Showing 114001 words to 117000 words out of 201974 words
suka Lula barcin su mai dadi cike da kwanaciyar hankali.
~ZEE~
Yau kimanin 3month kenan rabonta da Nigeria, zaune take a garding d'in gidansu ta mike kafafunta tana zaune a kasa ta shimfida dadduma, gaban ta littattafan addinine kanana irin su kawa'idi arba'una hadis durusul arabiya da sauransu, hannunta kuma kur'anine izifi biyar ta bude suratul jinn tana nazari a bayyane.
Daga bayanta taji an mata sallama, da fara'a a fuskarta ta juya ta kalli wacce ke mata sallaman ba wata bace illa malamarta dake zuwa har gida tana koyar da ita karatun addini, a wani babban Islamic school dake garin da suke a Malaysia ta dauki malama macce wacce zata dinga zuwa har gida tana koyar da ita, makaranta taso ta dinga zuwa tana daukan karatau saidai babban malamin ya nuna basa daukar matan aure balle ita gata harda ciki, hakan yasa ta nemi alfarman a bata malama mace wacce zata dinga biyota gida tana koyar da ita in yaso duk wata zata dinga biyanta albashi mai tsoka, babban malamin ya amincene kawai saboda ganin yadda ta nace da gaske tana son karatun, hakan yasa ya duba cikin yan unguwan da suke ya hadata da sumaita, balarabiya da zama ya kawo iyayenta Malaysia.
Zama sumaita tayi suka gaisa cike da mutunta juna , nan zee ta shiga biyo mata karatuttukan da sukayi jiya ba laifi kuwa kanta yana dan ja, kara mata sumaita tayi sukayi sallama ta tafi ita muka zee ta zauna tadanyi nazari na dam wasu mimtoci kafin ta lallaba ta tashi da'ker tukeken cikinta najanta gata ba auki ba,ta hada kayan karatunta a jaka ta linke dadduman ta ta nufo cikin gidan.
Sanda ta shigo falon mom da dad na zaune bata ce musu kala ba bayan sallamar data musu ta wuce dakinta da yanzu ya dawo falon kasa saboda hawa stairs na bata matukar wahala.
Da idanu suka rakata har ta kule ma ganin su, Dad ne ya sauke ajiyar zuciya yana kallon mom yace"lamarin daughter ya fara shamun kai, anya ba asiri wannan dan iskan yaron ya mata ba kike gani, ki duba kiga yadda ta canza gaba daya cikin dan wasu watanni ta zama wata silent da ita, ko magana bata mana idan ba da kwakwaran dalili ba, naji na hakura na janye na bar mata cikinta ta Haifa tunda dai ita taji ta gani zata iya , amma duk da haka ban tsira ba" mom tace "bana tunani asiri ya mata nafi tunanin soyyaya ce take mishi mai matukar girma, lokacin da ta fara zuwa makarantar koyan girki Dana tamabayeta dalili, direct ta gayamin saboda Aslam ne , saboda duk randa ta koma dakinta t,ya kasance ta iya girki Aslam zaiji dad'i zaiyi alfahari da ita" dad ya daura da cewa "haka nima dana tambayeta game da wannan karatun da takeyi, ce min tayi saboda Aslam ne, saboda yana son tasan addinta ni wannan lamari ya fara isana fa , yanzu cikinta yakai wata nawa" mom tace shekaran jiya da mukace asibiti dai akayi scanning Dr yace wata bawai kenan cif" sauke ajiyar Dad zuciya fuskar shi dauke da matsanan cin damuwa yace "Allah ya sauke ta lafiya" mom ta amsa da amen ya rab , itama zuciyarta babu dad'i...............
Comment nake so ta ko'ina kokuma mu koma tsallake tsallake baban gora😁 ehee kundai ji na fada ko naga comment kokuma update ya koma yau ayi gobe a huta.
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏.
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌
(In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls)
{Nasadaukar da wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiy,Allah kajiqan iyayen mu}
💖Tallah!💖 Tallah!!💖
💖Tallah!!!💖
💖
Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da
_Rantsattsun lesussuka💃,
_Atamfofi manya da k'anana💃
_Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃
_Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃
_Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃
Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzu..........
Ga numbern mu kamar haka👇
08062160424
08066891424.....
Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌
Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌
Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃.....
Page 103
Washe gari bayan sun tashi da asuba, taimaka mai tayi yayi alwala ya tafi masallaci, ita kuma a nan dakin nashi tayi sallah bayan ta idar zama tayi tayi azkar da sauran addu'o'i da takeyi, a karshe ta roƙi Allah yaba Aslam lafiya, alkur'ani ta dauka ta shiga karatun a bayyane.
