Showing 57001 words to 60000 words out of 175038 words

Chapter 20 - KASUWANCINA BOOK COMPLETE BY ASMA BAFFA.doc

25 Sep 2025

6855

da yawa,shi dai yana Shan tea yana jinmu, baiyi nisa da fara sha ba ya Mike shima tare da cewa ga tea dinki nan nima bana sha muje na saukeku a schl Meenat.

Ina tsaye suka tafi ni kuwa dadi naji yana kula yan uwana ko bai kulani ba in dai ya kula yan uwana Alhmdllh,akan ya wulakanta min yan Uwa gwara ni yayi min ko mene,sabo da wasu kai kadai suke so duk Wanda ya shafeka basa saurarsu bare su taimaka musu sai iya matarsu ko budurwarsu,Meenat suna fita suka hango Kwaja yana wankewa su Sajida takalmin schl,da Sauri Meenat tace Yaya Aayan ka ganshi to dan iskan da suke hadani dashi shegen ciki kamar an kifa kwarya.

Koda Aayan ya kalli Kwaja bai San sanda ya saki dariya ba tare da cewa lallai an cuceki am so sorry su Hanifa yan iska ne,kamar ya sani sai ga Kwaja ya dago kansa wanda ke dauke da keya me shegen tsini goshi rafkeke ya bude baki hakoran gaba cako yana sakin murmushi yasha uban askin kwal kwal jijiyoyi a kansa rada rada ya dago sirisiri hannunsa saitin Meenat yana kifta mata Ido kamar na Kwado, Kuka Meenat tasa sabo da takaici,Aayan da kansa ya kira Kwaja ya masa warning kar ya kara ganinsa ya kalli ko fuskar Meenat,kuma ko gidansu ya daina shigowa ya dinga tsayawa bakin gate,a gigice Kwaja ya dinga bada hakuri kan ba zai sake ba.

Bayan na gama komai nawa dana saba na gida shirin schl nayi 1:30pm Driver ya kaini schl tare da kawata muka hadu Sayyah,Muna hira Sayyah tace tunda kina da aure ki dinga zuwa gidanmu ana miki gyaran jiki,Maman Mu tanayi har shagon gyaran jiki ne da ita,idan kika je a gida ma zata miki naki,kuma gaki best frnd dina naga ke yarinya ce baki ma san auren ba,zata koya miki komai ta dinga tsumaki Oganki yaji zam zam,yanda kike me kyau fara idan ta gyara miki jiki sai Oga ya zauce wlh.

Baki na tabe tare da cewa ke ni bazan yi ba Natural wanda Allah min ya isheni yanzun ma a haka kinga yanda yake bani wahala ina ga na kara wani abu,Karya nayiwa Sayyah dan karma taji sirrin aurena amma sai ta dage wai dole na samu time a dinga yi min ko duk wata sau daya ne,sannan a bani na tsumi nasha,a raina nace hauka nake na Sha tsumi me gida baya ko kallona kuma ko yaushe zai iya Sakina mu rabu,jiya ne ma kadai muka taba hada makwancin shima hakan nice na je tsautsayi yasa kuma ban fadi maganar data kaini ba na bige da kwana a can,a fili nace Sayyah kenan zanzo to amma sai na sanar masa,kirashi a waya ki fada masa yanzu muji,sai yanzu na tuna bani da Number sa shima baida tawa amma sai nace yana Office yanzu he is busy sai na koma gida,tace to shike nan zan fadawa Umma ,nace ba matsala Insha'allah.

