Showing 213001 words to 216000 words out of 419207 words

Chapter 72 - Sarka Book Complete By Zainab Idris Makawa.doc

Mun shiga weekend hakan yasa washe gari ban fita zuwa ko ina ba gyaran gida nayi kamar yadda na saba yi din idan weekend yazo.
Sam ban sa rai da zuwan shi gidaba a ranan don ban ma saka shi a ido ba tsawon kwanaki ke nan.
Kwatsam ya fado min gidan kallon yanayin shi kawai da nayi nasan baya cikin hayacin shi a lokacin saidai halin sa sai ka fahunce shi zaka gane hakan.
Ina mai sannu da zuwa ya amsa da yawa yana zama saman kujera dan nisa dani kadan ya samu yakai zaune.
Kamar yadda anty ta fada min idan ya share ni in kula shi tunda halin sa ne kusan hakan.
Mikewa nayi na dauko mai abin sha na kawo mai gaban shi na aje na koma inda na tashi ina dan satan kallon shi.
Kallon inda yake zaune nayi na dan kura mai idanu cikin daurewa karo na farko zan gwada shawaran anty farida a fili nace.
Yaya me yake faruwa da ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????kaine ne na ganka a cikin wani yanayi na damuwa yau din ?
Yayi firgigit ya dawo cikin yanayin shi tare da dago kai ya dan kalleni kafin ya dauki lemon da na aje mai yana tsiyayawa kadan.
Haka ina kallon shi ya dan kurba kadan jiki babu kwari ya aje cup din saman table ya maida kanshi saman kujera tare da lumshe idanuwan shi gami da dafe goshin.
Na mike kamar yadda tace in daina jin tsoron shi in dinga fuskantar shi kai tsaye kada in nuna darin shi ko tsoro idan zanyi magana dashi nace.
Yaya ka fada min may ya samay ka ko da wani taimakon da zan iyayi sai inyi maka don Allah yaya kada kace zaka boye min damuwan ka ni kamar yar kace ko kanwaka ta jini a nan.
Hannun shi daya dafe goshin shi ya cire daga jikin shi yana kallona sai kawai naga ya dan zamo yana dan kallona a cikin mamakin kalamina.
Sai da ya kaea dubana da kyau sai ya tsunci kanshi da bani amsa kai tsaye a lokacin don ba wanda zai amayarwa zuciyan shi yadda yake ji din.
Fatima ina cikin tashin hankali sosai tun jiya da aka bugo min waya daddy baida lafiya kwana uku ke nan bai farfado ba.
Gaba daya na mayar da kallona gare shi cikin damuwa da tashin hankalin abindaya furta a lokacin.
Nace ya umar wai kawuna kake nufin baida lafiya har hakan yace tun jiya Aliyu ya bugo min waya yana sheda min nayi kokarin yau din nan in wuce zuwa Nigeria sai dai hakan bai samu ba gareni.
Bai farga da halin da nake ciki ba a lokacin sai daga baya ya kula da yanayin dana shiga a rude ya tashi zuwa kujeran danake zaune ya fara jijigani a hankali.
A rude yake kiran sunana yana son tabani yana jin shakku yi hakan gareni.
Ba yadda ya iya ya dagoni dole badon yaso ba ya fara jijigani a hankali kafin ya juya inda ruwa dana aje mai ya dan debo yana yayafa min.
A jiya zuciya na sauke a hankali tare da kokarin bude idanuwana a hankali na sauke a gare shi.
Yace ke fatima da dan karfi nace yaya idan kawu ya mutu na shiga uku a duniyan nan kawu da mamu sai Ammane kadai masu sosai a kano sai ko kakata data haifi mahaifina manjo da take misau zaune a yanzu cikin halin rashin lafiya ko yaushe.
Ido ya zuba min yadda nake magana kamar wata wacce bata cikin hankalin ta zama yayi gefen kujeran da nake zaune a kai yakai hannun shi a hankali ya rike hannayena yana fadin.
Waya fada maki kawun ki zai mutu a yanzu attack kawai ya samu karancin kayan aiki na kasan mu shine dalilin da yasa nake son zuwa a san yadda za ayi muzo dashi nan a dubashi.
Din haka ki kwantar da hankalin ki kefa kika ce in fada maki zaki iya taimaka min baki taimaka mi din ba kuma kina kokarin ki kara sakani cikin wani tashin hankali yanzu bayan wanda ke gaba a yanzu ?
