Showing 3001 words to 6000 words out of 9240 words
zuciya domin kare yacinye dazai iya dayanzu zaiyiwa Raliya saki
dubu sai dai bazai iya baiwa iyayensa kunya ba amman yau yakamata ya nunawa raliya shima
fa baya kaunarta ko sau daya cikin kallon isgilanci yace waikina zaton ina zaune dakene dan
kyawon fuskarki ko kyawon jikinki kiwata dabia maikyau dana gani agareki kiyi sani kamar
yanda kika tsaneni kika kuma tsani aure na kodon inasonki a a kodaya nima haka nakeji
harnawa ya linka naki tayi shewa da dariya tana kallonsa cikin tsakiyar idonsa da tsananin raini
da wulakanci Ahayye wannan shi akecewa shege yi da maizina kaiko rayiwarka kayace nikam
zan iya duk abinda naga dama nadawo natuba nakuma Auru sabanin kai da anriga anrubuto kai
shege ne babu kankara shut up stupid yadakamata wata irin gigitacciyar tsawa data sanyaya
firgita yaci gaba damagana cikin bacin rai koda nakasance shege wlh nafiki Albarka damutunci
a idanuwan kowa dabba shashasha kiyita gorin naki dafadar abinda kikaga dama domin halinki
irin na wawaye ne jahilai amman kisani idan har ga hannuna saki yake bazan taba sakinki ba
sokuwa kawai yajuya dazummar komawa cikin shagon saidai riko wuyan rigarsa datayi tabaya
ne yasanya yakasa cigaba datafiyar tarikeshi katamau tana fadin wlh ba indazaka saika sakeni
meye kawai banda naci banason aurenka dolene wlh yawon karuwanci yafimin wannan
kalgaggen auren naka zuciyarsa yadinga zillo datafasa afusace ya banbare hannuta cikin
zafinrai ya hanbareta tayi taga taga tafadi warwas akasa tayi karo dabango tafasa wata kara
domin hannunta yabugu da alama tayi targadema tafashe dakukan azaba ya kalleta dajan ido
yana fadin sokuwa kinyadda duka guda zai iya maganinki kisani bawannan rayuwa ce
agabanaba tadabbobi inada hankali da tunani idan har kinason rabuwa dani kije can kisami can
wadanda suka daura kisanar dasu yamaida kofar yarufe raliya kam dakyar
tatshi daga faduwar datayi tanakuka sakale da hannuta saidai bakinta bai mutuba taci gaba
datijara ta Allah ya isa shege tsinanne dan mahaukaciyar kan bola daba asan aslinsaba duk
abinda yazo bakinta fadi takeyi afatanta nata tunzirashi yafadi kalmar saki agareta kamar yanda
Lami tabata umurni tagayamasa kalaman dazasu tunzirashi amman baice uffanba saidai
hawaye
DAME AKE ADO part 8.
