Showing 3001 words to 6000 words out of 8856 words
Chapter 2 - DAN ALHAJI COMPLETE by his eccellenciy.txt
abin na neman tarwatsa masa zuciya waya ya dauka ya kira ta cikin sanyi murya tace "HELLO"! yace ke baki san ki yiwa mutum laifi baki bashi hakuri sai kawai ki share ni tace kai baka gane ba bani da wani laifi bacin ran iyaye na nake gudu dan ban son bacin ransu kokadan.{hmmm matan kwarai kenan amma banda na zamani}
.
maganar ta doki zuciyarsa sosai yace shikenan sankin ganni gobe tace Allah ya kaimu bai masa ba ya kashe wayar hannun yasa ya dafa kumatunsa yana tunanin maganar data gaya masa jikinsa yayi sanyi yace laalle wanan yarinyar wato dole ta guji bacin ran ubanta amma ni akanta na sakawa nawa iyayen bacin ran a kanta na dauke kafana daga gidanmu sai alhaji ya tau tsawon kwana bakwai bai sani a idonsa ba idan abin ya dameshi sai dai ya kirawoni a waya shima dakyar nake amsa maganar sa duk saboda ita zuciyata ta ringa zuga shi kawai ya dauki shawarar abokanansa idan kuma ya tuna da son da yake mata sai yaga hakan bai dace ba gwara ya bari ta zama mallakin sa yayi niyar ya share ta kar ya kuma zuwa gurin ta hakan ta faskara,
.
daukar mota sa yayi ya ratsa ta majalisa anan ma sun yaudare shi ya ki,ya zare jikinsa yace to zan tafi wajen ginbiya yana bala'in basu mamaki da shagala irin ta DAN ALHAJI yanzu yarinya karama ta dauke masa hankalinsa yafi tsohon minti goma bai sami yaron da zai aikaba yana daga idonsa suka hada ido da ita ta fito daga kusa da gidansu da kamal a hanninta yana kuka kayanda tsa sunyi mata kyau shirt da riga nena material ta yafa dan kwali a kanta ganin safuwan taji gaba daya gabanta ya fadi ba karamin dadi tajiba bata bari yagane ba fuskarta ba yabo ba fallasa ya mika hannu ya karbi kamal ya sake barkewa da kuka yamika shi tasa hannu zata karbe shi dan kwalinta ya sullube sakar baki yayi yana kallon gashinta har baya bashi da maraba dana india gashi rigar tayi bala'in fito da suran jiikinta haba ganin hakan yasa shi ya direrece ta lura da hakan tayi sauri ta shige gida har ta dawo sam bai san tana tsaye ba ya shiga duniyar tunani.sai da ta dan daki murfin motar sannan yayi firgit tace tunananin mai kakeyi haka?
.
yayi murmushi yace tunanin naya wuce naki na ga kin zama mallakina tace kar ka sami damuwa insha Allahu kamar yaune haka sukayi ta hiransu cikin faranta zuciya a hanyarsa ta zuwa gida ba abinda yake illa tunanin surar da Allah ya bata a gaskiya gani yake idan ya sameta yafi kowa sa'a ya buge siteri yace ai ni indai na sami wanan yarinyar ba kuma wata yarinyar da zata bani sa'awa a rayuwata wani tunani ya fado masa sai daya ji bugun zuciya wani tsoro ya bayyana a fuskarsa tunawa yayi anya mallam nasiru zai bashi yarsa idan yayi bincike ya gano halinsa dana mahaifinsa na kin talakawa idan ko ta bincike ne a gaskiya bazan sameta ba a halin irin na mahaifinta mai ra'ayin rikau saboda duk wanda ya kwana ya tashi cikin unguwarsu ba wanda bai san tabargazar da sukayi da shi da abokinsa ga kuma halin da yake ciki shi da alhaji har yanzu yana kan bakarsa ta bai yarda ya aureta ba ko jiya sai daya dada jadda masa akn ya samo ko yar wacece indai ya amsa sunansa na mai kudi yanuna masa indai bai aureta ba zai iya shiga wani halin tatshin hankali yana gama wannan tunanin duk saiya ji ransa ya baci ji yake kamar zuciyarsa zata fashe ta warwatse gaba daya a daddafe ya ringa tukin har yazo gida d kyar yana shiga cikin gidansa firiji ya zarce ya bude ya dauko kwalban barasarsa bai tsaya tsiyayawa ba kwalbar ya daga ya tittila a cikinsa sai da ya tabbatar da ba komai a cikin kwalbar sanan ya jefar ya samu waje ya zauna idonsa ya kada yayi jajawur saboda tsabar bacin rai.
