Showing 1 words to 3000 words out of 44304 words

Chapter 1 - SULTHANA Complete Document book .txt

09 Nov 2024

4824

ο»ΏCompiled by Umar Dalha.














πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’


By *Ummy Abduol*


*Page 1 to 5*


Yarinya ce da bazata wuce shekara sha uku bah rak'ube jikin katanga cikin duhun dare sai rawar sanyi take, bata ankara bah ruwa ya tsuge kamar da bak'in kwarya. Dasauri ta koma zauren gidan ta samu guri ta k'ara rakubewa dukda zauren yana zuban ruwa hakanan ta zauna tana matsar kwalla a hankali..


Ruwan sama ake tsugawa a garin kamar da bak'in kwarya, dakyar ta sulale k'asa ta kwanta tana Cigaba da rawar d'ari, Haka barci ya dauketa.
Kiraye Kirayen Sallan Asuba taji, a hankali ta gyara kwanciya saboda sai lokacin ta samu barci sosai, bata gama gyara kwanciyar bah taji tokari. Koba'a fada mata bah tasan Baffa neh, dasauri ta Mik'e zaune tana soshe soshe tana k'ara kallan Baffa dak'e tsaye ya hasketa da tochila.
"Dan Uwarki kinaji ana kiran Sallah bazaki tashi bah, waike Wacce irrin dabba ce zaki tashi koh saina mangareki"
Dasauri ta mik'e ta shige cikin gida tana cigaba da soshe soshenta.


Mama ta hango bak'in rijiya tana jan ruwa, ta k'arasa dasauri ta rik'e gugan
"Mama kawo naja mik'i"
D'an murmushi mama tai
"Aa Sulthana barshi, dauko butta na zuba mik'i kiyi Alwala"
Bah musu ta dauko buta ta k'araso bakin rijiyan, dai dai nan hafsatu ta fito daga dak'in barcinsu tana sosa kai dagowan dazatai taga hango mama na zubama Sulthana ruwa a buta
"Lallia ma Sulthana, dan tsabar iskanci mama ce baiwar ki?? Har tana jawo ruwa tana zuba mik'i a buta"


Nan da nan jikinta ya soma rawa dan tasan halin hafsatu sarai, yanzu ta kamata taimata dukan tsiya
"Haba Hafsatu, menene dan nazuba mata ruwa, yanzu tazo zata amsa na hanata"
Saurin K'arasowa wajan Hafsatu tai
"Haba mama ya k'ike irin wannan maganan, Baffa ya gaya mata duk aikin da zata rink'a yi a gidan nan ciki kuwa harda jan ruwan nan, Anma saboda iskanci tak'iyi saike zaki ja."
Hade rai mama tai tana cigaba da kallan hafsatu
"Banasan iskanci, ki wuce kije kiyi Alwala"
Zumburo bak'i tai ta juya ta kalli Sulthana dak'e tsaye kanta a kasa tayi kwaffa tabar wajan..


Mama ta maida dubanta ga Sulthana
"Ga ruwan maza jekiyi Alwala kamin Baffanku ya dawo"
Amsa tayi ta shiga bayi ta kama ruwa ta fito tai Alwalan, dai dai itama mama ta gama nata Alwalan
"Sulthana shigo dak'ina kiyi Sallan kafin Baffanku ya dawo maza ki hanzarta"


dasauri sauri ta sauya kayan jikinta zuwa wata kod'adiyar Atampha dogon riga, Hijabin mama ta sanya ta tada Sallah. Tana Cikin sallan taji sallaman Baffa, Hanjin Cikinta neh ya k'ada dakyar ta k'arasa idar da Sallan ko Addua bata tsaya yi bah ta fito daga dak'in. Hangoshi tai a Bukkan tumakin shi yana zuba musu Abinci, dagowan da zaiyi yaga ta fito daga dakinshi tana yan Rabe Rab'e kanta a k'asa..


