Showing 129001 words to 132000 words out of 154988 words

Chapter 44 - CIKI DA GASKIYA 2 COMPLETE by Billy Abdull .txt

24 Dec 2024

18235

namu da fad'ima tasani, mukagafa dolene musan yanda zamuyi tabar gidan, Idan bahakaba zata 6aro mana aikine, dama ga cikin jikinta yana bani haushi, kullum fargabata karta haifi namij, mun shareta alokacin, har zuwa wasu watanni sannan muka 6arar da cikin jiKinta, muka had'a kai da likita kuma yace dama tadad'e tana zubarwa, sannan Na ajiye mata maganin zubar da ciki ad'aki Abdallah yagani, domin nasan yanda yake da masifar son 'ya'ya dama. Munyi nasara kuwa, Dan alokacin Abdallah yasaki fad'ima, daganan muka koma burin ganin munraba Bilkisu da gidan itama, bayan muncigaba da bibiyar fad'ima muna ma rayuwarta barazana, har muka saka aka saceta dukdan dai tatsorata karta tona mana asiri watarana._
_banta6a goyaka abayanaba, banta6a cin kashinkaba, duk wani wahalar raino da uwa kanyima d'anta banta6a yimakaba, musamman na d'akko mai raino take rainonka, sai Bilkisu itama datakeyi idan ankaika kasha nono, tsakanina dakai nad'an d'aukeka, shima nata maka mugunta kenan kana kuka, amma babu wanda yafarga da hakan, bak'aramin k'ok'ari nadinga yiba wajen danne zuciyata ina nunamaka soyayya agaban mutane, dan wlhy nagama tsanarka tuni, natsaneka saboda kaid'in d'an mak'iyyatane, natsaneka saboda kowa yana nunamaka soyayya agidannan, Ammah, bilkisu, Abdallah, hakama su zuwairah, suk motsinsu nakanka, bada son ran innah jummai nake rainonkaba, dan bata ta6a d'aukarkaba tunda take, dukda namata bayanin dalilina na d'aukarka hakan baisa taji zata sokaba, yakamatama kakula da yanda nake nunama 'y'a'yana mata soyya fiyeda kai._
_Muncigaba da farautar cikin daduk Bilkisu tasamu amma ALLAH bai bamu nasaraba, babu dad'ewama tahaifi Rufa'ee (khaleefa), takuma yin Sultan, tayi mujahedeen, hakan yakuma haddasa wutar k'iyayyarta araina, gashi ALLAH yahananin damar d'aukar mataki, kuma nid'in haihuwar tama tsayamin cak, tunda muka haihu tareda Bilkisu tawa ta mutu bansake koda 6atan wataba har Bilkisu tayi haihuwa 5, sai bayan haihuwar Ramadan nasamu cikin Mugeedah ma, sannan kumane khaltum taja ra'ayina shiga k'ungiyarnan ta safarar yara mata, tacemin nabar wahalar banza akan jiran dukiyar daba tawaba, waddama alamomi sun nuna Bilkisu Ce zata gaje komai, inzo nanemi nakaina, harma sainafi Abdallah shahara, kamar yanda innah jummai take buri, ni inhar zan samu kud'i babu ruwana dawani tantance abinda zanyi, hakan yasaka Na sanarma innah komai, atake tabani goyon baya, dakuma jinjinamin, tanamai farincikin lokacinne zatafi Ammah komai, zata nunama Ammah itamafa karanta yakai tsaiko, ayanzu tafita komai da komai, lokaci yayi dazataga Ammah 'Yar uwarta ak'asanta, itama tadaina hawa samanta._
_wannan farincikinne danagani atattareda mahaifiyata ya k'arfafamin guywar Shiga wannan k'ungiya, Alhmdllh nasamu abinda kuma nake buk'atar samu, hakama mahaifiyata, dannafi Abdallah komai, dandai kawai bana nunawane, naginama mahaifiyata k'aton gida, nazubamata dukkan abinda take buk'ata, daga alokacin kuma takoma saka sutturar da Ammah bata saka koda kwatankwacinta, sannan bana jira Abdallah yamin komai, dan nafisa komai, nazama hamshak'iyar mace tamkar yanda mahaifiyata tayi buri, nashahara sosai, saidai girmankane yaso durk'usar dani, domin nakula kafara shigamin hanci tuni, wannan ne yasakani d'aura d'ammarar kasheka kafin kai kaga bayana, saidai kash, Ashe har zuwa yanzu fad'ima Na bibiyar rayuwata batareda nasaniba, duk zatona ta manta da komai, kosanda tace zata dawo gidan ba kishine yasakani binta kanoba, fargabata karta dawo da abinda yawucene kawai, banta6a jin kishin saudah ba, Dan lokacin data shigo gidan nasamu hanyoyin samun kud'i, Ashe munafukace ita, shiru-shirunta Na munafuncine itada Bintu, ALLAH ya Isa tsakanina daku, ziciyata bata ta6a kawo dabaibayin da fad'ima taminba kenan, saboda banta6a tunanin wani mahaluki agidan zaisan sirrin sana'ataba, tunda komai cikin taka tsantsan nakeyinsa, hankalina bai fara tashiba saida shegiyar yarinyarcan ta bayyana amatsayin d'iyar Fad'ima, harma tsohuwarcan tahad'a aurenku, saikuma fitar dare Dana kama mufeedah nayi, rushewar komaina shine cikin mufeedah😭, tak'are maganar da rushewa da kuka....._


