yi jazur ba abinda take sai sauke ajiyar zuciya tana kokawa da numfashinta da yake neman barin k’irjinta. Ba labarin Ayra bane bata son bayarwa, sai dai a duk labarinsu shine labari mafi muni da ko son tunawa ba tayi balle ta furta da bakinta. Yanzu me Hameeda take son tace mata, da zata iya tabbas da ta yi mata k’arya don ko kad’an bata son fitar labarin da ta kira bak’in labari daga bakinta. Sai dai ba abinda zata iya b’oyewa Hameeda tana jin Hameedar kamar y’ar uwarta ita take kalla Makwafin y’ar uwa ta jini da ta rasa don haka murya na rawa cikin hawaye ta ‘dago tana kallonta kafin ta yi k’asa da kanta ta ce. JikarNashe ce! Takaicin Uba… Nazeefah Nashe. 40. 💔💔💔💔 Idanun Talatu na ‘disar da hawaye ta dubi Hameeda da ta zuba mata ido cikin tarin jin tausayinta, don dai ta san ko mai ma Talatun zata fa’da ba zai zama mai kyau ba. Ta ja ajiyar zuciya itama tana jin taruwar hawaye a nata kwarmin idon, dafa Talatun ta yi cikin muryarta mai bayyana raunin da zuciyarta take ciki ta ce “In dai ba kya son tuna labarin Talatu ki bar shi nima na hak’ura da ji, daman abinda yasa nake son jin don na ‘dauke ki kamar y’ar uwa ne ga maganganun da suke ya’diwa a gari na mutanen da suke ganin ba kiyiwa Kabiru adalci ba, don haka ni dai na hak’ura.” Talatu ta girgiza kai ha’de da share hawayen da yake kwaranya daga idonta kamar k’orama murya a raunane ta ce “Fa’da miki ba zai zama aibu ba, nima hakan da zan yi zai saka na samu sauk’i a zuciyata don tunda abin ya faru ba wanda na gayawa ina ta fama da shi a zuciyata na tabbata kuma barinsa a raina shine yake assasa min ciwo a zuciyata, don haka na shirya fa’da miki don ina jinki kamar y’ar uwata ta jini…” GA YARDA LABARIN ZAI CIGABA…. Jin furucin Kabiru na cewa ya bar mata yaran yasa ta ji wani taratsatsi a zuciyarta ga shi har yana ikirarin siyar da gidan zai yi. Ta dinga kallonsa kamar mutum mutumi ta ma kasa motsi saboda tsananin b’acin rai da girgizar zuciya, Ina Kabiru yake son ta kai yaran da yake ik’irarin ya bar mata halak malak har duniya ta na’de a ina ake haka a rayuwa bayan tana sane da cewa musulunci shi ya k’allabawa wahalarsu cin su shan su, suturarsu duk suna k’ark’ashin Kulawarsa ne, duk da hakan ba sabon abu bane a wajenta dama ta saba duk wani nauyinsu a kanta yake, abu mafi ciwo a wajenta maganar cikin da yake neman sheganta mata. Murya a raunane ta ce “Kabiru ka ji tsoron Allah, kai da kanka ka san cikin jikina naka ne, kuma ka san ban tab’a kusantar wani ‘da namiji ba me yasa kake son sheganta shi tun kafin koma meye a cikin yazo duniya?” “Saboda bana son koma me za ki haifa? Shi yasa na gwammace na sheganta shi ‘din kuma maganar na ji tsoron Allah idan ban ji tsoron saba tsoronki zan ji? Kin ga wannan ba zata fishsheki ba ki tattara yaranki ku yi gaba ko bara ku je ki yi a birni ki ciyar da su ba matsalata bace, abu ‘d’aya da nake son ki lura da shi ki kuma ajiye a ranki duk inda za kije ki dinga tuna sark’afaffiyar igiyar aurena a kan ki, don ba zan yi saken da zan sake ki gaba ‘daya ni kuma na talauce ba.” Hawaye ne kawai yake bulbula daga idanun Talatu kafin ta samu k’warin gwiwar cigaba da tattara kayansu don yanzu ta tabbatar ba su da wani gata sai nata sai na Allah, ta amince ita zata maye musu gurbin Mahaifi da Mahaifiya gaba ‘daya, tana fatan Allah ya agajeta ya bata ikon ‘daukar duk ‘dawainiyarsu da tarbiyyarsu gaba ‘daya. Zuciyarta ta bushe ta ji gaba ‘d’aya garin Shagogo ma ya fice mata daga rai bata burin ta wayi gari a cikinsa. Da sauri take komai su Majeeda suna tayata da wasu aiyukan. K’arfe 4:00 na dare suka bar garin Shagogo, garin da ba zasu k’arar da farin ciki ko ‘d’aya a cikinsa ba sai tarin bak’in ciki, ko a mafarki Talatu bata fatan ta sake ganin garin na Shagogo ‘daid’aikun mutane ne ba zata manta da su a cikin su ba, ba kuma zata tab’a mance alherinsu ba cikinsu har da Mai gari. Bus da take shirin tashi ta shiga garin kano suka shiga, ta kama musu kujera biyu suka gwamutsa suka tafi ba tare da ta san inda zata dosa ba, kawai dai ta san garin na Kano akwai girma akwai kuma bayin Allah masu taimakon jama’a. Tunda suka sauka a garin suka fara yawo lungu lungu ba tare data san inda zata yada zango ba, kawai tafiya take yaran suna tare da ita, idan Deejah ta gaji sai Majeeda ta goyata har suka isa wata unguwa masu manyan gidaje kana ganin unguwar ka san masu hannu da shuni ne. Ta jikin layukan unguwar Majeeda ta karanta sunan unguwar Shara’da phase 2. Gajiya ce ta sa ta fara musu yawa ga yunwa ga kuma k’ishirwar da ta addabesu. Talatu ta samu wata mai masara a bakin titi ta siya musu da ragowar y’an ku’din da suke hannunta ta kuma siya musu ruwan leda sannan suka kutsa cikin layukan unguwa addu’oi fal a bakinta dafatan Allah ya kaita gidan da za a agajeta da y’an y’ay’anta ta amince zata rabasu aikatau a cikin gidajen da suke unguwar idan yaso ta rik’e Deejah kawai a wajenta. Wani gida suka wuce shi ka’dai ne kuma gate ‘dinsa a bu’de da mutane almajirai a bakin gidan da alama sadakar abinci suke karb’a. Haka kawai Talatu ta ji hankalinta ya kwanta da gidan ko aikin abincin sadakar zata rok’a ta dinga yi, don haka ba tare da wani tunani ba ta k’arasa bakin gate ‘din. Suka amshi abinci kamar yarda suka ga kowa ya amsa a cikin bak’ar leda har yaranta sai da aka bawa abincin. Talatu ta jasu Gefe suka fara cin abinci hannu baka hannu k’warya. Suna nan zaune sai ga Maigadi a guje yana fa’din “Kai bayin Allah ya da haka kuka zauna anan kuna cin abinci to ku tashi maza Hajiya zata fita da mota.” Talatu ta mik’e da sauri tana janye hannayensu suka rakub’e a gefe. Daidai fitowar wata zundumemiyar mota bak’a wuluk k’irar jeep. Har motar ta wuce sai kuma suka ga ta dawo da baya. Hajiyar da kanta ta sauke gate tana kallon Talatu fuskarta da mabayyanin tausayi “Baiwar Allah daga ina?” Da sauri Talatu ta zube a gaban Hajiyar murya cike da ladabi ta ce “Hajiya a taimaka min aikatau nake nema don girman Allah.” Hajiya ta yi shiru tana kallon Talatun sama da k’asa nazarinta take sosai kafin ta saki ajiyar zuciya “Yanzu ina sauri Amma ga driver nan zan saka ya baki wajen zama kafin na dawo muga yarda za’a yi.” Ta fa’da tana k’walawa Drivern kira “Rabe zo mana.” Ya k’araso da sauri “Maza shiga da su Guess side idan na dawo zan gansu ina da urgent meeting ne.” Rabe ya ‘d’aga kai da sauri yana fa’din “Shikkenan ke kakarki ta yanke sak’a Hajiya da kanta zata ganki Ai ganin Hajiya alheri ne.” Ya fa’da yana shigewa gaba su kuma suka bi shi a baya. Talatu tana fatan abinda Rabe ya fa’da ya zama hakan In sha Allah, tana fatan Allah yasa k’arshen wahalarta ne ya zo. B’angaren bak’in da Rabe ya saukesu waje ne mai kyau shi ‘din ma don su dai su Majeeda ba su tab’a ganin irin ginin gidan Hajiya ba, gidane canca’dede zubin ginin turawa daga wajen gidan har da swimming pool da Garden. Nan ‘din ma babban falo ne da ya ji manyan kujeru masu kyan gaske da Babbar Tv plasma ga Ac tana sanyaya Falon. Talatu ta sauke ajiyar zuciya mai nuna tsananin gajiyar da take ciki kafin su zube a kan carpet don da kunya su zauna akan kujerar abinda ba su tab’a gani ba. Su Majeeda sakar baki kawai suka yi suna nuna k’auyancinsu zalla don har gaban Tvn da Rabe ya kunna suka je suna tab’awa suna ganin mutanen ciki kamar za suyi musu magana. Sai da Talatu ta tsawatar musu sannan suka dawo suka rakub’e suka zauna. Rabe da kansa ya kawo musu ruwa mai sanyi da wani kalar lemo da basu tab’a sha ba har da kilishi da dambun nama duk daga umarnin Hajiya Dubu. Komai sai da suka masa cin wawaso kafin su koma su Majeeda suka baje a saman carpet suna barci abin su, itama Talatun barcin take ji Amma sai ta mik’e ta shiga inda take zaton toilet ne ta ‘d’auro alwala duk da ta sha wuya sosai kafin ta iya kunna famfon. Sallah tazo ta gabatar kafin ta zauna tana lazimi da addu’ar samun dacewa a wajen Hajiyar. Sai bayan Magriba Hajiya Dubu ta shigo gidan, bata nemi su Talatu ba duk da suna ranta sai da ta isa b’angarenta ta yi wanka tukunna ta ci abinci da Sallah, sannan ta nufi b’angaren da ta saka aka sauke bak’in nata cikin takunta na nutsuwa gefenta kuma mai kula mata da hidindimun gidanta amintacciyarta kuma. K’amshin da ya cika falon ne yasa Talatu ta ‘dago daga dogon tunanin data tafi da sauri ta mik’e tana gyara zamanta ta nutsu sosai tana gaishe da Hajiyar cikin k’asa da kanta. Hajiya ta zauna tana amsa gaisuwarta don Macece ita mai tausayi musamman ga mata masu rauni. “Baiwar Allah ya sunanki kuma meye mak’asudin zuwanki nan?” Talatu a nutse ta gaya mata sunanta ha’de da cewa “Hajiya taimaka min za kiyi ko aikatau na dinga miki a kuma raba min ‘ya’yan nan suma su yi aikatau ‘din a wasu gidajen.” Hajiya ta ‘d’aga kai tana duban su Majeeda da bata hango wani aikatau da k’ananan yaran nan za su iya ba. Ta saki ajiyar zuciya ha’de da cewa “Yaranki ne?” Da sauri Talatu ta ‘d’aga kai “To ina Ubansu don dai ga ki na ganki da ciki..” Hawaye ne ya fara ‘diga daga idanun Talatu tana sakin ajiyar zuciya ta ji ta aminta da Hajiya zata iya kuma bata labarin ta ba zata b’oye mata komai ba don haka murya da rauni ta fara bata labarin. Kafin ta gama tuni duk wani annurin fuskar Hajiya ya b’ace b’at jikinta sai tsuma yake kamar ana ka’da mata gangi ta zubawa Talatu idanuwnta da suka ka’da suka yi jazur abinda ya ka’da y’an hanjin cikin Talatun ta yi k’asa da kanta da sauri tana fatan Allah yasa ba wani abu bane daga cikin labarin nata ya b’ata ran Hajiyar. Cikin b’acin rai Hajiyar ta ce “Namiji ‘dan kunama! Namiji k’anin Ajali! Namiji tabarmar k’aya! Ta sake dunk’ule hannunta waje ‘d’aya kafin ta ce “Kin zo wajen da za’a share miki hawaye Amma da shara’di…..” Talatu ta ‘dago da sauri don ta amsa mata sai dai abinda ta gani ya girgiza zuciyarta da sauri ta runtse idanunta tana jin wani tsoro na shigarta……. Jikar Nashe… (Kada a manta gobe weekend ba na posting sai dai may be za ku iya jina jibi, don kada a yi ta min waya. Nagode sosai.”) Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe 41. 💔💔💔💔 Tsananin razana ya hana Talatu cigaba da kallon matar, Ba don komai ba sai don ganin yarda Matar ta zaro idanunta guda ‘daya ta sanya shi a tafin hannunta tana kallon Talatu da razanar da ta yi ya bayyana sosai a kan fuskarta. “Wannan shine ka’dan daga illar da namiji ya yi min, bisa son zuciya da zallar mugunta ya mayar da ni mai idon roba guda. Don haka wannan labarin naki ya sake tab’a ni na ji kuma ina son na taimaka miki ko don nan gaba ki taka wani matsayin da Mijinki zai raina kansa, amma da shara’di kada ki sake ki bari ya san inda kike, duk ranar da kika bari ya gano inda kike ba tare da gama cikar burikana ba ina tabbatar miki ranar za muyi hannun Riga da ke, don haka ki kiyaye duk wata hanya da zata sadaki da shi, tunda har yanzu ya mak’ale igiya guda ta aurenki kamar yarda kika ce, banda ina son na taimakeku har ku zamo wasu da a yanzu zan saka a binciko min mara mutunci in tozarci idan ta kama har uwar da ta kawo shi duniya, sai dai a yanzu idan ya bayyana na aikata masa tozarcin ina tabbatar miki ba zai bar miki yaransa ba ko don ya k’unsa miki takaici ni kuma burina yaran nasa da yake k’yama saboda an haifesu Mata su zo su zama wani abin don na gama zai yi da na sanin k’in kula da hak’kinsu da ya yi ki rik’e shara’din a ranki ban amince ko da wasa ku ha’du da Kabiru ba a fili ko a b’oye. Idan kika min haka zan ‘dau nauyin yaranki zan sanya su Makarantu masu tsada inda za su samu nagartaccen ilimi sannan zan ‘dauki duk wani nauyinsu ba tare da na kaisu aikatau ba ha’din kan ki kawai nake buk’ata, ke kuma ga Jummai nan sai ki dinga tayata aikace-aikacen gida,Allah yasa ki zamo mai rik’e amana.” Sosai Talatu ta fara zubar da hawaye tsabar farin ciki bata san sanda ta zube a k’asa ta kai goshinta k’asa ba alamar sujjuda. Kafin ta ‘dago ta zube a gaban Hajiya Kari tana mata godiya da duk wata fasahar harshenta sai da ta tattaro don jaddada godiyarta. Hajiya ta kamata ta sanyata a jikinta tana share mata hawaye “Bana buk’atar godiyar Ki Talatu, ni don Allah na yi a kuma gurinsa nake neman sakamako, ba ni da kowa ba ni da komai, iyaye sun rasu y’an uwana an kashesu sabida son zuciya, ba ni da ‘da ba ni da jika, Mijin da nake alfahari da shi tunda yaga iyayena sun mutu yake burin ya mallake abinda aka bar min, don haka ya shiga neman rayuwata ta k’arfi da yaji har ya janyo min sanadiyyar idanu guda bayan ya turo y’an fashi su min kisan gilla don kawai ya gaje dukiyata, na samu da k’yar na tsirar da kaina daga ranar ban sake saka shi a idanu na ba, sabida yarda y’an sanda suka baza jami’an tsaro suna nemansa da kaina na kai kaina kotu alk’ali ya sake ni kamar yarda shari’a ta tanadar bayan ya ‘d’au tsawon shekaru ba amo ba labarinsa, wannan shine tak’aitaccen Tarihin Hajiya Kari. Talatu ta tausaya mata sosai kafin cikin k’asa da murya ta ce “Allah ya saka miki Hajiya, hak’ika maza da waya suna da son zuciya da rashin kyautatawa iyali Yarda kike taimakon jama’a Ubangiji Allah ya baki aljanna ma’daukakiya nagode k’warai.” Hajiya ta ‘d’aga kai kafin ta ce “Bakomai, nan sashen dama ba kowa a ciki sai ya zama naki da na yaranki. Ku dinga kwana a ciki da kitchen da toilet da komai a ciki, abincin makarantarsu su dinga dafawa a nan don ni a k’aidata bana tashi da wuri, kuma idan ina barci bana son kwarafniya. Gobe In sha Allah Zan saka Sale ya samo musu makaranta mai kyau anan kusa da mu, Sale shine babban yaro na ana kiransa Sarkin gida, sai Jummai itace amintacciyata a cikin masu aiki, sai Driver Lawal sai mai gadi Malam Rabe, Ina fatan yarda suka zamo masu amana kema za ki zamo daga cikinsu.” Da sauri Talatu ta ‘d’aga kai “To ma sha Allah, idan kika yi haka kin ceci rayuwar y’ay’anki da kanki, don kin gansu nan mun kusa shekaru ashirin da su muna zaune lafiya tausayinki yasa na amince miki zama anan idan banda haka bana son abinda zai saka min damuwa.” Daga haka ta mik’e tana daidaita zaman k’wayar idanunta da ta zaro kafin ta kalli Talatu “Ki taso maza ki amsar muku abubuwan buk’ata a store Jummai a basu kayayyakin tea da sauran tarkacen da za su buk’ata including su Sabulu toothpaste da sauransu, kada ki manta da roll on da body spray kin san bana son jin mutum yana tsami ki gaya mata ta kula a bata abin shaving ma, ki nuna mata yarda zata yi using d’insa.” Jummai cike da kulawa ta ‘dagawa Hajiyar kai tana fa’din “An gama uwar ‘dakina In sha Allah zata kula,Ubangiji dai ya cigaba da taimakon ki kamar yarda kike taimakawa na k’asa da ke, Allah ya ja mana da ranki don girman zatinsa.” Hajiyar ta amsa ba tare da nuna alfahari ko ‘dagawa don tana da zurfin ilimin addini don haka ta san illar girman kai da fankama gami da K’ifa’di irin na wasu masu ku’din. Haka kuwa Talatu ta zauna tun a daren ta tsefewa yaranta kai ta wanke musu tas da shampoo da conditioner kamar yarda Jummai ta koya mata a nata kan, sai ga gashin yaran ya fito sai walwali yake abinka da masu suma da cikar kai. Su kansu a jikinsu suka ji sun samu canjin rayuwa ga Tv sun kunna sai kallo suke cike da nisha’di suna kuma zaune a kan luntsuma luntsuman kujera suna zuk’ar lemo da biscuit da Jummai ta kawo musu carton guda. Talatu kuwa tana gefe rik’e da carbi a hannunta tana godiya ga Allah ta hanyar jan subhanallah wal hamdulillah. Tabbas yau ta sake jaddada girman Ubangiji ashe barinta k’auyen Shagogo alheri ne zai bibiyeta ga shi nan dai rayuwa tana neman canja musu daga bak’i zuwa fari ashe suna da rabon jin da’din duniya kamar kowane ‘dan adam. Ta saka hannu ta share hawayenta da bai zamo na komai ba sai na zallar farin ciki. _________ Daga ranar rayuwa ta canja musu gaba ‘daya. Yara har sun fara k’iba cikin tsawon sati biyu a gidan fatar su ta sake murjewa an kuma saka su a makarantar IMAN da take nan shara’dar makaranta ce mai kyawun gaske, Hajiya ta siya musu kaya kala biyar biyar na zaman gida. Abinci sam baya yanke musu, suna cikin farin ciki sosai. Ita kuma Talatu cikin da yake jikinta yana ta girma da k’ara bunk’asa ga watsalniya da yake yi alamar yana cikin k’oshin lafiya kuma tun a ciki Ayra ta nuna mai kazar kazar ce ita. Don sau tari Talatun tana jiyo watsalniyarta a ciki kamar zata fito ta tilas. Ta kan shafa cikin ta ce “Oh, ni dai tunda nake haihuwa ban tab’a ciki irin wannan ba to ko namiji ne?” Sai kuma ta yi saurin yin istigfari ta ce “Allah koma me ka ban ina farin ciki da shi ina kuma murna fatana Allah ka musu albarka.” Bata nuna son jikinta ko ka’dan haka take zagewa ake aikin gidan da ita, kuma sun saba sosai da su Jummai da ma sauran ma’aikatan gidan Talatu jin su take tamkar y’an uwanta, haka nan ta dauki hajiya kamar mahaifiyarta. Cikinta wata tara daidai da watansu biyar a gidan, Ciwo ya kama Hajiya Kari, duk wanda ya ga ahalin gidan ya san ba k’aramin tashin hankali suke ciki ba, musamman jin labarin ciwon nata cuta ce ya Daji da ake kira Cancer ta mahaifa ta kamata, sun firgita matuk’a ainun da lamarin ciwon nata sai dai ita ko a jikinta gaba ‘d’aya ta sake kusanta kanta ga Allah ibada take sosai ta kuma cigaba da kyautatawa mabu’kata. Sai dai asibiti sun buk’aci a kaita k’asar waje ta amince zata je a ka fara mata processing visa da komai da za’a tafi da ita Egypt don duba idan da hanyar da zata samu lafiya. Ana jibi za ta tafi ta tarasu gaba ‘d’aya ta bar musu amanar gidanta musamman Talatu don Jummai da su za’a tafi ita da Sarkin gida. Tashin hankalin da ya dirar wa Talatu shi ya tayar mata da nak’udar da bata shirya ba a kuma daren cikin huwacewar Ubangiji ta haifo santaleliyar y’arta mai kama da Mahaifiyar Talatu sak, tun tana cikin jini ta ce “Na sanya miki suna Fatima Allah ya raya min ke Hajiya Kari.” Wato ta yiwa uwar ‘dakinsu ma gajiya. Sai da ta gyara y’ar da k’yar ta mayar da kai ta kwanta tana jiran asuba ta yi ta je ta sanar musu ta haihu. Ba k’aramar murna Hajiya Kari ta yi da jin an mata takwara ba, ta ‘d’aga Jaririyar tana sumbata a hankali kafin ta ce “Na ji da’di Talatu wannan ya nuna min ko bayan ba ni ba zaku manta da ni ba, nagode sosai da wannan karamci don haka tukuicina ga takwara wannan companyn nawa na kayan gine gine ko bayan raina na mallaka mata shi halak malak, sannan na ra’da mata suna Shuayra don na da’de ina burin na sakawa y’ata irin wannan sunan sai dai Allah bai bani ba, ashe Talatu ce zata haifa min y’a don dai wannan y’ar in dai na dawo da raina da lafiyata to ta dawo tawa Talatu.” Murmushi Talatu ta yi cikin karsashi da murna ta ce “Na bar miki halak malak Uwar Marayuz.” Hajiya ta rungumeta a k’irjinta tana karanta mata addu’oi a kunnenta, kafin ta sauketa nauyayyen barci ya ‘dauke Ayran da da take ta mutsu mutsu. Hajiya ta mayar da kallonta kan Talatu ta ce “Kin min alk’awari kin bar min ita ko? Jummai ku zama shaida?” Jummai tana dariya ta ce “Ai kuwa nice Shaida Hajiya muna dawowa za ki amshe a barki.” Ta zari check ta yi rubutu tana mik’awa Jummai “Maza aje a sake mata siyayya tunda takwara ce kuma y’ata ce kayan da duk wasu y’an gata suke sakawa zata saka itama…” Takaicin Uba.. Nazeefah Nashe 42. 💔💔💔💔 Jummai ta amsa check ‘din tana murmushi a zahiri, a ba’dini kuwa bakinciki ne ya cika mata da zuciya, abinka da shaid’an tuni ya rinjayi zuciyar ya shiga k’issima mata abubuwa da dama, me yasa Tunda suke da Hajiyar ita bata mata kyautar ko da fili ba, sai yanzu da Talatu tazo daga sama cikin watanni biyar kacal da zuwansu har an dank’ara mata company guda. Ranta ya b’aci matuk’a ainun ta shiga k’issimawa a ranta ta yarda zata bi ta kori Talatu da yaranta daga gidan itama ta ‘dauko jikokinta Hajiyar ta dinga wahalta musu kamar yarda take wahaltawa yaran Talatu. Sam Hajiya da Talatu basu ankare da yanayin Jummai ba, suka cigaba da hirarsu Hajiyar na sake jaddadawa Talatu ta kula da gidan sosai duk da b’angarenta ba a bu’de zata barsa ba, za dai ta bar musu duk wasu abin buk’ata dangin su Abinci. Ta sake Aikawa aka kira Sarkin gida ta bashi ku’di ya siyowa Shuayra ragon suna a yanka mata. Jummai tunda ta fita take sak’e sak’e abin duniya ya taru ya mata zafi, ina ma zata ga Mijin Talatu da ta nuna masa gidan ta tabbata hakan ne kawai zai raba Hajiya da Talatu da take nema ta zame musu k’arfan k’afa. Ina dalili su da suke zaune shekara da shekaru suna wahala ba a basu company ba sai wata Talatu. Allah dai ya dawo da su lafiya da kanta zata ja Sarkin gida su je har k’auyen Shagogo da ta ji Talatun ta basu labari ta nemi Kabiru ta gaya masa inda Talatu take, idan yaso ya zo ya tafi da matarsa da yaransa. Ta saki murmushi tana jin da’din shawarar da zuciyarta ta bata, hankalinta Kuma ya kwanta, kafin nan kuma zata yi k’ok’ari wajen ganin Hajiyar bata bawa Talatu takardun companyn ba kai koma ta bata sai sun k’wace ita da Sarkin gida bayan rasuwar Hajiyar don dai ta san Talatun bata da ilimin da zata nemi hakkin ta koda ta kai su kotu ne, Hajiya kuwa ta san tazo gangara kawai lokaci ake jira ciwon Cancer Ai da wuya a warke. Jummai kenan banda abinki wa ya san gawar fari? Bata yi bak’in ciki ba ta zage ta siyowa Ayran tsadaddun kaya duk da dai ta samu rarar canji sosai ta kwashi kayan cike da bayan boot ta nufi gida. A falon Hajiya ta zuba kayan Hajiyar ta dubasu sosai ta ga sun mata yarda take so sannan ta ce Jumman ta kai mata Talatun. Jummai tana tattara kayan ta ‘dan dubi Hajiya a kaikaice kafin ta ce “Amma Hajiya da zan baki wata shawara, sai dai ina gudun kada ki ce na miki katsalandan.” Hajiyar ta ajiye littafin Azkar ‘din da yake hannunta tana duban Jummai cike da kulawa ta ce “Ina jin ki Jummai, ai duk mutumin k’warai yana son a bashi shawara, ba kiji mai mutane suke cewa ba aikin me shawara ba ya b’aci.” Jummai ta saki ajiyar zuciya tana ‘dan wasa da zoben hannunta. “Maganar companyn da kika yi kyauta da shi dama nake son miki. Kina ganin hakan bai yi sauri ba? Musamman ganin ba wani jumawa aka yi da su ba, har wa yau kuma ba a tabbatar da sahihancin labarin da ta bamu ba, ina tsoron kada labarin ya zama k’anzon kurege ko ta yi amfani da halinki na tausayin jama’a ne ta zo miki a haka.” Hajiya ta da’de tana kallon Jummai tana nazarin kalamanta, har Jummai ta fara jin tsoron kallon ta yi k’asa da kanta cikin rawar murya ta ce “Allah ya huci zuciyarki Hajjaju, idan shawarar tawa ta b’ata miki rai ne..” Hajiya ta saki ajiyar zuciya tana girgiza kai “Sam ba b’ata min rai ta yi ba, abinda kika fa’da haka yake ‘dan Adam abin tsoro ne, sai dai ni zuciya ‘d’aya nake abu idan ka cuceni kanka ka yiwa tunda ni don Allah na maka, don na bata company ba abinda zai girgiza daga dukiyata ke da kanki kin san a cikin kadarorina wannan companyn shine koma baya, ina da kadarorin da ni kaina ban san adadinsu ba, Iyayena sun bar min, y’an uwana da Mijina ya yi sanadiyyar su zuwa duniya suma sun bar min dukiya mai tarin yawa tunda ana gaf da aurensu ya saka musu guba suka ci duka su biyun maza rus suka mutu, duk don ya ha’de dukiyar mu ya handame, ban san me Zan Yi da dukiyar na musamman a yanzu da nake gargarar mutuwa don haka na rubuta duk wata wasiyya na yarda za’a kasafta dukiyata na bawa amintaccen Lawyer na wanda na san ko bayan raina ba zai haince ni ba, zai aikata abinda na saka shi, don haka ba damuwa idan tazo ne don ta cutar da ni ita da Allah, sai kiga kuma Allah ya kareni daga sharrinta tunda ni ban nufeta da sharri ba. Don haka ki kwantar da hankalinki, duk wanda yake k’ark’ashina zai samu kwatankwacin abinda Talatu ta samu bayan raina In sha Allah.” Jummai ta saki ajiyar zuciya jin abinda Hajiyar ta ce duk da wani sashen na zuciyarta ya sanyaya bai hana Hassada tasiri a zuciyarta ta ba, ita fa wannan Kamfani da aka dank’arawa Ayra shine babban Tashin hankalinta, don haka sam wancan k’udirin da ta ‘dauka a zuciyarta ba zata barsa ba, da zarar sun dawo in dai ba ran Hajiya zata isa garin Shagogo ta gayawa Kabiru yanda suke. Fuskarta ba yabo ba fallasa ta shiga inda Talatun take, daidai lokacin Talatun na zaune da Ayra a jikinta tana gasa mata cibiya. Ganin Jummai yasa ta washe mata hak’ora tana fa’din “Sannu da k’ok’ari nagode sosai.” Jummai ta gya’da kai ha’de da fad’in “Ai ki godewa Allah kin zo a sa’a, lokaci guda a dank’ara miki company.” Talatu ta ‘dan saki murmushi kafin ta ce “Wai Jummai Hajiya bata da y’an uwa ne?” Jummai ta kalleta shek’ek’e kafin ta ‘dan tab’e baki ta ce “Idan ma tana da su Ai kin fiye mata su yanzu tunda ban ji ba, ban kuma ga wanda Hajiyar ta bawa company ba sai ke, wai ni Talatu ya kika ce sunan uban mijinki a garin Shagogo?” Talatu ta ‘dan yi Jim kamar mai son ta gane abinda Jummai take nufi sai dai ba abinda ta gane don bata da wani wayon gane makircin mutane. Jummai ganin yanayin Talatun sai ta yi saurin gyara zamanta ta ce “Akwai wasu y’an uwana da suka tab’a zama a garin naku ne? Nake son sanin ko wajejenkune shi yasa kika ji na tambayeki sunan sa.” Talatu ta mik’a mata Shuayra tana fa’din sunansa “Iro Na Lami, duk wanda kika tambaya an san gidan duk da dai baya raye Amma an san shi ya yi suna sosai a garin.” Ra’dam Jummai ta haddace sunan a kanta, ta kalli Ayra tana murmushi kafin ta ce “Wannan y’ar taki duk tafi sauran kyau, yarinya kamar ‘d’iyar larabawa Ma sha Allah.” Talatu tana murmushi ta ce “Kamarsu ‘daya da Innata kwabo da kwabo har wannan lotsawar hab’ar da kumatunta na Inna ne.” Ta shafa kanta ta ce “Allah mata albarka, bari na je na kikkintsa don na ji Hajiya ta ce jirgin asubahi za mu bi.” Talatu ta karb’eta tana fa’din nima ina gamawa Zan zo yiwa Hajiyar godiya, Allah dai ya ja mana da ran Hajiya.” Jummai ta gya’da kai kawai a fili a zuciyatta kuma ta ce “Ba amin ba.” Ta saka kai ta fice daga ‘dakin tana jaddada sunan Iro na Lami kafin ta je ‘d’aki ta kwafe sunan a bango don kada ta manta don da zarar sun dawo za ta fara aikinta. Kashegari kuwa jirginsu Hajiya ya lula suka tafi Suka bar su Talatu da kewa ta kuma yi alk’awarin dagewa da yiwa Hajiyar addu’ar samun lafiya don shine burinta, bata fatan Hajiayr ta mutu don ko ta ina tana jin Hajiyar kamar Uwa ce a gareta makwafin Uwarta da ta rasa. Talatu ce ta cigaba da kula da gidan da abincin sadakar da ake rabawa. Cikin sa’a aka yiwa Hajiya aiki ta kuma samu sauk’i sosai da sosai kamar ma bata yi ciwo ba. Tun tana gadon asibiti kullum sai ta yiwa Sarkin gida da Jummai zancen Talatu da jaririyar da ta bata, abinda yake yiwa Jummai ciwo, tun kuma a garin ta zuge Sarkin gida a kan idan basu tashi tsaye ba, tsaf Talatu zata ture gwamnatinsu a wajen Hajiyar. Sarkin Gida ya amince da abinda ta ce don haka suka shiga manak’isar yarda za su kori Talatu daga gidan. Hajiya da kanta Ta kira Maigadi ta ce ya bata numberr Talatu zasu yi magana. Mai gadi ya bawa Aysha da take waje tana karatu hannunta ‘dauke da Ayra y’ar wata biyu da ta yi b’ulb’ul da ita kana ganinta ka san tana samun ruwan nono mai kyau. Kyakykyawar gaske tun tana yarinya. Ya ce “Maza ki kaiwa Ammanku waya kice Hajiya ce a layi.” Da sauri Talatu ta amshi wayar bayan jin abinda Aysha ta ce ta kara wayar cike da zumu’di a kunnenta ta fara gaida Hajiyar, itama cike da kulawa take amsawa tana cewa “Ina takwara ta? To ku shirya tarbar bak’i gobe Talatu, wannan kunun naki na gya’da da tuwon dawar nan da kike yi mai da’di nake so.” Talatu tana murna ta ce “An gama Hajiya, Allah ya dawo mana da ku lafiya.” “Ameen” Hajiyar ta katse wayar tana kallonsu Sarkin gida da suke murmushi a junansu. Ba su da’de a ‘d’akin ba suka fice. Jummai ta kalli Sarkin gida “Ka tabbata yarinyar nan zata iya aikin da ka bata kada fa ta je ta mana shirme.” Yana dariya ya ce “Bana miki haufi Sidiya ba zata yi shirme ba, zata aikata kamar yarda na sakata tunda na mata alk’awarin aurenta don tunda ta zo gidan take so na na k’i bata ha’din kai yanzu kuwa don zuba guba a cikin abincin Hajiya ba abinda zai gagareta ki kwantar da hankalinki.” Jummai ta saki ajiyar zuciya “Shikkenan, fak’at zaman wannan annamimiyar ya k’are, haka kawai Mace daga zuwanki ki nemi lalata mana aikin da muka kwashi shekaru muna yi, yanzu kuwa salin alin dole a koma k’auyen Shagogo tunda mu dai ba ma nan ba mai zargin mu da saka guba a abincin Hajiya kuma tsawon zaman mu Ai ba mu tab’a, ita sabuwar zuwa itace abin zargi.” Suka yi shewa suka tafa ha’de da fa’din “Duniya Sabuwa mutumi na!” JikarNashe 08033748387 Takaicin Uba.. Nazeefah Nashe✍🏽 43. 