Showing 168001 words to 171000 words out of 180103 words
Waleed na gaishe shi wani zubin ya amsa wani zubin yyi kamar bai ji ba
Inna Amina ke ta kwantar min da hankali tana hanani yiwa Naseer magana akan Kar na damu komai zai warware tunda har Allah yasa sun fara dawowa hayyacinsu ko Kuma muce sun ma dawo tunda yanzu duk sun daina Abunda sukeyi Waleed abinda kawai bai bari ba shine saurin zuciya da fushi.
Itama Zahira hakane Amma ta dawomin zahirata yanda take a da.
Burina Zahira da waleed su koma makaranta Dan an barsu a baya sosai hakane yasa nayiwa Naseer magana take ya Nemo makaranta ya biyawa Zahira waec shi Kuma Waleed da k'arfi nasa ya nema Masa makaranta ya fara daga jjs 2 duk da ya girma da jss 2 din Amma haka ya fara zuwa dan a haka ma mun masa tsallake.
Sai a yanzu na samu kwanciyar hankali nake Kuma Godewa Allah da Kara neman kariyarsa a garemu gabaki daya
Naseer yanzu kanannan sana'oin daya koya dashi yake rik'e damu duk da Nima Ina taimaka masa sosai dan ban saki sanaar da nake ba na siyar da kananan Abubuwa a gida.
Zahira na dab da gama zana waec dinta tamkar yanda take da farin jinin samari awancan lokacin haka samari Suka hau layi a k'ofar gidanmu Wanda hakan ya sakani farinciki sosai dan inata addua Allah yasa Kar Nadeeya ta rigata aure tunda itace babba data samu Mai kaunarta Zan cewa Naseer mu aurar da ita.
A Rana sama da mutane biyar na sallama suna neman Zahira
Hakane yasa na zaunar da ita na gaya Mata a cikin masu kaunarta ta zabi wanda hankalinta ya kwanta dashi dan muna so tana gama jarrabawa idan Allah ya nufa tayi auren
Ta cigaba da karatu a gidan mijinta sai dai budar bakinta sai cemin take ita so take ta cigaba da karatu tamkar yanda Nadeeya ta cigaba da karatun dan ita burinta tayi karatu Mai zurfi ta Zama lawyer dak'yar na shawo kanta ta amince zata tsayar da mutum daya
Take kuwa ta tsayar da wani kabiru da Saurayine Mai Kuma kudi dan wlh duk Samarin Zahira ba karamin mutum.
Tana gama jarrabawa ya turo magabatansa da kudin neman aurenta.
Manyansa suka Kara da basa San a saka dogon lokaci kabiru yace zai dau nauyin komai ba sai mun wahalar da kanmu ba.
Naseer kafewa yayi akan su bashi Nan da wata shidda zai Mata komai shi Baya so ayiwa Zahira gori.
Sai dai dangin kabirun da roko da magiya da kyar suka shawo kansa ya amince aka saka wata daya da sati daya.
Fadar halin farinciki Dana tsinci kaina a ciki bata Baki ne kudi na hau tarawa Inna Amina Tama fi kowa farinciki na kasa yarda zahirata da aka so watsawa rayuwa ce ta samu nagartacen miji har baifi sauran sati uku Aurenta ba.
Dukanmu shiri muke har Naseer saura sati daya auren Zahira da kabiru aka kawo lefenta akwati shidda cike da kaya masu tsada a wancan lokacin.
Nadeeya da Minal iyayen doki ba Wanda Basu Kira ganin lefen Zahira ba.
Gefe daya Kuma dagani har Naseer da Inna Amina addua muka dukufa dashi ba dare ba Rana.
Ana saura kwana uku daurin Auren Zahira kabiru ya aiko yan uwansa akan a bamu hakuri ya fasa auren Zahira hmmmmmm....