Kowa kakalla awajen kallon mamaki sukema hajia babba da inna jummai, bakin Ammah bud'e tak'arasa gaban innah jummai.
"Jummai yanzunan har lalacewar zuminci tawannan zamanin takai kiringa bak'inciki dani?, nid'infa yayarkice ciki d'aya, mukad'ai iyayenmu suka Haifa, yanzunan jummai sabodani kika rusa rayuwar d'iyarki tall guda d'aya?, saboda son ki fini kika dinga walagigi da tarbiyyarta haka? Haba jummai, miyasa baki fad'ama iyayenmu kinason Malam Rufa'ee ba alokacin? wlhy dakin fad'a saina barmiki shi, Haba jummai, miye duniyama bare abinda ke cikinta, yau INA iyayenmu? dukfa sun mutu, INA Malam Rufa'een dakikayi danshi? Yamutu tuni ya barni, mumafa dolene mumutu, inhar d'an uwanka zaita wad'annan k'ulle-k'ullen dankawai yafika, to tayaya duniya zata zauna lafiya? tayaya zuminci zaiyi k'arko aduniya? Shiyyasa babu Abu mafi lalacewa awannan duniyar kamar zuminci, hassada da bak'inciki tamaidamu mak'iyan juna, kullum burinmu muzama saman 'yan uwanmu, bamason kowa yafimu, bamason ace wane shine wane, yakamata kigane wani sirri awanan labarin jummai, *Hassada ga mai rabo takice*, kullum kina bak'incikin ALLAH ya d'aukakani samanki, burinki kifini, amma kuma ALLAH nata d'agani sama, koda kinsamu abin, sainikuma nasamu mafiyinsa tawata hanyar. kin tsaidamin haihuwa, dukda nayarda hakan tsarin ALLAH ne, amma sai ALLAH yabani jikoki, kusan talatin, ga 'ya'yan jikoki kuma, burinki ki mallake dukiyar zuri'ata domin kifini, sai ALLAH yabama d'iyarki dukiyar dazata zame muku masifa keda ita, kinraba baiwar ALLAH da d'anta, sai ALLAH ya azurtata da haihuwar ninkin baninkin d'insa, sannan yasaka soyayyar juna tsakaninsu cikin hikimarsa, kin d'aukesa Dan gur6ata rayuwarsa sai ALLAH ya shiryasa yazama shine dodon dazai dinga tsorata rayuwarki, k'arshema shine zai ruguzata gaba d'aya.
Kin fidda fad'ima agidan mijinta sai ALLAH yabata ikon zuwa wani gida tahaifi wadda zatazama jagorar tarwatsa dukkan farincikin 'yarki da sarautar datake tak'ama da ita, sannan yahad'a Auren 'ya'yayen mak'iyanki domin yanuna miki ked'in bakomai baceba, wannan kad'an kenan daga ikonsa, cikin mufeedah ALLAH ya d'and'ana miki irin bak'incikin da iyaye kanjine lokacinda aka salwantar da mutuncin 'ya'yansu, duk wannan abubuwan kinsaka d'iyarki yinsu domin ki wargaza rayuwata, sai ALLAH ya nuna miki iyakarki, yaruguza dukkan taki rayuwar, gakunan acikin nadama dagake har ita, kai jama'a ALLAH yarabamu da hassada.


