Showing 12001 words to 15000 words out of 21643 words
Chapter 5 - Alaqaqai Part 1 Complete Hausa Novel By NAZIR ADAM SALIHI.txt
Ina zuwa saina nemi kofar shiga babban falon na tura kofa na shiga bayan nayi yan dube dube saina jiyo hayaniya awani daki. Hakan shi ya bani damar gane cewa shine dakin da nake nema.
A ina kika jefar da jaririn? Ya sake tambayarta banyi wata-wata ba saina tura kofar na fada cikin dakin babu sallama. Gaba daya mutanen uku miji da mata dakuma 'ya suka juyo a firgice suka dubeni kamar wani Aljani.
Kayi hakuri alhaji da shigowata babu sallama.
Nace dashi. Zuwa nayi na ceci ran 'yarka domin ba sai ka dora wukar a makogoronta ba. Ga Jaririn nan bai yi nisa ba dazun nan tayi min kyauta dashi amatsayin kyakkyawan jaruminta na shekara.
Nayi musu murmushin yake su kuma suka dubeni saroro kamar wadanda suke tunanin na tabu. Na ajiye akwatin agabansu sannan nace.
Jaririnta yana cikin nan yana barci ni zan koma Alhaji saidai kuma don Allah kayiwa masu gadin nan magana domin su Barawo suka kamani jiya da daddare adakin injin dake baku wuta na kwana. Allah ne ma yasa zan raba wannan rikici shiyasa na fito.
.
Karya yake Wallahi baba shine ya sace jaririn wallahi shi ya sace min fadila tace.
Yi min shiru munafuka mutumin ya buga mata tsawa na dubeta nayi murmushi sannan na lalubi aljihuna na dauko wasikar datayi min na mikawa mutumin nace.
Duba min nan Alhaji shin wannan rubutuna ne ko nata? Ni sauri nakeyi domin muna da fim din da zamu fara idan an jima. Idan kuma kana bukatar karin bayani to saurareni da kyau.
Mutumin ya amshi wasikar daga hannuna nikuma saina dubi Fadila itama ta dubeni nayi mata murmushi nace.
Kadan ya rage ki kai labari yan mata to saidai kuma kyautar da kikayi min tayi girma dayawa. In banda abinci ina ke ina yi min kyautar Jariri? Ai tayi min yawa ina laifin ma ki bani Kyautar
KWALBAR TURARE KO FULAWA
Adaidai nan naji sautin sawun masu gadin suna ta guje guje atsakar gidan.
Lafiya meye haka? Mutumin yace yana dubana nayi masa murmushi nace dashi
kada ka damu masu gadinka ne suke nemana.
Fadila ta daga kai idanunta cike da kwalla tace.
HILAL nace Na'am FADILA
Tace don Allah ka yafe ni. Na dubeta na tsawon dakiku sainaji tausayinta ya kamani saina dubeta da tattausan murmushi nace.
Na yafe miki Fadila saiki nemi kuma gafara agurin Ubangijinki dakuma mahaifinki.
Fadila ta fashe da kuka.
Adaidai lokacin ne masu gadin suka kwankwasa kofa.
Ku shigo nace dasu.
Waya saka? Mutumin yace dani na dubeshi nayi masa murmushin ko in kula.
.
HUDU 4
.
Kusan minti guda muka share tsaye muna duban kofar kodayake fadila bata kallon kowa sai ni.
Kofar dakin ta fara budewa ahankali kamar iskace ke turota sannan sai kakkausar muryar kartin nan tace.
Salamu Alaikum....Alhaji mu shigo ne?
Mahaifiyar fadila wacce ke tsaye rike da tsantsa tana huci kamar kububuwa.
Mamuda ne? Shigo kai kadai. Maigadin yace bakinsa na rawa
Garsakeken katon ya shigo dakin cikin sanda yana zuwa saiya dubeni ya rusuna agaban maigidansa yace.
