Showing 99001 words to 102000 words out of 180103 words

Chapter 34 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2503

a daidai lokacin da Tijjani ya shigo da vespa ya Parker

Murja kuwa ta hau cewa "kaga tunda kuka tafi nake fama dasu akan su shigo Suka k'i wanan kamar wata karamar Yarinya har da kukanta Wai sai tabi bayan Abbanta"

Fa karashe tana nuna Zahira

"Kukan me kike Yi Zahira bakya San ki zauna damu"?

Tijjani yace a daidai lokacin da ya karasa wajensu Yana ruk'o hannun Zahira

Girgiza Masa Kai Zahira tayi Murja kuwa ya harareta a fakaice sosai take ganin kamar Zahira munafinci ne yasa take kukan sabida ta hadata fada da Tijjanin.

Dan duk da kame Mata Tijjani da mahaifiyarta tayi wani zubin inya tashi sai ya botse Mata.

Cikin palon suka Shiga Tijjani ya zauna akan kujera Ya zaunar da Nadeeya a gefensa ya kalli Murja Yana "Dan Allah Kara Dora Mana wani abincin yunwa nakeji wlh"

"Wlh na dazu ma dakyar na dafa ko dandanawa banyi ba ka bawa yaran Nan da babansu"


"Toh sai nak'i Basu Murja wane irin magana kike Haka yayana na bawa abincin fa ke Mai yasa kike haka ne Mai da anzo wajenka ka bada abinci anci gaskiya ki gyara halinki Bari nayi Sallah na Shiga da kaina na dafa abincin

Daga Haka ya mik'e ya shige dakin
Murja ta bishi da wani irin kallo ta maido kallonta kansu Zahira datake ji kamar ta jawosu ta rufesu da duka

Ahaka ta daure tayi waje ta Dora musu jollof din taliya tana zagin Naseer da yayansa da take ganin sun zo sun takura Mata.

Taliyar kad'an ta dafa duk da basu da matsalar kayan abinci sabida su kadai ne Murja kuwa rowa bazai Bari ma ta dafa abincin da yawa ba ballantana har ya ragu su bawa almajiri.

A plate ta juyo musu abincin Dan tare suke ci


A Palo ta tarar da Tijjani dasu Zahira Yana ta jansu da Hira sabida su saki jikinsu sai dariya yake kyalkyalewa Dan Nadeeya sosai ta zage take Masa surutu ita kuwa Zahira da Bata da surutun murmushi kawai take.

Murja kamar ta fashe Dan bakin ciki tsabar jahilci ma kishi ne ya rufeta data ga yanda Tijjani ke kyalkyala dariya a Haka ta ajiye taliya ta zauna a gefensa zahira tayi saurin barin kujeran.

Nadeeya kuwa ko a jikinta

"Ina abincin su Nadeeya Naga kin zubo Mana mu kadai"?

"Ai Naga sunci abinci shiyasa ban dafa dasu ba ga saura can ma na Kai kitchen"

"Zahira kin koshi Wai"?

Da Sauri ta gyada tare da sunkuyar kai kasa sabida mugun kallon da
Murja ke jifanta dashi

"Nadeeya ke Kuma fa kin koshi"?

Girgiza masa Kai Nadeeya tayi

Shi kuwa yace toh shikenan Bari muci gabad'aya jeki wanke hannunki

Waje Nadeeya tayi da Sauri

Ta wanko hannunta Suka fara cin abincin
Murja kuwa tusa abinci kawai take Dan bakinciki ji take kamar ta shake Nadeeya
A takaice Tijjani da kansa yayiwa Su Zahira shimfida har da Kai musu bargonsa ya musu adduar kwanciya bacci tare da ja musu k'ofar

Murja kuwa tsabar bakin Hali Kamar ta fashe da kuka Dan gani take Tijjani Dan tattalata da yake yi daga zuwansu Nadeeya ya shareta.

Rai ba dadi Haka ta kwana tana Shan mugayen alwashi aranta


Naseer kuwa sai daya yi sallah ishai ya karasa gida

A k'ofar gida ya tarar da Hajara ita da Safiyya sunyi jugum jugum sai kalle kalle suke

Safiyya kuwa Tana hango Naseer ta diba da gudu tayi ciki

Hajara kuwa duk da jikinta rawa yake sabida tsoro Mai zata cewa Naseer game dasu Zahira da Basu dawo ba ahaka ta maze Yana isowa gabanta ya gaisheta Yana k'ok'arin Shiga gidan kamar Bai San komai ba


Hajara kuwa kamar ta Dora hannu a ka Shigar Naseer da Yan mintuna ya fito waje

Ya kalli Hajara datayi tsuru tsuru Amma tsabar karfin hali ta daura fuska

"Umma inasu Zahira ne ko kin aikesu"

"Aaaa eee kana ji wlh talaucin Nan da muke fama dashine ya isheni shine na Nemo kudi na d'afa abinci da suka dawo na dorawa Zahira da Nadeeya akan su kaimin bakin titi su dawo sabida ma mu samu abincin da zamu ci daddare.

