Showing 108001 words to 111000 words out of 180103 words
Tafi ba Nadeeya Amma zanzo kinji maza Kibi Yan uwanki ki tafi"
Hawaye ta hau Yi Tak'i motsawa
Ni kuwa na daka Mata tsawa Ina "Dan ubanki kizo ki wuce mu tafi"
Umma kuwa sai zagin Naseer take tana zagina Akan na asirice Naseer yace na tafi da yaran
Ga mamakina Nadeeya girgiza min Kai tayi tana "Umma idan bazamu tafi da Abba ba a wajen Abba Zan zauna bazan biku ba"
Ta karashe cikin kuka.tana kankame Naseer
Ni kuwa na Kara daka Mata tsawa Ina "kizo ki wuce mu tafi Nadeeya wlh Zan zaneki Dan idan Kika zauna a Nan duka Zaki ringa sha a Dora Miki talla ko makaranta ma bazaki je ba"
"Nidai ba Inda zani wajen Abba Zan zauna umma"
Naseer kuwa banbare ta yayi daga jikinsa cikin murmushi da kana gani kasan na yak'e ne ya sunkuya ya rik'e hannun Nadeeya Yana "Karki damu Nadeeya ta zanzo na sameku Kibi ummanki ki tafi kinji idan Kika zauna anan ba Wanda zakiyi Wasa dashi"
"Nidai ba Inda zani Abba indai bazaka bimu ba a wajenka Zan zauna"
A zuciye na nufi wajen Naseer da niyyar na fincikota ita kuwa ta dib'a aguje ta Shiga gidan tana hankada Umma dake bakin kofa........
Toh ga readmore biyu Nan tunda kun matsamin๐๐๐๐๐๐๐๐
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*๐ธ๐ธ
ยฎ๏ธ? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}๐ช๐ป_
*Free Novel*
*Page 41*
Har ciki na bita Nima Ina dan bangaje Umma datayi bake bake a bakin kofa ita kuwa tayi ta auna min zagi Wai na fito Mata daga gidan d'a Kar na Musu Sata.
Ban saurareta ba na bi Nadeeya har d'akina na da Dan Nan ta shige
Tana ganina ta kankame jikinta tana ihun kukan "Ba Inda zani Umma bazan biki ba a wajen Abba Zan zauna Umma idan Kika tafi damu waye zai zauna da Abba ba Inda zanje Umma"
Haushin taurin Kan Nadeeya yasa na Kai Mata duka na rik'e hannunta da Karfi da nufin janta a kasa sosai Kuma nake mamakin Inda Nadeeya ta samo taurin Kai
bazata Gane Gata nake Mata da rabata da gidanan ba daga Ni har sauran yaran nawa ai ba a San ranmu muka bar Abban nata ba Dan muma ba finmu San shi tayi ba
Kara fincike hannunta tayi da k'arfi ta hau burgiman ba Inda zataje Ni kuwa na cire takalmina da niyyar zaneta.
Naseer ya shigo da Sauri ya rik'e hannuna Yana "kiyi hakuri karki bugeta Bari na rarrasheta"
Ya saki hannuna ya durk'usa gaban Nadeeya tare da dagota ya hau rarrashinta Akan ta bini ita kuwa sai tirjewa take Akan bazata bini ba ita a wajensa zata zauna a karshe ma sai ta fita aguje
Ni kuwa na fara k'ok'arin bin bayanta aguje naji Naseer ya ruk'o hannuna ya Kuma jawoni jikinsa ya kamkameni ta baya tare da Dora kansa a kafadata naji dumin hawayensa a kafadar tawa daya haddasa min wani irin raunin zuciya da San na juya na rungumeshi na rarrashe shi
Cikin rawar murya ya fara magana Yana "kiyi hakuri Naeema nsan kinyi hakuri Zama da Mahaifiyata tsawon shekaru Wanda sai da Kika tafi nagane irin hakurin da kikayi da ita Naeema na kasa sauke nauyin da Allah ya doramin na gaza ciyar dasu na gaza tufatar dasu ba irin kudin da ban nema ba ban samu ba Naeema Dan Allah idan Kika tafi da yaran Nan ki Kular min dasu Allah ya Baki Lada ita kuma Nadeeya tunda ta dage bazata biki ba ki barmin ita Zan kula da ita insha Allahu na Kai su gidan Tijjani ne sabida Ina tunanin acan babu Mai musguna musu bansan matarsa itama ba matuniyar arziki bace na Miki alkwari bazan Bari Umma ta Taba Nadeeya ba indai ta Taba ta insha Allahu da kaina Zan kawo Miki ita"
Duk maganar Nan da Naseer kemin Yana kamkame Dani kansa Akan kafadata Yana zubar da hawaye nima hawayen nake sosai Dan. Har ga Allah a yanzu ne Naseer ke bukata ta a kusa dashi yau da Umma Bata sako mu agaba ba Dan abinda nake samu iya zaman duniya dai zai ishemu dagani har yarana da Naseer Amma Umma ta dage sai mun rabu.
