Showing 78001 words to 81000 words out of 180103 words
cikin ba Dole ya gudu ba Amma ba komai nasan abinda zanyi ngd Shugaba idan Ina bukatar taimakon Zan turara"
Suna k'ok'arin mik'ewa Safiyya tayi caraf tace "Shugaba inasan nayi aure sai dai babu mijin aure ba Wanda ya tab'a cewa Yana Sona ga Lami har tayi aure cikine da ita"
"Karbi kwallin Nan duk wanda Kika gani kikaji ya kwanta Miki a Rai ki saka kwallin wuyanta ku hada Ido.
Da tsananin farinciki suka dawo
Duk da kasan ran Hajara ba Haka taso ba taso ko Yaya ne taci Galaba Akan Murja.
A takaice kwanansu Uku suka shirya tsaf suka karbi kudi a wajen Lami suka dau hanyar kano.
Naeema
Sosai Nake samun bud'i ta sanadin siyar da Zobo da ruwa.
Zuwa yanzu Zan iya cewa idan akwai abinda yake damuna Bai wuce rashin Naseer ba har adashe na Shiga Ina tara kudi sabida cikin da nake d'auke dashi sosai nake adduar Allah yasa Kafin na haihu Naseer ya dawo inaso na ya dawo kafin ya haihu.
Cincin din danake Yi da Dankali da yamma shima ba karamin cinikinsa nake ba ahaka na Kara Tara kudi na siyi engine markade danaga layin namu babu masu engine markaden sai an fita titi.
Ba karamin ciniki nake ba da Wanan engine Dan Nadeeya da Zahira indai suna Nan ba islamiya haka zasuyi ta markaden ganin Ina samun kudi ko ta Ina yasa na fara gyara gidan namu Dan dakuna biyu ne kawai gyararru siminti nada araha a lokacin hakane yasa na siya wajen goma aka fara Mana plaster banida burin daya wuce na gyara gidan idan Naseer ya dawo yaji dadi a Ransa.
Kamar Wasa sai gashi nice har da pentin gidan gabadaya daga engine markade daya sai gashi na Kara ya zama guda biyu
Kayan abinci kuwa sai dai Nima na bawa wani Mai bukatar.
Yanzu da muka samu kwanciyar hankali banida burin daya wuce ganin mijina ko nasan halin da yake ciki har makarantar islamiyya su Zahira nake zuwa da waina na roki mallamin ya rabawa almajirai ya Tayani da Addu'a Akan Allah ya dawo min da mijina lafiya.
A Haka watarana daddare wajen karfe Takwas na iddar da sallah ishai Zahira tana tsakar gida tana markade.
Su Nadeeya Kuma suna tsakiyar palon Dana sakawa Leda suna home work dinsu
Ni Kuma Ina daga d'akina.
Haka kawai naji gabana ya yanke ya Fadi na ba gaira ba dalili hakane yasa carbina rik'e a hannuna na turo cikina na fito na tsaya a bakin kofa Ina kallon su Nadeeya jefi jefi Kuma Ina kallo tsakar gidan Sabida k'ofar Palon a bud'e yake Zahira na tsaye tana ta markaden
Banko k'ofar Gidan da akayi da k'arfi ne yasa na kalli k'ofar da Sauri gabana yayi wani irin fad'uwa dana hango Umma ta shigo Safiyya na biye da ita abaya.
Zahira kuwa Tana ganin ta ta saki robar hannunta ta kwaso aguje ta shigo palon ta buya abayana jikinta na rawa.
Umma da Safiyya kuwa a tsakiyar gidan Suka tsaya suna karewa koina kallo.
Ni kuwa sallati kawai nake jikina na rawa.........
*Nagode da kauna Allah ya saka da alheri ya bar zumunci Ina mutukar Kaunar Mai kaunata Fatima salis da Umma misbah Allah ya biya muku bukatanku na alheri Allah ya bar zumunci ga masu neman lambata ido rufe ga lambata Nan Mata kawai pls 08033719070*
8/19/21, 10:31 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 30*
"Lailai Ashe su Naeema haka aka samu duniya mu kuwa muna can muna garari Umma Kinga katon gidan da suke fa har tsinaniyar matar Yaya Tijjani ta ringa gasamu a wancan tsinannen gidan nata"
Cewar Safiyya tana zagaye tsakar gidan tare da lek'a ko'ina
Umma kuwa itama karewa koina kallo take
Ni kuwa ganin engine nata yi cikin Dan fad'uwar gaba na fito bansan Inda na aro jarumtaka ba na saki murmushi Ina "Umma Kune Ashe sannunku da zuwa"
Na karasa wajen da aka jona engine na kashe.