Kowa da amin ya amsa, su Anty zuwairah suka fice suna kuka, dukda k'aunar dasukema mahaifiyarsu bazasu iya kallon su Ammah ba, ashema momy basu taso amatsayin 'ya'yantaba, maza taso ALLAH yabata su.
Kowa da kallo yabisu, momy kuma tafashe da kuka tana fad'in innah kin cuceni, duk kece sanadin rugujewar rayuwata, dabaki d'orani akan wannan karatunba daban tashi akan dokin zuciyaba, wlhy bazan yafe mikiba keda khaltum, ALLAH ya Isa tsakanina daku, ALLAH yajik'an mahaifina, kullum nunamin yake karnabi hud'ubarki, Dan bazata kaini hanyar 6illewaba, watarana saina tsinci kaina a Dana Sani, gashi kuwa lokacin yazo, Takai 'ya'yanama NBASA buk'atar ganina, takuma fashewa da matsanancin kuka tana tari.
Khaleel Kansa aduk'e, idonsa yayi jajur, hakama jijiyoyin Kansa sunyi rud'u-rud'u, yama rasa yanda zai fassara wannan *bashin gaba* haka, kawai gani akayi yamik'e, ya tafa hannayensa saiga Adams yashigo, Kansa aduk'e yace, "Adams kowa yafita, Ammah da baffah da Anty Mamie, mama, ummi amarya, Aysha sausu Mujahedeen kad'ai nake buk'ata".


"OK sir".


Adams yafitada su Tasleem, su hasnah, da 'yan uku, matansu ya sultan.
Ahankali khaleel yatako har gaban Ammah, kowa kallonsa yakeyi da tunanin abinda zaiyi, gashi yayi k'asa da Kansa yak'i kallon kowa awajen.
Hannun Ammah Yakama yaje har gaban hajia babba da ita, sannan yakoma bayan Ammah yatsaya, yakamo hannayenta yad'ora saman bindigar hannunsa, kaitsaye hajia babba ya saita, nanfa kowa ya rikice, baffah namasa magana amma bai sauraresaba, ita kanta Ammah jikinta rawa akeyi, azatonta khaleel zaisata takashe hajia babba ne, innah jummai kuwa kuka da kururuwar ihu tafasa akan ataimaketa zasu kashe mata d'iya.
Dirimmm!! Sukaji fitar harbi da ihun hajia babba lokaci d'aya, khaleel yasaka Ammah rama harbinta a k'afar hajia babba kamar yanda itama ta harbi Ammah ranar.πŸ˜‚πŸ‘πŸ»


