Showing 1 words to 3000 words out of 6886 words
Chapter 1 - KUNDIN ALAJABI Book 2 Complete by Mansur Usman Sufi .txt
KUNDIN AL'AJABI
Rubuta Labari
Mansur Usman Sufi
Website:- www.arewanovels.com.ng
08137237071
Babi na biyar
A da can baya kimanin shekaru dubu ɗaya da ɗoriya da suka gabata, lokacin da Ƙarfin sihiri da na jarumataka suka zamto jari hujja, zalunci gami da yaudara suka yi katutu a zukatan bil'adama, kowanne sarki burin shi ya kai farmaki zuwa ɗan uwanshi ya mamaye ƙasar shi ta dawo izuwa ƙarƙashin masarautarshi.
A wannan lokaci akwai manyan biranen duniya da suka shura, waɗanda gaba ɗaya sune ke tafiyar da mulkin duniya baki ɗaya. Biranen sun haɗar da birnin Sin, Rum, Misra da birnin Hindu.
Birnin Sin na ƙarƙashin mulkin sarki Abul-uyum. Abul-uyum ya kasance gwarzon mayaƙi mai dakawa maza gumba a hannu, an ce saboda Jarumtakarshi yana iya shafe tsawon kwana uku yana yaƙi ba tare ya ci ko ya sha ba ballantana gajiya, batun ƙarfin sihiri, dukiya da rundunar mayaƙa kuwa ya yiwa gaba ɗaya sarakunan yammacin duniya zarra. Bisa wannan dalili ne ya sanya ya zamto gagarabadau kuma ƙadangaren bakin tulu ga sarakunan nahiyar.
Birnin Rum yana bisa jagorancin sarki Fitinatul-muluk ibnu Larab,
Fitinatul-muluk ya kasance hatsabibin matsafi, gwarzon jarumi ma'abocin tarin dukiya dangin lu'ulu'u da dabbobin ni'ima, masu hasashe da bincike sun tabbatar da cewa a iya fadar shi akwai dakarun aljanu da na bil'adama guda miliyan ɗaya, bayan waɗanda aka tanade su domin kai farmaki izuwa birane da ƙasashe domin FATAUCIN BAYI, kusan komai dake fadar shi an samar da shi ne da ƙarfin sihirin tsafi.
Bisa wannan dalili ya sanya sarakunan ke yi mashi laƙabi ya da ANNOBAR SARAKAI.
Sarki Hubaizu ibnu Shardas kuwa shine ke riƙe da Kambun birnin Hindu.
Hubaizu mutum ma'abocin sadaukantaka ta gaban kwatance, sanin alƙalumman sihiri, gami da tarin dukiya. A jerin sarakunan da aka yi a birnin Hindu shine sarki na saba'in, ya hau karagar mulki tun yana matashi ɗan shekara sha biyar, kuma a halin yanzu yana da shekaru saba'in cif a duniya, bisa binciken bokaye da masu hasashe sun gano cewa a kowacce rana sarki Hubaizu yana samun sabbin sirrikan tsafi guda miliyan ɗaya, yana samun sirrikan ne a duk sa'adda da sadu da wata kuyangarshi. Bokayen sun gano cewa duk sa'adda da hakan ta faru ƙarfin damtsenshi yana ƙaruwa sau hamsin cin ɗari.
Bisa wannan dalili ya sanya ya zamto wa sarakunan nahiyar ANNOBA ƊARI.
Birnin Misra na bisa jagorancin wani gwarzon mayaƙi ne da ake yiwa laƙabi da Ayumul-barƙas ibnu Zairul.
Sarki Ayumul-barƙas mutum mai tattare da abubuwan al'ajabi ba ya tsafi kuma sihiri ba ya tasiri akan shi, komai yawan sirrikan tsafinka idan kayi arba da shi take za su daina amfani.