Kayi hakuri don Allah Alhaji Wallahi adakin injin bada wuta muka sashi ya gudo.
Bari inyi waje dashi na hada shi da yan sanda. Yana gama fadi saiya yunkuro DAMKE NI............
.
17
Yana Tafe Anjima Insha Allahu Zan Biya Bashin jiya I banyi ba saboda balaguron da mukayi
[13:00, 1/24/2018] +234 806 858 0203: ALAKAKAI-17
.
(m) Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Yana gama fada ya yunkro zai Damkeni...
.
Uhm Uhm mamuda kada ka taba shi.
Maigidan yace cikin karaji. Mamuda yayi cak kamar ruwa ya cinye shi.
Alhaji barawo ne...
Kada ka damu mamuda jeka waje kaci gaba da aikinka kawai.
Toh yallabai katon yace cikin girmamawa lokaci guda kuma ya nufi kofa.
Af mamuda... Maigidan ya kira sunansa katon ya juyo cikin sauri na lura duk a rude yake me yiwuwa tunda yake gadi agidan bai taba shiga wannan dakin ba.
Wannan maganar daga kai sai mu ka.
Kafadawa abokan aikina ma bana so ta wuce tsakaninku. Kakuma kawo min akwatin daya bari adakin injin wutar. Katon ya gyada kai cikin fahimta sannan saiya dubeni. Kallon dayayi min na iya nufin komai.
Nayi masa murmushi cikin sanda ya juya kamar yadda ya shigo ya sulale daga dakin.
.
Muka sake yin shiru na tsahon mintuna akaro na biyu mahaifin fadila na kallon tattausan kilishin dake dakin yayinda fadila ke kallon. Nikuwa idanuna na kallon mahaifiyar fadila wacce ta kurawa fadila idanu bata ko kiftawa. Azuciya na yarda da maganar mahaifin fadila dayace da mahaifiyarta tun farko itace ta bata fadila domin na lura da alamun damuwa karara a fuskarta dakuma kauna ga fadila yarta.
Ku shiga daga ciki RASHIDA. Maigidan ya kira sunan matarsa akaro na farko. Nayi zaton zata hau masifa amma maimakon hakan saita dubi Fadila tace. Taho mu tafi. Fadila tayi min kallon gefe idanu tabi mahaifiyarta suka bi ta wata yar tsukakkiyar kofa suka shige ciki. Maigidan ya dubeni gamida sassauta yanayin dake fuskarsa yace.
Zauna bawan Allah ya nuna min kujera araina sainaji na kaunace. Hakan shi yasa nayi biyayya na zauna batareda nayi jayayya ba. Ya danyi shiru gamida sakin wani tattausan tari kana sai ya dago kansa..
.
Tun tana karama muke fama da ita kadarar yarinya ce ka ganta nan gashi da babu abinda ta rasa agidan nan na daga kayan alatu amma bata iya zama sai shegen yawo. Mahaifiyarta ce ta bata tun tana karama.... Yayi shiru akwai alamar takaici karara a fuskarsa. Na tausaya masa.
Babu daman nayiwa yar cikina fada sai mahaifiyarta ta hauni da masifa. Haka kullum nake fama kwatsam ran nan sai muka fahimci yar banzar yarinyar tayi ciki mahaifiyarta tayita uzura min sai a zubar da cikin. Nikuma ina tuna mata yin hakan barna ce domin kisan kaine saimu bata goma biyar bata gyaru ba. Haka mukayi ta fama har zuwa ranar data haifu shine yanzu don tsabar rashin imani suka hada baki ita da mahaifiyarta suka kashe dan jaririn wata daya kawai da haihuwa....hawaye ya fara kwarara akan fuskarsa.