Daga Umma har Safiyya ba Wanda ya amsa gaisuwar da na musu illa ma cikina da suka bi da kallo wanan kallon tsanar kamar su jefani a wuta suka ringa Bina dashi nikuwa a Zuciyata na hau adduar tsari daga duk wani sharri.
Bana San na wuce ciki suga Kamar rashin kunya na musu hakan ne yasa nace "Umma ku Shiga daga ciki Mana kuka tsaya a tsakar gida"
"Ai ko baki fada ba zamu Shiga ciki tunda ba gidanki bane gidan Dana ne Koda kudinki Kika Gina"?
"Aaa"
"Ke Dan uwarki bakida wani aiki ne sai haihuwa yau Naga masifar jarrraba a gurin yarinya Nan ke kenan Ana tab'a ki sai ciki ko ya aka Dan kwana biyu ba a ganki ba indai aka tashi ganinki sai dai a ganki da ciki"
"Umma Ni bakin cikina ma duk Mata take ta Tarawa Yaya Naseer Bata tausaya Masa da talaucin da yake ciki ba gashi ta Kara k'unsar wani cikin"
Cewar Safiyya tana harara ta.
"Haka kawai da lodin yaran Nan zaiji da Kika tarasu duk Mata zaiji ko da me kikeso yaji na ce bana San ki ki rabu da Naseer Kika k'i ke a lailai sai kin zauna shine yanzu ma halin da Naseer yake ciki Baki duba ba Kika Kara kwasar wani cikin ko to shikenan ki haifeta nagani shegiya tsinaniya Mayya"
Fuuu Suka wuceni ni kuwa naji wani Abu ya tsayamin a mak'oshi sosai Raina ya b'aci da abinda Suka min Naga Yara matan Nan Allah ne ya bani Kuma cikin Nan ma shi ya bani insha Allahu lafiya Lau Zan haifi cikina sosai na ringa mamakin abinda yasa banji azabar tsoro da rawar jiki Dana Saba ji ba Dana tsaya dasu waje daya gabana ba tsinke ba Dana had'a Ido da Umma duk da na Riga da na Saba da Jin tsoronta ko Yaya ma naji muryarta Zan Dan ji fad'uwar gaba.
Cikin palon na Shiga ga mamakina basa cikin palon sai muryarsu naji Yana tashi a d'akina yarana Kuma suna rak'ube a waje daya Zahira kuwa jikinta sai rawa yake Nadeeya ma kina ganinta kinsan a tsorace take daidai da Raheema da take karamarsu sai data nutsu.
Idan a da ne ban Isa na Shiga d'akin ba Amma sai na tsinci kaina da shiga d'akin a tsakiyar d'akin umma ke tsaye Safiyya ita Kuma ta zauna akan gadon tana "dakuna biyu ne fa kawai Mai katifa da fanka mu dau wanan din kawai ita Kuma taje ta karata da yaran"
"Aaa Aunty Safiyya Wanan d'akina ne sai dai ku zabi na d'aya b'angaren tunda a na gyara"
Wani irin kallo Umma ta juyo ta min tana "iyyeee lailai wuyanki ya Isa yanka wato wanan dakinki ne sai dai mu zab'a a daya bangaren gidanki ne ko gidan Dana ke har kina da iko da gidanan har kina da Bakin zab'a Mana inda zamu Zauna iyye"?