Gaba ɗaya sarakunan biranen huɗu, Abul-uyum, Hubaizu, Fitinatul-muluk da sarki Ayumul-barƙas sun kasance basa ga muciji da juna, burin kowannen su shine ya kawar da abokan gabar shi domin ya zamto sarkin SARAKAI na duniya.
Bisa binciken da sarakunan suka gudanar shine ɗyan su ba zau iya cimma wannan buri na shi ba face ya mallaki wani kundi da ake yiwa laƙabi da KUNDIN AL'AJABI dake ajiye a kogon GARUL-SHAMMAR.
shi dai KUNDIN AL'AJABI na ɗauke da sirrikan tsafi guda miliyan dubu hamsin, babu wani mahaluki a doron ƙasa walau mutum ko aljan da zai mallaki kundin face ya zamtowa duniya gagarabadau kuma ANNOBA ƊARI.
Koda mutum ya mallaki KUNDIN AL'AJABI ba zai iya sarrafa shi ba face ya mallaki wata kuba da ake yiwa laƙabi da Miftahul-sihir, a halin yanzu kubar Miftahul-sihir ta rabu kaso huɗu, kowanne sarki daga cikin sarakunan huɗu yana ɗauke da ɓari guda, dukkaninsu sun mallaki ɓarin kubar a hannun mahaifan su.
Sa'adda sarakunan huɗu suka ga wannan al'amari a cikin halarar tsafin su sai hankulansu suka dugunzuma ainun, abu na farko da ya dugunzuma hankulan su shine. Ta ya ya ɗayan su zai yaƙi sauran abokan gabar shi har ya raba su da sassan kubar guda uku, bayan cewa fiye da shekaru goma suna kwabza yaƙi tsakanin su amma babu nasara, sai dai a samu asarar rayuka da dukiyoyi masu tarin yawa.
Abu na biyu da yafi tayar masu da hankali shine a cikin su babu wanda yake da ikon shiga kogon GARUL-SHAMMAR har ya ɗauko KUNDIN AL'AJABI face wani barde da ake yiwa laƙabi da Yasiran jin Taufid.
Yasiran ya kasance mafarauci, fiye da rabin rayuwarshi ya yi ta je a daji tare da iyalan shi.
Abun tambaya anan shine ta ya ya ɗayan su zai mallaki mafarauci Yasiran?
Bisa dogon nazari da sarakunan suka yi sai suka samu mafita tsakanin su.
Mafitar kuwa ita ce kowannen su zai bayar da ɓarin kubarshi a haɗe waje guda, sannan a nemi taimakon mafarauci Yasiran, idan ya so bayan ya samu nasarar ɗauko KUNDIN AL'AJABI sai a kwabza yaƙi tsakanin su, duk wanda ya yi nasara sai ya mallaki kundi da kuba.
Kamar yadda sarakunan suka tsara haka al'amarin ya kasance, wata rana da la'asar sakaliya mafarauci Yasiran da matarshi Zarilat sai ni 'yarsu Sulaiza muna zaune a cikin bukka muna fira cikin nishaɗi sai kawai muka jiyo ƙarar takun sawaye haɗe da haniniyar dawakai sun cika dajin baki ɗaya.
Cikin matuƙar kaɗuwa abbana na miƙe tsaye zumbur yana mai ɗaukar KWARI DA BAKAN shi ya yunƙura ya durfafi ƙofar fita, har na yunƙura zan bi shi a baya sai ya dakatar da ni ta hanyar dafa kafaɗuna ya dube mu ni da mahaifiyata ya ce "ya farin cikin rayuwata bana so wani abu ya ɗaga maku hankali kawai ku zauna naje na duba domin naga mene ne ke faruwa".
Koda jin wannan batu daga bakin abbana, sai idanun mahaifiyata suka ciko da ƙwalla kuma ta janyo ni ta rungume ni a ƙirjinta, sannan ta dube shi muryar ta cike damuwa ta ce " ya muradin zuciyata kayi sani cewa yau tsawon shekaru ashirin muna zaune a wannan daji ba a taɓa samun wata muguwar dabba, ko dakarun sumame sun kawo mana farmaki ba sai a yau, jikina ya bani cewa babu alheri a tare wannan fita taka".
