Showing 3001 words to 3810 words out of 3810 words
Chapter 2 - JARABAWAR DA AKAIWA SARKIN BARAYI NOMAU, littafin Magana Jari Ce .pdf
 isa da kai. In ka 
lura ka ga annuri ya sake, ba kamar na yadda muka baro duniya ba.”  Ya yi ta jansa  har gidan
Sarki. Ya yi gaisuwa. Liman na ta alla-alla a bude shi ya ga abin da zai gani. Sarkin Barayi ya ce 
wa Sarki, “Ga wata ’yar  gaisuwa  irin tamu na kawo maka. Sai ka buda da kanka  ka  gani.” 
 
Sarki ya tashi ya buda waga, sai ga Liman ciki ido wuri wuri, da tasbaha a hannu  yana  salati  
yadda  Sarkin 6arayi  ya  ce  ya  yi.  Ko da Sarki ya gan shi haka bai san sa’ad da ya 6arke da 
dariya ba. Mutane suka yi kamar  za  su  suqe  don  dariya.  Sarki  ya  kama Sarkin Barayi, ya 
cire hular da ke kansa  da  rawaninsa  ya  nada masa, ya ce, “ Na tabbatad  da  sarautarka  ta  
6arayi.  Batun  aure kuma  sai  mun  yi  shawara  tsakaninka  da  ’ya’yayenka.”   Don  kunya 
Limamin nan ya  kasa  fitowa  sai  da  aka  kama  shi  aka  kai shi gidansa. 
 
Da aka watse Sarki ya dubı Waziri, ya ce, “To, Waziri, baki fa shi kan yanka wuya. Yaya ke 
nan?” 
 
Waziri ya ce, “Ba yadda za a yi sai mu san yadda za mu yi mu rarrashi sauran su dangana, mu 
kuwa mu ba Kosau. Don wanda ya gina wannan gida cikin dare guda,  ba mai jayayya da shi.” 
 
Sarki ya ce, “Gaskiyarka, sai  mu  aika  Sarkin  Noma  ya zo da su, su duka.” Da aka zo da su 
Sarki ya shiga rarrashin Jimrau da Nomau su yarda kosau ya auri ’yar tasa. Jimrau ya ce ya 
yarda. Nomau ya ce shi faufau ba ya yardam masa, sai dai in za a hana shi da karfi a hana shi, 
ya san Sarki ya bar batun adalci.  
Da Sarki ya ji haka sai ya dubi Waziri. Waziri ya fusata da maganan nan ta Nomau, ya dube shi, 
ya ce, “Mece ce sana’arka?” 
 
Ya ce, “Sata.” 
 
Waziri ya ce, “To, kai ko a ranka ka ga ya yiwu a ce ’yar Sarki ta rasa wanda za ta aura sai 
6arawo? In dai mu muka  haifi  ’yarmu, to, mun ba kosau.” Duk  fada ta watse.  Daga  nan aka  
tafi aka yi ta shagalin biki. 
 
Da gari ya waye Sarakuna suka taru za a daura aure, sai Sarki  ya ce wa Sarkin Gida ya je 
taska ya dauko masa kayansa na ado, da lambobinsa na girma. Sarkin Gida ya ruga. Jim  ya 
dawo  a  guje,  duk  ya  rude,  jiki  na  rawa,  ya  fadi  gaban  Sarki,  ya  ce, “Allah ya ba ka 
nasara, ai duk taskokin nan na tutafi  ba sauran  ko kyalle yau, sai wannan tsohon bargo da a 
ke daure alkyabbu.” 
 
Mutane duk suka yi zugudun suna jin abin mamaki, Sarki zai bude baki ya yi magana sai ga 
ma’aji kuma a guje rawani a hannu ya zube gaban Sarki, ya ce, “Allah  ya  ba  ka nasara,  ka ji  
qaina, na tuba, na bi  ka!” 
 
Mutane suka ce,  “Me   ya faru haka?” 
 
Ma’aji ya ce, “Ai yau baitulmali  6arayi sun  yi masa kat,  ban da ahu da na tarar bakin qofa ba 
abin da aka bari !’
Yana cikin ba da labari kuma sai ga Sarkin Zagi ya zubo a guje ya nufo fada, ba ko wando. 
Shantali zai yi masa magana sai ya ga ya durkusa gaban Sarki, ya ce, ,“Allah ya ba ka nasara,  
ai  barga yau ba sauran doki, duk an sace!” 
 
Sarki ya mike tsaye, sai kuma ga Jakadiya ta fito daga  cikin gida,  ta durqusa,  ta  ce  wa Sarki,  
“Mun  taru  za a  yi  wa amarya kunshi, mun duba, qasa da bisa cikin gidan nan duk ba mu gan 
ta ba.” 
 
Sai aka ga Sarki ya yi shiru. Can ya dubi dogarawa baki  na rawa,  ya ce, “Ku  yi maza ku zo 
mini da Nomau!” Dogarawa   suka zuba a guje suka nufi gidan Sarkin Noma. Jim kadan suka 
dawo, suka ce, “Ai an ce  rabonsa  da  gida  tun  jiya  da  dare.”  Sarki  ya baza mutane cikin 
kasa aka yi ta nema,  amma  ko duriyarsa  ba a ji ba.