💔💔💔💔 ____________ 🌎 Majeeda na tsaye a store ‘din babban kitchen ‘din cikin gidan ta ga shigar Sidiya cikin kitchen d’in da alamun rashin gaskiya a tattare da ita. Haka kawai Majeeda ta ji tana son ta lab’e ta ga mai zata aikata don haka ta mak’ale a bayan k’ofar store ‘din. A matsayin shekarunta ya kamata ta gane abubuwan rayuwa da yawa ciki kuwa har da gane mara gaskiya. Gabanta ne ya fa’di ganin Sidiyar ta kwance bakin zaninta tana shirin zaro k’ullin leda kafin ta bud’e miyar tuwon Hajiyar ta zazzage abinda yake cikin ledar ta saka ludayi kuma ta juya sosai sannan ta mayar ta rufe sai kuma ta fice daga kitchen ‘din da sauri. Majeedah ta ware ido gabanta yana fa’duwa ta tabbata ba abin alheri Sidiyar ta aikata ba. Don haka da sauri jikinta na rawa ta kinkimi abincin ta bi ta k’ofar baya zuwa hanyar chalet inda suke rayuwa da Ammansu. Talatu na tsaka da canjawa Ayra pampers ta ga Majeeda ta shigo da coolers ‘din abincin har haki take saboda ‘dan saurin da take ta durk’ushe gaban Talatun da ta zuba mata ido a fusace kafin ta fara sauke mata fa’da ta ce “Amma Sidiya…Sidiya na ga ta zazzaga wani abu a cikin abincin nan.” Amma ta zaro ido tana kallonta kafin ta ce “Ke Majeedah bana son k’arya?” Duk da ta san zai yi wuya Majeedah ta fa’di k’aryar tunda bata ‘dora su kan turbar k’arya ba. “Wallahi Amma da gaske nake, ina tsaye a kitchen cikin store naga shigowarta kamar mara gaskiya shine na b’uya naga abinda zata aikata sai na ganta tana zazzagawa.” Amma jikinta na b’ari ta saka salati ha’de da fa’din “Ke duniya ina za ki damu? Yanzu mai baiwar Allahn nan ta mata take neman cutar da ita, wa ya san mai ya barba’da, abinda nake so da ke Majeeda kada na sake na ji labarin nan a bakin kowa don idan baka iya kama b’arawo na shi sai ya kamaka, don haka ki ja bakinki ki tsuke zan saka ido sosai na ga mai son cutar da Hajiya a cikin gidan nan.” Ta mik’e tana kinkimar coolers ‘din abincin don har tuwon ma da kunun bata yarda da su ba, gwara ta sake yi a nan cikin sashenta za kuma ta kula sosai da abincin har sai Hajiyar ta dawo. Ta da’de abin yana mata kewaye a zuciya da tsananin mamakin halin ‘dan Adam mai sakanta alheri da sharri a dalilin son zuciya. Kayan aiki kawai ta ‘Debo ta girka anan sashen duk da rigimar da Ayra take sai ta hana Majeeda zuwa Islamiyya ta ce ta zauna ta rik’e mata ita. Jirgin k’arfe biyar na yamma ne ya sauke su Hajiya daga k’asar Egypt a filin tashi da saukar jirage na Aminu Kano International airport. Hajiya ta samu sauk’i sosai duk da dai ta yi rama ka’dan fuskarta ta fa’da sosai. K’arfe 7:00 kuwa a k’ofar gidanta da ke Shara’da phase 2 ta musu. Gaba ‘d’aya mutanen gidan suka fito a guje don tarar ta, Musamman Talatu da take jin tamkar ta tashi sama don murna ita da yaranta. Suka shiga sashen Hajiyar da sauri inda Hajiyar ta shiga itama tana murna da farin cikin ganin ahalin nata wanda ta ‘dauka sune makwafin danginta. Sai da ta zauna sannan ta mik’awa Talatu hannu tana fa’din “Bani y’ata dafatan dai kina kula min da ita? Don naga ke kin yi b’ulb’ul a binki Masha Allah kamar a tsaga jikinki jini ya fito.” Ta fa’da tana sauke ganinta a kan Ayra da take ta b’angala mata dariya “A’a Masha Allah, Lallai Talatu dole nagode miki da ganin yarda Ayra ta yi b’ulb’ul da ita kamar ba y’ar wata biyu ba.” Ayra kuwa sai sake b’angala mata dariya take Hajiyar ta lakaci kumatunta tana fa’din “Yi dariya da kyau Daughter Maminki ta dawo.” Talatu dai murmushi take, Jummai kuwa haushi kamar ya kasheta, a zuciyarta ta ce “komai dai ya kusa zuwa k’arshe gayyar na ayya yau yau y’an sanda za su damk’e ki yaranki kuwa zan ‘dau nauyin mayar da su garin Shagogo gidan Iro na Lami su cigaba da rayuwar da suka saba.” Ita ka’dai take zancenta a zuci a zahiri kuwa dariya ta yi tana kallon Talatu ta ce “Ai kuwa Hajiya k’arama ta yi jajur da ita Ma sha Allah, kema kin sake haske banda da aurenki Ai dai sai nace sai shirin aure.” Talatu ta ware ido ta ce “Ai ko ba aurena na shafe babin aure a rayuwata, balle wannan auren da shi da babu Ai duk ‘d’aya Jummai.” Hajiya ta ‘d’aga kai tana murmushi ta ce “Kin kuwa taimakawa kan ki Talatu, ba abinda ya dace da ke yanzu irin neman ku’di ki kuma afka Islamiyya ki yi yak’i da jahilcin da yake k’ok’on kanki don da kina da ilimi duk wasu abubuwan ba za ki yarda da su ba, Kabiru ya cutar dake sosai a rayuwa.” Talatu ta ‘dan saki murmushi kawai tana mik’ewa don kawowa Hajiyar abinci. “Bari na kawo miki abincin Hajiya.” “Ai kuwa ki yi maza don ina kewar sanwarki bana jin ko wanka zan iya ban ci abincin ba.” Jummai ta ‘dan saki murmushin gefen kumatu kafin ta ce “Ni bara na je na yi wankan, don ba yunwa nake ji ba.” Don ta san sarai Hajiya zata iya cewa ta zo su ci gaba ‘daya don haka ta tsere tana fatan kafin ta fito ta ji an rusa kukan mutuwar Hajiyar. Talatu kuwa tana zuwa ta ga Majeedah na nan zube bisa gwiwoyinta tana gadin abincin da ta saka ta. Tana sakin ajiyar zuciya ta dubi Majeedan “Baki dai mik’e ko nan da can ba ko? Kamar yarda na saka ki.” Majeeda ta ‘d’aga kai “Ba inda naje Amma.” Yauwa to maza biyo ni da sauran kayan abincin mu isar da su wajen Hajiyar.” Sosai Hajiyar ta ci abincin ta ta k’oshi har da si’de kwano. Sannan ta mik’e ta shige toilet don wanka. A sannan ne kuma Jummai ta iso sashen Hajiyar tana fatan ta tarar da gawarta. Da mamaki take kallon falon Hajiyar ga kuma Talatu ‘dauke da Ayra tana canja mata Riga. Da ido ta dubi Talatun tana furta “Talatu Ina Hajiyar ba abinda ya sameta ko?” Talatu ta ‘dago tana jifanta da wani kallo mai nuni da zallar mamaki da alama da gaske ta fara fuskantar Inda Junman ta dosa, murya a caku’de da takaici ta ce “Ba abinda ya sameta tunda bata ci gubar ba, Allah ya tsareta da kiyayewarsa.” Wani irin fito da idanuwa Jummai ta yi tana kallon bakin k’ofa ganin Hajiyar a tsaye kuma ba mamaki duk ta ji maganganunsu, Jikinta na rawa ta mayar da kallonta kan Talatu da itama take kallonta ko k’iftawa bata yi ga wani irin b’acin rai mabayyani a idanun Talatun tana cizar leb’e da furzar da numfashi ta ce…. (Idan naga ruwan comments zaku samu next page da yamma. Idan na ji shiru kuwa nima hutawa zan yi.) Jikar Nashe. Takaicin Uba….. Nazeefah Nashe✍🏽 💔💔💔💔 🌏 44. Da sauri Hajiya Kari ta juya ‘dakinta jin wayarta da take ta ringing ta barsu a falon Jummai tana hararar Talatun k’asa k’asa ta ce “Me kike so ki ce ne?” Talatu ta ha’de fuska ha’de da fa’din “Zan gaya mata yarda aka so kasheta, kuma bana raba ‘d’aya biyu da saka hannunki a ciki daga ganin yarda kika nuna.” Jummai ta ware idonta kafin ta saki murmushi wanda ya bayyana a iya kan fuskarta cikin zuciyarta kuwa tashin hankali ne na gaske, don har jikinta ya fara b’ari, ta ce “Ashe kin shirya komawa wajen Kabiru, don wallahi idan na ji zancen nan wajen Hajiya ki k’addara kamar kin koma waccen bak’ar rayuwar ta gidan Kabiru, don a yanzu na san inda yake da muhallinsa da komai don haka bismillah idan ta fito ki gaya mata kiga idan zata yarda bak’ar munafuka kawai.” Talatu ta ha’diye wani abu da ya tokare mata zuciya tana jin kamar ta kama Jummai ta mur’de wuyanta ta kasheta har lahira sabida tsabar tashin hankali, wato dai abinda ta Zarga ‘din ya tabbata da saka hannun Jummai a abinda Sidiya ta aikata. Tabbas a yau ta yarda da maganar mutane da suke cewa ka guji sharrin wanda ka kyautatawa kuma tabbas ta yarda D’an Adam butulu ne! Idan banda haka Ai Hajiya bata cancanci wannan tagomashin butulcin daga wajen Jummai ba, Macen da ta ‘daukesu kamar y’an uwa. Idanuwan Jummai ta kalla kawai ta tabbatar zata iya aikata mata abinda ta fa’da don haka dole ta ja bakinta ta tsuke don bata shirya komawa rayuwar da ta baro ba mai cike da k’unci da wahala Amma zata cigaba da kula da cimar Hajiya zata kuma san dabarar da ta yi duk wani abincin Hajiyar ya dawo k’ark’ashin kulawarta fatanta Allah ya zama gatan Hajiya ya tsyaa mata da tsayawarsa. Don haka da Hajiya ta fito ta tambayeta mai ta ji tana cewa kafin ta shiga ciki? Sai ta saki murmushi kawai tana gyara zama ta ce “Na ma manta hirar da muke da Jummai.” Ta fa’da tana jan dogon istigfari a cikin ranta. Tun daga ranar kuwa Talatu ta yi k’ok’arin maye gurbin mai abincin Hajiyar, itama Jumman bata sake k’ok’arin aikata abinda ta aikata ‘din ba don bata shirya barin gidan ba, ya zama ta tashi a tutar babu! Duk da da’dewar da ta yi tana jirayar lokacin mutuwar Hajiyar ta kwashi ganima. A gaban Hajiya dai tana kula Talatu Amma a bayan idon Hajiya kam tsana muraran take nunawa Talatun, ta kuma ci alwashin barinta gidan Hajiyar ko da ta k’arfin tuwo ne. _____________ Shekarar Talatu biyu a gidan Lokacin har Ayra ta tasa tana tafiya duk inda take so a gidan Hajiya kuma tana sake bada himma wajen kulawa da Ayran sosai, companyn da ta bata kuwa ta kira lawyer ya saka hannu a zuwan ta barwa Ayra halak malak ko bayan ranta. Lawyer ya rattaba hannu ha’de da shaidu har guda biyar ciki kuwa har da Jummai da sarkin gida. Ranar kam kwana suka yi zuciyarsu bak’a k’irin cike da haddasa sa tashin hankali. Jummai kuma ta yi alk’awarin a satin sai ta yi sanadin barin Talatun gidan don haka ta fara shirin zuwa garin Shagogo a b’oye ba tare da sanin Hajiya ko Talatu ba. Talatu tsaye a dinning area tana zubawa Hajiyar kunu, ita kuma Ayra na saman cinyar Hajiya da tuni ta dawo gurinta gaba ‘d’aya tana kalbace mata yauk’akkeb gashin kanta. Jummai ta shigo falon da sallama. Haka kawai Talatu ta ji gabanta ya fa’di sosai ta fara karanta addu’oin data fara koyansu a Islamiyya kafin ta ‘dauke idonta daga kan Jummai da take harararta k’asa k’asa. A zahiri kuma sai ta kama Ayra tana fa’din “Hajiya k’arama, kina nan kina damun Hajiyarmu ko?” Ta fa’da tana jan dogon gashin Ayran “Hajiya wannan y’a taki akwai suma sai kace ‘diyar larabawa.” Hajiya ta yi saurin cewa “Jummai ba nace a duk sanda za ki tanka yarinyar nan ki dinga cewa Ma sha Allah ba, haba wannan wani irin abu ne? Kullum sai kin tanka y’ar nan.” Jummai ta ‘dan b’ata fuskarta alamar bata ji da’din maganar ba ta ce “Tubarkallah mantawa na yi, a yi hak’uri Hajiya, dama zuwa na yi na rok’i alfarma a wajenki don Allah zan je wani k’auye nan k’asa da mu an min wata rasuwa Amma yau Zan dawo In sha Allah.” “Allah ya yarda, Allah kuma ya ji k’an rai waye ya mutu?” Ta ‘dan yi Jim kafin ta ce “Can b’angaren Innata ne ba za ki sansu ba.” Hajiya ta ce “To Allah ya ji k’an musulmi” ta bu’de jakarta ta zaro ku’di ta mik’a mata “Ga ku’din mota saura kuma ki bada sadaka Allah ya ji k’an mamaci, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.” Jummai ta amsa ku’din tana wa Hajiya godiya kafin ta wurgi Talatu da harara jin tana cewa “Jummai Allah ya ji k’an rai.” Ta amsa murya a cunkushe tana ficewa da sauri daga falon tana sake barin Talatu da fa’duwar gaba. Bata sha wahalar gane gidan Iro na Lami ba, kamar yarda Talatu ta sanar mata, aka rakata har gidan yaron yana nuna mata ya ce “Hajiya mun zo.” Jummai ta saki ajiyar zuciya tana mik’awa yaron gudar Naira ‘dari sannan ta shiga cikin gidan, tana fatan abinda tazo musu da shi su karb’eshi hannu bibbiyu. Bayan gaisawa da jama’ar tsakar gidan ta mayar da kallonta kansu tana fa’din “Mahaifiyar Kabiru nake nema.” Gaba ‘d’aya suka zubo suna kallonta kafin su nuna mata ‘dakin Innar Kabirun. Ta mik’e a ranta tana mamakin kallon tsoron da suka ga mutanen suna mata. Sai da ta kunna wayarta ta danna recording sannan ta shiga ‘dakin da matar take. Da alamar rashin lafiya a tattare da ita don da kyar ta amsa sallamar Jumman cikin dakusashshiyar murya. Jummai ta zauna tana fa’din “Sannu Baiwar Allah Allah ya baki lafiya.” Da k’yar Innar ta amsa tana gyara zamanta akan yankwananniyar katifarta ta mayar da kallonta kan Jummai tana fa’din “Yarinya daga ina?” Jummai na jin haka ta gyara zama tana fa’din “Daga Kano nake, dama Kabiru nazo nema” A razane Innar ta ‘dago tana kallonta “Kabiru kuma kike nema y’ar nan? Allah yasa dai lafiya?” Jummai ta ce “Lafiya lau, alheri ne yake tafe da ni matarsa Talatu ce ta turo ni.” Wannan karan jikin Inna har rawa ya fara ido waje ta ce “Talatun tana raye? A ina kuma?” Jummai ta gyara zama kafin ta ce “A gida na Inna, yanzu dai Ina Kabiru?” Innar ta gyara zama kafin ta ce “Kabiru….” Jikar Nashe. Takaicin Uba… Nazeefah Nashe✍🏽 45. 💔💔💔💔 🌏 “Kabiru fa ya doshi shekara ba mu saka shi a idanunmu ba yarinya, nima ki taimakeni ina nemansa idan kin gansa.” Shiru Jummai ta yi cike da tarin takaici take duban Innar Kabirun jin abinda ta ce, sannan da take cewa idan ta gansa tana nemansa ce mata aka yi ta san Kabirun? Kabirun da ko kalarsa bata sani ba. Ta ‘dan ja tsaki ka’dan duk wata k’warin gwiwa da tazo da shi sai taji ta nemeshi ta rasa, sai ma tarin nadama da jin haushin b’ata lokacinta da ku’dinta da ta yi a banza a wofi. “Yarinya yanzu ina ita Talatun? Y’ar banzar yarinya tunda ta saka k’afa ta bar garin nan ba mu sake jin labarinta ba ba mamaki ma Karuwanci ta fa’da.” Jummai ta zuba mata ido tana ha’diyar wani abu da ya tsaya mata a mak’oshi kafin ta furzar da huci ta ce “Tana can tare da mu, ni dama Kabiru nazo nema tunda ba ya nan bari na tafi sai dai zan bar sak’o idan yazo a ajiye masa.” Ta zage jaka ta yi rubutu da yake ta iya rubutun numberr wayarta ta rubuta ta kuma sanar masa idan ya tashi neman matarsa ta san inda take ya nemeta a wannan layin. Sannan ta mik’a wa Innar Kabirun ta mik’e tana fa’din “Ni zan wuce Inna Ki k’ok’arta ki ajiye masa takardar nan tana da muhimmanci sosai.” Sannan ta ajiye mata Naira dubu biyu a ku’din da Hajiya ta bata y’an d’ari bibbiyu ta fito daga ‘dakin tana yiwa matan gidan sallama da suke mata kallon k’urilla. Suna fitowa ta ha’du da Kamilu k’anin Kabirun, ya ‘dan washe baki yana kallonta kamar ya santa hakan yasa ta ‘dan tsaya suka gaisa, kafin ya ce “wani kike nema ne Hajiya?” Jin sunan da ya kirata da shi yasa tana murmushi ta ‘daga kai “Wallahi Kabiru nazo nema sai na taki rashin sa’a baya nan.” Kamilu ya jinjina kai “Ai Kabiru ya yi b’atan dabo shekara guda muma bamu da labarin sa ba zaki gansa a garin nan ba sai tasa ta ciyoshi idan sak’o ne ki bayar a ijiye masa.” Jummai ta zage jakarta ta sake cirar takarda da biro ta rubuta numberr wayarta ta mik’a masa tana fa’din “Don Allah ka mata ajiya mai kyau, ka sanar da shi idan ya tashi neman matarsa Talatu ya kira ta wannan layin ni na san inda take, tunda Talatun ta rantse min ba zata dawo ba, to ni kuma ina jin tsoron halin rayuwa kada nan gaba ya buk’aci haka shi yasa na yiyo tattaki nazo.” Kamilu ya amsa yana fa’din kin kyauta kuwa, ni kaina da a kimtse nake Ai da naje na ga Talatun, amma idan na tashi zuwa In sha Allahu zan kira ta wannan layin sai a min kwatance nagode sosai.” Jummai ta zaro dubu uku shima ta ba shi, a zuciyarta tana fatan Kabirun ya samu sak’onta kwana kusa. Wannan shine silar sanin Kabiru inda Talatu ta koma da yaranta. ___________ Bayan shekara guda da zuwan Jummai garin su Talatu ba wani labari da ya canja don har a wancan lokacin Kabirun bai je garin ba, shi kuma Kamilu da yake son zuwa Jummai ta k’i ba shi kwatance don bata son zuwansa yanzu kada asirinta ya tonu Kabirun dai take son yazo. Lokacin Ayra ta sake girma don shekararta biyar kenan cif har ta shiga makaranta mai tsada Hajiyan ta sakata ake kaita Intercontinental idan ka ga yarda ta sake kyau sai ka zata y’ar gidan wani hamshak’in mai ku’din ce, ta yi kyau na ban mamaki, duk Inda Hajiya zata Ayra tana manne a jikinta duk k’asar kuma da Hajiyar zata in dai ba lokacin Makaranta bane da Ayra take tafiya, duk wanda ya san Hajiya ya san Ayranta, mutane da dama zato suke jikarta ce. Tafi sabawa da Hajiya fiye da Amma mahaifiyarta da itama ta yiwa Hajiyar kara sam bata shiga sabgar Ayra. Ta rungumi sauran yaranta da suka zama y’an mata sosai. Ahalin gidan Hajiyar suna zaune cikin kwanciyar hankali, Jummai ma tuni ta zubar da makaman yak’inta, don duk ta inda ta bi da son soke Ayran a wajen Hajiyar bata samun nasara hakan yasa ta gaji ta zuba musu ido, sai dai bata fasa tuntub’ar Kamilu ta waya ba ta ji ko Kabirun ya shigo gari kamar yarda suke fata. A wani kira da ta yiwa Kamilu ya tabbatar mata Kabirun ya shigo gari har ma ya yi arzikin da ya bawa kowa mamaki sai dai da ya masa maganar zuwa wajen Talatun basu rabu da da’di ba, ya ce ba ruwansa da Talatu da yaranta ya bu’de sabuwar rayuwa a lagos bayan Karima ma, yanzu ya k’ara mata ‘d’aya kuma sun haifa masa yara mazan da yake so, don haka Ya barwa Talatu yaranta Mata ta k’arata. Wannan labari bai yiwa Jummai da’di ba don bata so jin haka ba da kuma Kamilun ya mata maganar zuwa sai ta ce ba yanzu ba ya jirayi lokaci. __________ Ana haka katsaham ciwo ya kama Hajiya ciwo mai zafin gaske, wanda duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata, ba kuma zaka tsammaci zata sake wayar gari ba. Ciwon ya ci k’arfinta, duk wani masoyin Hajiya yana cikin tashin hankali, kuma duk k’asar da aka je sai dai a jagwalgwalata a dawo Amma ba alamun samun sauk’i a tare da ita. A wani dare da Talatu ba zasu tab’a mantawa da shi ba, Hajiyar ta tarasu gaba ‘dayansu da suke k’ark’ashinta. Cikin wahala da zafin ciwo ta zuba musu ido duk hankalinsu a tashe yake musamman Talatu da take ta kuka ba k’ak’kautawa ji take da tana da iko da ta sarayar da ruhinta ga Hajiyar, Hajiyar ta rayu ita ta mutu. Sai dai bata da wannan ikon rai da mutuwa duka a hannun Allah suke. Cikin raunin murya da k’arfin hali Hajiyar ta saka aka mik’ar da ita zaune aka jinginata da filo. Muryarta k’asa sosai da sai ka saka kunnenka sannan zaka ji abinda take cewa ta ce “Ba shakka ina ji a jikina lokaci na ya yi, Alhamdulilah da Allah ya kawo ni har yanzu ba da k’arfi na ba ko dabarata ba, sai don shi yaso, yanzu kuma da yake son amsar rayuwata ban isa na hanashi ikonsa a kaina ba. Ku yi hak’uri ku yi hak’uri sannan don girman Allah ina rok’onku alfarma kada ku manta da ni a addu’oinku, ba ni da kowa ba ni da komai ba ni da mai yi min addu’a sai wanda ya dubi Allah ya tuna da ni. A tsawon zama na da ku idan na cuceku ina neman yafiya nima kuma na yafe muku. Abu na gaba na san idan na Mutu y’an uwa na dangin iyayena da suka yi saura da dama burinsu su gaji dukiyata shi yasa kuka ga da bani da lafiyar nan kullum suna tare da ni, to na san ba zaku samu komai daga kason gadona ba, ni ma kuma bana son dukiyar ta zama ta magada kawai nafi son na samu tagomashin lada ni da iyayena da y’an uwana ta sanadiyyar ta, don haka na saka aka gina masallatai aka kuma hak’a rijiyon boreholes a k’auyuka sannan aka gina majalissun ilimin addini, aka kuma damk’a kaso mafi tsoka a gidan marayu da gajiyayyu marasa gata.Abinda ya rage min shine ku da kuke k’ark’ashina kuma ku samu wani abin daga dukiyata don bana son bayan babu ni ku tagayyara na tabbata da zarar na mutu makusanta za su sallameku daga gidan nan, ina zaku? Wace Sana’a za ku yi ku dogara da kanku duk wannan ba shine a gabansu ba, don haka na gayyato lawyoyi har biyar ga su nan a zaune da nake son a yi komai a gabansu su zama shaidu. Sarkin gida Jummai Rabe, Talatu da Mai gadi akwai gidajena guda biyar a rijiyar zaki na bawa kowa ‘daya a cikinku ya zauna, da tsabar ku’di Naira miliyan biyar biyar. Sai Talatu da na bawa y’arta company bana fatan ko bayan raina wannan magana ta tashi. Akwai ku’di da na zuba masu tarin yawa a asusun companyn Ayra da nake fatan bayan babu ni a cigaba da kula da karatunta har gaba da secondary Talatu ki yi min alk’awarin Ayra Zata yi ilimi har sai ta ce ya isheta da zarar ta gama secondary kuma a kaita Jami’a a k’asar waje ta karanci business admin da shine Zata iya kula da companynta idan ta girma, ki min wannan alk’awarin.” Ta fa’da tana sauke kallonta kan Ayra da take mata wani irin so fiye da tunanin mai tunani Talatu kuwa kuka take tana fa’din “In sha Allah Hajiya zaki tashi har ki aurar da Ayranki Ai cuta ba mutuwa bace.” Murmushi ta yi tana fa’din “Mutuwa ce Talatu ina ji a jikina kuma lokaci na ya zo k’arshe addu’arku kawai nake buk’ata kada ku manta da ni bayan babu raina.” Duka gurin zuciyarsu ta karye kukan kawai suke mai bayyana tsananin tashin hankalin da zuk’atansu suke ciki. K’irazar sun raunana kamar yarda idanunsu suke ganin duffai basa gane komai ba kuma sa fahimtar komai sai sautin kukansu ne kawai yake tashi a ‘dakin. Hajiyar tana dubansu tana murmushi ta ce “Tun yau kuka fara min kuka? Ashe kada na saka rai da samun addu’oinku, don Allah idan na mutu kada ku min kuka, bana buk’atar kukanku kuka ga mamaci bala’i ne masifa ne. Ku tashi ku je ku yi sallah ku rok’a min gafara da samun sassauci zarar rai ya fiye min wannan kukan ba gata kuke min ba.” Kamar wa’danda aka zarewa laka haka suka dinga mik’ewa suna ficewa ban da Talatu da. Ayra da kuma Jummai da suka kasa matsawa daga kusa da Hajiyar da muryarta ta fara karyewa. Duk k’ank’antar shekarun Ayran bai hanata shiga tashin hankali ba, ta kwanta a jikin Hajiyar sosai tana hawaye ganin kowa ma kukan yake. Hajiya ta ‘dan shafa kanta kafin ta damk’i hannunta tana fa’din “Allah miki albarka yasa ki zama abin alfahari a rayuwar mahaifiyarki.” Ta damk’i hannunta cikin nata kafin ta kalli Talatu da ta shimfid’a sallaya tana shirin tada sallah ta ce “Amma zuba min Zam zam ki karanta min matayassara minal k’ur’an.” Da sauri Talatu ta ‘d’au robar zam zam ‘din ta tsiyaya a cup ta fara karanta suratul Mulk tana karantawa Hajiyar na binta a hankali har ta gama ta kama Hajiyar ta kafa mata a baki. Tas kuwa Hajiyar ta shanye kafin ta lumshe ido ta ce “Nagode Talatu, Allah ya saka miki da alheri ya dafa miki a rayuwarki.” Talatu ta amsa a sanyaye tana kwantar da ita kafin ta tada sallah. Itama Jumman Sallahr take duk zuciyarta ta raunana ance Sabo turken wawa musamman mutumin da yake kyautata maka dole ka ji mutuwarsa. Ana idar da Sallahr Asuba Itama Hajiyar ta yi bayan Jummai ta mata alwala daga sallah ta kishingi’da ta lumshe idonta sai suka ji shiru a zatonsu barci ta yi sai dai ina Hajiya ta yi barcin da ba zata tashi ba sai ranar alk’iyama. Suma da suka idar da sallahr barci ne mai nauyi ya ‘daukesu barcin da Talatu ta kira barci asara don dai sanda suka tashi farkawa tuni ta bayyana k’arara Hajiyar ta amsa kiran mahaliccinta ta hanyar ganin idanunta da suka yi sama fuskarta kuma da alamar murmushi. A razane Talatu ta dinga jijjigata tana kiran sunanta, sai dai ba alamun Hajiyar zata amsa, Talatu ta shiga tashin Jummai tana fa’din “Tashi Jummai Tashi hukuncin Allah ya sauka a kanmu.” A razane Jummai ta farka don dama barci ne yake yinsa mai wahalar gaske cike da munanan mafarkai. Koke-kokensu ne yasa Itama Ayra ta farka a razane tana lalubar Hajiyar tana kallon Ammanta ta ce “Amma menene?” Cikin kuka Amma ta ce “Ayra kin yi rashi, Ayra kin yi rashin uwa mai son ki.” Tuni Ayra ta fara kururuwa da k’arfin gaske…. Hakan ya ja hankalin duk wanda yake gidan, suka ji suka kuma shaida mutuniyar kirki Hajiya Kari ta amsa kiran mahallincinta. (Ba zan iya cigaba da typing ba, nima na tuna tawa mutuwar mahaifin shi da ‘dan uwana don Allah ku musu addu’a da ahalin musulmi gaba ‘d’aya da suka rasa rayuwarsu. Allah ya ji k’an su idan ta mu tazo Allah Yasa mu cika da kyau da Imani.) 😭😭😭 Takaicin Uba…. 46. 💔💔💔💔 Kafin kace meye wannan? Labarin rasuwar Hajiya Kari ya kara’de duniya, nan da nan dandazon jama’a suka cika k’ofar gidanta dama harabar gidanta dank’am da jama’a, tabbas Hajiyar ta dace don kowa alherinta yake fa’da da taimakon da takewa talakawa da miskinai. Almajirai kuwa da iyayen marayu suma kuka suke kamar wani nasu ne ya mutu. Haka nan k’usoshin gwamnati masu rik’e da manyan mak’amai suma sun halarci jana’izar. Gwamna da tawagarsa da ma sarakuna suma sun zo don jana’izar wannan baiwar Allah tabbas baka sanin waliyi bawan Allah sai a yayin da mutuwarsa ta riskeshi. Hajiya kam ta samu kyakykyawar shaidar da kowa yake kyautata mata zato, sai dai fatan Allah yasa ta mu muma ta yi kyau kamar yarda ta magabata suka yi kyau. ___________ Kwana bakwai rus a kai ana zaman makokinta ana ci ana sha, sai gidan mutuwa ya fara riki’dewa yana komawa kamar gidan biki. Kowa budirinsa Yake yi idan ka cire Talatu da Jummai da har rama suka yi saboda alhinin mutuwar Hajiyar. Abinci wannan Talatu bata iya shansa sai dai ta surka farau-farau ta sha ya tsaya mata a madadin abincin. A daren bakwai ne suna zaune da Jummai jugum-jugum. Tuni suka fara ha’da kayansu don daga yanayin kallon da dangin Hajiyar suke musu sun san ba za su barsu su ‘dara daga gobe ba. Don tun ranar kwana biyar suka sanar da su su ha’da kayansu su wuce don kashegarin bakwai za’a gark’ame gidan Hajiyar tunda ya zama na magada. Jummai ta saki ajiyar zuciya bayan dogon tunanin da ta fa’da gaba ‘d’aya ta sare da lamarin duniya tana kuma nadamar abubuwan da ta aikata wa Talatu don haka tana kallon Talatun ta ce “Talatu, zan rok’i alfarma wajenki, ki yafe min abubuwan da suka faru, komai ya faru ne bisa ingizar shai’dan.” Talatu tana kawar da k’wallar idonta ta ce “Dama ban rik’e ki da komai ba Jummai, na yafe miki tun tuni Allah ya yafe mana.” Jummai ta mata godiya kafin ta ce “Yanzu kenan gobe sai mu koma can inda Hajiya ta bamu, tunda da takardu da komai kuma shaidu sun tabbatar. Allah sarki Hajiya tabbas na ji mutuwarta sosai da sosai shekararmu ashirin fa tare.” Talatu ta sake share k’wallarta ta ce “Bana tunanin a duniya za’a samu mai karamci da mutunci irin Hajiya, zuciyarta daban take da ta mutanenmu na yanzu, da ba abinda suka sani sai taka Talaka da ci masa mutunci, amma dubi yarda Hajiya ta maye min gurbin Iyaye miji har ma da y’an uwa na tabbata har abada ba zan daina kukan rashin Hajiya ba.” Jummai ta saka hannu ta zaro wayarta da take cikin k’aramar jaka tana k’ara ta kara a kunnenta. Kamilu daga can b’angaren ya ce “Salamu Alaikum Hajiya, ai na kwana biyu ina neman ki baki ‘daga ba.” Jummai ta saki ajiyar zuciya ha’de da cewa “Lokacin zuwanka ya zo, zan turo maka da Adreshin da zaka same mu zuwa gobe da safe, don za mu bar gidan da muke ma sabida matar gidan ta rasu.” Kamilu ya saka salati yana fa’din “Ashsha, Allah ya ji k’anta da rahama ban sani ba Ai da nazo.” Jummai ta ce “Ai gaisuwa bata rib’a yanzu dai ka samu dama kazo kaga muhallinsu tunda ba zaku barta da kula da yara mata ita ka’dai ba.” Kamilu ya ce “K’warai kuwa, tunda dai shi Kabiru ya kafe Ai shikkenan rayuwa ce, Zan shigo In sha Allah na duba su.” “To sai ka ji ni.” Ta fa’da tana zare wayar daga kunnenta idanunta a kan Talatu data zuba uban tagumi, hankalinta sam baya kanta balle ta fahimci wayar da take. “Talatu, da k’anin Mijinki Kamilu muke waya, na gaya masa zai zo In sha Allah..” Da sauri Talatun ta ‘dago tana kallonta kafin cikin rawar murya ta ce “Haba Jummai ya zaki min haka? Na tabbata idan Kamilu ya san inda nake kamar Kabiru ya sani ya gama.” “Kabiru ya ce baya buk’atarku, ya ma sake aure yana can lagos da matansa da yaransa maza da yake so a haifa masa ke kuma ya ce Matan ya bar miki, Kamilu kuwa abinda yasa na shigo da shi cikin rayuwarki don ya zamewa yaranki garkuwa, bai kyautu ace ke Mace ke za ki yi tarbiyyar yara mata har biyar ba, babu mai saka muku ido, daga haka za’a k’ulla muku wani babban sharrin da zai ya bibiyarku a rayuwarku, don haka zan sadaukar da kaina na auri Kamilu tunda gidan mu a jikin na juna yake na tabbata zai saka ido sosai a kan yaranki. Ban kuma yi da mugun nufi ba, na yi ne don Allah da son nima na fara koyi da wasu ‘dabi’un Hajiya na son taimakawa wanda yake neman taimako.” Talatu idanu kawai ta zubawa Jummai tana mamakin k’udirar Ubangiji wato kowane mutum da ranarsa ashe ha’duwarta da Jummai shima alheri ne, tunda take bata tab’a hasashen haka ba sai yanzu da Jummai ta yi mata haka. Godiya ta shiga mata sosai kafin ta saka kuka. Jummai ta dafata ta ce “Kada ki damu Talatu, ki ‘dauke ni kamar y’ar uwarki ni kaina yanzu ina jin ki kamar wani sashe na jiki na, Allah ya ‘dora mu a kan Kamilun ya amince da buk’atar mu.” Talatu ta ce “Ameen, amma bana tunanin zai k’i tunda a zahiri taimakonsa kika yi da zaki auresa.” Jummai ta ‘d’aga kai kawai tana jin wani nauyi da ya da’de cunkushe a zuciyarta yana bajewa a hankali ko bakomai yau ‘d’aya ta farantawa Talatu tana kuma Allah ya duba hakan ya yafe mata kuskurenta. Talatu ta muskuta tana gyara zamanta sabida yanzu ta ‘dan yi k’iba ta murje ta ce “Amma Jummai ya aka yi kika san Kamilu?” Jummai ta saki malalacin murmushi mai bayyana tsantsar nadamarta ta fara bata labarin duk wasu abubuwan data aikata don ganin ta tunku’deta daga jikin Hajiya, ciki kuwa har da zuwan ta Shagogo. Sai data gama sannan ta ce “Amma don Allah Talatu ki yafe min, wallahi na yi nadama sosai.” Talatu ta saki murmushi ta ce “Wallahi na yafe miki Jummai. Amma yanzu ya zaki yi da yaranki da suka nuna basa son ki yi aure.” Jummai ta saki dariya “Yanzu kuwa ai dole su so, Ina ce su matan a ‘d’akin mazajensu suke kamar yarda su ma mazan suke da nasu Matayen, shikkenan ni sai su haramta min aure bayan da sauran jini na a jika.” Talatu ta saki murmushi kawai ta ce “Allah ya tabbatar mana da alheri, amma ni ko sha’awar aure ba nayi a raina, jira nake ma na maka Kabiru a kotu ya sahhale min ragowar igiyarsa da ta yi saura, don ko yana mutuwa yana dawowa ba zan amince na koma gidansa ba wallahi, gwara ko hul’i a yi mana na biyasa sadakinsa ya sakar min mara na yi fitsari don wallahi sai ya sake ni.” Jummai ta ce “Ina bayanki Wallahi Talatu, me za’a yi da Miji irin Kabiru? Tunda nake ban tab’a ganin matsiyaci ba irinsa, ki yi hak’uri dai uban y’ay’anki ne, amma dole na fa’di gaskiya.” Talatu ta yi murmushin takaici kafin ta ce “Wallahi zage shi son ranki, ya cancanci zagin ne ai shi ya jawowa kansa.” _________ Kashegari kuwa kamar yarda y’an uwan Hajiya suka ce haka suka zo suka sallami su Talatu ko nace suka musu kora da hali don k’arfe bakwai a gidan ta musu suka fitar da kowa har mai gadi basu bar sa ba. Cikinsu ba wanda ya damu tunda suna da mahallin zama, hatta da furniture sai da Hajiya ta zuba musu a gidajen nasu masu ‘dakuna bibbiyu da falo da kitchen da toilet a falo da kuma cikin kowane ‘dakuna. Gidan dai Ma sha Allah ‘dan madaidaici mai kyau da shi. Kuma cikin unguwa ‘d’aya a layi ‘d’aya. Gidan Talatu a jikin na Jummai yake. Talatu har hawaye ta yi da suka zauna suna kimtsa kayansu. Ayra ma Zugum Ta yi, haka sauran da su sun zama y’an mata Majeeda na da shekaru sha takwas ita kuma Zainab na da sha bakwai tunda tazararsu shekara guda ne, Ayshatu tana da sha biyar da rabi. Deejah ce mai sha d’aya sai Auta Ayra da take da bakwai. Majeedah da Zainab ma a wannan shekarar za su gama makaranta Aysha tana SS 1 Deejah na JS 2 sai Ayra mai primary 2 a intercontinental School. A yammacin ranar da suka dawo, sai ga Kamilu yazo. Jummai ce ta je har titi ta taro shi. Ta kuma rakasa har gidan Talatu inda Kamilu ya hau baza ido yana kallon yarda Talatun ta zama uwar mata ga yaranta mata kyawawan gaske. Ya dinga binsu da ido Suna gaisheshi cike da ladabi don yaran Talatu ba dai tarbiyya ba. Talatun ma ba yabo ba fallasa ta gaida shi, kafin ta saka Zainab ta kawo masa abincin da suka girka jallop ‘din shinkafa da bandar kifi ta kuma kawo masa zob’o a jug. Sai da ya ci ya yi hani’an sannan Jummai ta dubeshi ta ce “Kamilu ina son magana da kai, amma ka dubi girman Allah ka gaya min idan abinda zan gaya maka zuciyarka ta amince da shi.” Ya ‘daga kansa “Fa’di kan ki tsaye hajjaju ba abinda zan b’oye miki.” “Aurenka nake son yi, ba don komai ba sai don ka zamewa Talatu da yaranta da ni kaina Garkuwa.” Wani irin washe baki Kamilu ya yi ba wani ja’inja ya ce “Na amince Hajjaju ko yau kike so a ‘daura kawai, tabbas an yi aiki da hankali a nan.” Jummai ta yi murmushi ta ce “Ai dama yau za’a ‘daura a masallacin unguwar nan don na sanar da wanda zai amsa auren nawa ma.” Kamilu cike da nisha’di ya ce “Falillahil Hamdu amma fa ba ni da sadaki.” “Sai ka bayar daga baya.” In ji Talatu ta fa’da tana ‘dan sakin murmushi. Wannan ne mafarin auren Kamilu da matarsa Jummai. Daga ranar ya tare a gidan Jummai. Sai da sati ya zagayo, sannan ya ‘debi Jummai suka tafi Shagogo inda a can sauran matansa suke. Bata wani samu matsala da mutanen garin ba ta yi kwana biyu ta dawo. —————— Kwatsam bayan zuwan su da sati guda labarin rasuwar Innar su Kabiru ya riskesu, wacce ta zamo Uwa ga Kamilun ya gigita k’warai da zancen mutuwar Innar don haka da asussuba suka hau shiri shi da Jummai don su tafi Shagogo. Jummai tana gama shiri ta fa’da gidan Talatu don ta sanar mata. Talatu ta ware ido tana kallonta “Inna ta mutu Jummai?” Jummai ta ‘d’aga kai “Kinga kuwa zuwa Shagogo ya kama ki, ni ina son ma ki je suga yarda Allah ya mayar da ke duk wanda ya gan ki yanzu ya san Naira ta zauna Hajiya kawai ki shirya mu je.” Talatu ta yi ‘dan jim tana wasi wasi a ranta, sai kuma ta tuna yarda Kamilu yake kula da al’amarinsu bai kamata ta kallesa ta ce ba zata gaisuwar Mahaifiyarsu ba, ban da wani ga jikokinta har biyar da idan aka tsaga jikinsu za’a ga Jinin Inna ya zama dole ta je. Ta ‘d’aga kai “Shikkenan bari yaran su yi sauri su shirya sai mu ranka ya ga ba ‘d’aya ko bakomai ina son ganin Kabiru dama a yi wacce za’a yi.” Haka ta shiga wanka a gaggauce su Majeedah ma suka kimtsa kayansu suka kuma shirya cikin rantsatstsun dogayen riguna bak’ake haskensu ya sake bayyana ga wani kyau da suka sake yi gwanin sha’awa Ma sha Allah, har wani sihirtaccen k’amshi suke fitarwa. Talatu ma ta fito tsaf cikin wani lace ‘dinta mara nauyi coffee colour ya sake fitar da zahirin kyanta da kwarjininta. A tasha suka samu babbar mota wagon da zata kai su k’auyen Shagogo suka biya ku’dinta gaba ‘d’aya. Kafin su isa ma har an kai gawar Innah. Isarsu a motar yasa su Kabiru da suke zaman makoki zubawa motar ido, suna jiran su ga wa’danda za su fito daga motar. Yawun bakin Kabiru ne ya k’afe k’af sanda ya yi arba da Talatu da zaratan y’an matanta! To fa! Ko ya zata kasance mu ha’du ranar litinin In sha Allah, nagode sosai. Jikar Nashe Taku ce.😊 Takaicin Uba… Nazeefah Nashe 47. 