baice uffanba saidai hawayeí ½í¸í ½í¸ dayake zubdawa yana tasbihi ga Allah afili dazuci
harzuwa lokcin datagaji datijarar takama hanya tawuce dakinta tana kukan bakinciki kukan nata
kashi biyu ne nafarko narashin cikar burinta nasakinta dayakiyi nabiyu kuma nabugewar datayi
hartayi targade dayadaina jinmuryarta saiyamike yaci gaba da sallarsa yana kuka yana sanarda
Allah halin dayake ciki
..........DAME AKE ADO 2 .................Saiwajen karfe 3 dawani abu nadare yaji gwiwoinsa sunyi
sanyi idanuwansa sunyi nauyi babu abinda yake bukata illah yakwanta yahuta don haka yayi
addua yakwanta bisa tabarmarsa cikin kankani lokaci kuwa bacci yadauke shi saboda rashin
bacci daibaiyi da wuriba yasashi yamakara baitashi da asuba yayi sallah ba saida hasken rana
yashigo dakin ta wundo ya haskemasa ido sannan yafarka afirgice ya duba agogon dake jikin
wayarsa saiyaga yanuna karfe 7 nasafe yamike dasauri yana istigfari yanufi kofa yabude
kaitsaye cikin gidan yanufa don daura Alwala abinda yabashi mamaki yau baiwuce rashin jiyo
sautin kidan raliya ba wanda kullaum dashi take farkawa kamar shedaniya yashiga yakama
ruwa yadawo yatsuguna gundi rariya yana daura Alwala yana satar kallon dakin nata yana
adduar Allah yasanya harya gama Raliya batafitoba domin bayason ko kallon fuskarta cikin ikon
Allah kuwa har yakammala din bata fitoba yanufi shagonsa yayi tusur cike datsananin tsoro
domin ganin kofar gidan abude abinda yabashi tsoro kuwa tunda suke agidan raliya bata taba
bude kofar gidaba yawaiga cikin gida saiyaga babu takalman Raliya akofar dakinta dasauri
yadaga labule gamamakinsa saiyaga duk anwatsar da kaya acikin sif dakin yayi kaca kaca da
alamar andibi wasu kayan gabansa ya kuma faduwa badai gudowa raliya tayiba dagacan kan
gado yahango wata takarda ayashe ya isa dasauri yadauka yabude cikin wani cukurkudadden
Rubutu yaga sakon nata yafara karantawa BAKA BUKATAR SALLAMA DOMIN BATA DACE DA
SHEGE IRINKABA DUK WASU HANYOYI DA NASAN ZAN IYABI DON GANIN
KASAUWAKEMIN WANNAN KALGAGGEN AUREN NAKA NABI AMMAN KAKI SAUWAKEMIN
DON HAKA NABI HANYAR DATAFI DACEWA WATON NAGUDU NABARKA DA AURENKA
IDAN KAGA DAMA YANZU KA IYA AIKAMA IYAYENA DATAKARDAR SAKINA DOMIN SANDA
ZAKACI KARO DAWANNAN TAKARDA TUNI NAYIMAKA NISA KAIDA RAYUWARKA
SAIKUMA ACIGABA DAZAMAN GAURANTAKA DONNASAN HARKA KOMA GA ALLAH BABU
MACEN DAZATA YARDA TA AURI SHEGE BA .SAIWATA RANA RALIYA yaruntse idanuwansa
sanda yakai karshen takardar sako mafi muni dazafi da idanuwansa suka tabacin karo dashi
yajima tsaye yana tunanin meyadace yayi farincikin rabuwa da Raliya ko kuma bakin cikin
gudunshi datayi
1â£5⣠DAME AKE ADO2 Mlm jibrilu ne yafara tambayar yaya akayi yaya Allah dai yasanya lfy
domin naganku cikin damuwa malam sulaiman yamika masa takarda yana fadin karanra kagani
malam jibril yakalli takarda batare da ya amsaba yace yaya aikasan ban iya karatun boko sosai
ba danhaka bana gane kowane rubutu balle wannan danake ganinsa kamar zane tsutsotsi mlm
sulaiman ya gyara tsayuwa yanuna masa takardar yace kaga wannan takardace da raliya ta
rubuta kafin tatafi yawon karuwanci mlm jibrilu yadafe girji dadamuwa yaya wane irin yawon
karuwanci kuma A iya sanina Raliya tana gidan mijinta naji dadi dakace a iya saninka alama
bakasan gaibuba kenan to kabuda kunnuwanka dakyau kaji Raliya tabar gidan amadu yau da
asuba bayan duk tayi wani cinmutunci dazagi baikulataba tabar wasika takuma ce dazaman
auren Ahmadu gara taje tayi karuwanci yafiyemata kaga abunda nake nusar dakai tun abaya
ko? Mlm jibril yayishiru cike da tsananin damuwa yamarasa mezaice dan idanuwansa sunkada
