Showing 177001 words to 180000 words out of 180103 words
shi
Ranar sadakar uku ta farfado Ta na ihun Kiran sunan Bashir ta fara k'ok'arin yin waje
Sai sumbatu take tana ba Bashir tace ya mutu ba mijin Nadeeya tace Oban ya kashe Mata.
Tab'in hankali da ta dan samu yasa ta hau tona wa kanta asiri tana Naeema ta cuceta Oban ya cuceta.
Dak'yar aka Mata alluran bacci dan fusgewa take zata fita waje.
A takaice sanadin dan samun tab'in hankali Safiyya kenan
Dan har gobe bata cika hankali ba ita kadai haka za tayi ta zuba surutu tana fadar Abubuwan da tayi idan haukan ya motsa mata .
Oban da take shuka tsiyar dashi data koma wajensa a kwance ta sameshi ya kumbura yayi himmm Yana zabga wani irin doyi
Ita kanta Safiyya baka Isa tsayawa kusa da ita ba sabida warin da takeyi
Wata daya da rasuwar Bashir
Tana zaune ta zubawa waje daya Ido
Hankalinta ya dan dawo jikinta yaranta duk take bi da kallo da jikokinta.
Ita bata ga ma ribar da taci a rayuwarta ba Bashir danta namiji tilo Daya fi soyuwa a gareta ya tafi ya barta a lokacin da hankali ya fara zuwar Masa ya Shiryu
Yaranta biyu daga mahaukaciya sai Mai bin maza
Ba Wanda ya amfaneta da wani Abu.
Sai Rabia da take wahalar da ita da bata da bambanci da wata dabbar tana girma tana Kara zama abin tsoro
Tunani da abubuwa dake rayya Mata munanan abubuwa yasa ta d'auko wuka
Ta nufi d'akin da Rabia ke kwance tana Isa wajenta ta daga wuk'ar da zumar soka mata dan ji tayi gwara.kawai.ta kashe Rabia ta huta
Tana daga wuk'ar taji kamar anyi cilli da ita.
Wani iirn gugguwa Mai k'arfi ya zagayeta
Ta hau wani irin jijjiga tana Kara duk Aljannu dake azabtar da Rabia Suka bar jikin Rabia suka Shiga jikin Safiyya
Wani irin canza Mata hallitar fuskata sukayi fuskarta ta dawo bakikirrin wuyanta yayi wani irin kumburewa idonta yayo waje gabad'aya
Ihu kawai take Tana birgima.
Har gobe haka Safiyya take fama da kumburarren wuya da Ido a warwaje takan dan tab'a hauka wani zubin.
Daga ita har Hajara Basu nemi yafiyar.naeema ba suna Nan Kuma da tsanar Naeema dama ne kawai Basu samu ba
Safiyya k'arfi da yaji ta koma yin Abun mahaukatan aka koreta daga gidan hayan
Hajiyayye budurwar Bashir kuwa Yana rasuwa ta kama gabanta
Asmau kuwa tana nan a haukacenta
Safiyya data haihu guduwa tayi.ta bar gidan
Rabia kuwa aljnnun suna barin jikinta ta dawo daidai.
Ita kadai ce a yaran Safiyya bayan Aljannun sun bar jikinta wani Abu Bai sameta ba sai ita ke kula da yaran Safiyya da Asmau.
Naeema
Godiya kawai nake yiwa Allah daya bamu ikon ganin auren Zahira da Nadeeya da nake Jin tunda na auri Naseer ba Abunda ya tab'a faranta min rai sama da Aurensu.
Yarana suna cikin rufin asiri a gidajen mazajensu.
Yara na Kuma dake gabana suna cigaba da zuwa makaranta ina kula da tarbiyyarsu Naseer na cigaba da sana'oin hannunsa Wanda dashi asirinmu ke rufe.
Ranar da bazan taba mantawa ba watansu Zahira hudu da aure daga amai da gudawa na kwana uku Inna Amina ta amsa Kiran Mahallici Ko lokacin Dana rasa iyayena banyi kukan da nayi da rasuwa Inna Amina ba
Ba iya ni ba har Naseer da sauran yarana Allah ya jikanta ya Kai haske kabarinta sosai na ringa ji Kamar wani barin jikina ce ta tafi ta barni.
