Showing 3001 words to 6000 words out of 6997 words

Chapter 2 - BAKIN ARTABU Book 1 Cigaban Jaruma Yazila by Madakin Gini.txt

cewa yaki ba zai taba zuwa birnin tashwar ba? Ya kuma yanzu kake mini batun yaki ?"™Nasiru Muhammad™
Koda jin haka sai mahaifina yaja numfashi tamkar ransa zai fita, a sannan yace, "bana nufin yaki zai zo har nan ya riskeka, ina nufin za'a aikomaka da sakon gayyata. Lallai ka amsa gayyatar, amma kafita yakin kai kadai, kada ka kuskura ta tafi da kowa idan har kana son kasan addinin gaskiya.
Dangane da tambaya ta biyu dake ranka kuwa ba wani abubane face batun aure. Tun da mahaifiyarka ta rasu ban sake yunkurin aureba.
Haka mahaifina ya kasance, shima mahaifina haka rayuwarrsa ta wanzu har izuwa kan kakanmu na arba'in da daya.
Abinda nake nufi anan shine duk wanda yai aure acikinmu haihuwa daya yake samu kuma sai matarsa ta mutu, shima sai yamutu yabar abinda ya haifa.
Lokacinda aka haifeka sai naji babu abinda nake so a duniya sama da kai, kuma naji ina son kayi nisan kwana a duniya.
A cikin gidan sarautar nan akwai wani daki guda daya wanda ba'a shigarshi kuma kai ma baka taba ganin an shigeshi ba, haka ne?"
Kodajin wannan tambaya sai na jinjina kaina nace, tabbas na san da wannan daki kuma na dade ina mamaki da tunani akansa."
Mahaifina ya sake ajiyar zuciya yace, "Akwai wani aljani bawanmu a cikin wannan daki wanda bama bauta masa shima kuma baya bauta mana, amma zaman amana ne da kauna tsakanin zuri'armu da tasa. Duk abinda zai samemu a rayuwa shi wannan aljani ne ke sanar damu.
Zidane kd.
Marubucin ya cigaba da cewa:
==============================
=============================
A iya tsawon rayuwata ta duniya sau daya na taba. Ganawa da wannan aljani kuma shine ya gaya mini cewa kada na kuskura na kara yin aure a rayuwata. Idan kuwa nayi sai an kawo harin yaki izuwa kasata an kawar dani. Yakai dana kaima kayi amfani da wannan nasiha wacce wannan aljani yayi mini kuma kada ka kuskura ka shiga dakin da wannan aljani yake domin ku gana sai ranar daza ka fita wannan gagarumin yaki da aka gaiyaceka. "
Har kullum sarki Uhaisu baya mancewa da wannan jawabi na mahaifinsa don haka sai ya hakura da batun aure gaba daya a rayuwarsa saboda yana son yayi nisan kwana a cikin daular mulki daya tsinci kansa a ciki.
A ranar da wasikar gaiyata izuwa yaki ta riski sarki Uhaisu daga birnin kisra sai yacika da tsananin farin ciki domin yasan cewa lokacine yazo da zai cika babban burinsa na duniya domin yasan mahaifinsa ya gaya masa cewa bayan anyi wannan gagarumin yakinne zai iyayin aure har ya sami magaji kuma lallai zai yi tsawon rai a duniya.
Lokacin da maga-takarda ya gama karanta wasikar gayyata a fadar sarki Uhaisu fadawansa suka ga ya cika da farin ciki sai mamaki ya kamasu domin su a saninsu babu sarki ya tsana sama da yaki kuma babu abinda yafi so sama da zaman lafiya. ™Nasiru Muhammad™
Sarki Uhaisu ya kasance mutum mai adalci, tausayi da jin kai, gashi da karrama mutane, wato bai iya wulakanci ba bashi da izza da jin kai irin na sarakai, duk da cewa allah ya bashi karfi, kyawu da dukiya mai yawan gaske.
Bisa wannan baiwa da allah ya baiwa sarki Uhaisune ya zama cewa 'yan mata, 'ya'yan sarakai, attajirai da manyann matsafa suka kamu da tsananin kaunarsa, wasu da yawansu a dalilin kamuwa da sonsa ne ma suka kamu da cututtuka saboda rashin samun kaunarsa. Wasu ma sanadin ajalinsu kenan.
