Showing 1 words to 3000 words out of 13980 words
Chapter 1 - ZUCIYA DA KWANJI Book 4 End Complete Writing by MAIMUNA IDRIS SANI BELI .pdf
 Zuciya d kwanji 4 
1 
Su kawu basu can dade da fita ba laila ta 
shigo 
falon nata, lokacin tana tare da maryam 
kanwar 
Abdullahi wadda ta gayyato da kanta bayan 
su 
safiyya sun koma gida domin ta dinga debe 
mata 
kewa tana kuma taya ta da ayyuka. Tun da 
laila 
ta shiga falon fatim ta dora mata ido babu 
ko 
kiftawa, kallonta take da fatar ido, 
zuciyarta kuma 
na tattaro dukkan mukaman zalinci da 
ta'addanci 
tana nada mata. A hankali kuma sai ta fara 
kumbura kamar mai shirin fashewa, sai kila 
idon 
maryam ba zai barta ta fashe din ba. Laila 
ta 
zauna suka gaisa babu yabo babu fallasa 
laila da
maryam, domin fadima ta dinke bakinta dif 
sai 
huci kawai take. Hakan yasa laila duk ta 
diririce 
ta ce. "Tun satin da ya wuce na sami labarin 
fatima, ina ta kokarin in zo Allah bai nufe ni 
ba". 
Fatima ta ci gaba da binta da kallo kawai ba 
tare 
da ta tanka mata ba. Tsammanin maryam 
duk 
cikin ragowar kukan da ta gama gurza ne 
dan 
haka ta kasa tankawa laila. Maryam da ta ji 
nauyin din shirun da fatima ta yi sai ta shiga 
zancen, amma kafin ta yi sai ta shiga 
zancen,amma kafin kalamanta su fito sai na 
lailan suka riga nata fitowa da wani batun. 
"Na yi 
tsammanin ma kina gidanku,da har zan je 
can 
ashe kina nan". Fatima ta kara fakar idon 
maryam ta bugawa laila harara. Maryam din 
kuma sai ta sami gabar da za ta yi maganar 
da
za ta hado da fatima. "Haba yaushe za su 
tafi 
gida su ba kananan yara ba, ko Aunty?" Dole 
fatima ta yi murmushi da ya fi kama da 
yake,kuma ta kawar da kai ta kara barin 
maganar 
ta bi ruwa. Can ma sai ta mike ba tare da ta 
dubi 
kowa ba ta doshi dakin kwanan ta turo kofa. 
Ta 
bar laila da sake saken hanyar da za ta bi ta 
shawo kanta, ta fi kowa sanin wace ce 
fadima da 
shegen taurin kanta mai zafafa kiyayya 
idan ta ki 
kuma mara saurin yarda bare a gane abin 
da ta 
so. Daga karshe sai ta zabi mikewa ta bi ta 
duk 
kuwa da ba ta tanadi abin fada ba. Ta sami 
fatima kishingide kan sofa bed,kuma 
shigowar 
lailan ta sanyata ta dago,kuma ta tashi 
zaune 
cikin fushi har ma ta riga ta magana. "Ina
tsammanin ba karuwancin kare kawai kika 
gado 
ba laila har da rashin zuciyarsa,ina kashedin 
da 
maigidan nan ya yi miki? Ni ina wulakancin 
da na 
yi miki? Ai ina tsammanin ko mutuwarsa kika 
sami labari babu rawar kafar da za ta kawo 
ki 
gaisuwa ballantana da izinin Allah yana 
raye....." 
Laila ta yi saurin zama kusa da ita jiki a 
sanyaye 
ta dafa kafadarta. "Idan labari na samu 
fatima da 
kyar zan gasgata cewa ke ce kika zama 
haka, ke 
ce kike daga muryoyinki suke kare Abduullahi 
maimakon Alh. Ke ce kike ihun fada min 
bakan 
maganganun duk tsawon shekarun da muka 
dauka tare kin zubar da su...." Fadima ta 
bige 
hannunta ta mike tsaye tana huci. "Oh! Dan 
kin
suffanta muryoyin nawa fili ne a gidan 
radion da 
mutum ke zuge jaka ya siye sai a sarrafa shi 
yadda ya so? Takaici na kullum kara hawa 
yake,musamman idan na fado irin wannan 
shafukan da rainin wayo da son wawantar 
dani. 