Muna cikin class 4pm Saura 1hr a tashemu sai naji wani malami ya leko ta window wace Mufeeda Adam Fatima?nace Sir tare da daka yatsa sama,yace zo kinyi bako,Mamaki ya kamani bako kuma ni to wa na sani,Haka dai na daure muka Mike ni da kawata Sayyah cike da tsoro na fito motocin Aayan na hango mamaki da tsoro ya kamani ina ta Addua a raina nace Allah yasa lfy dai,Sayyah tace waye wannan haka wani hamshaki? Mijina ne,Sayyah tace kut dama kece matar Aayan Muhd Jabeer ta yanzu? Nace ae mana kin sanshi ne? Tace a labarai muke ganinsa a TV kuma akwai wata yar kawar Umma yar gidan Minister of finance ta Dade tana binsa tana sonsa sosai ta dinga kiransa duk inda yake sai ta nemeshi amma Sam ya dinga Wulakantata baya sonta,har yanzu bata hakura ba wlh sonsa takeyi,akwai ke yan mata da yawan gaske da na sani suna bibiyarsa don kawai ya kulasu amma ko sauraransu baya yi,nan take gabana ya fadi, bakin ciki ya taso min na fara masifa wlh idan ma kin Santa ki fada mata kar ta kara kiran wani da namiji a waya,aikin banza amma wannan kwai jaka, dabba, Akuya, tinkinya inba tsinanniya ba mene na bin mijin wasu a waya asararriya wacce ta rako mata duniya.

Sayyah shuru tayi tana kallon yanda na dage nake ta zazzaga masifa da zage zage,tace lallai kishinki yayi yawa,nace ai ba kishi nake ba kawai haushi ta bani mace na bin maza tana zubar da ajinta,Dariya kawai Sayyah tayi tace to nidai na koma class tunda mijinki ne bye ta juya abinta,a hankali naci gaba da tafiya kafin na karasa motarsa kawai ya fito ya tako har inda nake tare da kamo hannuna ya jani ya sani cikin mota ya shiga Suka ja motoci muka bar schl din gaba daya.

Nace lfy?bafa mu tashi ba,yace ae ni na tashi daga Office yau kuma abinci nake so kiyi min 5pm Yarima Bobo zaizo, shuru nayi ina gefensa a baya nayi shuru har muka karasa gida muka fito da sauri ya rike hannuna yana Jana fiiii,har cikin part dinmu,Hijab ya zare min ya kaini har kitchen yace fara masa Abinci me kyau yana son Founded yam da miyar kwai,nace to da sauri na fara aikin shi kuma ya fita,nan danan na shirya lafiyayyan Sakwara da miyar kwai tasha nama da alayyahu tayi dadi sosai,na hada lemuka kala biyu na zallan fruits me dadi yayi Sanyi,na shirya komai a Dining sannan na gyara kitchen din tare da kara gyara part din sosai.

Bedroom na koma tare da fesa wanka na shirya cikin wata Atamfa cotton Orange riga da skert na Sha kyau sosai nayi kyau na gasken gaske,ina kamshi na hau Saman bed dinmu na kwanta ina hutawa 15mnt sai gashi ya shigo sanye cikin jallabiya fara yace muje Ku gaisa,na Mike haka nayi hanyar fita,
Ya riko hannuna tare da juyo dani baya yace haka zaki fita? Nace mene to a nan?nayi waje abina a haka,da sauri ya jawo ni tare da cewa ki canja kaya bakiyi kyau ba kisa doguwar riga,banyi musu ba nasa Arabian Gown tare da mayafin kamar Balarabiya na fita har Palon da suke.








AsmaBaffa
[1/14, 4:32 PM] Asmabaffa:
KASUWANCI NA





56-60







Official






By
AsmaBaffa






SEEYAH IBRAHIM and UMMU SOPHIE ths page is for u tnx.








A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, daga mari kuma sai kuka koma Ma'aurata, murmushi nayi tare da cewa ai ka fini Sanin komai,dariya yayi yace gaskiya dai ai nasan watarana in kika ji labarin yanda na tsara sai kin bani gift ma,ya dai baka gift tunda Ku kuka San me kuka tsara,Aayan dai yana jinmu bai ce komai ba na Mike ina cewa ga abinci Fa yana Dining ko na kawo ma nan? Yace ai dole naci girkin Amarya guda kamar ma kin San yunwa nake ji,kai tashi Malam naje naci abinci.
Mikewa sukayi har Dining suka zauna nayi Serving dinsu, Yarima sai murna yake yi abin cin da yake so ne,suka fara ci Lauma daya Yarima ya fara Santi uhmm kaga yar yarinya da iya girki shi yasa naga mutumin sai kiba yake yi da kyau, Dariya nayi wace tasa nayi wani mugun kyau.

