Showing 156001 words to 159000 words out of 180103 words
tana saka Mana albarka Kamar yanda ta Saba wanan albarka da take sa Mana da gamawa da duniya lafiya da take mana adduarsa ba karamin faranta mana Rai yake ba
Sai da ta Gama saka Mana albarkan cikin murmushi ta kalli Naseer tana
"Babana yaushe zaka koma wajen aikin naka ne kasan zaman Haka bazai yiwu ba"
Murmushi Naseer yayi cikin Jin dadin kulawarta inama baiwar Allah nan ce mahaifiyarsa
"Mama Abunda yasa bazan koma ba nasan Indan na koma ma korata zaayi dan na kusa shekara Kinga banje ba Batare da na Kuma Gaya musu dalili ba hakane yasa nake neman aikin anan ko Allah zai saka na Dace na samu idan ma ban samu ba Zan ringa aikin ginin da nake yi abaya"
"Karka damu ka koma insha Allahu ba Abunda zai faru kana tare da Addu'a ta daukaka ma zaka samu"
"Zan koma.insha Allahu mama ngd"
"Mamana ke kuma wane sana'a zakiyi kinsan zaman haka ba dadi"?
"Nasani mama kudi nake nema wuyanta na samu kudin bazan rasa sanaar da zanyi ba"
"Allah ya dafa muku ya muku albarka ya yiwa yaranku albarka yanda Kuka taimaka min Allah ya taimake ku"
Cikin farinciki muka hau amsawa da ameen sosai adduar da take Mana ke Mana balain dadi a zuciya.
Washegari kuwa Naseer ya nemo kudi ya hada kayansa da zumar washegari zai tafi
Muna zaune gabad'aya mu da yamma muna Hira da yaranmu a can gefe Kuma Inna Amina na zaune.
Waleed nadaga Gefen Abbansa Yana Masa Magiyar ya tafi dashi Abujan gobe.
Hannayen Waleed ya ruk'o cikin so da kaunarsa sosai yake Jin kaunar Waleed a Ransa sabida hankali da tarbiyya da Naeema ta bashi ga tausayi kamar me a islamiyya da Boko shi yake zuwa na daya
Yan unguwar kuwa duk sun San Shi sabida sharan Massallaci Haka suke saka Masa albarka.
"Idan ka bini Waleed ya zakayi da makaranta kayi hakuri idan ka Gama primary sai na nema maka secondary acan sai muyi zamanmu ko"
Gyada Masa kansa yayi
Ya kalli Nadeeya dake ta fama da.booklet tana karatun pass question papers Dan shirye shiryen exams din waec suke.
Mita kawai take akan Bata iya Zane ba
Naseer na Mata dariya a hankali ya ringa tambayarsu game da karatunsu
Hankalina na wajen Zahira dake gefe tayi shiru ta kurawa waje daya Ido sosai tausayin yata ke dawainiyya dani dan badan wanan larurar bama da yanzu kila ta samu ma admission ko tayi aure Allah yasan su Umma sun cutar Dani said dai Allah ya saka Mana.
Yata duk ta Zama shiru shiru Dan dai Inna Amina na Dan kwantar min da hankali akan Kar na damu zata dawo daidai
Wuyanta ta gama Shan magungunan ta sosai na matsu ta dawo daidai na nemi kudi na biya Mata waec itama dan bana San kannenta su Mata nisa.
Sallamar Tijjani da matarsa da yarsu ne yasa muka d'ago
Naseer cikin farin ciki yaje ya tari Tijjani Dana ga yabi yafice a cikin hayyacinsa ya rame sosai bashi kadai ba har matarsa.
Nadeeya mik'ewa tayi da Sauri ta shige daki Bayan ta gallawa murja harara
Ni kuwa na hade Rai sosai Dan ban manta abinda tayiwa yarana ba har gobe da tabon dukan da tayiwa Zahira a jikinta,Nadeeya lokaci lokaci tana fama da ciwon ciki Mai tsanani sabida sabulun data ringa Bata a wake a gaskiya bana Jin Zan yafe Mata zalintar data yiwa yarana.
Ban amsa gaisuwar datamin tana rau rau da Ido ba illa Tijjani kawai Dana gaisar
Su Minal duk gaisheta sukayi
Zahira itama ta gaishesu cikin sanyin murya.