"Kiyi hakuri Umma ba Wai zab'a Muku nake ba Naga can din ma yafi Nan girma lokacin da muka dawo gidanan iya dakuna biyun Nan Naseer ya iya gyara Mana da Palo sai Dana samu kudi na gyara can din"
"Ahap Umma kinji ko sai data samu kudi Ni Dama nasan Yaya Naseer da baya nan bin maza take Haba umma.kiga ga yanda gidanan aka gyara ko Ina na kyalli wlh Ni nasan a Rina karki yi mamaki ma cikin jikinta bana Naseer bane"
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Aunty Safiyya wane irin magana ne wanan ya Zaki min kazafi da Kuka shigo injina nawa Kika gani ban bi maza ba Ina gidanmu bana Jin yanzu da yarana da Aurena Zan bi maza Koda Naseer zaiyi shekara hamsin Bai dawo ba Zan rik'e amanar aurensa har sai ya dawo gareni"
Na karashe da Bakin ciki sharrin da Safiyya ke neman Yi min
"Allah ya Miki Albarka Safiyya badan kin ganota ba da Haka zata linkemu ta cuci Dana da baiji Bai gani ba ta lika Masa cikin da ba nasa ba maza tashi kije ki shigo Mana da kayan mu"
"Umma kiyi hakuri ku koma can d'akin wanan d'akina ne"
Mamaki ne ya rufe Safiyya da Umma Ni kuwa bansan Mai yasa naji ko kad'an banji tsoronsu ba Taya ma sama ta ka zasu zo su rasa Inda zasu zabi su zauna sai dakina Inama laifin wani d'akin inyaso sai na Kai musu katifar su Zahira yarana su dawo d'akina mu ringa kwana gabadaya duk da tun ranar da Naseer ya bar gidanan waje daya muke kwana dasu katifarsu suke daukowa su kawo d'akin su saka a kasa su uku su kwanta akai Ni kuma da Raheema da Humaira mu kwana a Kan gadon
"Kikace Nan dakinki ne Naeema da kudin ubanki aka Gina da har kike zab'a Mana inda zamu Zauna"?
Safiyya tace a fusace tana doso Inda nake a tsaye "Mahaifina Allah ya Masa rasuwa aunty Safiyya Dan Allah ki daina zaginsa bada kudina aka Gina ba Amma Nima akwai kudina a cikin gyaran gidan"
"Uwarki Kike jira Safiyya da Bazaki zubar Mata da hakora ba ki naushe min tsinane Nan cikin Nan Naga da wane baki zatayi magana"
Kamar Mai jiran umarni tayo kaina nayi Baya da Sauri ina San juyawa Amma na rasa Mai yasa na tsaya akan kafafuna Tana isowa ta daga hannunta kafin ta sauke shi a jikina na rik'e hannunta jikina na Dan rawa "Ina Wai Mai na muku a rayuwata ne Mai na muku kuke San kuka ga bayana kiji tsoron Allah aunty Safiyya karki manta kema mace ce bakisan ya rayuwa zata kasance Miki a gaba. Ba abinda na muku Kuna ta cutar Dani Yayanki ya gudu ya barni da yayansa cikin azabar talauci ban karaya ba na zame wa yayana uwa da uba nake neman kudin da Zan kula dasu wlh gidanan dakuna biyu ne kawai gyare sai Palo da kudina na gyara gidan Rana da ruwa Haka nake neman kudi duk Dan na gyara Masa abinda ya rage Masa iya wanan Bai Isa sarara min ba sai an biyoni Nan ma an takani karku manta fa Nima haifa ta akayi"
"Baki haifu ba Safiyya idan Kika Bari na karaso Baki bajeta a kasa ba"
Kara kwace hannunta ta fara k'ok'arin yi kafin kace me k'ok'awa ya kaure Mana tana ta k'ok'arin harbina a cikina a ranar Zan iya cewa yin Allah ne ba yina ba kuka nake a zuciye muna k'ok'awa da Safiyya bansan ya akai na kayar da ita ba duk da sai da bayana ya amsa na hau Kai Mata duka.
Umma a guje tazo kanmu da balain k'arfi ta damke kafadata ta Jani daga Kan Safiyya ta wurgar Dani ta cillo kafarta da zumar harbina a ciki sai gashi zaninta ya tad'e ta tayi zaman yan bori a kasa tana washhh bayana Dan ba karamin buguwa tayi a da kasa ba
Washh wash kawai take Tana "Itama ta Shiga kungiya Safiyya yanda Murja ta zanemu itama take San zanemu"
Safiyya Kara mik'ewa tayi tayo kaina Nima na mike da Sauri muka cigaba da k'ok'awan na Kara bajeta a kasa Ina kuka Ina "Kasheni zakuyi Mai na muku haka"
Umma sosai ta ringa k'ok'arin mik'ewa ta kasa yarana kuwa suka shigo d'akina aguje suka hau kuka suna Jana daga Kan Safiyya da ta samu Saar kaimin naushi a cikina sau biyu a karshe dataji azabar nauyina abinka da Mai ciki Nishi ma dak'yar takeyi
Hannuna ta Kama ta hau ciza hakane yasa na fusge tare da dagata Ina cigaba da kuka.
