Showing 111001 words to 114000 words out of 180103 words
mika kafarta tana cigaba da kuka Tijjani kuwa Yi yayi kamar zai duba kafarta aikuwa ya zaro belt ya hau tafkarta tana daga zaune.......
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 42*
Sosai.ya ringa tafka Mata belt din Yana soka Mata Ashar sai daya Mata lilis ya koma gefe Yana "Maza tashi ki tafi gidanku shegiya makira na tsaneki wlh Allah na tsani mutum munafiki Ashe tunda na kawo yaran Nan Haka kike azabtar dasu ba iya jamilu ne ya tareni ya gayamin ba har Mallam Ashiru wajen aikina yaje ya sameni ya gayamin Ina dawowa shima jamilu ya tareni da zancen ke wacce irin muguwa ce kina d'auke da ciki a madadin ki ringa addua Allah ya saukeki lafiya aa sai Kika saka mugunta agaba kina zalintar yaran da basuji Basu gani ba shegiya munafika Mai fuska biyu Maza tashi ki barmin gida.
Tijjani yace a fusace ya ruk'o hannunta ya fara janta da kasa ita kuwa sai numfarfashi take tana Magiyar yayi hakuri sharrin shaidan ne Bai saurareta ba sai daya kaita har waje.
Ya watsar da ita ya koma ciki ya cillo Mata takalminta da mayafinta.
Ya kulle gidan ya danne vesparsa tare da bada Mata k'asa.
Sai data daina hango vesparsa ta mik'e dak'yar tana cije lebb'e sabida yanda jikinta ke balain rad'adi ko ta ina sabida ba karamin Jibga ya Mata ba.
Gidan dake jikin gidansu ta shiga ko Sallama babu
A tsakar gida ta tarar da matar gidan na zaune a Kan tabarma tana yiwa yarta kitso Mallam Ashiru Kuma na zaune akan kujera Yar tsugunno da buta agabansa da alama jira yake a Kira sallah yayi alwala.
"Lafiya Kika shigo Mana ba Sallama "
Dalla rufe min Baki Dan ba wajenki Nazo ba wajen wanan Dan iskan Mai dogon wuyan Nazo wato sabida munafinci shine kaje ka samu mijina kace Ina zalintar yaran da aka kawomin Ina ruwanka da rayuwata da ina ruwanka da abinda nakeyi shege munafiki tsinane kaji da matsalolin da ke gabanka Mana na me sai ka Shiga abinda Bai shafeka ba toh burinka ya cika ya ce na tafi gida wlh Allah kayi addua Kar munafirci da kayi ya zama sanadin mutuwar aurena Dan wlh idan Aurena ya mutu zakayi mamakin abinda Zan maka sai ka gwammace ma da baka sani ba"
Daga Mallam Ashiru har matar tasa ba Wanda ya iya magana har ta juya ta tafi.
"Sai Dana Gaya maka ba ruwanka Dan matar Nan wlh ba mutunci ne da ita ba kaf unguwar Nan ba Wanda take muamalla arziki dashi ba Mai Shiga harkarta sabida mugun halinta Amma gashi"
"Dalla kirufemun Baki Taya zakice Kar na Gaya masa tana zalintar yaran daya kawo gidanan ke kanki anan kin Sha kukan tausayin yaran idan kika jiyo tana jibgarsu aikin kenan Haka zatayi ta zaginsu tana duka Akan me bazan Gaya masa ba sabida yayi wa tufkar hanci kafin ta Kai ga tayi kissan Kai yanzu Dana fada Masa bashine ya sani ya dau mataki ba"
"Allah ya kyauta"
Kawai matarsa ta iya cewa
Shi kuwa yaja Tsaki Yana Dan Jin sanyi a Ransa Dan sosai yake tausayin Su Zahira idan Yana jiyo irin bugun da take musu Badai tab'a yiwa su Zahira magana bane.
Murja kuwa tana fitowa daga gidan
Shagon Jamilu ta tsaya sukayi ta zagin Juna tana rantsuwar sai taga bayansa tunda ya hadata da mijinta shima rantsuwa yake akan ba Abunda zata iya Masa Dan Kar yake kallonta idan takamarta uwarta matsafiya ce zata Masa wani Abu ta gwada ta gani wlh sai ya kawo karshenu shima ai ba Haka yake zaune ba"
Murja kasa magana tayi sabida mamaki yanda Jamilun yasan Mahaifiyarta matsafiya ce ba ta iya Kara magana ba ta fice daga shagon tana cigaba da Shan alwashin sai ta ga karshen Jamilun.