Sanin watarana dole ko muna so ko ba ma so mu ma zamu amsa Kiran Mahallici dan mutuwa ta zama Dole akan kowa
Haka muka bi Inna Amina da Addu'a dacewa da rahamar Allah
Mu ka cigaba da fuskantar rayuwa yau da Dadi gobe akasin haka har Allah ya sauki Zahira lafiya ta haifi yarta mace Mai Kama da ita Inda Abubakar yamin Kara ya saka Mata sunana ake kiranta da iman
Iman nada wata uku a duniya Abubakar da mahaifinsa da su kaje gaisuwa garinsu rano sukayi mummunan hatsari suka mutu
A shekara 2012/10/10 wanan Rana Yana cikin ranakun da bazamu taba mantawa ba anyi Mana rasuwar da ya dakemu da har yata Zahira sai da muka dage Mata da Addu'a kafin ta iya dawowa daidai
Bazan manta Abubakar da mahaifinsa ba har gobe Muna adduar Allah ya sadasu da rahamar Allah yasa Aljanna ce makomarsu
Zahira na fita daga takaba naso ta cigaba da zuwa makaranta ta nuna min bata son komawa makaranta tafi so ta cigaba da sanaarta ta dinki har yanzu Zahira tana nan tana dinkinta
Yarana dukansu rayuwar da Allah ya tsara musu shi suke dan Nadeeya yanzu haka yaranta uku Minal itama tayi Aurenta da yaranta biyu.
Sai Humaira yanzu da aka sawa Rana
Waleed toh sai dai nace Alhamdulillah Yana Nan da taurin Kai Bai koma min kamar Waleed din Dana sani ba abinda aka masa Kan motsa Masa wani zubin ba Kuma sa shiri sosai da mahaifinsa.
Naseer ko tuna Umma da Safiyya baya so yayi.
Shekara 2016 wani makocinmu Sagiru da muka zauna a garin calabar yazo garin Kano neman Naseer da kyar da.kwatance ya gane gidanmu.
Sai da ya huta yake fadawa Naseer dalilin zuwansa akan Umma yazo shima bai fiye zama ba sabida tafiye tafiyen da yake Yi
Sai kwanaki ya dawo ya Shiga kasuwa yaji an rik'e Masa Riga da kyar dak'yar ya Gane Umma Inda Umma ta fashe Masa da kuka dan ta Gane shi tace ya taimaka Mata ta Kira mishi Naseer yunwa zai kasheta mutane gudunta suke dak'yar take samun na abinci
A labarin yake fadawa Naseer kila umma hatsari tayi sabida yanda kamaninta Suka canja dayake a can kowa yasan waccece Umma daidaiku ne basu san halinta ba naseeha sagiru ya hau yiwa Naseer Akan Bai Dace ya wulakanta Umma ba ko Mai tayi Masa kuwa yayi hakuri yanzu tana bukatar taimakonsa
Naseer amsa shi kawai yayi akan zaije kwanan sa biyu ya koma
A zuciya irin tawa da tausayi halin dana ji Umma na ciki ya sanyaya min jiki ya Kuma Sakani Jin tausayinta hakane yasa na hau yiwa Naseer maganar yaje ya ganta dan uwa tabbas ba Wasa bace
Sai dai ga mamakina Naseer b'acin Ransa ya nuna min yamin gargadi Akan Kar na Kara Masa maganarta duk halin ma da take ciki ita ta jawowa kanta.
Naso na share kamar yanda ya share din sai naji zuciyata ta ki nutsuwa yanda sagiru ya bada labarin wuyan da Umma ke Sha ya tsayamin a wuya Ni nasan hakkinmu kawai bazai bar Umma da Safiyya su zauna lafiya ba sai dai idan har mun yafe musu.
Damuwarta Dana saka a Raina yasa har mukayi zancen da Zahira Zahira ta shawarci naje idan har abbansu bazai je ba mu Rama sharrin da suka Mana da alkhairi yanzu tunda tana samun kudi nayi amfani da kudinta na yiwa Umma siyayya nace Mata tana rayye tayi aure Allah kuma ya azurta ta da iman
Ni nasan da biyu Zahira take san naje Ni nasan so take ta nuna musu ranta baa hannunsu yake ba yanda suka so kasheta Allah baiyi ba gata Nan a rayye
Nima sai naji inasan na gansu Naga ya suka dawo din
Dana tari Naseer da zancen zuwa calaba nida Zahira bai Hana mu ba
Ya Mana fatan dawowa lafiya ya Kara da duk abinda ya biyo baya Kar muyi kuka dashi.
