Showing 120001 words to 123000 words out of 180103 words

Chapter 41 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2455

hakane yasa ta Kara tattara Kayanta da kudin mota ta nufi Tasha ta hau motar Kano Inda ta yanke Zama a gidan Tijjani tunda Bata da Inda zata zauna har.daji ta nausa Dan shugabarsu ta gano Mata Inda Naseer. Yake ta kuma.kara rokarta mudubin tsafi Dana karfinsu har ta karaci yaren tsafin dake sa ta bayyana a gabansu Bata bayyana ba.

A mugun gajiye ta isa gidan Tijjanin Inda taci Karo dashi a bakin kofa zai fita massallaci turus yayi daya ganta da Niki Nikin Kaya Hajara kuwa ta sauke kayan daga Kanta tana "Bani hanya na wuce ka tsaya kana kallona kamar baka sani ba ka shigo min da kayan Nan maza"


Tace tana matsar da Tijjanin tare da shigewa cikin gidan tana Kara hade Rai Dan so take ta gwada karfin uwa akan Tijjani ya mata biyayya kamar yanda Naseer ke Mata duk da kasan zuciyata tana Dan Jin shakkar Murjan

A.palo ta tarar da Murja da jaririyar ta a hannu da Bata fi kwana biyu da haifarta ba.

Kallon kallo suka yiwa Juna a daidai lokacin da Tijjani ya shigo da bacconta Yana "Umma Wai daga ina kike naganki da Niki Nikin kaya"?


Daga calaba nake na Kuma dawo Nan da Zama Dan Safiyya ta siyar da gidan Naseer tayiwa kanta kayan daki banida wajen Zama shiyasa nayo Nan Dan Ni na Haifeka Ina Kuma da iko dakai matarka Bata Isa ta hanani na zauna a gidanan horar yunwar datamin a baya wlh bazan dauka ba indai ta gwadamin kuwa wlh sai ka saketa"


"Mamakine ya rufe Tijjani a lokacin da Hajara tace Safiyya ta siyar da gidan Naseer anyiwa Safiyya kayan d'aki cikin mamaki yace "Umma Safiyya ta siyar da gidan Naseer fa kikace bangane ta siyar da gidan Naseer ba Umma yanzu gidan Naseer kuka siyar Dan ayiwa Safiyya kayan daki innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"


Hajara Tsaki tayi ta mik'e tana "Duk ba laifin Kai da naseerun bane kuyiwa Safiyya kayan daki kunce bakuda kudi karka sake ka dameni da tambayoyi kaji ko"


"Umma kinsan Allah bazan d'auki abinda kuke yiwa yaya Naseer ba bazan hanaki Zama a gidana ba Amma wlh bana San hayaniya da takura Dan gaskiya bazan dauka ba.

Daga Haka ya fice waje.yana Jin bakinciki siyar da gidan Naseer din datace sunyi har mamaki Naseer ke bashi daya bar Hajara take garashi yanda ranta keso.

Hajara kuwa Inda suka zauna da Safiyya Nan d'akin ta shige abinta da kayanta.
Ta fito daga d'akin ta shiga kitchen Kai tsaye ta zubo abincin da ta gani ta dawo palo ta zauna tana hararar Murjan dake Mata wani irin shu'umin murmushi tana girgiza kai Dan ta daga Mata kafa ne kawai Dan Tijjanin na Nan.

A takaice duk inda Hajara taso itama ta nuna iko da isarta kasawa tayi Dan Murja shu'uma ce ta gaske Dan haihuwa da tayi yasa danginta suka cika gidan Tijjani Kuma ba wani Zama yake ba yana fita zasuyi tayiwa Hajara rashin mutunci Bata Isa ta tanka musu ba idan kuwa ta saka Abu a bakinta sai dai idan Tijjani ne ya dawo ta rokeshi ya Bata makirci kuwa sai abinda ya dadu da Murja ta Karo Dan kawai ta bar gidan



Hajara kuwa duk yanda taso yiwa Tijjani bayani sai yace Mata shi Baya San tashin hankali Shifa ba naseeru bane.


Idan ta masa hargagin ita fa uwarsa ce Bai Kamata ya Fifita Murja akanta ba sai yace wane shi ya Fifita Murja akanta ahaka zai maidata mahaukaciya Yana Mata dariya.

