Showing 147001 words to 150000 words out of 180103 words
tana min kuwa nagane.
A Haka muka Dan Kara tab'a Hira ta tafi
Washegari kuwa da sassafe na shirya abinci a kula.
Na dibi danyen abincinmu na dauko xannuwa na guda biyu duk da Nima banida suturra na hada da sabulu na nufi gidan matar kamar yanda aka kwantan tamin
Dana Isa gidan inata Sallama baa amsa ba hakane yasa na Shiga d'akin Dana gani a bud'e
A kwance na tarar da ita tayi Kashi ma a jikinta ga kafarta a kumbure kamar rashin kudi yasa Bata iya Kai kanta asibiti
Sosai naji tsigar jikina ya tashi
Na ajiye kayayakin hannuna na Isa wajenta Ina "Sannu mama"
Da Ido ta ringa Bina ban ce Mata komai ba na dagata na fita Waje tausayinta na balain rufeni dak'yar na samo ruwa na wanke Mata Jiknta batare da naji kyankyaminta ba na duba tsumokaran Kayanta Naga duk ta batasu da Kashi da fitsari
Hakane yasa na dauko zanina Dana Zo dasu na daura Mata daya sosai naji kamar itace matar da nake ganin Mahaifiyata na taimakawa akwai dalilin dayasa nake mafarki da mahaifiyata kila matar Nan ke bukatar taimako.
Yanda take kallona hawaye na zuraro Mata yasa na dauko Kular abincin Dana Zo dashi
Sai dai Ina Isa wajenta jiki na rawa ta fusge abinci rashin k'arfi yasa ta kasa bud'ewa Ni kuwa hawayen tausayinta ya zubomin na bud'e Mata jiki na rawa kuwa ta hau ci da Sauri da Sauri tuna Nima halin Dana tsinci kaina a ciki kwanakin baya na azabar yunwa yasa na hau kuka
Sai data ci na Bata ruwa.
Ta sha ta fashe da kuka tana "Baiwar Allah daga Ina ya akayi kikasan Ina bukatar taimako yanda Kika ciyar Dani Kika shayar dani rabbi ya faranta Miki ya biya miki bukatunki na alheri nafi sati rabona da abinci
Bana iya tashi idan Kashi ya matseni ko fitsari sai dai nayi daga kwance sabida ciwon kafa banida kowa sai Allah banida d'a banida jika bansan dadin haihuwa ba ballantana na samu Mai taimakamin
Ngd yarinya Allah ya faranta Miki"
Ameen mama Nima banida uwa banida uba dafatan Zaki zama mahaifyata
Kalmar Nan ne yasakata kuka ta hau shimin albarka Nima dadin kalmar albarkar da take sakamin ya sakani kuka
Tuni na tattaro zannuwanta data Bata na wanke Mata su na gyara daki dayan
Ina kallo ta daga hannunta tana Godewa Allah daga adduoin da take nasan macece Mai ILimi da baiwa sai dai jarrabata da Allah ya mata hakane kuwa yasa na Sha alwashin faranta Mata har tsawon rayuwtaa
Sai uku na koma gida Naseer Bai tambayeni Ina naje ba
Nadeeya na Gama girkin dare na Kara zubawa a kula na saka hijabina na cewa Minal tazo mujr taga gidan
A takaice tunda ga ranar na dauke Mata cin safe Rana dare
Nakanje wajenta muyi hira sosai nake jinta Kamar mahaifyata
Ko ban samu zuwa ba nakan sa yarana suje gidanta su Dan Mata gyare gyare su dawo.kuma.wani ikon Allah ban Kara mafarki da mahaifiyata ba
Sabon da nayi da Inna Amina yasa na fara sakin jiki da ita Ina Bata labarin kaina har na Zahira da halin da take ciki
Sosai hankalinta ya tashi tace na kawo Mata Zahira ta gani
Washegari da yamma na goya zahira mukaje
Sosai ta kad'u da ganin zahiran
Tacemin zata taimakamin insha Allahu akan Zahira Allah ya Bata wnan ilimin ita da margayi mijinta
Ko.kadan maganarta Bata shigeni ba lura da macece ita Kuma.manyan mallamai sun Yi iya k'ok'arinsu Basu iya warkar da Zahira ba
Abubuwa ta lissafamun akan na siyo Mata har da su ruwan zam zam Jan miski ganyen magarya
Wasu Abubuwan dai na manta su na dai siyo Mata ne kawai ba Dan na yarda ba
A Haka tace na ringa kawo Mata zahiran tana Mata Addu'oi.