💔💔💔💔 Idanuwan Kabiru sosai suka shige cikin na Talatu, da tsananin mamaki yake kallon yarda Talatun ta canja gaba ‘dayanta. Ta yi wani irin murjewa da k’iba ga fatarta sai shek’i take tamkar dai zuwa aka yi aka saketa a engine. Bai tsinke da lamarin ba sai da ya ga yarda yaransa ma suka zama kyawawa da su gwanin sha’awa. Ta gabansu suka zo suka wuce ba tare da ko kallonsu sun yi ba, don Talatu bata basu tarbiyyar kula mutane akan hanya ba. Kabiru ya shak’i wadataccen k’amshin da haka kawai ya zauna a kayan Talatu ko bata saka kaya ba sai ka ji wannan k’amshin tun suna gidan Hajiya ya bi ya yi naso a kayansu. Sarai ta gan shi ta kuma ji kaifin idanunsa a kanta saboda yarda ya tsareta da ido ko mutanen wajen sun lura da shi. Nan hirar jama’ar wajen ya koma kanta fa’di suke Kamar Talatu ko? Hadi ‘dan kanzagin Kabiru ya ce “Wallahi itace, ai wato Alaji in dai ka ce zaka shiga harka ta karuwanci zaka aikta abinda ya fi haka ma.” Kamilu da yake gefe zuwan sa wajen kenan ya ji kalamin Hadi sai ya ja tsaki ya ce “Allah ya kyauta maka Hadi da wannan k’azafin da ka mata Ina tabbatar maka sai kun tsaya gaban shaidu ranar alk’iyama a ina kaje ka ga tana Karuwancin? Ku sam mutuwa ma ta kasa zame muku Ishara.” Ya fa’da yana kallon Kabirun da ya fa’da zuzzurfan tunanin Talatu da yarda ta koma zai iya rantsuwa kaf matansa ba wacce a yanzu ta kama k’afar Talatu wajen kyau da cikakken dirin jiki, ya zama dole ya yi wani abu kai dole ne ya mayar da aurensa da Talatu ko tana so ko bata so. Kamilu dai ya zabga tsaki ya shige cikin gidan a zuciyarsa yana nemawa Talatu add’oin shiriya da kariya daga sharrin su Kabiru da muk’arrabansa don a zamansa da Talatu ya fuskanci kyawawan halayenta da nagartattun d’abiunta sam bata ‘dau duniya da zafi ba, tana kuma da kyauta sosai da sosai abin hannunta bai rufe mata ido ba. Sanda Matan gidan suka ga Talatu sam basu ganeta ba, tunda shekarun da dama shekaru har bakwai rugis dole komai ya canja. Ta zauna tana gaishesu kafin wata daga cikin k’annen Kabiru mata ta ce “Ikon Allah! Sai na ga kamar Talatu ko?” Talatu ta ‘dan saki murmushi ta ce “Nice Sabuwa ya hak’urin Inna?” Sabuwa ta saki salati cikin alajabi ta fara k’walawa jama’ar gidan kira tana fa’din Jama’a ku zo ga Talatu.” Kan kace me gida ya cika damk’am kowa fa’di yake “k’warai na so na shaida kamannin to gaba ‘d’aya ta canza ga zaratan y’an mata wa zai kawo ita ce. Wata kuma ta ce “Oh Talatu rai kan ga rai yanzu duk tsawon shekarun nan ina kika shige?” Sakina mara kunyar cikinsu tace “Kema dai Yaya Algaje da wani zance kike, to har a wani tambayi in da ta shige ga alamu nan sun bayyana Ai yawon karuwanci ana samun ku’di k’arshe ne dai ba zai yi kyau ba.” “Eeh, k’warai kuwa y’ar nan na ga Alama, da Idanu na ya rife to Allah ya rufa mana asiri, ai kuwa idan haka ne Kabiru dole ya karb’i y’an matan nan a aurar da su ko su Lawandi a rok’a su auresu don ba a barta da yara mata a hannunta ta saka su a Hanyar banza ba.” A harzuk’e Majeeda ta ‘dago zata yi magana Jummai ta ‘dan harareta kafin ta ce “Yanzu ku fisabilillah wa ya ce muku Talatu yawon karuwanci ta tafi? Ku baku san girman k’azafi ba ko? To Talatu tunda ta bar gari nan muna tare kuma ban tab’a ganinta tsaye da wani Mijin ba balle ta kai ga maganar karuwanci.” Talatu ta saki murmushi mai ciwo tana mik’ewa ta ce “Jummai ki rabu da su, ba za su tab’a fuskantar kalaman Ki ba kin san akwai k’arancin ilimi kuma ni na janyowa kai na da nazo garin sai dai an yi na farko an yi na k’arshe, kuma karuwanci da kika ce Ina yi ina ce idan ma na yi ba matsalarku a ciki, kuma ba karuwanci ba ko me na saka yara na ina ce ba abinda ya shafe ku da su akwai abinda kuka tab’a basu ne tunda aka haifesu sai yanzu da suka girma ake nema ace za a gwada min k’arfi to ko shi Kabirun bai isa ya min iko da y’ay’a ba, yanzu na san mutuncin kai na na san kuma hanyar da ake bi a maka mutum a kotu don haka ku kiyayeni, yanzu na da bace bana shakkar kowa!” Tsananin mamaki da razani yasa suka kasa yi mata magana suka ja bakinsu suka yi tsit suna aikin kallonta a tsorace a hasashensu tabbas kamar yarda Talatun ta canja haka halayenta gaba ‘daya ya canja. Haka suka dinga jan jiki ‘d’aya bayan ‘daya suna ficewa daga ‘dakin don tabbas basu hango sauk’i da salama a idanun Talatun ba. Ba ‘digon sassauci a tare da ita sam. Har azahar suna gidan mutuwar, inda gidan mutuwar ya zama gidan gulma da tsegumi don wasu dai ba don Allah suke zuwa ba sai don su ga Talatun da yaranta da suka koma tamkar ba hausawa ba, fatarsu ta goge ga hasken ilimi da tarbiyya a tattare da su. Sam Kabiru ya kasa hak’urewa zuciyarsa har sai da ya mik’e bayan ya gama jin zugar da Hadi yake masa, ya nufi cikin gidan da zummar a yi wacce za’ayi. Sanda Talatu ta ji muryarsa sai da gabanta ya bada tsananin bugu ba don komai ba sai don tsanar ta gansa ‘din ba ta burin wata mu’amala ta sake ha’data da shi, da ta san kuma zasu ha’dun ba abinda zai kawota garin duk da dama burinta shine su ha’dun a yi wacce za’a yi. Ta ha’de rai ta tsuke fuskarta tamau kamar bata tab’a fara’a ba. Ta kalli su Majeeda da suke zaune a gefe a takure kamar ma a tsorace suke don rashin sabo. “Ku matso nan kusa da ni Majeedah.” Suka kuwa matsa ta na kallonsu ta ce “Ko ya shigo ban amince ku gaisa da shi ba don sarai na san kun gane shi, Deejah da Ayra ne kawai ba za su ganesa ba.” Majeeda sake ha’de rai ta yi kafin ta ce “Amma Yaushe za mu tafi?” Ta fa’da tana kallon Amman. “Yanzu In sha Allah.” Amman ta amsa mata daidai lokacin da sautin muryar Kabirun ya cigaba da k’ara kusanto su alamar nan ‘din zai shigo. Amma ta cizi bakinta tana hasashen wani irin rashin mutunci zata masa idan ya nufi yi mata magana. Sai ga shi kuwa ya ban ka’da labulan ‘dakin idanunsa a kan su Talatun da yake wa wani irin kallo mai cike al’ajabin yarda suka koma. Ya saka kansa ya shiga ‘dakin duk da yanayin fuskar Talatun ta firgita shi bai fasa himmar yi mata magana ba. “Su Talatu manyan gari, idan ke ban ci darajar da zaki gaisheni ba su kuma y’ay’ana da nake matsayin Ubansu me yasa ba za su gaisa da ni ba?” Talatu ta ‘dago cikin wani irin mabayyanin b’acin rai da Kabirun bai tab’a ganinta da shi ba ta ce “Y’ay’anka Kabiru? Y’ayanka fa kace? Yanzu ko kunyar furta hakan da bakinka ba ka ji ba, ai bai kamata a ji wannan kalmar a bakinka ba ko ka manta sanda ka ce ka bar min gayyar yara matan na je na k’arata da su har abada baka buk’atarsu? Yanzu ne kake kallon su kake kiran kanka Ubansu? Ta ina ka amsa sunan Ubansu? Ka yanka musu ragon suna? Ka ‘d’au nauyin ci da shan su? Ko ka san harkar neman iliminsu? Don haka kada ka sake duban yarana ka kira y’ay’anka, magana ta biyu shine ina son amsar takardar saki na a wajenka don na zama cikakkiyaf bazawara mai y’anci, duk da ban ‘dau gantalallen aurenka aure ba kawai dai ina son shaidar da zan kafata ko don gaba, ba zaka tare ni kace kana da aurena a kanka ba don ko mutuwa nake idan aka kai gawata gidanka ban yafe ba don haka ka bani shaidar takardar sakina ko kuma ka bani a gaban alk’ali.” Kabiru tsayawa Yayi yana kallonta cike da mamakinta, Talatu ce ta dawo haka? Talatu ce take iya tararsa tana gaya masa magana mai zafi haka, ashe kuwa za’a yi ta don aure yanzu ya fara bai ga kuma kotun da zata iya amsar takarda ta bawa Talatu ba a wajensa. Ina da sake yarda ya ga Talatun ta murje duk wata halitta ta matantaka ta sake bunk’asa a jikinta kamar ma yanzu mak’erin y’an mata yake k’erata sannan ta ce ya saketa, ta ina za’a fara tabbas za su buga wasa shi da ita don ko ana muzuru ana shaho sai ya maidata gidansa. Cikin k’arfin hali da dakewar murya ya ce “Kada ma ki fara wannan maganar Uwar gida na! Aure Ai yanzu na fara yi da ke, ni da ke mutu ka raba takalmin kaza.” “Kan uban can!” Talatu ta furta cikin muryar tashin hankali da sauri yaranta Suka kalleta suna mamakin jin zagin a bakinta “Baka so gamawa lafiya ba Kabiru dole ka sake ni, idan ka ga na koma gidanka ashe kuwa Ubana ne ya dawo duniya ya ce idan ban zauna da kai ba zai tsine min.” Kabiru ya saki murmushi yana wani kallonta k’asa-k’asa ya ce “Kin manta ko waye Kabiru ko Talatu ashe kuwa yau tuna miki, a yau zan sadu da ke na mayar da aure na cikin ‘dakin nan idan yaso na ga uban da zai raba min aurena, don yarda na kwa’daitu da ke dole ne yau na kaiwa gonarki ziyara, kai yara ku ba mu waje.” Ya fa’da yana mik’ewa tsaye yana k’ok’arin zage tazugensa bayan ya ga fitar yaran da sauri illa Ayra da ta ja ta tsaya ta k’i fita don gani take wani mugun abin zai aikatawa Ammanta. To fa! Amma Kabiru an yi tantiri. Ku yi hak’uri yau ciwon kai na yi shi yasa za ku ga typing ‘din ka’dan. Takaicin Uba. 48. 💔💔💔💔 Sosai Talatu suka fara kokawa da Kabiru kafin ta ciri hannunta ta zabga masa mari ta sauke hannun tana fitar da hucin b’acin rai “Ni kika mara Talatu?” “An mareka ‘din kuma ka sake kusanto k’azamin jikinka zuwa wajena ka ga idan ban maka abinda ya fi mari ba, Ka zata ni ‘din Talatun da ce? Talatun da ka mayar dabba ka haik’e mata duk sanda ka so a kuma lokacin da kaga dama, wannan karan a wanke idanuna su ke kuma na san abinda duniya take ciki, sam ba zan yarda ka take min hakkina ba da sunan wai igiyar aurenka ce a kaina, kuma da ka sake ni da kada ka sakeni uwarsu ‘daya uban su ‘d’aya na tabbata akwai inda zan kaika a saka kuma ka sakeni ta dole, bak’in mugu azzalimi Ai jikina yanzu yafi k’arfinka Kabiru ko kai idanunka basu nuna maka haka ba?” Ta sake zabga masa tsaki Daga haka ta ja hannun Ayra da take tsaye a gefe tana kallon Kabirun cike da tsana da jin haushin yarda ya mak’ure mata mahaifiya. Ba wanda ta yiwa sallama sai Jummai da ita ba zata koma a lokacin ba sai an yi sadakar bakwai ta saka kai ta fice. Shi kuwa Kabiru gaba ‘daya gwiwarsa ce ta sare ya kasa katab’us kafin ya ji sallamarta da Jummai da sauri ya ‘dau wayarsa ya kira Hadi yana ‘dagawa ya ce “Hadi maza ka bi min Talatu har can gidan da take kada ka dawo sai ka ga inda ta shiga tunda bata san motata ba mukullin motar yana hannunka ko?” Hadi ya ce “k’warai yana hannuna” “To maza kada ka yi wasa ka tabbatar ka bi motar da ta shiga kada ka bari wannan damar ta wuce mu, akwai alheri mai yawa tattare da zama na da Talatu da nake jin yanzu ina mata son da ba nawa mata macece shi.” “Hadi ya ce In sha Allah ranka ya da’de ga tanan ma ta fito bari na yi sauri na bi ta.” Ya katse wayar yana mik’ewa ya nufi can inda motar Kabirun take. Sam ba su san Hadin yana bin su ba har suka je gida, Hadi ya saki ajiyar zuciya bayan ya ga har unguwar da gidan ya kuma haddace ra’dam a kansa. Wannan shine mafarin sanin Kabiru inda Talatu take har ya bisu bin da ya zama mummuna kuma bak’ar k’addara a wajensu da su da duk wani mai son su. Hadi ya komawa Kabiru da dadda’dan labarin da ya samu kyauta mai tsoka saboda shi. Duniya kenan mai juyin waina yau dai ga Kabiru da ku’din sa yake biya don a gano masa mahallin Talatu da inda take zaune. Ga kuma soyayyarta da ta d’inke masa zuciya abinda bai yi zato ba ko tsammani. Bayan sadakar bakwai kafin ya koma lagos ya k’udiri aniyar zuwa Inda Talatu take ya kuma shirya tsaf zai je mata a yanda take so idan taso ya rarrasheta zai bita da rarrashi idan kuwa bata so ba zai bita da rashin mutuncin da ta buk’ata. Ba kowa a gidan sai ita ka’dai duk sun tafi Islamiyya saboda yammacin ranar laraba ne. Bata fiye kulle gida ba saboda y’an siye da siyarwa da take na kayyakin masarufi idan suna nan dai gidan a bu’de yake idan kuwa basa nan sai ta sakaya saboda bata son yawan mik’ewa bu’de k’ofa. Yanzu ma tsaf gidan a gyare yake don sai da y’an matan nata suka gyara gidan suka yi abinci sannan suka shirya k’annensu zuwa Makaranta. Gidan sai k’amshin turaren wutar da Zainab ta saka yake. Lokacin Talatu tana zaune da littafin Azkar a hannunta tana karanta na yammaci a kan farar kujera a ‘dan harabar tsakar gidansu. Daidai lokacin Hadi ya kawo Kabiru har k’ofar gidan yana kallonsa ya ce “To yallab’ai ga fa gidan Talatu.” Kabiru ya sauke nannauyar ajiyar zuciya ya ce “Ka tabbatar?” Hadi yana ‘d’aga kai ya ce k’warai kuwa Dahir nan ne gidan, a sha angwanci lafiya.” Ya fa’da yana dariya da sosa kai. Kabirun ma wani murmushi ya saki shi ka’dai yana fatan hakan ta kasance don da zarar ya Rufe ido surar Talatu ce da ta cika ta tumbatsa take masa gizo. Ya fice daga motar bayan ya sake gyara zaman hular sa ya kuma bulbula turare “Yauwa Hadi Idan na shiga gidan sai ka samu yara su sauke kayan abincin nan. A shiga da su Kai kuma sai ka je ka dawo da magriba don idan naga na samu waje to zama na zan yi sai na yi sati guda ina kwasar ganima.” Ya fa’da yana shafa gemunsa Hadi ya ce “Allah ya kai damo ga harawa mutumina Talatu yau ta fa’da hannun y’an maza Ai kai in dai wannan harkar ce kullum kar kake a leda sai ka ce k’akkarfan doki shi yasa matan Ai suke kawo kansu gareka da k’afafunsu.” Kabiru ya tsuntsire da dariya yana gyara zaman babbar rigarsa. Ya tura gate ‘din ya shiga. Jin takun takalmi yana tunkaro inda take ne yasa ta ‘daga daga karatun azkar ‘din da take, idanunta suka afka cikin na Kabiru da yake tsaye ya rungume hannayensa a k’irji yana sakin murmushi da ko kyau bai masa ba, don dai ita bata hango kyan ba tunda ba saba mata murmushin ya yi ba, asalima muninsa ta ga ni duk da Kabiru kyakykyawa ne ba shi da makusa ko ka’dan dirarren namiji ne mik’akke samb’al. Sai mugunta fal a cikinsa. Talatu takaici ne ya tokare mata mak’oshi ta fara jin haushin wanda ya bawa mijinta adireshin gidan duk da ta san ba zai wuce Jummai ko Kamilu ba. Kabiru ya cigaba da tunkarota yana sakin murmushi ha’de da cewa “Haba Uwargida na ba zaki kula ni ba kina ganin na biyoki ban yi fushi ba.” Wani zagi ta k’unduma kafin ta nuna masa k’ofa “Kabiru fita ta k’ofar da ka shigo da kanka ko na karya maka k’afafu a fita da kai ta dole” ta fa’da tana hucin b’acin rai Kabiru da ya ji alamun ba kowa a gidan bai San sanda ya shammaci Talatun ba ya yi mata ‘daukar amarya ya shige k’ofar da ta Sada shi da falonta kafin ya Saka Kai zuwa inda ya tabbatar ‘daki ne, Talatu da k’arfi take kokawa da shi don kwatar kanta amma ta kasa saboda ba k’aramin rik’o ya yi mata ba sai da ya direta a kan gadon sannan ya saka k’afa ya danneta ya fara k’ok’arin cire suturar jikinsa. Kafin itama ya saka hannu ya keta rigar da take jikinta. Ganin surarta da komai ya tsaya k’yam kamar ma bata tab’a shayarwa ba hakan yasa ya fara aikata komai kamar mayunwacin zaki Talatu ta dawo sabuwa a garesa sai yanzu mak’erin y’an mata ya fara k’era masa ita komai ya yi b’ul b’ul luhu luhu ihu yake kawai yayin saduwa da ita sabida wata duniya ya tafi mai wuyar fasali Talatu kuwa Allah ya isa kawai yake ja masa tana zaginsa Amma Inna ba ya ji ba ya gani gaba ‘d’aya ya fita hayyacinsa zai iya cewa bai tab’a jin da’din saduwa da kowace mace ba kamar yarda ya ji da’din Talatu komai ya cike tsaf ba wannan kwararon ko don an da’de ba a sadu da ita bane, tunda Talatun irin Matan nan ne masu fatar roba.” Sai da komai ya nutsa sannan ya jata jikinsa da niyyar rarrashi sai dai tuni ta tureshi cikin b’acin rai ta tofa masa yawu ha ‘ce da mik’ewa ta ja zaninta ta ‘daura a zafafe ta shiga kitchen cikin k’unar zuciya ta ‘dauko wuk’a a hannunta ta nufo ‘dakin da sauri cikin wani irin zafin rai ta ce “Ta shi ka bani takardar saki na ko na hallaka ka matsiyaci Wallahi da na cigaba da aurenka gwara na kasheka idan yaso nima a kashe ni.” Da sauri ya mik’e ganin ta nufoshi da gaske kuma tabbas daga ganin idanunta ya tabbata zata aikata abinda ta ce ‘din “Tsaya Talatu tsaya mu yi sulhu Wallahi na canja hali zan zauna da ke k’alau. Zan yi miki duk abinda kike so.” “Kada Allah yasa ka yi abinda nake so ‘din, wallahi sai ka sake ni a yanzu ko kuma na kwashe gabanka idan ma ban kasheka ba.” Ta nufe shi gadan-gadan da niyyar aikata abinda ta fa’da ‘din da sauri ya ce “Tsaya Talatu zan yi miki abinda kike so don Allah kada ki illata ni.” Ta sake nufarsa gadan gadan “To yi maza ka k’arasa min saki ‘dayan da ya rage ga takarda da biro nan.” Ta cilla masa hannu na rawa ya fara rubutu jin wuk’a a gabansa tana ‘din yi kamar zata durzata ta ya rubuta sakin ya bata. Talatu ta mik’e tana sakin murmushi kafin ta sake ha’de ranta ta nuna masa k’ofa “Zo ka fice min daga gida tun kafin yara na su dawo su gan ka.” Da sauri jikinsa na rawa ya zura rigarsa. Babbar rigar ma a hannu ya rik’e Talatu ta rakashi har bakin gate tana fa’din “A yanzu ba sauran alak’a tsakanina da kai, don haka kada na sake ganin k’afarka a gidan nan ‘dan akuya kawai” Shi dai ya fice yana jin wani irin tafasar zuciya ga shi ya janyowa kansa ya yi ‘dan’dani haukaci ya laso zumar ta mai zak’in gaske da zata yi wuyar gogewa a zuciyarsa gaba ‘d’aya Talatun ta canja ta ji kayan Alatu irin wa’danda yake son ya ga matarsa da su. Sai da ya samu guri a bayan layi sannan ya kira Hadi ya ce ya zo su tafi. Hadi ya ce “Haba mai Gida har an gama?” Kabiru ya ja tsaki ya ce kazo mu tafi na ce maka ko?” Ya kashe wayar yana jingina da garu nadama takaici da dana sani suka ha’du suka masa rufdugu. Ita kuwa Talatu sai da ya fita sannan ta saka hannu aka ta fara rusa ihu sabida takaicin kusantarta da Kabiru ya yi duk da ta wani fannin ta ji da’din ya kusanceta ya ji ta dawo ras da ita kamar budurwa daga yanayin yarda yake kakkarwa da ihu a jikinta ta san ya ji komai Zam zam, ta san ta wuce wulak’ancin ‘da namiji a yanzu kam. Tana wanka tana kuka kafin ta zura doguwar Riga ta fito idanunta na sauka kan kayan abincin da ya dire a tsakar gidan ta zauna ta yi zugum gefe guda kuwa wata salama take ji a zuciyarta na rabuwa da auren Kabiru babu saurin hakkinsa a kanta. ______Bayan Shekara ‘daya. Abubuwa da dama sun faru kafin zagayowar shekara. Talatu suna ta samun cigaba a komai harkar kasuwanci da komai da komai. Yayinda gefe guda Kabiru yake cikin matsin rayuwa don komai nasa nema yake ya k’are tamkar dai maganar bokansa tana neman ta tabbata da ya ce zama da auren Talatu shine abinda yafi masa alheri ga shi nan kuwa yana gani don tuni duk wani tattalin arzikinsa yake neman rugujewa. Ga kwana da tashi da yake da tunanin Talatu sha’awarta tana neman kassarashi duk macen da ya kusanta idan ya kwatanta da Talatu sai ya ga bata kama k’afar Talatun ba, a sura da komai da komai. Hankalinsa bai tashi ba sai da ya ji labarin k’onewar shagonsa da ya rage masa k’urmus a kasuwa mai ‘dauke da kaya masu yawa a ranar kam Kabiru bai kwana da lafiy ba kashegari kuwa ya ja Hadi suka nufi wajen Malaminsa ko nace bokansa. Bayan dube dube bokan ya d’ago yana kallonsa “Tabbas ka rabu da arzikinka rabuwa ta har abada Kabiru idan baka aikata abinda zan saka ka yanzu ba. Ka bani sunayen y’ay’anka mata zan duba wani aiki a kansu.” Nan Kabiru ya shiga zayyano musu sunayensu don bai manta da sunayen ba. Boka ya zana sunayen a k’asa kafin ya ‘dago yana murmushi ya ce “An samu masu k’ashin arziki irin na uwarsu, guda biyu a cikin y’ay’anka Amma taurarin ‘daya sun fi na ‘daya haskawa don haka so samu ne mu yi aikin mu a kan wacce tauraron arzikinta yake da k’arfi zaka je ka kusanceta irin kusancin da miji yakewa matarsa ka samu maniyyin ka kawo min shine maha’din aikin ka idan har ka aikata haka maganin matsalar ka tazo.” Wata zufa ce ta karyowa Kabiru ya ‘dago yana kallon malamin a firgice ya ce “Y’ata ta ciki na Malam?” “K’warai kuwa Kabiru wannan shine mafita, kuma wacce Tauraronta yafi haskawa itace Shuayra don haka da ita muke son yin aikinmu…” wannan karan ba Kabiru ka’dai ba har Hadi sai da hantar cikinsa ta ka’da ya zaro ido yana fa’din “Yarinya ce fa k’arama da bata zarta shekaru takwas ba!” “Hahhahah dama mun fi buk’atarta idan ba zaku iya ba ku tashi ku tafi bama buk’atarku.” Tirk’ashi! Jikar Nashe ce✍🏽 Takaicin Uba… 49. 💔💔💔💔 Jikin Kabiru yana rawa ya mik’e ya fita daga bukkar, a zuciyarsa yana tunanin rashin Imanin nasa bai Kai haka ba, ta yaya zai iya haik’ewa y’ar da ya yi cikinta tazo duniya abin da kunya ai, ba ya tunanin ko y’ar wani nasa zai iya kusanta. Gumi ne ta ko ina yake yarfo masa tunawa da ya yi idan bai aikata hakan ba yana nufin zai dawwama a cikin talauci kenan. Ya yarfe gumin yana kallon Hadi da shima ya zuba masa nasa idon, idan ta Hadi ne sam bai gano wani abin tashin hankali ba a cikin aikata abinda bokan ya fa’da tabbas idan shine zai aikata ko da ta hanyar basaje ne da bawa yarinyar maganin nauyayyen barci. Don haka ya ja ajiyar zuciya yana dafa shi ya ce “Haba Kabiru yanzu kana nufin da ka aikata abinda mutumin nan ya fa’da gwara ka dawwama a talauci, ka shiga fa talaucin nan ka ji sam ba da’di shine kake son ka sake komawa, ka san duk abinda mutumin nan ya fa’da yana tabbata aikinsa tamkar yankan wuk’a yake ni dai idan da zaka bi ta tawa ka aikata ‘din kawai a wuce wajen.” Kabiru ya waro ido yana kallonsa “Me kake nufi Hadi na je na haik’ewa y’ata ta cikina? Idan asiri na ya tonu me kake son na cewa Talatu da duniya ma baki ‘d’aya?” “Sai ka yi mursisi tunda ba akan ka aka fara ba, ba kuma zai zama k’arau ba, balle Allah na tuba da zarar ka yi ku’din duk za’a manta abinda ka aikata na tabbatama har ka yi ka gama mu bar garin ba wanda zai gan ka zan tsaya maka a inda zaka aikata har sai ka cimma burin ka.” Kabiru ya ja dogon fasali da ajiyar zuciya bayan ya gama nazari ya kuma bi zugar Hadi da shai’danin da yake sake ingiza zuciyarsa yaga idan ba hakan ya aikata ba ba shi da wata manufa, don haka ya gyara zama ya ce “Yanzu Hadi ta ya kake ganin za mu samu har mu cimma ga ci, ba tare da Talatu ta gan mu ba ko ta ji mu?” “Yauwa ‘dan gari.” Hadi ya fa’da yana gyara zama kafin ya ce “Basaja zaka musu, wato b’adda kama mu bi dare mu shak’awa yarinyar abin maye a hanci sai ka farmata kawai a zuwan y’an fashi ne ko b’arayi.” “Idan Talatun kuma ta farka fa?” Hadi ya tuntsire da dariya “Ai itama sai mun shak’a mata sannan za mu aikata balle ko ta farka Ai ba zata san su waye ba tunda a zuwan b’arayi za mu je mata sai ka aikata abinda kake so mu fito kawai salin alin.” Ya fa’da yana shek’a dariya. Kabiru ya amince da shawararsa don haka suka koma wajen bokan suka amso maha’din sirrin suka fito ha’de da fara shirin yarda za su tunkari gidan Talatu. _________ A wani dare da ya zama bak’in dare ga ahalin Talatu, daren da ya shige musu cikin ranakun tarihin da ba za su tab’a mantawa ba, daren da kai tsaye za su iya kiransa BAK’IN DARE saboda tsananin muninsa garesu. Dare ne da ya sanya zuk’ata k’unci idanu suka zubar da hawaye gangar jiki ya girgiza hankula suka tashi. Talatu ta yi nadamar ha’de zur’ia da Kabiru da kai tsaye ya amsa sunan dan Akuya a wajenta ko bunsuru. Mutumin da zai sadu da y’arsa Ai dole ka kira shi da wannan sunan. Daren ya kasance Talata. A tsakiyar damuna watan august. An sharara ruwan sama kamar da bak’in k’warya hakan yasa garin ya sanyaya mutane kuma da wuri kowa ya gark’ame gidansa aka kwanta barci mai cike da da’di da nutsuwar zuciya. Tun a safiyar ranar Ayra take fama da mummunar fa’duwar gaba da zarar kuma ta shiga wannan yanayin suke tabbatar da wani abu mummuna ko mai kyau da zai afku garesu. Sai dai zuwa dare da Amman ta dage da musu addu’a sai aka samu ta daina sai ajiyar zuciya da take yi akai akai. Ana ‘dauke ruwan Majeeda ta ‘daura musu net a ‘dakunansu. Ayra da Dijah a wajen Amma suke kwana su kuma y’an matan su kwana a ‘dakinsu. Ranar sai Ayra ta kafe a ‘d’akin su Majeedah zata kwana sabida Deejahn ta karb’o musu wani cd plate na indian series film. Ga shi ta na son film ‘din. Juyin duniya suka yi ta koma ‘dakin Amma sai ta kafe hakan yasa Amman ta ce su k’yaleta amma su tabbatar sun mata addu’a sun kuma tasheta sun rakata fitsari. Majeedah ta ja hannunta suka je suka kwanta a kusa da ita suna kallon tare tana ta dariya. Cikin daren Hadi da Kabiru suka yi wa Unguwar su Amma Talatun titsiye. Fuskokinsu sanye da face mask da ta b’oye kamanninsu haka nan suna rik’e da maganin barci mai saka maye. Ta Katanga suka haura gidan tunda a rufe gate ‘din yake kuma dama sun zo da tsanin k’arfe a cikin motarsu haka yasa suka kafa suka haye sannan suka dirga cikin gidan. K’ofar falon a sakaye take don haka ba su sha wahalar bu’dewa ba. A hankali suke komai ba tare da motsi mai k’arfi ba. Har suka shiga cikin falon. Turus Hadi ya yi jin motsin ana bu’de ‘d’aki aka fito Amma ce tsaye tana dallaresu da torch light jikinta na rawa ta ce “Inna lillahi b’arayi!” Da sauri Hadi ya zaro wuk’a da bindigar roba ya nufata gadan-gadan cikin kaurara murya yarda ba zata ganeshi ba ya ce “Ki mana shiru idan ba ki na son kiga rayukan ki da na y’ay’anki zube a nan bane.” Jikin Amma na rawa ta toshe bakinta tana kallonsu ta zube a gabansu ta ce “Me kuke so bayin Allah ku fa’di mai kuke so in dai akwai shi zan baku.” Hadi ya tuntsire da dariya daidai lokacin da y’an matan suka farka a razane suka dirgo daga gado zuwa falo jikinsu na rawa Ayra har ta fara hawaye musamman da ta ga bindiga. Suna fitowa suka ji Hadi yana fa’din gwala-gwalai muke so da ku’di.” Amma tana kuka ta ce “Wallahi ba mu da gold ba ni da ku’di cash sai dai a banki.” Hadi ya sauke idanunsa kan y’an matan kafin ya ce “Idan duk babu wa’dannan za mu fanshesu a cikin y’an matanki Mai gida wacce za’a kawo maka ka shiga gonarta.” Kabiru ya nuna Ayra da take tsaye jikinta na rawa. Da sauri Amma ta sha gabansa “Don Manzon Allah ku yi hak’uri kada ku cutar min da y’a shekararta bakwai fa kacal Ina zata iya ‘daukar nauyin k’addarar nan. Na amince ni ku kusanceni a madadinta Amma kada ku cutar min da yara mata.” Hadi ya sake tuntsirewa da dariya ya ce “Oga ba ya son manyan mata yafi son irin wa’dannan y’an Shilaan don haka ita yake so ko manyan baya buk’ata idan kin amince ba rayuwar wanda za mu tab’a a cikinku idan kuwa ba haka ba duka zamu hallaka ku.” Amma ta zube tana wani irin haki ta ce “Ku ‘dau rayuwata a madadin yara na Amma Wallahi ba zan amince ku kusantar min wannan k’aramar yarinyar ba.” Hadi ya ‘dana bundigar a fuskarta kamar zai harba. Sai ganin Ayra ya yi a gabansa jikinta na rawa ta ce “Amma ki matsa su yi min abinda za su min in dai za su bar ki da ran ki.” Amma ta k’i matsawa kuka kawai take kafin Hadi ya sake murza bindigar k’arfen ta wasan yara Yana fa’din “Mai gida cika aikinka ku shiga ‘d’aki da yarinyar komai ya kammala duk wacce ta yi k’ok’arin biyoka kuma zan harbeta da gaske!” Suna kallo Kabiru ya sunkuci Ayra ko ina na jikinsa rawa yake yana jin kamar ya fasa wannan wani irin abin kunya yake shirin aikatawa. Ya shige da ita ‘dakin ya bar su da runtse idanu Amma tana jin kamar zuciyatta ma ta daina aiki dukkanninsh zube suke a k’asa suna wani irin kuka mai azabar cin rai. Ihun da suka jiyo Ayra ta zabga a d’akin ne ya ‘dauke numfashinsu gaba ‘daya suka daina ji da gani na wasu lokuta. Amma na kawowa nan daga bada labarin abinda ta sani na dangane da Kabirun ta zube a kan gadon Hameeda tana sakin wani irin numfashi mai wuyar fita daga huhunta da alama ciwon zuciyatta ne ya motsa. Ita kanta Hameeda ji ta yi k’irjinta ya yi nauyin gaske da kyar ta goge hawayenta tana lalubar waya don kiran likitansu yazo ya taimakawa Amma da suka ga kamar bata numfashi. Da ta san haka wannan labarin yake da sam ba Zata so jin sa ba, wannan wace irin rayuwa ce? Kuka kawai take tana tur da halin Kabiru zuciyarta ta cunkushe tana jin itama kamar zuciyrta bata aiki yarda ya kamata. Likitan yana zuwa ta basa umarnin shigowa sai dai yana auna Amma ya ce “It’s an emergency dole mu kaita asibiti.” Hameeda ta mik’e da sauri tana fa’din “Mu je Doctor, baba son Talatu ta rasa ranta a yanzu tabbas zai iya zama nice sila” To kafin su je asibitin bari mu koma Moscow. ________MOSCOW_______ A razane take da kallon da ya kafa mata tun bayan fitowarta daga toilet sanye da rigar barcin da ta bayyana duk wata sura tata, ta bi lafiyar jikinta ta kwanta luf. Turaki kokawa kawai yake da kansa bai kai kansa inda take ya ha’deta da jikinsa ya matse sosai sun zama abu ‘d’aya ba. Sussulb’an gashinta ta shiga tajewa Kafin ta saka band ta kama shi ta ‘daure ya sauka har gadon bayanta. Jikin Turaki a salub’e ya taso ya zaro dogon hijabinta na sallah ya zura mata “Mu yi nafila.” Ya fa’da k’asa-k’asa da murya. Gabanta ya fa’di tunda ita ba jahila bace ta san wannan nafilar me take nufi. Hannunta ya kama rawa musamman jin ya damk’ota ya sakata a gefensa sannan ya yi gaba ka’dan ya tada sallahr. Suna idar wa ya kama kanta ya karanta adduoin da Annabin rahma ya koyar da mu. Har a lokacin jikinta shaking yake, hakan da ya gani yasa ya janye jikinsa ya na mik’ewa. Wajen fridge ya je ya tsiyaya fresh milk mai sanyi ya sha sannan ya cilla chewingum mai mugun k’amshin strawberry a bakinsa. Itama ya tsiyaya mata ya kuma b’allar mata chewingum ‘din ya isa gabanta yana mik’a mata. Bata yi musu ba ta amsa ta kafa kai ta shanye kafin ta cilla chewingum ‘din a bakinta. Tana kallo ya kashe wuta ya nufo inda take sai ji ta yi ya mik’ar da ita tsaye yana zare mata hijabinta ya kuma cire rigar da take jikinta daga nan duk wani labari ya canja jin wasu irin zafafan hot romances da yake zuba mata tuni jikinta ya fara rawa ta ji abinda bata tab’a ji ba ta fara k’ok’arin k’wace kanta sai dai bai bata damar hakan ba, don ji ya yi shi kansa k’afafunsa ba za su ‘daukesa ba wani irin taushi da sulb’in fatarta suke neman ‘dauke masa numfashinsa ya sunkuceta gaba ‘d’aya zuwa kan gado. Shi kansa wasu abubuwan bai san yana aikatawa ba tun kafin ma ya kai birnin ya birkice ya ‘dimauce wasu irin maganganu kawai yake fitar wa masu saka Ayra jin kunya kafin itama ya gusar da bata hankalin ta fara mayar masa da martani a ‘dimauce, sun fa lula wata irin duniya da Ayra bata tab’a tunanin akwaita ashe haka auren yake? Sai dai da Ayra ta ji y’an mazan sosai a jikinta ta gane shayi ba ruwa bane…….. Mu cigaba gobe Tired 😴 Takaicin Uba…. 50. 💔💔💔💔 A haukace kamar mayunwacin zaki ya fara k’okarin shiga birnin Ayra, inda ya ji gam babu hanya Ba alamarta alamar Ayran budurwa ce gal sabuwa a leda. Ya runtse idanunsa yana mamakin lamarin. Kafin ya yi azama ya shigeta da sauri yana shafa duk wasu sassan jikinta. Azaba da ra’da’di ya saka Ayran Sakin wani gigitaccen ihu. Bai hanata ba don shima nasa ihun yake yi. Don Abin yazo masa a bazata bai tsammaci haka ba. Ayransa dal sabuwa a leda ga wata irin zafaffiyar ni’ima da da’di da Allah ya mata baiwa da su. Bai tab’a ba bai tab’a jin mace mai baiwar Ayra ba. Don haka ba a nutsuwa yake aikata komai ba, yi yake da wani irin zafin nama cikin sambatu musamman an da’de ba a ha’du ba. Wasu irin alk’awarurruka kawai yake zuba mata. Ina Ayra take fahimta jin ta, ganinta duk sun ‘dauke ‘dif wata irin azaba mai gigitarwa ta saka ta ja bakinta ta tsuke, don sosai ta lura lamarin yafi k’arfin kuka ko ihu azabar ta wuce fa’dinta da baki jira kawai take mala’ika yazo ‘daukan ranta don tuni ta saddak’ar. Samun nutsuwarsa shi ya dawo da shi hankalinsa, sai a sannan ya lura da aika aikar da ya mata hankalinsa ya tashi da azama ya jata jikinsa ya rasa ma da bakin da zai rarrasheta ga wata irin kunya da ta masa rufdugu. Kunyarta yake ji sosai kunyar da bai tab’a jinta ba a rayuwarsa da wani ido zai kalli Ayra bayan duk kallon da ya dinga mata na Karuwa har ta kai shi ga furtawa. Dana sani ya dinga shigarsa. Gefe guda kuma wata irin soyayyarta mai zafi ce ta dinga shiga jiki da b’argon jikinsa. Ya matseta sosai a jikinsa yana aikin shinshina gashin kanta murya a d’ashe ya hau furta mata “Sorry Hayateey.” Sai a sannan Ayran ta saki ajiyar zuciya wani kuka ya kece mata murnarta d’aya ya sameta da budurcin da yake mata gorinsa duk da zafin ya gigita wannan ka’dai ya isa ya faranta mata rai saura mataki na gaba. Cikin kunnenta ya ra’da mata “Ki yi hak’uri kin ji sweet don Allah ki bar Kuka ni ne ko? Ba zan sake ba.” Ayra ta saki ajiyar zuciya a zuciyarta ta ce “Ai dama ba zaka sake ba, a ina zaka ganni ma da zaka sake.” Ta ‘dan janye jikinta da k’yar da niyyar ta tashi sai ta ji ta kasa. Da sauri ya mik’e ya jata jikinsa ya saka ta a tsakiyar k’irjinsa “Ba zaki iya ba ki kwanta ki huta ina zuwa.” Ya fa’da yana mik’ewa bayan ya ja pyjamas ‘dinsa da sauri ya suturce jikinsa. Yana kallon Ayran da take kwance k’udundune da alama sanyi take ji. Ya bata kyakykyawar sumbata a lab’banta masu taushi da sulb’i ta janye fuskarta tana harararsa, murmushi ya saki yana fa’din “Na cancanci fiye da haka sweety na.” Ya shige toilet ‘din ruwa mai zafi ya tara a bathtub ‘din kafin ya zuba duk abinda yake ganin ya dace sannan ya fito cikin fara’a yana jin kamar ya ha’diyeta ya zauna a gefen gadon yana fa’din “Oya taso first love yau a daren nan zan baki wani labari da zai ba ki mamaki.” Rintse idonta ta yi tana fatan ta tashi da kanta ba tare da taimakonsa ba, sai dai ta kasa ta gagara hakan sakamakon wani irin zafi da take ji kamar ana ba’da mata barkono. Kawai sai ta kifa kanta a filo. Turaki ya saki murmushi kafin ya sunkuya a hankali ya rungumota ta baya yana kallonta da sauri ta runtse idonta bata son kallon k’wayar idanunsa sai a yanzu take jin matsananciyar kunyarsa tare da dana sanin amince masa da ta yi. Ya sake birkito yana hura mata iska a fuska wacce ta caku’de da k’amshin mouthwash da na strawberry chewingum. “Please tashi mana ko sai na d’auke ki mhmn sarauniyata.” “Ni ba sarauniyarka bace kada ka sake kira na da wani sunan banda ainahin sunana Ayra Karuwa daka ra’da min.” Ya ji kalamin nata kamar dirar mikiya a k’ahon zuciyarsa don haushi bai san sanda ya saka yatsa ya ‘dalli bakinta ba. “Kada na sake jin kin kira min kanki da haka, kin ji Mace ta gari.” Turo bakinta ta yi ba tare da ta sani ba hawaye yana gangara daga idanunta ta ce “Ya zan daina kiran kaina da sunan da ka ra’da min. Matsa na tashi bana son ganinka kusa da ni.” Ta fa’da fuskarta na bayyana ainahin abinda take nufi da gaske yake daga k’asan zuciyarta. Da k’yar ta mik’e cikin dauriya da k’ok’arin son nuna masa bata buk’atar taimakonsa. Sai dai ina bata san sanda jiri ya ‘debeta zata fa’di ba da sauri ya tarota ta dawo jikinsa kafin ya sunkuceta zuwa cikin toilet. Suna zuwa ya zare towel ‘din ya yar da sauri Ayra ta runtse idanunta tana k’ok’arin rufe k’irjinta da ya dama da kallo. Turaki ya saki dariya a kunne ya ce “Bari rufe min kaya na Malama, wai banda abin ki wani dare ne jemage bai gani ba?” Daga haka ya saka ta a bathtub ‘din….. tuni idanuna suka daina ganinsu na yi saurin barin toilet ‘din don na san dai wannan wankan ba za’a gama sa k’alau ba. ______ Can na gano yau dai Ayra ta zama baby, don towel na ga Turaki ya saka yana goge mata jiki, ita kuma tana kwance a kan gadon idanunta a rufe ruf barci na fusgarta. Ya ‘dauko mai ya shiga shafa wa duk lungu da sak’o na jikinta cikin wani salo na soyayya mai cike da kulawa da nuna mata ita ‘din ta yiwa mata zarra a zuciyarta. Ita ‘din ma wani jin kanta take gefe guda tana murna da samun wannan kulawar ya kuma ‘debe mata kaso mafi yawa daga hasashen Maza duka halinsu ‘d’aya sai dai bata fasa tunanin ramuwar gayyar da ya tsaya mata a zuciyarta ba, da gaske sai ta rama ramuwar da ake kira ta Gayya. Wajejen k’arfe biyu na rana a can k’asar ta samu da k’yar ta mik’e daga nauyayyan barcin da take yi. Kan nata da ya dameta da ciwo tuni ya daina sai ‘dan tsamin jiki da take ji game da ciwon gab’ob’i na rashin sabo. Ta lumshe ido tana tuna moment ‘din daren jiya da komai ka ya wakana kamar a mafarki wai itace ta sallamawa na miji kanta? Da mamakin irin kalaman da ta dinga ji a bakin Turaki, ko kunya bai ji ba ya dinga fallasa mata sirrin zuciyarta. Ta saki murmushi ta na ware idonta a kan gadon. Sai ta tarar ita ka’dai ce a kwance da alamar yana toilet don ta ji k’arar zubar a toilet.” Ta kai dubanta saman bed sheet ‘din, sai ta ga an canja ko da yaushe ya canja shi? Wani irin barci ta yi haka. Tana daga kwancen rabin jikinta rufe da abin rufa na gadon. Ta shafa jikinta ta ji zip d’in rigar yaloluwr rigar a bud’e daga gaba. Murmushi ta saki don ta tuna sanda Turaki ya zuge zip ‘din yana fa’din “nafi son na ji d’umin matata sosai a jikina, don haka duk sanda za mu kwanta ki kiyaye bana son wani tarkace mhmn?” Ya fa’da yana jan karan hancinta ha’de da goga goshinsa a nata. Ayra da sauri ta mik’e jin alamar zai fito ta fara gyara mab’allan rigar tana fa’din “Ka samu wacce zaka dinga kwanciya da ita hakan ba Ayra ba.” Daidai lokacin ya fito daga shi sai towel ‘daure a k’ugunsa, tana ganinsa ta ‘dauke kanta da sauri don ta lura shi ko kunyarta ba ya ji. Murmushi ya saki yana cigaba da combing sumar kansa da ya gama drying a toilet. Ya k’araso wajenta yana ha’da jikinsa da nata ta baya “Kunyata kike ji Sweet? Why?” Gaba ‘daya ta ji amsa kuwwar maganarsa cikin jikinta tun daga yatsan k’afarta har zuwa kwanyar kanta. Ta zame jikinta da nufin shiga toilet ta ji ya yi sama da ita bai direta ko ina ba sai toilet yana fa’din “Ai ke yau y’ar gata ce, komai ma yi miki zan yi y’ar albarka Mace ta gari.” ____________ Sai dai ya gyara mata kai sannan ya mik’e yana fa’din “Bari na yi sauri na samo mana breakfast a k’asan hotel ‘din, bana son ki yi tafiyar da za ki wahala naga har yanzu ba ki warke ba.” Ya fita yana waigenta ha’de da blowing mata kiss cikin wata irin murya ya ce “Take care Hayateey.” Ayra ta bi bayansa tana murmushi kafin ta janyo briefcase d’insa da sauri ta fara bincike cikin ikon Allah kuwa sai ga Dollar card ‘dinta da take nema. Wani murmushi ta yi ta ‘dauke shi ta ajiyeshi a inda ba zai gan shi ba. Sannan ta mayar masa da sauran tarkacensa ta koma ta zauna a hankali tana tunanin ta yarda zata lalubi ticket ‘din komawa gida ta siya ba tare da ya sani ba. San da ya shigo tana zaune da waya a hannunta tana dannawa wayar Amma take ta kira ta WhatsApp amma bata online. Sauran yayyenta kuwa duk sun yi waya da safen Amman ce kawai har a lokacin bata sameta ba. Ya turo k’ofar ya shigo yana ajiye tray ‘din da ya amsa wajen mai aikin hotel ‘din da ya biyo shi. Yasa k’afa ya tura k’ofar don ba ya son ya gane masa mata, da yake jin ta kamar Diamond. Murmushi ya sakar mata yana isa kusa da ita ya saka hannu ya mik’ar da ita tsaye yana bin Riga da wandon da ta saka ya lafe mata a jiki. “Oya mu ci abinci akwai labarin da zan baki.” Ta zauna a kan filo da kyar sai ya janyota ta dawo saman cinyarsa a kunne ya ce “In dai ina nan, nan ne mazauninki na fi son in jiki a jikina.” Ya fa’da yana sake rungumarta sosai ya kai hancinsa k’ark’ashin wuynta yana shinshinar dadda’dan k’amshin turaren royal oud da take. Da gaske ji yake kamar ya Ha’diyeta ya huta sabuwar sha’awarta tana sake katantanwa da shi ya kasa sarrafa kansa sai dai tausayinta ya saka shi mayar da maitarsa ya bu’de musu abinci suka fara ci. Rabi cin abinci Rabi kuma yana aika mata wani irin hot romances. Sai da suka gama suka wanke hannuwansu sannan ya jata jikinsa suka koma gado suka kwanta. Yana laluban wayarsa ya bu’de mata wani hotonta tun wanda ya ‘dauketa a airport time ‘din ba zata zarce 18 yrs ba. Da sauri ta ware ido tana kallon hoton “Kin tuna sa? Za ki iya tuna lokacin?” Lumshe idonta ta yi tana ganin abin kamar wani majigi a idanunta kafin tunanin rashin auren da yake tsakaninsu a yanzu ya shigeta da sauri ta turesa tana kallonsa idon dishi dishi ta ce “Ban tuna komai ba, sannan ina son tuna maka abinda ka manta ba aure a tsakaninmu, ko ka manta da bakinka ka ce Duk ranar da ka kisanceni na k’addara kamar na amshi takardar sakin aurena ne? Don haka ka daina kusantata don haram ne ka aikata hakan.” Wani irin gumi ne ya karyo masa nadama ta shige shi idanunsa suka ka’da suka yi jajur, ya dinga jin zuciyar sa na masa wani irin suya kafin ya runtse idonsa ya ce……… Takaicin Uba…… 51. 