Showing 1 words to 3000 words out of 33918 words

Chapter 1 - Kulsum Part 3 Complete Hausa Novel By Sumayya Takori Kabara.doc

??ࡱ?>??  B????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????>?

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?FCWordDocument?????G0Table?????????Data
????????????P???? P? KSKS??G?i?????????''''??8? ?,'&??:??? ?$M??*?''uu@'''')L )? ) ??'  ?^`????^Normal d??,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJpA`????pDefault Paragraph Font,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJ?i`????? Normal Table0:V 4?4?l4?4?la?6 d??,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJ2k`????2No List d????o????0Header Char_b50fc32c-980c-4784-9af9-7ffdbee6fa27,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJj`??jheader
?H?$d??,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJ??o????0Footer Char_e6efe823-6ea5-49dd-a740-d9006ff1e3c1,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJj `??jfooter
?H?$d??,CJmH sH nH tH _HOJPJQJ^JaJ??
KULSUM




3









Littafin


SUMAYYAHABDULKADIR
takorikabara@gmail.com



SADAUKARWA
Ga dukkan matan da ke fama da lalurar 'nocturnal enuresis'(fitsarin kwance) a gidan aure.

GODIYA
Godiya ta musamman ga Nura Sada Nasimat sabida jimirinsa na bin rubutuna kafin bugawa da bada shawarwari. Allah ya raya mana zuri a rayuwa mai albarka.

JINJINA
Ga daukacin mambobin TAKORI'S ONLINE FORUM, littafin Kulsum ya jinjina muku, ni da ku hadin Allah ne. Allah ya bar mana zumunci har gidan aljannah. You are my source of inspiration.

GARGADI
Banyar da a karanta wannan littafi a kowacce kafa ta sadarwa ba ba tare da iznina ba, tun daga radio, facebook, whatsappp idan har ban yi izni ba, yin hakan karya doka ne, kuma abin tuhuma ne daga lawyer na Barrister Sadiq Rufa'I Wali.