"Sulthana! Daga wani dak'i naga kin fito yanzu"
Inda Inda ta soma yi chan sai mama ta fito sanye da hijabi da Alama Sallah ta idar
"Sallah nace tazo tayi"
Mugun kallo Baffa yabi mama dashi
"Sau nawa Saratu zan fada miki ki fita harkar Yarinyan nan anma Kink'i"
Sakin Bak'i mama tai da mamaki tana cigaba da k'allan Baffa
"Haba Mallan sai kace bakai ka haifeta bah, baka tsoron hakki. Yarinyan nan Amanace fah a Wurinka mai yasa Kake ha.."


"Dallah rufemin baki"
Maida Dubanshi yayi ga Sulthana dake tsaye har lokacin kanta a Kasa da Alama kuka take
"Keh kuma tsayuwa kikai kina Karemin Kallo bazakije kiyi aikinda Yakamata bah"
Dasauri tabar wajan ta Nufi kicin dinsu, kwanonin datti ta soma fitowa dasu tana kaiwa bak'in Rijiya tana Ajewa, lokaci lokacin takan share hawayen dak'e gangaro mata a fuska...


*Shin anya kuwa Baffa mahaifin Sulthana neh?"*
Ku biyoni dan jin Cigaban Labarin


*Ummy AbduAbduol✍🏻


πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’


By *Ummy Abduol*


*Page 6 to 10*


Lokaci lokaci takan share hawayen dake gangaro mata a fuska. Saida ta wanke kwanukan tas sannan ta share tsakar gidan tareda daura abin kari. Bayin gidan ta wanke ta Fito tadau Tsintsiya ta nufi dak'insu Hafsatu. A Kwance ta sameta tana barci gefenta kuma ameena ce zaune kan sallaya tana karatun alkur'ani, dan Rusunawa tai
"Ina kwana yaya Ameena"
Saida ta kamalla sannan ta juyo ta k'alleta da murmushi akan fuskanta
"Lapia lau Amal, kin Tashi Lapia"
Kanta na K'asa ta amsa da Lapia Lau.


Shiru ne ya biyo baya na wasu mintina, dakyar amal ta bude baki tace
"Dan Allah Yaya Amina ki tayani tashin yaya hafsatu inaso nai shara"
Batare da tace komai bah ta shiga tashin hafsatu, dakyar ta tashi suka bata waje ta gyara musu dak'in tsaf. Bata gama ayukanta bah sai wuraren karfe bakwai da rabi na safe, baffa ko sai masifa yak'e tak'i ta gama abin karyawa ga yara naso suje makaranta. Koko ta dama ta dafa musu dankalin Hausa, saida ta zubama kowa ta kaimai Sannan ta dau nata ta nufi zaure dashi.


Hafsatu da Amina suk'a leko dak'insu baffa bayan sun gama karyawa
"Mama, Baffa mun tafi"
Da Fara'a yak'e kallansu Tareda sa hannu cikin Aljihunshi, kudi ya Ciro naira Dari biyu
"Gashi ku raba"
Amsa sukai tareda mai godiya Suka wuce. Mama ta Kalleshi Fuskanta bah Walwala
"Mallan Idan nace inajin Dadin Abinda Kakeyi nayi K'arya"
Kallanta yayi da Mamaki
"Meh kuma nayi?"


Shiru tai dan Tasan Halin baffa Yanzu ya zazzage ta dah Masifa
"Keh nake sauraro"
Ta maza tai ta Kalleshi
"Haba Mallan, Baka gudun surutun mutane?? Koda yake surutu ni nake shanta bah Kai bah"
Kallanta yayi da Alamar mamaki
"Ki fito fili kiyi magana bah kwana kwana bah"
Akan Maganan Sulthana mana Mallan, Yarinyan nan batakai shekarunda zata Rink'a wadan nan Aikin bah, Sannan kuma ka hanata zuwa makaranta. Haba Mallan sai kace bakai ka haifeta bah"


Dogon tsaki yaja tareda mik'ewa
"Ina K'ara gaya miki ki fita Akan harkan Yarinyan nan Bah ruwanki"
Itama Mik'ewan tai tana kallanshi da damuwa
"Haba mallan wanne irin bah ruwana, yarinyan nan fah y'arka ce, jininka ce duk inda na zaga kallona ake ana nunani ana zagina akan ina cizgunama yarinyan nan, kowa laifina yake gani"


Gidon tsaki yaja yabar dakin a fusace, a tsakar gida yayi kicibus da Sulthana shigowanta kenan cikin gidan tana tattara kwanukan da aka ci abinci. Dasauri tabar wajan dan k'aramin aikinshi ne ya duketa batamai komai bah. Kwafa yayi ya fita daga cikin gidan a fusace..