👩‍❤️‍👨💘💘💘💘 “Haba mana, keep quite my friend wannan wane irin zance ki ke?” Ya fa’da yana k’ok’arin kamo hannunta, da sauri ta janye jikinta fuska a ha’de ta mik’e sosai cike da masifa ta ce “Kada ka sake k’ok’arin tab’ani am serious na haramta a gareka, dama don ka tabbata ni ba karuwar ba ce na amince ka kusanceni na san kuma by now ka gane ni ‘din ba namijin da ya tab’a kusantata don haka ka saka a zuciyarka hakan ba zai sake faruwa ba har abada.” Ta lumshe ido hawaye yana kwararo mata, sosai take jin zafin waccen maganar da ya dinga fa’da mata, haushinsa sosai take ji kamar ta dage ta yi ta dukansa ko ta samu sauk’in b’acin ran da take ciki. Turaki bai san sanda ya mik’e zaune ba hankalinsa a tashe ya sake k’ok’arin rik’ota ta fisge da sauri kamar mai aljanu. “Kada kuskura ka sake tab’a ni.” Zuwa lokacin abin nata ya fara bawa Turaki dariya ganin yarda take turjewa kamar irin da gaske ta fi k’arfinsa, ya saki murmushi yana mik’ewa ya isa daf da ita ba tayi auneba ta ji kawai ya ha’data da jikinsa ya kuma rik’eta gam kamar wani zai k’wace masa ita, duk da k’ok’arin k’wacewa da take Amma ta kasa cikin kunnenta ya ra’da mata “Ki tsaya ki daina wahalar da jikin ki ba sauk’i kika samu ba, idan kuma kin ji garas ne tell me na sauke miki abinda yake kaina don na tabbatar miki igiyar aurena na nan gam gam ba ta rawa ko ka’dan.” Shammatarsa ta yi ta fisge jikinta tana jifansa da harara “Shi kuma sakin nawa da ka yi ina ya je, let me tell you idan duk duniya za su ha’du ba zan koma gidanka ba abinda nake nema ne ya samu, tun tashi na saka raina ba zan iya rayuwa da wani namiji a inuwa guda ba balle makwanci guda.” Turaki yana murmushi ya ce “Ba duniyar da zata taru daga ni sai ke kuma aure na yana nan daram a kan ki, ko sakin na yi idan na ce na janye ina zaton kina nan matsayin matata ko? To na janye then what? Me kuma ya rage?” Ayra ji ta yi kamar ta kurma ihu ta zuba mata idanunta da suke cike da k’walla murya a ‘dashe ta ce “Wallahi baka isa ba don ni bana son ka kuma ba zan zauna da kai ba, da’din abin ina da evidence da zan nuna.” Shima zuciyarsace ta hassala jin cewa wai bata son sa, ashe da sauran aiki ja a gabansa har yau bai cuta mata son sa ba. Ya cije leb’ensa kafin ya koma ya kwanta yana lumshe ido takaici fal ransa. Ayra ta zabga tsaki ta ja blanket ‘din gadon mai laushin tsiya ta shimfi’da a k’asa ta saka bargo ta kwanta. Turaki bai kulata ba duk da ransa bai so haka ba, so yake ya jita a jikinsa Amma kalaminta na bata son sa shi ya tsaya masa a rai, ya da’de cije da leb’ensa na k’asa kafin ya saki ‘dan k’aramin tsaki a zuciyarsa ya ce “Dole ma ki so ni yarinya, don zama da ke yanzu na fara.” Ya mirgina yana lek’en fuskarta da ta sake wani fresh kuma barcinta take peacefully. Wayarsa ya zaro ya gayawa masu kula da gidansa na Moscow a kan yana nan shigowa da dare su gyara gidan. Sannnan ya mayar da kansa ya runtse yana fatan barci ya ‘dauke sa, sai dai ya kasa moment ‘dinsu na daren jiya ya tsaya masa a rai ji yake kamar ya janyota ta k’arfi ya k’ara kusantarta sai dai ya daure kawai ya hak’ura a ransa yana raya da kan ki za ki kawo k’afarki Ayra. Sai 6:45 ya farka daga barcin da ya ‘dauke shi, Ayra kuwa har a lokacin barcinta take peacefully da alama ta samu sauk’in jikinta sai da ya lek’a fuskarta yana kallonta kafin ya saki ajiyar zuciya yana mik’ewa. Bai san wani irin so yake ma yarinyar ba da ya tsaya masa a rai har haka, ko barci yake tunaninta ne ‘danfare a ransa. Ya shige toilet yana k’ok’arin sakarwa kansa ruwa don shi da kansa ya san wanka ya kama shi tilas. A gaggauce ya fito da tunanin kada lokacin sallah ya wuceshi. Sai da ya idar da sallah sannan ya shige toilet ya tara ruwa mai zafi a Cikin bathtub ya saka duk abinda ake buk’ata sannan ya fito. Idanunsa suka fa’da kan Ayra da take kwance ta k’udundune abin rufar ma ya zame can gefe daban gaba d’aya santala-santalan cinyoyinta a waje. Turaki ya k’arasa wajen yana k’ok’arin danne abinda yake ransa kafin ya ‘daga ta cak. Da sauri Ayra ta bu’de ido “Me ye haka ajiye ni bana so.” “Ni kuma ina so.” Ya fa’da yana kaiwa bakinta sumbata “Ki tsaya ki min shiru ko na sakeki a k’asan wajen nan, don kin ga ma ina tattalinki.” Ta bu’de idonta sosai a kansa sai dai da azama ta runtse don ba zata iya jurewa narkakken kallon da yake mata ba. “Ni nace ka yi tattalina?” Ta fa’da tana cuno bakinta. Murmushi Turaki ya yi yana kissing lips ‘dinta da suke da taushin tsiya kamar ana jik’asu kullum “Mara kunya, sai rakin tsiya bayan ba ki da juriya ko ka’dan. Idan ba ki wasa ba mata uku zan aura na ha’da ku da su.” Ta ‘dauke kanta kafin ta ce “Ka auri goma ma ina ruwana ba sai ka ganni ba.” Dai dai lokacin ya saka ta a bathtub ‘din yana k’ok’arin cire rigar da take jikinta ta yi saurin rik’e hannun. “Bari ba na so.” “Ni kuma ina so, bari ma ki ga sunnar annabi za mu bi tare za mu yi wankan.” Ayra ta runtse idonta ganin da gaske Turaki yake ta hau watsa masa ruwa tana fa’din bata so. Da sauri na juya don idanuna ba za su jure ganin wannan sirrrin nasu ba, na san dai yau Ayra ta gane Turakin mu first class ne a wannan fannin don luf ta yi a jikinsa tana amsar wasu irin sak’onni masu shiga rai a zuciyarta mamakin maza take da basu da kunya ko ka’dan, idanunsa rufewa yake idan an zo wajen nan. Duk abinda yake kallonsa kawai take don ta sakawa zuciyatta dole ya rabu da ita, tana kallo ya tattara duk wasu kaya da suka cire kafin ya k’araso wajenta hannunsa ‘dauke da black abayanta ya mik’a mata. “Oya maza saka mu tafi.” Tsayawa ta yi tana kallonsa kafin ta furzar da numfashi ka’dan ta ce “Ina?” “Our House mana, na saka an gyara tun ‘dazu, mu je ki ga gidanki.” Ta sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya kafin ta mik’e tana tsayen ya zura mata rigar. Ya bata hug sosai yana fa’din “Ki saki fuskar mana Hayateey.” Ta ‘dauke kanta ha’de da fa’din “Sunana Ayra.” Murmushi ya saki yana tallafar hab’arta ya fata lalubar k’wayar idonta so yake su ha’da ido sai dai ta k’i ba shi dama sai runtse idon take. Ya shafi lab’banta da suke fusgar hankalinsa ya ce “Ana so ana kaiwa kasuwa, mhmn?” Ya jata suka fice daga ‘dakin. Sai da ta jira shi a reception ya yi signing sannan ya k’araso wajenta suka fita wajen mai Cab ‘din da yake jiransu. Tun daga waje yanayin tsarin gidan da ya kasance duk glass ya yiwa Ayra kallon gidan kawai take tana jin yana sake burgeta tun kafin ma ta shiga ciki. Ga wata iska da take ka’dawa a hankali gefe guda k’aramin garden mai ‘dauke da nauikan tsuntsaye iri-iri, kowa dai ya san tsari da yanayin zubin gidajen turawa. Sanyin da ake ne yasa Ayra ta fara takurewa saboda har snow ne yake zuba ka’dan-kadan a nahiyar garin. Shigarsu parlourn ya sa ta sake jin wani uban sanyi musamman a.c ‘din parlourn a kunne take. Da sauri ta takure a kan kujera tana jin yarda sanyin yake neman kassara gab’obin jikinta. Kula da hakan yasa Turaki ya yi saurin kashe air condition ‘din ya kunna heater yana kallonta ya ce Kumama” ta ‘dauke kanta tana kallon yanayin falon da komai na cikinsa ya zama golden brown. Sai da ya kai kayan ‘d’aki sannan ya dawo ya tsaya a gefenta yana mik’a mata hannu. “Taso mu je in nuna miki bedroom.” Ta mik’e bata musa masa ba don ta gaji sosai akwai kuma tazara tsakanin hotel ‘din da anguwar da suka zo. Har tsakiyar babban bedroom ‘dinsa ya kaita da yake fitar da wani irin ni’imtaccen k’amshi ‘dakin ga shi ya ‘d’au ’dumi sai ya dace da yanayin sanyin da ake kwararawa a garin. Ayra ta tsaya tana kallon cikin ‘dakin kafin idonta ya kai kan hoton ta da yake jikin bango sai dai kamar zanawa a ka yi. Da sauri ta k’arasa jikin bangon tana k’arewa hoton kallo kafin ta juyo da niyyar yi masa magana, sai kawai jin ta tayi a jikin mutum ya rungumeta tsam a jikinsa a kunne ya ra’da mata “Kin san hoton nan?” Tana k’ok’arin zame jikinta ta girgiza masa kai “Ban san sa ba, a ina ka samu?” Ya juya bayan pic ‘din yana sakin murmushi kafin ya jata bakin gadon suka zauna jikinsa a jikinta ya ce “Na same shi 8yrs back, the same date da yake jikin hoton. A airport na ‘dauke ki a pic ‘din. Kin tuna wata rana da muka yi clashing aairport ina kallonki har kika yi tsaki kika yi saurin jan nik’ab ‘din ki.” Ayra ta yi shiru tana nazari duk da an da’de Amma sai yanzu abin yake dawo mata kamar majigi, tabbas sanda ta gan sa sai take imagining ta tab’a ganin sa Amma ta rasa a ina ne. “So ki daina cewa na rabu da ke, daman kece buri na you are in my dream all these years. Baki tab’a bari na na huta ba, kullum addu’a na Allah ya ha’da ni da ke, don haka dole na Ji ba da’di sanda na ha’du da ke aka kuma zo min da maganar wai kin tab’a yawo…” ya ciji leb’ensa “shine abinda yasa ki kaga hankalina ya tashi na ji ba da’di har nake miki abinda na miki, but am sorry please.” Zuciyar Ayra ta ‘dan rusuna sai dai ba wai don ta hak’ura ba, ta tab’a baki tana fa’din “Wallahi ba zan hak’ura ba, sai na je na fa’da a gida, kuma ni abinda yasa na yarda da kai don ka tabbatar bana hul’da da maza, amma ni ban tab’a son ka ba.” Turaki ya runtse idonsa cikin jin zafin abinda ta ce “Wai shine mace yau take cewa ba ta so, ransa ya ji yana b’aci kafin ya mik’e a hankali ya zameta daga jikinsa. “Na ji ba kya so na, nagode,but do me a favour, kada ki kai maganar nan gida ki yi zaman ki ni kuma ba zan sake kulaki da sunan mu’amalar aure ba har sai kin amince da ni da kan ki, amma don Allah kada ki kai maganar nan gida.” Ya durk’ushe a gabanta yana jan tattausan hannunta yana matsawa a hankali. Ayra ta yi shiru tana runtse idonta “Kada ki kai please! Ni kuma zan yi k’ok’arin koya miki so na.” “Never for ever!” Ta fa’da a zafafe tana zame hannunta “Na amince ba zan kai maganar gida ba, amma a kan shara’di guda kada ka sake kusanta ta kamar yarda ka ce har sai na amince da kaina, sannan ba zan dinga maka girki ba, ba abinda zai ha’da mu ko magana.” Turaki ya tsaya yana kallonta cikin tashin hankali ya ce “all these? Ya yi min tsauri ki na dai ba ni abinci kuma zan dinga mi ki magana, ai musulunci ya hana gaba.” “And Musulunci ya hana ka tozarta ‘dan uwanka musulmi ba. Hakan shi nake so idan fa ka amince idan ba haka ba kuma I should park my things and leave.” Murmushi ya ‘dan saki ya ce “Na ji na yarda amma idan kin yarda zan yi aure ko?” Ta bu’de idanunta tana kallonsa ta ce “Na yarda ka yi uku ma.” Turaki ya ciji leb’ensa yana tunanin da gaske yarinyar bata son sa, dole ya nemi mafita, kafin soyayyarta ta kassara shi. “Nextweek zan yi aure.” Ayra ta ‘dauke kanta tana fa’din Allah ya kai mu.” Turaki ya ciji leb’ensa yana kallonta ya ce “Ga can ‘dakin ki, ki ja kayanki ki fita, kuma duk abinda ya biyo baya ba ruwana don’t blame me okey?” Ta ‘dauke kai tana fitar da k’aramin tsaki ta ce “Oho, ni ina ruwana.” Turaki ya ja trolleynta yana fa’din “Na ji zo ki tafi.” Ta bi shi a baya kuwa suka fice daga ‘dakin sai da ya nuna mata har kitchen da komai na gidan sannan ya saki hannunta yana fa’din “Na amince ki shiga ko ina, ban da can part ‘din anan zan saka amaryata.” Ta tab’e baki tana shiga ‘dakinta… Takaicin Uba… 52. Turaki ya bita da kallo yana mamakin kafiya da taurin kai irin nata? Ya saki ajiyar zuciya don idearrsa ta k’are bai san me zai mata ba kuma ta hak’ura, don ba ya jin zai iya cika alk’awarin da ya ‘daukar mata. Ya da’de a wajen yana folding hannayensa yana sakewa. Kafin ya ja k’afafunsa a hankali ya koma kan three seater ya kwanta idanunsa a runtse yana tunanin haka dama soyayyar take don shi ko Hibba bai wa son da yakewa Ayra ba, Hibba kyawawan halayenta ya ja shi gareta ita kuwa Ayra gaba ‘dayanta yake son ta ba shi kuma da wani k’wakkwaran dalili. Ita kuwa Ayra tana shiga bedroom kifewa ta yi a kan gado zuciyarta ta yi rauni sosai da tunanin da Turaki ba a budurwa ya sameta ba wani irin wulak’anci ne zai biyo baya. Ta saki ajiyar zuciya tunani ya shigeta sosai ta fara tuno wancan halin da ta shiga Allah ne ya ceceta duk da a lokacin bata ga zahirin fuskar mahaifin ta ba, sai bayan da k’addara ta Riga fata a hankali komai ya dinga dawo mata kamar majigi kamar ma yanzu aka yi abin. ________________ Sanda Hadi ya ce Kabiru ya ‘dauketa Ayra runtse ido kawai ta yi, don bata san me zai aikata mata ba, tunda k’wak’walwarta har a lokacin ba ta san akwai wata mu’amala da take tsakanin namiji da mace ba. Sai da suka shiga ‘dakin idanunta ya raina fata ganin yarda a gaggauce ya cire mata kayan jikinta shima ta ga ya zare wandon sa ya kwantar da ita rigingine yana shirin aikata abinda ya yi niyya ganinsa a hakan yasa ta runtse idanunta ta kuma k’walla k’ara hakan yasa Kabiru saurin kashe fitilarsa da waya ya toshe mata baki. Daidai lokacin suka ga Ya. Majeeda ta rufta cikin ‘dakin da sauri hankalinta a tashe ta janye Kabirun a zafafe tana fa’din “Kada ka cutar da ita, ta yi k’ank’anta ni na amince ka min abinda zaka mata.” Ba wani shakka Kabiru da ya tuna a maganar bokansa dama Ayra ko Majeeda ya ce sai kawai ya jawo Majeedan ya haik’e mata. Ihun Majeeda shi ya gigita Ayra bata san lokacin da ta suma ba cikin wani irin gigitaccen k’ara Majeeda take jin azabar da take fisgarta bata san lokacin da ta tuge bak’ar fuskar da mahaifin ta ya sa a fuskarsa a kuma lokacin ne cikin hukuncin Allah wutar nepa ta dawo hakan yasa Majeeda ta yi ido hu’du da mahaifinta da razana da tashin hankali suka saka ya mik’e da sauri yana kallonta kafin ya yi aune Majeeda wani k’arfi yazo mata ta janyo katako ta buga masa tana ihu tuni ya zube a wajen ya suma banda buguwar da ya yi tashin hankali ma ya isa ya saka shi ya k’ara suma. Majeeda ta fita falon da gudu duk da azabar da take ji a zuciyarta bai hanata isa wajen Amma ta rungumeta ba cikin kuka ta ce “Amma Abba ne, Abbanmu ne a ciki.” Jin haka Hadi da sauri ya fice a guje jin an gane Kabiru ne a ciki ba ya son shima su gane shi. Amma jikinta na rawa ta kama Majeeda ta na fa’din “Majeedah mai kunnuwa na suke jiye min? Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna.” Kafin ta yi aune Majeeda ta zube a jikinta ta sume cikin wata irin mak’yark’yata Talatu ta ja k’afarta ta isa ‘dakin ido biyu kuwa ta yi da Kabiru kwance a wajen a sume. Amma ta runtse ido jikinta na rawa ta zube a wajen tana kukan tashin hankali kafin itama numfashinta ya fara sama ta zube a wajen a sume. Zainab hankalinta a tashe ta fice daga gidan ta hau buga gidan Kamilu tana kuka tana kiran Kamilu. Da sauri Kamilu da Jummai suka farka a ‘dimauce suka yi bakin gate jin muryar Zainab ya ‘daga hankalinsu. Kamilu ya bu’de gate ‘din hankali tashe yake duban Zainab “Ke nutsu Zainab yi min bayani Waye ya mutu?” Zainab da take aikin mayar da numfashi don k’irjinta ya yi nauyi ji take itama kamar ta suman ta ja hannun Kamilu kawai a fisge suka shiga cikin gidan. Ta kai su har cikin ‘dakin tana nuna musu Kabiru “Shi ya yiwa Ya. Majeeda da Ayra fyad’e.” Saura k’iris Kamilu ya zube a wajen banda Jummai ta yi saurin rik’e shi tana fa’din “Nutsu Maigida idan ka zube ni Kuma ya zan yi? Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna. Yanzu menene abin yi?” Kamilu ya ce “Y’an sanda zan kira Jummai, wannan lamarin Ai ya fi k’arfin a yi shiru.” Jummai ta girgiza kai tana jan hannunsa suka zauna a kan kujera “Kada Ka fara Kamilu, kiran y’an sanda ba shine mafita ba, illa tonawa kan mu asiri.” “To me kike so a yi Jummai? Kin ga fa abinda Kabiru ya yi kamar wani mahaukaci, y’arsa fa ya cikinsa Jummai sai ka ce ya sha k’waya.” Ya fa’da idanunsa yana zubar da hawaye. Jummai ta saki ajiyar zuciya itama kukan take sai dai bata son a kai maganar wajen y’an sanda gudun fallasuwar sirrinsu, hakan yasa ta dafa Kamilu murya a raunane ta ce “Ka yi hak’uri mu yi aiki da hankali Kamilu, yanzu dai zuba musu ruwa mu samu su farfa’do.” Kamilu ya kasa mik’ewa don ji yake idan ya mik’e zai iya fa’duwa saboda jirin da yake ‘dibansa. Jummai ce ta ‘debo ruwan ta shek’a musu. Sai ga Ayra ta farka a firgice tana ihu “Amma ya cire min kaya na shiga uku Amma ya hau kai na me zai yi min?” Surutai kawai take kafin Jummai ta kamata ta rungume cikin raunin zuciya tana dubata ta ga ita Kabiru bai tab’a ta ba. Sai Majeeda da ya Riga ya shigeta, tausayin Majeeda ya kama Jummai ta kamata da k’yar suka shiga toilet sannan ta tara ruwa mai zafi ta saka ta a ciki Majeeda na ihu tana fa’din “Ya Allah ka ‘d’au raina rayuwata bata da amfani.” Jummai ma kuka take. Can falo kuwa Amma ko motsi ta kasa yi shi kuwa Kabiru ya mik’e da k’yar yana jin wani irin nadama da ciwon kai mai tsananin gaske fata yake mutuwarsa ta riskesa a wannan lokacin da wannan abin kunyar da ya aikata. Ya runtse idanunsa bayan Kamilu ya zuba masa uban mari a duka kumatunsa guda biyu, sannan ya mik’e yana jan hannunsa daidai lokacin da aka yi Assalatu yana fa’din “Mik’e tsaye Kabiru, tafiya za mu yi da kai wajen y’an sanda yanzun nan su maka hukuncin da ya dace da kai, mahaukaci dabba, jahili ‘dan akuya. Wallahi ina tur da zamowarka ‘dan uwana Kabiru na tsaneka tsana mafi muni. In sha Allah tun a duniya sai Allah ya saka musu. Daidai lokacin da yake jan sa Jummai ta shigo hannunta rik’e da Majeedah da ta ke ta k’yarma idanunta na sake cin karo da mahaifinta ta sake zunduma ihu tana fa’din “Allah ya isa Baba Allah ya bi min hakkkina.” Kabiru ya runtse idanunsa yana jin duniyar na masa wani irin walagigi. Jummai ta kalli Kamilu tana fa’din “Wai ina za ku je ne? Na ce maka fa ka bar maganar zuwa wajen y’an sanda ka bari yanzu su gama shiryawa mu ‘dunguma a tafi Shagogo duk abinda magabata suka ce da shi za’a yi aiki, tunda dai cuta ya Riga ya cucesu ya gama da su.” Kamilu ba don ransa ya so ba ya saka Kabirun a wani ‘daki ya kullesa don kada ma ya gudu. Sannan ya fita samo musu shatar mota don su tafi Shagogo. Haka suka rankaya suka tafi Shagogo rayukansu a cunkushe da b’acin rai, musamman Amma da sam bata gane abinda ake yi kawai bin su take da idanu, ta ma kasa magana tsabar takaici da zuciyarta take ciki. Ayra kuwa ba a awa guda bata razana ta firgice ba, Majeeda zazzafan zazzab’i ya rufeta kafin isar su Shagogo. ________ Gaba ‘d’aya labari ya kara’de garin Shagogo, kowa ya samu labarin irin badak’alar da Kabiru ya yi ba ta yarda za’a iya b’oye irin wannan magana mai girma. Sai dai Maigari ya rok’i mutanen garin a kan su dubi girman Allah kada su k’etara da maganar wani gari duk da ya san hakan ba lallai ya yiyu ba. Mutanen gari suka taru suka dinga tsinewa Kabiru suna kuma rok’ar Talatu afuwa don a yanzu halin Kabiru ya fito muraran kowa ya yi tur da Allah wadarai da shi, aka kuma ce ba shi ba garin. Sai a sannan Talatu ta yi magana tana kallon Mai gari “Ka gaya masa ba shi ba y’ay’ana daga yau na zare sunan sa daga matsayin mahaifinsu, bana buk’atar ya sake kusanto inda nake ko ya kira kansa Uban y’ay’ana, Allah ya isa tsakanina da shi kuma In sha Allahu sai Allah ya saka min.” Daga haka ta ja y’ay’anta ta mik’e don ko garin Shagogon bata son gani, ranta a b’ace ya ke sosai. Haka nan suka bar garin Shagogon bayan ta masa kallon da ta kira na k’arshe don bata jin ko ita ko ahalinta wani zai k’ara ziyartar garin. Kabiru ma a ranar mutanen garin suka masa tofin Allah tsine suka raka shi har da masu jifansa shima ya bar garin zuciyarsa cike da dana sani da tarin nadama. Daga lokacin kuma komai ya caku’de masa, duk abinda ya tab’a madadin riba in dai da sunan kasuwanci ne sai dai ya tafka gagarumar asara. Har ya dawo matalauci na bugawa a jarida ‘daya matar ta zube masa yara uku maza ta bar gidan sai Uwar gidansa da take zaune da shi da da’di ba da’di don ita ta zama mijin shi kuma yake mata biyayya kamar mata. Yaransa maza kuwa gaba ‘d’aya ba na gari a cikinsu, ba kuma sa tausaya masa, daga mai shaye-shaye sai tantirin b’arawo da ‘dan daba. Talatu kuwa kafin ta samu ta nutsu an ‘d’au lokaci Ayra kanta sai da ta dinga kaita ganin likita sabida yarda kanta yake nema ya tab’u kullum a cikin razana da firgita take, ta kuma sakawa kanta tsanar Maza gaba ‘daya. Ta zama mara sukuni mara magana daga ita har Majeeda da sauran y’ay’an sai da Amman ta saka aka dinga musu addu’oin da saukar alkur’ani sannan suka samu zuciyarsu ta daidaita. Suka koma makaranta Ka’in da na’in. Don su Majeedah har sun fara jami’a ita da Zainab. Companynsu na k’ara hab’aka da arziki. A lokacin ne suka samu mazajen aure masu son su da gaske kuma duka masu hali ne, duk da an sha hak’ilo kafin dangin mijin su yarda a cewarsu y’a’yan mata ne, Kamilu ne ya kai su har garin Shagogo suka ga asalin su sannan suka amince. Ita kuwa Majeeda mijinta bai da uwa bai da Uba sun rasu sai y’an uwa don haka ba wata matsala da aka samu a danginsa aka yi komai cikin kwanciyar hankali, duk da Amma bata yarda ba sai da ta kirasa ta gaya masa k’addarar da ta fa’dawa Majeeda. Bai ce komai ba don ya san k’addara Kuma shi soyayyar Majeeda a jininsa take ba don budurci yake son ta ba, ya ce ya ji ya gani yana sonta a haka zai aureta. Amma ranar sai da ta raba dare tana sallah don farin ciki. Haka aka aurar da su cikin farin ciki kuma suke zaune k’alau a gidajensu. Bayan shekara guda kuma Aysha ma ta samu miji shima mai hali da wadata itama aka aura mata Justice Abdul Kareem Har’do. Ya rage daga Jidda sai Ayra. Ayra har mamaki suke bata idan ta ga sun yi aure, don ita bata ji a duniya akwai mijin da takewa kallon salama ta tsani maza sosai. Tana Ss 3, JIDDA na level 1 aka yi auren Jidda da wani ‘dan majalisa da ya mutu a kanta yana da ku’din gaske. Amma har tsoron aurensa take ji, amma Jidda ta kafe sai shi, haka Amma ta hak’ura ta aurar da ita bayan ta tabbatar da nagartuwar halayensa. Ya rage daga ita sai autarta. Bayan shekara guda ne suka gina gidan su da yake railway gidan da ya lamushe mak’udan ku’dade don ma Mazajensu sun taimka musu. Ayra kuma ta fara running business ‘din tun tana level one a Sky line don ta k’i yarda ta fita waje karatu, sannan ta toshe duk wata kafa da zai zama tana tarayya da ‘da namiji. Wannan shine tarihin su Ayra Gaya da duk wasu k’addarori da suka same su a rayuwa. Tana kaiwa nan ta saki ajiyar zuciya tana gyara kwanciyarta. A hankali ta ce “Tabbas sai na rama Turaki.” 𝕹𝖆𝖟𝖊𝖋𝖆𝖍 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊👌 Takaicin Uba. 53. ______ Turaki kasa runtsawa ya yi a daren, ya yi dakacen bai kusanci Ayra ba balle ya jangalo wa kansa, yanzu ji yake duk duniyar ta masa zafi. Da k’yar ya mik’e ya nufi parlour don gwara ya je ko barci ya samu ya yi a jikinta ya samu sukuni. Sai dai yana isa parlourn ya mur’da k’ofar bedroom ‘din da ya zama mallakinta sai ya ji sa a kulle gam. Tsayawa ya yi a bakin k’ofar cikin tashin hankali kafin ya ja k’afarsa da k’yar ya koma parlour ya yi zaune a kan kujera yana murza goshinsa da ya ya dameshi da ciwo. Tunani yake wani abu zai ma Ayra ya samu ta huce daga fushin da take yi da shi, ta kuma yafe masa ta amshesa a matsayin Mijinta kamar yarda zuciyarsa ta cika da tsananin son sa shima ya samu ya cilla nasa son ko da kaso ‘d’aya ne a cikin ‘dari cikin tata zuciyar. Wai ma me yasa tun a fari daga jin jita-jita ya amincewa kansa Ayran tana bin maza tun bai tabbatar da hakan ba. Ya runtse idonsa yana jan numfashi da k’yar kafin ya sake tashi ya ja jikinsa ya koma bedroom. Alwala ya yi ya tada sallah ya da’de a sujjada yana rok’on Allah ya sassauta zuciyar Ayra ta so shi koda a ce ka’dan ne. Da asuba da ta mik’e ta ji jiknta wasai ba wannan ciwon da yake mata. Sai da ta yi sallah sannan ta shiga wanka. Ta fita parlourn gidan don tsaftacewa don sam bata son k’azanta ko ka’dan. Kan kace me? Wani irin sihirtaccen k’amshin turarukan wutan data kunna a burner ya kara’de lungu da sak’on gidan. K’amshin da ya kai har hancin Turaki da yake barcin wahala. Tana gamawa ta sake shiga kitchen ta musu omelette da Chips sai ruwan tea mai kayan k’amshi da ta dafa. Ta tsaftace kitchen ‘din ta fito. Haka kawai sai ta samu kanta da tsananin annashuwa a zuciyarta. Wanka ta sake yi ta saka wani white skin tight d’inta da body hug red ta kama kanta ta k’ulle da red band. Lipsticks ta shafa nude colour ta bi kuma lungu da sak’o na jikinta ta ba’de da turaruka sannan ta koma saman gado ta kwanta tana danna wayarta har a lokacin layin Amma take nema amma still not reachable yake saka mata. Ta ‘dan ja tsaki ka’dan tana lalubar numberr wayar Yaya Deejah. Deejah da take zaune gefen Amman da aka samu ta farka da kyar daga dogon suman da ta yi ta mayar da kallonta kan wayar tana sakin murmushi don ta tabbata Ayra ce. Da fara’a ta ‘d’aga wayar “Ayrateey Ayran Amma, ya gida ya amarci hope dai an kashe boss ‘don yanzu an daina k’in maza.” Ayra ta ja tsaki a hankali kafin ta furta “Allah ya shiryeki Ya Deejah, k’in maza a jinina yake ba zan daina kin su ba. Ina Amma na yi kiranta severally bana samunta.” “Amma na lafiya ta ‘dan yi fever ne amma da sauk’i.” Cikin fargaba Ayra ta ce “Allah sarki Ammata mai ya sameta?” “Missing autarta, so ya Moscow ya honeymoon?” Tsaki Ayra ta saka ta ce “Yana garinku. Don Allah bani Amma ta.” Deejah ta ce “Idan muka gan ki da baby za mu ji labarin in da kika samo shi, ga Amman taki.” Ta fa’da tana kara wayar a kunnen Amma. Cikin k’arfin hali da son danne ciwon da take ji ta ce “Ayraty ya gida? Ya bak’unta kin tafi kin bar mu da kewa, don Allah Ayra ki kula ki bi Mijinki sau da k’afa kada ki yi abinda zai zo yana jin haushin ki, kin ji? Ba duka maza ne suka taru suka zama ‘d’aya ba irin Babanku.” Ayra ta share k’wallar idonta tana fa’din “Zan bi sa Amma ko don ke zan masa biyayya.” Amma ta ji da’di sosai ta ce “Allah miki albarka, ki kira Ummeey ku gaisa.” Ayra ta ce “To Amma, Zan kirata.” Sun da’de suna waya kafin Ayran ta sake tana sakin ajiyar zuciya. Ita bata ma da numberr Ummeey ‘din kuma ya kamata kam kamar yarda Amma ta ce ta kirata su gaisa don haka ta mik’e ba tare da ta ‘d’au mayafi ba, ta fice a haka zuwa parlour don ta ga idan ya fito ta amshi numberr Ummeey ‘din. Ta kusan 30 minutes a parlourn Turaki bai fito ba, har ta gaji ta yi joining vidmate tana kallon wani film. Azababben k’amshin turarensa na companyn Rasasi ya ba’de parlourn. Tsaf yake cikin shigar English wears da suka sake fito da kyawu da cikar kamalarsa. Fuskarsa ta ‘dan tasa ka’dan ya isa kusa da inda take zaune ya zauna idanunsa cikin nata da yake lumshe su kamar mai jin barci. Kallon ne ya saka ta a wani yanayi ta yi saurin ‘dauke kanta murya a cunkushe ta ce Ina kwana? Madadin amsa mata, sai kawai ya bu’de mata hannunsa yana sakin tattausan murmushi “Zo nan mana na ji d’uminki Hayateey.” Ta ‘dauke kanta tana cuno bakinta kafin ta ce “ka manta alk’awarin da kai min kenan?” Ya ‘dan shafi gefen fuskarsa kafin ya ce “A yi hak’uri a min afuwa banda na gaisuwar safe, just hug and kisses pls.” Ayra ta ‘dauke kanta ya taso a hankali ya zo kusa da ita ya saka hannu ya mik’ar da ita “Ki min wannan favor ‘din daga shi ba zan k’ara ba.” Ayra ta runtse ido kawai tana jin yarda ya jata jikinsa ya rungume yana sakin ajiyar zuciya a hankali. Kafin ya kai mata sumbata a k’asan wuyanta kiss ‘din da yasa jikinta ya fara shaking. Turaki ya saka hannunsa a gefen wuyanta yana fa’din “Just a minutes Ayra pls.” Ya sake hugging ‘dinta sosai kafin ya saketa yana sakin murmushi. Shiru Ayra ta yi ta ja jikinta ta zauna a kujera. Turaki yana kallonta k’asa-k’asa a zuciyarsa ya ce “a hankali za ki kawo kan ki Ayra, wannan abin ba a iya ‘dauke masa kai.” A fili kuwa shafa gefen fuskarta ya yi a kunne ya ra’da mata “That’s my Angel. Oya zo mu je mu yi break fast, ko na ‘dauke ki.” Da sauri ta girgiza kai “No I will go by myself.” Ta fa’da cikin kakkarwa murya. Turaki ya saki smilling kawai ya wuce Dinning. Ayra kuwa ta da’de zaune kafin ta samu nutsuwa ta bi shi Dinning ‘din. Idanunsa a kanta har ta zauna yana ha’da tea yana kallon ta Jefi-jefi kafin ya ce “Kun yi waya da gida?” Ta ‘d’aga masa kai “Kin zama kurma ne?” Ta ‘dago kai tana kallonsa. Ya shigar da idonsa cikin nata yana sake narkar da duk wani saran k’arfin da take da shi. “Ki min magana.” Da sauri ta kawar da kanta murya ciki-ciki ta ce “Mun yi, ka bani numberr Ummeey ina son kiranta.” Hannunta da ta ke k’ok’arin zuba sugar ya rik’e yana dubansa “Me yasa ba ki yi lallen biki ba?” Ta janye hannun tana jin shock ‘din da ya biyo bayan hannun “Bana ra’ayi.” “Ko kuma saboda za ki auri mak’iyinki ba.” Ta ‘dago da sauri tana kallonsa. Ya ‘dan saki murmushi “Hakane mana, Right?” Samun kanta ta yi da saurin mik’ewa ta bar wajen don ba zata jurewa wannan sabuwar ‘dabi’ar ba. Turaki ya bita da kallo yana sakin murmushi a hankali kafin ya fisgota da k’arfi ta fa’da jikinsa ya saka hannu ‘d’aya ya yi hugging ‘dinta ‘Dayan kuma yana d’iban omelette ya kai bakinta idanunta a runtse ta tauna abinda ya saka mata kafin ta yi saurin mik’ewa ta ce “Naga alama ba zaka iya cika alk’awarin mu kawai zan tafi kada ka saka na fara abinda ban shirya ba.” Ya mik’e da sauri ya sha gabanta “Zan iya mana, waye ya ce miki ba zan iya ba? Wannan Ai ba komai bane ba dai zan yi having sex da ke ba sai dai idan kin amince da kan ki. Wannan shine alk’awarin da na miki.” Ta janye jikinta da yake k’ok’arin rik’ewa. “Ni dai na gaya maka bana so” murmushi ya yi ya cikata yana fa’din “Shikkenan to zan yi aure dama Shaheedah ta matsa min, anan neighbor suke, so zan nemi aurenta kawai don ba zan iya sake rik’e kaina ina ganin ki kusa da ni ba, da na aikata haramci kuwa gwara na yi auren.” Ya fa’da yana shafa gashin idanunta da suke kulle “Na amince ka yi auren in dai ba zaka kusanceni ba.” Turaki ya saki ajiyar zuciya yana mik’ewa ha’de da kai wa lips ‘dinga peck “Okey thanks, zan samu Shaheedah mu yi magana, bari na je office sai na dawo.” Sai da ya juya Ayra ta bu’de idanunta tana kallon bayansa, yana juyowa suka ha’da ido ta yi saurin ‘dauke kanta. Shi kuma ya fita kafin ya shiga mota ya tafi office sai da ya kira numberr Shaheedan ya ce mata za su yi magana idan ya dawo. Sannan ya shiga mota ya tafi office. _________\ Jikin Amma ne ya yi tsanani sosai, har abin yafi k’arfin likitan da yake kula da ita. Don haka ya dubi Ummeey bayan sun shiga office ya ce “Hajiya na son kamu wa da ciwon zuciya, don jininta ya hau sosai tun kafin abin ya yi nisa akwai wani special Doctor da ya dawo daga germany last week yana aiki a national hospital why not na samar muku appointment ku kaita can.” Ummeey da sauri ta ce “Bakomai Doctor ka samar mana idan yaso ko gobe sai mu yi booking flight mu wuce, dama da yaranta mazauna Abujan duk muna nan tare da su, to zaman can ‘din ba zai mana wuya ba.” Doctor ya girgiza kai kafin ya ‘daga waya ya kira Doctorn da ya kasance amininsa. Bai sha wani wahalar samar musu appointment ba za su je su gan shi gobe.. Flight ‘din 7:00 suka bi zuwa Abuja da Amma da yaranta gaba ‘d’aya sai Ummeey da Tasleem. Private room suka amsa don su samu sakewa sosai. K’arfe hu’du da Rabi likitan ya nufi ‘dakin Amman don ya dubata. Cikin takunsa na nutsuwa yake tafiya kana ganinsa ka ga kammalallen mata shin Dattijo mai ji da ilimi ya tura k’ofar bayan ya yi nocking ya shiga. Amma da idonta biyu a lokacin ta sauke ganinta akan mutumin da yake tsaye wanda ake kira Doctor J. Cikin muryar ru’dani Amma ta ce “Jabiru?” Shima idanunsa bu’de ya ce “Anty Talatu…..” 