Wlh tun uku Suka fita har yanzu basu dawo ba naje titi nida Safiyya yafi sau biyar ko Mai kama dasu bangani ba ba Inda ban dubasu ba a unguwar Nan wlh ban gansu ba yanzu ma Haka daka ganmu a k'ofar gida wlh daga nemansu muke

"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Umma talla Kika dorawa Zahira da Nadeeya kinsan kuwa akwai Yan yankan Kai a garin Nan Umma Kar fa masu satar mutane ne ne fa suka sacemun Yaya Umma Akan me Zaki Dora musu talla haba Umma kema kinsan idan na dawo ko ba yawa Zan taho Mana da abinda zamuci irin Haka nake gudu tun farko shiyasa naki Bari a Dora musu talla yanzu daga Ina Zan fara ta Ina Zan soma neman su Umma"?


"Insha Allahu baa sacesu akayi ba abincin dari takwas fa na Dora musu da hamsin"


"Umma ta abinci kike ko yarana Umma ta kudinki kike ko yarana Ina Miki zancen yarana kila sun b'ata kina min zancen abincin dari takwas Kika dora musu"

A takaice sosai Naseer ya tashi hankalinsa kamar gaske baiyi bacci ba Bai Bari Hajara tayi ba Dan itama sosai hankalinta ya tashi da rashin dawowarsu zahiran.

Tana ta bakin cikin asarar da tayi kasan zuciyata Kuma tana addua Allah yasa ba sacesu akayi ba.


Abinda suke turarawa shugaba ta bayyana kuwa sun nemeshi sama ko kasa sun rasa ballantana tasa shugabarsu ta gano Mata Inda suke.

Ahaka washegari Naseer ya bar gidan da wuri Akan ya tafi neman su Nadeeya

Bai damu da tsayawa ya bawa su Minal abinci ba Dan ya karanci a yaran nasa tafi San Minal Humaira da Raheema har abinci tana ragewa ta basu idan taci duk da Minal na musu rashin kunya wani zubin hakan Bai saka ta wani tsaneta ba.

Zahira ma ta tsaneta ne sabida balain Kama dataga tanayi da Naeema

Hankali ba a kwance ba Haka Hajara ta shirya su Minal suka tafi makaranta bayan sunci abinci.


Tijjani kuwa karfe shidda yake barin gida hakane yasa Yana dawowa daga Massallaci yayi wanka ya shirya ya kalli Murja dake Kan sallaya Yana "Zan fita Zahira da Nadeeya Basu tashi daga bacci ba Dan Allah Dan annabi ki Basu abinci suci su koshi Dan Allah nace Miki karki damu da Wai Dan kin bayar zai Kare wlh Zan Kara siyo wasu yaran Nan Kinga amanarsu yayana ya bani Dan Allah ki Tayani kula dasu kinji"


"Wai toh Mai ya kawo maganganun Nan baka yarda Dani bane Akan me Zan k'i Basu abinci bana San Haka wlh"

"Allah ya baki hakuri ba Haka nake nufi ba Bari na tafi sai na dawo Mai Zan taho miki dashi"?


"Ayaba kawai nake shaawa"
"Toh shikenan sai na dawo"

Daga Haka ya fito daga d'akin ya lek'a d'akinsu Zahira da har lokacin suke sharar bacci.

Har waje Murja ta rakashi sai data daina hango shi ta rufe gidan.

Direct ta Shiga kitchen ta bud'e karamin fridge ta d'auko karamin bokitin fenti dake cike da ruwan da ya fara Dan kankara.

Tayi d'akin dasu Zahira suke kwance
Sai data janye bargon da suka lulluba sabida Dan sanyin da suke ji ta daga robar sama ta watsa musu.


