Showing 174001 words to 177000 words out of 180103 words

Chapter 59 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2493

duk Wanda yazo ma ta daina bashi fuska ballantana ta saurareshi


Aikin koyan dinkinta kawai ta saka agaba da Kuma shirye shiryen bikin Nadeeya da duk ba wani dokinsa muke muna wani shiri ba dan gani nake ba iya Zahira aka yiwa mugunta ba kila har dasu Nadeeya.

Banida k'arfi banida kowa Amma inada Allah duk abinda sukeyi min Allah Yana kallonsu nasan zai kawo karshen komai wuyanta nayi hakuri.

Tashe tashen hankulan dana gani a rayuwata yasa yanzu na Riga da na fara sabo da duk wani jarrabta da Zan gani a ruyuwata ba abinda ya Kai lafiya dadi a wajena.

Idan dai har bazasu cutarmin da Yara ta hanyar tab'a min lafiyarsu ba zasu barmu a haka inaga alhamdulillah banga abinda zai daga min hankali ba tunda na Riga da nasan Aure da mutuwa lokaci ne idan har lokacin auren Zahira yayi ni nasan ko mai zasuyi basu Isa su hana ba duk masu zuwa neman aurenta ba mijinta a cikinsu.

Ban saka damuwar komai a Raina ba na Kara fawallawa Allah komai na cigaba da kai kukana gareshi.

Naseer Zan iya cewa shi ya saka damuwa a Ransa sosai yanda hawan jininsa ke motsa Masa akai akai sabida damuwa yasa nida inna Amina muka Masa nasiha

Dak'yar shima ya cire damuwa ya cigaba da gayawa Allah

Alhamdulillah yarana sanin muna da masu San ganin bayanmu yasa Suma Basu Zauna haka ba Suka dukufa yiwa kansu addua kariya duk a cikin yarana Nadeeya da Humaira Zan iya cewa suna da Wanan k'ok'arin sosai wajen raba dare suna kaiwa Allah kukansu balle Nadeeya data ga Aurenta na matsowa sosai take adduar Allah yasa Kar wani Abu ya Hana auren dan Naga itama jikinta a sanyaye yake.


Yanda muka amshi kaddarar mu da hannu biyu yasa komai ya zo Mana cikin sauki cikin rufin asiri muka cigaba da shirye shiryen auren Nadeeya

Dan Abubuwan da muka siyawa Zahira muka yanke Kara Mata akai dan Umar Mai neman Nadeeya na Dan sakar mata kudi dashi muke samu mu rage wasu Abubuwan


Bana Jin dadin yanda Zahira ke kin saurararen manemnta da duk da fasa Aurenta da ake tururuwar zuwa nemanta suke
Kuma so suke mata ba na Wasa ba sai dai da mun Mata maganar ta kulasu sai tace mana ko ta kulasu ma a karshe guduwa zasuyi bata ga amfanin kula sun ba ita fa kila bata da rabon auren ne a duniya dan haka ta hakura.

Sai dai a mane manta akwai wani Abubakar da babansa ya kasance babban mallami shima yayi gadon mallinta a wajensa ga ilimi ga kudi.


Ba karamin naci yake yiwa Zahira dake wulakanta shi ba dan ko kad'an bata saurarenshi ballantana har ya Shiga zuciyarta ta sa rai da aurensa a karshe Kuma yazo ya fasa auren

Har tausayi yake bamu yanda yake.sintirin zuwa wajenta tana kin bashi fuska

Duk Kuma maganar da zamu Mata akan ta kulashi bazata kulashi ba idan an matsa mata kuwa sai ta saka kuka.

A karshe sai Inna Amina ce ta samu dak'yar dak'yar ta fara kula Abubakar duk da ta Masa gargadin duk ranar da ya mata zancen aure sai sun rabu.


A haka ya cigaba da zuwa sanin da aure yake Santa yasa daya tabbatar ta tafi wajen koyan dinki yazo ya tarar da Naseer a gida ya Gaya masa bukatarsa na san auren Zahira.

Naseer bai b'oye Masa komai ba ya bashi labarin duk Abubuwan dake faruwa game da zahiran da yanda aka zo neman aurenta sai ana dab da yi a fasa.