Bayan an idar da sallah a masallaci, shima dai zama yayi a can yayi dukkan addu'o'i shi a karshe ya roki Allah yasa Asmah ta soshi koda Rabin sonda yake mata ne, Allah ya kawo mishi karshen komai cikin sauki, daga nan kuma gida ya dawo direct.
Tun daga bakin kofa yake jin zazzakar muryarta tana karanta alkur'ani mai tsarki cikin suratur nisa'i, dakatawa yayi daga sallamar da yayi niyya, ya tsaya yana saurarenta yana lumshe idanu, godiya da kirari ya shiga jerowa ubangiji daya mallaka mishi Asmah a matsayin matar sa, take kuma zee ta fado mishi a rai, ya tuna fama da gwagwarmayar daya ke sha kullum idan yana koya mata karatu, sai ranshi yayi matukar baci, ya mata jan ido take maida hankali, kuma washe gari idan yace ta biya da'ker take iyawa.
Minti kusan 15 ya kwashe a tsaye a wurin yana saurarenta kafin kuma, a hankali ya tura kofar bakin shi dauke da sallama, bata amsa ba saida takai wayar da take karantawa sannan ta yi sadakallahul azim, ta amsa sallaman shi, kara sowa ciki yayi ya zauna a bakin bed, addu'o'i tayi ta shafa sannan ta juyo ta kalleshi tace mashi "in kwana Mr Aslam " murmushi yayi cikin jin dadi ya amsa mata da "lafiya lau, kin tashi lafiya ya hidima dani" martanin murmushin ta mayar masa sannan tace"lafiya qlau alhmdllh ya jikin ka" ya amsa mata da cewa "da sauki"tace "Allah uban giji ya kara afuwa, ni zanje nayi wanka a dakina, daga nan zan shiga kitchen me kake so na girka maka" shiru yayi kafin yace "yau dai na baki zaɓi ki dafa duk abinda kike son ci nima zanci" OK kawai tace sannan ta tashi ta nade pray mat ɗin ta ajiye a ma'ajiyar sa ta fice daga dakin,
Dakinta ta je ta fara gyara wa ta share duk da ba wani datti yayi ba, tana gamawa ta shiga toilet dan tayi wanka.
Bayan fitar ta zama yayi ya dauki alkur'ani data ajiye yana karantawa shima, daga gefen sa wayar sa dake ajiye ya fara ringing, daukan yayi ya duba mai kiran, Amir ya gani dan haka ya saki murmushi kafin yayi picking call ɗin yana dagawa daga cen bangaren Amir yace"sannu hakimi, wai har yanzu baka gama cin amarcin bane, yau wata nawa rabonka da da kaje office" dariya Aslam ya kwashe dashi sannan yace"yau kuma wutar masifa ke cinka, naga ko gaisawa bamuyi ba ka hauni da tambaya" Amir yace"abin naka ne ai ya fara wuce gona da iri idan ka ajiye aikin ne sai ka faɗa kawai ayi replacing din wani da kai, haka kawai kabar dan taliki da aiki,kai kana na can kana sharban amarci kama manta da mutane idan ba mutum ya kira ka ba kai baza ka kira ba" Aslam yace"sannu daddy ai sai kayi replacing dina da wanin mu gani, da kake ta wani maganar amarci amarci, ni na gaya maka amarci nake sha " dariya Amir ya kwashe dashi kafin yace"ai nasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya" Aslam yace " kai dai bari kawai ka tayani da addu'a ina nan inata kokarin kafa gwamnatina" Amir yace "rannan muna waya naji ka sako min wasu soki burutsu" kwashewa da dariya Aslam yayi, take kuma ya shiga bama Amir labarin abinda ke faruwa.
Kyalliyarta tayi kamar kullum sai tashin kamshi takeyi, fitowa tayi ta nufo hanyar kitchen don hada musu breakfast,kunun tsamiya takeson yi yau da alale, la'akari da tayi da bai da lafiya bakin shi ba dadi ƙila zaizo Abu mai dan tsami tsami, har ta dauki sacet din garin kunun ta fara gwabawa sai kuma ta tsaya tana tunanin anya zai sha dan dai ko a gida bata taba ganin yasha wani kunu ba inba na gyada ba, zuciyarta ta bata shawara da cewa kije ki tambaye shi mana, ki cire kokwanto aranki, shawaran zuciyarta tabi ta ajiye kwabin da tajeyi ta nufi dakin shi.
