Showing 30001 words to 33000 words out of 44304 words

Chapter 11 - SULTHANA Complete Document book .txt

09 Nov 2024

4827

bama muba har y'ayanmu"


Hawaye ne suka gangaro daga idon Hafsatu


"Haka neh ya Ameenatu, tho menene dalilin Baffa na cewa Sulthana bah y'arshi bace"


Girgiza kai Ameenatu tayi


"Ki cire wannan Maganan a ranki, bah gaskiya baneh wannan"


Hafsatu ta mik'e tana share hawayen Fuskanta


"Yaya Ameenatu yanzu ya zamuyi? Gashi Baffa ya koreta"


Itama ta mik'e tana cewa


"Zamu fita neh nemanta ta dawo gida mu zauna mu nunama Baffa rashin Amincewan mu akan abinda yake mata"


D'aukan Hijabi hafsatu tai suk'a fito tsakar gidan, a nan suka samu Mama zaune tayi tagumi, basuxe komai bah suka fita suka soma nemanta.


Duk inda suke tunani Sulthana zatace bah inda basu jeba anma duk maganar d'aya ce batazo bah. Hankalinsu bah k'aramin tashi yayi bah, koda Suka samu Mallan sani Aminin baffa da maganan bah K'aramin Mamaki yayi dajin abinda Baffa Yayi bah.


Sadiya sai kuka take jin k'awarta ta bata, haka ma Mamanta ta shiga Cikin tashin hankali sosai. Ganin hadarin dake garin yasa suka dawo gida duk'ansu jikinsu a sanyaye. Tun daga nesa suke hango Almajirai tsaitsaye a kofar gidansu, dasauri suk'a karasa aka matsa musu suka shiga cikin gidan. Nan ma mutane suka gani zagaye, Hafsatu ce ta k'usa ganin Baffa tayi kwance kan tabarma yana numfashi Sama sama Mama na kusa dashi tana kuka..


Hankali tashe Hafsatu ta shiga tambayan meya faru, Mama ce ta bata amsa da cewa


"Wai a bakin Masallaci ya fadi shine aka kawoshi gida"


Ameenatu ta k'araso wajan ta tsugunna kusada Baffan itama tana hawaye


"Allah gamu gareka, idan Laifi mukai maka Allah ka gafarce mu. Mun tuba, Mun tuba.."


Kuka take sosai tana k'allan Baffa dake kwance rai a hannun Allah. mutanen dake wajan kowa ya watse aka barsu su kadai sunata kuka..


Da taimakon Babban Almajirin Mallan da wasu almajirai aka shiga dashi d'akinshi saboda hadarin dake garin..


Magani aka hau yima Mallan Anma kamar ba'ayi, mallan Sani duk inda yaji Mallami sai ya nemoshi ko ya amso maganin Anma Abin dai gaba yake. Su Ameenatu da Hafsatu idan ka gansu gwanin ban tausayi, abu ya hadu musu biyu ga rashin Sulthana ga rashin Lapian Baffa...


Mallan ya koma kamar bashi bah ko magana baya iyayi, idanunshi kullum a bud'e yana k'allan sama komai saidai aimai baya iya komai... _niko Ummy Abduol cewa nai Allah ya k'ara_




Fareeda yayi Parking a haraban gidanshi ya d'an kalli sulthana daketa bin Gidan da Kallo


"Muje koh?"


Bah musu ta bud'e kofan motan kamar yanda taga yayi dazu ta fito shima ya fito suka nufi cikim gidan. Kofan main palour ya bud'e Ya shiga Sulthana na biye dashi, zama yayi kan Kujera ita kuma ta zauna k'asa kan Carpet ta makure tana bin Falon da Kallo cikeda kauyanci


"Meyasa kika zauna a k'asa tashi ki zauna kan kujera, ki saki jikinki ki rink'a min magana kinji"


Kai ta d'aga ta mik'e ta zauna k'an kujera tana cigaba da bin Falon da k'allo. D'an dariya yayi k'asa kasa yace


"Falon ya miki kyau neh?"