Banki tata ba Dan bansan baiwar da Allah ya Mata ba na Kuma ga tabbas tana da ilimin
Dakaina nayiwa zahira alwala itama da alwala a jikinta sai ta sa na samo kasko ta zuba wani turare data hada
A.farkon ranar da tayiwa Zahira turaren
A ranar Naga tashin hankali Dan sosai Zahira ta ringa ihu tana murya kala.kala tana rantsuwar kashe Inna Amina yarika sai datayi yafi kala ashirin yanda take k'ok'awa da Inna Amina sabida tana watsa Mata ruwan zam zam data kwana tana addua akai yasa.na baxama na Nemo maza
Suka ririketa Amma a banza Haka ta watsar dasu
Sosai muryarta ya dawo na maza na tsorota danaga yanda Inna Amina ta bada himma wajen turaren.
A takaice sai gashi Aljannun da aka turawa Zahira suna magana wajen su bakwai a jikinta maza da mace daya Kuma arnaye yanda Inna Amina ke konasu da ayoyin Allah ta daure manyan yatsunta guda biyu yasa Suka hau cewa zasu fita Kar ta konasu aikosu akayi
Take Inna Amina tace waye ya aikosu sukace Shugabansu ne ya aikosu tace waye suka Kira sunansa
Inna Amina kuwa ta cigaba da gana musu azaba suna zuba yarika
Haka muka kwashi kwana bakwai Inna Amina na fama da Zahira ko bacci bama Yi Dan gidanta muka koma gabadaya tunda muke zuwa wajen masu rukkiya ban taba ganin wanda ya haukata Zahira Haka ba sai Inna Amina
A kwana na takwas zahira ta hau amaye amaye har da gashi Haka ta ringa amayo shi
Inna Amina kuwa ta cigaba da zabga turare data hada sai gashi zahira na muryoyi kala kala Akan zata fita a yau su koma wajen wayanda Suka turo su
Inna Amina dak'yar ta tsagaita tace sunyi alkawarin fita suka ce ee tace ta Ina zasu fita suka ce ta Baki a take kuwa Naga Zahira ta hau atishawa ba kakautawa.
Can ta saki Kara Naga idonta nata fitowa waje daya saka hankalinmu tashi gabadaya Inna Amina kuwa tayi saurin cewa karka fita ta idonta Zan Kona ka sai dai ina aikin Gama ya Gama sai da daya ya fita ta idon Zahiran da har yau idan ka Kura Mata Ido zaka ga idonta daya ya Dan fi daya girma
Kamar a mafarki Zahira ta zube a kasa.
Hallitar jikinta ya hau canjawa idonta na komawa ciki Jikinta na cikowa
*Alhamdulillah sadaka maganin Masifa wlh Tallahi akwai sirri a sadaka da ba kowa ne zai Gane ba ba sai kin Zama Mai kudi zaki iya sadaka ba akwai mabukata kana cikin matsala tsanananta da Addu'a da sadaka duk biye biyen da sukayi a sanadin farantawa baiwar Allah Nan Rai sun samu maganin matsalarmu Allah yasa mudace*
*Comment*
Wlh exactly irin abinda ya faru dani nikuma kishiyar mamanah ce tafara ne akan mamanah Allah bai bata sa,a ba sai tadawo kaina saboda mamanah tafiji dani duk cikin diyanta shine tayi amfani dani don ta kuntatawa mamanah wlh yadda idon zahira suke da bantsoro haka nau suke inka kalleni so daya baka marmarin kasake kallona wlh har kuka akeyimin ina sati kwance babu babusha kuma da anje dani asibi duk bincikenda za,ayi sai ace lpy ta lau banida matsalar komai duk inda mukaje bidar magani aikin banza munyi na asibiti ba,a gane komai ba aka komo na hausa shima shiru haka za,a kiro malamai suyita yimin rukiya amma basu magana wlh wani wuri da aka kaini hadda turaren barkono akayimin amma suka ki magana na wahala na wahala nasha azaba sosai wlh haka mamana zata sakani gaba tayita yimin kuka wlh gurin da muka fara zuwa da aka gayamana kishiyar mamanah ce bamu yarda ba sai da mukaje wuri yafi uku anagayama itace kafin muyarda itace tayimin ije da bakin aljanu guda uku wai su haukatani kuma su hanani aure da kyet da taimakon Allah akasamu naji dama nadaina rashin lpy amma duk da haka wlh basu rabu dani gaba dayaba don sunki barina inyi aure inaji Ina gani aure ya gagareni munyi magani munkashi kudi har karfinmu yakare amma wlh haryanxu shiru yanxu shekarata goma kenan cikin wannan matsala wlh matsalar sihiri babbar matsala ce.