Wanene Baffa?


Dan Asalin jahar kano ne a kauyen karaye. Cikakken Sunanshi Mallan Jamilu dan Mallan, mahaifinshi Mallami neh mai tara Almajirai. Shi kadai mahaifinshi ya haifa, bayan rasuwan mahaifinshi ya cigaba da kula da Almajiran mahaifinshi kasancewar shima yanada Ilimi sosai. Ya gaji gado mai tarin yawa wanda idan ana lissafin masu kudin kauyen zai zo saahu na biyu ko na uku.
A Haka Allah ya hadashi da Rabiatu yarinyar wani buzu da sukazo Cirani nigeria, Shida Rabi sunyi auren soyaiya da Kaunar juna. Sun shafe shekaru masu tarin Yawa har Mallan Jamilu ya sak'e Aure inda ya auri saratu, aurenta da shekara daya ta haifo Amina, bayan Shekara biyu ta K'ara Haifo Hafsatu. Rabiatu da Saratu sunyi zaman lapia sosai wanda ba wanda kejin Kansu duk da kuwa bah Gida daya suke zaune bah. Hafsatu nada Shekara biyar Rabiatu ta Samu Ciki, Cikin Ikon Allah ta Haifi Yarta Ranar Suna Ita da Kanta tasa mata suna Sulthana wato (Sarauniya)


Sam Mallan baiyi Farinciki da Haihuwan nan bah, Tun a Sannan Rabiatu ta fara Fuskantan Wulakanci da Cin Mutumci gurin Mallan, Sulthana nada shekara Sha Biyu mahaifiyarta Allah ya mata Rasuwa ta sanadin Ciwon zuciya wanda Mallan Yak'i kula da ita har Allah ya dauki rayuwarta. Bayan Rasuwan mahaifiyarta Mallan ya dawo da ita gidan d'ayar matarshi Saratu, inda Ya hana sauran yayanshi kowane aiki sai Sulthana, mama wato Saratu na matukar tausayama halinda take ciki itada Aminatu. Mallan Ya cireta a makaranta wanda dama ummanta ce ta sata, ya hanata Hulda da kawayenta, Gashi yan uwan mahaifiyarta bah a kasan suk'e bah..
Wannan knan.....


*Ummy Abduol✍🏻*
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’


By *Ummy Abduol*


*Page 11 to 15*


Wannan knan..


Kwanaki sunja Sosai, Kullum Sulthana Fuskantar Wahala wajan Baffanta tak'e, sai in baya gida tak'an danji dadi wajan Mama ko Ameenatu.
Zaune Tak'e tana tsince Shinkafa lokaci lokaci takan sah bayan Hannunta tana share hawayen dak'e Gangaro mata, Baffa neh ya fito daga daki yana K'allanta
"Bah Rashin Lafiya bah Allah Yasa mutuwa zakiyi sai kinyi Aikin nan, Dan tsabar iskanci harni zaki duba kice bakida lapia"
Ameena ce ta fito daga bayi hannunta rik'e da buta
"Baffa dan Allah kai Hakuri, na Yarda ni zan mata aikin na yau"
Kini kini yayi darai
"Ban yardah bah kuma ban lamunta bah, Karna Sak'e na ganki kindau Tsinke a cikin Gidan nan. Anfaninta knan Ki Barta tayi"
Bai kara cewa komai bah yayi shigewansh dak'i..


Hafsatu ce ta fito tana dariya mai sauti harda rik'e ciki
"Yaya Ameena knan, menene na takura kanki kan Wannan Kuchakan Yarinyan, Nifa Wallahi na Tsaneta Shegiya sai kyau kamar Aljanna"
Dogon Tsaki Ameena taja batace Komai bah Ta wuce dakinsu, Binta da Kallo Hafsatu tai Sannan ta maida dubanta ga Sulthana
"Yarinya Koh kukan jini zakiyi sai kinyi Aikin nan, kima gama kizo ki wankemin Uniform"
Batace Komai bah ta Cigaba da Tsintar shinkafanta..


