Showing 84001 words to 87000 words out of 180103 words
nunamin ya gwammace ya rabu Dani mahaifiyarsa daya rabu dake fitarkin shine ki kwashe yaran naki ki bar gidanan kqmar yanda Kika fada idan ba Haka ba sai na samu cikar burina akanki Zan samu kwanciyar hankali bana kaunarki bana jin akwai ranar da Zan kaunaceki na gwammace ya auro koma wacece da dai ya cigaba da zama dake Ban taba ganin yarinya mai taurin Kai irinki ba gashi sai cika gidan Naseer kike da mata marasa tarbiyya masu irin halinki kiyi addua Kar wani Abu ya Samu Safiyya idan ba Haka ba zakiyi mamakin abinda Zan Miki
"Wane dare ne jemage Bai gani ba Umma mai zakimin da zai zame min sabo magani kuka zuba abinci Dan naci Allah ya tsareni ya Dubi zuciyata Ita data zuba garin magani da kanta Kuma ta d'auko abincin taci iya wanan ya Isa kigane Umma Allah ba azzallmin sarki bane Koda wani Abu ya Samu Safiyya ita ta jawowa kanta Dan ta Haka Ramin da Zan fada da zurfi sai ya zama itace ta fada"
Fuuu ta taso tayo wajena abinka da Mai ciki kafin na mik'e har ta iso ta rufeni da duka tana zagin uwata da ubana wai.maganar da nake Mata rashin kunya ce
Nidai fuskata da cikina kawai nake ta karewa Ina cigaba da Magana cikin kuka da a ce Safiyya ce zanyi k'ok'arin Rama dukan da tamin Amma wanan mahaifiyar Naseer ce bazan iya ramawa ba ko maganar da nake ta fada Mata baa San Raina nake fada ba Dan gani nake dgske rashin kunya nake Mata Amma Naga sai nayi maganar Zan jin sanyi a Zuciyata sai data gaji Dan kanta ta kyalleni na mik'e dak'yar na Shiga d'akina jikina namin ciwon dukan da Umma tamin.
Kuka nayita yi Ina tunanin Abunda ya dace nayi Sosai nake ji Kamar na hada kayanmu a goben Nan mu bar musu gidan.
Sai dai karatun yarana da suke tsaka da yinsa suna Kuma Jin dadinsa na hau tunani yanzu suna zango na karshe da zaayi canjen aji Zahira ta tafi primary 4 badan rayuwa data juya ba yaci ace tana jss 2 Nadeeya Kuma tana primary 3.
Shigowar Umma a fusace yasa na mik'e zaune Dan a kwance nake
dube dube da hau yi bance Mata komai ba ta hau daddaga kayana tana watsi dasu.
Nidai Ido na zuba Ina kallon ikon Allah sai data hargitsa d'akin ta juyo a fusace ta mik'amin hannu tana "Bani Kudi Zan Kai Safiyya asibiti Dan ta zubar da jini da yawa Ina binki cikin Salama Naeema kulleki a d'akin Nan na banka Miki wuta ba wahala zaimin ba Maza bani kudi karki batamin lokaci.
Sauka nayi daga Kan katifar na d'aga na Ciro kudin da na kakkasa a.karkashin katifar na zaro dayake ware biyar biyar goma goma.har zuwa hamsin nayi cikin Ikon Allah kuwa biyar biyar din na zaro.ina k'ok'arin duba kudin ta fusge daga hannuna tayi waje.
Inajin motsin fitarsu a daidai lokacin da Isihu ya dawo Ni kuwa na mike na fita jinin palon Naga Yana bi da kallo Ni kuwa na bashi umarnin ya wanke palon gabadaya Ina tsaye a bakin kofar karamin palon ya wanke palon sai karni ke tashi hakane yasa na saka ya amso min garwashi muka saka turare wuta Nasa ya Shiga karamin Palo na zubo Masa abincin da lokacin tafiya da ruwa.da.zobon yayi.
Sai daya fara ci ya ke gayamin kudin katifar dana saka ya tambayomin.
Ban ce Masa komai ba Dan yanzu Bata katifa nake ba wani abune Kuma a Raina.
Sai daya gama cin abinci ya fita da ruwa da zobon da sukayi sanyi sosai akwai wani shima dake tayashi dauka Suka tafi
Ina nan a zaune su Zahira suka dawo.