suyi jajir gwanin bantausayi itakuwa Lami babu wata damuwa ko kyas atare da ita saiwani fici
fici take da idanu irin namarasa gaskiya tana kara tsare gida mlm jibril yace yanzu to yaza ayi
kenan kobin sahunta za ayine? Abita ina Raliya bayarinya bace tunda har taiya hada kayanta
tagudu takuma furta kalmar tafiya karuwanci abin yakai intaha saidai Abinda tace Ayau
zankaryatashi da tace sai dai Ahmadu yamutu babu Aure to tayi karya itace zata mutu babu
Aure ba Ahmadu yaron kirki ba taje duniya fadine da ita wanda baizobama jiransa take yakada
kai yashige dakinsa yana huci Umma kam saicika take tana batsewa tamkar tashako lami
domin tariga tagane dasanya hannun lami takuta tace idan anguji dan wata illah abanza domin
shi baida laifin kimai wanda kuma yake aikata irin laifin kumafa ? Karuwanci sana ace babba
mai lasisi saidai tanada darussanta muna zuba ido muga karshen butulci darashin tarbiya lami
takulu da kalaman umma tayamutsa fuska tana fadin oho kome za afada taba tarago tunda
aibamu mukace raliya tatafiba duk kuma inda take Allah ne zaikareta Allah bazaikare Raliyaba
lami yarinyar data tafi da hakkin mijinta da Aurenta kike zaton zatasamu kariyar Allah wlh ta
barranta daga rahamar Allah bakuma zanyafemata wannan tozarci da cinmutunci dajamini ba
Ahmadu dayake namiji yayi hakuri amman ita takasa taje duniyace mlm jibril yakarasa maganar
tamkar zairushe dakuka domin yana ganin iyakacin tozarci raliya tayimasa Lami takuma cika
afili tace Allah dai shike raba rahama ba mutumba mlm jibril yabita da kallo kamar yashakota
amman saiya dake yakyaleta ya gyada kanshi yana kallon kofar dakin yayansa yace malam
kafito mukarasa maganar nan kayi hakuri Ahmad dai yana durkushe yana kallonsu.
DAME AKE ADO part 9.
1⃣6⃣ DAME AKE ADO 2 Daga masallaci makarantar su Asma u yanufa yadaukota daga can bakin
kofa yaji wata sinio tana kwala mata kira Asma'u sulaiman tana ina tamike dasauri jikinta yana
rawa tayi zaton wani laifi tayi kokuma dealing dinne yamotsa na sinio hajara domin shegiyar
kazamace kayanta har tsami suke dahaka takwace kanta da maryam kemata kalbar da maryam
keyimata tanufi wurin sinio hajara tana fadin tanafadin senio hajara gani senio hajara takalleta
sama da kasa da alama yarinya uwarki ko ubanki sun mutu domin sir Abdul yace kije kitafi da
dukkanin kayanki domin gidanku zaki wuce ma'u tadafe kai cike da fargaba sai tafashe da kuka
tana fadin wayyo nashiga ukku Allah yasanya ba umma ko abba bane suka mutu ba wayyo
Allah ni ma'u nazama marainiya ihu takeyi iyakacin karfinta gabadaya hostel akayi shuru
anakallonta kawayenta tuni sun iso inda take dasauri suna tambayar abinda yafaru senio hajara
takama masifa ke sakarya nibance miki wani naki yarasuba cewa nayi kawai inajin kihado
kayanki muwuce kusai kutayata debo kayan nata ta kalli sauran kawayen nata dasauri ma'u
tanufi gurin kayanta taci gaba da hadawa tana kuka sosai kawayenta suna bata hakuri da
rarrashunta sanda suka isa wurin sir Abdul yakalleta damamaki yana fadin ma'u meyasanyaki
kuka? Cikin sheshshekar kuka tace senio hajarace tace wai babana ko ummana sunmutu
yabata rai matuka yace inji ubanwa? Hajara tanada matsala kawai nace kihado kayanki babanki
zaitafi dake shike nan zatace haka barta kawai karya takeyi hankalin ma'u yadan kwanta saidai
tana cike da tsananin mamakin abinda zaisanya babanta yazo daukarta bayan anfara jarabawa
bukin yayanta kuma ankammala tuni domin alissafinta yau sati biyu kenan da bikin yayanta
kokuma dagawa akayine dawanna tunanin tayi sallama dakawayenta sir Abdul yadaukar mata
