Showing 1 words to 3000 words out of 34864 words
Chapter 1 - Cin Amana Ko Fansa (1 to End) Compelet By Zahra Muhammad Mahmud.txt
๏ปฟCompiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)
๐๐๐๐๐๐๐๐
*CIN AMANA*
*KO*
*FANSA*
๐๐๐๐๐๐๐๐
*(TRUE LIFE STORY )*
Zahra Muhammad Mahmud
ยฎ *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
*PML*
*Godiya ga Allah mad'aukakin Sarki, tsira da Aminci sutabbata ga annabinmu Muhammad rasulullahi sallallahu ala'ihi wasallam.*
*Wannan labari ba k'agagge bane yafaru dagaske,duk abinda ke ciki anyine da gaske, suna kawai na wa'inda abun yashafa Nasauya,da d'an abinda ba'a rasaba.baya ga haka babu abinda Nasauya*
Ya Allah, yadda nafara rubuta littafinnan lfy,Allah kasa nagamashi lfy.
*page 1*
Y'anmatane su biyu, y'an kimanin shekara goma sha shida da haihuwa,suka rugo da gudu zuwa Cikin d'akin kakarsu suna ta kiranta, uniform ne ajikinsu, alamar daga makaranta suke,
"Grany!!! Grany!!! where are you? we miss you so much,mekika tanadarmana yau."
A zaune suka ganta tana Kallonsu, k'arasawa jikinta sukayi, suka rungumeta, kowacce tamata kiss a gefen kumatunta.
"Kai ni banason iskancinnan naku, ace gird'a gird'a daku Amman har yanzu baku girmaba,wato abinnaku gaba yakeyi,yau kuma harda sumbatata ko?".
Dariya sukayi suka K'ara rungumeta,Khairat ce tace,
"Haba Grany, danma kinsamu munzo gidanki yau shine harda yimana wulak'anci,ni dama wlh banso zuwa ba,Fatima ce da shegen naci tace muzo gidanki,gashi daga zuwanmu kinfara halinnaki."sakin Grany tayi takoma gefe tazauna,
Fatima tace, "Wayyo Sis kiyiwa Grany uzuri, bakiga se kallonmu takeyiba, alamun taji dad'in ganinmu, hala taji haushin bamuyi sallama bane, ko Grany?",tawaiga Tana kallon kakar tasu.
Grany dariya tayi sannan taruk'osu dukansu tace ,
"Haba kha'iriyya ta fushi kikeyi danine?, nicefa babbar k'awarki ranar bikinki,"dariyace takwacemusu dukansu,khairat tace,
"Wai,dagwargwajiya kenan Grany ansha gwargwaro ranar aurena,"cigaba sukayi da dariyar.
Ranar wuni sukayi agidan Grany,seda la'asar suka mata sallama suka wuce gida.
Khairat da Fatima sa'annin junane, dan anhaifi Fatima da Sati biyu aka haifi Khairat.
Iyayensu mata ya da k'anwane,haka zalika, Iyayensu maza suma wa da k'anine.
Alhaji Nasir Abubakar shine mahaifin Fatima,suna kiranshi da Abba,mahaifiyarta Mesuna Hajiya Salamatu suna kiranta da Umma.yaran Alhaji Nasir hud'u biyu maza biyu mata,Yaya Jameel shine babba, se Yaya Umar mebimasa,se Fatima, da autarsu Yasmeen.
Alhaji Mukhtar Abubakar shine mahaifin Khairat,suna kiranshi da Daddy, Wanda wa yake agurin Alhaji Nasir,uwa d'aya uba d'aya,
Matarshi d'aya Hajiya Binta,wacce take yaya ga mahaifiyar Fatima, yaransu guda shida,hud'u mata biyu maza,Aunty Fareeda Itace babba ,se Yaya Kamal mebimata,se Aunty Khadija,se Kha'irat, se Fa'eeza,da autansu Yusuf.
