Showing 3001 words to 6000 words out of 6886 words
Chapter 2 - KUNDIN ALAJABI Book 2 Complete by Mansur Usman Sufi .txt
sun kai shi ƙas.
Ana cikin wannan artabu ne wani daga cikin aljanun ya shammaci mahaifina ya kafta mashi sara a cinya, take inda ya yanke shin ya dare jini ya yi tsartuwa, abbana ya kurma ihu sakamakon zafi da raɗaɗin da ya ji amma saboda JURIYA DA BAJINTA irin ta JARUMAN DUNIYA sai ya ci gaba da yaƙin a haka ba tare tsaida zubar jinin ba, haka ya ci gaba da yaƙin jiri na ɗibar shi a wasu lokutan har yanke jiki yake ya faɗi ƙasa amma sai ya miƙe tsaye zumbur ya ci gaba da yaƙin a haka.
Kaico! Haƙiƙa jarumtaka baiwa ce daga Ubangiji, dukiya, mulki basu bayar da ita face baiwa daga Allah, komai hassadar mutum idan ya ga yadda mahaifina ke ragargazar dakarun cikin baƙin zafin nama da kafin tsiya, dole ya jinjina mashi ya tabbatar da cewa ya cika gwarzon mayaƙi mai ƙarfi na Allah ya isa.
Kasancewar masu iya magana na cewa SARKIN YAWA YAFI SARKIN ƘARFI qna cikin wannan artabu ne mayaƙan suka samu nasarar kai abbana ƙasa suna niyyar hallaka shi, koda ya ga irin mawuyacin halin da yake ciki da yake tsakanin RAYUWA DA MUTUWA, bai san sa'adda ya buga kubar Miftahul-sihir a ƙasa ba, faruwar hakan keda wuya nan take wani farin haske ya yi fitar burgu daga kubar, ya shiga sassan jikkunan sauran aljanun, nan take suka kama ci da wuta suna ihu da kururuwa neman taimako, kafin wani lokaci mai tsawo baki ɗayan su sun sheƙa barzahu.
Cikin matuƙar farin ciki abbana ya miƙe tsaye da ƙyar ya sake kunna kai izuwa cikin kogon,
Tsawon daƙiƙa ɗari huɗu yana tafiya sannu-sannu,
lokacin da rabin sa'a ta shuɗe a dai-dai lokacinne ya iso wani waje mai matuƙar sanyi, hatta durakun dake wajen na dusar ƙanƙara ne, babu wani waje da mutum zai ajiye ƙafarshi face dusar ƙanƙara ce.
Sa'adda mahaifina ya tsinci kanshi a cikin wannan hali sai hankalinshi ya dugunzuma ainun, domin baya sanye ɗauke da rigar kariya daga sanyin.
Cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi mai zafi ya kama mahaifina jikinshi ya kama ƙyarma, tun yana iya takawa da ƙafafuwanshi har ya zamana ya zube a ƙasa magashiyan nunfashin shi na fita daƙyar.
Yana cikin wannan hali ne kwatsam! Bazato babu tsammani sai kawai wani irin ƙatuwar halitta tayo fitar burgu daga dusar ƙanƙarar ta fito waje, Ita dai halittar takasance wata shirgegiyar macijiya mai kauri tamkar bishiyar kuka, jelar murtukekiya ce, bayan ƙaton kanta tana ɗauke da ƙarin wasu guda biyu, na farko yakasance na zaki, ɗayan kuma na raƙumin dawa.
Kaico! Wannan halitta ta kasance mai matuƙar kwarjini da ban tsoro, babu wani jarumi da zai yi arba da ita face ya yi nadamar wanzuwar shi a doron ƙasa.
Babi na bakwai
A can bakin ƙofar shiga kogon GARUL-SHAMMAR sarakunan duniya huɗu suna tsaitsaye suna jiran fitowar mahaifina fuskokinsu a murtuke babu annuri cike da matuƙar kiyayyar juna.
Kwatsam! Bazato babu tsammani sai suka ga sararin samaniya ta yi duhu dunɗum! Tamkar DARE UKU ne ya haɗu waje guda mutum koda tafin hannunshi baya iya gani.
Sannu a hankali duhun dake sararin samaniya ya fara raguwa, sai ga waɗansu halittu masu tarin yawa suna ketowa daga cikin gajimare suna sauka a kan tekun Bahar-rum.