Yaya kayi hakkuri na daina daga ma hankali don Allah ka samowa kawuna lafiya ban son wani abu ya samu kawu a duniyan nan na fada gwanin ban tausayi.
Kafadana ya dafa a hankali yana mikewa tare da fadun insha Allahu kawun ki zai samu lafiya very soon ya fada ya fara tafiya a kasalance.
Yaya yaushe zakaje can din nima in shirya mu tafi na fada kamar wata yar karamar yarinyar da bata da wayau.
Dan juyowa yayi ya kalleni da mamaki kamar na isheshi a lokacin da surutu yace karatun naki yaya zakiyi dashi .
Bayan hakan ai nan zamu dawo tare dashi a duba lafiyan jikin shi idan mun tafi dake wa zai tare mu a nan ya fada yana tsureni da ido.
Sai kuma ya juya ya fara tafiya bayan yaga na dukar da kaina a kasa kamar ina tunane lokacin.
Har ya shiga dakin shi yana tunanen wani itin so da shakuwane haka tsakanin mu da daddy su don yanzu ya fahinci yadda shima daddy yake ji da al,amarin nawa a ranshi duk da yana boyewa don sauran iyalin shi.
Shiga yayi ya zauna a bakin gadon shi tare da hade hannayen shi guri daya ya sauke kanshi kasa yana tunane.
A gaskiya yayi kuskuren rike wanan yarinyar da kowa ke nanata mai ya rike amana marainiyar Allah a kasan mutane.
Yasan dole yayi hakan don kare mutuncin shi da lafiyan shi saidai kuma yasan rabuwa da fatima kamar yadda ya shirya zaiyi .
Hakan zaiyi matukar yin nadaman hakan mara adadi a rayuwan shi dolene yayi hakkuri da zabin mahaifin shi a gareshi.
Don a yadda ya fahinci yarinyar tana da saukin kai gara yabita a sannu yana kwantar mata da hankali tunda tana mashi biyayya yadda yake so.
Amma sai ya biyewa zugan shedan wanda haksn ke nufin bijerawa mahaifin shi a rayuwa yayi ke nan.
A yanzu zai yaki zuciyar shi akan zama da wanan yarinyar ko a hakan da yake mata sai dai zai rage daure mata fuska da takuran da yakeyi din ya bata freedom din ta a matsayin tana yar adam dayasan yana tauye mata.
Sai dai merry ce matsalan shi yanzu don sanin dokar kasan nan daman shi ma da yake suna zaune a central London inda kowa ke iya yin al,adun shi a nan kai tsaye don da dama sosai sama da American.
Yasan zasu kwasa da merry duk ranan da ta fahinci fatima matar shi ce ta aure matar da iyayyen shi suka zaba mashi ya aura a rayuwan shi.
Kwance yakai yana sauke ajiyan zuciya a hankali yana ci gaba da tunane tare da shirya abubuwa da dama a ranshi.
Wayan shine yai kara ya dauka Steven ne abokin shi yake fada mai an gama komai na tafiyan shi a cikin daren nan zasu tashi.
Bayan gama wayan ne ya mike ya shiga bandaki ruwa ya watsa a jikin shi tare da dauro alwala ya fito ya tayar da sallah ya jima a gurin yanawa mahaifin shi addua kafin ya mike ya shirya duk abinda zaiyi tafiya dashi don merry bata kasan tana can American ya barta a can gurin aikin ta.
Sai yamma lis ya fito ya samu har na hada abinci nayi mamakin ganin shi yau yana magana dani tun kan ya sauko kasa yace yar gidan kawu har yanzu tunanen kawun kike ko ?
Ina zaune nayi tagumi da hannayena kafauwana suna saman kujeran na takure a wurin daya tare da zubawa kasan falon ido.
Yace shike nan yau dai nayi maki Aprilfull don na ga yadda kike son kawun ki da mamaki a fuskana na dago kai ina kallo shi yadda yake magana kamar bashi ba yau.
A dan maraice nace yaya dama wasa kake min don Allah kasani a wani hali da ban taba shiga ba a rayuwata ?
Yaya bana son in rasa kawu yanzu kamar yadda na rasa mahaifina a baya tun ina karama bai more min ba shine nake tunanen yanzu idan na rasa kawu fa ?
