Showing 3001 words to 6000 words out of 54763 words
Chapter 2 - FAREEDAH NABEEL COMPLETE BY A'ISHA FULANI GAL .txt
fito kenan?
"Murmushi NABEEL yayi tare da rungumota jikinsa na 'yan wasu dakiku ita kuwa kara shigewa jikinsa tayi ta langabar da kanta akirjinsa ayayin daya daga hannunsa nadama yana shafa tundaga tsakiyar kanta harzuwa karshen kitson dake kanta sannan yadagota daga jikinsa yadan ja dabaya kadan yakura mata idanu kamar baitaba ganintaba
sannan cikin murmushi NABEEL ya buɗe bakinsa yace"
Eh rabin rai ɗina
HAR na fito,..
Barka da aiki yar aljanna!
"Yawwa ina kwana?
"Lafiya kalau
Cikin nutsuwa NABEEL yah Kai hannun sa ya ja kujera sannan ya zauna a saman kujeran , Cikin kulawa NABEEL ya dubeta
tare da faɗin"
Baiwar Allah kenan
kafin na tashi daga... na tabbatar da kin kammala min komai ,...kai tsaye nike shiga banɗaki , dan na tabbatar da cewa kin riga kin had'a min ruwan wankah sai dai ince zan watsa ruwa,.ko ince zan yi wanka zance
"Murmushi kawai FAREEDAH ta ke famar sakewa batare da tace masa komai ba
"Yayinda shi kuma NABEEL ya cigaba da cewar"daga na fito parlourn kuma na tabbatar da cewa kin gama komai na karin-kumallo na wanda zan ci insha Kafin in tafi wajen aiki .bazan bukaci komai ba
"Kallon kyakkyawar fuskarsa FAREEDAH tayi Kafin cikin tsantsar farin ciki FAREEDAH ta furta"
Haka ne kalbinerh
To yanzu a nan gurin mai kake so a fara zuba maka?
"Kamar kullum yar aljanna .inji cewar NABEEL sannan cikin murmushi NABEEL ya buɗe bakinsa ya ɗora da cewar"nasan kin fini sanin abun da nike fara karin-kumallo dashi,da kuma wanda nike gamawa da shi , cikin nutsuwa FAREEDAH ta shiga serving ɗinsa
"Cikin sauri NABEEL ya furta"
Aaaa,Ai yayi yawa ,
kice gara dakika ankarar dani badan haka ba da kin zuba min abinci da zan kasa ci
itadai FAREEDAH girgiza kai kurum tayi tana mai famar sakin murmushi
Zaunar da Ita yayi asaman cinyarsa kafin cikin tsantsar farinciki NABEEL yake fad'in "
Allah ya yi maki albarka, mata ta,rabin rai Allah yasa ki gama da duniya lafiya kema Allah ya baki wanda zasu kula da ke kamar yadda kike kulawa dani, Allah ya ƙara miki lafiya Tare Da nisan kwana, FATAN ALKHAIRI NiKE MAKi A DUKKANiN RAYUWAR Ki UBANGIJI YA KAREKi DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKi HASSADA
NAGODE
NAGODE FAREEDAH
NAGODE FAREEDAH
NABEEL TAWA
"Cikin smiling FAREEDAH ta kai hannunta a kansa tare da shafa masa lallausar gashin kanshi kafin ta furta
"AMIN YAH RABBIL A'ALAMIN my sugar baby,nima haƙa ina matuƙar godiya da kulawar ka agare ni Allah ya bar mu tare
Wash nagaji FAN'S
Inason kusani idan har naji shiru banga zazzafar comments naku ba
To shakka babu kuma kunji shiru
Lovers😍🥰😘
HEY
MARAICIN AZRAH FAN'S CLUB
daku nike
Ku tashi daga barci
Wallahy Allah ko
NARUFE gidan
Kuma kusan Wannan ƙaramin aiki nane ehem🤷🏻♀️Haba mana malam kullum gida kenan shiru shiru kamar makabarta ko yar Sada zumunci nan bakuyi*
*ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI*
#COMMENT'S PLEASE !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!