Abubakar murmushi yayi Yana Kar Naseer ya damu daga bashi labarin da yayi yasan da akwai aikin makiya a fasa auren zahiran Amma indai sihiri ne ko wani Abu da yardar Allah bazai yi tasiri akansa ba sai dai idan Allah ya rubuta Dama zahiran ba matarsa bace

Shi dai a bashi dama ya turo manyansa dan aka biyewa Zahira cire rai zata yi daga auren sabida duk abinda ya faru da ita a baya


Badan duk mun yarda wani Abu bazai biyo baya ba aka bawa Abubakar dama ya turo manyansa.

Da.kudin aure Inda ya nemi a hada dana Nadeeya Amma ayi a sirrince Kar a nuna Dana Zahira zaayi sabida kar ma makiyan mu suji labari.

Addua mukayi akan Allah ya tabbatar muka cigaba da Addu'a muna Shirin auren Zahira da Nadeeya Dan Ni har cewa Naseer nayi dama kawai a daura auren zahiran da Abubakar Kar a wani ja lokaci dan gani nake lokacin da ake ja ma yasa suna samun Galaba akanmu

Amma Naseer yace Kar na damu mubi komai a hankali.

Allah yasan da Auren Zahira da Abubakar zai tabbata da nafi kowa Jin dadi da gani zanyi na gama samun cikar burina.


Ana saura sati uku bikinsu aka kawo leffen Nadeeya.

Abubakar kuwa mu muka hana ya kawo na zahira sabida yanzu hankalin ta a kwance yake gani take Umar wahalar da kansa kawai yake aure tsakaninsu bazai yiwu ba duk da a ranta tana San sa Amma haka zata hakura dashi yanzu tana sanin da ita zaa hada auren zata tashi hankalinta.

Sosai ta zage suke shirye shiryen auren Nadeeya ta d'au ragamar komai Kamar wata kawarta Ni Kuma yanda ta daukaki auren Nadeeya tausayi take bani.

Har azumi.na tsiri yi akan Allah ya cikamin burina Naga auren Zahira.

Ana saura kwana goma Sha biyu bikin Nadeeya da Zahira

Daddare karfe daya da rabi Kamar yanda na Saba tashi na rayya Daren na mike na Shiga band'aki na daura alwala

Naseer Ina jiyo karatunsu daga d'akinsa dan Yanzu bamu fiye kwana waje daya dashi ba sai dai idan ta kama ko Dan idon yaranmu da muke ganin sun kawo girma da Kuma wayonsu.

Na fito kenan daga bandaki jiri ya d'ebbeni duhu ya mamaye min Ido ban Kara sanin Inda kaina yake ba.


Sai dana yi.kwana uku bansan Inda nake ba kafin na iya bud'e idona nagani a gadon asibiti na Sha Karin ruwa.

Azabar da nakeji a jikina da kaina danaji Kamar guduma ake bugamin yasa na runtse idona na hau girgiza Kai Ina sallati

Wlh duk yanda Zan kwatanta abinda nakeji a jikina makaranci da ke da kike rubutawan bazaku gane ba

Azabar Dana Sha a cikin Minal da kumburin da nayi duk nafila ne akan abinda nake ji

Ina Jin yarana da suka zagayeni har da Naseer suna min sannu

Inna Amina itama Ina Jin tana min tofi

Ban iya bud'e idona ba sabida dai azabar da nake Sha

Kirjina kamar an doramin Abu Mai balain nauyi.

Tunda ga lokacin ban Kara iya bud'e idona ba Amma duk abinda ake Ina ji.

Azabar da nakeji kawai a jikina yasa na fara kuka Ina rokon Allah ya dau raina dan a ganina gwara mutuwa da Wanan azabar da nake Sha

Ina Jin yanda yarana da Naseer ke jigilar yawo dani a asibiti daga wanan asibitin zuwa wancan sai kashe kudi suke.

Amma duk a banza likitocin sun kasa gano Mai ke damuna.

Karshe sai wani private aka kaini da suka rubuta ayimin scan din duk jikina agano Mai ke damuna

Daruruwa kudin da suka caza yasa dolen Naseer ya siyar da gidan da iyayen Khalid suka mallaka Mana ya tashi Yan hayan daya zuba a gidanmu Suka koma.

