Showing 60001 words to 63000 words out of 180103 words
bazan daga hannu na Mari Umma ba bansan.mai ya hau kaina ba burina kawai lokacin na Hana Umma ta kasheki burina kawai lokacin na tseratar da ita daga Halaka kar ta d'au nauyin kissan Kai a yanda na taho so kawai nake na ceceki ba wai na Mareta ba bansan Mai ya sameni ba da ilimina na aikata irin wanan danyen aikin ya Allah ka yafemin ka sauko da zuciyar Mahaifiyata innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"
Yanzu ma Bai b'aci ba Naseer kaje ka Bata hakuri burinta kawai ka sakeni ka Kai mata takarda sakina ni nasan zata yafe maka"
"Bazan iya hada Ido da Umma ba tunda na Mata ba daidai ba na kasa hada Ido da ita Naeema ki kyalleni naji da ciwon dana keji a kirjina da asuba zanje zuwa lokacin nasan kila ta sauko Kuma Zan bi umarninta tunda Haka take so"
A Ranar daga Ni har Naseer bamu runtsa ba sosai Naga tashin hankali a tare da Naseer Duk jarumtarsa ranar haka ya zama kamar mace Haka nayita bashi baki.
Haka nayita bashi magani sabida zazzabin dake ta rufeshi.
Washegari da asuba Naseer ya nufi goron dutse duk a hargitse Dan sallar ma ba a nutse yayi ba.
Turus yayi a lokacin da yaga gidan a kulle da kwado sosai yaji hankalinsa ya tashi yayi zaman dirshan a k'ofar Gidan lailai ba karamin fushi Umma tayi dashi ba yanzu ya zaiyi"
Yana zaune a wajen su Lukman suka fito suka hau gaishe shi suna tambayarsa dafatan lafiya Dan kana ganinsa kasan baa hayyacinsa yake ba
"Bai iya musu magana ba Dan ji yayi idan zaiyi magana zai iya fashewa da kuka hannu Lukman din ya saka a Aljihu ya dauko mukullin gidan ya mik'awa Naseer Yana gashi Hajiya ce ta bani jiya Akan na baka idan ka dawo sun koma garinsu jiya daddare inata ma hanasu tafiyar Taki saurarata.
A zuciya Naseer ke nanata innalillahi wa Inna ilaihi rajiun.
Bai ma ji Mai Lukman ke cewa ba ahaka ya mik'e ya hau taxi ya dawo gida.
Ni kuwa tunda Naseer ya fita massallaci Ina iddar da sallah na dawo Palo na zauna na buga tagumi Ina ta tunanin abinyi hankalina gabadaya na wajen Naseer ko ya zasu Kare da Umma tunanin hada kayana Dana yarana ne ya fad'omin Dan Naseer na dawowa Zan tafi garinmu bazan Kara Sakan daya ba
su Zahira ma a ranar da suka gani a zaune basu min zancen na shiryasu su tafi makaranta ba suma duk jikinsu ba kwari Haka suka tashi daidai da Humaira karamar yarinya ma kamar tasan Mai ke faruwa Haka tayi lamo da ita.
Wajen bakwai da rabbi Naseer ya dawo duk a firgice mik'ewa nayi da Sauri na tare shi Amma sai ya matsar Dani gefe ya shige daki.
Ahaka na bi bayansa Inda Yana shiga daki kwanciya yayi ya fara hawaye nayita tambayarsa Mai ya faru yak'i kulani.
Hasali ma da yaga na dameshi da tambaya sai ya daka min tsawa akan na fita na bashi waje yaji da Abunda ke damunsa
Haka na fito daga d'akin Nima Ina hawayen Inna zuwaira Bata Nan balle nace ta dafawa su Zahira abinci jiya bansan ya akayi ma ta bar gidan ba ahaka na daure na Shiga kitchen na Dora musu ruwan tea Yana tafasa na juye a flask na hada musu tea na ajiye musu bredi na koma Kan kujera na zauna sosai naji Haushin abinda Naseer yamin Naga dai duk shi ya jawo Mana wannan tashin hankalin da yabi umarnin Umma da duk Haka Bai kasance ba ina Jin ciwon tsanar da umma tamin na ba gaira ba dalili na rasa Mai nayiwa Umma a rayuwata k'arfi da yaji take so ta tasheni daga Kan yayana.