Koda jin wannan batu daga bakin mahaifiyata sai ya dube mu cikin alamun matuƙar tausayi ya ce "ya abar kaunata ki kwantar da hankalinki da yardar abun bauta zan dawo gare ku cikin ƙoshin lafiya".
Koda gama faɗin hakan sai mahaifina ya juya ya fice daga turakar yana mai kunna kai izuwa ɓangaren da yake jin takun sawayen, yana cikin wannan hali ne kwatsam! Bazato babu tsammani sai mahaifina ya yi arba da waɗansu zaratan mayaƙa su huɗu zaune a bisa ingarmun dawakai, dukkanin su suna shirye cikin gagarumar yaƙi mai matuƙar kwarjini daban tsoro sun rufe fusakunsu idanunsu kaɗai ake gani.
Kafin abbana ya yi wani yunƙuri sun yi mashi ƙawanya suna masu kewaye shi,
cikin dakewar zuciya mahaifina ya dubi mayaƙan cikin matuƙar fushi ya ce "ya ku waɗannan mayaƙa shin mene ne nufin ku a gare ni? Koda jin wannan tambaya sai kowannen su ya ɗora hannunshi a kanshi ya cire hular ƙarfenshi take fusakunsu suka bayyana a fili ƙarara.
Sa'adda mafarauci Yasiran ya yi arba da fusakun na su sai hankulanshi ya dugunzuma ainun tsoro ya kama shi,
Domin a iya tsawon rayuwarshi bai taɓa gani ko jin labarin sadaukai masu matuƙar kwarjini da ban tsoro tamkar mayaƙan ba.
Daga can sai wani daga cikin mayaƙan mai ƙirar samudawan farko fuskarshi a murtuke take babu annuri tamkar an watsa mashi garwashin wuta akan ta,
ya buɗi baki cikin wata irin kakkausar murya mai kama da haniniyar doki ya ce "ya kai Yasiran ibnu Taufid ka yi sani cewa bamu zo gare ka domin cutar da kai ba sai domin mu taimaki juna tsakaninmu, don haka sai ka tsaya ka saurari bayanin da zan yi maka da idanun basira. Ya kai Yasiran kayi sani cewa bakomai ne ke tafe damu izuwa gare ka ba, face muna so ka tafi izuwa tekun Bahar-rum ka shiga kogon GARUL-SHAMMAR domin ka ɗauko mana wani littafi da ake yiwa laƙabi da KUNDIN AL'AJABI, domin mu tseratar da al'ummar ƙasashenmu daga annobar fari da junya dake addabar su, ka yi sani cewa matsawar ka cika mana wannan buri namu, ni Ayumul-barƙas da sauran 'yan uwana Fitinatul-muluk, Hubaizu, da sarki Abul-uyum zamu baka ladan dukiya mai tarin yawa wacce kai da zuri'arka ba su taɓa cinye ta har tattaɓa kunnen ka, sannan kai da kan ka zaka zaɓi inda kake don ka zauna tare da iyalan ka a ɗaya daga cikin biranen mu huɗu".
Lokacin da sarki Ayumul-barƙas na birnin Hindu ya zo dai-dai nan a zancen shi sai sauran sarakunan suka gyaɗa kai dake nuni da tabbatar da maganar da ɗan uwansu ya faɗa, suna masu cewa a ransu haƙiƙa sarki Ayumul-barƙas ba ƙaramar hikima ya yi ba da ya ɓoyewa Yasiran gaskiyar batun KUDNIN AL'AJABI ba, amma a ɓangare guda zukatansu cike suke da mugun tanadi.
