Showing 1 words to 3000 words out of 98763 words

Chapter 1 - ANA MALIK HAUSA NOVELS BY HUMAYRA BULAMA .doc

??ࡱ?>?? ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?WordDocument????1?0Table?????????Data
???????????????????? P??XKSKS?1?T)???????rr7 7 7 7   ??s?7 ??????????$??*r7 7 ??7 7 7 7 ??? ?? ?? ??7   ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJTA`????TDefault Paragraph FontOJPJQJ^Jfi`????f Table Normal :V ?4?
l4?a? OJPJQJ^J(k`????(No List T) ?;?[???h???H??? ??*:=?T?e?v??T?4?B???4??????#j58N?g?Bismillahirrahmanirrahim.

ANA MALIK!!
Book 01.
Page 01.

Humairah Bulama.
Mikiya writers Association.


 'ND3ND'EO 9NDNJRCOE HN1N-REN)O 'NDDGP HN(N1NC'*OGO

*Jan hankali*
K addara mai kyau ko marar kyau ta kan samu bawa a duk lokacin da Ubangiji ya so ba dan saboda wayonsa ko akasin haka ba, ya kamata mu sake yarda da cewa bawa baya tab a haure k addararsa domin ita k addara yashi ce ko
an dunk uleta ba ta dunk uluwa.

A ko da yaushe ana so musulmi ya kasance mai fatan alkhairi ga d an uwansa musulmi domin shi harshe yana da kaifi kuma gatse ga k addarar wani kuskure ne babba! Sannan gori da kyamata ga d an uwa musulmi ba abune mai kyau ba tunda mutum ba shi ya tsarawa kansa tasa k addarar ba& & .

Ya ku samari matasa manyan gobe, shaye shaye da harkar dabanci babu inda take kai mutum sai dai ta nakasta shi, shin ina riba ga wanda bai tsaya ya mayar da hankali wajen gina future d insa a wannan k asa tamu da kowa kansa kawai ya sani ba?
Ku daina yiwa mutanen da ko kad an bazasu so ganin nasu y ay an a rayuwar da kuka jefa kanku a ciki ba hidima, abincin ku ba a hannunsu yake ba ku tashi ku nemi na kanku, ko wanne bawa yana da tashi kalar baiwar dan haka ku daina treating kuna kallon kanku as jobless..dig deep into that beautiful brain of yours there is definitely a gift in there!.

*Gargad i*
Littafin ANA MALIK k agaggen labari ne wanda ni Humaira Bulama na k irk ira na rubuta, ban yi dan kwaikwayo ko cin zarafin wani ko wata ba, idan ka/kika ci karo da abunda ya yi kamanceceniya da rayuwarka/ki to arashi ne.

Ban yarda kuma ban lamunta sannan ban amince wani ko wata ya juya min labari ta ko wacce fuska, ba tare da izinina ba. Yin hakan babban kuskure ne.

*Farawa*
Ina rok on Allah da ya yi ruk o da hannayena ya bani ikon rubuta dai dai da kuma abinda zai amfani al umma baki d aya. Yadda na fara lafiya Ya Ubangiji ka bani ikon gamawa lafiya.

 (P3REP qDDNQpGP qD1NQ-RENpFP qD1NQ-PJEP

Dare mahutar bawa! In ji masu iya magana, Hausawa.
A lokacin da hankali ya kan kwanta, shiru yake maye gurbin hayaniya, nutsuwa take maye gurbin karafniya sannan hutu yake maye gurbin gajiya. Ga kusan kowa hakanne dan in dai aka ce dare ya yi to ko wanne bawa ba shi da wani burin da ya wuce ya sanya hak ark arinsa a nutsuwa ya huta.

Tsakar gida ne mai d auke da d akuna barkatai! Da alama mutanen gidan ba su kai ga yin barci ba dan ko wanne d aki kana iya hango fitila ko kendir d insa a kunne ga kuma maganganu da ake iya jiyowa suna tashi sama sama kamar dai ba dare ba.