Haka nayita zubar hawaye sama da awa biyu sai dana gaji Dan kaina kafin na mik'e na Kara komawa d'akin Dan so nake Naseer ya gayamin yanda sukayi da Umma ya bani takarda ta na tafi Dan indai ya sakeni bazan zauna ba tafiya zanyi tsinuwar da Umma tayiwa Naseer sosai ya tsayamin a zuciya tsinuwar kawai idan na tuna sai gabana ya tsinke ya fadi sosai duk kalmomin suka tsayamin a Rai suke razanani"
Rawar Darin da Naseer keyi yasa nashiga d'akin da gudu Ina tab'a shi naji jikinsa zafi zau.
Ahaka na kwasa nayi waje na Nemo Mai taxi ya shigo ya Tayani kinkiman Naseer mukayi asibiti bayan na Kai su Zahira gidan mak'ota a takaice sai da Naseer yayi sati a asibiti Inda aka ce jininsa ne yayi balain Hawa sabida damuwar daya saka a ransa.
Sai da aka sallamo mu da kwana biyu yake bani labari su Umma sun koma Calabar Wanda hakan na nuni da Umma ba karamin fushi yayi ba shi Marin daya matane inya tuna yake daga Masa Hankali.
Shawara na bashi akan yabi bayanta zuwa Calabar ya nemi Mallam Musbahu ya raka shi su bawa Umma baki ya Kuma tabbata da ya sakeni sabida Taji dadi idan na furta kalmar saki Ina ganin wani irin tashin hankali a idon Naseer Amma ahaka yake daurewa.
Sai da jikinsa ya Kara kwari kafin ya shirya tafiya Calabar tunda abinan ya faru bana iya cikakken bacci idan bacci ya d'aukeni haka nake mafarkai marasa Kan gado masu firgitarwa nayita ganin Naseer a mumunan yanayi idan na farka sai na danganta Haka da tsinuwar da Umma tayiwa Naseer na saka a Raina dayawa hakane yasa nake mafarki da Naseer.
Sosai na sake zage damtse wajen kaiwa Allah kukana Ina Addua Allah yasa Kar bakin umma yayi tasiri akan sa Dan nasan duk a dalilin yak'i sakina tayi Masa wanan bakin uwa Kan sadaukar da farincikinta sabida yaranta Akan Umma na fara ganin uwa Mai San danta ya wulakanta ya tozarta har da su kudi sai ya Masa wahalar samu sai dai ya gani a hannun wasu Mai yayi zafi haka.
A ranar da Naseer ya tafi a Haka nayi jigum Kamar Mara lafiya ba lokacin da ake da yawaitar waya bane ballantana na kirashi naji ya sukayi.
Naseer kuwa addua d'auke a bakinsa Akan Allah ya sauko da zuciyarta ta yafe masa ya Isa gidan Hajara a lokacin da ya sauka a Calabar
Sai dai me Yana zuwa gidan yagan shi a kulle Wanda hakan ya haddasa Masa fad'uwar gaba sai daya tambayi mak'ota akace Masa ai sunce sunyi tafiya sai an kwana biyu zasu dawo.
Sosai hankalin Naseer ya tashi Dan yaga alamar Umma ta d'au zafi gashi Bai San ta Ina zai soma nemota ba har tsohon gidanta yaje shima a kulle jiki ba kwari a Haka ya nufi gidan Mallam Musbahu shima sai ce Masa akayi sun bar Calabar sun koma garinsu Dan Dama kasuwanci ne ya kawo Mallam Musbahu sosai Naseer Yaji baiji dadin abinda ya faru ba duk Inda yake tunanin zai ga mahaifiyarsa ya nemi yafiyarta ya samu nutsuwar zuciya ya nema Bai sameta ba yasan Umma tasan zai zo neman yafiyarta shine ta nisanceshi ahaka yayi kwana biyu a Calabar kafin ya juyo ya dawo.
A takaice zuwan Calabar biyar Yana dawowa Bai samu ganin Umma ba Akan dole ya hakura da nemanta muka dage da Addu'a Akan Allah ya sauko da zuciyarta daga fushin data hau.
Addua Naseer keyi sosai ba dare ba Rana Akan Allah yasa Kar bakin data Masa ya bishi.