Advertisement
Treat/repair your skin with mg's skincare today,are you battling with pimples,
Black spot
cream reaction
eczema,acne, sunburn,spot, stretch mark, discoloration/skin damage, stretch mark ❌then mg's skincare is the plug for you,mg's skincare gat solution to all ur skin prblms😍everyone deserves a blended skin🌿 when it comes to skin issue😢gv it to mg's skincare 💯🔥 now is the time to take care of ur skin,this product is the real deal 🙌clears white patches✅dark patches✅dark feet's/knuckles ✅reduces the appearance of greenveins,it clears pimples,spot and make ur skin fresh nd glow like never before just gv it a try nd ur skin will definitely thank you💋✅evn if you don't HV anything mg's skincare gat you a soap that will maintain ur skin nd make the skin to glow🥰
Soap price:3k
Chat 08062991549 to plc ur orders
Call:08064532391
We deliver Nationwide buh delivery is not free🙏
we can't wait to be a part of your beauty story🤭
8/22/21, 9:25 AM - Alhmdllh: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
Page 62
Suman zaune nayi bakina yamin nauyi ballantana na tambayesu dalilin daya sa kabiru yace ya fasa auren tunda Suka Fadi abinda ya kawosu naji kamar an sokeni da kibiya a kirji har yau da nake labarin nan Ina fama da Wanan ciwon kirjin idan abu ya girgiza ni.
Muryar Zahira naji da bansan lokacin da ta fito da ga daki ba sai ganinta nayi a tsakiyarmu
Kwalla cike da idonta ta zub'e a gaban wacce take yayar kabirun da itace Kan gaba wajen Shirin bikin kanin nata ba ma a garin Kano take aure ba daga Abuja tazo.
"Aunty Mai nayi Masa yace ya fasa aurena"?
Aunty yau saura kwana uku aurenmu ba Wanda Bai San zamuyi aure ba Mai nayi Masa da sai a yanzu zai janye"?
"Wlh bansani ba Zahira jiya ya sako mu a gaba akan muzo mu baki hakuri akan ya fasa auren ba yanda ba muyi dashi ba ya gaya Mana dalili yak'i da yaga mun dage Masa ma sai ce Mana yayi idan muka matsa Masa Zai kashe kansa Akan Dole yasa muma muka zo yanda Kika ga Kuna ta Shiri wlh muma haka muke shiri ba Wanda bai zo ba duk gidan mu baki ga yanda muke kaunarki ba amma kabiru lokaci daya yace mu zo mu baki hakuri ga wasika nan ya bani na Baki"
Yayar kabirun ta karashe kamar zatayi kuka tare da mik'awa Zahira da hawaye ya jika gaban bak'ar doguwar rigar da ke jikinta hannunta ya Sha Jan kunshi da baki gashinta har baya ya sauko dan Kamar yanda naji su Nadeeya na shiri a yau zasu yi kamu a gidan wani Alhaji dake kallon gidanmu yanzu haka ma su Nadeeya na can suna ta shirya wajen.
Zahira ba ta iya karbar wasikar ba illa mik'ewa da tayi ko taku biyu ba tayi ba ta zub'e a kasa.
Nayi kanta aguje a daidai lokacin da Waleed ya shigo hannunsa d'auke da kayan rabon da zasuyi a kamu.
Zubar da kayan hannunsa yayi yayo wajenmu agujen ya Tayani tallafar zahira dan Nima jikina rawa yake d'aukar ta yayi cak yayi daki da ita.
Ni Kuma na cewa yayar kabiru "Ba komai Allah yasa Hakan shiya fi alheri kila da ma Zahira ba matarsa bace shiyasa ya janye"
Hakuri Suka cigaba da bani nace musu ba komai suyi min hakuri Nasir ya dawo na Masa maganar kudin auren da kabiru ya kawo a mayar musu da lefen da suka kawo dan dama Allah cikin ikonsa ban Bari ta tab'a komai ba ganin kabiru ya rage Mana nauyi sosai yasa nida Naseer muka Mata dinkuna daidai karfinmu.
Mik'ewa suka yi da Sauri suna "wlh yace ya yafe mata komai ba sai mun karbo komai ba kuyi hakuri dan Allah"
Nima da Sauri na girgiza musu Kai Ina "ba za'ayi haka ba idan har zai fasa Aurenta banga dalilin da zai saka ya bar mata lefensa har da kudi ba.
Nayi dakina da Sauri Ina kwallawa Raheema da Humaira Kira da nake Jin shewarsu a d'akin Inna Amina da alama Basu San me ke faruwa ba kunshi ma ake musu a d'akin.