*** DAN ALHAJI 5 ***
.
ya saka wata kara yace DAN ALHAJI kace ka komo ruwa kenan? yace tsindim dan jiya zuwa yau tima ta shayar dani da. suka bushe da dariya" safuwan yace inna son ganinka akwai magana yace gani nan zuwa dama ina kan hanya zuwa gidan ke neni da mubashar suna gama wayar sulaiman ya daki kujera yace waya ce maka ana yiwa bariki fitar gaggawa mubashar yace DAN ALHAJI kenan, sulainman aa guje ya fada kan DAN ALHAJI yana cewa WELCOME TO BARIKI (Allah ya sawwaka dai) safuwan ya saki wata wawar dariya yace aini yanzu na zama bokan bariki yau wata goma dai na barta firij ya nufa ya balle kwalba ya tuntula safuwan yace ba'ayi bani ba mikomin haka dai suka ta yin kayan shirme shirme , mubarshi yace ya mutumiyar safuwan?
.
yace tananan da ai a kanta nake cewa zamuyi wata muhimmiyar magana ni fa ina ganin aurena da ita ba mai yuyuwa abne sulainman ya karkata hula ya ce kai kace kai da kan ka mutu ka raba kai da ita ku shawota can kai da ita kai da nasan iskancinka baka rabo da halin ka ka tsya muyi magana ya kakr gani yanzu za'ayi yace wannan maganar da muka gaya maka a majalisa itace abinyi ya nisa yace nifa yarinyar kwarjini takeyi min kasan duk tsawon lokacin da mukayi ban taba tabata ba ko da hannunta ba kuma kasan ban taba sati da yarinya ban san taba.a gaskiya ina son yarinyar dan haka bana son taba mata rayuwa tace to dan gidan rufaida ai ka zuba ido kanta kana kallonta kana hadiyar yau kana gani wani zai zo ya dauke ta tsawon minti goma ba wanda yayi magana yace to ni ya zanyi na shawo kanta?
.
suka hada baki suka ce ya kake yi da sauran yan matanka" munarshir ya kama kunnensa ya rada masa wata magana yace kwarai da gaske suka dau dariya gaba daya suka tafa gaba daya sulainman yace kabar min komai a hannu na kai dai ka dauke kafarka kwana biyu ka kuma hakura da yi mata waya ko da kuwa ta kiraka a waya ka kaheta ku dai ku bani lokaci dana daukar maka za kaga aiki da cikawa ya girgiza kafadarsa yace Allah ya kaimu gaba dayan su suka amsa da ameen ni dai nace allahumma a'a kwana biyu bata ji duriyarsa ba hankalinta ya tashi soasai ko ta name shi a waya baya dauka ta ringa turawa da message amma shiru ba amsa ba karamin tashin hankali ta sake shiga ba abin duk ya biya dameta ta ringa tunani anya lafiya kuwa ita dai a iya sanin ta ba abinda ya shiga tsakanin su shihowar wani yarone ya katse ta daga tunanin wanda ya zame mata abincinta a kullum yace "Assalamu alaikum wani ana sallama da rufahda inji wani a waje dakwa tayi kamar bata jiba umminta tace baki ji abinda yace bane? tace iye iye? tace ana kiranki a waje ki leka ki gani mana tace jeka kace wane ne?