Murmushi tayi wanda saida dimples dinta suk'a lotsa. Kallanta ya tsaya yi ganin irin kallan dayake mata yasa ta duk'ar dakai. mik'ewa yayi yaja Trolleyn kayanta Yana cewa


"Taso na nuna miki"


Bah musu ta mik'e tabi bayanshi, wani bedroom dake hannun dama ya bud'e ya shiga juyawa yayi bai ganta bah ya lek'o ya ganta bakin kofa tsaye yace


"Shigo mana"


Zuciyanta na bugawa ta shiga dakin, wow tace a ranta dan tunda uwarta ta haifeta bata taba ganin daki mai kyau irin wannan bah. Murmushi ya mata ya kamo hannunta ya zaunar da ita kan katafaren gadon dake dakin


"Meyasa kike d'ari dari dani neh. Bazan cutar dake bah, daga yau nan neh dakinki"


Batasan lokacinda ta saki lallausan Murmushi bah har saida Fararen Hak'oranta suka baiyana


"Dagaske?"


Shima murmushin yayi dan Yaji dadin yanda tad'an saki ranta. Gani yayi kuma ta bata fuska tana k'okarin kuka, hankali tashe yace


"Menene"


Bai ankara bah ta fashe da kuka tana shesheka


"Shiknan bazan koma gidanmu bah? Meyasa Baffa baya sona. Dan Allah kaje ka bashi hakuri idan namai laifi neh, ni y'arshi ce"


Tausayi ta bashi ya zauna kusada ita tareda rik'o hannayenta


"Ki daina kuka, insha Allahu nan bada dad'ewa bah komai zai daidaita zaki koma wajan Baffanki kinji"


Kai kawai ta gyada tana cigaba da matsar k'walla. Kawar mata da damuwan yayi ta hanyar cewa


"Tashi na nuna miki yanda ake anfani da komai"


Bah musu ta mik'e tana binshi a baya, da cikin d'akin suka fara sannan suka shia toilet nan ma ya nunnuna mata suka fito zuwa sauran sauran wurare dake cikin gidan..


Ummy Abduol✍🏻


💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐


By *Ummy Abduol*




*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*


_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_


*Page 166 to 170*




Kwanan Sulthana Uku a gidan Fareed, Kullum cikin tunanin Y'an uwanta take dakuma Masoyinta Masroor, takanyi kuka idan ta tuna koranda Baffa ya mata da kuma gudunta da Masroor yayi. Har yanzu sanshi da kewanshi na mak'alle a zuciyarta, bah lefi cikin kwana ukun sun d'an saba da Fareed yakan jata da hira duk da ba wani amsan kirki take bashi bah.


Aranan na hudun Sa'ood yazo gidan suna zaune a falo suna hira Sulthana na dak'i tana barci. Sa'ood ya nisa yace


"Magana nakeso muyi dakai Fareed"


Gyara zama Fareed yayi Sannan yace


"Ina jinka"


Sa'ood ya soma magana yana k'allan Fareed


"Zamanka da mace ku biyu bah abu baneh mai kyau, shedan ake gudu."


Ajiyan zuciya Fareed yayi


"Gaskiya neh Sa'ood, saidai kasan Matsalan Ummah bazata taba yarda Sulthana ta zauna da ita ba kuma ma kagani yanzu bah zama take bah"


Shiru Sa'ood yayi yana tunani chan yace


"Dole mu nemi mafita dan wannan bah abu mai yuwuwa baneh"


Fareed ya d'ago yana cewa


"Ga shawara"


Sa'ood ya ce


"Ina jinka"


"Mezai hana nasata a boarding school har zuwa sanda zan sanar da Abba da ummah"


Murmushi Sa'ood yayi


"Yes haka ya kamata"


Sun aje akan ranar monday da Sassafe zasu kaita zaria academy dan mata registration..