Wani irin ihu Suka saa Suka mik'e a gigice sabida yanda ruwn sanyin ya ratsa su

"Shegu Yan bura uba dole kuyi ta sharar bacci ku ga gidan ubanku maza ki fita waje kuje ku dau tsintsiyarku ku sharemin ko'ina kumin wanke wanke yanzu Nan ku Shiga d'akina kuzo ku gyara min"

Daga Haka tayi waje tana cigaba da danna musu Ashar.

Zahira da Nadeeya kuwa Suka kankame jikinsu suna rawar sanyi kayansu sai digar ruwa yake ahaka suka fito Suka daura alwala da jikakken kayan sukayi sallah suna ta rawar sanyi Zahira kuwa har da kukanta Dan Abu kad'an ke sakata kuka

Cikin awa daya Suka Gama aikin da Murja ta saka su dan gyara gida Kam sun Riga da sun Saba Koda Bata saka su ba zasuyi.

Murja kuwa ba karamin mamaki tayi ba a lokacin data fito taga koina fes ko ita kanta bata taba gyara gidan kamar yanda Suka gyara ba.

D'akinta tace su shiga su gyara Mata Nan da Nan suka gyara d'akin suka wanke band'akin tas.

Duk aikin data saka su Nan da Nan taga sunyi har a karshe ma ta rasa aikin da zata saka su

Wajen karfe goma ta Shiga kitchen ta dafa ruwan tea Kofi daya ta soya kwai guda hudu tayi hadin kauri ta zauna a Palo ta fara ci Tana kallonsu Zahira dake rab'e a gefe Nadeeya kuwa sai had'iyar yawu take Dan ita Bata Wasa da cikinta


Zahira kuwa tsoro ma yasa ta kasa d'ago Kai ta kalleta.

Suna kallon Murja ta Gama Shan shayinta tsaf ta rufe sauran bredin ta mik'awa Zahira Kofin Akan ta wanke ta mayar kitchen.

Zahira jiki na rawa ta mik'a hannunta Dan ta karba Murja ta Kara daka Mata tsawa akan ta karba mana aikuwa tana karbar kofin nan ya sulmiye daga hannunta ya fashe........



*Wlh babu fiction a rayuwar da su Zahira sukayi a gidan Tijjani akwai Abubuwan da bazan rubuta ba sabida wasu zuciya bazata dauka ba sabida tausayi Kuma kamar Yanda na fada labarin nada tsayi masu Dan mahimmancin Zan rubuta sabida Allah na fara gajiya Ya Allah kar ka kawo sanadin da zamu rabu da yaranmu kasa mutuwa ce zata rabamu ameen*
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*


*Page 38*


"Kutumar uba kofin danake ji dashi Kika fasamin"


Zahira kasa ta zub'e akan gwiwarta jiki na rawa ta hau Bata hakuri.

Murja kuwa kofin kawai take kallo

Wani irin mik'ewa tayi ta fusgo Zahira ta hau dirmarta Kamar ta Samu babba sai wuli take da ita sabida Zahira siriiriya ce Bata da jiki Nadeeya sai kuka take Tana rik'e Murja da idonta ya rufe ko tausayin Zahira da ta kasa kuka bata ji ba sai data gaji Dan kanta ta kyalleta tana sosoka mata Ashar.

Tsawa ta daka Mata akan ta tashi ta kwashe Mata fasassun kofin kafin ta Mata bille a fuska


Zahira ta rarrafa wajen da kofin ya fashe jikinta yayi jawur sai rawa Yake.

Fasassun kofin na yayanke Mata hannu Haka ta kwashe ta Kai dustbin

Ta tsaya a tsakar gida.
Murja kuwa ta hankada Nadeeya tsakar gida ta rufo k'ofar Palon tana kiransu shegu.

A Haka Suka zauna a tsakar gidan cikin rana.

Daga Zahira har Nadeeyan kuka suka ci su ka Godewa Allah har gwara gidansu sau Dubu da gidan da mahaifinsu ya kawosu Dan Safiyya ce ma take takura musu Hajara kuwa ita zagine tsakaninsu sai rankwashi Bata Kuma tab'a Hana su cin abinci ba

Ga zafin Rana gana dukan da zahira ta Sha Haka Suka zauna a ranar Dan tsakar gidan a wawuke yake iya dakuna ne masu rufi ballantana su samu inuwa su rab'e

Murja Bata fito ba sai karfe Biyu da rabi na Rana ta musu wani irin kallo ta nufi kitchen.

