Showing 6001 words to 8023 words out of 8023 words

Chapter 3 - HAQQI COMPLETE BOOK BY Princess Aysha Muhammad (Humaira) .txt

because i have now started reaping all bad things that i have been sowed since" yana kaiwa nan a zancen sa ya duk'ar da kansa kasa yana wani irin kuka mai karya zuciya yana maimaita astagfirullah! Wa'atubu ilaihi Astagfirullah! wa'atubu ilaihi!!...




Kai jama'a Allah yasa mu dace, matasa dan Allah mu kiyaye shaye-shaye bashi da wani anfani sai ma cutar da lafiyan d'an adam da yake yi. Likitoci sun bayyana cewa shaye-shayen cigarrete, wiwi ko shi-sha yana ru6ar da huhun d'an adam, yana ta6a lafiyar kwakwalwa sai kaga mutum shi kad'ai yana ta surutai, yana jawo cutar daji wato cancer, uwa uba kuma yana zubarwa da mutum mutuncin sa a idanun al ummah. Su kansu masu company'n me suka ce? Cewa su kayi (the federal of ministry of health warns that smokers are liable to die young) abunda suka rubuta a jikin kwalin kenan, abu mai kyau ba sai an fad'a maka cewa wannan abun mai kyau bane kai kanka ka sani, ai ido ba'a nuna masa bacci. Sanadin shaye-shayen nan kwanaki a damaturu na samu labarin cewa wani matashi da bai wuce 22 years ba yaje sha kwaya ya dawo gida ya hallaka mahaifan sa duka biyu har hoton sa na gani, dan Allah me anfanin shaye-shaye ya y'an uwana matasa? bakwa bukatan karin haske ku kanku kun karanta labarin kunji me late muhammed abdullahi ya aikata, kar kuyi zaton ko fictitious story ne wallahi it is true. Bani da ta cewa sai dai nace Allah ya jikan sa da rahama yasa tuban sa kar6a66iya ce mu kuma Allah ya kyautata karshen mu ameen thummah ameen.




😊mr. melody


🍉
[5/17, 15:33] Umar Dalha: ☠HAQQI☠















🌙April-2017


.








✍🏾mr. melody💥












Page9⃣&1⃣0⃣










*```this page is dedicated to you my besty ana mugun tare wallahi nawan```*








Bayan yayi ta istigfari daga bisani yayi murmushin yak'e sannan yace “a rana mai kamar ta yau monday itace babban ranar nadama a gare ni, kuma babban ranar farin ciki a gare ni domin ta sanadiyar wannan ranar na nema gafarar *MAHAHAIFIYA TA* kuma ta yafe min masha Allah, my only mum may Allah (s.w.a) reward you jannatul fiddaus ameen thummah ameen i really so much love my momma you are one in a billions".


“I thought ranar da muke zaune a chamber'n kofar gidan mu tare daku muke zaune ko?" zallan Kai kawai muka gyad'a mai alamun a'a ”no bad yau za kuji komai" ya fad'i hakan ne yayin daya d'an kora ruwan faro saboda an hana shi shan ruwan randa kona fan-fo sai swam ko faro.


WAto ranar misalin karfe 8 bayan sallah'r i'sha, kwance muke a chamber muna shan iska kasantuwar zafi ake sosai, wani almjiri ne wanda da kyar ya kai 13 years ya shige cikin gidan mu yayi ta bara yak'i fita ni kuwa abun ya bani haushi sai na harzuka na shiga cikin gidan na fito dashi na wanke shi da gigitacciyar mari take ya fad'i kasa sumamme y'an uwan nasa da suka ga haka sai suka kira manyan su suka tafi dashi makarantar su.


Wannan yaron dana mara ba-barbare ne (kanuri) Haka y'an makarantar nasu ma duk kanurai ne harda malaman. Haka dai na kwana lafiya a wannan ranar kamar maye yaci shirwa. Safiya nayi guraren karfe goma zuwa sha-d'aya da y'an kai, zaune muke a chamber muna break fast da fara da mai (garau-garau) wanda mamar su shukura take yi na sayar wa.


Garadan makarantar su almajirin dana mara daren jiyan ne nayi tozali dasu sunyo gayya kwannen su yana rik'e da allon sa sun nufo kan mu, ganin hakan yasa na tuno da abunda na aikata jiya. Gida na shiga na biya ta kofar baya na gan-gara kasan kwari na gudu.