Tana Isa gida ta zub'e a tsakiyar palon nasu ta hau kuka.
Mahaifiyarta Rabi ido ta zuba Mata Bata ce Mata komai ba.
Sai da Murja ta gaji Dan kanta ta bud'e baki da zumar Mata magana Rabi ta daga Mata hannu fuskarta hade tana "Ba sai kin gayamin komai ba Naga duk abinda ya faru dazu kawai na dauko tukunya ta Dan na duba halin da kike ciki Naga Yana ta jibgarki ai sabida Dan iska ne shi bashida mutunci Bai ga cikinsa da kike d'auke dashi ba yayi ta dukanki ai ba jaka na aura masa ba Amma ba komai yyi na farko yayi na karshe shi da ganin Haske sai dai a lahira"
Rabi tace Tana k'ok'arin mik'ewa
Murja kuwa cikin tashin hankali ta dira gabanta tana "Mama Dan Allah karki Masa komai wlh inasan mijina Dan Allah karki Masa komai wlh ba laifinsa bane Mama karki makantarmin da miji Dan Allah
Fusge kafarta Rabin tayi tana "wlh sai nayi Abunda nayi niyya Dan ya kaini bango na tsani mijin Nan naki wlh tunda Naga Yana da taurin Kai duk aikin Dana Yi akansa Baya ci na tsane shi na rasa Mai yasa Kika nace kina San zama dashi"
"Nidai Ina San shi mama Dan Allah karki Masa komai nidai burina kimin aiki akansa Mai zafi yazo da kansa ya maidani gidansa a Kuma mallake min shi ya daina min taurin Kai duk abinda nace yayi shi zaiyi.
Mutane biyu nakeso kimin maganinsu wani jamilu da wani Ashiru makocina su nake so ki Gama min dasu Dan su suka hada min munafirci Nan sai Kuma uwar mijina da kanwar mijina Umma inaso Suma ki kawomin karshensu duka sukamin yau har kasa suka bani naci"
Tsaki Rabi tayi ta janyo bakin tukunyar tsafinta gabanta dake cike da wani irin ruwa tana "Daga Kan shegen mijinki zan fara Dan wlh Bai daki banza ba
Take ta hau surkulle Tijjani ya bayyana saman ruwan Yana Kan vespansa Yana ta tuk'i
Murja cikin tashin hankali ta hau ihu tana Mama Dan Allah karki Masa komai ki taimaka min wlh inasan mijina"
Wani dogon Abu Rabin ta d'auko kamar kibiya zata caka a ruwan.
Murja ta fizge kibiyar da k'arfi.
Rabi kuwa ta girgiza tukunyar da Tijjani har lokacin yake bayyane Yana tuki.
Take kuwa vespan nashi ya hau tangal tangal dashi har sai daya bige wani Mota dake gabanshi ya hantsulo daga Kan vespan.
Ta daki ruwan Tijjani ya b'ace Murja ta hau zunduma ihu
Ita kuwa ta daka Mata tsawa tana ban masa.komai ba na dai Masa gargadi ne kawai
Dan wlh wanan shine na farko na Kuma karshe idan ya Kara tabaki wlh sai na raba shi da numfashinsa
Sai wa kikace "Nidai nunamin shi nagani na tabbatar ba Abunda ya sameshi"
"Ba Abinda ya sameshi dalla karki dameni wlh Kika batamin Rai Zan Masa Mai gabad'aya
Tace a tsawace Tana Kara surkulle Sai ga Mallam Ashiru ya bayyana a cikin Massallaci a zaune tana daga kibiyar tsafin ta ya b'ace
Duk abinda take Murja na kallo
"Wanan sai anyi da gaske Dan Baya Wasa da Addu'a"
Surkulle ta Kara Yi amadadin Jamilu ya bayyana sai Murja ce ta bayyana
Hankali a tashe Rabi ta girgiza tukunyar tana "wanan Dan iskan ne Ina tab'a shi kanki zai dawo shima sai na shirya sosai Dan bahaka yake zaune ba
Ita Kuma uwar mijinki da kanwar mijinki kibarni dasu sai kin koma.zaki dau fansar abinda suka Miki
Wanan mijin sai nayi dgsk Zaki mallakeshi taurin Kai ne dashi"
Sosai Murja ta ringa Jin dadin mallake Mata Tijjani da mahaifiyarta tace zatayi
Tijjani kuwa Yana hanya zaije gadon Kaya wajen Naseer yana dab da Isa wajensa yaji Kan machine din na rawa Yana neman kwace Masa duk yanda yaso rik'e Kan machine din kasawa yayi har sai daya buge wani Mota dake gabansa ya hantsula.