Kuka Murjan ta fashe dashi tana nuffar wajen Zahiran ta kamo hannayenta tana "Bayan duk abinda na Miki har inada mutunci a idonki da Zaki gaisheni bayan duk zalintarki da nayi bayan horar yunwa Dana Miki Zahira har ki iya gaisheni Dan Allah dan annabi ku yafemin keda Nadeeya wlh hakkinku ke dawainiya dani Yarana biyar Dana Haifa na shakku dasu mutuwa Suka yi sabida zalintar Dana muku na biyewa San zuciya ta Ina ganin ku ba yarana bane Dan Allah Zahira ki yafemin mmn Zahira ki yafemin Abban Zahira kaima ka yafemin wlh sharrin shaidan ne"
Kuka take sosai cikin sheshek'ar tana bamu labarin yanda yaranta suka koma ga Allah take Kuma naji zuciyata tayi laushi tausayinta ya rufeni Zahira yata Yar albarka take tace Mata ta yafe Tijjani godiya suka hau mata Nima nace na yafe Dan Alhamdulillah tun a gidan Duniya Allah ke hisabi Murja a gidan Duniya Allah ya hukuntata
Duk yanda mukayi da Nadeeya ta fito kin fitowa tayi Murja kuwa ta bita har d'akin
Ta.kuwa shige bandaki ta rufo k'ofar tana "wlh bazan tab'a yafe Miki ba kin cutar damu batare da mun.miki komai ba kin bani sabulu a cikin wake kin Mana horar yunwa har yau Ina fama da ciwon ciki sabida sabulun da Kika bani naci wlh bazan yafe ba"
Ta karashe tana kuka."
A Haka Suka Mana Sallama Suka tafi batare da Nadeeya ta fito balle tace ta yafe ba sai Naseer ne ya kwantar musu da hankali akan Kar su damu zata yafe a hankali
A waje Naseer da Tijjani Suka kebb'e Suka bawa juna labari halin da duk suka tsinci kansu a ciki
Sosai Tijjani ya tsorata da hajara har Safiyya yacewa Naseer ya zama Dole ya Kara nisantar su Dan shi yanzu kaduna zasu koma zai nemi aiki a can ko zasu Dace
Sai da suka tafi Naseer ya dawo yayi ta yiwa Nadeeya fadan Abunda tayi sai Inna Amina ce ta saka Baki bayan tayiwa Nadeeya naseeha kafin ta iya cewa ta yafe.
Washegari da sassafe Naseer ya tafi cikin Ikon Allah kuwa Basu koreshi ba suka Karbeshi.
Bayan tafiyarsa da wata biyu na fara lura da canji a wajen Yata Zahira na farko Bata San tayi sallah sanan abu kad'an sai ta hau yiwa kannenta masifa tana neman dukansu idan kuwa nayi magana sai ta dakamin tsawa
Ba iya Zahira ba har Waleed na fara lura da canji a halayensa.......