Gidan Alhaji Nasir dana Alhaji Mukhtar ahad'e suke sede katanga data rabasu,
Suna zaune da iyalansu agarin Kaduna awata anguwa Mesuna Tudunwada dede layin k'osai kan katagum road,
kansu ahad'e yake haka na iyalansu komai nasu tarene ko kasuwancin suma a tare sukeyi inda suke Saida kayan sawa kama daga na maza zuwa na mata, da yara, komai suna saidarwa a kasuwar checheniya dake Kaduna.
Zumunci ne me k'arfi a tsakaninsu inda ahalin yanzu babban d'an Alhaji Nasir yana auran Y'ar gidan Alhaji Mukhtar Khadija, harda yaransu guda biyu suna zaune a kinkinau dake Kaduna,ita kuma Farida wani ma'aikacin nepa take aure harda yaranta guda uku.
Rayuwar wannan family rayuwace mecike daso da k'aunar juna.
Grany,wacce sunanta na aynihi Hajiya Asiya amman jikokinta nace mata Grany,yayinda y'ay'anta da sirikanta kecemata Hajiya, Itace tahaifi Iyayensu maza,kuma a kakanninsu ita kad'aice tarage musu sauran duk sunmutu
Kha'irat da Fatima kansu ahad'e yake ko bacci tare sukeyinsa babu abinda ke rabasu suna matuk'ar k'aunar junansu ko kad'an ba'ajin kansu,ajinsu d'aya Boko da Islamiyya, suna da k'ok'ari sosai dan sotari twins ake cemusu,dan duk jarabawa sede suyi bracket, kowa cikinsu beson b'acin ran d'an uwansa.
Maman Yusuf
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
*CIN AMANA*
*KO*
*FANSA*
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
Zahra Muhammad mahmud
*LOSING SOMEONE WHO DOESN'T RESPECT OR APPRECIATE YOU IS ACTUALLY A GAIN, NOT A LOSS.*
*pure moment of life writers*
*p.m.l*
*page 2*
Rayuwar Fatima da Khairat rayuwace mecike da son juna.
Khairat irin matannanne masu azababen kyau don ko daga nesa ka hangota kasan me kyauce,farace me hanci ga yalwar gashi tamkar indiya, komai da akeso ajikin mace Allah yabata,wannan baiwa da Allah yay matane yasa ta d'auki dogon buri akanta tanaji da wannan kyau da Allah yay mata shiyasa ko saurayi take burin me kud'i,in talaka yazo gurinta seyasha wulak'ancin dako a hanya yaganta baze sake marmarin kulataba,
har k'awayensu na makaranta sunsani shiyasa yanzu kirarin dasuke mata shine matar Manya,jin dad'i take insuka kirata da sunan.
Fatima nada kyau dede misali Amman bata Kama k'afar khairat ba,sede dirin halitta na y'a mace itama Allah yabata,batada da wulak'anci ga kowane ne yanuna yana sonta burinta de Allah yabata miji nagari.
Akan wannan halin na Khairat sunsha yin fad'a da Fatima sabida hakan,inkaji fad'ansu to akan wannan halin na Khairat ne Sam Fatima batason halin.
Yau ba makaranta dan haka su Fatima suka tsefe kansu sukaje Kitso,ahanyarsu ta dawowane wani me liffan yatsaresu,saurayine matashi ba laifi akwai natsuwa da kamala atattare dashi sallama yamusu,
"yan mata barkankude," yafad'i yana kallon Khairat da alamun ita yabiyo.
Khairat bata amsaba sema wata uwar harara data watsa mishi.Fatima ce ta amsa,
"barka kadai malam".
murmushi yayi sannan yace,
"Don Allah kuyi hak'uri da tsaidaku da nayi wlh son yar uwarkine yakamani tunda na hangota duk danaga ita ranta kamar beyi na'am daniba Don Allah kubani number d'inku da Address dannazo har gida nasameta,"yafad'i yana kallon Khairat.