Kwance take cikin d aya daga cikin d akunan gidan ta inda ta yi kwanciyar rigingine ta na kallon fasashshen silin d in da ya yiwa saman d akin nasu k awanya, a zahirin gaskiya idan ka kalleta silin d in take kallo amma a asalin gaskiya gaba d aya hankalinta ba ya a kan silin d in dan inda ace za a tambayeta meyene shi d in to da ba lalle ta iya bada amsa tashi d aya ba.
A karo na uku ta sake juyawa ta kallesu ta tabbatar da sun yi barci dan har gwartin su take ji yana tashi sama sama.
A hankali jikinta a sanyaye yana wani irin karkarwa zuciyarta tana dad a yin zafi ta mik e ta zauna idanuwanta a kansu suna masu cicciko da ruwan kwalla sai dai ita kanta ta san hawayen ba iya zubowa za su yi ba.
Mik ewa ta yi tsaye har yanzun idanuwanta a kansu, ba ta da kowa sai su kuma tana matuk ar jinsu a cikin ranta..kamar yadda ba ta da kowa sai su haka nan a nasu b angaren suma ba su da kowa sai ita shiyasa ta ke da tabbacin za su yi k ewarta dukda kuwa a cikin bala in da ta zamo silar jefasu amma ta san tabbas za su sake shiga cikin mawuyacin hali idan ta barsu sai dai kuma ta san hakan da yin hakan a gareta da su gaba d aya shine dai dai..Gara ta tafi su ji zafin tafiyarta na kwanaki kad an daga nan ta san za su ci gaba da rayuwa mai dad i sab anin idan ta ci gaba da zama da su wanda ta ke da tabbacin komai sake tab arb are musu zai yi! Tabbas ita a karan kanta ta yarda kuma ta amince da sunan da kowa yake kiranta da shi a yanzu  Annoba , ba ta jin akwai alfanun ci gaba da rayuwa a tsakiyar su kai ba ma iyaka su kad ai ba al umma kanta gaba d aya bataga amfanin zama a cikinta tana janyo musu bala i dami-dami ba!
Dan haka ta juya a hankali cikin tafiyar da a yanzun ta zame mata jiki kamar ba ita ce ma abociyar kazar kazar da karafniyar nan ba ta fara tafiya kamar marar lakka a jiki yayinda jikin nata yake wani irin karkarwa& . A haka ta nufi k ofar fita daga d akin zuciyarta tana mai dad a tabbatar mata  Tabbas abinda kika shirya yi shine dai-dai!!! .
Babu kowa a tsakar gidan dan yanzun misalin k arfe sha biyu na dare ake nema amma fa baya ga mutanen da ta baro a d aki suna bacci ta sanadiyyar alluran da aka yi musu babu wanda yake da ma shirin yin barci a kaff cikin gidan wanda dalilin rashin kwanciyar tasu da wuri yana da nasaba da alhinin da suke a ciki yayinda waenda basusan Annabi ya faku ba zaman munafurci ne suka zauna yi.
D akunan ta bi da kallo, duk da yawansu amma ta gaza dukan k irji ta nuna guda d aya tak! Wanda za ta ce ba ta saka y an d akin a cikin alhini jafa i tare da damuwa ba.
A hankali ta juya ta kalli d akinsu a karo na farko tunda satin nan ya kama ta ji hawaye ya silalo ta cikin idanuwanta dan a lokacin da masifa ta kai masifa kuka yaji ya yi mata ya k aura ya bar cikin kwayar idanuwanta. A take ta fara jin kamar ba zata iya aikata abinda ta shirya ba, gudun fasawartata da ta ji wani sashe na zuciyarta yana shirin bijiro mata da shi ne ya sanya ta wuce cikin sassarfa ta nufi tafkekiyar rijiyar da ke a chan kusurwar tsakar gidan. Ta na isa ta saka hannu ta jaa katokon da yake rufe da rijiyar a hankali ta bud eta gudun kar a jita, so take sai da safe idan sun fahimta su tsinci gawarta a ciki idan kuma ba su fahimta ba ta rub e a ciki su k araci nemanta su hak ura.

Iyaka kallon rijiyar kad ai ya Isa ya sanya ka ji tsoro tsabar girmanta sai dai gareta sam ba hakan bane ba dan ko d igon tsoro ba ta ji ba saboda rayuwar da take ciki a yanzu ta fi k unci! Azabtarwa!! Kad aici..
fiye da rayuwar da ta san zata yi na wucin gadi a cikin ruwan rijiyar kafin Allah ya karb i ranta, sannan ko ba komai babu wanda za ta ji kunyar had a ido da shi a cikin rijiyar sab anin yanzu da take ji kamar ta binne kanta& & .(
A hankali ta taka dakalin rijiyar ta hau ba ta bari ta tsaya b ata lokaci ba ta yi tsalle ta afka ciki tsundum!.
& & .
Hayaniya mai tsananin firgitarwa ce take tashi a tsakar gidan dan harda koke koke yayinda hankulan makusantanta ya kai k ololuwa wajen tashi!
Zuwa yanzu hayaniyar ta su ta fara gushe mata
sab anin daa da take iya jiyosu& .a hankali ta lumshe idanuwanta tana sake nutso a cikin ruwan rijiyar da ta yi lamooo a cikinsa dukda kuwa azabar rashin numfashi ta kai k ololuwa wajen azabtar da ita amma tabbas hakan ya fiye mata akan azaba da k uncin da zuciyarta suke ciki a doron k asa.