KULSUM-3
Har tana tuntube, saura kadan ta fadi& ta samu ta rike marikin kofar ofishin ta yunkura ta fice da mugun sauri. Ba ta tsaya a ko ina ba sai a jikin motar Taufeeq. Babu inda ba ya rawa a jikin ta, ta tabbata Turaki ne ta gani ba mai kama da shi ba. Fatan ta a lokacin kawai shi ne ta hango fitowar Taufeeq su bar asibitin gabadaya, amma har aka shafe mintuna goma babu Taufeeq ba mai kama da shi.
Sai can ta hango su su biyu suna tahowa a tare, da shi da Turakin, sai waige-waige suke yi. Rasa inda za ta sa kanta ta yi, sai kawai ta daddage ta taka da gudu ta boye a bayan wasu shuke-shuke. Daga inda ta ke tana iya hango su har cikin motar Taufeeq suke dubawa, daga baya Turaki ya juya cikin tafiyar nan tasa ta  ya yan saraki ya koma cikin asibitin, Taufeeq kuma ya dauko motar sa ya tuko a hankali yana bin gefen hanya da idanunsa, tana iya hango tashin hankalin da ke shimfide baro-baro a kan fuskar sa.
Sai da ta ga ficewar sa daga get din asibitin, sannan ta fito daga bayan shuke-shuken ta zo bakin get domin ta fice ta tari taxi zuwa Victoria Island gidan Sakeenah. Tana zuwa get masu gadin suka taso suka kulle get, suka koma gefe suka fuske, suna kiraye-kirayen waya.
Wani mugun takaici ya kama Kulsum, ko kallon arziki ba su yi mata ba, amma sun kulle kofa sun hana ta ficewa. Ba'a jima ba ta ga mota kirar Acura na fitowa daga cikin asibitin zuwa inda suke. Tun daga nesa ta gane mai tukin nan cikin tsananin nutsuwa kamar bai son taka kasa. TURAKI ne.
A wannan lokacin ba gilashi a idon sa, wannan ya ba ta damar gane shi sosai. Da gane irin canjawar da ya yi. Juyawa ta yi ta karasa gaban masu gadin ta soma rokon su su bude mata kofa. Ko daga ido su kalle ta ba su yi ba, har motar Turaki ta iso ta yi parking a gaban ta kamar za ta take mata  yan yatsun kafar ta.
Zama ya yi cikin motar yana kare mata kallo. Ga wani makalallen murmushi a gefen bakin sa. Ya bude motar ya fito gaba-gadi, rataye da falmaran din bakaken suit din jikin shi a kafadun sa. Gaban ta ya zo ya tsaya suna fuskantar juna. Kallon ta kawai yake da idanun nan nasa da ke zuwa mata kullum cikin mafarki, ko a ido biyu. Yayin da ta yi kicin-kicin da fuska, za ka rantse da Allah bata taba sanin fuskar da ke tsaye gaban ta ba a tsayin rayuwar ta.
 Malam lafiya? Kulsum ta yi tambayar, muryar ta na rawa, tana mai dojewa kallon tsakiyar lumsassun idanun sa.
 Na zo fita ka sa an tare ni, na ci bashin ku ban biya ba ne?
Ba ta yi aune ba ta ji hannun ta cikin na Turaki, shidewa ta kusan yi na wucin gadi, kafin ta tantance me ke faruwa, ya ja ta tana tirjewa ya bude motar shi ya sanya ta, tare da rufe kofar da key din hannun sa. Ya zagaya ya shiga mazaunin sa ya tashi motar. Masu gadin suka wangale masa kofa ya fice, suna daga masa hannu cikin girmamawa.
Tafiya kawai yake bisa shimfidaddun titunan garin Lagos ba tare da Kulsum ta san inda aka nufa da ita ba.
 Malam sace ni za ka yi? Malam ina ruwan ka da ni ne? A ina ka sanni? Malam ni matar aure ce ko ba ka gan ni tare da miji na bane? .
Tambayoyin Kulsum kenan ga Turaki, cikin rawar muryar da ke gab da rushewa da kuka.
Idan stiyarin motar ya ba ta amsa, to mai tukin motar ma ya ba ta, inda ta ke wannan bai kalla ba, sai sharara gudu yake, amma makalallen murmushin da ke kan tattausar fatar bakin sa ya kasa bacewa.