.
yarobya dawo yac sulainman ne abokin safuwan wani tashin hankali taji ya dada karuwa ta tabbata ba lafiya ba.tana fita ganin sulaiman yasa ya taji wani faduwar gaba ta karasa inda yake suka gaisa duk ta matsu taji halinda safuwan yake ciki yace baki tambayeni mutumin kiba? tace shine abinda nake so ji yace to mutumin an binciko file dinsa ta dafa kirjinta tace bashi da lafiya mai ya same shi? wallahi zazzabi ne oai zafi ya kamashi ko abinci baya ci a gaskiya zazzabi bai kama shi da wasa ba shine naga ya dace na zo na sanar `a ke dan kar kiji shiru tace hakan yayi kyau na gode shi kuma Allaj ya bashi lafiya yana gida ne ko .......?
.
yace a'a suna da likitansu a gida shi yake buba shi gashi bansan gidan su ba inji ta sulainman yace gidansu ba boyayye bane ko kuma kar na baki wahala kawai ki gaya min ranar da zaki sai na zo mu tafi tsaya na baki lambata idan kina da bukatar hakan sai ki neme ni tace ba damuwa in haka ta taso na neme ka sukayi sallama ta shige gida ta sanar da ummin ta safuwan bashi da lafiya sosai shine abokinsa yazo ya gaya mata habiba tace aiya shi yasa kwana biyu baya zuwa Allah ya bashi lafiya tace ummi dan Allah ki barni naje na duba shi tace kin san dai bazan mu tunkari abbanki da wannan maganar ba ta sake sasaauta murya ummi har naje na dawo ba tare da ya sani ba tare da halima abdullahi ta raka ni hakan yayi kyau sai ki shirya ku tafi nan da nan ta shirya cikin wani leshi madan karen kyau gashi ta tsara kwalliya mai daukar hankali tayi kyau sosai abinka da kyakywa ta sake tsokano shi ita da kanta da ta duba madubi sai data firgita gashi kayn fitet ne ta dauko mayafi ta yafa tana fitowa umminta tace baza ki tafi a haka ba ita kanta kyaun rufaida ya firgita ta duk dacewa kamar su daya sai dai ta fita haske.ta koma daki ta kuma duba madubi ta tabbatar umminta tayi gaskiya kamar ta cire sai wata zuciyar taba ta shawarar dora after dress akan kayan ta after dress mai ratsn ja gashi jan less ne ta saka zaka zata wata yar india ce tafito tace ummi haka yayi?
.
tace ko kefa to je ki daki ki dauko min wannan karamar jakata ta dauko ta mika mata ta dauko kudi naira dubu uku tace ki sai masa kayan dubiya tace mai zan sai masa? tace abinda kika gaya dace ta rataya jakarta tace sai na dawo habiba tace af! kin kira habiba a wayar kin ji tana nan?
*** DAN ALHAJI 6 ***
.
Na manta bari in kira ta ta dauko wayar ta a cikin jakarta ta kira halima sau uku shiru wayr taki shiga ummi kin ji wayar taki shiga ina ga maysalar bata da cajine bari naje gidan suna gani tace to dai dan bata anan ki dawo kar ki tafi ke kadai kuma ku kula da kanku ku tsare kan ku ku kila da mutuncin ku ku dawo da wuri kafin ya dawo tana zuwa ta tarar gidan su halima a rufe jikinta yayi sanyi tasan uma idan ta koma gida shikennan babu tafiya gashi ta matsu taga yadda jikin nasa yake da dade tana tunani ko ta koma gida ummi baza ta barta ta tafi ita kadai ba uma gashi batsan ranar dawowar su halima daga garinsu ba indai kika ga sun kulle gidan gaba daya to sun fita gari ta kuma dada sanar da ita sun kusa tafiya gashi bata da wata kawa da umminta ta yarda da ita bare ta dauke ta,
.