"Daga Bauchin Kika zo"?
Naseer yace
Girgiza Masa Kai nayi Ina k'ok'arin Magana naji muryar Umma cikin ihu tana "Yau Naga karuwa har cikin gida yau Naga ikon Allah yanzu har daki Kika shigo Dan ki yaudari Naseer ya Kara miki wani cikin kenan kamar yanda Kika Saba Kai jamaa wannan yarinya anyi jarababbiya kwartuwa"
Fusge jikina nayi daga na Naseer da har lokacin yake rik'e Dani tsayuwar Umma a bakin kofar d'akin Bai saka ya cikani ba Ni kuwa na ja Tsaki na bangaje Umma dake bakin kofa ta kawo hannu zata kawomin duka Dan sai data Kusa fad'uwa dana bangajeta na kauce "Shegiya karuwa Dole ki hankadani tunda na kamaki kina k'ok'arin yiwa Dana fyad'e"
Bance Mata komai ba na fice waje ta biyoni har waje tana min ihun kwartuwa
Naseer kuwa magana yake Mata Yana k'ok'arin hanata Amma sai ihu take cigaba da yi.
Hannun Raheema kawai na rik'e Dan Waleed na hannun Aunty su Zahira Kuma suna can gaba dasu Minal.
Muka hau tafiya Ina danne kukan dake neman fitomin ta karfi Dan har waje Umma ta fito tana min ihun kwartuwa karuwa.
Wai nice karuwa ban waiga ba duk da naji Naseer ya daka Mata wani uban tsawa akan tayi shiru Amma a madadin tayi shirun sai cewa tayi "Saukar Mari nake jira naji Dan ka Riga da ka Saba marina Maza Mareni sabida wancan karuwar data biyoka har gida zata maka fyad'e.
Naseer bakin ciki ne yasa ya koma ciki ya lek'a dakin Umma ya ruk'o hannun Nadeeya suka fice daga gidan.
"Gaskiya ban taba ganin uwar miji irin Taki ba Naeema duk yanda Zaki bawa mutum labari bazai Gane ba sai ya ganta da idonsa wlh rabuwarki Da Naseer yafi alheri Kai wanan Mata anyi tsinaniya yanzu Nadeeya dagewa tayi bazata bikin ba"? Mai yasa Baki tilasta Mata ba Naeema kinsan yarinta ke damunta ita gani take ba Wanda zai zauna da abbanta shiyasa ta dage bazata biki ba"
"Hmmm"
Kawai na iya cewa Aunty Dan Sam bana Jin yin magana sabida abinda ya tsayamin a mak'oshi yak'i tsirgamin
Muna fita titi na tare Mana taxi su Zahira suka Shiga na karbi Waleed daga hannun Aunty
A k'ok'arina na inyi magana na fashe da kukan dake cina tundazu
"Sai hakuri Naeema Allah dai ya shiryi matar Nan idan tana da rabon Shiriya
Ban ce Mata komai ba na Shiga taxi Ina cigaba da kukana.
Sunkuyowa Aunty tayi daidai window motar tana "zanzo jibi kafin na Zo dai Zan lek'a gidan Naga ko Zan iya shawo Kan Nadeeya dan inaga sai kinfi samun kwanciyar hankali idan Kika gansu a gunki gabadaya.
Kai na gyad'a Mata muka wuce.
Muna Isa Muka sauka gabadaya na karbi kudi a wajen Hassana dake ta markade na bawa Mai taxi.
Na dawo muka zauna a palo gabadayan mu.
Yarana sai kalle kalle suke.
Sosai nake Jin ba dadi da Nadeeya Bata biyoni ba da nasani na Mata tsinannen duka na taho da ita Dan ai ba fin karfina tayi ba Naseer ne ma yake wani lallaba ta.