wasu kayan su maryam da jamila suna bata sakon abinda zatasawomusu idan zatadawo tana
cewa to batasan wannan ce rana takarashe dazata kara komawa wannan makaranta ba
dasunan karatu ba yaune dazata rabu dakawayenta rabuwa tahar abada kuwa ta isa ta tadda
abbanta zaune a ofis din principal suna wasu magunguna dabata fahimci komaiba hankalinta
yadan kwanta saboda ganin abbanta bakuma cikin wata da muwaba ta durkusa tagaisheda
abbanta tagaida principal Abban nata yamike yana fadin to hajiya nagode Allah yataimaka
yakuma kara daukaka principal tamike tana fadin Ameen amman munyi missing daliba
maikwazo da hazaka Ubangiji yatsareta aduk inda take malam yace Amin dasauri principal
tadaga kan ma'u tana fadin Allah kaddara saduwarmu kidage bisa kyawawan halin danasanki
kinjiko? Itadai ma'u to kawai take cewa batasan me ake nufiba abbanta yadaukar mata wasu
daga cikin kayanta tadauki sauran suka nufi titi sanda suka isa gida anata kiraye kirayen sallah
magriba Umma tana kicin tana kokarin hura wuta da alama tayi daren tuwo ne tajiyo sallamarsu
ta mike da mamaki tanafadin malam kamar muryan ma'u nakeji mamaki yakoma karuwa ma'u
cedai biye da Abbanta yakalli Asma u yace bakama bace deeje itace yanzu na daukota daga
makarantarsu mamaki yakoma cikata tace malam amman banji lbr anyi hutuba naji kamar
jarabawa suke ma lfy yanufi kofar bandaki ya dauki wata buta da aka ajiye daruwa yana
magana lfy kalau kidai kiramin dukkan yaran gidannan awaya kice inason ganinsu idan nadawo
daga masallaci zakiji karin bayani yashige cikin bandaki don yakama ruwa Umma tamaida
kallonta ga ma'u kamar zata koma tambayarta sai kuma tafasa tace shiga dakayan cikin daki
kizo kidaura Alwala ma'u tayi abinda mahaifiyar tata ta umurceta bayan tacire uniform din dake
jikinta tasake kaya tafito ta daura Alwala itakuma Umma kokarin fara kiran wayoyin yaran gidan
ta isar da sakon da mahaifinsu tasanardasu sannan tadaura Alwala tashiga sallah
1⃣7⃣ DAME AKE ADO 2 Har suka kammala taruwa malam din baishigo ba domin saida ya tsaya
yasiyo goro da alawa yataho dasu suna tsakar gida bisa babbar tabarma anata tattaunawa
akan maganar gudun Raliya Rabiu yace wlh dani tahadu dashi datuni lbr yasha bamban
shegiya kodaddiyar banza kawai taje indai duniya ce wanda baizobama jiransa take shidai
Ahmad jinsu yake yana jin tamkar Anrabashi da wata babbar masifa ne arayuwarsa domin
kallon raliya bayason yakoma yi yasan Allah ne ya.amshi adduar sa yayi gaggawar rabashi da
ita saidai kamar yanda tace din yasan shida aure har abada domin bazai iya kara tunkarar wata
mace da sunan yana sonta ba balle haryajawa kansa wulakanci ba zaici gaba dazama ahaka
idan yaji zai takura sai yayi azumi Sallamar malam dince ta katse musu hirar su Ahmad yamike
da sauri ya amso kayan da malam din yashigo dasu yana fadin sannu abba yakarasa yazauna
akan tabarma da yaran ke kai daya bayan daya suka dinga gaisheshi ya .amsa sannan ya kalli
Umma yace ina ma'un take kuma? Umma takalli kofa tana cikin daki kasan indai yayanta suna
hira bata fitowa cikinsu tazauna wata kilama tayi bacci kotayi bacci atasota yakalli kofar dakin
ma'u Asma'u kina inane tafito dasauri tana goge idonta inaciki Abba kadawo sannu dazuwa
ya.amsa yauwa samu wuri zauna sannan yaturawa Umma buhun Alewa da goro dake gabansa
yana fadin bude kigani deeje Umma taja buhun tafara budawa tadaga kai takalle shi da mamaki
goro da alewane kowakilcin Aure zakayi kodaya goron daurin Asma'u da Ahmad ne an daura
tundazu a masallacin jumu'a na gidan maimartaba mamaki yakama kowa har akarasa mai iya
karfin halin.