𝕹𝖆𝖟𝖊𝖊𝖋𝖆𝖍 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍️ Takaicin Uba…. 54. Tsananin mamaki yasa Talatu mik’ewa da ‘dan hanzari duk da nauyin da k’irjinta ya mata. Da sauri Hameeda ta dafata tana fa’din “Be careful Amma.” Shi Kansa Jabirun an hanzarce ya ‘daga k’afarsa ya Isa Inda Talatun take cikin tsananin farin ciki. Su Majeedah kuwa binsa suke da ido saboda ita da Zainab ba zasu mance kamanninsa ba, don da wayansu sanda ya bar gida. Yana nan yarda yake a farin bafulataninsa sai da ya ‘dan manyanta ka’dan hakan ma sai ka lura da kyau zaka ga y’ar furfura tsilla-tsilla a gemunsa. Ya yi kyau jikinsa ya murje kana ganinsa ka san yana cikin kwanciyar hankali da rufin asirin rayuwa. Amma har a lokacin kallon mamaki take masa da jinjina girman Ubangiji Sarkin da ba ya barci kullum ta yi Sallah sai ta rok’i ubangiji ya bayyana mata Jabiru yasa yana raye cikin k’oshin lafiya. Murmushi ya k’i ‘daukewa daga fuskokinsu duka, a hankali Jabiru yake bin manyan yaran Amma da kallo ya ganesu tsaf musamman Majeeda, Zainab da Aysha. Deejah ce ma sai da ya waro ido yana kallon Majeedah ya ce “Auta ce ko?” Majeedah ta girgiza kai ta ce “Ba Auta ba ce Abba Jabiru, Auta na Moscow sunanta Ayra.” Ya ‘dan lumshe ido yana ‘dan durk’usawa ya gaida Amma. Amma ta shafa kansa tana fa’din “Alhamdulillah da wannan rana yau ga babban yaro na Jabiru a gabana Allah nagode maka.” Ya juya yana gaida Ummeey kafin ya sauke idonsa a kan Tasleem da take gaishe sa cikin siririyar muryarta haka kawai sai ya ji gabansa ya fa’di ya ‘dan maze yana dafa Hannun Amma. “Bari na duba ki Anty, kafin labari ya biyo baya, don na k’agu na ji bayan rabuwa da irin yarda rayuwa ta sauya muku na ganku cikin jin da’di da walwala fiye da yarda na dinga rok’a muku ubangiji. Wallahi kullum kuna raina ko lastweek sai da na yi niyyar zuwa Shagogo to ina tuna abinda aka min sai na ji sam bana sha’awar komawa garin.” Amma ta lumshe ido haka kawai sai ta samun kanta da jin sanyi a zuciyarta, wani dunk’ulallen abu da ya da’de da taruwa a k’irjinta ta ji ya fara raguwa a hankali, tun lokacin da wancan sharri da aka musu da Jabiru abin ya tsaya mata sai yau ya kau da ta ga Jabirunta fes cikin k’oshin lafiya da kwanciyar hankali. Nauyin da zuciyarta ta yi ya ragu sosai da kaso Sittin cikin ‘dari bata da wata sauran damuwa yanzu a rayuwarta Ayranta ta yi aure kamar yarda take buk’ata kuma alamu sun nuna tana zaune lafiya a gidan Mijinta, ga Jabirunta yau Allah ya ha’data da shi. Me ye sauran burinta ganin dangin mahaifiyarta, ta ji zuciyarta ta bata amsa. A hankali ta lumshe ido tana fa’din “Shima zai cika In sha Allah.” Ta mayar da kallonta kan Jabiru da ta k’agu ta ji bayan rabuwarsa da gida ya yi da rayuwarsa har yanzu da yake durk’ushe a gabanta. “Jabiru Amma dai ka yi aure ko?” Jabiru ya saki murmushi yana murza gemunsa da ya masa kyau a fuskarsa “Ban yi ba Anty.” Ta waro ido tana fa’din “Me yasa Jabiru?” Ya girgiza kai “A duk sanda na je neman aure sai an buk’aci ganin danginsa da sanin asalina abinda ni kuma har abada na shafesu a tarihin rayuwata su kuma iyayen yarinya idan suka ji ba ni dangi sai su hana ni auren y’arsu. Wannan dalilin ya hana ni aure.” Amma ta saki ajiyar zuciya a ranta tana cewa Ina ma ba duka yaranta ta aurar ba tabbas da ta bawa Jabiru Mata. “Allah ya kawo ta gari tunda yanzu ga ka ga danginka. Ya labarin bayan rabuwa?” “Sai alheri Anty, komai ma ya faru Amma dai bayan bari na gida ban wani wahala ba na samu scholarship ‘din da aka da’de ana gayyata ta ina kaucewa, bari na gida sai na nufi Kano gidan su wani amini na a can muka nemi scholarship da shi muka dace aka tura mu k’asar Egypt zamu koyi karatun likitanci. Shikkenan tunda na saka k’afa na bar Nigeria ban sake waiwayarta ba sai yanzu da k’addarar ha’duwa ta da ku ya sa na zo Nigeria a kan Health Minister yana son ganin mu, likitocin Nigeria da suke aiki a wata k’asa. Last month na zo aka kuma rik’e mu a k’asar mu a kan cewa Nigeria ta fi buk’atarmu fiye da k’asashen da mukewa bauta. Ina nan zaune a Abuja a Maitama.” Amma ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Barinka gida Alheri ya zame maka Jabiru, Allah ya sake yiwa rayuwarka albarka.” Ya amsa da ameen yana cewa “Amma saura ku ya labarin taku rayuwar?” Amma ta saki murmushi ta ce “Ta mu rayuwar sab’anin taka ce Jabiru mun fuskanci k’alubale iri iri kafin Allah ya warware mana komai. Karo na farko da Amma ta fara bada labarinsu ba tare da kuka ko hawaye ba ba kuma nauyin zuciya ko ka’dan duk wannan tarin bak’in cikin da take ji ya kau sai wanda ba za’a rasa ba. Kafin ta gama Jabiru ya jik’e handkerchief d’insa da hawaye gaba ‘d’aya ji yake da ace zai ga Kabiru ba abinda zai hana sa sumar da shi idan ma bai zama ajalinsa ba. Ummeey ce ta yi k’ok’arin ba shi hak’uri kawai don kowa a ‘dakin kukan da Jabeer yake ya kashe musu jiki. “Ka yi hak’uri Jabeer, komai ya wuce shi kuma Kabiru Allah ya shirye shi ko da yake tun a yanzu ya fara ganin hukuncin Ubangiji a kansa. Ku gode wa Allah da ni’imomin da ya yi muku, ba mamaki da Kabirun bai cutar da ku ba da baku samu wa’dannan tarin alhairan da suka bibiyeku a rayuwa ba, da tuni kuna nan a can k’auyen ba tare da kun kai matsayin da kuke kai yanzu ba. Allah ya kiyaye mu daga halayya irinta Kabiru, ba zan ce ku yafe masa ba, amma zai kyautu ku ba shi hak’kinsa na Mahaifi kada hakan ya zama Hujjar da gobe alk’iyama Allah zai yi fushi da ku. Kada ku zama d’aya ku da shi, shi ya tauye muku hak’kinku kuma kun tauye masa shikkenan ranar alk’iyama duk za ku tashi a tutar babu! Ku kula da hakkinsa da yake kanku ko da ba ku yi mu’amala mai kyau da shi ba.” Amma ta saki ajiyar zuciya tana jin sauk’in zuciyarta sosai kuma ta yarda abinda Hameeda ta fa’da yana kan hanya, tabbas Kabiru yana da ha’k’ki akan y’ay’ansa ba zata hanasu kula da Babansu ba idan sun yi niyya sai dai da bakinta ba zata saka su su yi ‘din ba, kamar yarda take ganin su ma ba za su saki jiki su kyautata masan ba. “Hakan ni’ima ce babba idan kuka yi masa, ya zama kun tura masa aniyarsa kenan, ku ‘din da yake gudu kune dai kuka zame masa majingina a rayuwa, amma fa ku yi tunani shawara ce na baku, da kuma tunawa da girman Ayar nan da ta bayyana girman iyaye.” Hameeda ta sake fa’di jikinta a sanyaye. Duka ‘dakin tsit aka yi musamman Majeedah da take jin da ku’dinta dai ba zata iya taimakawa mahaifinta ba. Ta rufe idonta kawai ruf tana jin tsohon mikinta yana taso mata, don ma tata zuciyara akwai juriya sab’anin Ayra kuma ta samu Miji mai share mata hawaye wanda baya son ganin b’acin ranta ko ka’dan. Hameeda ta saki ajiyar zuciya don tabbas ta san daga ganin yanayinsu shawararta da nasiharta bata karb’u ba, ba kuma ta jin zata karb’u nan kusa sai dai za tai ta nusar da su har su gane inda ta dosa. Sai bayan isha duk suka tafi gidajensu suka bar Ummeey Hameedah da Aysha da za su kwana da Amma. Jabiru kuwa har past 11:00 Yana tare da su kafin ya tafi gida zuciyarsa cike da tunanin irin rashin mutuncin da zai wa Kabiru da ma Hadi d’an kanzaginsa gaba ‘daya ya saka a ransa da zarar an sallami Amma k’afarsa k’afarsu zai je har Kano ba don komai ba sai don ya ga Kabiru ya sauke masa kwandon rashin mutuncin da ya tanadar masa. ________________ Cikin dare Ayra tana barci ta dinga jin bugun k’ofa a hankali kamar za’a b’alla. A tsorace ta mik’e tana kunna switch ‘din fitilar da yake gefen gadonta. Kafin ta mayar da gashinta da ya bar baje ta saka band ta k’ulle sa ta mik’e tana ‘daura igiyar rigar barcinta. “Waye?” Ta furta a hankali bayan ta isa bakin k’ofar “Please Ayra ki bud’e ba ni da lafiya, wallahi kamar zan mutu.” Ayra ta ‘dan waro idonta sai dai jin muryarsa ya bayyana mata tsananin ciwon nasa don haka bata kawo komai ba ta bu’de k’ofar. Tana bu’dewa ya k’ank’ameta jikinsa na wani irin shivering kamar mai jin sanyi. Ayra gaba ‘d’aya hankalinta ya tashi jin jikinsa kamar ana hura masa wuta. Ta rintse idonta tana k’ok’arin janye jikinta. “Kada ki janye zan fa’di.” Ya fa’da cikin muryar wahala. Ayra cikin d’an tashin hankali ta ce “Kan bed zan mayar da kai.” Sannan ya ‘dan raba jikinsa da nata ta samu ta ja hannunsa kan gadon ta. Kwanciya ya yi ruf da ciki hannayensa a damk’e da k’asan cikinsa ya ce “Ayra mutuwa zan yi.” Ayra hankali ta ce “Me ya sameka?” Sai ji ta yi kawai ya yi yana kishi sama-sama. A razane Ayra ta ce “Ina wayarka na kira Doctor.” “Tana bedroom.” Ta juya da sauri zata nufi waje don ‘dauko wayar ta ji kawai ya fisgota “Ke ce maganin Ayra, don girman Allah ki yi hak’uri ki yafe min laifina Wallahi idan baki amince da ni anything can happen cikin daren nan.” Ayra ta zaro ido kafin ta ce “Oho! Shine sanadin ciwon naka kenan, ai kuwa ba zaku samu sauk’i ba wancan ‘din ma da kaga na yarda na gaya maka dalili don haka gwara ma ka je ka nemi maganin ka ba Ayra ba.” Ya sake kamata yana ‘dora k’irjinsa a bayanta ya rungumota ta baya “Ki yarda Ayra ba maganin da zai iya yi min aiki a daren nan, na sha Wallahi ba su yi min ba sun ga ji da yi min aiki.” Ayra ta cije leb’enta tana jin wani abu mai kama da tausayinsa yana son lullub’eta kafin ta runtse idonta tana jin yarda hannunsa yake shawagi a jikinta yana tab’a duk inda yake so. Kawai sai ta dinga jiyo amsa kuwwar maganarsa yana ce mata duk ranar da na kusanceki ki k’addara kamar kin amshi takardar sakin ki ne a hannunki me Zan Yi da karuwa! Da k’arfin gaske Ayra ta tureshi daga jikinta duk da ganin ya kai wani yanayi da ba zai amsa kira ba, so yake kawai ya kai ga harawa ya ga ta angajeshi sam ba shi da k’arfin rik’eta yana ji yana gani ta fice parlour duk da kiranta da yake yana fa’din “Please sweety ki cike ladanki” amma ta fice ta na rufo k’ofar da k’arfi. Bedroom d’insa ta wuce ta shige tana mayar da numfashi bayan ta murza key ‘din k’ofar. Ta saki ajiyar zuciya tana k’arewa ‘dakin nasa kallo da abinda yake fitarwa sai zallar k’amshin turarukan da yake amfani da su, sun kama d’akin ra’dam. Ayra ta gyara y’ar k’aramar rigar barcinta don ta yarda top ‘din a can. Ta koma kan gadonsa ta kwanta tana jan abin rufarsa k’amshin turaren ne yasa itama ta dinga jin wani feeling da bata tab’a ji ba a rayuwarta. Ta dinga juyi cikin tashin hankali kafin ta dam’ki pillow tana jin kamar ta tashi ta kai kanta wajensa. Tsawon daren Ayra ta kasa runtsawa kamar wacce ta sha wani abu saboda yarda Turaki ya bi ya tayar da duk wata sha’a wa da take jikinta. Tsam ta mik’e ta nufi k’ofa ba abinda zuciyarta take gaya mata irin “Tafi Ayra ki samu ladan kan ki da na mijinki kada ki halaka!” Ta saka hannu ta murza key ‘din kafin ta runtse ido tana fa’din “Anya na je kuwa? Me Zan ce masa idan na je.” Da alama Turaki zai ci wasan nan,,, tunda ga Ayra tafe zata kai kanta 😂 Takaicin Uba.. 55. Mayar da k’ofar ta yi da sauri, tana k’ara murza key ‘dinta jin kamar takun da Sawayen Turaki. Ta jingina da k’ofar tana mayar da idonta ta runtse ha’de da sakin ajiyar zuciya. Tana jinsa ya mur’da handle ‘din key ‘din alamar zai bu’de sai ya ji ta a kulle. Ya ‘dan yi knocking nan ma bata bu’de ba tana juyowa ya saki ajiyar zuciya kafin ya sake jan k’afafunsa ya bar wajen. Ayra ta runtse idanunta tana jin tausayinsa na tsirga mata sai dai da sauri ta wancakalar da tausayin da tunanin shi ne ya hanashi tausaya mata a lokacin da yake tunanin ta rasa budurcinta. Kuka ne ya kufce mata tana jin k’unar abin a cikin ranta, kamar yanzu komai ya faru. Ta shige toilet tana sakarwa kanta shower da sauri kafin ta ‘dauro alwala ta fito. Sallah kawai ta tayar. Kafin ta zaro wayarta ta fara booking ‘din flight da zai ta shi jibi wanda zai isar da ita Nigeria. Da k’yar ta tashi k’arfe goma na k’asar can saboda rashin barci da bata samu ta yi ba. Ta gyara gidan kamar yarda ta saba da sauri ta kuma yi musu break fast sannan ta shiga wanka. Mai kawai ta mutstsika ta kawo y’ar rigarta wacce da ka’dan ta wuce mata gwiwa. Rigar ba ‘dan ka’dan ba ta yi mata kyau sai dai duk ta bayyana duk wata sura ta jikinta. Cikin zuciyarta ta ce “Allah ya isa Deejah. Don ita ta cuceta da ya fitar mata irin wa’dannan kayan. Ta kama gashin kanta da sauri kafin ta murza sihirtacciyar Humra a jikinta. Ta fice falo tana ‘dan ji music a hankali cikin wayarta. Barci ne yake son sake fisgarta ita kuma bata son yi don haka ta ‘debi oat ka’dan ta zauna tana sha. Kusan 12:00 ya fito black jeans ne a jikinsa da farar Riga. Yau ko gashinsa bai taje ba sabida ba shi da nutsuwa sam a tare da shi. Jikinsa a sanyaye kamar mara lafiya ya isa cikin jeren kujerun falon ya zauna ba tare da ya sake yiwa Ayra second look ba. Itama ba bata kulashi ba tana ta shan oat ‘dinta. Da peppe soup da ya gama cika wajen da k’amshi. Tana gani ya saka hannu a aljihu ya zaro wayarsa ya shiga daddannawa kafin ya saka a kunne bata ji me ya ce ba ta dai ji ya ambaci Shaheeda cikin k’asa da murya sosai. Haka kawai sai ta ji ranta ya b’aci ta fara kallonsa ta gefen ido shi ma a sace yake kallonta suka ha’da ido sai ta ga ya ‘dan kawar da kai yana tsaki. Ba a fi 10 minutes ta fara jin knocking k’asa-k’asa. Ba shi da courage na tashi don haka cikin k’asa da murya ya ce “Please Open the door.” Ayra ta zuba masa ido kafin ta mik’e don kawai sai jikinta ya bata Shaheedan tasa ya kira. Don haka ta mik’e daga ita sai b’ingilar rigar da take jikinta ta nufi bu’de k’ofar. Turaki ya runtse idonsa yana jin wani irin bugun zuciya ya lura so yarinyar nan take ta kashe sa. Ya sake shak’ar Humrar yana jin kamar ya janyota ta k’arfin gaske sai dai ya yi alk’awarin ba zai sake kusantarta ba har sai ya dasa mata soyayyarsa mai girma a zuciyarta. Ta saka hannu ta bu’de k’ofar Budurwa ta gani tsaye cikin shigar black jeans da red shirt. Sai mayafi da ta yi rolling jikinta ka’dan. Shaheedah ganin Ayra ya saka gabanta fa’duwa ta fara matsa yatsunta tana kallon Ayran k’asa k’asa tana jin gwiwarta na sanyi. Ayran ma naga gaban fa’duwa ya yi kafin ta finciki leb’enta tana lumshe idanunta da ta ji suna neman bayyana damuwarsu k’arara. “Menene?” Ta fa’da tana ware idonta a kan Shaheedan. “Matsa” ta jiyo Turakin da yake gefenta bata san da isowarsa wajen ba ya fa’da. Cikin mamaki ta juyo tana kallonsa ba tare da ta matsa ‘din ba. Ya cafki hannunta ya matsar gefe yana kallon Shaheedah ya ce “Shigo” ta ‘dan saki murmushi tana bi ta gefen Ayra ta shige cikin takun da yake nuna isa da iko. Ta isa falon ta zauna kan kujera. Ayra tsoro ne yasa ta ware idonta kan Turaki da yake damk’e da hannunta. Ya watsa mata wani kallo kafin ya saki hannun ya juya yana zama daf da kujerar da Shaheedan take. Ayra ta tsaya cak tana kallonsu suna magana k’asa-k’asa sai kuma suka saki dariya suna Kallon Ayran. “Shaheeda ta maza ki samar min something special a kitchen you know i like your special cooking.” Shaheedan ta mik’e cike da yauk’i tana fa’din “Your wish is my command Habibeey.” Ta ‘dan kalli Ayran da take tsaye ta yi folding hannayenta kawai tana kallonsu. Kafin ta tab’e baki ta shige kitchen wani bak’in ciki ya dugunzuma zuciyar Ayran a fisge ta kalli Turaki tana jin wani irin hucin b’acin rai ta ce “You mean wannan ka kawo gidanka ta maye gurbina?” Sai kuma ta saki murmushi ta ce “Ashe kai ne ‘dan iskan shi yasa baka son ka auri y’ar iska… so let me tell you nima ba zan zauna da ‘dan iska mai kule-kulen ko wasu tarkacen mata ba, yarda ka tabbatar ni nutsatsstiya ce haka zan auri kind husband wanda ya fika.” Sam bata san sanda ya iso gabanta ba sai ganinsa ta yi a gabanta ya saka hab’a ya ‘dago fuskarta ta runtse ido tana jiran ta ji saukar hannayensa a fuskarta. Ya k’arewa fuskar kallo kafin ya saki murmushin takaicin “Idan ban kulata ba ya kike so na yi? Kina son na kai kaina wajen turawa ne? Tunda ke kin kasa ba ni abinda nake so, ki rik’e kayanki ki jik’a a ruwa ki sha, ga mata nan da yawa a gari…” Ayra ta runtse ido tana fa’din “Matan ma suna suka tara.” Ta fincike jikinta tana kallonsa “Kada ka sake tab’a k’azamin jikinka da ya Riga ya gama gogayya da y’an matan bariki da nawa.” “Ni kike gayawa haka?” Bata san sanda ta ce “Na fa’da ‘din ko k’arya na yi.” Ya ciji leb’ensa kafin ya ce “Ba kiyi k’arya ba.” Ya juya ya barta nan a tsaye yana komawa kitchen ‘din. Ayra ta runtse idanunta da sauri ta shiga bedroom ta mayar da k’ofa ta rufe har da murza key sannan ta ji wani irin kuka ya zo mata. A hakan ta shiga tattara kaf kayanta ta ha’de su waje ‘d’aya a akwati. Tana jin tafasar zuciyarta na k’aruwa ji take dama ta bu’de idonta ta ganta a gaban Amma right now. Da ta sani flight ‘din ranar ta nema ba na next day ba. Ta kwanta lamo a kan gado haka kawai sai idanunta yake gano mata Turaki rungume da Shaheeda suna wasu al’amura masu girma. Takaici da haushi wanda kai tsaye za’a iya kira kishi suka rufe ta duk da ita bata yarda kishin take ba. Shaheedah na gama yi masa abincin suka fice tare ya sauke ta a school kafin ya nufi office ‘dinsu. Ayra kuwa ta da’de kwance a d’akin tana jin wani irin tafasar zuciya a ranta, kafin ta sake duba Internet ta ga ta samu flight da zai tashi 6:30 na safe. Ta saki ajiyar zuciya gwara ta tafi ta je ta gaya ma Uwars ba aure a tsakaninsu yanzu ta sahalawa kanta auren idan yaso idan ya shirya neman aurenta ya faro daga farko ba mamaki ya san mahimmancinta lokacin. Ta sake lumshe idonta tana tunanin yarda zata ja masa aji, tunda ba zata rabu da shi ya yi mata a yanzu ita da kanta ta amince tana son sa, amma ya kamata ta nuna masa Ayra Gaya ba karabitin matan da ya saba kulawa a titi ba ce, Ayra Gaya mai quality ce ajin farko. Kuma sai ta kafa masa shara’din daga ita ba zai sake kula kowace mace ba da sunan yi mata kishiya. Sai dare ya dawo gidan, bai kuma nemeta ba don haushinta yake ji sosai. Ya isa kan dinning yana bu’de warmers d’in har a lokacin abincin safe ne a ciki alamar bata sake wani girkin ba, idan ma ta yi to iya cikinta ta yi wa. Ya ‘dan tab’e baki yana sakin ajiyar zuciya, ji yake kamar ya je ya kai kanta inda take Amma yana tsoron abinda zai biyo baya, don baya son yana kusanta kansa da ita shi ka’dai ya san azabar da take ba shi. Ya shige bedroom ‘dinsa kawai ya kulle. Tana idar da sallah ta ja k’aramar trolley ‘dinta don ba duka kayan ta ‘diba ba ta fice da sauri bayan cab d’in da ta yi order ya gaya mata ya iso. Tana fita ta ja masa gidan ta kulle don ta tabbatar zuwa lokacin ya koma barci. Ba su da’de da isa airport ‘din ba jirginsu ya tashi. Ayra ta saki ajiyar zuciya tana jin wata salama a zuciyarta da tunanin zata ‘d’aga hankalin Turaki. Kuma direct wajen Ummeey zata fara zuwa kafin ta isa wajen Amma. Sai 9:00 ya fito daga ‘dakin sai zabga k’amshi yake a gaggauce ya isa dinning sai dai yana bu’de warmers ‘din ya ga still abincin jiya ne a ciki. Da sauri ya juya yana k’arewa falon kallo ba abinda ta gyara a cikinsa bai san sanda ya isa bakin k’ofar ‘dakinta ba yana fatan Allah yasa lfiya. Yana murza handle ‘din ya ji shi a bu’de mamaki ya kama shi yarda ya ga yanayin ‘dakin komai a hargitse ga k’ofar toilet a bu’de alamar bata ciki. Hanjin cikinsa ne ya juya cikin tashin hankali ya isa kan gadon inda ya hango takarda a ajiye. Hannunsa har rawa yake ya ‘d’au takardar “Na tafi na sanar da iyaye ka sake ni, tunda da bakinka ka fa’da, bana buk’atar aurenka ka k’addara har abada Ayra Gaya ta fita daga rayuwarka.” Gaba ‘d’aya gab’obinsa suka fara rawa ya yi saurin ficewa daga ‘dakin ya nufi ‘dakinsa. Brief case ‘dinsa ya ‘dauko ya shiga bincikawa Dollar card ‘dinta yake nema nan yaga bai gansa ba, hantar cikinsa ta ka’da ya tabbata da gaske Ayra ta bar garin ta tafi Nigeria, ya kuma san ya ka’da har ganyensa idan Ummeey ta ji labari yarda take da saurin fushi ya san kafin ta yafe masa za a sha fama. Ya runtse idanunsa yana dukan hannunsa da ‘daya hannun ya ce “Why Ayra Gaya?” Ya zauna kawai ya dafe kansa kafin ya yiwa wani mutuminsa a airport waya ya tambayesa jirgin da zai tafi Nigeria ta tashi a ranar? Nan aka sanar masa ya tashe tun 7:30 Turaki ya runtse idanunsa ya sake tambayar za’a samu flight mai tashi yau zuwa Nigeria mutumin ya sanar masa babu ko na gobe ba za’a samu ba sai jibi. Turaki ya yi cilli da wayar yana fa’din “Na mutu kawai! Innalillahi wa Inna ilaihirrajiuna!” 𝕹𝖆𝖟𝖊𝖊𝖋𝖆𝖍 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍🏽 Takaicin Uba… 56. Jirginsu na dira Nigeria Ayra ta saki watt ajiyar zuciya tana lumshe ido, haka kawai sai ta dinga jin kamar abinda zata aikata d’in bai dace ba. Ta dinga ganin tamkar bata kyautatawa Turaki ba, kafin wata zuciyar ta sake k’arfafarta da cewa abinda zata aikata ‘din shine ya dace, gwara ta nuna masa matsayinta ya san ya aikata kuskure. Bata wuce gidansu ba direct gidan Ummeey ta tafi don ta sanar mata, kuma ko bakomai ita da kanta tana shakkar fa’dan da Amma zata mata. Knocking biyu kawai aka yi Tayseer ta bu’de k’ofar. Mamaki ya kamata ganin Ayra ‘dauke da trolly. Ayra ta sakar mata murmushi ta ce “Ya dai?” Tayseer da gabanta yake fa’duwa ta saki ajiyar zuciya ta ce “Na yi mamaki ne? Yaushe kuka dawo?” Ayra murmushi ta yi kafin ta ce “Mu shiga ciki, kafin wa’dannan dogayen tambayoyin naki?” Tayseer ta ja trolly ‘din nata jikinta a sanyaye sai kuma zuciyarta ta bata ba mamaki ko Amma tazo dubawa. Sai da ta zauna sannan Tasleem ta juya kitchen don samar mata abin sha kafin ta samar mata abinci don daga ganinta daga airport take. Ta sha juice ‘din ka’dan kafin ta ce “Ummeey fa?” Tayseer tana sake dubanta ta ce “Ai suna can Abuja wajen Amman.” “Amma kuma? Me ya kaita Abuja?” Ayra ta yi saurin jefowa Tayseer ‘din tambaya. Jikin Tayseer ya yi sanyi tabbacin Ayra bata san Amman bata da lafiya ba hakan na nufin tahowarta akwai matsala kenan, tunda ba Amman ta zo dubawa ba. “Ta ‘dan yi ciwo ne, amma jikinta da sauk’i sosai.” Ayra ta waro ido tana kallonta kafin k’walla ta taru a k’asan idonta, bata san sanda ta rarumi waya ba ta fara booking flight mai zuwa Abuja a yammacin ranar. Ganin hankalinta ya tashi sosai Tayseer ta ce “Ya. Ayra kin kwantar da hankalinki fa, ta samu sauk’i sosai.” Hawaye kawai ya goge tana kallon Tayseer ta ce “In sha Allah thank you.” “Mu je ki samu ki huta naga kin ‘Debo gajiya, Ina Ya.Turakin na ganki ke ka’dai?” Ayra ta saki murmushi tana fa’din “Yana can, nima akwai abinda ya dawo da ni.” Tayseer jikinta a sanyaye ta tura k’ofar ‘dakin tana fa’din “Allah yasa lafiya.” Ayra ta saki murmushi ganin yarda damuwar Tayseer ‘din ta bayyana k’arara akan fuskarta.” Tana kallo ta fice tana ja mata k’ofar. Ayra ta zauna gefen gado cike da damuwa ta fara k’ok’arin kiran Wayar Deejah. Cikin mamaki Deejah Take kallon wayar ganin numberr Ayran ce ta Nigeria. A tsorace ta ‘d’aga kiran. Ayra ta saki ajiyar zuciya tana fa’din “Ya. Deejah, yanzu shine Amma bata da lafiya baku gaya min ba? Sai da na zo yanzu Tayseer take gaya min.” Wata irin zufa ce ta ketowa Deejahn cikin rawar baki ta ce “Kika zo ina Ayra? Kuma ke da wa Kuka zo?” Ayra ta ja tsaki don ita ba tambayar da take son ta ji ba kenan, “Ko ma ni da wa na zo ina ruwanki? Ki gaya min wani hospital kuke kawai, don mugunta kawai Uwata bata da lafiya sai a k’i sanar da ni har sai da na zo k’asar.” Deejah ta katse wayar kawai don ta lura Ayran tsiwa take ji. Ayran ma bata sake kiranta ba sai kawai ta kira Zainab, Zainab ‘din ce ya sanar da ita suna National Hospital “Amma Ayra me ya kawo ki Nigeria?” Nan ma Ayra katse wayar ta yi kawai. Duk ‘dakin aka zubo musu ido,ana son jin k’arin bayani musamman Amma da Ummeey da wani tashin hankali ya ruskesu. “Wace Ayran ce a Nigeria.” Ummeey ta jefo mata tambayar don ta kasa jurewa. Deejah tana sakin ajiyar zuciya ta ce “Ayra Gaya.” Ummeey ta dinga jin kamar saukar aradu a kanta. Murya na rawa ta ce “Yanzu tana ina?” Deejah ta ce “Wai tana gidanki tare da Tayseer amma yau zata zo nan ‘din.” Amma kasa magana ta yi, Ummeey kuma ta yi zugum kafin ta kasa jurewa ta mik’e ta fita waje ta dinga kiran wayar Turaki sai dai ana ta sanar da ita number not reachable. Ta ‘dan dafe kanta kafin ta sauya akalar kiran zuwa wajen Tayseer. Tayseer da take kitchen tana ha’dawa Ayran abinci. Ta ‘dau wayar da sauri ganin Ummeey ce. Ko amsa gaisuwarta Ummeeyn bata yi ba ta ce “Tayseer Ayra da ita da wa suka zo gidan nan?” Tayseer ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Ita ka’dai.” “Tace miki ina mijinta?” Ummeey ta fa’da murya a raunane. Tayseer ta saki murmushi kafin ta ce “Cewa ta yi wai yana can ni na ‘dauka ma Amma tazo dubawa, to ga dukkan Alamu bata san Amman ma bata da lafiya sai da na gaya mata.” Ummeey hankalinta a tashe ta ce “Maza ki kai mata wayar.” A kwance ta samu Ayran a kan gado idanunta lumshe. Sallamar da ta yi yasa Ayran bu’de ido tana kallonta. Tayseer ta mik’a mata waya tana fa’din “You’ve a call.” Ayra ta bi wayar da kallo tana fatan ba Turaki bane ya kira, da hannu ta mata alamar waye? Tayseer ta ce “Ummeey ce.” Sai sannan ta kara wayar a kunnenta ta mata sallama da gaisuwa. Da sauri Ummeeyn take amsawa burinta kawai ta ji me ya faru. “Ayra me yasa kika taho?” Ayra ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “Bakomai Ummeey.” “Gaya min gaskiya, gaba ‘daya hankalina ya kasa kwanciya…” tausayinta ya kama Ayra kafin ta ce “Bakomai Ummeey.” “Shikkenan idan kin zo za mu ji, amma idan kin san wani abu ne mai muni pls kada ki fa’di ma kowa, ki fari gani na tukun ki min wannan alfarmar.” Ayra ta ‘d’aga kanta ha’de da fa’din “To Ummeey, In sha Allah.” Hankalin Ummeey sam bai kwanta ba, don haka ta dinga jan wasu addu’oi a zuciyarta kafin ta sake kiran Turaki, sai dai still wayarsa bata shiga. Har Magriba Ummeey dai kallon kowa take, sam hankalinta ya kasa kwanciya, ana mur’da k’ofa take ‘d’aga kai ta ga waye? Jira kawai take ta ga Ayra. Zainab ce ta je ‘daukota a airport bayan ta musu waya jirginsu Ya yi landing. Tun a mota Zainab take tuhumarta dalilin zuwan ta ita dai murmushi kawai take ta ce “Bakomai.” Har suka isa asibitin bata sanar mata abinda ya faru ba. Zainab dai ta ja bakinta ta tsuke tana addu’ar kada Allah yasa hasashenta ya zama gaskiya. Ita kuwa Ayra burinta kawai taga Ammanta, don haka ta k’agu su isa ‘dakin da Amman take a hanya Zainab ta dubeta da murmushi ta ce “Ke Abba Jabiru ya dawo.” Ayra ta waro ido don duk bata san shi ba, bata mantawa kullum Sai Amma ta saka su masa addu’a tun suna yara. “Ya. Zee da gaske?” Ta fa’da cikin farin ciki. Zainab ta ‘d’aga kai “Da gaske Ayra, Abba Jabiru ma cikakken Doctor ne a asibitin nan, last month ya dawo daga egypt shine likitan da muka zo gani da Amma, ashe rabon zamu ha’du da shine.” Ayra ta ce “Alhamdulillah! Na san yanzu kam Amma tana cikin farin ciki.” “Sai ma kin ganta.” Zainab ta fa’da tana tura ‘dakin da Amman take ciki. Ayra ta saki ajiyar zuciya ganin Amman a zaune tana ci abinci, da sauri ta k’arasa wajenta ta rungume cikin farinciki. Itama Amman rungumeta ta yi tana fa’din “Oyoyo Auta ta.” Ido biyun da suka yi da Ummeey ne yasa ta ji kunya, sai ta saki Amma ta k’arasa wajen Ummeey ta niyyar durk’usawa Ummeey ta janyota jikinta ta rungume tana fa’din “Na k’i wayon, ita Amma a ka rungume ni kuma a durk’usa min, bayan yanzu ni ce Mamanki.” Ayra ta saki murmushi kawai tana hugging Ummeeyn. Mintuna ashirin kawai Ummeey ta barta ta yi sai ta mik’e tana kallon Ayra “Taso dear mu je masauki, naga kin kwaso gajiya, mu je ki huta, jikin Amma Ai da sauk’i gobe na za su wuce gida, mu kuma za mu biya Gombe za mu je na’din sarautar Kakansu Turaki an ba shi Sarkin Fulanin Gombe.” Amma tana murmushi ta ce “Shikkenan, daga nan Ayra sai ta ga dangi, dama bata ha’du da su ba da biki an yi biki a tsatstsaye.” Ayra ta yi shiru kawai don ita sam wannan hukuncin bai yi mata ba. Haka dai jikinta a sanyaye ta mik’e ta nufi in da Ummeey da Tasleem su ke. Deejah kuwa sai dariya take mata ganin yarda fuskarta ta nuna alamun bata so ba. Ummeey na lura da haka ta janyota “Rabu da Ita Dear, ai gobe kafin su tafi za mu je gidan Jabiru mu ganta, don ma ta k’i ne da sai ta yi zamanta a nan, to ta ce wai Jummai aminiyarta sun zo daga Shagogo ta tsayar da su a can gidanta don haka zata koma.” Ayra dai ta saka k’afa ta bita ba don ranta ya so ba sai don kunyar idon Umeeyn da k’arfi da yaji take neman yiwa Amman k’wacen y’a. Tunda suka fita Ummeyn take Allaha-Allaha su isa masauki ta ji dalilin zuwan Ayran bagatatan. A gidan Turaki na Abuja suka sauka, wanda yake Maitama drivernsa ne yazo ‘daukarsu. Hannun Umeey a cikin na Ayra kamar wani zai k’wace nata ita suka shiga tsararren gidan, da ya tafi da Imanin Ayran don tsari kam ita tsari gidan ya tsaru. Ummeey ta jata wani ‘d’aki tana duban Tasleem ta ce “Maza ki samar mana ko Chips ne a kitchen ba ma kwana da yunwa ba, ki dama min oat.” Tasleem ta amsa mata tana shiga wani b’angare da zai kaita har babban kitchen ‘din gidan. Suna shiga ‘daki Ummeey ta zaunar da ita a bakin gado tana kallonta “Oya gaya min me ya faru? Don dai na san ba k’alau ba. Don’t tell me bakomai.” Ayra ta saki ajiyar zuciya haka kawai sai ta ji k’walla ta zubo mata. Ummeey ta dinga jin sautin bugun k’irjinta yana k’aruwa, da gaske hankalinta ya tashi sosai, har zufa ta fara jik’a mata Riga duk da sanyin A.cn da ake kwarara a zuciyarta ta hau raya in dai har da gaske Turaki ya saki Ayra tabbas zai gane kurensa… ta ciji leb’enta tana fa’din “Ina jin ki Ayra, me ya faru?” Zuwa lokacin sautin kukan Ayran ya ‘Karu sosai ta fara zaro wayarta a jaka kafin ta runtse idonta ta kunnawa Ummeey abinda ya ka’da y’an hanjinta ya razanata lokaci guda, b’acin ranta ya bayyana fuskarta ta canja daga Ummeeyn da aka sani mai fara’a mai yalwar murmushi zuwa wata irin fuska mai bayyana b’acin ranta a fili k’arara……. 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊. Takaicin Uba…. 