A duk sa'adda sarki uhaisu ya ci ado kuma yayi hawa ya fito daga cikin gidansa sai dai kaga mata suna fitowa da gudu domin kawai su ganshi. Idan dakaru suna hanasu zuwa kusa dashi sai kaga suna kuka kamar wadanda akayiwa mutuwa.
Duk wacce ta sami nasarar koda taba dikin sa ma kuwa sai kaga sauran mata na rungumeta don su sami albarkaci. Idan kuwa maca tasami nasarar koda taba hannun sarki Uhaisu ne sai dai kaga ta yanke jiki ta fadi sumammiya saboda tsananin farin ciki.
Daga wannan rana kuwa mata sun dinga kai mata ziyara kenan suna bata kyaututtuka ba adadi.
Hakika a tarihin nashiyar kasar tashawar ba a taba samun saurayi mai farin jini ba a wajen mata kamar sarki Uhaisu, kuma labarinsa ya bazu ko ina, har zuwa ake yi daga kasashe daban-daban domin kawai aganshi.
Tabbas duk mutumin da yake shakka akansa da zarar yazo ya ganshi dole yake gasgatawa. Komai hassadar mutun da kushensa idan yayi arba da sarki Uhaisu take yake sallamawa.
Sukansu maroka idan sarki Uhaisu ya fito suka fara yi masa kirari sai masu rasa irin kalmomin dazasu rinka fada wadanda suka dace da shi akwai wani maroki wanda yafi kowa iya kodashi, shine ya kance dashi:
Kaico! Ina gwanin wani ganawa? Ga saurayi uban samari tauraron kyawawa mai magance yunwa da kishirwar yan mata. ™Nasiru Muhammad™
Gaka jarumi. Sarki sadauki mai ragargazar maza yau fa ga mai tekun zinare mai shanye kogunan attajirai. Ga ruwan sanyi mai sanyaya zuciya talakawa kufara nan ga bargon kankara mai kashe gobara daga kogi. Marhaban da babbar gona nomanta sai shekara dubu ! Aduk sa adda marokin ya haukace ya kama sambatu saboda sai da dinare ya rufeshi ruf tamkar an nutsar da shi a cikin yashi tun yana kirari. Ya koma yin waka sannan ya fashe da kuka ya dinga mari da cizon kansa har sai da aka tattarashi shi da dukiyar daya samu aka kaisu gidansa lokacin da sarki uhaisu yaga fadawansa sun cikada mamaki bisa ganin yadda ya kamu da farin ciki don jin sakon gaiyata izuwa yaki. Kuma ya fahim cewa hankalinsu ya dugunzuma ainun sai ya dubesu yayi murmushi sannan yace. ” Yaku yan majalista ku kwantar da hankalinku. Ku sani cewa wannan yaki bai shafi kowa ba awannan kasa tawa face nikadai. Don haka nikadai zan shirya na tafi wannan yaki. ”
Koda jin wannan batu sai mamaki da fargaba suka dada kama yan majalistar wazirin sarki uhaisu wanda ake mazwan ya dubishi cikin tsananin damuwa yace. ” Haba ya shugaban kasani cewa mu da sauran talakawanka muna. Matukar kaunarka kuma tunda ka hau kan karagar mulki bamu taba rabuwa da kaiba dai-dai da rana daya.
Mun tabbatar da cewa idan babu kai babu wanda zai iya yi mana mulki acikin adalci irin naka. Tayaya kake tsammanin zamu iya barinka ka tafi yaki kai kadai ? Katuna fa cewa baka da mai gadonka bare idan muka rasaka musami halifanka?"
Lokacin da waziri yazo nan a jawabinsa sai sarki Uhaisu ya mike daga kan karagarsa yayi tafiya izuwa tsakiyar fadar sannan ya tsaya ya dubi jama'a gabas da yamma, kudu da arewa, kawai sai hawaye ya zubomasa ya ce, "ya ku jama'ar birnin tashwar kuyi sani cewa a iya rayuwata ta duniya babu abinda nake kishinsa kuma ™Nasiru Muhammad™ nake matukar kaunarsa sama da birnina da jama'ata.
Yau shekara a shirin da takwas a duniya amma ban taba zuwa yakiba.
Duk wannan daukaka da ni'ima wacce nake da ita a duniya bata gani ba sai jitake yi kawai.