Daidai lokacin Aslam ya fara ba Amir labari, har takai hannu zata tura kofar ta tsinkayi muryarsa da abinda yake fadi cike da nishadi yake bada labarin, yanayi yana kwasan dariya, kusan suman tsaye tayi a bakin kofar nan, kanta ya daure, yanzu dama duk wannan rashin lafiyar na Mr Aslam na karya ne dama pretending yake yi, yaji sauki tuntuni, take taji ranta ya baci, tunani ta shiga yi ta shiga ne kota koma, wani zuciya ya bata shawara ki shiga kawai ayita ta kare, dakewa tayi ta tura kofar ta shiga ranta a bace, ya juya baya baima San da shigowarta ɗakin ba daidai lokacin Amir yana cewa"lallai Aslam ka cika ɗan air, wato sanyi kakaji zai kashe ka ta rungume ka ko" kwashewa yayi da dariya yace "baiwar Allah har hawaye takeyi saboda tsabar tausayina, haka zataji tana sannu Mr Aslam jikin ne innalillahi na shiga uku,dan Allah Mr Aslam karka mutu" yana mganar ne cikin kwaikwayon muryarta, suna dariya shida Abokin cin mushen nashi,dai dai time d'in kuma Allah ya bashi ikon juyowa, idanunshi ya sauka a kanta ta rike ƙugu tana wani huci, take hantar cikinsa ta kaɗa gadaishi rike da waya a hannu, shi tsoran shi daya baisan tsawan lokacin data ɗauka tsaye tana sauraran shi ba, duk da haka bai karaya ba , maida murya yayi ya komar dashi na marasa lafiya yace"wlh dan uwa husnah yar Aljannah ce tana kokarin kula dani sosai, tana da zuciya mai kyau" yanayin yana dafe kirji yana sakin yan ƙananun tari, daga daya bangaren Amir najin haka ya gane abinda ke faruwa, shiru yayi yana suraren diramar nan, yana jin nishadi.
Harara ta wulla mai tare da cewa "yau dubun ka ya cika kabar wani pretending na gano ka, sannu da kokari ka kyauta" iya abinda ta iya fada kenan ta juya ta fice daga dakin, kasa koda kwakwaran mosti yayi, gadai waya a kunnenshi har zuwa wannan lokacin ya kasa saukewa,a baiyane ya furta"innalillahi wa inna alaihi rajiun shike nan ta kare min "daga can bangaren Amir ya kwashe da wani irin dariyar keta don duk abinda ke faruwa yana sauraren su, sai lokacin ya tuna wayar ma a kunne take Ashe budar bakin shi sai cewa yayi "Allah ya isa tsakanina da kai Amir, ina zaman zama na da safen nan ka jawomin tonuwar asiri" cikin dariya Amir yace"Allah ya kara sauƙi Mr Aslam sai munzo dubiya, ka gaida min kanwa da kokari " tsabar haushi yanke wayar yayi, tare da yin jifa da shi Allah ya taimaka ya fadi akan gado.
~BATOOL~
Haka suka ci gaba da Rayuwa har tsawon sati hudu babu wani sauyi a game da zaman su, Dr bash yayi iya kokarin da zaiyi ya shawo kanta yayi Abu yaci tura, dole ya koma gefe ya zura wa sauarautar Allah ido ,gefe daya kuma ya dukufa da addu'a, kuma alhmdllh yaga alfanun hakan dan yanzu rawan jikin nan da takeyi idan ta ganshi ta daina, takan fito falo ta zauna tayi kallo wani bin ma suyi tare ammafa tana a takure dan ko kallonshi bata iya yi, idan ya mata magana zata amsa shi amma ba tare da hada ido dashi ba, yakan shiga dakin ta idan bukatar hakan ta taso yanzu ta daina garkamewa, shima kuma bai kara nuna yana son koda rike hannunta bane,duk da a matukar takure yake, kullum daren duniya daker yake iya bacci amma ya daure yaci gaba da gayawa mai duka, hakan kuma yasa ta dan fara sakin jiki kadan kadan dashi.
Zaune take a dakinta a gaban dressing mirror fitowarta daga wanka kenan, zata yi shafe shafe,cike take da tsantsar damuwa tun last 2 Weeks take ta zuba idon ganin period dinta amma shiru, abin tun tana dauka wasa har gashi ta kwashe sati biyu cur ba amo ba labari, abinda bai taba faruwa da Ita ba, tunda ta fara al'ada bai taba kin zuwa mata ba, kuma bai taba canza mata lokaci ba, imma ya canza baifi ya kara kwana uku ko biyu ba amma wannan karon gashi har 2 weeks, da wannan tunanin ta shiga shafa man shafa warta, tun kan tayi nisa ta fara jin kamshin man da take mutuwar so yana shiga mata hanci yana tayar mata da zuciya daure wa tayi ta CI gaba da shafawa a jiki, ta gama da jiki tana kai hannunta fuska wani irin yun kurin amai ya taso mata ba shiri ta mike da gudu zuwa toilet ta shiga kelayawa.