"Dank'ari mune zamu baka address d'inmu harda number waya,to wlh bakaji da kyauba gwara tun wuri kanemi dede kai danmu ba sa'anninka bane dahar zaka wani ce kana sona Allah yakyauta wlh farashin gold beyi karyewar da za'ayiwa jaki mangala dashi ba,"tafad'i rai abace taja hannun Fatima da niyar suwuce subarshi, kwace hannunta Fatima tayi ta tsaya,itako Khairat gaba tayi abunta,cikin sigar tausayawa Fatima tace mishi,
"Don Allah malam kayi hak'uri wlh banji dad'in abinda tayi maka ba, kuma in zan baka shawara ka hak'ura da ita wlh tunda tanuna bata sonka banajin akwai abinda zesa tasoka kayi hak'uri kanemi wata don katsira da mutuncinka kaji,don Allah kuma kayafemata pls,"tafad'i cikin sigar rarrashi.
Murmushi yayi Yace, "bakomai baiwar Allah nagode dake kika saurareni, Amman kinsan sharrin so wlh jinake bazan iya hak'ura da ita ba kitaimaka kibani address d'inku da sunanku pls banak'i shawarar ki bane zuciyata ce bazata iya hak'uraba ki taimakamin pls",yafad'i kamar zeyi kuka.
Ba musu Fatima tabashi abinda ya buk'ata dan ta tausaya mishi daga k'arshe tamishi fatan alkairi, dazasu rabu yafad'a mata sunanshi Ahmad.
A hanya tasamu Khairat se cika take tana batsewa kotakanta bata biba sabida inda sabo tasaba da halinta, ahaka suka ci gaba da tafiya bamecewa kowa uffan.
Suna shiga gida d'akinsu suka wuce dan ajiye hijabansu ananne Khairat tacewa Fatima,
"Wai don girman Allah sis se yaushene zaki gane darajata tafi k'arfin irin wa'innan samarin? kina zubarmin da ajina wlh ni matar manyan mutanece,yakamata kigane har yanzu ban samu kalar mijin daya dace daniba, amman ke da Kare da doki kowama address d'inmu kike basu suzo su takuramin dan Wlh wannan ma nasan kinbashi address d'in watak'ila ma harda rakiyar phone number mitsss,"tayi tsaki ranta ab'ace.
murmushin takaici Fatima tayi ta dubeta tace,
"Sis kenan wani lokacin inkikayi wani abun senaga kamar ba'a family d'aya mukeba,dan de tarbiyya dede gwargwado iyayenmu suna bamu kuma sunsamu a makarantun da ake koyar damu sanin darajar d'an Adam.Haba Sis kituna fa Allah dakanshi yace yakarrama bani adam kewacece dazaki dunga wulak'anta mutane?,kituna Allahn daya baki kyaun dakike wulakanta mutane sabida shi shine yayi kuma wainda kike wulak'antawar bayan yahanemu dayin hakan, tabbas nabashi address sede inyazo shima ki koreshi kamar yadda kika saba,ni narasa mekike nema aduniyar da watarana ko labarinki baza'aji acikintaba, haba Sis yakamata ki farka daga wannan banzan mafarkin dakikeyi."
"Mafarki fa kikace Sis to wlh kece kike mafarki ni reality show nake yi, koma mezakice naji amman wlh babu yadda za'ayi nakai kaina gidan talauci sede kita fad'in abinda kika ga dama,kuma wlh shima wannan dakanshi ze kama kansa dan bade niba sede wata wlh."kiran da Umman Fatima tai musune yasa suka bar maganar suka tafi gurin kiran.
Maman Yusuf
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
*CIN AMANA*
*KO*
*FANSA*
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
Zahra Muhammad Mahmud
*pure moment of life writers*
*pml*
*page 4-5*
Koda suka isa gida Khairat gaban mirror taje ta tsaya tana k'arewa kanta kallo,can kuma tasake fashewa da kuka ta fad'a kan gadonsu,Fatima wacce dariya tagama kamata da k'yar ta daure tace.
"Sis lafiyarki k'alau kuwa?, wai kukan me kikeyine haka?".
Cikin kuka Khairat tafara magana.