*A'ISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹
*FAREEDAH NABEEL*
🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹
By
*AISHA FULANI GAL*
*EDITED BY UNCLE YUSEEP NADABO*
*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*
*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network
Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*
*I'm
selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951
*🌺chapter 3-4🌺*
BOSSO ESTATE
__________NABEELAH _______
Wata kyakkyawar yarinya ce tabugawa a jarida na hango, fara ce sol kyakkyawar matashiyar budurwa ce, Asalin kyakkyawar kuwa domin duk inda ake batun kyau to wannan matashiyar budurwar zata amsa first number, Sanye take cikin wata koriyar atamfa me ratsin ruwan hanta ajiki ɗinki babu karya yayi matukar kyau sosai sai dai anci ma atamfan mutunci sosai riga da sket ne aka yi mata 8piece's kuma ya yi mata kyau dan duk wani kyawun dirin ta yagama bayyana ...
_____NABEELAH KENAN ____
Wanda bata haura shekara goma sha shida...... A duniya ba ta had'u iya haduwa dan komai nata me kyaune, gwanin birgewa,,.. Tsaye NABEELAH take a cikin bedroom d'inta, daga ganin alamunta waya take yi,
wayace kare a kunnenta, , cikin zazzakar muryarta mai matukar dad'in sauraro take magana, "..
Alright to gani nan fitowa
Cikin nutsuwa ta juya kana ta nufi hanyar fita daga cikin ɗakin cikin salon takun tafiyar ta mai
matukar ɗaukan hankali,....
Acikin parlourn su ta tadda Hajiya Nafisat tana zaune a saman two-seater daga ganin alamunta tana zaman jiran fitowar y'ar tatace,..
Zaune take a cikin hamshakin parlour d'inta, kallo daya zaka mata kasan dukiya sun zauna mata, ga wata Tsaleliyan phone d'inta kiran iPhone 15 agefen tah,.
Ta hakince Sai takama take yi da gadara, yayinda wata Ma'aikaciyar Gidan take ta famar mata fiffita, duk da uban sanyin dake falon kuwa, daga ganin alama ita ko sanyi bataji. a cewa ita zafi take ji,
da sanyi safiyarnan, Cike da izza take kad'a yan-yatsun tah wanda suka sha gwala-gwalai, Saman kyakkyawar wuyanta Shima yasha ado da sarka Mai ban mamaki.
Sannan ta gyara sumar kanta, Sai sheki yake, sannan ta daura mashi, Dan kwali irin daurin ture kaga tsiya nan.
______HAJIYA NAFISAT KENAN, WATO MAHAIFIYAR SU NABEEL D'IN FAREEDAH,
Ita ko Ma'aikaciyar Gidan Tana ganin fitowar Nabeelah ta d'an d'ago kanta,sai da ta d'an kalli NABEELAH tukkun kafin daga bisani cikin girmamawa ta Dan dukar da kanta,tare da furta...
"Barka da fitowa
Karamar hajiya!...
Ina kwana!! da fatan kin tashi lafiya ?..
Kallonta Nabeelah tayi tukkun kafin daga bisani cikin kulawa ita ma ta bud'e bakinta tace..
"Lafiya kalau
Cikin nutsuwa ta maida Kallonta izuwa gurin Mommyn su A inda take zaune.
Smiling Nabeelah tasake tare da fad'in "
Mommy yau kuma sai ina da sassafen nan,halan unguwa zaki?
Mik'ewa tsaye HAJIYA Nafisat tayi cik'e da gadara cikin izza da isa, sannan a hankali ta bud'e bakinta tafara magana, "...
Sai gidan uban ki cewar Mom tana mai d'aure fuska
Sannan cikin d'aure fuska mommy ta cigabada cewar "
Dan Allah ki yi kokari ki shiga kitchen, ki had'a mana abinchin breakfast kafin In dawo,don kema kisan bana iya cin girkin kazamai yan aikina ,saura kuma ki tsaya tsumulmulah da iya yi irin naki..........
"Okay..
To anyi angama yanzu ma kuwa zan shige cikin kitchen d'in Insha Allahu inji cewar NABEELAH sannan ta cigaba da cewar "
Dama na tsaya yin wanka ne shiyasa kikaga ban fito da wuri ba,..
"Cikin d'aure fuska Mommy tace" nizan wuce gidan NABEEL , Dan so nake da sassafen nan naje na ci mutumci matarr sa , Dan nagaji da jiran gawan shanu ba kaho,..." ɗaure fuska NABEELAH
tayi kafin cikin ɗaure fuska had'i da b'ata fuskarta Nabeelah ta furta"..