Yau gashi dama tazo wacce za a sanni. Bugu da kari. Ina mai sanar daku cewa wannan yaki da zan fita ne zan cika babban burina na duniya harna sami damar aure na sami wanda zai gajeni yaci gaba da yi muku irin mulkin da nake muku bayan babuni. "
Koda sarki UHAISU yazo nan a zancensa sai fadar gaba daya ta rude da shewa, mutane suka cika da farin ciki asannanne sarki Uhaisu ya sallami kowa fadar ta watse nan labari ya bazu ko ina a kasar cewa gobe sarki Uhaisu zai fita yaki shi kadai kuma ga sakamakon da zai biyo baya idan ya fita yakin.
Nan fa jama'a suka yi farin ciki da bakin ciki ba face rabuwar daza a yi da sarki izuwa tsawon kwanaki ko watanni ba a san ranar da wowarsa ba. Haka kuma ba a san irin hadarin da sarki zai gamu da shiba akan hanyarsa, babu tabbacin zai iya tsira da rayuwar sa duk da an san irin gagarumar jarumtakarsa amma kuma ai ba a taba ganin kwazonsaba a filin yaki ba.
Dayawa daga cikin jama'ar gari kuwa basu yi bacciba a wannan dare, musamman mata. Duk gidan da kaje sai kaga ana koke-koke tamkar mutuwa akayi.
Yayin da dare ya raba sai sarki Uhaisu ya shiga cikin wannan daki na musamman wanda tunda aka haifeshi bai taba shiga ba.
Kofar dakin a lullube take da yana gaba dayanta alamar cewa an dade ba'a shigaba tsawon shekara da shekaru.
Batare da fargabar komai ba sarki Uhaisu yasa kwagirin sarauta ya share wannan yana sannan yasa daya hannun nasa ya murza marikin kofar dakin nan take kofar ta bude ya kunna kai ciki.™Nasiru Muhammad™
Da shigarsa sai ya ga dakin faba daya a haskake yake da wani irin haske na musamman wanda bai taba ganin irin saba kuma yarasa daga ina hasken yafito. Babu komai acikin dakin face wata farar kujerar karfe guda daya jal a ajiye agefe daya. Sai sarki uhairu ya dubi gabas da yamma. Kudu da arewa na dakin. Amma bai gawata halita nai rai acikiba. Kawai saiya ya juya da baya domin ya fiche daga cikin dakin. Har ya iso bakin kofa yasa kafarsa guda a waje sai yaji an kira sunansa da wata murya wacce tabbas ya taba jin muryar amma sai yakasa tuno mai muryar cikin hanzari da mamaki uhairu ya waigo. Kawai sai yayi arba da wani tsohon aljani. Siriri mai dogon fuska gashin kansa da gemunsa fari ne fat kai da gani kasan cewa yadade aduniya. Aljanin na zaune akan wannan farar kujera fuskarsa cike da annuri. Kallo daya mutun zai yiwa aljanin ya tabbata da cewa yana cikin koshin lafiya domin akwai alamun kuzari a tare da shi babu wata nakasa mai nuna alamu tawaya ko gazawa bisa dalilin tsufa. Aljanin ya sake kiran sunansarki uhaisu akaro na biyu yace. ” Haba dan uwana ya zaka juya ka fito ko gaisawa bamu yiba alhalin yau ne ranar farko da zamu fara ganawa ”. Koda jin haka sai sarki uhaisu ya mai dawa aljanin martanin murmushi yataho gareshi cikin sanyin jiki. Da isowar uhaisu daf da aljanin sai ya mike tsaye cikin girmamawa yayi masa nuni da kujerar da yake zaune akai yace dashi ya zauna. Uhaisu ya dubi aljanin cikin mamki yace. ” Saboda meza kace na zauna akan kujerarka wacce kasaba zama a kanta tun kafin a haifi kakan kakana ? ”. Da jin wannan batu sai kwallah ta ciko a idanun aljanin sannan yace. ” Yakai uhaisu ka sani cewa kaine sarki na arba in da biyar daga cikin sarakan da suka yi sarauta a gidannan kuma kowanne sarki yayi zamaninsa tare dani. Amma gaba ™Nasiru Muhammad™dayansu babu wanda ya shigo cikin dakin nan ya mai da mini da martanin murmushi sai kai kadai.