Ta dafa taliya daidai cikinta ta zubo a plate ta shige palon ta hau ci

Zahira da Nadeeya kuwa zuwa lokacn yunwa taci ta cinye su Zahira ta Dan fi Nadeeya dauriya dan Bata da ci sosai tafi auki a wajen kayan kwadayi su biscuit da alewa Haka.
Nadeeya kuwa Sam Bata da juriyar yunwa tana da balai ci Dan bama tasan koshi ba in zaka Bata abinci sau goma sai ta karba taci

Cikinta ta rik'e tana kuka wiwi ganin Murja da plate din taliya yasa ta Kara Jin wani azbar yunwa.
Bata iya jurewa ba tana ganin ta shige ciki ta mik'e ta nufi kitchen Zahira kuwa ta hau kwala Mata Kira cikin karamin murya akan ta dawo

Nadeeya kuwa ko kallonta batayi ba

Ta shiga kitchen din

Tsakin garin masara data gani ta zuba a kwanu ta zuba suga akai da ruwa

Ta saka cokali biyu cikin sand'a ta karasa wajen Zahira dake a tsorace tana suci.

Zahira girgiza mata Kai tayi tana "ki Mayar Nadeeya Kar ki janyo Mana wani dukan Dan Allah "


"Wlh bazan iya mayarwa ba Aunty Zahira yunwa nakeji kici Dan Allah"

Zahira Bata kulata ba tayi ta kallon k'ofar palon tana tsoron Murja ta fito

Nadeeya kuwa ta hau Danna tsakin massarar da ruwa ya shanye da suga a bakinta

Sosai take zabga Loma kamar wacce ta samu garin kwaki

Fitowar Murja da plate din data Gama cin abinci yasa Zahira ta mik'e a tsorace jikinta na d'aukar rawa.

Nadeeya kuwa dayake Baya ta Bata Sam Bata San da fitowar Murjan ba Murja kuwa ganin Nadeeya da plate dinta yasa ta nufi wajenta da gudu tana "Barauniya uban me Kika dauko kikeci iyye wato har kitchen Dina Kika Shiga waye ya Baki izinin shiga"

Kafin kace me ta fusge plate daga hannun Nadeeya itama ta hau kilarta

"Gobe ko Tijjani ne yace ki Shiga kitchen Dina Zaki ji tsoron shiga shegu Mayyu Haka kawai Ina zaman zamana an kawomin jarraba maza kuje ku dau bokiti ku debomin ruwa"

Ta karashe tare da daka musu tsawa

Zahira kuwa a guje ta kinkimi bokiti Nadeeya itama tabi bayanta
Ta dau Wanda Bai Kai na zahiran girma ba har waje Murja ta rakasu ta ce suje can kasan layin wajen makabarta akwai rijiya su debo Mata ruwa maza tana jiransu.

Siyan ruwa take Kuma tana da ruwan tsabar mugunta yasa ta aikesu diban ruwa.

Nadeeya Dan tsakin data ci ya Dan rage Mata yunwar da take ji

Zahira kuwa kasa tafiya tayi sabida rawar da jikinta keyi kafin su karasa karshen layin ta samu inuwa ta zauna ta rik'e cikinta Tana kuka.
Nadeeya kuwa cewa take "Aunty Zahira mu ajiye bokitin mu gudu"

"Ai bamu San hanya ba Nadeeya Kar mu Bata nidai idan baba Tijjani ya dawo Zan rokeshi ya maidamu gida yunwa nakeji cikina ciwo yake da Umma tana Nan da Abba Bai kawo mu Nan ba"


Zahira tace tana fashewa da kuka

"Wai toh Ina Umman ta tafi ne ta barmu"?

"Bansani ba Nadeeya Abba Bai fada min ba"

"Idan Baba Tijjani ya dawo sai na Gaya masa dukan data Mana ta Hana mu abinci"

Nadeeya tace itama hawayen na zubo Mata.

Ta mike ta nufi shagon data gani a bud'e tana zuwa ta zub'e a kasa tana "Dan Allah ka bani bredi na bawa yayata yunwa takeji tace cikinta ciwo yake"

Mai shagon kallo Inda ta nuna Masa yayi yaga Zahira a zaune sosai yaji wani irin tausayin su ya rufeshi ya hau yiwa Nadeeya tambayoyi Ina iyayensu suke Mai ya Hana suci abinci

Nadeeya dake tana da surutu take ta hau bashi labarin abbansu ne ya kawosu gidan kaninsa shine matarsa taki Basu abinci.

Tambayar Nadeeya yayi gidan da suka zo ta kuwa nuna Masa gidan

Ya girgiza Kai gidan Dan ya San Murja zata Kuma aikata basa shiri da ita sabida Tijjani na zuwa wajensa hiran Dare.