"Haba ki dubenifa wai ace duk had'uwar nan tawa manyan mutanennan bawanda yakalleni bare yace yana sona,nibama wannan ne yake sani kukaba more than 3hours nad'auka ina Kwalliyar nan Amman wai ace me hotone kawai na burge ay dole nay kuka,"taci gaba da kukanta harda majina.
Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi sabida gaba d'aya takasa magana abun yabata dariya sosai. Fita Khairat tayi a d'akin sabida dariyar da Fatima take mata.
Tunda wannan D'an majalisa ya amshi number Fatima se yau ya gwada kiranta kimanin sati guda kenan da had'uwarsu,lokacin daya kira suna zaune ita da Y'ar darunta wato Khairat suna labarin wani littafi da ake rubutawa na online writers nawata marubuciya Zahra Muhammad mahmud me suna *Allah gatan bawa*.ajiyar zuciya Khairat tayi tace.
"Ya Ubangiji nima kasa nayi irin wannan dacen da jarumar littafinnan ilham tayi,nima nasamu miji kamar Anwar Tunda nima kyakkyawace",ta fad'i harda d'aga hannu sama,dariya Fatima tayi tace.
"Allah yataro minke Sister".
k'arar wayar Fatima ce takatse musu hirar,number tagani da kamar karta d'aga cande kuma ta d'auka,tace,
"Salamu alaikum".
"Wa'alaiki salam ya ma'abociyar natsuwa da hankali,".
Tsigar jikinta seda ta tashi sabida jin daddad'ar muryar me maganar, katseta yayi da cewa.
"Am sorry princess tunda na amshi numberki ban kiraki ba se yau please ayimin afuwa, al-amurane suka sha kaina tuba nake sarauniyar mata".
Murmushi ne ya sub'ucewa Fatima kamar yana kallonta,sabida ba k'arya muryarshi kad'ai dataji tasa taji takamu da son mamallakin wannan murya.cikin salo najan hankali tace.
"Ammaka afuwa duk da bansan dawa nake maganaba pls can you tell me more about your self?".
muryarta se yau yake k'ara jin dad'in muryar da k'yar yace.
"Am Hydar Jibrin Lamid'o, wanda yaturo kibashi number ranar bikin friend d'inki Jameela sati guda daya wuce, so inbazaki damuba inason address d'inki dannazo mugaisa kinji pls badan na isa ba sedan Allah."
Fatima tunani tashiga yi agame da sunannashi dan ita tabbas tasan d'an majalisarsu me wakiltarsu a Abuja sunanshi kenan,toko suna ne yazo d'aya?, ko shine dakanshi?,kai mezeyi dani?bashi bane.haka tadunga tunani ita kad'ai shine dayaji shurun tayi yawa yakatseta.
"haba princess wlh ba cutar dake zanyiba kidaure kibani address d'in kinji zuwa anjima da yamma zan shigo mugaisa,"ba musu Fatima tai mishi address d'in gidansu,yay mata godiya yace se yazo anjiman sukayi sallama. Tana ajiye wayar Khairat wacce tun d'azu kallonta kawai takeyi tace.
"Sister wlh tunda nake bantaba ganin budurwa me arha irinkiba, haba don Allah shikenan kowa yataya ba jan aji kike siyarwa Wlh kina badamu,nide gani nake yadda akasan address din gidanmu ta dalilinki ko gidan gomna se haka ace ayi mutum sam bajan aji wlh kigyara halinki ni nafara gajiya da hakan,"tafad'i har da tsakinta.
murmushi Fatima tayi tace.
"Sister kenan shi wannan Jan ajin dakike magana ba irinshi addininmu yakoyar damuba, sabida duk wacce takeyin irinshi ba sunanshi Jan ajiba wulak'anta halittar Allah sunanshi wanda kinsani nasani ba abune me kyau ba dan haka ni inde hakan danakeyi shine rashin aji to nayarda har atashi duniya bazanyi ajiba arayuwata".
"to Allah ko yakyauta miki wlh,yanzu kuma wanne d'an wahalar ne yakiraki?"inji Khairat.
