Showing 3001 words to 6000 words out of 6723 words
Chapter 2 - BAKIN ARTABU 2 Cigaban Jaruma Yazila By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt
tsoron allah ki gaya mini gaskiya ke kanki baki ji kin kamu da sonsa ba ? Rantse da girman iyayenna ban taba ganin kyakkyawan da namiji ba kamarsa gashi da kyan sura. Gashi sarki kuma gawurtaccen jarumi. “ Yazila ta maidawa dabira murmushi sanna tace. “ Ai koda ina sonsa kuwa daga yanzu da na daina sonsa tun har kika yi masa irin wannan yabo. Domin alama ce cewar kin kyasa kema kina so idan har zai karbi addinin allah nan gaba zan tsaya tsayin daka naga kin aureshi “.
Koda jin wannan batu sai hankalin dabira ya dugunzuma ainun tace, "Ai koda nima ina sonsa ba zan yarda na bashi soyayyata ba tonda ke ya gani yace yana SO ba niba. Ina nufin ke ya fara gani, don haka lallai keya kamata ki mallakeshi".
Abu kamar wasa sai gardama ta karde tsakanin jaruma yazila da jaruma dabira. Daga karshe bayan itama Yazila ta sawa Dabira magani sai ta mike tsaye ta fice daga cikin dakin nasu domin kawai ta katse wannan muhawara dake tsakaninsu.
*** *** ***
A can sansanin su sarki Daksur kuwa, lokacin da sarki Uhaisu ya iso bakin tantinsa sai ya sauko daga kan dokin nasa ya daure dokin. Har yayi nufin shiga cikin tantin nasa sai ya fasa ya taka da kafafunsa ya shige izuwa cikin daji ya shige duhuwar wadansu dogayen bishiyoyi ya sami karkashin inuwa mai sanyi kusa da wata korama mai ruwa garai-garai.
Koda ganin wannan korama sai farin ciki ya lullubeshi tun sa'adda yake fafata yaki. Nan take ya tsugunna a gaban wannan korama ya zuba hannayensa guda biyu ya kwarfo ruwan domin ya kai bakinsa ya sha.
Kawai sai yaga hoton fuskar jaruma Yazila a cikin ruwan tana yi masa murmushi.
Nan fa ya kasa shan ruwan ya zubar ya sake debo wani ruwan, aikuwa sai ya sake ganin yazila a ciki, sai da ya yi hakan sau uku sannan ya rintse idanunsa ya sha ruwan. Koda ya bar bakin koramar ya koma karkashin bishiya ya jingina bayansa a jikin bishiyar yaci gaba da ganin yazila a wuri daban-daban tana masa gizo.
Koda ya fashinci cewar idanunsa ne suke yaudarar sa han kalinsa ya duguntsuma ainun don yagane cewa ya fada cikin tekun SOYAYYA kuma tekun da bai san iyakar zurfinsa ba.
Nan fa yaji babu abinda yake so a duniyar gabadaya sama da sake ganin JARUMA YAZILA a zahiri.
Ta yaya zan sake ganinta har ya nuna mata abinda ke zuciyarsa ko ya furta da bakinsa alhalin ta kasance abokiyar gabarsa suna kokarin hallaka juna ? Yanzu haka ma ai yazila tana can cikin birnin misra kuma an kule kofar garin.
Koda ba a rufe ba ai baza a barshi ya shiga ba domin ana ganinsa maza a afka masa don hallakashi.
Nan fa sarki Uhaisu ya fara tunanin zuci yana mai cewa, Ai kuwa idan sarautata da jarumtakata basu sana mallaki wannan kyakykyawar budurwa ba, to kuwa basu da wani amfani a gareni".
Nan take sarki Uhaisu ya kudurce a cikin zuciyarsa cewar ta kowanne hali sai ya tabbatar da cewa ya mallaki Jaruma yazila.
Al'amarin sarki daksur kuwa, lokacin da suka dawo sansanin su inda suka kafa tantinsu sai suka ga dokin sarki Uhaisu a daure a kofar tantinsa sai suka yi tsammanin ko yana ciki dan haka sai sarki ya tura aje akirawoshi a gaya masa cewa yaje tantin sarki Daksur domin su tattauna dan gane da wannan gagarumar matsala da aka samu a filin yaki.
Kai tsaye sarki daksur da sarkin yakinsa da dukkan sauran wakilan sarakunan da suka halarci wannan yaki suka dunguma suka shiga cikin tantin sarki Daksur aka zauna aka fara tattaunawa dangane da a bubuwan da sukafaru a wannan yaki na ban al'ajabi wanda miliyoyin mutane suka kasa kawar da 'yan tsiraru.