Na yunkura akan kujerar cikin damuwa ni duk maganganun sun fara gundurata duk da dai basu shafeni ba ni abinda kawai nake so shine yabar ni na tafi dan na lura tuni har gari yafara haske. Duk da yake banga agogo ba ina kyautata tsammanin biyar na safe ta wuce. Fita fim dinsu Alhajiji ne araina.
Alhaji.... Allah ya sawwake.. Nace dashi ina ganin in babu wani sauran abu to ni zan tafi alhaji domin kaga duk wannan abubuwan da kake fada bai kamata na sani ba domin sirrinku ne ku kadai bai shafe ni ba. Mutumin ya dago kai yana girgiza shi.
Ya shafe ka bawan Allah. Awannan karon ni na dube shi cikin mamaki.
Tayaya ya shafeni? Mutumin ya sunkuyar da kai na tsawon lokaci yana girgiza kai. Can saiya dago alamar damuwa a fuskarsa a fili. Ga mamakina sainaga ya mike tsaye ya nufo inda nake ya sunkuya akaina ya dafa kafadata yace.
Bantaba neman alfarma agurin kowa ba tun da nake.... Amma yau zan fara. Abinda yace sai ya daga rudani.
Ban fahimce ka ba. Ya daga girarsa sama kamar biri na lura karfin ikonsa da kwarjininsa na attajiri sun fara dawowa gare shi.
Abinda nake nufi shine ina neman kayi min alfarma guda biyu bawan Allah.
Ni kuwa zan saka ma da abinda baka taba zato ba. Numfashina ya dauke abinda ban taba zato ba? Indai ba kuskuren fahimtarsa nayi ba nasan abinda kalmar ke nufi muddin ta fito daga bakin ATTAJIRI.
Wa.... Wacce alfarma kake so? Ya dubeni na tsawon lokaci kana yace.
So nake ka rufa min asiri maganar jaririn nan ta zama daga kai samu don Allah na rokeka ka rufa min asiri domin idan ta fito fili nagama yawo... Kaga shekara mai zuwa nake son tsayawa takarar GWAMNA zuciyata ta harba tsakanin hakarkarina. Bakina na rawa nace dashi.
Indai don wannan ne Alhaji kada ka damu in Allah yaso babu wanda zai kara jin ta abakina. Nayi tsammanin zai saki fuska cikin jin dadi amma sainaga haryanzu dai tana nan yadda take babu yabo babu fallasa.
Sai kuma alfarma ta biyu bawan Allah yace. Lokaci guda kuma naga akwai alamar razana a fuskarsa.
Fadi muji ranka ya dade. Nace dashi ina dada kwantar da murya domin kalaman dayayi ne zaiyi min abinda ban taba tsammani ba yasa zuciyata lissafe-lissafe,,,, na tuna da dimbin bashin da ake bina.
.
Bawan Allaj me ye sunan?
Sunana Hilal.
Yawwa hilal.
Alfarmar danake nema tanada nauyi amma kamar yanda nace dakai abaya zan saka ma. Ya danyi shiru sannan saiyace,
Zaka iya hilal? Na dubeshi cikin mamaki nace to ai bansan me zanyi ba Alhaji.
Ya dada saurarawa lokaci guda kuma saiya daga kansa ya dubeni ido da ido yace.
SO NAKE KA AURI 'YA TA FADILA.
.
************ ************** ************* *********
.
KU HUTA TUKUNNA SAI MUCI GABA
.
NA SADAUKAR DA WANNAN KASHI NA 17 GA DUK WAYANDA SUKA JE KADUNA TA'AZIYAR ABOKIN HULDA AWANNAN DANDALIN IBRAHIM TAREDA DUK WAYANDA SUKAYI TA BUGO WAYA SUNA MIKA TA'AZIYAR SU TA HANNUN MU DAKUMA MASU COMMENT A CIKIN POSTING DINA NA RASUWAR DA TAFIYA TA'AZIYAR ALLAH YAYI MANA RAHAMA DA RAHAMARSA BADON AIKIN MU BA
[13:22, 1/27/2018] +234 806 858 0203: ALAKAKAI-18
.