Da Sauri suka fito daga d'akin hannun humaira d'auke da kunshi
Dangin kabirun suka gaisar suka yo d'akin nawa.
Danne zuciyata nake Ina mayar da kukan da ke neman cin karfina ya fito da k'arfi.
Indai na nuna rauni na a gaban yarana su ya zasuyi kenan ya zama Dole nayi k'ok'arin danne zuciyata.
Umarni na bawa su Humaira da su kai min akwatunan waje yanzu nan kar su b'ata min lokaci.
Dan jikina rawa kawai yake ballantana na iya d'aukar wani akwati.
Had'a Baki sukayi wajen cemin "Umma lafiya kuwa Mai yake faruwa ne"?
Tsawa na daka musu a daidai lokacin da kuka ya kwace min Ina "Ku fitarmin da akwatin nan nace ku daina min tambayoyi sunce sun fasa aurenta"?
Kamar wayanda na watsawa ruwan zafi haka suka ja da baya suna dafe kirjinsu
Ni Kuma na zauna a gefen gadon na rufe fuskata Ina cigaba da kukan da na kasa dannewa.
Ni kadai nasan mai nake ji a kirjina
Waje sukayi gabad'aya Basu dau akwatin kamar yanda na umarce su ba sai ji nayi cikin muryar kuka suna tambayar danginsu kabiru mai Aunty Zahira ta yiwa kabiru da zai fasa Aurenta
Raheema har da cewa "Ku rufa Mana asiri karku Mana haka yau fa zaayi kamu ba Wanda bamu gayyata ba Mai aunty Zahira ta Masa da zafi haka da saura kwana uku aurensu zai ce ya fasa idan laifi tayi muku dan Allah kuyi hakuri"
Ta karashe tana fashewa da kuka dayake akwatin irin Mai taya dinan ne a zuciye na mike na hau Jan babban nayi waje.
Ina zuwa na Kara daka musu tsawa Ina su je su debbo min sauran akwatin Ana dole ne.
Humaira aguje tayi d'akin nawa Raheema kuwa ta cigaba da magiya bakin ciiki yasa nayi kanta a fusace wata dattijuwa a cikinsu ta tareni da Sauri tana "Kiyi hakuri mmn Zahira wlh baa San ranmu haka ya kasance ba yarone ka haifeshi baka Haifi halinsa ba wlh nasan da ciwo Abunda yaron Nan yayi Amma ba yanda zamuyi dashi"
Da sauri na katse ta Ina "kabiru da ma ba mijinta bane shiyasa Allah baiyi zasuyi auren ba halin da yarinya kawai zata Shiga ganin Aurenta saura kwana uku an fasa ni shine damuwa na Allah yasa hakan shi yafi alheri Allah ya musanya Mata da Wanda yafi kabirun ga akwatunan ku nan kudin auren na wajen baban Zahira idan ya dawo ya turo a karba Masa"
Kuka Humaira da Raheema kawai suke Waleed da ke tsaye a bakin kofar d'akinsu zahira da duk Abunda muke Yana kallonmu sai hucci yake.
Suna kokarin Kara magana ya daka musu uban tsawan daya sa suka gigice dattijuwan tayi hanyar waje da Sauri
"Dan ya fasa Aurenta sai me ku gaggauta kwasar kayanku.ku bar Mana gidanan kafin na muku watsi da kayan waje Banda kaddara Mai aunty Zahira zata yi da wannan Mai zubin tsofaffin"
Tsawa na ringa dakawa Waleed akan yamin shiru Amma ko kallona baiyi ba
Abinda har gobe ke hadani dashi kenan tunda aka tab'a shi zuciya da taurin Kai ne dashi wani zubin baka isa ka Hana shi ya hanu ba ko wani Abun yayi idan babansa zai dakeshi baya guduwa haka zai tsaya a ga ma jibgarsa har sai dai idan Naseer din ne ya gaji dan kansa.
Inna Amina ce ma tace ya bar Masa irin wanan dukan sabida Kamar hakan na Kara taurara Masa zuciya mu cigaba da binsa da Addu'a
A karshe Waleed da kansa ya rakasu waje da akwatunan su
Suka hau ja da sauri dan ba karamin tsorata su Waleed yayi ba.