Kulsum ta soma bugun gilashin motar da duka hannayen ta, fatan ta gilashin ya fashe ko da zai yanke ta ne, ta yi ihun da mutane za su ji su kawo mata dauki. Amma ta lura gilashin motar ko sound ba ya badawa kuma ko za ta shekara tana bugunsa ba zai fashe ba.
Kawai sai ta fashe da kuka tana kiran Goggon ta da Baffan ta. Abin da ya yi matukar bai wa Turaki dariya. Ya dube ta da lallausar murmushi ta gefen lumsassun idanun sa, cikin rada ya ce,
 Saura Batulu da Umma! .
Idanun ta cike da kuka, amma hararar shi ta ke, daidai lokacin da suka kawo wani check-point na  yan sanda. Daga murya ta yi sosai tana kwarara ihu ba ta san cewa murya ba ta fita daga gilashin ba. Sai ta daga hannuwa tana yi wa  yan sanda alamar da ta sa daya daga cikin su ya zo jikin motar tare da kwankwasa gilassan, Turaki ya sauke glass a hankali ya kuma nuna masa katin shaida (I.D card) na shaidar aikin sa, nan da nan dan sandan ya yi baya yana daga masa hannu, ya yi sama da gilassan motar da sauri ya sake shan round ya shiga unguwar Ikoyi.
Kulsumu ba ta bar kuka ba, don ta gane in ma sata ce Turaki ya gama sace ta. Sun wuce kyawawan gidaje kamar guda biyar kafin su shiga wani kyakkyawan lodge mai hawa daya. Maigadi ya zo ya bude, Turaki ta zura hancin motar sa cikin gidan.
Ya yi parking a rumfar adana motoci wadda ke dauke da wasu motocin guda biyu, ya kashe motar tare da sakin ajiyar zuciya. Ya dubi Kulsumu wadda ta ki dagowa daga cinyoyin ta balle ta san inda ya kawo ta. Sautin kukan ta kadai ka ke ji a motar, kamar wadda aka gaya wa sakon mutuwar iyayen ta.
Kirjin sa ne kawai yake dagawa yana sauka da sauri-da-sauri. Wani lokacin excitement zai iya haifar da bugun zuciya. Mutum ya fadi ya mutu farat daya. To hakan ce ta faru ga Turaki, wanda ke ganin komai da ke faruwa da shi yau kamar a mafarki& wai shi ne da Kulsumu a gabansa!
Idan mafarki yake yana rokon Allah kada ya farkar da shi daga wannan mafarkin, har sai ya ga karshen sa, har sai ya gan shi tare da Kulsum matsayin ma aurata a karo na biyu.
Ashe duk mahaukacin neman nan da yake wa Kulsumu tana cikin kasar Nigeria, a garin da yake yawan rayuwa? Allah shi ne shaida kan babu abinda ya wahalar da shi a duniya irin neman da yai wa Kulsumu, shekaru dai-dai har guda hudu. Shi Allah da yake Gafurur-Raheem ne, yau ga shi ya tankado keyar Kulsumu ya kawo mishi ita har cikin ofishin sa. Shin shi wane irin wawa ne da zai yi saken da za ta sake kufce masa???
 If you are done with the cry (idan kin gama kukan) ki wuce mu karasa ciki .
A matukar fusace Kulsum ta dago ta dube shi, idanun ta a rufe sabida bacin rai, ta ce,
 Da wacce hujja zan bi ka inda ban sani ba? Me ye hadin ka da ni? A ina ka san ni, ko na yi maka kama da  yammatan da ake daukowa bisa titi a garin Legas a kawo su guest house ne?
Kyabe baki ya yi, ya ce,  Ni ma ban san me ye hadin nawa da ke ba, kuma ba ki yi kama da  yammatan bisa titi ba, sannan nan ba guest house ba ne, gidan mutane ne, hujja ta ta cewa ki bi ni ciki mu zauna mu yi magana ta nutsuwa ita ce; kin yi min kama da matata ne, matar da ban saki ba har gobe, amma na neme ta na rasa .
Ya karasa maganar da kasalallen murmushin sa na gefen baki.
 Ina so in tabbatar ne, I just want to confirm ko Kulsumu na ce wannan....I just want to confirm idan matata UmmuKulsum da na rasa nake nema ce& I just want to confirm idan reaction dinta saboda gani na a inda ba ta yi tsammani ba, yana nufin itama ta gane ni ne take pretending....ko kuwa wani abin ne daban ya firgita ta ta ke gudu tana neman mafaka&  .