Ana cikin wannan hali sai manzon da aka tura tantin sarki Uhaisu ya shigo ya sanar da sarki Daksur cewa sarki Uhaisu baya cikin tantin.
Koda jin haka sai hankalin sarki Daksur ya duguntsuma ainun yarasa abinda kemasa dadi. Nan take ya tashi mutun goma yace su bazama neman sarki Uhaisu a cikin daji.
Bayan tafiyar mutane goman ne sarki daksur ya dubi jama'ar tasa cikin nutsuwa yayi gyaran murya. Sannan yace, "ya ku rundunar karya makiya kuyi sani cewa a duniya ba a taba yaki na ban mamaki irin wanda aka linka abokan gaba sau dubu amma suka zo suka gagara. Babban wani abu daya bani tsoro kuma ya firgitani shine ganin yadda a bin dogaronmu sarki uhaisu ma ya sare a wannan yaki koda yake ba sarewa yayiba, ga dukkan alamu akwai wani abu daya faru gareshi.
Ko dai sihirin wadannan abokan gaba tamu ya shigeshi ko kuma ya fada tarkon soyayya domin tabbas ya sami damar da zai kashe daya daga cikin jaruman matan nan walau Yazila ko Dabira amma sai ya fasa. Ina kyautata zaton dai abinda nake zargi gaskiyane. Koma dai menene ai an ce waka abakin mai ita ta fi dadi. Idan ya zo zai yi mana bayani da bakinsa.
Yaku 'yan uwana ina so kusani cewa wannan ita ce kadai damar da muke da ita wacce zamu iya hallaka wadannan abokan gaba tamu. Idan muka yi sakaci aka tashi daga wannan yaki bamu baje birninsu. Ba mun kama dukkan mazajensu mun yankasu,sannan mu afkawa matayensu muyi ta saduwa dasu har sai sun haife irinmu to har abada bazamu sami nutsuwa da kwanciyar hankaliba a wannan nashiya domin sai an wayi gari ma sun rushe dukkan addinanmu kuma sun kama kasashenmu".
Lokacin da sarki daksur yazo dai-dai nan. Zancensa wadannan mutane goma da aka tura neman sarki Uhaisu suka shigo cikin tantin.
Take suka zube kasa a gaban sarki babban cikinsu yace, "ya shugabana mun duba ko ina a cikin wannan daji bamuga sarki Uhaisuba a nan kusa ba, kuma bamuga inda sawayensa sukeba" koda sarki daksur yaji wannan batu sai hankalinsa ya dugunzuma ainun ya mike tsaye zumbur yace, "ai kuwa bamu ga ta zamaba domin nasararmu a wannan yaki ta dogara ne akan kokarin sarki Uhaisu, yazama dole muje mu nemoshi mu dawo dashi wannan sansani namu kafin a sake busa kahon cigaba da wannan yaki"
Koda gama fadin hakan sai sarki Daksur yaja dakaru sama da mutum dari uku suka nausa izuwa cikin daji.
====================================
Anan zamu dakata
Amma Kafinnan nine Nasiru Muhammad Tijjani nake cewa ku kasance tare dani
[7/2, 11:12 PM] ᴬᴮᵁᴮᴬᴷᴬᴿ Quyraemey: ***★BAKIN ARTABU**cigaban
**JARUMA*YAZILA★***
Littafi Na Daya {2}
TYPE B
***Nasiru**Muhammad**Tijjani***
Marubucin ya cigaba da cewa:
==============================
=============================
AL'amarin Sarki Uhaisu kuwa lokacin da tunani ya addabe shi sai kawai ya yanke shawarar kawai ya tabi birnin kisra ya mika kansa amatsayin ganimar yaki wata kila ya sami damar da zai sake ganin kyakykyawar fuskar yazila a karo na biyu koda kuwa zai rasa rayuwarsa.
Koda sarki Uhaisu yagama aiyana hakan a cikin zuciyarsa sai ya zagaye ta bayan tantin sansanin nasu ya bita cikin duhun ciyayi da rub da ciki har sai da yayi tafiya mai nisa ya isa bakin kofar birnin misra ba tare da ya rike makami ba.
Batare da shakkar komai ba sarki Uhaisu ya durfafi bakin kofar inda dakaru masu gadi suke tsaitsaye wa danda adadinsu yakai mutum dari uku.kowannensu rike da kwari da baka ya dameta iya karfinsa.