Ba zaki rasa kawun ki ba Fatima ya fada yana jawo kujera ya zauna naso ma in kira maki shi sai dai nasan zaki iya fada mai gwada kin da nayi yai min fadan hakan.
Ba zan fadawa kowa tsakanina da kaiba yaya ka yarda dani mamu ta haneni da yayin hakan tace in zama mai boye sirin tsakanin mu.
Kallin wata yar karamar baby yake min mara wayau ga yadda nake fadin magana abincin ya fara budewa yayin da nake sake ajiyan zuciya daga inda nake zaune din.
Bai kara magana ba ya gama ya fita ina zaune mamaki ya cika min ciki wai yau ni yaya kewa April full a gidan nan in dai hakane yako kamani da kyau sosai don na shiga wani hali a lokacin.
Ya dan jima bai shigo ba da zai dawo ne sai gashi da kayayakin abinci dans sha kala kala ana shigo min dasu gidan ina dakina lokacin don haka har yagama jida ya kai min store dina ban san hakan ba.
Bayan isha,i ya leko dakina yana fadin in rufe gida zai tafi can gidan ya kwana yana da aikin da zaiyi a can din sai da safe nayi mai ya tafi ya barni da mamakin sauyawan shi a raina.
Ashe Steven yazo ya dauke shi tafiyan ke nan Nageria yayi ban sani ba nikan yana fita na rufo gidan tare da kashe komai na kwanta sai safe.
Da safe koda na tashi ban tsaya komai ba shirin fita nayi do har lokacin ina ji zuciyata babu dadi daga wasan ciwo kawn da yayi min din .
Duk da ya kamata inji dadi hakan ganin sakin fuska harda wasa irin na al,adan nasara da yai min a karo na farko do har lokacin kaina bai kawo wuta ba in gane cewa watan April ya wuce ai tun lokacin bukin su merry .


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:18 - ??5惙5惙5?: ASSALAMU ALAIKUM WARAMATULLAH, , , , , ,

Washe gari bayan na gama komai har nayi wanka na shirya banji duriyan ya umar ba gidan.
Har nakai kofa zan fita na dawo don in sallamay shi kamar yadda anty farida ta fada min in dingayi idan yana gida.
Na tura kofan a rufe yake sai mamakin hakan ya kamani don bai faye rufe kofan shi ba idan yana gidan.
Juyowa nayi da niyar in wuce takardan dana hango ne saman dining table aje yasa na sauko da sauri na isa gurin na dauka ina dubawa.
Fatima nayi tafiya ban sani ba ko in dauki lokaci ban dawo ba komai da zaki bukata na amfanin gida na tanadar maki shi a store da fatan zaki kula da kan ki daga yayan ki umar.
Kamar ba school zanje ba a lokacin sai naga nz kai zaune ina faman tunane a raina gabin zan batawa kaina lokaci yasa na mike na rufo gidan na tafi.
Da kyat na samu mota don bus sun dan wuwuce saboda sakkon da mutane keyi zuwa wurin aiyukan su na yau da kullun.
Na kusa makara don ina shiga mai koya muna na shigowa lokacin haka akai lecture rabin hankalina yana ga tunanen ina yaya ya tafi.
Karfe daya saura muka fito daga daukan darasi don yin break da sallah a ka,idan makarantan kamar kullun duk wanda zaka hadu dashi a irin wanan gurin muke haduwa din girman makarantar ya baci department ne kala kala gasunan sai inda idon ka ya tsaya.
As usual mun san inda muke zama mu hadu a kullun a gurin na samu anty farida tana waya samun wuri nayi na zauna ina dakon ta mu gaisa jin da hausa take wayan ya fahintar dani a gida Nigeria take yin wayan lokacin .
Tun ina sauraren ta har na fara tunane sai can naji muryan ta kamar a mafalki tana fadin waiko yau lafiya kike yar gidan ya umar kamar yadda nake kiran shi a gaban ta idan wani magana ya taso itama haka ta fada min.
Na dawo cikin hayacina ina dan murmushi nace anty mun wuni lafiya yaya jama,an gidan ki cikin kako murmushin dole nake maganan.
Ta amsa da duk suna lafiya sai dai yau yanayin ki ya nuna kamar kina cikin tunane da damuwa sister ?
Bakomai bane anty na fada ina bude jakkata da nake amfani dashi a school din na dauko wayana dake cikin zip din ciki.