Sallati mutane Suka saki sabida duk an dauka Tijjani bazai Kai labari ba sabida ya daki motar gabansa sosai
Ga mamakin.mutane Kuwa suka ga ya mike tsaye Yana karkad'a jikinsa
Mai motar kansa da aka buge sai daya fito ganin Tijjani Bai ji ciwo ba yasa ya koma ciki yaja motarsa batare da ya tsaya sauraran hakurin da Tijjani ke bashi ba Dan ya fasa Masa glass din motarsa.
Vespa din ya hau ya koma gida dan kayansa sun b'aci washegari da sassafe ya dau hanyar gidan Naseer sai daya fara tsayawa a tsohon gidan Naseer ya tambayi Inda suka koma da kwatance yaje har k'ofar gidan.
Da Sallama ya Shiga gidan
Nadeeya dake shara a tsakar gidan ce ta amsa ganin Tijjani ne yasa tayi wurgi da tsintsiya hannunta taje ta rungumeshi tana Masa oyoyo.
Naseer dake kitchen fitowa yayi da kofin shayi a hannunsa.
Duk da Yana Jin Haushin tijjanin Haka ya saki fuskarsa
Ya Yi wa Tijjani iso har palon
Hajara dake zaune da Safiyya a daki suna Shan shayi kamar a mafarki taji muryar Tijjani ta kuwa Mike da Sauri tayo waje Dan ta gaskata zarginta
Wani irin hade Rai tayi ta fito daga d'akin a daidai lokacin. Da Tijjani ya zauna Akan tabarma dake shimfide a palon hannunsa cikin Na Nadeeya
"Uban me kazo nema a gidanan Tijjani"?
"Aaaa hajajju makatu Ashe kina ciki Rai kanga rai hajiya Umma"
Tijjani yace Yana dariya dayaga yanda Hajara ta had'e Rai
Hajara kuwa tace "ubanka kake rainawa Hankali Tijjani bani ba maza kafin na kirga uku tashi ka bar gidanan Dan na Gaya maka na yafeka banasan ganinka"
Dariya Tijjani ya sakeyi Yana "Sai hakuri fa Umma nazama Dolenki ba ynda zakiyi inkika koreni Ina kikeso naje"
"Kaci ubanka Tijjani ka dauka Wasa nake ma ko Ni da ka kora daga gidanka har da biyomu da kudin mota ka zabi Zama da matarka Tijjani akan dai kabi Umarnina baka darajani ba a matsayina na mahaifiyarka ka zabi tsinaniya da Bata tsoron Allah k'arfi da yaji ta zaneni Akan shegen bredi kana shigowa ta had'a makirci ka k'i yarda da maganata har sai daka koreni daga gidanka ka dauka Wasa nake Akan na yafe ka a cikin yarana Murja tazama uwarka tunda ita ka zaba akaina Tijjani idan baka San na Kara maka wani bakin ka tashi ka bar gidanan Dan wlh ganinka b'acin Rai yak'e Kara sani"
"Umma Nima fa bansan makira na aura ba wlh sai Jiya nama koreta tana gidansu yanzu Haka Dan wlh bansan Haka take ba kinji na rantse Miki ban taba sanin munafika bace Mai fuska biyu ba sai Jiya da makocina da Mai shagon unguwarmu ya gayamin yanda take yiwa su Zahira bantaba sani ba sai Jiya shiyasa ma Nazo Dan na bawa Yaya Naseer hakuri kema na baki hakurin"
Sai a lokacin Hajara ta Dan saki fuskarta tana "Kana nufin yanzu Haka tana gidansu"?
"Eee tana can"
"Saki nawa kayi Mata"?
"Ban dai sakenta ban nace taje gida"
"Zancen banza baka saketa ba zaka dawo da ita kenan"?