Ita kuwa ta mik'e ta zauna idonta ya kad'a yayi ja sai numfarfashi take.
"Zoki dagani ni nasan ba ita take da Karfin yi Miki dukan Nan ba kungiya ta Shiga Dani take maganar wlh ta janyowa kanta sai na gana Mata azaba da sai ta nemi mutuwa da kanta tashi ki dagani"
Umma tace tana cije lebb'e
Safiyya mik'ewa tayi tana "ba dai ni Kika daka ba wlh Zaki ci ubanki mu zuba nidake Kuma wlh d'akin nan zamu Zauna Zo ki fita damu nagani"
Ta karasa tana nufar wajen Umma tare da dagata tana wash wash suka nufi bakin gado ta zauna.
Ni kuwa tunda naji suna Zan ci ubana jikina ya hau rawa tsoro ya rufeni ban manta cikin Minal wuyan Dana Sha ba ban.manta kumburin da nayi a cikinta ba Ina tono wahalar Dana Sha gabana har fad'uwa yake zama nayi a d'akin Nima a kasa.
Yarana suka zagayeni Umma da Safiyya kuwa sukayita zagina suna tsinemin yarana kam ta musu baki yafi cikin kwando duk Kuma a cikinsu sunfi zagin Zahira da ta d'auko komai nawa har da tsoro sosai.nake hango kiyayyar da suke Mata na daban ne ita kuwa jikinta sai rawa yake kamar ta tsaga jikina ta shige Nadeeya ita ma sai kuka take kasa kasa.
"Ki tashi ki dauko Mana abinci Dan uwarki ko sai mun roka"?
Umma tace tana jifana da harara
Ni kuwa ko gezau banyi ba Dan gani nake idan na bar d'akin Yar tsana Mai ciki zasu binne a bakin k'ofata na hau kumbura kamar lokacin cikin Minal zuwa yanzu da zasu lura zasu ga azabar rawar da jikina yake sabida tsoro.
Haka suka yi tamin magana na sharesu Suka cigaba da zagina a karshe sai Umma cewa Safiyya tayi ta fita ta samo musu abincin
Banyi magana ba Safiyya ta fice ta zubo tuwon Massara Dana tuka da miyar kubewa da har dumame nayi Dan yarana suna so Kuma basu ci abinci ba.
Haka suka zauna Akan gadona suna cin abinci
Mu kuwa muna rab'e a gefe Raheema ce ta hau zungurina Tana Jin yunwa sai kallonsu take.
Safiyya ta hau zaginsu tana basuda tarbiyya karuwai.
Sai anan nayi.magana Ina "yarana ba zasu tab'a karuwanci ba insha Allahu"
Kamar wacce aka tsikara na mike na nufi wajen da akwatin kayanmu yake dayake ba wardrobe a d'akin.
Na hau Kai akwatuna na waje sai Dana kwashe komai tsaf ya rage daga su sai.gadon da suke.kai.
Na fito da yarana cikin.kuka na cewa yarana su hau kai Mana kayanmu daya b'angaren.
Dake d'auke.da karamin Palo da dakuna manya guda biyu Dan ginin gidan Kamar na mai Mata biyu Naseer yayi sai da shi lokacin wanan da muka koma shine b'angarensa Wanda na barowa Umma shine b'angarena Dana yarana.
Dan gyaran danayi ma so nake na zuba Yan haya na fitar musu da kofa ta tsakar gidan ganin gidan ya Mana girma idan Ina Jin motsin mutane ma zanfi Jin dadi inyaso idan Naseer ya dawo sai na sallamesu sai gasu Umma sun duro.