Hajia babba Na kwallah k'ara khaleel yamatsa daga kusada Ammah, yabatta da bindiga a hannu, yajuya yafita yana hawaye, duk binsa da kallon tausayawa sukayi, inkacire hajia babba dake ihun azabar shigar bullet cikin k'ashin k'afarta, saikuma innah jummai dataje tarik'eta tana salati.
Tarine ya sark'e hajia babba, tafara yinsa babuji babu gani, saiga jini nafitowa, amatuk'ar tsorace ta kwallah k'ara tana kallon hannunta cikin zare idanu waje.
Adams ya kar6i bindigar hannun Ammah, sannan yayi waya akazo aka d'auki hajia babba data fara galabaita, ga aman jini, ga jini nazuba ta k'afarta, sai aminiyarta khaltum daduk ta tsure da tsoron Khaleel, tunda har ya iya aikata haka ga hajia babba air kowama saiya shafama Kansa lafiya, tunda yakasa sauraren tsawatarwa da mahaifinsa kemasa akan karyabharbi hajia babba.
Dole suma suka fito, duk suka Shiga motoci bisa umarnin Adams.
Khaleel kam office d'insa yashige ya kulle kansa yana kuka tamkar mace.


Haka aka maidasu gida jikin kowa a sanyaye, babu mai iya koda tari acikin motocin.............✍🏻








_wayyo, ALLAH nagaji, nak'agara nagama, kuhuta nima Na huta yasin😒._










*_ALLAH ka gafarma mahaifanmu baki d'aya._*😭


*_I miss you so much baba, nakasa hak'uri da rashinka wlhy, ALLAH ya kai rahama makwancinka._*
πŸ€šπŸ»βœ‹πŸ»πŸ˜­πŸ˜­πŸ˜­πŸ˜­πŸ˜­




[10/26, 4:28 PM] Aysha Galadima: *_TypingπŸ“²_*




🀰🏻
*_CIKI DA GASKIYA!!......._*
_{πŸ”ͺwuk'a bata hudashiπŸ—‘}_


*_Bilyn Abdul ceπŸ€™πŸ»_*




*_HASKE WRITERS ASSO......_*
_(Home of experts & perfect writer's)_




*_part 2_*
_(littafi na biyuπŸ“˜)_


*_k'yak'yk'yawar addu'a da fatan alkairi su iso agareku, inasonku da k'aunarku wlhy._*


Ashcute the group admin, Fauziya, Mrs abdul'azeez, Maman salma, Maman Adam, Binta Suleiman, Yusuf amina, Amina ali adam, MUMMIETIE, Maimuna kulloma, Auta khan, Fmujeedat9, Aisha yakubu, Maryam khamis, Aisha,
Ummu basma, Aisha Mustapha maina, Momyn twins, maman haneef, Zahra maigari, Mmn Ahmad, Hauwa saleh, Hajara Iliasu musa, Jamila D Iliasu, mom ashraft, ummin assiddiq, safiya tanimu, Sauda, Aisha gambo, Hauwa chindo, Ummu mufeeda, Zainab (Nafzee), Rahmat, MMN musty, Yar mamanta, Sanzee, bbyn dady, Ummi Ahmad Iliasu, Hawwa zakari, mmn khady, Eman, ummu aysha, fadila, fauxiyya Hussain. maryam hassan, Maman salma, Zainab Yusuf Abdullahi aji, Adama Abubakar sumaye, Aysher wali, Maman muniba, Mrs Useef, Deeja mashi, Maman mus,ab, Meeral mash, Princess Ayeeesha, Maryam lawal, Hadiza Abbas, Yar AmmiπŸ’•.


_alkairin ALLAH yakai garekuπŸ˜πŸ˜πŸ˜πŸ˜πŸ˜πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹β€πŸ’ƒπŸ»πŸ‘πŸ»._




4⃣7⃣


Yau bayan Anty Zuwairah tagama shirinta tsaf tashiga dukkan d'akunan matan gidan, tamusu sallam dasake neman gafararsu, musammam akan abinda taitamusu abaya narashin girmamawa, hakama tanemi gafarar gwaggo bintu akan k'untata rayuwarta dasukayi sanda ta zauna a Lagos, gwaggo bintu tace babu komai yawuce aii, kuma tayafe mata.
Hakama d'akunan matansu Ramadan Duk saida tashiga tamusu sallama, sannan tashiga mota hafeez da Muhseen sukatafi kaita airport.
Anty shukurah ma tanufi gidanta, dansuma sundawo nan Nigeria baki d'aya.