Kafin ya rufe baki Kulsumu ta amsa,  ni ban gane ka ba, babu wani sani da na yi maka. Ban sanka ba, ban taba ganin ka ba, sannan ni matar aure ce, kuma tare da mijina ka gan ni, amma ka sa aka rufe min kofa saboda tozarci, saboda ka sato ni ka kawo ni guest house. To tsakani na da kai Li ilafi dubu .
Turaki ya yi wani murmushi, wani tattausan murmushi da rabonsa da yin emotional murmushi irin sa ba zai iya tunawa ba. He salute her courage! Yau ji yake babu wanda ya kai shi sa a a duniya, babu wanda ya kai shi samun cikar buri. Ashe zai ga Kulsumu komai daren dadewa! Sai dai kuma watakila ganin nata ya zo at a wrong time, idan har abin da ta ke fadi gaskiya ne na cewa (wanda suke tare mijin ta ne). Idan har wannan ikirarin nata gaskiya ne, shi ya ya zai yi da rayuwar sa?
Saboda ita ne har yau bai kara aure ba. Saboda ita ne har yau babu diya macen da ke burge shi. Saboda ita ne yake jin zai iya kare rayuwar sa single idan har bai same ta ba. Ashe ita tuni ta manta shi, she have move on tare da wanin sa. A zahiri bai kamata ya ga laifin ta ba, amma sai ya ji gabadaya duniyar na juya masa. Idan har da gaske matar auren ce, ya san hatta wannan kebewar da ya yi da ita a cikin motar sa haramun ne, sai dai ji yake in wannan shi ne haramun din da zai halaka shi& ba zai bari ta sake kubuce masa ba.
 Look Ummukulsum, duka cikin mu nan ba yaro karami, ki yi ta pretending din ki ba zan hana ki ba, amma in kin ga na barki kin bar gidan nan, to kin fito mun shiga ciki ne, mun zauna mun yi magana, na fahimce ki kin fahimce ni".
Kulsumu cikin shesshekar kuka, ta ce,  Ta ya ya zan yarda in bi ka ba ni da masaniyar ko za ka cutar da ni? Ta ya ya ka ke tunanin zan yarda in shiga inda daga ni sai kai babu muharrami a tsakanin mu, alhalin na kasance matar aure?
Turaki ya lumshe idon sa na sakan biyu ba tare da ya bude ba, kalmar auren nan tata da take ambata ta kasa yi masa dadi, ta kasa zauna masa a rai, haka ta kasa daina gasa zuciyar sa, sannan ya kasa yarda da ita, ya ce,
 ki sa a ranki cewa, kina cikin amana ta, ke da auren naki. Amanar da idan na ci ta sai Allah ya saka miki. Ki yarda komai lalacewar duniya har gobe akwai sauran masu amana da kokarin cika alkawari .
Kulsumu ta ce,  babu ruwana da amanar ka, ko me za ka gaya min ka gaya min yanzu ka sallame ni in tafi, ni dai na san ban san ka ba, ban taba ganin ka ba ko a hanya. Kawai ka ga matar mutane a titi ka sako ta a mota ta karfi ka dauko ta, wannan ai cin mutuncin aure da keta haddin dan Adam ne .
Ba ta rufe baki ba Turaki ya bude motar ya fito, cikin zafin nama ya zagayo ya bude tata kofar, kama duka hannayen ta yayi ya dunkule a cikin nasa. Sannan ya janyo ta ta karfi daga motar.
 Ni ma ban ce ki ce kin san ni ba, mu je a ba ki san nin ba, ni ma ai ban sanki ba Kulsum, amma dole mu yi magana ni da ke .
A haka suka shiga falon gidan, falo ne tsararre english parlour, bata ankara ba ta ga ya sa mukulli ya rufe kofar ya jefa mukullin cikin aljihun trouser din sa.
A tsaye Kulsumu ta tsaya ta ki zama, Turaki ya tako har gaban ta ya tsaya hannayen sa duka biyu zube cikin aljihu kamar yadda yake a al'adar sa. Ya yi kokarin kallon tsakiyar idanun ta ya sakar mata signal. Ta dauke kai, amma hatta hantar cikin ta kadawa ta ke yi. Yana da wani irin effect (tasiri) a kan ta tun zamanin kuruciyar ta. Ta yadda idan ya kasance a gaban ta, ko ya gifta ta gaban ta hatta hantar cikin ta rawa take yi. Yau da ya kasance a gaban ta cikin wani sabon yanayi da bata taba tsammata daga gare shi ba, babu inda ba ya rawrawa a jikin ta, including tsokar zuciyar ta.