Kai ne kadai sarkin daya shi shigo wajena cikin kwanciyar hankali da saukin kai bada jin tsoro ko izza ba. Turbude fuska kamar wanda aka aikawa da sakon mutuwa yace. ” Bani ne zan sanar da kai wanna addini ba kai da kanka zaka ganeshi zuciyarsaka ta gamsu da shi “. Koda gama fadin haka sai aljani aznaihul markas ya bace bat tamkar bai taba wanzuwa ba a cikin dakin muryarsa na cewa sai mun sake saduwa idan har ka dawo gida a raye cikin nasara. ”Nan take sarki uhaisu ya fice daga cikin dakin ya janyo kofar ya rufeta. Aikuwa yana rufe kofar sai yaga yana ta sake lullubeta tamkar ba a taba bude kofar ba. Nan dai sarki uhaisu ya tafi izuwa turakarsa zuciyasra cike da sake sake da zullumi abinda ya fara yawo a ransa shine. Bayanin karshe da aljani aznaihul markas yayi masa cewa sai sun sake saduwa idan ya dawo a raye kuma cikin nasara. "
Shin wannan batu yana nufin kenan babu tabbacin zai tsira da rayuwarsa ? Kuma babu tabbacin zai sami nasara acikin burinsa na duniya?"
Nan take hankalin Uhaisu ya dugunzuma. Ya rasa abin da ke masa dadi aduniya, amma da yatuna matsoraci bashi zama gwani, kuma ya tuna shima jarumine sadauki mai tarwatsa maza, sai yaji dukkan tsoro ya kau daga zuciyarsa.
Haka dai sarki uhaisu ya isa cikin turakartsa ya kwanta. Kwanciyarsa keda wuya sai barci ya saceshi domin shidai a rayuwarsa bakin ko kishiyarsa, tunani ko ™Nasiru Muhammad™fargaba basu taba hanashi yin barciba domin ya kasance mutum wanda bai taba sa wani abu a ransa ya dame shiba.
Kashegari kuwa tun da dukudukun safiya sarki Uhaisu ya tashi ya kintsa aka kawo masa wani farin ingarman doki gami da isasshen guzuri. A wannan lokaci sarki uhaisu yayi gagarumar shigar yaki, kuma yasa hular karfe wacce ta rufe fuskarsa idanunsa kadai ake ake gani.
A lokacin ne gaba dayan fadawansa da jama'ar gari suka taru a fadar don yin bankwana da shi. Fadar tacika ta batse babu masakar tsinke duk inda mutun ya duba fuskarsa maza da mata daga masu kwalla sai masu zubar da hawaye saboda alhinin rabuwa da sarkinsu uhaisu.
Yayinda sarki uhaisu yaga jama'arsa acikin wannan hali sai ya kamu da tsananin tausayinsu yaji kamar ya fasa yin wannan tafiya amma daya tuna cewa wannan tafiya itace fa cikar burinsa na duniya sai yaji bazai iya fasa taba.
Nan take sarki uhaisu ya cire hular karfen kansa sannan ya hau kan mumbari dake tsakiyar fadar ya fuskanci jama-arsa ya shiga jawabi na rarrashi gami da ban baki, kuma yanuna musu mushimmancin wannan tafiya da zai yi cewar a dalilinta ne zai samu tsawon rai kuma birninsa zai samu daukaka irin wacce bai taba samuba.
Duk da jin wannan bushara sai jama'a suka ji sudai basa son su rabu da sarki Uhaisu domin ji suke kamar zasu rabu da hanyar kirjinsu.
Lokacin da sarki Uhaisu ya gama jawabinsa ya sauko daga kan mumbari ya hau kan dokinsa ya sanya wannan hular karfe. Koda ya kada linzamin dokinsa ya nufi kofar fita daga fadar sai jama'a suka rude da ihu, kuka da dimauta mata kuwa da yawansu yanke jiki suka rinka yi suna faduwa kasa sumammu saboda bakin cikin rabuwa da masoyinsu wanda suka dade suna begensa a cikin zuciyarsu.
Hakika sarki uhaisu ya cika tauraron samari, maganin ™Nasiru Muhammad™ yunwa da kishirruwar 'yam mata, domin babu wata 'ya mace a cikin birninsa wadda bata kamu da sonsaba face matan aure da tsofaffi. Kai wadansu matan auren ma idan sarki Uhaisu zai auresu zasu iya kashe aurensu haka dai sarki Uhaisu yacigaba da tafiya babu waiwaye, kuma babu sassauci har ya fice gaba daya daga cikin birninsa. Sai da ya kwana ashirin ba daya yana keta dazuzzuka da birane sannan ya isa birnin kisra.
Kafin ya iso birnin kisra yayi arangama da 'yan fashi iri-iri da kuma muggan dabbobin daji amma komai yawansu da karfinsu sai ya ga ya tarwatsasu ya kashe na kashewa, masu nisan kwana kuwa saidai su gudu.
