Showing 1 words to 3000 words out of 35767 words

Chapter 1 - BEELAL BUK BOOK 1 BOOK COMPLETE BY MAMAN AFRAH.doc

??ࡱ?>?? ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?WordDocument????1?0Table????????
Data
???????????????????? P?,?KSKS?1??????????rr+8??;??? ? ? ? ? ? ? ? ? $O ? *r? ? ? + ?c+ ? c? + c? ? c BEELAL


*BILAL*



NA



MAMAN AFRAH


FCW

Page1? ?'2?


*Da sunan Allah mai rahma mai jin ?ai.Godiya da yabo sun tabbata ba Allah maWaukaki da ya bani ikon fara wannan littafi Allah bani ikon kammalawa cikin aminci amin.*


Rayuwa tana da matakai kala-kala, sannan tana cike da ?alubale wanda rayuwar ke sanya lamura su juya, wani lokacin idan ta maka wani sauyin sai ka ji tamkar an lasa maka zuma a baki.SaSanin wani sauyin nata da ke zama mafi munin WanWano tamkar maWaci.Kowane Wan adam yana da ?addara a rayuwarsa, wani rashin iyaye, wanda hakan yake sanya shi ya ji babu wani abu da ya fi maraici rashin galihu, wani kuma ?addararsa talauci musamman idan bashi da wadatar zuci .Sai ya Wauki hakan wani abu mai girma, wani ma har yake nema ya yi saSo, dan yana gani kamar shi kaWai aka toshewa hanyar samu.Wani kuma rashin abokin rayuwa na gari, wala mata ko miji, mai nagarta hakan na zama tamkar nakasu a duk rayuwar Waya daga cikinsu, idan namiji ya yi rashin mce ta gari to tamkar ya rasa wani Sangare na jin daWi ne a rayuwarsa.Manzo S.A.W ya ce duniya wani waje ne na jin daWi amma mafi jin daWin ta shi ne mace ta gari.A Sangaren mace ma rashin dace da abokin zama na gari idan bata dace da samun miji na gari ba mai tsoron Allah da kiyaye dokokin ubangijinsa, ta kan rayu ne a gidan aurenta tamkar baiwa, tana rayuwa ne ga ta dai a raye amma tana jinta tamkar matacciya! Domin za ta rayu ne a cikin gidanta, tamkar ma?abarta take jin gidan nata, domin kuwa bashi da bambamci da kabari.

Shi ya sa ake so a koyaushe mu nemi zaSin Allah, ba wai son zuciyar mu ba.
Wannan tana daga cikin babbar ?addarar da mace take samun kanta a ciki, har hakan ke sanya ta ji ina ma bata yi auren ba, saboda babu wani farinciki da za ta yi ikirarin ta samu kanta a ciki daga mijin nata.Wannan ?addarar ita ce ta afkawa Fatima, domin kuwa gabaWaya abubuwan nan guda uku ta samu kanta a ciki, maraici domin kuwa ta rasa gabaWaya iyayen ta, da kuma kakaninta da suka taso a hannun su bayan rasuwar mahaifan nasu.Abu na biyu shi ne talauci, sai kuma uwa uba ginshi?in rayuwar mace bayan barin gaban iyayenta idan ta yi aure, wato miji! Domin kuwa auren Idrisu ya sanya tana jin a koyaushe zuciyarta na cikin ?unci da takaici,haWe da, da na sani marar misaltuwa.Tana jin a ranta ina ma ba ta yi aure ba ina ma za a dawo da baya gaba da kuwa ba ta auri Idrisu a matsayin miji ba, da bata zaSi Idrisu abokin rayuwarta ba, da babu yadda za a yi ta zaSi Idrisu ya zame mata uban ?a?anta ba, domin kuwa Idrisu bai zame mata bango abin jingina ba.Dan kuwa ya yi watsi tare da yin fatali da duka Wawainiya da kulawarta da suka rataya a wuyansa.Hannu ta sanya ta share hawayen da ke ta safa da marwa tare da rige-rigen sakkowa daga kumburarrun idanunta, a hankali ta juya ta kai kallonta wurin da take ajiye kayan abincinsu, wasu hawayen ne masu zafi suka sake zubo mata domin kuwa ba ta jin akwai abincin da za su ci yau Win nan, cikin sanyin jiki ta tashi daga kwancen da take tana jin jiri na Wibanta ga kuma wani nauyi da zuciyarta ta mata tamkar an Wora mata dutse, saboda tarin ba?inciki da takaicin da ke ?unshe a cikinta ga yunwa da kuma rashin ?arfin jiki suka sanyata kwanciyar dole.?aramin buhun da take zuba shinkafa ta duba duka bata fi gwangwani Waya ba, bokitin da take zuba wake ta duba duk da ta san ya ?are amma sai take ganin idan ta buWe kamar za ta samu saura ko kaWanne amma shi ma babu ko ?waya a ciki, haka ta dinga dudduba sauran ma'ajjin kayan abincin amma komai ya ?are hatta taliya ma kwalin ne kawai ta ajiye amma babu komai a cikinsa.Cikin sanyin muryarta wacce ta ci kuka ta ?oshi muryar har sha?ewa take ta ce