"Ummukulsum yaya rayuwa? Yaya bayan saduwa? What is special a bayan rabuwar mu?"
Bata bashi amsa ba, illa sunkuyar da kan ta da ta yi. Kamshin one man show ya cika hancin ta. Turaki ya kara takowa zuwa gaban ta, space din dake tsakanin su bai fi taku biyu ba. Ya ce.
"Aka ce ba kya kasar? Aka yi ta wahalar da ni? Ashe kina cikin kasar nan Kulsumu? Kin samu rayuwa yadda kike son ta kin manta da ni ko, ni ina can ina ta wahalar neman ki lungu da sako, , Kulsum tell me about you ko dan yaya ne. I'm extremely intrigued! Me ya kawo ki Lagos?"
Wannan karon ne ta dago kai ta dube shi cikin ido. Kai tsaye ta gatsine fuska ta ce "AURE! Aure ne ya kawo ni, ba zan gaji da gaya maka cewa ni matar aure ba ce. Ka mayar da ni inda ka dauko ni, tun kafin miji na yayi karar ka".
Zuba mata ido ya yi kamar ya hadiye ta. Hannayen ta duka biyu Turaki ya kama kafin ayi haka ya rungume ta da wata irin azama, wata irin kyakkyawar runguma wadda ta hade bugun zuciyar su wuri guda, yana sauke numfashi da sauri, yana barin dukkan excitement din zuciyar sa ya na fita ta cikin numfashin sa.
"Ko waye ya aure ki yayi aure kan aure UmmuKulsumu, ni da baki na ban taba sakin ki ba..... kuma har abada bazan yi ba! Kuma na rantse sai kin dawo gidan ki da yardar Ubangijin sammai da kassai. I don't mind your pretendings.... ki cigaba da yi, shekaru takwas da nayi ina dakon wahalar soyayya baza su tashi a banza ba..... this is a promise (wannan alkawari ne)".
Kokari take ta zame daga jikin Turaki amma ya ki bata damar hakan. Kawai sai ta saka masa wani gigitaccen kuka da yasa dolensa ya sake ta, amma bai saki hannun ta ba, sunkuyawa yayi ya sumbaci goshin ta, karan hancin ta da saman bakin ta, abinda ya kara gigita Kulsumu, ta fizge daga rikon sa da karfi ta ja da baya tana hararar sa, tamkar idanun sa fado, murmushi ya yi, ya bude kofar falon suka fita. Bai sake ce mata komai ba.
Shi da kan sa ya bude mata kofar motar ta shiga, shima ya zaga mazaunin sa ya zauna, sai da ya kara bata lokaci yana kallon ta da murmushin da bata taba ganin sa da shi ba. Gabadaya ta canza masa, ta koma masa sabuwar Kulsumu, ba 'yar ficikar yarinyar da ya aura a kauye ya gudu ya bar ta ba, tana ta sharar hawayen dake gudu a fuskar ta da gefen mayafin ta. Alamu ne dake nuna zuciyar ta na tono old memeories masu daci a kan sa da ta dade da binnewa lokaci mai tsaho.
Ya kunna motar ya taka totur din ta, reverse ya yi ya fita daga ma adanar motocin ya doshi get cike da kuzari. Maigadi ya bude musu kofa ya hau bisa kwalta yana jan motar tamkar tayoyin ta sun yi faci, sabida rashin gudun ta.

 Wace unguwa zan kai ki Ma am?

 Ka kai ni bus stop zan samu taxi zuwa gida .
 Wannan ne kuma ba ki isa ba, sai na damka ki hannun solobiyon mijin ki, kamar yadda na yi masa alkawari .
Wayar sa ya dauko ya kira lamba ya sa a kunnen sa, tare da saka wayar a handsfree, tarrr ta ji muryar Taufeeq yana fadin,
 Doctor kun gan ta? Ga mu nan duk hankali a tashe .
Turaki ya ce,  security sun ganta, muna kan hanya yanzu haka. Fada min address din naku .
Tana ji Taufeeq na fadin lambar gidan Aunty Sakeenah da sunan unguwar Victoria Island. A ranta ta ce,  Shi ke nan tawa ta kare!". Amma a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login