Abubuwan sunma Yasir yawa gashi kullum sai Masroor ya kirashi akan Zuwa kauyensu Sulthana. Yau yana barin School kauyen ya nufa kai tsaye. Batareda wani d'ar bah yasamu Almajiri yace yamai Sallama da Sulthana. Almajirin yace


"Ai Sulthana ta b'ace ba'a ganta bah yanzu sati uku knan"


Hankali tashe Yasir yace


"Garin yaya?"


Almajirin ya tab'e baki yace


"Nima ban sani bah, andai ce Mallan ne ya koreta."


Ran Yasir ba karamin Baci yayi bah yace


"Mallan din na nan"


Yaran yace


"Ai mallan bashida lapia tun ranar data bace ya fadi a bakin Masallaci har yanzu bai warke bah"


Hannu yasa a Aljihu ya ciro d'ari biyu ya mik'ama yaran yana murmushi


"Gashi abokina nagode"


Amsa yaran yayi tareda godiya shi kuma ya shiga motanshi yabar kauyen Hankali tashe. Yanzu taya zai gayama Masroor wannan mummunan labarin.


Yini yasir yayi cikeda fargaban yanda zai fadama abokin nashi wannan labarin. Yakoyi sa'a bai kirashi bah sai washe gari, da kyar ya dauka suka gaida Masroor yayi saurin cewa


"Yasir kakoje?"


Shiru Yasir yayi har saida Masroor yace


"Kana jina kuwa?"


Ajiyan zuciya Yasir ya saki yace


"Ina jinka friend, naje anma ban samu ganinta bah"


Nan da nan Masroor ya rud'e ya shiga jeromai tambayoyi


"Meyasa baka ganta bah?? Bata nan neh? Ko taje talla?? Pls Yasir yimin magana uh sound strange"


Ta maza yasir yayi ya zaiyanema Masroor duk yanda sukai da Almajirin daya samu a kofar gidansu Sulthana. Wayan dake Hannun Masroor ne ya fadi hawaye suka cika idonshi, kuka ya saki mai sauti tana kiran sunanta da k'arfi. Neighbours dinshi suka fifito suka tsaya a bakin kofan hankalinsu tashe jin yanda yake kuka da k'arfi yana fashe fashe..


Saida yayi mai isarsa sannan ya mik'e idanunshi sunyi luhu luhu ya shiga toilet yayi alwala ya soma kai kukanshi ga ubangiji _oh Masroor I pity uh_


Washe gari da safe Fareed da Sulthana suna kan dinning suna breakfast kamar yanda suka saba y'an kwanakin. Maganan sata a makaranta ya mata. Tayi farinciki sosai daga baya kuma ta hade rai


"Yanaga kuma kin chanza meya faru?


Rau rau tayi da ido


"Yaya Fareed yanzu shiknan bazan k'ara ganin Mama da yaya Hafsatu da yaya Ameenatu bah"


Goshinshi ya dafa


"Oh God! Sulthana ki cire wadan nan mutanen a ranki su basa sanki kece kawai kika damu dasu"


Hawayen dake makalle a idonta suka zubo tana girgiza


"Ina Sansu Yaya Fareed suma suna sona"


D'an jim yayi ya mik'e yana cewa


"Shiknan yanzu dai bansan kukan, ki shirya gobe da Sassafe zamu tafi. Idan akai hutu saiki je"


Ihu ta saki tana Y'ar Murmushi


"Nagode Ya fareed"


Kai kawai ya gyada ya bar wajan a zuciyarshi yana raya. Lallai rashin kula da gata yasa Sulthana shiru shiru dan yanzu data d'an wartsake ya hango k'iriniya da shagwaba a idanunta..


Washe gari da wuri da wuri suka tashi, da kanshi ya shirya mata kayanta a trolley da duk abinda take buk'ata. Saida ya tsaya a wani babban supermarket yayi mata sayaiyya sosai sannan suka biya ta gidansu Sa'ood ya daukeshi suka nufi zaria..