Koda ganin hakan sai sarki Fitinatul-muluk da sarki Hubaizu suka yi wuf suka fito da maduban tsafin su suka shiga gudanar da bincike, koda kammala binciken sai suka taƙarƙare suka bushe da dariyar mugunta, ba komai suka gani ba face halittun da suka bayyana sun kasance rundunar sarakunan duniya biyu, sarkin aljanu baƙaƙen fata da farare.
Sun turo tawagar ne domin su ƙwaci KUNDIN AL'AJABI da kubar Miftahul-sihir da zarar mahaifina ya samu nasarar ɗaukowa.
Sarki Hubaizu na birnin Hindu ya katse shirun da ya wanzu a q hanyar duban sauran 'yan uwanshi fuskarshi a murtuke babu annuri ya ce "yaku manyan abokan gaba a gare ni ku yi sani cewa waɗancan dakarun aljanu da suka bayyana ba su ba ne face Tawagar sarakunan aljanu da suka zo domin ɗaukar kubar Miftahul-sihir haɗe da KUNDIN AL'AJABI, saboda haka yanzu dole mu haɗa kai mu kawar da waɗannan sabbin abokan gaba, idan ya so daga baya kuma sai a raba rai tsakanin mu ga wanda zai zamo zakara a, da zai zamo mamallakin KUNDIN AL'AJABI".
Koda jin wannan batu daga bakin sarki Hubaizu na birnin Hindu sai sauran sarakunan uku suka zare makaman yaƙin su suka yi ɗauki kan dakarun aljanun, koda ganin hakan sai aljanun suka tare su suna ihu da kururuwa mai firgitarwa.
Ana haɗuwa aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matuƙar kwarjini da ban tsoro.
***
A cikin kogon GARUL-SHAMMAR kuwa kafin mahaifina ya yi wani yunƙuri wannan macijiya ta kafta masa sara a hannayenshi da ƙafafuwanshi, nan take nunfashin shi ya fara sarƙewa kuma ya faɗi ƙasa magashiyan".
Lokacin da kyakkyawar baƙuwar jaruma ta zo dai-dai nan a labarin da take bamu sai hawaye suka kwaranyo daga idanuwanta.
Al'amarin da ya sanya jikinmu ya yi sanyi ni da Raudat har ƙwalla ta zubo mana.
Cikin alamun matuƙar tausayi na dubi jarumar na ce "haƙiƙa labarin mahaifinki cike yake da abun tausayi darasi da abubuwan al'ajabi. Kuma ya cancanta ki ɗauki ko wane mataki domin daukarwa mahaifinki fansa, duk da cewar ba mu ji ƙarshen abin da ya faru tsakanin abban ki da manyan sarakunan duniya huɗu ba, duk da cewar da farko mun nufi mu yaƙe ki, amma a halin na ji a raina ni da abokiyar tafiyata za mu taimaka miki ki cimma wannan buri na ki. Amma bisa sharaɗin cewa ba za ki cutar da wani mahaluki ba idan har kin samu nasarar mallakar makaman yaƙin sarkin bokayen duniya".
Sa'adda na zo nan azance na sai fuskar baƙuwar jarumar ta faɗaɗa da murmushi mai taushi, ta dube mu sannan ta yi gyaran murya ta ce "ya ku waɗannan jarumai haƙiƙa nayi matuƙar farin ciki da wannan taimako da za ku ba ni, kuma ina mai tabbatar maku da cewa ba za ku same ni da wani abu na cin amana ko yaudara ba.
Kuma a halin yanzu ba zan iya ci gaba da ba ku labarin mahaifina ba sai dai anan gaba, sai dai ban sanar da ku suna na, mahaifna na kira da suna Sulairat bintu Yasiran".
Sa'adda Sulairat yar mafarauci Yasiran ta zo dai-dai nan azancen ta sai na yafito aljani Jauharul-layal dake tsaye a gefe guda da hannu da ya iso inda muke, taku ɗaya kacal ya yi ya iso gare mu ba tare da wani jinkiri ba Raudat, Sulairat suka haye gadon bayan shi, take na yi koyi da su ina mai zama da daf da inda suke yazamana tazarar dake tsakaninmu bata huce kamu ɗaya ba,
A halin yanzu tafiya ta sauya salo daga mutum biyu izuwa uku, wato ni Raudatul-abyad sai jaruma Sulairat.
