Showing 90001 words to 93000 words out of 180103 words

Chapter 31 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2464

ta siyi engine biyu Kai Kaga irin kudin datake rik'ewa kuwa Amma dayake zuciyarka ta mace idonka ya rufe duk baka gani ba ka hau rawar kafar ta haifo ma namiji indai Jininka ne ai mace zata haifo iya wanann ma ya Isa yasa ka Gane Dan Nan ba naka bane"


Yanda nakejin zuciyata da jirin dake d'ibana sabida tsananin bakinciiki sheganta min da da Umma keyi da kazafin da take neman yimin yasa.na shige palon Dan Ina cigaba da tsayuwa zuciyata zata iya bugawa Ni Kam wane irin nauyin kiyaya Umma zata gwadamin Wanda Bata gwadamin ba ya isa Haka ai batare aka halliceni da Naseer ba tafiyar Naseer ban fasa numfashi da rayuwa ba Dan Haka barin rayuwar Naseer na huta bazai Hana shi rayuwa ba Haka Nima idan akwai abinda ke damuna Bai wuce yarana ba Dan Ni nasan matsawar na tafi dasu kamar inasan Naseer ya dawo rayuwata ne.

D'akina na Shiga na kwanta ganin Banga kayan makarantarsu Zahira da jakunnan makarantarsu ba yasa nasan sun tafi makaranta.

Hawaye kawai nake Ina tunanin hanyar da Zan bi wajen barin rayuwar Naseer na har abada.

Allah yasan Ina kaunarsa Amma ya zama Dole mu rabu idan kuwa ya zargeni sabida bashida kudi na rabu dashi baimin adalci ba Dan ko kanwarsa ake matsawa Haka ya Bata shawarar ta hakura da auren.

Ina jiyo Naseer na Mata kana Nan rantsuwa Akan yasan Halina ko shekara goma zaiyi Zan rik'e Masa amanar aurensa wlh Dan Nan NASA ne Dan Allah ta karbi jaririn taga yanda Suke kama.

Ita kuwa Umma dagewa kawai take Tana rantsuwar ba dansa bane Wai Ni Mata nake Haifowa inaji tana balai Yana Bata hakuri.

Inaga Safiyya ce ta saka Baki naji ya daka Mata wani uban tsawa daya saka jaririna razana ya saka kuka.


Naseer kuwa kukansa Bai sa ya bar wanke Safiyya.kamar zai ajiye jaririn ya rufeta da duka ba yayi ta cewa ta Kai shi bango wlh xai koreta daga gidansa Dan bazata Zo tana hura Masa wuta a gida ba shiyasan wani zubin ita ke zuga Umma.

Ita kuwa Umma cewa take "Kar ka wani wayance Ni zaka yiwa fada ba ita ba tunda Ni nake Maka magana"

Kukan Jaririn yasa Naseer bai ce wa Umma komai ba ya nufo d'akina Ransa a balain b'ace Yana shigowa d'akin.

Ya mikomin shi na karbe shi take kuwa yayi shiru na Ciro abincinsa na saka Masa a baki tare da bismillahi ya kuwa cafe da Sauri a fili nace "Allah ya rayaka Walid ya shiryaka bisa tafarkin musulunci"

Ameen Naseer yace can kasar murya idonsa ya kad'a yayi jawur ban nuna Masa naji Haushin abinda umma tamin a fuska ba Amma ya juyo ya hau bani hakuri Yana na taimaka masa mahaifiyarsa ce babu yanda zaiyi da ita Yana Nan Yana gayawa Allah.

Murmushi kawai nayi Dan daya bani hakuri da Kar ya bani hakuri na Riga da na yanke hukunci a raina.

Ce Masa nayi ba komai kar ya damu.

Sai a lokacin ya saki ajiyar zuciya masu markade da suka zo yasa ya mik'e Yana Bari ya markada musu.

Amma kafin Nan Bari ya saka Safiyya ta dafamin ruwan tea da Sauri na ce ba sai ya sakata ba ya Bari na Gama bashi Zan fito na Dora ruwan da kaina tunda Dama Ina bukatar ruwa Mai yawa sabida ma nayi wanka na wanke Walid.

Har zai Musa min Kuma ya fasa Yana bari ya fara doramin ruwan inyaso sai ya fara markaden.