sai kawai ta ynke shawarar tayi tafiyarta tana isa bakin kasuwa tayi masa siyayya ta kira sulainman tayi masa kwatancen inda take akayi sa'a lokacin suna gidan safuwan da suka tsara yadda za suyi inta zo a zuciyar sa sai ya ji tausayinta amma ina shedan ya rinja yeshi wani hadaddan lemon kwali suka bude suka zuba wasu kwayoyi masu sa maye suka rufe suka mayar firij ya sami wani shinfideden bargo ya lullubu ya kwanta a kan gado ba wanda zai ce ba mara lafiya bene.ayya Allah sarki rufaida,bai fi awa daya ba ta dawo hayyacinta a gigice ta tashi ta ganta akan gadon sa wata kara ta saka marar misaltuwa hade da wasu zazzafan hawaye suka ringa fitowa mata tayi zinbir ta mike ta dau kayanta tasa shi kuma ya zuba mata ido yana kallon kyakykyawan surar da Allah yayi mata a cikin mata da banbanci duk iya neman mata irn nasa bai taba gamuwa da irin taba ko tima bata kama kafartaba ya kudiri niyyar kota halin kaka sai ya mallaketa a matsayin matarsa cikin rudani ta juya ta kalle shi tasana mara misaltuwa da tsiya wacce baza dada son komai kama dashi ba tace
.
KA CUCE NI!!! KA YAUDARENII!!! KA BATA MIN RAYUWA!!!! KA CUCI IYAYENA!! KA DAU ALHAKINSU!! KA ZALINCESU!!! ALLAH YA ISA!!
.
kukan da keyi ya sake tsanan ta tacu gaba da cewa sun dauki shekaru da dama suna tarbiya ta amma sa'a daya ta tashi a banza cikin kuncin zucita tace Allah ya isa! tsakanina da kai yadda ka sani cikin takaicin rayuwa in Allah ya yarda kai ma haka zaka kare da sari ta fice daga dakin ta nufi hanyar fita waje
duk tausayinta ya dame shi da na sanin da bata da amfani tashi yayi ya ringa zagaya dakin ya rasa abinda yake masa dadi can hangin jakarta da hanzari ya dauka ya bita ya kwalla mata kira amma ina ko kallo bai isheta ba motarsa ya hau ya bita har titi ya tsaya dai dai inda ta tsaya yace ga jakarki ba tare da kallon shiba tasa hannu ta fisge tayi gaba bitaa yayi da kallo yana cewa ta shiga ya kaita gida yana kallo ta tayi wata mota tayi tafiyarta ta bar tsaye sai ga sulainman nan suka tyaya suna tambayar sa ya DAN ALHAJI da fatan ka rubuce ka wanke ko kallon su baiyi ba yaja motarsa ya barsu a nan tana shiga gida ta tarar umminta na bacci lallabawa tayi ta shiga bandaki ta gama abinda zatayi tata gyara fuskarta sannan ta koma dakin ummi tayi sallama tace ta dawo tace yaya jikin nasa tace da sauki ummi tace ninaji a jikina dk ba dadi shine na kwanta ina kuma halima?
.
tace ta wuce gida ita sauri take wai zasu tafi garin su yau kwana da kwanaki tana cikin bacin rai ta kasa gayawa kowa ta bar abin a zuciyarta yana damuntako baccin arziki batayi ga wani sauyi da take ji a jikinta ta kara razana.kullum sai yayi mata waya data gaji ta babbalata ta watsar duk wani abu da tasan inta kalle shi zata tuna da shi ta rabu dashi kullum yazo sau hudu ko biyar taki fita duk umminta na lura da hakan tace wai ke me yaka hakan to?