_____________________
Dayake yau takasance asabar kowa yana gida babu aiki.
Aysha dataji d'an k'arfi-k'arfin jikinta tatashi tunda safe tahau gyaran gidan, khaleel kam Na d'akinsa kwance yana shak'ar barcinsa.
Bayan tagama tsaftace ko'ina dukda tagaji sosai haka tadaure tashiga kichin, duk tanayine domin faranta ran ya khaleel, aganinta itama yakamata yanzu ta maida hankalinta sosai wajen kulawa da mijinta kamar kowacce mace, burinta yacika akan mafi yawan tanadinta, to shima yakama ta fuskanceshi, Abu mai sauk'i ta shirya amma masu dad'i, bakuma tayi masu yawaba yanda zai zama almabazzaranci da abinci, dai-dai cikinsu tayi, sai kad'an data k'ara koda wani yashigo, dukda haryanzu takanyi amai idan abinci baimataba.
Bayan tagama wanke kayan data 6ata tafara sharan kicin d'in, jiri takeji kad'an-kad'an amma haka taita dafe bango tana morphing, wani yuuuu dataji acikin kanta yasaka saurin zama akaujerar plastic dake kichind'in, tadafe kanta tana sauke numfashi.
Ya khaleel datun d'azun ke tsaye yana kallonta ya jinjina kansa yana guntun murmushi, aransa yace agaida jaruma.
Takowa yayi ahankali har inda take, ya durk'usa agabanta tareda d'ora hannayensa bisa guywoyinta, d'ago ido tayi ahankali tasauk'esu akansa. Ya d'age gira d'aya yana kallonta shima, da hannu yamata alamar mike faruwa?.
Kanta ta girgiza masa tana murmushi.
Yace.
"banason k'aryafa".
Murmushi tayi, tace, " jirine kawai, kuma nadainaji".
''Yanzu nan waya sakaki duk wannan aikin? ana lalla6a d'an cikin kekuma kina gingimo masa wahala".
"Sadauki kenan, idanfa zan biye tawani lalla6awa babu abinda zanma kaina, insha ALLAH ma sonake wannan week d'in dazamu shiga nakoma aikina".
" yayi k'yau babie". 'Ya khaleel yafad'a yana mik'ewa, morper d'in data ajiye yad'auka yak'arasa morphing d'in kicind'in, itakam sai binsa da kallo takeyi da mamakinsa.
Bayan ya kammala yace, " oya tashi muje muyi wanka, yau zuminci zamuje".
"Zumunci kuma sadauki? Ina da ina zamuje?".
juyowa yayi yana kallonta, ya kashe mata ido d'aya, "to ganin babe zamuje, matar Joseph ta haihu baby boy".
" woow! Sadauki da gaske Dan ALLAH".
"I'm telling you my Angel".
Cikin farin ciki Aysha ta rungumesa, kaikace itace ta haihun, sai gero addu'ar fatan alakairi takeyi akan jaririn.
Cikin amsawa da ameen ya d'auketa cak, bai direta ako inaba sai toilet.


Nidai najawo tsumman k'afata nadawo falo.
πŸšΆπŸ»β€β™€




Ganin sunk'i fitowa nad'an kwanta jiransu, 'Yar wayata nad'auka nabud'e data, banzame ko ina sai group d'in ciki da gaskiya fans daketa suburbud'a firarsu ya khaleel, can nahango 'yan BBC hausama, suma nad'an lek'a muka gaisa, pherty novels ma hirar suke, dansuma akwai k'ok'arin comments, nashagala sosai a charts najiyo dariya khaleel cikeda nutsuwa.
Tashi nayi zaune nad'auk'i d'an takardana da alk'alami nacigaba daga Inda Na tsayaπŸ˜‰πŸ‘πŸ»πŸ˜‚.