"Aaa bazan dawo da ita ba hajiya Umma ai kina da kudin da Zaki aura min wata matar tunda gashi Nan kin raba Yaya Naseer da Aunty Naeema ya zama gwauro na k'arfi da yaji Nima ba sai na dawo gabanki kiyita kallonmu ba"
"Gwara nayita kallonku a gabana da dai ku zauna da wadanan shegun matan naku"
"Murja dai nasan shegiya ce tunda ta iya makirci ita aunty naeema fa mai ta Miki bakya santa"?
"Bansani ba ubana zaka iya matse bakina in gaya maka Naga alamar ka ma Raina min hankali toh gwara da kazo ma auren Safiyya Nan da wata biyu masu zuwa jibi xaaje neman Aurenta can wajen baffaninku kasan yanzu Naseeru bashida ko sisi Haka Muke zaune Dan Haka ka kawo kudi mu fara rage wani Abun "
Duk maganar da Tijjani da Hajara sukeyi Naseer Bai tofa musu Baki ba kansa a sunkuye yama tafi wata duniyar tunanin
"Umma kema da abin dariya kike Ina Naga kudin da Zan siyawa Safiyya wani Abu ai ko sisi bana magani nima.murja ke ci damu a gidanan tunda Kika Mana abinda kikayi arzikinmu ya tafi muke fama wanan Dan canter da Kika Sani dashi har yanzu shine Dani maneji kawai nake Dan Haka ki San yanda zakiyi da ita"
Dagowa da Naseer yayi ya kalleshi yasa ya kifta Masa Ido
Hajara kua ta dage wlh su biyu su nemo kudin da zasu yiwa Safiyya kayan daki ko satane suyi ita ba ruwanta
Tijjani dariya yayi Dan shi Sam Baya d'aukar ma maganar Hajaran da wani mahimmanci inzata matsa Masa ma saka takalminsa zaiyi yayi tafiyarsa
Hakuri ya bawa Naseer game da abinda ya faru
Naseer kuwa yace masa ba komai
Suka hau Hira da Nadeeya da ta hau bashi labarin irin dukan da Murjan ke musu ba abinda ta rage a azabar da ta gana musu Inda ran Tijjani ya Kara b'aci sosai dayaga tab'a b'unan jikin Nadeeya wake da sabulun ma datace Ana Basu suci yafi balain kona Masa Rai Bai taba sanin muguntar Murja ya Kai har. Nan ba Bai taba sanin ma Haka halinta yake ba.
Ita kuwa Hajara cewa take zatayi abinda yafi wanan Dan Haka ya saketa.
Tijjani cewa yyu in ya koma gida zai aika Mata da saki daya Naseer kuwa yayi saurin girgiza Masa Kai Akan Kar ya saketa ya dai Mata fada sabida ita kanta Bata San ya rayuwa zata kasance Mata a gaba ba ko shi kansa Bai taba tunanin akwai ranar da wani Abu zai saka ya Kai yaransa wani wajen ba sai gashi kaddara ta sa ya Kai su Zahira gidan nasa.
Tijjani sosai yaji tausayin Naseer Dan har ga Allah yasan dauriya kawai yake Yana cikin damuwa.
Bai bar gidan ba sai wajen Sha daya na Rana tare suka fito da Naseer da Nadeeya.
Hajara duk rokon data masa.akan ya Bata kudi dagewa yyi bashida ko sisi Naseer har mamakin Tijjanin ya ringa Yi Dan abinda Sam bazai iya ba kenan.
Har wajen da Naseer ke aikin ginin Tijjani ya raka shi Suka samu inuwa suka zauna
Naseer ya Dan Kara bashi labarin yanda Naeema tazo ta Debi yaran
Da yanda Nadeeya ta dage bazata bisu ba da shi zata zauna
Ajiyar zuciya Tijjani ya sauke Yana "can garin nasu ta Kai yaran"?