Sosai ta gwammaci zama a koina da zaman gidan Tijjanin Dan sau uku kenan Murja na Mata duka.

Ba yanda batayi da Tijjani ya saketa ko ta tsine masa ba yak'i sakinta yace Mata Yana San matarsa.

Ahaka zata rufe ido. Ta Masa mugayen kalamai idan Murja ta Mata wani Abun shi kuwa Tijjani sai ya fice ya bar gidan

A ranar data cika wata uku a gidan Tijjani
A ranar Safiyya itama ta duro gidan da cikinta da takardar sakin da Umar ya Mata wiwi tana kuka da lodin Kayanta.

Tijjani kuwa rantsuwa yayi bazata zauna Masa a gida ba sai dai ta nemi wajen Zama sai da.hajara ta hau Masa kuka ya bar Murjan ta zauna Dan ko ba komai taji dadin ganin Safiyya da sakin da aka Mata Dan zuwanta zai saka ta Dan samu saukin wani abun daga wajen Murja su Kuma nemi hanyar da zasu ci uban Murjan su dau fansar duk abinda ta musu.


Sai dai zuwan Murja gidan yasa.tijjani ya bud'e kwandunan. Rashin mutunci Baya dagawa Safiyya kafa ko kad'an duk da kanwarsa ce ya balain tsanarta

Ga Murja itama a gefe tana Gana musu azaba Dan kudin da Safiyya tazo dashi na kayan d'akinta data siyar a can calaba da baiyi albarka ba dashi Suke siyan abinci idan Murja ta hanasu

Sosai suke rufe Ido suna neman bokon da zai.musu aiki akan.murja,Hafsa da Umar da suke ganin sune makiyansu a Duniya Bayan Naeema.

Ganin kudin su ya tasama karewa yasa Suka yanke shawarar fara siyar da kosai a waje.

Safiyya ce ta tafi siyan kayan da zasu bukata na kosai

A wani shago dake can kasa dasu

Kamar ance ta waiga ta hango Naseer da Tijjani a tsaye nesa dasu suna magana hakane yasa ta gwallo Ido tana kallonsu

Ganin Tijjanin ya hau vespensa ya tafi shi Kuma Naseer ya fara k'ok'arin tarar taxi yasa tayi saurin fitowa daga shagon itama ta nufi titin da Sauri tana rufe fuskarta.

Tana Isa titin Naseer.ya samu taxi ya shige

Itama.ta tari wani da Sauri ta shige ta ringa bin bayan Naseer.

A takaice ahaka ta rufe fuskarta tabi Bayan Naseer har k'ofar gidan Naeema

Ta gwallo Ido a lokacin da ga su Minal sun fito suna Masa oyoyo.

Ya rik'e hannunsu Suka Shiga gidan

Sai da Safiyya ta Fadi ya Kai sau uku sabida azabar saurin ta koma gida ta Sanar da hajara Kamar ta tashi sama.

Ido rufe ta Kara Hawa taxi ya maidata unguwar su Tijjani tace ya jirata gata Nan fitowa.

Hajara kuwa Safiyya na Bata labari ta hau had'a Kayanta tana Godewa Allah.

Cikin kankanin lokaci suka jiddi kayansu suka zuba a taxi Suka dau hanyar dorayi Kamar su karbi tukun Dan gani suke Kamar ba tafiya taxin keyi ba.....



*Inaso na Dan Yi shi a gurguje mu shiga ainihin chapter 3 na labarin Naeema Dan na Gaya muku Yana da tsayi ahaka ma masu Dan mahimmancin nake rubutawa*
8/19/21, 10:32 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*


*Page 46*


Suna isowa k'ofar Gidan jiki na rawa suka mik'awa Mai taxin duk kudin hannunsu kowacce ta fito da kayanta da kanta bakinsu a washe Kamar gonar auduga sosai sukeji Kamar sun samu yancin kansu.

A k'ofar shagon da Isihu ke sallamar mutane suka tsaya suna karewa gidan kallo.

Hajara ta Shiga shagon ta daga Kai sama tana kallon yanda shagon yake cike da Kaya har da buhunan danyen abinci ake siyarwa a shagon

Da farko Bata Gane Isihu ba sai daga baya tace"Shege Ashe kaima Nan din ka gudo shiyasa baa ganinka Kai Kai kai Safiyya Kinga katon shagon da Naseer ya bud'e amma muke zauna a gidan Tijjani muna Shan bak'ar wahala kawai sabida an siyar Mai da gida sai yamin karyar zai Shiga duniya Ashe Yana. Nan Yana Jin dadin rayuwarsa da Naeema da yayansa.