UNGUWA UKU (Babban layi& .)
Juma atu babbar rana..Kamar ko wacce rana ta Juma ah haka itama wannan Jum ar ta kasance ranar sada zumunci da yawace yawacen gidajen k awaye ga y an Yara Yaran layin saboda yau d in babu makaranta sai hutu wasa da tsalle tsalle a garesu.
Misalin k arfe biyu da mintuna arba in kenan..masu zaman majalisu na yi masu gaishe gaishe na yi masu yawo da tsalle tsalle suma suna na su.
A bakin kiosk d in wani mai p.o.s kusan duk samarin layin suka taru ana hira ana raha dan basu dad e da dawowa daga masallacin na Juma a ba wanda hakan shi ya taimakawa layin wajen sake yin albarka ya cika taff tubarkallah.
Da gudu wata Yarinya ta k araso wajen, tana zuwa ta sauk e idanunta a kan wani kyakkyawan saurayi dogo bak i, tana haki cikin mayar da numfashi ta ce  Ya Aminu! Ya Aminu!!! Ga su Ma a chan sun tarewa Dije hanya a bakin filin kashu.
D iff!! Haka maganar kowa ta tsaya chak! Kamar an yi ruwa ya cinye su yayinda tsoro mai had e da firgici ya maye gurbin raha da annashuwar dake kwance a kan fuskokinsu yanzun nan.
Da kyar wani daga cikin samarin ya ce  Minu, kuma tunda har kun san ya takura mata ku daina aikenta inda kuka san shima yana yawan zuwa mana.

Da kyar k irjin Ya Aminu ya na dukan uku uku ya iya cewa  na hana, ban san me ya kaita chan ba.
Sai kuma ya yi saurin yunk urawa ya ce  bari in je .

Y an layin koma ace anguwar gaba d aya suna da masifar had in kai, duk abinda ya shafeka to ya shafi kowa haka nan suke rayuwarsu saidai a yanzun da kyar aka iya samun mutum biyu suka bi Minu ragowar kuma suka fake da tafiya police station dan su je su taho da y an sandan da kowa ya san basu isa su iya yiwa Ma a d in uwar komai ba.


Duk da cewa ita d in budurwa ce mai tashe dan a k alla shekarunta sun haura sha shidda da kad an amma still yanayin k irar jikinta ta fi shekarun nata dan kallo d aya za ka yi mata ko daga kusa ko daga nesa ka fahimci ita d in tana cikin jerin matan da Allah ya wadata su da k ira mai kyau& ..Daga ido idan ka kalli yanayin jikinta za ka yi mata kallon babbar budurwa duba da yadda komai na girma ya gama baiyyana da tabbata a tattare da ita, sai dai kuma yanayin d abiarta zai sanya ka fahimci har yanzun akwai ragowar k uruciya a tattare da ita.
Shekarun nata sun haura sha shidda amma ba su kai sha bakwai ba wanda idan ka matso ka yi mata kallon k urilla to yanayin fuskarta ma kawai zai iya k iyasta maka adadin shekarun nata.

Tsaye take ta kama k ugu tana masifa da tujara babu alamun tsoro ko sassauchi a tattare da ita, wasu zaratan samari su uku ne a tsaye a gabanta wanda ko da wasa bai kamata ace ta tsaya yi musu kallon banza ba ma ballantana masifar da take ta zazzage musu kamar ta samu y ay an cikinta! Ba wai iyaka shekarunsu ne ya kamata a ce ya sanya a ji tsoronsu ba! Yanayi da suffar su kad ai ta Isa ta firgita Yarinya mai shekaru irin nata, ba ma ita ba ko Babba bai isa ya ce zai kalli su Ma a ya yi musu da su ba ma ballantana fad a&

D aya bayan d aya ake watsewa a wajen, hatta masu kiosk rufewa suka fara yi masu trader suma tuni suka fara tuttura abun sana ar su suna barin wajen, dama tun tunkarowar Ma a da shi da Yaransa guda biyu wajen aka fara tarwatsewa to kuma yanzu behavior d in wannan y a marar ta ido ya sanya kowa yi ta kansa tun kafin Ma a ya yi kan mai uwa da wabi.

Dai dai lokacin da su Minu suke isowa wajen suna haki dan gudu suka tsula dai dai ita kuma ta durk usa ta tittilo k asa a duka hannayenta biyu zata b ulawa Ma a shi da su scorpion sakamokon kunnen uwar shegun da suka yi mata (sun k i tanka mata kuma sun k i su bata hanya ta wuce).