Tsaki muka ji ya ja tare da gasa min harara,shuru nayi tare da sadda kaina kasa,kallona yayi tare da cewa je bedroom ki dauko min wata paper saman Bed,ok nace tare da mikewa zan tashi kawai na bige flask din miya ta dan zubo min a hannu ga Zafi sosai,hannuna na yarfe tare da cije lips dina,da sauri ya Mike tsaye tare da rike hannun nawa yana min sannu ya tsotse min yatsun da miyar ta zuba yana hura min da bakinsa kuma fuskarsa ba alamar rahma Sam sai ma fushi da yakeyi,ni dai kallonsa kawai nakeyi har ya gama ya kalleni tare da cewa ba Zafi? Kai na daga tare da cewa yeah,jeki to ki kawo min.
Ina tafiya Yarima ya dura masa ashar yana cewa amma kace min wani fada ma kukeyi munafuki,to me nayi na wani soyayya a nan? Ku fa bakwa ganewa Hausawa ba dama aga mace da namiji sunyi ko magana sai ace wani love ni zan iya kwana da mace same Bed naked ma ba abinda zai faru.

Dariya Yarima ya dinga yi yace Allah ya taimakeka ba kyau ganin sirrin wani da sai an gwada na gani a gabana,kai har kana da bakin magana dan Iska da ban sanka bane sai ka fadawa wani abinda har wani Fyarfadiya kakeyi idan ta ciwo ka shine zaka zo kana min kuri,Dariya Aayan yayi tare da lashe lips din kasa kamar an tuno masa wani dadi daya taba ji yace lfy ce yaro,Kai aka bawa wahala wlh tunda kana iya sha'awa amma baza ka iya aikata komai ba akwai wahala abin har tausayinka nake ji frnd,Aayan yace kama daina tausayina yaro ni ba abinda nake ji,suna ganin na fito sukayi shuru tare da canja hira basu San naji komai ba,mika masa nayi na zauna kusa dashi a Dining din nima harda leka cikin paper daya bude nace mu gani,miko min yayi sai da ya bari na karba yace to ki rike du tunda Sa'idon naki ya kai haka,Murmushi nayi tare da mika masa nace amma da niyyar karantawa nayi tun a dakin zan tsaya na duba yanzu ma izininka nake nema,yace bazai karba ba Sam yayi fushi na masa shishigi, mikewa nayi da paper zan tafi ya jawo hannuna ta bayan kujerarsa na zagayo tare da zuro kaina a hankali ta saitin kansa fuskata na daura a wuyansa nasa hannayena tare rungumesu ta kirjinsa sannan na rada masa a kunne ina dariya ga paper dinka Dan Daddy mene na fushi na daura saman table din na juya tare da barin wajen na shige Bedroom.

Yarima yana ta dariya yanda yaga Aayan yana jin kunyarsa,yace ah to yarinyar nan naga Alama wise ce kai a boye kake yi kana mana karya gashi ita wlh ta birgeni baka taba auren ma irin wannan kalar ba sauran tsoronka suke ji magana basa iya yi maka,haka idan munzo basa iya zama a kusa da kai tare da bakinka lallai kana kwasar Harka wlh ga shawara ka fara tunanin fara Sex da wannan maybe ma ka warke kake batawa kanka lokaci, Allah kiyaye da wannan yarinyar karama ai sai na balla mata Hips cewar Aayan, nan dai suke ta faman zancensu ban san me suke shiryawa ba sai tafawa suke suna dariya.