Hakane yasa ta zo har shagonsa ta Masa tas akan shi munafiki ne ya Rabar Mata da miji k'arfi da yaji ta kuwa rabasun yanzu Haka ko siyan Abu batayi a shagonsa ta gwammace taje wani wurin .

Bredi ya d'auko Mai Dan girma ya bawa Nadeeya da kananan lemo guda biyu

Nadeeya kuwa jiki na rawa ta hau mishi godiya tana tambayarsa Dan Allah ya sunanshi

Murmushi ya Mata dayaga yanda take da wayo yace sunansa Jamilu bud'ar bakinta sai cewa tayi "Allah ya saka ka a Aljannna Yaya jamilu daga Haka ta diba a guje ta koma wajen Zahira dake rik'e da cikinta Zahira kuwa na ganinta da bredi da lemo ta fusge bredin daga hannunta ta yaga ledan ta hau dannawa a bakinta ko ta Kan lemon Bata bi ba.

Nadeeya itama sosai ta ringa cusa bredin a bakinta sai da suka ji Dama Dama suka Kora da lemon hannunsu.

Zahira kuwa tuni taji ta Dan koshi sanin Nadeeya Bata San koshi ba yasa ta fusge bredin tana "Karki cinye duka ki kawo na boye Mana anjima daddare muci Dan nasan bazata bamu abinci ba"

Daga Haka Zahira ta danne bredin ya kankance ta cusa a skirt dinta.

Suka dau bokitansu Suka dau hanyar karshen layin sai da suka tambayi Inda rijiya yake aka nuna musu Yana gaba da makabarta kad'an abinka da yarinta ko tsoro Basu ba ahaka suka Shiga ta cikin makabartar kafin su Isa wani ya taresu tare da tambayarsu Ina zasuje

Gaya Masa sukayi ruwa zasu d'ebo

Mutumin kuwa yace "Wane mahaukacin ne zai aiko ku Nan diban ruwa duk rijiyar unguwar Nan maza ku juya ku koma baa bi ta nan"

Juyawa sukayi da Sauri.

Suka koma suka Kara d'aukar hanyar da suka biyo Zahira kuwa ta hau cewa "idan muka koma bamu Kai Mata ruwan ba zata dakemu mu nemi wani wajen mu dibi ruwan

"Toh ai ba Inda muka sani"

"Kije ki tambaya mutumin Nan daya bamu bredi haka.kuwa akayi Nadeeya na tambayarsa ya nuna musu wani gida a kusa da shagon suka shiga gidan suka dibi ruwan suka tafi gida.

Sai da suka dade da ruwan Akansu Kafin murja ta fito tana zaginsu Akan Ina suka tsaya suka Dade haka a amadadin ta sauke musu ruwan Bata sauke musu ba ta Shiga kitchen.

Zahira kuwa bokitin sai rawa yake akanta

Nadeeya kuwa data ga bazata iya ba sakin bokitin tayi ya Fadi kasa ya fashe

Murja kuwa ta lailayo Ashar ta fito ta daya kitchen ta wawankawa Nadeeya Mari da rankwashi tace Mata ta d'au tsintsiya ta share Mata Inda ta jikam

Zahira kuwa tsabar tsoro Kara rike bokitin tayi akanta sabida Kar ya Fadi

Sai da Murja ta Dora girkin dare.

Ta fito.ta sauke mata bokitin data ga yanda jkin Zahira ke rawa tana kuka.

Sai data Gama girkin da take tsaf ta daka musu tsawa akan suje suyi wanka ta Kara da "Mitsiyacin ubanku ma daya tashi kawoku ko hadoku da Kaya baiyi ba ai kuwa shi zaku Kara maimaitawa maza kuyi wanka ku maida kayan jiknku kuzo ku sameni a Palo"


A band'akin Tsakar gidan sukayi wanka.

Jikin Zahira yayi jawur sabida dukan data sha

Nadeeya ma. Yatsun Murja sai daya fito a kumatunta

A Haka suka Shiga palon suna rab'e rab'e sai data Kara daka musu tsawa Suka zub'e a gaban ta jikinsu na rawa.
Wukan data ajiye a gaban ta ta Dago musu tana "Mai wanan"?

Hade jikinsu sukayi waje daya jkinssu na balain rawar tsoro Zahira har wani fitsari ne ya matseta

"Dan ubanku nace me wanan"

"Wukane

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login