Sai da muka shafe tsawon sa'a huɗu muna keta gajimare cikin matsanan gudu na keta sa'a, ɗa ya daga cikin mu bai ce uffan ba, a wannan lokaci ne Raudatul-abyad ta lura da cewa Sulairat na satar kallo na lokaci zuwa lokaci, koda ganin hakan sai ta daka mata wata harara dake nuna tsantsar kishi da soyayya.
Ana cikin wannan hali ne kwatsam! Sai mu ka ga aljani Jauharul-layal ya tsaya cak! A sararin samaniya, cikin fushi Raudatul-abyad ta dube shi tana mai daka mashi tsawa ta ce "ya kai Jauharul-layal shin ina dalilin wannan tsayuwa ta ka bayan ka san cewa muna so mu isa fadar sarkin bokaye Bazzagul-nadiyar cikin sauri ?
Koda jin wannan tambaya sai Jauharul-layal ya risina cikin ladabi ya ce "ki gafarce ni ya shugabata bakomai ne ya sanya na dakatar da tafiya ba face bisa jiyo ƙanshin 'yan uwana aljanu a daf da mu, hakan ya tabbatar min da cewa akwai waɗanda ke biye da mu…"
Karfin jauharu ya gama rufe bakinshi kwatsam! Bazato babu tsammani sai mu ka ga tawagar waɗansu zaratan aljanu kimanin dubu hamsin, sun bayyana a suna masu yi mana ƙawanya, su dai aljanun sun kasance bakaƙe wuluk, masu girma, kwarjini da munin gaske, fuka-fukansu irin na mikiya ne, a gadon bayansu suna ɗauke da wani ƙusumbi da ya tamkar duwatsu aka saka masu, duk sa'adda da suka buɗe bakunan sai wani ruwa mai yauƙi mai warin gaske ya zubo. Baki ɗayan su suna shirye cikin gagarumar shigar yaƙi mai matuƙar kwarjini da ban tsoro, kuma girman kowannen su ya ninka na aljani Jauharul-layal sau goma.
Wohoho! Haƙiƙa waɗannan tawagar ifritai ta cika abar tsoro ga duk wata halitta mai numfashi, nan fa muka zo tamkar an ajiye kyanwa a gaban garken raƙuma.
BABI NA TAKWS
Lokacin da boka Matawus yazo dai-dai nan a hikayar da yake bawa sarki Sabrul-marhut sai ya ja dogon goron numfashi sannan ya ɗora da cewa.
Lokacin da aka fara kallon-kallo tsakanin mu na tsawon daƙiƙa arba'in sai daga bisani ne shugaban tawagar ifritan aljanun ya ratso ta tsakiyar ya matso daf da mu ya dube mu da turɓunanniyar fuskarshi da ninka ta sauran muni, cikin wata irin kakkausar murya mai kama da saukar aradu ya ce "ya ke Raudatul-abyad tare da tawagarki kiyi sani cewa yau tsawon shekaru dubu da ɗoriya ina jiran zuwan wannan rana da zan karɓi taswirar fadar sarkin bokaye daga hannunki, tsawon shekaru ina bibiyar mahaifinki domin ya mallaki taswirar amma saboda sirrin dake tare shi ban samu wannan dama ba sai a yanzu".
Koda jin wannan batu daga bakin shugaban tawagar sai Raudat ta tari numfashinshi tana mai daka masa tsawa ta ce "ya kai wannan rafkananne kuma tsohon AZZALUMI ka yi sani ce wa, ire-iren ka ba za su taɓa cimma buƙatar su domin mallakar wannan taswira ba, domin shimfiɗa BAƘIN ZALUNCI, shawara ɗaya zan baka ita ce ka janye waɗannan 'yan tsakin mayaƙan na ka, idan kuwa ba haka ba zaka yabawa aya zaƙinta…".
Koda jin wannan batu daga bakin Raudatul-abyad sai shugaban tawagar ya fusata ainun jikinshi ya kama tsuma ya ƙyarma tamkar mazari, idanuwanshi suka kaɗa suka yi jajur, ya buɗi baki a karo na biyu cikin matuƙar fushi har wani irin tururin baƙin hayaƙi na fita daga ƙofofin hancinshi, baki da kunnuwa ya ce " kaicon ki yake wannan ƙaramar ƙwaruwa haƙiƙa kin tafka babban kuskure, wanda ba zan iya yafe miki ba face na shayar dake gidauniyar azabata da dukkanin abokan tafiyar ki, sai dai kafin hakan akwai buƙatar na sanar dake wane ne ni, da farko dai suna na ifritu Sulsainil-auman ibn Turbus, shugaban ifritan aljanun duniya baƙaƙen fata. Da wannan nake yi miki bankwana ga maza nan bisa kan ki".