Bayan kwana Uku muka shirya dasu Meenat mukaje tsohuwar unguwarmu tare da gaisawa da abokan arziki a dalleliyar mota,kowa mamaki yake,Nawwara ma yanda taga mun canja mun koma yan gayu ga hutu ya nuna a jikinmu ta dade tana mamaki, na bata Address na gidan mijina,Haka Uwaliya still suna zaune a gidanmu nace su zauna sai nan gaba zan gyara gidan.
Mun shirya dasu Meenat idan anyi Hutu zasu je Maiduguri dangin babanmu tare da Rimin Gado dangin Ammah can zasuyi Hutu sabo da zumunci kuma muna kiransu a waya muna gaisawa.
Tun daga Ranar da Aayan yayiwa Kwaja magana bai kara yiwa Meenat magana ba sai dai idan ya ganta a gefen gate ya fara lashe lips yana mata signa da ido ita kuwa sai tayi kamar bata gani ba.

Ana haka wataranar Asabar sun dawo daga Islamiyya sai ga wani ya Parker a motar eban kaya wacce ake cewa yar Kurkura ya fito ya taresu a hanyar gida,wani dan Gajere daf da kasa kamar a kifeshi da kwando me kwalelen kai sai ka rantse baza a samu Hula size din kansa ba,harda sa wata barmemiyar suit tsohuwa tasha duniya,Handkerchief ya zaro tare da goge wani kwafjejen takalminsa ya kalli Meenat yace Hajiya Meenat ko? lfy Malam idan tambaya kakeyi kayi sauri muke,murmushi yayi tare da cewa yan mata kenan wato Allah ya zuba baiwa a nan wajen yana maganar yana watsa hannayensa kafta kafta yan gajeru dasu kutuf ,ya kara cewa Allah yayi Kudirarsa anan,baki ya rike yace kai Kudirar Allah kenan,harara Meenat ta maka masa,Maeesha ma taja tsaki yace ahh harda ke yar ficika? kema kin hadu har kinfi babbar ma naga kinji haushina ke ban yabeki ba mata akwai kishi to kema kina da kyau ai baki sani ba kinfi ma babbar kyau shike nan ko?

Saura kadan Meenat tayi dariya kawai taja hannun Ma'eesha sukayi gaba,da gudu ya datse gabansu,in kina kaunar Allah ki saurareni in dai akan nace kanwarki ma me kyau ce to na janye dama dan kar ranta ya baci ne ace kamata bata ji yabo daga gareni ba naga tana kumbura shi yasa amma ai kin fita komai,kinga gaki fara,gaki doguwa yar tsakiya,ga sura,ga idanu,ga kamshi gaki me ilmi wayyo sai naji dama munyi aure,Meenat ta kara hade rai tace bamu hanya mu wuce,ya wani shagwabe fuska tare da canja murya kamar dan iska zan miki shagwaba Allah wayyo Baby,ai basu San sanda suka sheke da dariya ba,shi kuwa gani yake ai yaci gari ya birgesu,yace kin gani tun ba a je ko ina ba,ina me tabbatar miki zaki san Allah ya baki miji na gari,zan miki soyayya,zaki ji dadi,zan baki kulawa,zan miki duk wani abu wanda mace take so take nema a duniya komai,kawai ki bani dama,ki kula dani ki yarda dani zaki ji dadi,sai kinyi alfahari da wannan rana ta Asabar da muka hadu,da ace ana harba namiji sama ina tabbatar miki idan muka yi aure nasan sai kin harbani sabo da yanda zaki koma sona da ganin mutunci na,

Bari kar na dameku da surutu sunana Nasuru ko kuma ki kirani da OPERA,amma a unguwarmu anfi kirana da Nasuru me Hali, yayi dariya ya kara goge rigarsa yace Business man ne ni ina da yara dasu ke ci a karkashina sanadiyar wannan motar da kika ganni da ita domin daya a yarana shike Jan wannan motar,mutum biyu kuma sune masu tayashi lodi da saukewa,ba inda basa kai kayan miya da fruits,irin su tomatoes,Kankana,ke in baki a takaice har yalo suke daukowa daga Sumaila zuwa Lagos Agege, da sauransu,Meenat taji baza ta iya ji ba ta figi hannun Ma'eesha suka barshi nan tsaye bakin gate,suna shiga suka hango Haneefa da Sajeeda sun labe ta jikin gate suna ta dariya da alama Nasuru Opera ma su suka turowa Meenat shi tunda sunga an kori Kwaja.
Meenat ta hararesu su, sai kuma suka sheke da dariya Sajeeda tace a haka zaki kare in Allah yarda sai dai ki auri irin wannan wai ku masu kyau,anzo gidan daula za a ce sai me kudi zaku gani wlh nan gaba da kafarku zaku bar mana gida.