Bayan gwajinda akai mata Mallaman sukace za'asata a js1 rok'onsu Sa'ood yayi asata a js3 saboda ta girma she is 15. Hakan ko akai saida akai mata komai aka kaita hostel dinsu sannan su Fareed suka dawo gida...


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. Ta bangaren Masroor kuwa
Kullum da tunanin Sulthana yake kwana dashi yake tashi, yanzu Masroor ya koma shiru shiru bashida hayaniya. Hoton Sulthana shi yazan mai tv, lokaci lokaci yakan sa Yasir yajemai Kauyensu Sulthana ko da wani labari gameda ita anma bbu. Yasir na matuk'ar tausayama abokin nashi hakama Mami dan Yasir ya sanar da ita duk abinda ke faruwa...


Sulthana taji dad'in makarantan sosai dan a ranar datazo tai k'awa mai suna Aisha ibrahim itama y'ar jahar kano ce. Yarinyar wani senator ne a gwamnatin dakaci yanzu. Y'ar gayuce sosai ga Rashin ji da Tsiwa, tasu tazo d'aya sosai da Sulthana, wajanta take koyan Abubuwa kamar karatu da sauransu..


*Bayan shekara d'aya*


Sulthana na hango tsaye a wajan makaranta sanye da k'ayan hostel hannunta Rik'e da trolleynta, ta k'ara tsawo da cika, fatanta ya murje tayi kyau sosai. gefenta k'awarta Ayoush itama tsaye da Alama hutu akai saboda yanda dalibai keta fitowa da jakunkunan su. Hira suk'e suna dariya chan saiga wata had'adiyar mota k'irar doddge tai parking. Fareed ne ya fito daga motan sabye da Farar yadi sai baza k'amshi yake. K'arasowa inda suke tsaye yayi yana y'ar murmushi,


"Am sorry Queen I know i'm late"


Zaumbure baki tai ta kauda kai gefe, dariya Ayoush take k'asa kasa ta gaidashi da kanta ta saka jakan Sulthana a motar sannan ta karasa inda take tsaye


"Queen kiyi haquri mana kuje kinji"


Murmushi Sulthana taima Ayoush suka rungume juna sannan Sulthana ta shiga yaja sai kano ta dabo..


Fushi Queen dinshi keyi dashi, bah yanda beyi bah daran ranar ta rakashi yanada Dinner anma taki wai ita barci take ji. Hakanan ya hak'ura ya kira Sa'ood sukaje tare..


Masroor ne xaune cikin jirgi yau cike yake da farinciki zai dawo nigeria wajan iyayenshi. K'arfe hudu na shidda na yanma jirginsu ya dauka a kano, koda ya dauko Yasir ya gani tsaye shida Mami da Umma'n Fareed sai wasu mata dake bayanshi dukansu fuskokinsu d'auke da murmushi..


Dasauri ya k'arasa ya rungume Mami cikeda farinciki sannan ya rungume Yasir sunama Juna Dariya. D'an rusunawa k'adan yayi ya gaida Umman Fareed ta amsa fuska a sake, Mahnoor ta fito daga mota da gudu itama ta rungumeshi


"I missed uh bro"


Kanta ya shafa yana murmushi


"I missed uh too lil sis"


Yasir ya k'araso wajansu yace


"Dare yayi muje gida kwayi maganan"


Hannun Mahnoor Masroor ya kama suka shiga mottoci suka dun guma zuwa government house. A chan ma taron jama'a ya gani dan murnar dawowanshi da kuma murnar kammala karatunshi. Cikin taron harda Fareed da abokinshi Sa'ood suma sun samu halarta, anyi ciye ciye da adduo'i sannan kowa ya tafi gida..


Washe Gari dasafe Mahnoor zaune itada Masroor suna breakfast, Mahnoor tace


"Bro yaushe zamuje wajan Sulthana tunda ka dawo"


D'agowa yayi dasauri ya kalleta tareda sakin Fork din dake hannunshi..