"Yaya shin me ya hanaki zuwa kwanaki da yawa, kinsan dai ke kaWai gareni kuma ke kaWai ke taimakona, wanda nauyinmu ke kansa da alama ma ya manta da wanzuwarmu a doron ?asa bare har ya tuna da ha??inmu da ke kansa ya waiwayemu" Ta kai ?arshen maganar tana sakin wani kuka dan ita ba ta kan ta take ba, ta fi tausayin Beelal idan har ita za ta iya jurewa to shi ba lallai ya jure ba.Bare yunwa babba ma da yaya bare kuma yaro.

Shinkafar nan ta Wakko ta fito daga Wakin nat,a tana so ta dafa wa Beelal kafin ya dawo daga makarantar boko in ya dawo ko da gishiri da mai ne sai ya ci, dan ta ga lokacin taso su har ya yi.Cikin sauri ta shiga haWa wuta da sauran itacen da suka rage, haka ta hura wutar ta Wora ruwan duk da ba ta jin ?arfin jikinta.


"Mai ?afa a lan?washe"

"Beelal"

" Baki a karkace"


"Beelal"

" Hannu a lan?washe"

"Beelal"

"Ba ya iya magana"

"Beelal"

Fatima ta jiyo muryar yara suna faWa da ?arfi suna tafi idan Waya ya ce mai ?afa a lan?washe, sai sauran yaran su ce Beelal, duk abin da ya faWa sai su masa amshi.Wani abu ne ya tokare mata a ma?oshi tana ji kamar ta kurma ihu saboda takaici, shin sai yaushe ne yaran gari za su bar Wanta ya sarara? Sai yaushe ne za su barshi ya yi karatu hankali kwance ? Shin mai ya sa iyayensu ba sa kwaSarsu a kan abin da suke? Mai ya sa Malaman makarantar ko ta kai musu ?ara amma yaran ba sa dainawa, shin ba sa tsawatar musu ne ko kuma yaran ne suke da taurin kai? Duk cikin ranta take jefowa kan ta waWannan tambayoyi.

Da sauri ta shiga Waki ta Wakko hijabinta ta sanya ko gama dai daita wuyan hijabin bata yi ba, dan wuyan a karkace yake, hanyar ?ofar gidan ta nufa cikjin zafin nama tana jin tamkar idan ta fita ta fara dukan yaran sai an ?waci gabaWaya yaran a hannunta.Tana fitowa ta ga dandazon yara ne ?an makarantar su Beelal Win sanye da kayan makaranta suka rako shi kamar yadda suke yi a kullum.Idan ta aikeshi ko kuma in zai je gidan su Hameeda, haka zalika ko makaranta ya je bai tsira ba, hakan ya sanya ta gwammace duk inda za ta aike shi ta jr da kan ta.Tana fitowa suka fara watse wa kowa na kama gabansa, amma kuma bakinsu bai bar faWar wa?ar da suke ba.Beelal da ke dur?ushe yana kuka sai Hameeda da ke tsaye a kansa tana kukan ita ma, cikin sanyin jiki Fatima ta nufesu tana ?arasawa Hameeda ta rungumeta tare da sakin kuka cikin kukan take cewa.