57. Ummeey ta sake jan ajiyar zuciyar, da take nuni da tsananin tashin hankalin da take ciki, kafin ta saka hannayenta ta kamo na Ayra cikin kwantar da murya ta ce “Ayra ina neman alfarmarki don Allah kada ki bari kowa ya ji wannnan maganar ta Turaki, idan da hali ka ki gogeta da kaina zan yi maganin abin, wallahi zan k’watar miki y’acinki a wajensa har sai ya amsa laifinsa da kansa mun kuma hukuntashi ba tare da kowa ya sani ba, ba dai kin ce ya janye sakin ba tun kafin ki dawo.” Ayra ta ‘d’aga kai tana jin tausayin Umeey da yanayin da ta shiga, da na sani ya fara rub’anya a zuciyarta sai dai hakan da ta yi ta tabbatar shine abinda zai siya mata mutuncin ta a wajen Turaki ya dawo ya sake neman aurenta da soyayyarta ma gaba ‘d’aya duk da ba a buk’atar sake auren. Ummeey ta sake dafa ta, murya a raunane ta ce “Za mu wuce Gombe, daga can akwai inda zan kai ki a b’oye min ke zan kuma sanar dake cewa ba ki zo ba, zan garga’di su Tasleem ma, zan kuma san hanyar da na bi na hana shi zuwa wajen Amma ko kuma na sanar da Amman ba don komai ba sai don kada ta sanar masa kin zo gari. Zai gane shayi ruwa ne.” Ayra ta saki murmushi tana jin wani farin ciki a ranta. Umeey ta fita bayan lokaci ka’dan ta sake dawowa tana kallon Ayran “Tashi maza ki koma ‘dakin Mijinki ki kwana a can kafin gobe mu tafi Gombe.” Ayra ta mik’e tana jin wata matsananciyar kunyar Ummeeyn. Ummeey kuwa bata ma lura da ita ba tana ta danna wayarta don neman layin Tayseer don ta sake garga’darta kada ta sanar da Turaki zuwan Ayran. Ayra ta saki ajiyar zuciya bayan Ummeeyn ta fita, ta cigaba da kallon Bedroom ‘din Turakin da yarda aka tsara shi kamar ba za’a mutu ba. Sannan gaba ‘d’aya ‘dakinsa wani k’amshi yake fitarwa wanda ya ha’de da nasa k’amshin na turaren da yake amfani da su kullum. Ta gefen gadon ta hango hoton matarsa da na Aman sai na sa, Matarsa sai sakin murmushi ta ke, a ‘d’aya side bed drawer ‘din ta ga nata hoton da ya fisgi hankalinta, don dai zana da aka yi ta kuma fito ra’dam kamar dama itace a zanen. Bata san sanda ta saka hannu ta ‘dauki hoton ba daga ganin yanayin hoton lokacin ba zata zarce shekaru sha takwas ba, ta tuna irin ha’duwar da suka yi da Turaki a airport da yanayin kallon da yake mata wanda ya ja tayi saurin jan nik’ab ‘dinta ta rufe fuskarta, lamarin ya shiga dawo mata kamar majigi, a yanzu kam ta tuno inda ta san fuskarsa da a kallo guda ta dinga tunanin kamar ta san shi. Wanka kawai ta yi ta saka nightwear ‘dinta kafin ta ‘Dane gadonsa ta kwanta tana lumshe ido, k’amshin turarensa ya dinga tayar mata da wani irin feeling da zarar ta rufe idonta sai ta ga Turaki yana mata wasu irin wasanni da suke ‘dauke mata wuta, da kyar ta samu barci mai nauyi ya ‘d’auketa cike da tarin mafarkin Turaki mai tsayawa a zuciya. ___________________ K’arfe 9:45 jirgin su Turaki ya sauka a k’asar Nigeria, don ya kasa hak’uri sai da ya nemi Jirgin da zai isa Nigeria ko da ace zai yi transit ne. Bai kira kowa ba kamar yarda bai sanar da kowa zuwansa ba ya tari taxi ta nufi da shi gidan su. Gidan tsit kamar yarda yanayin gidan yake daman can musamman kasancewar rashin yara a gida sai Aman kawai shi kuma yana boarding a Nigerian Turkish. Mai gadin gidan ya yi saurin amsar jakar sa y wuce da ita sashen sa, shi kuwa Turaki Direct part ‘din Ummeey ya tafi don burinsa ya ji labarin zuwan Ayran. Shiru wajen kamar ba kowa sai da Tayseer ta fito daga bedroom ‘dinta jin motsi sannan ta yi arba da shi. Sannu da zuwa take masa Amma hankalinsa sam ba ya kanta ta ji ya jeho mata tambaya “Ina Ummeey?” Tayseer ta danne dariyar da take son kamata ta ce “Bata nan Ya. Wani abu ne?” “Ina taje?” Ya fa’da yana fesar da numfashin tashin hankalin da ya cunkushe masa zuciya. “Tana Abuja. Amma na ji ta ce yau za ta wuce Yola wajen…” da sauri ya tsayar da ita “Kin ji labarin Ayra ta zo?” Tayseer ta ‘dan yi jin kafin ta girgiza kai ta ce “Nop, gaskiya ban ji ba, but am not sure ko tana gidansu.” Ya zauna yana murza goshinsa kafin ya ‘dago idanunsa har sun shige sabida tashin hankali ya mik’e “Oya ba ni key ‘din motar koma waye? Ki zo mu je gidan nasu.” Tayseer zuwa lokaci ta kasa danne dariyar da ke cin ta sai ta wayance da tari kafin ta dakatar ta ce “Ammanta fa bata da lafiya suna Abuja, Umeeyn ce ma ta kaita tun last week.” Ya sake komawa ya zauna yana jin kamar jiri ne ma yake neman ‘dibansa ya san shikkenan yanzu kam ya ga ta kansa Ayra ta sanar da kowa duk abinda taga dama. Wayarsa ya laluba ya fara booking flight da zai tashi in the next few Hours zuwa Abuja. Sannan ya mik’e zuwa sashensa don yin wanka bayan ya karb’i numberr Ayra da take amfani da ita a Nigeria. Ya dinga kira amma wayar ana gaya masa busy take da alama ta sakata a Do not disturb, mik’ewa kawai ya yi yana zirya a ‘d’akin cikin tashin hankali zuciyarsa kuwa gaya masa take Turaki you are finished, ya san in dai Ummeey ta san maganar nan ya ka’de har ganyensa. Jikinsa a sanyaye ya shiga wanka duk da gangar jikinsa ce kawai take buk’atar wankan zuciyarsa da ruhinsa ba ta wankan suke ba. Burinsa kawai ya ga Ayra kafin ta kai ga kunnawa Ummeey wannan recording ‘din. _____________ Sanda Turaki yake can hankalinsa a tashe, su su Ayra tuni sun isa jihar Gombe wajen na’din sarautar Kakan Turakin wanda za’a bawa Sarkin Fulanin Gombe. Tuni ainahin Family House ‘din nasu ya cika dank’am da jama’a da alama ba k’aramin taro aka shiryawa na’din sarautar ba. Tun daga harabar gidan Ayra take waige-waige don al’ajabi da mamakin ginin da kai tsaye ana ganinsa za’a danganta shi da sarauta. Bata tsinke da lamarin ba, sai da suka isa ainahin babban falon Matar Kakannasu, duk da tsufanta hakan bai hana bayyanuwar kyanta ba, game da nutsuwarta, tana ganin Ummeey ta ‘dan saki murmushi tana nuna mata wajen zama. Ummeey ta zauna cike da girmamawa hakan yasa itama Ayra ta samu waje ta zauna kamar yarda ta ga Umeey ta yi, suka gaisheta a nutse irin gaisuwar da ake wa Sarauniyoyi masu ji da mulki. Murmushi kawai ta yi tana duban Ayra ta ce Noy belle Didi? Matar Aminullahi ce?” Ummeey ta ‘d’aga kai, Fulani ta ‘d’aga kai “Ma sha Allah, kin ga wani abin mamaki sai ta yi min kama da Kwairanga Ko kuma idona ne?” Ummeey ta ce “Ba mamaki, kin san a duniya sai ka ga wani yana maka kama da wani.” Ta fa’da ba tare da kulawa ba ko don bata san wacce ake nufin bane, don tun kafin a aurota ta rasu ita ce Mahaifiyar Kakan su Turakin. Ayra dai duk ta bi ta takura saboda duk sanda zata ‘d’aga ido sai ta yi arba da Fulani tana kallonta irin kallon da ake kira na k’urilla. Ummeey ta lura da hakan don haka sai ta mik’e tana kallon Fulani ta ce “Bari mu isa masauki.” Fulani ta sake ‘d’aga kai tana sake bin Ayra da kallo, har sun ‘dan fara tafiya suka ji ta ce “Hameeda, Ku zo nan.” Suka sake juyawa suka isa wajenta ta ‘dan mik’e zaune tana kallonsu kafin ta ce “Wannan yarinyar y’ar waye? Kuma daga wace jiha aka aurota?” Hameedah ta ji tambayar ta mata wani banbarakwai sai dai ta dake ta ce “A garin Kano aka aurota kuma sunan Mahaifinta Kabiru ‘dan garin Shagogo mahaifiyarta kuma Talatu duk daga can suka zo?” Jinjina kai Ta yi kafin ta ce “Ku je.“ ta mayar da idonta kawai ta lumshe tana jin dama abinda take hasashe ya tabbata. Ayra dai ta bi Ummeey jikinta a sanyaye tana mamakin wannan tambayar ta ya Uwarka ta haifeka. Jirgin k’arfe 8:30 na dare ne ya dire sa a garin Abuja, zuciyarsa cike da tarin tsoron yarda za su ha’du da Ummeey. Tun daga bakin gate ya tambayi Maigadi Ummeey tana nan? Maigadin ya girgiza kai kafin ya ce “Sun tafi Gombe yesterday Morning.” Turaki ya rik’e kansa kawai ha’de da fa’din “Ya Allah! Ita da waye?” Da yake Ummeey ta garga’di mai gadin hakan yasa ya ce “Ita da Tasleem.” “Babu wata a tare da ita?” Turaki ya fa’da hankalinsa a tashe. Ibro mai gadi ya girgiza kai “Gaskiya Yallab’ai su ka’dai ne kawai.” Turaki ya ja tsaki yana shiga gidan jikinsa a sanyaye ya tabbata Ayra tana gidan su kenan ta kuma sanar da Ammanta abinda yake faruwa duk da bai so hakan ba. Wayar Tasleem ya danna ya kira bugu biyu ta ‘dauka da alamu suka nuna tana cikin hayaniya zata fara gaishe sa ya yi saurin tsayar da ita “Dakata, ke da wa kuka zo Abuja?” “Ni da Ummeey.” Daga haka ta ja baki ta tsuke kafin ya sake watso mata tambaya “Ayra fa?” “Ba ita Ya, wani abu ne?” Ya sake cizar leb’ensa kafin ya ce “Is she coming or not?” Ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “She isn’t. But am not sure ko tana gidansu yau dai Amman suka koma Kano.” Turaki ya daki hannunsa da bango kafin ya ce “Sun koma Kano?” Ta ‘d’aga kai kafin ta ce “Sure, na ji suna waya da Ummeey, tana ce musu sun je lafiya.” Turaki ya saki ajiyar zuciya kafin ya katse wayar ya sake calling Ayra still busy kawai sai ya yi cilli da wayar yana mik’ewa ya shiga ‘dakinsa. Mamaki ne ya kamasa jin mayataccen k’amshin turaren Ayran a ‘dakinsa ga toilet ‘dinsa yana fitar da k’amshin Almusk ‘din da take yawan Using. Ya shak’i k’amshin sosai ya tabbatar ba hancinsa ne yake gaya masa ba, K’amshin Ayransa ne. Kawai sai ya samu kansa da sakin murmushi A fili ya ce “Sure, Ayra ta zo gidan nan.” Ya k’arasa bakin gadon yana jan pillow ya kai hancinsa still dai k’amshin Ayra ne, kawai sai ya samu kansa da sakin ajiyar zuciya yana rungume pillow ‘din tsam a k’irjinsa kamar ya samu Ayran. Da safe kuwa Ayra tana gama shiryawa Ummeey ta shigo tana kallonta tana murmushi ta masa gaisuwarta tana fa’din “Jiya Turaki ina ji ya min missed calls sun kai ‘dari, don haka yanzu muna zuwa kika gaida Mai martaba zan wuce da ke gidan Sisterr mai gidan nan, Adda petel ki yi zamanki a can.” Murmushi Ayra ta yi, Ummeey ta mik’a mata babban mayafi ta ce “Yafa maza mu je ki gaida Mai martaba Jauro.” Ayra ta amshi mayafin da yake zuba wani k’amshi kamar an tsoma a ruwan turare suka fita ta wata k’ofa da zata kaika sashen Mai martaba kai tsaye. Duk inda suka shige sai an durk’usa an gaida su har suka shiga k’aramar fadarsa. A kishingi’de suka same sa da carbi a hannunsa gefensa Fulani ce tana sake dama masa furar da zai sha kafin ya fita fada. A nutse yake kallon Ayra kafin ya mik’e cikin tarin mamaki ya ce “Ikon Allah wannan kam Ai sai na ce K’anwata Danejo ce tana yarinya.” Ummeey ta ‘dago tana kallon Ayra da take durk’ushe a gabansu. Fulani ta saki murmushi ta ce “Abinda nake gaya maka kenan, kamannin nasu har sun b’aci.” Ya sake k’ura mata ido yana sake ganin tsananin kamarsu ba banbanci ko ka’dan. Ya amsa gaisuwarta yana fa’din “Sannu yarinya, ni kuwa zan so ganin Mahaifiyarki akwai tarin tambayoyin da zan mata ina ji a jikina ke jinin Danejo ce.” Ayra ta sunkuyar da kanta tana matsa hannunta kafin ta sake ‘dagowa ta kallesa gabanta yana fa’duwa tana fatan duk hasashenta ya zama gaskiya ace wannan su ne dangin Ammanta da wani irin farin ciki Amman zata shiga. Itama Hameeda tunanin da ta shiga kenan, da sauri ta ce “In sha Allah zan kirata za kuma za su zo kafin na’din sarautar gobe.” Ya jinjina kai yana fa’din “Haka ya kamata a yi, kullum addu’ata na ga jinin Danejo ko da ace ita bata raye, ashe ma tana raye don jikina yana ba ni wannan daga duk inda ta zo jinin Danejo ce. Suka masa sallama suka tafi, zuk’ata cike da tunani kala-kala, da jiran zuwan gobe su ji daga bakin Amma, idan hakan kuwa ta tabbata ba su san wani irin farin ciki zuri’ar za su ji ba, shikkenan tafiya gidan Adda petal ya sha ruwa. Aka zauna zaman jiran gobe a ga mai Amma Talatu zata ce…. 𝕹𝖆𝖟𝖊𝖊𝖋𝖆𝖍 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍️ Takaicin Uba… 58. Da mugun speed ya danna hancin motarsa cikin harabar ajiye motoci ta masarautar. Ya saki ajiyar numfashi bayan ya yi parking ya lumshe idonsa yana addu’ar Allah yasa komai ma yazo masa da sauk’i kada Ummeey ta yi masa bore. Tsawon mintuna biyu ya ‘dauka zaune a cikin motar kafin ya kalli mudubi yana kallon yarda rashin nutsuwa ya ranar da shi in just a few days. Wayoyinsa kawai ya ‘d’auka ya sauko daga motar tasa don long driving ya yi from Abuja zuwa Gombe. Nan da nan Hadimai suka yi cincirindo a gabansa kasancewarsa mutum mai barkwanci da yawan kyauta. Hannu kawai ya zira a aljihunsa ya ciro ku’din da bai san adadinsu ba ya mik’a musu, sannan ya ‘d’aga musu hannu alamar ba ya son dandazon rakiyar da za su masa. Ya cigaba da takunsa cike da nutsuwa yana kallon gefe da gefen masarautar yarda bak’i suka fara cika wajen. Sashen Mahaifinsa ya nufa don ya tabbatar Ummeey tana can tunda a can ‘din ta saba sauka. Yana tura k’ofar idanunsa suka fa’da cikin na Ayra da take tsaye da Tasleem tana nuna mata wani abu a waya. Wata irin fa’duwar gaba ce ta samu Ayra, da sauri ta juya tana runtse idonta, ashe shine zai zo shi yasa tun safe take jin yanayin sauyawar bugun k’irjinta. Ya k’arasa wajen su yana niyyar yi musu magana Ayran ta yi saurin shigewa ‘dakin da ta sauka ta murza key. Murmushi Turaki ya saki yana kallon Tasleem da ta zuba masa ido ganin yarda ya bi k’ofar da Ayran ta shiga da wani kallo yana cije leb’ensa “Kallon fa?” Ya fa’da yana gimtse fuskarsa “So na fara wasa da ke kenan, shi yasa na tambayeki ta zo kika ce bata zo ba ko?” Tasleem da sauri ta fara ja baya tana fa’din “Am sorry Ya. Ummeey ce ta ce kada mu fa’da maka.” Ya ‘dauke kansa yana zama kan kujera ha’de da cusa hannayensa cikin tarin sumar kansa a hankali ya hau furta “Ayra!” Sai kuma ya Lumshe idanunsa yana tunanin wani irin hukunci zai mata idan ya kamata don ta wahalar da shi sosai, Tasleem dai tana tsaye tana kallonsa tana sakin murmushi k’asa-k’asa. Idanunsa ya ware a kanta ya ce “Samo min coffee mai zafi Malama.” Da sauri Tasleem ta juya ta shiga babban kitchen ‘din su tana y’ar wak’a don idanun Yayan nasu kawai za ka kalla ka hango tsagwaron soyayyar da yake wa Ayra Gaya. Tsam ya mik’e ya isa bakin k’ofar ‘dakin ya ‘dan yi knocking , Ayra da take ciki da sauri ta ware ido tana fa’din “Waye?” “Idan kika bari na kamaki ko? Zaki gane kurenki, ina wasa da ke ne?” Ayra ta tab’e baki tana fa’din “Ba zan bu’de ba, me ye naka a wajena.” Turaki ya yi k’wafa yana barin wajen, jin takun tafiyar Tasleem. Sai da ya karb’i Coffee cup ‘din sannan ya kalleta “Ummeey fa?” Ta nuna masa ‘daki. Ya rik’e cup ‘din ya nufi ‘dakin Ummeey yana fatan Ayran bata gaya mata komai ba. Ummeey ta bi shi da kallo bayan ta kashe wayar da take amsawa. Kallon ne ya tada hankalin Turaki da k’yar ya ‘daga k’afarsa ya isa inda take, idanunsa a rusune ya zube daf da k’afarta. “Ummeey ina yini?” Bata amsa ba illa zuba masa ido da ta yi tana jin wani takaicinsa yana cika mata zuciya. “Me kazo ka ce min Turaki? Ko ka zo ka kawo min takardar sakin ne? Tunda magana da fatar bakin ba ta yi ba?” Hanjin cikinsa ne ya ka’da ya ware idonsa sosai yana fa’din “Saki kuma Ummeey? Sakin wa?” “Sakin Ayra da ka yi mana.” Da sauri ya ajiye cup ‘din da yake sipping coffee ‘din ya ce “Haka ta zo ta ce miki Ummeey? Wallahi ni ban sake ta ba, ban kuma furta mata saki ba, wancan furucin da na mata idan ma shine na janye.” “Saboda yanzu ka sameta a cikakkiyar budurwa ko? Sab’anin da da kake tunanin fanko ce, shi yasa ka janye sakin? Ashe Turaki ba zaka iya rufa wa Ayra asiri ba, ko da ace abinda kake tunani haka ne, to bu’de kunnenka da kyau ka ji, tunda har ka yi wannan furucin to ina tabbatar maka dole ne ka saketa don ni ba zan bari ta zauna da wanda bai san mutuncin mace ba, ce maka aka yi duk macen da ta rasa budurcinta bata da mutunci kenan? Kada ka manta wasu fa tsautsayi ne yake ruftawa da su, ya zaka yi idan k’anwarka Ko y’arka aka yiwa fya’de shikkenan za ka ji da’di idan wani ya saketa saboda rashin budurci, to ba zan amince ba dole ne ka saki Ayra, tunda ka tabbatar bata rasa budurcin ba, ni kuma ina goyon bayanta ba zan saka ta zauna da kai ba dole, idan ka ga har na amince Ayra ta koma gidanka sai dai idan da kanta ta furta tana son komawar, don haka sai ka je ka fara shirin kafa gwamnatinka a wajenta har sai ta amince a kan kin kanta Zata koma sai ku zo ku same ni tare ku sanar min kun sasanta.” Turaki ya zaro ido kafin zuciyarsa ta shiga bugu da k’arfin gaske tunaninsa ta ina zai fara shawo kan Ayra, a hankali ya furta Ya Allah! Ummeey ta kalleshi tana tab’e baki ta mik’e tana nufar k’ofa “Idan ka fito ka kulle min k’ofa.” Turaki ya ‘d’aga kansa kafin ya mayar da ido ya lumshe yana tunanin ta wace hanya zai shawo kan Ayra Gaya, daga ganinta zata yi kafiya da taurin kai…. Ya saki hucin numfashi yana fa’din God help me! Yana kwance a ‘d’akin Ummeeyn ya ji an turo k’ofa. Ayra ce a tsaye ta yi kicin-kicin da fuska Ummeey ce ta aikota ‘daukar mata Hijab zata gaisa da bak’i a fada. Turus ta yi ganinsa kwance a kan hannayensa idanunsa a lumshe kafin ya bu’de ya ware su a kan Ayra da take tsaye ta ha’de rai. Mik’ewa ya yi a hankali da niyyar gyara kwanciyarsa ya shammaceta ya jata jikinsa sai gata a kan ruwan cikinsa ta zaro ido tana kallonsa kafin ta ce “Malam me ye haka?” Ya ja karan hancinta kafin ya ce “Mele ne, ke zan tambaya me ye haka? Me kika zo kika cewa Ummeey?” Ta hau zame jikinta a hankali tana cewa “Abinda ka ce min, ni ka sake ni.” “Na k’i na sake ki ‘din, ashe baki da kai, wa yace miki ana wasa da kalmar saki, Karen hauka ne ya cije ni da zan sake ki? Kin san tsawon lokacin da na ‘dauka ina dakon soyayyarki, sannan na je na ‘dan d’ano abin can ba dama ki ce kuma na sake ki, Auren mu na nan mutu ka raba.” Ta sake k’ok’arin k’wace jikinta don tana jin wani irin yanayi a duk sanda ya yi magana hucin numfashinsa ya sauka a wuyanta, “Ka cika ni na kai mata Hijab wajen ba’ki zata je.” K’ura mata ido kawai ya yi yana kallon yarda lab’banta masu d’an tudu suke shining suna fusgar hankalinsa idan tana magana. Yatsansa ya saka yana zagaye leb’en kafin ya kai masa kyakykyawar sumbatar da ta kusa matar da Ayra a zaune, ya saketa yana ja baya ha’de da runtse idanunsa “Je ki Ayra kada ki jawo na aikata komai a ‘d’akin nan, don Allah ki yafe min ki ce ma Ummeey kin yafe min kin ji?” Ayra ta mak’e kafa’darta irin yarda yara suke yi idan sun so rigima. Turaki ya lumshe ido yana jin yanayin nata yan saka a duk wasu gab’ob’insa amsawa “Ki wuce tun kafin na sauke gajiyar da na kwaso a jikinki yanzun nan, ba ki san yarda nake missing ‘din ki ba ko?” Ta tureshi da sauri tana mik’ewa jin inda hannunsa ya kai. Da sauri ta fice daga ‘dakin tana ‘dan haki, sai da ta tsaya a corridor ta gyara gashinta da ya barbaje da yamutsewar rigarta sannan ta nufi falon, duk da bata san k’amshin turarensa ka’dai ya isa a gane daga inda take. Wayam ta ga parlourn ba kowa, da sauri ta isa kitchen wajen Tasleem da suke shiryawa su Amma girki ta tsaya tana kallonta kafin ta ce “Tasleem Ummeey fa?” Dariya ce ta so kama Tasleem ta ce “Ta gaji da jiranki ta ‘dauki nawa ta fita.” Ayra ta lumshe ido tana sakin ajiyar zuciya “Toilet na shiga shi yasa na da’de.” Wannan karan Tasleem kasa ha’diye dariyar ta yi sai da ta dara sosai sannan ta ce “A toilet kika kwaso k’amshin Turaren Mijinki kenan?” Ayra ta waro ido tana shinshina jikinta da sauri ta fice a guje, Tasleem ta bita tana fa’din “Kina canja kaya kuma zata yi tunanin babban lamarin ne ya afku, kin ga shikkenan sai ta tattara ta koreku ke da mijinki.” Ayra ta dafe kanta tana zama a kan kujera ta ce “Ya Allah! Yanzu Tasleem ya zan yi?” “Mursisi za ki yi, ki daina wahalar da Yaya na haka Wallahi yau ya bani tausayi.” Ta ha’de rai tana mik’ewa ta ce “Never! Kin san kuwa me ya yi min? Mu je dai kawai mu k’arasa aikin mu.” Shi kuwa Turaki da k’yar ya mik’e ya isa ‘dakinsa da yake nan sashen ya baje a kan gado Gaba ‘d’aya kwanyarsa ta tsaya masa cak, matarsa kawai yake buk’ata. Mafita kawai yake nema. Suna aikin Ummeey ta dawo daga wajen bak’in, Ayra na jin shigowarta ta ji kamar ta nutse a wajen don kunya, Ummeey kallonta kawai ta yi ta ‘dauke kai tana murmushi ha’de da bu’de dishes ‘din ta ce “Yauwa komai is ready sai jiran zuwan su Amma.” Ayra ta saki murmushi tana saurin ficewa ha’de da cewa “Bari na yi wanka kafin su zo” Ummeey ta bita da kallo tana murmushi kawai ganin yarda duk take a firgice ga k’amshin turaren da ya mak’ale a jikinta. Tasleem ma murmushin take tana mamakin rashin wayo irin na Ayra kamar yarinya k’arama. ___________ Sai Yamma su Amma suka iso, a guje Ayra ta taresu tana jin kamar ta mayar da su cikinta. Amma ta dafa kanta kawai tana murmushi ganin yarda Ayran ta sake cika ta kuma yi fari tas da ita. Nan suka baje don cin abinci kafin su yi wanka a rakasu wajen Mai martaba. Bayan sun yi wankan suna zaune a parlour Turaki ya fito cikin rantsatstsiyar shigarsa ta Farin voile tas da shi, sai baza k’amshi yake ga hula da ya kafa a kansa ta sake fito da tsananin kyansa da cikar kamalarsa. Kallo ‘d’aya ya yiwa Ayra da ta mak’ale jikin Amma kamar zata shige cikinta, ya durk’usa ya gaida Amma a ladabce kafin ya gaida Majeedah, Zainab, Aysha da kuma Deejah sai Inna Jummai. Suka amsa masa da walwala fal fuskarsu, kafin Umeey ta ce “Ka gaida Babanta Kamilu yana Babban falo, k’anin Babanta ne shak’ik’i.” Turaki ya ‘d’aga kai kawai yana sake kallon Ayra ta gefen ido da itama take kallonsa a sace. Ya mik’e ya wuce ta gefenta ta shak’i k’amshin turarensa ta ‘dan lumshe ido ka’dan tana jin fa’duwar gaba na sake kamata. Sai da suka gama abinda suke, sannan Ummeey ta mik’e don musu iso duk da bata sanar da su dalilin kiran ba, ta ce dai ya kamata suma su zo na’din sarautar shine suka zo a zuwan y’an gayya. Tunda Amma ta saka idonta cikin na Mai martaba ta ji fa’duwar gabanta ta k’aru saboda tsananin kama da ya yi mata da Innayo. Jikinta a sanyaye ta k’arasa ta zauna, har a lokacin shima kallon ta yake duk da dai ba abinda ta ‘dauko na Innarta amma tsananin kamar da suke da mahaifiyar su Adda ya yi yawa. Girmama girman Ubangiji yake kawai a zuciyarsa kafin ya mik’e yana sake zame rawaninsa ya kalli Ummeey da Fulani ya ce “Ga duk wanda ya san Adda ya san wannan jininta ce saboda yarda ta yi kama da ita kwabo da kwabo, ya sunan Mahaifiyarki?” Amma Talatu ta ‘dago da sauri tana kallonsa ta ce “Sunanta Hauwa Kulu, ana kiranta Danejo.” Kowa sai da ya ‘dago yana kallnta musamman Maimartaba cikin mamaki ya ce “Hasashena ya tabbata yau ga jinin Danejo a gaba na, Alhamdulillah ya Allah mahaifiyarki ciki ‘d’aya muke da ita ni na sha Nono na sakar mata, masu satar mutane ne suka raba mu da ita, rabawar da ta zamo ta har abada shikkenan har yau ban sake jin labarin ‘dan uwa na ko ‘d’aya ba sai yau da Allah ya ha’da ni da ke, Alhamdulillah ya Allah.” Shikkenan guri ya ru’de da murna, Kamilu yana gefe yana jaddada girman Ubangiji Ai kuwa zai je Shagogo ya sanar da su wacece Talatu da ake wa gorin dangin Mahaifiya ga shi nan wan Mahaifiyarta ne zai zama Sarkin fulanin Gombe, ashe dai Ayra tsatson su ‘d’aya da Turaki, shi kansa Turakin mamaki ne yasa ya tsaya cak yana duban Ayra bai tab’a zata ko a mafarki Ayra y’ar uwarsa ce ta jini ba. Talatu kam murna take sosai ta kama hannun mai martaba ta rik’e gam tana jin sa kamar Innayonta ashe zata ga wannan ranar, ashe zata ga dangin mahaifiyarta bayan ta gama fitar da rai. Har dare murna bata bar ahalin nan ba, haka aka zauna aka dinga labarin lokutan baya, Mai martaba ya dinga bada labarin y’an uwansa da ya rasa. Sai da suka koma sashensu Ummeey ta kalli Ayra da Tasleem da Tayseer da itama ta iso a yammacin ranar ta ce “Maza ku tafi gidan Addarku Adda petal ku kwana a can, za ku fi sakewa tunda gidan nan a cike yake damk’am. Suka mik’e suka shiga ‘d’aki don ‘Debo abinda za su buk’ata, Turaki da yake gefe ya yi kamar bai ji me suke cewa ba ya mik’e tsam yana kallon Ummeey ya ce “Sai da safe.” Sannan ya kalli Amma ya ‘dan rusuna ya ce “Amma sai da safe.” Duka suka amsa da Allah ya tashe mu lafiya. Ya isa can inda ake ajiyar motocin fadar, ya hau kan motarsa ya zauna yana jiran ya ga ta inda za su b’ullo. Suna isowa gurin sam ba su kula da shi ba sai ji suka yi ya ce “Hey, ku shiga mu tafi.” Ba su kawo komai ba suka shiga motar. Ayra ta saka kai zata shiga ta ji ya fisgo hannunta ya ce “Shiga gaba madam, ba driver bane.” Ta ‘dan ha’de ranta tana kallonsa kafin ta bu’de k’ofar ta shiga. Ya saki murmushi yana shiga b’arin driver shima ya fisgi motar da mugun speed dama yanayin tuk’insa kenan. Daidai gidan Adda petal ya tsaya yana kallon su Tasleem bayan ya bu’de motar ya saka hannu ‘d’aya ya damk’i hannun Ayra ya ce “Oya ku je ku ce ina gaishe ta ita zan bata sak’o yanzu zata shigo.” Suka fita shi kuma ya sake locking motar ya fisgeta da sauri, Ayra ta ‘dago tana kallonsa “Ina za mu je.” Ya gimtse fuskarsa yana sake matsa hannunta ya ce “Neman lada…….. 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍️ Takaicin Uba…. 59. Gaba ‘daya walwalar fuskar Ayra ta b’ace b’at ganin yarda Turaki ya kawota. Idanu ta zuba masa cike da son k’arin bayani. Shima nasa idanuwan ya zuba mata yana lumshe su “Sauka Mu je, Malama.” Ta ji furucinsa a cikin kunnenta, da sauri ta janye jikinta jin yarda ya kusantota sosai, ya ‘Dan ‘dauke kai yana dariya k’asa-k’asa “Ki sauka na ce.” “Ba zan sauka ba, ta yaya zaka kawo ni Hotel bayan ga yarda Ummeey ta ce mu je.” Ta fa’da tana kawar da tsoro da shakkar da suke ranta. “Ummeey ce ta biya min ku’din sadakin auren ki?, ki fita ta Lislama ko kuma na fitar da ke da kaina, ba kunyar kowa zan ji anan ba kowa harkar gabansa yake.” Ta sake lafewa a jikin kujerar alamar bata ji maganarsa ba. Turaki ya ji ransa ya fara b’aci kawai sai ya fita ya zaga ya bu’de k’ofar yana fincikota zai kinkimeta. Da sauri ta ture sa “Ka bari zan fita da kaina.” Ya saki hannunta yana murmushin k’asan leb’e. “Da dai kin tsaya kiga ko zan kasa ‘daukar ki.” Ta suri jakarta ta fita tana k’unk’uni da sauri Turaki ya rufe k’ofar ya fita suka shiga cikin hotel ‘din. A reception ya zaunar da ita ya k’arasa don samo musu D’aki. Ayra ji take kamar ta rusa ihu, tana tunanin duk wani plan nata ya rushe, tana kallonsa ya taho cikin takun isa yana ‘d’aga mata gira ya ce “Ya dai y’an matan Ummeey, yau ga ni ga ki ba Ummeey mai tare miki fa’da.” Ta ‘dauke kanta a hankali ta ce “Akwai Allah, shi zai min maganinka.” Ya sunkuya daidai fuskarta yana murmushi “Yi hak’uri y’an mata, har kin karaya?” Wata jarumta ce ta zo mata ta mik’e tana kallonsa a zuciyarta tana fa’din ba dai jikina kake yi wa ba, ai kuwa yau k’walelenka. Kamar yana karanta yanayinta ta ji ya ce “Dole dai komai wayon amarya a sha manta.” Bata kulasa ba ta bi shi suka k’arasa ‘dan ku gun da zai sadaka da ‘dakunan Hotel ‘din. Yana bu’de k’ofar ya saki murmushi yana kallon Ayra “Ma sha Allah, wajen nan zai yi da’din baje amarci.” Ayra ta ha’diye wani abu da ya tsaya mata kafin ta kai idanunta kan gadon ‘dakin da ya ji wani tattausan bedsheet. Ta ajiye jakarta a saman kujera kafin ta bi jakar ta zauna ta zame tana kwanciya a kan kujerar ha’de da fa’din “Allah ya tashemu lafiya. Turaki ya zuba mata ido kafin ya ce “Me ye haka?” “Da aka yi me fa?” Itama ta jefa masa tambayar tana kallonsa da lumsassun idanunta “Don k’azanta haka za ki kwanta ba ki wanka ba, balle uwa Uba Brush.” Ayra ta tab’e baki ha’de da fa’din “Yau dai kam na yafe wankan brush kuma na yi a gida kafin na fito.” Turaki ya tab’e baki yana ‘daukar towel ya shiga toilet yana fa’din “Za ki yi na dole yanzu.” Yana gama nasa wankan ya fito jikinsa ‘dauke da towel, sai ya tarar har ta fara barci a takure kan kujera, ya k’arasa kusa da ita yana sunkuya wa kanta cak ya ‘daga ta, Ayra da barci bai yi nisa ba sosai ta fara mutsu-mutsu na son k’wace jikinta “Bari Malama, if you don’t want me to smash your face.” Shiru ta yi tana jinsa ya shiga toilet ‘din ya ajiyeta cikin showerr da ruwanta yake zuba sosai. Ayra a ru’de ta fara kallonsa yana k’ok’arin zare rigarta “Bari zan yi da kai na.” Ya saki murmushi yana fa’din “Bar shi dai na yi miki mai kike b’oyewa ne? Wani daren ne jemage bai gani ba.” Turaki please!” Ya yi cak yana kallon yarda ta furta sunan nasa, kamar a bakinta aka ra’da ko don bai tab’a jin ta kirasa da sunan ba ne.” Ya kai hannu yana kewaye lab’b’anta ya ce “Say ita again, it sounds so good in your voice” Ta ture hannunsa tana shammatarsa zata fita da sauri ya sake janyota jikinsa yana jin yarda kowane gab’a na jikinsa yake amsa soyayyarta da tsananin sha’awarta “Ki bari madam, kada ki saka komai ya faru anan, kin san yarda na yi missing ‘dinki kuwa? Haba Ayra kada tsinuwar mala’iku ta kamaki.” Ta runtse idonta tana fa’din “To me na yi kuma?” “Komai ma, fita ba da izinin mijinki ba rashin ba ni ha’din kai, ke abubuwa da yawa, yanzu kuma ina son…..” ya fa’da yana k’ura mata ido, gaba d’aya kallon ya hargitsa kanta tana ji tana gani Turaki bai kyaleta ba sai da ta yi wankan nan na dole, sannan ya fita ya barta yana jin wani farin ciki da annashuwa da alama dai tarkonsa ya kama kurciya……😀 Da k’yar ta iya saka kaya a gabansa, kallonta kawai yake yana mamakin da mai yasa idonsa ya rufe ya amince Karuwa ce, bayan ba abinda ya yi kala da karuwanci a jikinta, shi yasa ba a son ka yi aiki da jita-jita, ya lumshe ido kafin ya mik’e ya isa in da take zaune a gaba dresser tana aikin sake k’udundune jikinta da hijabinta don kunyar ya ganta da rigar barcin take. Fuskarta sam bai hango alamar zata masa sassauci ba. Ya durk’ushe a gabanta yana kamo hannayenta masu taushi da sulb’i ya ce “Afuwa Hayateey let forget the past and look for the future.” Ta sake ‘daure fuskarta tsam kafin murya a sauk’ake ta ce “Ba zan iya ba.” What?” Ya furta a ‘dimauce yana kallonta “Me yasa ki ke da rik’o ne? Kin san tsawon rayuwata ban tab’a begging wani ‘dan Adam ba, amma dube ni durk’ushe a gabanki ina rok’on ki kina ce min you will never forget.” Ta lumshe idonta kafin k’arfin zuciya ya zo mata ta mik’e tana kallonsa cikin ido “Kana zata abinda ka min zai yi sauk’in mantawa a wajena? Karuwa fa ka ce min? Ka san tsananin b’acin ran da mutum yake ji idan aka danganta shi da abinda bai tab’a aikatawa ba? Bana jin a rayuwa akwai abinda ba zan manta ba kamar a min k’azafi a danganta ni da abinda ban aikata ba it hurts me so badly, ba zan sake yarda ka kusance ni ba na amince ka auri waccan budurwartaka ni ka bar ni kawai.” Turaki lumshe idonsa ya yi kawai yana jingina da kujera bai san kuma me Ayra take son ya mata ba. Yana ji ta zame hannunta ta juya bu’de fridge ta yi ta ‘dau robar ruwa ta sha sosai kafin ta isa gefen kujerar da yake kwance rik’e da kansa ta ce “Ka tashi ka koma kan gadon, zan kwanta a kujeran.” Bai amsata ba illa murza goshinsa kawai da yake cikin tsananin b’acin rai, yana jin da yana da iko da ya janye wancan furucin, ba ya son Shaheedah kuma bai shirya auren ta ba, duk abinda ta ga sun yi set up ne kawai. Shak’ar k’amshin humrar ta da yake yana sake gigita masa nutsuwa. A hankali bata yi aune ba ta ji ya fisgota jikinsa, ta fara kiciniyar k’wacewa “Bana so Turaki.” “Ni kuma ina so Ayra, Ina ji shine abinda na fi so fiye da komai a rayuwata na ji ni a jikinki ina samun wata irin nutsuwa mai wuyar fasaltawa.” Ya fa’da yana bata hot romances, Jikin Ayra har rawa yake jin abubuwan da yake mata sun fi k’arfin tunaninta, duk wata tsiwa tata ta ‘dauke. Kafin ta ji Turaki ya kinkimeta zuwa tsakiyar gadon. Sai sannan tunaninta ya dawo ganin abinda yake shirin aikatawa gaba ‘daya hankalinsa ya gushe burinsa kawai ya isa mak’ura ya ji Ayra ta ingijeshi ta sauka a guje. “Wallahi ba zan sake yarda ka kusance ni ba….” Cak ya ji ji da ganinsa suna neman ‘daukewa bakinsa na rawa cikin karyayyiyar murya ya ce “Please Ayra! Don’t kil me.” Ta runtse idonta kafin ta shige toilet tana jin duk wasu kalamai da ya dinga amfani da su wajen k’untata mata suna amsa kuwwa a dodon kunnenta. Turaki jikinsa na rawa ya mik’e ya isa bakin toilet ‘din ya mur’da ya ji sa a kulle. A hankali ya zame ya durk’ushe a k’ofar toilet ‘din don k’afafunsa ba za su iya ‘daukarsa ba, yanayin da yake abin tausayi da ace ya iya neman karuwai tabbas da ranar ya nema. Muryarsa a raunane ya shiga rok’on ta “Please ki bu’de zan miki duk abinda ki ke so.” Ayra tana jinsa tana jin kamar tausayinsa ya rinjayeta sai kuma ta runtse ido tana tuno zafafan kalamansa. “Idan ba ki bu’de ba, wallahi gobe zan saka a ‘daura min aure, ba zan zauna kina wahalar da ni ba.” “Ba matsalata bace ka auri goma ma idan ana yi.” Turaki ya saki ajiyar zuciya ganin duk irin magiyar da ya mata bata saduda ba ya koma gado yana futar da numfashin wahala, haka kawai yana zaman zamansa Ummeey ta janyo masa idan banda haka yaushe rabonsa da sha’awar wata mace balle ta ‘d’aga masa hanci. Ya kwanta yana jin kamar ya yi ihu. Da k’yar ya samu nauyayyen barci ya ‘daukesa cike da tunanin dole ne ma ya yi aure in dai Ayra ba zata canja ba. Jin shiru ya sa Ayra a hankali ya fito daga toilet ‘din ta kwanta a saman kujera, sai sannan tsoro ya shigeta ta fara tunanin yanzu da tsinuwar mala’iku zata kwana? Ta runtse ido tana jin hawaye na zubo mata. A hankali ta mik’e ta isa bakin bed ‘din ta fara bugawa a hankali. Turaki ya bu’de idanunsa yana wara su a kanta. “Menene?” Ya furta a shak’e “Ka yi hak’uri ga ni nazo.” Tsaki ya zabga yana kallonta sama da k’asa “Kin zo me?” Ayra ta runtse idanunta tana matsa yatsun hannunta “Bana so ki je ki jik’a ki shanye, mata dai ga su nan bila adadin a gari zaki sha mamaki a gobe zan fara neman aure idan ma ba ‘a d’aura goben ba.” Ya juya yana sake sakin tsaki ya ja duvet ya rufe har kansa don da gaske haushinta yake ji sosai da sosai. Ayra jikinta a sanyaye ta shiga toilet alwala ta ‘daura ta shiga sallolin naiflfili tana jan istigfari barci ya ‘d’auketa da k’yar don komai itama dawo mata ya shiga yi daki-daki wata irin sha’awa ta dinga fusgarta ta dinga jin tamkar ta janyo sa ta dole. ________ K’arfe 9:00 su Tasleem da Adda petal suka isa ainahin main house ‘din nasu, gida har ya fara cika don taro aka shirya ba na wasa ba. Ummeey ta dinga kallonsu kafin ta ce “Ya na gan ku ku ka’dai Ina Ayran?” Kallon juna suka fara suna murmushi kafin Adda Petal ta ce “Wace Ayran? Ai ni su ka’dai suka je min.” Ummeey ta bu’de baki tana kallon ta “Ban gane ba? Matar fa ‘dan ki Turaki nake nufi.” Ta girgiza kai “Ba su je da ita ba, ba su ce min ma tare suke ba.” Ummeey ta mayar da kallonta kan su. Tasleem tana sinne kai ta ce “Wallahi Ya. Turaki ne ya mana wayo ya tafi da ita, daga cewa bari ya bata sak’o.” Ummeey ta girgiza kai tana cizar leb’enta kafin murmushi ya sub’uce mata ta ce “Ai kuwa zai zo ya same ni.” Adda petal ta ce “Wani irin zai sameki kuma shi da matarsa?” Amma ta ce “Gane min y’ar uwa.” Ummeey shiru ta yi tana murmushi don bata son su san menene ya faru. Nan aka zauna y’an uwa da abokan arziki suna ta shigowa ana gaida su Amma Talatu, farin ciki gaba ‘d’aya ya cika zuciyarta ta san tabbas y’an uwa rahma ne. Jummai kanta mamakin yarda y’an Uwan Talatun wanda duk zuri’ar Jauro ce da ya hayayyafa y’ay’a da jikoki tunda matansa hu’du y’ay’ansa talatin da biyar biyu daga cikinsu ne kawai ba su yi aure ba. Don haka suke da yawa sosai. _________ Tun bayan sallahr asuba da suka sake komawa ba su farka ba sai da agogo ya buga k’arfe 11:30. Da sauri Ayra ta mik’e tana kallon yarda hasken rana ya b’ullo ta wibdown da sauri ta kai idanunta kan wayarta da taga missed call rututu ta mik’e da sauri tana shiga toilet. Wanka ta yi sosai sannan ta goge jikinta ta shirya a cikin toilet ‘din tana fitowa mai kawai ta shafa sai ta yi makeup sama-sama ta shafa body mist na royal oud sai humrar ta, kayannata sai k’amshin turaren wuta da aka musu gabbasa yake. Tana d’aure gashin kanta ta ‘dan bugi pillownsa. Da k’yar ya bu’de ido Saboda yarda kansa yake sara masa zazzab’i ne ma a jikinsa sosai. “Kada mu yi late a wajen taro, ga shi a gida ma ba a san muna tare ba.” “And so what? Shi ya ba ki damar ki tashe ni ina barci, idan ba za ki iya jira ba ki tafi bana son damu.” Jikinta a sanyaye take duban yarda yake mata masifa kafin ya sake lumshe idonsa ya juya mata baya. Ayra ta ja ajiyar zuciya tana zama a hankali gefen gadon ta ha’de hannayenta ta zuba kumatunta a kai tana jin kamar ta saka kuka, sam bata son b’acin ransa , sai ta ji ta damu da damuwarsa. Ta koma kan kujerar tana kallon yarda kiran Ummeey yake shigowa wayar akai a kai. A kunya ce ta d’aga wayar tana gaisheta Ummeey ta amsa tana cewa “Ba zaku zo na’din sarautar bane ko kun wuce Moscow.” Kunya ce ta ratsa Ayra cikin rawar murya ta ce “Zamu zo Ummeey ba ya jin da’di ne.” “Ayya, me ya same sa? Maza ki basa wayar na san sa idan ba shi da lafiya sai a hankali.” Ta k’arasa wajensa ganin ya ‘dan motsa ta kara masa wayar a kunne muryar Ummeey da ya ji ya saka shi mik’ewa da k’yar yana amsa wayar “Me ya sameka?” A hankali ya ce “Headache, amma yanzu za mu taho In sha Allah.” “To sai kun zo, Drive carefully don Allah, ko ka bawa Ayran motar ta tuk’a idan inda ku ke ‘din ba nisa.” Daga haka ta kashe wayar. Turaki ya lumshe idanunsa kafin ya mik’e ya shige a hankali ko kallon Ayran bai yi ba. Wayarsa ce ta dinga k’arar shigowar messages ganin sunan Shaheedah yasa Ayra ta ji kawai tana son jin mai message ‘din ya k’unsa da sauri ta ja wayar ta kai dubanta kan messages d’in “Alhamdulillah! Buri na ya cika, after long years sai yanzu ka amince da aure na, yau za ku tura gidan namu na fa’da musu?” Wata irin zufa ce ta shiga zubowa Ayra ta sake ware ido tana kallon Address ‘din da Shaheeda ta turo Abuja Gwarimfa……. “Ke! Wa yace ki tab’a min waya?” Shi ya dawo da ita daga suman wuncin gadin da ta tafi, ta ware ido tana kallonsa kafin ta ji saukar ruwa masu ‘dumi a kumatunta wanda ba ta raba ‘daya biyu hawaye ne. “Da gaske aure za ka yi Turaki?” Ya ‘dauke kai kamar bai jita ba, har ta furta ran zai amsa sai kuma ta ji muryarsa a sama yana cewa “Ko za ki hana?” 