Sukaci abinci suka Kara gyara gidan har lokacin su Umma Basu dawo ba.
Har Isihu ya dawo ya Kara fita da wani ruwa da zobon.
Zahira da Nadeeya kafin su tafi islamiyya.suna ta Tayani markade sai da lokaci yayi suka.shirya.suka tafi.
Na cigaba da markaden wajen hudu da rabbi Isihu ya dawo lokacin na Gama markaden na hade Kan kudadena na zuba su a Leda Dana kasan gadon na canza musu wajen ajiya.
Na saka hijabina na kulle gidan na nufi makarantarsu su Zahira.
Mallam ala ramma shine babba a makaranta Yana da balain mutunci Isihu na saka ya kiramin shi
Yana zuwa na tsugunna na gaishe.shi shima sabida sanin darajar mutum Haka shima ya zub'e yasan komai a Kan gidana yasan babbnsu Zahira baya Nan Ni na fada Masa sabida shima sananne ne a unguwar Kar Yan unguwar suga ba namiji a gidan su Raina min hankali.
Koda yanzu shawara na yanke Na Masa magana Ina bukatar ayimin sauka a gidana ko na kwana bakwai ne sabida Allah ya Kara tsareni daga sharrinsu Umma da lokacin da Naseer ke Nan ne da sauki yanzu daga Ni sai yarana Ina bukatar tsari daga sharrin masu sharri.
Banma Gama iddawa ba yace min Kar nadamu zai turo yaransa su ringa zuwa karfe Tara suna karatun Qurani a gidan karfe goma sai su dawo zasuyi Haka har tsawon kwana bakwai zai Kuma ringa min addua daga nan Akan Allah ya saukeni lafiya ya dawo da mijina lafiya.
Godiya na ringa Masa na dauko kudin sadaka na bashi ya dage bazai karba ba ahaka na dawo gida Ina Dan Jin nutsuwa insha Allahu albarkacin Quranin da zaa sauke a gidan ba abinda su umma zasu min.
Tundaga nesa na hango masu markade da Umma da.safiyya a zaune a k'ofar Gidan.umma Nata magana tana yarfa hannu alamar masifa take sun dawo na fita na kulle gidan
Safiyya kuwa ta Yi wani sanyi kalau Dan kwance ma.take jikin Umma
Ina karasawa Umma.ta hau zagina wai.na tafi.karuwanci na kulle gidan bazata laminta ba daga Yau idan Zan tafi gantalina Kar na Kara kulle mata gida Agaban wayanda Suka kawo markade tayi ta zagina har na bude na Shiga suka shigo ni kuwa na kunna engine na fara markaden
Ahaka na bawa banza ajiyarsu Safiyya Bata iya magana sai Umma
Sai wajen Shidda na Gama markaden a daidai lokacin dasu Zahira suka dawo
Muka Shiga babban palon gabadaya Zahira na hada Ido da Umma ta zub'e ta hau gaisheta.
Kannenta take suma Suka zub'e suna gaida Umma.Minal ce ta tsaya cak Bata zub'e ba hasali ma cunno bakinta tayi ta kau da Kai.
"Shegu Yan iska marasa tarbiyya uwarku duk ta koya muku munafinci da gulma ke Dan uban uwarki wa.kike cunnowa Baki"?
Umma tace tare da mik'ewa su Zahira kuwa kafin ta karaso suka baje Suka shige Palona a guje.
Amma Minal ko gezau batayi ba Ina tsaye Nima a bakin kofar mamakin abinda Minal din tayi nake.
Umma kuwa Tana Isa wajenta ta rufeta da duka Ni kuwa na runtse idona inaji kamar Ni take bugu sai cewa Minal take tsinaniya Minal ko tari batayi ba ballantana tayi kuka kafa ta daga zatayi ball da Minal sai gashi kamar Jiya zaninta ya tadeta ta tafi gabadaya akan fusktarta ta Fadi.