Insha Allahu ba Abunda zai biyo baya Nima inaso suci arzkin yarana da suka so watsa rayuwarsu
Zahira cemin tayi zata bini muje can calabar da biyu Kuma naji inasan zuwa sabida na cigita Mallam Musbahu dan har na mutu bazan manta alherinsa a gareni ba.
Nadeeya har da turmin zaninta da kudi Wai mu bawa Umma muce Mata itama tana cikin rufin asiri a gidan mijinta.
Dak'yar na gane unguwar da.muka zauna dan garin ya sauya sosai anyi gine.gine unguwar ta Kara cika ba kamar da ba
Da taimakon Sagiru Muka gano Inda Umma ke zaune a rumfar mahaukata.
Ganin Umma kawai da nayi yasa na fara yiwa annabi sallati mun kad'u mun razana da yanda ta dawo dan Zahira har buya tayi abayana sabida tsoratan da tayi
Mun dauka ganinmu zai saka ta hau hawaye tana neman yafiyarmu.
Sai dai fuskar ta a karkace.
Take jifanmu da mugun kallo
Da da yanzu ba daya bane
Ina daga tsayen na gaisheta Ina karewa wajen da take kwana kallo.
Akan tsomokara take zaune rumfar sai doyi yake.
Bata ce Mana komai ba ta cigaba da shafa wani Abu a kumburarren kafarta.
Ni kuwa ledojin da muka ciko Mata da kayan abinci na ajiye mata ina gashi inji zahira akwai sakon Nadeeya a ciki da kudi.
Yarana dukansu sun hada kudi Akan mu bata.
Na dauka zata watsar da ledar ga mamakina da hannu biyu ta fusge Leda fuska a karkace take hararana Tana
"Wlh ko duk duniya Zaki bani Naeema bazan tab'a sanki ba har gobe Ina Kan bakata bana sanki bana kaunarki Dana Kuma da Kika rabani dashi Allah ya Isa tsakanina dake Kaya Kuma na karba Dan nasan bada kudinki Kika siya ba"
Mai Umma zatayi da zai bani mamaki ban ganshi ba hakane yasa kalamnta ma Basu bani mamaki ba illa tausayi ma da tabani dan nasan Umma har yanzu Bata da rabo kila shiyasa ta kasa Gane gaskiya da tana da rabo iya karkacewar Nan da tayi ya isa.yasa taji tsoron Allah"
Amma gashi a wulakance da take tana Nan da kiyayya ta a ranta
Koda Muka bar wajenta
Sai Dana siyi katifa na aika Mata dashi.
Yanda akayi nasan halin da suke ciki kenan Safiyya ban samu na sakata a idona ba Amma naji labarin irin wuyan da take Sha da haukar da take dan tab'a wa Allah ya tsare Mana imaninmu
Bazan iya cewa matsalarmu ya kau gabadaya ba ba a rasa dan jarrabta na rayuwa da bawa ke fuskanta yau fari gobe baki sai dai muyi fatan Allah ya bamu ikon cinye jarrabawarmu wanan shine labarina nakan ji labarin wahalar rayuwa da Umma da Safiyya suke sha ta wajen iyalan Sagiru duk wanan bai.isa su gane gaskiya su nemi yafiyar wayanda suka zalunta ba rayuwa tun a gidan Duniya Allah yake yin hisabi Allah yasa mu cika da kyau da Imani ameen
Naeema.