Slm.don Allah hide my ID wallahi wannan labarin yatuno min danawa rayuwan haka ya faru dani nima haka uwar mijina da kanwar mijina uwa daya uba daya sukayimin ni haihuwar fari danayi wallahi yaron tun bayan suna muka dena barci dashi haka xaiyi ta kara duk wanda yake kusa dani sai ya tausayimin dagaa karshe ma hannu da kafanshi aka canzama halitta😭😭😭haka na dunga wahalan neman magani baban kuma da farko yaki yarda sai daya ya ganinma idon shi sannan ya yarda muka fara neman magani maganan danake miki har yanxu ban huta ba kuma yaron ya xama saurayi har kanwanshi datake bimishi itama haka nayi wannan faman babancina da neema shine ni uwar mijina bata kungiyar matsafa sai dai tana bin matasfa da kuma bokaye iya wahala na wahala😭😭wani shari'an sai a lahira don nikam har yanxu abin yana damuna😭😭😭wallahi na manta rabon danayi barcin 2hrs da daddare dani dayarana haka xamuyi alwala mukaima sarkin sarakuna kukanmu ngd
*Advertisement*
Hlo sister's if you dnt use this soap before try and buy one use it you will never use any other soap again except mg's herbal whitening black soap🧖🏻♀? it treat all skin prblms like
Sunburn
Acne
it fade away black spot
Clears pimples
Reduces stretch mark it treat all skin prblm even if you don't HV any skin issue you can still use the soap it nourish nd keep ur skin fresh nd smooth,it will make ur skin to glow like never before nd gives ur body a pleasant smell🤭
This soap you jst HV to try it and see for yourself is one in a million this soap is organic soap 100% natural it does not bleach it will just bring out the beauty in you
just give it a try your skin will thank you
Just chat or call 08062991549 to plc ur orders
Note you will not get this soap in the market it hvnt reach market for now you will only get it via this number
Soap price:3k
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free
Hurry nd grab urs dnt left behind😊
Mg's makeover
Chat 08062991549 to buk for ur casual or bridal makeup @affordable price
Location:kd
You can still order ur slice cake, cupcakes,meatpie,samosa nd spring rolls,shawarma@mg's bakery for ur events at affordable prices kindly chat 07067210195
08062991549
Are you guys looking for where to buy ur kitchen stuffs,abayas,shoes nd bags,laces,Ankara,fabrics mg's collections is there for you,you can chat 07068707979
08062991549
Call
07046881166
08064532391 to plc ur orders
May Allah bless you all🙏mg's lv you all fisabilillah🤭
8/19/21, 10:33 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 55*
Haka na kurawa 'yata Ido Ina ganin yanda jikinta ke b'ari tana cikowa a hankali idonta Dake warwaje na komawa ciki
Na kasa gasgata abinda nake gani har matse hannuna nayi Wai Dan na tabbatar da irin mafarkan Dana Saba yi bane nakeyi Akan Zahira ta warke ta dawo yanda take
Amma da alama Kam ba mafarki nake ba.