*Wlh Nagaji alhamdulillah duk sakon danake ya isa a gane an dauka a novel dinan yanzu maganar da nake labarin Naga ta kaina bashida karshe gaskiya Dan Haka a iya Inda aka bani labari anan Zan tsaya baifi saura 3 to 4 pages ba page 60 Zan tsaya idan Allah ya bani iko*
*Comment*
Dn Allah ki boyeni shiyasa n biyoki PC Namiki Nawa bayani koni antabamun wani Abu d yasa arayuwa nakara gasgata kada ka tsananta soyayya HK km kada ka tsananta kiyayya nima antabamin wani asiri saukarmin d jini saedae shekara cif Ina zubar d mini tsawon shekara dinnan baitaba tsaya dai dai d second daya ba cinyoyina hr sillewa sukayi sukayi baki km indai zan tsaya d namiji Wanda b muharramina ba zuban jinin zai karu ainun aka km aka hanani nutsuwa dmin kuwa zuciya ta kmar ana huramun Wuta kullum saena dingajin kawae na gudu n bar Gidan km al'amarin ubangiji hk aka dauke hankalin mahaifiyata akaina kwata a filli bata damuwa d halin d nk cikin saedae itama tayi ta rama alamun wani Abu n damunta arai gashi idn dare Yy bazantaba iya bacci ba hk zanyi taji motsi km nidin n kasance irin Yara masu kiba dinnan ne ainun amma duk saedae n kare n rame tas ta ynd idn akacemiki n nayi wannan kibar zaki karyata saeda na shekara cur Allah y budi Bakin mahaifiyata t fadama mahaifi na washegari d nj agaisheshi hankalinsa y tashi ainun toh akwae abokin babana a office babana Yy masa zancen t sanadinsa akasamamun magani mai maganin yace duk me wankekken ido toh zaifadamusu hayaki ne yake FIta ajikina dmin ansone n haukace sbd mahaifiyata tana sona acikin yaranta toh idn an watsar d rayuwata baxata taba samun nutsuwa ba saukin abun shine ni bana wasa d addu'a km lkcn ma ba Waya amma idn zan kanta xansa cassette a radio inajin karatu hr nayi bacci toh wannan abun shiya takaita guduwa ne n bar Gida amma agari mutane hr sunfara kirana mahaukaciya SBD ni daya HK zakiganni INA t Fada kokm INA tafiya INA surutu some some hauka😭😭😭 kai jama'a duniya INA zaki samu aranda n fara magani wani ikon Allah aranar n fara bacci koma saenakejin wani Abu me nauyi yn sauka kaina dafarko km Neman magani hr wani mutumin Ghana saeda y ban amma dif masu magani yn uwan mamana hr suka gaji d nema mun magani tunda lkcn mamana hnklin ta Baya kaina Masha wahala ainun.
8/19/21, 10:33 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 57*
Ina yiwa Zahira uzurin kila Aljannu da suka Shiga jikinnta suka fita ke haddasa Mata saurin fushi da kunci da take yi kwana biyu
Hakane yasa na cigaba da lallab'a ta
Yau da safe Bayan yarana sun gama shirin makaranta sai na ga Waleed a madadin ya saka uniform d'insa bayan ya ga ma cin abincinsa sai Naga ya koma d'aki ya kwanta.
Nadeeya da Minal Basu iya jiransu Humaira ba suka tafi dan ba makarantar su daya ba.
Humaira da Raheema da Waleed ke makaranta daya yanzu haka Waleed da Raheema ne kawai a matakin primary.
D'akin na Shiga cikin mamaki uniform din da bai saka ba ya shige daki ya kwanta gasu humaira sun shirya alamar shi suke jira
"Kai Waleed ya baka saka uniform dinka ba kazo ka kwanta"?
"Ba zanje makarantar ba yau"
"Dalili baka da lafiya me"?
Nace cikin mamaki ma yanda yamin magana Yana wani fusgewa
"Lafiyata Lau banyi niyyar zuwa bane kawai"
"Kana da hankali kuwa makarantar dama sai anyi niyya ake zuwa yau Mai ya Shiga kanka ne ka tashi maza ka saka uniform dinka kafin ranka ya b'aci"
Na karashe cikiin b'acin rai Ina mamakin abinda ya canza Waleed ya dawo haka yarone Mai ladabi da biyayya hasali ma yana riga yayyensa shirya wa idan zasu tafi makaranta duk ranar da kuwa ya min laifi raina ya b'aci haka zai ta bani hakuri yana bazai sake ba har sai yaga na saki fuskata yake kyalleni
Ga mamakina Waleed din ke min magana Kamar da sa'arsa yake magana
a madadin ya tashi yabi umarni na ya hada da bani hakuri ma kamar yanda ya Saba sai Kara gyara kwanciyarsa yayi.
Inda naji raina ya balain b'aci banida saurin duka Amma abinda yamin yasa na isa wajensa tare da janyo wayar heater na tsulla Masa ya mik'e da sauri Rai a had'e ya rik'e wayar Yana wani hucci Kamar zai kawo min duka
"Nifa bazan je makaranta ba gaskiya Kar a takura min"
Kamar ya buga min guduma.haka naji rawar da jikina keyi yasa ya sakar min wayar yayi waje batare da na iya Kara tab'uka komai ba.
"Umma mu fa Waleed na Bata mana lokaci yau bazai je bane mu tafi"?