Duk Wanda yasan Naseer a baya idan ya ganshi tunani zaiyi shekara yayi Yana jinya sabida damuwar daya saka a ransa sai nice ma nake Dan kwantar Masa da hankali sosai yake nadamar k'in bin umarni Umma Dan tunda ta tafi ya rasa nutsuwar zuciya.
Ni kuwa kullum cikin addua nake da sadaka Dan sadaka maganin masifa ce idan wani abune ma zai Same mu Allah ya kawo Mana da sauki.
Mafarkan danake na d'aga min hankali Amma bantaba gayawa Naseer ba.
Naseer kuwa har tausayinsa nakeji nayita kuka a boye.
A cikin wanan yanayin Allah ya saukeni lafiya na Kara haifar mace sosai naso ace namiji na Haifa amma Ina ganinta naji kaunarta ya rufeni.
Addua na Mata Naseer shima kadaran kadahan Bai nuna komai ba ya saka Mata Raheema yamin komai kamar yanda ya saba na kyautata wa.
A Haka rayuwa ta cigaba da tafiyar Mana tun muna dari dari daga Ni har Naseer har muka zo muka saki jiki.
Naseer kuwa sai Kara samun budi yake duk da Yana Dan samun sarari Yana zuwa Calabar Amma har lokacin baya ganin Hajara.
Ahaka akayi shekara biyu babu abinda ya faru sai a lokacin Hankalina ya fara kwanciya sai na danganta yawan mafarkin danake da kila dan na Saka abinda ya faru tsakanin Naseer da umman ne a Raina.
Shima Naseer zuwa Lokacin ya Dan saki jikinsa duk da abin na Fado Masa a Rai Kuma Yana addua sosai
Sai watarana ran Monday bazan tab'a mantawa ba Na shirya su Minal Dan lokacin Zahira na iya yiwa kanta komai ita da Nadeeya tana da shekara goma lokacin Nadeeya nada takwas da watani Zahira na primary 3 a lokacin Nadeeya na primary one Minal da Humaira Kuma suma nursery section Raheema ce kawai Bata fara makaranta ba
Naseer ne ya shirya Kai su makarantar Dan Dama shi ne yake kaisu
Har k'ofar gida na rakasu sai danaga tafiyarsu na dawo Ina kwanciya bacci yayi awon gaba dani na hau mafarki Wai gidan danake ciki ya Kama da wuta.
Da sallati na tashi a firgice ai kuwa na jiyo kauri da Sauri na mik'e na nufi kitchen Ashe Wai heater na kunna ruwan ya kone shine heater tayi jawur shap na manta cikin zafin nama na zare socket din na koma Palo na zauna Ina Dan Jin fad'uwar gaba ahaka nayi jigum na zauna na rasa Mai kemin dadi.
Naseer kuwa yana sauke su Zahira ya bisu har cikin makarantar sai daya ga shigarsu Aji ya juyo ya hau motarsa ya fara k'ok'arin tayarwa
Kamar ance ya juya yaga wata Mata ta tsaya a bakin gate din makaranta ta yafito shi Akan yazo.
Fasa tada motar yayi yana mamakin Kiran da matar ke masa anan ya fara tunanin kila a cikin mallaman makarantar ne shine take so ta fada Masa wani Abu game dasu Zahira hakane yasa ya fasa tada motar ya fito.
Yana barin jikin motar da taku biyu.
Motar ta Kama da wuta. .......
*Wlh Haka Naseer ya tsallaka rijiya da baya da ya Bata lokaci wajen fitowa daga motar da yanzu sai dai wani bashi ba*
8/19/21, 10:31 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 24*
Wani irin murmushi kawai Umma keyi tana cigaba da jijjiga kafarta
Naseer kuwa ya Shiga palon da rarrafe Yana "Umma kiyiwa girman Allah ki yafemin Umma nabi Allah nabiki ki taimaka min ki sakamin albarka a rayuwata Umma nayi nadamr k'in bin umarninki Umma Dan Allah ki yafemin"
",Waccece ummanka? Ina ka baro Naeema Ni asuwa dazan saka maka albarka Naseer Ni ai ba komai bace a wajenka ai Naeema Uwarka ce Kuma matarka Kuma rayuwarka da idan kuka rabu mutuwa zakayi Naseer ai ba abinda kayimin Banga dalilin da zai saka kazo kana neman yafiyata ba kaga Dana nan"
Tace tana nuna Tijjani Shi na sani sai su Safiyya Kai na Dade da Sallama ka na dade da barwa Naeema Kai banida wani had'i da Kai Naseer ka daina batawa kanka lokaci ka tashi ka tafi"
"Wai me ke faruwane Umma"?