Takaici na kullum kara hawa yake, 
musamman 
idan na fado irin wannan shafukan da 
rainin wayo 
da son wawantar da ni. Kar ki manta fa da 
radin 
kaina na amince hawa turbar da zan kuma 
rayuwa da alh,babu wanda ya sami ko ya yi 
min 
jan ido. Idan dai da dalilai nake jin ya 
kamata na 
komawa Alh ya wajaba ne a yi min uzuri a 
duba 
dalilan ne idan na nemi janyewa. Kuma cikin 
masu duba dalilan nawa ma bai kamata a 
same 
ki ba laila,dan na san in na janyewa 
komawa
auren Alh ke tuni kin tattare hannun zani za 
ki 
shiga....." Laila ma ta mike suka jeru suna 
kallon 
juna kai tsaye, amma fuskarta cike da 
damuwa,ko 
dai ta karya ce, to za ta zauna daram a 
fuskar 
tata ta debo rawar baki ta ce. "Haba..... Don 
Allah fatima...ki kori shaidanun da ke son 
giftawa 
tsakaninmu,ki tuna matsayina a wajenki ta 
zarce 
a iya kore duk wani abun alkairin baya, 
kaunar da 
na nuna miki duk tsiya da yadda sabanin ya 
shiga 
tsakaninmu ta wuce a ce kin debe min. 
Like · React · Report · May 21, 2015 
Amierah S-Man 
Zuciya d kwanji 4 
p2 
Dukkan kauna.... Ni mai kaunar ki ce ki 
dinga 
tuna haka....." Yanzu hawaye fadima ta ke
sosai 
kuma murya a raunane ta hau nuna ta tana 
cewa. 
"Wallahi laila tun da nake ban taba ganin 
maci 
amana irinki ba. A ina. Kika kaunace ni? A 
kan 
wa Alh dangin Alh dangina da Abdullahi 
maganar 
cikina kika nuna min kaunar ko a wannan 
service 
din da kika zamewa Alh?. Kar ki wawantar 
dani 
kin ji? Ba fa daga kauye aka lalubo ni ba. A 
mafarki aka nuna min kina cikin masu 
kaunata 
sai na rsantse miki da Allah idan na farka 
sai na 
yi tofin korar shaidan da na tabbatar shi 
yake 
zuga ni amincewa da ke ki kuma cutata". Ta 
kara 
rushewa da kuka,sannan ta ci gaba magana. 
Tsinanne ma irinki na taba gani a duniyata 
laila,in
ta so da iyaye na shekaru aru aru basu taba 
tir 
dani ba sai da na hada sirri da ke, kika 
mayar 
dani suke min kallon hatsabibiya kuma 
makaryaciya. To amma albishirinki, iyayena 
ba 
irin naki da na Haj. Sa'a ba ne,sun isa da 
ni, 
kuma na tarbiyantu da tarbiyarsu, ba. Sai 
kin 
dogara da na zubar da ciki ba, ba sai haj 
sa'a ta 
yi kurarin biyana kudi duk zan bar muku Alh 
ba. 
Cikin ruwan sanyi da umarnin iyayena zan 
bar 
Alh.haj sa'a ta aure shi ko ta aura miki shi 
idan 
ta so,dan na ga kun fini bukatarsa,dama 
can ni 
bai taba dada ni da kasa ba, ki je ki 
tambaye shi 
ki ji ba shi da abin da zai rude ni 
wallahi....." A
dan rikice laila ta debo rauni za ta yi 
magana,fatima ta tare ta cikin tsawa. 
"Wallahi ba 
zan ji komai daga gare ki ba laila, in kuma 
kin 
matsa sai na ji zan iya yi miki rashin kirkin 
da zai 
sa kila ki canja min suna, in je kawai na 
yarda kin 
yi nasara a kaina tunda kin hadani da 
iyayen da 
ban taba karbar ko harara daga gare su ba 
sai ta 
dalilin aminci da ke. Suka yi min birki daga 
burina 
na sake zama da Alh kuma na barku sannan 
ki 
aurenki ya yiwa haj sa'a kyau ko da bai yiwa 
alh 
ba,nima bai min ba. Sai dai ban taba saka 
rai zan 
bambamta daga jerin diyan mutunci ba kaf. 
Alhamdulillahi cikina bai zube ba, watakila 
daga 
yanzu zan fara rayuwar da kika zaba mini".
Yanzu 
laila ta fara yanke kauna da cewa fatima za 
ta 
saurare ta, amma duk da haka haka ta kasa 
hakuri ta cire rai, a tausashe ta ce. "Ya 
kamata ki 
saurare ni fatima, ba ki san abin da ya kawo 
ni 
ba, amma kin zauna kishi zai hana ki 
saurare ni, 
ban da abinki fadima ina ni ina ajin Alh? 
Ki....." 