DAME AKE ADO part 10.
Umma ce tafara karfin halin yin magana tace malam kaji abinda kace kuwa ? Malam ya gyara
zama kwarai da gaske saidai idan kece bakiji ba nasake maimaitamiki goron auren diyata
Asma'u da Ahmad ne wanda aka daura dazu a masallacin gidan sarki Ahmad yaji wani abu dim
akirjinsa tamkar ancaka masa mashi gabadaya kuzari da tunaninsa ya kwace yama rasa
meyada ce yayi Auwalu yayi kokarin yin magana cikin yaran Allah yasanya Alkhari yakuma
zaman lfy da zuri'a dayyaba gabadaya suka amsa da Ameen sani yace baba yabatun karatunta
kuma wannan yana hannun mijinta dukkan hukunci da yazartar shine daidai daman karatun
badole bane ba
1⃣8⃣ DAME AKE ADO 2 Umma ta girgiza kai tace hakane to yanzu yaya za ayi kenan malam
Gyalenta zata dauka tayafa suwuce gidan mijinta wannan goron kuma da alawar kirabashi
gidan makota domin suma sushaida Ahmad yakalli abbansa Afirgice daidai lokacin da Asmau
takalleshi itama saitake ganin abin kamar amafarki anya kuwa dagaskene haka daman ake
aure Umma takwantar da kai tace malam da anbari har ashirya ahankali sai akaita yadaga mata
hannu babu wani shiri dazaayi kidauko mata hijab dinta suwuce da mijinta duk wanda kika
aikawa da goron kice har tatare gidan mijinta fakat akayi shiru babu mai abincewa malam
yadubi Ahmad wanda yakasa motsi tamkar anzare masa dukkan lakkar jikinsa yace tashi
Ahmad kama matarka kuwuce gidanku Ahmad yayi firgigit yamike har alokacin yana tsammanin
zolayace amman yasan Abbansu bayamasa irin wannan wasar Umma tamike tashiga cikin daki
tadauko hijab tamikawa Asma'u tana fadin Allah yayimaki Albarka yabaku zuria dayyiba yasa
Anyi kenan sauran suka amsa da Amin ma'u ta amshi gyalenta tasanya takasa yin komai don
tsabar fargaba kamata kuwuce mana malam yakara basu umurni Ahmad saiyake ganin da
kunya yakama hannun ma'u musaman da malam ya ambaci matarsa ce wai ayau don haka
yawuce dasauri yanufi soro agobe yake kokarin yatattara kayansa yadawo rayuwa da ummansa
ashe bashida rabon sake zama tare da ita wato yabarta kenan har abada Umma takama
hannun ma'u domin takula duk tarude tarikice gabadaya abinda kedamun umma dayane yanda
bata taba koyarda ma'u komai na rayuwar gidan mijiba atsammaninta saitakara girma takara
wayo da hankali ashe bazatakai wannan lokacin ba ayimata aure ba bata tsammanin kofar
shinkafa ma'u ta iya dafawa wannan kadai shine abinda zaidameta har abada har saida takaita
bakin zaure sannan tatsaya tana fadin maza wuce kutafi Allah yayi muku Albarka
Malam dasauran yaran suka taso suka rakosu hargaban babur din sannan yakarkatamata
takama ta hau yatuka suka tafi suna daga musu hannu malam yadubi sauran yace to masu iyali
suwuce gidansu kukuma marasa iyali kushiga kutaya mahaifiyarku kullin kayan daurin aure
nizan wuce gidan malam habu nasanar dashi dahaka yawuce suma yaran kowa yakama
gabanshi sai samari dakanana ne suka shiga cikin gida suka fara din Salisu yace Umma
