Showing 27001 words to 28059 words out of 28059 words

Chapter 10 - GOGA SHA FAMA Complete by Mansur Usman Sufi .txt

Advertisement

sai suka cika da matukar mamaki da farin ciki.


A bangaren Dabbobin hubairu kuwa koda sukayi arbda da Baddadul-ulƙas sai kawai suka afka masa suka shiga yaga sassan jikin shi kafin wani lokaci babu wani abu na jikinshi da basu cinye ba face kans hi.


Kaico! Haƙiƙa mutuwar azzalumai ba ta da daɗin kallo, yanzu dai gashi duk kasaita da dukiya, sihiri gami da jarumtaka da sarki Baddadul-ulƙas ke takama dashi sun zamo a banza yayi mutuwar wulakanci, wacce dabbobi ne ma marasa daraja suka kashe shi wanda shi bai ɗauki rai na ɗan adam a bakin komai ba.


Cikin matukar kwaɗuwa hubairu ya durƙusa a gaban baƙuwar jaruma domin yaga a wane hali take ciki, amma sai yaji taja dogon Gwauron numfashi ta miƙe tsaye cikin koshin lafiya, dai dai lokacin da jaruma Amirat ta iso inda take tsaye suka rungume juna cikin matuƙar farin ciki, koda ganin sai hubairu ya riga izuwa inda mahaifinshi yake tsaye suka rungume juna suna masu fashewa da kukan farin ciki.


A sannanne gumbiya Zarifa dake tare Amirat ta hango mahaifinta sarki uslaim don haka sai ta ruga gareshi suka rungume juna suna masu zubar da hawayen farin cikin sake saduwa da juna,


Ashe shi ma aljani Marhutul-Azab ya lura cewa wanɗannan tawagar aljanu da ke tare da Amirat ba wasu ba ne face zuri'arshi dake bukatar jarumi Hibairu ya ceto su daga fadar sarkin bokayen Duniya, kawai sai ya ruga garesu cikin farin cikin saduwa da juna.


Bayan komai ya samu lafawa kuma jama'ar gari sun taru a wajen lokacin alfijir ya keto sai jaruma Amirat ta shiga yiwa jama'a bayanin yadda akayi ta samu nasarar zuwa fadar sarkin bokayen Duniya a cikin sa'o'i kaɗan har ta ceto rayuwar gimbiya Zarifa yar sarki uslaim tare da zuri'ar aljani Marhutul-Azab da ruhukansu dake ajiye a cikin akwatun shiri, tun daga farko har ƙarshe ta zayyanewa jama'a.


Sa'adda jama'a suka ji wannan bajinta gami da karfin Ubangijin halitta sai suka kara cika da mamaki da imani da Allah (SWT).


Jarumi Hibairu da mahaifinshi Shabbaru ne suka fara ƙarbar kalmar shahada a hannun Amirat, sannan jaruma sunaila, Hizmal, Abidatul-auliya,Nuwairat,yaro Humair makaho, matsafi shubairu, budurwa Nihla,sarki shazwan da tawagar bokayen shi,gimbiya, boka ƙarzum, aljani Darmanu tare da tawagar aljani Marhutul-Azab sai dukkan jama'ar gari da suka bayyana a wajen,


A wannan waje ne wani abu ya faru domin kuwa bayan sarauniya Abidatul-auliya da masoyinta matsafi shubairu sun faɗi kalmar shahada nan take suka ji wannan cutar kuturta dake tsagin jikin su ta daina yi musu ciwo yayin da suka duba kuwa sai suka ga babu komai tamkar cutar bata taɓa wanzuwa ba, yaro Humair makaho kuwa shi sai yaga idanunshi yana iya ganin kowa alamar ya samu lafiya.


Nan fa suka ji sun ƙara imani da ubangijin musulunci.