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍️ Takaicin Uba….. 60. Ya cigaba da b’alle mab’allan rigarsa yana hango fuskarta ta mudubi yarda kalamansa suka saka ta firgita kamar ta tsala ido. Bai bi ta kanta ba don da gaske ta ba shi haushi ya d’auke key ‘din motarsa da wayoyinsa yana zuba mata ido murya a cunkushe ya ce “Shall We?” Ayra ta saki ajiyar zuciya tana mik’ewa a kasalance ta yafa gyalen doguwar rigar da take jikinta ta mayar da siririn glasses ‘din idonta ta bi bayansa don tuni ya fice, tana fita ya ja musu k’ofa ya kulle. A mota suna tafe tunani ne kawai ya cunkushe zuciyar Ayra, sam bata son kishiya a rayuwarta ji take kamar ta bawa Turaki hak’uri Amma wata zuciyar na sake tunzirata. Ganin ta kasa jurewa ta fara jan yatsun hannunta tana fa’din “Turaki” bai kalleta ba ya amsa “Ya aka yi?” Ta kasa furta abinda ta yi niyya sai kawai ta mayar da kanta jikin kujera ta lumshe idonta tana jin yanayin yarda sautin zuciyarta ke bugawa, kuma kowane bugu da zuciyar tata zata yi da son Turaki a cikinta, wani kyau ya mata a zahiri a yau musamman yarda yake shan kunu da tsare gida irin na mazan da suka amsa Sunansu maza wanda ba sa ‘daukar raini a wajen matansu. Daga gani yau ta kai sa bango. Duk wani yanayi da ta shiga Turaki yana ankare da ita, sai dai ko a fuska bai nuna mata ba, illa cigaba da bin karatun Alk’ur’anin da ya yi cikin suraturrahman sautin karatun Sudais. Har suka isa gidan bai sake mata magana ba, duk da hango karaya k’arara a k’wayar idanunta, so yake ya nuna mata shine Mijinta kuma Miji ba abin wasa bane kada ta yi amfani da son da yake mata ta ce zata raina sa. Ya yi parking yana kallonta don bata san sun zo ba ta zurfafa cikin tunani, jin alamar idanunsa na yawo a jikinta ya saka ta bu’de lumsassun idanunta tana wara su a kansa, gaba ‘d’aya yanayin kallon da yake mata ya sake jefa zuciyarta cikin matuk’ar rauni da tsananin soyayyarsa, har zai yi magana sai kuma ya ‘d’auke kansa yana Unlocking motar ya fita cikin takunsa na k’asaita Ayra kam ta gane kurenta don da alama yau sarautar y’an mazan ta motsa. Jikinta a sanyaye ta fito ta bi shi da sauri a baya, saboda yarda filin gidan ya fara cika da mutane da dama. Har ya ‘dan yi nisa sai kuma ya dawo ya ja hannunta ya rik’e cikin nasa, ganin kamar idanun mutanen wajen duk a kanta suke. Tattausan hannnunsa da ya gamu shi ya saka su lumshe ido da sauri Suna jin bugun zuciyarsu na k’aruwa. Suna zuwa bakin k’ofar sashen Ummeey ya saki hannunta ya sake gimtse fuskarsa ya yi hanyar b’angarensa ya bar Ayra a tsaye cikin tashin hankalin yarda zata iya zuwa ta kalli fuskar Ummeeey da wani idon? Amma Turaki ya iya tsiya bai kyauta min ba, yanzu ne zan ce da jama’a. Gaba ‘d’aya kunya ta hana ta shiga har zuwa sanda dabara ta zo mata na kiran Tayseer a waya. Tayseer tana murmushi ta amsa mata “an gama Amarcin an tuna da mu?” Ayra d’an tsaki ta ja “Ke ban san magana, ina bakin k’ofa zo ki rakani ciki.” Tayseer tana dariya ta ce “Shi Ina angon naki ba zai rako ki ba?” “Ni dai ki zo na ce Malama.” Ta fa’da tana katse wayar. Tayseer ta saki murmushi kafin ta fito daga ‘dakinsu, ta tarar da duk iyayen nasu a babban parlour da su Ya. Deejah. Dariya Tayseer ta yi sosai ganin yarda Ayran take tsaye fuskarta cike da damuwa, kamar ta saka kuka ta ce “Su Ummeey suna nan ko?” Tayseer ta ‘d’aga gira, Ayra ta dafe kai ha’de da fa’din “Na ga ta kaina.” “Wai meye haka Ya. Ayra sai kace wata villager daga wajen mijinki fa kike Amma duk kin wani kin firgice kamar wacce ta kwana gurin saurayi, ki zo kawai ki maze ki shiga Ai suma sun san me zaki yi tunda suka muka aure.” Ayra ta girgiza kai “Ba zaki gane ba Tayseer amma mu je.” Ta fa’da tana sake jan mayafi ta rufe fuskarta. Sallamarta ya saka duk wajen suka d’ago kai suna kallonta Ya. Deejah ta ce “A’a ka ga Malaman Soyayya an dawo kenan?” Ayra ta watsa mata harara kamar ta saka kuka. Duk gurin dariya aka saka kafin Ummeey ta janyota “Taho nan rabu da su haka ake son Mace ta zama duk inda Mijinta ya saka k’afa tana nan, sai ki ga ta mak’ale a zuciayrsa shima ya kasa aikata komai idan bata kusa da shi. Kada wanda ya sake tsokanar min y’a.” Ayra ta ‘dan ji sanyi tana zama jikin Ummeeyn da k’arfi da yaji ta yiwa Amma fashin y’a. Adda petal dariya suka yi sosai kafin ta ce “Surikar zamani, kai Ummeey Ai kya bari mu yi miki kara?” Umeey ta girgiza kai “Rik’e kayarki karar in dai a kan y’ar ki ne, ga su nan da yawa na bar miki.” Wani farin ciki ya ratsa zuciyar Amma ta san tabbas Ayra ta dace da Uwar miji ta gari.” Tunda ya shiga bedroom ‘din sa ya kulle ya kwanta yana jin sam yanayin jikinsa ba da’di Ayra ce kwance a zuciyarsa amma ya lura yarinyar taurin kai ne da ita sai ya b’ullo mata ta bayan gida. Ya lumshe idonsa kafin wayarsa ta damesa da k’ara ya ‘daga yana ganin sunan Shaheedah na yawa a kan screen ‘din tsaki ya ja ka’dan yana tunanin shikkenan ya janyowa kansa yanzu zata fara damunsa. Da k’yar Ya kara wayarsa a kunnensa murya k’asa sosai ya ce “Hello Shahee ya aka yi?” Ta saki ajiyar zuciya kafin ta ce “I called you several times baka ‘daga ba, hope fine?” Ya saki ajiyar zuciya Zan kira anjima yanzu am busy.” Ya katse wayar kawai. Yana jiyo yarda gidan ya kaure da hayaniyar y’an na’din sarauta, tsaki ya ‘dan ja ka’dan yana sake lumshe idonsa. Ayra ta dinga bulayin neman ta ga ya shigo parlourn Ummeeyn amma shiru, Ummeeyn ma shirun nasa ya dameta ga kayansa da zai saka an kawo daga wajen masu aikin alkyabbar sarauta zuwa can da ta gaji da jiransa ta kalli Ayra ta ce “Maza Ayra Je ‘dakina kan gado da kayan Turaki ki kai masa ya shirya ya fita fada don tuni an fara hallara mu ma fita za mu yi, idan ya gama shiryawa sai ku tafi tare.” Ayra ta mik’e tana jin da’din Aiken da Ummeeyn ta yi mata ko bakomai zata gan shi har su yi maganar da za su yi. Haka ta ratsa corridor ‘din da zai sadaka da ‘dakin wajen shiru sai sanyin a’c da yake tashi da k’amshin turaren wuta. Ta mur’de handle ‘din k’ofar da zata shigar da kai ‘dakin da Turakin yake, lumshe idon ta yi tana shak’ar k’amshi turarensa da ya gauraye parlourn ganin ba ya parlourn kai tsaye ta nufi bedroom ‘dinsa ta mur’da k’ofar. D’akin ba haske dun’dum yake da duhu sai azababben sanyin A.c. Shiru Turaki ya yi duk da ya ji motsin mutum ya kuma tabbatar Ayra ce don jikinsa ya ba shi. Wayar hannunta ta kunna fitilar tana haska ‘dakin tana sallama a hankali. Hango shi ta yi a kan gadon don haka ta k’arasa a hankali da tunanin barci yake. Ta zauna bakin gadon tana sake haske kyakykyawar fuskarsa duk abinda take Turakin yana jinta ya yi shiru kawai yana amsar gashin da dafin idanuwanta yake saka shi jin wani iri a gab’bansa. Ta saka hannu a hankali tana ‘daukar wayarsa da take ta faman ringing tana jin wani takaicin ganin sunan Shahee yana yawo a kan screen ‘din. Ji ta yi kawai ya ja hannunta ya cire wayarsa ya kara a kunne yana magana k’asa k’asa. Ayra ta fara jin hawaye na neman zubo mata, Turaki ya juya mata baya yana kunna fitilar ‘dakin murya k’asa k’asa yana magana da Shaheedah. Kafin ya katse wayar ba tare da ya kalleta ba ya ce “Menene kika shigo min ‘daki, ko kin zo ki sake birkita min tunani ne?” Ayra ta lumshe ido tana girgiza kai “Ummeey ce ta ce na kawo maka kaya.” Ta fa’da muryarta na rawa ta sauka daga gadon sai dai kafin ta yi wani motsi ta ji ya fisgota ta dawo samansa ya saka hannu ya ‘Daga hab’arta yana kallo kafin ya kai yatsansa kan hanwayen da suke zuba a idonta murya a cunkushe ya ce “Tears? Na menene?” Ayra ta kawar da kanta. Sai kuma ya tab’e baki yana mik’ewa ya ce “Tashi ki tafi tunda kin kawo sak’on?” Zama ta sake yi a kan gadon fuskarta a ha’de ta ce “Cewa ta yi I should wait for you mu tafi tare.” “Ni kuma nace ki tafi.” Ta ‘dago tana kallonsa kafin ta mik’e jikinta a sanyaye tana tunanin yanzu Turakin ba ya sonta. Har ta kai k’ofa ta ji ya janyota yana ha’data da bango ya ce “Wipe those tears off Malama kafin ace na miki wani abin.” Kukan sosai ta saka Turaki bai hanata ba kawai samun kansa ya yi da tsura mata ido kafin ya saki ajiyar zuciya ya ce “Kee wai kukan me kike yi Malama?” Kawai sai ta fa’da jikinsa Turaki yaji wani yarrr a jikinsa tsawon lokaci yana jin yarda ‘dumin jikinta yake kassara duk wata garkuwa ta jikinsa. Ya ‘dan janyeta kafin ya ce “Ki min shiru in don nace ki tafi ne kike Kuka zo ki zauna.” Ta janye hannunta da sauri tana fita a guje. Turaki ya bi bayanta da kallo yanzu kam ya san meye damuwarta kishi ne shi kuwa ba zai fasa abinda ya yi niyya ba, haka kawai ya zauna da ita ita ka’dai ta kashe shi. Ko da ta koma ‘d’aki kwanciyarta ta yi tana jin yarda zuciyarta take k’una ga wani irin Soyayya Zazzafa da takewa Turakin da ta lumshe ido shi kawai take gani. Ta kowane side Turakin ya isa ya amsa sunan Mijin Ayra don shine mafarkinta tunaninta da kuma burinta! Ta ina zata hana shi aure? Shine kawai damuwarta a yanzu. Turaki ya fita wajen ya dinga zagaye idanunsa yana son ganin inda zai gan ta amma ba labarinta. Sai kawai ransa ya ba shi tana cikin ‘d’aki murmushi ya yi kafin ya hana zuciyarsa zuwa inda take. Da daddare ya samu Ummeey da Abeey d’insa zaune a parlourn Abeey ‘din su Amma suna sashen Umeeey. Kulawa da tarairaya Umeeeyn take ba shi don in dai suna tare bata son ya tuna yana da wata matar. Turaki cike da sha’awa ya dinga kallon yarda Ummeeyn take feeding Abeey ‘din ya shiga da sallama yana fatan su amince da abinda zai je musu da shi d’in. Ummeey ta amsa masa tana ‘dan janye jikinta daga abeey ‘din suka mayar da hankalinsu kan Turaki da ya durk’usa a gefe yana gaishesu. Sannan ya cigaba da murza hannunsa murya cike da damuwa ya ce “Abeey na samu mata zan k’ara aure….” Cup ‘din Hannun Ummeey ne ya sub’uce ya fa’di sabida yarda sautin bugun k’irjinta da ki’dima da ta shiga suka sanya hannunta rawa. Maganar ce ta zo mata a sama, ranta a b’ace ta soma kallon Turaki kafin ta saki murmushi wanda ya bayyana zallar b’acin ranta ta ce “Allah ya sanya alheri, a ina matar take?” 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊 Takaicin Uba… Nazeefah Nashe… Gangara💫 __________________ Kamilu ya ji da’di sosai da furucin Abeey, a yanzu kam tabbas yana tausayawa ‘dan uwansa abinka da jini da shi yake kwana kuma yake tashi a ransa don haka ma suka shirya da Jummai a kan su biyo Talatun har a Gombe duk da ba su san y’an uwanta ma aka gani ba, sai bayan zuwansu hakan yasa Kamilu ya ga ba abinda ya dace irin ya saka dangin Talatu su sake rok’a masa ita ta yafewa Kabiru don hakika yana cikin jarrabawar rayuwa kuma daf yake da rasa rayuwarsa. Duk sanda kuma zaka je wajensa rokonka zai yi ka nema masa afuwar Talatu ko zai samu sassauci a cikin kabari, duk abokansa sun gujesa Hadi ma yana cikin bala’in rayuwa ya dawo kamar almajiri saboda rashi, ga abin kunya da ya faru a gidansa ta yarda ‘dansa ya yi lalata da y’arsa har ciki ya bayyana duk Shagogo an ‘dauki maganar Y’ay’an Hadi sun yi lalata da junansu, har ciki ya shiga wannan shine abinda ya saka Hadin shima ya fa’di warwas. Sanda Jummai take gayawa Talatu murmushi kawai ta yi ta ce Hakkine Ai shi Allah ba azzalumin sarki bane ka’dan ma ya gani.” Jummai dai Shiru ta yi bata sake magana ba. Kamilu ransa wasai ya mik’e ya fice daga parlourn da suke ganawa da S.Turakin. Yana jin kamar warakar ‘dan uwansa ta zo. _______________ Ya ja bargon da sauri Ayra ta sake ja tana k’udundune jikinta fuskarta ‘dauke da murmushi duk abinda ya wakana a daren yana dawo mata tiryan-tiryan da irin kalaman da ya dinga gaya mata a kunnenta masu saka nisha’di ba wanda ta rik’e irin yarda yake ce mata “Ba Shaheedah ba har abada Ayra Wallahil azeem ba zan miki kishiya ba! Ni ka’dai na san irin ni’imarki da na ‘dan’dano please ki min alk’awarin ba za ki sake min rowar kan ki ba.” Ta ‘dan lumshe idonta Turaki yana tsaye yana sake bin ta da kallo ji yake kamar ya mayar da ita ciki ya huta da zazzafar k’aunarta da take masa walagigi da zuciya “Tashi mana, Sweet ko so ki ke na koma ruwa.” Da sauri Ayra ta mik’e tana kawar da kanta don bata son ha’da ido da shi. Ya jawota jikinsa yana ‘dago hab’arta ya ce “Kunyar ta mecece? Bayan kin gama rikita min kwanya.” Ta sake runtse idonsa Turaki murmushi kawai ya yi yana ha’deta da jikinsa ya sake rungumeta tsam yana sakin ajiyar zuciya ya ce “Allahumma barik, Allah ya sake ninka miki ni’ima akan ni’ima ki dinga hauka tani kina susutani sai ki ji ana Turaki ya koma Mijin kan ta ce.” Ayra dai ba ta yi magana ba illa sake k’udundune kanta da ta yi tana sake jin k’amshin jikinsa da yake tado mata duk wani dafin k’aunarsa Turakin ma lunshe idonsa ya yi yana jin dama su dawwama a haka har abada ba zai tab’a gajiya da jinta a jikinsa ba.” Tsawon mintoci kafin Ayra ta zame jikinta tana duban agogo ta ware ido ganin k’arfe 11:00 shima idanunsa ya kai kan agogon ya ‘dan ware ido ganin lokaci ya ja. “Ayra kin shigesu? Me za ki ce da mutane?” Ya fa’da yana kwaikayar maganarta. Da sauri Ayra ta bi shi tana cillinsa da pillow har kan gadon da ya koma, yana ganinta ya sake janta jikinsa yana fa’din “Shikkenan kin sake kawo kan ki.” Ayra ta bu’de baki Zata yi magana ta ji kawai ya Aika mata wani salo da ya sata jan bakinta ta k’unshe don ta kasa bijirewa Turaki lamarin mai girma in dai har ya cigaba da yi mata haka bata jin zata iya bijirewa umarninsa zata bi shi sau da k’afa fiye da tunaninsa. Ummmeey dai da ta gaji da jiransu kawai sai ta aika musu da abincin breakfast parlournsu ita ka’dai ta dinga sakin murmushi don ko bakomai burinta ya gama cika, Ayra da Turaki sun zaman tif da taya. Daga haka ta ja Amma suka nufi fa’da gaida mai martaba da su Deejah da suke shirin tafiya ranar su kuma su Amma da su Ummmeey sai jibi za su rankaya su koma Kano. Sanda suka je gaida Maimartaba yana murmushi ya mik’e yana amsa gaisuwar su kafin ya kai dubansa kan wazirinsa yana fa’din Kaya ya tsinke a gindin kaba ga Talatun da kake min magana a kanta.” Waziri ya kai dubansa kan Talatun yana murmushi ya ce “Ai mun gama magana da kai, ka ce in dai har ka isa da ita kada na ji komai.” Haka kawai sai Talatu ta ji gabanta ya fa’di ta zauna dai jiki a sanyaye tana gaishe da maimartaba Ummeey da fulani kuwa sai murmushi suke don sarai sun gane inda maganar Maimartaba ta dosa. Bayan gaishe-gaishe Maimartaba ya dubi Talatu yana murmushi ya ce “Alhamdulillah Y’ata na miki mijin in dai ban miki shigar sauri ba.” Da sauri Talatu ta sunkuyar da kanta tana jin wata fargaba na dirar mata ita fa ko kalmar aure bata son ta ji an ambata mata balle ina zata kai aure da shekarunta da komai duk da shekarun sun yi gaddamar nunawa a jikinta. Sai dai ba zata iya kallon idon maimartaba ta wofintar da maganarsa ba musamman yanzu shi take kallo a matsayin Uba mahaifi. “Waziri ku daidaita da ita in dai har ta amince a gobe juma’a zan saka a ‘daura muku aure In sha Allah.” Murna ce ta bayyana a fuskokinsu gaba ‘d’aya har su Deejah in dai Amman zata yi aure a inda zata huta suna murna da haka don ko bakomai ya cancanta Amman ta ji da’din da ake samu a rayuwar aure in dai ka yi dace da Miji na gari, don haka zuciyoyinsu ba su ji komai ba sai na murna suka yi za kuma su rok’i Amman ta amince ko da zuciyarta bata so. Suna ganin hakan shi zai k’ara mata kima da martaba a idanun mutane tunda dai ba wuce auren ta yi ba. Mai martaba ya sallamesu sai dai kafin su tashi Kamilu ya rok’i alfarmar yana son magana da su. Suka zauna duk da yana jin nauyin maganar bai b’oye komai ba ya shiga rattabowa maimartaba duk irin halin da Kabiru yake ciki ya kuma bawa Maimartaban labarin abubuwan da suka faru da. Ran mai martaba ya b’aci sosai da jin wannan labari da ya kira da bak’in labari fuskarsa a ‘daure tamau yana duban Kamilu ya ce “A haka kake son kuma su yafe masa? Bayan wannan tozarcin da ka zayyano ya musu?” Kamilu ya rausayar da kansa ya ce “Ba don halinsa ba za su yafe masa ba, sai don suma su sauke hakkinsa da yake kansu kamar yarda Ubangiji ya musu umarni idan banda haka Kabiru bai cancanci yafiya ba.” Maimartaba ya yi tsam da ransa yana jin zuciyarsa tana tafasa ya kalli Kamilu ya ce “A gobe nake son ganin Kabiru a gabana, zan nuna masa dangin Talatu zan kuma ‘daura mata aure da mutum mai nagarta mai arziki a gabansa zan nuna masa gidan da Talatu zata je ta yi aure ta huta sannan idan ma yafiyar zata biyo baya sai su yafe masa tunda a yanzu sun masa fintinkau Allah kuma ya nuna masa isahara. Ashe har yanzu Akwai masu halin dabbobi irin Kabiru? Tabbas ban da darajar yara sai na saka an kulle shi sai dai yanzu ma bai tsira ba don abinda zan masa sai ya gwammace d’aurin rai da rai. Zan bada motoci a ‘d’aukoshi da abokin nasa, a kuma ‘dauko jama’ar garin ko da su ashirin ne su gani su shaida Talatu ba matsiyaci ya bace da gatanta.” Ba wanda ya yi magana ganin yarda ran maimartaba ya kai k’ololuwar b’aci, bai kuma sake bi ta kan Talatu ba don ya shirya aurar da ita da sonta ko babu. Burinsa yanzu ya inganta rayuwarta ta samu duk gatan da ta rasa a lokutan baya. Nan da nan Maimartaba ya saka aka ha’da manyan motoci don tafiya k’auyen Shagogo. Waziri kuwa jin wannan labarin bai saka ya ji son auren Talatun ya fita daga ransa ba, sai ma wata tarin k’aunarta da ya ji ta sake shiga ransa don a rayuwarsa burinsa ya auri Mace mai hak’uri sab’anin nasa matan guda uku da suka zama duk marasa hak’uri. Ya sake daidaita zamansa a kan kujerar da take fuskantar Talatun a parlourn Maimartaba. Murya cike da nutsuwa da dattijantaka ya ce “Ki amince da aure na Talatu ba za ki yi nadama ba, na yi alk’awarin baki farin cikin da kika rasa a baya zan nuna miki aure suna ya tara zan ‘daga darajarki in baki kulawa ta musamman matsalolin yaranki za su zama nawa zan kuma basu kulawa kamar yarda Zan bawa yaran cikina.” Talatu ta yi shiru tana wasa da zoben hannunta haka kawai sai ta ji tana kunyar fuskantar mutumin kwarjininsa da kyawun kamalarsa yana sake rikitata ainun, ga wani irin fa’duwar gaba da take ji a duk sanda ta ji sautin muryarsa abinda bata saba ji ba idan tana tare da Kabiru “Kin amince?” Ya fa’da a hankali yana rankwafowa yana kallo fuskarsa. Talatu ta kawar da kai tana sakin murmushi a hankali ta ‘d’aga kanta. Waziri ya furta “Alhamdulillah yana sakin ajiyar zuciya, burinsa zai cika na samun kammalalliyar mace mai tarin nutsuwa da kamala kamar yarda ya da’de yana fata. “Allah ya yi albarka a aurenmu yasa ace gwara da aka yi.” Talatu ta amsa a zuciyarta sai kunyarta ta sake burgesa don ya na cikin kammaluwar mutuncin y’a mace ta zamo mai kunya. Da zai tafi sai da ya ajiye mata ku’di dollars ‘din America Talatu ta amsa hannu bibbiyu don da kunya ta ce ya bar shi. Waziri ya sake jin kansa a sama don abu ne da bai saba gani ba matansa ba sa saka hannu bibbiyu idan zai ba su abu. Ya saki murmushi kawai yana jin kamar ya janyo Talatun ya rungumeta ya fita daga parlourn a zuciyarsa yana furta “Na ji a jikina yanzu zan yi aure” Talatu ta shiga cikin gida haka kawai sai ta samu kanta a cikin tarin farin ciki da walwala. Musamman da ta sake ganin fuskokin yaranta suma cike da walwala. Ta zauna a cikinsu Ummeey tana waya da tailor a kan ya kawo mata rantsatstsen lace da ya amsa sunansa lace kuma ready made take so. Tana kashewa ta sake janyo waya ta kira mai gyaran jiki. Da sauri Talatu ta kalleta “Haba Hameeda sai kace wasu yara?” Ummeey ta Zuba mata harara “Sai kin tashi tsaye matansa da kike gani kilallune idanunsu a bu’de yake taryau, sai an yi miki gyaran jiki na sati biyu don haka ba yanzu ma za ki tare ba sai mun gama shirin mu.” Talatu ta zuba mata harara tana nuna mata yara. Ummeey sai ta saki murmushi kawai tana fa’din “To bari za mu saka labulai.” Lokacin Turaki ya shigo shi da Ayra da take sunnewa a bayansa. Ba wanda ya mata magana hakan yasa ta ‘dan saki jiki bayan sun gaishesu ta ‘dago tana kallon Deejah ta ce “Wai murnar me kuke ne? Na ga kuna ta dariya.” “Gobe Amma zata yi aure da wazirin Gombe.” Cak numfashin Ayra ya tsaya ta kafawa Deejah ido cikin b’acin rai ta ce “Ban gane ba, Auren lafiya? Gaskiya a’a…..” 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝖓𝖆𝖘𝖍𝖊✍️ Takaicin Uba…. Nazeefah Nashe✍🏽 Saura k’iris☺️ Gaba ‘d’aya wajen suka zubo mata ido, cikin jin mamakin furucin da ya fito daga bakinta. Majeeda ta wurga mata harara ha’de da fa’din “Ban gane a’a ba Malama, Auren ne ba zata yi ba ko me?” Ayra ta sake zumb’ura bakinta kafin ta isa kusa da Amman ta rusuna a gabanta tana dafa cinyoyinta ta ce “Ki ce min ba haka bane Amma, don Allah kada ki yarda da wani aure a yanzu da shekarunki suka riga suka ja, ba zan jure ganin namiji na wulak’anta ki ba kamar yarda Babanmu ya wulak’anta ki.” Wannan karan Zainab ce ta fusata a zafafe ta ce “Sannu uwarta, waye ma ya gaya miki duka maza sunansu ‘daya Ai yanzu da kika yi auren kin fahimci na ki mijin sab’anin halayen Uban mu ne da shi, don haka aure fa kamar ta yi ta gama tunda har aka samu mai sonta duk da tsufan nata, ke ki ke ganin ma ta tsufa shi gal yake ganinta.” Ayra ta sake gyara zama a jikin Amman wannan karan sosai idanunta suke zubar da k’walla gaba ‘d’aya Turaki ya ji zuciyarsa ta cunkushe ganin yarda kowa ya taso mata ya dinga jifansu da wani irin kallo a zafafe sai dai su ba su san ma yana yi ba. Sai ganinsa kawai suka yi a gaban Ayra yana mik’a mata Handky murya a cunkushe ya kalli Zainab ya ce “Kowa ya fa’di ra’ayinsa Ai itama sai ku barta ta fa’di nata dalilin Ban ga dalilin wannan hayaniyar ba.” Zuba masa ido suka yi har Ummeey da ya kusan bata dariya ganin yarda ya ha’de rai kamar ba da surikansa yake magana ba. Jin Ayran ba zata yi shiru ba yasa shi jan ‘dan k’aramin tsaki ya saka kai ya fice daga parlourn. Amma murmushi ta yi wani farin ciki yana ‘darsuwa a zuciyarta ta san ko yanzu burinta ya cika Ayranta ta samu Miji irin wanda ta da’de tana mata fatan samu. Mijin da ake kira ‘d’aya tamkar da dubu. Mijin da zai kula da lamarinka ya kuma baka farin ciki ko a gaban waye. Ummeey ce ta dafa Ayran murya can k’asa ta ce “Tashi daughter tashi rabu da su mu yi magana.” Ayra ta koma jikin Ummeeyn tana cigaba da hawaye gaba ‘d’aya zuciyarta ta jagule bata son wani zancen auren Ammanta. Mu je ‘daki saboda y’an saka ido” Ummeey ta fa’da tana jan hannun Ayran suka tafi ‘dakinta. A gefen gado ta zaunar da ita murya a tausashe ta ce “Kina son damuwa da ka’dai ci su saka Amma ta samu ciwon zuciya?” Ayra ta girgiza kai “Yauwa, to ki k’yaleta ta yi aurenta, don a yanzu mai ‘debe mata kewa take nema, mai saka ta nisha’di saboda ta doshi shekaru 45 idan ba ta yi aure ba zata iya shiga damuwa kuma wancan tabon da Kabiru ya yiwa zuciyarta ba zai goge ba, Baba Waziri kuwa na tabbata zai bata dukkan kulawa ya saka mata farin ciki a zuciyarta walwalar ta zata dawo zata ji da’din da ta rasa a shekarun baya, k’warin gwiwa za ku bata ba ki sagar mata da gwiwa ba. Kin ga ba ke a kusa ba kowa damuwa zata mata yawa ga yanayin ciwonta ba’a son ta shiga damuwa auren Baba Waziri kuwa zai saka ta manta da waccan bak’ar rayuwar kin gane?” Ayra ta ‘d’aga kai tana sauke wata nauyayyiyar ajiyar zuciya duk wani kulli da b’acin rai na zuciyarta ya silale ya bi iska, Ummeey ta bata courage da gasken gaske ta ji ta samu nutsuwa ta kuma fahimci cewa tabbas auren shine abinda ya dace da Amman yanzu. Ummeey ta saki murmushi tana jan kumatunta ta ce “Kin amince yanzu?” Ayra ta ‘d’aga kai tana murmushi “Good girl, kada ki sake nuna mata damuwa kin ji?” Ayra ta sake sakin murmushi tana fa’din “In sha Allah.” “Yauwa amaryar Turaki mu je ki cire mata shakku ta gane kin amince da auren na san zata ji da’di yanzu kuwa Kuka Ki ya saka ta samu rauni.” Suka mik’e tare hannunta cikin na Ummeey suka nufi falon fuskar Ayra ‘dauke da murmushi ta fa’da jikin Amma tana fa’din “Ammata Am happy for you, Allah yasa auren Baba Waziri ya zame mana alheri.” Amma ta saki ajiyar zuciya tana jin damuwarta ta kau, da kam zuciyarta ta ji ba da’di duk da ta yi na’am da auren sai dai idan har Ayra bata amince ba itama Zata turesa gefe yanzu kuwa sai ta ji ta samu sukunin zuciya ta rungume Ayra tana fa’din “In sha Allah Autata.” “A’a fa ki canja Auta wannan ba autar Ki ba ce ga Tayseer nan na bar miki Ayra autata tace” Ummeey ta fa’da tana dariya shikkenan aka cigaba da zancen auren Amma da y’ar walimar da za’a ha’da mata ranar da zata tare. Turaki dai tunda ya lek’o ya ga Ayra ta saki jiki sai ya ji hankalinsa ya kwanta ya fita k’arasa ragowar harkokinsa don so yake a jibi ya tafi turkey kafin ya dawo ya sake tafiya da Ayra. ______________ Lamarin Allah da girma yake kuma kowa ya ja da girman Ubangiji ya yi asara. A ranar juma’ar da za’a d’aura auren Motocin da suke d’auke da ahalin Kabiru suka iso daga garin Shagogo. Tunda suka shigo fadar gaban Kabiru yake fa’duwa bai san me Suka zo yi ba tunda Kamilun bai gaya musu ba sai dai gaba ‘daya jikin sa a sanyaye yake. Matarsa Mai da’din na gefensa sai cika take tana batsewa ‘d’aya daga cikin yaransa maza su takwas shine ya yi k’ok’arin biyosu don shine mai ‘dan dama-dama a cikinsu yake ‘dan kula da Kabirun wani Sa’in. Sai sauran ahalin gari ciki kuwa har da Maigari da shima tsufa ya kama sa da k’yar ma yake tafiya sai yayyen Talatu da suka ha’da Uba ‘daya. Jabiru ma ranar ya diro garin don Amman ta gaya masa maganar auren ta waya. Sai dai bai iso fadar ba so yake sai gaf da ‘daurin auren ya yiwa su Kabiru shigar bazata ya ga da wani idon Kabirun zai kallesa. Fada fa ya cika mak’il da Sarki ya bada sanarwar a yi shela akwai ‘daurin auren Wazirin Gombe da za’a yi bayan sai kowa daga masallachi. Amma suna cikin gida ta sha Ubansu lace an kuma na’deta da laffaya da ta sha gabbasa sai zabga k’amshi take. Fuskarta ta sake kyau sosai sam ba zaka ce ita ce ta zubo yaran nan mata da jikoki reras ba, ko don auren wuri aka mata sannan tana da k’aramin jiki irin na fulani. Fatarta ta sake murjewa ko don ta fara gyaran jiki ne. Su Ayra ma gaba d’aya sun sake kwalliyarsu cikin rantsatstsen lace da ya mata kyau sosai. Tun a jiya Kuma ta gujewa Turaki don ba k’aramin Gurzuwa ta yi a hannunsa ba ranar. Tun yana aikowa a kirata har ya zo da kansa Amma Ayra ta yi k’ememe da gaske har lokacin bata saba ba tsoron Turakin take ji don ta lura ba sanya a lamarin sa. Yanzu ma tsaf ya shigo cikin farin yadin filtex babbar rigar a hannunsa bai saka ba sai zabga k’amshin turare yake ya shiga parlourn Ummeeyn inda duk suke zazzaune idanunsa a kan Ayran da ta masa wani fitinannen kyau har bai san sanda ya shagala da kallonta ba sai da Ummeey ta yi gyaran murya sannan da sauri ya ‘dauke kai yana ‘dan sosa k’eya ya maze yana fa’din “Ayra zo mana 2 minutes.” Ayra ta ‘dago da sauri tana kallonsa ya ‘d’aga mata gira ‘d’aya abinda ya zame masa jiki sannan ya juya abinsa yana fa’din “Yi sauri ana jira na sak’o zan ba ki.” Ayra na jin haka ta mik’e a hankali tana sake yafa gyalenta don kayan ba k’aramin cikata suka yi ba har mamakin kayan ta yi da alama k’iba ta k’ara don sanda aka ‘dinka lace ‘din duk da fitted gown ne bai matseta haka ba. Ta bi bayansa cikin jin kunya duk da ba wanda ya lura da abinda take. Bata gansa ba a babban parlourn tana juya ta jita a jikinsa ya mata wata kyakykyawar runguma yana fa’din “Na kama mai gudun Miji.” Da sauri Ayra ta bu’de ido tana k’ok’arin janye jikinta ya sake rungumeta tsam a jikinsa “Bari mana, kin san irin wahalar da kika ba ni daga jiya zuwa yau.” Ya fa’da mata cikin ra’da a kunnenta Ayra idanu ta ware ganin yarda ya kama lips ‘dinta yana tsotsa. Tsawon lokaci kafin ta ji ya ‘dagata cak ya yi b’angarensa da ita “Ka bari kada wani ya gan mu.” “And so what? Haramun na yi?” Ya fa’da yana kaiwa karan hancinta sun bata “Mu je ki yi biyan bashin da kika ci jiya.” Ya fa’da yana tura k’ofar ‘dakinsa da k’afa sannan ya direta yana bin ta da kallo yarda rigar ta fitar da duk wata sura ta jikinta tuni wani kishi ya zo ya tsaya masa a zuciya a hankali ya ce “Bala’i, hope ba wani k’aton da ya gan ki a haka?” Ayra ta dubi jikinta a kunyace tana girgiza kai ganin yarda yake bin jikinta da kallo kafin ya saka hannunsa ya kai in da yake Tsole masa ido “Da kin cuceni idan aka ce wani banzan ya ga wa’dannan kayan nawa. Kada ki sake saka irin wannan kayan in dai ba daga ni sai ke ba.” Ya ja hannunta suka isa gaban mudubi yana fa’din “Kalli kan ki ki ga irin surar da Allah ya ba ki ba namijin da zai gan ki ya kasa raya wani abu a zuciyarsa don haka Blacks Hijabs d’in da kika saba sakawa su za ki cigaba da sakawa nik’abs and socks don zan iya aikata komai akan wanda ya yaba min surar jikin ki.” Ayra dai Shiru ta yi tana jinsa ya sake janta jikinsa yana budirinsa shi ka’dai tun tana iya jurewa har ta gaza jikinta ya soma rawa ba shiri Turaki ya ‘daga cak zuwa kan gado……. Yana busar mata da kai bayan fitowar su daga wanka ya kalleta yana fa’din “Ma sha Allah Matata mai kyauce In and out, fa’da min menene sirrin?” Ayra ta saki murmushi har hab’arta tana lotsawa ta ce “Ba wani sirri, ka yi sauri ka tafi kada ka makara ‘daurin Aure.” Ya janye jikinsa yana fa’din “Ina zuwa.” Waya ya ‘d’auka ya kira Tayseer yana gimtse muryarsa ya ce “Ki samo wa Ayra wasu kayan, ki ha’do da Black Hijab d’inta da nik’ab.” Ayra ta Zuba masa ido “Me Zan Yi da Hijab kuma yau?” “Abinda kike yi da shi da, ai ni yanzu na san amfaninsu ban da su na tabbata da maza ba zasu barki ba idan ba su dinga bin ki suna miki fya’de ba, oh ni Aminu da an cuce ni.” Ya fa’da yana rik’e hab’a Ayra bata san sanda ta shiga tuntsira dariya ba ganin yarda yake kwaikwayar mata shima murmushin ya saki ya ce “Zan yi missing ‘din ki gobe zan wuce turkey zan dawo idan An gama tariyar Amma sai ki musu sallama ke da su kuma sai Baba ta gani ba mamaki sai kin haihu. Yanzu ni matsalata ya zan yi da tarin sha’awarki?” Ayra da sauri ta rufe fuskarta da tafukan hannunta ya dafa kafa’dar ta yana rankwafawa wuyanta ya ce “Am serious kin Riga kin shayar dani wata irin zuma mai da’din da ba kwatance sai dai a yi kurum kawai ga visar ki ta turkey bata kammala ba, ga shi ina da tarin ayyuka a can. Ni dai Aminu na ga ta kaina Wallahi na jangalowa kai na.” Ya fa’da yana goga kumatunsa a nata. Ayra ta lumshe ido tana jin itama tun a yanzu ta fara kewarsa ga shi zuciyarta ta kasa yarda akan cewa ba su rabu da Shaheedah ba, don haka cikin raunin zuciya ta ce “Ba ga Shaheedah ba sai ka aureta kawai.” Ya bita da kallo yana mik’ar da ita tsaye ya ce “Shaheedo ba Shaheedah ba ba ki yarda da alk’awarin da na miki na ba ke ba kishiya ba ko? Ko kin zata duk a cikin giyar jin da’di na yi furucin to it’s true from the buttom of my heart ke ce Uwargida kuma amaryar Aminu da ga ke ba k’ari idan da wata ma ta narke.” Wani farin ciki ya kamata har bata san sanda ta kankameshi ba tana ba shi wani irin tattausan kiss leb’ensa Turaki ya lumshe ido yana jin wani farin ciki na ratsa sassan jikinsa tunda yake aurensa bai tab’a karo da mai zazzak’a tattausan lab’ba kamar Ayra y’ar mutanen Gaya ba. Ayra ta zare leb’en tana d’auke idonta ganin yarda Turakin ya lumshe ido ya rik’o hannunta murya a sark’afe ya ce “I need more….” Da sauri Ayra ta ja jikinta tana jan towel ‘don da yake son zamewa ta ce “Ana knocking.” Turaki ya kasa motsi daga yarda yake sai Ayran ce ta zura Hijab ta je bu’de k’ofar. Tayseer da take tsaye da kaya a hannu tana kallon Ayran ta ‘dan k’unshe dariyar da take son kamata ta ce “Juliet ta romeo..” Ayra ta k’wace kayan tana harararta ta sake mayar da k’ofar ta rufe tana shirin saka kaya amma Turaki ya nuna bai san wannan ba don dole ta sake hak’ura ta biye masa. Kafin ya sake wanka ya shirya a gaggauce ya fice ‘daurin auren surikarsa. Ayra ta bi bayansa tana murmushi zuciyarta wani farin ciki take ji mara misaltuwa ta tabbata dai ta k’wace zuciyar Turakinta har abada ta cire masa kwa’dayin kowace y’a mace a cikin ransa. __________________ Fadar ta sake d’inke wa dank’am su dai su Kabiru sai baza ido suke don har a lokacin ba su san me ya kawo su wannan aljannar duniyar ba. Ga manyan mutane da suke sake cika a fadar kowa cikin shiga ta kece raini sai busar algaita ce kawai take tashi a wajen. Daidai lokacin Liman ya gyara zama ya ce “Za’a d’aura auren Maimartaba Waziri wanene waliyyin amaryar?” Mai martaba ya dubi mutanen Shagogo ya ce “Wanene zai zama Wakilin Talatu daga cikin ku?” Gaba ‘d’aya mutanen Shagogo suka zubo ido cikin mamaki Mai gari ya ce “Wace Talatun?” 