Tsawon daƙiƙa hamsin mafarauci Yasiran yana nazarin maganar da sarki Ayumul-barƙas ya yi mashi. Abu na farko da ya faɗo mashi a rai shine, mene ne ya sanya waɗannan sarakuna suka zaɓe shi a matsayin wanda zai ɗauko masu KUNDIN AL'AJABI bayan cewa dukkanin su manyan jarumai ne da za su iya aiwatar da hakan? Sannan ma shin wane tabbaci kake da shi cewa zaka dawo ka tarar da iyalanka cikin ƙoshin lafiya, wani ɓangaren a zuciyarshi kuma na cewa da shi ka tuna asarar miliyoyin rayukan jama'ar da zaka ceto idan ka ɗauko KUNDIN AL'AJABI.
Sa'adda mahaifina yazo nan a tunanin shi, sai kawai ya cire kai ya dubi sarki Ayumul-barƙas, sannan ya yi gyaran murya ya ce "na amince zan biya maku wannan muhimmiyar buƙata amma ina buƙatar ku bani lokaci na yi nazari".
Koda jin wannan batu daga bakin abbana sai sarakunan suka sake duban juna gami da yiwa juna murmushi mai tattare da tsantsar mugun tanadi.
A can dajin Harbul-zawat kuwa ina zaune tare da mahaifiyata cikin tashin hankali, sai mu kaji abbana ya yi gyaran murya ya tura ƙofar hujjar, koda muka yi arba da shi sai muka riga izuwa inda yake suka faɗa kan ƙirjinshi ya rungume mu, muna masu fashewa da kuka.
Sai daga bisani ne ya janye jikinshi daga namu ya dube mu fuskarshi cike da annuri, nan take ya zayyane mana abin da ya wakana tsakanin shi da sarakunan tun daga farko har ƙarshe.
Koda jin wannan jawabi sai mahaifiyata ta cika da matuƙar farin ciki, amma kuma sai hankalinta ya dugunzuma ainun, abin da ya dugunzuma hankalin nata shine shin akwai tabbacin cewa abbana ba zai rasa rayuwarshi wajen shiga tekun Bahar-rum ba?
Sannan wata shaida gare shi dake tabbatar da cewa sarakunan ba su ci amanar shi ba?
Cikin alamun matuƙar damuwa mahaifiyata ta dubi abbana ta ce "haƙiƙa nayi matuƙar farin ciki bisa jin wannan gagarumin aikin ceton al'umma da zaka yi,
sai dai ina matuƙar tsoron ka rasa rayuwarka a wannan hali, sannan kar mutanen da ka aminta da su suci amanarka".
Koda jin wannan batu daga bakin ummina sai mahaifina ya yi murmushi a gare ta ya ce "ki kwantar da hankalinki babu wani sharri da zai same ni, kar ki manta cewa NASARA DA ƊAUKAKA na tare da ma'abocin gaskiya da riƙon amana, kuma ciki da gaskiya wuƙa bata huda shi. ke dai ki kasancewa mai yi mani fatan alheri a kodayaushe.
Koda jin wannan batu sai muka sake rungume shi cikin matuƙar farin ciki maral-musaltuwa.
Babi na shida
A ranar da tafiya kogon GARUL-SHAMMAR ta zo mun sha kukan baƙin cikin rabuwa da mahaifina, tamkar ba za mu ƙyale shi ya tafi ba.
Tun daga wannan rana ummina ce ke ɗawainiya da rayuwata, kullum cikin kewar abbanmu nake, wasa-wasa sai gashi ya shafe tsawon mako uku ba tare da mun ji ɗuriyar shi ba, al'amarin da ya sanya mahaifiyata ta fara tsammanin ko ya rasa rayuwarshi ne.