Kitchen na fita na Dora Mana ruwan tea Dan Nima ban karya ba na fita shagon k'ofar gida da Isihu shima tafiya da nayi karbowa Waleed magani Nazo na same shi ya dawo daga garinsu rashin nutsuwa yasa ban ma bi ta kansa ba
Hassana dai tacemin shi yake jire min shagon
Kayan shayi na d'aukar Mana da manyan bredi har da kwai wajen goma
Na koma ciki na soya Mana na fito da kofuna na kwallawa Zahira Kira tazo ta d'aukar Mana flask din shayin.
Sosai jikin yarana ya ringa rawa farinciki shimfide a fuskarsu ahaka na zubawa kowace Madara da bournvita Dan gwangwanin su na dauko.
Kwan Kuma na ajiye a tsakiyarsu.
Sosai jikinsu ya ringa rawa wajen Shan shayi Kamar basu tab'a cin abinci ba.
Bare Zahira da duk zafin shayin Haka take kurba sosai tausayinta yasa kwalla zubomin Dan ga shattin tsintsiyar Nan a kwance a wajen idanta ga jikinta Nan ma yayi rudu rudu sabida duka.
Hannunta kuwa ya Kara sirrancewa kasancewarta Mara jiki.
Ganin ta a irin halin Nan yasa nama.kasa cin abincin nace "Zahira Mai ya samu jikinki haka"?
Hadiye kwan data saka a baki tayi tana "Aunty ce take zanemu kullum"
"Da kuka Mata me take zaneku kullum"?
Shanye shayin daya Mata saura tayi ta hau bani labari irin rayuwar da sukayi a gidan Tijjani da yanda Take dafa wake Mai uban attaruhu da sabulu Tana bani labarin tana kuka Dan Abu kad'an ke saka Zahira kuka ko tsawa ka daka wa Zahira yanzu Nan zaka ga idonta ya ciko da hawaye
Sosai na ringa kuka Ina duba jikin Zahira daya Sha tabon bulala da dorina "Allah ya Isa tsakani na da ita bazan tab'a yafe Mata cutarmin daku da tayi ba Mai kuka Mata da zata azabtar daku Haka har ta muku horon yunwa ta ringa bawa Nadeeya Sabulu da wake sabida mugunta Allah ya Isa bazan yafe Mata ba Allah sai ya muku sakayya tun a gidan Duniya idan Allah ya yarda Allah sarki Nadeeya yanzu Haka ta ringa cin wake da sabulun babu abinda ya sameta"?
"Eee umma sai dai tayi ta kashi Mai kumfa tacemin duwawunta na yaji idan na hanata cin wake sai tacemin yunwa takeji sai taci"
Kaina har ciwo yamin sabida kukan zalincin da matar Tijjani tamin
Sai da Hassana ta Gama markaden tazo ta zauna na Dan Bata labarin duk wuyan dayarana suka Sha taci kuka itama tana Dama Nadeeya ta biyoni .
Nima iirn wuyan da Zahira ta bani Akan nadeeya ta Sha naji inasan na dawo da Nadeeya gabana na kula da ita
Ita da Minal suna da balain ci
Anan Zan Basu duk abinda suke so ta dawo Nan tabar Naseer Yaji da kansa
Hassana ce ta Tayani tsefewa su Raheema Kai har Minal ta musu wanka ta wanke musu Kai.
Zannuwana na raba musu Suka daura na janyo gwangwanin na danake Tara kudi .
Na duba Naga kudin ciki da Dan yawa na dibi yanda zai isheni karfe uku na nufi Sabon gari Dan acan na Dan Tsintowa Waleed Kaya masu kyau kamar sababi Kuma a kudi kalilan.
Sosai na jiddo wa yarana Kaya har da panties Zahira danaga ta fara kirgen dangi har ves ves na siya Mata dasu under wear duk abinda na daukarwa Zahira sai Dana d'aukar wa Nadeeya
Dan nasu zahiran yadan fi yawa.
Kala.uku na daukarwa Isihu shima Dan ya zama tamkar Dana Tinda barina gadon Kaya yasa shima ya hakura da makaranta ya dawo wajena duk da ba a gidana yake kwana ba a wani makaranta Allo dake unguwar yake kwana a Kuma Nan yake karatu.
Sai wajen Magriba na isa gida.
Yarana sai tsalle tsalle suke suna Wasa Zahira itama sai washe baki take abinda ya ragemin Jin dadin kasancewata dasu shine Nadeeya da Bata Nan Dan da tana Nan da kila hankalina Bai rabu gida biyu ba.