Munga ya fita batare da ya saka uniform ba
Dak'yar na iya magana Ina
"Kuje kawai Ina ga yau bashida lafiya"
Da sauri suka fita ni kuwa na koma na zauna Ina mamakin canjawar da Dana yayi tunda na haifeshi bai taba min haka ba na kasa yarda ma a hayyacinsa yake.
Ko dai shima Aljannu ne suka shiga jikinsa bansani ba
Mik'ewa nayi Rai ba dadi na nufi wajen Inna Amina da ban samu Shiga ba tun safe dan dama sai na gama sallamar Yara sun tafi makaranta nake Shiga wajenta da abinci karyawarta
Su Nadeeya na iya k'ok'arinsu wajen kulawa da ita dan ko band'aki zata Shiga su suke taimaka Mata ta Shiga tayi uzurinta tunda kafarta na ciwo.
Har wanka ma wani zubin su suke mata sai dai idan basa nan.nayi Mata
Ban ma yi Sallama ba sabida tashin hankali da nake ciki tana zaune ta jingina da bango tana jan carbi da har a bacci ma bakinta motsi yake tana sallati da istigifari
A gabanta na zauna na sunkuyar da kai.
Ina Jin ta idda sallatin da take na dago na hau gaisheta
Bata amsa ba damuwa bayyane a fuskarta tace "Mamana lafiya kuwa ya naganki haka Mai ke damunki"?
ina jinta a raina sabida yanda take damuwa da damuwata ko Yaya nake cikin damuwa tana ganewa
Sai dana share hawayen daya zubo min nace "Mama Waleed a yan kwanakin nan naga ya canja min Kamar ba Waleed Mai sanyi hali da ladabi da biyayya ba
Mama kema shaida ce a dan zaman da kikayi nasan zaki fuskanci halinsa yarone Mai gudun fushina
Mama wai yau ni yaron nan yake yiwa rashin kunya har Yana Kar in takura masa bazai je makaranta ba iya wanan bai Isa ba sai daya galla min harara Mama Kamar ba Waleed Dina ba ya canza gabad'aya"
Na karashe Ina fashewa da kuka
Mama cikin damuwa ta hau kwantar min da hankali tana "karki damu mama na kila ya fara haduwa da mugayen abokanai ne ko Kuma wani abu ke damunsa bamu sani ba ki share hawayenki ki bar damuwa idan ya shigo Zan Masa magana ai bai tab'a Miki haka ba ki bari mu bincike shi a hankali muji mai ke damunsa"
"Mama ko shima Aljannun ne Suka shige shi wlh ba haka Waleed yake ba Zahira ma mama Kinga tunda Suka bar jikinta bata koma yanda take ba itama yanzu wani irin hali ta koya kina cemin mu bita a hankali,mama Ina tsoron wani abu aka yiwa yarana
ba abinda umma da Safiyya baza su iya aikata min ba bare idan sunga alamar anyi nassarar cire Aljannun daga jikin Zahira"
"Karki damu Mamana ita Zahira dama sai a hankali zata dawo daidai indai na samu tana Shan ruwan adduoi da nake baki da turaren wuta zata dawo daidai
Shi dai babana nake so ki bari mu bincika abinda ke damunsa wlh duk abinda Kika ga ya samu bawa rubutacce ne daga Allah wayanda kike tunani basu Isa su Miki komai ba sai idan Allah ya hukunta dama hakan sai ya faru tunda mumuni dole ya yarda da kaddara Mai kyau ko akasin haka alhamdulillah daga labarinki Allah na kaunarki mamana tunda duk Kika iya tsallake duk wani sharri da aka nufeki dashi Allah daya jarrabceki yana ta kareki ba hanyar da basu bi ba dan su ga bayan ki Amma da ikon Allah gaki nan a rayye ba abinda ya Sameki insha Allahu yaranki ma Allah zai karesu burina kawai ki dogara da Allah kiyi ta yiwa yaranki addua gabadaya.
Da nasihar Inna Amina naji sausauci a zuciyata na fito na Kai Mana abin karyawa Muka karya a tare duk da zuciyata cike take fal da damuwa.