Tijjani yace cikin rashin fahimtar abinda ke faruwa Sam bai San abinda ke faruwa ba ya dai San Umma Bata San Naeema haka ma kannensa shi dai ba ruwansa da tsanar da suka Mata shi irin mutanen Nan ne da Bai fiye Shiga abinda Bai shafeshi ba"
"Mai ka Mata ne Yaya Naseer"?
"Ba abinda ya Shafeka Babu Kuma ruwanka idan ba kana San b'acin Raina ba uban waye yace ma ka kawo min shi gida"?
"Umma Mai yayi zafi Haka Yaya Naseer ne fa'?
Tsaki Hajara tayi ta d'auke kanta tana cigaba da jijjiga kafarta.
Naseer kuwa ya cigaba da magiya Yana "wlh Umma yanzu Zan bi umarninki a gabanki Zan rubuta takarda ki aiki Tijjani ya Kai Mata Amma Dan Allah ki yafemin ki janye kalamanki Umma na fara ganin masifa tun ba'aje koina ba Umma ki tausayamin"
Wani irin kallo Hajara tayiwa Naseer ta mik'e cikin wani irin B'acin Rai ta Isa wajen da Naseer ke zub'e akan gwiwarsa
"Sai a yanzu Dana rufe babinka na sallamaka zaka cemin zaka bi umarnina sai da ka fara ganin masifa zaka bi umarnina toh ka makara Naseer ko ka rubuta ko baka rubuta ba babu abinda ya shafeni kudin da kake dashi yasa kake Jin Kai wani ne bazaka iya bin umarnina ba ka fifita mace Naseer a kaina Sabida matarka ka daga hannu ka Mareni"
Wani irin jijjiga Kai Umma tayi cikin fushi ta cigaba da Magana tana "kaci Sa'a Kai Dana ne Ni na Haifeka Naseer da ace wani ne ya mareni da yanzu sai dai ayi labarinsa Bazan janye kalmata ba Naseer da sai da kaga alamar masifa na tunkaroka ka taho wajena wlh baka ga komai ba Naseer"
"Haba umma wane irin magana ne wanan haba Umma Naseer Bai cancanci Haka daga wajenki ba karki manta fa duk abinda kike takama dashi daga ke har mu shine fa ko gidanan da Kika siya Umma da kudinsa ne yau idan kina jifansa da irin kalaman Nan ya Shiga cikin masifa ai muma sai ya shafemu"
"Kayimin Shiru Tijjani wlh Kai ma Zan maka baki Dan ubanka kayimin Shiru idan Kai ma Marin nawa zakayi kamar yanda ya mareni zaka iya matsowa ka Mareni da kake cewa shine rufin asirinmu Dan ubanka yanzu a gidansa nake zaune ko shi yake bamu abinda muke ci yaje can ya rik'e arzikinsa ya zauna da matarsa ban rokesa ya Kara min komai ba bana bukatar komai nasa yaje can ya karata"
"Umma Dan Allah Dan Annabi kiyi hakuri ki yafemin Tijjani Dan Allah Tayani Bata hakuri wlh Zan saki Naeema yanzu indai haka zai saka ta yafemin ta janye kalamnta akaina"
Wani irin kallo Umma ta jefashi dashi taja Tsaki ta shige d'akinta.
Naseer kuwa ya cigaba da kuka Yana Tijjani ya taimakeshi Tijjani kuwa cikin b'acin Rai yace "Mai kayi Mata da Zan Bata hakuri sabida me Zan Bata hakuri Dan Allah Yaya ka tashi kayi tafiyarka Umma Haka halinta yake duk da bansan Mai asalin abinda ya faru ba Ni nasan laifinta ne Kai Kuma kuskuren da kayi da ka Mareta Amma ka tashi kayi tafiyarka insha Allahu babu abinda zai sameka karka sake ka danganta abinda ya sameka da ko bakinta ne arzikin Nan waye ya baka"?