Al'amarin abbana kuwa tun sa'adda mu kayi bankwana muna masu zubar da hawayen rabuwa da juna, sai kawai ya kunna kai izuwa cikin daji yana tafiya cikin hanzari, tafiyar daƙiƙa hamsin kacal ya yi ya iske su sarki Fitinatul-muluk zaune a bisa kan wani narkeken aljani mai matuƙar kwarjini muni da ban tsoro shi kaɗai suke jira, ba tare da wani ɓata lokaci mahaifina ya haye bisa kan aljanin ya zauna kamar yadda sarakunan suka yi.
Cikin kuzari aljanin ya buɗe manyan fuka-fukanshi ya luluƙa izuwa sararin samaniya yana mai keta gajimare cikin matuƙar sauri tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya.
Tafiyar sa'a uku kacal aka yi aka iso tekun Bahar-rum, cikin hanzari aljanin ya saki fuka-fukanshi ya yi ƙasa luhh! Ya sauka a dai-dai ƙofar shiga kogon, cikin hanzari sarki Ayumul-barƙas ya fara sakkowa sai Fitinatul-muluk, Hubaizu, Abul-uyum mafarauci Yasiran ne a ƙarshe.
Ba tare da wani jinkiri ba sarakunan suka zira hannayensu a aljihun rigar su sai ga shi kowannen su ya fito da ɓarin kubarshi, fuskokinsu cike da murmushin mugunta suka haɗa su a waje guda, faruwar hakan ke da wuya sai aka kwantsama wata tsawa da walƙiya a sararin samaniya, kubar ta kammala jikinta baki ɗaya.
Fuska a murtuke babu annuri sarki Fitinatul-muluk ya miƙawa abbana kubar ya sa hannu ya ƙarba, sannan ya dube shi fuskarshi babu yabo babu fallasa ya ce "ya kai Yasiran kayi sani cewa wannan kuba ta Miftahul-sihir da muka baka da ita ne zaka buɗe kofar wannan kogon dutse har ka samu nasara ɗauko KUNDIN AL'AJABI daga cikin shi".
Koda jin wannan daga bakin Fitinatul-muluk sai mahaifina ya yi jim! Tamkar mai tunanin wani abu, koda ganin halin da mahaifina ya shiga sai sarakunan suka bayyanar da murmushi akan fuskokinsu, da ganin hakan sai abbana ya ji ya samu nutsuwa kawai sai ya juya ya durfafi ƙofar kogon GARUL-SHAMMAR yana isa ya sanya kubar a cikin wani kwaroron rami da ke jikin makekiyar ƙofar kogon da aka yi ta da zallar mulmulallan baƙin ƙarfe, ya murɗa kubar sau huɗu da dukkan ƙarfin shi, take sakatun suka shiga ƙara, zuwa can sai ƙofar ta yi wani ƙara da ya cika dajin baki ɗaya, sannan ta buɗe kanta, wani irin tururin hayaƙi ya surnano daga ciki, ba tare da wani tsoro ko fargaba ba, mahaifina ya kunna kai izuwa cikin kogon tare da sanya kubar Miftahul-sihir a cikin aljihunshi, lokacin da ya kammala shiga sai ƙofar ta mayar da kanta ta rufe ruf!.
Daga ciki kogon GARUL-SHAMMAR ya kasance makeke mai matuƙar tsawo da faɗi, yana ɗauke da saƙarƙaƙiya da lunguna, gaba ɗaya gine ginen dake ciki an yi su ne da waɗansu manyan duwatsun wuta masu ƙwarin gaske, gaba ɗaya kogon dutsen a haskake ta yadda koda allura ce ta faɗi a ƙasa da ya duba zai gani, kuma a ƙasa a zube akwai kwarangwal ɗin bil'adama da wasu halittu gasu nan birjik.
Kaico! Haƙiƙa rashin sani yafi dare duhu, inda a ce abbana ya san abin da zai faru da bai ya gangancin kutsawa kai cikin kogon ba, domin abin da bai sani ba shine, waɗannan kwarangwal ɗin sun kasance tarin miyagun aljanu.