"Wanan ba shagon Yaya Naseer bane shagon aunty Naeema ne"


Isihu yace Yana had'e Rai tare da fusge bredin da Safiyya ta d'auka Dan bak'ar yunwa takeji cikin jikinta balain sakata cin abinci yake.

"Iyye a gidan uwarka ya Zama shagon Naeema wato abinda aka kitsa maka kenan ka.ringa fada zaka ci ubanka Bari nashiga gidan wlh sai na saka Naseer ya koreka daga shagon Nan"


Daga haka ta fito daga shagon Safiyya na dannawa Isihu zagi tare da dumbuzar garin kwakin dake cikin buhu ta tura a bakinta Dan kamar taci babu Haka takeji.

Ba Wanda yayi Sallama a cikinsu suka Shiga gidan.


Ina zaune a tsakar gidan Ina yiwa Zahira kitso su Nadeeya su Kuma suna cin shinkafa da miya da kifi Naseer kuma ya Shiga d'akina yayi wanka Dan ya canja Kaya ya Kara fita Dan Tijjani ya Nemo Masa irin aikin da yakeyi a wani company duk da albashinsu ba yawa Haka Naseer ke fita da sassafe idan sun samu break sai ya dawo gida yaci abinci ya Kara watsa ruwa ya fita bazai dawo gidan ba sai wajen Goman Dare.

Dawowar Naseer da siyar Masa da gidan da su Umma sukayi sai Dana Yi dgsk Naseer ya iya fawwalawa Allah komai Dan sosai yayi rashin lafiya gidansa.

A ranar da Umma taje gidan Tijjani take Sanar.masa da sun siyar da gidan

A ranar Tijjani ya nemi gidanmu yazo ya kuwa tarar da Naseer a gida.

Sosai ya nuna Jin haushinsa da Naseer ya Bari Suka cutar dashi Bai dau mataki ba har korar Hajara yayi niyyar yi ya Bata kudin mota ta koma calaba wajen Lami ko Safiiyya Naseer yayi ta rokonsa akan yayi hakuri Kar ya koreta tausayin Naseer yasa ya Nemo Masa aikin dak'yar da albashin ba wani taka Kara yayi ba Amma ya gwammace ya ringa fita din daya zauna Haka Naeema na d'aukar Nauyin shi da yaransa.

Naeema kuwa budi take samu ko ta ina Dan har katon fili ta siya da Sunan Waleed.

Tunda Naseer yayi ramar siyar da gidansa da su Umma sukayi Bai Kara maida jikinsa ba.

Ni kuwa daga Ni har yarana munyi sharr damu ban taba tunanin Zan danyi kib'a a rayuwata ba sai yanzu Zan iya rantsewa ban taba jina a cikin kwanciyar hankali batare da fargabar komai ba sai a yanzu da babu umma da Safiyya dake dagamin hankali Ashe Zan tab'a tsintar kaina a cikin kwanciyar hankali Haka kudin da nake samu Bai taba sawa na Raina Naseer ko na nuna Masa iko da dukiyata ba duk da Naga alamar Yana da gudun zuciya Dan karfin Hali irin nasa yasan muna da komai Amma idan aka bashi allowance din sati ko albashi sai ya Dan tsinto Mana wani Abu ya kawo na amfanin gidan.

Sai danayi dagske ya daina siyowa nace ya ringa Tara kudin ya samu na siyan fili Dan Naga rashin gidansa har yau yasa bashida walwala Kuma Yana fama da ciwon kirji har yanzu.

Yarana kuwa duk suna ingantaciyar makaranta Dan Zahira yanzu tana jss 2 San Sai da aka Mata tsallaken jss1 sabida tsayinta.

Sosai nake mamakin girman Zahira da kyaun da Allah ya Bata da ko Ni Dana haifeta wani zubin bana iya d'auke idona akanta.

Ga balain farin jini da Allah ya Mata na kawaye tun ma ba'aje koina ba Wai wasu ke zuwa Sallama da Zahira.

Nadeeya ce take primary 5 yanzu Minal a primary 4 Humaira 3 Raheema a primary 2 Waleed Kuma na nursery Dan makaranta ma Dana saka shi na daban ne.