Meenat tayi murmushi sannan tace masu gida manya gidan wasu dai har iyayen naku basu da gado a nan bare Ku,a haka zaku kare banzaye marasa class,tass Meenat taji saukar mari tana dagowa taga Mujaheed ne ya mareta gasu Ameer nan a tsaye suna huci,Ma'eesha tace Allah ya isar mana,aiko Mujaheed ba imani kato dashi ya zage ya dinga Marin Ma'eesha yar yarinya karama ya Ciro takalmi ya fara kwada mata ta ko ina tana ihu,Meenat bakin ciki yasa ta dauki wani dutse kato ta buga masa a kai nan take jini yayi tsartuwa a kansa ya fashe,ya Dafe wajen yayi baya Su Ameer sukayi kansa suka rikeshi,Kafin kace me gida ya dau Alert sai kowa ya fito harda Hajja,Su Meenat tuni sun arce part dinsu da gudu,lokacin Mufeeda ta fita shopping,Hajja Bala'i take zubarwa kawai a tsakar gida an kashe mata jika,haka Ma su Abbi sai gasu duk sun dawo da motocinsu gida,haka ma iyayen su Mujaheed mata har da kuka,aka daukeshi sai asibiti don tuni ya Sume,sabo da hauka gaba daya suka bisu asibiti kamar wani Gomna haka dukkan yan gidan,Matar Abbi da Hajja sai Haneefa su kadai ne a Compound suna jimami tare da shirin daukan fansa,suna cikin wannan Hali sai kicif ga Driver na mun dawo daga shopping tun daga yanayin da na gansu gabana ya fadi haka na daure na fito ban fito da kayan dana siyo ba sabo da nima cikin shirin ko ta kwana na fito,ina taku dai dai nasha wanka sosai,

Ban san me ya faru ba,ba zato naji sun rufeni da duka,sunfi karfina ma'aikata si hakuri suke basu amma suka ki ji musamman Hajja kamar mahaukaciya ta dinga dunkule hannu tana dukana,Haneefa da takalmi me tudu,Matar Abbi ma ta ko ina,har sai da Hanci na ya fara jini ina habo, ana haka matar Abbi ta kara dauko Wayar charger tace duk kowa ya kyaleta dani sai ta ramawa Danta haka ta dinga tsula min wayar nan sai da suka min lilis,da kyar nake iya numfashi,sai lokacin hankalinsu ya kwanta suka koma can part dinsu suna murna.

Ina kwance a wajen hancina na fitar da jini sai ga Aayan ya dawo ya iskeni haka,da sauri ya daukeni kamar Jaririya don shi yasan yan gidan ne suka min haka,kawai ya sani a bayan mota shima ya shiga gefena Driver yaja da sauri sai Hospital,a motar ya kwantar dani saman cinyarsa yana min sannu duk ya damu ya rude,Hadadden asibiti ya kaini,suka min allurai da karin ruwa sannan suka bamu magunguna ya siya,na danji sauki da karfin jikina,ina tsaye zamu tafi ina cije lips ya tsuguna a kasa yace hau baya na, na kaiki cikin mota,bayansa na hau na lumshe ido sakamakon wani dadi da sanyin Ni'ima naji ya ratsani shima bangarensa hakane,haka ya dinga taka Steps ana ta kallonmu har mota ya kawo ni ya sani ciki a hankali shima ya zaga ya shiga Driver yaja

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login