Ummy Abduol✍🏻


💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐


By *Ummy Abduol*




*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*


_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_


*Page 171 to 175*
Dedicated dis page to Aunty Nurse (Ayoush) Allah dawo min dake nigeria Lapia.


D'agowa yayi dasauri ya kalleta tareda sakin fork din dake hannunshi. Ta fama mai tsohon kumin daya dad'e a zuciyarshi baice mata komai bah ya mik'e yabar wajan. Mahnoor ta bishi da kallo cikeda Mamaki..


A kauye Mallan ciwonshi sai gaba yake kullum cikin magani anma babu abinda ya chanza. Rayuwa knan! Duk yan kudadenshi sun tafi wajan magani, Almajiranshi duk sun gudu sun tafi gida. Yanzu Mallan da iyalinsu sun zama abin tausayi Abinci ma dak'yar suke samu watarana ma haka suke kwanciya basuci komai bah. _niko Ummy Abduol nace dama rayuwa haka take, yau gareka gobe ga wani. Abinda ka shuka shi zaka girba in Alkhairi ka shuka shi zaka gani, in kuma sharri neh shidin dai zaka gani_

_Allah kasa mufi k'arfin zuciyarmu. Ka bamu ikon aikata Alkhairi ka nisantar da zuciyarmu da Aikata sharri Ameen_


Sulthana zaune a palour yana k'allo taji bud'e gate din gidan, mik'ewa tai dasauri ta fito haraban gidan dan dama shi take jira. Yana parking ta bud'e mai murfin motan tanamai Murmushi


"Ya Fareed tun dazu nake jiranka, ko ka fasa kaini yawon"


Goshinshi ya fada tareda furzar da aska


"Oh God! Queen bakya mantuwa neh?"


D'an zaro ido tayo cikeda shagwaba tace


"Yauwa nama tuna kace zaka saimin phone"


Muryan shagwaba yayi shima yace


"Tho Queen sai ki bari idan na huta"


Dariya ta kyalkyale dashi ya mik'a mata breifcase dinshi ta amsa tana tafe yaba binta a baya. Abinci mai rai da lapia ta dafamai ta jera a dinning, kallan warmers din yayi da Mamaki


"Waya kawo wadan nan abincin"


Bubuga k'afa tayi a kasa tana turo baki


"Nifah na dafa fah"


Iyeh yace cikeda mamaki


"Waya koya miki girki?"


Hannunshi ta kama ta zaunar dashi kan kujeran dinning din tana murmushi


"A school mana, ai munayin Home economics"


Gyada kai kawai yayi dai dai lokacinda ya saka loma d'aya. Ya lumshe ido ya bud'e


"Umm! Wannan ai saiya ciremin kunni"


Dariya tayi ta zauna itama ta zuba nata, saida yaci yayi nak Sannan ya mik'e yana cewa


"Bari nayi wanka na shirya sai muje"


Tsalle tayi tana dariya


"Thank uh ya Fareed dts why I love uh"


Da mamaki ya k'alleta tai saurin juyawa ta shiga dakinta tana cigaba da dariya.


Masroor neh yayi paking a kofar gidansu Yasir. Waya ya dauka ya kiranshi ya sanar dashi isowar shi, ba'adau lokaci bah ya fito yana murmushi


"Har ka gama hutawan?"


Kai kawai Masroor ya gyada ya shiga mota ya zauna, yasir na ganin haka shima ya shiga ya zauna yana k'allanshi


"Yadai friend meke faruwa?"


Batareda ya kalli yasir bah yace


"Inaso neh muje gidansu Beauty"


Yasir ya yatsine fuska


"Muje muyi meh kuma Masroor? Duk sanda naje bana samunta bata dawo bah. Pls Friend ka cire yarinyan nan a zuciyarka myb ma bata raye"


Dago jajayen idanunshi yayi ya zubama Yasir,


"Wannan wanne irin magana neh Yasir? Na cire beauty a raina fah kace??"