A Daren nida hassana har da zahiran muka wanke kayan gabadaya.
Suka saka vest din Dana sisiyo.musu.
Zahira akwai San.kallo Dan tv black and white Dana siya karami da lokacin tashar Nta ne kawai da ctv suke Dan drama Dan sai kana da video kake iya siyan cassette kayi kallo.
A gaban tv tayi zaman dirshan tana ta kallo har kannenta sukayi bacci suka barta.
Sai da zamu kwanta na umarceta data kashe.
A daki daya muka kwana gabadaya Banda hassana.
Ni kuwa Sam baccin ma Bai min wani dadi ba sabida zuciyata dake wajen Nadeeya.
Naseer kuwa Yana barin gidan Bai zame ko Ina ba sai wajen da aka basu kwangilar gini.
Ya samo benci ya zaunar da Nadeeya ya siyo Mata shayi da bredi har da kwai ita kuwa ta hau ci tana Masa hiran sabulu da waken da Murja ke basu sunaci.
Ta dage rigar jkinta tana nuna Masa shattin bulala dake kwance a jikinta tana "Abba kaga yanda ta zanemu kullum sai ta dakemu ta zageka ta zagi Umma Wai an kawo Mata jarraba"
Naseer kasa magana yayi Sabida tsananin b'acin Rai dayake Nadeeya tana da surutu a take ta bashi labarin duk rayuwar da sukayi a gidan.
Naseer sosai ya daure baiyi kuka Agaban Nadeeya ba sabida yanda yake ji a Ransa wai da Ransa aka zalunci yaransa Haka Bai taba tunanin Murja Haka take ba Taya yaransa zasu Sha wanan bak'ar wahalar Tijjani yace ko sau daya Bai taba Sani ba baya ganin jikin yaran nasa ne Zahira dake ruwa ruwa wajen kuka ai ko kallon minti uku ya Mata yaci ya Gane Ana gana musu azaba.
Sosai ya rik'e tijjjani a Ransa.
Dan Bai ga wani laifin Murja ba Tijjanin da Bai saka Ido a gidansa ba yaga laifinsa.
A Haka ya saka kayan aikinsa suka hau aikin ginin.
Nadeeya nadaga inuwa tana surutai har ta Saba da Yan aikin wajen wani ya siya Mata shinkafa da miya har da nama surutunta da manyance ta yasa tayi farinjini akayi ta Mata siye siye tana Jin dadi Dan inda tafi kwarewa kenan
Ahaka wani Abba magini da gidansa ke kusa da wajen da suke aiki ya Dan hau tambayar Naseer dalilin dayasa yazo da Nadeeya wajen.
Shi kuwa yace Masa ba kowa a gidan ne iyalinsa sunyi tafiya shiyasa ya taho da ita Dan mak'otan nasa Basu fiye shiri ba.
Take shi kuwa Abban yace Mai zai Hana idan sunzo ta ringa Shiga gidansa idan sun tashi Kuma sai su koma gida tare.
Sosai Naseer Yaji dadin maganar Abba Dan Dama Yana ta tunanin Inda zai na Kai Nadeeya Dan Sam Baya San barinta a gida makaranta ne dai sai ya samu kudi zai saka ta islamiyya Kuma zai nema anan din har uniform ya Dinka Mata ta ringa zuwa Wanda yaran Abban ke zuwa.
Sai da suka Gama aikin Suka koma gida Naseer ya Dan siya musu kayan shayi ya tafar musu dashi.
A tsakar gida ya samu Safiyya taci uban kwalliya tana zance da wani.
Shi kam ya gaji da kwashe kwashen da Safiyya ke Masa a gida hakane yasa ya Isa wajensu Ransa a had'e ko amsa gaisuwar da suke Masa baiyi ba
Naseer yace Masa "idan dagaske kake kana San ka Aureta ka turo magabatanka"
"Dama yau tacemin na maka magana Dan inaso na turo magabatan nawa sai Kuma fad'uwa tazo daidai da Zama acan garin da dangin mahaifinta yake anan nake aiki.
Inada Mata daya da Yara shidda
"Zanje jibi insha Allahu mu tsayar da Magana Dan Nan da wata biyu nakeso ayi bikin namu"
"Allah ya yarda"
Kawai Naseer yace Dan har ga Allah gani yake Safiyya ta na cikin wayanda suke Masa Karen tsaye a rayuwarsa shiyasan ita ke saka Umma yin wani Abun.