Da mugun sauri Minu ya kamo ta ya juyo da ita ya kakkab e hannuwan nata cikin fushi ya ce  sai yaushe za ki fara jin magana ne? Eh??
Ya fad i  eh d in da mugun k arfi kamar mai shirin rufeta da duka!&
..Yanzu haka Inna tana chan a kwance jininta ya hau jiya da kyar ya rage ba a basu gado a asibiti ba duk a ta sanadiyyar fad an DIJE da Kaka wanda daga k arshe ya k are a kan Innar dan babu kalar cin mutuncin da Kaka bata yi musu ba a jiyan, amma shine yanzu tsabar Iskanci ta zo zata zubawa Ma a da Yaransa k asa a jiki salon ta janyo musu masifa& .
Da kyar ya iya lallab a zuciyarsa da take ingiza shi akan ya rufe ta da duka, ya juyo a hankali bayan ya sakata a bayansa ya na kallon k asa dan a k a ida ba a had a ido da Ma a ya ce  ka yi hak uri dan Allah, Yarinya ce za a yi mata fad a.

Irin tsayuwar sojoji ya yi& ..ta inda ya saka hannayensa duka biyu a bayansa ya d an raba k afafunsa ba sosai ba ta hanyar bubbud a su kad an! Yayin da ragowar samari biyun suke tsaye a ta gefe da gefensa d an bayansa kad an dan basu jera da shi ba!
Dogo ne sosai sannan yana da fad in k ashi amma bai cika k iba ba sam, yanayin surar jikinsa dai a murje take sannan a murmure kuma a murd e wanda hakan ya taimakawa surar jikinsa ta giant sake baiyyana. Ba bak i bane ba kuma ba za a kirashi da fari ba, yanada dogon hanci da madaidaitan idanuwa masu tsayi da asalin kyau, da matsakaicin baki wanda yake nan bak i k irin wuluk! Kyakkyawa ne idan ka k ura masa ido wanda tsage-tsage da tabubbunan da suke a fuska har ma da ilahirin jikinsa ne suka bada gudunmmawa wajen b oye ainahin kyawun nasa& . Daga kan tsakiyar goshinsa wata mahaukaciyar sara ce ta taho a karkace ta bi ta kan idonsa na hannun hagu ta sauk a a dai dai setin k arshen kunnensa, Allah ya taimake sa bata tab a masa idon ba dan tar yake kallonta kuma kana ganin idon ka ga mai lafiya sai dai ta bi har ta kan saman fatar idon nasa ana ganinta tarr! Sai kuma yanke yanke wajen kala
biyar a sashe daban daban na fuskar tasa. Kamar yadda fuskarsa take haka nan jikinsa shima yake babu kyan gani, gashi dai shi d in musulmi ne amma jikinsa har da tattoo a wajen damtsen hannunsa na dama an rubuta  mamana da wani font mai kyau da heart a gaba y ar k arama.
K arafuna kuwa su sark ok i da zobuna da belt da takalmin jikinsa kamar wani kare.
Yana sanye da jeans d in khakin sojoji da bak ar vest kanshi babu hula sai wani d an Iskan aski. Yaransa kuma gajerun wanduna ne a jikinsu sai tshirt da p cap a kan d ayan, yadda jikinsa yake haka nan suma nasu ya b aci da tabubbuna d ayan har da k unar wuta a kafatarin ilahirin b arin fuskarsa.

Tunda Minu ya fara magana ya kafe shi da idanu ba tare da ya ce komai ba. Sai da ya dire aya tukunna ya sa hannu ya turesa gefe ya gyara tsayuwar sa sannan ya yi taku biyu ya isa gaban Dije yana zuwa ya sa hannu ya finciko hijabinta ta tafi zata afka jikinsa Minu ya yi kalmar shahada ya yi kukan kura ya shiga tsakaninsu ya sake ture Dije daga garesa a karo na biyu.
Cika mata hijab d in nata ya yi ta hanyar ware hannuwansa duka biyu da k arfi kuma a lokaci guda kamar wanda aka cewa action! D an taku d aya ya yi ya ja baya dan sosai Minu ya shige cikin jikinsa wajen k ok arin raba kusancinsa da Dije, sai da ya runtse idanunsa ya yi iyaka bakin k ok arinsa wajen tausar kansa dan kar ya yiwa Minu illah tukunna ya bud e idanunsa da suka rine da b acin rai ya zubasu a kan Minu wanda ya sha jinin jikinsa ya fara karkarwa, bakinsa na karkarwa yana shirin yin magana d aya daga cikin Yaran Ma a d in  Oscar ya d aukesa da wani irin gigitaccen marin da saida ya tafi kamar ana ingizashi ya je ya bugu da wani k aton dutse.
Dai dai nan motar y an sanda ta doso wajen wanda hakan ba k aramin mamaki ya bawa mutanen da suke d an lellek owa ba dan basu san amfanin zuwan y an sandan ba.
Aikuwa ilai!..Suna hango shi suka ja suka tsaya suka k i k arasawa wajen, suna mamakin k aryar da samarin suka yi musu suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login