Ina godiya ga duk masoyan da suka kaunaceni daga fara rubuta labarina duk sakon masoya na isa gareni idan tana bani labari ko ta turamin sakon makaranta na kanyi murmushi yanda mutane suke so su gani har wasu na San kulla kawance dani toh daga labarina kunsan Na tsufa tunda nayi hamsin har da doriya tsakanina daku fatan alkhairi ne da shawara da Zan bada akan duk runtsi duk wuya duk wahalar da zaka Sha a rayuwa ka dogara ga Allah zai isar maka ba Abu dawwwama me da baya wucewa Kamar baayi ba wani zubin Ni kaina Ina mamakin yanda Allah ya tsallakar dani duk Abubuwa da nagani gani Nan a rayye har da jikokina ma Koda Naseer arzikinsa bai dawo ba Amma muna cikin rufin asiri Allah Alhamdulillah ayita hakuri da rayuwa dan duniya kurkukun mumuni ce Aljanna kafiri Ina muku fatan alheri gabadaya masu San su gani ko abasu lambata kuyi hakuri akwai abinda nake jira idan na samu Zan Kara yiwa Marubuciyar magana ta dan rubuta gajeran labarin da lambar tawa shima banyi alkawari ba dan Ina San Kare martabar ta data yayana Dan akwai abinda aka tab'a yiwa yarana Kuna dai kallo bamu San komai ba Amma laifin mahaifiyar Naseer da kanwarsa na iya shafar yarana har a musu kallon Ashe fa kakarsu Bata da hali ta Taba tsafi da sauransu
Da yawa badan tausayi kila suke San saninmu ba ko dan aga ya muke zaa so ganinmu ayi hakuri an gajarta labarin ne Amma halin mahaifiyar mijina yaso ya dan shafi.yarana agujesu har wasu.ma na ganin hada zuria dasu matsalar ne tunda kowa yasan labari irin wanan ba lailai ya buya ba idan an tashi bincike wasu sai sun Kara abinda ba haka ba dafatan duk zaku fahimceni Ina muku fatan alheri Marubuciyar Kuma Allah ya saka Mata da alkhairinsa idan wani Abu na karuwa ko darasi ga rayuwarmu ya Kara afkuwa da ya Kamata mutane su karu dashi Zan Kara Bata ta rubuta Dani da iyalaina muna godiya da Addu'oi da soyayarku mungode.
*HUDAH HUDAH HUDAH*
*LABARIN TA LABARI NE DA KOWA ZAI SO YA KARANTA SABIDA YANDA YA SHAFI RABIN ABUBUWAN DAKE FARUWA A ZAHIRI RABI GASKE YA FARU RABI FICTION NE AMMA SAKON DA NOVEL DIN KE DAUKE DASHI ZAI ISA GAREKU*
*Ban san iya adadin lokutan da zan dauka ina gayawa duniya da wasu ginshikokin rayuwata cewa Shi din zab'ina ne*.
*Ban san yadda aka yi har na fada siradin rayuwa haka ba, na zata dan karamin motsi da nayi zai sanya a kalle ni da sanyin idaniya*....
*A'a sai gashi tun banyi nisa ba, na fara gane da naga ta kaina! Ba tare da na gama kimtsa tafiyar da take gabana ba, na fada rana zafi inuwa kuna*
*Duniya tana bamu abubuwa da yawa masu kyau da marasa kyau, sannan duk wani majibanci yakan tsaya ka'in dana'in domin samawa wasu bigiri nashi kyakyawan makoma da tushe mai nasaba ta Alkhairi! Haba Hudah! Me aka yi jiya balle yau, mu iyayen ki ne kuma Muna fatan Alkhairi a gare ki karki juyawa kyakyawan niyyar mu fuska" inji Mahaifiyar Hudah ta faɗa cikin rarrashi da kulawa*.
*Cike da bakin ciki yake kallon ta, shekaru sha yake rike da yarinyar nan a cikin tsuma. Koda yake ba wani abu bane idan yayi dubi da juyin juya halin da aka samu ta rayuwa inda har takai wasu abubuwan suka iya sauyawa ba tare da sanin ka ba*
*Ba zan fusata ba, kuma ba zan d'aga amo na domin duniya ta Fahimci abinda nake nufi ba, amma nayi imani da Allah, na kuma yi alkawarin ba zan juya daga kudirina ba, matukar ina raye Tabbas al'amarin tabbataccen al'amari ne kuma zai faru da Yardan Allah" inji Baban Huda*
*Cikin wani irin murmushi me had'e da kuka na kalle shi na wasu lokuta, kafin na dukar da kaina ina me harde hannuna*.
*Wannan alƙawari nayi da makagina, kowacce taki da zira'i, ta rayuwata kai ne shugaba kuma kai ne jagorana, zan ajiye kalmar ka da yakinin ka, domin ya zame maka abun dubawa ga madubin gobe na, zan tattara duk wani mataki da nau'i irinta yanayi na ajiye a matsayin wannan shine kaddarata, amma kai na tsayar da kai ne a matsayin babban harsashin da zan a za duniya ta! Ka yarda Ni din daban ce kuma mai fada da idarwa wancan sauran baya gabana domin kai ne yankin rayuwata ka saka a ranka babu wanda ya isa nisan kiwo a da'irar ka" inji Hudah*
*Dandano*
*Hudah*
Tun Ina yarinya karama na taso da maitar kallon Fina finan indiya bansan Mai yasa indiyawa suke burgeni ba a yarinta irin tawa har hasaso kaina nake a cikinsu tun bana gane mai film din ke d'auke dashi har na fara mallakar hankalina Ina gane Inda film din dana kalla ya dosa na fi karkata da San na kalli film din soyayya soyayar cikin film din indiyawa na balain burgeni nakanji inama nice wani zubin idan Ina kallon soyayan.