Fatima na tuno yadda ta ga laila da Alh a 
bayan 
mota sai ranta ya kara mugun baci,hakan ne 
kuma ya sa ta nunawa laila kofa. "Na ce ba 
zan 
ji ki ba,in kuma akwai dole cikin jin naki sai 
in 
gani.... Malama ki bace min da gani". Laila 
ta yi 
saroro tana kalon ta, akwai alamar 
hakurinta ya 
kare don fuskarta ta baci sosai. Ta jima 
tana
kallon fatima kallon na kamar ta rufe ta da 
duka,amma babu hali. Kawai sai ta yi kwafa 
ta 
kada kai ta wuce ta bar fatima da bin ta da 
dogon tsaki. *************** 
*************** 
************ Tun a mota laila ta kira Alh a 
waya 
cikin zafin zuciya. "Alh ina muradin ajiye 
wannan 
aikin da ka ba ni". A dan rikice Alh ya ce. 
"Ban 
gane ba,domin me?" Ta shaki numfashi hade 
da 
takaici da ya cika makogwaro ta ja hanci ta 
ce. 
"Dan in tsira daga dabi'antuwa da halayyar 
karnuka,ya kyauta ka dinga tunawa yadda 
fatima 
ta makanta ka ba lallai ni a ce na makantu 
haka 
ba, maganata gaskiya na gama shakar 
iyakar 
abin da zan iya...." A dan kufule da 
sarkewar
numfashi ya tare ta. "Ki takaita 
maganganun 
bana son dogon surutu don Allah.... Sai 
neman 
kike ki fada min abin da ranki ke so..... Kar 
ki 
jagula min lissafi kin ji." Laila ta hadiye 
ciwon 
tsawa da na mayar da ita ba a bakin komai 
ba da 
Alh ya yi, ta tattare dukkan abin da za ta 
iya na 
jin zai fahimtar da shi ya kuma kawo 
karshen 
hannunta cikin lamarinsa da fatima ta ce. 
"Idan 
magana ta gaskiya zan fada maka ita ce, 
fatima 
ba ta ra'ayinka a yanzu na san fatima farin 
sani 
saboda haka ban taba daukar yada take 
bijirewa 
da wasa ba. Na san tana nufin abin da take 
fada 
har cikin ranta tsakani ta da Allah,ba zan
iya ci 
gaba da wahalar da kaina ba,idan kana da 
abin yi 
kawai ka yi ni dai na zare hannuna....iyakar 
abin 
da zan iya ce maka kawai..." Alh ya sauke 
wani 
gwauron numfashi wanda ke cike da alhinin 
tserewar fatima a bajad din rayuwarsa. Sai 
dai 
karfin hali na kwatanta masa fatima ta 
shirya yin 
biyu babu kawai, abdullahi kuma ya yi 
alwalar yin 
badi babu rai, matukar shi yana numfasawa. 
Ya 
jinjina kai cikin bacin rai ya ce . "Shi ke 
nan,ban 
taba tunanin yanke wa Abdullahi danyen 
hukunci 
ba, sai dai kamar ya zama dole tunda shi ya 
zabi 
hakan". A dan tsorace laila ta ce. "Me za ka 
yi?" 
Ya hura iska a baki ya fesar sannan ya ce.
"Zan 
wanke kafa na bar kasar nan a yau ko 
gobe,ma'aikatan da suka sakaya abdullahi 
ma'abota biyayya ne, in na shekara goma 
ban 
dawo ba za su ci gaba da tsare min shi 
shekaru 
goma" Laila ta sauke numfashi kawai ba tare 
da 
ta tanka ba. 
1 · Like · React · Report · May 21, 2015 
Amierah S-Man 
Zuciya d kwanji 4 
pg3 
****************************** 
************ Sai da 
Abdullahi ya sami watanni biyu a tsare 
sannan da 
taimakon sagiru da irin zazzafan shige da 
ficen 
da yake sannan ya samu aka basu izinin 
ganawa 
da Abdullahi,shi da yayyen abdullahi biyu, 
abdullahi da abdu wahab. Abdullahi ya fita 
kamanninsa matuka,duk da cewa babu
mahalukin 
da ke taba lafiyarsa da fatar jikinsa amma 
yunwa 
da takura na yara masa irin nasu harshen 
sai ko 
tsananin fargabar laifin da ake tuhumarsa 
da shi 
wanda har yau bai san shi ba. Tsoronsa Allah 
tsoronsa kar q zarge shi cikin manyan yara. 