Shikansa sarki Uhaisu yayi matukar mamaki bisa ganin irin jarumtakarsa domin bai taba tsintar kansa a cikin irin wannan haliba na yaki a daji da mutane da yawa ko dabbobi.
Lokacin da sarki uhaisu ya iso fadar sarki Daksur sai ya iske fadar a cike makil da manyan baki da sarakai wadanda ke zaune a can saman fadar kusa da karagar sarki Daksur. A kasa kuwa, sauran dakarun yakine masu yawan gaske wadanda suka rako sarakuna don zuwa wannan gagarumin yaki wanda za a yi abirnin Misra.
A wannan lokaci fadar tsit, sarki daksur ne kadai yake bayani ana sauraron muryarsa, kwazam! Sai akaga mutun yashigo fadar bisa kan doki sanye da kayan yaki ya rufe fuskarsa da hular karfe.
Karar kofatun dokin nasa ne tasa sarki Daksur yayi shiru kuma kowa yajuyo yana kallonsa. Mahayin yaci gaba da tafiya kai tsaye ya durfafi inda karagar sarki take batare daya tsaya ya gabatar da kansa ba.
Koda ganin haka sai dakaru sama da dubu suka yunkura zasu afka masa.
Cikin hanzari sarki Daksur ya daka musu tsawa suka tsaya cak! Shima mahayin dokin sai yaja linzamin dokin nasa ya tsaya a waje guda.
Sarki daksur ya mike tsaye ya tako da kafarsa, yazo har gaban mahayin sannan ya risina a gareshi yace, "lale marhaban da sadaukin sadaukai, kuma sarkin sarakuna na wannan nashiya tamu, mai birnin tashwar wato sarki Uhaisu bin kairuf".
Koda akaji sarki Daksur ya ambaci wannan suna sai idanun kowa ya zazzaro aka cika da tsananin mamaki bisa ganin yadda sarki Uhaisu ya iso fadar shi kadai batare da dakarunsa sun rako shiba, sannan kuma sai kowa ya zuba ido domin yaga fuskarsa domin da yawan jama'a basu taba ganinsaba labarinsa kawai suke ji.
Abinda yakara baiwa mutane mamaki shine, yaya aka yi sarki daksur ya gane cewa sarki uhaisune wannan har ya taso ya taryeshi alhalin ba a gabatar da zuwansaba.
Abinda suika manta shine, sarki daksur babban ™Nasiru Muhammad™matsafine.
Nan take sarki uhaisu ya sauko daga kan dokinsa sai sarki daksur ya rungumeshi cikin tsananin farinciki tamkar wanda yaga dan uwansa na jini.
Batare da sarki Uhaisu ya cire hular karfen dake kansa ba sai sarki daksur ya jashi suka tafi izuwa har can inda karagarsa ta mulki take take suka zauna akan karagar mulkin su biyu. Abinda ya daurewa kowa kai kenan, domin babu wani mahaluki wanda sarki Daksur ya taba girmamawa haka ya darajashi sai sarki UHAISU.
Nan take aka kawowa sarki uhaisu abinci da abin sha iri-iri mai daraja irin na sarakai na alfarma wanda babu kamarsa a wajen sarki uhaisu ya saki jikinsa yaci abinci sosai har sai da yaji ya koshi sannan ya dubi sarki Daksur yace, "a kaini masaukina ina da bukatar na kwanta na huta domin na huce gajiyar tafiyar da na sha ".
Batarte da gardamar komai ba kuwa sarki daksur ya kira wani Hadimi yace da shi ya kai sarki uhaisu izuwa masaukinsa, wani wuri wanda shine mafi kyau da tsaruwa a gaba daya gidan sarautar. Nan take kuwa aka tafi da sarki Uhaisu,
A she gaba dayan sarakan dake zaune a cikin fadar ransu ya baci bisa ganin yadda sarki daksur ya tarbi sarki Uhaisu cikin karramawa da girmamawa fiye da yadda aka tarbi kowannesu.
Bayan bacewar sarki uhaisu da hadimin da ya tafi kaishi masaukinsa sai wani sarki mai ji da kansa wanda ya kasance babban abokin sarki daksur wanda ake kira ma aruf bn saurud ya dubi sarki daksur yace "haba abokina ka tuna fa cewa yau kwanamu arba'in anan muna taruwa kullum muna tattaunawa da shiryawa akan yadda

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login