Showing 6001 words to 6723 words out of 6723 words
Chapter 3 - BAKIN ARTABU 2 Cigaban Jaruma Yazila By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt
komowa.
Al'amarin da yai matukar girgiza hankalin Jaruma yazila kenan, ta rasa abinda kemata dadi a duniya kuma taji kamar ta dora hannu aka ta rafka ihu.
Al'amarin sarki Uhaisu kuwa, bayan yaci ya sha yai hani'an sai ya baje akan gado.
Abinka da gajiyayye nan da nan jikinsa ya mutu amma duk da haka sai barci ya gagareshi saboda tunanin zuci nan fa yaji kamar ya mike tsaye yaje ya nemi iso a wajen sarki raihan domin su gana ya sanar da shi abinda ke ransa, amma sai ya kanne domin kada ya nuna zalamarsa.
Haka dai sarki Uhaisu yayi ta juye-juye akan gado ya rasa sukuni har tsawon sa'a biyu. Yana cikin wannan hali sai kawai yaji an kwankwasa masa kofa.
Cikin hanzari ya mike tsaye yaje ya bude kofar kawai sai yaga sarki Raihan a tsaye fuskarsa cike da murmushi.
Sarki raihan ya dubeshi yace, "ka gafarceni ya kai abokina, kayi sani cewa na kasa yin komai saboda zakuwa da son jin bukatar da zaka zo mini da ita, shiya sa na zo maka yanzu tun gabannin ka sami cikakken hutu".
Sa'adda sarki Uhaisu yaji wannan batu sai yayi murmushi yace, "ya kai abokina kayi sani cewa irin halin da kashiga nima haka na tsinci kaina, don haka yanzu sai mu zauna na sanar da kai bukatar da na zo maka da ita nan take suka zauna a tare bisa gefen gado. Sarki Uhaisu ya nutsu kuma yai gyaran murya yace, 'ya kai abokina kayi sani cewa a iya sani rayuwata tun daga kuruciyata kawo izuwa girmana ban san daci da zakin so yayyaba sai a yanzu dana halarci wannan yaki da muka fafata mu daku.
Ina mai sanar da kai cewa na rasa sukuni da kwanciyar hankali sakamakon kamuwa da tsananin son jarumtar wacce tayi yaki dani. Tun a lokacin dana sami nasarar bugeta ta fado kasa a galabaice har hular karfen dake kanta ta cire, ina yin arba da kyakykyawar fuskarta na kamu da sonta nan take.
A cikin kowacce da ika begenta nake, a yanzu haka idan ban gantaba a yau dinnan rayuwata zata iya shiga cikin mugun yanayi.
Ni yanzu a binda nake so da kai shine ka bani auren wannan jaruma a shirye nake na dawo bangarenku a wannan yaki muddin zan samu wannan biyan bukata, kuma duk abinda kuke bukata na dangane da dukiya zan bayar.
Kai in takaice maka ma ko karagata kake so zan iya baka ita muddin zan mallaki wannan jaruma domin babu wani abu da yakai matsayinta a cikin zuciyata".
Lokacin da sarki Uhaisu yazo nan a zancensa sai sarki Raihan ya cika da tsananin mamaki domin bai taba tunanin cewa wannan ce bukatar da sarki Uhaisu zai zo masa da itaba.
Sarki raihan ya sunkui da kansa kas, alokacin da ransa ya baci, zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone don haka sai ya dubi sarki uhaisu a fusace yace, "A ina ka taba ganin ruwa da wuta sun hadu a waje daya?
Kai kafirine mu kuwa musulmine, babu yadda za a yi mu baka auren 'yarmu idan har kana son na baka auren wannan yarinya dole ne kayi abu uku.
Abu na farko shine, dole kakarbi addinimmu. Abu na biyu, dole ne ka je ka yankomin kan sarki daksur da kan sarkin yakinsa.
Abu na uku wanda shine na karshe, dole ne kaje ka kafa tutar addinin musulunci a birninka da birnin sarki Daksur.
Duk sai na tabbatar da cewa ka sami nasarar aiwatar da wadannan abubuwa guda uku sannan zan baka auren wannan 'ya tawa"
Lokacin da sarki Raihan yazo nan a jawabinsa sai idanun sarki Uhaisu suka ciko da kwalla yace, "tabbas kazo min da manyan al'amura wadanda bazan iya gabatar dasuba don kawai biyan bukata taba.
Kafin sarki uhaisu ya gama rufe bakinsa tuni sarki raihan ya tafa hannayensa sau biyu kawai sai sarki Uhaisu yaji anmaka masa makami akeyarsa.
Nan take ya sulale kasa maga shiyan cikin mummunanan hali.
Nan take wasu dakaru su uku suka baiyana suka turmushe sarki Uhaisu aka sake zuba masa sarkoki a hannunsa da kafafuwansa.
Sarki raihan ya dubi dakarunsa yace, "kutafida shi izuwa kurkuku ku kulle shi.
Nan take kuwa dakarun suka dauke sarki Uhaisu suka fice dashi.
~WANNE MATAKIN SU SARKI DAKSUR ZASU DAUKA IDAN BASUGA SARKI UHAISU BA?
~SHIN ZA A CIGABA DA WANNAN YAKI NE KO KUWA ZA A DAKATAR DA SHI?
~TSAKANIN YAZILA DA DABIRA WACECE ZATA MALLAKI UHAISU?
Muhadu a BAKIN ARTABU na uku don jin cigaban wannan kasaitaccen labari