Runtse ido yayi ya bude


"Bazan iya bah yasir, bazan iya bah. Indai zaka rakani to idan kuma bazaka rakani bah"


Ya nunamai kofa


"Zaka iya tafiya zanje ni kadai"


Murmushin takaici Yasir yayi


"Muje"


Kunna Motan Masroor yayi suka d'au hanya..


La'asar lis suka isa kauyen, masallacin kusada gidan sukai Sallah sannan yasir yayi sallama a kofar gidan. Hafsatu ce ta fito duk tayi bak'i ta fige kamar ba ita bah, Masroor na ganinta ya had'e rai. Yasir ne yace


"Munzo neman Sulthana neh"


K'uri tama Masroor tana k'allanshi shiko gogan ya kauda kai sai cika yake yana batsewa. Sai a sannan taganesu tad'anyi Murmushin y'ake tace


"Ina wunin ku?"


Yasir ne ya amsa ita kuma ta cigaba da cewa


"Sulthana ta b'ace ba'asan inda take bah shekara d'aya knan da k'usan rabi"


Hankalin Masroor ya tashi ya juyo ya kalleta murya na rawa yace


"Dan Allah bakuji wani labarinta bah?"


Kai Hafsatu ta girgiza tana matsar kwalla


"Bah wani labari. Muma Mallan na kwance bashida lapia tun lokacin"


Yatsine fuska Masroor yayi ya juya yana cewa


"Sai anjima Allah bashi lapia"


Rufamai baya Yasir yayi suka shiga mota suka bar k'auyen..


Yawo sosai sukasha ranar itada Fareed, Sannan daga baya sukaje plazer yasai mata hadad'iyar waya k'irar iphone5. Murna wajan Sulthana ba'a magana sai tsalle take a plazern cikeda Farinciki. Biyan kudin yayi suka fito tana Murmushi mai k'ara mata kyau, saida suka shiga mota sannan ta kalleshi da fara'a


"Thank uh ya Fareed"


Kai ya gyada yace


"Keh koh Queen! Wai aina kika koyo wannan shagwaban da rashin ji haka"


Turo baki tayi ta sauke kai tana duba kwalin wayan. Baice komai bah ya tada motan suk'a d'au hanyan gida.


Masroor driving yake anma hankalinshi sam bai jikinshi, ji yake kaman ya fashe da kuka. Gabanshi ne ya soma faduwa yad'an dago ya kalli Yasir Sannan ya maida dubanshi ga Titi. Yasir ne ya taboshi tareda nunamai Motan dake gabansu yana cewa


"Wannan bah benz din dr Fareed baneh"


Wani faduwa gaban Masroor ya k'arayi ya d'ago dasauri yana k'allan motan


"Eh itace"


Murmushi Yasir yayi


"Lallai Fareed d'an duniya neh, shine rannan yacemin baida budurwa anma ji kamar wata nake gani a motan"


Faduwan gaban Masroor neh ya tsananta, wuri ya samu yayi parking yana k'allan motan Fareed har suka b'ace. Ganin halinda yake ciki yasa Yasir ya fito ya zagayo tareda bud'e kofan wajan Driver


"Fito sai nai driving"


Bah musu ya fito ya koma inda Yasir din yake suka nufi Gida..


Kwanaki nata tafiya tunanin Sulthana ya hana masroor sukuni, abin ya soma damun Mami da Daddy, daddy baida choice hakanan ya k'ara tura mutane dan neman labarin Sulthana anma bah wani bayani..


Mahnoor tayi kuka sosai jin labarin bacewan Sulthana saboda yanda take santa. Abin Masroor sai gaba yake hankalin Mami da daddy ya tashi sosai bama kamar Mami basatan wani abu ya faru da d'an nata..


Yau Sulthana na cikin farinciki saboda yau bestynta Ayoush zatazo, har Mamaki Fareed yake yanda yaga taketa b'are b'are. Girki kala kala ta hada don taran k'awar nata. Wuraren k'arfe hudu da rabi Sulthana na dak'i kan dadduma bayan ta idar da Sallah taji horn din mota, zumbur ta mik'e ta fito

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login