"Wanda ya turo nabashi number na ranar dinner d'in Jameela Habib,yacema zezo anjima mu gaisa."
Dariya Khairat ta kwashe da ita tace.
"lalle Sis wato ke baki d'au ishara akainaba kina ganin duk kyannan nawa me hoto kawai na burge agurin,ayko tunda haka ko tafaru akaina Allah Sis may be megadin gurinne ya turo kibashi number,"tasake fashewa da dariya.
Fatima itama dariyar takeyi tace,"to in megadine seme?, shiba mutum bane?,koko shi ba Allah ne yayi shiba?,kinga rabani da wannan shirmen naki koma waye ni ina maraba dashi,tunda wannan Karon gurina megadin zezo ay da sauk'i bagunki naturoshi ba bare ki tsine mishi son ranki."
Wata shewa Khairat tayi tace, "ina wlh Sis ayni nafi k'arfin irinsu sede ke, ni ay matar manyace ko kin mantane?".
"Natuna matar Donald Trump,"
Fatima tabata amsa tana dariyar tsokana ita ta d'auka Khairat zataji haushi ga mamakinta seji tayi Khairat tarungumeta tana fad'in.
"Wlh Sis kinyimin fata me kyau,ni abin yace yana sona wlh auransa zanyi baruwana da kafircinshi yayi addininshi nayi nawa,nazama First Lady a America wai ranar ina zansa kaina dan dad'i".
Tureta Fatima tayi cike da mamaki tace.
"Sis ke har son kud'in naki yakai ki auri kafiri matuk'ar yanada kud'i kuma sunanki ze fita as celebrity a duniya wato zaki iya auransa kenan?Allah yashiryaki lamarinki yafara bani tsoro wlh,"tafad'i cike da damuwa.
Khairat ko ko a jikinta mik'ewa tayi tad'auki gyalenta tace ni natafi gidan su Zainab Umar zan amso note book d'inta na chemistry na kwafa sabida banida complete note sena dawo Ummu shuhada",tafad'i tana dariya tafice a d'akin tabar Fatima baki bud'e.
5:30pm Hydar yazo gidansu Fatima,acikin wata arniyar motarshi Range Rover new model fara tasha tinted glass bak'i sosai bame ganin naciki,numbar motar sunane ansa Hydar 1,gashi yayi shiga ta alfarma wacce duk macen data ganshi seta koka ba laifi Hydar kyakkyawane ajin farko dan yafi Fatima kyau nesa ba kusaba.
Kiranta yayi a waya ya shaida mata gashi ya iso.
Hijabi tasa bayan tad'an k'ara gyara fuskarta tafesa turare tafito zuwa k'ofar gidan, lokacin Khairat bata dawo daga anso littafinba.
Fatima koda tafita wata arniyar mota tagani a k'ofar gidansu wanda batai tsammanin acikinta me nemanta yazo ba, waige waige takeyi tarasa ina wanda yazo gurinnata yatsaya,shiko daga cikin motar K'are mata kallo yakeyi yana k'ara godiya ga Allah daya had'ashi da nutsatsiyar yarinya irinta,ganin tana nemanshine yasa yakirata a waya yace gashinan acikin motar dake gabanta,dasauri yaga ta kallo motar sannan tace.
"to kafito mana,"yace.
"Princess inda hali mushiga daga cikin gidanku in akwai inda zamu zauna peacefully banason intsaya awaje kowa yazo yaganni kinji pls,"amsa tabashi dacewa.
"sekace mara gaskiya".
dariya yayi wacce tasa Fatima k'ara fad'awa kogin sonshi yace.
"watak'ila hakanne banida gaskiyar ay ba laifi bane dan na nemi mafaka daga gareki," murmushi tayi sannan tajuya cikin gidan,gurin maman Khairat tanufa tace mata tayi bakone tade fad'amata yadda sukayi dashi yanzu tanason abata key d'in sit room d'in Abban su,jamata kunne maman tayi sosai akan tade tsare mutuncinta sannan ta bata key d'in.
zuwa tayi tabud'e sannan tafita takirashi awaya tace yafito to yak'araso sushiga daga ciki, ga mamakinta me makon taga yafito setaga ya tuk'o motar har zuwa k'ofar gidan sosai sannan yay parking yafito.