"Allah"
Naseer yace Yana Jan majina
Toh kasa a ranka zai iya karba Dan ya jarrabceka yaga ya zakayi Dan shagonka da gidanka.ya kone bashi yake nufin Wai Dan Umma na fushi dakai Dan ko dan ta maka kalamai ne marasa dadi ko mu Nan Bata barmu ba idan muka Bata Mata Rai kamar ta Mana baki har tanayi din ma ka daina wahalar da kanka ka tashi kaje kawai"
Tijjani "naji duk Mai kace burina kawai tace ta yafemin ko Zan samu nutsuwa a Raina"
Haka Naseer yaje bakin kofa d'akin Hajara Yana ta kuka da magiya Inda b'acin Rai ma yasa Tijjani ya ficewarsa ya bar sa a wajen
Ahaka Safiyya da ta fita yawon gantali ta dawo ta tarar dashi
Tana ganin Naseer ta Shiga da Sauri Dan har ga Allah Naseer na ranta daga canjin rayuwar ma kawai da suka samu da basa komai waja waja tunda Umma ta dawo gwammaja ta siyi karamin gida yasa takeso taga Naseer ko ta San halin da yake ciki.
Ummansu Bata tab'a kudurta mugayen Abubuwa data Sha alwashin samun cikar burinta ba sai Akan Naseer har rokonta tayi akan ta yafewa Naseer ta kashe Naeema tak'i sosai ta fusata da ko maganar Naseer din Bata so ayi Mata
Ita dai tasan sun Cutu Kuma suna Kan cutuwa dan badan Tijjani shima Yana musu abubuwa ba da abinda xasu saka a bakinsu sai ya gaggaresu
Lami kuwa Tana Calabar abinta tak'i ma zuwa kanon a satin Nan ma take cewa ta samu wani zai Aureta zasu zo wajen Umma ta Kai su wajen dangin babansu Dan ba saninsu sukayi ba
Da Sauri ta Shiga palon tana Yaya lafiya naganka Haka"?
"Dan Allah ki Tayani bawa Umma hakuri nayi nadamar abinda nayi Mata Kuma wlh yanzu a shirye nake Dana bi umarninta Safiyya jiya motana ya konne yau Kuma gidana na goron dutse da shaguna ukun.ya kone kurmus kinsan kuwa yawan dukiyar danayi asararsa kuwa Safiyya ki taimaka ki bawa Umma hakuri Ina tsoron bakin umma ya kamani"
Tunda yace gidansa na goron dutse ya kone Safiyya ta zaro Ido waje tana Kara tuno girman gidan da shagunan Naseer uku dake cike da.kaya.
Sosai hankalinta ya tashi itama ta hau bubuga kofar d'akin tunda ta nunawa Umma tana tausayin Naseer Bata San wani Abu ya sameshi Umma ta fara Mata boye boye ba komai ta sani ba yanzu game da.umma Umma yanzu ta kara canjawa tundaga lokacin da suka baro gidan Naseer Amma daga abinda Naseer yace yanzu yasa ta fara zargin tabbas da saka hannun Umma a konewar gidan Naseer da motarsa
"Umma Dan Allah ki bud'e k'ofar nan haba Umma ke yanzu Sabida Wata Naeema Zaki juyawa Yaya Naseer baya yanzu bakisan Haka Naeema keso ba Dan Allah kifito ki saurari Yaya"
"Safiyya"
Naam
Saffiya
Naam
"Wlh ranki zaiyi mumunnan b'aci inkika Kara Shiga maganar Nan babu ruwanki ku kyalleni Naseer ya fice ya barmin gida Dan wlh idan Bai fita ba Zan Kara Masa wani bakin na barwa Naeema shi ya dauka karya nake ko? ya d'auka duk rantsuwar da nayi akansa zai tashi a banza ne ko? Ya tun Bai fara ma.ganin komai ba zai zo neman yafiyata ai Bai ga komai ba ba dai Naeema ya zaba a kaina ba"
"Umma kiyiwa Allah ki yafemin Umma Allah ma muna Masa laifi mu nemi yafiyarsa ya yafe mana Umma nasan nayi kuskure Dan Allah ki yafemin"
"Tashi ka fitar min daga gida Naseer idan na fito daga d'akin Nan kalmar da Zan maka sai yafi wancan Muni"
Naseer da Sauri ya mik'e yayi waje
Safiyya cikin Sanyi jiki tabi bayansa tana bashi hakuri.
Har wani jiri Naseer keji Tijjani kuwa a