Nima.fada kawai nayi bazan iya tashi ba sabida jirin danake ji.

A kitchen ya tarar da Safiyya itama ta juye musu ruwan zafi a jug ga kwai ta soya a faranti duk a kudin Naeema da suke Mata fin k'arfi su kwace.

Yanda Naseer ya hade Rai yasa ta fice daga kitchen din da Sauri.

Tana fita ya Dora ruwa a babban tukunya ya fito ya kunna engine ya fara markaden.

Yana cikin yi ma Isihu ya shigo ya fara markaden.

Shi kuwa Naseer ya koma.dakin ya d'auko ledar zanin da Naeema ta Bata ya zuba a katon baho dayake akwai Omo da dettol a bandaki ya zuba ya koma kitchen

Ganin ruwan yayi zafi sosai yasa ya cika flask ya Kai daki ya juya sauran a katon Bokiti.

Duk abinda yake Umma da Safiyya binsa kawai suke da kallo.

Umma kuwa kamar ta fashe Dan bakin cikin yanda Naseer yake neman Zama bawan Naeema

Shayi Mai kauri ya hadamin ni kuwa na fara sha

Ganin Yana k'ok'arin fita yasa nace Masa Dan Allah ya bawa Isihu kudi idan ya gama markaden ya siyo.min nama bakina ba dadi.

Zama yayi a gefena Yana "Naeema ba asan Raina Kika haihu banida ko sisi ba wlh bana Jin dadi Amma ba yanda zanyi Haka Allah ya hukunta Naeema na baki labarin ban zo gidanan da ko biyar ba Kar muzo muyita kashe kudin ya Kare kiyi maneji da Abunda Kika samu gaba idan Allah ya hore duk Zan Miki Abunda ban miki ba a haihuwar Nan"

Murmushi nayi na ajiye kofin hannuna Dana Gama shanye shayin na kalli Naseer Ina "Naseer karka damu Ni Mai fadawa wani ne halinka idan kana dashi ma baya b'uya amma karka damu Ina da kudi ba iya na hannunka ne damu ba a d'akin Nan ma akwai kudi Banda dashin danake har ajiya nake badawa ka Bari idan na samu Kaina sosai zamuyi shawara ko zaka fitar da shago ka Dan zuba provision ka ringa siyarwa da zaman hakan.

Tun kafin na karasa Naga Naseer ya washe baki ya hau murna Yana shimin albarka.

Yana "Kice idan su Zahira sun dawo na fita kasuwa da kaina na siyo Dana Kaya Dan Naga kayan mata Kika siyo Masa yanzu na kashe duk kudin wajena"?


"Gyad'a Masa Kai nayi Ina murmushi"

Ya fice waje da Sauri Yana murmushi Ni kuwa Jin na Dan ji kwarin jikina yasa na mik'e na hada ruwan zafi a na wanke Walid na shirya shi na rufo kofata Nima na Shiga wankan.

Naseer kuwa Yana fitowa daga d'akina kayan Naeema daya jika ya sunkuya Dan ya wanke.

Hajara ta mik'e a fusace Tare da daka Masa wani uban tsawa "Kai yanzu Dan asara da mutuwar zuciya Mai aiki Naeema ta maidaka kenan sabida baka da kudi shine ta hadoka da wankinta kayi Mata kana matsayin mijinta?


Da lokacin da kake da kudi Kai kake mata wankin dayake Bata da mutunci sabida taga bakada ko sisi shine zata ce ka wanke mata kayan jini toh wlh bazaka wanke ba indai nice na Haifeka bazaka yi wankin Nan ba"

"Umma wlh Ni nake Mata wanki idan ta haihu bawai ita ta Sakani ba Dan gani nake Bata da Mai matan idan bani ba"

"Toh wlh bazaka wanke ba idan Kuma ban Isa dakai ba zaka iya wanke Mata"


Umma tace tana jijjiga k'afa.

Duk Inda Naseer yaso shawo Kan Umma tub'urewa tayi.

Ni kuwa Ina Jin duk abinda ke faruwa hakane yasa Ina saka Kaya na fito

Ban ko kalli Inda Umma da Naseer suke tsaye cirko cirko ba na jawo bahon na hau wanke kayana.

Umma kuwa ta hau zagina tana ita tasan asirce mata da nayi ban Isa na bautar Mata da D'a ba.