Dafa Dukan shinkafa ta dafa Musu, Saida ta zubama Kowa Sannan Ta kankare K'anzon ta juye a Leda Dan Ko kwanukan Gidan Baffa ya hanata Anfani dasu, Zaure ta nufa wanda a yanzu ta maidashi kamar dak'inta, Muryan Baffa taji yana Kiran Sunanta
Dasauri ta Sak'i ledan K'anzon ta nufi wajanshi tareda Durkusawa
Kwano ya ajiye mata a gabanta cike da Gyada Danye
"Maza ki Wanke shi ki daura a Wuta dan Yau zaki fara min Talla"
Dasauri ta Dago ta K'alleshi da Mamaki
A ranta ta maimaita "Talla"
Mama ta Fito Dasauri jin Abinda Ya Ambata
"Haba Mallan, Wallahi kaji Tsoron Allah bai kamata kana irin Wannan bah, dur Arzikin dah Allah ya maka kace kuma zaka Rinka daurama Yarka Talla"
Baice Komai bah Ya Kalli Sulthana
"Zaki dau gyadan ko saina B'aballaki a nan"


Da Sauri jiki na Rawa tadau Gyadan ta Nufi Bakin Rijiya Hawaye na Gangara a Idonta, Runtse ido tai jin Kanta Na Sara mata, Dakyar ta Wanke Gyadan ta Hada wuta ta daura ta koma Gefe tana Dubawa, Jin Zazzabi na neman Rufeta Yasa ta Mik'e dakyar ta shiga dak'insu Ameena gabanta na Faduwa
Tako ci Sa'a Hafsatu Bata Dakin
"Dan Allah Yaya Ameena ki taimakeni da Maganin Ciwon Kai"
Kallanta Ameena tai cikeda Tausayawa
"Kiyi Hakuri Sulthana, Duk Tsanani Sauk'i na nan Zuwa Kinji"
Kai Kawai ta Gyada batare da Tace Komai bah. Maganin Ameena ta bata Da Ruwa Tasha Sannan tai mata Godiya tabar dakin..


Saida ta dafa Gyadan ta Juye Sannan Tayi Sallama dak'in Baffa, Fitowa Yayi
"Yauwa Kin Gama?"
Kai ta Gyada Kanta a Kasa
"Maza ki juye a Faranti ki dauka ki Shiga Gari, Kuma Wallahi idan Kika Dad'e Nida Keh neh, Sannan gwangwani naira Goma"
"Tho" Kawai tace tabar Wajan, Gyadan ta Dauka ta Dau Hijabinta daya Sha Miya da kura tasa Kafanta ko Takalmi babu tabar Gidan. Tafiya kawai take batareda Tasan Inda zata nufa bah dan Talla Bakon Al amari neh a wajanta, Kicibus sukai da K'awarta Sadiya Tana Dawowa Daga Islamiya, Turus tai da Mamaki tana K'allan Sulthana


"Yau Kuma meh idona keh Gani Sulthana, Talla??" cewar Sadiya
Dan Murmushi Kawai Sulthana tai Tana Kokarin Wucewa, Hijabinta Sadiya taja Hakan Yasa Ta Tsaya batare da ta juyo bah, Gabanta Sadiya taje ta Tsaya tana K'allanta
"Sulthana Nice Fah Sadiya yau kuma Hanaki Magana da Kowa akai"
Dakyar ta Iya bude Bak'i Tace
"Dan Allah Sadiya kiyi hakuri ki bani hanya na Wuce, Wallahi Ance idan na dade sai an Dukeni"
Nan da Nan idonta ya cik'o da kwalla..