(m) Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya.
.
Ya dada saurarawa lokaci guda kuma saiya dago kansa ya dubeni ido da ido yace.
SO NAKE KA AURI 'YA TA FADILA.
.
********* ******** ***********
.
Ba karamar girgiza nayi da kalamansa ba. Kaduwar danayi ita ta sani zaune nayi mutuwar tsohuwa na kasa cewa dashi komai domin bansan me zance dashi ba. Na auri fadila? Chab babbar magana.
Yaya kayi shiru Hilal ko baka sonta ne? Na girgiza kaina cikin kaduwa.
Bahaka bane Alhaji... Kaga dai yan sa'o'in da suka wuce na santa kuma.... Ya daga min hannu.
Hilal basai ka fada ba nasan abinda kake tunani. Auren yarinyar banza kamar fadila ko?
Yarinyar data yi cikin shege ko? Ya danyi shiru sannan yaci gaba.
Abinda yasa na baka duk tarihinta abaya shine so nake ka aure ta da halinta. Kuma ko da yake baka dade da saninta ba kai kasan fadila kyakkyawa ce bata da wani aibu in ya wuce na dabi'unta na banza.
Hilal inason ka sani cewa in dai kana sonta zaka aureta da halinta to zan saka maka da babban alheri domin tuntuni na gaji da zamanta agidan nan. Ganin sharrin dataso ta dora ma shi yasani tunanin babu wanda yadace ya aureta sai Kai.
Na gama rudewa zuciyata sai dum dum dum takeyi duk abubuwan dake faruwa ji nake kamar amafarki.
Mecece sana'ar ka hilal? Mutumin ya tambayeni hakan dayace shi ya sani dada gyara zama.
Harkar shirin fim nakeyi... Nace dashi cikin gaggawa mutumin ya shafi kansa da tafin hannunsa na dama yace.
Saurareni da kyau hilal zan baka lokaci kayi shawara zan kuma sami Fadila nayi mata maganar.
Ya danyi shiru sannan yaci gaba. In dai zaka yarda zaka aureta da halinta nayi maka alkawarin zan sayo maka duk abubuwan da kake bukata na harkar shirin fim idan nafita kasashen ketare. Ko gobe ka amince kazo ka sameni ka fada min zan aika cikin sati guda a sayo maka duk abinda kake bukata inason kuma ka nemi gida mai girman gaske a ko ina ne zansa arugujeshi agina maka kamfanin fina finanka zan kuma zuba maka jarin naira Milliyan biyar kyauta. Na shiga uku nace cikin zuciyata. Milliyan biyar?
.
Alhaji zanyi shawara.... Abubuwan sunyi yawa akaro na farko sai ya saki wata tattausar dariya yace.
Ai kadan ma ka gani ya mike tsaye sosai zo muje in rakaka. Jikina na rawa na bishi abaya.
Ruwan saman ya tsaya cak. Tuni gari har yafara haske naji sa'ar da agogo ya buga karfe shida na safe. Muka bi ta wata yar kofar sai na ga mun bulla a filin ajiye motoci.
Motovi bakwai ne ejere kusan duk sababbi ne akwai jeep guda biyu Lexux daya marsandi biyu da honda shudiya da ja. Ga mamakina sai naga ya tsaya ajikin motocin.
Alokacin ne fa nayi masa kyakkyawan kallo dogo ne siriri fari mai gashi irin na buzaye yalo yako me yiwuwa bafilatani ne kokuma mutumin Mali. Allah masani. Sa'ar daya dubeni yayi dariya sainaga hakorinsa na sama guda daya a bantare.
.
Zan baka sati guda kayi shawara hilal abinda ka yanke saika zo ka fada min ni da kaina zan sami iyayenka.
A ina kake ne? Ya tambayeni hannunsa na dama akan rufin motar lexux.