"Mama wallahi kullum ba ma tsokanar kowa, amma su sai sun biyo mu hanya idan aka tashi daga makaranta suna tsokanar Ya Beelal babu abin da ya musu" Cewar Hameeda tana ?ara rushewa da wani kukan.


Wani sabon kuka ne ya taho mata tare da tsananin tausayin yaranamma sai ta danne kukan dan tana so ta lallashe su, musamman take jin ?aunar Hameeda har cikin ranta saboda ?aunar Beelal da yarinyar ke yi ba tare da ?yamatarsa ba kamar yadda sauran yara ke yi kai har ma da manya, domin wasu ba sa duba da cewa kowane Wan adam Allah ke halittarsa, kuma uwa idan ta haifi Wa duk muninsa tana son kayanta sannan idan duk duniya za su taru a kan su canja wa mutum halittar da Allah ya masa babu wani abu da za su iya canjawa.Kawai mutane na shagala ne da abubuwan rayuwa har su kan manta cewa Wan adam daga taSo aka halicce shi, sannan mutum ba komai bane fa ce wanda aka samar daga Wigon maniyyi, sai dai ?an adam da ba a iya musu har suna iya tantance tare da bambamce kyakkyawa da kuma mummuna, ba?i da kuma fari wani lokacin ma har ka ji ana cewa har da ruwan tarwaWa!

Mutane na mantawa cewar Allah shi ke samar da halittarsa, shi ne mahaliccin mutane da aljannu, shi ke yin su yadda ya so kuma babu wani Wan adam da zai iya ko da canza halittar farcen mutum ne! Amma ake cewa wance mummuna wane hanci shi gajere wance dogon goshi da dai sauran kushe halittu.Bare kuma a ce mutum nakasashshe ne, sai mutane su Wora masa karan tsana ake masa wani kallo na da ban bashi da ikon shiga cikin jama'a kamar kowa bashi da halin aiwatar d rayuwarsa kamar kowa shin shi ne ya halicci kan sa? Ko shi ne ya ce a halicceshi haka? Ko kuma ita uwar Wan ce ta halicci Wan nata a haka, bayan ita ma bata taSa sanin mai za ta haifa b sai ranar da Allah ya ?adarta fitowar Wan duniya!!!

Allah ne ya halicci masu tafiya a kan ?afa biyu (Mutane) Da masu tafiya a kan ?afafu huWu (Dabbobi) Da kuma masu tafiya a kan cikin su (Miciji d.s) Allah shi ke halittar abin da ya so.


Hannun Hameeda Fatima ta kama ta ri?e gam, ta ja ta zuwa inda Beelal Win ke dur?ushe ya kifa kan sa a gwiwa yana rera kuka kallon Hameeda ta yi yarinyar duka -duka shekararta huWu, shi kuma Beelal Win shekararsa shida ita tana primary 1 shi kuma a primary2 saboda babu nursery a makarantar ?auyen nasu.Cikin sanyin jiki ta dur?usa a gaban Beelal Win tana jin wani tausayinsa na ?ara rufe ta, ga nakasa ga rashin galihu na uba! Hannu ta mi?a ta kamo hannunsa mai lafiya ta ce.


"Haba Beelal Win Mama yaron kirki, kai da na ce maka duk wanda ya tsokane ka, kar ka yi kuka ka ce masa haka Allah ya halicceka ko zai gyara maka amma shi ne yau ka zauna ka na ta kuka"

"Ma...ma, naaaa...ji...maganarki...amma fa...yau ma Malam ma ...korata ya yi...da zan karanto masa karatu, wai...ba ya son, in,innaa"


Ya faWa har lokacin kan nasa na kan gwiwarsa kuma bai fasa kukan ba duk da yana in,innaa amma hakan bai hana Fatima gane mai yake faWa ba, kuma har cikin rai da zuciyarta ta ji haushin abin da Malamin ya masa duk da ba yau ne aka fara ba amma dai abin ya sosa ranta sosai dama kowace uwa ba ta son damuwar Wan ta bare kuma Wa mai nakasa dan mace ko ?a?anta goma idan dai guda Waya yana da nakasa ko yaya ne ko da kuwa wata jinya ce Allah ya jarabci Wan da ita kamar sikila ko aljannu ko dai wata tawaya a jikinsa to uwar Wan nan ta kan ji ta fi ?aunarsa.Duk cikin ?a?anta ta kuma fi tausayinsa sama da sauran Wiyan nata...