Jan Hannunta Sadiya tai duka koma Gefe
"Kiyi Hakuri Sulthana, Banajin Dadin Yanda Nak'e Ganinki, Inasan Zuwa wajanki Anma ina tsoron Kar Baffa yamin Fada koya Dak'eni, Kinsan meh?"
Kai Sulthana ta Girgiza Alamar Aa
Kullum da Daddare Zan Rinka kawo Miki abinci a zaure ko in Rinka turo Sani yana kawo miki
Murmushi Sulthana tai Wanda Saida Dimple dinta Masu K'ara mata kyau suka Bayyana
"Nagode Sadiya"
Itama Murmushin Tai, A Haka Suka Rabu Cikeda Kewar Juna.
Rasa Inda Zata Nufa Tai, Yanke Shawara tai ta Nufi Bakin Kasuwa da Gyadar, Cikin Ikon Allah Nan da Nan koh aka siye ta dawo gida. Baffa ta mik'a mah kudin Yanata Washe bak'i
"Yauwa haka Akeso, Gobe mah zak'i sake dafawa"
Mama na gefenshi sai K'allanshi tak'e Cikeda Takaici.
Koh hutawa batai bah Ta daura Aikin da yakamata tai na yanma, Bata Gamaba Saida Aka Fara Kiraye kirayen Sallan Isha'i. Alwala tai Ta koma zaure tai Sallanta tana zaune Hafsatu ta shigo Gidan Tana Wani Girgiza tana Waka
Mama dake tsakar Gida Ta K'alleta da Alamar Mamaki
"Hafsatu daga ina Kike? Tunda Akai Sallan Azahar kika Fita Gidan nan sai yanzu kike gadaman Dawowa"
Turo Bak'i tai ta Turo dan kwalli Gaban Goshi
"Haba Mama ni shiknan banida Yancin Kaina Duk inda Naje Sai aita Tambaya nah"
Ameenatu ta Fito daga dakinsu Sanye da Hijabi da Alama Sallah ta Idar
"Hafsatu Ashe Bakida Hankali, Yanzu Mama kike gayama Irin Wannan Maganan??"
Batace Komai Bah Tadau Buta Tayi Shigewanta Bayi tana Magana K'asa K'asa


*Ummy Abduol*✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’


By *Ummy Abduol*


*Page 16 to 20*


Batace Komai bah tadau buta tayi shigewanta bayi tana Magana Kasa kasa. Girgiza kai kawai mama tai batareda tace Komai bah, Wuraren Karfe tara na safe Lokacin Baffa ya shiga gida Sadiya ta shigo zauren dauke da kwanon Abinci. Da fara'a Sulthana ta tareda suna dan hira K'asa kasa Tanacin Abincin
"Sulthana kin daina zuwa makaranta, bah Islamiya bah Boko Kullum sai Mallamai sun tambayeni keh"
Dan murmushin takaici Sulthana tai
"Baffa ya hanani zuwa makaranta, ko dah chan dama umma ce keh biya min"


Hawaye ta share tana cigaba da kallan Sadiya
"Bansan menai ma baffa bah, Ni kadai a Garin nan nake shan wuya bansan menai bah"
Kuka neh yaci karfinta, Sadiya ta rungumota K'irjinta ta shiga Lallashinta
"Kiyi Hakuri Sulthana, ko kin manta Karatun dah Mallan Dauda ya mana, Innallaha Ma'a Sabirin, Allah yana Tareda masu hakuri"
Shiru Sulthana tai tana cigaba da kukan K'asa kasa
"Ki daina kuka kinji, Kinsan menene?"
Kai Sulthana ta girgiza Alamar Aa
"Gobe idan Kikaje Gaida Baffa ki kara mai magana akan Makarantan ki, idan Allah ya dauraki a kanshi zai yarda"
Kai Kawai Sulthana ta daga batare da tace komai bah..


Mikewa Sadiya tai,
"Zan tafi gida kinga dare yayi gobe ma zan dawo kinji"
Kai Sulthana ta daga mata tana murmushi, Sauran Abincin da ta rage ta juye a kwano ta mik'a mata kwanon
"Nagode Sadiya ki gaida Goggo"
Zataji cewar Sadiya ta Fita daga zauren Cikeda Tausayin Kawar nata..