𝖏𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍️💫 Takaicin Uba….. Bakin da Allah ya tsaga….. Mai Martaba yana murmushi ya zuba idanunsa cikin na Kabiru ya ce “Talatu dai Talatun Kabiru…” Kabiru ya ji kansa yana juyawa kafin ya yi wani yunk’uri suka ji sallamar wani bafade yana fa’din “Ranka ya da’de akwai bak’o yana neman iso. Ya ce a ce maka sunansa Jabiru.” Mai martaba ya ‘d’aga kai don Talatu ta sanar da shi zuwan Jabiru “Ka ba shi izinin shigowa.” Sannan ya sake mayar da kallonsa kan Kabiru da ya yi mutuwar zaune yana jin wani sanyin nadama da dana sani yana kwaranya a b’argo da gangar jikinsa, a yau ya tabbata mara rabo a duniya idan bai yi wasa ba har a lahira matu’kar Talatu da ahalinta ba su yafe masa ba. Jikinsa ya fara rawa ya fara jin tsanar kansa musamman ganin kallon da jama’ar wajen suke binsa da shi wanda yake bayyana yarda suke Allah wadarai da halinsa ya tabbata gaba ‘d’aya labarinsa ya gama bazuwa a duniya. To tun fa anan kenan ina ga An je lahira yarda za’a tara mutane a sanar da su abinda ya aikata a kuma nuna musu su gani da idanunsu ya dafe kansa da ya ji yana sara masa kafin ya ce “Ya Allah ka yafe min.” Sai kuma ya runtse idanun nasa yana jin yarda hawaye suke kwaranya a idanunsa kamar an kunna famfo Kaico na ni Kabiru sharrin zuciya da son duniya na biyewa da kuma bin zugar aboki ya Allah ka yafe min ka tausashi zuciyar Talatu da yaranta su yafe min….” Sallamar Jabiru ce ta dawo da shi daga duniyar tunanin da ya lula. Yana ganin Jabiru ya ganesa don kullum da tunaninsa yake kwana yake kuma wuni da kuma mafarkin sa don haka duk canjawar da Jabiru zai yi ba zai rasa shaida sa ba. Zuciyarsa ya ji tana neman wuntsilowa daga k’irjinsa da ya tuna bai san da me Jabiru shi kuma ya zo ba. Jabiru ya k’araso cikin shigarsa ta kamala ta had’adden yadin fitex da aka masa ‘dinki iya gwiwa sai gajeran hannu da ya sake bayyana dattijantakarsa sai dai idan ka gan shi ba zaka je zai lamushe shekaru arba’in da ‘doriya ba, saboda yarda shekarun suka yi gaddamar nunawa a jikinsa da kamanninsa. Fuskarsa ba walwala sosai ya shiga fadar inda hankalin y’an shagogo gaba ‘d’aya ya dawo kansa. Ba za su mance da fuskar Jabiru ba fuskar da suka kora suka yi wa tofin Allah tsine. Jabiru ya zubawa Kabiru ido yana jin duk wani b’acin rai da ya taho da shi ya na zagwanye wa kamar aikin sihiri. Bai sani ba ko don ganin Kabirun a cikin wani hali na abin a tausayawa gaba ‘d’aya k’afafunsa sun shanye da alama kuma b’arin jikinsa ba ya aiki ma’ana ya samu paralyze. Sai dai yana kauda idonsa sai ya dinga hango hoton wancan lokacin da Kabirun yake cikin tashensa har yake aikata musu rashin mutuncin da ya ga dama. Idanunsa suka sake hasko masa ranar da ba zai tab’a mantawa da ita ba ranar da Kabirun ya runtse idanunsa ya musu sharri shi da Talatu matar da yake ‘daukar ta kamar mahaifiyarsa. Murya a cunkushe cikin ‘dacin rai ya yi furucin “Ba zan tab’a yafe maka ba.” A hankali yarda kowa ba zai ji me yake cewa ba. Sannan ya durk’ushe gaban Mai martaba yana jin kamar ya tashi ya shak’e Kabiru da ahalin da suka rakosa daga Shagogo. Da idanunsu ya dinga bin su da kallo ‘d’aya bayan ‘d’aya jin suna ambatar sunansa cikin mamaki suna fa’din “Jabiru dama kana raye?” Ya d’an saki murmushi mai ciwo kafin ya ‘daga musu kai yana mayar da kansa a kan Maigari yana tuno idanun Maigarin da suka dinga masa kallon tausayi sanda y’an garin suka jefe su da wancan mummunan sharrin. Murya a tausashe ya sunkuya gaban mai garin yana gaishe sa. Maigari ya d’an yunk’ura a hankali yana dafa Jabirun ya ce “Hukumullahi La ajabun, jama’a kun ga ikon Allah ko? Kun yarda da girman Allah ko? Ga shi nan cikin shekaru k’alilan Allah ya sauya rayuwar bayin Allahn nan, Wanda da ba’a yi musu duk abinda aka yi musu a Shagogo ba da tabbas ba su samu albarkar da Suka samu a rayuwarsu ba, a yau na yarda da maganar Malam bahaushe da yake cewa Wani Hanin ga Allah baiwa ne. Kabiru kai kuma ka ga ishara kai da abokinka ga shi nan tun a duniya ubangiji ya k’ask’antar da ku ya kuma fifita Talatun da Jabirun zuwa wani matsayi da baku isa ku taka shi ba.” Mai martaba ne ya yi gyaran murya jin wajen yana neman ya kaure da hayaniya ya ce Liman ya ‘daure aure. Ai kuwa nan da nan aka ‘daura auren Talatu da Baba Waziri akan sadaki dubu ‘dari biyar lakadan ba ajalan ba. Lamarin da ya sake gigita Kabiru da mutanen Shagogo jin yawan sadakin da kuma irin Mijin da Talatun da zata aura. Zuciyar Kabiru ta sake nauyi yana jin da yana da iko da ya tariyo Rayuwarsa ta baya ya gyara abinda ya gurb’ata a cikinta, sai dai tuni wannan damar ya kufce masa ya Riga ya aikata abinda ba zai tab’a gyaru wa ba har yaumuttanadi. Yarda wajen ya yamutse da hanayaniya da ihun marok’a yasa wani ba ya jin abinda na kusa da shi yake cewa har sai da Maimartaba ya tsawatar sannan ya mayar da kallonsa kan Kabiru ya ce “A da na yi niyyar idan aka kawoka na ‘daureka anan ‘daurin da ba me iya belinka a bursuna, amma a halin da na ganka na tabbata hukuncin Allah ya Riga ya sauka a kan ka tunda yanzu Allah shi tun a duniya yake hisabi saboda ba ya yafe hakkin wani a kan wani, haka ka’dai da Allah ya mayar da kai ya isheka ishara ya kuma nuna maka girman Hakkin Talatu da ka ci ba na wasa ba ne, ba’a tab’a bayin Allah Ubangiji ya kyale, saboda Allah da kansa yakewa bawansa yak’in musamman idan bawan nasa ya zama mai mayar da dukkan lamarinsa gareshi sai Allah ya dinga masa yak’i a kan duk wani abu na cuta da zai tunkaro shi ba boka ba Malam sai ka ga mutum ya gagari mak’iya da mahassada har a yi zaton da wani abu da yake aikatawa ta bayan fage alhali ba abinda yake aikatawa sai tsananin dogara ga Ubangiji da mayar da dukkan lamarinsa gareshi don haka y’an uwa mai rik’o da addini da bin abinda Allah ya umarcemu da kuma gujewa sab’a masa shine abinda zai sa ka ka gagara irin gagarar da za ka ji ana Ya gagari gasa. Zan saka Talatu da yaranta su yafe maka har Jabiru ma don tun a duniya ka ga shaida girman hakkin wani ka kuma shaida Allah yana amsa addu’ar wanda aka zalunta don ka zaluncesu kuma na tabbata daka zaluncesu sun yi addu’a sun ce Allah ya saka musu ga sakayyar nan ka na gani Allah yasa y’an baya su yi koyi da darasin da ya sameka idan suna da niyyar cin zali su san ba abu bane mai kyau. Allah ya kyauta yasa kuma wannan ya zamewa duk wani mai hali irin naka Ishara.” Kabiru da Hadi sunkuyar da kansu kawai suka yi Jabiru ma ya sake bin su da kallo ya ji har a zuciyarsa ya yafe musu don a yanzu sun zama abin tausayi duk da ba a san gawar Fari ba Amma ya tabbata ba za su ja lokaci mai tsawo ba. Mai martaba ya saka aka mayar da su fadarsa ta cikin gida kafin a kai musu abinci da ruwa da lemo aka musu tarba dai ta alfarma sannan yasa a kira Talatu da yaranta su zo su gaisa har ma da Mazajen yaran Talatun da duk suma suka zo Gombe a safiyar yau ‘din. Ayarin Talatu suka sak’o ta a gaba har da Ummeey suka nufo fada Ayra ma Turaki ya saka mata alkyabba sannan ya rik’o hannunta suka nufi fa’da cikin takun k’asaita yana tafe yana murza hannayenta da ya sake jin sun yi taushi na masifa. Gaba ‘daya ahalin Shagogo zuba ido suka yi suna kallon zuri’ar Talatu shi kansa Kabiru kallon yaransa yake cike da k’auna yana mamakin yarda y’ay’an nasa suka hayayyafa suka samar masa da kyawawan jikoki, Jikokin Talatu 18 maza da mata daga yaranta guda hu’du nan gaba kuma ba’a san me Ayran zata haifa ba da sauran Da ba su daina haihuwa ba. Yara kyawawa da su kalolin y’ay’an hutu yaran da ake kira ajeboters. Kabiru ya dinga kallonsu kamar ya janyosu duka ya rungume su yana tunanin yaran mazan da ya dinga alfahari da haihuwarsu a yanzu ba wani da zai nuna ya yi alfahari da zamowarsa ‘dansa har gwara Ahmad shine mai dama dama a cikinsu. Ayra ta zube idanunta cikin nasa tana jin zuciyarta tana sake tafasa musamman da ta runtse ido tana gano shi a kanta yana k’ok’arin keta mata haddi. Kawai sai ta ji jikinta ya fara rawa Lura da hakan Turaki ya sake damk’ar hannunta yana janta kujera ya zaunar da ita a gefensa yana ‘dan Petting bayanta. Hawayen da ya gani a idanunta shi ya sake b’ata ransa shima ya dinga kallon Kabirun cike da tsana don Ummeey ta ba shi labarin Kabirun in briefly. “Relax Ayra! Ba abinda zan bari ya cuceki in dai ina nan.” Ayra ta kwanta a jikinsa sosai tana jin yarda amai yake k’ok’arin zubo mata da gaske bata son ganin fuskar mahaifinta da ta san kuma shi zata gani ba abinda zai kawota nan. Amma kuwa ko kallon Kabirun bata sake yi ha tunda ta masa kallon farko. Ta ‘dauke kanta cike da takaici tana k’arasawa gaban Mai gari jama’ar wajen na kallonta cike da sha’awar yarda ta koma ta durk’ushe a gaban Maigarin tana gaisheshi. Murmushi ya yi yana amsa mata cike da kulawa ya ce “Allah Ubangiji ya miki albarka, ga Kabiru na kawo miki don Girman Allah ku yafe masa ko a haka aka tsyaa yaga isharar rayuwa ba zan so ya tafi lahira da wannan babban zunubin ba. Ki tuna Allah ya miki komai a rayuwa ba abinda ki ka nema kika rasa shi kuma ki ga yarda Allah ya mayar da shi a rayuwa ki yafe masa Talatu idan kika aikata haka ko a wajen Ubangiji kin fi shi.” Talatu ta runtse idanunta tana ha’diyar wani abu ga wani sanyi da yake ratsa zuciyarta tana jin wancan b’acin rai yana melting yana zama farin ciki a zuciyarta, hannayen Baba Waziri ta ji a cikin nata ya mik’ar da ita tsaye ba tare da la’akari da mutanen da suke wajen ba ya zaunar da ita a kujera ta musamman inda yake zaune a gefenta murya a tausashe ya ce “Bu’de idonki Bod’do ba abinda zai sake tayar min da hankalinki matuk’ar ina kusa, ki yafe masa kawai kin ji Gimbiyar Waziri.” Ya fa’da yana mik’a Mata handkerchief ‘din hannunsa Talatu ta saki murmushi a hankali tana mayar da kallonta kan mutanen da suke wajen Musamman Kabiru da ya kafeta da ido yana jin zuciyarsa kamar ta b’alle ta fito don turirin bak’in ciki, a yanzu kam ya san Talatu ta masa nisa har abada ta kuma samu Miji na kere sa’a. Talatu ta sake gyara zaman ta tana fa’din “Ya ci albarkacin Mai gari ya ci albarkancin Uba na Mai martaba ya kuma albarkacin Mijina na yafe masa, ina kuma rok’a masa yara na su yafe masa Allah ya yafe mana baki ‘d’aya.” Gaba ‘d’aya wajen aka ‘dau Kabbara Kabiru ya saki wata ajiyar zuciya yana rik’e k’irjinsa da ya damesa da ciwo ya koma ya jingina da keken guragun da yake zaune a kai ya lumshe idanunsa yana jin hawaye na sake shatata daga idanunsa. Haka nan Taron ya watse bayan Maimartaba ya tabbatar da Yaran Kabirun sun yafe masa har Ayra duk da dai a da ta turje Amma daga baya da Turaki ya dinga lallashinta ya na nuna mata mahaifinta ya kusa rasuwa yafiyarta kawai yake nema sai ta ji zuciyarta ta karye ta ce ta yafe masa hawaye yana zuba a idanunta. Zuciyar Kabiru ta ‘dan yi sanyi daga zafafar da ta yi sai dai yana jin yarda zuciyarta da take aiki kamar ba daidai ba don tana tsayawa cak a lokaci guda kamar zata daina aiki. Ganin dare ya yi Maimartaba ya hana su tafiya ya saka aka bu’de musu wani b’angare ya ce su kwana zuwa da safe su tafi. Sai dai cikin daren Kabirun wani irin ciwon k’irji ya matsa masa ga shi zuciyarsa ba ta bugawa yarda ya kamata. Numfashinsa ma sama-sama yake fita yana furzar da wani irin haki mai bayyana halin da yake ciki. Kamilu a guje ya je kiran Jabiru sai dai ko kafin Jabiru ya zo Ran Kabirun ya yi halinsa sakamakon zuciyarsa da ta daina aiki ta tsaya cak da alama ya samu heart attack. Jabiru da ya k’araso a ki’dime hankalinsa a tashe ya dinga duba Kabirun, sai dai ba numfashi ba alamarsa. Idanunsa sun ka’da sun yi jajir ya ‘dago yana kallon Kamilun da ya shima ya kafa masa nasa idon cikin tashin hankali “Jabiru me ya faru ka yi magana mana.” Jabiru ya ‘dan d’auke kai murya a dakushe ya ce “He passed away. Allah ya gafarta masa.” Wani irin kallo mutanen wajen suka dinga bin sa da shi a ru’de suna duban agogo da yake buga k’arfe 4:00 na asuba daidai safiyar Alhamis. Kamilu ya runtse idanunsa yana sake bu’dewa ya ware su a kan Kabirun da ake kira gawa. Shikkenan yanzu Kabiru ya mutu ba zai sake jin muryar ‘dan uwansa ba, shikkenan rayuwar fa shikkanan an yi an gama, ashe Kabiru yana da rabon sake ganin zuri’arsa y’ay’a da jikoki shi yasa suka zo Gombe ashe rabon ganawarsu ta k’arshe ne, rabon Talatu zata yafe masa ne Ya Allah ka yafe masa don girman zatinka Allah ya ji k’an ka Kabiru.” Kamilu ya fa’da yana jin zuciyarsa na karyewa tsoron Allah na sake shigarsa. Ya ja mayafi ya rufe fuskar Kabirun da shi. Sai da aka fita sallahr asuba, sannan suka sanar da rasuwar Kabirun. Ba wanda bai girgiza da lamarin girman Ubangiji haka nan mutuwar ta dinga kara’dawa a masarautar har sanda Talatu da ahalinta Suka Ji. Ayra ce ka’dai bata ji ba tana can ‘b’angaren Turaki tana barci don bata samu cikakken barci ba dalilin zazzafan zazzab’i da amai da ya sakata a gaba. Turaki mutuwar ta daki k’irjinsa ya dinga kallon Jabiru da yake sanar masa da mutuwar kawai sai ya ji hankalinsa ya tashi. Ana idar da Sallah ya ja k’afafusna da suka masa sanyi ya isa gidan yana tunanin ta yarda zai sanar da Ayra mutuwar mahaifinta Mahaifinka komai ya yi maka dole zaka ji mutuwarsa. Cikin sanyin jiki ya tura k’ofar d’akin. A bakin gadon da take kwance ya tsaya yana bin fuskarta da kallo ya ‘dan shafa wuyanta ya ji still da zazzab’in a hankali ya saki ajiyar zuciya yana saka hannayensa ya ‘dagota kafin ya ha’data a jikinsa a Kunne ya dinga kiran sunanta. Ta bud’e idanunta da suka mata nauyi tana kallonsa. “Sallah.” Ya fa’da a hankali “Tashi kada ki makara.” Da k’yar ta mik’e sai da ya taimaka ta ta shiga toilet ‘din ta yi wanka sannan ta yo alwalar ta zura doguwar rigarta bak’a da ta shigo da ita a daren jiyan ta tada sallah kakkarwar da jikinta take tana k’aruwa. Turaki na ankare da ita. Sai da ya barta suka yi Azkar don shima bai yi ba sannan ya mik’ar da ita “Tashi mu shiga cikin gida idan Abba Jabiru na nan ya duba jikin ki zazab’in nan da amai ya takura miki.” Ta saka kanta a kafa’darsa a hankali ta ce “Abban Amaan don Allah ka k’yaleni na yi barci.” “Mu je mu dawo sai ki yi barcin.” Ya damk’i hannunta ha’de da sakata a b’arin jikinsa d’aya ya rungumota ta sake lafewa a jikinsa tana jin kamar k’afafunta ba za su iya ‘daukar ta ba. A haka ya dinga jan ta a hankali har suka isa b’angaren Ummmeey nan Ayra ta ga kowa yana ta kuka musamman y’an uwanta su Zainab. Hankalinta a tashe ta fara ware ido tana neman in da Amma take don kawai sai ta ji zuciyarta ta tsinke saboda kukan da suke ya yi kama da wanda ya rasa Uwa ko Uba…. 𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗 𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊✍🏽 Takaicin Uba. Episode finale….. Komai ya yi farko zai yi k’arshe yau ne na kawo k’arshen book ‘din Takaicin Uba, ina rok’on Ubangiji ya yafe min kuskuren da na yi a ciki. Ku da kuka samu damar karantawa da ba ni lokacin da kuka yi da dukiyarku Ubangiji ya saka muku da alheri. Nagode sosai da sosai musamman y’an group ‘din JIKAR NASHE REAL FANS JIKAR NASHE SPECIAL GROUP (Mutane na musamman da ba zan manta da ha’din kan da kika ba ni ba alherin Allah ya kai muku a duk inda kuke. Ina mik’a sak’on godiyata da ahalin group ‘dina na MIKIYA WRITERS ASSOCIATION Musamman NIMCY LUV AYUSHERCOOL ZEE KUMURYA And all the member. Sakon godiyata ga ANTY SURAYYA (Halin Yau) ina muku albishir d’in zuwan littafinta Bak’ar Ta’ada nan ba da da’de wa ba In sha Allah dafatan za ku min kara ku siya. Mutane na musamman da ba sa gajiya da comments a koda yaushe kuma ina godiya gareku Ubangiji ya fi ni yabawa. Nagode sosai. 1.Balaraba Alhassan 2.Bishira Aybo Kano 3.Abidatu Alhassan 4.Halima Sadisu Dankaka 5.Salima Abdullahi Dan Sabau 6.Mum Intisar 7.Samira Ameer 8.Ummu isma’il 9.Mami Yahya 10.A’isha Umar 11.Amina Umar Uk 12.Bintu Nouh Kd 13.A’isha Muhammad Lawal 14.Hidayah Lahmad 15.Zulaihatu Umar 16.Aisha Biochemis 17.Amira Sadik Dakin gari 18.Aisha Kawu gujirya 18.Fatima D.Isa 19.Aisha Jamilu Nashe 20.Hadiza Yahya R.lemo 21.Zainab Dankaka 22.Asma’u Dankaka 23.Habiba Muhd Nayaya 24.A’isha Mustafa Sa’id 25.Ummussalama M Makam 26.Hadiza Muhd Mahe 27.Jamila Musa 28.Maryam Abba Zanna 29.Zulaihatu 30.Habiba Bello Sarki 31.Aisha Aliyu Shanono 32.Ummi cindo 33. Saeedat Aminu Musa 34.Ummu Raymond _____________ Yarda ta hango Amman a zaune kanta a cikin gwiwoyinta shi ya saka Ayra sakin wata ajiyar zuciyar da bata shirya fitowarta ba ko bakomai ta ji da’di da ta ga Amma she is alive sab’anin bak’in tunanin da ya zo cikin zuciyarta. K’afafunta sun yi sanyi k’alau ta k’arasa in da suke. Ummeey ce ta mik’a mata hannu da mata alamun ta iso in da take. Ba tayi nawar fa’dawa jikinta ba don haka kawai sai ta samu k’afafunta da yin rawa ga wani irin zazzafan zazza’bi da yake sake rufe mata jikinta. Ummeeey ta rungumeta a jikinta tana fa’din “Don’t cry Ayra, yanzu addu’arku ya fi buk’ata da sake nema masa gafarr Ubangiji mutuwar Uba Mahaifi akwai ciwo Amma sai an daure an cije sannan kaso mafi rinjaye daga k’unar zuciya yake raguwa.” Ayra ta ji wata fa’duwar gaba ta zo mata, kafin idanunta su cigaba da hasko mata fuskar Mahaifinta a jiya yana sakar mata murmushi, murmushin da ta kasa mayar masa a she sallama yake mata, haka kawai sai ta samu kanta da yin murmushin kamar dai ace Yana nan yana kallonta yana kuma jin ta sai dai Ina ta san yanzu ya mata nisa nisan da ta san har abada ne sai yaumul tanadi ita da ta sake ganinsa shikkenan ya tafi. Sai ta ji wani hawaye yana zirya a idanunta ga wani tashin hankali da ya risketa lokaci guda. Ta runtse idanunta tana jin yarda zuciyarta take suya da wani alhini mai sanya jin sanyi a zuk’ata da gangar jiki. Idan ta rufe idonta Mahaifinta take kallo a cikin keken gurarunsa jiya yana sakar mata murmushi. Sai da aka masa wanka aka masa sutura sannan aka zo aka ce Iyalinsa su je su masa sallama. Jikinsu a raunane suka mik’e don isa falon da gawar take. Hawaye suke sosai suna jin da suna da dama da sun dawo da rayuwarsa sun nuna masa gatan da ba su nuna masa ba sai dai ina lokaci ya k’ure musu ba abinda za su masa ya amfaneshi a yanzu sai Sadakatul Jariya. Haka suka durk’ushe a wajen suka yiwa Mahaifinsu kallon k’arshe kallon da sun tabbatar da ga shi sai a darussalam idan suna da rabon ganin juna. Ayra hannunta na rawa ta saka ta shafi fuskar Mahaifinta tana fa’din “Mun yafe maka Baba Allah ya yafe maka Allah ya sadaka da rahmarsa.” Shikkenan ta runtse ido tana hawaye duk da ba Sabo a tsakaninsu Amma akwai wannan feeling ‘din na tsakanin zuciyar Y’ay’a da iyayensu shi su Ayra suka dinga ji har zuwa sanda suna ji suna gani aka zare hannayensu daga jikin makarar aka d’auketa Ayra ta mik’e tsaye da niyyar bin makarar sai ta ji an rik’eta an rungumeta ko ba a fa’da mata ta san Turaki ne don k’amshin turarensa ya bayyana mata haka. Sai da ya jata ya mayar da ita b’angaren Ummeey sannan ya tafi don raka gawar bayan ya tabbata ya sanyata a jikin Ummeey saboda ba ya son wani abu ya samar masa ita. ————————— Kwana uku aka ‘dauka ana zaman makokin hakan ya janyo Turaki ya jinkirta tafiyar sa ya kuma cigaba da neman Visar Ayran don ba ya jin wannan lokacin da ta yi kakagida a zuciyarta zai iya tsallakewa ya barta A nigeria. Bayan ko nisa baya iya yi da ita wani irin so yake mata mai zafin gaske da shi kansa har mamakin kansa yake yi sau tari sai ya zauna ya dinga tunanin irin son da yake mata kamar ya shallake misali kamar aikin sihiri. Yau ma da wuri ya dawo hannunsa ‘dauke da ledar Yalo da D’ata da Guiva da Ayra ta mayar da su abincinta tunda aka yi mutuwar su Suka zama abincinta cin su take kamar wacce ta samu abinci. Ko kallon abinci ba tayi ga wani irin fari da ta yi na masifa sai kuna saurin fushi nan da nan ta hassala duk sai ya ‘dora alhakin hakan da mutuwar mahaifinta. Ya tsaya a parlourn Ummeeyn yana kallon Ayran da ta yi kamar bata gan sa ba don bata son ya ce tazo su tafi sashensa tunda aka yi mutuwar a wajen y’an uwanta take kwana. Murmushi kawai ya yi ya zauna yana masa gaisuwar k’annensa da suke gaishesa har da su Majeedah da yanzu itama ita take gaisheshi tunda matsayin wa yake a wajenta. Idanunsa cikin na Ayra tana zaune ta mik’e k’afa Tayseer tana kankare mata farce. Su Amma duk suna wajen shi yasa bai kulata ba. Sai da aka gama ta mik’e don shiga bedroom ta ji ya ce “Ki kawo min abinci ina part ‘dina.” Ayra ta ‘dan turo baki alamar ranta bai so ba, ta shige kitchen ‘din tana nazarin abinda zata zuba masa don ta san bai fiye cin abinci bai nauyi ba ya fi ta’ammali da Vegetables da fruits kawai sai ta saki tsaki ta bud’e fridge ta d’ebi fruits don ta ha’da masa Fruit salad, don ba zata iya girki ba ita yanzu bata son jin k’amshin komai ma kuma komai ma haushi yake bata. Sai da ta saka a bowl mai murfi sannan ta ‘dora a kan Tray. Kawai kuma sai ta ji kunyar ta fita Parlourn a ganta zata tafi wajensa. Da k’yar ta fito daga kitchen d’in tana sakin ajiyar zuciya ganin ba wanda ya kula ma da ita ta yi saurin shigewa b’angarensa. A zaune ta gan shi bakin gado da Laptop a gabansa yana ta aiki. Sallamar ya amsa yana ‘dagowa ya sauke idanunsa a kanta yana ‘dan murmushi ya ce “Ai na zata ba zaki zo ba?” Ta langwab’e kanta tana shirin zama bakin kujerar da take ‘dakin ta ji ya ce “Kada ki fara, matso nan na ji waye yake tab’a min ke kwana biyu na ganki ba walwala.” Kamar ba zata je ba sai kuma ta tuna da hu’du bar da Yaya Aisha da Ya.Zainab suka mata da safe na yarda ake kama miji a hannu. Don haka ta mik’e tana jin kamar k’afarta zata hard’e ta fa’di a wajen don har yanzu tana jin kunyarsa ba wai ta saba bane. Shi kuwa kallonta kawai yake yana sakin murmushi ganin yarda take komai a kunyace. Tana shirin zama ta ji ya jata jikinsa yana shinshinar wuyanta Ayra ta lumshe ido tana jin yarda yake bin duk sassan jikinta da zazzafan kiss shaidar dake nuna mata ya yi missing ‘dinta sosai in just 4 days. Don dole Ayra ta ajiye kasalarta ta biye masa mamaki ne ya kamashi sosai ganin yarda take neman zautar da shi da wasu irin hot romances da take zuba masa. Ya lumshe idanunsa kawai yana gidiya ga Allah da ya nufeshi da auren irin matar da yake so matar da zata jiyar da shi da’di daga tarin baiwar da Allah ya bata. Towel a hannunsa ya fito daga wanka ya zuba mata narkakkun idanunsa yana fa’din “Alhamdulillah for the gifts of God. Tabbas yanzu na yi aure.” Ayra ta lumshe ido tana jin da’din zuzuta ta da yake. “Jibi za mu tafi inda muka fi wayo don haka ki fara shiri.” Ayra tana ware ido ta dubeshi “Tafiya kuma?” Ya ‘d’aga mata gira yana lumshe ido “Yes tafiya, ba zan iya barinki a nan ba ni ina can idan ba so kike na samu matsala da aikina ba, da yau ne ma to na ‘daga tafiyar ne saboda yau Aman zai dawo daga makaranta ina so na gan shi mu yi sallama don Ummeey ta ce ba zan tafi da shi ba, ni kuma bana jin zan dawo k’asar nan in the next one year ma.” Ayra ta zaro ido ya sake ‘d’aga mata girarsa “Mhmnn, na gaji da yawo a iska ina son nayi concentrating a kan k’wadagon da nake ba zan dawo ba sai kin haihu mun zo kawo musu Baby su gani tukun.” Ayra ta mirgina tana rungumar filo ha’de da lumshe idonta sam bata son tafiya ta bar Familynta Amma kuma shima bata son ta yi missing ‘dinsa musamman yanzu da ya jiyar da ita duk wani da’di da bata tab’a zaton a duniya akwaishi ba. Sai dai bata son nuna masa zulamarta a fili don haka ta ‘dan zunb’uro baki ta ce “Ni dai da ka bar ni sai mu dinga zuwa hutu da Aman.” Ya tsyaa cak yana kallonta yana jin wani abu yana bin jikinsa tsoro yake ji kada dai a ce har yanzu bai gama kame zuciyarta ba tunda har take tunanin iya zama babu shi. Jikinsa a sanyaye ya zauna a gefen gadon yana mirginota ta dawo saman cinyarsa idanu ta runtse don ba zata iya kallonsa ba a haka yarda take a jikinsa ko Riga babu. “Ayra open your eyes.” Ta sake runtse idanunta “Ki bud’e idonki ki gaya min kin fi son zama a nigeria ba kya son bi na.” Idanunta a lumshe ta ce “Bana son tafiya na bar Amma da Ummeey na.” Ya saki murmushi ka’dan ya ce “Ba kya so na har yanzu?” Bata san sanda ta ware idanunta a cikin k’wayar idanunsa ba “Wa ye yace maka bana son ka?” Ya lumshe idanunsa “Idan kina so na ba zaki ce na tafi na barki ba tunda kin san ba zaki iya barci ba idan ba kya kusa da ni, na sani ba kya so na ni nake ki’da na nake rawata.” Ya mik’e yana ajiye kanta a saman pillow. Fuskarsa ba walwala ya ce “Thank you” Da sauri Ayra ta kamo hannunsa tana mik’ewa “In dai binka ne zai saka ka gane ina son ka na amince zan bika mu zauna a can sama da shekara goma ma, ka daina cewa bana son ka.” Bai san sanda ya zube a gabanta yana jan hannayenta ba yana murzasu a hankali wani farin ciki yake ji mara misaltuwa “So You loved me Right?” Ayra ta lumshe idanunta a hankali ta furta “Surely I can do without you.” Bai san sanda ya rungumeta tsam a jikinsa ba yana fa’din Alhamdulillah!” ______________ Kashegari Baba Waziri ya uzzirawa Maimartaba akan yana son Talatu ta tare. Mai martaba ya dinga kallonsa yana murmushi ya san a shekarun Waziri ya na buk’atar sake aure tunda ya girmeshi nesa ba kusa ba sai dai bai yi zaton zai yi rawar k’afa kamar akan Talatun ya fara aure ba ko kuma Budurwa ya aura. “Wai saurin me kake ne Waziri? Sai kace wani wanda yanzu ya fara aure? Ita Talatun nan fa ba yarinya ba ce.” Waziri yana sakin ajiyar zuciya ya ce “Ba zaka gane yarda nake jin Talatu a raina bane, soyayya nake mata fiye da soyayyar da saurayi zai wa budurwarsa ni da Talatu ta fiye min y’an mata dubu. Don Allah ta tare yau na saka an mata komai.” Maimartaba ya ‘daga kansa “Shawarar da zan baka ka nemi Hamida itace zata kai maka Talatu har ‘dakinka a yau, don idan aka bi Ta Talatu ba zata tare nan kusa ba.” Haka kuwa aka yi Hameeda ta amsawa Baba Waziri akan zata kawota a yau ba kuma tare da ta sanar da yaranta da ita kanta Talatun ba. Don haka ana idar da Sallahr Magriba Hameeda ta shirya wasu y’an kaya a akwati ta saka aka fitar mata da shi ta k’ofar baya don bata son Talatun ta gani tunda Kabiru ya mutu yanzu ba wani Walima da za’a yi. Tana kallon Talatun ta ce “Shirya Don Allah ki raka ni dubiyar wata k’awata.” Talatu bata kawo komai a ranta ba ta mik’e ta shiga ‘d’aki ta saka zumbulelen Hijabinta sannan ta fito. Suka rankaya da Hamida da Fulani matar Sarki sai Jummai aminiyar Talatu a motarsu sai wasu Bayi guda Uku da za su taho a wata motar guda. _______Gidan Talatu______ Tun daga bakin gate za ka san gidan ya amsa sunansa na sabon gida na zamani sai walwali yake da hasken fitilu kamar rana. Talatu tun a waje ta fara sha’awar gidan kafin su shiga ciki. Suka zube a falo Hameeda tana kallonta tana murmushi ta ce “Ma sha Allah, Allah ya kawo mu gidanki Talatu Allah ya baku zaman lafiya ke da Baba Waziri ya kawar da dukkan abin k’i.” Da hanzari Talatu ta d’ago tana kallonta Fulani da Jummai da sun Riga sun san komai suka ce “To me za’a jira Talatu ke ba yarinya ba Waziri sai suntiri yake a ba shi matarsa shi yasa muka zame muka kawo ki Allah ya baku zaman lafiya.” Daga haka suka mik’e suka bar Talatu a zaune da sakakken baki ta zama sai kace Statue. Tana k’ok’arin mik’ewa ta bi bayansu Waziri ya shigo cikin shigar Jallabiya sai ya zama kamar ba shi ba ta saba ganinsa a cikin manyan riguna. Ya sakar mata murmushi ya ce “Alhamdulillah barkanki da shigowa gidan ki Talatu Allah ya yiwa auren mu albarka.” Ya fa’da yana janta a jikinsa ya bata kyakykyawar runguma yana jin kamar ya mayar da ita ciki. A kunnenta ya dinga sauke ajiyar zuciya yana fa’din “Alhamdulillah nagode ya Rabb da ka cika min Burina.” Talatu ta lumshe idanunta tana jin wani iri a jikinta abinda bata tab’a ji ba, Waziri ya jata ya cigaba da nuna mata ‘dakunanta to Fatan Alheri BODDON WAZIRI. TALATUN KABIRU. Ummeey tana komawa gida yara suka dinga kallonta kafin Ayra ta ce “Ina Amman?” Ummeey ta saki murmushi ta ce “Amma tana gidan Mijinta” duk sai suka bu’de baki suna kallonta cikin mamaki Ayra ta ce “Ko sallama babu? Gobe fa mu ma zamu tafi” Ummeey ta ce “Sai ku je goben ku mata sallama ke da Turakin ku ga gidan Aurenta daga nan.” Suka saki murmushi duk da jikinsu ya yi sanyi amma burinsu samun farin cikin Ammansu, don haka suka ja baki suka yi shiru bayan sun ce Allah ya sanya alheri. Ummeey tace “Ina Tasleem?” Ayra na murmushi ta ce “Tana wajen Abba Jabiru Ai da alama da shi za’ayi don naga ya kafa gwamnatinsa.” Amma ta saki murmushi tace “Allahu yasha, ai Jabiru mutumin arziki ne da kowa zai so ha’da zuri’a da shi.” Kashegari kafin su Ayra su wuce suka je gidan Amman dukkansu hankalinsu ya kwanta ganin yarda Amma take walwala da farin ciki da alama komai ya tafi mata yarda take so. Baba wazirin ma ba inda ya je yana nan gidan Amman tunda ba gidansu ‘d’aya da matansa ba ya dinga jan su a jiki musamman Ayra da aka ce zata tafi yau ita da Mijinta. Suna kallon yarda yake kallon Amman cike da soyayya, sai hankalinsu ya kwanta sun san Amma ta fa’da hannu na gari a yanzu ne zata san Maza suna suka tara! A daren ranar Kuma Su Ayra suka tashi ta airport ‘din Abuja Ayra ta dinga jin kamar ta yi Kuka Amma da ta tuna tare da wa take masoyinta na gaske sai ta ji hankalinta ya kwanta ta sake kwanciya a jikinsa a cikin jirgin shi kuma ya saka hannu ya rungumeta yana sakin ajiyar zuciya. Haka rayuwa ta cigaba da gara musu cikin farin ciki da kwanciyar hankali. Har cikin Ayra ya isa haihuwa wani dare ta tashi da nak’uda suka nufi asibiti sai Ga Ayra ta haifo y’an biyunta Maza zar masu kama da Turaki kwabo da kwabo. Sanda aka mik’o mata yaran sakar baki ta yi tana kallonsu duk da an gaya mata Twins ne bata tab’a kawowa a ranta zata haifi twins ‘din ba. Turaki yana kallonta yana murmushi ya ce “Shikkenan Ayra ta zama Maman Boys ko ya za’a yi da k’iyayyar Mazan?” Ta ‘dago tana kallonsa tana murmushi ta ce “Ai na tuba na daina tunda Allah ya cusa min soyayyar Babansu.” Ya had’asu da yaran yana murmushi ya ce “Y’an Nigeria suna hanya.” Ayra ta ware ido ta ce “Serious?” Ya ‘d’aga mata gira yana cewa “Ban gaya maka ba ne dama Just to surprise you.” Ayra ta lumshe ido. Sai yamma aka sallamesu suna zuwa gidansu ta ga gidan a cike ta tsyaa tana kallonsu cike da farin ciki ba wanda bai zo ba a cikin ahalinta y’ay’an gidansu da jikokinsu har da K’annensu Maza da suke Uba ‘daya don tuni suka ya da makaman yak’insu suka shiga cikin y’anuwansu su kuma suka nema musu aiyukan yi da sana’a. Ayra da sauri ta rungume Ummmeeey da Amma cikin tsananin farin cikin ganinsu har da hawayenta. Aman kuwa ‘dauke yaran ya yi ya hana kowa ‘daukarsu yana ta kallonsu. Tasleem Ayra ta kalla tana murmushi tace “Ina Abba Jabiru yaushe ne Bikin?” Tayseer ta ce “Saura 2Months In sha Allah.” Ayra ta ji da’di don ko bakomai zata samu damar halarta bikin. Deejah ta tashi tana kallon Ayra tana murmushi kafin ta kunna T.v ta yi connecting da wayarta sai ga vedion Ayra lokacin tana budurwa a gidansu gwiwarta zube gaban Amma tana hawaye “Amma kada ki bi tata tasu, ni ba zan tab’a aure ba na tsani namiji kuma duk randa ku ka min aure wallahi sai na kashe kai na.” Ayra ta lumshe ido tana murmushi kafin ta bu’de idon ta wara su akan Turaki ta ce “The Winner!” Aka saka tafi da dariya gaba ‘d’aya. Turaki yana kallonta ya ce “Ga shi ta haifi Murad da Mujahid ko ina zata kai su yanzu.” Ummeey ta ce “Ku saurarawa d’iyata waye ba ya kuskure.” Ayra dai ta saukar da idonta tana murmushi a hankali ta ce “Alhamdulillah” sai ta ji kowa ya ce “Ma sha Allah” a she da k’arfi ta yi. To nima Jikar Nashe anan nake cewa Alhamdulillah sai mun ha’du a sabon littafi na GASKIYAR LAMARI….. (Na tab’a yin sa lokutan baya Amma zai zo muku ta fuskar zamani akwai wasu sauye-sauye a cikinsa.. sai kun ji ni In sha Allah!) 08033748387