Bance Mata komai ba Naseer kuwa kamar yayi kuka sai neman kwayar idona yake Dan ya bani hakuri nak'i kallonsa.

Sai Dana Gama wankina na shanya na Shiga kitchen Dan Ni Dama tunda na auri Naseer bansan Zama Wai na huta idan na haihu ba Ni nake komai nawa.

Girki na Dora naje na dauki robar custard da gwangwanin da ya cika da kudin markade

Na zuba a ledar dana gani na ajiye gwangwanin custard din na koma d'akina.

Ina cikin had'a kudin Naseer ya shigo yana k'ok'arin Magana nayi sauri na dakatar dashi.

Ina Kar yace komai indai Umma ce na Riga da na Saba da kome zatamin ba wani Abu sabo.

Bai iya cemin komai ba yayi shiru Ina Gama hada Kan kudin na cusa a akwatina ganin waleed na bacci yasa na Kara barin d'akin na koma kitchen na zauna Dan girkina yayi na sauke.

Ina cikin juye abincin su Zahira suka dawo.

Ina ganin ta dawo na bar kitchen din dan nasan zata karasa min girkin.

Su Minal kuwa d'akina sukayi aguje suna murna sunyi Kani irin murnar da suke ne Yasa na manta da damuwar da nake ciki.

A takaice da kudina na wajen Naseer Naseer ya siyowa Waleed Kaya har dasu Zahira ya taho da Naman danace Masa.

Duk abinda Muke ciki Umma idonta na Kai.


Kudin dashina kwana uku da haihuwa nasa aka karbomin na bawa Isihu Dubu goma akan ya kaiwa Matar Ala.ramma Dan a gidansu na siyi katon ragon da zaa yanka duk da ba haihuwar fari nayi ba Amma kasancewar namiji ne hakane yasa na saki bakin Aljihu nayi dinkuna nayi komai na taron Sunan Waleed Naseer sosai.nake ganin farinciki kwance a fuskarsa Dan shima burinsa yayi taron Amma bashida kudi

Shima dinki na Masa kala biyu.

Umma kuwa ta Kira shi ta hau balai tana masifar sai ya tambayeni Ina na samu kudi Haka sanan ya zaayi nayiwa kowa dinki har da shege Isihu ita da Safiyya ban.musu ba.


Naseer kuwa ce Mata yake ba shi yayi dinki ba Ni na musu komai.na gidan Ni nayi.

Ita kuwa Umma dagewa tayi sai Nima na musu dinki.

Ni kuwa Naseer da Yar murya ya zo wajena Yana na bashi Rance Ni kuwa na murzawa idona toka nace Masa bazan bayar ba Dan kudin karuwanci ne Ashe Umma na labe tana jinmu ita kuwa ta hau tsinemin tana gwara Kar na Bata mantawa.ma tayi kudin karuwanci ne.


Sosai sunan Waleed ya cika da mutane har k'ofar gida.

Abinci kuwa sai da aka rabawa mak'ota mmn Mannir ma sai data zomin itama da abun arzkiki har da.makotana da mukayi zaman mutunci dasu.


Na yarda idan kana da abin hannun ka mutane har rububin muamalla suke Yi dakai.

Bazan iya lissafa Abubuwan Dana samu a sunan Walid ba Dan har na kusa maida kudin Dana kashe masu kawomin markade da customers Dina masu siyan zobo da ruwa duk baa barsu a baya ba Haka suka ringa zuwarmin barka da abin arziki.

Daga Ni har yarana da Naseer Shar mukayi bazaka yarda muna cikin wani matsala ba.

Umma kuwa da Safiyya tsabar bakin ciki barin gidan sukayi Basu dawo ba sai da aka Gama taron

Makotan arziki suka Tayani wanke komai da gidan.

Ai fa Bayan suna Umma kamar ta jefani a wuta matsamin tayi ta sakoni a gaba a gaban Naseer zata Zo har d'akina tayi ya zagina tana tsinemin Wai nayi asiri na kwace dukiyar Naseer.

Naseer ya zama kamar Dan aiki a gidan Dan Haka na fada Mata Inda naje nayiwa Naseer asiri.

Idan Ina San nayi magana sai ta saki ihu ta hau cewa na Mata rashin kunya Naseer na kallo.