Duk kudin gidan a asibiti ya Kare a sanadin rashin lafiyar da nake aka daga bikin Nadeeya da Zahira

Naseer shima gadone kawai ba a bashi ba sabida tashin hankali

Duk ba Wanda ya kawo ciwon nawa bana asibiti bane duk Inda aka ji kwararrun likitoci sai a tura mu can

A haka nayi wata biyu a wahalce kafin saurayin Zahira ya bawa Naseer shawara akan a mayar dani gida cutar tawa bata asibiti bace.

Sai a lokacin Inna Amina da Naseer da Kamar aka mantar dasu muna da makiya suka dawo hankalinsu aka mayar dani gida.

Aka dukafa da min addua Naseer Inna Amina har da sirikina Abubakar da shima bazan tab'a manta shi da mahaifinsa ba

Mahaifinsa Mallam isah ba karamin ilimi ne dashi ba.

Abubakar na samunsa da zancen rashin lafiya ta yace a kawoni.

Haka aka daukeni akayi gidansu Abubakar dani.

Cikin Ikon Allah kwana bakwai da kaini na fara dawowa hayyacina har na bude idona nasan Inda nake.

Kwana mahaifin Abubakar keyi Yana min addua

A gidan Naseer da Waleed suke kwana

Da asusuba yarana zasu dura gidan gabadaya.

Cikin sati biyu na warke sumul kamar bani ba dan nakan iya tashi na zauna duk azabar nan danake ji a jikina na daina ji sai dai rashin kwarin jiki.

A haka mahaifin Abubakar ya bamu ruwan adduoi a ranar da zamu bar gidan

Ya zaunar da Naseer Dani yayi gyaran murya yana "Rashin lafiyar Nan turensa aka mata a gaskiya Kuna da makiya da suka shirya ganin bayanku Mata biyune suke ta k'ok'arin ganin sun tarwatsa rayuwarku adduar da nayi Naga kamar matan nada kusanci da kai duk auren yarku da ake sawa Ana fasawa duk sune yanzu Haka ma Allah ya nuna min duk wani shiri da suka Kara yi akanku nayi addua ya warware da ikon Allah Ina Baku shawara ku Kara dagewa da Addu'a yarku zahira sun balain tsanarta zasu iya komai dan suga bayanta dan haka insha Allahu Zan taimaka Mata.

Mallam Naseer idan bazaka damu ba inaso a daura auren Zahira Yarka da Dana Abubakar a yau.

Dagani har Naseer kasa magana muka yi duk maganar sa ba abinda ya bamu mamaki mun Riga da mun San su Umma ke San ganin bayanmu

Maganar auren Zahira daya ce a daura a yau shi ya daskarar damu har naji na fara Jin kwarin jikina.

Ban.yarda ba mafarki nake ba sai dana.ga Naseer ya shigo d'akin da aka ajiyeni da goro da alewar daurin Auren Zahira da sadakinta a hannu Dubu hamsin

Hawayen farinciki ne.ya hau zubomin.

Ashe dai yata tana da rabon aure daurin Auren Zahira tamkar Kara samun lafiya yayi

Godiya sosai muka ringa yiwa mahaifin Abubakar bakin Abubakar a washe dan murna.

A haka muka nufi gida cikin farinciki tun a hanya na fara sadaka a Raina Ina Godewa Allah.

Umarnin mahaifin Abubakar nabi Dana Isa gida na fito da duka kayana daya ce Kar na sake sawa Kar Kuma na bawa wani dan zai iya cutar dashi.

Dan kayan nawa ma an yi asiiri a ciki.

Naseer da kansa ya Kona kayana.

Yarana sai.murna suke na warke.

Bamu fadawa Zahira an daura Aurenta ba.

Sati biyu da samun sauki na aka cigaba da shirye shiryen auren Nadeeya Abubakar har akwatin kayan sawa ya kawo min


Ranar 15 ga watan biyar shekara ta 2010 aka daurawa Nadeeya aure

Aka hada da bikin Zahira da itama bata sani ba sai a satin auren Nadeeya kukan farinciki kawai ta ringayi tana a Ashe tana da rabon aure.

Cikin rufin asiri akayi shagalin bikin yarana suka tare a gidajen mazajensu alhamdulillah


Calabar

A ranar da mahaifin Abubakar ya karya asirin da Hajara tayi daddare Hajara na kwance tana bacci.

Taji kamar Abu ya ruguzo Mata a jiki

Azabar data ji.yasa ta bud'e idonta.