waidaman kunshirya hakanne da Abba bakusanar damuba Umma tagallamasa harara tace
bansaniba tambai sarkin tambaya sainaji matsa zanbaka Amsa yanda ta amsa maganar
afusace yadan bashi tsoro yace Allah yahuci yahuci zuciyarki Umma kiyi hkr hakan datayiwa
salisu yasa kowa yakunshe tashi acikinsa saiwani lokaci Ahanya suna tafe bisa babur kowa da
abinda yake sakawa cikin ransa itakam ma'u har lokacin bata yadda ba mafarki takeba domin
ko alittafin hikaya bata tabajin irin wannan lbr maiban mamaki ba shi kam Ahmad jinjina
kyautayin da karamcin bayin Allah nan ne aransa dama zai iya sakamusu da karamcin dasuke
yimasa waye zai iya aikata irin wannan abin dasuka aikata awannan zamani daya lalace
darayuwa irinta jari hujja tabbas sai antona harsuka isa kofar gidan kowa yana sakawa da
kwancewa yatsaida babur din yasauka yarike yana fadin sakko 1⃣9⃣ DAME AKE ADO 2 Yakalleta
da kulawa saiyaji duk kunya dafargaba sun kamashi wai ma'unsa kanwarsa yau itace tazama
matarshi Allah sarkin iko dabuwaya yadaure yacemata muje mana Tashige yanabinta abaya har
suka isa kofar yasanya makulli yabude suka shiga tatsaya atsakar gidan tana karemasa kallo
bata kawo komai arantaba sai daman anshirya komai itace kawai ba asanarwa ba tunda gashi
har gidan antanada ansanya komai yakalleta amman baibari sunhada idoba yace kije dakin can
kiyi sallah ki kwanta dasauri tace to tanufi dakin kamar wacce ke kan kaya daman yabita dakallo
har tashige sannan yanufi dan dakinsa shago yasamu wuri yazauna yadafe kumatu Raliya ta
tafi Asma'u tashigo shin ita wanne irin zama zasuyi kenan ko amafarki baitaba hango wannan
ranana balle idan yafarka yayimata wani nazari hakan yasanya yakasa tabuka tunanin komai
sai gyada kai kamar dan kadangariya tana shiga daki tazauna gefen gado tana karewa dakin
kallo daga gani natane sabuwar amarya amman yaya akayi ba asanarda ita komaiba duk wani
shirin da akeyi meyasanya sanda yaje baisanarda ita cewar za ahada auren su ba sai yabata
lbr Aurensa da Raliya amman da alama shima baida masaniya akan komai tuno raliya datayi
yasanya zuciyarta yin kunci waton daman ita kishiyar raliya ce a iyakacin tunaninta bata taba
tunano zasa hada miji da Raliya ba meyasanya su Abbanta sukayimata haka tadafe kirjinta
yana bugu kamar zaibullo yayo waje idanuwanta suka ciko da kakwalla jikinta yadauki rawa
saitakejin kamar ana likamata kiyayyar raliya aranta kishi maigirma yarufeta saita fashe dakuka
meya sanya rayuwarta tazomata da wannan akasin itama matar yayanta Ahmad ce tadade tana
kukanta kamin tayunkura tafito tsakar gida tadauro alwala takoma daki domin yin sallah ta idar
da sallah tana kallon dakin tana lazimi tana sakawa da kwancewa harzuwa sanda tagaji tamike
da hijab din jikinta dakomai tahaye gado takwanta saidai me haushin karnuka datake jiyowa
akan titi dakukan gyare sun sunhadu sunbirkitama ta tunani sun assasamata tsananin tsoro
bata taba