Haba mana Mommy wanann wacce irin masifa ce haka
Yanzu ke bakijin kunyar tashi tunda sassafe kije gidan surukan ki neman rigima ba, wannan wacce irin masifa ce haka!
ke kenan kullum cikin masifa da bala'i dan Allah Mommy kibar matan Yaya Nabeel tah huta haka, dan Allah ki sakar mata mara tayi fitsari, ki duba kigani
Sabida tsabar masifar ki ne fa yasa suka bar gidan nan ba shiri.......
Cikin fusata Mommy ta daka mata tsawa tace "..
Ke
Naci gidanku idan baki rufe min bakiba
"Cikin sanyi murya Nabeelah ta bud'e bakinta tace "kiyi hakuri, Allah ya huce zuciyar ki dear Mom, sai kin dawo Allah ya tsare hanya ta k'arasa maganarta tana mai kama kunnenta "batare da Mom tace da ita komai ba tanufi hanyar fita daga parlourn cikin bacin rai mai tsananin gaske
, tana k'arasa fitowa tsakiyar compound d'in Gidan, ta tadda Idi drivern-ta a tsaye yana jiran fitowar ta, ai kuwa yana ganin fitowar Mommy cikin sauri Idi driver ya bud'e mata marfin motah, ta shiga sannan ya rufe, cikin sauri ya zagaya yashiga cikin motar shima, Kallon sa tayi tare da fad'in
"Kai Dan kutumar ubanka baka iya gaisuwa bane!?
Atsorace Idi drive yace.
“Ina kwana Hajiya Nafisat?.
"Mtswww
Batare da Mommy ta amsa masa gaisuwar tasaba taja masa wani dogon tsoki,
cikin sauri Idi ya tada motar kana gate man ya wangle masu kofar gate d'in Gidan suka fice cikin gudu kamar zasu tashi sama Dan yasan halinta yana fara tafiya kadan kadan zata daka masa Tsawa tace masa ya kara wuta
_______*GIDAN NABEEL*____
Bayan 30minutes mommy ta iso GIDAN NABEEL ,cikin sauri MOMMY , ta shigo cikin parlour,tare da furta "
Asallamu aleykum!
Assalamu alaikum!!
Assalamu alaikum....
"Cikin sanyin murya had'i d'an d'aga murya ! FAREEDAH Ta katse Mom ta hanyar fad'in".
AMIN WALKSLM
"FAREEDAH ta amsa ma Mom sallamar tata, cikin sauri FAREEDAH ta fito daga cikin kitchen,Wani irin Dam! Kirjin FAREEDAH ya bada wani mugum sautin na bugu saboda ganin Mommy NABEEL da FAREEDAH tayi atsaye acikin parlourn su kafin kace k'obo tun jikin FAREEDAH yafara rawa sai wani irin mugum k'aduwa sassan jikinta yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,,,
Kai tsaye inda Mommy take tsaye ta nufa ,cikin sauri FAREEDAH ta k'araso gurin Mommy a inda take jikinta sai wani kad'uwa yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,
cikin nutsuwa had'i da fad'uwar gaba ta durk’usa akan gwuiwowin ta Wanda suka lume cikin lallausar carpet d'in dake parlourn ,sannan cikin tashin hankali da kuma firgicin da ta samu kanta aciki,murya na rawa tamkar wacce aka jonawa shocking tace.
"Momma Dan Allah kiyi hakuri ina kitchen ne banji shigowar kiba! , Good morning hope kin ta tashi lafiya? bismillah zauna mana..... ....cikin fusata!Mommy ta katseta ta
hanyar fad'in "....
Kin Ci Gidan ku! Tana mai aika mata da dakuwa, nace kinci ubanki Malamin tsubbu shegiya yar matsiyata
.Bakar juya...
Sannan ta buɗe baki cikin tsantsar masifa haɗi da bala'in da suke cinta tana mai cigaba da faɗin"
Da ban kwana ba zaki ganni,nace, da ban kwana ba zaki ganni Nazo Gidan d'ana NABEEL!