Ko Ina Waleed din yayi yanzu Zahira dama tun safe bata tashi daga bacci ba Ina mamakin sababin halayyen da nake gani a tare da ita bansan na saka damuwa a raina hakane yasa muna gama karyawa da Inna Amina na d'auko qurani na dan ta karamin sosai nake Kara amfani da damar da na samu wajen Kara neman ilimi Kuma alhamdulillah Ina fahimta.
Karatun da mu kayi tare ya sanyaya min zuciya sosai wajen Sha daya na fito daga d'akinta ita Kuma tace min zata dan kwanta tayi bacci tunda bata fiye baccin ba ta Kan rayya daren itama.
Ina fitowa naci Karo da Zahira ta fito da Kofin kunu da alala ko kallona ba tayi ba ta fara k'ok'arin wuceni
Haka kawai na kasa yarda wai Zahira ta ce ta dawo haka Koda lokacin da Aljannun Suka fice a jikinta magana ne kawai naga Bata yi ta zama shiru shiru,amma tana nan da sanyi halinta da ladabi da biyyaya na kasa gane Mai yasa kwanankin nan ta kara bijiro da sababin halayye da na kasa ganewa
"Zahira baki iya gaisuwa bane wai Mai yake damunki ne"?
Ciki ciki ta gaisheni ta shige daki ba Kuma tsayawa tayi ta gaisheni ba Sam ban yarda abinda suke shigeta suka fita ke saka ta haka ba dan da suka fita ma ta dawo min yanda take magana ne kawai bai dameta ba
Kaina dana ji ya fara min ciwo yasa ban tsaya takura kaina da tunani ba na hau aikace aikacen gida da kafin ta Kara canjawa tana Tayani
Hankalina Sam baya jikina Yana wajen Waleed daya fice bai dawo ba dan baya yawo daga gida sai makaranta abokinsa guda ne dan yadikko Abubakar a iya sanina ma dashi sai dai abubakar din ya zo wajensa bai fiye zuwa ba har tsokanar sa su Nadeeya keyi akan ko dan ball dinan da aka San maza nayi shi baya yi Yana nanike dasu Yana koyan jajjage da yanka albasa.
A haka na gama girkin Rana.
Ina zuba idon dawowar yarana har da Waleed da hankalina yafi karkata wajensa.
Sai dai har Suka dawo suka ci abinci Waleed bai dawo ba.
Sai tambaya ta suke Ina yaje nace musu bansani ba su dai dubo min gidan yaddiko ko Yana can wajen Abubakar.
Dawowar Humaira aguje tana hakki tare da cewa "Umma Kinga Waleed can a tsakiyarsu shagari Yana ta Wasa da Kare nace kina kiransa ko kulani baiyi ba Umma shagari fa dan gidan dan kwaya"
Tunda ta ambaci shagari yaron daya addabi Yan unguwar da fitina naji gabana ya yanke ya fadi sallati na hau yi
Nadeeya ta mik'e da sauri tana "Humaira kina da hankali kuwa Waleed din Kika gani da shagari"?
" wlh Aunty Nadeeya Waleed na gani har na Masa magana ya shareni"
"Nadeeya bata iya magana ba daga ita sai doguwar rigarta tayi waje da Sauri"
Nima tsintar kaina nayi da binta a bayan Ina sallati
Shagari sa'an Waleed ne karamin yaro da bazan iya kirga sau nawa aka Kai shi a ka kulle ba sabida rigimamme ne na tashin hankali har d'auke d'auke Yana yi ga dukan Yara fitinanne ne na karshe shaye shaye ne kawai bamu sani ba Yana Yi ko baya Yi
A zaune yake a tsakiyar su shagarin Yana ta Wasa da karnukan
Nadeeya a tsawace ta Kira sunansa tana yazo nan
Waleed yarone Mai girmama na gaba dashi dan daidai da Raheema da yake bi aunty Sama aunty kasa yake ce mata ga mamakina ko dagowa baiyi ba ya kalli Nadeeya
Data ishe shi ma sai cewa yayi "mallama karki takura min idan Kuma Zaki iya daukana zo ki d'aukeni"
Nadeeya sakin baki tayi tana kallonsa ta juyo ta kalleni......
*A yi maneji wlh abubuwa sun Sha kaina a ringa hakuri dai Kar