Da zuwan su chamber'n suka tambayi abokan yaron dana mara d'in cewa “a cikin wad'annan wanne ne ya mari baana?" Yaran duk suka kid'ime suka kasa tunano fuskata sai suka nuna modu, modu na ganin an nufo kan sa da saran allo yasa ihu yana cewa “wallahi tallahi bani bane wanda ya mare sa ya gan-gara k'asan kwari ya gudu".


Wani babba daga cikin su yace “ya gudu?, toh wallahi baza mu kyale shi ba sai mun d'auki fansar d'an uwan mu" jama'ar unguwa su kayi chaa! A gun kowa naso yaji meya faru. Many'an unguwa suka karaso jama'a suka bub-bud'a musu suka shigo inda garadan nan suke.


“Meke faruwa ne aaramma?" Baban su ishaq ne ya tambayi jagoran nasu, yana huci yace “alan-guro wani yaro a gidan nan ya mari d'an uwan mu daren jiya dan yazo yayi bara, yanzu a haka yaron yana can a kwance ba lafiya toh wallahi tunda ya gudu sai mun d'auki fansa" yana kai aya a zancen sa yace “kai kuzo mu tafi" baban su ishaq da sauran jama'a su kayi ta basu haquri amma ina sun kafe a kan magana d'aya sai sun d'auki fansa.


Nine ban dawo gida ba sai bayan sallah'r magharib. A nan ne aka labarta min komai, a cikin daren baban mu ya nemo min kud'in motan zuwa maiduguri akan naje can nayi zama na a gun k'anin sa after magana ya lafa sai na dawo gida saboda idan na tsaya naki tafiya zasu iya dawowa ako da yaushe kuma babu shakka zasu d'au fansar su.


Dama banyi kwana biyu da yin d'aurayan kayaki na ba, wad'anda suke da datti baza su wuce set biyu bane a ciki, da asuba na kin-kimi jaka ta na wuce tashar motoci terminors.


A maiduguri nayi spending 2 months bayan komai ya lafa harma na manta da rikicin daya koro ni daga garin *biu* jiki na ya fara kumburi da naga cewa abun baya yin sauk'i sai na tattara na dawo gida gudun kada jikin nawa yayi worst bana gaban mahaifana.


Abu kamar wasa Duk asibitin da muka je sai ace mana wannan bana asibiti bane, na gargajiya ma idan muka je sai ace mana muje asibiti har muka gaji da yawuce-yawuce, daga nan dai aka yiwa baban mu kwatancen gidan wani malami yana can a unguwar nasarawa muka je, baban mu yayi masa bayanin dukkanin abunda ya wakana malamin ya jin-jina kai ya kalle ni sannan yace “kana d'auke-d'auke ne?.


“A'a bana d'auke-d'auke"
malamin yayi shiru yana nazarin wani abu finally yace “kayi tunani dai, baka ta6a d'aukan kayan wani ba?" Same answer na basa, ya sauk'e sassanyar ajiyar zuciya yace “ba shakka wannan kumburin naka yana da nasaba da wani, amma babu wani abu daya shiga tsakanin ka da wani?" “Allah gafarta malam a gaskiya kusan kullum sai munyi rigima da jama'ar unguwar mu kafin lalurar nan ta same ni".


“Toh ya zama dole kaje ka bisu d'aya bayan d'aya ka nemi tuba idan Allah yasa wanda yayi ma wannan d'anyen aikin yaji tausayin ka zai war-ware insha Allahu, bayan kwana biyu in kuka babu wani canji sai ku dawo" godiya sosai muka yi masa sannan muka fice. Haka kuwa aka yi duk sai dana bisu d'aya bayan d'aya na nemi gafarar su, alhamdulillahi duk wanda na tunkare shi da maganar yafiya cewa yake ya yafe min duniya da lakhira.


Bayan kwana biyu babu alamar canji sai muka koma gidan malamin. shiru yayi yana nazari, sosai ya 6ata lokaci a haka daga bisani yayi ajiyar zuciya yace “lallai al-amarin nan babba ne".


“amma kayi tunani da kyau dai" nayi shiru ni gaba d'aya nama manta da wancan almajirin, ina tunowa da shi naji gabana ya fad'i ras! Take hawaye ya gan-garo min baki na yana rawa nace “ba shakka akwai bare-baren almajirin dana mara kwanakin baya har sai da ya suma, kuma y'an uwan sa sunyi ikirarin cewa sai sun d'auki fansa".