Sannan kuma ni HAJIYA Nafisat ban shigo Gidan nan dan in zauna a matsayin gidan surukata ba, tun da kin d'aura Dan-maran zama anan gidan, to ni kuma Sai na tuka miki tuwon kaya. Miyar allurah.. Sannan
Kuma Sai na shimfid'a miki, tabarman kashi. Wanda dolenki ki zauna a sama, ,kuma barikiji... tunda kince ke ba zaki bar NABEEL ya kara aure ba, duk matan duniya nan, NABEEL yace bai-ga kowa ba .Sai .ke. zai Aura.. ga ki nan juya, Wanda ta gaji bakin kishi daga gurin kakanintah, tunda kika hana NABEEL auren Azmerh . Yar kanwar MAHAIFIYAR sa,..
To ke ma Sai kin bar Gidan nan, domin ni HAJIYA Nafisat na koshi. Da bak'in cikinki, abin ya isheni hakanan!
Sabida haka in ya dawo, kice masa Ina nemansa da gaggawa..
Saura kuma ki ki fad'a masa insake dawowa inci mutuncinki, wadda batada wani amfani shashsha kawai mai mugun hali,
Tana Gama ƙarasa maganarta tanufi hanyar fita daga parlourn tare da ficewa daga gidan gabadaya Abinta.
"Na shiga uku
!!! Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un FAREEDAH ta fad'i tana mai fashewa da kuka sannan cikin sheshshekar kuka ta cigaba da cewa "
Sai yaushe ne zan samu sauyin lamari acikin rayuwa ta? , d'a Namijin da nake tattalinsa fiye da komai nawa , haka kuma d'a mijin tilo da nake ji dashi acikin zuciyarta, rayuwarta komai nawa , lallai kam tabbas idan har Mommy tayi nasar raba nida farin ciki na shakka babu mutuwa zanyi Dan tasan nawa yakare bazan iya rayuwa babu shiba,Cikin zubarda hawayen take cigaba da fad'in "I don’t know how to love somebody, but mah feelings for you justified how much I love you, NABEEL Ina MATUƘAR SONKA
Share kwallar dake zuba a cikin idanuwanta tayi haka dai tacigaba da sharara kuka ita dai har NABEEL ya DAWO daga masallacin ya tadda ita ahaka, "NABEEL ne ya shigo cikin parlourn tare da furta "
Asallamu Aleykum!
tsayawa yayi turus yana kallon matarsa, da take Famar zubda hawaye..
Kai tsaye gurinta ya nufa yana mai mik'ar da ita tsaye, suka kurawa juna ido yayinda idanuwanta suke famar zubar da hawaye, fuskarta ya tallafo cikin tafin hannuwansa kafin ya sanya bakinsa saman kumatun yana mai fitoda halshen sa waje cikin nutsuwa ya fara lashe mata hawayen dake zubowa daga cikin idanuwanta , ta rintse ido ta na mai jin tsayawar hawayen ta chak alokaci guda saikace d'aukewar ruwan sama..Jiki a mace ta kwanta a jikinsa ya rungumeta tsam-tsam! a haka suka nufi kujera mak'ale da juna, A sanyaye ya zauna a Saman lumtsumemiyar kujera yana mai zaunar da ita akan saman cinyarsa
Ko yana mai ɗaurata akan saman cinyarsa zance
, duban ta yayi tukkun kafin daga bisani cikin sanyin murya ya bud'e bakinsa
yace " FAREEDAH tah damuwar ki. ciwo ne agare ni, Wanda baya warkewa..
Meye ya faru!
Bayan kuma kinsan zubar hawayen ki, sune Abubuwa mafi kona min zuciya, shin meye ya faru?
"Ita FAREEDAH d'in dubansa tayi kafin cikin sheshekar kuka FAREEDAH tace "NABEEL shekara ta biyar kenan a Gidan ka, ko 'batan wata banTaba yiba, bayan kuma Kai nasan mutum ne Maison d'aukan d'a ko y'a.
Bare kuma yan uwanka, da suke son suga sun samu jika.......
kuka ta sake fashewa ,dashi kafin ta gyara zama asaman cinyarsa sannan ta cigaba da cewar "
NABEEL
INA MATUƘAR SONKA! ba zan iya kwatanta maka irin MATUƘAR KAUNAR da nake maka ba. Kaunar Ka da sonka yana yawo a jijiyoyin jinin jikina,NABE..... "CIKIN SAURI NABEEL
ya katseta ta hanyar fad'in "..