Minal dariya ta kyalkyale dashi ta nufo palona a guje tare da tureni danake bakin kofa
Umma.kuwa ta dago tana rik'e da bakinta data Bugu sosai ta hau zagin Minal "Tana tsinaniya yarinya Mara albarka Zan kamaki idan uwarki ce ma ta zugaki kikamin Haka akanta Zan Rama ke Kuma zaki.bamu abinci muci ko sai mun roka"
Bance komai ba na juya na Shiga palona Ina zuwa na rik'e hannun Minal Tare da Jan kunnenta na hau Mata fadan rashin.kunyar da tayi wa Umma a yarana Ni nasan Minal nada zuciya bansan ta had'a har da rashin kunya ba
Hakuri tayi ta bani akan bazata sake ba
Ni kuwa na zuba abinci a flask.
Da Zan aiki Zahira ta Kai na tuna halin Umma na Kai abinci na ajiye musu a Palo Dan sun shige daki sai Masifa take ita kadai.
Daki na dawo nayi Sallah na juye Mana abincinmu a faranti muka ci gabadaya.
Ahaka mukayi sallar Isha ban Kara Jin motsin su Umma ba Ido na rufe Ina Jin gajiya da ciwon jiki Naseer na fad'omin a Rai inasan naji haushinsa a Zuciyata na kasa inaji kamar Inda yake wuya yake Sha.
Ahaka nayi zurfi a tunanin halin da Naseer yake da Kuma dalilinsa nak'i waiwayarmu motsin da naji cikina yayi ya Sakani sakin murmushi tare da bud'e idona Dan wani ikon Allah indai Zan Yi tunanin Naseer sai cikina ya motsa Ni nasan macece a cikina Dan na riga da na cire Rai da haihuwar maza inama cikin jikina namiji ne na haifo Mai Kama da Naseer.
Su Zahira Ina kallonsu Suka Gama home work dinsu Humaira da Raheema da Minal tuni bacci yayi awon gaba dasu.
Akan katifa ta kwantar dasu ta shimfida bargo ita da Minal suka kwanta a kasa.
Sallama Isihu danaji a Palo yasa na fita Inda yake sanarmin masu karatun sun zo
Iso nace ya musu na Kara shimfida musu tabarma a babban Palo
Suna shigowa Umma ta fito da Daurin kirji tana binsu da kallo ban kalleta ba nace su zauna su fara karatun
Kafin ma tayi Magana na koma ciki abuna
Ina Jin muryar ta tana Ashe maza nake kawowa gidan karuwanci ma Agaban idonta zanyi na shigo da Tika tikan maza hudu su kuwa Suna ganin alamar rigimamiya ce Basu saurareta ba Suka hau bud'e Quraninsu suka hau karatunsu.
Sai goma Suka gama suka tafi.
Na fito na kulle gidan
Hankalina a kwance a ranar ma ban wani Yi bacci ba sai Dana rayya daren.
Kafin bacci yayi awon gaba dani da asuba Ina iddar da sallah na Dora Mana abinci kamar dai jiya na Mana tazarce na Kai komai d'akina na ajiyewa su Umma nasu a kitchen.
Sosai nake taka tsantsan da duk abinda zanci.
Indai zanyi girki bana barin kitchen sai na Gama ko cokali na daina Bari a kitchen din sai risho
Tsakanina da Umma kuwa zagi ne da tsinuwa idan tsautsayi yasa yarana suka Dan tsaya wajen da take sai ta Kai hannu jikinsu
Safiyya kuwa Bata samu kwarin jikinta ba sai da aka yi sati biyu itama ta cigaba da Taya Umma wajen musgunamin Amma ban taba tanka musu ba indai Safiyya tamin sai na rama.
Alaramma har cassete ya aikomin Mai dauke da izzu sittin na siyo karamin radio na ringa kunnawa duk dare.
Ni kuwa ganin na samu kudi dayawa yasa na siyi katifar na saka a daya dakin har da sip Mai saukin kudi na sakawa su Zahira.
Cikina na da wata takwas da sati biyu na siyo kayan jaririrai na mata mai saukin kudi shima.
Sosai nake adduar Allah ya saukeni lafiya Dan insha Allahu indai na haihu na samu kaina sai na bar gidan Amma bazan tafi ba sai na siyar da gidan tunda takardun gidan. Na wajena.
Hakane yasa na cigaba da Tara kudina Banda dashin da nake.