Daidai wannan time d'in Dr bash cikin shirin shi na tafiya hospital, ya nufo dakinta dan ya mata sallama, wayar shi kare a kunnenshi, waya yake yi da maah, tana kara jaddamai mai ya kula da batula da abida ke cikinta kuma in ya tashi aiki ya biyo akwai jike jiken da masu ciki kesha maganin zaki da sanyi , tasa an hado ma batool d'in ya biyo ya karba, shidai kawai da to yake amsa mata yana mata godiya, a karshe ta nemi ya hada ta da batool d'in taji lafiyar ta.
Yana isa kofar dakin yayi sallama har sau uku bata amsa ba hakan yasa ya kutsa kai kawai cikin dakin yana shiga yaji kakarinta a toilet ga kofar toilet d'in a bude, baisan sanda ya katse kiran maah ba ya ajiye jakar sa ya nufi toilet d'in da sauri, aamunta yayi duke a toilet din ta dafa kwamin wanka da duka hannayenta, sai kwarara amai tajeyi baji ba gani, da gudu ya karasa ya tallabota jikinshi, a haka ya samu ta gama aman, amai tayi bama wasa ba don babu abinda yayi saura a cikinta na daga ruwa da abincin da taci.
Jikin ta gaba daya ya saki lokaci gudu, taimaka mata yayi ta kuskure bakin ta ta wanke fuskarta, rungumota yayi ya fito da ita a toilet d'in, yadda tayi lamo a jikinshi abin ya matukar bashi mamaki, idan ya kula da kyau harda kara cusa kai yaga tanayi a kirjinshi tana shaqan kamshin jikin shi tana sauke ajiyar zuciya a wahalce, kan gado ya direta yana binta da kallo, matsayin shi na Dr baya bukatar Karin bayani daga bakin wani tsab ya fahimci meke damunta, farin ciki ne fall a ransa kamar ya daddage ya tsala ihu haka yakeji amma sanin wacece batool yasa ya Adana farin cikin shi ko a fuska bai nuna wani abuba, ba karamin aikinta bane ta saka mai rigima bata son cikin, bazai yi gangancin sanar da ita ba har saiya tabbatar tana son cikin tukunna, take kuma idan shi ya sauka akan wayar shi dake ajiyar bakin bed, maah ce ta fado mai arai baisan sanda wani kayataccen murmushi mai sauti ya subuce mai ba, Wanda har saida batool dake kwance kan bed idonta a runtse, ta ware idanu akan fuskar shi.
Wani yarr taji a jikinta, tsigar jikinta ya fara tashi, wani irin azabebben feeling taji ya ziyarce a lokaci daya, bata San ta ƙura mai idanu ba, Dr bash mamakin irin kallon da take binshi dashi yake yi, tunda abin nan ya faru a tsakanin su bata taba bari sun hada idanu sun kalli cikin idan juna ba , amma yau a lokaci daya ji yadda take binshi da wani irin mayen kallo kamar zata cinye shi.
Dage mata gira daya yayi tare da cewa "yadai" sai lokacin taji wani kunya ya kamata tayi kasa dakai, murmushi ya saki tare da cewa "zan tafi office inada theater da karfe goma sha daya, amma zan kira maah ta turo miki Afrah tazo ta zauna dake kafin na dawo bazan wani dade ba yau saboda ke ina gama abubuwa masu mahimmanci zan dawo" ba tare da ta kalleshi ba ta gyada mai kai, sa kai yayi ya fice daga dakin bayan ya dauki wayar shi da jakar shi.
Da kallo ta raka bayan shi har ya kule ma ganinta, ji take kamar ta jawo shi ta shige jikinshi ta shaki daddaɗan kamshin turarensa ko zata samu sauki akan abinda takeji yana taso mata game da shi,rutse ido tayi tana matse kafa, a bayyane ta furta"innalillahi wainnailaihi rajiun, meke shirin faruwa da nine ni batool na shiga uku na ya rabbi ka kawo min dauki"...............
Masu comment dina,ina mika muku dinbim godiya wlh naga zafafan comment ɗinku jiya kuma na karanta na yaba, wlh saboda ku kawai yau nauyi typing, kuyi min hakuri kar kuga ban yi reply ba, bani da isahen time da kuma caji ne, amma wlh duk na gani naji dadi sosai wlh inayinku irin totally dinnan💋 a ci gaba da gashi dama ta biyu insha Allahu yazo gangara saura kiriss💖
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌
(In 👂👂👂 yaji gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls)
{Nasadaukar da