Naseer masifar.umma yasa Dan kwanciya hankalin daya samu ya fara Rama.

Ni kuwa a hankali na fara kwashe.kayana Ina bawa Isihu Yana kaimin gidan matar Ala ramma Dan Bayan mmn Mannir itace mace ta biyu Dana bud'ewa cikina duk da shawarar data bani na sakani zubar da hawaye naji kamar bazan iya ba Amma babu yanda zanyi Haka Allah ya kaddaramin.


Kwana hudu kenan Ina rashin lafiya da kuka a b'oye da Naga lokacin Dana saka wa.kaina barin gidan Naseer nata matsowa.

A cikin yarana ba wacce nake balain tausayi kamar Zahira da Raheema ba Naseer ne a gabana ba yanzu yarana kawai nake tunani.

Idan Naseer yaga Ina kuka hakuri yake bani Dan ya d'auka takurar da Umma takemin ne Nan kuwa bai San tunanin da nake daban ba.

Ahaka dai ranar Dana sakawa kaina Bayan da Naseer ya tafi massallaci nayi sauri na goya Waleed a bayana.

Na Shiga d'akin yarana a zaune na tada Zahira kamar ma batayi bacci ba Haka kawai naji hawaye na neman zubomin nayi sauri na mayar Ina ta tashi kanennta suyi sallah.

Yanda na hade Rai yasa ta Shiga band'akin tana waiwayena kamar tasan tafiya zanyi.

Dak'yar ta Shiga band'akin.
Ni kuwa na toshe bakina sabida kukan dake neman k'wacemin na karewa yarana kallo na fito daga d'akin na ajiye zungureren wasikar Dana rubutawa Naseer a bakin kofar dakina na na fice daga gidan nabi ta Bayan gidanmu ta hanyar da ba fiye bi ta hanyar ba inayin Nisa da gidan Waleed ya fara tsalla kuka.......
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*

*Page 35*

"Kana kallo Suka fita da engine baka hanasu ba yanzu ta Ina zamu ringa samun kudin da zamu kashe"?


"Toh Mai engine ta siyar da kayanta Mai shi yazo ya d'auka ta Ina Zan Hana Umma abinda ba nawa ba"


"Kai Amma yarinya nan Allah sai ya tsine Mata muguwa idan ba mugunta ba ai ko Dan yaranta ta bar engine dinan sabida a samu na kula dasu Amma dayake bata da mutunci shine ta siyar da engine duka biyu idan ma tayi hakane Dan mugunta ai har da yayanta ta cuta wlh dadin abin ba iya markade akeyi a gidan ba Ana kulla zobo da ruwa Kuma a siyar Nima dai ba kuturwa bace inada hannun da Zan kula ruwa da zobon na samu na kaina wlh ko kallon yaranta bazan yi ba Kai Kuma zaman gida ai Bai kamaka ba tashi zaka Yi ka fita ka nemo kudi ba kazo ka shige daka ka kwanta Kai ga uwarka ta rabu da Kai ai Zama Bai kamaka ba ya zama dole kaje ka Nemo duk inda kudi yake ka nuna Mata Kai Dan halak ne insha Allahu sai kafi da arziki tashi Maza idan wanan shegen isihun yazo Zan aikeshi yamin cafenen zobon na hada ya kaimun"

"Ko na fita Umma bazan samu ko sisi ba ko na samu ma bazai Yi albarka ba Dan kin riga da kin tsinewa samuna Umma ko mantawa kikayi kin Kona duk dukiyata ta bakin naki kudi sai yamin wahalar samu yanzu gashi ai kingani kudi Yana min wahalar samu Umma kusan wata Takwas nayi a Abuja Ina neman kudi cikin tsananin wahala Umma Wanda ma na Dan samo sai da Yan fashi suka kwace a hanya ba abinda na taba yanzu dayake albarka"



"Duk ba Kai ka jawo ba sabida tsinanen taurin.kanka zuciya ya debeni nayi abinda nayi da Nima yazo ya shafeni Dan Haka batun ma Ni na jawo duk laifinka ne na saka albarka yanzu idan Allah ya yarda zaka samu kudi ka shirya kaje ka nemi kudi"

Daga Haka ta fito tana tsinewa Naeema akan ta siyar musu da engine.