MMN AFRAH=?
?>?p?=??



*BILAL*



NA



MAMAN AFRAH



FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

Da sunan Allah mai rahma mai jin ?ai.Godiya da yabo sun tabbata ba Allah maWaukaki da ya bani ikon fara wannan littafi Allah bani ikon kammalawa cikin aminci amin.


Page 3?? ?'?4??


.
Cikin raunin zuciya da sagewar ?afa jin furucin Beelal, na sanya hannu na tashe shi tsaye, tsayawa ya yi amma har lokacin hawaye na zuba a idanunsa da alama ma idanun a kumbure suke saboda kukan da ya yi.Rungume Beelal Win na yi a gefen hannun damana, hagun Win sai na rungume Hameeda ?aran sheshshekar kukan da suke na taSa min zuciya ji nake kamar in maida damuwar tasu cikin raina duk da na san yadda nake ji a raina ya linka yadda suke ji.Sai dai babu wani abu da zan iya yi a kai wanda ya wuce in lallashe su in basu ha?uri tare da addu'ar Allah ya kawo mana ?arshen wannan hali da muke ciki da kuma ?alubalen rayuwa da muke fuskanta tun da dukkan tsanani yana tare sa sau?i babu wani dawwamammen abu daWi ko wuya, duk masu wucewa ne.Haka na ja su muka shiga cikin gidan dan na san Hameeda ma babu inda za ta tafi har sai ta ga Beelal ya daina kukan dan duk lokacin da yake cikin ?unci haka take kasancewa tare da mu har sai ta ga walwalarsa, al'amuran yarinyar tamkar wata babba haka take yin abubuwa ga sanin ya kamata.



Muna shiga cikin gidan na zaunar da su a kan tabarma na shiga lallashin su har sai da na ga sun saki ransu sannan na tafi domin in iza wutar da na Wora abincin.


"Mama kin ga fa har takalminsa ya tsinke da ?an makarantar suka biyomu" Muryar Hameeda ta katse min hura wutar da nake, ko ma in ce ta dawo da ni daga tunanin da na lula dan a zahiri ina hura wutar ne amma zuciyata tana can wani waje da ban, dan kuwa na tafi tunanin mahaWin abincin da zan basu, domin kuwa ko Wigon mai bani da shi a gidan bare yaji gishiri kawai nake da shi.Tsaye na mi?e daga sunkuyen da na yi ina fifita wutar da mafici na kama ?ugu tare sa sauke wata ajiyar zuciya na ce.


"Babu komai Hameeda zan san yadda za a yi"

"Za ki siya masa sabo" Ta ?ara jefo min tambaya.

"Idan Allah ya hore min zan siya masa idan kuma ban samu kuWi ba zan baiwa mai gyaran takalmi ya gyara masa" Na ce ina maida kallona kan Beelal da ya yi tagumi da hannun hagun Winsa dan shi ne mai lafiyar, yana bin mu da ido.

"Ma...ma ki ba da ...aaaa ...gyara min na san baaaa...ki...da ku...kuWi" Ya ?arashe maganar cikin sanyin murya.

Shiru na yi ina jin tausayin Beelal na tsarga min saboda yaron akwai hankali idan ya yi wata maganar ma ba za ka taSa tunanin yaro ne mai ?arancin shekaru ya yi ba.


"Kawai ka bari idan ta samu kuWin ta...

"Assalamu alaikum" Sallamar Umma Hafisa wato Ummar Hameeda ta katse maganar da Hameedar ke yi.


'Wa alaikumus salam" Na amsa ina ?ir?iro murmushin ya?e.

"To sarkin surutu kina nan kina ta zuba ko?' Ta faWa lokacin da ta ?araso tsakar gidan.


"Umma ba fa zuba nake ba magana nake yi" Hameeda ta faWa tana washe ha?ora.