“Ba-barbare? Tab! Babbar magana" malamin ya fad'a a d'an razane hakan yasa jiki na yayi sanyi matuka “a gaskiya bani da kokwanto suna da alaka da wannan ciwo naka, kuma in kana son lafiya ya zama dole kaje ka nemi yafiyar su dan wallahi kanuran nan suna iya yiwa mutum abunda yafi naka ma, amma kayi tattaki izuwa makarantan nasu ka nemi gafarar su shine kawai mafita a gare ka" godiya sosai mu kayi masa mahaifi na yayi masa d'an dunkuli sannan muka tafi.


Kamar yadda malamin nan ya shawarce ni da naje can makarantar nasu neman tuba, haka kuwa nayi amma da naje tsangayar da mamaki na, naga babu kowa a makarantar alamun sun tashi kenan, zubewa nayi kasa on my knees ina kukan fitan rai dan kuwa yanzu na dad'a tabbatarwa da kaina cewa ciwo na yana da alaka da wad'annan mutanen ne. A garin ba inda bamu neme su ba amma sam koda d'uriyar su bamu ji ba.


Gaba d'aya tausayin sa ya shige mu sai tsiyayar da kwalla kawai muke dan wallahi ban ta6a ji ko ganin haka ya faru da wani ba koda kuwa a film ne ballantana a history. “Allah yasa kaffara ne ya kuma yaye ma wannan bala'i shine kawai addu'ar, yanzu dai maghariba ya karato kuma ya kamata mu kyale ka hakan nan kaima ka huta" aliyu yayi maganar yayin da yasa hanky yana wiping off na hawayen sa.


“Ameen thummah ameen, nagode! Nagode!! Kwarai da gaske da irin kulawar da kuke nunawa a gare ni, Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da “ameen" muka amsa masa sannan muka fice bayan munyi sallama da mahaifiyar sa da sauran mutan gidan. *(Allahu akbar! Ashe dai sallamar mu ta karshe kenan Allah sarki rayuwa, Allah kasa mu cika da imani ameen)*.


The following day muna da exam na mathsmatics from 9:30㏂ sai 3:00㏘ muka fito daga hall so exhausted ga kuma wani irin fad'uwan gaban da nake ji tun shigan mu cikin hall d'in har muka fito bai daina ba kuma ban san dalili ba, a haka dai muka tsaya da sauran friends namu muka d'an has-haska pictures, a hanya ma muka idar da sallah'n la'asar sannan muka wuce gida. Muna zaune akan d'an benching dake kofar gidan mu nida amini na aliyu sai muka hango keke napep ya shigo layin zuciya ta, ta buga da karfi mai mashin d'in yana wucewa a gaban mu na saki salati saboda mahaifiyar muh'd na hango tana rik'e da tea flask a hannun ta da tabarma.


Not long enough muka jiyo karan jiniyar amblance yana shigowa ashe tun tafiyar mu makaranta aka d'ebi muh'd sakamakon jikin nasa ya tsananta fiye da kima. Salati kawai muka rinka yi har aka wuce da gawar sa.


Muka d'ugunzuma izuwa makabarta tare da y'an unguwa, wallahi bakwa bina bashin rantsuwa in dai iri na za'a binne a cikin kabarin wallahi sai dai mutum biyu. Bayan an kawo mamacin ramin yayi masa kad'an ta saman kafad'ar sa sai da aka yi ciko da duwatsu sannan aka jera itatuwa followed by gany'e da kwa6a66iyar kasa da busasshiya sai bayan sallah'r i'sha muka baro makabartan. Allah yasa aljannah ce makomar ka muhammad ameen thummah ameen.

Allah yasa mu anfana da wad'annan darussa ameen. Allah muna rok'on ka da kasa mu fi karfin zuk'atan mu, mu kuma cika da kalimatil *la'ilaha il-lal-laa muhammadun rasulullahi sallallahu alaihi wasalam* ameen




```dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah shi kad'an sa malikil quddus, wanda ya ciyar damu, ya shayar damu, ya tufatar damu, ya isar mana. Na rubuta wannan littafi ne dan isar da sako kuma alhamdulillahi na isar, Allah yasa masu irin halayyar sa su gyara dama wad'anda suke yunk'urin bin wannan hanyar ameen. Ya Allah ina neman afuwar ka gare ni bisa kuskure ko tun-tu6en harshe da nayi a bisa rashin sani a dukkanin lamura na, ka bani ladan abunda na fad'a dai-dai ka kuma karamin kaifin basira na rubuta abunda d'umbin jama'a zasu anfana da shi ameen```




мυsα м sαεεd
(mr. melody)




*```WABIHAMDULLAH```*




Complied by Princess Aysha Muhammad (Humaira)

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login