.
da taga hakan gudun kar ta takura mata sai taji abinda yake faruwa idan yazo sai tayi kamar ta fita sai ta shige wani daki a sororon gidan ta kifa kanta tana kuka bata zata umminta ta ganta bata shigo daukar itace ba karamin faduwar gaba tayi ba tace me kike yi anan? kuma kukan me kike yi? zaki gayamin abinda yake faruwa ko sai ranki ya baci na lura lura da ke tun ranar dakikaa je duba yaronan kike cikin kunci to me ke faruwa in baki gaya min ba wazaki gayawa? ko dole akace ki saurareshi? ai dama ke kika ce kina sonsa cikin shekar kuka tace ummi ba komai ji nayi bana son sa akwai wani abu haka kawai baka ce baka son mutum sai da dalili shike nan dga yau idan yazo sai kin boye a nan nba kawai kice bakya nan rufaida inkin huce inda rabo sai ku shirya tashi ki shiga gida ta bita da kallo tana murmushi a zuciyarta inadai fada ne irin na saurayi da budurwa nawa akayi aka shirya ta dauki itacen ta tashiga gida itama kawana biyu a tsakanin haka laulayi ya bayyana tashin zuciya da tsirtar da yawu amai da sauran sauransu Rufaida ta fara hankalin habiba ya tashi data lura da halin da yar take ciki tace ke! gaya min gaskiyar abinda yake faruwa dake? yau rabonki da ganin al'adar ki wata nawa?
.
*** DAN ALHAJI 7 ***
.
Tayi shuru ta sake zare mata ido cikin fada tace zaki gaya min ko saina ci miki mutinci cikin raway murya tace wata biyu batasan lokacin data makureta ba tana cewa ni zaki bawa kunya duk irin tarbiyar da muke miki a banza ashe duk wannan abin da suke akan idon mallam nasiru cikin tsawa yace saketa aikin gama ya riga ya gama cikin wata mahaukaciyar tsawa ya sake cewa zaki sake ta ko sai kinyi kisan kai tana sakinta ta fadi a sume cikin gigita akayi asibiti da ita bayan an gama aune aune da dube dube da kuma bugun zuciya da suka gani suka kira mallam nasiru.suka tabbatar masa tana da ciki na wata biyu da kwana goma sannan matsalar duk sanda wani abu ya faru wanda zai fadar mata da gaba zata iya rasa tunaninta in dai ta razana suka sallameta suka bata magunguna a haka suka bar asibitin a sabule bayan sun je gida ne ta tambayita wanda yayi mata ciki bata boye musu komai ba a lokacin a lokacin habiba ta sha fada dan me ta bar ta taje buba wani saurayi?
.
to iyaye mata ayi hattara akan irin wannan tabargazar kobuba saurayi ko zuwa gidansu ko a gaiyace ki party koh gidan aboki,to dai yan mata ayi hattara iyaye musa ido akan shige da fitar yayan mu yan mata a guji karbar abuna shi kona ci a wajen samari,ayi hattara mutunci daya ne idan ya zube rayuwarki ta shiga ibtila'i dan Allah mu kula Allah ya kare mana har kukan dan kan daru YANCIN KU GIDAN MAZAJEN KU.
AMEEN!!!!}
.
gidan Alhaji muazzam ya nufa yayi sa'a ya same shi aja yo masa sallama da shi ba dadewa yana tsaye wanda ya aiki yafito yace wai waye yace kace bako ne yake son ganinsa ya ske dawowa yace an ce ka shigo wani falon alfarma aka shiga da shi yana shiga ya tabbatar alhaji ba karamin mai kudi bane amma hakan bai sa zuciyarsa ta karaya yaji tsoron fadin abin da yake tafe dashi ba suka gaisa yace na zone na sanar da kai cewa dan ka safuwan ya yiwa ya ta fade saboda haka har ciki ya shiga zirbir Alhaji ya mike yace au ta haka kuma ka bullo? kana ganin hakan zai sa na yarda ya aure ta? to tsaya na gaya maka har yanzu ina nan kan bakata ka nemi wannda ya yiwa yarka ciki tun da wuri kuna sakin yayan ku kamar awaki sai sun dauko muku abin kunya ku rasa