"To na ji dai, Beelal kuka ka yi ne?" Ta tambaya tana kafe Beelal Win da ido fuskarta na nuna alamun damuwa.

"Kuka muka yi ?an makaranta ne suka biyo mu kin san kullum fa sai sun biyomu suna tsokanarsa"Cewar Hameeda tana kallon Ummarta.

"To zabiya ke na tambaya?" Ummar ta faWa tana harararta.Ni dai murmushi na yi na Wakko kujerar ?ar tsugunno na ajiye mata na ce

"Ummar Hameeda ga kujera, kuma dai kin san idan kika tambayi Beelal abu tamkar kin tambayi Hameeda ne dan kuwa kin san ba a raba hanta da jini"


"Ai na sani Hameeda da Beelal sai Allah,amma kin santa faWi ba tambayeki ba ce.Yanzu ma na ji shiru-shiru shi ne na biyo sawu dan na san tana nan, matu?ar dai ba gani ta yi ya daina kuka ba na san ba yarda za ta yi ta taho gida ba"Ta ce tana zaunawa a kan kujerar da na ajiye mata.

"Wallahi kam ai tsakaninsu sai Allah"Na faWa ina kallon yaran.

"Fatima dan Allah ki ci gaba da ha?uri kamar yadda na sanki komai mai wucewa ne wataran sai labari, labarin ma wata rana ba a ji ba"

"Babu komai na Wauki hakan a matsayin ?addarata"

"Yawwa Fatima haka ake son bawa ya kasance mai yarda da ?addara mai kyau ko saSanin hakan, idan da rai da lafiya wataran sai hakan ya zama tarihi"

"To Ummar Hameeda na gode"

Hannun ta da ke cikin hijabi ta fiddo, ta mi?o min ba?ar leda.

"Ga wannan kaWan ne ba yawa"

Hannu biyu na sanya na karSa idanuna na cikowa da ?walla.


"Na...

Hannun da ta Waga min ne ya dakatar da ni daga maganar da nake shirin yi, dan babu abin da Ummar Hameeda ta tsana irin ta baka abu ka mata godiya.

"Tashi ke mu tafi har an fito daga masallaci"


"Ki barta mana idan ta ci abincin sai ta taho"Na faWa ina kallon Ummar Hameeda da har ta mi?e tsaye.

"Ni dai a gida zan ci, Ya Beelal sai na biyo maka islamiya" Hameeda ta faWa tana mi?ewa tsaye ta sanya takalmanta.


"Tooo...Ha...ha ...meeda" Ya ce har yana runtse ido saboda in, innar da ta sar?eshi.


" Maman Beelal mun tafi sai zuwa jimawa"


"To Ummar Hameeda mu jima da yawa"

Suna fita na yi saurin buWe ledar man gyaWa ne rabin kwalba, da jan yaji dakakke a wata ?ar roba, sai dakakken ?arago a farar leda a ?ulle da kuma garin kwaki.Wata ajiyar zuciya na sauke mai ?arfi na ajiye ledar tare da Waga hannaye na sama na godewa Allah d wannan kyauta da ya mini tabbas ubangiji mai ji ne kuma masanin komai yana tare da bawansa a koyaushe.

"Ma...ma me...me..nene?" Beelal ya faWa yana washe baki.

Wani daWi ne na ji ya baibayeni ganin murmushi a fuskar yarona tabbas babu abin da ya fi ka ga Wanka cikin farinciki.


"Gari ne da yaji da kuma mai har da ?arago" Na faWa cikin farinciki.


"U...U...Umma tana son ...Mu, amma... Baa...Baa ba ya zuwa wurin mu bare ya kawo mana abinci." Cewar Beelal yana kallona.

Jikina ne ya yi sanyi da jin furucinsa, yaro ma kenan ya san mai kulawa da shi, idona ne ya kawo ?walla, amma sai na yi saurin mayarwa dan ba na son na yi wani abu da yaron zai fahimci wani abu saboda yana da kyau uwa take Soye damuwarta ga ?a?anta, tare da kawar da duk wani abu marar kyau daga zuciyar yaran dan gudun kar su sanya hakan a ransu musamman dangane da mahaifinsu gudan kar su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login