Suna fita na zub'e a Palo na cigaba da rusa kuka takarda da ya bayar a bawa Zahira na hannuna
Tunani iri iri haka suka cikemin zuciya Ina tunanin Mai dalilin fasa auren Zahira da kabiru yayi
Raheema da Humaira d'akin Inna Amina suka Shiga suka gaya mata Ina jinta tana ta zuba sallati.
Waleed Kuma ya zauna Akan kujera Yana hucci Yana girgiza kafa.
Mik'ewa nayi na nufi d'akinsu zahiran dan Naga halin da take ciki
Akwance na tarar da ita ta juya bayanta tana kallon bango daga gani kasan kuka take kasa kasa
Daga gefen ta na zauna banyi Mata magana ba na warware takarda da aka saka a envelope dan na ga mai kabiru ya rubuto a cikin takardar
*KIYI HAKURI BAZAN IYA AURENKI BA ZAHIRA DAN BURINA NAGA NA AURI MACE TA GARI NAJI LABARAI AKANKI KALA KALA A CIKI HAR DA WAI KIN ZUBAR DA CIKIN SHEGE BAN YARDA BA SAI DANA JE GIDAN KAWAR TAKI TA TABBATAR MIN DA HAKA ASHE BA KARAMIN RASHIN JI KIKAYI BA INA SANKI AMMA A HAKA ZAN HAKURA DAKE NA BAR MIKI KOMAI ALLAH YA KAWO MIKI WANI MIJIN AUREN*
ban Iya karasa karantawa ba na runtse idona kirjina na min nauyi Abunda nake ta tsoro kenan sai gashi kabiru yaji labarin rashin jin da zahira tayi da ba halinta bane juyar min da Kan ya akayi ko da tayi rashin jinta Alhamdulillah Allah ya karemin ita da Karfin Addu'a baa rabata da budurcinta ba sai dai wayanda tayi muamallan dasu ne idan za'a kwana Ana rantsuwa ba halin Zahira bane ba lailai a yarda ba dan kawayenta duk ba mutanen arziki ni nasan zasu iya komai suma dan su rama abinda Zahira ta musu dan da ta dawo hayyacinta da kanta ta musu rashin mutunci tace su daina zuwa nemanta tana kuka tazo ta sameni tana wlh bata San ya akayi tayi kawance dasu ba ita da take da kunya Mai ya had'ata dasu.
Murmushi kawai nayi dan ni nasan da ma ba halin Zahira bane sai gashi duk da mun bar unguwar suna nufarta da sharrin ta zubar da cikin shege Ina mamakin halin wasu mutanen da Basu da burin daya wuce su bika da sharri
dak'yar na taushi zuciyata na rik'e hannun Zahira na hau rarrashinta Ina Mata nasiha.
Nasan itama kawaici kawai take min tana nuna min ba komai.
Shigowar Nadeeya da Minal ya Kara hargitsa gidan suna koke kamar gidan rasuwa sai dana musu da gaske suka Shiga hankalinsu Nadeeya ta hau jawa kabiru Allah ya Isa har da cewa zata je gidansu.
Inna Amina ta taimaka sosai wajen kwantarwa da Zahira hankali ta hade har da kannenta ta musu naseeha.
Wajen karfe Takwas Naseer ya dawo niki niki da kayan abincin biki har da dinkin Daurin auren da zai saka inaga farinciki da yake ciki bai bari ya karanci yanda mukayi cirko cirko ba dan duk mun kasa walwalar har gwara ni Ina dan dauriya sabida yarana Amma kannen Zahira da suka ci buri Kamar an musu rasuwa haka su kayi cirko cirko.
Daga yanda suka gaishe shi yasa ya fara lura da halin da muke ciki.
Sai a lokacin ya kalleni ya tambayeni Mai ke faruwa ya Kara da Ina Zahira take
Dan har Waleed Yana zaune a palon Zahira ce kawai a daki
Ban bashi amsar tambayarsa ba dan bansan ya zan Masa bayani ba illa takardar hannuna kawai Dana Mika Masa.
Kafin ya bud'e Naga ya kallemu duka Yana "Wai Mai hakane ba zaku gaya min mai ke faruwa ba"
Ya bud'e takarda hannunsa ya hau karantawa
Sallati kawai yake ni kuwa na kalli su Nadeeya take Suka mik'e suka hau barin palon sukayi dakinsu Waleed ya mike yayi d'akin Inna Amina.