Kasusuwan jikinta Suka ringa kaskas Kamar Ana karyawa


A firgice ta mik'e zaune data ga kashin jikinta na murdawa shi kadai kafin ta ankara sai gashi ta karkace gabad'ayanta gabanta ya koma gefe idan kana kallonta a madadin a tsaye straight sai ta karkace Fuskarta ta koma gefe

Ihu ta saka da iya karfinta mahaukatan dake zagaye da ita Suka sakata gaba suna kallonta

Masu wucewa Kuma idan Suka ganta sai su tsorata dan Basu tab'a ganin mutumin daya karkace haka ba.

Wanan shine farin Shigar Hajara wahala Mai tsanani Dan mutane tsoron ta Suka koma yi ko tayi baran bata samu.

(Har yanzu wlh Tallahi baiwar Allah Nan a karkace take a fadar Naeema ko accident mutum yayi Bata Jin zaiyi karkacewar da tayi
Allah ya tsare Mana imaninmu na dai kusa gamawa Dan Safiyya da Hajara na rayye Basu mutu ba ba kuma su tuba ba yanda Naeema ta bani labari haka Zan Baku sai dai Kuma idan wani Abu ya biyo baya nayi alkwarin rubutawa insha Allahu)


*TALLA*
_Mai talla shike da riba_

*Mg's herbal whitening black soap*

Idan akaji gangami to tabbas akwai labari. Ina Amare, Uwargida kai har ma da 'Yan mata masu tasowa, hakika mata da kwalliya aka sanmu, shin kuna so ku kara kyau fatarku tayi luwai luwai ki zama 'yan caras kamar madubi?

To ga dama ta samu, mun zo muku da Sabulun Mg's a kan farashi mai sauki, duk wacce ba tayi anfani da sabulun nan ba an barta a baya, domin duk masu korafin cewar sabulan gyaran jiki basa Aiki to ina so ku cire Mg's a ciki domin shi kankat ne wajen mai da tsohuwa yarinya. Ko yaushe Mg's sai sambarka dan haka ku hanzarta ku samu naku, siyan na gari maida kudi gida, Mg's sabulu ne daya tamkar da dubu.

Masu bukatar fatarku tayi haske to Sabulun Mg's herbal whitening black soap ya waratar daku, jikin ku zai yi kyau da sheki da kamshi. Kayanmu baya bleaching organic ne, zai fiddo muku da ainahin natural beauty dinki ne, dan haka duk wanda ya gwada shi ne zai bada labari. Amare da sauran Mata kuyi kokari ku mallaki Mg's domin ba ruwanku da zuwa a dirje muku jiki zaku ga yanda fatarku zata dinga walwali. Ina masu.

Pimples
Tabo(spot)
Sunburn
Nankanwa
Dama duk wani matsalar fata kuyi kokari ku nemi soap din Mg's, insha Allah before 2weeks zai share muku hawaye, ku zama abun kwatance.

You have to try it and see for yourself 100% tested and trusted.

Soap price: 3k
Location: Kaduna
Muna turawa ko ina, amma delivery is not free

Mai so kindly WhatsApp message to 08062991549 or
Call 08064532391

_Note: Yan sauran state Babu in da zaku sami mg's herbal whitening black soap sai a number din nan, now Akwaisu available_yan kd akwai shops da zakusami sabulu ynx kuyi mgn 08062991549 abaku address
Masusan suzama distributors a other state uw kindly drop a message via 08062991549🤭

we can't wait to be a part of your beauty story😍
8/27/21, 9:02 PM - Alhmdllh: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*


Page 64

Duk masifar da ta Shiga da b'acin rai bata taba tsintar kanta a farinciki kamar lokacin da Oban ya haska Mata rashin lafiya da Naeema ke fama dashi ba

A karyar Oban ce mata yayi shi yayi aiki akan Naeeema tayi ta rashin lafiyar har ta mutu.

Kamar wacce aka yiwa kyautar hajji da umara haka Safiyya ta ringa ji.

Da kuwa Naseer ya siyar da gidansa akan rashin lafiya Kamar ta taka rawa Bata da burin daya wuce har daya gidan su siyar su koma ba suda gidan kansu kamar yanda itama bata da gidan.

Idonta na Kan komai dake wakana dasu Naeema har irin wahalar da ake sha akanta.