Lokacin da ya zamana ya iso tsakiyar kwarangwal ɗin, nan take ruhikansu suka fara dawo jikkunansu kuma surar tana haɗuwa, kafin cikar daƙiƙa hamsin baki ɗaya halittun sun miƙe tsaye.
Aljanun sun kasance gabza-gabza masu ƙirar samudawan farko, jikkunansu irin na bil'adama ne amma kawunansu irin na tsuntsun batoyi ne, idanuwansu jajur suke tamkar garwashin wuta, a ƙugunsu suna maƙale da wata murtukekiyar jela irin ta kada, sannan dukkanin suna shirye cikin gagarumar shigar yaƙi mai matuƙar kwarjini muni daban tsoro, a hannayensu suna ɗauke da waɗansu irin makaman yaƙi masu kama da zarto.
Haƙiƙa Waɗannan aljanu sun kasance ababan tsoro da razani ga duk wata halitta mai numfashi.
Lokacin da mahaifina ya yi arba da halittun sai jikinshi ya kama tsuma yana kyarma saboda matuƙar tsoro, amma sai ya yi wuf! Ya zare takobinshi aka fara kallon-kallo tsakani, tsawon daƙiƙa arba'in ɗayan su bai yunƙurin afkawa abokin gwamin shi ba.
A lokaci guda tamkar haɗin baki dakarun suka ɗaga makamansu suka yi ɗauki kan Yasiran suna ihu da kururuwa mai firgitarwa, tare da kai mashi miyagun hare-hare cikin matuƙar zafin nama JURIYA DA BAJINTA ta gaban kwatance. Take mahaifina ya tare su aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matuƙar kwarjini da ban tsoro, a lokacin da dakarun suka yanyame shi tamkar yadda dandazon ƙudaje ke yanyame ƙwallon mangwaro.
Wohoho! Haƙiƙa masu iya magana sun yi gaskiya da suka ce inda babu ƙasa nan ake gardamar kokowa, kuma KARON MAZA sai GWARAZAN JIYA da suka saba gwagwarmaya a filin fama, nan fa ƙarar karafniyar ƙarafa haɗe da ihu da hargowar dakarun aljanun ta cika kogon baki ɗaya, kuma kogon ya ɗauki zafi ainun, tamkar zai yi bindiga ya tarwatse, sai da aka shafe tsawon sa'a ɗaya da daƙiƙa ɗari uku ana wannan ɗauki ba daɗi.
Al'amarin da ya yi matuƙar ɗaurewa aljanun kai kenan kuma ya ba su mamaki, domin fiye da shekaru dubu biyu suna gadin wannan kogon na GARUL-SHAMMAR ba su taɓa ganin halitta mai matuƙar zafin nama da ƙwarewar yaƙi tamkar na mahaifina ba.
Al'amarin mahaifina kuwa lokacin da ya fahimci cewa babu alamun nasara, kuma koda alamun gajiya babu a tare da dakarun sai hankalinshi ya dugunzuma ainun ya faɗa izuwa kogin tunani domin samun mafita, koda samun mafitar sai kawai ya mayar ta takobinshi izuwa cikin kube, ya yi wuf ya zaro kubar Miftahul-sihir ya shiga dukan dakarun da ita da dukkan ƙarfin shi.
Wohoho! Haƙiƙa masu iya magana sun yi gaskiya da suka ce, idan kiɗa ya canja dole ne rawa ma ta canja, nan fa abbana ya gano lagon tsuntsayen ya zamana cewa duk wanda ya daka da kubar sai kaga ya kurma wawan ihu ya tarwatse, nan fa ihu da kururuwar shaiɗanu ta ƙara cika kogon, kafin shuɗewar rabin sa'a, nan fa dakarun suka ɗimauce suka kama guye-guje da ifice-ifice, wasu suka shiga ƙoƙarin ƙwace kubar Miftahul-sihir daga hannun abbana, wasu na kai mashi sara da suka cikin matuƙar zafin nama, domin ganin