Hakane yasa na taso da burin na gwada soyayya irin wacce nake kallo a fina finai Dana Zo na hada da karanta littattafai soyayay zalla sai Kuma na fara burin yanda Zan Gina rayuwata da Wanda nake Jin a Raina Zan kaunace shi ya kaunaceni kamar dai yanda na taso da kallon Ana Yi a indiya film da littattafai soyayyan da nake karantawa.
Ina balain San soyayya a rayuwata a ganina indai na samu Wanda ya kwanta min a raina zai ga soyayya a wajena Zan iya Sadaukar Masa da komai nawa indai Ina sanshi.
Na taso da burin San auren kyakyawa saurayi Dan a ganina shine Zan samu duk burikana su cika muyi irin soyayya da nake mafarki.
Soyayya shine kan gaba da komai a wajena a raayina indai na hadu da Wanda nake kauna nake so a zuciya ta ko rumfa ne zan iya rayuwa dashi.
"Na kasa yarda yanda lamura suka juye lokaci guda duk mafarkina da ke dab da tabbata a idona Naga Yana watsewa yana tarwatsewa shekara biyar Ina Gina soyayya ta Mai zafi tashi daya kaddara ta hadani da mutumin da duk fitar numfashina da tsanarsa yake fita.
Ban ma hasaso yanda Zan fara rayuwa da Wanda ya girmewa mahaifina ba.
Ina dai kallon fin karfin da ake San gwadamin na tilastamin Alhaji idris da ko ganinsa bana San yi.
Yayyen mahaifiya ta da suka dage da mun kwalliya kawai nake bi da kallo idan na runtsa idona sai na hango Habib da San sa ke nukurkusar zuciyata Ina hango yanda aka min adon nan wajen sa naje ya ware hannayennsa ya rungumeni a kirjinsa Ina shak'ar daddan kamshin turarensa.
A irin burina ya dagoni daga kirjinsa ya hade fuskarsa da tawa ya sumbaceni ya kaini wani duniyar da nake mafarkin idan ya kaini bazan dawo ba.
Indai Zan tuna Habib a rayuwata sai nayi murmushi Ina Kaunar bawan Allah nan.
Muryar yayar mahaifyata ne ya dawo dani tunanin Dana tafi.
"Maza Yar albarka tashi kije waje Yana jiranki wlh bazaki yi nadamar Yi Mana biyayyya ba ko dan hajji da zaa kaimu ki nuna Mana kin haifu ke Yar albarka ce a gidan Nan waye yayi goshin da kikayi iyye zamani ya canja baa auren wani soyayya yanzu wlh ke matar manya ce ba kalar wanan sirrin yaron Mai fama da takardu ba"
Mik'ewa nayi da Sauri dan a rayuwata na tsani inga an tab'a Habib data zagarmin shi gwara na fita wajen tsohon Dana tsana Mai zuciyar yara.
Wajen nayi da sauri Ina Jin zuciyata namin nauyi da balain tsanar ganin wanda ya min Karen tsaye a rayuwata yake San rabani da farinciki rayuwata.
Ina fita waje na coge a bakin kofa Ina kallon katuwar bak'ar Jeep din dake ta zuba kyalli.
Da sauri drivernsa ya fito ya bud'e Masa k'ofar motar ya zuro k'afafun sa ya fito waje Ya nufoni Yana washemin jajjjayen hakoransa
Ya kusa sabain Amma sabida budurwa zuciya kananan Kaya ya saka Kai da gani kasan dak'yar rigar ta shigeshi sabida yanda tumbinsa ya baje acikin rigar.
Jikinsa har wani rawa yake daya Iso Inda nake tsaye.
Ni kuwa isowarsa yasa na fara tunanin Taya ma Zan iya auren tsohon nan lebbensa na kalla Mai kauri tunanin har munyi auren