FAREEDAH HAJIYA Momma
ta zo Gidan nan ne???..
"Eh
Inji cewar FAREEDAH sannan ta cigaba da cewar "
Bata Dad'e da fita ba..
"CIKIN ransa NABEEL yace da sassafe nan! wannan wane i'rin masifa ce Haka!!
Kwantar da ita yayi asaman kirjinsa kafin cikin kwantar mata da hankali had'i da rarrashinta NABEEL ya buɗi bakinsa yace
"FAREEDAH rayuwa ta bata da amfani, matuk'ar babu ke atare da ni ,FAREEDAH ba zan iya had'a rayuwar ki da wata y'a mace ba, ko da kuwa zan rinka ganin fuskata a cikin fuskar ta,
FAREEDAH dukan d'a namiji da yace yaji. Ya gani a kan mace, to babu wani iska ko damuwa da zata raba su.
Matukar dai namiji nan saurayi ne. na kwarai. FAREEDAH na d'aukar miki alkawari ,alkawari tamkar buzu da nad'inta , Wanda in kika ga yawarware to ba karamin Al'amari bane.
"Ai kuwa kafin kasani tuni FAREEDAH ta saki murmurshin sannan cikin murmurshi FAREEDAH
Ta buɗi bakin ta
tace " NABEEL Ina Alfahari da soyayya da Kake min daga nan har ranan karshe,..
Shima NABEEL d'in cikin murmurshi ya bud'e bakinsa yace "FAREEDAH ni kuma zan ta miki addua daga yau har ranar karshe, Allah ya bar mu tare
_________Da misalin karfe takwas na dare in the evening at 8:pm,
SU FAREEDAH da NABEEL ne, na hango,acikin hamshakin parlourn su, Zaune FAREEDAH take asaman 2-seater a cikin Parlourn ta ,da ita da NABEEL yayin da NABEEL yake a agefen FAREEDAH ,, daga ganin Alamun hiran suke cikin nishadi had'i da farinciki, haha haha haha FAREEDAH ta fashe da dariya cikin dariya FAREEDAH tace"
Allah ko kalbinerh?
"CIKIN smiling NABEEL yace "Eh zumanerh, "
Cikin fara'a
FAREEDAH tace "to yayi,ni dai Bari in kawo maka abinci..... Cikin sanyi ya katseta ta hanyar fad'in "..
Aa
yi zaman ki, mu cigaba da hiran mu, kinsan ni kullum haka nake so. in saki agaba ina baki dariya
Sannann kuma in ta miki hirar soyayya Ina mai kallon kyakkyawar fuskar ki, so nake nayita ganin dariyarki har sai dariyarki ta Kare
""Haha😹 haha 😹haha FAREEDAH ta fashe da dariya sannan cikin dariya FAREEDAH tace " Kai dai ba Ka rabuwa da zolaya
Suna cikin haka.
,.. sai kawai NABEEL yaji wayar sa Tana ringing,wayar sa ce tayi ringing cikin sauri yayi picking call d'in kana ya manna wayan a kunnesa,sakamakon sunar dayagani yana yawo asaman screen d'in wayarsa, cikin sanyin murya NABEEL yace
"....Assalamu alaikum, barka da warhaka HAJIYA Mommah ina wuni ,yayinda gabansa yake fad'iwa..
"A,bangaren HAJIYA Nafisat kuwa batare da ta amsa masa sallamarsa da gaisuwar saba cikin tsantsar masifa had'i da bala in da suke cinta ta bude bakinta tace" kai NABEEL inason maza maza kabar duk wani abunda kake kazo gidana ina son ganin ka
Yanzu yanzu nan
"To Mommah to shikenan, HAJIYA GAni nan zuwa, batare da yajira cewar taba ya katse wayar sa abinsa
"Wani marayan Kuka NE ya subcewa fareedah
Kallonta yayi kafin yace "
"FAREEDAH!
"Na'am NABEEL! Inji cewar FAREEDAH cikin kuka
"Cikin sanyin murya NABEEL yace "
Me yasa kike kuka??
"Cikin kuka FAREEDAH tace "
NABEEL nasan rabuwar mu ta zo !
"Haba FAREEDAH
Inji cewar NABEEL sannan ya cigaba da cewar