Yanzu wani Abu da su Umma suka tsiromin idan nayi girki sai suce bashi zasu ci ba sai su zabi wani abincin suce shi zasu ci
Idan nace babu bazasu cemin komai ba sai sun ga Isihu ya dawo daga tallan Yana shigowa sai su kwace kudin
Sau uku suna min Haka Ni kuwa nace ya daina kawomin kudin ya ringa kaiwa matar Ala ramma Dan muna mutunci da ita Nan ma ban tsira ba idan nayi markade na Gama hada kudin sai Umma tazo da k'arfi ta rabani da wani abun.
Sosai zamana dasu waje daya ya gundureni na matsu na haihu na bar gidan.
Wanan ma Bai musu ba da suka ga Ina d'auke Kai sai Suka koma Kan zahira
Tana dawowa daga makaranta Umma da Safiyya zasu tsiri sakata aiki tayi.musu wanki ta wanke.musu bandaki sunayi suna zaginta wani zubin har duka suke Kai.mata tun Ina kawaici Naga abin ya fara yawa Dan ta Kai ma sai ta shirya zasu tafi islamiyya Haka Safiyya zata kirata ta hau sakata aiki karshenta makaranta da bazata je ba kenan tana Shan aiki.
Ni kuwa ganin abin yayi yawa yasa na fara takawa Safiyya birki idan ga saka ta aiki zance ta Bari sai ta dawo
Anan Umma zata hau zagina bana ce musu komai
Amma Zan rik'e hannun Zahira tabi Yan uwanta.
Idan Kuma ba ranakun makaranta bane a daki nake cewa tayi Zamanta karshenta sai Umma ta biyoni har d'akin ta min tas daga Ni har Zahira Tana Shan mugayen alwashi akanmu .
Ahaka Watarana lokacin daya kasance alhamis ba makaranta Ina kitchen Ina girki Zahira namin markade Nadeeya Kuma na wanke uniform din bokonsu.
Minal Kuma tana Taya su Humaira home work
Umma da Safiyya suka fito daga d'aki hannayensu d'auke da lodin wanki
Kansu tsaye suka.nufi wajen da Zahira take suke zuba kayan wankin a kasa Safiyya ta Kai hannu ta kashe engine tana "ke maza hada Mana kayan Nan ki wanke Mana yanzu yanzu"
Na gaji sun kaini bango
Ludayin hannuna na ajiye na nufi wajensu Ina "Nagaji aunty Safiyya Kun takura wa yata Kun hanata sukuni koni kuka bawa wankin Nan bazan iya ba sabida yawansu ku Bari na nemi almajiri yazo ya muku Zahira bazata iya wankin Nan ba"
"Wlh ita zata Mana wankin Dan uwarki ke Nan kin dauka tarbiyya kike musu yaranki ma baa Isa a saka su aiki ba"
Umma tace tana k'ok'arin jawo Zahira da har ta fara kuka jikinta na rawa.
Ni kuwa na shiga tsakiyarsu Ina "Wlh bazata yi wankin Nan ba"
A zuciye umma.ta saka hannu biyu ta hankadani
Yarana Suka saki ihu gabadaya nima na Gama sadakarwa fad'uwar Nan da zanyi na iya haddasa min komai amma a madadin najini a kasa sai ji nayi na an tareni ban Kai kasa ba.
Bud'e idona nayi na kalli Wanda ya tareni numfashina naji Yana neman daukewa da mukayi Ido biyu.......
🙆🏻♀️NAGA TA KAINA🙆🏻♀?
Page 1 to 30
Assalamu alaikum barka da warhaka🙋🏻♀?
Ta bangarena abinda na samu acikin wannan buk din shine
1-duk wani dabara da wayo naka da wani inda-inda bazai taba sawa ka gujewa kaddarar da Allah ya rubuto makabah ako'ina kake sai dai addu'ah tana ragemata kaifi sosai fiye da tinani mai tonani dan idan ba karfin addu'ah ba babu wanda zai taba tinanin naema zata rayu kafin ta haifi nadeeya kinga kuwa addu'ah ce taragewa wannan kaddar tata kaifi ta dawo mata da hankalin mijinta a ranar da aka yanke mutuwa zatayi
2- akwai riko da addini, sallah akan lokaci da yawaita addu'o'i da kuma rage yawan bacci da daddare, sallah shine jogsran
cewa kai cikakken musulmi ne sannan sallah akan lokaci yana tunkude masibu kala-kala. Addu'o'i suna rage kaifin kaddara wani lokacin ma yakan chanja maka ita daga mummuna zuwa kyakykyawa sannan takan shiga tsakanin nagari da mugu misali a page 30 din nan karfin addu'ah ne ya ceci naeema akan hajara da ta fadi kunkuru ya rike mudage da addu'a koda lokacin bamuda tsarki a jikinmu.