Hasbunallahu wani'imal wakil itace kalmar dake fita a bakin Fatima sanda tai arba dashi,ba iya kyan shine ya ruda ta ba a'a sanin wayeshi a jihar kaduna shine ya rud'ata, shiko se murmushi yake sakar mata me kashe zuciya har yak'araso gurinta bata saniba,Ta tafi tunani hura mata fuska yayi sannan tadawo daga duniyar data tafi,kashe mata ido d'aya yayi yad'aga gira yace.
"yadai princess wannan kallo ay sekisa nafad'i ayimin dariya", kunyace takamata da k'yar tace mishi su shiga daga ciki.
koda suka shiga gaisheshi tayi sannan takawomishi drinks kad'an yasha sannan yace.
"Princess the way you act for the first time dakika ganni nasan kinsan koni waye so no need natsaya ina cemiki nine wane, kawai abu d'aya zan iya sanar dake shine tunda naganki Allah ya jarabceni da sonki so me tsanani,don haka nake rok'on alfarmarki kisoni koda rabin son danake miki ne pls,"yafad'i cikin sigar tausayi.
Fatima bata hana kanta abinda takeso inde be sab'ama addini da al-adar ta ba don haka bata jamishi raiba ta amshi soyayyarsa kuma dama Hydar ba irin mazan da ake cewa kaje senayi shawara bane.
yaji dad'in amsar soyayyarshi datayi batare data wulak'antashiba, abinda y'anmata suka d'auka wai Jan ajine,hirarsu ta soyayya suka shigayi duk da Fatima kunya ta isheta takasa sakin jikinta dashi shine ke mata hirar.
Khairat ta dawo daga amsar littafin lokacin datayi arba da motar Hydar a k'ofar gidansu seda tayi tuntub'e ta fad'i sabida kallon datakewa motar,Allah yasota bakowa agurin da sauri ta Mik'e tashiga cikin gidan tana waigen motar.
tana tunanin gurinwa me motar yazo a gidansu,zata wuce cikin gidane taga takalmin Fatima a k'ofar sit room d'in Abban su da kamar ta wuce se tafasa taje tayi sallama a k'ofar d'akin,Fatima ce ta amsa gami da cewa.
"yauwa ga Sis d'ina ta dawo danake baka labarinta Sis kishigo mana kintsaya",bud'e k'ofar tayi tashiga da sallamarta.
Ya Ilahi!!!!.
ita Khairat ta furta sanda tai arba da fitaccen d'an siyasa kuma d'an majalisa me wakiltar kaduna South a Abuja mutumin da Nigeria ansanshi sabida motion d'in daya kaiwa majalisa, uwa uba shine mutumin data dad'e tana mafarkin samunshi a matsayin mijinta na aure.
Zama takeso tayi akan kujera amman dayake arud'e take zamewa tayi tafad'i ak'asa sabida hankalinta nakanshi, dasauri Fatima tazo takamata Ta tashi itako ko ajikinta k'ok'arin gaisheshi takeyi,amsawa yayi bayabo ba fallasa danshi mutum ne miskili ba kowa ke ganin fara'arshiba.
memakon dasuka gaisa tabasu guri ay ina k'ara shishshigewa take tana kwarkwasa ita game kyau hakan beyiwa Hydar dad'i ba don haka sallama yay musu gami da cewa Fatima.
"My Princess zamuyi waya innaje gida kinji take care of your self OK".
amsa mishi tayi da Allah yakaishi gidan lfy Ta gode da ziyara.
bunch d'in one thousands yaba Khairat yace, "to k'anwarmu ga wannan kisha ice-cream,"juyawa yayi yafita bayan yabata kud'in,har gurin mota ya tilastawa Fatima tarakashi sannan sukayi sallama ya wuce.
Maman Yusuf
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
*CIN AMANA*