Koda shugaban ifritai Sulsaini ya zo nan a zancen shi sai ya yi ihu da kururuwa mai firgita GWARAZAN JIYA a FAGEN FAMA ya afka Raudatul-abyad, take sauran yaran shi suka afka mana ni da Sulairat da Jauharul-layal.
A can ƙololuwar sararin samaniya inda Allah (SWT) ya yiwa dukkan halittu iyaka kuwa, anan ne uwar mayu Ummul-sharri ta kafa fadarta domin gudanar da ƙasaitaccen mulkinta,
A wannan lokaci Ummul-sharri tana zaune a bisa karagar mulki a cikin gawurtacciyar fadarta, Ita dai fadar ta ƙasaitacciya tamkar gari guda, gaba ɗaya ginin fadar an yi shi ne da zallar waɗansu irin duwatsu masu ƙwari gaske suna sheƙi da ƙyalli tamkar gilashi, duk inda mutum zai ajiye ƙafarshi wani irin koren gilashi ne mai kama da darduma, idan mutum ya kalla yana iya ganin surarshi, gefe guda kuwa 'yan majalisa na jinsin mutum da aljan na zaune bisa ƙayatattun kujeru na alfarma, a kowa ce kusurwa a fadar dakarun tsaro ne na jinsin mutum da aljan ɗauke da miyagun makamai suna kai komo domin tabbatar da cikakken tsaro, a bisa wata matattakala mai hawa goma anan aka ajiye karagar mulki da aka yi ta da sallar jauhari, kai tsayawa masalta tsaruwa da ƙawatuwar fadar ya huce hankali, kai wani abun ma ko jin sunan shi bai taɓa yi ba, kana gani ka san aiki ne na sihiri.
Shiru ne ya mamaye wajen tamkar mutuwa ta kawo ziyara, uwar mayu Ummul-sharri ce ta katse shirun da ya wanzu ta hanyar sanya hannunta a aljihun rigarta ta ɗauko madubin tsafinta da girmanshi bai zarce faɗin tafin hannuna ba, ta shafe da hannunta na hagu gami da runtse idanuwanta ta karanta waɗansu ɗalasiman tsafi, tana gama furtawa sai ga taswirar gumurzun dake wanzu tsakanin tawagar ifritu Sulsainil-auman da su jarumai Raudatul-abyad ya bayyana a kan madubin.
Koda ganin hakan sai uwar mayu ta taƙarƙare ta bushe da dariyar mugunta, mai kama da haniniyar dawakai, sautin ta ya mamaye fadar baki ɗaya, al'amarin da ya firgita wasu daga cikin jama'ar fadar kenan cikinsu ya ɗuru ruwa, domin sun san cewa duk sa'adda uwar mayu tayi wannan dariya to za ta zartar da wani baƙin zalunci, tsawon daƙiƙa arba'in tana cikin wannan hali sai daga bisani ta murtuke fuska tamkar an aiko mata da WASIƘAR AJALI, kawai sai ya mayar da madubin izuwa ma'ajiyar shi, kana ta dawo da dubanta zuwa ga wani mummunan aljani daga cikin 'yan majalisarta, tamkar ya san abin da take nufi kawai sai ya miƙe tsaye ya matsa daf da karagar mulki ya zube ƙasa ya yi sujjada a gare ta, sannan daga bisani ya ɗago kanshi a ya buɗi baki cikin kakkausar murya mai kama da haushin kare ya ce "gani gare ki ya SARAUNIYA MAI DUNIYA, gajimare kike mai shayar da duniya mugunyar annoba.
Guguwar musiba mai share TAWAGAR ZARATA.
ina gagararre ko hatsabibi ya zo ga GAWURTACCIYA uwar matsafan dunya"
Kin ci dubu sai ceto kin yi KARO DA DUBU kalacen safe, ina mazan suke ne ga sa gudu maganin ƙi gudu"
ANNOBA ƊARI kike duk wanda ya ja dake zai baƙunci barzahu".
Lokacin da ɗan majalisar ya zo nan a kirarin na shi sai uwar mayu ta yi murmushi mai kama da yaƙe da ya ƙara tona asirin munin fuskarta, bisa jin daɗin kirarin da yake yi mata.