Anan unguwar nake can ciki nake (No 106)
Af ashe ma makwabvina ne. Ya fadada murmushinsa ya laluba aljihun doguwar jallabiyar shudiya dake jikinsa ya dauko dan makullin mota sannan ya nufi shudiyar motar honda.
Alha..... Alhaji bama sai.... Ka bari kawai saina karasa ma akasa. Murmushinsa ya fadada.
Uhm hilal kenan kaifa nace dakai yanzu ka dan ma ka gani. Ungo rike wannan. Ya miko min dan makullin mota ya nuna shudiyar motar da baki yace.
Gata nan nabaka kyauta. Wannan kyautar bata cikin wancan yarjejeniyar tamu koda baka amince ba wannan motar dai taka ce... Na bude baki cikin kaduwa da mamaki chab. Dan saurayi hilal anya kuwa ba mafarki kake ba?
Bansan irin godiyar da zanyi maka ba alhaji na gode Allah... Ya katse ni ta hanyar daga min hannunsa a fuska..
Kada ka gode min Domin asirin dakayi alkawarin zaka rufa min yafi dahaka. Da'ace ciniki zamuyi.
Ya dan saurara yana dan dukan saman motar da yan yatsunsa.
Shikenan hilal sainaji daga gareka kana iya shiga motarka Allah yabamu alheri nakuma gode domin nine da godiya. Yana gama fadi saiya juya yayi ciki da sauri. Yakoma cikin gidan ta inda muka fito.
.
Na dade anan saroro a rude domin abin kamar a mafarki awani bangare kuma na zuciyata sai cewa akayi dani wannan yaudarar ce irin na aljanu.
Amma sa'ar dana bude hondar na lume acikin kujerar direba sai na gaskata faruwar dukkan al'amarin.
Ada na dauka dana shiga motar zan ga ta bace saina tsinci kaina kwance akan tsohon gadona. Amma tabbas ko shakka babu duk abinda nagani tun daga dare har zuwa wayewar gari gaskiyane babu zancen aikin aljanu KAMAR A FIM.
.
Nayiwa motar key na tashi sannan na fara tukata ahankali na nufi kofar gidan azuciyata nace Allah mai yadda yaso yan sa'o'i kadan nine ke yawo da mataccen jariri ina neman inda zan jefar dashi sannan lokaci guda kuma na tsinci kaina amatsayin barawo sai gashi akarshe cikin ikon Rabbana motovina da bashi ya cinye daya ta dawo daga cikinsu.
Koda na fara tuka motar sai na juyo da nufin na yiwa ginin gidan kallon karshe gabana yayi RAS. Sa'ar dana hangi.....
.
AKWAI CIGABAN ANJIMA IDAN KUNA SO
[13:24, 1/27/2018] +234 806 858 0203: ALAKAKAI-19
.
(m) Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Gabana ya fadi ras sa'ar dana hangi FADILA tsaye agindin taga tana daga min hannu ba ganin nata ne yasa zuciyata ninkaya ba sai tunanin cewa ayanzu abinda ke tsakanina da zama miloniya shine kawai na yarda zan aureta. LAURIYYA ta fado min arai.
Ga koshi ga kwanan yunwa nace araina.
Koda masu gadin suka hangoni tafe sai sukayi sauri suka bude min kofa atunaninsu ubangidansu ne koda suka fahimci nine sai suka bi ni da kallo bakunansu a bude cikin kaduwa. Dankareren katon daya kamoni amatsayin barawo idanunsa suka firfito cikin kaduwa kamar idanun kwado. Na daga masa hannu harda murmushi na take sabuwar motata abina na nufi gida.
.
********** ********* *********
.
Tun daga nesa na hangesu tsaye akofar gidana motoci biyu da mutane biyar kowannensu nata waige waige suna ta duban hanya akwai alamar damuwa a fuskokinsu.