Cikin shagwa6a Aysha kefad'in "nidai kakema dariya ko? Babu komai zan ramane aii, kuma saina had'aka da Ammah jar wuya".
Dariya yakuma tuntsirewa dashi, yamatso kusada Aysha, ''kinga sorry my Angel d'ina, aii had'ani da Ammah tamkar taro March ne."
''Kadai gaya musu saina fad'a d'in".
"OK OK naji, fad'i mikikeso amatsayin cin hanci?".
" la ila sadauki! Kaima kana karya doka?".
Cikin d'age gira yace, ''aii kezan bama cin hancin bawaniba, yanzu dai zan saya miki ice-cream, saikuma mi bayanshi".
"Dan ALLAH da gaske?".
" eh mana, amma saimun dawo daga ganin baby".
"Shikenan muje to muyi break fast".
Break fast suka zaunayi, adaddafe dai aka gama, Dan anyi nisa dacin abincin zuciyar Aysha tafara tashi.
Cikeda kulawa khaleel yake kallonta, yace, "lafiya kuwa?".
'Dan yatsine fuska tayi, da hannu tamasa nun amai.
Tausayi tabashi, yasan tanason abincin wani lokacin, amma data faraci sai labarin ya canja. jikinsa ya zawota, ahankali yayta shafa bayanta, lokaci-lokaci yakan mata sannu.
Kanta kawai take d'aga masa, talafe ajikinsa tana shak'ar k'amshin turarensa.
Zuwa wani lokaci yad'agota. Idonsa akan fuskarta yace, " ya daina?".
"Ya daina, amma nahak'ura da abincinnan kawai, k'arasa mutafi".
Jinjina mata kansa yayi, k'asan ransa kuwa yana jinjina k'ok'ari da jarumta irinta iyaye mata, amma ahaka har ake samun azzalumai irinsu hajia babba dake iya raba d'a da mahaifiya, wani bak'inciki ya tokare mak'oshinsa, daurewa yayi ya danne, Dan bayason hankalin Aysha yatashi.
Amma dukda haka taga fuskarshi ta canja, badai tace dashi komaiba.
Shima tashi yayi, Dan duk abincin yafitarmasa arai.


Ajere suke tafiya gwanin sha'awa, dolene kagansu su burgeka, domin sunyi bala'in dacewa da juna, lamarinfa zaaaaam fansπŸ˜‰πŸ‘πŸ».


Cikin gida suka shiga, afalo suka iske mama da ummi amarya, zaune suna hira, saisu Adeel daketa wasa agefe, rissinawa sukai suka gaidasu, cikin tsokana ummi amarya tace, " amarya da ango sai ina kuma da gayu haka?."
Aysha tasaka hannu tarufe fuskarta tana 'Yar dariya, khaleel kam k'asa yay da kansa yana murmushi, akunyace yace.
"Zamuje ganin babyn matar Joseph ne".
" tofa, yanzunan matar Joseph d'in ta haihu amma baka fad'aba babanmu?".
"Amin afuwa ummi, dama nazo sanar mukune yanzun, babu dad'ewa muma yakira yafad'a".
" ayya to ALLAH ya raya, mi'aka samu?".
"Baby boy".
" masha ALLAH kuma kunfara zama iyaye, ALLAH ya raya", 'cewar mama dabatace komaiba tun d'azun'.
Khaleel ya amsa da ameen.
Saiga Anty Mamie tafito daga 6angarensu samarin gidan itama, hannunta rik'eda Khaleefa.
Cikin ladabi duk suka gaisheta, ta amsa idonta akan Aysha.
"d'iyata ya jikin? Incedai yau babu aman?".
Akunyace Aysha ta jinjina kanta alamar eh.
" to Alhmdllh, ALLAH ya d'orar da lafiya".
Ummi amarya ta amsa da ameen, khaleel ma a kan la66ansa ya amsa, sannan suka mik'e, sallama suka musu suka fice.

25, February 2025
Mufeedarh

I love it πŸ₯°

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login