Shigowar Umma da Safiyya yasa na saki baki Ina kallon ikon Allah.

Yarana dake cin abinci kuwa duk suka Mik'e tsaye Suma Kamar sun ga dodon Ni

Safiyya kuwa idonta kur Akan abinci da yarana keci Umma Kuma ta tsaya a tsakiyar gidan tana karewa ko'ina kallo tana "Lailai Naseeru Ashe Haka yake.jin dadin rayuwarsa shine muke cin ubanmu a gidan tsinannen yaron can Banda abin Naseeru Dan zai zauna da Naeema har sai yamin karyar zai Shiga duniya"


Muryar Hajara ne yasa Naseer dake sallah yin saurin Sallame sallahrsa ya fito Dan ya gasgata muryar wacce yake ji.

Daskarewa yayi a bakin kofa a lokacin daya daga labule ya hango Hajara da uban Kaya agabanta tana karewa gidan kallo Allahuma ajirni fi musibati wa aklifnin khairin minha ya hau fada a fili Sam bai lura da Safiyya ba sai daya ji tashin muryarta tana "Mai kuka wani tsatsaremu da Ido kamar Baku sanmu ba shegu Wanan uban abinci da kuke ci Haka har da kifi lailai kun samu duniya Umma Bari na fara cin wanan tukunna na samu nutsuwa kafin a zubo Mana Dan Naga matar gidan kanta a sama yake Bata so ganinmu ba"


Ta nufi wajen su Nadeeya gadan gadan

Naseer kuwa ganin Safiyya ya tayar Masa da ciwon kirjinsa Yana jin ciwon siyar Masa da gidan da tayi na dawo Masa tamkar a lokacin ta siyar.

Bai San lokacin da ya isa gaban Safiyya dake k'ok'arin Zama Dan taci abinci ba Ido rufe ya cakumeta ya tsayar da ita ya hada kanta da bango tare da shake Mata wuya Yana k'ok'arin rabata da numfashinta da yakeji a Ransa tabbas kashe Safiyya ne kawai zai saka ya daina Jin ciwon dayake ji a kirjinsa.

Hajara. Hankali a tashe ta nufi wajen Naseer ta fara ihun ya cikata kar ya kasheta Bai ga cikine a jikinta ba

Amma Naseer ko gezau baiyi ba sosai ya Kara shake Safiyya Yana ta biyashi kudin gidansa.

Ni kuwa ko kallonsu banyi ba na ja hannun yarana na turasu dakina na rufe k'ofar dakina na nufi daya d'akin shima na rufe na saka kwado.

Kitchen Dina ma Haka na koma na zauna akan kujera danake Kai na dau Reza na fara gyara farcena.

Dan Basu isheni kallo ba wajen Naseer Suka zo ba wajena ba so nake su Gama abinda suke su juya su bar min gida.

Dan Naseer a yau zai San da da yanzu ba daya bane ko kusa ko alama bazan dau abinda sukamin a baya ba a da Dan Ina zaune a gidansa ne suka min abunda ransu keso Amma yanzu kuwa gidana ne Bari Naga iya gudun ruwansu.


Azaba ne yasa Safiyya sumewa

Dan ba iya shak'a Naseer ya Mata ba sai daya hada.mata da duka.

Duk dukan da Hajara ke Kai Masa tana ihun kuka har da su cizo Naseer Duk baiji ba sabida yanda idonsa ya rufe.

Sai dayaga Bata motsi ya cikata Hajara ta zub'e gaban Safiyya tana zagin Naseer akan gida zai kashe Mata 'ya Naseer kuwa a tsawace yace"Umma Mai kuka Zo Nema Kuma a gidanan"?


Hajara butar data gani da ruwa ta watsawa Safiyya.

Safiyya kuwa taja dogon numfashi

Hajara ta saki ajiyar zuciya tana "Naseer bakada hankali ko kasheta kake so kayi sabida kawai ta siyar maka da gida ba na baka hakuri ba a gidan uban wa kakeso ta samo kudin da zata biyaka.