Har tarkacen d'akin su Zahira sai da muka kwaso daga b'angaren
Na dawo dashi b'angaren Naseer na saka katifar d'akinsu a daki daya Zahira ta.musu shimfida.
Ni kuwa na Shiga kitchen na juyo musu tuwon a faranti da Miya har da ruwa na kullo kitchen din
Abinka da Yara Basu ma.wani San Mai ke faruwa ba sai zahira Nan da Nan suka hau ci.
Zahira.kuwa sai Daka Mata tsawa ta yarda ta fara ci Dan sosai ta Shiga damuwa da hawayen dake zubomin Ina daukewa haka na zauna Ina tunanin masifar dake neman kunno min tashin hankalina Bai wuce karsu cutar Dani ba Kar bacci ya d'aukeni su biyo dare su caka min wuka gashi Naseer baya Nan.
A Haka nayi zurfi a tunani har bacci yayi awon gaba da yarana Zahira ta gyara musu kwanciyarsu.
Tare da.kunna musu maganin sauro.
Sai data tab'ani na dawo daga duniyar tunanin Dana tafi.
Abincin da suka ci Suka rage ta kawo gabana cikin karyayar murya da tayi kasa.dashi sosai ta hau magana tana "Umma kiyi hakuri kici abinci insha Allahu ba Abunda zasu Miki"
Maganarta kuwa kamar tunzurani yayi na hau rera kuka Ina Mata surutai Kamar wata babba na hau Bata labarin irin abinda su Umma suke min Dana rasa Mai na musu suke San kasheni"
Bansani ba ko kwakwalwarta zata d'auki maganganuna kuka kawai take itama Ni kuwa na mike na fito karamin Palo Naga ko sun fito daga d'akina sai dai Ina lek'awan Naga har sun turo k'ofar sun rufe Kamar d'akinsu.
Ina mamakin Halin Umma da Safiyya k'arfi da yaji sun kwace min d'akina.
Haka na koma dakina Ina Jin inama inada halin da Zan samu kudi Mai yawa a daren Nan na kwashe yarana na bar musu gidan.
Tunda na samu ciki Ina da Jin bacci ina Kuma bacci Mai nauyi ban fiye tashin dare ba idan bacci ya d'aukeni Amma zuwansu Umma yasa na nemi baccin na rasa Zahira itama haka ta zauna wajen karfe daya na dauro alwala Ina kallon Zahira ta biyoni itama tayi alawalar tazo gefena ta tsaya muka hau nafilfili.
Ban iya yin raka'oi Mai yawa ba na zauna na dau carbi nayita sallati da istigifari har lokacin hawaye Bai d'auke daga idona ba sosai na saka a Raina a wanan lokacin da wasu ke bacci Ni Kuma na zo gaban Mahallicina ina kuka zai magance min damuwata A da Inada Allah Ina da Naseer Amma yanzu banida kowa sai sarkin sarakai da baya zalunci da idan ka Kai kukanka wajensa zai magance maka damuwar ka Ni nasan badan baya sona nake rayuwar azaba a gidan Naseer ba yanda ya halliceni Haka ya hallici Umma dake neman rayuwata shi Zan kaiwa kararta yamin maganinta yau ko Umma tayi nassarar kasheni nasan a rubuce yake a ita zata zama silar mutuwata Dan kowa da hanyar tafiyar sa.
Tsabar Jan carbi da adduar zuci sai da yatsuna Suka hau ciwo.
Inajin Zahira na adduar "Allah kasa Kar suyi wa Umma komai Allah ka dawo da Abban mu lafiya Allah kasa Kar su cutar damu su cutar da Ummana"
Ahaka ta Gama hada Addu'ointa bacci ya d'auketa Nima bansan lokacin da bacci yayi awon gaba dani kaina jingine da bango ba
*2am*
Hajara ce zaune da Safiyya a tsakar d'akin da wani bak'in tukunya suka dibi abinda shugaba ta basu Suka watsa take hayaki ya fara gauraye d'akin Shugaba ta bayyana da fitila a hannunta
Safiyya da Umma Suka zub'e a kasa Umma ta hau magana "Naeema yau dukan Safiyya tayi Nima ta zubar Dani a kasa a sanadinta nayiwa Dan cikina mugunta ya rasa komai nasa na