Nayi fakin da dalleliyar hondar adaf dasu ina ganin alhajiji ta cikin gilashin motar yana duban agogo baiko damu daya kalli motar data tsaya afad dasu ba domin nasan babu wanda acikinsu yake tsammanin nine na bude kofar motar ahankali.
Sannunku da zuwa furodusa. Nace dasu da faffadan murmushi. Duk su biyar din suka juyo acikin mamaki ganin nine sai fuskokinsu suka washe.
Dan Banza daga ina a ina ka kwana? Tun dazu karfe biyar da rabi muke nan muna jiranka duk sauran yan wasan sunyi gaba kai kawai ake jira na dubeshi bayana jingine da motar ina karkada dan makulli.
Kun aika gidan kawuna ne nemana? Na tambayesu gabana na faduwa.
A'a bamu aika ba daman USMAN ne ma yace mu aika nikuwa nasan da wahala in kana ciki. Nayi ajiyar zuciya da sun aika gidan kawuna nemana da sun janyo min jaf'i.
Bari in shiga gida in dan wasa ruwa sai mu tafi ko? Usman dake ta kallona tun zuwana yasaka magana saboda kullewa sai kawai safa da marwa yake.
Kaga malam tun dazu da muke jiranka fa anan sai zamuyi ta jira har rana tayi mana dubi fa karfe shida da rabi. Na fashe da dariya.
Dubi rigata fa usman ka gani gaba dayansu suka zubo min idanu sabodar tsabar kaguwa da sukayi basu ko kula da yanayin da rigar ruwan dake jikina take ba.
Me ya sami rigarka haka naga duk a yayyage... A'a kaima ai duk a jike kake da chabi. Duk jikinka tun kafin suyi tambayar nagama tsara amsar da zan basu cikin zuciyata.
Ai jiya muna rabuwa dakai lokacin daka bar mu da Lauriyya sai wasu suka daukeni muka tafi daukar wani fim. Da Allah da Annabi suka janyeni domin wai jarumin da sukayi niyyar fim din dashi baya gari kuma daukar da zasuyi suna bukatar ruwan sama. Shiyasa suka takura sai mun tafi acan na kwana. Kai jiya munyi fim da wuya. Don nasha dukan ruwa....
To indararo.... Don Allah alhajiji barshi yaje ya shirya yafito mu tafi inka biye tashi sai yayita zuba kenan daga nan har azahar. Kasan ba gajiya yake da magana ba.... Usman yace cikin fada. Na dube shi nayi masa gwalo... Sannan da gudu gudu na shige cikin gidan.
.
Bayan mintuna ashirin nafito nayi wanka na sanya kayana tsaf dani inka dauke zunzurutun tunanin dake raina. In banda na amsa musu tun jiya da ba zanje fim din ba milliyan biyar.
.
Mu tafi nace dashi cikin sauri na nufi sabuwar motata.
Hilal mota ka sake ne? Alhajiji ya tambaya na san gatse yake son yi min ya dauka arota nayi domin duk fadin duniyar fim babu inda labari bai watsu ba cewa taurarona ya daina haske.
Daman ai chanji zanyi shine yasa na saida wadancan nan da sati guda ma za'a kawo min marsandi daga kwatona.
Alhajiji ya dubeni cikin kaduwa akwai alamun hassada karara a fuskarsa. Hakanan kuma na lura da cewa kamar dai na barshi cikin wasi wasin gaskiyar abinda nafada. Ganin ya kasa magana saina ce dash.
Ina lauriyya? Fuskarsa ta washe nan da nan. Ai ka fini kusa da ita.
.
BIYAR 5
.
Ina ganinta tsaye sa'ar dana nufo ofishin ta raba hannuwanta ajikin kofar tana ta hange hange ko shakka banayi ni lauriyya take hange taga ta inda zan bullo to amma har sa'ar danayi fakin da