Sannan ta buɗe tafkeken bakinta mai ɗauke da waɗansu wargatsattsun haƙora baƙaƙe babu kyawun gani ta ce "an gaishe ka ya kai Darmanu maganin ƙananan ƙwari abin da nake so a gare ka shine ka tafi cikin hanzari izuwa gaɓar dajin Zarutul-shammar domin ka ƙwato min taswirar fadar sarkin bokaye a hannun jaruma Raudatul-abyad, ina mai farin cikin sanar da kai cewa burina ya kusa cika na shiga fadar sarkin bokaye domin na gaje komai nashi, sirrikan tsafi da kayan yaƙinshi, dole ne duniya ta zamto a tafin hannuna, na juya ta tamkar yadda ake sarrafa waina a tanda,
Wannan ita ce dama ta ƙarshe a gare mu domin shiga fadar sarkin bokaye don haka ina mai gargaɗarka ka kula sosai kar a samu kuskure a cikin wannan aiki”.
Sa’adda Uwar mayu Ummul-Sharri ta zo nan a jawabinta sai aljani Darmanu ya risina ya ce “an gama ya shugabata wannan aiki abu ne mai sauƙi a gare ni tamkar cire silin gashi daga cikin tandun mai”.
Ummul-Sharri ta ce “tsafi ya baka kariya ka dawo cikin aminci ya kai Darmanu”.
Koda gama faɗin hakan sai Darmanu ya risina ga uwar mayu sannan ya rikiɗa izuwa wani baƙin haske ya ɓace ɓat daga fadar tamkar bai taɓa wanzuwa ba.
Wannan shi ne abin da ya wakana a fadar uwar mayu ta duniya matsafiya Ummul-Sharri.
Lokacin da muka kacame da azababban yaƙi tsakaninmu da shugaban ifritai Sulsaini da yaranshi sai muka wanzu muka kaiwa juna hare-hare cikin matuƙar zafin nama JURIYA DA BAJINTA ta gaban kwatance, ana fara wannan artabu ne dukkaninmu suka fara gane cewa shayi ruwa ne ba abinci mai nauyi ba, domin matuƙar zafin nama gami da ƙarfin damtsen ifritan ya ninka namu sau biyar, babban abin da ya dugunzuma hankalinmu shine yadda duk sa'adda makaman yaƙinmu suka sari jikkunan ifritan sai mu ji tamkar dutse muka sara, ko gezau ba sa yi sai dai tartsatsin wuta ya tashi gami da ƙara ƙal! Ƙal!.
A duk sa’adda makaman yaƙinmu suka haɗu da juna sai ka ji an kwantsama wata tsawa gami da walƙiya, nan fa sararin samaniyar ya cika da ƙarar karafniyar ƙarafa, ihu gami da hargowar MAZAJEN DUNIYA.
Sai da aka shafe tsawon daƙiƙa ɗari biyu da goma ana wannan ɗauki ba daɗi babu sassauci.
A cikin wannan artabu ne na fahimci Sulairat tafi mu ƙarfin damtse da salon dabarun yaƙi, domin a hankali yanzu tana iya samun nasarar yankan jikkunan ifritan, koda suka fahimci irin ɓarnar da Sulairat ke yi masu sai suka yanyame ta suna kai mata sara da suka gami da yakushi da faratansu.
A ɓangaren aljani Jauharul-layal kuwa ya wanzu yana kai FARMAKI da fuka-fukanshi, bakinshi gami da faratan hannunshi, cikin matuƙar zafin nama JURIYA DA BAJINTA ta gaban kwatance.
Lokacin da shugaban ifritai Sulsaini ya ga cewa sa'a ɗaya ta shuɗe ana wannan baƙin artabu sai ya fusata ainun zuciyarshi ta kama tafarfasa tamkar zata ƙone, ya fahimci cewa wankin wula zai kai su dare, wani abu da ya fusata shi shine tun da yake yin GABA DA GABA da jarumai bai taɓa haɗuwa da bil’adama masu matuƙar zafin nama da ƙarfin damtse tamkar mu ba.
Lokacin da sa'a ɗaya da rabi ta shuɗe ana wannan ɗauki ba daɗi, sai ƙarfin damtsenmu ya fara raguwa yaran ifritu Sulsaini suka fara galabaitar da mu, faruwar hakan ke da wuya sai