Harsun yunkura zasu saki harbi sai shugabansu ya daka musu tsawa yace, "kada dayanku ya kuskura yayi harbi shin bakwagani abokin gabartamu bai zo da makami ba, kuma shi kadaine ya durfafomu? Ku tsaya yazo muji abinda ke tafe dashi".
Duk dajin haka dakarun basu saki jikinsuba, kuma basu sauke makamansuba, sai suka jirashi.
Ai kuwa yana isowa kusa dasu wasu suka rufeshi daduka har suka kaishi kas, a garin hakanne suka fasa masa baki da hanci saiga jini yana yoyo.
Nan dai suka turmusheshi. Da karfin tsiya suka sanya masa sasari a hannayensa da kafunsa, a sannan ne aka bude kofar birnin aka tusa keyarsa gaba aka shiga da shi ciki aka sake rufe kofar.
Kai tsaye aka nufi fadar sarki Raihan da shi, dakaru kimanin mutum dari na kewaye da shi rike da makamai suna rakashi.
Duk da cewar dakarun na rike da makamai a tsorace suke gani suke kamar ko yaushe zai iya tsinka sasarin jikinsa ya hallakasu. Babban ma abinda ya daure musu kai shine, tunda aka shigoda shi cikin birnin sai kalle-kalle ya keyi yana ta murmushi kai kace wanda akayiwa albishir ne da sarautar duniya duk da wulakancin da akai masa bai dameshiba.
Shi kansa yan mamakin yadda ya tsinci kansa a cikin wannan matsayi, don haka sai ya fara zancen zuci yana mai cewa aransa.
"Hakika SO makaho ne, domin idan yakama mutum idanunsa rufewa suke yi kuma hankalinsa gushewa yakeyi har ya aikata abinda zai zubar da kimarsa da darajarsa. Yanzu in banda aikin SOYAYYA ya za ayi nabari na wulakanta haka a matsayina na sarki mai isashshen iko kuma sadauki mai jarumtaka taban al'ajabi. "
Tun kafin su isa gidan sarauta da sarki Uhaisu labari ya riski Sarki Raihan cewa gashi nan an kamo sarki Uhaisu.
Koda jin haka sai sarki Raihan yace karyane, wannan ai zan cen banzane zancen wofi. Ya ya za a zo masa da abin da bazai taba yuwuwaba? Ai ko dakarunsa ne na yaki zasu taru bazasu iya kamo sarki Uhaisu ba da karfin tuwo ba".
Sa'adda manzon da ya kawo labarin yaji abinda sarki raihan yafada sai ya rantse masa da girman allah akan cewa labarin da yazo da shi na gaskiyane, amma idan sarki yana shakka ne to yaje da kansa yaga zahiri ko kuma ya saurara a iso da sarki Uhaisu domin ana hanyar kawoshi nan fada".
Koda jin wannan batu sai farin ciki ya lullube sarki raihan yaji ma ba zai iya jira ba.
Nan take yasa aka kawo masa dokinsa ya hau sannan yasa aka shirya dakarun yaki sama da mutum dubu uku suka take masa baya suka bi hanya.
Ai kuwa suna isa tsakiyar gari suka hango sarki Uhaisu a daure cikin sasarai an taho da shi ana ingiza keyarsa a wulakance. Cikin tsananin mamaki sarki Raihan yaja linzamin dokinsa yatsaya cak, suma dakarun dake bayansa sai suka yi cirko-cirko.
Koda aka iso da sarki Uhaisu daf da sarki raihan sai aka tsaya cak aka kama kallon tsakanin Raihan da Uhaisu, a lokacin da uhaisu yake ta faman murmushi.
Sarki raihan ya kurawa uhaisu idanu ya kare masa kallo tsaf cikin nutsuwa sannan yace, "yakai wannan sarki, kai kuwa menene dalilin daya sa ka kawo kanka garemu alhalin karfimmu bazai iya sawa mu kamakaba?
Tabbas ruwa baya tsami banza, lallai akwai dalilin daya sa ka kawo kanka cikin ruwan sanyi. Ko dai kana son ka yaudaremu ka cutar da mu, ko kuma kana da wata bukata a wajenmu wadda bamu santa ba. Kayi min bayani na gaskiya ko yanzun nan nasa a hallakaka".