Rai a bace Haka Suka zauna a tsakar gidan suna ta kwashewa Naeema albarka Dan canjin daya musu saura tasa Safiyya ta d'auko Suka lissafa abinda zasu kashe na hadin zobon suka zauna zaman jiran Isihu sai dai har karfe Sha biyu Basu ganshi ba ahaka Hajara ta lek'a da kanta Wai ko zata hango shi Nan ma Bata gan shi ba haka ta dawo ta Kara komawa d'akin Naeema ta tarar da Naseer a zaune a Kan Sallaya Dan tunda ya iddar da walha Bai bar Kan sallaya ba carbi kawai yake ja.

"Kaga shegen almajirin Nan Bai zo ba inata jiransa tundazu ko dashi ta tafi ne"?

Alama ya Mata da hannu alamar Bai Sani ba

Hajara kuwa ranta ya b'aci tana "Kai bana San iskanci Naga duk abinda ma shegiyar matar Nan tayi ba abinda ya dameka sai Abu kake Kamar wani maraya toh tunda Bai zo ba Kai Kuma ka k'i fita ka Nemo Mana kudi sai ka tashi kaje kayo min cafenan zobo idan zuciyarka ta mutu Ni tawa ba ta mutu ba idan tafiyar Naeema ne ma yasa kake wani nonok'ewa zaka ware me dalla tashi ka siyomin zobo da suga da farin Leda"


Ta karashe tana jefa mishi kudin hannunta.

Naseer ya d'ago da rinannun idonsa Yana "Ina Safiyya Umma da Ni zanje na siyo Umma Dan banida kudi Bai Kamata na zama kamar yaro da sai yanda akayi dashi wanan ma na iya janyo min raini a wajen Safiyya Ina gaba da ita ki wuceta kizo ki aikeni haba Umma"


"Kace kawai ban Isa dakai ba Naseer ai kafita sanin unguwar Nan sai ka fita sanin Inda ake siyar da kayan zobon shiyasa na kawo maka"

"Ki Bata idan ta fita tayi tambaya zaa nuna Mata"

"Nifa bazaka zauna a gida ni Kuma na ringa fafutukar neman kudi ba Dan Haka ko bazaka siyo ba ka zura rigarka ko dakone kaje kayi Dan Idan ma takamarka Kayan abinci da ake dashi a gidanan ne kwanan Nan zai Kare wlh Nima yanzu sama na da kasana iya kudin Nan ne Dani Dan Haka nemo kudi ya kamaka"


Daga Haka ta fice daga d'akin ta bawa Safiyya kudin ta lissafa mata abinda zata siyo Mata ta karbi kudin tayi waje tana zagin isihun da Bai zo ba

Naseer kuwa Yana fitowa

Kitchen ya Shiga ya fara k'ok'arin dorawa su Zahira abincin Rana Hajara kuwa tace ya fita idan Safiyya ta dawo zata Dora musu abincin.

Naseer Bai. Ce Mata komai ba ya cigaba da abinda yake Dan wasikar da Naeema ta bashi na ya rik'e amanar yayansa ya rik'e gam akansa bazai soma barin Safiyya ko mahaifiyarsa su dafawa yaransa abinci ba.

Haka Hajara tayi ta bambamin fad'a har Safiyya ta dawo.

Dayake taliya Naseer ya Dora musu Nan da Nan ya Gama Dan akwai Miya Mai yawa a freezer din dake d'akin Naeema Dan har freezer ta siya da ta samu kudi ta daina siyan kankara.

Haka take Miya Mai yawa sai dai su dafa shinkafa ko taliya Miya tuwo ma Haka take yinshi da yawa.

Yana gamawa ya zuba wa su Hajara a kularsu ya d'auki sauran ya Kai daki Kamar yanda yaga Naeema nayi

Ya daura alwala ya fice daga gidan Hajara da Safiyya dake kula zobo da ruwa suka bishi da kallo har ya fice.

A Kular da Naeema take zuba zobo da ruwan Suka zuba

Hajara ta nufi d'akin Naeema Dan ta dauko kankara sai dai tana zuwa taga k'ofar a kulle.

Masifa ta ringa surfawa akan me Naseer zai kulle k'ofar d'akin Mai ya mayar dasune.

Haka ta koma ganin Bata San lokacin da Naseer zai dawo ba yasa ta bawa Safiyya sauran kudin hannunta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login