Ta kara fadin ko yau da kewan yaya ki kika tashi ne hakan na dan dago kai ina dariya tare da fadin kai anty yau yaya din ai a gidana ya kwana sai dai da safen nan ne naga takarda daya bar min wai tafiya ya kamashi ya tafi bai tasheni ba .
Amma dai wana yayan naki da yawan tafiya yake fatima kamar agogo ko yaushe yana saman hanya shi ?
Ai dama nasan kina kewan shi ne tunda mutum kike ba dabba ba duk mace mai lafiya da jini a jika ai zatayi kewan mijin ta na sunna ko ?
Haba anty har wani sabawa nayi da yaya umar ni na fada ina kokarin hade abinda nake ji a raina.
Tace da sannu zaku saba ai ki barshi kawai ya gama iskancin shi da iya shegen su na maza shi da kansa zai kawo kanshi inda kike sister.
Nace jiya yazo min da wata magana sai daga karshe yake fada min wai April full yayi min da sauri tace wani irin April full kuma ana April full sau biyu ne a shekara ?
Da sauri na dago nace na shiga uku anty watau yaya wayau ke nan yayi min ashe da gaske yake zancen ciwon kawu ganin hankalina ya tashi yasa yace mi wai april full yayi min.
Take idanuwana suka fara tsiyayan ruwa hankalinta ne ya tashi a rude take fadin maynene haka sister zaki jawo hankalin mutane gare mu kuma ?
Cikin dan rage sautin muryana nake fadin watau da gaske yaya keyi kawuna baida lafiya ganin hankalina ya tashi shine yace min wai wasa ne.
Kinga ki kwatar da hankalun ki kimin bayani yadda zan fahince ki mu san mafita tace dani.
Da kyat na hade kuka nayi mata bayanin komai tana saurarena sai dana gama tace banda abinki sister ai ciwo na Allahne.
Damu dake da lafiyan bamu fishi ga Allah ba sai kiga mai lafiyan ya tafi ya bar masu lafiya a jika shi lamarin Allah idan ya taso addua ake so bawa yayi don yanzu adduan mu yafi bukata ba wanan kukan da kikeyi ba.
Mijin ki yayi maki wayau manyane ya wuce ya barki don kada ki daga mai hankali idan kin matsa sai kin bishi can zuwan may zai karaki dashi ?
Ai addu,an ki kawai kawun ki yafi bukata gareki ki kwantar da hankalin ki Allah yasa mijin ki yayi farar tafiya ya tad kafadan kawu lafiya.
Cikin murya mai kama da rada na amsa mata da amin anty ina kada kaina ina fadin amin anty cikin damuwa.

KANO
Ba wanda yasan da zuwan shi suna zaune cikin halin damu har lokacin ga fargaban halin ciwon da maigidan ke ciki ga kuma kishin da ba,a daina shiba har lokacin.
Sallaman shi yasa su gaba daya dago kai suna amsa mai mai a yanayin yadda ya shigo cikin damuwa ganin su ya kara sa hankalin shi tashi tun bai gamsu ba.
Hjy jummai tunda tayi arba da dan nata tayi saurin kawar da kai daga kallon shi.
Yanzu idan zata kirga shekara daya da rabi kenan rabon data ganshi tunzuwan da yayi ya samay ta gidan wanta sai wanan ganin da tayi mai.
Ga al,adan bahaushe girmamawa gana gaba duk da fadin da malaimai keyi baida kyau malam bshaushe bai yarda ya yar da wanan al,adan na tsugunawa gaida mahaifanshi ba wani lokacin.
Shima Umar hakan yayi don bai gaida kowa ba duk da sannu da zuwan da suke mai sai daya samu wuri ya dan rage tsawo ya gaida su a cikin jimmila ga baki daya wanda ke gurin.
Su mama hadiye sukace ashe kun samu labari rashin lafiyan yace eh gwaggo Aliyu ya kirani yake gaya min abinda ke faruwa naso tasowa saidai hakan bai samu ba saboda wani dalili.
Yau ai jikin nasa da dama sosai don yana dan motsa idanun shi kadan kadan hakan yasa hankalin su ya dan fara kwanci.
Yai masu yaya mai jiki duk a cikin jam,i ya mike tare da tambayan wanda ke cikin dakin a lokacin suka bashi amsa kusana tare banda mamu da hjy su da suka kawar da ido daga kalo shi.
Dakin ya shiga su kawu balarabe ne da kawu mustapha a cikin

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login