Kabbarar da Naseer ke tayi durk'ushe a gaban zahiran da jikinta ya bar B'ari sosai 'yata ta dawo yanda take sai dai Rama da idonta da naga ba Haka yake ba ya dai koma ciki sosai sai dai tuwon idonta dake warwaje ko iya Haka ta tsaya alhamdulillah bansan ma hawaye nake ba sai da naga Naseer ya d'ago Zahira da idonta ke rufe jikinta a mace kirjin ta sai sama da kasa yake
Tana maida numfashi wahalar data Sha.
"Naeema Kinga Zahira ta dawo daidai Zahira ta samu Lafiya Naeema ki tab'ani na tabbata ba mafarki nake ba?
Naseer yace Yana d'ago Zahira da jikinta bashida k'arfi sosai har lokacin idonta a rufe yake
Na kasa yarda da duk wuyan Nan da na Sha Ashe Mai Mana magani na kusa damu duk uban kudin da muka kashe Ashe Inna Amina ce zata Zama silar warkewar Zahira
Ban tab'a tunanin ko turen da aka mata sun bar jikinta zata maida jikinta yanda take har ta koma siffar mutane kamar yanda take da kirijinta ya ciko.gashinta ya dawo komai nata ya dawo Inka d'auke ramar da tayi da baya rasa Nasaba da abinci da Bata iya ci amma ta dawo zahirarta Alhamdulillah.
wajensu na karasa na durk'usa tare da ruk'o hannayen Zahira Na dag'ata tare da fashewa da
Kuka Ina Godewa Allah.
Dan na fidda rai samun saukinta gani nake kamar mafarki nake Bayan shekara daya da watani Zahira a karshe ta warke ba tare da mun kashe ko sisi ba.
A hankali ta bud'e idonta tana "Zan Sha ruwa Umma kaina ciwo yake"
Da Sauri na mik'e na fara k'ok'arin nufar randar ruwan Inna Amina Dan na d'ebo mata ruwa
Inna Amina ta dakatar Dani tare da mik'a min wani Kofi da ta cika da ruwan zam zam Mai dauke da Addu'oi tace na bata Tasha
Da sauri na karb'a na bawa zahiran ta kuwa shanye gabad'aya.
Naseer kuwa yaje ya zub'e a gaban Inna Amina ya hau Mata godiya kamar zai kwanta rabon da naga Naseer cikin farinciki Haka har na manta
Nima wajen Inna Amina na karasa na hau Mata godiya
Ina "Bazan manta ki ba a rayuwata kin share Mana hawayenmu bayan mun fida ran samun sauki Allah ya saka miki da Aljannatul firdausi insha Allahu Zan iya k'ok'arina Dan na faranta Miki kin Zama uwa a gareni"
"Nima Kin Zama Mahaifiyata daga Yau ki d'aukeni tamkar Dan cikin ki da Kika Haifa Mama mun sha wuya nemawa Zahira magani Ashe kece Zaki zama silar warkewar ta Mama ki d'aukemu tamkar 'yayanki Zahira kuma jikarki
Naseer yace Inna Amina kuwa ta fashe da.mugun kukan daya daga Mana Hankali
Hankalinmu a tashe muka hau tambayar ta abinda ya sakata kukan
Dak'yar ta tsagaita kukan da take tana "Dadi nakeji da kuka kirani da kalmar mama Ashe Haka ake Jin dadi idan an Kira da mutum wanan kalmar ba'a tab'a kirana da kalmar mama ba Dan ban tab'a haihuwa ba ballantana na San dadinta ko iya wanan matsayin kawai Kuka bani kuka kirani da Sunan mahaifiyarku Kun Gama min komai 'Ya'yana ban Rasa komai ba a lokacin kuruciyata ba sai rashin haihuwa Da Allah ya jarrabceni dashi nakan ji inama ko Mara lafiya Allah ya bani amatsayin d'a a gareni Amma nasan kila haihuwar ba alheri bane agareni Amma a yau matsayin da Kuka bani yasa naji tamkar Allah ne ya amsa min addua ta ya bani ku a daidai lokacin da nake bukatar Mai kula Dani Mai tsayawa a kaina idan na koma ga Allah Alhamdulillah ya Allah