To 
shi ba dan kasuwa ba, shi kuma ba dilan 
kwaya 
ba, wanne laifin ya yi da za a masa wannan 
kamun na rashin mutunci? Wuya ta sa 
abdullahi 
kallon yayyensa da sagiru kawai,ya kasa 
amsa ko 
sannun da gaisuwar su balle tambayoyin 
neman 
ba'asi da suke jero masa wanda shi ma bai 
san 
dasu ba. "Me ka yi abdullahi? Ka yi rigima 
da 
wani ne? Kudin wani ka ci bashi.....? Kalar 
tambayoyin da yayyen nasa ke faman yi
masa ke 
nan har da kwalla a idanuwansu. In ka 
dauke 
sagiru da bai tambaye shi komai ba tunda shi 
dai 
tuni ya san daga inda siyasar ta bullo. A 
karshe 
har lokacin su ya cika, sai a sannan jarumi 
abdullahi ya motsa kwanjinsa dan tafiyar da 
abin 
da ke zuciyarsa cikin magana da hutawa. 
"Yaya 
don Allah a kular min da fatima,a sanar da 
ita 
ban laminci ta taka ko kofar gida ba, idan 
lalurar 
rashin lafiya ta riske ta a je da ita kar a 
barta ta 
ji da kanta.... Duk suka zubo masa ido da 
duban 
mamaki. Yayansa Abdulwahab ya gaji ya ce 
"Wace ce haka? Abdullahi ya amsa cikin 
kawar da 
kai. "Amaryarsa da yayi baka gari". Sannan 
matan naka a barsu su fita barkatai,kuma
in 
larura ta kama su a barsu su ji da kawunan 
su? 
Babu kuruciya cikin maganar nan taka?" 
Suka ci 
gaba da dubansa su duka da alamun jiran 
amsa, 
shi kuma kai tsaye ya amsa. "Ta fisu 
rauni,kuma 
ta fisu hatsari". Duk suka kara tsira masa 
ido,sai 
dai babu wanda ya nemi karin bayani duk da 
kuwa maganar tasa na bukatar fashin baki. 
Suka 
yi masa sallama bayan sun cika shi da 
nasihar 
tawakkali da mayar da lamari ga Allah,tare 
da 
ambatonsa cikin ko wanne hali. 
*************** 
*************************** Bayan sallar 
ishar 
ranar abdulwahab ya kai ziyara gidan 
abdullahi 
cikin rakiyar babban dan wansa sahabi.
Hindatu 
da sadiya tare da shi a falon Abdullahi yana 
musu 
bayanin da ke akwai game da Abdullahi,tare 
da 
jawabin kwantar da hankali. Har wani lokaci 
bai 
ga fatima ba, kasancewar kannen hindatu 
sun zo 
sun gaishe da shi, ya tambaya wace ce 
amaryar 
abu turab a ciki aka ce babu. Dan haka 
yanzu da 
kansa bayan ya duba agogo ya bukaci a kira 
masa ita. Hindatu ta je ta sanar da ita 
sannan ta 
dawo. Can jimawa sai gata ta shiga a 
nutse,tana 
sanye da hijabi wanda bai iya boye cikinta 
ba, 
wanda a yanzu yake da watanni kusan 
bakwai. 
Sai dai babu abin da ya ragu cikin shan 
kamshi 
da kasaitar ta. Ba karamar kaduwa
Abdulwahab 
ya yi da ganin fatima ba, dan sai da ya ya 
maimaita sunanta a zuci lokacin da abdullahi 
ya 
ce........ A kular min da fadima. Sannan ma 
ya 
fara tantamar ce matar Abdullahi ko kuwa? 
Cikin 
wannan rudin ya dinga satar kallon ta har ta 
rusuna ta gaishe shi. Ya amsa cike da alamun 
mamakin sannan ya kama sunanta. "Fatima 
ce?" 
Ita ma muryarsa ce ta ja hankalinta ta 
daga kai 
sosai ta kalle shi,sai ta tarar da aminin Alh. 
Ya 
sha zuwa gidanta. Lokacin da take auren 
Alh, Alh 
ya rakito ta da kyar tana zuwa gaishe shi ba 
tare 
da fuskarta ta boye masa dole ta zo gaishe 
shi 
ba. Ta dade da sanin yanda Alh ke ji da shi 
saboda yawan ambatonsa da ya ke. Ta amsa 
ambaton sunanta da ya yi cikin hadiye
mamki ko 
sanayyar dai cikin 'yan sakanni,ta girgije 
ranarta 
ta mike sosai ta zauna kan kujera. Amma shi 
sai 
ya kasa hadiye nasa mamakin ya ce. "Ya yi 
aka 
yi haka? Ke ce amaryar kanina Abdullahi?" 
Ta 
dan yi murnmushin mai kama da na dole,ta 
kuma 
kawar da kai ta bar tambayar ta sha ruwa. 