Abubakar data ga Yana San Zahira Yana Kuma taimaka.musu yasa ta roki Oban akan ayi ta tsorata shi idan har yak'i janyewa Oban ya kashe shi

Haka kuwa akayi Oban ya hau tura Aljannu dan su tsorata Abubakar sai dai duk tsorata shi da suke ko gezau Abubakar baya yi daya tashi ma Kona Aljannun ya ringa yi yayi wa Oban barna sosai ta hanyar lalata Masa wasu kayan aikin nasa da Karfin Addu'a.
Duk yanda Suka so yin aiki akansa hakan baiyi tasiri ba har aka daura auren Zahira da Abubakar da yasa Safiyya tayi karamin hauka tana sumbatun tsinewa Naeema da ita rayuwar yaranta gashi a watse Amma Zahira tayi aure.

Dan Safiyya itama ta santalo Mata jika shegiya ga budurwar Bashir itama d'auke da ciki.

Duk an cike mata gida da shegun yaya

Gabadaya rayuwarta ta wulakance ta lalace ita da yaranta

Amma gashi zahira ta samu tayi aure kenan ma Naeema taci riba akanta

A hauakacen ta sa Oban ya Mata aiki akan Umar saurayin Nadeeya akan ya fasa auren Nadeeya sai dai tana ji tana gani aka daura aurensu.

Bakin ciki yasa ta roki Oban akan a kashe mata Umar dan da alamu Abubakar yafi karfinsu dan duk abinda suka ringa tura Masa baya tasiri akansa Nan kuwa basu San mahaifinsa ba karamin aiki yayi akansa ba ba iya shi ba har su Naeema.

Ba yanda ba suyi dan suga sun tab'a Zahira ko Nadeeya Amma Allah bai basu iko ba

Hakane yasa Safiyya ta so maida Nadeeya bazawara a washegarin da Nadeeya ta tare a gidan ta.

Wani Abu Oban ya bata Akan taje ta binne a tsakiyar titi kafin ta binne ta Kira sunan Umar sau uku

Indai Umar a ranar ya hau mota ya hau kan kwalta sai yayi mumunan hatsari.

Cikin mugunta ta binne kamar yanda ya umarceta

Ta koma gida tana murna bakin cikin da Naeema zatayi har Naseer idan suka ga kwana daya da tariyar Nadeeya mijinta ya rasu

Tana komawa gida ta iske Bashir a tsakar gida a zaune ya balain nutsuwa kamar bashi ba.

Sannu da zuwan da ya mata yasa ta daskare waje daya tana murza idonta dan ta gaskata Bashir danta dai take gani ba wani ba

Murmushi ya Mata Yana ta daina mamaki shine sati biyu da yayi baya nan Allah ya shiryeshi ya Kuma Gane duk abinda yakeyi ba daidai bane daga Yau ya daina.

Safiyya tsabar farinciki kuka ta saka tana shiwa Bashir albarka

Fadar farinciki da take ciki ma Bata bakine Ashe Bashir dinta zai tab'a nutsuwa haka har ya dawo hayyacinsa

A takaice hirane ya barke tsakanin Safiyya da bashir

Safiyya ta ringa ji kamar ta goyashi dan farinciki tuni ta hau tsare tsare a Zuciyarta.

Murna da take ciki yasa tace Masa Bari ta Shiga daki ta yo musu cafene

Bashir kafewa yayi ta bar kudin shi zai yo Mata cefanen.

Safiyya da kallo ta bishi har ya bar gidan Kaunar Bashir na balain mamaye Mata zuciya kaf yaranta ba Wanda takeji a ranta kamar Bashir.


Fitarsa da minti goma taji hayaniya a waje.

Kafin ta gane Mai ke faruwa har mutane sun duru cikin gidanta suna zabga sallati
Hankalinta a balain tashe ta fara tambayar me ke faruwa

Sai dai baa iya bata amsa ba in Banda wani daya hau Jan hannunta.

Kamar sokuwa haka tabi bayansa gabanta na fad'uwa.

Mutanen da suka cika titin da ta binne abinda Oban ya bata yasa gabanta tsananta fad'uwa dak'yar ta suka bata hanya

Bashir ne kwance cikin jini male male

Idonsa a bud'e Yana kallon sama kana ganinsa kasan rai yayi halinsa.


Wani razanannnen ihu ta kwalla ta zub'e a kasa.

Bata Kara sanin Inda kanta yake ba har aka yiwa bashir sutura aka binne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login