Sosai na fashe da kukan tausayin Inna Amina wato a rayuwa kowa da irin jarrabawarsa wani gudun haihuwar yake wani kuma nema yake Ido rufe haihuwa ma arziki ce Ashe Alhamdulillah da Allah ya bani shidda da Umma take min surutun na fiye haihuwa banida bambanci da akuya
( *Ya Allah duk mai neman haihuwa ya Allah ka Bata Dan tsarkin mulkinka ya Allah ka dubi bayinka da idon rahama da ka jarrabta da rashin haihuwa ka musu wanan arzkin Dan su kadai suka San Mai sukeji a zuciyarsu da rashin haihuwa Nan idan Kuma Basu da rabon haihuwa Allah ka Basu hakuri da dangana ka sa hakurinsu ya Zama silar shigarsu Aljanna alfarmar annabi Saw*)
"Banida uwa Nima mama ki rik'eni tamkar danki ki ringa saka min albarka bansan Mahaifiyata ba sai wata Dana d'auka Mahaifiyata ce mama tunda na Santa a matsayinta na uwata take azabatar Dani
Sakin Baki nayi Ina kallon Naseer da ke magana cikin Jin zafin maganar dake cinsa a Rai ya hau bawa Inna Amina labarin daya girgiza ta tana sallati gani take Taya ma yanda take Jin da ta samu haihuwa zata iya Sadaukar da rayuwarta wajen farantawa abin da ta Haifa har tsawon rayuwar ta sabida so Amma har Allah ya Bawa mahaifiyar Naseer ta ringa azabtar dashi har dasu Zahira data kasance jikarta gaskkya badan tasan ba yanda zaayi Naseer ya kirkiri karya ba da ta karya tashi.
Naseeha ta hau yiwa Naseer akan ya nemawa Hajara Shiriya a wajen Allah Kar yayi fushi
Maganganu Inna Amina ta Mana cikin ilimi da muka Karu gabad'aya na ringa Jin tabbas na samu wacce zan ringa yiwa kallon mahaifiya Kuma sosai nake jinta a Raina tamkar Mahaifiyata.
Adduar da ta ringa Mana da Naseer na dacewa da rabon duniya da lahira yafi komai faranta mana.
A takaice sai ga Naseer ya rok'eta ta yarda ta bimu gidanmu ta koma can da Zama
Sosai naji dadin shawarar da ya yanke.
Inna Amina na zazamewa Dan gani take zata D'ora Mana nauyi mu kuwa muka dage
A takaice silar komawar Inna Amina gidanmu kenan da muke jinta tamkar mahaifiyar mu.
*Waiwaye*
Har ni Naseeru zai yiwa wanan dukan har ya Kai ga ya ciremin hakori daya Umma Kinga fa yanda ya kumburamin jikina Umma Kinga idona? Duk akan Naeema iya station da Matarsa ta kaimu muka kwana Wanan tsinaniyar Yar Sanda tayi ta dukana kamar ta Samu jaka duk Wanan Bai Isa ba sai Naseer ya had'a da dukana toh na rantse da girman Allah sai Naga karshen Naseeru wlh sai Naga bayansa Koda kuwa zai mutu sai na zamewa Naseer da Naeema balai da Masifa bazan iya lissafa sau nawa ya dakeni duk Akan Naeema ba
Ita Kuma Naeema Ni kadai nasan Mai Zan Mata wlh"
Safiyya tace da kumburarren idonta da Baki Tana duba jikinta da yayi jajur
"Naseeru fa ba'a hayyacinsa yake ba Asirce shi Naeema tayi kema kinsani ko Ni sai na dau fansar abinda ta Mana wlh sai tayi nadamar kullemu da tayi hakuri zakiyi Naseer Bai Mana komai ba Naeema dai zamu ga bayanta tunda har wuyanta yayi kaurin da zata kai kararmu ta kullemu"
"da ya Zama a hayyacinsa da Kar ya Zama a hayyacinsa ba Abunda ya shafeni wlh sai na dau fansar dukan da ya dade Yana min idan na tashi ki hanani ko ki tsinemin"
Hajara Bata ce Mata komai ba Dan tasan tana Kara magana tsaf zata zageta
Safiyya mik'ewa tayi da kumburarren idonta ta yi waje Bata zame ko'ina ba sai gidan Alhaji Saad da isarta ta zub'e a gaban matar Alhaji Saad din ta hau cewa ta taimaka Mata