Washe Gari ana Sallan Asubah tahau Aikin Gida, Baffa na dawowa ta Karasa kusa dashi ta gaidashi, Bai amsa bah saima tsaki dah yayi ya bar wajan ya shige dakinshi. Komawa tai ta cigaba da Aikinta kamar yanda ta saba, da wuri Ta gama ayukan tah tana zaune bak'in murhu dan lokacin ana dan sanyi
Hafsatu ce ta fiti daga daki tana mik'a
"Keh Sulthana, Maza dauramin Ruwan wanka"
Tho tace ta mik'e dan Daurawa jin Muryan Amina tai tana cewa
"Karki sakeki daura wani ruwa, Idan bazata daura da kanta bah tah bari"
Da Mamaki Hafsatu ta Kalli Ameena
"Haba Yaya Ameena, Makaranta fah zani ki kyalleta ta daura min mana"
Murnushin takaici Ameena
"Hafsatu ki tausaya mah yarinyan nan mana, duk aikin gidan nan ita tak'eyi yakamata ki tausaya mata"
Tsaki Hafsatu taja
"To ni ina Ruwana, Ai bani kesata aikin bah, Baffa neh dan haka ni bah ruwana"
Jin Hayaniya a tsakar Gidan Yasa Baffa ya fito
"Lapia meke faruwa neh naketa jin hayaniya"


Shiru Ameena tai tana Muzurai, nan da nan Hafsatu ta maida bayani. Baffa ya Kalli Ameenatu da Mamaki
"Lallai Ameenatu, Wuyanki ya Isa yanka, Tho bari kiji Baki isa ki chanzamin Abinda nai niya bah. Wallahi Ameenatu ki fita idona in rufe"


Bataco komai bah kanta na Kasa, Sulthana tun fitowan baffa ta hau kiciniyar Daura ruwan, yana waigowa yaga ta daura yayi kwafa ya koma daki abinshi. Mama najin ya shiga dakinshi Ta fito tana kallan Ameenatu
"Ameenatu kisa ido kamar yanda nasa, Allah bah Azzalumin Bayinsa baneh"
Kai Ameenatu ta gyada batace komai bah
"Keh bazaki makarantan baneh" cewar Mama
"Aini jiya muka zana jarabawanmu na k'arshe"
Dafe Goshi Mama tai tana Murmushi
"Oh na manta, Tho Allah yasa An gama Makarantan a sa'a"
Ameen Ameenatu tace ta wuce dakinsu Cikeda Takaicin Abinda Baffa yakeyi..


Ruwan nayi ta sauke ta surka mata takai mata bandak'i sannan taje ta Sanar da Ita. Tana fitowa ta tsaya bak'in Kofar dakin Baffa Gabanta na bugawa cikeda Tsoro, Daurewa tayi tai sallama a bakin Kofar dakin, Fitowa Baffa Yayi yana k'allanta
"Menene"
Dan Jim Tai Jikinta na rawa
"Keh nake Saurare"
Duk'ar dakai tai sannan tace
"Dan Allah Baffa inaso na cigaba da Zuwa makaranta"
Bude Baki Baffa yayi da mamaki yana K'allanta
"Lallai na Yarda Bak'ida Kunya Sulthana, Ki Kalli tsabar Idona Kice Makaranta Kikeso ki Koma"
Jin Daga Muryan Baffa Yasa Mama dasu Ameena suka Fito
Kara Kallanta yayi rai bace
"Ki Sani Kin Gama zuwa makaranta, keda makaranta har Abada kisan wannan"
Kuka sosai Sulthana tahau yi
"Zakimin Shiru koh sainq zaneki a nan wajan"
Nan da nan ta hadiye Kukan sai hawaye datake fitarwa


Mama ta Kalli Baffa itama Rantq Bace
"Wallahi Mallan Karinka jin Tsoron Allah, Bai Kamata Masani kamarka yana irin wannan bah, Ya Za'ayi ka hanata Zuwa makaranta kuma gasu Hafsatu na zuwa"
"Saboda su yadace suje makaranta bah ita bah" cewar Baffa
Tsaki Hafsatu tai tadau kwandon Soson Wanka tai shigewanta bayi.
Murnushin takaici kawai Ameenatu tai itama ta koma dak'i,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login