Naseer karka manta nifa Mahaifiyarka ce kaina Kuma babbn D'ana yanzu Dan an siyar ma da gida shine zaka min karyar ka Shiga duniya Ashe kana Nan kana Jin dadinka da Naeema Ni danake mahaifiyarka Ina can Ina Shan wahala abinci ma na neman gagararmu Tijjani dayake tsinanne daga shi har matarsa azabtar damu suke idan baka rik'eni ba wa kake so ya rik'eni Safiyya ma da ciki tsinannen mijinta ya korota bamuda kowa sai Kai d'in Dan Haka hakuri zakayi mu zauna a nan gashi Allah nata Buda maka ga katon shagonka cike da Kaya ga Dan karamin gida karka wani damu tunda ka dage zaka zauna da Naeema ba yanda zanyi Haka zamu zauna"


Sai a lokacin na Dago kaina daga yanken farcen da nake na mike Ina "A Ina zaku zauna Umma ba dai a gidana ba ko? Dan wanan karamin gidan da kike gani halal Dina ne da kudina na siya babu ko sisin Naseer a ciki.

Gashi Nan agabanki ki tambayeshi kiji shima Dan yaransa na barshi yake zaune a gidanan Dan Haka ki nemi wani gidan ki zauna ba dai gidana ba idan ma Dan Naseer na gidan ne shima wlh Tallahi Zan hado masa kayansa ku tafi Dan bazan yarda ku zauna a gidana ba kamar yanda Baku yarda na zauna a gidan Naseer ba"


Hajara tsananin.mamakin Naeema yasa ta kasa magana Naseer kuwa b'acin Rai ma Bai Bari ya iya magana ba sabida karfin halin mahaifiyarsa da kanwarsa shi kam badan Kar yayi sabo ba dayace Allah ya dau Ransa da Wanan abinda mahaifiyarsa ke Masa

"Karya kike Yi Naeema wanan ba gidanki bane gidan Naseer ne Kun hada Baki da Naseer ne Dan kuce min ba gidansa bane Dan Kar mu zauna toh karyarki ta Sha karya wlh sai mun zauna dan bake Kika haifamin shi ba da zai tare a gindin keda yaranki gida Wasa ne da Zaki iya siya ki bude katon shago ga injinan markade har biyu yanzu Naseer Dan Kar mu zauna a gidanka shine zaku hada Baki kucemin gidan Naeema ne toh ko uwar gidan Naeema ne wlh sai mun zauna Dan itama ai da kudinka tayi arzkin.

Hajara tace tana k'ok'arin komawa ta zauna a gefen Safiyya da ta Dade da farfadowa tsoron Naseer yasa ta kasa bud'e idonta


Tana Jin duk abinda suke cewa


Ni kuwa Ina ganin ta zauna na kalli Naseer nace "Kasan wlh Tallahi bazan yarda su zauna min a gida ba Naseer kasan yanda zakayi dasu.

Idan dai har Dan kaima na barka ka zauna ne suka biyoka suna takamar kana gidana ne a zaune wlh sai dai kayi hakuri ka bisu Abunda na dauka a Baya wlh Tallahi bazan dauka yanzu ba"

"Umma wlh Nan ba gidana bane Nima albarkacin yarana nake ci shiyasa ta barni na zauna Kun siyarmin da gida hakan Bai Isa ba sai Kun biyoni Inda zaa taimakamin

"Nima albarkacin jikokina zanci ta hakura ta barni na zauna Dan na Gaya maka ba Inda zanje kaji na rantse maka"

Umma tace tana Kara gyara Zamanta

Ni kuwa mik'ewa nayi da zumar shiga daki Naga Naseer ya rigani Shiga d'akin Rai a b'ace ya fara tusa kayansa a cikin bakkonsa ban ce Masa komai ba ya gama had'awa ya fito daga d'akin ya kalli Hajara Yana "idan ma Ni kuka biyo toh na barwa Naeema gidanta sai kusan Inda dare ya muku bazaku kasheni da Raina ba"


Daga Haka ya fice daga gidan Ransa a b'ace yarana na San suyi magana na daka musu uban tsawa Suka koma ciki da Sauri.

Na Kara rufo kofata na kalli Umma da ta bi k'ofar gidan da kallo tana mamakin tafiyar da Naseer yayi ya barta

Ni kuwa Isihu na kwallawa Kira ya shigo da Sauri

Na nuna Masa bacconsu Umma Ina "Fitarmin da kayan Nan can waje Zan Shiga daki idan sun tafi ka rufemin k'ofata Dan wlh bazasu zauna min a gida ba"

Safiyya da Umma mik'ewa sukayi da ganinsu da zasu samu wuta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login