Kashe gari tun da duku-dukun safiya fadar margayi shaibat ta cika ta batse da jama'a babu masaka tsinke domin yin naɗin sarautar hubairu sarkin sadaukai tare da ɗaurin aurenshi da Budurwa Nihla, sarauniya Nuwairat, jaruma Amirat da gimbiya haya'ul-nur yar mai girma shaibat tare gumbiya Rumaisat yar sarki shuraih,tare naɗin wazirin shi sarkin yaƙi abu-Damraz bayan shima ya karbi addinin Musulunci,


Saurayi Hizmal suka zai auri jaruma sunaila da baƙuwar jaruma ba wata bace wannan baƙuwar jaruma ba face amrita wacce suka kasance Hassana da Husaini ga jaruma Amirat, lokacin da fuskar ta ta bayyana a fili sai da kowa ya cika matuƙar al'ajabi bisa ganin yadda kamannin baƙuwar suka zo ɗaya sak da na Amirat tamkar an tsaga kara.


Sarki shazwan kuwa zai auri gimbiya yar uwa ga jaruma sunaila,


Sarauniya Abidatul-auliya kuwa da matsafi shubairu masoyin ta.


Sarki Hamza mahaifin jaruma Amirat ne ya zamo waliyin amaren, wani hadimin shi mai suna Salman kuwa ya zamo waliyin angwaye.


Bayan anyi shagin ɗaurin aure da naɗin sarauta dukiyar da za'a bawa hubairu ta nasarar cinye gasar GOGA SHA FAMA kuwa sai yayi umarni aka dunga rabawa talakawan gari tare bawa dukkanin bayin kurkuku da aka 'yan tasu.


Haƙiƙa anyi gagarumin shagalin da ba'a taɓa yin kamar shi ba iya Tsawon wanzuwar birnin madinatul-shaja'a, domin kowa ya wadata da arziki mai tarin yawa.


Bayan mako guda ne da faruwar hakan sai sarki Hubairu yayi umarni ga waɗannan aljanu yan uwan aljani Marhutul-Azab suka ɗauki Sarauniya Abidatul-auliya da angwanto, sunaila da nata aka kai su izuwa kasashen su,


A inda matsafi shubairu yazama sabon Sarkin birin Tehran,saurayi Hizmal kuwa yazamo sabon sarkin birin Baitul-mausul, bayan ya warkar da sarki ishwar mahaifin jaruma sunaila daga lalurar dake damunshi bisa ikon Ubangijin musulmi batare da anyi amfani da tsumin tsafin dake fadar sarki bokayen Duniya ba , yarima ubaiyu ya zama wazirinshi, yarima zaiyum kuwa ya zama shugaban majalissar sarki bayan sun karɓi addinin Musulunci, kuma suka janye gabar dake tsakanin su da yar uwar su jaruma sunaila.


Sarki shazwan da amaryar shi Gimbiya Hushriba yar uwata ga sunaila suka kasance cikin aminci,


Lokacin da aljani Darmanu ya ɗauki sarki uslaim, boka ƙarzum da gimbiya Zarifa bai zame ko ina sai tsakiyar birnin baharen ya sauka a turba,


Nan fa farin ciki ya kama jama'ar bisa dawowar gimbiya Zarifa da sarki, kuma a wannan rana aka ɗaura auren boka ƙarzum da gimbiya Zarifa


Sarki Hamza mahaifin jaruma Amirat ya koma izuwa birnin madinatul-salam bayan ya aika da malaman addini izuwa dukkan kasashen daban-daban.


Yaro Humair makaho ya ci gaba da kasance tare da sarki Hubairu, daga wannan rana hasken musulmi ya mamaye ko ina a duniya, a kawo KARSHEN ZALUNCI da azzalumai, adalci ya cigaba da wanzuwa.


ƘARSHE


Alhamdulillah






Daga mai ɗebe maku kewa a kullum da Koyaushe
Sarkin marubuta littattafan Yaƙi
MANSUR USMAN SUFI
08137237071

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login