Lokacin da sarki Uhaisu yaji wannan batu sai yayi murmushi yace, "ya kai wannan sarki kayi sani cewa na rantse da girman iyayena da kuma darajar karagata banzo gareku domin na yaudare kuba kona cutar daku ba nazo ne domin ina da wata bukata guda daya a wajenku wacce sai ni da kai zan iya fadinta".
Koda jin wannan batu sai sarki raihan ya cika da tsananin mamaki, kawai sai sarki raihan ya cika da tsananin mamaki, kawai sai ya dubi dakarun dake janye da uhaisu ya basu umarni su kwanceshi. Nan fa dakaru suka tsorata ainun suka kama noke-noke, har sai da sarki ya daka musu tsawa sannan suka cika umarni. .
Maimakon sarki raihan ya sake hawa dokinsa sai ya jera tare da sarki uhaisu a kas suka tako kafafunsa suka nufi fada su biyu kacal tamkar sun kasance aminan juna. Domin tuni sarki raihan ya sallami dakarunsa gaba daya sunyi gaba.
Lokacin da sarki uhaisu da sarki raihan suka jero suna tafiya sai suka kama hira, inda sarki raihan yace, "ya kai abokina yanzu ai saika sanar dani dalilin daya sa ka kawo kanka garemu tunda babu mai jinmu".
Koda jin haka sai sarki uhaisu yayi murmushi ya ce "haba abookina hanzarin me kakeyi ne haka ? Ai a matsayina na bakonka kamata yayi ka bani masauki tukunna da abinci domin na huta sannan sai muyi magana cikin nutsuwa".
Koda jin haka sai sarki raihan yayi murmushi ya ce "ka gafarceni, hakika nayi kuskure kuma nayi gaggawa amma ba komai ne yajanyo hakan ba face tsananin kaguwa da zumudin sonjin bukatarka da kazo mana da ita tunda aka fara wannan tafiya a cikin birnin misra sarki uhaisu ya cika da tsananin mamaki bisa ganin yadda mutanen garin suke tafiyar da harkokinsu sabanin irin na jama'ar birninsa.
Abinda ya fara daure wa sarki uhaisu kai shine, duk inda suka gifta sai yaga mutane cikin shiga ta mutunci maza da mata babu inda yaga anyi shiga mai nuna tsaraici.
Kowa ya kalla kuma sai yaga ko dai yana sana'a ne ko kuma yana gabatar da wani aikin mai muhimmanci, ko sau daya baiga inda ake ashararanci ba ko wata dabi'ar banza wacce bata dace ba nan take sarki uhaisu yaji dabi'ar mutanen birnin misra ta burgeshi gami da bashi mamaki domin shi irin labaran da ake kai masa akansu ba haka ya gani ba da idanunsa.
Lokacin da suka zo zasu gifta ta masallaci kuwa ya hango mutane a ciki wasu suna nafilfilu wasu kuma suna karatun Qur'ani sai nan take yaji tsikar jikinsa ta tashi gaba daya yagane cewa lallai wannan addini addinine wanda yakamata ba tsangwamawa ba. Saboda ana yinsa ne a cikin hankali da nutsuwa.
Addini ne wanda yakamata ayi bincike sosai a kansa domin a gano gaskiyarsa ko rashin gaskiyar.
Haka dai raihan da uhaisu suka ci gaba da tafiya har suka iso cikin gidan sarauta.
Duk inda suka ratsa sai kaga mutane suna ratsewa da rakubewa cikin alamar tsoro domin gani suke yi kamar ako yaushe sarki Uhaisu zai iya birkicewa ya hau mutane da sara da suka amma har suka iso tsakiyar fadar babu abinda ya faru.
Abinda ya daurewa sarki raihan kai shine, yaga sarki Uhaisu yana ta waige-waige da kalle-kalle alamar cewa so yake yaga wani.
Abin tambayar anan shine waye wanda sarki uhaisu ke son gani kokuwa wata makarkashiya ya shirya ne so yake jama'arsa su hauro katangar birnin su afkamusu da yaki? Koda gama aiyana hakan sai kuma wata zuciyar ta ce da shi "ai kuma hakan bazata taba yiwuwa ba tunda akwai dakaru akan ganuwa wadanda suke kula da tsaro dare da rana, ko yaya suka ga wani abu zasu gaggauta sanarwa bayan sun iso tsakiyar fadar sai sarki raihan ya kirawo sarkin gida ya umarceshi da yakai sarki uhaisu izuwa ga masuki na musamman inda aka saba saukar manyan baki.
Har sarki uhaisu ya budi baki zai tambayi sarki Raihan wani abu sai kuma yafasa.