"Wlh bansni ba Ina cikin tambayarta Umma ta shigo ta hau ce Mata karuwa k'arfi da yaji Umma ta hanani zaman lafiya ta hanani na samu nutsuwa inasan na kasance da iyalina ta hanani"
"Kaine ka barta fa Yaya Naseer wlh Kai kabari take maka abinda ranta keso Ni bazan iya d'aukar abinda take ma ba Kai ma kagani ai Umma wani zubin zuma ce ita sai da wuta idan inasan Abu wlh sai dai tayi hakuri ta kyalleni ai ba Dole bane sai ka zauna da ita ka Kama Mata haya ka dawo da iyalinka gabanka idan tak'i ka siyar da gidan ka gudu ka barta Dole dai ta koma Calabar"
"Mahaifiyarmu ce fa Tijjani idan na siyar da gidan na gudu a Ina zata zauna Naga basa shiri da matarka balle nace gidanka zata dawo bama Zan Sam kwanciyar hankali ba idan Naga tana garari"
"Toh naji yanzu dai abinda zaayi kayi k'ok'ari ka nemi Inda Naeema take ka ringa zuwa kana dubasu Koda baka Kai musu komai ba yaranka su ringa ganinka Suma suna Jin dadin kaima sanin halin da suke ciki zai saka ka Dan samu kwanciyar hankali Sanan Nadeeya gaskiya gwara ka maidata wajen Naeema Sabida daga Kai har Naeema sai kunfi samun kwanciyar hankali bazai yiwu ka ringa fita kullum da ita sai kace namiji ba ke Nadeeya ki Bari Abbanki ya maidaki wajen ummanku shima Nan zai dawo idan an kwana biyu"
Nok'ewa tayi Tijjani ya hau rarrashinta da Mata alkawarin siya Mata kaza da nama take ta hau washe baki tace ta yarda.
Tijjani kuwa yacewa Naseer yayi kokari yasan Inda su Naeema suka koma Bauchin ne ko Kano ya maida Nadeeya ya Kuma ringa lek'a su akai akai.
Naseer godiya ya Masa sosai Yana Jin dadin shawarar Tijjani Dan kwana biyun Nan sosai ya ji Yana k'ewan Naeema.
Har kyautar kudi Tijjani ya bashi kafin ya tafin
Naeema
Washegari da safe na bazama nemowa yarana makaranta Mai Dan saukin kudi.
Dan Zahira Naga ta tsayi Tama Zama budurwa tunda a yau na wayi gari Naga period ya zo mata boye boye ta ringa min duk da ciwon marra da take fama dashi Amma kasancewar waje daya muka kwana yasa nasan halin da take ciki.
Zaunar da ita nayi na Bata ilimin Shi kansa haila banji kunyar ta ba na fada Mata komai da yanda zatayi wanka idan jinin ya d'auke har yanda zata tsaftace jikinta da Kuma Kara kame Kanta daga wasa da maza
Daidai da kuzungu ma Ni na koya Mata yanda zata saka Dana saka tayi wanka ta wanke zanin data b'ata sai wani sunne Kai take Wai kunya ta takeji.
Ni kuwa a Raina ma mamakine nake yaushe har nayi auren wai Yar cikina ta fara period kila kwanan Nan ma naga ana Sallama da ita Akan Ana Santa.
Hakane yasa Dana karya na bazama nemo makaranta Dan so nake ma ta fara secondary daga jss 1
Wani karamin makaranta na samu Mai Dan saukin kudi.
Sai dai ba secondary sch Wai sai dai ta zanna common entrance tunda baifi saura sati biyu a zanna ba samun secondary bazaiyi wahala ba indai ta zanna common entrance din.
Sai Dana koma gida na tafi dasu Zahiran gabadayansu sabida tace zata musu gwaji sabida tasan ajin dazata saka su.
Ba laifi yaran nawa na da Dan kokari duk da akwai slow learner's a cikinsu kasancewa na biya duk kudin da aka bukata har na uniform text books kawai Zan siya musu littattafai Kuma inadashi a shago
Nadeeya ce kawai nace mata Zan kawota Bata Nan ne ta bani uniform dinta na tafi dashi yarana kuwa kamar Wasa Naga sun shige aji.
Zahira Kuma ta wuce primary 5
Cikin farinciki na dawo gida
Na dau littattafai dozen uku da fensura na bawa Isihu ya Kai musu da biscuit ya zama Dole na dauko Nadeeya Dan nasan Bai Zama lailai Naseer ya samu kudin sakata a makaranta ba.
Safiyya
Kwana biyu da maganar da Naseer yayi wa Saurayinta Umar akan ya tura neman aurenta.
Yaje har garin calabar ya nemi kanin mahaifinsu ya gabatar da kansa dayake a shirye yake har Sadaki ya bayar Dan sosai kwallin da Safiyya ke sawa ya rikita shi yaji idan Bai Aureta ba bazai samu nutsuwa ba.
Anan garin calabar yake zaune da matarsa Hafsa da yayansa.
Matarsa macece Mai balain