Mamaki ya kara kashe shi, dan shirunta ya 
tabbatar masa da cewa amsar ke nan, 
lamarin ya 
yi kama da almara. Ya jinjina ya kara 
jinjinawa, 
ita kuma ta girgije ta ki taya shi mamakin 
har dai 
ya sauke numfashi ya fara ba ta bayani. 
"Mun 
sami abdullahi dazu,kuma alhamdulillahi 
mun 
same shi da koshin lafiya,illa iyaka abin da 
ba a
rasa ba. Sai dai shima bamu sami jin ta 
bakinsa 
ba na masaniya a kan kamun da aka yi 
masa.sai 
dai ba zamu kosa da yiwa Allah godiya ba, 
komai 
ma zai zo cikin sauki tunda dai an san inda 
ya 
ke". Fadima ta yi ajiyar zuciya kawai tana 
kurawa 
faratan yatsunta ido,har yanzu ba ta tanka 
ba, 
kuma babu alamu na za ta tanka din. Yaya 
abdulwahab bai damu ba,dan ba tun yau ya 
san 
halinta na shariya ba ya kuma ce mata 
Like · React · Report · May 21, 2015 
Amierah S-Man 
Zuciya d kwanji 4 
pg4 
"Ya bayar da sallahu a fada muku,duk wata 
take 
da bukatar fita idan ta taso ta tambayi 
daya daga 
cikinmu ko a waya ne.Amma ke ki yi hakuri
kar ki 
fitar masa ko ina,idan yana da dalili mu dai 
bai 
fada mana ba. To sai ki yi hakuri ki kiyaye". 
Ko 
motsi ba ta yi ba bare alamun za ta 
tanka,sai dai 
fa ta cika taf! Da mamaki,wato duk halin 
kuncin 
da abdullahi ya shiga ba zai fasa motsa 
kwanjinsa a kanta ba, ko da kuwa motsawar 
kawai zai tsira ba tare da sun tasirantar ba. 
Duk 
da za ta iya karyata kanta cewa ba sa 
tasirin 
wanda su suka kawo ta matsayin da ta tsinci 
kanta a yanzu,na yana ja tana ja. 
Abdulwahab da 
ya gaji da jiran cewar ta yana kuma so ya ji 
ta 
bakinta sai ya kuma kalato ta. "Sannan ya 
ce ayi 
miki sannu da jiki". Ta kokarta da kyar da 
tarin 
kwalla a idonta ta ce. "Na gode". Ta ci gaba
da 
sharar kwallar wadda ta faru sakamakon 
tuna. 
Maraicinta da ta yi ta kowanne 
bangare,kamar jin 
jiki tare da rashn mai tattali da tausasan 
kalamai. 
Sannan ga jin jiki na rashin mataimaki a 
ayyukan 
gida, wanda take fama jar da na Allah ya 
tsine,kuma duk a lokacin da ta fi bukatar 
mai 
caring din da kuma mai taimako da aikin. 
Ta 
dinga share kwallarta tana kuma 
sharewa,abin da 
kuma ya kara daure kan Abdulwahab ke 
nan,Ya 
shiga sassanyan nazarin da ya ke a kanta. 
Da ya 
kasa canka kawai ya cika su da kudi masu 
kauri 
ya yi sallama dasu ya fita. Ya tafi da 
tsananin 
mamakin yadda aka yi abdullahi ya samu
nasarar 
auren wannan 'yar darun ta Alh wadda 
kuma Alh 
ya dauki dakkan so da fatan duniyar nan ya 
dora 
mata,har bayan Allah ya kaddari rabuwarsu. 
A 
lokacin ya halarci aikin hajji daga sudan 
inda 
yake karati,kullum sai Alh ya yi masa waya 
yana 
rokon ya yi masa addu'a Allah ya dawo masa 
da 
fatima. Sai dai gaskiyar maganar ya yi 
matukar 
murnar aurenta da kaninsa abdullahi,dan 
tuni ya 
tsufa da sanin tarangahuma abdullahi a 
kwarewa 
da gudunar da mulki,wadda yake yi da 
karfin 
zuciya da na kwanjinsa, wadannan ne kuma 
za 
su ba shi damar iya shugabantar 
kasaitacciyar
mace kamar fatima. Wannan gabar ce kuma 
ta 
ankarar da shi tantamar anya babu sanya 
hannun 
Alh cikin sakacewar da aka yiwa abdullahi? 
Lallai 
biri ya so kama da mutum,dan haka ya yi 
alkwarin binciko gaskiyar al'amari. Ya fara 
da 
neman wayar Alh tun a daren ranar,amma 
duk