3- Hakuri wanda yaxama jagora akan rayuwar zaman duniya wanda shine yake zaune da naeema agidan naseer har wannan lokacin Allah yakara mana hakuri da imani
4- Biyayya koda kuwa wanda kake yiwa baya gani indai akwai hakkin biyayyarshi akanka to kayi iya bakin kokarin ka matukar batakaika ga shirka ba biyayya ma wani babban jagora ne arayuwa misali, koda babu auren naseer akan naemah a yanxu tinda har 'ya'ya suka shiga tsakani to akwai hakkin biyayya atsakanin umma da naeema Allah yasa mudace👏🏻
5- neman nakai rashin zaman banza da ace naema ta cigaba da zaman banza babu sana'a da ayanxu sun tagayyara arayuwa Amma dayake ita sana'a maganin takaici kuma idan ka dace da Allah ya sa maka albarka akai to wllh zaka samu rufin asiri acikinta. Ina bama 'yan'uwanmu mata akan mutashi munemi sana'a dan zaman banza na abune mai amfani bah.
Allah yakara rufamana asiri duniya da lahira yasa muyi kyakykyawan karshe yamana katangar karfe da makiyanmu aduk inda suke
Ina mika jinjinata ga sadnaf daya tamkar dubu Allah ya kara baseera ya biyaki albarkacin wannan fadakarwar da kike
Ina mika gaisuwata ga naeema jarumar mata Allah yayi ma rayuwar 'ya'yanki albarka ya karamana hakurin zaman duniya
Mrs naseer ceh👉🏻
8/19/21, 10:31 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 32*
*ZAFIN NEMA*
*baya kawo samu*
Lokacin da Naseer ya bar gida Bai zame ko'ina ba sai Tasha baiji tsoron duhun dare ko karnuka ba Haka ya rungume kayansa kala biyu ya rungume a kirjinsa ya samu waje ya zauna dan lokacin ba wani motoci Haka ya zabga tagumi Yana tunanin Naeema daya bari da Yara Yana tunanin Anya shawarar daya yanke Na guduwa ya nemi kudi shi ya dace yayi ko kuwa ya koma su cigaba da zama a haka.
Ko shi daya fito daga gida Bai San garin daya nufa ba.
Ahaka ya zauna zuciya fal da tunani har akayi Kiran a sallah asuba
Ya nufi Massallaci dake kusa da tashar yayi Sallah Asuba sosai yayi ta addua Akan iyalinsa Ji yake kamar Bai kyautawa Naeema ba kamar tafiyar tashi ba mafita bace a garesu Amma tunanin barin garin ya danne tunanin Haka a Ransa.
Karfe Bakwai yaga wani karamin mota na loda fasinja Abuja
Haka ya shige motar Yana tunanin zuwansa Abuja zai saka ya samu kudi.
Duk tafiyar da suka Sha zaune kawai yake a cikin motar Yana tunanin Naeema zuwa yanzu yasan ta tashi taga wasikar da ya bar Mata ko ya zataji a ranta.
Sai da wani a gefensa ya taba shi ya dawo daga duniyar tunanin Daya tafi
Nan fa Kuma daya Bai San Ina zai nufa ba Bai Kuma San ta Inda zai fara ba
Hakane yasa ya sauka daga motar ya samu wani benci ya zauna.
Yana kalle kallen mutane pure water kawai yayi ta durawa cikinsa.
A takaice Haka yayi ta zama a cikin tashar har tsawon sati guda Dan ya lura Abuja ba kamar Kano ba kowa shaanin gabansa yake.
Wani Abdullahi Mai lodin mota daga Kano zuwa Abuja ne ya fara Gane halin da Naseer yake ciki.
Dan ya Dan Saba da Naseer a Haka Naseer ya Dan bashi labarin halin da yake ciki shi kuwa ya Masa alkawarin taimaka masa ta hanyar nemo Masa motar haya ya ringa ja.
Cikin Sati daya da maganar Abdullahi ya had'ashi da wani Alhaji Idris