Raihan ya dubeshi cikin murmushi yace, Bakinnan naka akwai magana. Amma kuma kayi shiru bakace komaiba".
Sarki uhaisu ya maidawa sarki raihan martanin murmushi yace, "babukomai idan muka zauna don tattaunawa zaka ji komai".
Nan take suka yi sallama sarkin gida ya tafi da sarki Uhaisu izuwa ga masaukinsa.
Har suka yi nisa a cikin gidan sarautar suka kule sarki Uhaisu bai daina waige-waige da kalle-kalle ba. Kai da gani ka san cewa a cikin zakuwar son ganin wani yake.
Lokacin da sarki Raihan ya isa turakarsa ya kwabe damarar dake jikinsa sai ya shiga kewaye sannan ya fito ya zauna a harabar turakarsa yana alwala domin ya tafi masallaci saboda lokacin sallar azahar ya kusa.
A dai-dai wannan lokaci ne ya hango jaruma Yazila da Jaruma Dabira sun taho gareshi da sauri fuskokinsu na nuna alamun tsananin damuwa da fargaba.
Da isowarsu daf da shi sai suka durkusa suka kwashi gaisuwa sannan suka yi shiru har sai da ya idar da alwalar sannan Dabira tayi gyaran murya tace "ya kai abbanmu kayi sani cewa labari ya riskemu cewa sarki Uhaisu ya shigo cikin birnin nan harka bashi masauki acikin gidannan.
Bayan su dabira sun koma tura karsu sun zauna Dagacan sai Dabira tayi ajiyar zuciya sannan ta dubi YAzila tace, "yake 'yar uwata nifa abinda na fahimta shine, sarki Uhaisu ke ya biyo.
Duk yadda akayi tunaninki da begenki ne suka addabeshi yakasa hakuri, shine ya sallama rayuwarsa ya kawo kansa domin kawai ya kashe kishirwar rashin ganinki".
Koda jin wannan batu sai jaruma Yazila ta hade fuska cikin alamun fushi tace, "Ai wannan tunanin naki dai-dai yake da mafarki, yaya za a yi sarki kamar Uhaisu mai daraja, daukaka da jarumtaka haka zai zubar da kimarsa da mutuncinsa saboda kawai soyayya?
Ni kam ina kyautata zaton lallai akwai wani mugun nufi a zuciyarsa amma ba wai soyayya ba".
Sa'adda dabira taji wannan batu sai ta kyalkyale da guntuwar dariya sannan tace, "ko da yake dai ni dake duk bamu taba yin SOYAYYA ba, amma ai ga yadda muke samun labarin zafinta da sharrinta babu abinda masoyi ba zai iya yiba domin ya mallaki masoyinsa.
Ko shakka bana yi saboda ke sarki Uhaisu ya mika wuyansa.
Ni shawarar da zan baki itace, idan har zai karbi addinin allah toki amince masa ya aureki domin yin hakan zai janyo miliyoyin mutane su karbi musulunci. Idan kuwa hakan ta faru ladan daza ki samu ba kadan bane.
Koda jin haka sai yazila tayi murmushi tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa yadda nake kaunarki a yanzu cikin zuciyata nafi son ace kece kika sami wannan lada mai tsoka bani ba. Kuma duk yadda zanyi saina yi domin na tabbatar da cewa kece kika samu wannan lada. Kada ki sake zuwa mini da uzurin cewa ni sarki Uhaisu ya fara gani kuma nice wadda ya kamu da SO Ina soki gane cewa ni dake kammanninmu daya ne sak tamkar an tsaga kara.
Ko a yanzu in banda mahaifiyarmu babu wanda yake iya bambantamu a zahiri. A matsayina na wacce ta fara zuwa duniya kafin ke, naci girma na bar miki sarki Uhaisu idan har ya karbi addinin musulunci.
Idan kuwa yaki karbar musulunci tofa dani dake duk zamu hakura da shi".
Lokacin da yazila tazo nan a zancenta sai hawaye ya zubowa Dabira ta kama kafadun Yazila ta rike tace, "yake 'yar uwata kiyi sani kina son ki dora mini nauyin da zuciyata bazata iya dauka ba. Na rantse da girman iyayenmu indai kina raye bazan iya auren mijin dana san cewa sonsa ya darsu a zuciyarki ba koda kuwa gwargwadon kwayar zarra ne. "
Koda gama fadin hakan sai Dabira ta juya da sauri ta fice daga cikin turakar tana ta zub da hawaye, Yazila na kiranta amma sai taki