A ranar Nadeeya ce ta ringa deb'e Masa kewa da surutanta ya hada da Bata tarihi annabi Yusuf Dan surutan nata ma ba wani Kan gadone dashi ba hakane yasa ya hau Bata tarihin Annabi Yusuf ta kuwa nustu tana ji ahaka har bacci ya d'auketa shima ya d'aura alwala Yana iddar da shafai da wutr ya d'auko Quraninsa Dan ya karanta.
Hajara ta fado d'akin kamar an hankadota.
A Gefen katifa ta zauna tana "Kai Naseeru dazu naji kana cewa saurayin Safiyya ya turo da fatan ka tanadi kudin da zaka Mata kayan daki Dan kasan banida ko sisi ban Kuma bawa wani ajiya ba".
"Banida ko sisi Umma Nima ban bawa kowa ajiya ba idan sun turo taje wajen dangin mahaifinta su harhada kudi su Mata kayan daki kamar yanda sukayi wa Lami Umma Nima ta kaina nake bazan iya zuwa nayi sata ba"
"Ai nasan da dangin mahaifin nata nace ka Mata kayan d'akin Dan ko Lami da iya katifa aka kaita har gobe Gori ake Mata ita kuwa Safiyya tana da kishiya Dole ayi Mata kayan daki "
Naseer Bai ce Mata komai ba ta Gama surutanta ta tafi.
Murja kuwa tana komawa gida ta fara tunanin hanyar da zata bi batare da Tijjani ya zarge ta ba Dan tasan Ransa sai ya b'aci idan yaji Mai tayi Su Hajara kuwa bashi suka dauka sai ta Rama abinda suka Mata idan ta samu ta Shawo Kan matasalar daya kunno mata Kai Sosai ta ringa tsinewa Nadeeya da Zahira tana Jin inama taga Nadeeya a gabanta da ba abinda zai Hana ta shaketa har lahira.
Bata San Mai yasa duk kamun da take wa Tijjani baya kamuwa ba tsinanen taurin Kai ne dashi ta Rasa dalili ballantana ta Mallakeshi Wai a Haka ma Mahaifiyarta tayi aiki babba akansa.
Daba haka ba da tuni ya saketa Dan bashida mutunci ko kad'an daga aurensu zuwa yanzu ya Mareta ya Kai sau uku gashi ita Kuma balain San shi take.
Ahaka ta zauna a gidan cike da fargaba dawowar Tijjani duk da ta gama.hada makircin da zatayi idan ya dawo.
Karfe shidda taji karar vespa dinsa.
Tayi sauri.ta zauna a tsakar gidan kafarta a kumbure Yana kyalli Dan ta kware a kumbura jikinta da wani hoda da Mahaifiyata ta Bata sai numfarfashi take idonta ya kad'a yayi.jawur
Abinda ya Bata mamaki Bai wuce yanda taji har lokacin Bai shigo ba hakane yasa ta lek'a cikin sand'a Inda kuwa ta hango Tijjani a tsaye ya Kama kugu Jamilu Mai shago nata kwara Masa bayani.
Gabanta ne ya yanke ya Fadi a lokacin data ga Tijjani idonsa ya kad'a yayi jajir sunyi musabiha da jamilun ya nufo gidan
Ita kuwa Murja cikin tashin hankali ta Shiga palo da sauri ta zauna jikinta na Dan rawar tsoro tana tunanin hanyar da zata Kare kanta
Daga yanda ya bugo k'ofar hantar cikinta ya kad'a
Ta daure ta mik'a kafarta tana ta adduar Allah ya dorata akansa.
Wani irin kallo ya hau jifanta dashi daya shigo cikin wani irin murya yace "Ina zahira da Nadeeya"?
Kuka ta fashe dashi ta Kara Mika kafarta daya suntume Yana kyalli ta hau cewa "Kaga k'afata wlh a garin na bisu nayi tarkade Nazo Zan Shiga wanka naji mmn Hafsa ta shigo aguje tacemin gasu can zasu gudu kwana uku kenan suna cewa zasu gudu wlh a garin nabi bayansu na Fadi har bugewa nayi a cikina"
Ta karashe tana fashewa da kuka
Tijjani kuwa ya karasa wajenta Yana "Muga kafar ya sunkuya ita kuwa cikin makirci ta Kara