Yanda muryarsa ke rawa yasa hawaye ya hau zubomin Ina "Dalilin da yasa wai ya fasa aurenta kenan abinda nake ta gudu kenan Naseer duk da dukanmu munsan Zahira baa hayyacinta duk tayi wanan rashin Jin ba Amma ba Mai yarda ba halinta bane kila wanan ya zame mana bakin fenti kenan tsorona Kar ba iya ita kadai ba abin yazo ya shafi su Nadeeya
An cutarmin da Yara Naseer wlh an cutarmin dasu bazan tab'a yafewa ba yanzu idan har masu neman auren Zahira zasu ringa Jin irin wadanan maganganun dak'yar Zahira ta samu Mai Aurenta"
Na karashe Ina fashewa da kuka
Naseer bai iya magana ba har lokacin illa sallati da yake yi idonsa ya kad'a yayi jajjur
Bai hanani kukan ba illa mik'ewa da yayi Naga ya nufi d'akinsu Zahira da shigarsa su Nadeeya suka Kara fitowa Suka barshi da zahiran da zazzabi ya rufeta
Nasiha ya Mata ya rarrasheta da kabiru ba mijinta bane shiyasa bai Aureta ba
Insha Allahu zata samu Wanda yafi kabirun.
Sai daya bata magani da kansa ya fito daga d'akin ya shige dakinsa tare da rufo kofarsa nima ban bi takansa ba na Kara duba jikin Zahira na koma dakina dan nima zazzabin naji Yana neman rufeni.
A haka cikin kunya muka hada karyar an daga bikin Zahira sabida Wanda zai Aureta bashida lafiya
Nadeeya ma karyar mutuwa ta ringa lankayawa kabirun.
Ba Abunda baya wucewa
a haka fasa auren Zahira ya wuce kamar baayi ba.
Ana samun kamar wata biyu Zahira ta sameni a daki tana min zancen San cigaba da makaranta dan Nadeeya har ta kusa diplomarta dan itama Wanda ke santa so yake tana gamawa ya turo mune muke dan ki da tuni ya turo,na karanci saurayin Nadeeya yana balain santa abu daya ke sanyaya min jiki wani zubin sai naga kamar laifin Zahira zai shafesu Amma Ina adduar Allah yasa Kar a Kai ga haka a Kuma burina Zahira nakeso ta fara aure kafin Nadeeya sabida zanji wani iri ace Zahira na zaune Nadeeya ta rigata aure sosai na dage da Addu'a akan Zahira har da yarana gabadaya ban saki jiki akan kila su Umma sun kyallemu ba hakane yasa daga ni har Naseer muke addua duk abinda ma zasu yi Allah ya maida kansu ko ya kawo Mana da sauki.
Hankali na maida wajen neman kudi dan idan result din Zahira ya fito mu nema Mata admission itama ta cigaba da makarantar Nadeeya Saurayinta ne ya tsaya Mata wajen cigaba da makaranta ba dan Haka ba dak'yar in zamu iya sanin Nadeeya ta tsayar mana dashi akan shi zata aura hakane yasa bamu hana shi hidimanta Mata ba dan koda Naseer ya hana shi dagewa yayi.
Lokacin da result din din Zahira ya fito bai yi kyau ba daga ni har Zahira bamuji dadi ba ganin damuwar da Zahira tayi yasa na boye nawa damuwar na kwantar Mata a hankali na Dade da karantar kamar taba Zahira da akayi yasa ta rage k'ok'ari bata Kai sauran kanenn nata kokari ba ko ni nakan ci gyaranta wani zubin.
Rashin cin jarrabawar ta ne yasa bata samu admission ba Naseer yaje ya biya Mata wajen da ake koyan dinki da zaman da zatayi haka zuwa wani shekarar mu Kara biya Mata waec din
Daga fara fita koyan dinki Samari Suka Kara yiwa Zahira caa abin har tsoro ya ringa bani da farko zahira rashin mutunci ta ringa musu dan na lura tun abinda kabiru ya mata take ganin kamar duk mazan haka suke dak'yar nida Naseer muka shawo